[29/04 12:05 pm] 🔳◾◼▪💙: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ Email:realhausafulaniwritersforum@gmail.com Facebook:www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITTERSFORUM.com https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R Labari me tab'a zuciyata.... Karatu cikin harshen hausa... Tafiya cikin nutsuwa da tunani me kyau... Yanayi na d'aukar hankali..... Soyayyar gaskiya me tafiya da qauna Zallah.... Bani da lokacin b'ata lokaci akanku dan kunsan dawa kuke... Da marubuciyar data nishad'antar daku cikin Novel nata na Y'AR QAUYE KO Y'AR BIRNI.... MASEEFAR SOO... Birnin masoya... SADEEQ.. Amakirci na... SAMAREEN BANAH.... HAYATUDDEN.. *Ban yarda kina budurwa ko kina bazawara. Ko kana saurayi. Koka tab'ayin Aure Ku karanta min littafi ba. Nayi shine kawai DON Ma'Aurata🙉 ba dan Kuba...* Jaruman cikin labarina.... ADAMSY NUFAISAT TAUDAT MUSLEEMAT RAHMA NALELE Auntyn Luv☆ Junior Ramadan nah👌🏻 ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 01☆ ADAMSY Likitan zuciya... Aka rubuta ajikin allon bangwan dazai sataka da cikin ofishin nasa.. Da rikicewa wata Yarinya me sanye da kayan asibiti farare (Norse) take kwankwasa k'ofar ofishin nasa.. Kyakkyawan mutum ne.. Wanda ya had'u tako ta'ina. Shekarunsa bazasu wucce 33 ba. Saidai idan kagansa zakayi tunanin d'an shekara ishirin da shidda ne. Yana sanye da rigarsu ta likitoci kan kujerar da take mallakinsa. Yana da dogwan hanci me d'auke siririyar fuska wacce take da fad'i kaɗan.. Ma'ana dai anan shine fuskarsa baza'a kirata da ririya ba kuma baza'a kirata dame fad'i ba. Tana dai tsaka tsaki.. Sannan yana d'aya daga cikin mutanan nan waƴanda sudai baza'a kirasu da dogayeba. kuma baza'a kirasu da gajeru ba.. Saidai yana da ɗan ƙiba kaɗan.. Wacce bazamu kirata dame muni ba. Sannan yana da faɗin ƙirji me ɗaukar hankali.. Yana da San ƙamshi yana da San tsafta. Yana da San kwalliya. Yana da San gaye. Yana da San abu me kyau. Yana San gaskiya. Yana San mutum me bin ra'ayinsa. Yana San wulɗa da mutanan kirki. Yana San matarsa San gaskiya. Yana san iyayansa. Yana San yara so me tsanani. Yana San temakwan su. Yana San temako arayuwarsa. Yana San mutumin da yake San shiga al'amuransa. Yana San sana'arsa ta ceton rai da kasuwancinsa da yakeyi Ga Y'a mace kuma. Yana San mace me SHAGWAƁA. Me kirki. Me nutsuwa. Me San KWALLIYA. Me tsafta. Me kissa. Me iyayi. Me iya kalaman qauna. Me nutsuwa yayin da yake jinta. ME IYA GIRKI... Baya San rainin hankali da wulaƙanci haɗi da munafunci.. Mutum ne me aji!!!. Aji!!!! Fah😳. Irin sosai d'innan.👌🏻 Baya shiga harkar daba tashi ba. Sam ADAMSY bashi da yawan abokanaye.. Saidai ko'ina ya shiga afad'in garin KADUNA sanshi ake. Ƙaunarsa ake. Jinsa ake.... Saboda halinsa nagari ne. Me kyauta ne. Me tsausayine. Me kwantar dakai ne agun duk wani mutum Wanda yasan ya girme masa ya haifesa.. Toh ADAMSY yana da halin bashi girmansa.. Wannan kad'an kenan daga cikin halaye na ADAMSY.. ***** "Yas shigo... Yace da wannan yarinyar da take kwankwasama mai ƙokar Ahankali tashiga tana cewa.. "Sannu doctor. Dama mahaifiyatace aka kawota yanxu. Shine doctor RAMADAN yace pls kazo kad'an samai hannu.. Yau baya jin dad'ine. Sannan yace dan Allah kayi hakuri yasan lokacin tafiyanka yayi. Danya kiraka baka d'auka ba. ɗan rintse ido yayi kad'an. Sai hakan ya qara masa kyau.. _Sarki ya tabbata ga Allah. Mamallakin kowa me komai. Allah kabani miji irin ADAMSY. Me kyau. ne me tausayi. me dukiya._ duk da mahaifiyarta ce kwance rai ahannun me dukka. Amman bai hana zuciyarta fad'in wannan kalamai cikin ranta ba!!😌 Ahankali cikin sanyayyiyar muryarsa me dad'in sauraro yace.. "Owkie. Jeki ganinan zuwa.. Da Murmushi akan fuskarta tayimai godiya da ficcewa daga ofishin.. Sauri-sauri gudu-gudu ya saka laptop ɗinsa a jaka tare da ɗaukar wayarsa ya fitto da kulle office ɗin nasa.. Cike da nutsuwa yake tafiya kamar yanda ya saba.. Cikin nutsuwa masu tsaran lafiyansa sukaxo garesa da karb'ar laptop ɗin tasa. Da wayansa. Suka saka cikin motar da yake hawa. Sannan yace musu baya fitto tafiya bane. Zai d'an duba wata ne a part na doctor RAMADAN Yanxu zai fitto. Ai da ladabi suka mai fatan alkairi yanufi part ɗin doctor RAMADAN "Bayan doctor RAMADAN ya gama yimasa bayani akan tana da ciwan sugane.. Sai kuma yanxu ya lura Kamar tana da matsala da zuciyarta. Hakan yasa ya nemi saka hannunsa... Shuru doctor ADAMSY yayi yana duba matar. Can yace... "Eh. Zuciyarta tafara karɓan wasu sakwanni. Wanda ada bata karɓarsu. Wannan dalilin ne yasa take qoqarin San taga taba me ita wahala. Kafin tabuga. Zan mata wani aiki da ɗorata akan wasu magunguna. Idan Allah yaso. Zata samu lafiya. Saidai fah dole ta kaucema waƴancen sakwannin da suke San tarwatsa mata zuciyar tata.. Jan numfashi doctor RAMADAN yayi da cewa.. "Masha Allah. Naga zuciyar tafi buƙatan kulawa ayanxu. Dan haka kagama naka aikin nayi nawa.. "Toh akai min Ita part d'ina... Ya faɗi hakan yana me ficcewa daga gun. Da "toh doctor RAMADAN ya bishi dashi.. Awa d'aya ya d'auka yana mata aikin. Kafin ya gama ya baro asibitin.. Motoci bakwai ne suke tafiya akan titin.. Uku a baya uku a gaba.. D'aya ƙaramar a tsakiya.. Kaf dukkansu motacin anrubuta.. ADAMSY.. Kina dai gani kinsan dukiya na aiki.. Direct supermarket d'insa suka nufah Wanda yake da girman gaske. Babuce kawai babu a supermarket ɗin.. Ma'aikata wajen suna ganin tawowarsa kowa ya gyara kansa.. as oga yaxo..👌🏻 ɗan zagaye zagayensa kawai yayi da duba wasu mahimman abubuwa sannan ya kalli wani qaninsa Salim Wanda ya ɗorasa akan al'amuran. Yace dashi... "Ka qara kula sosai da aikinka.. Dan naga kamar kana wasa dashi.. "Insha Allah zan qara kula.. Amin afuwa.. Maida gilashinsa ADAMSY yayi da sakin wani Murmushi ya juya yana bashi amsa da cewa.. "Anyi maka. Dafatan zakayi qoqarin kiyayewa. "Insha Allah.. Salim ya faɗi cikin sauri da girmamawa.. [29/04 12:05 pm] 🔳◾ [29/04 12:05 pm] 🔳◾◼▪💙: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. *☾•RAHMA* MUH'MD RUFA'I NALELE..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ Email:realhausafulaniwritersforum@gmail.com Facebook:www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITTERSFORUM.com https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 02☆ Gidan marayu matuqan nasa sukayi dashi Kamar yanda suka saba.. ADAMSY duk wata yana kaima gidan marayuwa tallafi.. Sannan kullum Idan ya tashi daga aiki bayan yaje duba wajen kasuwancinsa toh Lalle saiyaxo ya duba yara agidan marayun nan yaga Ko suna lafiya... Bama wannan kad'ai ba. Kaf yaran dayake temako bawanda bai san shi ba. Suna matuƙar sanshi da ƙaunarsa.. Yana zuwa wajen dama suna tsaye wajen jiransa. dan haka yana fittowa suka sungumesa suna masu suna murna da farin cikinsu na ganinsa.. Yafi kula yara qanana. Irin waƴanda suke da shekaru uku biyar takwas goma Sha d'aya Sha biyu. Qasa da haka.. Toh yauma haka yana fittowa ya gansu zaune kawai shi suke jira.. Aƙalla zasukai hamsin. Haka sukazo da gudu suka rungumesa suna murna Duk sun cukwikwaiya masa kaya.. Saiya ɗaga wannan ya sauke.. Ya ɗaga wancan ya sauke.. Sanda ya gama raba musu alewa as sadaka. Sannan yaba masu kula dasu wasu kayayyaki Wanda yake da tabbacin akullum yaran suna buƙatansu.. Sannan yayi musu sallama ya fito masu tsaransa suka bud'e mai ƙofar mota ya shiga suka rufe kana sukaja motocin.. Basu tsaya yanxu ako'ina ba. Sai'a gidansa.. Gidane Wanda yatara abin duniya. Gidane Wanda kana kallansa zaka kirasa da aljannar duniya.. Ya haɗu iya kar haɗuwa. A far fajiyan gidan motucine na alfarma guda uku... Bayan Wanda aka dawo dashi dasu. Da alama wannan na Matar gidan ne.. Wajen parking na motocin kansa abin kallo ne Dan yana da girman gaske.. _Haka Allah yake ikwansa.. Wasu yabasu wasu kuma ya hanasu. Kaidai karoqesa ya baka na halak ba haram ba; ya baka Wanda zai maka amfani. Wanda zaka bisa akan tsarin addinin musulinci!!! Ahankali suka bud'emai motar ya fito da karb'ar y'ar jakarsa. Dan dokace baya barin masu tsaran nasa su shigamai cikin gida inda iyalinsa take. Kawai Idan yana gida toh suma suyi nasu shashin.. "Assalamu-alaikum MESONA Ya shigo falan da Murmushi akan fuskarsa yana me leqen ta'inda zaiga masoyiyar tasa... Aiko canya ganota da qawarta suna masu hira cikin farin ciki da qaunar juna.... Lokacin da NUFAISAT tayi ido hud'u da Mijin nata tashi dayi da Sauri tazo ta rungumesa tana me nuna murna da farin cikin dawowarsa... "Amma sweety banji shigowarku ba... "Tayaya zakiji. Bayan kina tare da wannan wacce tabi ta kanannad'eki da zaqin baki..... Ya bata amsa da fad'in hakan yana me nuna mata qawarta TAUDHAT.. Da wani yanayi.. da wata shagwaɓa.. Da wani kallo.. tace... "Zaƙin bakinta agareni. bazai tab'a shagaltar da ruhina daga lura da jinka ko kuma ganinka ba... Kawai kaidai kayarda banjika bane da gasken gaske. 🙂 Murmushi yayi da zareta daga jikin nasa ya nufi part nasa yana cewa. "Na yarda sweetyna. Murmushi tayi da binsa da kallo. Kana takoma ta zauna sukaci gaba da hira da qawarta tata TAUDHAT BATARE DATA BISHI DAN TATEMAKA MISHI WAJEN CIRE KAYA BA.🙂 Can yafitoh falan da wata sabowar shiga. kallo d'aya zakamai kasan yayi wanka ne.. ADAMSY kenan mekatu.... Zama yayi a dining teble Ga mamakina sai naga TAUDHAT tataso da Murmushi zuwa garesa tana cewa.... "Sannu da dawowa *MIJIN K'AWA*.. Fatan kadawo lafiya.. Allah yasa ba wani Wanda ya b'ata maka rai awannan ranah.. Wajen zaman ka wajen kasuwancinka. Konace a asibitinka.. Da Murmushi yace da ita... "Ba Wanda ya b'atamin rai. Kuma lafiya lau nadawo ga matata.. Fatan dai girkinki agareni yau yafi na jiya d'and'ano..😌 Wani shuqumin Murmushi ta kai masa🤔 da fara zuba masa abubuwan data b'ata lokaci wajen girka masa tana cewa... "Ai akullum qara Neman sani nakeyi. Indai akanka ne. Nayi alƙawarin bazan tab'a bari kakawoma K'AWATA Kishiya akan girki ba...... Lumshe ido yayi lokacin daya kai farfesun kayan ciki bakinsa... Gaskiya yayi dad'i sosai.. Hakan ne yasa daya bud'e idan nasa ya sakar mata murmushinsa me tsada da furta kalmar... "Ki daure ki rayu da qawarki dan bani San nayi missing girkinki Murmushi taƙarayi da zubamai drink a cup tajuya da nufar aminiyar tata tana cewa.... "Karka damu.. zan rayu da ITA da KAI.. har izuwa qarshen rayuwata... Rungumarta NUFAISAT tayi da fad'in... "Nagode Aminiyata. Kina kula min da Mijina. Kina kulamin da cikinsa fiye da tunanina... Nagode sosai fah "La😀 karki damu Aminiya.. Ai hidima ga Mijinki dani ya dace Idan da kara... Shine fa abin sanki abin qaunarki Wanda kikaso kashe kanki saboda shi. Idan ban kulam miki dashi ba dawa zan kula. Kawai damuwata d'aya. kyautatawata agaresa. Allah yasa ta maqale cikin zuciyarsa. yaƙi mantawa dani. ta dami zuciyarsa hakan yasa yaqi qara miki abokiyar zama dan ina kishin wata Y'a mace tarab'ar miki miji sanadin girki kawai.😀... TAUDHAT ce me fad'in hakan.. Qara Rungumarta NUFAISAT tayi da cewa. "Nagode... Alamu sun nuna zashi gun Dady... Dan haka kijirasa ya gama saiya sauke ki agida. Tunda yanxu kin fara qin tawowa da motarki... Jan numfashi TAUDHAT tayi da fad'in "Toh Qawa... `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. *☾•RAHMA* MUH'MD RUFA'I NALELE..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ Email:realhausafulaniwritersforum@gmail.com Facebook:www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITTERSFORUM.com https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 03☆ Yana jinsu ahaka ya gama da tashi ya goge bakinsa da tishu yana fad'in.. "Toh my luv. Kamar yanda kikayi harsashe. Zani gunsu Dady. Kina da buqatan wani abu ne natawo miki da shi... "Bana da buqatar komai.. Saidai kawai kasauke Y'AR UWA agida dan Allah. "Angama my luv. Ya fad'i hakan yana me kallan TAUDHAT kana ya ficce daga falan. "Toh Y'AR UWA Ni zan tafi. Sai Allah ya tashemu lafiya "Nagode Y'AR UWA.. Ki gaishe min dasu mamah. "insha Allah zataji.. TAUDHAT tabata amsa da ficcewa dana sakar mata Murmushi Itama Murmushin tasakar mata.. Sanda taji tashin motarsu sannan tanufi dining da kwashe kayan kai. Takai kitchen. Tadawo tagoge wajen. Sannan takoma kitchen d'in tawanke kayan da adanasu a inda ya dace Sannan tanufi bedroom nata tana nazarin qara yin wanka.. ADAMSY da TAUDHAT ko. Kamar yanda suka saba. Idan bataxo da motarta ba.. Toh Idan ya d'auketa atashi motar bamema wani magana Kasancewar shi d'in miskiline kuma me Aji Dama Ita kanta tasan ba wani dalilin da zaisa yayi hira da ita imba tana tare da matarsa ba Kawai zai kulatane da hira ne idan tana tare da NUFAISAT matarsa Dan tasan shi mata basa gabansa Kawai matarsa itace agabansa Wannan dalilin yasa Idan tana tare dashi takan d'auki wayarta tata danne dannanta.. Dama shi yasan kansa ba wata hira da zaiyi da ita. Dan baisan me kuma zasuce ba Shiyasa kawai yake maida hankalinsa kan tuqinsa dan baya tafiya da masu tsaransa zuwa gidansu Wannan tsarinsa ne!!! Ahankali ta kallesa da lankwashe harshenta tace dashi... "Nagode Mijin Qawa Da Murmushi ya bata amsa da cewa... "Kinfi qarfin hakan. Kuma har yaushe zaki dena godemin Idan nakawoki gida.. Itama da Murmushin tabashi amsa da.. "Ai kaima kullum cikin godemin kake.. Da zaka dena da naji dad'i "Hidima dani fa kikeyi Kullum.. Idan ban gode miki kullum ba. Me kikesan nayi "Alamu dai sun nuna ba wanda zai dena godema juna a tsakaninmu.... Kan yabata amsa wayarsa tayi qara.. Koda yaga me kiran nasa. Murmushi yasake da d'auka yana cewa... "Hankalinki ya kwanta my luv. Yanxu na sauke miki qawa.. Murmushi NUFAISAT tayi dai-dai lokacin da take d'aura tawul ajikinta dan shiga wanka tace da shi... "Hankalina kuma bazai qara kwantawa ba. Harsai najika kaje gasu Ammee lafiya kadawo gareni lafiya. "Fatan alkairi kawai matata "Na kwana inayi maka Mijina "Toh kiqara gyaramin kanki da kyau. Dan gajiyar yau.. ta Musamman ce.. "Kace na shirya karb'ar dukkanin tarin gajiyar.. "Abinda nake nufi kenan "Toh ka kulamin da kanka.. "Naji my luv Sanda ya ajiye wayar gefansa Sannan ya kalli TAUDHAT da sakar mata Murmushi yace... "Haka kawai kin zauna kina jin sirrina da matata.. Murmushi TAUDHAT tayi da ficce daga motar tana cewa.. "Amin afuwa bansan lefi nayi ba.. Kuma mah banji komai da kuke cewa ba.. Jan motarsa yayi kawai da Murmushi Ita kuma tad'an cije harshenta da shigewa gidan nasu Bata tarar da kowa a falan nasu ba. Dan haka saitai jifa da jakarta.. Ta zube akan kujera tafad'a tunani Ahaka mamah mahaifiyarta taxo tadafata tana cewa... "Niko zanga ranar dazaki dawo daga gidan NUFAISAT ba tare da tunani ba Murmushin yake tasakarma Maman nata da cewa. "Nima ina fatan naga ranar dazan dawo daga gidanta da farin ciki. "To Wai meyasa hakan take faruwa dake "Wallahi mamah San mijinta nakeyi😔 Ina San ADAMSY Danya tara duk wani abun da mace me aji takesan samu agun Mijin Auranta.. Duk da cewar yanxu kin manyanta.. Amman hakan bai hanaki cewa ADAMSY ya had'u ba Dan Allah kiyarda mu had'a kai nashiga gidansa matsayin matarsa ta biyu... Mamah ko kin manta ranar da kika gayamin cewar ya had'u.. "Ban manta ba TAUDHAT.. Kuma yanxu ma zan qara nanata miki.. ADAM ya had'u.. Dan ban tab'a ganin yaro Wanda ya had'e komai na rayuwa irinsa ba Amman hakan dace da kamata yasa ki soshi aranki ba.. Saboda matarsa Y'AR UWA ta d'aukeki. Wannan cin AMANA ne Ina rokwanki daki dena San ADAM.. Dan kwata kwata baku dace da juna ba. Duk da cewar ke Y'ata ce. Bazanso kici amanar ADAM da NUFAISAT ba.. Saboda shi nagari ne Shiba walaqantacce bane Shi mutum ne me kamun kai Bai kyautu da had'in kaina kizama mata a garesa ba Kefa karuwace.. Wacce take karuwanci da manyan y'an iska.. Ko kin manta hakan ne Shekarunku ashirin da biyar da NUFAISAT.. Amman bata tab'a sanin hakan ba NUFAISAT bata tab'a sanin kina da wasu mugayan d'abi'u ire iran waƴannan ba..... Cikin fusata da tsawa TAUDHAT tatashi tare da katse mahaifiyar tata da hannu tana cewa... "Ya isa haka mamah.. Bansan har sai yaushe zaki fara sona ba Dalilin halin rayuwar da muka shiga nafad'a wannan halin da kike fad'a Ke wacce irin uwace Mara imani Kin tambayeni damuwata nagaya miki ita. Mazaisa bazakibi bayana ba Saikace bake kika haifeni ba.. Sai kace bani kad'ai bace y'arki aduniya.. Ina ganin iyayan da suke bin ra'ayin y'ay'an su. suna jinjina basira irin tasu. Idan sunxo musu da wata shawara. Ko wani abu da suke san aiwatarwa kuma su qarfafa musu gwiwa.. Daga yau idan har zanzo miki da wani batu kuma bazaki bi bayana ba. Saidai kibini da mugayan maganganu.. Toh ina farawa kicemin bazaki iyaba.. Idan har kika barni nakai qarshe kafin kikace bazaki iya ba. Wallahi ba abinda zai hanani hukuntaki... ******** Kasancewar mahaifin TAUDHAT ya rasu tun tana shekara goma.. Hakan yasa abubuwa dadama suka canja na rayuwa acikin gidan nasu Ya zama talauci yayi musu qatutu.. Hakan yasa mahaifin NUFAISAT da mahaifiyarta suke temaka musu kasan cewarsu makwaftan juna Toh ZUCIYA da buri Hakan yasa TAUDHAT taga bata mallakan komai na rayuwa kamar yanda NUFAISAT take mallaka Saboda mahaifin NUFAISAT Babban mutum ne. Yana da arziqi Toh ance Idan har da hassada azuciyar Wanda kake kyautatama baizai tab'a ganin abunda kakemai ba Da TAUDHAT nake.. Dan NUFAISAT ta kasance me tausayinta.. Idan za'a dinka mata kaya daru take sawa sai'an d'inka mata Ita da TAUDHAT Tun mahaifiyarta najin haushi. Har taxo tadena. Jin haushin Saiya kasance komai da zakasan NUFAISAT dashi. To katabbatar zakaga TAUDHAT dashi Dan komai biyu iyayan NUFAISAT sukeyi D'aya na NUFAISAT d'aya na TAUDHAT Amman hakan bai hana TAUDHAT lalacewa ba Dan bataso komai ace iyayan NUFAISAT ne suke musu Wannan dalili yasa tafara bin maza Tun ana amfani da ita abata kud'i kad'an hardai tazo ta kile tafara karb'ar manyan kud'ad'e Saiya kasance rabin kud'in zata dinga kawowa gidansu tana amfanin yau da kullum dukda ba abinda iyayan NUFAISAT suka ragesu dashi Tun mahaifiyar TAUDHAT bata ganewa hardai tazo tagane me y'arta takeyi take samun kud'i haka Hankalinta ba qaramin tashi yayi ba data san me Y'ar tata takeyi Saidai kash... lokacin data sani ya qure dan ba qaramin bokaye da malamai TAUDHAT tasani ba.. Wancan rabin kud'in da take b'oyewa a wajen bokaye da malamai yake qarewa da maganin mata. dan kawia tasamu maza yanda takeso.. Wannan dalilin yasa data ankare mahaifiyar tata tagane me takeyi sai kawai takaima wani boka sunan mahaifiyar tata tace ya rufe mata bakinta sai yanda tayi da Ita Aiko haka akayi.. Koda mahaifiyar tata tanufeta da batun mekaita aikata karuwanci. Tashi tayi tahau mahaifiyan da fad'a tana nuna mata bazata iya rayuwar saidai wasu su basu ba Shuru mahaifiyar tata tayi mata.. Ganin hakan yasa TAUDHAT d'in tasan aikin boka yaci mahaifiyar tata.. Saiya kasance tafara tsola tsiyarta yanda take so agaban mahaifiyar tata... Dan tasan ba abinda uwar ta'isa tayi mata Saidai duk abinda takema mahaifiyar tata bata tab'a yarda tayi mata agaban NUFAISAT. Ta hakan ne mahaifiyar tata tagane duk abinda TAUDHAT d'in takeyi NUFAISAT bata da sani akai... [29/04 12:05 pm] 🔳◾◼▪💙: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ Email:realhausafulaniwritersforum@gmail.com Facebook:www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITTERSFORUM.com https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 04☆ Abin na damun Maman TAUDHAT d'in yanda lokaci d'aya tafara jin tsoran TAUDHAT d'in Ana haka ADAMSY ya fitoh Auran NUFAISAT Saboda ganinta da yayi a bikin Yayarta Zainab Kallo d'aya tamai ta amince dashi Har akayi bikin NUFAISAT da ADAMSY TAUDHAT bata da nutsuwa Dan tun ranar da NUFAISAT tazo mata da batun ADAMSY yace yana santa... Tun daga lokacin take shirye shiryen yanda zatayi tajuyo da hankalinsa izuwa gareta Tak'i samun nasara danshi me ibada ne. Shi me nema agun Allah ne. Wannan yasa har akayi bikin NUFAISAT dashi bata samu yanda takeso ba Dukko da irin bin bokayen da takeyi da malaman... Wannan dalilin shiyasa tacusa kanta ga yimasa abinci tunda tasan ba abinda NUFAISAT bata iyaba sai girki... Shima dan batayi agidansu ne.. Sai hakan yaba TAUDHAT damar yimai barbad'e cikin abincin da takemai. Dan kawai karya gaji dacin girkin nata. Wannan dalilin yasa kobaiyi dad'i ba. Baya ganewa.. Dan yarigada ya saba da girkin nata Kuma iyawar tata ba wani can bane Saidai tafidai NUFAISAT d'in dabata iya ba. Wani malaminta ya tabbatar mata da cewar saita dage sosai wajen d'auke hankalinsa akan kowane abincin da zaici inba nata ba. Sannan zata shiga ransa har tasamu damar shiga gidansa matsayin matarsa ta biyu... Wannan shine dalilin dayake sawa qarfe goma Sha d'aya na safe nayi take zuwa gidan NUFAISAT tayi mata girkin rana akai masa. Sannan tayi mata na dare tajirasa ya sauketa agida.. Tayi wani saban boka. Wanda yace mata tasan yanda zatayi takawo NUFAISAT ya ganta. Kawai ganinta Idan yayi azahiri shi zaisa ADAMSY ya Aureta ko aranar ne... Kullun tunani takeyi. Ya zatayi takai NUFAISAT gunsa Dan tasha cusama NUFAISAT d'in ra'ayin bin kalamai akan matsalar haihuwan datake fama dashi Yau shekarunta da ADAMSY shidda kenan amman bata tab'a samun ciki ba suna karb'ar magani sosai Saidai komai sai Allah yayarda A binciken da ADAMSY yasa kwararrun likitoci sukama NUFAISAT d'in sun gano bazata tab'a aihuwa ba!!! Ita bata da kwan haihuwa.... ADAMSY yaqi gaya mata Dan baqaramin so yake mata ba Kasancewar tatara duk abinda yakeso agun mace Ta iya duk wani abu da yake so agun mace Matsalarta biyu ce agaresa Shine bata iya girki ba Kuma bata damu ta'iya ba Yana San mace me shagwaɓa. Amman baya samun hakan agunta Saidai yanaji aransa zai rayu da Ita a hakan Yana matuƙar San yara Hakan yasa yajema iyayansa da batun zai d'auko yaran marayu biyu ya rainesu.. Dake mahaifiyarsa itace amarya agidan mahaifin nasa. Kuma bata isa tayanke wani hukunci akansa ba Saboda uwar gidan mahaifinsa tagama da mahaifin nasa. Watoh Hajjiya Salma Kuma itama haihuwanta d'aya da mahaifin nasa... Saida mah mahaifiyarsa hajjiya Rahma ta haifesa bayan wasu shekaru uwar gidan hajjiya Rukayyat ta haihu.. Dan har tacire rai da haihuwan.. Shine take haifan Salim Wanda yanxu shima ya girma yake kula da supermarket d'in ADAMSIN... Wannan abu yana b'ata ma Hajjiya Rukayyat rai... Yanda ADAMSY yake juya nera. Hannunsa me albarka ne Dan duk abinda yasa agaba zaiyi kasuwanci akansa tosaiya samu albarka... Gashi doctor.. Ga kasuwanci.. Gashi duk fad'in garin KADUNA bawanda baisan ADAMSY ba Kowa fatan alkairi yake masa. Saboda kyautatawarsa ga al'uma Ga qaninsa Salim d'in yana San d'an uwan nasa ADAMSY... dan baya nuna masa komai Shiyake masa komai na rayuwa.. Dake shi Salim d'in kasuwanci ya karanta. Shiyasa ADAMSY ya barsa a supermarket d'in nasa... Burin hajjiya Rukayyat ADAMSY ya mutu. Salim ya zama kamarsa.. Su gaje dukiyarsa.. Wannan dalilin yasa dataji zaije ya d'auko yaran marayu tayi tsalle ta dira tace bata amince ya ibi yaran marayu ya rainesu ba Ganin hakan yasa mahaifinsa shima yace bai yarda ya d'aukosu ba. Koda ADAMSY ya kalli mahaifiyarsa a lokacin nunamai tayi dole yabi umarninsu Dan yasan bata da y'anci agidan Kuma mahaifinsa yana da zafi.. Idan ya yanke hukunci akan abinda hajjiya Rukayyat tayanke shikenan ya zauna.. Wannan rayuwar da mahaifiyarsa takeyi agidan tana baqanta ran ADAMSY Saidai ba yanda zaiyi. Amman zuciyarsa cike take da tsanar uwar gidan Dadyn nasa hajjiya Rukayyat Sannan hajjiya Rukayyat bata san ADAMSY ya haihu dan bokanta yace mata duk randa ADAMSY ya haihu toh aranar duk wani asirce asircen da takema mahaifin nasa aranar zai fara warwarewa... Ita kuma irin nata salan qaddarar asirce asircen nata kenan Wannan shine labarin TAUDHAT da dangantakar dake tsakaninta da NUFAISAT. Da kuma d'an rayuwar ADAMSY dana d'auki muku.... ********** Ba abinda Maman TAUDHAT ta iya cema TAUDHAT d'in sai tashi da tayi tabar mata falan... Aiko wani matsiyacin tsaki TAUDHAT d'in taja wai adole ranta ya b'aci. (Allah ka shirya mana zuri'a Amiin) Toilet ta shiga tayi wanka da fad'awa bed nata. tana tsaka yanda zatayi taja hankalin NUFAISAT suje wajen saban bokan nata Duk ta k'osa tazama Matar ADAMSY Itama yadinga damawa da ita cikin soyayyarsa ADAMSY ko yana kaiwa gidansu duk da cewar dare ne Amman hakan bai hana ma'aikatan gidan rugowa da gudu suka zube agabansa suna masu kwasar gaisuwa ba.. Suna San ADAMSY kasancewar yana kyautata musu da basu kulawa... Da Murmushi yake amsa gaisuwarsu ahaka har ya shige falan Dadynsa Dake yau hajjiya Rukayyat ce da Dadyn nasa tare ya gansu suna hira.. Dan haka yana gama gaishesu saiya nemi daya tashi yaje shashin mahaifiyarsa.... Da sauri Dadyn nasa yace dashi... "Dakata ADAM.. Dama ina San magana dakai Cikin ladabi ADAMSY ya koma ya zauna yana cewa.. "Ina jinka Dady Jan numfashi Dadyn nasa yayi da cewa.. "Dama ina San.. ka ƙara Aure ne.... Cikin sauri da rikicewa tsakanin ADAMSY da hajjiya Rukayyat suka had'a baki wajen cewa.. "Aure😳.. Suna masu kallansa Da wani hali Dadyn ya maida kallansa ga hajjiya Rukayyat yace.. "Eh Aure.. Aure nakesan ya qara ko za'a samu rabo daga matar dazai Aura.. Yanxu fa shekarun auransa kusan Bakwai.. Ina San yara da yawa Rukayyat.. kinfi kowa sanin hakan Daga shi sai d'an uwansa Salim nake dasu.. Hakan yasa nake kwad'ayin samun jikoki Gaskiya ina san ganin jikokina nan kusa Da wani hali hajjiya Rukayyat tace... "Amman Alhaji ai ADAM baiyi dad'ewar daza'ace ya ƙara Aure dan rashin haihuwa ba.. Murmushi Dadyn nasa yayi da cewa... "Haba Rukayyat. Kiyi aiki da hankali mana. Yaran nan ya haure shekaru talatin.. Idan bai haihu yanxu ba. Saiya tsufa kikesan ya haihu.. Gaskiya Ina San naga y'ay'ansa yanxu.. Nagansu kan cinyata suna jamun gemuna.... Ya ƙarashe furucin da Murmushi😀 Aiko nan take ta murtuƙe fuska.. Ta nuna ƙarara bataji dad'in furucinsa ba.. Dan haka da ɓacin rai tace.. "Toni gaskiya ban amince ADAM ya ƙara Aure yanxu ba.. Dan haka aƙaramai wasu shekaru Idan anji shuru abarsa ya ƙara Auran Shuru Dadyn nasa yayi.. Can yace. "Toh shikenan an qara masa lokacin. Allah ya dubesa ya basa nan kusa.. Da Murmushi tace.. "Amiin Amiin..😀 Shiko ADAMSY shuru yayi yana jinsu.. Da farko yaji fad'uwan gaba dayaji furucin mahaifin nasa nasan ya ƙara Auran Dan ko'a mafarki baiji aransa yana San qara Aure ba.. Saidai kuma yaji mamaki sosai yanda hajjiya Rukayyat ta nuna damuwarta akan batasan ya ƙara Auran Hakan yasa kwakwalwarsa tashiga tunani dan tagano dalilinta.. Yadai fahimci koma menene dalilin nata bame kyau bane Ya gane da daɗewa ba sanshi take da haihuwa ba Toh me take nufi da hakan.. Shuru yayi na wani d'an lokaci... Danya raasa gane manufarta.. Dan haka Ahankali ya kalli Dadyn nasa yace mai... "Nasan kana San yara Dady.. Kuma dama nima ina San gaya maka Inasan ƙara Aure.... Kawai jira nake mugama dai dai tawa da Ita yarinyar nazo maka da batun... Ai da sauri Dadyn nasa ya tashi daga shigingiɗan da yake cikin farin ciki da murna yace... "Masha Allah.. Allah abin godiya. Gaskiya naji dad'in hakan Ku dai dai ta Inasan ganin yaranka ADAM.. Allah yasa nagansu da raina Da Murmushi ADAMSY ya kama hannun Dadyn nasa yace... "Insha Allah Dady zaka gansu kana raye.. Har suxo kan cinyarka suja maka gemu..😀 Dariya sosai Dadyn nasa yayi yana shimai albarka.... Afusace hajjiya Rukayyat ta gallama ADAMSY harara tace... "Ka kalleni ADAM. Kasan bana magana biyu anan gidan. Dan haka bazaka ƙara Aure yanxu ba.. Sai nan da wasu shekaru.. Har yaushe kayi Auran dazakace zaka ƙara. In banda zalama irin taku ta yaran zamani meye matarsa NUFAISAT bata had'aba Yarinya me hankali da nutsuwa ga ladabi da biyayya Kai yanxu baza kaji kunyar idanta Idan taji zaka ƙara Aure ba!!! Yanxu ADAMSY ya ƙara tabbatarwa tana da manufa me qarfi kan bata San ya ƙara Aure Dan haka da Murmushi cikin sanyin murya yace da Ita... "Momy ina San ƙara Aure ne badan matsalar haihuwa ba. Saidan karna fad'a ga halaka. Azahirin gaskiya ina da ra'ayin yin mata hud'u.. Wannan shine dalilin dayasa zan ƙara Aure badan NUFAISAT tarageni da komai ba Dake mun fahimci juna da Ita na gaya mata dalilina nasan na ƙara Aure Kuma tafahimta har ta'amince dana nema mata abokiyar zaman tagari... Ki kwantar da hankalinki momyna.. Insha Allah mata bazu wahalar miki dani ba... Dan nasan matsalarki kenan.... Ya ƙarashe furucin da tashi yana mah Dadynsa sallma da Murmushi akan fuskarsa yake cemai daga gun Amminsa zai wucce gida basai yadawo ba Fatan alkairi mahaifin nasa yayi masa shiko ya ficce da sauri dan bayasan hajjiya Rukayyat d'in tace mai wani abu... Aiko yana ficcewa itama taficce zuwa shashinta dan kiran aminiyarta Susan yanda zasuyi😂 Shiko Dady da kallo yabita... Kana ya tab'e irin zakiji dashi d'innan... [29/04 12:05 pm] 🔳◾◼▪💙: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018. Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 05☆ Shiko ADAMSY can a bed yaga Ammeen nasa tana qoqarin kwantawa.. Aiko da Murmushi ta kallesa tace... "Yanxu nake tunaninka d'an albarka... Fad'i nake araina kodai yau bazan ganka bane nayi baccina Zama yayi kan kujerar dake kusa da bed d'inta yana cewa.. "Wane ni da qin zuwa ganin iyayena. Koda ace NUFAISAT shed'aniyace. Bata isa hidimarta tasani mantawa da iyayena ba. Ina sanki Ammeena.. Zanyi komai gareki dan kiji dad'i Jan numfashi tayi dajin daddad'an kalamansa. Kana ta zauna gefan gadan nata tana me qara cigaba da kallansa tace.. "Abu d'aya yanxu zai qara faranta raina agunka ADAM.. Shine naga y'ay'anka.. Duk da cewar ina qaunar NUFAISAT.. Bazan so ka had'ata da wata mace ba. Danta tara duk abinda yadace asamesa agun Y'a mace.. Saidai zuciyata na gayamin.. Kodai zaka qara Aure ne.. Wallahi ADAM ba abinda nake buri ayanxu kamar naga y'ay'anka.. "Ammee kenan.. Insha Allah zakiga y'ay'ana. Yanxu ma maganar da muka gama kenan da Dady Yana San na qara Aure amman kamar momyn Salim bata San na qara Auran Saidai na tabbatar mata da cewar zan qara dan ina da burin Auran mace hud'u Murmushi Ammeen tasa tayi da cewa. "Masha Allah.. Saika gaggauta neman wacce zata dace dakai... Dan Idan ka d'auki lokaci ba makawa zatayi wani abu akai.. Tunda kaga kamar bata so ka qara.. "Insha Allah kuwa Ammee Sun d'an jima suna shirarrakinsu irin na d'a da uwa.. Sai daga bisani ya numfasa yace.. "Yanxu ni zan tafi.. Naga dare nayi.. Ko akwai wani abinda kike buqata. "aa nidai gareni babu komai.. Saidai gobe baqin da zaka gana dasu da safe suna da yawa.. Murmushi yayi da tashi yana cewa.. "Ba damuwa. Allah ya qara shige mana gaba.. "Amiin. Tace dashi tana me Murmushi Shima da Murmushin ya fitta daga d'akin.. Direct wajen shiyan kayan sanyi ya nufa.. Inda ya siyama Matar tashi ice-cream. Dasu mittifai da sauransu.. Kana ya nufi gida Tun daga farfajiyar gidan yake jiyo ƙamshin turaran da Matar tasa tasaka a falan nata.. Murmushi yayi da girgiza kai. Yana tuna tsafta da kwalliya irin na Matar tasa.. Da cikakken nishad'i ya shiga falan yana cewa.. "Inafa jin daɗin turaran nan... Ahankali tafitoh daga wani d'an sak'o tana Murmushi tace... "Har sai yaushe zaka dena wannan furucin da zaran kajiyo wannan ƙamshin.. Da wani salo. Da wani yanayi yake qare mata kallo tun daga sama har qasa.. Tayi mai kyau irin sosai ɗinnan👌🏻 Danji yayi kamar ya saceta ya gudu.. Wani mini siket ne tasaka da wata riga wacce tatsaya mata a dai-dai na fulaninta.. Nan wajen kawai ta iya sitircewa a jikinta.. Haka kazanika shi mini ɗinma ba wai ya saukan mata bane.. dan Idan tayi kyakkyawan juyi zaka iya gano gabanta nan kusa basai kasha wahala ba.. Yafa kwaɗaitu fa sosai da yanayin.. Dan taga yanda yayi saurin haɗiyan yawo.. Shi dai yana San matarsa. Dan yana samun farin ciki daga gareta.... Rungumarta yayi yana kissing ɗinta tako ta ina yana cewa.. "Kinyi kyau sosai matata... Ina sanki.. Ina ƙaunarki Ina fatan kasancewa dake har ƙarshen RAYUWANA... Tafi kowa sanin mijinta... Bai iya ganinta ya barta haka kawai ba Saidai Idan da baqi yayi musu alkunya Ji take aranta tafi kowa Sanshi da ƙaunarsa Taƙyer takwaci kanta tana cewa.. "Nakasa banbancewa Shin awane yanayi kafisan kaganni.. Na saka ƙananun kayane ko nasaka kayanmu na hausawa.. Idanshi ya kaɗa yayi jah yace da ita.. "Me kika gani.. "Gani nayi a kowane yanayi kaganni rikicewa kakeyi.. Murmushi yayi da cewa.. "My luv bazaki gane qaunar da nake miki bane.. Yanxu dai muje ki bani nasamu nutsuwa.. Amman dan Allah ki barni nayi yanda nakeso.. Hararar wasa tasakar mai da cewa.. "Yaushe zaka dena wannan futunar taka... Cikin sauri ya katseta da cewa.. "Randa namiki Kishiya ranar zan dena damunki da yawa... Aiko nan take ta zumɓuro baki tace... "Zanfa babbakaku daga kai har kishiyar.. Dariya yayi sosai yana kallanta da bata amsa.. "Toh Idan kuma ya kasance Y'ar uwarki ce fah "Wake nan..😳 Wai kana nufin TAUDHAT... ɗaga mata kai yayi yana kunshe muguwar dariyar dataxo masa.. Aiko turmuƙe fuska tayi kamar zatayi kuka tace... "Dan Allah kabari... Kaima kasan abune bame yuhuwa ba.. Nasan ko'a mafarki TAUDHAT baza tataɓa zama kishiyata ba.. "Ko..... Ya katseta da faɗin hakan yana me cigaba da cewa... Amman kinsan da cewa TAUDHAT tana matuƙar sona.. Jan numfashi NUFAISAT tayi da cewa. "Na lura yau sokake ka zautar dani da zolaya... Kaga zomuje na shayar dakai dannaga a kwaɗaice kake dasu... Ta ƙarashe furucin nata tana me karɓar ledar dake hannunsa da kama hannun nasa tajashi bedroom ɗinsa Buɗe mata kayan sanyin yayi su ice-cream ɗin tasha San ranta... Kana ya fara sarrafata yanda yakeso... Sanda ya tabbatar yasamu nutsuwa da kwanciyar hankali kana ya maƙaleta yana juya na fulaninta cikin bakinsa yana jin daɗi.. Sanda ya ɗauki lokaci ahakan kana ya bar matasu ya rungumeta yana ce da ita... "My luv. Ina samun dukkanin wani farin ciki daga gareki Sannan a iya sanina ba ma'Auratan da suka kaimu fahimtar juna.. Dan kina san abinda ni nake so Haka kaza nika nima Ina san abinda ke kike so. Duk da cewar nasan kishiya da zafi take.. Ina baki haƙuri wajen gaya miki dazanyi cewar ina San zan ƙara Aure..... Sosai yaji bugawar da girjinta tayi.... Sakamakwan dama a ƙirjinsan take.. ƙokari tayi dan ta raba kanta da ƙirjinsa Amman saiya ƙara ƙamƙameta.. Shuru na wani ɗan lokaci... Zuwa can ya fara jin zubar hawayenta a ƙirjin nasa Cikin wata siririyar muryar tace dashi... "Me zaisa ka ƙara Aure... "Zan ƙara Aure ne saboda ina San na faranta ran iyayena Ko Allah zaisa nasamu rabo... Bayan hakan ina addu'a akan Allah yasa wacce zan Auran ta iya girki... Dan ina San mace wacce ta'iya. Nasha gaya miki batun yau ba. Sannan bawai zanyi Auran bane danna musguna miki Zanyine kawai dan farin cikin iyayena da kuma kwad'ayin samun wacce ta iya girki... Danna San zamammu da TAUDHAT na wani ɗan lokaci ne. Kasancewar Dole tazama matar wani. Idan hakan ta kasance yazanyi... Ya faɗi hakan yana me kallan fuskarta daci gaba da cewa.... Nayi nayi dake akan ki daure ki d'an iya. Amman kinqi Toh ya zanyi dake my luv.... Kuka take sosai. Dan baqamin shiga tashin hankali tayi ba Tasani.. Mijin nata me magana ɗaya ne.. Kuma duk abinda zai gaya maka gaskiya ne Tasan tsakaninta dashi ba batun wani ƙunbiya ƙunbiya Duk abinda yace mata zaiyi zaiyi ne kawai Wannan yasa tafara jin tausayin kanta Dan tasan zamani ya lalace... Batasan wazai kawo mata ba Tasan yana dasan yara. Shin idan yasamu daga wajen kishiyar tata wane baƙin ciki zata kwasa.... Cikin kuka tace dashi.. "Yanxu awane matsayi zaka barni... "Wallahi bazan taɓa canja miki matsayin da kike dashi a cikin zuciyata ba... NUFAISAT umarni nake baki akan bana San naga wani tashin hakanlinki akan Auran nan Sannan bana San naga kin canja daga abubuwan da kike min Hakan zai iya tunzura zuciyata Dan kinsan baki isa dakatar dani daga ƙin aikata hakan ba Kinfi kowa sanin magana ɗaya nake dake. Wacce ta kasance bata wasa ba. Ina San ki saka aranki abokiyar zaman ki zata iya zuwa miki a kowane lokaci Daga ƙarshe ina Sanki. Kuma bana tunanin zanso wata Y'a mace KAMAR yanda nake sanki.. Jan numfashi tayi cikin cigaba da kukan nata tace dashi... "Zanbi umarninka Ya mijina.. Dan abinda ya kawoni kenan gidanka... Saidai yanxu ina buƙatar kaɗaici Dan Allah kabarni naje bedroom nawa na kwana.. Murmushi kawai yayi da saketa ta sauka daga gadan da suturce kanta har takai ƙofa yace da Ita "dakata Tashi yayi shima da sitirce gabansa yaxo gabanta da kama fuskarta yace... Dawai ina San ki tayani wankan ne kamar yanda kika saba.. Ya fad'i hakan yana me janye hannunsa Share hawayenta tayi dayi mishi Murmushin yaqe tace... "Toh muje.. ɗaukarta yayi kamar wata baby ya nufi toilet d'in da Ita KAMAR yanda yasaba mata Akan idansa tayi wankan tsarkin. shima yayi.. Sannan sukabi da wankan sosu da sabulu Kamar yanda tasaba temaka masa. Hakan tayi.. Bayan sun fitoh ne dukkaninsu jikinsu d'auke da tawul. Ya kalleta yace.. "Da'ace kamar yanda kike bani kulawar nan Idan mun kusanci juna wajen yin wanka. Da'ace hakan kike bani kulawa Idan kina tare da TAUDHAT dana qara sanki da qaunarki.... Dan sosai nake jin takaicin yanda baki San kulawa dani Idan kina tare da TAUDHAT.. Abin na d'auremin kai Idan kina bani kulawa bayan idanta Kawai dai magana d'aya anan itace.. ina San kulawa akowane lokaci koma kina tare da waye.. Murmushin k'arfin hani tamai da cewa... "Ayanxu zan kula sosai ya Mijina.. Kama fuskarta yayi ya fara aika mata da wani make✔.. Kiss. Wanda yake tafiya cikin wani salo Sanda yay mata San ransa kana ya barta yana mece mata.. "Zanso ki sami kaɗaicin da kika nemi alfarma akansa.. Murmushin dai taƙara sakar masa da cewa... "Nagode... Tana fad'in hakan taficce daga d'akin _yau rana d'aya kacal.. Kin raba shinfid'a dani NUFAISAT.._ Ya fad'i hakan aransa Kana ya zauna yana tunanin maraicin dazaiyi yau Dan yasaba da d'umin jikinta yayin baccinsa... Shuru yayi... Zuwa can ya canja kaya da shinfid'a dadduma ya fara aikin bada lafula. Yana gaisar da ubangijinsa Itako Sanda ta tabbatar da cewar ta kulle ƙofar bedroom natan.. Sannan ta zube a gadanta tarushe da wani uban kuka wiwi.. Ta sani... Mijinta na matuƙar santa.. Kuma ayanda take kyautatama iyayansa baici ace su mata haka ba.😭 Har shekara nawa tayi da Auran da zasuce ya qara Aure dan kawai bata haihu ba.. Abayyane take cewa.. "Wai meyasa mutune suke haka ne Meyasa Ammee zakimin hakan Me yasa. Meya Dady zakamin haka.. Shin bakusan Kishiya da zafi da ciwo take ba.. Ji nake kamar nayi hauka.. Ba qaramin kuka taci ba. Candai daga bisani dataga kanta na Sara mata alamar zata cutar da kanta.. Sai kawai tatashi tayo alwala tahau lafula.. Tana rokwan Allah akan ya biya mata buqatarta na yasa Auran karya zama tashin hankali agareta Allah yasa yinshi shine farin ciki agareta Allah yasa hakan ya zama alkairi agareta Allah yayaye mata baqin cikin duniya dana lahira. Allah ya BATA DAMAR B'OYE KISHINTA agun amaryar da shi kansa uban tafiyar... Haka tadinga addu'a kamar bazata dena ba.. Sannan kuma tadawo tafara karanta Qur'ani Sanda taji idanta na rufewa sannan ta kwanta Aiko bacci me nauyin gaske ne yayi awan gaba da ita... Shiko Sam bai iya wani baccin kirki ba Dan tunda yake da NUFAISAT wani abu bai tab'a shiga tsaninsa da Ita sun raba shinfid'a ba Wannan dalilin yasaka ya kasa baccin kirki.. [29/04 12:05 pm] 🔳◾◼▪💙: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018. Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 06☆ Asuba nayi kamar yanda tasaba... Watoh bayan kammala sallar asubarta.. Tana shiga toilet d'insa da nata ta wankesu Bayan ta fitto tayi shara da saita saka turara nan zakaji ko ina ya d'auki ƙamshi Kana tayi wanka sai tatarama ogan nata nasa ruwan wankan Kasancewar baya dawowa daga masallaci har sai gari yayi haske... Hakan yake bata damar kammala way'annan ayyukan saidai kawai ya dawo ya ganta fes Ita da dakunanta... Toh yau abin yaxo da wani saban salo.. Kasancewar tatashi da wani yanayi ba kamar yanda tasaba tashi ba Saidai tagodema Allah daya amshi addu'arta... Dan bata tashi da muguwar damuwar nan da mata ke tashi da Ita lokacin da mazajensu suka gaya masu zasu qara Aure ba... Hakanne mah. Ya bata damar tagama komai kamar yanda tasaba.. Yanxu haka tana tsaye a kitchen d'inta ne.. Lokacin bakwai dai-dai.. Alokacin kuma take sakaran dawowar Mijin nata daga Masallacin Dama shine yake dafa musu Lipton da soya musu kwai da sauransu..😂 Shine yau take San gwadawa.. Taga zaiyi dad'in da yake musu.. Saka ruwa tayi da d'an jefa citta dasu kanunfari ta cika ruwan.. Nan tatsaya har ya tafasa ta juye a fulas.. Sannan ta fasa kwai guda shidda tasaka magi dunƙule shima guda shidda... Sannan takad'a ta soya.. D'aukar wayarta tayi takira yayarta Zainab akan tagaya mata yanda ake had'a farfesun kaza... Da iya adadin magin da zata sakama kaza d'aya Dariya Zainab tayi mata Da cewa.. "Ina y'an aikinki suke.. Larai da Aseeya.. Kikara larai tayi miki mana... Kamar NUFAISAT zatayi kuka tace da Ita.. "Kisan bana sakasu aikin daya shafi shashina. saidai imbanda lafiya.. Aikin su shine kawai su dafa nasu daba ma'aikatan gidan.. Bama wannan ba. Shi Wanda zanyi dominsa baci zaiyi ba.. Ko kin manta yanda nasha wiya wajen cusa masa San cin girkin TAUDHAT Kinsan Daga na Ammeensa saina nata Yanxu kawai yakeci Jan numfashi Zainab tayi da cewa.. "Toh meyasa yau kikesan kiyi masa da kanki.. Bayan nasan shine yake had'a muku breakfast.. "Ki bari kawai y'ar uwa.. Ina San ganinki pls idan kin tashi daga office yau Ina san gaya miki wani abu.. "Ok.. Zainab tace da ita.. Sannan tagaya mata yanda zatayi.. Cikin iko na Allah ko sai tayi dai-dai da yanda tagaya matan... Dan duk gidansu Zainab ce kawai tayo momynsu wajen iya girki.. Shidai ADAMCY daya dawo yayi mamakin ganin NUFAISAT a kitchen.. Bama wannan ba. Mamakinsa yafi tsayawa akan yanda yake jiyo ƙamshin farfesun kaza.. Yasani wannan aikinsa ne na safe 😂 Murmushi kawai yayi da girgiza kai yayi part d'insa yana dad'a jin mamakinta.. Dan yafi kowa sanin koda wasa NUFAISAT bata shiga kitchen dasunan wai tashiga dan yin girki.. Wato Kishiya ba abinda bata saka mata... Haka yata surutansa a ZUCIYA.. Har yayi wanka da saka kayansa ya feshe jikinsa da turaransa me maƙalewa azuciya.. Kana ya nufi wani shashi na gidan nasa Wanda yake basa damar ganawa da baƙinsa.. Watoh tunda yau ta kasance asabar.. Baya zuwa asibiti ranar asabar da Lahadi Kawai yana zuwa kasuwancinsa ne.. Amman kafin nan yana ganawa da talakawa way'anda basu dashi wajen temaka musu daga ƙarfe takwas da rabi zuwa ƙarfe goma.. Toh da zaran ya gama dasu d'inne yake dawowa ga matarsa yaci breakfast d'in daya had'a musu. Kana ya nufi wajen kasuwancin nasa... Toh yau ƙarfe takwas ya nufi shashin dayake ganawa dasu... Kasan cewar yau Matar gidan tatashi da himma😀 ta canjesa wajen girka musu abin da zasuci. _Hmmm yau zaici girkin NUFAISAT_ ya fad'i hakan aransa.. Itako bayan tagama jitayi jikinta ya dauki ƙamshin girkin.. Hakan yasa taqara shaqa wanka tayi shigarmu irinta hausawa. Inda tasaka wata doguwar rigar atamfa... Kasancewar kalan ja da bak'i ne saiya haskata... Ba abinda zai baka sha'awa sai d'aurin data kafa... NUFAISAT nada kyau naban mamaki.. Macece so sweet.. Abin San kowane namiji.. Matsalarta biyuce inji ADAMCY.. shine bata masa shagwaɓa yanda zatana tsuma zuciyarsa.. Kasancewarsa d'an luv.. Sannan bata iya girki ba.. Waƴannan sune matsalar agun ADAMCY.. Falo tadawo duk ƙamshi ya rufeta.. Anan ta zauna ta d'auki wani littafin sister Rahma Nalele me suna *YA FARU AKAN KAINA* daniyar San karantawa.. Saidai kash.. Bai cancanta amatsayinta na wacce akace za'ama kishiya zuciyarta tabarta haka kawai ba.. Dan haka kasa karatun tayi.. Tayi shuru kawai da afkawa cikin kogwan tunanin ya zatayi da ganin mijin nata da wata mace.. Tafi kowa sanin waye shi.. ADAMCY daban yake acikin mazaje... Komai ya iya.. Bataga abinda ADAM bai iya ba.. Yanxu duk abinda yake mata haka zaima wacce zai Aura....... Jitayi an shafi gefan fuskarta.. Koda ta d'ago da kan nata ADAM d'in tagani.. Aiko nan ya sakar mata Murmushi yana me cewa. "Nasan tunanina kikeyi. Banda abinki waya isa ya kwace miki ni.. Ƙaryar wata mace takwace miki ni uwar ƴaƴana.. Sanyayyan Murmushi tasakar mai da cewa.. "Har yau nakasa gane yanda akeyi kake gane tunanina... "Saboda nine me GYARA TUNANIN NAKI.. Ina mamakin yanda kike manta cewar zuciyarki da tawa abu d'aya ne.. "Idanko haka ne. ya dace tunaninmu shima ya kasance abu d'aya.. "Tabbas.. Ya bata amsa da fad'in hakan. Yana me cigaba da cewa. Ƙamshi ya dami hancina.. Zan rigaki zuwa dining fah😀 Dad'i ya cika zuciyarta.. Tatashi ahankali daniyar zuwa ga dining d'in.. Shi kuma ganin hakan yasa shi rungumarta ya d'ago da fuskarta izuwa kallansa yana cewa... "Anya akwai ranar da zatazo nadena ganin kyen fuskarki kuwa.. Lumshe ido tayi da bud'ewa Ahankali tace.. "Ranar na zuwa.. Dan gashi nan alamun sun fara bayyana Yanxu... "Toh gayamin.. Ina alamun suke.. "Banda hakan. Mezaisa ka ƙara Aure.. "Izuwa gaba zanji ba dad'i idan kika ƙara alaƙanta maganar Aurena cikin maganata dake.. Shuru tayi najin wani iri.. Wai ADAM wane irin mutum ne.. Tafad'i hakan aranta.. D'an qara tsaida kallanta tayi akansa kad'an tace.. "Insha Allah bakina bazai qara gangancin furta wata kalma dangane da Auran naka ba... "Dts gud my sweetheart.. Nasan kina San mijinki... Kina kuma tsoran wata ta mallake miki shi. Kina san ganin kin haihu dashi.. Kina fatan kasancewa dashi har iya qarshen rayuwa. Ina sanki NUFAISAT. Adai yanxu yanda nake jin ZUCIYATA!!! Bana tunanin zanso wata mace!! Kamar yanda nake qaunarki.. "Da'ace zai kasance har iya qarshe rayuwa zakaji hakan aranka ba iya yanxu ba. Dana tabbatarmah da kaina!!! Nayi dace duniya walahira Cikin wani hali ya bata amsa da cewa. "Todai a'iya yanda nake jinki araina.. Ina tabbatar miki da cewar.. Kice afarkwanfarko cikin matan dazan rayu dasu cikin Auratayyata. Zatayi magana sai yayi saurin had'e bakinsa da nata Yana me juya harshensu cikin wani hali.. Sanin makomarta Idan tabari ya d'auki lokaci ahakan yana me mata kiss d'in.. Shiyasata yimai cakulkulu tana me kyalkyalewa da Dariya... Aiko nan take yasake yana cewa... "Watoh kinyimin hakan dan nabarki ko "aa... Kawai gani nayi kana shirin cinyemin baki nah🙃 Da Murmushi yace "aiko da gaske wata ranah zan iya cinye miki shi. Dariya taqarayi da kama hannunsa suka nufi dining tana cewa.. "Naka ne Mijina. Kayi duk yanda kaga dama dashi... Dan bani fatan naga ranar dazaka dena nunana qaunarka garesa Murmushi yayi dai dai lokacin daya zauna tana qoqarin zubamai farfesu... Bayan tagama ta tura mai kwan data soya had'e da had'a mai komai Wanda ya dace dashi. Sannan ta zauna itama ta d'an saka nata agaba cikin tsoron Allah yasa bata kwafsa ba.. Shuru ADAMCY yayi lokacin daya kwurb'i ruwan Lipton din data samai dan baya shansa da madara.. Eh.. Tayi qoqari ba lefi. Duk da cewar tamanta da abu biyu.. Wato ganyan na'a na'a da ganyen giris.. Yaji ba dad'i lokacin daya kai warnar kwan nan bakinsa.. Dan magi yayima kwan yawa over Gashi ta kafesa da ido.. Kawai jira take taga me zaiyi Ganin da tayi ya rintse ido sanadin kai wainar kwan bakinsa. Tasan Daurewa kawai yayi ya had'iye.. Zai qara tayi saurin riqe hannunsa Kamar zatayi kuka take cewa.. "Ban sanka da fulako ba.. Alamu sun nuna banyi abinda ya dace ba.. Idan nayi duba da yanda ka rintse idanka yayin had'iyewa. Shuru yayi mata.. Ganin hakan yasa tad'an gutsiri kad'an takai bakinta.... Aiba shiri tadawo dashi.. Dan magin yayi yawan dazai iya yima mutum illah.. Shuru tayi da sunkuyar da kanta.. Bai mata magana ba ya jawo farfesun kazar yakai bakinsa yana addu'ar Allah yasa tayi dai dai ashi.. Aiko addu'arsa ta karb'u.. Dan yayi dai-dai irin kadaran kadaham d'innan.. Dan haka ya zage yaci sosai.. Bayan ya gama ya kalleta kad'an dayin Murmushi dan har lokacin bawai ta d'ago da kan nata bane.. Kan natan yana qasa da alama ma kuka takeyi.. Jawo biran dake jikin rigansa yayi da wata y'ar fefa. Nan yayi mata wasu rubutu kad'an ya ajiye mata... Kana ya tashi da d'aukar laptop d'insa da wayoyinsa ya ficce daga falan yana addu'ar fita daga gida... Sanda taji tafiyansa shida maso tsaran nasa. Sannan ta d'ago da kanta ta sauke akan farar takaddar daya ajiye mata.. Ga abinda yace.. _Da'ace haka kike min tun da farko dana qara sanki da qaunarki.. Gaskiya ban taɓa cin farfesu me dad'in Wanda naci yanxu ba. Dan haka ina sauraran qaracin wani irinsa da rana idan zan samu.._ _Kisani Yanxu bana San naqara cin girkin TAUDHAT.. Idan kika bari wani ko wata ya qara saka miki hannu akan abinda zanci daga gareki!!! Lalle zanji ba dad'i. Zanji kamar kin munafunceni. Zanji zafinki sosai. Aqarshe koda kinyi nadama. Bazan kalleki ba.._ _Ina sanki matata.._ _Kidena wannan kukan da kikeyi.. Dan zai iya ɓatamin farin cikina ayau..._ _Sannan ki qara nutsuwa sosai wajen saka magi akwai. Dan idan kikaci gaba da sakawa da yawa kamar hakan... Lalle bazanƙici ba. Saidar cuta takamani.. Dan ayanxu nayima zuciyata alƙawarin duk abinda kika dafa zancishi ko Yaya yake.._❤ Jan numfashi NUFAISAT tayi da sakin Murmushi.. Abayyane take cewa.. "Bazan qara barin TAUDHAT tayima girki ba Ya Mijina. Yanzu na shirya kula da cikinka kamar yanda duk mata tagari takeyima mijinta... Tana gama furucin. tatashi ta kwashe kayan da kaiwa kitchen tawankesu tsaf... Daga falan nata taji muryar Aseeya da Larai suna gaisheta.. Da Murmushi tafitoh tana amsawa.. Tana me tambayarsu kowa dai yana lafiya ko.. D'aga mata kai sukayi alamar tabbatarwa Zama sukayi KAMAR yanda suka saba wajen tayata hira.. Can da misalin ƙarfe goma Sha d'aya saiga TAUDHAT taxo gareta.. Ganin zuwan TAUDHAT d'in yasa su Aseeya barin falan.. Da wani hali yau NUFAISAT d'in ta tarbi TAUDHAT d'in.. Ganin hakan yasa TAUDHAT d'in tambayarta ko tana lafiya Jan numfashi NUFAISAT tayi cikin kuka tace... "Yazanyi Y'ar uwa.. ADAMCY Aure zai ƙara...... "Aure😳... TAUDHAT ta nanata had'e da dafe ƙirji da waro ido. "Eh Aure zai qara TAUDHAT.. Saboda yana San ganin farin cikin iyayensa.. Wai so suke suga yaransa.. Yazanyi TAUDHAT.. Ji nake kamar nayi hauka. Kinsan baqaramin San ADAMCY nake ba Ina jin tsoran karya kasance wacce zai Auran shed'aniyace. Taxo ta rabani dashi.. Shuru TAUDHAT tayi.. Dan tafi NUFAISAT d'in shiga tashin hankali.. Dan numfashi har wani sama sama yakeyi... Cikin tashin hankali tace.. Towa zai Aura.. "Ban sani ba TAUDHAT.. Bansan wacece ba Saidai ya gayamin in saka ran zuwanta akowane lokaci.. Sannan bazai qara cin girkinki ba.. Nawa yake San ci.. Shuru dai TAUDHAT taqarayi... Zuwa can tunaninta ya bata mezai hana tayi amfani da wannan damar wajen Jan NUFAISAT d'in zuwa ga saban bokan nata.. Tabbas Idan ya ganta ba makawa Auran yarinyar dazaiyi kanta zai koma.. Yin wannan tunanin nata yasata Jan numfashi ta kalli NUFAISAT d'in cikin tausayawa tace... "Dama akwai wani malami me bada magani... Wanda wata mata tayimin kwatancen inda yake d'azu.. Ta tabbatar min Idan har yaba Wanda bai tab'a haihuwa magani. To Sha Allahu asatin mutum yake samun ciki... Shine fa hankalina ya tashi naketa sauri Nazo na gaya miki... Ashe da raban zanji wannan mummunan labari... Shuru NUFAISAT tayi.. Can tace.. "Mezai hana yanxu muje wajensa ko Allah zaisa mu dace.. Aiko da mafificin farin ciki TAUDHAT ta wangale mata baki wajen cewa.. "Maza kirasa awaya muje yanxu pls. Ba musu NUFAISAT ta d'aga wayarta takira ADAMCY Wanda yake wani companynsa na had'a kafet.. Cikin muryar lallashi take cemai dan Allah zata wanigu yanxu zata dawo.. Dafarko yaqi yarda. Sai Daga baya ya yarda.. Aiko da murna tashirya suka ficce... TAUDHAT ce me tuk'i. Yayinda NUFAISAT taketa addu'ar Allah yasa ta dace agun wannan malami... Sunyi tafiya me d'an nisa inda suka dire tafiyar a wani daji.. NUFAISAT ta kalli TAUDHAT ad'an tsorace tace.. "Me zaisa wannan malami yaxo cikin daji haka ya zauna... Murmushi TAUDHAT tayi da cewa.. "Ai kinsan manyan malamai bayin Allah basu cika zama cikin gari ba. Sunfi zama cikin daji saboda hakan yafi basu damar bautar Allah cikin nutsuwa.. Gyad'a kai NUFAISAT tayi dan tagamsu da abinda TAUDHAT d'in tace... Fitowa sukayi tare da nufar matan da suke zauna jikin bukkar wajan.. Kallo d'aya zaka musu kasan jiran fitowar wata suke jira daga cikin bukkar.. Da Murmushi TAUDHAT tagaishe tare da shigewa cikin bukkan kai tsaye.. Azahiri wasu daga cikin matan wajen sun nuna mamakinsu ganin hakan da tayi.. Hatta NUFAISAT tayi mamakin hakan... Hmm kodai menene gwara suyi sutafi dan haka kawai taji gabanta na fad'uwa da wajen... Sam sai taji hankalinta bai kwanta da wajen ba.. Itako TAUDHAT tana shiga cikin bukkan ƙarema Matar dake shirin cire kayan jikinta kallo take.. Da alama zata tsinannan zai aikata masha'a da itane kamar yanda yasaba yima duk wacce tazo neman temako garesa.. "Wai me yake damunki ne TAUDHAT.. Mezayasa baki tashi shigowa gareni sai kinga ina niyar San biyan buqatata... D'an gajeran bokan Wanda kallo d'aya zakamai kasan tsinannene banda fad'uwar gaban da zakaji agaresa shike fad'in hakan... Murmushi TAUDHAT tayi da fad'in.. "Na d'auka kasan da zuwana yau.. "Aikin San zan sani.. Ko bada NUFAISAT kikazo ba. "Eh da Ita nazo.. Kecewa yayi da wata shegiyar dariya yana me cewa... "Tunda nake arayuwata ban tab'a ganin macen data had'e kamarki ba... Saidai NUFAISAT tayi miki zarra.. Koda zakiyi zaman kishi da Ita. Dolene kiyi hakuri da ita.. Watoh TAUDHAT.. Yau burinki zai cika tunda naga NUFAISAT kamar yanda na gaya miki.. Dama ƙamshin jikinta kawai nake San d'an ugwalli yaji.. Dazaran tashigo bukkan nan yaji aikinki yaci... Saidai kuma tun daga nan zatayi miki tsana me me muni..... "Idan buqata zata biya.. Ban damu da tsanar da zatamin ba... TAUDHAT takatseshi da fad'in hakan tana meci gaba da cewa.. Bara na turota yanxu.. Saika sallami wannan matar Idan mungama tadawo Ku d'ora daga inda kuka tsaya.. Takai ƙarshen zancen nata da nuna matar nan data shigo tagansa da ita gami da ficcewa daga bukkan... Atareko suka fito ita da Matar dan tana ida zancenta yama matar nuni da ido akan taficce.. "Wai zaki iya shiga.. "OK.. NUFAISAT tace da TAUDHAT tana me shigewa cikin bukkan... Saidai cak tatsaya tana me ƙarema cikin bukkan kallo tun daga sama har qasa Gabanta ne yayi mugun fad'uwa... Nan take ranta yayi mugun b'aci.. Danta gane inda TAUDHAT takawota.. Miye had'inta da boka Meyasa TAUDHAT tayi mata haka.. Meyasa. Meyasa ta yaudareta.. Kallo d'aya zakama cikin bukkan kansan durk'ushe kake gaban boka.... Aiko azuciye ta fitto daga cikin bukkan ta nufi TAUDHAT d'in idanta ya kad'a yayi jah.. Cikin jin zafinta tace da ita... "Ina kika kawoni TAUDHAT.. "Wajen malami mana NUFAISAT. Koba haka na gaya miki ba. "Ƙarya kike TAUDHAT.. Ba wajen malami kika kawoni ba wajen boka kika kawoni.. Me nayi miki TAUDHAT.. Meyasa kika yaudareni Kinfi sanin na yarda dake fiye da kowa arayuwata.. Tunda nake ban tab'a kawowa araina zanzo wajen boka danya temaka min da wani abu nashi ba.. Kashi yau kin kawoni wajensa TAUDHAT.. Kin kawoni wajen La'ananne. Kin kawoni wajen tsinanne. Kin kayoni wajen matsiyaci.. Me zai bani imba tsiya ba.. Toda Allah na dogara bada kowa ba.. Kin nunamin kema baki sanshi ba... Saidai alamu sunnuna kinmai farin sani... "Haba bawar Allah.. Meyayi zafi haka. Kema imbanda kanki akulle yake. Aiyaci kigane tun farko wajen boka takawoki.. TAUDHAT bayau tasaba zuwa nan wajen ba.. Ni nan nizan gaya miki wacece TAUDHAT.. Kin gani dai akan idanki yanda tana zuwa tashige garesa kai tsaye... Kiyi hakuri Idan kuka koma gida kyayi mata fad'an yanda ranki kesu... Amma bawai kitsaya nan kina mata fad'a ba.. Gaskiya kiyi gaba karki jawo mana fishin boka. Dan kaf bokayan garinnan ba Wanda baisan TAUDHAT ba. Gata kyakkyawa. Gata karuwa. Gata me San kud'i. Gata mesan maza. Gata mebin bokaye... D'aya daga cikin matan wajen ce ta katse NUFAISAT da fad'in hakan.. Jin hakan yasa ran NUFAISAT qara b'aci. A zafafe ta tafigge makullin motarta tashige cikinta da sauri tatadata saiji kake jinnnnn nananana...😰 ta figi motar kamar zata tashi sama.. Kowa awajen sanda ya tsorata da yanda tatashi motar... Tab'e baki TAUDHAT tayi ganin tafiyar NUFAISAT d'in... Cikin nuna rashin damuwa haka ta fad'a cikin bukkan tana me kallan bokan nata zatayi magana ya d'aga mata hannu da nuna mata wani turare yana cewa.. "Kawai kwanta najiki da kyau.. Ba musu TAUDHAT ta cire kayanta da kwantawa gefansa.. Nan suka aikata masha'arsu Wanda tad'aukesu awanni.. Sanda yayi yanda yakesu da Ita San ransa. Kana ya barta da bata turaran yana me gaya mata tasan yanda zatayi tasa ADAMCY ya shaqi ƙamshin.. Yana tabbatar mata da lalle Idan ADAMCY ya shiqi ƙamshin ko alokacin Idan tayarda saiya aureta ba makawa... Dariya TAUDHAT tayi damai godiya zata ajiyemai kud'i yace tabarshi yayi mata abin kud'inta... Haka TAUDHAT tasaka kayanta da barin dajin zuciyarta tam cike da farin ciki.... Muje zuwa masu karatu.. Auntyn luv takuce [6/11, 11:56 AM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 08☆ Da mutuƙar ɓacin rai NUFAISAT ta jefar da gyalanta akan kujer falan nata.. Nan tahau zaga ɗakin tana me cije leɓe da tunano abinda ya faru tsakaninta da TAUDHAT.. TAUDHAT ta yaudareta.. Yaushe TAUDHAT ta lalace haka.. Yaushe tunaninta ya juye haka. Yaushe al'amuranta suka canja haka.. "Hmm mutum kenan.. Ta furta hakan abayyane tana ƙoƙarin zama.. Saidai kanta idda zaman nata. Zainab yayarta tashigo falan da sallama... Aiko da sauri taje ta rungumeta tana me fashewa da kuka. Faɗi take... "Ashe haka mutum yake Aunty Zainab.. Ace kaf mutanan duniya arasa wacce zata yaudareni sai TAUDHAT... "Ke waime yake faruwa ne.. Zainab ta tambayeta hankali tashe lokacin da tasamu nasarar zaunawa kan ɗaya daga cikin kujerun falan tare da ita... Babu ɓata lokaci nan NUFAISAT ta kwashe duk abinda ya faru tsakaninta da ADAMCY daran jiya da yau da safe.. Sannan taƙare da bata labarin abinda ya wakana tsakaninta da TAUDHAT.. Shuru Zainab tayi cike da mamakin komai.. Ta tausayama ƴar uwar tata Dan tasan kishiya da zafi take.. Sannan tasha mamakin TAUDHAT matuƙa Cikin wani hali ta dubi ƴar uwar tata tace.. "Kwantar da hankalinki sister.. Kishiya ba abar tada hankali bace.. Musamman idan kika yarda da kanki.. Nasan tunanin dazai fara ziyartar kwakwalwarki duk lokacin da kika tuna za'ayi miki ita.. Shine baki haihu ba. Kina tsoran kar mijinki ya wulaƙantaki.. Kina tsoran kar sanadin hakan kishiyar ta rainaki.. NUFAISAT karkisa tunanin ko ɗaya daga cikin waƴannan aranki. ADAMS ba irin waƴannan mutanan bane.. ADAMS bazai taɓa wulaƙantaki ba.. B'cos yana miki wani so. Wanda yafi ƙarfin akirasa da MASEEFAR SOOH.. Zaiyi Auran ne dan mahaifansa badan ya gaji da ƙaddarar da Allah yasaukar miki ba... Kiyi nazari. Kiyi tunani. Ki nutsu kiyi amfani da iliminki wajen kishin da yake shirin tumfaroki. Kiyi hakuri kamar yanda mummy ɗinmu tayi lokacin da Dadynmu ya qara Aure.. Amatsayina na ƴar uwarki.. Zan nemi wata alfarma daga gareki.. Karki ƙara kaima wani kukanki imba Allah ba.. B'cos ba abinda wani zai iya yimiki akan abinda Allah ne ya lamince musu da suyi.. Nasanki da ibada. Toki dage wajen gayama Allah buqatarki kamar haka.... _ALLAH KAINE ALLAH. ALLAH BA WANI SARKI A BAYAN KA ALLAH. ALLAH NA ROK'EKA IDAN WANNAN AURAN ALKAIRI NE AGARENI DA MIJINA ALLAH KA TABBATAR DA ALKAIRIN.. ALLAH IDAN BA ALKAIRI BANE AGAREMU ALLAH KA HANA YUHUWARSA. ALLAH IDAN YA KASANCE SAI ANYI. ALLAH KADUBENI DA FUSKAR RAHMA. KAYAYEMIN KUNCI DA BAQIN CIKI DA TASHIN HANKALI DA DAMUWA. BAMA NI NASAN KA YAYAEMIN BA. KOWA DA NAKE TARE DASHI YA SHEDA HAKAN. ALLAH KA DORANI AKAN MIJINA DA ABOKIYAR ZAMANA. KA HANA MUNAFUKAI DA MAHASSADA SHIGOWA CIKIN AL'AMURANA DA MIJINA DA ABOKIYAR ZAMAN TAWA.. ALLAH KA MALLAKAMIN MIJINA. KA HANESA KUNTATAMIN KAHANESA WULAƘANTANI KA HANESA AIKATAMIN ABINDA ZAISA MAQIYANA SUYIMIN DARIYA. ALLAH NABAKA AMANAR KAINA. DA DUK WANI ABU DAYA SHAFI RAYUWATA. KA KYENTANI FIYE DA WANNAN BAIWAR TAKA DA ZAKA HAD'ANI ZAMA DA ITA..._ Sister ki dage da wannan addu'ar karki qara yarda da wata qawa arayuwarki.. Batun TAUDHAT idan tazo gareki. Karki nuna mata kin canja mata matsayi afuskarki. Nuna mata tabi Allah. Tadena aikata duk wani abu da wannan matar tagaya miki akanta... Daga nan saikice mata daga yau ba'ita bake.. Karki kuskura ki qara qawance da TAUDHAT.. Nagaya miki.. Share hawayenta NUFAISAT tayi da kama hannun yar uwar tata tace. "Insha Allah Aunty Zainab zanyi duk abinda kikace min.. Nagode ma Allah daya bani ƴar uwa kamarki. Kin bani shawarar dazata kaini ga hanyar dacewa.. "Yauwa ƴar uwata.. Ki sama zuciyarki hakuri da dangana. Komai yayi farko zaiyi qarshe kinji Gyaɗa mata kai NUFAISAT tayi alamum amsawa... Haka dai Zainab tadinga kwantarma da NUFAISAT hankali har NUFAISAT ɗin tafara tunanin toh kishiyar tazo mana mezata tare mata..😀 Nan Zainab tatayata abincin ranah wanda za'a kaima ADAMS d'in. Ta koya mata wasu qananun abubu na girkin saboda yamma tayi tana San tafiya gida... Ba qaramin farin ciki sosai NUFAISAT taji ba. Lokacin da mijin nata ya kirata awaya yana nuna mata farin cikinsa na yanda yaji dad'in abincin da ta aikomai Da misalin qarfe shidda ne TAUDHAT tafesa wankanta me matuƙar kyau. Ita kanta bata buqatar ace mata tayi kyau dan da gasken gaske tayi kyau d'in.. Cikin jar atamfa me ratsin blue. ɗinkin doguwar riga me bajajjen hannu irin na yara ƴan zamani.. Sosai ɗinkin ya karɓi jikinta abinka da farar mace.. Nan tafeshe jikinta da turaran da boka yabata. Kana tad'auki jakarta da gyalanta ko kallan mahaifiyarta batayi ba tasaka takalminta taficce daga gidan sai gidan NUFAISAT... Dake lokacin NUFAISAT take sakaran dawowar ADAMSY kasancewar lokacin lokacinne lokacin dawowawarsa. Hakan yasa take fes da ita kamar yanda tasaba kimtsa kanta kan lokacin dawowarsa.. Tana zaune kan ɗaya daga cikin kujerun falan nata TAUDHAT tashigo da sallama murya a sanyaye... D'auke kanta NUFAISAT tayi bayan ta amsa mata sallamar.. Amunafunce TAUDHAT tazauna tana me fuskantar NUFAISAT d'in cikin sanyin murya tace.. "Nasan da cewa ban kyauta miki ba. Ina neman gafararki. Dan Allah kiyafe min. Hakan baza taqara faruwa ba. Wallahi nayi miki alƙawari.. Ahankali NUFAISAT ta kalleta da cewa... "Karki nemi gafarata TAUDHAT. Kije kinemi gafarar Allah. Dan nasan kinfi sab'a mishi fiye dani.. Nasani kin sani.. Dan haka kiji tsoran Allah ki koma garesa kidena aikata duk abinda wannan matar tafad'a min akanki. Ki tuba ki koma ALLAH. Allahn yasa mu dace gabaki d'aya amiin... "Nagode NUFAISAT. Kuma insha bazan qara aikata ko d'aya daga cikin abinda kikaji ba.... TAUDHAT tace da ita hakan... Kan NUFAISAT tayi magana saiga ADAMCY ya shigo falan da sallama... Da wani yanayi NUFAISAT taje ta rungumesa tana me nunamai farin cikinta naganinsa da tayi Gaskiya ADAMS yaji dad'in hakan. Kasancewar bata saba yimishi hakan agaban TAUDHAT ba.. Yana San tadinga bashi kulawa agaban kuma waye ba wai TAUDHAT bama.. "Wow uwar gidana. Kinga yanda kika tafi da zuciyata kuwa.. "Hmm.. aikai LEEKITAN ZUCHIYA ne. Tunda natafi da ita. Sai kasan yanda zakayi kadawo da ita.. Lakuce mata hannu yayi cikin matuƙar farin ciki yace.. "Abubuwa biyu sun sauya daga safe zuwa yanxu.. "Toya zanyi da raina💋. Tunda na ɗaura ɗammarar bama megina dukkanin abinda zai sashi farin ciki... Qara rungumarta yayi cikin so da k'auna... Kana yaɗan zareta kaɗan daga jikinsa ya kalli TAUDHAT tare da sakar mata murmushi yace. "Yau qawarki ta shareki takulani ko. Murmushin itama ta mayar masa da cewa.. "aidama abinda yadace dani kenan Idan dai kana cikin gidan nan... Tafadi hakan da tashi tana me sab'a jakarta ta ƙaraso kusa dasu yanda ADAMS zai shaƙi ƙamshin tana. Tana meci gaba da cewa.. Nizan tafi.. "Tofah🤔 yau bazaki bari ya rage miki hanya ba.. Cewar NUFAISAT Kan tayi magana sai ADAMSY Wanda kansa yayi masa wani dum kasancewar ya shaqi qamshin turaran na TAUDHAT. ya sakarma NUFAISAT kiss awiya. Wanda yasata qanqamesa a lokaci d'aya kuma ta kallesa. Yace.. "Barta tatafi sweetheart. Yau bazan rage mata hanya ba. Kasancewar tasaka wani turare mara dad'i. Saidai duk da hakan yana tab'a ZUCHIYA.. Yana aika mata da wani saƙo. Sakwan da yake barazanar tarwatsata... Azahirin gaskiya idan nace zan d'auki lokaci ina shaqar qamshin. Ba makawa komai zai iya faruwa da ZUCHIYATA... Afurgice NUFAISAT tazare jikinta daga nasa. Taqara tsaida idanta akansa sosai tace.. "Ba wani saƙo dazaiyi barazanar tarwatsa ZUCHIYARKA idan har banice nabaka wannan sakwan ba.. Mezaisa kaji hakan daga TAUDHAT.. Taɓe baki yayi tare da kallan TAUDHAT ɗin ya maida kallan nasa kanta yace.. "Bansan me zance miki ba. Kasancewar yau nafara jin hakan. Kuma.. "Kuma me.... Sannan meyasa kaji hakan... NUFAISAT ta katseshi da faɗin hakan cikin sauri.. Da wani hali Yakama hannunta da cewa.. "Nima ban sani.. Ya kamata kiyi wani abu akai. Dan yanayin yana qara shigata sosai fah.. Saurin kallan TAUDHAT tayi wacce kawai tayi saƙale tana kallansu kamar bata gane me suke cewa ba tace da ita.. "TAUDHAT kificce daga falan nan kije gida kawai sai nazo. Dannafi buqatar daidaituwar ZUCHIYAR MIJINA fiye da tsayuwarki anan... "Laaa😦. Karki damu!.. Wata ranah nidake zamu daidaita zuciyar inda muna raye.. TAUDHAT na faɗin hakan taficce daga falan zuciyarta tam farin ciki. Dan tasan tunda ya shaqi qamshin. Kuma ya magantu akan qamshin tasan yarigada ya shigo hannu... Saidai tatsorata sosai ganin bai rikice ba Dan tatab'ama wani alhajinta shigen irin hakan. Alhajin na shaqar qamshin. Nan take ya rikice mata.. Tobataga hakan agun ADAMCY ba. "Hmm. indai kere na yawo zabo na yawo wata ranah zasu had'u.. Tafad'i hakan abayyane lokacin da masu gadin gidan suka bude mata get d'in gidan danta fitta.... NUFAISAT ta kalli ADAMS tace.. "wai me TAUDHAT take nufi da wannan kalmar na zumu dai-daita ZUCHIYAR nida ita. Janta ADAMS yayi izuwaga shashinsa yana cewa.. "Ki kula dani awannan lokacin yafi ki tsaya kina min wannan wawiyar tambayar... Shuru NUFAISAT tayi kawai bayan sun kasance a bedroom nasa tana me tayasa cire kayan jikinsa dan yashiga wanka... Muje zuwa. Rahma nalele ce🧕🏻 taku ƴan hannuna...👐🏼 [6/11, 11:57 AM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 9☆ Bayan ya fitto ya tarar da kayan data fito mai dashi na bacci Doguwar rigace dai me santsi. Sanda ya feshe jikinsa da turare da mayika kana yasaka da gabatar da sallar magrif saboda lokacin da ake kira har akayi sallar yana wankan. Sanda ya sallame sannan ya fitowa falan yana me wurga ido alamun nemanta. Aiko can ya ganta kan dining tayi dagumi kawai alamar tana cikin wani hali. Rungumarta yayi ta baya batare dayace komai ba. Can data samu nutsuwa daga d'uminsa saita kama hannunsa ta zaunar dashi kan d'aya daga kujerun wajen wacce yafi zama akanta. Ta had'a mishi komai na abin data girka masa tare da zuba nata ta zauna idanta cikin nasa tace. "Ina fatan wannan yafi na d'azu dad'i. Murmushi yayi tare da cewa. "Ai daga ganinsa zaifishi dad'n. Musamman idan nayi duba da yanda yaketa zuba qamshin nan. Murmushin jin dad'i tayi da fad'in. "Saidai kamin afuwa abisa Kalmar daka fad'i d'azu. Na wai karna qara bari wani yasamin hannu akan abinda zakaci. Wallahi duk aunty Zainab ce tasamun hannu daga na d'azu harna yanxu da zakaci "Karki damu matata. Saida nayi furucin nagane dole sai ansaka miki hannu kafin nasamu yanda nakeso. Murmushi tayi dad'an duqawa ta sakar mai kiss agoshi tace. "Nayi maka alqawari mijina. Daga aunty Zainab ba wacce zata dinga samun hannu akan abinda zakaci. Ita d'imma nawani d'an lokaci ne. Dantace 2 month kawai zata d'auka tana koyamin Murmushi yayi shidai yana San matarsa. A hankali yace mata. "Allahma yasa ki iya a 1 month kawai.. "Insha Allah zanyi qoqarin iya duk wani abu Wanda nasan zai dace dakai Wanda zaka soshi. Ka qaunaceshi. Kaji dad'in shi koda a 1 month d'inne Yaji dad'in furucinta sosai. Hakan yasa yace mata idan tagama taje ta canja kaya. Tace ina zasu. Yace yau rakiya zatamai zuwa gidansu dady amman saiya dawo daga sallar isha kannan ma itama tayi sallar.. Toh tace mai tare dajin wani mafificin dad'i saboda yanda yake kod'a abincin yana nuna mata santinsa azahiri danya qara qarfafa mata gwiwa Haka daya dawo ya d'auketa basu zame ako ina ba sai'a gidansu. Nan masu gadin gidan suka hau zubewa kamar yanda suka saba wajen girmama shi Yayi musu kyauta me tsoka inda suka dinga saka mai albarka. Anan babban falan gidan suka tarar da Dadyn nasa da Amminsa harda Hajjiya Rukayyat da Salim Nan suka sube suka shiga gaishesu. Da farin ciki Dady da Amminsa suke amsa musu. Banda Hajjiya Rukayyat. Dan dama haka abin yake awajenta. Idan har Ammin ADAMS ce da girki bata sake fuska a wannan ranah. Dukko da cewar rabin lokacin nata ne.. Salim ya gaida Adams da NUFAISAT. Suka amsa da kulawa. Sannan Dady ya qara tsaida idansa akan Adams yana cewa. "Sannu ADAMS kunzo lafiya? "Eh Dady dafatan muma mun sameku lafiya. "aa lafiya lau lau. Yanxu nake maganarka kuwa da d'an uwanka Salim. Ashe kana kan hanya. "Eh Dady. Allah yasa ba lefi nayi ba. ADAMS ya fad'i da murmushi cikin wasa. Murmushin shima Dady yayi da cewa.. "Bakayi komai ba. Kawai hirar taka tazo ne. Nayi farin cikin yanda kazo min da NUFAISAT. Dan dama ina San mata magana akan Auran dana saka kayi. Murmushi ADAMCY kawai yayi Dady ya numfasa da kallan NUFAISAT yana me cigba da cewa. Kiyi hakuri NUFAISAT. Bawai zai qara Auran bane danke. aa zai qarane sabodani. Nasan kina da nutsuwa da hankali koda abin ya faru bazaki kawo wata matsala ba. Tuna hakan danayi shiya bani qarfin gwiwar ce mishi yayi. Allah yayi miki albarka ki dage da addu'a idan kina da rabo Allah yabaki me albarka.. Qara sunkuyar dakai NUFAISAT tayi cikin ladabi tace.. " Dady ba komai insha Allah baza'a samu matsala daga gareni ba.. Murmushi Dadyn yayi cikin jin dad'in furucinta yace. "Allah yay miki albarka "Ameen tace. Ammi tadafa kanta cikin jin dad'i tace. "Nagodema Allah daya bani sirika me hankali. Me kaifin tunani. Allah ya dubeki yabaki masu albarka. Kwantar da kanta NUFAISAT tayi kan cinyar Ammin tana cewa amiin Ammina... Tsaki Hajjiya Rukayyat taja tare da tashi tana kallan NUFAISAT tace da ita. "Kizo falo ki sameni Inasan magana dake. Tana fad'in hakan tabar falan afusace. Jiki asanyaye NUFAISAT takalli mijinta Adams Ya gyad'a mata kai alamar taje. Nanko tatashi tabi bayanta inda tataddata afalan nata tana zagaye. "Momy gani. (Dake haka suke kiranta dashi ) Da sauri Hajjiya Rukayyat takalleta da cewa. "Ke wata irin shashashace. Waya gaya miki kishiya dad'ine da ita. Kishiya ba'abokiyar zama bace abokiyar gabace. Karki kuskura ayi miki ita. Banda sakarci irin naki wata macece me hankali zatayi abinda kikayi. Ko'an gaya miki so haukane. Wallahi kika yarda Adams yayi Aure kashinki ya bushe agunsa. Bar ganin yanxu yana wani nuna miki so yana samun d'a daga wajen wata zaifara wulaqantaki yaga toke amfanin me kike masa daga qarshe ya turaki gidanku da farar takarda na saki.... Da sauri NUFAISAT takalli Hajjiya Rukayyat cikin matuqar tsoro. Itako ta gyad'a mata kai alamar tabbatarwa. Gaban NUFAISAT yashiga fad'uwa ganin halin data shiga yasa Hajjiya Rukayyat cigaba da cewa.. Wallahi kima kanki qiyamal lalli kisan duk hanyar daza kibi kibi dan hana wannan Auran tabbatuwa. Idan kin kasa kizo zankaiki inda za'a share miki hawaye. Gumi NUFAISAT tagoge da mayafinta tace da ita. "Toh momy zanyi tunani nagode.. Tana fad'in hakan taficce daga falan da sauri ta fad'a falan Ammi tazube kan ɗaya daga cikin kujerun falan tana maida numfashi kamar wacce tayi gudun falfalangi. Itako Hajjiya Rukayyat murmushin mugunta tayi tare da cije leb'e tana rayawa aranta wata qila ta'iya cin galaba akan NUFAISAT. Danta hango tsoro muraran akwayar idanta... Murmushin jin dad'i tayi tare da gyad'a kai tashige bedroom d'inta Suko su Dady da Ammi da Adams da Salim hira suka b'arke da ita sosai duk akan halin NUFAISAT ne Wanda suke ganin da wiya yasamu mace me hankalinta. Sanda goma tayi Adams yama Dadynsa sallama sukafito daga falan shida Amminsa Sunyi mamakin ganin yanda lokaci d'aya sukaga canjawar NUFAISAT. Danga damuwa muraran akan fuskarta har wani gumi take. Ahankali Ammi tazauba dab da ita tare da dafata tace. "Y'ata meya sameki kike cikin damuwa haka. Shuru NUFAISAT tayi mata. Ganin hakan yasa Ammi murmushi tacigaba da cewa. Wato Rukayyat ce tajefaki cikin wannan halin ko. Ahankali NUFAISAT ta gyad'a mata kai tare da rushewa da kuka.. Ammi bata tambayeta miye ba. Amman tayi kokarin rarrashinta har tasamu tayi shuru. Sannan tayi mata nasiha akan taguje sakama zuciyarta zancikan da zasu dameta gudun kar wata ranah tasamu babbar matsala da ita. Kuma duk abinda zataji akan sharhin da za'a mata kan matsalarta taji tsoran Allah wajen yanke hukuncin daya dace da ita. Godiya sosai NUFAISAT tama Ammiin sannan Ammin tabada turare suka mata sallama da barin gidan Shuru haka suke tafiya amotar bame magana acikinsu har suka iso gida. Wajen baccinsu ne anan Adams ya kasa jurewa ya rungumeta yana tambayarta me momy Rukayyat tagaya mata Wanda yasata shiga cikin wani hali haka. To dama bawai tagama kukan nata bane agidansu dan haka saita qara b'arkewa da kuka wiwi Cikin rikicewa yahau lallashita yana cewa tunda batasan cewa komai to tabar kukan haka ya ishesa. Bata dena ba. Sanda ya had'e bakinsa da nata yahau aika mata da wani shu'umin kiss da wasu sakwanni kana tadena kukan tahau manne masa dajin dad'in yanda yake aika mata da sakwannin Can da suka samu nutsuwa saita fara cewa. "Dan Allah mijina kamin aikin gafara kai kad'ai nake so. Nake ji. Nake qauna. Nake fatan kasancewa dakai har agidan Aljanna. karka wulaqantani kamar yanda momy Rukayyat tace zakamin. Tace min zaka wulaqantani dazaran kasamu d'a daga wata mace badaga gareni ba. Sannan zaka korani gidamu da farar takadda na saki saboda lokacin zakaga bani da amfani agareka. Idan hakan ta kasance agareni mijina hauka zanyi. Wallahi mijina harkacewa zanyi. Dan Allah kamin aikin gafara karka bari zuciyarka taraya maka hakan ko'a mafarki ne bare a zahiri. Wallahi sanka nake irin dayawa d'in nan. Murmushi yayi da qara maqaleta jikinsa yana me shafa kanta cikin soo da qaunarta. Yasani Hajjiya Rukayyat ta tsoratata da yawa. Gashi ita bata iya shiga damuwa da tsoro ba. Gaskiya Allah ya sakama matarsa dan tacutarmai da ita cikin lokaci qanqani. Da sanyin murya yake cemata... "Ki kwantar da hankalinki matata. Bana d'aya daga cikin waƴannan mazajen da suke aikata hakan ga Uwargijayensu. Wallahi NUFAISAT idan aka cire mahaifana bani da wani sauran abin so arayuwata kamarki. Hatta haihuwan bata shigeni ba kamar yanda qaunarki tashigeni. Dan Allah kibar ZUCIYATA tasamu nutsuwa wallahi bazan tab'a wulaqantaki cikin hankalina ba. Dan bana tunanin zan qaunaci wata mace kamar yanda na qaunaceki. Saidai kinsan d'an Adam agizine koda hakan tafaru dani agaba karki zargeni kimin uziri dan Allah... Zatayi magana ya hanata maganar saboda aika mata da yayi da wani sakwan na soyayya... NUFAISAT tana qaunar qaunar mijinta irin sosai d'innan Shiyasa tsoro yake kama zuciyarta idan aka kawo mata batun rabuwa dashi. Haka Adams ya raya mata wannan daran da bata farin cikin da ita kanta sanda tayi mamaki Danji tayi kamar aranar yafara Love da ita❤ Itako TAUDHAT tana zuwa gida tacire kayan jikinta dan itama kanta turaran na bokan nata ya isheta. Dan bashi da dad'i da gaske kamar yanda Adams yace Wanka taqarayi dayin sallah kana tamiqe agadanta tare da fad'awa tunanin gata a qirjin ADAMCY..... Nanko take ta lumshe ido tare da rungume filo cikin San kasancewa a yanayin. Bata d'auki lokaci tana tunanin ba wani Alhajinta ya kirata akan yana San kwana da ita. Aiko tana jin hakan tadiro daga gadan nata da zarar jakarta da key na motarta tacema mahaifiyar tata bazata dawoba sai gobe. Bata jira cewar mahaifiyar tata ba taficce abinta. Haka uwar tabita da kallo tana me addu'ar Allah ya shiryar mata y'ar tata ya kuma cire mata tsoranta dan tasamu damar yanke mata akan abinda takeyi kamar yanda kowace uwa tagari takema y'arta. Rahma Nalele ce Y'an hannuna 🤝🏻🧕🏻 [6/21, 12:22 AM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 10☆ Washe gari da cikakken farin ciki Adams ya yabar gidan nasa. Kasancewar yabar matar tashi da farin ciki. Da misalin qarfe biyu ne na ranah Adams da abokinsa Yusuf suke tare cikin ofishin Adams d'in. Abincin da NUFAISAT ta'aikuma da Adams d'in suke ci Sai Adams yake ma Yusuf bayani akan Auran da yake San qarawa. Yusuf ya qara tsaida kallansa akansa da murmushi Yace.. "Toh yanxu ta ina zaka fara. Bayan nasan NUFAISAT ita kad'aice madubin dubawarka. Bayan ita ba wata wacce kake da ita afannin so. Yanxu ta ina zaka fara kenan Shafa kansa Adams yayi da murmushi Yace. "Da wai na yanke shawaran Auran TAUDHAT. Kasan cewar itace tasan NUFAISAT fiye da kowa. Ba wani abu dazata mata wanda zai zama na Allah wadai. Sannan ita kanta NUFAISAT nasan hankalinta zaifi kwanciya da TAUDHAT d'in. B'cos tana Santa sosai na tabbatar zan iya samun zaman lafiya agidana tunda sunsan kansu. Shuru Yusuf yayi cikin nazari yana tuna yanda TAUDHAT da NUFAISAT suke. Tabbas Auran TAUDHAT shine abinda ya dace da Adams. Kasancewar TAUDHAT tafi kowa sanin NUFAISAT. Kuma zasu iya samun zaman lafiya me d'orewa. Saboda suna San junansu. Kuma sun taso ne tun yarinta. Kallan Adams Yusuf yayi da cewa. "Gaskiya kam ka Auri TAUDHAT. Saboda na tabbatar bazata cutar da NUFAISAT ba. Saboda kaga yanda suke qaunar junansu. Sun taso tun yarinta. Kuma kowa yasan halin kowa. Sunsan abinda in sukama junansu zai b'ata musu rai. Haka sunsan abinda idan sukama junasu zai faranta ransu. Ka aureta kawai. Murmushi Adams yayi da cewa. "Nima abinda na duba nagani kenan.. "Gaskiya kayi tunani me kyau Amman wani hanzari ba gudu ba. Shin ita TAUDHAT d'in tana sanka kuma zata amince da hakan kuwa. Jan numfashi Adams yayi da cewa. "Hmm ai nadad'e ina hango qaunata cikin kwayar idanta. cikin dariyar Yusuf yace. "Lalle kace zata fad'o hannu. "Sosai ma kuwa. Adams ya bashi amsa cikin sauri. Girgiza kai kawai Yusuf yayi dacigaba dacin abincinsa dan yafi kowa sanin irin farin jinin da Adams yake dashi agun jama'a. Maza nasu San daban haka mata nasu San daban Yusuf abokin Adams ne tunna k'uruciya. Yawancin halaiyar Adams Yusuf yana dasu. Hakan yasa Adams yafi yarda da Yusuf fiye da kowa a cikin abokanayansa. Haka shima Yusuf d'in ya yarda da Adams fiye da kowa Yusuf yana kyau hankali da nutsuwa san soyayya. su biyu ne iyayansu suka haifa shi da qanwarsa Nazifa. Iyayansu sun rasu sun suna qanana. Hakan yasa suka tashi a qarqashin kulawar kakarsu Hajjiya Delu. Saidai iyayan nasu sun tafi sun bar musu dukiya me tarin yawa.. Dake Yusuf d'in kasuwanci ya karanta sai kawai ya karb'i dukiyar tasu gun qanin babansu yahau juya musu ita. Sosai Adams yake qara bashi haske akan kasuwancin. Duk da shi karanta yayi Amman Adams ya fishi wayewa akai. A yanxu dai Nazifa qanwar Yusuf d'in tana secondary skull. A islamiya kuma takusa yin sauka. Yusuf yana ji da ita sosai. Yana Santa sosai. Hakan yasa yaqi yin aure da wuri saboda yana San yasami mace tagari wacce zata kulan mishi da qanwar tasa tasota ta qaunaceta dan Allah Wannan dalilin yasa yaketa gwada mata da nuna musu yana matuqar ji da qanwarsa dazaran yaga kin fara nuna masa wani hali akanta na yanda yake nuna miki kulawarsa akanta. Toh nan take zai rabu dake. Har yanxu a haka yake. Wannan shine labarin Yusuf a takaice. TAUDHAT ko sun tsula tsiyarsu sosai ita da Alhajin nata. Dan bai barta ba sai kusan sha biyu na safiyar yau. Bata koma gida ba sanda tabiya supermarket tayi sayayyanta dan ba qaramin kud'i ta cajesa ba A haka takoma gida da kaya niqi niqi. Naci dana sawa dadai sauransu Ita dai mamah mahaifiyarta ido ne kawai nata akanta. NUFAISAT ko Auntynta Zainab na tare da ita tana qara ganar da ita tafannin girki. Dan yanzuma da daddare wani kayataccen girki take had'ama megidan nata. Bayan TAUDHAT ta huta wanka tayi tanufi gun bokan nata tazayyane masa abinda ya faru tsakaninta da Adams wajen jin qamshin turaran da yaji. Wai tajishi shuru bai nemeta ba. Anya turaran ya bigesa dakyau kuwa. Dariya bokan ya sheqe mata dashi yana me cewa. "Ai ina tabbatar miki tunda ya sheqa saiya aureki. Kuma ga ranar Auran naku dashi nan. Ya shafi gefansa dawani abin shed'anancinsa. Aiko muraran saiga TAUDHAT da ADAMS cikin d'aki d'aya. Tana zaune kan gado shima yana gefanta. Da lillib'i akanta irinna amare. Aiko ganin hakan yasa TAUDHAT fashewa da dariya tace. "Ina sanka boka. Dan aikinka nakyau. Yanxu yaushe zaizo gareni. "Ai kisha kuruminki kawai cikin daran nan zaki gansa. Godiya tamai sosai bayan ya d'anata ta karkad'e jikinta ta koma gida da matuqar farin ciki yau Adams zaizo gareta. Sai farin ciki NUFAISAT take ganin yanda yake nuna santinsa akan girkin nata. Tace. "Yau fa nakai awanni ina had'a komai. Ba mamaki shiyasa yau santinka yafi na jiya. Murmushi ya mata cikin so da qauna yace. "Allah ya dad'a miki albarka matar aljannah. "Amiin mijina Bayan yagama ne tana kan ciyarsa yake ce mata. "My luv kinsan wacce na yanke shawarar Aura. Girgizamai kai tayi kuma da sauri tace. "aa. Sannan bana San nasan kowacece tunda dai auranta zakayi ai dole nasanta. "Nasan zakiyi farin ciki da ganinta. Saboda kina qaunarta kuma.. "Haba mijina. Dan Allah kabar batun haka. Dan zuciyata tafara rawa. Karka b'atamin farin cikina. Murmushi yayi da kama fuskarta yace. "Har abada bazan tab'a b'ata miki farin cikinki ba matata. Kiyarda dani Kwantar da kanta tayi akan kafad'arsa tace "naji ana kiran sallah in tashi maka daga kan cinya ko. "Eh. Amman daga masallaci zan wucce wajen qanwar taki kina da sak'o gareta Wanda zan bata ne. "Aa Saidai kagaya mata ina gaisheta. Sannan ta kulammin dakai sosai. Idan tabari kadawo min gida rai ab'ace saina hukuntata. "Insha Allah ko zan gaya mata. Haka NUFAISAT tatashi daga jikinsa ya sakar mata kiss da rungumarta kana ya ficce daga falan. Tana jin fitarsa wajen get hawaye ya zubo mata. Ahankali tace "baka iya yimin qarya ba mijina. Sannan wannan gaskiyar da ciwo take. Zan iya jure komai arayuwata amman bazan iya jure ganinka da wata ba. Tana kaiwa qarshen zancen nata tarushe da kuka wiwi. Harda d'aga hannuwanta ta d'ora aka tana me cigaba da cewa.. Wayyo Allah mijina aure zaiyi. Mijina kishiya zaiyimin. Mijina yau ya tafi zance gun wata. Dan Allah zuciyata kimin adalci kidena jin wannan zafin da rad'ad'in nan ki sake kibarni na huta dan wata rana bama zance ba wallahi raba shinfid'a zanyi dashi...... Haka NUFAISAT ta dinga sambatu ita d'aya. Daga qarshe dai tayi toilet tayo alwala ta gabatar da sallar i'sha tare da kaima Allah kukanta akan ya cire mata damuwa da kishi akan Auran mijin nata Da gaske Adams daga masallaci gidansu TAUDHAT ya nufa. kunsan dama a kintse TAUDHAT d'in take. Tunda bokanta ya tabbatar mata da zuwan Adams gareta cikin daran Dan haka tana ganin wayarsa tamiqe jikinta na rawa ta d'auka da cewa. "Ina maka fatan ALKAIRI mijin k'awa. Da murmushi Yace "Tare dake. Ina ƙofar gidanku Allah yasa ina da raban ganin kyakkyawar fuskarki. "Mezai hanaka gani. Bayan nida qawata duk mallakinka ne. "Insha Allah kuwa. Zanso dai naganki yanxu kafin kicinye min lokaci na awaya. "To kakashe mana. Daka juyo da fuskarka izuwa ƙofar gidamu daka ganni katabbbatar bazan cinye maka lokaci ba. Murmushi yayi bayan ya juya ganinsa ga kofar gidan nasu nanko ya gantan a kofar gidan. Hakan yasa ya kashe wayan. Dayi mata nuni data shigo cikin motar. Ba musu tashiga gaban motar tana me kallansa da cigaba da cewa. Nasan dai ba abinda zai kawoka ƙofar gidamu adaidai wannan lokacin imba wani abu me mahimmanci ba. Allah dai yasa qawata tana lafiya. Danna farajin fad'uwar gaba. "Ai dole kiji hakan. Dan kina San aure mata miji. Wato TAUDHAT Nazo miki da wata magana me mahimmanci. "Kafin ka Sanar min da maganar ina San naji batun lafiyar qawata. Dan wallahi da gaske zuciyata tasaka tsayuwa waje d'aya. Sannan meyasaka cemin zan aure mata miji. "Tana cikin k'oshin lafiya. Dan tacemin mah in gaya miki ki kula dani sosai. Dan idan nakoma mata gida rai b'ace saita hukuntaki. "Masha Allah. Naji dad'in yanda take cikin koshin lafiya. Batun zan aure mata miji fah. "Shine ya kawoni. Kuma ina San kima abin kyakkyawar fahimta. NUFAISAT tafi saninki fiye da kowa arayuwarta. Sannan tana sanki fiye da kowa a qawayenta. Hakan yasa nazo da k'okwan barana akan kiyarje min na Aureki matsayin matata ta biyu dan nasan idan kece kika zamo kishiyarta bazaki tab'a bata matsala ba. Amma fa idan kin yarda dan babu dole aciki. Kawai farin cikin matata nake nema. Jan numfashi TAUDHAT tayi kamar gaske tace. "Idan har dai NUFAISAT ta amince zan aure ka Adams. Saboda katara duk wani abu da y'a mace take fatan samu agun mijin auranta. Ina sanka Adams. Amman dan qawata nake sanka. Inasan inciga da raya mata wannan San nata acikin zuciyarka. Dan bana sha'awar wata can tazo ta b'ata mata gininta.... "NUFAISAT bata San ke nayanke shawarar aura ba. Bare har aje batun amincewa. Taqi bani damar na gaya mata hakan. Hakan yasa ban takurata ba. Dan nasan idan taganki matsayin abokiyar zamanta zataso hakan kuma zatayi farin ciki sosai. Murmushin mugunta TAUDHAT tayi dayimai wani kallo qasa qasa tace.. "Idan ko haka ne nayarda da Auran ka. Ko yanxu kace a d'aura wallahi nabaka goyan baya. Murmushi yayi da cewa. "Ina San kiyimin iso wajen mama acikin daran nan Haka ko tamai iso wajen mama. Hankalin mama ya tashi sosai da buqatar da Adams yazo mata dashi. Dan tanuna mai hakan bai dace ba sam. Bai dace ya Auri TAUDHAT ba kuma yana Auran NUFAISAT Nutsuwa sosai Adams yayi yabata hujjojinsa nasan yin hakan kafin tayarda. Sun yanke shawarar limamin unguwar shi zai bada Auran TAUDHAT d'in. Kasancewar basa da kowa masu ganin mutuncinsu Adams yaji dad'i sosai. Dan haka acikin daran bai duba qurewar lokaci ba ya nufi gidansu. TAUDHAT Adams na fitta ta rufe mahaifiyarta da masifa wai akan me zata nunama Adams bai dace ya aureta ba Wannan wane irin baqin ciki take mata. Ita dai mama shuru tayi mata hakan yasa ta qare mata rashin kunya ta nufi d'akinta da mafificin farin cikin burunta ya kusa cika Adams ya tadda Dadynsa na qoqarin kwantawa. Anan ya zayyane masa komai kuma Dadyn yayi farin ciki da hakan. Yace Allah ya kaisu gobe ya qara nazari akan lamarin. Toh yace masa ya nufi gun Amminsa. Saidai ita Ammi yana gaya mata komai yaga jikinta yayi sanyi bata wani nuna farin cikinta ba. Shidai ahaka ya lallab'a yabarta lafiya dan yasan idan ya d'auki lokaci agunta ba makawa saita kawo mishi dalilinta na rashin nuna farin cikin nata. Kuma ya saba bin abinda take so. Yanxu saita canja mishi ra'ayi. Kuma abinda bayaso kenan akan wannan lamarin. Dan yana ganin Auran TAUDHAT shine mafi ALKAIRI agaresa da kuma matarsa NUFAISAT. Da farin ciki yakai gidansa lafiya lokacin qarfe goma sha d'aya na dare. Tun NUFAISAT nasaran dawowarsa hardai ta hakura bacci yayi awan gaba da ita Shiko ganinta tana bacci hankali kwance sai kawai yayi wanka da gabatar da lafula kana yabi jikinta ya kwanta anan taji ajikinta yada dawo. Dan har ta bud'e ido Amman bata nuna mai ta farka ba. Tunani kawai takeyi akan yanxu sai sha d'aya zai dinga dawowa. Hmm Allah ya sanyaya zuciyarta.. Wàshe gari bata nuna mai komai na dad'ewar da yayi jiya ba. Sam baiga wani alamu na b'acin agareta ba. Hakan yasa yaji dad'i sosai harya tafi office da nutsuwa. Amman ta gayamai zata gida tagaida momynta Ya amince mata dan yasan tana buqatar tattaunawa da mahaifiyartata akan lamarin Auran nasa dan tabata shawara. Kuma yana da tabbacin zata bata shawara tagari dan yafi kowa sanin halin momynsu nata wajen nutsuwa da hankali sanin ya kamata da hak'uri... Aranar qanin Dadynsa dashi Dadyn kansa sukaje nemammai Auran TAUDHAT d'in. Dan Dadyn yayi tunani yaga dacewar hakan. Kuma wani iko na Allah ko kad'an abinciken dayasa amai akan TAUDHAT d'in ansamu kyakkyawar sheda akanta. Sam basuci karo da mummunar sheda akanta ba.. Wannan dalilin yasa suka kai sadaki awashe garin ranar. Sannan suka buqaci da asaka ranar d'aurin aure nan da sati d'aya☝🏼.. Murna wajen TAUDHAT ba'a magana Sai bayan kwana biyu Adams ya gayama NUFAISAT Auran nasa nan da kwana biyar Duk da taji fad'uwar gaba amma bata nuna masa ba. Ita yasa agaba sukaje manya manyan boutique suka had'o lefe na kerema sa'a. Dan Wannan tsarin Amminsa ne tace mai yaje da NUFAISAT susuyo komai. Duk abinda ta d'auka ta d'aukarma amaryar. Hakan yasa komai bibbiyu NUFAISAT take d'auka. Ba lefi sun samu akwatina shidda shidda ammafa manya manyan...😨 Qanwar Hajjiya Rukayyat da qawayenta ne sukaje gidansu TAUDHAT sukakai lefan awashe gari. Anan Hajjiya Rukayyat taja TAUDHAT gefe tana kitsa mata wasu kalamai kamar haka.. Kasan cewar bokanta ya bata tabbaci akan bazata samu nasara akan NUFAISAT ba. Saboda tana da qarfin imani. Zadai ta iya cin galaba akan TAUDHAT. Ya bata wani magani yace taba TAUDHAT d'in cikin wani abun ci. idan har taci bazata tab'a haihuwa da Adams ba. Idanko ta haihu da Adams toh wallahi cikin wani ne bana Adams ba Wannan dalilin yasa Hajjiya Rukayyat ta dafama TAUDHAT kaza da maganin tabata yanxu amatsayin wai kyautarta na maganin mata. Har tana qarama TAUDHAT da qarya wai shi tabama NUFAISAT shiyasa Adams yake qaunarta kamar ransa. Aiko jin Hakan nan take TAUDHAT ta miqe agaban Hajjiya Rukayyat tacinye kazar nan harda sid'e flasks. Dariyar mugunta Hajjiya Rukayyat tayi da jinjina kishi irin na TAUDHAT Hmm tab'e baki tayi da cewa aranta.. tunda buqatata tabiya banda matsala dake.. Dan haka da farin ciki sosai Hajjiya Rukayyat tadawo gida tana bama Ammin Adams da Dady labarin karramawar da mama mahaifiyar TAUDHAT tayi musu. Sosai tanuna taji fad'in zuwanta gidan. Jin hakan yasa Ammi da Dady jin dad'i sosai Gobe ne d'aurin aure dan haka Adams yasa akazo aka canjama NUFAISAT wasu abubuwan d'aki Duk da cewar shashin amaryama shiyayi mata komai Amman hakan baihana idan kashigo shashin NUFAISAT kaga nata yafi baka sha'awa da birgewa ba. Ita amarya nata shashin komai Skye blur ne. Yayinda komai na NUFAISAT ya kasance ash color n black Gidan ya qara fitowa fiye da tunanin me tunani. NUFAISAT ta kalli ADAMS da kulawa tace. "Gabe zaka zama ango Amman banji kana maganar yin wasu bidi'o'eh da shagalewa ba Murmushi ya sakar mata da bata kiss a wiya yace. "Amaryama tabuqaci ayi hakan amman nace mata banda ra'ayi. Saboda bani San nuna miki d'okina. Saidai yau sunyi walima da qawayenta har nayi mamakin yanda baki halacci wajen ba kamar yanda tace min Murmushi NUFAISAT tayi da cewa. Ba'a gayyaceni ba. Hasalima bansanta ba. Aganina abu me wiya ne zaisa taganni wajen. Gaskiya naji haushin kawo maka wannan qarar tawa da tayi. "Toh ai gani nayi Ku qawayene. Ai basai ta gayyaceki ba. Zadai tazama y'ar uwata idan tashigo gobe. Dan bazan barta a matsayin qawa ba. Kaga mubar batun nan mubarma goben kawai haka kawai naji bana jin dad'i azuciyata. Dake dama suna zaune ne akan kujerar falo saiya janyota jikinsa ya rungumeta dan ya hango bama baman kishi b'aro b'aro a tattare da ita. Dan haka yau baija da nisa ba. Yashiga lallab'ata. Shi sai Yanxu ma ya tuna ai batasan TAUDHAT zai aura ba. Washe gari asabar NUFAISAT da yayarta Zainab da sauran y'an uwanta harda momynsu dake wayayyiyar macece tazo gidan haka suka saka NUFAISAT agaba suka dinga mata nasiha dajan hankalinta akan ta qara hak'uri akan komai karta saka damuwa akan zuwan wannan amaryar tata. Aiko da misalin qarfe gamo sha d'aya aka d'aura auran ADAMSY da TAUDHAT... Kowa ya watse a gidan yazamana shuru daga NUFAISAT dake shashinta sai y'an aiki dake shashinsu sai amarya TAUDHAT dake nata shashin. A haka Adams ya dawo shida masu tsaransa da abokanayansa biyu wato Yusuf da wani wai shi Suleiman B'angaran NUFAISAT suka nufa nan suka ganta afalo cikin kyakkyawar shiga ta doguwar rigar less jah. Ya haskata sosai abinka da fara. Tashi tayi tana musu barka da zuwa cikin yaqe... Da wani hali suke gaisawa da ita suna masu kiranta da uwar gida ran gida. In bake ba gida. Murmushi kawai tayi musu da kama hannun mijinta tana mece musu dasu tashi aje rakiyar da ita zuwa d'akin amaryar... Ta basu mamaki sosai haka taja mijin nata gaba Yusuf da Suleiman sukabi bayansu Adams na qara janta jikinsa yana kuma hango farin cikin dazai ganta aciki idan taga TAUDHAT ce amaryar tata... Hmm😌 masu karatu yake nan.. By Rahma Nalele Auntyn luv [6/21, 9:11 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 11☆ Sunsami TAUDHAT d'in akan gadanta kanta lullub'e da mayafi. NUFAISAT ta zauna kusa da ita da kama hannunta ba tare data bud'e mata fuska ba tace. "Aminci agareki ya y'ar uwata. Yau gaki agaidan mijina matsayin matarsa ta biyu. Ina rokwanki da Allah daki d'aure kiba mijina kulawar data dace. Wallahi ina San farin cikinsa. Allah ya bamu zaman lafiya da rayuwa me d'orewa.😀 TAUDHAT batayi magana ba. Amman tad'an motsa alamun tajita. Ganin hakan yasa NUFAISAT sakar mata hannu da tashi tama abokanayen nasa sallama ta ficce daga d'akin Tana fitta Yusuf da Suleiman suka ma TAUDHAT nasiha kana itama suka ajiye mata kaza da madara kamar yanda suka ajiyama NUFAISAT suka fito suma daga d'akin A can waje Yusuf ya dingama Adams tsiya akan yadai bi TAUDHAT a hankali danyaga har wani rawar kai yakeyi. Adams yayi murmushi da cemai. Haba dai rawar kai. Sai kace wani saban shiga. Bana tunanin zatazo min da wani abu wanda NUFAISAT bata zomin dashi ba. Kudai kawai kujira gobe. Koma miye zaku gani akan fuskata dan kyakkyawan amarci baya b'oya.. Dariya suka sheqemai da ita kana suka shine motocinsu damai sallama megadi ya kulle gida. Part d'in NUFAISAT Adams yayi. Amman yana murd'a kofar tata saiya jita a kulle. Ahankali yashiga bugawa yana kiran sunanta amma shuru wai malam yaci shirwa. Haka ya koma part d'in TAUDHAT lokacin tana toilet da alama alwala takeyi. Hakan yasa ya zauna jiranta yana tunanin meyasa NUFAISAT kulle mishi kofa ba tare da sun yima junansu sai da safe ba.... Fitowar TAUDHAT ne ya katse mai tunanin. Ya kalleta da murmushi yace. "Amarya kinsha qamshi. Dafatan kina tare da alwala mu gabatar da sallar godiya ga Allah daya bamu damar zama ma'aurata. Da matuqar farin ciki tace.. "Dama banyi isha bane shine nayo alwalar. "Toki gabatar kafin nan na shirya saimu gabatar da wannan. Toh tace mai ya ficce ita kuma tacanja kaya zuwa wata doguwar riga ta bacci. Kana ta saka hijab ta gabatar da sallar i'sha'in. Yana zuwa room nasan yayi wanka da qara d'auro wata alwalar ya canja kaya shima zuwa na bacci duk NUFAISAT ta tsaya mishi arai. Dan haka kwanciya yayi agadansa yahau kiran number nata. Saidai ya kira yafi sau goma amman taqi d'aga wayar. Nanko take hankalinsa ya tashi ya nufi part d'inta yana bugawa da kiran sunanta. Bata bud'e kofar ba. Saidai yaga shigowar message d'inta cikin wayar tasa. Hakan yasa ya dena buga kofar ya shiga duba abin data rubutomai kamar haka. _Haba mijina. Bayan ina tare dakai. Kawai bazan iya jure ganinka kazo yimin sallama zaka gun tawa bane. Hakan yasa na kulle kofata. Kuma idan na d'auki wayarka kuka zan fashe maka dashi wannan dalilin yasa naqi d'aga wayanka. Kaganni nan ina cikin koshin lafiya. Aci amarci lafiya da qanwata. Saidai Karka wahalar da ita. Dan bazan jure zuwa yin jinya da safe ba😌._ Murmushi ADAMS yayi da mamakinta. Kai shiyama kasa gane wane irin kishine da ita. Yau tanuna gobe kuma kaga kamar bata da matsala da dashi. Da wani hali ya tura mata da... _Allah ya barni dake matata. Wallahi zanyi maraicinki sosai cikin wannan dare. Kasancewar shine na biyu atarihin rayuwarmu da muka tab'a raba shinfid'a._ Yana tuna tura mata da hakan yabar ƙofar ɗakin nata. Akan sallaya yaga TAUDHAT tana zaman jiransa yace da ita.. "Amin afuwa nabar amarya da jiran ango "Batun afuwa babu tsakaninmu. Nasan dai akwai abinda ya riqemin kaine. "Kwarar kuwa yanxu tashi mu gabatar da sallar.. Haka tatashi suka gabatar da sallar Yayi musu addu'a da tambayarta yanda take wankan tsarki tako gaya masa. Yaji dad'in haka. Sosai. Haka yasa mata kaza a gaba da madara yace ta daure suci. Ba wani kunya can tasake sukaci suka koshi. Kana labari ya canja. Dan koda wasa Adams baiji aransa zai iya tsallakema TAUDHAT wannan dare batare da wani abu ya shiga tsakaninsu ba. Ya jata jikinsa yana aika mata da wasu sakwanni. Yana me jin dad'in yanda doguwar rigarce kawai a jikinta. ADAMS gwanine qajen iya sarrafa mace. Danko a wasan ni ya barki bazaki tab'a San yabar rayuwarki ba. Yasan kan mace fiye da komai arayuwarsa. Yasan yanda zai sarrafaki kimanta duniyar da kike. Sannan idan yagane inda kikafi mutuwa agun yakan iya b'ata lokaci wajan ganin ya qara b'ullo miki da wata hanyar da zatafi wacce kikafi sani wajen mutuwa akanta. Lamarin yana tsuma TAUDHAT sosai fah. Dake tayi shaye shayen maganin mata hakan yasa Adams yaji dad'inta sosai. Saidai hankalinsa ya tashi sosai dayaga ƙofar bashi bane ya fara bud'eta. A hankali ya tashi da zama gefan gadan ya sauke kallansa akanta bayan komai ya wakana. Yasani ya bata wahala sosai. Dan yasan ba kowace mace bace wacce zata iya dashi imba NUFAISAT ba. Saidai TAUDHAT tabashi mamaki. Bayan yanda kofa take bud'e harda wasu salo data kware wajan nuna masa su. D'an tashi tayi a hankali ta jingina da bangwan jikin gadan nata ta kallesa kad'an ganin ita kawai yake kallo saita sadda kanta qasa tace dashi.. "Kamin rai Ya mijina. Nasan na b'oye maka shi. Abun ya faru ne wata ranah danaje bikin wata qawarmu. Lokacin da aka tashi daga bikin. Sai wasu samari suka buqaci dana shiga motarsu suragemin hanya. Har nayi musu musu amma saboda nacinsu da qaddarar da take kaina saina shiga motar tasu. Adams ban tashi tsintar kaina ba sai a wani gida cikin wani d'aki kan gadan wani. Yana d'aya daga cikin SAMARIN dake cikin motar da suka d'aukoni. Yana gefena lokacin dana samu kaina. Anan nagane yayi min b'arna yayi min illa ya rabani da mutuncina da kimata. Nayi kuka nayimai Allah ya isa amman da dariya yabini da ita. Daga wannan ranah nake cikin kunci amman na kasa gayama kowa. Duk da cewar naje asibity an tabbatar min da lafiyata qalau bana tare da wani ciwo. Amman hakan bai sani nasamu nutsuwa ba. Dan nasan zan fuskanci qalubale agidan aurena. Wannan dalilin yasa nayi saurin amincewa da auranka dan nasan kai kad'ai ne wanda zaka iya rufamin asiri ka rayu dani cikin aminci batare da nuna min tsana ko tsangwama ba. Da TAUDHAT tazo nan azancenta sai kawai tarushe da kuka kamar gaske☹ Shuru Adams yayi dajin tausayinta. Hakan yasa ya rungumeta da lallashinta akan tayi shuru insha Allah bata da matsala dashi. Amman zai ibi jininta gobe dan yaje asibiti ya tabbatar da lafiyarsa. Ba qaramin jin dad'i TAUDHAT tayi ba. Dan batayi tunanin shirin nata zaiyi tasiri agunsa nan take haka ba. Shiko Adams har a zuciyarsa yayarda da abinda tace mai. Hakan yasa yacire duk wani mugun tunani akanta da wani mamakinta dayaji yanzun yasaka aransa zai rayu da ita dan ya tabbatar ba qaramin lada zai samu agun Allah ba. Haka ya tsaftace kansa itama ta tsaftace kanta. Ta koma da kwantawa shikuma yahau yin nafula da qara godema Allah akan al'amuransa. Saidai yaji ya qara San NUFAISAT aransa dan koba komai shine dai ya bud'eta aleda. Sannan uwa uba tafi TAUDHAT dadin harka. Duk da cewar yaji dad'in TAUDHAT d'in. Amman gamsuwar tashi yafi jinta agun NUFAISAT. Gaskiyama babu had'i Haka kafin ya bar kan sallayar sanda ya tura ma da NUFAISAT message akan takula sosai da kanta. Babu wata y'a mace daza tasha gabansa akanta. Wallahi yanxu ya qara tabbatar da hakan. Yana tura mata ya tashi da tashin TAUDHAT yana ce mata tatashi suje bedroom nasa su kwanta bazai iya kwana a d'akinta ba. Dan bai saba da hakan ba Ba musu tabishi d'akinsa suka kwanta yana me rungumarta saboda sabo da yayi da NUFAISAT... NUFAISAT ko tunda tasama ƙofarta key. Tayi sallar i'sha fad'awa tayi a gadanta kawai tana tunani barkatai akan yau ba ita ba kwana da mijinta. Zaije ya kwana da wata ba ita ba. Ya dinga mata abinda yake mata. Ai bata ankara ba!!! Wani kuka me ciwo ya kufce mata. Nan tadinga yi tana sambatu. Tana jin bugun kofarsa na farko bayan ya raka abokanayen nasa amman taqi bud'emai. Dan wani haushinsa ne yazo ya rufeta. Gani take baiyi mata adalci ba Tana jinsa yabar wajen Haka kiranta daya dingayi awayama tana kallan wayar tayi burus da ita. Daya dawo ne yana qara buga mata kofar saitaji sanyi azuciyarta tatabbatar ya damu da ita. Hakan yasa ta tura masa da text message har yake bata amsar nan ta d'azu Ganin ya qara turo mata da wani text d'in kusan biyu na dare hakan yasata ganewa komai ya wakana tsakaninsa da amaryar.. Hawaye me zafi yashiga bin kuncinta Lokacin tana kan sallaya dan takasa bacci kwata kwata. Hakan ne yasa ta yanke shawarar d'auro alwala tafara bada lafula tana rok'ar Allah. Sanda taji idanta na rufewa kana tabi gado ta kwanta. Ko baccin awa biyu batayi ba taji ana kiran sallar asuba. Nanko ta duro da qara d'auro alwala tagabatar da sallar raka'atailinfijir kana tayi sallar asuba tana cikin lazimi bacci me qarfi yayi awan gaba da ita☹ Ba ita ta farka ba sai kusan goma da rabi... Aiko da sauri tatashi hankalinta ad'an tashe tana tuna abinda momynta ta gaya mata akan ta daure zuciyarta ta had'a musu breakfast qarfe takwas. Aiko cikin sauri sauri gudu gudu tahau had'a musu me sauqi. tia da soyayyan dankali da kwai had'i da fafesun kazar da auntynta Zainab tayi mata jiya tasa cikin furish dama dan tabasu tayi mata... Sanda tayi wanka tasaka wasu fitunannun kaya riga da siket ne na atamfa d'inkin ya karb'e irin sosai d'innan. da feshe jikinta da turaranta sannan taje taleqa ta window taga Sam ADAMS bai fitta ba. Amman kamar ana kwankwasa mata kofa d'azu. Tayi ma tunanin ko shine ya fitta. Tab'e baki tayi da sake labulanta tana rayawa aranta qilama su Asiya ne Haka ta nufi baban falo falan dazai sadata da shashin TAUDHAT haka dana Adams d'in to anan tajera komai na abinda tayi musu kan dining.. Sannan tayi shashin Adams d'in.. Bata ganshi ba. Sai taji gabanta ya fad'i tatsaya tana tunanin taje d'akin amaryar ne kota koma shashinta... Abinda da yafaru ko da Adams da TAUDHAT shine.. Bayan yata sheta sallar asuba sai shi yayi masallaci. Bai dawo ba sai kusan qarfe bakwai da rabi kamar yanda ya saba dawowa. Anan ya dinga buga kofar NUFAISAT da kiran wayarta amman shuru Yana cikin hakan ne kiran wayar Yusuf ya shigo mai waya akan dan Allah yazo asibitinsa yanzu zaikai Hajjiyansu can ciwan zuciyarta ne da alama ya tashi dan gashi tana dafe da zuciyar wai tana mata zafi kuma tana numfashi sama sama. Da sauri Adams yace toh ya kaita gashi nan zuwa. Aiko da sauri ya koma shashinsa ya shirya ya ficce shida masu tsaransa basu dire ako ina ba sai'a asibitin nasu. Anan yaga harsu Yusuf d'in sunzo Da sauri ya shiga nubata. Aiko ya samu nasarar gane me yasa hakan tafaru da ita. Wai damuwace.. Yusuf Yace "narasa me yake damun Hajjiya wallahi Murmushi ADAMS yayi da cemai. "Yaci ace Yanxu ka gane miye matsalarta. Zata samu kanta nan da awa biyar. pls ka temakemu kagano damuwarta dan Allah. Toh Yusuf yace mai. Anan suka bar qanin babansu Yusuf da matarsa dan Yusuf d'in yace yunwa yakeji Adams yace toh yazo su koma gida susamu abinda zasuci. Lokacin da suka dawo gidan ne NUFAISAT ta shiga wanga Lokacin sha d'aya saura. Shine sukayi shashin TAUDHAT inda tayi farin ciki da hakan amman bata nuna musu ba tace musu bara ta shiga ciki ta had'a musu abinda ya dace. Anan Yusuf yake mata tsiya wai amarya da aiki anya basu takurata ba Murmushi kawai tayi mai da nufar kitchen d'in nata Adams yace wallahi na zak'u naga NUFAISAT. Kagafa har Yanxu banji motsinta ba kusan 11. Yusuf Yace "mu bata minti goma idan bamu jita ba sai'a b'alla kofar muga ko lafiya. "Aiko haka za'ayi. Adams ya bashi amsa da fad'in hakan cikin damuwa.. Wannan shine abinda ya faru Har NUFAISAT ta nufi yin shashinta sai kuma ta kalli agogwan falan Adams d'in taga sha d'aya daidai. Dan haka sai kawai tayi qarfin halin murd'a kofar dazata sadata da falan amaryar tana meyin sallama Aiko karab ta had'a ido da Adams da Yusuf Murmushi ta sakar musu da qarasa shigowa falan tana me cewa.. "Amin afuwa tunda nake arayuwata ban tab'a makara irin nayau ba. Tsaki Adams yaja da kallan Yusuf Yace.. "Kasan Allah na manta da wannan kofar da zata sadani da ita. Yusuf yayi murmushi da cewa. "Nima nayi mamaki sosai danaga ta b'ullo tanan NUFAISAT tazauna kusa da Adams tace kaddai kanata bulayin buga min waccar kofar. "Yanxu ma muka yanke shawarar zuwa mu b'alle ƙofar taki muga ko kina cikin k'oshin lafiya.. "Ina lafiya lau. Yanxu dai bara na gaisa da amarya sai muje babban falo danna had'a muku komai na breakfast Murmushi yayi da shafa gefan fuskarta yace. "Nayi missing d'inki matata. Dana jiki shuru wallahi duk bana cikin nutsuwata. "Yanxu dai ina kadawo normal Kiss ya sakar mata a kumatu da fad'in. "Sosai mah.. Bara na kira miki amaryar dan tashiga kitchen ne had'a mana abinda zamuci. "Toh na hutashat da ita dannayi komai. Murmushi ya sakar mata da kwala ma TAUDHAT kira da AMARYA... Da sauri TAUDHAT tafito daga kitchen tana niyar amsawa. Amman ganin NUFAISAT kusa da Adams saita tsaya cak tana me yarfe hannu da alamata wanke hannun tayi.. Da sauri NUFAISAT tatashi ta nufi TAUDHAT da mamaki take ce mata. "Har sab'anin da muka samu yakai kishigo cikin gidan nan kikasa fara shigowa shashina saina abokiyar zamana har kina tayata aiki. Sosa qeya TAUDHAT tayi cikin wani hali dan taji wani iri tace da ita. "Aina d'auka ya gaya miki jiya cewar nice Amaryar taki..... Cikin furgita NUFAISAT tace.. "What😳. Da zaro ido... Ta juya da kallanta ga Adams sannan tadawo da kallanta gareta tacigaba da cewa... Me kike cewa. Kina nufin kicemin kece wacce ADAMS ya Aura matsayin matarsa ta biyu✌🏼.. D'aga mata kai TAUDHAT tayi da cewa.. "Eh ni ce ya Aura. Saboda yasan zakiyi farin ciki sosai da hakan.... "Farin ciki. Wane irin farin ciki. Kefa TAUDHAT ce. Aminiyata wacce na d'aukeki amatsayin y'ar uwata. Yau kece agabana kina gayamin wai mijina keya Aura saboda yasan zanyi farin ciki da hakan. Haba TAUDHAT wannan wata irin amsa kike bani. Daga tambayarki saiki jefeni da muguwar kalma irin wannan. Tayaya kike tunanin ADAMS zai iya rainon zuciyarmu nida ke.. Dafa Y'ar uwa kike kirana. Aminiya qawa. Amma jiya ki rasa wanda zaki Aura sai mijina.. Shuru TAUDHAT tama NUFAISAT tana me kallan qasa. Ganin hakan yasa NUFAISAT tafe kanta dayake barazanar tarwatsewa ta kalli Yusuf arikice tana me cemai!!! Kana ganin abinda yake faruwa tsakanina da TAUDHAT Yusuf.. Waifa fad'amin take wai mijina ADAMS ta aura.. Ka tuna natashi da ita tun yarinta. Na rayu da ita har gidan aurena. Wai yau itace take amatsayin kishiyata YUSUF Shuru Yusuf yayi cikin matuqar tashin hankali danshi wallahi sai yanzu ya gane kuskuran da suka tabka.. Sam alkairin Auran ya hango wallahi ko kad'an bai kawo cewa hakan zata faru ba. Sam ya manta kishi irin na mata.. Adams ya tashi cikin tashin hankali idansa akan NUFAISAT yace.. "Wai me yake shirin faruwa ne. Nayi hakan dan naga farin cikinki amman yanaga sab'anin hakan. Cikin zubda hawaye NUFAISAT ta kallesa da wani b'acin ran da tunda yake da ita bai tab'a ganinta cikinsa ba tace dashi... "Dalla rufema mutane baki munafuki azzalimi wanda ya manta abinda ya dace ya duba wanda bai dace ba karasa wacce... Ai bata qarasa futucinta ba!!! ya wani d'auketa da marin daya daqarqare iya qarfinsa da shi. Dan kalmar munafuki azzalimin data ambatasa dasu ta shigesa sosai.. Da gaske sanda NUFAISAT taga wasu taurari suna mata yawo afuskar. Dan bata tab'a cin karo da wannan azafaffen marin ba. Hakan yasata dafe wajen da sauri ta tsaya dan dawowa hayyacinta na sakwanni. Kana kuma tafara ja da baya da baya tana kallansu d'aya bayan d'aya cikin matuqar razana da sanyin murya tace. "Na shiga uku ni NUFAISAT.. Qarshen rayuwata tazo.... Tana fad'in hakan ta fad'i sumammiya.. Da sauri dukkansu su ukun sukayo kanta. TAUDHAT fad'i take.. "Na shiga ni TAUDHAT. Dan Allah NUFAISAT ki tashi kiraya zuciyar dake qaunarki. Idan ba ADAMS bazan iya rayuwa ba. Zuciyarsa na tare dake. Idan kika mutu binki zaiyi. Wallahi a daran jiya yaqara jefamin qaunarsa a zuciyata kuma ina da tabbacin idan nayi k'ok'arin bar miki shi saina fara haukacewa kafin nabar duniya.. Ba qaramin tashin hankali ADAMS ya shiga ba. Haka ma Yusuf dan ko kad'an ba motsi ajikin NUFAISAT.. By Rahma Nalele Aunty luv... Ina yinku y'an hannuna🙌🏻 [6/23, 3:14 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 12☆ Da sauri ya d'auki wani ruwa dake cikin gora a gefansa ya fara yayyafa mata... Fad'i yake. "Ki tashi NUFAISAT dan Allah ki tashi. Nayi kuskure na kuma yarda da duk abinda zaki cemin. Sam NUFAISAT bata da alamar motsawa. Ganin hakan yasa ya kinkimeta bai direta ako ina ba sai cikin motarsa. Haka Yusuf da TAUDHAT suka shiga motar ko sauraran masu tsaran baiyi ba ya fige motar ahargitse yabar gidan. Aiko masu taransa da sauri sukabi bayansa. Kaf y'an asibitin basu tab'a ganin rikicewar ADAMSY ba sai yau. Dr Aryan ne yashiga duba NUFAISAT dan ko kad'an Adams baiyi tunanin dubata da kansa ba. Dan duk hankalinsa a tashe yake. gani yake kamar ta mutu. Dan hakan bai tab'a faruwa da ita ba... To idan tamutu yayi yaya da rayuwarsa. "Kai ina NUFAISAT ba zata mutu ba. Ya fad'i hakan a bayyane cikin tashin hankali Da sanyin jiki Yusuf ya kama hannunsa da zaunar dashi yana me masa magana cikin sanyi da lallashi.. "Kanutsu ADAMS. Insha Allah NUFAISAT zata tashi kamar komai bai faru ba. Kuskure ne dai munyi shi arashin sani. Gyarashi kuma kaine da alhaqin hakan.. Shuru Adams yama Yusuf kawai "ADAMSY ka kwantar da hankalinka. Gata can nasamu kanta ta farfad'o... Ai dajin hakan dukkansu sukayi d'akin da take batare da sun tsaya sunji qarashan abinda Dr Aryan zaice musu ba. Tana kwance akan qaramin gadan na d'akin. Hawaye ne yake zuba mata dan tuno da abinda ya faru da tayi. Tana ganin shigowarsu tawani rumtse idanta. Ganin hakan yasa ADAMS zuwa ya durqusa a gabanta da kama hannunta yace.. "Nayi kuskure matata. Nayi miki lefi my luv. Saidai bazan qara aikata miki hakan ba. Bud'e idanta tayi da saukewa akansa tace.. "Ka rigada kayimin komai ADAMS. Ka b'ata tunani na tuntuni da qaunarka. Ba yanda zanyi in cire hakan daga zuciyata. Yanzu kazo ka Auri qawata aminiyata wacce tasanni ciki da bai. Hakan bai isheka ba kabini da abinda ban tab'a tunani ba. Marina fa kayi ADAMS. Marin daban tab'a jin irinsa ba arayuwata. Wallahi saika sakeki dan bazan iya zaman kishi da TAUDHAT ba. Saboda ina MASIFAR SANKA DA KISHINKA. Inda ace wata ce ba TAUDHAT ba na tabbatar bazanji ciwo azuciyata kamar haka ba... Dafe kansa Adams yayi da hannu d'aya. Yayinda d'ayan yake riqe da hannayenta. Idansa ne ya kad'a yayi jajar saboda b'acin rai. Bai tab'a tunanin akwai ranar da NUFAISAT zatace mai wallahi saiya saketa ba. A hankali ya maida kallansa gareta yana mece mata. "Wallahi NUFAISAT saidai ki mutu da Aurena akanki. Dan kalmar saki bata cikin agenda ta! Har abada nidake zamu rayu rayuwar da bata qarewa. Dan har agidan aljanna ina rokwan Allah dayasa ki zama matata.. Na aikata miki hakan da zuciyar d'aya ne NUFAISAT.. Wallahi ban iya yi miki qarya. Na rantse miki da Allah na Auri TAUDHAT ne dan kawai na faranta ranki. Ganin danayi kinfi kowa saninta. Kinfi kowa amincewa da ita. Kinfi kowa jin dad'in zama da ita. Shiyasa na aureta dan aganina zakifi kowa farin ciki da hakan.. "Kadena danganta wannan had'in naka da matsayin zan samu farin ciki acikinsa. ADAMS akwai abubuwa da dama da ban sani ba agame da TAUDHAT. Wallahi Zuciyata zafi take min tana tafasa da k'una idan natuna TAUDHAT itace kishiyata. Bazan iya da TAUDHAT ba Adams. TAUDHAT tafi qarfina. Ina da tabbacin alkairin da kake hangowa agareta kuma agareni bazaka tab'a samunsa ba. Danta b'ata tunanina lokacin dana san wasu abubuwa akanta.. Dan Allah mijina ka sawwaqe min dan ayanxu nafi buqatar qaunarka ta kasheni agidanmu dana zauna zaman kishi da TAUDHAT.... Miqewa ADAMS yayi da sakin hannunta. Yace "bazan sakeki ba NUFAISAT. kuma idan har ayanzu ma ina amsa sunana na mijinki' ina umartarki daki tashi namai dake gidana yanzu yanzu. Wannan shine qarshen maganata dake anan. Ya qarashe furucin da miqa mata d'ankwalinta.. Kuka NUFAISAT tafashe dashi wiwi tana cewa. "Wayyo Allah kakawomin d'auki cikin wannan matsalar data kusantoni. Allah Kaine kace nayima mijina biyayya akan komai banda sab'anka. Narok'eka Allah daka sanyayamin Zuciyata na iya bin duk abinda yacemin acikin wannan halin da nake ciki dan bana San na sab'a maka. Tana gama fad'in hakan tatashi da karb'ar d'ankalin nata tayafa akanta gami da tashi tana me tafiya cikin yali yali. Ganin hakan yasa TAUDHAT nufanta amunafunce danta riqeta alamar temako.... Aiko azafafe NUFAISAT ta wurga mata wani mugun kallo daja da baya tace. "Karki kuskura ki tab'ani... Jan numfashi Yusuf yayi da bugan kafad'an Adams da yake kallansu. Aiko cikin sauri Adams ya gane me Yusuf yake nufi Dan haka saurin matsawa ga NUFAISAT yayi cikin kulawa ya tarota jikinsa. Zata mishi masifa saidai suna had'a ido tafasa. A haka ya kaita har motar tashi gidan gaba. TAUDHAT tashiga baya. Shi kuma ya zauna wajen mazaunin direba. yana niyar tada motar ne d'aya daga cikin masu tsaransa yace.. "Oga daka bari nakaisu gidan. D'aga mishi hannu Adams yayi alamar aa. Sannan yaja motar yana gayama Yusuf ya jirasa yanxu. Girgiza kai Yusuf yayi cikin damuwa dan har ga Allah baiji dad'in abin daya faru ba. Ji yake kamar basu kyautama NUFAISAT ba. Haka yana ji kamar abin da sukayi shine ya dace. Tunanin dayafi tsaya mai arai dai shine basu kyauta ma NUFAISAT ba kawai.. Haka yayi shashin da suka Kwantar da Hajjiya kakarsu. Anan yaga Nazifa qanwarsa taxo da abinci. Dan haka yaci kad'an bawai dan har alokacin yana tare da yunwar tasa ba. Kawai dai yaci ne dan karta mishi illah... Su Adams ko babu me magana acikinsu. Ahaka suka iso gida yace duk susamesa a babban falan nasu... Qarfin hali kawai NUFAISAT tayi taje falan bayan tawanke fuskarta a part d'inta Adams sasu yayi a tsakiya ya kalli NUFAISAT data d'aure yace da ita... "Ki tausasa zuciyarki matata. Dan bazan iya rayuwa babuke ba. Ina San kiyi hakuri na d'auki lefina na Auran TAUDHAT da nayi. Na kuma yarda nayi miki lefi. Dan Allah ki yafemin ki zauna da lafiya a d'akinki dan samun farin cikina. Sannan kiriqe girmanki ki saki ranki ki rungumi y'ar uwarki Ku zauna lafiya dan kinfi kowa sanin bana san fitina da tashin hankali Shuru NUFAISAT tamai bata da alamar cewa komai. Ganin hakan yasa ya maida hankalinsa gun TAUDHAT yaci gaba da cewa.. TAUDHAT na aureki ne dan samun d'orewar farin cikin matata. Saidai kinga yanda al'amuran suka sauya. Ina San matata ina San rayuwa da ita. Dan Allah ki zauna da ita lafiya ki riketa kamar yanda kuke da. Dan nasan zata dawo tayi miki kallan dada take miki danna samu sukuni acikin gidana... Kima NUFAISAT biyayya TAUDHAT ki bita idan kina San samun farin cikina agidan nan Jan numfashi TAUDHAT tayi ranta yayi masifar b'aci. fad'i take aranta Wallahi saita gyarama NUFAISAT zama acikin gidan. Dan bazata d'auki rainin hankali agabanta mijinta ya dinga nuna mata yafi San uwargidansa akanta ba... Tsaida tunanin nata tayi da kallansa ta sakar mai murmushi da cewa. "Ba komai mijinmu insha Allah zanyi abinda kace min. Da sauri NUFAISAT takalleta ranta cike da tsanarta taja mugun tsaki da cewa. "Nidai bazan shiga harkarta ba. Amma katabbatar idan tashigo harkata zan yaga mata rashin mutuncin da bata tab'a ji da ganinsa ba Wallahi. Kallanta Adams yayi da mamaki dan shi ko'a mafarki idan akacemai NUFAISAT zata nuna tsana ga TAUDHAT haka wallahi bazai yarda ba. Bare a zahiri. Girgiza kai yayi dace mata. "Watoh bakiji abinda na gaya miki ba kenan. Zaman gaba zakiyi da ita kenan... Sanda ta gallamai harara kana tace "Allah ya bamu zaman lafiya... Tana fad'in hakan tatashi da saurin shigewa part d'inta Da kallo ya bita kawai. Ganin hakan yasa TAUDHAT tashi itama tabar mishi falan tana kisa abubu aranta. "Mata mata saidai abarku. Ya fad'i hakan abayyane tare da tashi ya koma dining ya fara cin breakfast d'in da NUFAISAT d'in tayi musu d'azu dan suci. Sanda ya gama yaje ya ibi jinin TAUDHAT kamar yanda sukayi shida ita a daran nasu na jiya sannan ya ficce daga gidan zuwa offishinsa. Yusuf bai tafi ba. dan nan ya tarar dashi yako bashi labarin yanda yayi dasu. Yusuf ya kallesa yace. "Gaskiya Adams sai yanzu naga rashin dacewar Auranka da TAUDHAT. Murmushi ADAMS yayi da gyara zamansa kan kujerar offishin nasa yace da Yusuf d'in.. "Koma dai miye yanxu ya wucce Yusuf kawai fuskantar gaba zamuyi. Nidai bazan iya rayuwa babu NUFAISAT ba. Haka kuma bazan iya sakin TAUDHAT ba saboda wani dalili nawa. Dan haka Dan Allah ka tayani da addu'a kan Allah ya shiga tsakaninsu ya daidai tamin kansu. Jan numfashi Yusuf yayi dace mai toh kawai... Kakar Yusuf tasamu sauqi tashin datayi. Danji tayi kamar tafi kowa lafiya aduniya. Dama hakan Adams yake fata. Nan Yusuf yasata agaba kan tagayamai me yake sata shiga damuwa haka. Murmushi tamai da cewa Aurenka nake San gani Yusuf. Jin hakan yasa Yusuf dariya dace mata zanyi kwanan nan. Adams shima dariyar yayi da basu sallama Kana yabi takan bincikensa akan jinin TAUDHAT... Aiko baida matsalar komai. Ma'ana baya tare da cuta... NUFAISAT ko shigewarta part d'inta fad'awa tayi kan gado cikin kuka takira momynta tazayyane mata komai akan ba wata bace kishiyarta Ashe TAUDHAT aminiyarta ce😭 Mommy tayi mamaki sosai dajin hakan. Dan haka tace mata taxo gobe gida zata bata shawara akan yanda zata zauna da TAUDHAT d'in Sosaifa mamakin Mommyn d'in NUFAISAT ya qaru bayan sun ajiye waya ita da NUFAISAT d'in Dan ita sai yanzu tatuna jiya Marwanatu y'ar aikinta tagaya mata kamar maman TAUDHAT tana taro. Sai momyn take ce mata ba yanda za'ayi maman TAUDHAT tayi wani taro batare data gaya mata ba. Saboda ko babu komai ai akwai hakk'in makwaftaka da mutunci.. Qila dai ko qawayen TAUDHAT ne suke kawo mata ziyara. Tuno hakan da mommy d'in tayi sai yasa ranta b'ata taga kamar abinda maman TAUDHAT d'in tayi mata kamar bai dace ba. Idan tayi duba da irin zaman amanar dake tsakaninsu. Hmm mutum kenan. NUFAISAT ko bayan ta gayama mommy d'in tasu kira Zainab yayarta tayi itama ta gaya mata komai Wannan karan taga tashin hankalin Zainab d'in. Dan ce mata tayi gobe itama zata gida su had'u acan. Toh NUFAISAT tace mata da kashe wayan. Sanda tayi sallah raka'a biyu taroki Allah daya sassauta mata lamarin sannan tasamu nutsuwa. Kiran asiya tayi tace taje babban falo ta kwaso kayan breakfast d'in datayi d'azu taba masu so takai yakan kitchen dan Allah ta wankesu. Cikin ladabi ta amsa mata da toh. Sai wajen qarfe Tara da rabi na dare Adams ya dawo gidan. Saboda bai tashi da wuri a asibitin nasu. Sannan ya biya gun iyayansa ya gaishesu kamar yanda ya saba. Koda ya murd'a kofar NUFAISAT akulle yajita. Haka daya duba tacikin babban falan nasu ma tasaka key Dan haka murmushi yayi kawai dajin rashin jin dad'i aransa dan wallahi ya dawo da muradin San ganinta da sakawa aransa sai sun daidaita shi da ita cikin daran nan. Dan bai saba fad'a da itaba. Jinsa kawai yake wani iri haka. Zama yayi afalan ya dinga kiranta bata d'auka ba. Haka yayi hakuri dayin part d'insa yayi wanka da canja kaya ya nufi part d'in TAUDHAT Ba lefi shashin Nata yana tashin qamshi amman baiji kamshin ya ratsa ba kamar yanda yake jin na NUFAISAT Anan falan ya tarar da ita tana kallo hankali kwance. Aiko tana ganinsa tatashi da tsayawa dana sakar mai murmushi cikin nuna jin dad'inta da ganinsa da tayi. K'arasowa yayi gareta da rungumarta yace... "Nayi farin ciki da ganinki cikin kwanciyar hankali Qara kusanta kanta garesa tayi da cewa.. "Nafi kowace mace farin ciki awannan lokacin saboda naga mijina ya dawo gida cikin k'oshin lafiya "Gaskiya na dawo cikin k'oshin lafiya ammafa Zuciyata babu dad'i. Nan take tazare jikinta daga nasa tace.. "Ayya.. Har yanzu Aunty NUFAISAT bata gane qaddarace ta had'ani dakai ba. "aa bance miki. Kawai ki share zancen nan. Komai zai tafi daidai insha Allah. D'an b'ata fuska tayi alamun nuna damuwa. Ganin hakan da yayi saiya qara janta jikinsa da cigaba da cewa. Ban yarje miki kisaka wannan lamarin cikin ranki ba. Saboda bana san natsinci kaina cikin matsala biyu gatata gataki. Dan Allah ki sake nasamu nutsuwa agunki. danna tabbatar natamma na d'an wani lokaci ne.. Jin hakan sai yasa TAUDHAT sakin murmushi tace.. "Muje dining kaci abincin dana girkama. "Kamar ko kinsan tun break d'in danayi d'azu banci komai ba. Saidai kamar bai dace kifara girki tun yanxu ba. "Duk abinda zanyi wanda zai zama farin ciki agareka bana duba dacewa. Kawai Zuciyata gaya min take nayi shi. Gaskiya yaji dad'in amsar data bashi hakan yasa ya kama hannunta sukayi dining d'in yana me gaya mata suna ci zasu kwanta dan haka kawai yake jin gajiya yau. Murmushi tayi mai kawai da fara zuba mai abincikan datayi mai tana sakawa aranta saita kwace zuciyar Adams ya dena damuwa da wata NUFAISAT... Itako NUFAISAT tana jin dawowarsa da ganin kiran da yake mata taja tsaki da cewa "Allah kasaka min. Tana fad'in hakan taja bargo abinta.. Asuba tagari ADAMS TAUDHAT & NUFAISAT 😍 Rahma Nalele Auntyn luv. Ina gasuwa y'an hanuna🙌🏻 [6/26, 8:17 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 13☆ Koda wasa washe gari NUFAISAT batayi tunanin ta had'a musu breakfast ba. Qarfe takwas daidai tagama dukkanin abinda zatayi tashiga wanka. Bayan ta fito daga wankan tad'auki wayarta taturama da Adams text message kad'an haka👌🏻. Kana tagyara kanta nan tafito fes da ita. Doguwar riga tasaka me kalar ja. Ta yane kanta da d'ankwalin rigar da saka takalminta med'an tudu. Sannan ta d'auki wayarta da key d'in motarta tama masu yimata hidima sallama ta ficce daga gidan.. Bata dire ako ina ba sai'a gidansu. Da Dadynta taci karo lokacin dazata shiga falan nasu. Ya kalleta ad'an nazarce yace.. "Mamana kece agidan haka da sassafe. ( dake da haka yake kiranta kasancewar sunar mamansa yasa mata ) Turo baki tayi da durqusawa tace.. "Ina kwana Dady. Murmushi yayi da bata da amsa da. "Lafiya lau. Saidai baki ban amsata ba mamana. Qara turo baki tayi da cewa. "Momy ce tace nazo saboda na gaya mata ADAMS ba wata bace wacce ya Aura face TAUDHAT aminiyata. Dady ADAMS bai kyauta min ba Sam. Wallahi ban hanasa Aure ba. Saboda nasan dalilinshi nayin hakan. Sannan duk mata ta gari idan tana San taqara samun kusanci da ubangijinta to ya zaman mata dole tayima mijinta biyayya taso abinda Allahn ya halatta mishi da yayi. Sannan tadinga bashi gudun mawa idan taga zai kauce hanya. Dady kun bani tarbiya wacce nataso akanta har ake sha'awata dan ita. Saidai ina ganin kamar bazan iya yima Adams biyayya ba ayanxu. Dan ina mishi kallan munafuki azzalimi wanda ya aikata abinda bai dace ba.... Taqarashe maganar tata da sakin kuka. Murmushi Dadyn nata yayi da cewa aransa.. Mata mata halinsu sai su. Banda haka miye abin tada hankali dan kawai mijinki ya Auri aminiyarki. Afiliko ce mata yayi. Tashi mamana kukan ya isa haka nan. Muje falo Haka tatashi tabishi har falan nasa. Anan yayi mata nasiha da nuna mata wannan ba komai bane. Ita dai ta riqe sirrin gidanta. Taci gaba dayi mai ladabi da biyayya. Wallahi komai zaixo mata da sauqi idan har tasaka Allah agabanta... Godiya tayima Dadyn nata sosai sannan ta nufi gun momyn nata lokacin tana kan sallaya da alama warha tayi. Tana jiranta ta idar d'inne saiga Zainab yayarta taxo. Aiko nan tatashi ta rungumeta sai yaxo da dai dai da lokacin da mommy d'in nasu tashafa addu'ar da takeyi... Aiko bayan sun gama gaisawa NUFAISAT ta gyara zama tabasu kaf labarin abinda ya faru... Ran mommy ya b'aci amman bata nunama NUFAISAT d'in ba Zainab kam tausayin y'ar uwar tatane ya kamata. Mommy tayi shuru tana nazari can tace da NUFAISAT d'in... "Ki bud'e kunnanki da kyau ki saurareni kiji abinda zan gaya miki. Tattaro dukkan hankalinta NUFAISAT tayi tana sauraranta.. Mommy taja numfashi daci gaba da cewa.. Sirrin zama da kishiya uku ne NUFAISAT.. Nafarko kisaka aranki zaki zauna da ita tsakaninki da Allah. Bazaki munafunceta ba. Bakuma zaki cutar da ita wajen aikata mata wani mugun abu ba. Sannan bazaki danne mata hakk'inta ba. Na biyu . ki rungumi danginta da y'ay'anta da qawayenta runguma ta tsakani da Allah wacce babu batun kai qararta ga d'aya daga cikinsu ku zauna kuna munafuntarta. Saboda duk yanda kikai da abinki saiya koma mata kunnanta wata ranah.. Karkisa aranki zaki cutar da y'ay'anta agaban idanta ko'a bayan idanta. Dan bakisan alkairin dake tafe dasu ba. Ko wata rana sune zasu temakeki. Koki mutu suna masu yi miki addu'a. Ki riqesu amana ba ruwanki da nuna musu wani hali na mugunta. Na uku shine uwa uba.. Kisa aranki bazaki dena yima mijinki ladabi da biyayya ba dan kawai ya aurota. Ya zamana lokacin ne zaki ninka ladabin da kike masa da zak'ulo duk wani abu da kikasan zai faranta ransa Ya kasance kowane lokaci cikin bincike kike akan San sanin me yafi so. Meyafi d'aukar hankalinsa. Meyafi tafiya da tunaninsa. Meye idan kika masa yake tsayawa aransa wanda idan ya kalleki zaisa ya sakar miki murmushi. Idan kika san way'annan saiki kasance cikin yimasa su. Gefe guda kuma kina yaqi da zuciyarki wajen San zak'ulo abinda idan kika masa zai bashi mamaki. Idan kika gama karantar way'annan saiki koma lura da abinda bayaso. Idan kika gama lura da abinda baya so. Sai kiyi yaqi da zuciyarki wajen nisantar wannan abun.. Wannan shine sirrin zama da kishiya. Kinga baki nuna mata baqin hali ba. Baki cutar da ita ba. Baki danne mata hakkinta. Baki aikata mata wani mugun abu. Ke kawai mijinki shine agabanki ba kishi da ita. Toki saiki gayamin ta inda zata fiki kwanciyar hankali acikin gidan... Magana ta qarshe dazan gaya miki NUFAISAT itace. Bana San wasa da sallah. Lokacin sallah nayi kitashi kije kiyi. Dan duk macen da take yin sallah akan lokaci wallahi tafi qarfin kishiyarta tako ta ina.. Sannan duk sallar da zakiyi idanga rokwan Allah ya cire miki kishin abokiyar zamanki. Sannan ya fifita qaunarki acikin zuciyar mijinki Yasoki ya qaunaceki fiye da kowace y'a mace afad'in duniya dama gidan lahira. Amatsayina na uwarki mahaifiyarki ban yarje miki ki sararama TAUDHAT wajen kishi akan abinda Adams yake so ba Na baki dama kije ki kwace mijinki agun TAUDHAT ki nuna mata ko babu haihuwa bazaki tab'a wulaƙanta agun mijiki ba. Ki nuna mata ita da banza duk d'aya kika d'aukesu Ki nuna mata ita bata kai kiyi kishi da ita ba Ki nuna mata Adams naku ne ku biyu amman kece abar qaunarsa... Toh saiki tambayeni. Tayaya zaki nuna mata dukkanin way'an nan abubuwan. Ta hanya d'aya ce itace HAKURI da nazari wajen yanke hukunci Na sanki da San fad'an gaskiya atake idan aka miki abu. Saidai kisani Yanzu dole ki koyi yanda ake danne abu. Koda kin ganshi gashi gaskiya ne kuma ke aka cuta saiki share nunu sam abinda aka mikin bai dameki ba. Dan idan kikayi hak'uri ga wanda yake sab'a miki wallahi wata rana shida kansa zai zauna yayi tunani da nazari akan ya dace yadena miki abinda yake miki... Ki iya kirsa da kisisina da basarwa akan komai da zakiyi agidanki. Ammafa me kyau banda mara kyau. Sannan kisa aranki raguwar mace itake kuka da buri da fad'ace fad'ace idan anyi mata kishiya. Kedai kisa aranki abokiyar zamanki ba abar tsoranki bace. Ki riqe Allah duk abinda zakiyi kiyi damunsa Wannan itace nasihata agareki. Kuma itace gaskiyar dazan gaya miki. Kuma daga yau bazan qara zama dake irin wannan dan kinrasa yanda zakiyi da kishiyarki ba.... Mommy na kawowa nancikin zancenta taja numfashi da d'auke kallanta daga kan NUFAISAT d'in taciga da cewa. Naji kince text message kika masa wajen wajen gaya mai zaki nan gidan. Kuma bai turo miki amsa ba kawai kikayo gaban kanki kika tawo ko.... D'aga mata kai NUFAISAT tayi jiki asanyaye. Ganin hakan yasata murmushi taci gaba da cewa.. Kishi da tsanar TAUDHAT yana neman ya canjamin ke NUFAISAT a lokaci d'aya Hmm ba komai. Idan kikayi abinda nace miki zanga aikinsa ajikinki. Idan kuma naga akasarin hakan. Zaki ban mamaki dan zan d'auka da gaske TAUDHAT tafi qarfinki. Ta gaske tsoranta kikeji. Da gaske takwace miki farin cikinki Wallahi NUFAISAT idan naga hakan atare dake da baqin cikinki zan mutu... Da sauri NUFAISAT ta kalleta. Aiko mommy d'in ta gyad'a mata kai alamun tabbatarwa. Kana taci gaba da cewa. Ki tashi kije gidanki ki gyara kanki da ingantattun magungunan mata da kayan marmari. Ki wadata kanki da qamshi da kuma d'akunan ki. Kici gaba da koyan girki agun y'ar uwarki. Kisa aranki kina da Allah baki da damuwa da albarkacin manzan Allah. NUFAISAT tashi ki tafi gidanki Allah ya miki albarka ya d'oraki akan mijinki da abokiyar zaman naki. Zan bama Y'ar uwarki Zainab magungunan gyaran jiki anjima saita kawo miki gobe.. Tashi NUFAISAT tayi hawaye na zubo mata tayimusu sallama da ficcewa daga gidan. Da kallan tausayi mommyn tabita dashi kana ta kalli Zainab dake kuka tace "miye naki na kuka kuma. "Momy ina kukan rashin adalcin da TAUDHAT tama NUFAISAT ne. Sannan tausayin NUFAISAT d'in ya kamani. Sannan godiya nake ga Allah daya bamu iyaye kamarku.... Murmushi mommy tayi da tashi tana nad'e sallaya dace mata. "Naji futan Dadynku bara na kirasa nagaya masa zani unguwa. Kinga kanki tashi daga office nagama had'a mata komai da komai. Sai kawai ki biyo ki karb'a idan Allah ya kaimu gobe kya bata kamar yanda nace mata.. Toh Zainab tace mata tare da share hawayenta ta d'auki jakarta da key na motarta tanufi wajen aikinta. Lokacin da sakwan NUFAISAT ya iske ADAMS shida TAUDHAT suna kan dining yana cin breakfast d'in da tayi mai. _Na tafi gidanmu ba wani jimawa zanyi ba._ Wannan shine sakwan data tura mai. Murmushi ADAMS yayi dajin takaicinta. Kana ya ture wayar gefe yana me sanyin sauri ya gama yaje ya sameta. Dan baya San kiranta TAUDHAT ta ankare da wani abu Saidai kanya ida gamawa yaji tashin motarta. Sanda ya rintse idansa dan takaici. TAUDHAT ko duk ta fahimci NUFAISAT ce ta fitta tsaresa tayi da ido tana me tambayarsa ko wani abu ne ya shigar mai ido. Bud'e idan yayi da sakar mata murmushin yaqe batare dayace mata qala ba. Sanda ya gama ne ya sakar mata kiss a kumatu da d'aukar jakarsa ya ficce daga falan. Ai tana jin fitansa da masu tsaran nasa tafad'a tunanin me NUFAISAT tafutayi da sassafe haka. Ganin takasa ba kanta amsa sai kawai ta saka wani layinta cikin wata qaramar wayarta takira wani malaminta akan ya duba mata ina kishiyarta taje yanxu da safen nan. Murmushi ya mata da cewa su TAUDHAT yau an tuna damu. Yaushe kikayi Auran da har kike magana akan kishiyarki baki bamu labari ba Da murmushin yaqe tabashi labarin yanda akayi tasamu Adams d'in kana ta qara mishi da cewa ita dai yanxu ya gano mata me NUFAISAT tafuta yi Sanda yayi mata kirari kafin yace zai duba mata takwantar da hankalinta. Saidai koya duba bazai gaya mata sakamako ba sai indai tazo garesa. Waro ido TAUDHAT tayi da cewa "Ina matar aure me zan maka idan nazo. Murmushi yayi da bata amsa... "Lalle TAUDHAT. Mata nawa ne suke da Aure amman suke cigaba da abinda sukeyi. Gaskiya bazaki samu nasara akan kowane abu daga gareni ba har sai idan zaki dinga zuwa ina d'anaki. Dan yanxu kika gama bani labarin yanda kike sakarma da boka jikinki. "Kaga da Allah dakata. Me zakace akan boka. Naga ai duk aikinku d'aya ne dashi. Kawai shi yana amsa sunansa na boka ne kai kuma d'an iskan malami. Sheqe mata da dariya yayi da cewa. "Ya San ranki mutuniyata. Kawai malama idan zakixo kizo kawai. Idan bazakizo ba kisha zamanki "Zanzo amma gaskiya sai nakai kwana bakwai d'ina kafin nan na lashe amarci na. Dan bazan Bari kalashi tanadin da nayima mijina nan kusa ba. Dan haka ka adana binkikenka akan udirin nawa idan nazo ka gaya min komai... Tana fad'in hakan bata jirayi cewarsa ba ta kashe wayartata danya bata haushi. Gashi bokan nata baya da waya bare takirasa taji ina NUFAISAT d'in taje... Kwantawa tayi tana tuna yanda Adams yake da dad'in mu'amala. Komai nashi daban yake. Dole mace taso shi dan yana da abubuwan da za'a soshi dansu. Duk yawan bud'e idanta afannin karuwanci da iskanci taga Adams oganta ne ta wannan fannin. Saboda yasan kan mace fiye da tunaninta. Wannan kad'ai ya isa yasa NUFAISAT hauka akansa. Dan itama taji abinda NUFAISAT d'in take ji akansa. Nan tunaninta ya fara juyewa akan gaskiya itace tadace da Adams ba NUFAISAT ba. Kuma dole NUFAISAT tabar mata Adams taje can tanemi wani mijin ta aura😌. Dan bazatayi sake da duk wani abu da yake dashi ya mazana su biyu ne ita da NUFAISAT suke da mallakinsa ba.. Haka dai tadinga sak'a sharri aranta har taji lokacin da NUFAISAT d'in tadawo. Yarda wayarta da key na motarta NUFAISAT tayi akan gadanta. Kana tad'an zauna agefen gadan tana me nazarin maganganun da momyn nata tayi mata.. Sai yanxu kanta ya bud'e tagane wasu abubuwa dadama. Sam idan kirsa na magani bai dace tafito ta nunama TAUDHAT tsana haka afili har ADAMS ya gani ba.. Idan zata nuna mata ya dace ta nuna mata ita da ita ne. Saboda idan ta nuna hakan ita TAUDHAT d'in kwantar da Kai zatayi agunsa. Kuma tasan halin mijinta sarai dasan abashi kulawa da tattalinsa. Duk da bai cika d'aukar iskancin mace barkatai ba. Toh mezai hana ta danne zuciyarta tayi kamar batasan ya Auri TAUDHAT ba. Idan ya ficce sai suci junansu ita da ita. Murmushin jin dad'i NUFAISAT tayi saboda tanad'e komai na makaman yaqi da TAUDHAT akan duk abinda zata zo mata dashi. Sai tayi nazari kafin ta yanke mata hukunci. Ta saka aranta Wallahi bazata tab'a barma TAUDHAT d'in shi ba.. Dan haka yamma nayi tashirya kanta kamar yanda tasaba. Sam bata kulle kofarta kamar yanda takeyi a kwanaki biyun nan ba Aiko da misalin qarfe shidda da rabi tana kitchen tana had'a complex taji qamshin mijin nata ya daki hancinta. Bata juya ba dan tana da tabbacin shine ya shigo kitchen d'in... ADAMS dake bakin kofar kitchen d'in shigowa yayi yana jin dad'i aransa na ganinta da yayi. Gaskiya yayi missing d'inta sosai. Da'ace zata gane ko kad'an baya jin dad'in TAUDHAT da mu'amala da ita.. Da Ita kawai yake san rayuwa dajin dad'in mu'amala. yasan da zatafi kowa jin d'adi. Saidai bazai iya gaya mata ba. Ita da kanta zata gane hakan. Dan shi ya dad'e da yima zuciyarsa hud'uba akan taji maganganun kowa akan soyayya saidai tafi d'aukar na NUFAISAT da mahimmanci. Dan da ita yafara soyayyar. Wannan dalilin shiyasa duk yake jinsa wani iri idan yana kallan TAUDHAT tana zuba masa kalaman soyayya. Shi dai bazaice bata iya ba. Amman yafi jin na NUFAISAT fiye da nata aransa. Kodan yanxu ya fara sabawa da ita ne ta wannan fannin🤔..... A hankali yaje ya rungumi NUFAISAT d'in ta baya yana ne sauqe ajiyar zuciya. Cikin wani salo yake shaqar qamshinta yana cigaba da sauke ajiyar zuciyar.. A hankali NUFAISAT tafara juyawa garesa ta rungumesa tsam. Dan nan take taji abinda takwana biyu bataji shi ba. Wato d'umin mijin nata. A hankali taji ranta na mata dad'i dasan su kasance ahakan. Shima yaji mafificin dad'i da hakan data mai. Kamshinta kawai da yayi sabo dashi yana saukar masa da nutsuwa da kwanciyar hankali. Cikin sanyin murya tace da shi. "Kayima Zuciyata illa da yawa mijina. Tunda karaba fatata dajin d'uminka kullum. Karaba idanuna da San ganinka cikin dare kullum. Karaba kunnena da sauraranka kullum. Kagayamin wane hukunci ya dace dakai Murmushi ADAMS yayi da d'ago da hab'arta yace.. "Wallahi ganinki yanxu da nayi ji nake kamar na cinyeki d'anye. Dan komai naki nayi missing d'inshi da yawa my luv. Dan Allah matata kiyima Zuciyata gata kidena kullemin kofa. "Yanxu ka gayamin hukuncin daya dace na yanke akanka.. Wato zan hana ganinka da zuciyarka ganina. Zan hana kunnuwanka da fatar jikinka saurarona da jina... "Haba matata dan Allah kimin aikin gafara wallahi bazan qara yimiki wannan kuskuran cikin hankalina ba. Nayi nadama nayi dana sani nayi Allah wadai da wannan tunani nawa daya kitsamin na rasa wacce zan auro miki sai TAUDHAT.. "Kadena Allah wadai da tunaninka mijina. Dan abinda kayi shine ya dace dani. Shed'an ne ya shiga Zuciyata har yakaini dayi muku wannan borin. Sanda naje gun mommy na tabani haske akan manufarka da dalilinka da kuma nufinka. Nagode Allah daya bani kai amatsayin mijina mesan ganin farin cikina akowane lokaci. Tabbas kayi gaskiya TAUDHAT itace ta dace da zama abokiyar zama. Agareni. dan baza tata aikatamin abinda bai dace ba Haka nima nasanta bazan tab'a aikata mata abinda bazai dace ba. Na yarda da TAUDHAT yanxu mijina d'ari bisa d'ari. Kuma ina San rayuwa da ita rayuwa tahar abada. Yanxu muje na ganta na kama hannunta na gaya mata ita qawata ce kuma y'ar uwata ce har yanxu. Fatana takulamin dakai kamar yanda nake kula dakai.. Qara rungumarta yayi dan yaji dad'in bayanan nata. Ya tabbatar mahaifiyarta uwace dan ta'iya gyara masa gida.. Ahankali ya fara neman bakinta amma taqi dana nuna masa yanxu ba lokacinta bane lokacin TAUDHAT ne dan haka ya kula.. Baiji abinda ta gaya masa ba. Dan bai barta ba sanda yaji bakin dakyau... Aiko tana manne ajikinsa suka nufi part d'in TAUDHAT d'in zuciyarta na bugawa dan baqaramin tsanar ganin TAUDHAT d'in take ba. Aha dai suka samu TAUDHAT d'in a falo taci riga da wando kayan sun matseta ainun dan komai nata ya bayyana ya fito fili qara qara. Hankalin NUFAISAT ya tashi matuqa😨 danta tabbatar lalle TAUDHAT so take ta kwace mata mijinta acikin lokaci qanqani tabarta can baki sake tana kuka da ihun aminiyarta ta cutar da ita ta aure mata miji. ADAMS ko dagaske har cikin ransa kwalliyar TAUDHAT d'in ta birgesa amman yaga saurinta nayin hakan. Dan NUFAISAT sanda tayi sati biyu kafin tafara saka mai qananun kaya. Koda yake zamanine yazo da hakan. Dan kullum dad'a wayewa ake. Nan ya qara kallanta dakyau Saiya fad'a tunanin dukfa da hakan idan da kayan ne ajikin NUFAISAT ya tabbatar saiyafi d'aukarta. Saboda tad'anfi TAUDHAT abubuwan d'aukar hankali. Ita kuma TAUDHAT ganin NUFAISAT da murmushi gata kuma manne jikin Adams ba qaramin fad'uwar gaba taji aranta ba. Nan take ta dibibice dan ranta b'aci yayi ainun. Ba qaramin yaqi da zuciyarta NUFAISAT tayi ba wajen cewa.. "Nagode ma Allah dayasa nasameki cikin koshin lafiya haka. Takai qarshen zancen nata da sakarma Adams kiss a gefan kumatunsa shima ya sakar mata cikin kulawa kana ta zare jikinta daga nasa taje takama hannun TAUDHAT d'in daci gaba da cewa... Dama nazo nakama hannunki ne nanemi afuwarki daga takaicin dana nuna miki akan kyakkyawan udirinki na auransa da kikayi wajen San faranta min. Nagane gaskiyar mijina nufinsa akanki na aurokin da yayi. dan haka dan Allah kicire komai aranki kici gaba da d'aukata a matsayin qawa aminiya y'ar uwa. Dan muhad'u mu bama mijinmu farin ciki me d'orewa. Kallan Adams taudhat tayi da maida kallan nata ga NUFAISAT tace "La.. karki damu. Ai dama nasan da wuri zaki gane manufarmu.... Galla mata harara NUFAISAT tayi tunda ta fahimci ta juyama Adams baya bayi ganinta sai tayi saurin bata amsa da cewa.. "Ina jin dad'in yanda kike da sauqin kan nuna komai ba komai bane Cikin muryar qasa qasa TAUDHAT tace mata. "Hmm.. Wane saban shiri ne kuma wannan. NUFAISAT ta wurga mata kallan tsana itama cikin muryar qasa qasa tace.. "Irin shirin da kika d'auki lokaci kinayi wajen aure min miji. "Idan ko haka ne kidena yinsa tun yanxu dan bazaki iya irinsa ba! "Na rigada na shirya makaman yak'i dake taudhat. Wallahi ko'ana ha maza ha mata saikin gane ADAMS na irinmu ne mu kad'ai ba irinku karuwai mushirikai ba. "Ni kuma saina nuna miki da irinmu ya dace bada irinku shashashai banzaye dolaye ba "Idan da gaske na riqi Allah ke kuma kin riqi boka zanga tsakanin nidake wayake dacin galaba.. "Kasancewar ni ce nake fuskantar mijinmu ayanxu na lura ya fara zargin wani abu muke kullawa akansa. Dan haka ki adana kalamanki yanxu idan gobe tayi bayan ya fitta zanzo shashinki kifad'i maitarki ni kuma na baki amsarki "OK. Ina nan ina jiranki me zuciyar maciya amana.... Kan TAUDHAT ta batama NUFAISAT amsa sai Adams yace.. "Wai me kuke fad'ama junanku ne haka naji kuna magana qasa qasa da alama akaina kuke maganar... Murmushin yaqe TAUDHAT tayi da saurin figge hannunta daga na NUFAISAT tana niyar bashi amsa sai NUFAISAT tayi saurin juyawa garesa tace. "Hud'uba nake mata akan takulamin dakai. Dan idan tabarmin kai haka ba kulawa zan hukuntata irin sosai d'innan. Shine fa take ban hakuri... taqarashe maganar da kallan TAUDHAT d'in tana cigaba da cewa. Ko ba haka bane. D'aga mata kai TAUDHAT tayi da cewa. "Haka ne man. hmm haka. Murmushi ADAMS yayi da qarasowa ya kama hannun NUFAISAT ya sakar mata kiss da cewa.. "Nagode matata. Sannan kulamin da kanki. Ina miki fatan ALKAIRI akan kitashi lafiya. Mayar mishi da kiss d'in tayi itama a hannunsa tace... "Tare dakai mijina. Kana taje ta rungumi TAUDHAT dacigaba da cewa.. Tare dakema Yar uwata... Tana fad'in hakan ta ficce daga d'akin tana jin wani iri aranta Ko ba komai taji dad'in aranta. Yanxu ta fahimci agaban kowa Adams zai iya bata kulawa. Kuma Wallahi saita nunama TAUDHAT iya karta. Adams ko part d'insa ya nufa yana me cema TAUDHAT gaskiya Kinyi kyau sosai Qawarmu. Zanso nayi wanka na biya kud'insa Murmushi baqin ciki tayi da bashi amsa da cewa. "Nagode mijin qawa... Har yakai kusa da part d'insa ya juya da kallansa gareta da cewa.. "Wato baza'a canjamin suna daga mijin qawa na koma wani ba ko. "Toh ai sunan daya dace dakai ne. "Kuma fa haka ne. Tunda NUFAISAT tace kuci gaba da d'aukar junanku kamar yanda kuke dah. Kici gaba da kirana da mijin qawa. Zanci gaba da kiranki qawarmu. Zataci gaba da kiranki y'ar uwa. Ki had'amin komai na abinci dan nadawo da yunwa sosai. Murmushi tayi dace masa "Toh.. Yana shigewa part d'in nasan tasakar mai harara da cewa. Ba kana rawar kai wai kai ka shirya da matarka ba. Wallahi duk sainayi maganinku.... Kuyimin afuwa y'an hannuna. Bana jin dad'i ne shiyasa kuka jini shuru. Sosai nagode da kulawar da kuka bani sisters🙋🏻‍♀ MUSLEEMAT na zuwa gareku cikin wannan labari nawa😌 [6/28, 11:46 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 14☆ Da b'aqin ciki ta nufi dining dan had'a masa abincin NUFAISAT ko zama tayi afalanta tasauke numfashi sannan ta nufi toilet tayo alwala da gabatar da sallar Magrib... Washe gari da misalin qarfe takwas da rabi Adams ne ya gama shirinsa nasan zuwa ga asibitin nasu A hankali ya kalli TAUDHAT dace mata. "Ki duba yanda kwanaki suke shigewa. Mutane na cigaba da aikata abinda sukeyi. Wai yau idan Allah ya kaimu dare kwanan mu hud'u kenan da aure.. Murmushi ta sakar mai da cewa. "Eh wallahi. Allah dai yasa mu dace. "Amiin "Gaskiya kayi kyau mijin ƙawa.. Kallan kansa yayi da d'aukar jakarsa yana me cewa. "Nagode ƙawarmu ya fad'i hakan da ficcewa daga falan nata ya nufi kofar da zata sadashi da shashin NUFAISAT cikin sauqi. Hard'e ya ganta akan kujera taci uban ado kamar ba NUFAISAT d'insa ba. Dan gani yayi tayi irin wannan adan da matan yanxu keyi wajan fitar da tsarin jagira me kyau. Ga wani salan d'aurin d'an kwali datayi me d'aukar hankali. Falan sai qamshi yake zubawa me tafiya da zuciyar masoyi. Riga da siket ne ajikinta y'an kanti. Sun matseta da fitar mata da tsarin halittarta. Kalan kayan milk colour ne. Gaskiya matar tashi tayi mai 💯. Hakan yasa yaqi qarasawa cikin falan ya tsaya cak da sakar jakarsa ya ware hannuwansa alamar tazo garesa. Aiko da gudu taje ta rungumesa tana me sakar mai kiss a baki.. Fad'i take. "Gaskiya na zaƙu kadawo gareni naji d'umin jikinka da kyau mijina. "Kwantar da hankalinki my luv. Dan saura kwana uku kacal nadawo gareki. "Ina sanka mijina. "Ina ƙaunarki matata... Sun d'an b'ata lokaci suna masu shaƙar ƙamshin juna tare da ɗumin jiki. Kana sukama juna sallama cike da qauna.. TAUDHAT naganin fitar Adams tafito da sauri dan zuwa shashin NUFAISAT Saboda ta kwana da abinda ya faru tsakaninta da ita jiya. Sam bata wani bama Adams kulawa cikin daran nasu na jiyan ba. Saboda tsabar tunani. NUFAISAT na k'ok'arin neman inda tasa wayarta saiji tayi kawai an banko mata kofa alamar wanda yazo garetan afusace yake. Ta d'aga kai taga TAUDHAT ce. Aiko nan take ta b'ata fuska dace mata. "Haba malama miye haka. Ya zaki shigomin falo kamar wata y'ar arna babu sallama sannan afusace. Idan fad'a kikayi da Mijinki ko kin samu sab'ani da masu aikin gidan nan naga bai dace kizo ki sauke akan ƙofata ba. Galla mata wata muguwar harara TAUDHAT tayi da cewa. Idan fatanki inyi fad'a da miji dan kiji dad'i ne to kisa aranki wannan ranar bazata tab'a zuwa gareni da Adams ba Sab'ani ko da ma'aikata saidai ke kisamu dasu keda kika sakar masu. Dan wallahi ko baqi nayi basu ba samun sab'ani da ma'aika. Bare ni matar gida aisai kawai kiga babusu agidan nasa an koresu. Mezai kawoni shashinki idan ba kece kika ja nazo ba. Idan kin manta ne nazo muyi magana akan maganganun da mukayi dake jiya "Ayya kice da abin kika kwana aranki. Kinga ko duk da nice na tsokano zancen amman ban kwana dashi arai ba. kiyi hakuri na manta ashe haka nan ayanxu gari banza bazaki iya zuwa shashina ba saboda cin amanar da kikayi agareni. Yanzu dai gayamun meke tafe dake. Dan da gaske ayanzu na manta kalaman dasuka shiga tsakanina dake awannan lokacin. Murmushin baqin ciki TAUDHAT tayi da cewa... "Nima ayanxu na manta. Kawai dai bari naja miki kunne akan ADAMS. Ya dace ki gane ayanxu Sam bai dace dake ba. Dani TAUDHAT ya dace. saboda nice zan iya d'aukar kowane abu idan yaxo dashi. Kasancewar nafiki sanin abubu dadama. Ina baki shawara datun wuri kinemi takaddar sakinki agunsa kije can kisamu daidai dake tunkan nafara nuna miki TAUDHAT d'in da kika sani da! Ba itace yanxu agabanki ba. Kallan raini NUFAISAT tayi mata da sheqewa da dariya tace... "Ikwan ALLAH. Idan daranka bazaka dena ganin daqiqai aduniya ba. Idan daranka zakaga abubuwa dadama na faruwa. Idan da ranka zakasha kallo inji malam bahaushe. Nufaisat na kawowa nan azancanta. ta tsaida dariyarta da kama gudunta ta kafe TAUDHAT ƙirr da ido taciga da cewa... Toke yanzu in banda daƙiƙanci ya samu zama a kwakwalwarki yaushe zaki dubeni sama da qasa kice wai ban dace da Adams ba. Naga nafiki wayewa tunda nafiki ilimi da sanin abinda yadace me hankali ya aikata ma d'an uwansa musulmi. Ma'ana bazan tab'a cutar da mutumin daya bani gaskiya da amana ba. Bazan tab'a cin amanar wanda yayarda dani ba. Bazan tab'a aikatama wanda yasoni tsakani da Allah da wani abu wanda zai d'aga mishi hankali ba.. Naga nafiki komai wanda maza keso ajikin y'a mace. Ma'ana nafiki kyan fuska. Nafiki kyan sura. Nafiki kyan mazaunar da nonuwa masu kyau nad'aukar hankalin maza. Uwa uba na fiki kyan hali halin da Allah keso manzan Allah keso ki gayamin ta inda kikafi dacewa da ADAM wanda ni NUFAISAT y'ar gaban goshinsa ban dace dashi ba Sannan da kike wani maganar zaki nunamin TAUDHAT d'in dana sani da zaki nunamin ba itace yanxu agabana ba. An gaya miki ban dad'e da canja miki matsaya bane akan sanin danayi miki da dana yanxu. Da nasan TAUDHAT d'in dana sani kamulalliyace wacce tasan abinda ya dace da ita. Me sona me nuna min qauna agaban kowa. Yanxu kuma ta canja kamar yanda yanayi yake canjawa takoma karuwa me bin bokaye da malamai tsubbu ta kuma muguwa maciyiya amana. Tayaya kike tunanin zanci gaba da barinki awancan matsaya dana barki dashi azuciya tunna k'uruciya. Bakiyi tunanin zan canja miki matsayi saboda canjin da nagani zahiri agareki ba Toki kama kanki tunkan dare yayi miki dan tun ranar da kika kaini wajen boka da nuna min malami ne. Tun daga Wannan ranah nasaka azuciyata TAUDHAT d'in dana sani ba itace yanxu ba. Saiyakasance daga ranar dana gane kice kishiyata nacanja nima nazama wata NUFAISAT wacce keda kanki zaki furta nan gaba ba wacce kika sani bace. Sannan da kike cewa naje nanemi takaddar sakina a wajensa naje can nanemi daidai dani. To ADAMS shine daidai dani. Ko an gaya miki ina d'aya daga cikin jerin matayen da suke barma karuwai mazajensu ne. Wallahi idan ni banje nace yaban takaddata ba ke zakije kice mai ya baki taki saboda qarfinki da zanfi akan komai.. Ya kamata kigane lokacin dazan iya baki yaxo qarshe dan haka kifitarmin daga d'aki saboda y'ar uwata Zainab zatazo ina San nayi mata wani abu wanda zatasa abakinta. Kinsan yanxu NUFAISAT ta iya girka fiye da tunaninki. Murmushin takaici TAUDHAT tayi. Wato NUFAISAT batasan wacece ita ba. Rai bace tace da ita.. "Ke kin isa ki jefeni da mugayan kalamai sannan na futta daga d'akinki batare dana mayar miki kona d'auki fansa ba. NUFAISAT tayi mata kallan tsana tace. "Na k'ara miki lokaci to. Kina da damar mayar min koki d'auki fansar... Ai NUFAISAT bata ida zancenta da numfashi ba TAUDHAT ta ɗauketa da wani shegen mari... Cikin b'acin rai saboda jin wata sabowar maguwar tsanarta da taji tsanar datafi tako yaushe muni.. Cikin matuk'ar mamaki tayi saurin dafe kuncin tana tare da cewa.. "TAUDHAT ni NUFAISAT ni kika Mara..😨 Girgiza mata kai TAUDHAT tayi da murmushin mugunta tace.. "aa.. Kawai dai na maimaita miki irin wanda mijinki yayi miki ne agabana. Saboda na lura idan haukarki tatashi sai'an tab'a lafiyarki kike dawowa cikin hankalinki. Saidai zanso kikoma gefan kujerarki. B'cos idan kin tashi sumewa ki sume kan kujerarki. Saboda ayanxu bame rikicewa wajen San ki farfad'o saidai ki wucce daga nan idan kuma kina da nisan kona ki farfad'o da kanki. Oho na manta kince zainab zatazo idan tazo tatemaka da yayyafa miki ruwa wajen farfad'owan...... Aiko itama TAUDHAT d'in bata ida zancen nata da numfashi ba NUFAISAT ta ɗauketa da wani masiyacin mari... Wanda hakan bai isheta ba sanda taqara mata da wani. Daga ƙarshe kuma ta rufeta da duka tana cewa bara na nuna miki cikakkiyar haukan... Lokaci d'aya fad'a ya kaure tsakaninsu..... Dai dai da lokacin da Asiya me yima NUFAISAT hidima tashigo falan ita da Zainab yayar NUFAISAT d'in. Hankalin Zainab ya tashi matuqa dan ita macece wacce bata saba da ganin fad'a haka manya dasu ba... Duk yanda sukaso ita da Asiya su rabasu amman abin yaci tura. TAUDHAT ta d'auki wata kwalba ta turare ta rotsama NUFAISAT agefan ka🙆🏻‍♀.. Ai daga nin haka cikin Zainab ya d'uru ruwa... Bata San lokacin data danna number na Adams ta gaya mai gashi NUFAISAT da TAUDHAT suna fad'a zasu kashe junansu ba... Zuwan Adams office d'insa kenan yaji wannan mummunan labarin abakin TAUDHAT... Ai ba shiri ya fitto daga office d'in ya shige mota da tsawa yake cema direbansa yayi sauri yanxu ya maida shi gida... NUFAISAT najin azabar rod'a mata kwalbar da TAUDHAT tayi nan taje tararomo wata bishiyarta dake gefan TVstan d'inta tanufo TAUDHAT da ita gadan gadan da nufin ta caka mata aciki kasancewar bakin bishiyar yayi sirisiri tsini tsini haka. amman TAUDHAT ta kauce aiko sanda NUFAISAT ta caketa agefan mazauninta... Nan ko jini ya fara fitta daga wajen kamar yanda jini ya wanke fuskar NUFAISAT... Ai bashiri Zainab da Asiya suka kwalla qara da rabtaba salati suna masu neman akawo musu agaji. Dan ahakan ma ba denawa sukayi ba.. Dan NUFAISAT yar da bishiyar tayi da niyar cakamo wiyan TAUDHAT saidai kamar TAUDHAT d'in ta ankare nan ita tafara kamo wiyan NUFAISAT suka zube kan tiles duk jini ya b'ata musu jiki... Dai dai nan Adams ya sawo kai cikin falan dan anan yaji hayaniyar... Taqer ya iya rabasu ransa yayi matuqar b'aci basoda yanda jini ke fitta daga jikinsu amman dan bala'i basu sararama junansu ba.... (Shed'an la'ananne daya had'a futunar yana gefe yana musu dariya.) _Allah ka karemu daga sharrinsa Ameen_ Haka Adams ya danne zuciyarsa yasamu suka lallab'asu suka shiga cikin mota harda shi direban yajasu yana cema Zainab dan Allah tad'an jirasu yanxu zasu dawo.. Toh tace mai cikin damuwa. Dr Aryan ne dai ya dubasu.. NUFAISAT tasha nani wajen saman kunnanta Yayinda TAUDHAT tasha gyara a gefan mazauninta Adams baice musu komai ba. haka suka qara shiga motar wannan karan shiya jasu. Ababban falan nasu ya had'asu yana me tambayarsu meya tayar musu da wannan futunar.. Duk shuru suka mai. Ransa ya qara baci afusace yace da NUFAISAT... "Ke nakeso ki fara bani amsar tambayata... Shuru tamai.. Ya maida kallansa ga TAUDHAT yacigaba da cewa.. Ke fad'amin Jan numfashi tayi da cewa.. "Kawai kayi hakuri.. Qara maida kallansa ga NUFAISAT yayi da wurga mata wani kallo Yace.. "Wato ban isa ba ko.. Jan numfashi tayi da tashi taje ta kama qafarsa da marairaicewa tace. "Dan Allah kayi hakuri mijina. Wallahi ba yanda zanyi da ita ne dole saina kulata.. Nasan kana sane da canjin dana samu jiya akan na amince da zama da ita matsayin abokiyar zamana kuma y'ar uwata. Ashe abin bai mata dad'i ba dan taso na dauwama cikin jin tsanarta saboda tana San yin amfani da Wannan damar dan kawai kadinga ganin lefina Wannan dalilin yasa kana fitta d'azu tabiyoni part d'ina akan wai munafuncine yasani canjawa ba canjin Allah da annabi bane.. Raina ya b'aci mijina hakan yasa nace mata ita batakai matsayin dazan canja mata dan munafunci ba. Waime zaisa nace mata haka. Kawai saiji nayi ta fallamin mari. Kaima kasan bazan iya jure hakan ba Gaskiya. shine na rama fad'a kuma ya kaure tsakaninmu. Ina ganin shigowar Aunty Zainab naso barin fad'an amman nakasa saboda TAUDHAT d'in taqi barina... Na rigada na yafe mata mijina kawai fatana tayarda da abinda nace mata adaran jiya dan musa ma maka farin ciki. Ban iya qarya ba mijina. Toh akan me yasa zanma TAUDHAT bayan nasan tafi kowa sani nah.... NUFAISAT na kawowa nan azancenta tafashe da kuka tana meci gaba da cewa "Wallahi ina sanka mijina.. Dan Allah ka gaya mata ina San zama da ita lafiya tunda mommy tamin magana akan bada niyar ta bak'anta min rai ta aureka ba. Dan tasan TAUDHAT bazata ta tab'a cutar dani ba. Ashe ba gaskiya bane da wani abu aranta. Pls ka gaya mata har gobe bazan dena qaunarta ba... Saboda qaunar da nake mata ta jinice hakan yasa bazan iya jure zaman tashin hankali da ita ba... Jan numfashi Adams yayi da d'agata daga durqushen da tayi ta zauna a gefansa kana ya kalli TAUDHAT da cewa... "Kinji abinda tace.. Shuru TAUDHAT tayi dan bata tab'a tunanin cikin lokaci qanqani NUFAISAT zata iya sharara qarya cikin makirci haka ba Kanta ya kulle sosai.. kodai dama kallan biri take mata ita kuma tana mata kallan ayaba.. Hmm idan ko haka ne dole tatanadi makaman yaqi ta nunama mata ruwa ba sa'an kwando bane Kwata kwata yanxu bata San mema zatacema Adams d'in ba Shiko ganin tayi shuru sai kawai ya yarda itace bata da gaskiya saboda hakurin data bashi tun da farko. Dama kuma bai tab'a kama matar tashi NUFAISAT da qarya ba. Ji yayi ya gamsu da abinda tace mai.. Dan haka ya kira Zainab yayar NUFAISAT dake falan NUFAISAT d'in awaya ya tambayeta akan me tasani akan fad'an nasu. Ta tabbatar mai ita kawai zuwa tayi tasamesu suna yi wallahi batasan meya had'asu ba... Jin hakan yasa ransa ya qara b'aci da TAUDHAT dan ya yarda itace bata da gaskiya Wato kamar yanda NUFAISAT d'in tafad'a ita TAUDHAT tafisan taga tashin hankalin NUFAISAT d'in ita kuma ta dinga binsa bin munafunci... Hmm mata mata... Ahankali ya kalli TAUDHAT d'in da cewa.. "Banyi tunanin hakan kuma daga gareki ba. Watoh da wani abu aranki.. To bari kiji zan iya yimiki komai akan NUFAISAT matuƙar zaki cutar da ita. Danna aureki ne saboda iyayena da suka sani qara Aure Sannan na zab'eki ne dan ina da tabbacin bazakiba NUFAISAT matsala ba Ada tayima Auran namu kallan bamuyi mata adalci ba Hakan yasa tayi mana buri cikin rashin fahimta Yanxu kuma data gane gaskiya me yasa kika d'auki hakan amatsayin munafunci tayi.... Kallansa TAUDHAT tayi da niyar yin magana amman yayi saurin katseta da cigaba da cewa. "Bana San kicemin komai Danna fiki sanin matata duk da atare naganku. Bata tab'a zama tayi min qarya ba. Haka kuma na tabbatar bazata fara min akanki ba Dan haka kinutsu karna qarajin kinje shashinta kin nemeta da fad'a dan ina San rayuwa da ita sosai sannan ina San rayuwa dake saboda ina fatan nasamu abinda iyayena suke fata daga gareki... Yana kaiwa nan ya ficce daga falan zuwa ga motarsa direba ya jasa cikin sauri... Tashi NUFAISAT tayi da kallan TAUDHAT kallan tsana tace. "Shegiya annamimiya ina zaman zamana da mijina kika wani kama kika shigo rayuwarmu danki b'ata tunaninmu. Tota ALLAH ba taki ba Kuma wallahi yanxu mukasa qafar wando d'aya dake. Cikin ni dake zanga waye zaije yace yabashi takaddarsa. Tsananniya me jin d'and'anan maza.. Tana gama gaya mata hakan ta ficce daga falan zuciyarta cike da farin ciki dan ganin yanda ran TAUDHAT d'in ya b'aci kamar tad'auki bindiga ta harbeta.. Haka ne kuwa dan da sanyin jiki TAUDHAT d'in tatashi dayin part d'inta tana tuna mezatama NUFAISAT itako ta wucce arayuwarta... Na gaida kowa kyauta🙋🏻‍♀ [7/1, 10:18 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم ☆page 15☆ Zainab na ganin NUFAISAT taje ta rungumeta tana cewa... "Masha Allah. Nagode ma Allah dayasa bata cutar min dake da yawa ba.. Taqarashe tana me sakar mata kiss a kunci.. Zama sukayi NUFAISAT ta kwashe abinda ya jawo musu fad'an dayanda sukayi da Adams kaf tagayama Zainab d'in. Sannan taqara da cewa.. "Wallahi Aunty Zainab natsani TAUDHAT tsana mafi muni.. Kuma wallahi nashirya karb'an kowane irin sak'o daga gareta. Zan bata mamaki matuqa ta gane NUFAISAT d'in data sani me sanyi ba itace yanxu ba.. Jan numfashi Zainab tayi da cewa.. "Bana San tashin hankali NUFAISAT.. Dan haka ki barta haka nan. Dan nafi buqatar rayuwarki fiye daki kulata.. Kinga taso nakasamin ke aka.. Gaba bamu San ina zata kai miki hari ba. "Kar wannan ya dameki Aunty Zainab. Hakan ma daya faru qarin ilimin zama da itane nasa muh. Dan haka karki gayama mommy saboda bani San hankalinta ya tashi.. "Bazan gaya mata ba. Amman dan Allah karki qara kulata.. Murmushi NUFAISAT tayi da cewa.. "Toh zan kiyaye.. "Kinga Asiya ta share miki ko ina tsaf. Sai idan Allah ya kaimu gobe zan tawo miki da wasu kwalaban turaran kimaidasu wajen da way'ancan suka fashe.. "Ba damuwa aunty Zainab nagode Janyo jakarta Zainab tayi da bata ingantaccun magungunan da mommy ta bata ta bata Nan tashiga mata bayanin yanda zatayi amfani dasu. Sosai NUFAISAT taji dad'i aranta.. Zainab ma sanda ta'ibi nata raban tana me cema NUFAISAT d'in.. "Na lura momy tafi ji dake aduk cikinmu... Murmushi kawai NUFAISAT tayi mata dan da gaske mommy tafi bata kulawa.. A haka agurguje sanda Zainab ta qara bata haske kan girki kafin tabar gidan zuwa ga office d'inta dan yau kam tayi latti over. TAUDHAT wini tayi da baqin ciki da takaici. dan har kuka sanda tayi. Ranta bai tab'a baci irin na yau ba Tasha alwashin saita sa Adams ya wulaqanta NUFAISAT agabanta kamar yanda yanuna mata qiri qiri yafi san NUFAISAT d'in akanta. Wato ita ya Aureta ne dan kawai samun wani buqatarsa.. Kwafa tayi dajan tsaki tana me cije leb'e Ashe fitan Adams gidan mommyn d'in Nufaisat yayi. Bayan sun gaisa yayi mata kyauta me tsoka dace mata dan Allah ta qara Jan hankalin NUFAISAT dansu zauna lafiya da TAUDHAT.. Mommy tace wani abu ya faru ko. Yace mata aa kawai dai yana buqatan taqara Jan kunnanta ne akan hakuri.. Mommy ta tabbatar mishi zataja kunnanta shima dan Allah yayi hakuri da ita.. Murmushi yayima mommy d'in kawai Yana fitowa daga gidan ya shiga gidansu TAUDHAT.. Inda suka gaisa da mamah cikin kulawa. Kana ya bata kyauta itama me tsoka sannan ya gaya mata dan Allah itama taja kunnan TAUDHAT su zauna lafiya ita da NUFAISAT.. Murmushi mamah tayi cikin damuwa tace dashi.. "Wato Adams saifa kayi hakuri da TAUDHAT. Dan ni nasan wacece TAUDHAT Ina rokwanka da Allah kayi hakuri da halinta sannan kada kayi gangancin yarda da duk wani abu da zata gaya maka akan NUFAISAT danta had'aka da ita. Wallahi wallahi wallahi kaji rantsuwar uku kenan. NUFAISAT tafi TAUDHAT kyen hali nesa ba kusa ba Kar gigin dad'in bakinta ya ibeka ka musguna ma baiwar Allah NUFAISAT. Danni nasan halin TAUDHAT bata da dad'i. Dan Allah kayi hakuri da ita.. Jan numfashi ADAMS yayi da kallanta yace.. "Ba komai Mama. Insha Allah komai zaizo da sauqi. Tayi Murmushi da cewa.. "Toh madallah... Shine daga nan ya wucce office... Da misalin qarfe shida da rabi ko na yamma ya tashi daga office kamar yanda yasaba Kofar NUFAISAT arufe take data wajen data cikin baban falan nasu. dan haka yayi part d'insa dayin wanka yayi masallaci sanda akayi sallar Isha'i dashi sannan ya wucce gidansu ya gaisar da iyayen nasa. Kana ya dawo gidan nasa. A can uwar d'aka yau yatarar da TAUDHAT.. Tana jin shigowarsa ta wani rumtse ido. Ganin hakan sai yayi tunanin tayi bacci ne.. Dan haka bai tasheta ba yayi dining inda yaci abindata dafa mai.. Bayan ya gama yaje bedroom d'insa yana saka abubu da dama.. Gaskiya mata suna da matsala... A hankali ya danna number na NUFAISAT dan kiranta.. Lokacin tayi nisa abacci. Kuma abin dayasata baccin kanta ne ya dameta da ciwo sosai. Hakan ne yasata kwantawa tana idar da sallar isha... Taji dawowarsa d'azu lokacin tana toilet kuma kofar tata arufe take. Da d'an magagin baccin nata ta amsa wayar tasa da "hello "Bacci kikeyi ne "Kaina ne yake min ciwo "kin sha magani "Eh dama na shane na kwanta "Bari naxo na dubaki naga jikin ko "Aa kabari sai gobe jikin da sauqi "Kin tabbatar "Na tabbatar mijina "Toh ki kula min da kanki tare da addu'a kinji Murmushi tayi da cemai.. "Toh ya jikin TAUDHAT itama "Tayi bacci "Ok. Kaima kayi bacci da wuri haka. dan ina San katashi da qarfin jiki.. "Toh.. yace mata da kashe wayar.. Shuru yayi yana tunin gaskiya bazai iya bacci shi kad'ai ba.. Dan haka tashi yayi ya koma bedroom na TAUDHAT danya tasheta suje su kwanta anasa bedroom d'in. Saidai dayaje ya qare mata kallo sai yaga tabashi tausayi. Dan ga gunda aka mata gyara ya kumbura kad'an.. Dan haka a hankali ya ratsa gefanta ya kwanta da rungumarta.. Tana jinsa ta qara rintse idanta.. Dan zuciyarta cike take da qarin jin haushinsa. Saboda d'azu daya dawo yayi wanka ya fittan nan taji ciwan yanda ya baibi takanta ba. Haka kwanan bakwai d'in TAUDHAT yayi sam bata wani ji dad'insa ba Dan Adams d'in ya d'an canja mata kad'an Itako NUFAISAT ranar daya dawo d'akinta ba qaramin dad'in juna sukaji ba.. Saboda yanda sukayi missing d'in juna sosai taga zalamar Adams d'in akanta Ranar dazai koma d'akin TAUDHAT sanda ta lura da canjawar da yayi alamar baiso hakan. Jan numfashi tayi da cewa aranta nafika buqatarka mijina dan kai d'in na musamman ne Yau da safe TAUDHAT take cema Adams zata gidansu ta duba mama dan tayi wani mugun mafarki akanta. Shine take San taje ta dubata ko hankalinta zai kwanta... Kallanta yayi kad'an da cewa. "Toh ki shirya na sauke ki.. Da d'an marairaicewa tace.. "Daka tafi abinka naje tunda ban gama aiki ba.. Wani kallo ya aika mata wanda nan take ya shigeta. Saidai bazata iya cewa ga abinda kallan yake nufi ba. "Ko bayan nan akwai inda kike San zuwa ne. Yace da ita hakan bayan ya kauda kallan nasa daga garetan. Saurin girgiza mai kai tayi da cewa.. "Bani da wajen zuwa gaskiya.. "Imma kina da shi saidai kiyi hakuri. Dan lokacin dana d'aukar miki ki fara fitta bana kusa bane.. Tashi tayi da cewa.. "Na hakura da aikin idan na dawo nayi. Bara na d'auko gyalena muje. Shima tashin yayi da d'aukar jakarsa yana me bata amsa wajen cewa. "Bara naga NUFAISAT ki sameni a mota.. Ya samu NUFAISAT kwance kan gado da alama bacci take Sanyi "Good morning my lau. Fatan ka tashi lafiya. "Lafiya lau my dear. Kema kin tashi lafiya. "Lafiya lau.. "Toh masha Allah. Lokaci yayi zan tafi office. "OK. Allah ya kaimin kai lafiya ya dawomin dakai lafiya. "Ameen. yace mata da sakar mata kiss a goshi kana yaci gaba da cewa.. Da alama TAUDHAT tayi kewar mama ne. Dan haka zamu sauketa agunta mu wucce.. "Ok. Amman dan Allah kace mata karta dad'e tabarni ni d'aya "Baki da matsala. Yace da ita hakan da ficcewa. Murmushi NUFAISAT tayi. Amotar yasami TAUDHAT tawani saka wani qaramin gyale. A hankali yace mata.. "Bana san ki qara saka gyale qarami haka.. Da wani salo tace mai. "Insha Allah zan kiyaye.. Haka suka sauketa yana ce mata qarfe nawa zata koma gida tace da yamma. Yace toh idan ya tashi zasu biyo su d'auketa. Da murmushi tace mai toh. Mamah na wanke wanke sai ganin TAUDHAT tayi. Cikin mamaki tace.. "ALLAH dai yasa lafiya.. D'an yatsina baki tayi dace mata.. "Lafiya lau. Dama inasan karb'ar wani abu ne agun wata qawata shine nama Adams qarya akan ke nake San gani shine ya saukeni yanxu. Da yamma zai biyo ya d'aukeni. Dan haka bara naje na dawo... Tana gama fad'in mata hakan ta ficce daga gidan bata saurari cewarta ba. Mamah ta girgiza kai tacewa aranta Allah ka shiryar da ita.. TAUDHAT bata zame ako ina ba sai akan layinsu tatari kekenafaf sai gidan malamin nata... Dan tayi tunanin idan tace zata gun bokan nata zai d'auketa lokaci me tsawo. Shiyasa taso fita da motarta abin yaqi yuhuwa.. Malamin nata na ganinta yasaki murmushi da cewa. "TAUDHAT kenan. Sai gaki kamar ruwan sama agabana "Toya zanyi.. ina San naci uban NUFAISAT da sauri ne "Wacece kuma haka "Kishiyar tawa mana "Hmm! Matsalarku mata kishiya dai.. To bara na fara duba miki ita d'in. Shuru TAUDHAT tamai tana ganin yanda yake zana qasa cikin gwanancewa.. Can ya dubeta da cewa naga komai. Dan haka tashi muje ciki kafin kiji kanun labaran.. Babu musu TAUDHAT tayi cikin wani daki dake cikin inda suke. Gado ne da katifa wajen atsaftace yake. Haka malamin nata ya tashi ya kulle kofar tashi yabita ciki Ba abinda kakeji sai qarar gado da gurnaninsu.. "Komai ya kammala.. inji malamin nata dayake kallanta cikin wani hali. Murmushi tasakar mai da cewa.. "Hmm naga ka qara fawa kamar ba shekaru kake qarawa ba. Yace.. "Gani nake kodai kece yasa abar tawa take qara qarfi nan da nan "Anyi shegen malam anan.. tace dashi hakan tana me tashi daga gadan dan d'aukar kayanta tasaka... Binta da kallo yake from up 2 down yana ganin yanda tsarin halittarta take. Dukdako bayau bane yasaba ganin hakan Nan da nan kwad'ayinsa ya qara tashi ya wani rarumota da sauri yana cewa dan Allah ayanxu kiban minti biyar kacal.. "Malam Isma'il kenan. Idan da sabo yaci ace nasaba da wannan gyaran naka Danna lura Sam baka iya ganina babu komai jikina kabarni ta hanyar lallami. Har sai munyi fad'a hankalinka yake kwanciya. Duk duniya ban tab'a cin karo da mutumin daya ke d'aukar sama da awanni bakwai yana jina ba saikai da mijina.. Da nayi tunanin daga kai babu wani. Ashe akwai maza asamanka. Danna mijina yaci uwar naka.. Saidai kayi hakuri ayanxu babu maganar gyara tsakaninmu.. Idanko kaci gyaranka katabbatar gaba idan nazo babu kai babu jina... Murmushi yayi ganin takai qarshen zancen nata yace. "Yanda na qara kwad'aituwa dake ayanxu. bani tunanin iya barinki. Dan haka komai ma ya faru nan gaba... Ba kunya ba jin tsoran Allah haka sukata aikata masha'arsu.. Bashi ya barta ba sai kusan biyu da rabi na narah Dan haka tsasashi agaba kan ya gaya mata komai d'in daya gano.. Jan numfashi yayi da cewa.. "Gaskiya TAUDHAT kishiyarki ba qaramar hatsabibiya bace.. Wato kallan kitse kikeyima rogo.. Dan NUFAISAT ta wucce dukkan tunaninki.. Kawai kibar kaza acikin gashinta.. Dan tsefeta ba qaramin wahala zakici gaba ba Yanxu dai ki fuskanci matsalarki kawai dazan gaya miki.. "Ban gane me kake nufi ba. Kana nufin cin mutuncin da tamin da abinda mijina yamin agabanta nabarshi ya tashi abanza kenan.. "Eh haka nake nufi "Toh wallahi bazai yuhu ba "TAUDHAT kina da taurin kai akan abubu da dama. amman tunda so kike na tsefe miki komai kiji dalla dallah tobara kiji kyau. Bazaki tab'a cin galaba akan NUFAISAT wajen asirce asirce ba. Dan aranar da kukayi fad'an ba qaramin dafa'i uwarta ta aiko mata dashi tasha ba. Sannan kin Santa da ibada akan lokaci da tsayuwar dare. Bata zuwa wajen boka ko malam akan lamuranta Allah d'aya tak tasa agaba. Ina tabbatar miki Idan kikace zaki mata wani mugun abu wallahi kanki zai dawo. Bar kuri da cika baki akan kinyi wani babban kamun boka idan kikaje wajansa ya miki wani mugun abu akanta wallahi TAUDHAT koba jima ko ba dad'e saiya dawo kanki.. Dan haka kisama kanki kwad'an mutunci ki kasheta da kirsa da kisisina irin taku ta mata. Sannan zan baki wani magani ki saka agabanki wanda idan mijinki ya kusanceki bayan kin saka maganin? Wallahi bazai qara jin dad'in Kishiyarki NUFAISAT wajen auratayya ba..😎 Idanko kikaga yaji dad'inta ba qaramin aiki taje aka mata ba.. Amman kina da damar da zaki iya sawa amata wasu qananun abubuwa saidai su d'inma ba tasiri zasuyi sosai akanta ba. Jan numfashi TAUDHAT tayi cikin matuqar jin haushi. Ta yarda da malamin nata akan fad'a mata gaskiya da yake yi. Kuma ba wani abu bane yake sawa yake gaya mata gaskiya tasani dan baya San yayi missing d'in jikinta ne. Tasan ita kad'aice take iyawa dashi kamar yanda ya tabbatar mata.. Ita yanxu babban baqin cikinta d'aya shine yanda bazata iya aikatama NUFAISAT wani mugun abu ba. "Kai gaskiya da sake... Ta fad'i hakan abayyane tana me kallansa taci gaba da cew.. "Hmm nasan kana da dabara akan abubuwa da dama na mugun abu ga wani. Ina San na musguna rayuwarta pls ka taimaka min mana. Dariya yayi da cewa. "Ke wani zubin kamar baki da wayo Sam. In banda abinki ai babbar cutarwa dazaki mata d'ayane shine kisa mijinta ya dena kusantarta. Ina akan abinda kukema kishi kenan mata. Idan kika mata haka kin kasheta da ranta. Dan zata zama photo ne agidan kece matar gida. Dan azahiri ADAMS zai dinga nuna miki kulawa dan kin d'auke madarajarta agaresa. Amman idan kikace zaki haukatar da ita ko kisaka fad'a atsakaninsu ko kizama kece kyentattatciya agidan ko yarabu da ita ko ya dinga wulaqantata da sauransu nagaya miki hakan dawowa kanki zaiyi.. Shuru TAUDHAT tayi tana nazarin maganar tashi.. Can taja numfashi da kallansa tace nayarda da abinda kace. Kuma na gamsu.. Yanxu bani maganin na qara gaba.. Miqa mata wani kulli yayi da cewa.. Ki kwab'a da jinin al'adarki ko ruwan ni'imarki. Karb'a tayi da cewa "nagode bara naje.. "Ai bakiji qarashen zancen nawa ba. "Toh kuma menene yanxu. "Kishiyar sirikarki Hajjiya Rukayyat tayi miki illa fah. Waro ido waje TAUDHAT tayi cikin tsoro tace.. "Metayi min😳 "Tabaki wani abinci kinci wanda yake d'auke da magani.. Gyara zama TAUDHAT tayi da cewa.. "Eh haka ne. Dan sunzo kawo kayan aure na tabani nama me d'auke da magani akan maganin mata ne. Wai tabama kishiyata mah? Shiyasa take juya Adams yanda take so. Dan haka gashi nima naci danta d'aukemu duk d'aya ne.. Murmushi yayi da gyara zama shima yace.. "Toh ba gaskiya bane. Kinsan maganin me tasaka miki aciki.. Girgiza mishi kai TAUDHAT tayi.. Yaci gaba da cewa. Maganin hana d'aukar ciki ne.. Maganin dabazaki tab'a haihuwa da ADAMCY ba tabaki. Ammafa shi kad'ai. Zaki iya haihuwa da wani amman banda Adams. Wannan shine gaskiyar zance... D'ora hannu aka TAUDHAT tayi ta zambad'a ihu dana cewa.. "Kutumar bura'uba.. Meyasa tamin haka. Tab'e baki malamin nata yayi da cewa.. "Nima ban sani ba. Dan nayi duba nagane meyasata yi miki hakan banga komai.. Da b'acin rai TAUDHAT ta katseshi da cewa. "Hmm lalle ta ibo ruwan dafa kanta.. Dubamin kagani itama banda ikwan yi mata komai kamar na NUFAISAT ne.. Gayara zama yayi dayin zane zanansa can yayi murmushi dace mata.. "Kina da ikwan yimata komai dan tana wasa da sallah.. Sannan itama ai biye biye takeyi sosai.. Qilama tafiki yi. Dan daga dukkan alamu tayi mugayan abubuwa sosai akan jama'a.. Sheqewa da dariya TAUDHAT tayi da cewa.. "Kasan me zaka mata.. Girgiza mata kai yayi.. Taci gaba da cewa. So nake kajefeta yanxu ka kwantar min da ita yanda zata kasa komai arayuwarta.. "Kai TAUDHAT. Ayi haka "Mezai hana kuwa. Kashe min rayuwa tayi fah. "Kuma fa haka ne. "Ashe kagane. Maza jefe gangan jikinta naji sanyi araina. Ba b'ata lokaci yahau yin wasu surkulle nan take ya jefa wani dutse sannan ya kalleta da cewa.. "Tashi kije gida zakiji tana asibiti. Kuma ba abinda zasu iyayi mata.. Dariya TAUDHAT tayi da cewa.. Tukwicin wannan abun daka min shine zan had'a kai dakai kamin ciki mijina ya raini d'an malam.. Washare baki yayi cikin matuqar jin dad'i yace.. "Kai amma TAUDHAT kin biyani dan naji dad'i sosai.. Tashi tayi da yafa gyalanta ta sab'a jakarta tace.. "zaka jini bayan kwana biyu. "Ina nan ina jiranki sarauniyar mata.. Takawarki lafiya. Ba wata mace daza tasha gabanki Hajjiya TAUDHAT.. "Kwad'awar taka ta isa haka. Kaidai kaga tafiyata.. Cije baki yayi cikin matuqar jin dad'i. Shi kad'ai yasan abinda yake ma murnah Sam bata wucce gidansu ba gidanta ta wucce. Amman takira Adams ta gaya mai ta wucce gida basai yaje gidan nasu d'aukarta ba.. Dan tayi baqi ne. "Ok. Yace mata.. Sannan takira mamanta tagaya mata ta wucce gida.. Da misalin qarfe tara na dare NUFAISAT ce kwance kan d'aya daga cikin kujerun falanta. Tunani take meya hana ADAMS dawowa gida da wuri Yau A hankali tad'auki wayarta dan takirasa sai kuma taji dawowarsa damasu tsaransa... Da sauri taje ta bud'e mai kofar falanta dan tasan nan zai fara murd'awa.. Aiko haka ne. Dan part d'inta ya fara nufa kamar yanda ya saba. Ganinta a bakin kofar ya bashi mamaki. Kan yayi mata magana ta rungumesa tana cewa.. "Haka kawai naji gabana na fad'iwa na rashin ganinka da banyi ba lokacin daka saba dawowa. Duk dako. Bayau bane karo na farko daka tab'ayin hakan. Murmushi yayi da d'ago da fuskarta da yayi ya manna mata kiss da cewa.. "Wallahi momy Rukayyat ce bata da lafiya.. Wai tana shiga kitchen sai qarar fad'uwarta akaji.. Salim ne ya kawota asibiti. Saidai duk binciken da doctors sukayi basuga abinda ya haifar mata da hakan ba.. Cikin damuwa NUFAISAT tace.. "Ikwan Allah. Toh yanxu me yake damunta. "Komai fa najikinta yanxu ya dena aiki.. Kawai bakinta ne yake aiki wajen magana da idanunta da suke ganin mutane NUFAISAT taja numfashi tace.. "Toh dama mutane sunayin irin wannan ciwan ne.. "Gaskiya ban tab'a gani ba. Ki kwantar da hankalinka zata samu lafiya.. Cikin damuwa taraba jikinta da nashi tace.. "Toh Allah ya yarda.. "Amiin yace daci gaba da cewa. Bara naje nayi wanka naga qawar tamu dan kwata kwata a gajiye nake.. Murmushi tayi da cewa. "Kadai fara cin abinci danna hango yunwa cikin kwayar idanka.. Shafa gefen fuskarta yayi da bata amsa.. "Dama anan nake danafi jin dad'i danfa gaskiya kinfi TAUDHAT kula dani. Murmushi taqarayi da fad'in. "Zan koya mata komai wanda zaisa kaji tafini kula dakai. "Bana tunanin hakan. Nadaifi yarda dazaki koya mata daidai da yanda kike min "Toh idan nayi mata hakan aizata qara da tata basirar. Kaga kenan dole tafini kula dakai "Kawai dai naji saida safe. "Dan Allah katashi da wuri dan musamu zuwa duba momyn akan lokaci.. "Murmushi yayi da cewa.. "Kema kinsan bana wucce lokaci.. "Nafa fad'ane kawai dan naji dad'in bakina "Idanko haka ne nayi miki alqawarin bazaki ganni ba.. sai qarfe goma na safan.. "Wayyo Allah mijina dan Allah karkamin wannan horan.. Duk da cewar a d'akin y'ar uwata kake zanji ba dad'i sosai idan nakai wannan lokacin banga kyakkyawar fuskarka ba.. "Alk'awarifa nayi. Dan haka ki kwantar da hankalinki dan saina cika.. Yana fad'in mata hakan ya ficce daga falan yana murmushi.. Dafe kanta tayi da kulle kofar tata tana cewa. "Najama kaina. Kai baka san kuncin danakeji araina bane idan naga ka fito daga part d'in TAUDHAT.... .... Da gaske Adams yaji canji agun TAUDHAT canjin dabai tab'a ji arayuwarsa ba.. Dan sanda ta aikata abinda da malamin nata yace tayi.. Dan zama tayi tajanyo sha'awa tayi amfani da ni'imar tata wajan kwab'a maganin.. Sannan tasaka bayan sallar Isha'i Daqer da sid'in goshi Adams ya iya barinta acikin wannan dare Shi kansa yayi mamakin kansa.. Dan kwata kwata wannan dare bai samu wani ishash shan bacci ba Hakan yasa ana idar da sallar asuba bai wani tsaya zakirorin daya saba ba. Ya dawo gida ya kwanta. bashi ya tashi ba sai kusan tara saura Kuma ahakan ma yana had'a ido da TAUDHAT saiya tuno da daran nasu na jiya nan take sha'awa ta kamasa. Har saida yasamu biyan buqatarsa agaggauce sannan hankalinsa ya kwanta.. Lokacin daya gama shirinsa na fitta office goma saura minti uku.. A hankali ya kalli TAUDHAT yace.. "bazan tab'a yarda da cewar ba abinda kikamin fittarki jiya da kikayi. Kallansa tayi da murmushi tace.. "Ni TAUDHAT me zan yima mijina kuwa. Murmushi yayi da cewa "Nafa jiki jiya fiye da yanda nasaba jinki.. "Inaga dai addu'atace ta karb'u wacce nakeyi babu dare babu rana akan Allah yasa kadinga jina fiye da kowace ranah arayuwarka.. Murmushi ya qarayi da fad'in.. "Hmm.. Najiki kuwa. Dan atahirin rayuwata bana tunanin natab'a kaiwa wannan lokacin ba ranar asabar da lahadi ba? ban fitta ba. Ina tunanin tun angwanci na da NUFAISAT.. Dariya tayi da cewa. "Wata qila nima dai kanasan kayimin kara ne wajen hakan... "Ai kin rigada kinci amarcinki babu kara. Kawai dai naji can jin yayimin ne. Dan ALLAH gayamin miye sirrin.. Tashi tayi cikin shauqi tayafa gyalanta da cewa. "Babu wani sirri. Kaga jeka kaga qawata ina mota ina jiranku kar Ammi tace meyasa bamuzo da wurri ba.. Waro ido ADAMS yayi cikin wani hali yace.. "Ya Allah. Kinsan na manta momy na asibiti. Allah yasa su doctor Aryan sunyi mata wani qoqari.. "Lalle kace kanka ya kulle da yawa.. Bai kulata ba ya ficce daga falan ya nufi na NUFAISAT Kallan harara NUFAISAT d'in tayi masa.. Yayi murmushi da rungumarta yana cewa.. "Amin afuwa nayi lefi yau ko Kwace kanta tayi da cewa.. Sam ban d'auka da gaske zaka kai qarfe goman dakace ba.. Shi sai yanxu ma ya tuna wasan nasu na jiya. Dan haka ya fake dace mata ai alk'awari yayi mata... Da hakan yasamu kanta. A mota suka tadda TAUDHAT Sanda sukama kansu kallan kallo ita da TAUDHAT kana ita TAUDHAT d'in tayi mata murmushin qarfin hali dace mata.. "Barka da safiya k'awa da fatan kin tashi lafiya.. Da nuna farin ciki sosai NUFAISAT tace da ita.. "Barka dai.. Fatan kema kin tashi lafiya.. Daqer tace mata lafiya lau. Shima dan taga Idan Adams na kansu ne... Haka NUFAISAT ta shiga motar ADAMS shima ya shiga direban ya jasu masu tsaran lafiyarsa suka sasu a tsakiya cikin motocinsu suma.. Da suka iso asibitin NUFAISAT kamar tayi kuka ganin halin da mommy Rukayyat take ciki.. Ganin da gaske kukan take sanyi sai kawai taficce daga d'akin taje gun Ammi da kwantar da kanta kan cinyarta ta fashe da kuka tana ce mata. "Dama Ammi irin wannan ciwan yana kama mutum lokaci d'aya haka.. Ammi tace "bar kuka NUFAISAT addu'a take nema. Nima wannan shine karo na farko dana tab'a ganin ganin hakan.. ADAMS ganin NUFAISAT ta fitta sai yabi bayanta.. Ganin hakan yasa salim fitta shima danya d'auko wayarsa amota.. Saiya kasance daga TAUDHAT sai Hajjiya Rukayyat.. Dama Dady yana gida.. Dan haka sai TAUDHAT ta kalli Hajjiya Rukayyat da yatsina fuska tace da ita... "Hmm.. Bake tantiriya ba. Haka siddan dan baqin hali kika bani nama naci dan kawai karna haihu da ADAMS. shine dana gane kece kikamin hakan nima nayi miki hakan. Dan haka kisa aranki bake ba tashi saidai abaki abinci a baki awanke miki kashi da fitsari har qarshen rayuwarki.. Zaba mata ido Hajjiya Rukayyat tayi da mamaki tace.. "Wai kina nufin kece kikamin wannan abun.. TAUDHAT ta gyad'a mata kai cikin taunar cingam tace. "Nice mana.. Yasan ranki. Wallahi nice nan nayi miki..😃 Aiko nan take Hajjiya Rukayyat tafara gurnani nasan tashi amman abin ya faskara. TAUDHAT tayi dariya daci gaba da cewa.. kaji banza. Wai tunaninki zaki tashi ne. Da b'acin rai Hajjiya Rukayyat tace.. "Zako kici ubanki idan natashi. Dan saina miki abinda harki mutu bazaki tab'a mantawa dani ba... Dalla mata harara TAUDHAT tayi da cewa.. "Muci uban juna dai. Dan inke kin kwana kina shiri ni a hanya na kwana. Kajimin muguwar mata haka siddan ki hanani haihuwa da mijina. Shegiya azzalima... Shigowar Adams da NUFAISAT ne yasa TAUDHAT saurin yin shuru.. Dan fittan Adams rarrashin NUFAISAT d'in yayi dace mata.. Yanxu ba kuka momy take so ba. Addu'a takeso. Dan haka tatashi taje tayi mata addu'a zaifi da kukan da takeyi... Muje zuwa y'an hannuna👐🏼... https://www.instagram.com/p/BkZOMcllfcw/?utm_source=ig_share_sheet&igshid=15ya4yksqqc7d&r=wa1 [7/4, 3:13 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 16☆ Gefanta NUFAISAT taje tazauna tana cewa.. "Sannu momy. Bara nayi miki addu'a.. Shuru momy tayi mata dan ranta ba qaramin b'aci yayi ba. Jin TAUDHAT ce tayi mata wannan abu. A hankali taji tana jin dad'i ajikinta kasancewar addu'ar da NUFAISAT take mata. Jitake kamar ana fusgar wani abu ajikinta. Idan kuma NUFAISAT tayi shuru sai taji abin ya dawo mata.. Anan taqara yarda da abinda TAUDHAT ta gaya mata.. Ammi ta koma gida tayi wasu y'an aikace aikace sanda tadawo sannan su NUFAISAT suka bar asibitin.. Saidai suna tafiya Hajjiya Rukayyat ta d'agama su Ammi da salim da Dady hankali akan amaida ita gida Wannan ciwan nata bana asibiti bane. Abin ya basu mamaki sosai.. Nan suka shiga lallashinta kan tayi hakuri ad'an gwada sa'a anan d'in aga abinda Allah zaiyi.. Saidai fur taqi yarda. Lokacin data tayar musu da borin bakwai na dare ne... Dan haka a lokacin ko suka maida ita gida.. Abinda dako yasa Hajjiya Rukayyat rikice musu shine.. Wata aminiyarta Hajjiya Hadiza ce tazo dubata bayan tafiyarsu NUFAISAT. Shine Hajjiya Rukayyan take bata labarin TAUDHAT ce tayi mata hakan. Shine ita Hajjiya Hadizan take ce mata tota koma gida. Dan wannan ba aikin asibiti bane. Dan saidai su b'ata mata lokaci. Dan haka takoma gida zata dinga zuwa tana kawo mata magani harta samu sauqi Hajjiya Rukayyat tace yanxu bazata iya samun sauqi lokaci d'aya ba Kallan mamaki Hajjiya Hadiza tabita dashi tana bata amsa. Kema kinsan cuta lokaci d'aya take kama mutum. Sauqi ko sai'a hankali. Kedai ki kwantar da hankalinki. Tunda yanxu munsan meyajawo miki ciwan. Baki da matsala wajen samun magani. Kawai bakin aljihu zaki bud'e dan idan tana taqama ita gwanace toh wallahi mune gwanaye. Zataci ubanta ne. Badai tatab'omu ba. Murmushi Hajjiya Rukayyat tayi danta yarda da qawar tata Hajjiya Hadiza... Toh wannan shine abinda yasa ta hura masu Ammi wuta kan sai ammaida ita gida.. Kuma ita Hajjiya Hadiza tace mata Hakan ne dan tasamu nata raban ajikin Hajjiya Rukayyat d'in Dan tasan tunda taganta cikin wannan hali ba qaramin sakar mata bakin aljihu zatayi ba wajen san tabi bokayen da suke bi tasamo mata makarin aikin da TAUDHAT d'in tayi mata Ataqaice dai Hajjiya Hadiza tasa aranta zata nema mata magani ammanfa saita d'auki biyar ko bakwai tana samun nata kafin ta nemo mata maganin Suna isa gida ko Ammi takira NUFAISAT da TAUDHAT awaya ta gaya musu komai dan haka duk ran da suka tashi dawowa suxo gida kawai dan sunbar asibitin.. Toh sukace mata. Salim ya kalleta da murmushi yace.. "Ammi dakin bari nasan ya Adams zai gaya musu.. Itama murmushin tayi da cewa. Gwara dai dana gaya musu dan ka sanshi da mantuwa.. Hajjiya Rukayyat na jinsu tayi shuru tana saqa hukuncin da zata d'auka akan TAUDHAT idan tatashi... Dake shi Adams yana da matsala. Sam baya iya kwana baiji mace ba. Idan ko kikaga ya kwana bejiki ba. To qila kunyi fad'a ne ko yaga kina bacci me nauyi ko rashin lafiya. Toh shine zai barki amman bazai raba kansa dake ba wajen jin d'uminki. Hakan yasa yaji NUFAISAT a wannan dare. Kasancewar ranar girkinta.. Abin yazo mishi awani saban salo.. Yadai sani yafi samun nutsuwa da kwanciyar hankali agun NUFAISAT. Dan nesa ba kusa ba tafi TAUDHAT gamsar dashi. Amma sai gashi jiya yaji dad'in TAUDHAT dad'in dabai tab'a tunanin samu daga gareta ba. Ga kuma NUFAISAT Sam sai yajita babu dad'in komai ko kad'an. Wai me yake faruwa ne.. Kamar zaima NUFAISAT magana washe gari lokacin da yake breakfast.. Sai kuma ya fasa.. Abinfa bai canja zani ba. Dan yauma hakan ne ya qara kasancewa dashi agun NUFAISAT d'in Har Allah Allah yake washe gari tayi wato girkin TAUDHAT yajita ko zai dad'a jin abinda yaji daga gareta.. Haka ko akayi.. Yana shiga girkin TAUDHAT yaji komai zamzam.. Washe gari yana breakfast ne kawai amman hankalinsa na kan NUFAISAT.. Tunani yake wane irin canji ya samu agunta ne haka me d'aga hankali.. Shuru yayi da barin abin aransa har izuwa lokacin daya koma girkin NUFAISAT d'in.. Still abinda yaji awancan girkin nata shiya qara ji.. Dan haka da safe suna breakfast ya kalleta cikin so da qauna yace.. "Kiyi hakuri matata zan gaya miki wani abu Sam bana San kiyimin wani kallo na daban. dan zan gaya miki ne saboda bana San rashin fahimta ya shiga tsakanina dake. Dan sirri na naki ne. Kuma aganina idan nabar wannan batun da zan gaya miki araina ban miki adalci ba. Saboda zan nuna miki wasu hali wanda bamu saba dasu ba ni dake. Hakan yasa na yanke shawarar gaya miki dan karkiga canji ki zargeni.. Shuru NUFAISAT tayi gabanta na fad'uwa dan tunkan taji miye abun taji hankalinta ya tashi... Ahankali ta kallesa da cewa.. "Babu hakan tsakanina dakai. Magana indai ta fahimtace kaima kasan ina fahimtarka. Dan haka fad'i kawai babu wani abu.. Zan gaya miki Amman ki tabbatar bazaki canja min ba. Dan nasan zakima maganar wata fassara ta daban. "Nace maka Karka damu. Nime sauraranka ce da fahimtarka aduk lokacin dakaso na saurareka kona fahimcekan.. Jan numfashi yayi da cewa.. "Wancan girkin na TAUDHAT daya wucce ba Wannan na shekaran jiya ba. Naji dad'in TAUDHAT fiye da kowace ranah arayuwata.. Nasan da cewa kece macen da kike iya sarrafani yanda nake jin dad'i kuma nake samun gamsuwa gamsuwar da take zama a Zuciyata nake kasa mantawa dake. Sosai na shiga mamakin meyasa naji canji kuma yanxu daga gareki. Wato matata tunda naji TAUDHAT a wancan girkin nata na rantse miki girkin da kika shiga kafin Wannan jinki nayi wani iri. Sam na nemi Wannan jin dad'in da nake samu daga gareki na rasa. Jinki nayi babu dad'in komai ko kad'an.. Cikin tashin hankali ta qara kafeshi da ido tace... "Banfa gane me kake nufi ba. Ban fahimta ba. Wallahi kwakwalwata ta d'auke. Dan Allah me kike nufi. Wallahi ban gane ba' "Yafa dace ki gane ki kuma fahimta. Wannan abu ne bana wasa ba. Yanda kikaji na gaya miki haka shine gaskiyar zancen. Ina San jinki kamar yanda nasaba jinki matata. Dan ALLAH ki temaken kisan yanda zakiyi ki dawo kamar da. Dan bana San abin yayi nisa. Saboda na saba dake. Ke kanki kinsani. Wannan bakwan abu ne ya shigo rayuwarmu. Sam bana San na fuskanci wata matsala daga gareki.. Nasan kuma kin dad'e da fahimtar hakan... Adams na kawowa nan azancensa ya tashi da d'aukar jakarsa har yakai kofar fitta daga falan ya juyo da kallansa gareta yaci gaba da cewa... Ki fara neman canjin daga yanxu. Dan idan na dawo girkin naki naji canjin.. Tashi tayi a hankali tazo gabansa jikinta a sanyaye cikin wata murya tace mai. "Zan iya fitta unguwa yau.. "Zaki iya fitta akone lokaci banda dare kuma aduk lokacin da kikaso indai akan matsalar ne.. Murmushi ta sakar mai da cewa. "Nagode. Shima Murmushin ya mayar mata da rungumarta ya sakar mata kiss a kumatu da d'ayan gefan kumatun kana ya ficce daga falan.. Ko shashin TAUDHAT baiyi ba ya shige mota masu tsaran nashi suka jashi. Sanda sukayi nisa a tafiyar ne sannan ya tuna da TAUDHAT d'in saiya kirata awaya kan tayi mai uzuri ammishi kiran gaggawa ne. Sanda ta magantu dan ganin da tayi yau lahadi ne kuma har ya iya ganawa da masu neman temako gunsa. Ya kuma qara komawa ga qawarta NUFAISAT amman ita ya kasa tsayawa ganinta koda na minti biyu ne.. Hakuri ya bata da cewa tamai uziri hakan bazata qara faruwa ba.. Tayi mai uzirin sannan tabishi da kalamai.. Murmushi kawai yayi da kashe wayar.. Itako NUFAISAT dafe kanta tayi cikin damuwa tana tunanin meyaja mata haka.. Can dataga tunanin bazai bata shawara ba dan haka sai kawai takira asiya da larai kan su qarasa mata aikin ta zata fitta ne..... Aiko nan suka mata aikin cikin gaggawa sun fahimci tamatsu dasan tafitan akan lokaci.. Haka kawai suke jin tausayinta. Dan ganin yanda TAUDHAT ta aure mata mijin nata. qawarta aminiyarta.. Sun rasa ya akayi hakan ta faru. Sudai suna Santa da qaunarta dan macece ita agaresu me kulawa da kyautata musu. sam bata y'amatarsu... Suna gama yimata ta kulle shashinta sai gidansu.. Cikin nutsuwa ta zayyane ma mommy nata komai ba wani batun kunya taqara da cewa.. "Nifa ina tunanin TAUDHAT tayi wani abu ne fitanta ranar mommy. Dan aranar yace yaji canji agareta.. "Idan ma tayi wani mugun abin ne kanta tayima bake ba.. Dan yanzu zanje na nema miki qaiqayi koma kan masheqiya kisha da Lipton insha Allah komai zaizo miki da sauqi.. Da murmushi NUFAISAT ta sakarma mommy d'in kiss a hannu tace.. "Nagode mommy.. "Ba komai ki jirani gun Hajjiya shuwa zani na ganta dashi da yawa satin daya wucce.. Dake acikin layin nasu ne Hajjiya shuwan take hakan yasa mommy d'in batafi minti goma ba tadawo da wani koren ganye shar adake.. Nan ta had'a mata Lipton tasaka mata maganin tabata tasha. Sannan ta kulle mata sauran tace taje dashi gida tasha na kwana uku insha Allah komai zaizo mata da sauqi Saidai koda Adams ya dawo girkin NUFAISAT abin bai canja zani ba... Aiko NUFAISAT na gane hakan ta fashe da kuka.. Bata kira mommy natan tagaya mata ba. Sai ta duqufa kaima Allah kukanta.. Ahaka Sanda suka shafe kusan wata uku da kwanaki ba abinda ya canja Dan Yanxu ko kad'an Adams ya dena daurewa yana amfani da NUFAISAT d'in Sam ya dena kulata ta wannan harkar.. Dan idan ya kulata gabansa zafi yake mai kamar ya saka kansa a rami me zafin wuta Dan haka saiya denayi da ita ya kama kansa ran girkinta.. Tun abin na damun NUFAISAT har yazo ya dena damunta. Amman ganin da tayi sunfara d'aukar watanni nan hankalinta ya tashi dan koba komai ai ita mutum ce. Tana buqatar kulawar mijin nata.. Duk da cewar ko kad'an bai canja mata ba akan komai. Amman yanda wani lokacin yake juya mata qeya wajen kwanciya ai dole yafi d'aga mata hankali. Gashi taqi qara zuwa ta gayama mommy d'in nata. Ko zainab taqi gayama. TAUDHAT tasamu yanda take so. dan wani ji da ita Adams yakeyi kamar ya cinyeta.. Dan kam yana samun yanda yakeso agunta.. Shiyasa yake yaqice damuwar rashin samun NUFAISAT da batayi akan hakan..... Hajjiya Rukayyat tananan yanda take. Dan Hajjiya Hadiza sai shafe mata jiki take da jiqakken ararrab'i a zunmar shine maganin da bokaye suke bata. Hajjiya Rukayyat bata wani damu ba dan tunda Hajjiya Hadizan tagaya mata babban bokansu yace bazata samu lafiya ba saita d'auki shekara d'aya ahaka ana shafe mata jinkinta da maganin da Hajjiya Hadizan take shafeta dashi Sannan zata samu lafiya. Wannan yasa tasama kanta hakuri har izuwa lokacin daya iban mata.. Ammi na kallansu dan kotace ga wani agwada mata Hajjiya Rukayyat bata yarda dan Hajjiya Hadiza ta hure mata kunne akan karta yarda a mata amfani da wani magani. Dan bokan yace kar'a had'a mishi maganinsa dana wani.. Yau mommy takawoma NUFAISAT ziyara. NUFAISAT tayi murna sosai. Sai ajima mommy d'in nata take Wannan ta ajiye mata wancan agabanta.. Komai dai Sanda mommy ta cakala dan nacin NUFAISAT d'in Sunsha hira sosai har mommy d'in ta buqaci da NUFAISAT takaita shashin TAUDHAT su gaisa. Nan take gaya mata ai tun safe fitan Adams itama ta ficce daga gidan bata san ina taje ba.. Mommy tace.. "Bakwama junanku sallama ne.. NUFAISAT tace "Munayi. Yanxu ne dai daga baya bamama junan namu saboda ita ta faro hakan. Nima saina kasance idan zan fitta bana yimata. "Toh hakan bashi da kyau NUFAISAT. Idan batayi miki ba ke duk sa'adda zaki fitta kiyi mata.. "Toh mommy na gode. "Ba komai. Saidai naga alamu sun nuna kamar har yanxu kina da damuwa. "Eh ina da ita gaskiya mommy. "Toh mecece damuwar. "Akan dai wacce muka tattauna dake ne watan nin baya Shuru mommy tayi.. Sai zuwa can tace. "Wai kina nufin wannan qaiqayi koma kan masheqiyar dana baki baiyi miki ba.. D'aga mata kai NUFAISAT tayi. Hakan sai yasa mommy Jan numfashi da mamakin y'ar tata. Ganin yanda tad'auki wannan watannin ahaka.. Can taqara Jan numfashi taci gaba da cewa.. Aida kinyi min magana dabaki kai iyanzu da matsalar ba. Dan duk cutar da take damun bawa idan ya duba qur'ani maganinta na nan Dan haka ki kwantar da hankalinki. Zanje wajen malam me y'an makaranta nasa shi ya rubuta miki suratul maryam da suratul Alrahama insha Allah ni'amarki data dawo za kuma kisha mamaki Murmushi NUFAISAT tayi mata dan taji dad'in hakan sosai Nan mommy tayi mata nasiha sosai dace mata idan suka kammala rubutun zata turo mata dashi.. NUFAISAT tace mata toh. Mommy d'in tafitoh kenan zata shiga motarta saiga TAUDHAT nan tadawo daga anguwar tata.. Aiko da sauri tayi parking ta fito daga motar tata tagaida mommy d'in.. Da murna sosai mommy d'in ta amsa mata. Kana ta shige part d'inta Ita kuma mommy d'in ta shige motarta tatafi.. Ashe TAUDHAT d'in tana cikin farin ciki ne yau. Dan bata dena sheqa ayarta da malamin nata ba.. Kwatsam yau taje garesa dan ya bata wasu magungunan mata shine yake gaya mata anya ba ciki bane da ita.. Ai dajin haka tace mai ya duba mata. Abincikensa na duba ya gane mata da gaske tana da cikin.. Ta kalle shi da murna tace.. mai yanxu zan fara rainan d'an malam bana mijina ba. Kai amma wannan tsinanniyar mata tacuceni.. Dariya malamin nata yayi mata kawai batare daya ce komai Shine da take kan hanyarta na dawowa gida ta biya wani qaramin asibiti kan amata gwajin ciki dan Allah Suma sun tabbatar mata tana d'auke da ciki.. Toh wannan farin cikin ne yasata fittowa da sauri ta gaida mommy d'in NUFAISAT tayi part d'inta d'azu Sai juyin jin dad'i take afalo tana murnar yau dole Adams ya nunama NUFAISAT iyakarta.. Tana San kwana dashi kuma gashi ba girkinta bane.. Shine take San yanxu ta kirasa tagaya masa cewar tana da ciki. Dan idan dare yayi ta kirasa tamai qaryar bata jin dad'i dan Allah yazo ya tayata kwana.. Tasan tunda yana san haihuwa bazai mata musu ba. Qilama ko gayama NUFAISAT d'in bazaiyi ba zaizo gareta da sauri... Dan haka da sauri sauri tahau kiransa yana d'auka tace mai.. "Ako da yaushe fatan alkairi nake agareka... Jan numfashi yayi dace mata "Nagode qawarmu. Ya akayi ne. "K'aramin labari ne. Amman bansan ko awajenka babba bane.. "Toh gayamin. ina jinki. "Dama ciki ne dani... Murmushi ADAMS yayi da fad'in. "Mun gode Allah Tabbas awaje qaramin labari ne. Agun iyayanmu kuma babban labari ne.. Zanso ace da zaki iya kizo asibitinmu yanxu na tabbatar da hakan da kaina... Duk da taji ba dad'in yanda yace awajensa qaramin labari ne amman hakan baisa tanunamai ba. Dan cike da murna tace mai gata nan zuwa.. Tana isa Adams ya tabbatar da hakan.. Saidai yayi mamakin zuciyarsa dabaiji wani cikken shauqi a cikinta ba.. Dan yayi tsammanin duk lokacin dayaji matarsa nada ciki zaiji mafificin farin ciki. Sai kuma yaga abin ba haka bane.. Wata zuciyar ce mishi tayi kodan ba NUFAISAT bace.. Haka dai ya nuna jin dad'insa ba wani can ba. Dan azahiri ma ita TAUDHAT d'in tafishi zumud'i.. Haka tadawo gida da d'an damuwa dan yanda tayi tunanin zai haukace mata da murna sai taga baiyi mata hakan ba. Dan haka sai takira malamin nata tagaya mai wai bataga wani farin cikin Adams akan cikin ba Dariyar mugunta yayi mata da bata amsa.. Haba TAUDHAT. Kema kinsan mutane d'ai d'ai kune matansu suke musu irin hakan sununa farin cikin su nan take Amman wasu basa jin shauqin hakan aransu tunda ai ba jininsu bane. Haka dai zasuji farin ciki dan sun kasance sune mazan nasu. Amman Sam basa jin irin sosai d'innan.. Yanxu TAUDHAT ta fahimta. Amma taso daya nuna farin cikinsa da yawa da abin zaiyi mata dad'i sosai Tana kashe wayar dashi Ammi takirata dayi mata murna ita da Dady Da daddare ne da misalin qarfe gama sha d'aya da rabi na dare lokacin NUFAISAT na jikin Adams har sun fara bacci sai kiran wayan TAUDHAT ya shigo wayar Adams d'in bayan ya d'auka ne take cemai. "Mijin Qawa bana jin dad'in jikina Sam bana jin dad'insa... Da damuwa Adams ya tashi kad'an yace.. "Meyake damunki.. "Gashi nan dai kamar zazzab'i ne da ciwan kai harda amai da ciwan baya. Ga ciki na na juyamin kamar zai fitta. Abin dai gashi nan babu dad'i Sam. Dan ALLAH kazo ka kwana dani ko zanji dad'i. Wallahi duk a tsorace nake gani nake kamar mutuwa zanyi acikin daran nan. Saurin qarasa tashi Adams yayi da janye NUFAISAT daga jikinsa yace.. "Gani nan.. Har yakai kofa NUFAISAT tace mai "lafiya.. me yake faruwa naji kamar kana waya da TAUDHAT cikin wani hali. "Eh wai batajin dad'i ne. Kuma wai cikin kamar zai fitta. Waro ido NUFAISAT tayi gabanta na fad'uwa tace.. "Wane ciki kuma. Dafe kansa Adams yayi da cewa.. "Kinga na manta in gaya miki. Ai tana d'auke da Ciki har na tsawan wata biyu.. Jan numfashi NUFAISAT tayi cikin mamaki tatashi da fad'in. "Muje. Allah yasa karya fittan.. Haka ko suka nufi shashin TAUDHAT d'in sun sameta a can bedroom lullub'e cikin bargo. Adams ya yayeta dace mata sannu... Nanta amsa daqer.. Saboda b'acin ran dataji naganin da NUFAISAT yazo. Nan ya fara duba jikinta baiga wani abin tashin hankali ba. Hakan yasa shi cewa.. "Jikin da sauqi ashe.. Shine kika wanibi kika rikitani Da Sanyin murya tace.. "Bakaga yanda yayi min d'azu bane.. "Toh Allah ya sawake ya bada lafiya "Amiin tace.. NUFAISAT tace.. "Allah ya bada lafiya. Na tayaki murna sosai Y'ar uwa Allah ya saukeki lafiya.. Da baqin ciki tace mata Amiin Sai sukayi shuru dukkansu kawai suna masu kallanta. Gaskiya Adams bazai iya kwana da TAUDHAT ran girkin NUFAISAT ba. Dan yayi mata alk'awari bazai nuna mata wani hali akan samun cikin da wata matarsa zata samu ba.. Dan haka yace da TAUDHAT.. "Zamuje mu kwanta tunda jikin da sauqi basai an tayaki kwanan bako "Zanso hakan idan za'a tayani gaskiya. Danni nasan abinda nake ji.. Cikin sauri NUFAISAT tace. "Kaga kaje ka kwanta nina kwana da ita. Kamar ya dalla ma NUFAISAT mari haka yaji. Saboda baiji dad'in hakan. Shi bazai iya kwana haka batare dajin d'umin d'aya daga cikinsu ba. Kuma ya lura tsaf futuna TAUDHAT takeji Wallahi ba wani abinda yake damunta. B'cos ba wani alamar komai na ciwo ajikinta.. Ahankali ya ficcewa daga d'akin yana cema NUFAISAT d'in.. "Hakan yayi.. Yana fitta NUFAISAT ta kulle kofar da zama gefan gadan tana meyi mata kallan tausayi. Aiko nan take TAUDHAT d'in tatashi da cillar da bargwan jikin nata ta gallama NUFAISAT harara tace. "Ke kam ke kam wannan akwaiki da baqin hali D'an kwanan dazaki bar shi yayi anan shine abin baqin cikin naki da zakiyi saurin cewa ke zaki kwana dani. Idan kin kwana dani me zakimin.. Kingafa lafiyata qalau. Ba abinda yake damuna. Kawai Babyn cikina ne yake san jin d'umin babansa.. Da mamakinta NUFAISAT tace "Ikwan Allah.. Wai yaushe zaki dena san kanki da yawa ne TAUDHAT.. Toh har ki mutu baza kiji dumin Adams ranar girki na ba. Dan haka kinga tafiyata.. Kumama tsaya... Da kike maganar Baby nasan jin d'umin jikin ubansa. Ai saikije can wajen wanda yayi miki Cikin yaji d'uminsa dan ba abinda momy Rukayyat bata gayamin ba. Kasan cewar kar tafito tace kece kika kwantar da itan nan asirinki ya tuno shiyasa tayi gum da bakinta dan bata san asirinta ya tonu. Dan idan naki ya tono itama nata dole ya tonu. Wannan dalilin yasa ta gayamin duk abinda ya faru tsakaninki da ita Tace duk ran da kika fito kikace kina da Ciki ba Cikin ADAMS bane Cikin wani ne can. dan ita tasan abinda tayi miki. Dan haka tace idan kinfito kince kina da ciki na tona miki asiri nace ba cikin Adams bane.. Sai dai Na gaya mata bazan iya hakan ba. Saboda Allah na ganinki ni bazan tona miki asiri ba. Amman nasan komin daran dad'ewa shiALLAHN zai tona miki asirin.. Wannan yasa nacika da mamakin dayanzu yake gayamin wai ai kina da ciki. Nayi mamaki sosai dan banyi tunanin zaki iya aikata hakan da gaske da auranki ba.. Dan abin da mamaki matuqa yanda kike da auranki da mijinki dan neman duniya ki iya zuwa wajen wani qatan gard'e ya danqara miki ciki kizo kuma kina pretending kan na mijinki ne.. Nasan komai akanki yanxu TAUDHAT. Dan haka sai gayama wanda bai sani ba kina da cikin Adams. Amma nikam kar nake ganinki. Dan haka kishiga taitayinki ki fitta daga idona karki qara gigin shiga min hakk'i ran girki na akan wannan shegen cikin... Dan zan miki rashin mutuncin dahar ki mutu ba'a tab'a yi miki irinsa ba.. Sannan ina nemamma momy Rukayyat afuwa kije can wajen bokan naki kice yayi hakuri ya karya wannan mugun asirin da kikayi mata.. Idan fa kinga zaki iya. Idan bazaki iya ba! ba dole dan tsakaninku ke da ita.. Da matuqar mamaki TAUDHAT take kallan NUFAISAT.. Cikin borin kunya tace da ita.. "Kimma kanki gata dabaki ce komai akan cikin nan ba.. Dan wallahi da kince dasai kinga abinda zai faru dake.. Dallah mata harara NUFAISAT tayi da cewa. "Angaya miki tsoranki ne yasani in cewa komai. Ko an gaya miki ina jin tsoran kiyimin wani abu ne.. Kawai dai naga dama ne na qashin kaina nace bazance komai ba. Dan bansan me Allah yake nufi da hakan ba..tana fad'in hakan ta bod'e kofa ta ficce daga d'akin... Cije yatsa TAUDHAT tayi cikin matuqar baqin cikin yanda NUFAISAT tasan komai... Adams yayi murnar ganin NUFAISAT dan sai juyi yake ya kasa baccin. Duk dako ba wani abu bane zai shiga tsakaninsu. NUFAISAT ce mishi tayi TAUDHAT d'in ce tamatsa mata kan tatawo dan zata iya kwana mah ita kad'ai dan taji jikin da sauqi Jinta kawai yayi dan dama alamu sun nuna mai lafiya lau take Na gaida ku y'an hanuna...👐🏼👐🏼👐🏼 [7/6, 11:50 AM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 17☆ Washe gari mah gar Adams yaga TAUDHAT.. Yace da ita.. "Wow kice jiki Alhamdulillah.. Murmushi tamai da cewa "Masha Allah.. Kwana uku da zuwan mommy ta aikoma da NUFAISAT rubutun suratul maryam da suratul Alrahaman.. Wanda aka wanke da ruwan kankana.. Aiko tunda NUFAISAT tasha taji tanata zuba. Nan murna ta cikata hankalinta ya kwanta. Ita da kanta ta nemi mijin nata. Ya kalleta sosai zaiyi magana amman ta hanasa tana cewa "yau nice da ranar.. "Kwananki ne kiyi duk yanda zakiyi dani.. Ya fad'i hakan da murmushi akan fuskarsa. Sannan yaci gaba da cewa.. Amma Allah yasa an samu canji.. Ya fad'i hakan da wani hali.. Fari tamai da ido da cewa.. "Tunda yau kaga hakan. inama kaina fatan alkairi kawai. Ai dajin hakan yayi saurin rungumarta. cikin farin ciki da jin dad'i dan wallahi duk da yana jin dad'in TAUDHAT sosai yayi missing d'in matar tasa.. Tabbas ya tabbatar tadawo normal Dan yajita yanda ya dace. Yaji dad'inta fiye da jin dad'in dayake samu agun TAUDHAT ayanxu.. Komai yayi daidai yanxu. Dan NUFAISAT matsalarta takau.. Sam ayanxu ta rage jin tsanar TAUDHAT aranta. Sannan tasaka aran nata zamanta da ita na wani d'an lokaci ne. B'cos duk ranar da Adams ya san ita wacece cikin dake jikinta ba nasa bane. Tasan bazai qara rayuwa da ita ba Ita kam ko ajikinta Dan sai rainan cikinta takeyi yana girma dajin wani san shi cikin ranta. Sam bata dena sheqe ayarta da malamin nata ba. Haka tasaka aranta zatayi hakuri ta zauna da NUFAISAT tunda ba yanda zatayi da ita.. (TAUDHAT kenan) Adams bashi da matsala takone b'angare. Dan baisama zuciyarshi matsalar ba Duk wani abu da TAUDHAT zatayi danta fake da cikinta dan ya nunama NUFAISAT wani hali toh yayi fatali da wannan abun. Shi mamaki mah take bashi idan tana irin hakan. Dan Sam baiyi tsammanin hakan daga gareta ba. Shi yama aureta ne dan yasan ita bazata nunama NUFAISAT d'in wani hali irin hakan ba Amman sai gashi tana sai lalle saita nuna mata... Shine tun da ya fuskanci hakan ya taka mata birki shi da ita. Dan tun ranar da NUFAISAT tayanke mata bata qara gigin aikata mata hakan ran girkinta ba Amman idan itace da ADAMS d'in tata ja mishi lokaci yayin dazai fitta tace nan na mata ciwo can na damunta. Bata jin dad'in komai. Ire Iran way'annan abubuwan dai. Haka takeyi dan kawai tadinga cinye masa lokaci duk ran da yake a d'akinta.. Saiya fuskanci NUFAISAT tafara fushi dashi Dako yayi duba sai yaga duk ran girkin TAUDHAT baya fitta da wurri yayin zuwansa office.. Dan har sama da awa d'aya yake qarawa asaman yanda yasaba fitta.. Sai NUFAISAT tafara tunanin ko yafara gajiya da ita ne. Saboda ganin da tayi ita baya kaiwa tsawan wannan lokacin a d'akinta saina TAUDHAT d'in Dan haka sai kawai tahau fushi dashi Idan yazo da safen zai mata sallama saitaqi bud'e mai kofa Dan tasan koya shigo cikin sauri sauri yake ficcewa wai yayi latti. Takance mishi tome yake tsayawa yi duk ran da yake d'akin TAUDHAT d'in dahar lokaci yake tafiya mishi haka.. Baya bata wata cikakkiyar amsa.. Wannan dalilin yasa tadena bud'emai ƙofar kwata kwata Toya gama fahimtar da biyu TAUDHAT take mishi hakan. Daya lura sosai ya gane raina mishi hankali take da zummar batajin dad'in jikin nata toh shine yayanke mata ranar ya gaya mata ta nutsu baya san iskancin banza da hofi. Kota manta shi doctor ne. Yasan yanayin me ciwo yasan yanayin wanda yake da lafiya.. Dan haka ta nutsuwa tadena b'ata mishi lokaci idan zai fitta office. Duk abinda zatamai tamai da dare idan ya dawo gareta.. Toh tunda ya mata haka saita dena mai hakan NUFAISAT Kuma tadena kullemai ƙofar tata.😂 ADAMS ya kanyi murmushi da cewa aransa mata halinsu sai su.. Hajjiya Rukayyat ko tasama zuciyarta hak'uri tana nan tana jiran lokaci yayi tatashi taci uban TAUDHAT Mommy kullin kiranta ga NUFAISAT nasiha da jan hankali ne. Zainab tayi nasarar koyama NUFAISAT duk abin daya dace na fannin girki atak'aice.. ******* Da misalin qarfe hud'u4 na yamma TAUDHAT tatashi da nak'uda... Ba shiri takira Adams awaya. Yace bata gayama NUFAISAT bane. Tace wai takira number nata akashe. Da sauri shi ya kira sai kuma yaji a kunne. Cikin saurin yake gayama NUFAISAT d'in taje part na TAUDHAT ta temaka mata da had'a kayan Baby gashi nan zuwa wai nak'uda tatashi mata ne.. Cikin tausayawa ko NUFAISAT taje gareta.. Aiko tsameta tana jin jiki sosai. Nan tatambayeta inda tasa kayan baby bako musu ta gaya mata.. NUFAISAT na had'a komai saiga Ammi tazo dan Adams d'in ya kirata ya gaya mata. Haka dai Ammi tadinga bata temako irin nasu na manya har sa'adda Adams d'in ya iso Nan suka shigar da ita mota sai asibi.... TAUDHAT ba ita tasamu kanta ba sai wajen qarfe tara na dare. Inda tasamu Haifo Baby girl.. Bebinta mace kyakkyawa da ita fara soll Dangi kowa sai murna yake da zuwan wannan jinjira.. Sanda ta kwana aka sallamota b'cos bata tare da matsala Sosai TAUDHAT ta yarda dangin Adams suna san ganin jininsa. Shuru tayi kawai tana saka dama ace namiji ta haifa... Mamanta ta kirata akan zata aiko mata da kayan data siya mata dan asaka akayan suna.. Nan take ta dakatar da maman wajen gaya mata karta aiko mata da masu araha. Tabarshi ita tayima kanta kaya na gani na fad'a Shuru maman nata tayi.. Itafa har yau bataje gidan nasu ba.. Dan tunkan bikin Adams d'in da TAUDHAT d'in rabanta da gidan NUFAISAT d'in Amman ko kad'an TAUDHAT bata damu da taje d'in ba.. Dan haka ita sai tayi aiki da hankali ana kwana uku da haihuwan taje gidan nasu amman a d'akin NUFAISAT tatare. NUFAISAT d'inko taji dad'in hakan. Dan har labarin yanda auran na ADAMS da TAUDHAT d'in sanda maman tagayama NUFAISAT. Bayan kuma abinda TAUDHAT d'in take mata Sanda NUFAISAT tayi kuka. tace narasa wanda ya b'atama TAUDHAT tarbiya.. Mama dai shuru tayi mata dan ji take dama NUFAISAT d'ince y'arta Ganin irin dad'ewar da maman tayi a part d'in NUFAISAT d'in sai TAUDHAT ta balbale maman da fad'a lokacin da taje part d'inta Wai akan wane dalili zataje part d'in NUFAISAT ta zauna Ai wannan munafunci ne. Dan haka karta qara zuwa mata gida dama ai ba gayyatarta tayi ba bare tazo ta nunama duniya bata qaunarta kishiyarta take qauna dan tsabar munafunci... Ran mama yayi matuqar b'aci nan take taji LAMARIN Y'ar tata ya isheta haka. Dan haka saita kalleta cikin matuqar b'acin rai... Tace "TAUDHAT Ni kike gayama haka. Aiko TAUDHAT ta galla mata harara tace... "aa da iska nake badake ba. Kinsan ai mu d'ari ne acikin d'akin dazaki wani ce dake nake. Tashi mama tayi da yafa gyalanta tace.. "Har abada bazan qara zuwa inda kike ba TAUDHAT.. Haka ni bazan hanaki zuwa inda nake ba saidai ni bazan qara zuwa inda kike ba... Maman na kawowa nan a zancenta ta ficce daga bedroom na TAUDHAT d'in tama y'an barka na falan nata sallama sannan taje gun NUFAISAT tayi mata sallama NUFAISAT ta bata turare da atamfa biyu. Nan tamata godiya sannan tabar gidan dajin haushi da tsanar y'ar tata... Ranar suna yarinya taci Sunan maman TAUDHAT d'in.. Wato HAFSAT. Dan Adams Sunan Amminsa yaso sawa sai Ammin tace ya saka Sunan maman TAUDHAT d'in.. Bai san dalilinta nayin hakan ba. Haka aka saka ma yarinyar sunan.. TAUDHAT ansamu abinda akeso dankam tasamu kaya kasancewar ADAMS me bayarwa ne hakan yasa kowa yake san yayi masa bajinta.. Anyi bidiri bired'e awannan suna Dan qawayenta tantiran y'an iska sanda sukazo mata.. Kallo d'aya NUFAISAT tayi musu gabanta ya fad'i.. Dan ita ko'a mafarki idan akace mata TAUDHAT zatayi aminta da waƴannan qawayen zata qaryata.. Amma gashi dake ba'a shedar mutum gashi nan tagani a zahiri... Baqin cikin da TAUDHAT taso taga NUFAISAT aciki ranar sunan nata sai taga Sam bata tare da wannan baqin cikin.. Dan Sai warwala takeyi abinta tana Shiga tana fitta hankalinta kwance.. *(Yo Allah yaga zuciyarta ya kuma dafa mata*) Saiya kasance TAUDHAT d'ince kicin b'acin rai dan haka kawai taji ranta baya mata dad'i. *( duk abinda zakayi idan ba dan Allah zakayi ba na banza ne. Kuma ALLAHN bazai baka yanda kake so d'in ba)* Wasu matan masu jego suna barin miji agun abokiyar zamansu bisa al'ada... Amman rashin barin shiyafi alkairi ga maso jegwan dan sune da riba. Akwai wani d'umin juna na qara so da shak'uwa dayake samuwa yayin da me jego takwanta gado d'aya da mijinta da abinda ta haifa.. Wannan dalilin yasa masana sanin SOO da qauna basa barin matayensu dan suna jego. Haka Matan masana sanin K'AUNA basa tab'a yarda su yada mazajensu yayin da suke jego. Duk da cewa ba wai wani abu bane zai faru tsakaninsu. Kawai ana buqatan sudinga jin d'umin junan nasu ne.. TAUDHAT bata san da hakan ba. Amma ADAMS yasan da hakan. Saidai dama ita TAUDHAT ko kad'an bataji aranta zata iya barma NUFAISAT Adams har na tsawan wata da kwana goma ba.. Wannan dalilin yasa tayanke hukunci akan koda Adams yazo mata da zancen tabarshi gun NUFAISAT zatace mishi bata yarda ba..😡 _(Toh tama kwantar da hankalinta inji Rahma Nalele)_ Dan a washe garin ranar sunan dama itace da girki. Dan haka Adams yazo gareta dan su kwana Amma me. Sam taqi ta kula da jikinta yanda ya dace dan yana daga nesa da ita yake jiyo qarnin jininta Dan haka yace mata dama yazo ne dan ya tayata kwana sanadin yanda take jego basai tazo garesa ba.. Amman tunda har yanxu qarnin jininta bai rabu da ita ba zaije part d'insa. duk sa'adda ya d'auke tamai magana.. Tace mai toh ammadai ba da NUFAISAT zai dinga kwana ba ko. Murmushi yayi mata da mamakinta yace. Ko kad'an. Kamar dai yanda suka saba hakan ne zaici gaba dayi musu.. Murmushi tayi batare da tace mai komai ba Ganin hakan yasashi ficcewa daga d'akin dan qarnin ya ishesa Hakance ko ta kasance. Yana bama kowa hakk'inta na kwananta kamar yanda ya saba. Ran girkin NUFAISAT yana manne da ita ran na TAUDHAT kuwa saidai ya rungumi filo Ahaka TAUDHAT tayi arba'in amman duk da hakan sanda Adams ya qara mata kwana biyar kafin ya kulata ta fannin kwanciya... ********** Komai yayi daidai dan Haneepha yarinyar tasu (deke haka suke kiranta dashi). Tayi wayo ayanxu Dan shekaranta d'aya yau. gudunta take yi ko'ina ga baqin magana.. NUFAISAT duk da tasan ba y'ar Adams bace hakan baisa taji wani abu naqin ciki akan yarinyar ba.. Dan sosai take qaunarta.. Tun TAUDHAT na hanata y'ar hardai ta hakura tafara bata. Dan ba qaramin cin ubanta Adams yayi wata ranah Da yayi mantuwa ya dawo d'auka yaji TAUDHAT d'in tanama NUFAISAT gori akan haihuwa dan kawai taje tace tabata yarinyar tamata wasa.. Ran Adams bai tab'a b'aci irin na ranar ba.. Anan yayima TAUDHAT d'in saki d'aya yace tatattara tatafi gidansu ya saketa. Sannan ya kuma kwace y'ar yaba NUFAISAT ita Hankalin TAUDHAT ba qaramin tashi yayi ba daqer da sid'in goshi Amminsa da Dadynsa suka samu kan Adams d'in ya dawo da TAUDHAT d'in Dan maman TAUDHAT d'in da TAUDHAT d'in tazo mata da maganar ko kallanta batayi ba. Dan tana nan da jin haushinta na wulaqancin data mata kafin sunan haleephan Hakan ne yasa TAUDHAT jan tsaki taje tasa su Ammi agaba da magiya shine dalilin da yasa suka samu kan Adams d'in ya maida ita.. Tana dawowa ko NUFAISAT taje tabata y'ar tata. Da cewa wallahi TAUDHAT kibi duniya Ahankali idan da kara da mutunci baici ace kinyimin gori akan haihuwa saboda wannan Y'ar taki ba. Nasani kin sani ba y'ar Adams bace. Ta wani ce can daban Amman sabo mugun baqin halinki kina neman rasa igiyar auranki akan baqin tunaninki... Dalla mata harara TAUDHAT d'in tayi da fizge yartata.. Tunda daga ranar bata qara hana NUFAISAT yarinyar ba. Idan har NUFAISAT d'in tazo d'aukarta zata bata ita.. Kawai shed'an ne yake yawo akan TAUDHAT dan sarai tasan NUFAISAT bazata cutar mata da Y'a ba... ****** Ayau ne Hajjiya Hadiza tagaji dacin kud'in Hajjiya Rukayyat. Tasaka aranta zata nema mata magani na Gaskiya Dan takai shekara d'ayan da kusan rabi fiyema da haka shuru Sai dad'in baki da take mata Toh yazu gata gaban wani malami tagaya masa matsalarta ya bata magani yace taje tabata tasha sannan ta shafe mata jiki dashi... Aiko tunda tazo tayi mata haka cikin iko na Allah saiga Hajjiya Rukayyat tatashi.. Kwananta uku da dawowa normal taje wajen bokanta akan ya haukatar da TAUDHAT Aiko nan yake gaya mata aiki akan TAUDHAT ba qaramin abu bane.. Dan wani malaminta nayi mata aiki Saidai idan tana san ayi mata wani abu toh tayi qoqarin kawo mishi jinin al'adar ita TAUDHAT d'in da ruwan ni'imarta Hankalin Hajjiya Rukayyat ya tashi Anan taqara tabbatarwa lalle dole TAUDHAT tacika mata baki. Amman ba komai idan kere na yawo zabo na yawo wata rana zasu had'u ne. Wallahi tasha alwashin zaita wargaza rayuwar TAUDHAT.. Lokacin da TAUDHAT taji tashin Hajjiya Rukayyat d'in ji tayi kamar taji hauka Nan takira malamin ta yace takwantar da hankalinta dama haukatata tasoyi. Amman ai tana dashi. Kawai taci gaba da lura mishi da y'arsa... Jin hakan yasa hankalin TAUDHAT kwanciya kamar tsumma aranda..😀 ✋🏻✋🏻✋🏻✋🏻✋🏻✋🏻✋🏻✋🏻✋🏻 "Stop.. Ya kamata NUFAISAT TAUDHAT ku tsaya a haka... Naje can qauye nagano MUSLEEMAT... Nice Rahma Nalele ce me fad'in😌 Junior RAMADAN dake gefena yace "Ya kamata kam my Aunty. Yanxu kin shiryane nakai ki can qauyen cikin daqiqa biyu.. Murmushi nayi da cewa. "Aiya kamata ADAMS yayima su NUFAISAT sallama me tsayawa arai. Yace "kuma fa haka ne.. 😂😂😂😂😂 👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻Na gaida y'an hannu na👐🏼👐🏼👐🏼 👯🏻‍♀ [7/9, 2:44 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 18☆ Dalilin dayasa ADAMS yake tare da masu tsaro shine... Ashe shekarun baya tunda ya fara tashen kud'i sai mahassada suka sashi agaba. Sam baza'ace gasu ba. Saboda sunqi fitowa su nuna kansa bare ad'au hukunci akansu. Wata rana yana dawowa daga wajen kasuwancinsa. Dan ranar bata zuwa asibiti bace agaresa. Haka wasu mutane suka taresa suka mai dukan mutuwa. Sanda ADAMS ya shafe wata d'aya yana jinyar kansa. Haka daya tashi bayan kwana uku da tashin nasa still suka qara taresa suka dad'a mai irin wannan dukan.. Suna gayamai Wanda yasa ogansu wannan aikin rayuwarshi yake so. Su basuso su kashesa saboda alkairin daya tab'a yima ogansu. Suna bashi shawara yabar garin Kaduna ya koma can wani gari da rayuwa... Wannan karan sanda ya kai wata biyu kafin yasamu kanshi. Shiga tunani yayi sosai wajen tuna kalaman da suka gaya masa yayin da suke mai wannan duka. Shi sam baisan waye wannan ogan nasu da yake san rayuwarshi ba.. Haka kazalika bai tab'a ganin fuskokin masu mai dukan ba. Dan idansu arufe yake ba wata alama da suka bari yanda zai ganesu... Wannan yasa hankalin Dadynsa ya tashi yace dole ya dinga yawo da masu tsoro.. Da Adams yama Dadyn nasa musu akan me zaisa ko'ina zashi sai yayi yawo da masu tsoro. Shi baya sha'awar hakan sam. ALLAHn daya yisa shizai karesa.. Ba qaramin yaqi Dadyn yayi dashi ba kafin ya yarda ya samu matsaron lafiyar tashi. Sai Allah ya had'asa da nagari wanda sam basu da niyar cin amanarsa. Saboda yanda suke tunanin zai kyautata musu sai sukaga aihar ya zarce hakan wajen kyautata musun.. Dan haka sukaqi bama wanda yake san ganin bayan nasa had'in kai. Dansu sun sanshi sarai sundai k'i gayama ADAMS d'in ne saboda sun gaya masa yanda suke da ilimi wajen saran lafiyar mutum zasuyi amfani da wannan ilimin nasu wajen gujema duk wani hari dazai kawo ma Adams.. Dan haba bazasu gayama ADAMS ba. Dan sunsan zai d'auki mataki ne. Kuma kunga su shikenan fa sun rasa wannan garab'asan da suke samu agunsa ba.. Sannan sunyi ilimi da Allah zasu tsare lafiyarsa dayakar qarfinsu da aiki da iliminsu... Wannan yasa mekaratu yake ganin Adams da masu tsaro tun farkwan fara karatunshi.... ******* Yana breakfast a falan NUFAISAT Yayinda Haneepha take kan cinyarsa sai zubamai surutu takeyi irin na yara.. Sam hankalinsa baya kanta yana kan NUFAISAT da tayi tagumi kawai saboda maganar daya gaya mata tun shekaran jiya na wai zaiyi tafiya... D'an shafan gefan fusakarta yayi cikin so da qauna yace.. "Haba my luv. Wai miye ne haka. Ke dazaki bani qarfin gwiwar zuwa amma saiki jefa kanki cikin tunani dan kisa ZUCIYATA rawa ko.. Kallansa tayi cikin damuwa tace.. "Wallahi ba haka bane mijina. Kawai dai kasan baka tab'ayin tafiya bane kabarni haka Murmushi yayi da cewa.. "Kwana hud'u nefa kawai zanyi. Kuma ya kamata kibani qarfin gwiwa dan nagaya miki waye Ibrahim agaremu. Ibrahim shine wanda mukayi skull kaf dashi. Kawai bamu cika shiga harkarsa bane nida Yusuf saboda halinmu ya bambanta da nashi.. Ko yaushe yana san jammu cikin al'amuransa mune dai muke kauce masa. Amman yanxu ya dace mununa masa bama qinsa mununa masa farin cikinmu akan abinda ya samesa na alkairin nan. "Toh shi kenan dama haka kawai ne naji gabana na fad'uwa akan tafiyar sam bana san kayita Wallahi. Bana so. amma tunda ka kafe Allah yakaika lafiya ya dawo min dakai lafiya.. "Yauwa matata dama hakan nake sanji daga gareki. Yana gamawa ya sauke Haneepha da rungumar NUFAISAT d'in ya b'ata lokaci sosai yana kissing d'inta kamar bazai barta ba. Can dai ya barta da nufar part d'in TAUDHAT itama dai tanuna mai bata san tafiyar amman tunda yana so itama tanai mishi Fatan alkairi... Tabbas shima yaji wani iri lokacin daya shiga motar tashi dan ganin yanda jikin NUFAISAT yayi sanyi.. Haka ya sakar mata murmushi yace direban nashi yaja motar.. Haka sufa ficce dashi daga gidan yana me d'agama Haneepha hannu alamun bye bye... Direct gidansu yayi.. Nanko yagasu Dady da Amminsa cikin damuwa. alama tanuna suma hankalinsu bai kwanta da tafiyar tashi ba... Ibrahim abokin Adams da Yusuf ne.. Sam halinsu yasha bambam da nashi. Wannan dalilin yasa ba kowa bane yake yarda ma abokinsu ne. Saboda yanda suke guje masa sam basu san wuld'a dashi tunda suka dawo daga karatu daga waje.. Katsam acikin satin nan saiya kirasu yake gaya musu ya bud'e wani asibiti nashi na qashin kansa a garin da mahaifiyarsa take jahar Gwambe. Amman dan Allah kar suce mai basu suzo ba dan yana san yayi walimar bud'e asibitin tare dasu.. Walimar biyu ce. Data ranar jumma'a data ranar lahadi.. Kuma yana san dukka ayi dasu. Sunji kunyarsa sosai hakan ne yasa suka amsa masa dato zasuzo kuma za'ayi komai dasu... Tunran alhamis Yusuf ya tafi dan lokacin jikin Dadyn Adams bai gama warwarewa ba kasancewar yayi zazzab'i kwana biyu da suka wucce.. Hakan yasa Adams yace yaje shi yaxo ran asabar yasamu walimar ta ranar lahadin Haka ko akayi nan Yusuf ya tafi.. Kuma har ya tabbatar mishi da cewa ya sauka lafiya dake tafiyar jirgi ne. Toshi haka kawai Adams ya tsinci kansa dasan tafiyar mota.. Danya ankawo masa wata fitacciyar mota me inganci wacce tazarce kowace mota cikin motocinsa a kud'i... Dan haka sai yaji yana san tafiya da motar.. Kuma baya san tafiya da maso tsaran lafiyansa. Dayake gayama su Dadynsa da Amminsa sai hankalinsu ya tashi sukace basu yarda ba Dan basu manta yanda aka mishi lokacin baya da yake yawo shi kad'ai ba Murmushi yayi dace musu haba dai. Yanxu koma waye maqiyin nasa ai yaci ace ya haqura ya dena bibiyarsa tunda yanxu rabansa dashi kusan shekaru takwas kenan. Jin hakan yasa hankalin nasu kwanciya.. Amma yanxu ganin da gaske tafiyan zaiyi sai kuma sukaji tashin hankalin ya dawo musu... Murmushi ADAMS yayi dan ganinsu cikin damuwa. Haka ya kalli Dadyn nasa yace.. "Dama Dady nazo muku sallamar ne.. Murmushin yaqe Dadyn yayi masa dacewa.. "Anya bazan hanaka tafiyan nan bako ADAMU Da sauri Adams ya qara tsaida idanta akan na Dadyn nasa yace... "Dan Allah karka hanani Dady.. Bafa wani abun dazai faru. Kawai addu'arku nake nema nasan idan har kukamin bazata fad'i qasa banza ba.. Jan numfashi Amminsa tayi da cewa toh Allah ya saukeka lafiya ya dawo mana dakai lafiya.. Sannan ka kula da hanya kasan ba sanin wajen kayi ba.. "Insha Allah Ammina Kuma ai kinga tare da Sunusi zamu dan yaje gwamben kusan sau biyar tunda acen Mahaifinsa yanxu yake da zama. Dan haka baza mu sami wata matsala ba Jin hakan yasa hankalinsu kwanciya amman duk da hakan sunso da ace girgi yabi. Da hankalinsu yafi kwanciya... Haka yayi musu sallama duk da baqin hali irin na Hajjiya Rukayyat sanda itama taji aranta kamar karya tafi.. Salim mah jiyayi kamar yayan nasa yayi tafiyar shi.. Haka lokacin da yakema matsaransa sallama akan su kwantar da hankalinsu ba abinda zai samesa yaudai ranah d'aya ai ba wani abu bane. Fatansa dai suba matansa kulawa dan baya san yaji wani abu ya faru dasu... Da sanyin jiki suka bashi mukullin motar da zaiyi tafiyar da ita. Haka yaba Sunusi ya shige bayan motar Sunusin ya zauna wajen mazaunin direba yajasu sukabar harabar gidan zuciyar Adams cike da qaunar iyayen nasa.... Biyan Sunusi akayi wato d'aya daga cikin direbobin Adams d'in.. Kasancewar direbobin nasa uku ne.. Kuma shima kansa Sunusin sanda yayarda zaiyi abinda suke so sai daga baya kuma yazo yana na damar yanda yake qoqarin cin amanar ogan nasa wanda yayi masa dukkanin gata.. Wannan dai maqiyin nasa ne har yau yake san neman rayuwarsa.. Dan dad'ewar da yayi wajen lamfo kamar ya rabu da Adams d'in shekara da shekaru. Ashe dad'ewar shirye shiryen yanda za'ayi ya cimma burin nasa akansa ne.. Toh yau yana neman cin sa'a da nasara akansa... Dake ADAMS bai san yanyar garin Gwamben ba shiyasa sam baisan inda Sunusi yake jefa k'afar motar tasu ba... Hasalima shi karatun jaridarsa yake yi idan yaji Sunusin ya tsaya awani waje yakan kalli wajen idan yaga da mabarata ko gajiyayyu sai yaba Sunusin kud'i ya basu.... Sunsha uwar tafiya wanda sai yanxu nadamar qin shiga jirki tazoma Adams.. Danshi arayuwarsa bai tab'a tafiya irin wannan ba.. Cak ADAMS yaji Sunusi ya tsaya da tuqin mota. Duk da bacci ya fara fuzgarsa. Jin tsayuwar motar shiyasa shi bud'e idansa.. D'ago kansa da zaiyi kawai saiya gansu kan titi gashi gabas da yamma cikin daji suke.. Dajin dabazai iya cewa ga inda suke ba.. Gashi abin mamaki wasu mutane ya gani su goma.. Murd'add'u da alama ma kad'an daga cikinsu sune way'anda suke kawo mai hari shekarun baya dan yaga hakan atattare dasu.. Uku bindiga ne ahannunsu sauran kuma qarfuna ne da sandina a nasu hannayen.. Fitowa Adams yayi kamar yanda Sunusi ya fitto.. Cikin Dariyar mugunta suka d'aga bindigarsu sama suka setata akan Adams.. Cikin sauri Sunusi ya fashe da kuka yace dasu. "Dan Allah karku cutarmin da oga na. Karku kashesa. Nayi muku abinda nayi muku amman ina cikin nadama. Saboda naci amanar wanda ya yarda dani. Na munafurcesa bayan yayi min dukkan gata.. Wallahi me gida nayi maka abinda bai dace ba. Dan Allah ka yafemin.. Sunusi ya qarashe maganar da kallan Adams ya kama qafarsa alama ban hak'uri.. Cikin mamaki Adams ya kalli Sunusi yace.. "Wai me yake faruwa ne.. "Oga way'annan mutanan ne suka bani kud'i me yawan gaske sukace duk yanda za'ayi nayi dan kayo tafiyar nan dani. Dan sun samu labarin zuwanka gwamben kuma a mota. Shine sukace nakawo musu kai cikin dajin nan da zaran tafiya tayi nisa. Oga ban san manufarsu ba. Kawai na duba yawan kud'in da suka ban ne.. Sunusi ya fad'i hakan daci gaba da kuka.. Nan ADAMS ya rintse idansa yana tuna yanda yabar matansa iyayensa. Ya tabbatar tunda ya had'u da way'an nan mutanan wannan karan ba barinsa zasuyi ba. Dan haka da wani hali ya kalli Sunusin da cemai. "Karka damu Sunusi nayafe maka. Aiko kan Sunusin yace wani abu wani daga cikin masu d'auke da bindigar ya harbe kan Sunusin da bindigar hannunsa...😨 Jikake fasss.. Ai arikice Adams ya tashe yaje ya rungumesa yana me kiran sunansa.. "Sunusi Sunusi Sunusi katashi katashi dan Allah.. Amma ina ko alamar motsawa Sunusi baiyi ba.. Saboda rai yayi halinsa... Gabaki d'aya Adams ya rikice fad'in musu yake.. Kun kashesa fah. Ya mutu. Wallahi kun kashesa.. Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un... Haka Adams yaketa fad'a hankalinsa tashe.. "ADAMCY kenan.. Mun gayama kabar garin Kaduna idan kana san ganinka da lafiya kuma a raye.. Sai kaqi. Ka zauna abinka baka tare da wani tashin hankali. Saboda kayima kanka gata kana da masu tsaro.. Sai gashi yau tunaninka ya toshe ka fito inda baka tab'a zuwa ba batare dasu ba.. Oganmu ya gaya mana bokan Wanda yasa shi wannan aikin akanka ya gaya masa idan har kana garin Kaduna sunansa da azziqinsa bazasu tab'a suna ba. Bazai tab'a zama wani ba. Shi kuma yana san ya fika tako ta'ina.... Wannan dalilin yasa yace mu kashe masa kai. Saidai mu bamu san muyi maka hakan saboda katab'a temakwan oganmu. Shine yasa muke maka dukkan tsiya dan mu hanaka tashi bare kaci gaba da aiwatar da harkokinka. Saiya kasance katashi. Muka dad'a maka wani dukan dace maka kabar garin Kaduna idan kana san zama da rayuwaka. Amman kaqi. Yanxu ma ba kasheka zamuyi ba. Saboda mu ba butulu bane munsan wanda yayi mana. Zamu qara maka wani dukkan ne wanda bazaka moru ba bare kaci gaba da aiwatar da ayyukanka ka hana wancan maqiyin naka cika burinsa... Kan ADAMS yace wani abu sun fara kai masa duka a inda suke da tabbacin idan suka dakai bazai iya muruwa ba.. Da qarfuna da sandinansu suka fara kai mishi wannan duka Duk da cewar bawai kallansu yake ba. aa yana qoqarin kare kansa. Dan sosai suma yayi musu b'arna. Wajen rama abin da suke masa. Toh kunsan ance sarkin yawa yafi sarkin qarfi.. Hakan ne yasa yaqi cin galaba akansu.. Dan d'aya daga cikin su yana d'aga sandarsa saiko ya sauke ta a qeyarsa wanda nan take ADAMS ya jirkice ya zube awajen tamkar wanda ya mutu. Dan babu alamar rai atare dashi Ba qaramin tsoro bane ya kamasu.. Dan ogansu yace musu kada su kuskura su kasheshi. Sudai mai dukan daba zai moru ba. Shiyasan abinda zai cema wanda yasa shi aikin... Aiko Ahankali suka fara tab'ashi suna cewa.. "Mun kashe shi fah. Yanxu me zamucema oga.. D'aya daga cikinsu yace.. "Ga shawara.. Me zai hana mukaisa *Rugar malam jauro..* Kasan rugace wacce ba kowa bane yake da sani akanta. Saboda tayi cikin daji da yawa. Me zama a wannan ruga sai Wanda ya taki abubuwa da dama. Dan bakowane mutum bane yake iya rayuwa awajen. Kasancewarta muguwar riga.... Cikin sauri wani cikinsu shima ya amshe da cewa.. "Kaga shike nan asirinmu ya rufu agun oga.. Dan idan mukace mai munyi yanda yace muyi zamu zauna lafiya dashi. Idan ko mukace mun kasheshi saiya d'auki ran d'aya daga cikinmu.. Kaga rugar Malam Jauro bame zuwa bare asan da zaman gawarsa awajen. Idan ko muka yar dashi anan kaga dole atsince shi kuma labari yajema oga.. Shuru sukayi suna nazari Can wanda ya harbi Sunusi yace. "Wannan shawarar tayi. Kunga sai musa Sunusi shi kad'ai a buhun barkonan kamar yanda ogan yace. Sai muce mai gabaki d'ayansu ne mukasasu a buhun bamu san ya akayi aka rasa ADAMS d'in ba. Kowa cikinsu yayarda da wannan shawarar.... Dan haka suka kinkimi ADAMS suka sashi cikin motarshi. Sannan suka saka Sunusi abuhu irin babban nan wanda yake d'auke da barkono aciki. suka kullesa. uku daga cikinsu suka shiga motar ADAMS d'in d'aya yajata.. Sannan sauran suka shiga cikin dajin inda suka ajiye motarsu dan kar'a ankare dasu. Sannan suka kusa cikin wani daji me nisan tsiya. Dan sai tafiya suke kamar basa tafiya.. Akalla sunkai kusan biyu na dare kana suka iso rugar.. Saidai basu bari sun qarasa cikinta ba dan sunsan illar dake cikinta.. Ad'an nesa da rugar cikin dajin suka yada Adams... Suka juya abinsu da barin wajen... Washe gari da misalin qarfe takwas suka samu fitowa daga rugar... Nan suka d'auki hanyar garin Kaduna. Sanda sukayi awa uku kana suka samu kansa a garin Kadunan. Sannan sukaje unguwar su Dadyn ADAMS suka bar Sunusi cikin motar da key na motar Adams d'in sannan suka bar unguwar. Amman sanda suka zaro wata kwarab'abbiyar waya suka kira num na Dadyn Adams kamar yanda Ogansu ya basu suka gayamai ga Adams nan da direbansa cikin unguwarsu da alama yana cikin wani hali... (Kuji fa masu karatu) Suna gaya mai hakan suka kashe wayar da cillar da ita awajen sukayi tafiyarsu.. Lokacin da Dady ya d'auki wayar tasu yana zaune ne shida Hajjiya Rukayyat da Ammi. Suna magana akan rashin jin Adams d'in daba suyi ba awaya. Gashi basu da number na Yusuf kona Ibrahim d'in.. Aiko da sauri Dady ya tashi jin abinda suka ce mai yana me cewa "Subhanallah.. Nan su Ammi suka buqaci suji meya faru. Da sauri ya gaya musu ya fito waje yana cilla ido yaga ta'inda zaiga motar Adams d'in Aiko ya d'anyi nisa da tafiya cikin layin nasu saiya hango motar.. Da sauri ya qarasa gareta yana duba amman baiga kowa aciki ba sai wayoyin ADAMS dana Sunusi.. Yana bud'e Boot na motar sai yaga qatan buhu fari kallo d'aya zaka mai kasan na barkono ne. Yayi duba iya duba wajen wai kozaiga Adams alayin amma baiga kome kamarsa ba. Hankalin Dady ya tashi matuqa dan haka nan ya shiga kiran wayar da suka kirasa da ita nan yaji akashe.. Saiya kira wani amininsa babban d'an sanda yana gayamai yaxo yanxu unguwarsu ankawo mai motar d'ansa Adams kuma baya ciki da alama wani abu nasan faruwa. Ai dajin hakan yacema Dadyn gashi nan zuwa.. Haka yazo da yaran aikinsa suka hau caje motar basuga komai ba. Sai kwarab'abbiyar wayar da suka yar nesa da motar. Ogan nasu yace abud'e mai buhun barko nan nan. Aiko dan yaransa suka bud'e mai saiko ganin sunusi sukayi cikin barkono.. Nan suka fitto dashi anan suka gane yazama gawa dan ga shedar harbi nan akansa bai b'uya ba.. Hankalin Dady yayi matuqar tashi nan ya yanke jiki ya fad'i sumamme.. NUFAISAT da Ammi da sukaji labari nan suma haka suka zube sumammu. Masu qarfin halin Hajjiya Rukayyat ce da TAUDHAT.. Nanfa zance ya baza gari an nemi ADAMS ba'a agansa ba.. Hankalin y'an uwa da abokan arziqi ya tashi matuqa.. Dan b'atan mutum yafi mutuwarsa Shiga tashin hankali. Saboda idan mutuwa yayi ba shakka damuwar ta dabance. Idanko b'ata yayi kullum tunani mutane zasu shiga yi koyana wane hali koya mutu koyana raye oho Wannan yasa hankalin kowa yayi mayuqar tashi. Nan aka fara sanarwa a gidajen radio da gidan talabijin yanar gizo wajen nemansa. Anan Yusuf yasan Adams ya b'ata... Dan haka ba shiri ya baro garin gwambe dan shima ya rasa nutsuwarsa ganin baiji Adams d'in ba. Dama Ibrahim bawai agarin gwanben yake ba. aa Aure ne kawai mamansa takeyi agarin dan tarabu da mahaifinsa. Hakan yasa shi yake gun Mahaifinsa anan cikin garin Kadunan. Dan haka tare da Yusuf suka dawo Kaduna suna masu san jin ba'asin yanda akayi Adams ya b'ace. Babufa ADAMS babu labarinsa sam cikin garin Kaduna. Dan har y'an sanda da masu farin kaya kaf sunyi iya binkikensu basuji labarin Adams ba.. Dare da rana safe da yamma malamai addu'a suke akan Allah ya bayyana Adams.. Dan a binciken istaharan duk malamin da yayi ya nuna ADAMS yana *RAYE* saidai yana cikin wani mawiyacin hali Jin hakan da Dady yayi shiyasa jininsa qara hawa a asibiti.. NUFAISAT ko ba ita tasamu kanta ba sanda tayi sati a asibitin tadawo hayyacinta.. Saidai tasaka salloli agaba dare da rana akan Allah ya fitto mata da mijinta ya karesa aduk inda yake. Haka TAUDHAT duk ta karad'e malamanta da bokayenta sun bata tabbacin Adams yana raye saidai baza suce ga inda yake ba. Gaskiya itama hankalinta ya tashi sosai. Ganin hakan yasa masu tsaran lafiyar Adams d'in suka fito sukace su suna zargin Ibrahim shine ya b'atar da ADAMS kuma ba mamaki shine ya kashe Sunusi. Jami'an tsoro sunsasu agaba kan sufad'i dalilinsu na fad'in hakan.. Nan suka gaya musu shine yasa wasu suka kaima ADAMS d'in hari a shekarun baya. Kuma yaxo ya buqaci dasu kulle dashi dan shi rayuwar ADAMS d'in yake buqata.. Ai dajin wannan batu nan take ogan y'an sanda yasa yaransa suje su nemamman Ibrahim aduk inda yake.. Sunci sa'a tare da Yusuf suka dawo daga gwamben dan haka basusha wahalar ram dashi ba.. Dafarko yayi musu gaddama akan baisan komai akan labarin ba. Kuma qarya masu tsaran lafiyar Adams suka masa na wai shine yasa wasu suka kai mai hari.. Sam jami'an tsoran basu wani yarda da Ibrahim d'in ba Dan haka nan suka hau gana masa azaba cikiko harda guntule mishi y'an yatsu guda biyu.. Ai yana jin azaba ya gaya musu shine yasa aka kai mai hari shekarun bayan. Kuma da gaske shine yasa yanxu a kashesa akuma kashe Sunusi dan karya tona musu asiri.. Jami'an basuji mamakinsa ba dan sun saba ganin abin mamakin irin hakan Dan haka sai suka buqaci suji dalilinsa nayima Adams d'in hakan... Ba wata kwakkwaran magana dan cemusu yayi.... Tun suna skull ADAMS yake samun nasarori arayuwa amman shi baya samu. Haka shi LEEKITAN ZUCHIYA ne hakama Adams d'in shima LEEKITAN ZUCHIYA ne.. Saidai sunan Adams yafi fitowa duniya tasanshi fiye dashi.. Haka tafanni kasuwancin da yakeyi nan ma ya qara fito da sunansa ko'ina aka sanshi... Wannan dalilin shiyasa yaji hassadar Adams d'in takamasa. Saiya bara bin bokaye kansu dak'ushe tauraran Adams su d'aukaka nashi.. Saidai abin bai yuhu ba. Sakancewar shi me ibada ne. Shine kawai ya yanke shawarar yasa akasheshi. Nanma way'anda yasa sumai hakan baisan dalilinsu na kasa kasheshin ba har akaro na biyu.. Shine yanxu yayi amfani da wannan damar dayaji Adams d'in yace bazaibi jirgiba ba motarsa zaibi. To shine yacema yaran aikin nasa duk iya wiya kadda subar ADAMS darai awannan karan.... Sosai jami'an tsaran suka jinjina hassada da baqin hali irin na Ibrahim. Sun buqaci daya gaya musu inda yaran suke. Way'anda yasa su kashe Adams d'in Ya gaya musu inda suke. Amman anyi duban duniya suma ba'a gansu ba Wannan yasa hankalin jami'an tsaran ya tashi dan Ibrahim ya tabbatar musu da cewar wallahi bayan inda ya gaya musu baisan inda kuma suke ba... Ayanxu dai Ibrahim yana hannun jami'an tsaro dayi musu aiki me tsanani.. Dan sunce bazasu sakesa ba har sai ranar da akaga ADAMS. dan ba zama zasuyi ba zasu dinga nemansa ne har Allah yasa adace.. Ammin Adams tana cikin wani hali. Kullum tunaninta ADAMS ne Ba dare babu rana rokwan Allah take kan ya fito mata da d'anta cike da lafiya.. Haka NUFAISAT itama tunaninta ADAMS d'in ne kuka take cikin dare tana rokwan Allah ya bayyana mata mijinta.. TAUDHAT mah tana cikin damuwa dan har tafara tunanin yanxu idan ba'aga ADAMS ba. Ya zatayi wajen rayuwa da wani namijin.. Yusuf ma ba'a barshi abaya ba. Dan kullum addu'a yakema Adams babu dare babu ranah. Haka indai zai fita saiyaje gurare da dama wai kozaiga Adams d'in.. Dady kam jiki babu sauqi dan likita yace saiya cire damuwar Adams aransa sannan zai samu lafiya.. Lokaci na tafiya amman har yanxu shuru kakeji babu labarin Adams. Yau kusan watanni tara kenan babu amo babu labari... TAUDHAT da NUFAISAT sunsa aransu bazasu tab'a barin Auran Adams ba suna nan suna jiran dawowarsa dan sunji aransu da gaske bai mutu ba.... Wannan kenan me karatu🙅🏻‍♀ Kuci gaba da bibiyata ni Rahma Nalele ina tare daku y'an hannuna👐🏼👐🏼👐🏼.. Jiya naso turo muku Allah bai yarda ba [7/11, 2:55 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 19☆ Sannan way'anda sukama ADAMS dukan nan suna nan cikin garin Kaduna suna jinyar kansu cikin b'oyayyan guri... Dan nagaya muku shima Adams bawai kallansu kawai ya tsaya yi ba. Yayi musu b'ar me yawa. Dan dai kawai suna jin tsoran karsu kasheshi ne ogansu yad'au hukunci akansu banda haka da tun fara artabun nasu zasu sakar mai bindiga. Dan duk da suna tare makamai ahannunsu sanda ya nuna masu iyakarsu. Ya fasama d'aya daga cikinsu gefan ido d'aya Wanda nake kyautata zatun yama rasa idan.. Haka ya karya wani ma acinya. Yama wani duka a gabansa. Inda kunsan da wiya mutum yake tsallake duka awannan waje batare daya shiga ukunsa ba. Sannan ya kaima Wanda ya kashe Sunusi mugun bugu a hanci Wanda nan take kamanninsa suka canja. Dan hancin ya samu mugun rauni. Ga baki hak'ura sun zube.. Wannan tunda yayi masa haka yar iyanxu kansa yaqi dawowa daidai.. Ogansu yayi mamakin hakan sosai. Dan bai tab'a kawowa masu jin dad'in rayuwa suna tare da qarfi haka Wannan kenan me karatu ************ Rugar malam jauro wata hatsabibiyar ruga ce da take nan cikin d'aya daga qauyukan garin gwambe. Saidai tayi daji da yawa kasancewar malam jauro yana da arziqin shanu masu yawan gaske.. Wannan dalilin yasa mutane suke zagawa suke mai sata san ransu. Lokacin daya ankare da hakan shine yayi wani abu Wanda duk Wanda ya shigo rugarsa da niyar sata to ba makawa mutuwa zaiyi.. Abin da yayi yana amfani da haline da abinda kazoyi. Wannan yasa jama'a da dama suke ganin rugar ba wajen zuwa bace saboda yanda suke ganin kawarwaken mutane da sun shiga wajen.. Duk Wanda ko sukaga yaje rugar lafiya ya fitto lafiya cewa suke akwai abinda ya taka.. Babbar Ruga ce sosai danta tara ainiyin fulani masu wayan gaske. Way'anda basu san hayaniya. Dan kallo d'aya zaka musu ka kirasu da fulanin daji. Basu san komai na rayuwa ba sai kiwo... Saidai sun bambanta da jahilan mutane saboda malam jauro shahararran malami ne. Yana da sani akan ilimi na addinin musulinci. Wannan yasa duk inda suka fito idan zasu aiwatar da al'amuransu gabanka bazaka kirasu da jahilal ba. Dan sunsan ilimi na addinin musulinci Malam jauro ya koyar dasu Qur'ani me girma su fiqhu ahalari qawaqidi da sauran littattafai na addina.. Bayan wannan basu da sani akan komai sai kiwo.. Gwaggwa Yawo wacce suke kira da Yawo tana d'aya daga cikin mutanan da suke zama cikin wannan Ruga.. Saidai ba'a wajen ainihi tayi rayuwa ba aa zama ne dai ya kawo ta cikin dajin ita da d'anta Musa.. Dan ita asalinsu y'an qauyen Jos ne BASA. Yawo yaranta biyu ne aduniya. Rahma da Musa qaninta.. Mahaifinsu ya mutu ne bayan sati uku da Aurar da Rahma da yayi ga wani d'an garin Kano. Wanda bai sanshi ba haka kawai dan ya ganta yace yana Santa Sai kawai ya bashi ita wai ya yaba da hankalinsa.. Dan kawai ya d'auki wata d'aya yana zuwa tad'i wajenta.. Dake kunsan Bafulatan mutum dasan kud'i nan take shiko saurayin ya dinga masa kyauta kala kala. Hakan yasa yace wai yayarda da hankalinsa. Amman ya masa alqawari idan ya aura masa y'arsa Rahma zai dinga zuwa duk wata biyu yana kawo musu ita suna ganinta.. Shiko saurayi yayarda da hakan. Ita dai yawo hankalinta bai wani kwanta ba. Gani take saurayin d'an yankan kaine. Yana aure mata y'a zai yanke mata kai. Dan haka tanuna ita bata amince da auran ba. Shi kuma mijin nata yace ya amince. Haka tanaji tana gani ya d'aura ma Rahma aure da wannan saurayi ya kuma saka Rahman gaban motar saurayin yace tama mijinta biyayya dan yayarda dashi😨😨😨 Yowa tafi kwana uku tana kukan rabuwa da Rahma Lamarin d'aurin Auran ya faru da kwana uku tayi mafarkin saurayin ya yanka mata y'a.. Aiko wayewar wannan safiya data tashi ba abinda take Sai kuka.. Shiko mijin nata ce mata yayi Dan tasa hakan aranta ne shiyasa tayi mafarkin hakan.. Jinsa kawai tayi Amman tasa aranta da gaske sirikin nasu ya kashe mata Y'a... Tana cikin jimamamin hakan ne kuma da sati biyu mijin nata ya rasu.. Wannan yasa tsoro ya kama zuciyarta.. Ana yin Arba'in d'in rasuwan mijin nata sai tace da Musa ya saida shanunsu kaf zasu tashi daga basa nan qauyen Jos su koma qauyen yola ko gwambe.. Haka musa ya yarda da zancenta ya sayar dasu kamar yanda ta buqata shine fa basu zame ako ina ba sai'a garin gwambe Ahankali suka fara gane kan garin. Kasancewar Yawo tafi san zaman daji saita dinga neman sani akan dajikan da suke qauyen gwambe. Anan taji ta gamsu tayarda da zama a Rugar malam jauro.. Sai Musa yasai musu shanu agun Malam Jauro ya fara ciwansu. Aiko cikin iko na Allah nan shanun nan suka dinga haihaifafa ya tarasu da yawan gaske. Anan yaga wata wacce yake so ya Aura sunanta Hasiya.. Hasiya macece me hankali da nutsuwa tunda Musu ya furta mata yana santa da aure taji tana sanshi da qaunarsa.. Hasiya y'a d'ayace agun iyayenta. Wanda makwaftan junane su dasu Musan Suma iyayenta basu da wasu danji dan suma zuwa rugar sukayi kamar yanda su Yawo d'in sukazo.. Sun yarda da auran Musa da Hasiya iyayenta nan aka d'aura musu aure. Saidai watansu takwas da auran Musa ya rasu ya bar Hasiya da ciki.. Anan hankalin Yawo ya tashi matuqa dan dama su biyu gareta. Gashi bata san inda Rahma take ba. Da gaske saurayin nan ya kasheta kobai kasheta ba oho..🙂 Shid'in kuma da take kallansa taji dad'i Gashi ya tafi.. Wannan dalilin yasa tad'auki san duniya ta d'ora akan cikin da Hasiya take dashi... Hasiya na tashi haihuwa tahaifi mace santaleliya me kama da ita sak. Saidai ita baqa ce. Irin baqin nan da bature ke cewa black beauty.. Kallo d'aya zaka mata kasan kayi gamo da baqar bafulatana.. Gashi Mahaifiyarta fara mahaifinta fari danginta farare amman ita tazo baqa.. Ranar suna yarinya taci suna Faɗima. Dake malam jauro ne ya rad'a mata sunan haka kawai yaji yana qaunar yarinyar. Dan yarinya ce me shiga rai tun zuwanta duniya haka mutanan wajen suke tururuwa wajen san ganinta. Dan da wiya kamata kallan farko bakaji tashiga ranka ba.. Hakan yasa Malam Jauro yake kiranta da Musulma.. Shine Yawo take kiranta da MUSLEEMA. San duniyar nan haka Yawo da mahaifan Hasiya suka d'auka suke nunama MUSLEEMA Kaf cikin Rugar nan babu black beauty Sai MUSLEEMA Hakan yasa kowa yasan da zaman MUSLEEMA awannan Ruga.. Ayanxu shekarunta goma sha biyu. Kuma a qa'idar Rugar malam jauro yara y'an mata suna kaiwa shekaru goma sha uku ake Aurar dasu.. Wani d'an malam jauro ne yake san MUSLEEMA. Ayanxu haka har an saka musu ranah.. MUSLEEMA yarinyace me sanyi haka. Tana da d'an surutu tsiwa idan tasanka kuka saba.. Tana da manyan ido shanyayyu irin na me jin bacci d'innan. Ga dinful d'inta me sata kyau idan tayi murmushi ko dariya. Ga jiki na d'aukar hankali.. Zara zaran yatsunta abin kallo ne. Sannan tana da Gashi me tsawo me santsi da sheqi irin na ainiyin fulani. Alamu sun nuna MUSLEEMA bazatayi irin wannan tsawan nan me yawa ba. sannan bazatayi qajarta irin me munin nan ba Sannan baza'a kirata siririya ba. Haka baza'ace mata lukuta ba. Idan me karatu yana san ya hango yanda jikin MUSLEEMA yake. Toh yayi amfani da jikin wannan jurumar Y'ar film d'in wasan hausan nan wato MARYAM BOOTH... Abu uku kawai MUSLEEMA zata nunama Maryam booth shine tafita mazaunu HP. Zata fita breast idan taqara girma. Haka kaza lika zata fita diri na jiki na d'aukar hankali idan taqara girma still.. Sannan ita bata da hanci can. Hacinta gajere ne🙂 Sam idan Mazaje masu san mata kyawawa sukaci garo da MUSLEEMA baza su d'auketa ba. Dan ko kusa baza su sata a sawun mata masu kyau ba.. Cewa zasuyi gata baqa gata da gajeran hanci sam bazasu kirata da kyakkyawar mace ba Amman ga mutumin dayasan ailihin kyau ga y'a mace yana ganin MUSLEEMA zaiyi gudu dan saceta ya b'oyeta inda babu Wanda zaina kallanta bare ya gane masa sirrin dake tare da ita.. Mahaifiyarta tayi wani aure saidai itama bata wani dad'e ba tarasu dan haihuwanta d'aya cikin rashin sani tana jan ruwa a rijiya tana magana santsi ya kwasheta tafad'i Sai jinta akayi acikin rijiyar tafad'a tsumdum. Tayi mutuwar shahada Dan ba'a kaiga I cirota ba tace ga garinku nan... Iya tashin hankali iyayanta da Yawo sun shiga. Dan Hasiya mutum ce.. Haka iyayenta suka roqi alfarma kan iyayen mijinta subar musu d'an data bari Suleiman.. Dake mijin yayarda haka suma suka yarda... Shine fa ya kasance Yawo take riqe da MUSLEEMA su Kuma iyayan Hasiya suka riqe da Suleiman.. Wannan shine labarin MUSLEEMA da yanda tazo duniya... ****** Abinda ya faru awashe garin ranar da Y'an iskan nan sukama ADAMS wannan duka suka yadashi Rugar malam Jauro shine.. Ita dai MUSLEEMA bayan tayi sallar asuba makarantar malam jauro ta nufa kamar yanda tasaba. Yana karantar dasu karatun bayan sallar asuba zuwa qarfe takwas na safe.. Qawarta Aisha ce me biyo mata to jiya a gidan kusa dana malam jauro ta kwana gidan yayarta data haihu.. Hakan yasa take tafe ita kad'ai yau.. Taga Adams akwance Sai tsoro ya hanata kulawa dashi.. Dake makarantar tana da d'an nisa da gidansu haka ta dinga tafiya tana waige dan ganin Adams ya tsaya mata arai.. Duk da ba ganin fuskarsa tayi ba.. Amman ya tsaya mata arai matuqa Har aka tashi daga makarantar hankalin MUSLEEMA nakan ADAMS.. Dama malam jauro na lura da ita Dan haka da'aka tashi saiya kirata yana tambayarta me yake damunta ne yau. Yaga kamar hankalinta baya kan karatu.. Cikin nutsuwa ta gayamai taga wani mutum ne a can kusa da gidansu. Kuma da alama mutuwa yayi.. Murmushi malam jauro yayi Dan tunaninsa ko masu zuwayi masa sata ne sukazo rai yayi halinsa.. Dan haka saiya kira liman da yaransa biyu ciki harda Wanda zai Auri MUSLEEMAN yace suzo akwai wani Wanda ya mace can kusa da gidansu MUSLEEMA.. Aiko cikin sauri suka rangad'o zuwa ganin wanene kuma wannan.. MUSLEEMA tana gaba suna binta a baya har takaisu inda taga ADAMS. Aiko yana nan kamar yanda ta gansa... Hankalin me gari da liman yayi matuqar tashi ganin Adams haka. Sun gane mugun duka aka masa Wanda duk Wany'anda suka masa wannan duka sun ilmantu da dukan mutane a inda suke da tabbacin zai zamame mutum illa arayuwa.. Duk wani gu Wanda ido yake tsoran a tab'a mai ajiki Sanda suka tab'amai Malam jauro yaga sab'anin abinda yake tunani.. Nan take tausayin ADAMS ya kamashi yace maza su kinkimesa su kaishi gida. Wajen d'aukar nasa ne liman yake tabbatarma da malam jauro karaya bakwai ce a jikin ADAMS. Malam jauro yaqara jinjina wannan rashin tausayi irin na mutane.. MUSLEEMA ko tunda taga fuskar ADAMS hankalinta ya tashi. Tausayinsa ya cika zuciyarta.. Nan take tafara kuka tana me qarajin tausayinsa aranta. Daqar malam jauro da liman suka iya shawo kan kukan nata tatafi gida. Sun tabbatar da lalle yarinyar me tausayi ce.. Da kuka tashiga gidan nasu lokacin Yawo na dama kokon safe.. Aiko da sauri tatashi ta tareta tana tambayarta... "Meya faru dake yanxu kuma da sassafe. "Wani mutum nagani kusa da gidanmu d'azu zani makaranta. Shine da aka tashi malam dasu Iro da liman suka biyoni na nuna musu shi. Yawo bakiga yanda akamai duka ba. Wasu ne suka jimai ciwo sosai ajikinsa. koma ya mutu ne oho Shuru Yawo tayi dan tayi tunanin ko masu zuwa yima malam jauro d'in sata ne. Amman dataji batun duka Sai tunaninta ya canja.. "Kinga ba komai zauna kiyi kalacen ki. "Ni bazan iya cin komai ba. "Toh yanxu me kika san ayi. "Nidai kizo muje gidan malam kiga mutumin kinga saimu dinga zuwa dubasa ko☹ "Ohni Yawo.🤔 zamuje amman Sai munyi kalace.. Jin hakan yasa MUSLEEMA d'auko tabarma ta shinfid'a a tsakar gidan nasu wanda yasa sumunti ta d'auko kokon nasu da kosai suka zauna ita da Yawon suka cika cikinsu.. A al'adar MUSLEEMA idan tawowa daga makaranta bayan taci abinci shara takeyi da wanke wanke saitayi wanka saita zaga wajen ciwansu ta duba lafiyar dabbobin da taga zata iya dubawa. Idan da matsala tazo ta gayama Yawo idan babu matsala haka zata zauna cikinsu tana me kula dasu na lokaci me tsawo. Sallah ce take tadata. Idan tayi takan fitta su had'u da qawarta Aisha suta wasansu da hirace hiracensu.. Toh yau ko sharan da wanke wanken batayi ba tatashi ta azalzalama Yawo wai saidai tatashi suje gidan malam taga wannan mutumin... Yawo tace bazata ba saitayi mata wanke wanke da shara tukunna Haka MUSLEEMA tayi tana turo baki. Wai adole ranta ya b'aci... Tana gamako suka kullo gidan da nufar gidan malam jauro. Kallo d'aya Yawo tama Adams gabanta yayanke ya fad'i.. Hankalinta kuma ya tashi.. Saboda ganin da tayi yayi mata kama da y'arta Rahma. Ga irin idansa nan irin na Rahma ne. Irin na MUSLEEMA. Ga hancinsa mah irin na Rahma Y'arta ne.. A dibibice ta kalli malam jauro tace... "Malam a ina Kaga wannan bawan Allahn.. " aa MUSLEEMA bata gaya miki bane. Ai itace taban labarin yanda tagansa. "Eh nima taban labarin na dai d'auka ko a kid'ime take ne. "aa gaskiyar kenan tagaya miki... "Ammako ko suwaye ne suka mishi haka suncika azzalimai. "Wallahi yanxu ni da liman zancen da muke kenan. Ko daga ina yake. Wayaxo ya yayada shi Allahu ya'alamu. Amman nasa su Iro suje kewayenmu su bincika ko wani nasu ya b'ace. Dan ga wani cikin rugata yana jin jiki.. "Eh hakan yayi. Allah yasa anan kusa yake.. "Amiin.. Jan numfashi liman yayi da kallan malam jauro yace. "Na gyara mai karayoyin dake jikinsa. Gashi nasaka mishi magani a raunukan nashi. Allah yasa a samu kansa nan da kwana biyu.. Da sauri MUSLEEMA ta katse liman da cewa. "Babba yana da rai koya mutu. Murmushi duk sukayi yace mata shi yace da ita. "bai mutu ba MUSLEEMA.. Malam jauro yace. "Nasa Suleiman yaje can cikin garin na gwambe ya kira ɗana Usman. Dan naga kamar saiya saka hannu cikin lamarin ciwan nasa.. Gyad'a kai liman yayi da cewa.. "Ya kamata kam. Kan malam jauro yayi wata magana saiga Usman ya shigo da sallah shi da Suleiman d'in.. "Kaga yanxu muke maganarka nake gaya musu na tura Suleiman ya kiraka kaduba mana Wannan bawan Allahn.. "Eh had'uwa mukayi dashi ahanya dan nima nan na nufo dubaku. Sai yake gayamin wai dama guna zaizo dan kana san nazo na duba wani Mara lafiya.. "Ni na manta ma yau qarshen wata Yayi ranar zuwanka. Ka ganshi nan Mara lafiyan matso ka ganshi dakyau.. Duba na tsanaki Dr Usman yakema ADAMS yana jin mamaki cuwukan dake jikinsa.. Can ya kalli malam jauro mahaifin nasa yace. "Wannan fa Sai an kaishi asibiti dan maganin gida bazai gamsheshi cikin sauri ba. Dan haka ya zama lalle yau na kuma saimu tafi tare daku dan kuji binciken da za'ayi akansa. Liman yace.. "Wannan ai ba damuwa. Jeka duba umman taka ka fito muje. Tashi Dr Usman yayi yashiga can cikin gidan malam inda mahaifiyarsa take. Anan take bashi labarin yanda aka damu Adams. Usman ya tausayama Adams sosai. Hakan yasa zuciyarsa takasa nutsuwa.. Dan haka sai kawai yay ma Mahaifiyar tashi sallama ya fito. Daidai lokacin da liman ya fito daga gidansa dan gayama iyalinsa. Haka suka saka Adams a motar Usman d'in. Liman da malam jauro suma suka shiga motar MUSLEEMA tace zata bisu. Daqer suka lallasheta kana Usman ya jasu basu zame ako ina sai'a ba sai'a cikin garin gwambe cikin asibitin DOCTOR AHMAD... Anan aka shiga duba lafiyar Adams lungu da sak'o. Bancike ya nuna TUNANIN ADAMS YA D'AUKE.. Bashi ba tuna wani abu daya faru dashi arayuwa. Sai in yaqa wani nasa ko an ambaci wani abun daya sani wannan ne kawai zai iya sawa asan shi asan daga inda ya fito.. Kasancewar daga cikin garin gwambe zuwa rugar malam jauro akai tafiya me d'an nisa. Sai kawai liman da malam jauro suka tare a gidan Usman danshi ya buqaci dasu zauna kasancewar ana saka ran marfad'owar ADAMS d'in nan da kwana biyu.. Dan yana jiye musu wahalar da zasu sha wajen dawowa idan suka koma gida Hakan yasa suka yarda. Anan ko Ruga MUSLEEMA tana cikin wani hali. Dan tunanin Adams ya damu Zuciyarta. Haka kawai taji tana sanshi tana qaunarsa tana tausayinsa. Yawo na lura da ita. kallanta kawai takeyi dan itama Adams d'in ya bala'in shiga ranta.. Gani take kamar shi d'in jininta ne.. Kwanan Adams hud'u a asibitin ya farfad'o. Saidai kamar yanda binken ya nuna ya manta komai na rayuwa akansa. Hakance ta kasance.. Malam jauro ko sai tambayarsa sunansa yake. Ido kawai Adams yake binsa dashi. Usman yayi murmushi yace.. "Angayama Baffa tuninsa ya d'auke yanxu ba abinda zai qara tunawa arayuwarsa sai in yaga wani nasa kutunna. Kwana d'aya su malam jauro suka qara sukace ma Usman zasu koma Ruga dan Allah ya kula da ADAMS kamar jininsa zasu dinga zuwa duk qarshen sati suna dubasa. Nan yabasu tabbacin zai kula dashi kamar yanda zai kula da kansa.. Dasu malam jauro suka dawo gida Yawo da MUSLEEMA sunzo sun tambayesu ya jikinsa.. Nan liman yake gayama Yawo ga matsalar da shi Adams ya fuskanta na d'aukewar tunani.. Da tausayawa Yaro tace Allah ya dawo mai da tunanin nasa nan kusa. Saiya kasance kullum Idan MUSLEEMA tazo karatun asuba gun Malam jauro saita tambayesa jikin ADAMS Tun yanace mata jiki da sauqi harya gaji da amsa mata.. Dayaga tafara zuwa da ranah da yamma tana tambayarsa Saiya fara d'aukarta duk sanda zasu duba Adams d'in shida Liman. Hakan ne yasa hankalin Musleema kwanciya. Dan tana ganin Adams d'in yana samun sauqi sosai. Yau malam jauro ya shirya shida liman suka nufi cikin garin na gwambe lokacin watannin ADAMS bakwai Usman na lura da lafiyarsa su kuma suna masu zuwa dubasa.. Adams ya samu sauqi sosai.. Ba abinda yafima Malam jauro dad'i da kulawar da Usman yabama Adams d'in sai ganin yanda ADAMS din yake amfani da ilimin addinin da Usman d'in ya bashi. Sallarsa anitse. Komai nasa dakeyi a nitse yakeyi. ADAMS yafi gane yaran Hausa dan shi Usman yafi masa ba fullanci ba. Dake dama rugar malam jauro had'akata ce. Ana jin Hausa ana jin fillanci. Hakan yasa su malam jauro jin dad'in yanda ADAMS din yaji hausa. Usman yace da mahaifinsa malam jauro yasama ADAMS suna Ahmad kasancewar basu san sunansa ba. Sunji dad'in sunan dan haka suma sukace da sunan zasu dinga kiransa. Haka suka dawo da ADAMS cikin Rugar malam jauro suna masu yimai addu'a akan Allah ya dawo mai da tunaninsa Susan daga inda ya fito.. Saidai da suka dawo MUSLEEMA taje tasama malam jauro daru kan saiya bata Yayanta Ahmad ya koma gidansu.. Murmushi yayi da kallanta yace idan naba Yawo shi a'ina zata sashi. Tace ai akwai d'akuna agidansu tashare ko'ina duk inda ya zab'a anan zai zauna.. Da farko malam jauro yaso qin yarda Amma dataje tasa Yawo agaba da kuka dole Yawo tazo ta ruqi malam jauro yayarda Adams ya koma gidansu MUSLEEMAT Abin yama MUSLEEMA dad'i.. Dama shima Adams baya san nesa da MUSLEEMA. Saboda tun lokacin dasu malam jauro suke zuwa da ita dubasa ya lura da qaunar da take masa. Hakan ne yasa yafi sakewa da ita fiye dasu su malam jauro d'in.. Saboda yanda take da dad'in hira Gashi Yana tsintar kansa cikin nisha'i idan Yana tare da itan.. Sosai itama Yawo taji dad'in yanda ADAMS ya dawo gidan nasu.. Yana zuwa gun malam jauro d'aukar karatu da safe da yamma idan ya dawo kuma ya shiga daji cikin awaki yana dubasu. Tunda ya fara kula da dabbobin nasu Sai Yawo taga kamar yafi kowa iya kiwo Dama ya hutashar da MUSLEEMA dan yanxu bata zuwa ciwan.. Dan Idan kaganta a wajen ciwan to taje hira da yayan nata Adams ne wato Ahmad kamar yanda suke kiransa dashi.... Sha kuk'uwa me tsanani tashiga tsakanin MUSLEEMA da ADAMS ******** Malam jauro ne da liman amininsa da Yawo da d'ansa Iro da MUSLEEMA suke zaune kan tabarma a kofar gidan malam jauron.. Malam jauro yace.. "Dama abinda yasa na taraku magana nake san nayi daku akan alqawarin Auran dake kan MUSLEEMA da d'ana Iro ganin da nayi Yanxu takai shekarunta na Aure.. Murmushi Iro yayi dan shi aduniyar nan ba wacce yake so kamar MUSLEEMA. Yana mata wani mugun so wanda shi kansa bazaice ga ranar daya soma yi mata shi ba. Dan ya dad'e da santa aruhinsa shine ma ya gayama mahaifin nasa yana Santa har dai alqawarin Auran nasu ya hau kansu shi da ita. Jan numfashi Yawo tayi da cewa. "Ai wannan ba matsala bane malam. Yaran nan duk naka ne. Kawai asaka ranah ayi musu auran babu wani damuwa.. Murmushi jin dad'i malam jauro yayi da kallan MUSLEEMA wacce taturo baki gaba yace da ita. "Lafiya dai y'ata kike turo baki ko aran ne baki so. Da sauri ta d'aga mai kai. Yaci gaba da cewa. Toh meyasa baki so. Cikin zubar hawaye tace.. "Ni Wallahi malam bani san Iro ni YAYANA nake so.. Gyara zama malam jauro yayi da cewa.. "Waye yayan naki.. "YAYAH Ahmad mana.... Saurin bige mata baki Yawo tayi dayi mata dak'uwa tace. "Saiki mutu dasan nashi aranki ai. Aure dai tsakaninki da Iro sai anyi. Ni dama nasan ba banza ba kika ninema Ahmad d'in nan tun ran farko... Aiko dajin hakan MUSLEEMA tafashe da kuka tana cewa.. "Ni wallahi YAYANA NAKE SO. Shi nake so.. Shuru kowa yayi ba abinda kakeji sai tashin kukanta. Ahankali malam jauro ya kalli Iro yace.. "Kai jeka ka kiramin Ahmad.. Yawo tace.. "Daka fitta daga harkarta malam yarinyar nan bata da kai.. Murmushi yayi mata da cewa.. "Bazan d'aura mata aure da Wanda bata so ba. Dan tunda tazo duniya nake qaunarta kamar yanda nake qaunar y'ay'ana.. Jin abinda yace sai yasa hankalin Yawo kwanciya dan dama ita har ga Allah bata san Auran Iro da MUSLEEMA. Saboda Iro halinsa ya bambanta da sauran yaran malam jauro d'in... Shiyasa dawowar ADAMS gidanta sai taji tana San ya Auri MUSLEEMA. Saboda nutsuwarsa da kamewarsa.. Iro ko ransa ne yayi matuqar b'aci hankalinsa ya tashi matuqa. Gani yake in ba MUSLEEMA bazai iya rayuwa ba.. Haka da b'acin rai yaje ga Adams wanda yake wajen ciwo da qur'@ni a hannunsa yana tulawa yace dashi. "Kar kayi qoqarin ruguzamin rayuwata. Dan wallahi kayi min haka saina b'atar dakai duk daran dad'ewa. Sannan wai kaje Mahaifina nasan ganinka yanxu Yana fad'in hakan ya juya abinsa ya tafi. Da kallan mamaki ADAMS ya bishi. Me kenan yake nufi da way'annan kalmomin nasa... Tab'e baki yayi da tashi dan zuwa amsa kiran... Yana zuwa yaga MUSLEEMAT na kuka sosai.. Ai baisan sanda yayi jifa da sandarsa gefe ba yaje gareta da kama hannunta yana goge nata hawaye fad'i yake.. "Waya tab'amin ke. Waya tab'amin qanwata. Meya sameki.. Ahankali cikin shagwab'a tace mai "Wallahi YAYA nikai nake so. Dakai nake san k'are rayuwata. Dan Allah karka bari a d'aura min aure da Iro nagaya musu gaskiya nikai nake so.. Shuru ADAMS yayi da sakin hannunta ya qarasa kusa da Malam jauro wanda yasaki baki yana kallansu yace.. "Gani Baba Iro yace min kana san ganina.. Jan numfashi Malam jauro yayi da cewa. "Eh haka ne. Dama ina san naji kaima kana san MUSLEEMA ne. Kallansa Adams yayi da murmushi yace.. "Kayi hakuri Baba. A duk duniya bani da abin so kamarta. Ina san MUSLEEMA kiye da komai arayuwata.. Saidai karka daka ta shirmanta. Kaga ita yarinya ce. Ka duba Iro ka Aura mata shi. Dan shine ya dace da ita. Musamman idan kukayi duba da yanda naji mutane na fad'i cikin Rugar nan na wai ni ba'asan ko wanene ba. Bai dace ka duba zancenta ba. Ya dace ka bata wanda kasani ina ganin hakan shi zaifi alkairi.. Jan numfashi Malam jauro yayi cikin matuqar jin qaunar ADAMS d'in aransa. Yayi imani ko daga ina Adams ya fito shid'in ba mugun mutum bane. Kuma zai kasance d'an dangi ne. Haka zai kasance nutsattse ne.. Yana jin qaunar MUSLEEMA aransa kamar shine ya haifeta. Dan haka bazai tursasa Zuciyarta kan lalle saitayi rayuwa da d'ansa Iro dan san zuciya ba. Dan haka cikin taushash shiyar murya irin tasu ta manya yace dashi. "Naji abinda nake sanji daga gareka. Kuma MUSLEEMA bata da wani miji bayan kai. Indai kakarta Yawo ta amince.. Da sauri Yawo tace.. "Ni kam duk yanda kayanke shawara kan auran MUSLEEMA na amince... "Toh shi kenan. Zan d'aura mata aure da Ahmad ran jumma'an nan. Sannan zan turo masu gini suzo su kewaye d'akin Ahmad d'in da fitar musu da bayan gida dan susamu inda zasu zauna. Dan nasan bazaki so suyi nisa dake ba. Da murmushi Yawo tace "hakan yayi malam mungode Allah ya saka.. "Ba komai Allah shige mana gaba. Shi kuma Allah ya dawo mai da tunaninsa nan kusa Liman yace "amiin.. Yanxu kai Iro sai kayi hakuri ko... Murmushin yaqe Iro yayi wanda ake cewa yafi kuka ciwo yace. "Ba komai Babba. Haka sukayi addu'a suka tafi zuciyar Iro na gaya masa mezaima Adams wanda zaisa ya hucce kwacen matar da yayi masa.. Yayi alqawari saiya baqanta rayuwarsa. Ayi Auran komai daran dad'ewa saiyayi masa illah.... Na gaida y'an hannuna👐🏼👐🏼👐🏼 [7/14, 1:49 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 20☆ Bayan su Adams sun koma gida Yawo barinsu tayi a tsakar gidan nasu ta shige kicin dan kama aiki. ADAMS ya kalli MUSLEEMA cikin tsokana yace. "Wallahi YAYA ni kai nake so. Dakai kad'ai nake san k'are rayuwata.. Murmushi MUSLEEMA tayi da galla mishi hararar wasa. Shima murmushi Yayi daciba da cewa. Toh nima wallahi qanwata nake so. Kuma ke kad'ai nake san qarashe rayuwata. "Toh dan Allah yaya karka barni. Duk wiya duk matsi duk tashin hankali kada ka gujemin. "Ko'a mafarki bazan tab'a iya guje miki ba. Bare azahiri ina ganinki ido da ido na gujemiki. Bazan iya hakan ba. Dan nasan idan na aikata hakan na aikata babban zunubi.. Saboda na gujema tauraruwa me haskake hasken taurari... Ba qaramin jin dad'in furucinsa MUSLEEMA tayi ba hakan yasa ta rungumesa tana cewa. Zan girka maka abinci me dad'in gaske anjima. Shafa kanta yayi dabata amsa.. "Tona gode qanwata ki kula min da kanki sosai dan bani san naji ance wuta ta qona min ke.. "Zan kiyaye YAYANA.. "Yauwa qanwata bara naje dan nabar shanunmu can cikin daji. Janye jikinta tayi daga nasa tana sakar mai murmushi. Shima murmushin ya sakar mata kana ya ficce daga gidan.. Aranar malam jauro ya aiko da masu gyara suke kewayema Adams da MUSLEEMA inda zasu zauna Itama Yawo daga ranar tafara damama MUSLEEMA wata gamba da madarar shanu tana bata tana sha. Sannan dama ita MUSLEEMA ba'abinda tafi so kamar shan madarar shanu farar tasa wacce ba'a dafa ba. Babban sirri ne ga Y'a mace tadinga sha dan yana wanke mara da sakama mace wata ni'ima me tsayawa aran miji. sannan ko baki shan maganin mata ked'in tada bance acikin matan... Sannan tana bata rubutun suratul Yusuf wacce ake wankewa da ruwan kankana.. Haka akwai wasu suna darai na sirrin bafulatanin mutum wanda shima duk sanda ta bata.. Sannan ana sauran kwana biyu d'aurin Aure ta siyar da Saniya biyu tasiya musu gado da katifa harda ladar d'aki da abubuwan buqata. Yau takasance ranar jumma'a kuma an d'aura auran ADAMS wanda suke kira da Ahmad shi da MUSLEEMA.. Jama'ar rugar sai qananun maganganu suke akan yanda Yawo ta amince taba ADAMS Auran jikarta tilo d'aya bayan ba'asan daga inda ya fitto ba. Ai yanxu kai ya waye andena irin wannan kwad'an... Tajisu Amman ta toshe kunnnata dan ita alkairin hakan kawai take hangowa bata hango wani sharri ko faruwar wata matsala.. Da misalin qarfe takwas da rabi Yawo takira Adams ta danqa masa amanar MUSLEEMA tace.. "Gata nan qanwarka ce ka riqeta amana kamar yanda na baka ita amana.. "Insha allah Yawo bazaki tab'a nadama da bani ita da kikayi ba. "Masha Allah. Saiku tashi kuyi shashin naku. Haka suka tashi sukayi shashin nasu wanda ya kasance ciki ne da falo sai d'an fili idan suka fitto daga falan nasu. Bayangida kuma dama had'e yake dana Yawo.. Haka Adams yace da MUSLEEMA taje tayo alwala suyi sallah.. Aiko nan tatashi ba musu dan dama ita bata mishi musu akan komai. Bare kuma yanxu da Yawo taja kunnanta sosai akan hakan.. Bayan tadawo nan suka gabatar da sallah raka'a biyu Adams yace da ita.. "Qanwata kin fara wannan al'adar ne irin ta mata. Sunkuyar da kanta qasa tayi batare da tabasa amsa ba. Sanda ya qara maimaita mata tambayar sannan cikin jin kunya tace dashi.. "Na fara wancan watan. "Toh gayamin kwana nawa kikayi ya d'auke miki. Tace kwana hud'u.. Yace "Yaya kika aiwatar da wankan... Kallansa tayi da sauri.. Yako gyad'a mata kai alamar yana san sani. Tunani tashiga yi Ashe dama yaya Ahmad d'an iska ne.. Kamar yasan tunanin da takeyi yaci gaba da cewa. Qanwata karfa zuciyarki tagaya miki cewa ni d'an iska ne. aa haka aure yake dole ki gayamin yanda kike aiwatar da ibadarki dan nasani nasan daidai kikeyi koko akwai matsala. Jin hakan yasata sakewa tagaya masa kanta a sunkuye. Yaji dad'in yanda ta'iya dai dai da yanda ake so dan haka saiya qara mata tambaya akan yanda take ibadunta. Namma bata bashi kunya ba tagaya masa. Nanya kama kanta yayi mata addu'o'eh. Kana ya jawota jikinsa ya shiga bata kazar da Aliyu abokinsa ya gasa masa da madarar shunu me d'umi da Yawo tabashi.... MUSLEEMA kad'an ta rage. Hakama madarar. Dama shi ba wata yunwa yake jiba. Hakan yaci sauran. Ahankali ya shiga sarrafa MUSLEEMA yana mata wani wasa me d'aukar hankali. Dama ita MUSLEEMA bata tab'a tsintar kanta a yanayin ba. Dan haka saita dinga mannemai tana shigemai. Lokacin daya raba kansa da komai itama ya rabata da komai ba qaramin shigemai tayi ba. Aiko nan ya fara aika mata da babban sak'o wanda nan take tunaninta ya d'auke.. Ya samu na fulaninta yanda yake so asaye kyem. Saidai basuyi cikan dazasu hargitsashi ba. Kasancewar yanxu suka fara tasowa. Dake yasaka gaba saiya maida ita mace. Nanta fashe mai da kuka wiwi... Yana aikin tana kuka. Dake yana sane da yarinya ce bai bata wahala da yawa ba. Saidai yaji dad'inta sosai. Wanda nan take ya qara jin kifiyar qaunarta ta qara cikar masa zuciya.. A maqale tsam take a qirjinsa yana aikin lallashinta saboda kukan da take mai. Ji yake kamar ya cinyeta d'anye. Gaskiya yarinyar tabashi abubuwan tsayawa arai da yawa.. Duk da kukan da take mai hakan bai hanasa qara tsotsar nafulaninta.. Asuba nayi yafara tunanin a'ina zai sama musu ruwan wanka.. Haka ya daure ya fitto waje ahankali ya nufi kicin inda Yawo take girki saiko yaga ta d'ora ruwan zafi. Nanya haska ruwan dakyau ya tabbatar me kyau ne gashi har yana tafasa.. Ai ba shiri ya juye musu cikin wani babban bokiti. Yaje bakin rijiya yaja da sirka ruwan. Yaqara saka wani bai wani d'auki lokaci ba yajuye musu cikin botoci. Sannan yamayar ma da Yawon wani ruwan kan wutan saiya nufi bayin nasu Bayan ya ajiye ruwan zuwa yayi yasa MUSLEEMA agaba wai tad'aure suje suyi wankan kan gari yayi haske. Nanta tubure masa akan badai suyi su biyu ba saidai ya kaita bayin idan ta fito saishi yaje yayi. Murmushi yayi yana nuna mata babu lokaci idan basuje sunyi tare ba Allah zaije yayi abinsa. Idan gari yayi haske taje tayi nata. kuma abin kunyane Yawo taganta tanayi. Jin hakan yasa MUSLEEMA yarda ya d'auketa yakaita bayin. Nan ma sanda qauna tashiga tsakaninsu. Bayan sunyi wankan tsarki ta gasa gabanta da kyau. sosai ya temaka mata wajen wankan soso da sabulu. Duk yanda MUSLEEMA takai da kunyarta sanda ta daure ta fuskance shi tayimai abin da yake so awannan lokacin. Dan cewa yayi tunda yayi mata wankan soso saitayi mishi idan ba haka ba saidai su kwana a bayin. Hakan yasata daurewa tayimai yanda yake so.. Bayan sun dawo d'akinsu sallah sukayi suna idarwa MUSLEEMA dasan jiki shigemai jiki tayi. Haka ya kasance da ita yana karatun Qur'aninsa. Da gari yayi haske ya maida ita gado. Shima ya kwanta gefanta haka wani bacci me dad'i yayi awan gaba dasu... Dama Yawo tun cikin dare takejin kukan MUSLEEMA. Hakan ya tabbatar mata Ahmad injisu da fad'a yana cika aiki. Dan haka asuba nayi biyar daidai tatashi ta hura wuta ta d'ora musu ruwa. Dan haka akan kunnanta Adams yayi komai da asuba. Har wankan da sukayi.. Yanxu tagama had'a musu abin Karin safe tana cikin tunanin harsai yaushe zasu fito ne. Sai kawai tajisu a bayanta sun tsungunna suna gaisheta. Da Farin ciki ta amsa musu da nuna musu taburmar da dama suke zama akanta suke cin abinci. Tace... "Kunga na gama komai dan haka kuzauna muci. Haka suka zauna suna cikin cine tacigaba da cewa. Ga ruwan wanka can nabar muku. ADAMS ya kalleta yace. "Toh sannu da aiki. Bayan sun gama ci y'ar hirar da suka saba ita dai sukayi. Yawo taga har tafiyar MUSLEEMA ta canja. Dan haka sai tashiga daji tahad'o mata ganyayyaki na gyara tadawo tazo tatafasa su tace tadinga iba tana tsarki dasu. Aiko tun alokacin da MUSLEEMA tafara amfani dasu taji dad'in jikinta. Haka Adams ya dinga more MUSLEEMA. Sai dirjatta yake kamar me. Danshi yasan me yakeji aguntan Wata qauna da soyayya sukema junasu sosai. San ADAMS MUSLEEMA take kamar tayi hauka. Komai yace mata yi take babu zancen musu. Sannan duk abinda tace mai tana so shima yimata yakeyi... Wata goma da Auransu ciki ya shiga MUSLEEMA. Nan tafara laulayi dan cikin me irin bada wahalar nan ne.. Gata qaramar yarinya hakan yasa ADAMS damuwa da batun cikin ganin irin wahalar da take sha. Yawo tace mai karya damu dama da haka kowace mace take zama uwa. Hankalin ADAMS atashe yake matuqa yaqi bari hankalin nasa ya kwanta saboda cikin yaqi barin matar tasa da lafiya.. Yau da ciwo gobe da sauqi aikin kenan kullum. Itako Yawo bata wani damu ba dan tasan ciki ya gaji haka.. Saidai tana mamakin girman ciki irin na MUSLEEMA ayanxu watanshi shidda. Amman idan kaganshi saikace tashiga watan haihuwanta.. ______________ Da misalin qarfe tara na dare ne suna zauna ita dashi cikin falansu. Futulace dai irin tamu ta gida ta haske musu falan nasu. Danna mata qafa yake ganin yanda ta kunburah.. Da murmushi akan fuskarsa yake ce mata.. "Qanwata anya ba y'an biyu zaki haifamin ba kuwa. Murmushi tayi da cewa. "Gaskiya kam YAYAH zai iya zama hakan. Dan bakaji yanda nake ji ajikina ba.. Koma dai miye ai yanxu ina watan haihuwan nawa. Zan haifene muga me Allah ya bamu.. "Toh Allah ya saukar min dake lafiya. Saidai gaskiya ina ganin gobe zamuje cikin gari wajen Usman ya dubaki. Dan atsorace nake da wannan kunburin naki... "Kadena jin tsoro YAYAH. Bakaji abinda Yawo tace ranar bane. Tace su azamaninsu basu san wani zuwa wajen doctor dan suna da ciki ba. Sai'a wannan zamanin na jikokinsu. Dan haka YAYAH kabari kawai taci gaba da ban maganin nasu dan ina jin dad'insa. Insha Allah zan haihu lafiya. Mu raini yarammu cikin k'oshin lafiya.. Matsawa yayi jikinta da kama bakinta ya bata make kiss me tsayawa arai yace. "Na bari matata. Zanci gaba dayi miki addu'a har bayan haihuwan naki kisamu ingantacciyar lafiya me d'orewa.. "Ni dai ina sanka YAYANA. Ina san kasancewa dakai akowane lokaci. Ina san komai da kake min. "Nima haka qanwata. Ina sanki da yawa ina qaunarki babu iyaka. Ina jinki araina kamar wani kwai. Insha Allah nidake mutuwace kawai zata iya rabamu.. "Itama idan zatazo zan rok'eta data d'aukemu tare. Dan ina san nayi wata daddad'ar rayuwa dakai agidan ALJANNAH... Qara bata kiss yayi cike daso da qauna... "Zaki iya dani kuwa yau. "Ko zan mutu bana fatan ka buqaceni na hanaka kaina. Saidai na lura yanxu bakajin tausayina kamar lokacin da nake amarya agareka... "Har yanxu a mazaunin amarya kike agareni qanwata. Saidai kinsan da dayanxu da bambanci. Saboda yanxu kike cika kike qara zama mace y'ar budurwata😀.. Rufe idanta tayi cikin jin kunya tace. "Kai YAYAH... Yace.. "ALLAH y'ar qanwata.. Kwana uku tsakani da hirar nan tasu Nak'uda tatashima MUSLEEMA qarfe gama sha d'aya na safe... Lokacin ADAMS baya gida. Dama Yawo tana tare da maganinta irin na fulani wanda idan hakan tatashi suke jiqama me naquda tasha.. Aiko nan tajawo ganyan. Tajiqa shi tabata tasha. Cikin iko na Allah MUSLEEMA bata wani d'auki lokaci ba. ta santalo d'anta na Miji.. Amman ciwo bai tsaya ba. Can sai ga wani d'an🤔 nan ma ciwo bai dena ba. Tana dad'a wani nishin saiga Y'arta mace sandaleliya itama ta fito.. Yawo taga abin mamaki.... Sai nishin wahala MUSLEEMA takeyi wani bacci nasan d'auketa.. Haka kan yawo tagama yima yara wanka bacci yayi awan gaba da MUSLEEMA... Sanda Yawo tagama tsaftace komai ta binne mahaifa sannan tatashi MUSLEEMA tatemaka mata taje bayi. Anan tabata ruwan magani na ganye tayi sarki dashi sannan tayi mata wanka da sauran ruwan. Ba qaramin jin dad'in jikinta MUSLEEMA tayi ba... Koda suka dawo d'aki bayan MUSLEEMA tayi k'unzugu miqewa tayi a gado taci gaba da baccinta ko takan yaran batabi ba. Nan Yawo ta leqa makwafta ta gaya musu MUSLEEMA ta haihu... Kankace me😳 nan gidan Yawo yacika maqel da y'an barka.... Kowa fad'in albarkacin bakinsa yake kan yanda yaran sukaxo dakyau.. Sun had'une iyakar had'uwa. Saikace yaran larabawa.. Anan wasu yaran suka ruga daji da gudu suka gayama ADAMS MUSLEEMA ta haihu ta haifo y'an uku🤱🏼👩‍👦‍👦 Da mamaki ADAMS ya nufi gidan nasu cikin sauri yana atunanin anya kuwa zancen da yaran suka gayamai gaskiya ne.. Aiko ya tabbatar. Jiyayi kamar yasa ransa ame dan Farin ciki. Yawo ta kalli ADAMS tace.. "Kaga ikwan Allah ko. Dama na gaya muku kudena biyema y'an asibitin nan wajen haihuwa. A kwai sinadarai namu na gargajiya irinsu ganyayyaki itacuwa ingantattu da muke zuwa daji muke iboma me ciki take sha. haka zakaga ta haihu sumul da ita. Bata tare da wani ciwo ko kad'an.. Yaranta suzo duniya jikinsu luwai luwai gwanin ban sha'awa dashi. Murmushi ADAMS yayi baice mata komai ba. Dan yasan Yawo wajen musu idan akan ciki ne. Shi kuma gani yake kamar ya dace idan Mace nada ciki taje doctors su dubata. Saidai yanxu ya qara tabbatarwa Allah ne kawai me karewa. Har kwana hud'u da haihuwan amma sam yaran basu da kuka basu da wani matsala. Sai shan nonon uwarsu suke me gard'i da lafiya. Saboda sinadaran da Yawo take bata dan qarama nonon inganci.. Ranar suna raguna uku da shunuwa d'aya aka yankama yaran. Yawo tace idan bamma Y'ay'an MUSLEEMA ba banga y'ay'an wanda zamma ba. Dan haka ko d'ari ne ayanka dabbobin arziqinsu ne. Jin hakan yasa ADAMS murmushi yace mata aa raguna uku shanuwa d'aya sun isa.. Tace to badamuwa. Y'an tattun suna aka sama yaran kamar... Musu da Aliyu sai qaramarsu Rahma... Wannan suna ya tara mutane ba d'an kad'an ba. Saboda bajintar da Yawo tayi asunan bad'an kad'an bane. Haka shima Adams ana saura kwana biyu suna sanda ya saida saniyarsa irin way'anda Yawo take basa yaba usman kud'in yace dan Allah yaba matarsa tashiga kasuwa takwaso masa rugunan yara da atamfofi masu kyau irin na mejego.. Wannan yasa sunan MUSLEEMA ya zarce dukkan wani sunan yara da akeyi a rugar.. Sunan dai kam ya zama sunan kwatance... Dan kowa yaci shinkafa da nama san ransa. Wannan shine kawai abinda akayi asunan kuma ya qayatar ya gamsar da al'umar rugar... Matar Usman kasance warta doctor itama kamar mijinta data zo sunan sanda takeb'ance da MUSLEEMA ta duba gabanta tatabbatar bata samu qari ba sannan hankalinta ya kwanta.. Saidai tayi mamakin yanda bataje asibiti ko sau d'aya ba Amma cikinta ya rayu da lafiya. Gashi itama da lafiya ga yaranta gwanin ban sha'awa. Duk da haka sanda tabama yaran kulawa irin tasu ta likitoci. ____________________________ San duniyar nan haka ADAMS ya d'auka ya d'ora kan MUSLEEMA da yaranta.. Yara suna rayuwarsu rayuwa me inganci. Usman da matarsa yaran sun shiga ransu hakan yasa suke zuwa suke ba yaran kulawa irin tasu ta likitoci acewarsu bai dace su zauna haka ba kulawar likitoci ba... *************** Ayanxu shekarar yaran biyu da wata d'aya.. Yaran sun taso gwanin ban sha'awa abinsu. Ga surutu ga wayo.. Idan kagansu Sai kace sunkai shekara uku. Saboda girmansu da lafiyar da suke tare da ita.... Da kanta MUSLEEMA take kaisu wajen malam jauro d'aukar karatun Alqur'ani me girma. Zanso gaji yanda suke d'auke komai akansu idan an biya musu.. Yau take Asabar tun safe MUSLEEMA taji gabanta na fad'uwa haka kawai.. ADAMS na lura da canjin yanayinta dan haka bayan sun idar da karyawa ya kalleta da cewa.. "Na lura yau tunda kika tashi baki da kuzari.. Jan numfashi tayi da kallansa shima tace.. "Eh wallahi. Haka kawai naji gabana na fad'uwa kamar zan rasa wani abu me mahimmanci arayuwata. "Niko kinga bani jin komai. Dan haka kishare dan ba mamaki ko alkairi ne yake san zuwa gareki. Murmushi Yawo tayi da cewa.. "Eh nima fa haka nake ji araina haka kamar wani abu zai faru damu.. "Haba Yawo kema da tsufanki zakina fad'in hakan danki tsurar min da mata. Kunga nima fa shuru nayi. Dan Wallahi yanda kukeji haka nima nakeji.. Da marairaicewa cikin shagwab'a MUSLEEMA tace.. "Bana san nayi rashin koma wane irin abu ne haka arayuwata. Dan Allah mijina katayani da addu'a. Kama hannunta yayi cikin so da qauna yace. "Baki da matsala da hakan matata. Fatana yanxu ki kwantar da hankalinki dan ba abinda zaki rasa.. Murmushi kawai tasakar mai. Yawo ta girgiza kai. Tana tuna wane irin so ADAMS yakema MUSLEEMA ne.. Ahankali tatashi daqer tabar musu wajen. Saboda ciwan da yake damunta na duk jiki. Wanda yake haka ga kowane mutum idan ya d'auko hanyar tsufa. Ganin hakan yasa ADAMS jan matarsa d'aki dama yaran nasu suna makarantar malam jauro.. Acan uwar d'aga ya ritsata yana cewa.. "Ban tab'a jin muguwar sha'awa irin tayau ba.. Kallansa dayi da muradi tace.. "Nima haka YAYANA.. Sun faranta ran juna kamar bazasu bar juna ba. Tana qirjinsa yake cewa.. "Maganar gaskiya qanwata ina jin wani iri araina yau kamar yanda kika fad'a d'azu. Kallansa tayi da Qara shige masa tana me fad'in. "Nidai koma dai miye Allah kabarni da mijina da yarana da kuma kakata.. Shafata yahau yi da yana amsa mata da "amiin.. Lokacin da suka fitto Yawo bata nan da alama ta fitta ne.. Suna jin dad'in yanda suke wanka a tare. Kuma sun lura kamar idan suka keb'e da juna da ranah Yawo shiga makwafta take.. Hakan ne yake basu damar yin wankan tare da ranar ma Da gaske Yawo bar musu gidan take.. Saboda tana jin kukan MUSLEEMA idan suka keb'e da juna. Ta tabbatar ADAMS ya gama samun MUSLEEMAN ne shiyasa koyaushe cikin yimai ihu take.. Ba dare ba ranah.. Toh abin naba Yawo kunya🙈 shiyasa take barin musu gidan. Gwara da daddare tayi bacci wani lokacin bata jinta. Dan idan kaji tajita da daddaran to dama ciwan qafarta ne ya dameta ya hanata bacci shiyasa take jinta. Allah yasa yaran a d'akin Yawon suke kwana ba'a d'akinsu ADAMS d'in ba. Dan inda ace a d'akin su Adams d'in suke kwana ba makawa tashinsu MUSLEEMA zata dingayi da ihun nata idan abin ya ciyota.🙈 Shiko ADAMS tun abin nata na bashi kunya kar Yawo tajiyota har ya cire kunyar ya ajeta gefe tunda ya fuskanci kamar halittartace haka.🤣 Ga ita MUSLEEMAN ko bata san Ashe Yawo tana jin kukanta da ihunta haka ba. Shiyasa bata tab'a tunanin denawa ba. Haka suka saka ruwa sukayi wankansu. Wannan ranah duk jikinsu a sanyaye yake. Haka ADAMS ya shafi gefan faskar MUSLEEMA yace.. "Bara naje wajen shanu na duba lafiyarsu na dawo ko. Kallansa tayi cikin so da qauna tace.. "Ka kula da kanka YAYANA karka bari wani abu yasamar min kai. "Zan kula miki da kaina qanwata fatan kema kijimin da kanki. Ahankali tamatsa jikinsa tasakar mai kisa a baki tace.. "Zan kula ma da kaina.. "Kinyi alqawari.. "Nayi maka mijina.. Qara shafar fuskarta yayi da sakar mata murmushi ya fitto daga d'akin.. Yazo zai fitta waje kenan sukaci karo da Yawo. Tace. "Har kafito zaka daji ne. "Eh amman ina jin yanxu zan dawo dan ina jin kamar zazzab'i ne yake san kamani. "Toh kadawo kawai ka kwanta mana. Idan kaji dama dama ka fitta anjima..... Kan ADAMS yayi mata magana saigasu Khalit da Khalil da Rahma sunshigo (dake haka ake kiransu. Wannan ma malam jauro ne yake kirasu da hakan. Wato Musa shine Khalit. Aliyu Kuma Khalil. Shekenan sai Yawo tafara kiransu da hakan shine ya bisu dan Rahma ita ba'a mata wani inkiya ba.) Wata Rabi ce a makwaftansu take dawowa dasu idan MUSLEEMA takaisu. Da Farin ciki sosai ADAMS yake d'aukarsu. Idan ya sauke Wannan saiya d'auki wancan. Suko sai murna suke dan baqaramin San uban nasu suke ba.. Sanda ya koma gidan ya zaunar dasu sannan yama Yawo sallama yana cewa gwara yaje dai ya duba tabbobin yaga ya suke idan yaso ya dawo ya kwantar.... Jin hakan yasa tamai fatan dawowa lafiya.... Saidai ADAMS baiyi nisa a tafiyarsa ba Iro da wasu abokansa uku suka taresa wai yaje inji malam jauro.. Har ADAMS yayi haryar gidan Malam jauro d'in sai Iron ya dakatar dashi wajen cewa ai baya gida kadaixo muje daji acan yake yaje sassaq'o wani magani ne. Jin hakan yasa ADAMS binsu da zuciya d'aya Sai tafiya suke cikin daji can Adams yace "Wai har ina malam d'in yake ne. Shuru sukamai. Ganin hakan saiyaja bakinsa yayi shuru sukaci gaba da tafiya.. Dake Iro tashin wajen ne. Yasan lungu da sak'o na dajin. Dan haka nan kusa suka kusa b'ollowa titi. Ahankali Iro ya fara dawowa baya da baya dayima d'aya daga cikin abokan nasa nuni da ido wai ya wuccesa. Aiko cikin sauri abokin nasa ya wuccesa saiya kasance yana gabansu su suna bayansa.. Da haka da haka Iro ya koma baya can ya kasance shine a qarshensu suna gaba yana binsu a baya.. Aiko ganin ADAMS ya tattara hankalinsa kawai a gabansa. Sai ko Iro ya d'aga sandarsa sama 🙄 ya sauketa a ƙeyar ADAMS. Saiji kake gubbb😳..... Ai nan take ADAMS yaji kansa nayi masa hajijiya. Bai samo nutsuwarsa ba Iro ya qara sakar masa wata sandar awajen.. Aiko wannan karan sai zubewa qasa ADAMS yayi warwar alamar sumewa.. Dan bugu ne na shammata. Kuma na mugunta. Sannan nasan illatarwa.. Dariya Iro yayi da cewa.. "Dama nayi ma ZUCIYATA Alqawari bazan tab'a garinka kaci gaba da rayuwa da MUSLEEMA ina gani ba. Nayi alqawarin saina maka illah. To gashi ka gani... Sanda ya gama duk iskancinsa sannan suka kinkimesa sukayi titin dashi... Basu qarasa titin ba suka ajiyesa dan hutawa Suna cikin hutawar ne zai sukaga wata mota tatsaya wani na miji ya fitto daga motar da mata biyu suna masu duba motar... Can sai sukaga matan sun fara nufo inda suke da gorar swan water a hannunsu. Kan suyi wani qoqari na b'oye ADAMS kar matan su gansa saiya kasance har sun iso wajen nasu. Lokacin Yayi daidai da rungume Adams da Iro Yayi D'aya daga cikin matan tace dan Allah ku temaka mana da ruwa musama motarmu.. Kan subata amsa d'ayar tabigi kafad'ar wacce tayi maganar tace.. "Kinga salma wannan mutumin baya miki kama da LEEKITAN da yake duba momy wanda take gaya mana ya b'ata shekarun baya... Qura ma ADAMS ido wacce aka kira da salma tayi. Can tace. Kuma fa suna kama. Saidai wannan yad'anyi baqi da rama. "Nima abinda magani kenan. Waccan yafi wannan fari da gogaggiyar fata Wannan kuma Yayi baqi da siranta.. D'ayar tafad'i hakan danuna tabbaci Salman tace... "Niko mema sunan wancan d'in... "Ni dai nafi saninsa da LEEKITAN ZUCHIYA kamar yanda momy take fad'a yafi duba ZUCIYATA akan kowa b'angare na jiki. Bacin hakan bansan ainiyin sunansa ba. Kinga munemi abinda zamu nema gunsu lokaci na tafiya. Jan numfashi salman tayi da qara kallansu tace.. "Dan Allah kuna da ruwa.. Girgiza mata kai iro yayi alamar basu dashi. "Toh yanxu a ina kuke ganin zamu samu "Gaskiya bamu sani ba. D'aya daga cikin abokan Iro yace da ita hakan Ganin hakan sai suka tafi dan su gayama saurayin da suka fitto tare dashi daga cikin motar wanda ya bud'e murfin gaban motar yana dubawa. Ahankali ya kallesu yace dasu aina samu ruwan. Sukace a'ina ya samu. Nan yake gaya musu Ashe yana dashi a bayan but na ledar pure water. Sukace toh yanxu gyaran me yakeyi. Yace kawai yana dad'a duba motar ne bawai badan tana da wata matsala ba. Jin hakan sai yasa suka shige cikin motar shima ya rufe murfin gaban motar yashiga ciki sukayi gaba abinsu.. Iro ya kalli abokansa yace "Yanxu ya zamuyi dashi ne. "Kawai mubarshi anan.. Inji wani daga cikinsu. Iro yace.. "Kai baka da kai. Idan muka barshi anan wani na temaka masa ya farfad'o zai iya gaya masa inda yake. Kaga shikenan ya qara dawo mana ruga kenan. Kawai mu jira wata motar Lodi wacce zata gari me nisa saimu biya direban yakaishi can. Idan ya tashi duk wanda zai gayama daga Rugar malam jauro yake baza'a kallesa ba. Dan ba wanda ya Santa a garin. Kunga shikenan zaiyi hakuri ya kama wata rayuwa. Ni kuma na aure MUSLEEMA.. Sun yarda da shawarar tasa.. Dan haka suka zauna awajen sunata hirarrakinsu. Suna kallan motoci na wuccewa daga nesa. Tunda su motar Lodi suke nema tazo..🤔 Suna nan a haka saiga wani me motar Lodi zai wucce.. Ai da sauri Iro yaje ya taresa. Direban ya zaci kayansa ne wani ya kunce ya fad'i. Saida ya tsaya yaga tsab'anin hakan D'an tsohu ne direban. Irin tsofaffin y'an iskan nan. Dan kana masa kallo d'aya zaka san d'an bariki ne. Gashi ya bugu alamar yasha kwaya tamai karo kamar yanda suka saba sha. Da wani yanayi ya kalli Iro yace.. "Kai Yaro menene dalikinka na tareni.. Iro ya kalli bayan motarsa da take abud'e hanhai kamar ta d'aukar gawa. Sai kullun kayayyaki da suke cikin buhu burjik alamar lodi. Saiya dawo da kallansa garesa Yace.. "Dan Allah wane gari zaka. Direban yace.. "KANO na nufa... Da sauri iro yace.. "Dama ko wani d'an uwanmu ne zashi KANON gashi can. Dan Allah sai musamaka shi abaya cikin kayanka. Kana zuwa saika saukesa.. Direban ya kalli Iro a wulaqance yace. "Ban gane kusamin shi cikin kayana kamar wani kayan wanke ba. Shi bashi da rai ne daba zai hau da kansa ba sai kun sashi... "aa ba wai haka bane yana da ciwan bacci ne. Yanxu baccin yayi.. Ga wannan dan Allah katemakemu musa maka shi.. Iro ya fad'i hakan da miqara masa kud'i har naira dubu uku.. Kunsan direbobin nan da san kud'i. Bare wannan dayake a make. Ainan da nan ya amsha kud'in yana cewa kusashi. Nan take Iro yakira abokansa dasu tawo da ADAMS d'in. Cikin sauri ko suka kinkimosa suka kawosa nan. Haka suka temaka ma iro suka sashi cikin kayan lodin nan cikin hikima wanda kana gani zaka zaci bacci ne ya d'aukesa. Dan sun ajiyesa da tsari.. Suna gama sashi suka cema direban sun sashi. Nan ko yaja motar shi abinsa. Iro da abokansa suka sheqe da dariya suka koma cikin dajin dan nufar Rugarsu... Lokaci lokaci sojoji masu tsaran hanya suka cema direban daya d'auki ADAMS d'in.. Shiko wannan baccinsa yake abinsa.. Direban ya kan basu amsa da cewa. Eh yayi bacci.. Lokacin dayaga yafara nufo kano tsayawa yayi anan d'an wani daji ya fitto ya karema Adams kallo yadai tabbatar babu numfashi atare dashi. Aiko saiya saukesa ya barsa nan bakin titi yana cewa "Y'an iska qilama matacce suka samin dan nashiga uku. Haka direban nan yayi gaba abinsa yabar Adams anan yashe... Minto goma tsakani wani Alhaji yazo wucce da motarsa me d'an kyau haka shi da yaransa da alama suna kan hanyarsu ta nufar wani gari ne. Sai kawai yaga ADAMS a yashe kan titi. Nan ya yatsaida motar tashi suka fito shi da d'ansa dan ganin abin mamakin waye haka akan titi.. Suna zuwa alhajin nan ya qarema ADAMS kallo ya tabbatar lalle wannan idan ba doctor ADAMS bane LEEKITAN ZUCHIYA ya tabbatar d'an uwansa ne. Dan haka yasa d'ansa ya temaka mishi su sashi cikin motarsu. Suna mamakin ya akayi yake kwance haka a gefan titi inda babu kowa agun haka. da alamama ko rai yayi halinsa. Fatansu dai yanxu su isa garin nasu na kaduna su kaishi asibiti suji yana da rai koko baya dashi dan sunji jikinsa bai sake irin na mamaci ba .. Cikin ikwan Allah sun iso garin kaduna lafiya basu zarce ako Ina ba sai'a wani asibiti wanda ya amsa sunansa new yan hospital.. Anan masana sirrin lafiya suka shiga caje ADAMS. Nanko suka gano yana da matsala babba. Suna tunanin tunaninsa ya tab'a d'aukewa a baya. Yanxu suna fatan idan ya tashi farfad'owar tunanin nasa ya daidaita.. Jin hakan da alhajin yayi sai kawai ya kira Dadyn ADAMS a waya dake amininsa ne yace mai dan Allah yazo nan asibitin yaga wani mutum me kama da ADAMS nasu. Shifa yana ginin kamar Adams ne mah. Ai Dady najin batun abokin nasa ya tashi zunb'ur daga falansa ya saka takalmi ko bin kan d'aya daga cikin matan nasa baiyi ba ya ficce daga gidan sai asibitin... Dady Suma yayi dayaga ADAMS. Dan babu wani canji da ADAMS zai samu a rayuwarsa wanda zaisa Dady ya kasa gane shi.. Bayan ya farfad'o kuka ya sake yana me hangen ADAMS ta jikin window saboda likitocin sunqi yarda ya qara zuwa ga ADAMS a karo na biyu dan karya qara sumewa.. Dady yasha kuka dan yacire tsammanin qara ganin ADAMS d'insa... Dady ya tabbatar ma da abokin nasa Adams ne ba wani ba.. Anan abokin nasa yake basa labarin yanda akayi yaga ADAMS d'in. Da bayanan da likitoci suka fad'a akansa.. Jan numfashi Dady yayi. Ya tabbatar Allah shine me iko. Dama saidai idan ADAMS baya cikin tunanin shine zai iya d'aukar way'annan shekaru batare da yayi waiwayen gida ba... Anan Dady yakira su Ammi ya gaya musu Amman Yace karsu gayama su NUFAISAT har saiya farfad'o.. Ammin Adams bata tab'a jin labari me dad'i irin nayau ba... Jin dad'in nata yaqara tabbatuwa ne lokacin data hangi ADAMS d'in tajikin window ita da Hajjiya Rukayyat.... 🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻 Me karatu idan kayi tunani ya kamata kasan koda ADAMS ya farfad'o bazai iya tuna wata rayuwa yayi da wata MUSLEEMA ba.. Koda zai tuna wani abu tunanin zai dinga masa wasa ne kamar yayi mafarki ne ya tashi. Kuma mafarkin bazai nuna mishi komai yanda zai ankare ba. Sannan kunsan ambar baya da q'ura tafannin su MUSLEEMA.. Kuci gaba da bina a LEEKITAN ZUCHIYA inda zamuga wacece cikin matan Adams take da mallakin wannan sunan abakinta na LEEKITAN ZUCHIYA ina zata ganshi ya gyara tunaninta..🤫 [7/17, 3:49 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 21☆ Zama Amminsa tayi tana me godema Allah daya bayyana mata d'an nata.. Hajjiya Rukayyat ko haka kawai sai taji bataji daɗin bayyanar ADAMS ba. Dady ko sallar godiya ga Allah yake tayi dan ba qarya yaji mafificin Farin ciki sosai da yanda ADAMS ɗin ya bayyana. ADAMS bai samu kansa ba sanda yakai kwana uku kana ya samu kansa. Lokacin daya bud'e idansa qarema ɗakin dayake kallo ya fara yi. Yana tunanin meya kawosa asibiti haka... Dake shigowar doctor Suleiman kenan wanda yafi bashi kulawa sai yayi murmushi dace mai. "Masha Allah. Allah abin godiya. Wlcm da tashi. Murmushi ADAMS yayi masa da faɗin. "Yauwa. meya kawoni asibiti haka. Murmushi doctor Suleiman ya qarayi yace.. "Bara dai na kira maka iyayenka sai kaji daga garesu. Amman kafin nan ɗan bani dama na qara tabbatar da lafiyarka.. Murmushi ADAMS d'in yayi mai kawai. Ganin hakan saiya fara dubasa dakyau ya tabbatar yanxu bashi da wata matsala sai ɗan ciwan kai dayace mai yana damunsa. Magani ya basa da ficcewa ya gayama su Dady ya farfad'o. Ainan take sukayi ciki da murnarsu. Dady ya kama hannunsa yana nuna masa zahirin Farin cikin da yake ciki. Yace dashi. "Yanxu Ina ne yake kama ciwo my son. ɗan ɓata fuska ADAMS yayi da cewa. "Kai na ne dai kawai.. Wai Dady meya faru dani ne aka kawoni asibiti. Shuru Dady yamasa. Sai Amminsa ce ta amshi zancen da cewa. "kai zamu tambaya meya faru dakai. Amma ba yanzu ba sai mun koma gida. Sun ɗan jima suna hira. Can dai ADAMS ya kasa haƙuri yace. "Ammi ina NUFAISAT da TAUDHAT ne & my daughter Haneepha.. "ADAMS kayi haƙuri mu koma gida mana. Yanzufa ka tashi ya dace kabama kanka lokaci ko kaɗan ne. Ta gayamai hakan da damuwa Shuru ADAMS yayi. Yanxu jikinsa ya fara basa akwai wani abu da ya faru wanda basu san su gaya masa.. Haka zuwa can yamma bayan likitocin sun tabbatar da bashi da wata matsalar daza tasa su riƙesa sai kawai suka bashi sallama. Adams yayi mamakin yanda ba asibitinsu aka kaishi ba. Mamakinsa ya qara tabbatuwa ne lokacin da suka isa gidansa. Yaga canji dadama agidan. Dan Dady tun randa yaga ADAMS ɗin yasa aka fara gyaran gidan nasa. Anyi saban fanti anyi gyaran sauri dai gaskiya ba lafe gidan ya qara kyau. Anan yake sanar da masu tsaran Adams ɗin cewar anga Adams ɗin Shiyasa yanxu da sukazo gidan sai shigowa suke suna masa barka da dawowa. Shi dai amsawa kawai yake yi amma azahiri bai san meyasa suke mai barkan ba.. Lokacin daya shiga toilet wanka matsama kansa yayi da tunani yana san tuno wani abu. Amma sam bai tuno komai ba. Bayan ya fitto yana shafa mai da alamama kayan shafe shafen nasa sabbine ne aka saka mai awajen. Murmushi kawai yayi yana tuna NUFAISAT dan itace ta fad'omai. "Wai suna ina ne.. Yayi furucin abayyane. Sauri sauri gudu gudu haka ya gama kintsa kansa ya dawo falan nashi inda su Dady suke jiransa.. Anan sukace ya gaya musu bayan tafiyarsa garin gwambe meya faru dashi... Ai dajin haka nan take ya fara tuno abin daya faru.. Sanda ya gaya musu komai wanda y'an iskan yaran nan suka masa. Sannan yaqara da cewa.. "Wallahi Dady bayan hakan bansan kuma meya faru dani ba. Sai yanxu dana tsinci kaina a asibitin da muka dawo yanzu.. Jan numfashi Dady yayi sannan shima ya kwashe duk yanda al'amuran suka faru dasu anan.. Sosai ADAMS yayi mamakin abokin nasu Ibrahim. Ya tabbatar da lalle mutum abin tsoro ne. Amma banda haka hujjar dashi Ibrahim ɗin ya bayar wai akanta yake neman rayuwarsa sam ba abar dubawa bace awajensa shi. Dan gani yayi ai ɗaukaka awajen Allah take kuma mutum baya tsallakema arziƙinsa Hankalin ADAMS ya tashi sosai dajin yanda ya ibi shekaru masu tsawo haka. Gashi shi ya kasa tuno komai bare ya gaya musu gashi gashi ga rayuwar da yayi.. Saidai ya dace ya koma inda aminin Dadyn nasa ya tsinceshi yaga ko akwai wanda ya sanshi agun... Nan dai yaci abinci me rai da lafiya wanda Amminsa tasa laraba me aikinta tayi masa tun sa'adda ya farfad'o. Sanda ya gama ci take gayamai yau yaci girkin ƴar aiki. Da mamaki yake kallan Ammin tasa da cewa dama ba ita ce tayi mai ba. Hajjiya Rukayyat tace yi shuru dai kawai dan yau kaci girkin ƴar aiki.. Murmushi shida Dady da Salim sukayi. Anan Dady yake cemai bara yaje gida ya kira iyayan matan nasa NUFAISAT da TAUDHAT dan agyara musu auran nasu.. Komai yayi daidai inji ADAMS. Karb'ar wayarsa yayi gun Amminsa ya kira Yusuf awayar yake cemai... "Kai gauro ban mutu ba. Dena nemana nadawo gida cikin hankalina😂.. Yusuf dake kan gadansa damuwar kakarsa ta ishesa kan saiya nemo matar aure sai ganin kiran ADAMS ɗin kawai yayi awayarsa. Da matuqar mamaki ya amsa kiran yana addu'ar Allah yasa yaji muryar ADAMS d'in.. Aiko yana jin muryar tashi ya tatashi zumbur dace mai.. "Alhamdulillah.. Allah na gode maka daka dawomin da aminina ɗan uwa na. ALLAH kabarni dashi ko'a gidan ALJANNAH NE... Dariya ADAMS yayi da faɗin. "Wato saida na ɓace kasan mahimmanci na agareka ko. Yace "kamarko kasani ɗan uwa. Yanxu dai kana ina ne wallahi na zaƙu najika na ganka ko Farin cikin nawa yayi low. "Saidai yayi hai✋🏻. Dan daga lahira nake magana dakai..😂 Dariya sukayi gabaki ɗaya.. Adams yana meci gaba da cemai yazo gidansa ya samesa yana so yaje yaga ƴan matansa wato NUFAISAT da TAUDHAT Ai ba shiri Yusuf ya fito daga ɗakinsa direct ga motarsa ya nufa bai tsaya ako ina ba sai'a gidan ADAMS. Anan ko falansa ya gansa ya rungumesa suna masu jin daɗin ganin juna. Sanda ADAMS ya bashi labarin komai. Sannan shima Yusuf yace. "Wallahi na shiga damuwa daban ganka a garin gwambe ba. Haka nashiga tashin hankali da Ibrahim yake bayanin wai shine wannan maqiyin naka me neman rayuwarka. Wato ADAMS wallahi yanxu mutum tsoro yake ban. Shiyasa naqi yarda da kowa tun bayan ɓatanka bani da aboki. Yanxu naji mafificin Farin ciki sosai dana tsinci muryarka cikin wayata. Dole na qara Alwala nayi salla danna godema Allah daya qara haska fuskokinmu gani gaka... Qara rungumarsa ADAMS yayi dan ga zahiri nan na damuwar rashin nasa ta bayyana ajikin Yusuf ɗin danya rame sosai gashi bashi da kuzarin da yake dashi kamar yanda ya sanshi. Ahankali yace dashi. "Har abada bazan samu abokin gaskiya kamarka ba Yusuf. Wallahi ina sanka ina qaunarka kaci gaba da suna da amana nima zanci gaba dasanka da amana. "Baka da matsala da hakan ADAMS. Yanxu dai ina muka nufa. Sannan banga su Dady ba. "Eh su Dady sunyi gida. Yanxu dai rakani wajen matana zakayi naga awane yanayi suke. Duk da na samu labari agun Dady kana kulamin dasu sosai. Wannan ma yasa nake san qara gode maka.. "karka damu da wannan ma. Dan Idan baka waje komai naka abin dubawa nane. Haka nasan idan nima bana waje komai nawa abin dubawarka ne. Yanxu muje Kagansu hankalinka ya kwanta. Dan naga har wani rawar kai kake... Murmushi ADAMS yayi da dakar kafaɗar Yusuf d'in Suka ficce daga falan... Da sauri masu tsaransa sukazo dan bud'e musu mota sukaisu inda zasu. Dakatar dasu ADAMS yayi da cewa.. "Yanxu na gane maqiyin nawa me neman rayuwata. Zanyi zama daku ran lahadi in sallameku dan dama nifa ba wani san yawo daku nake ba. Cikin sanyin jiki suka kallesa da cewa. "Bamu fatan barinka oga. Saboda kai mutum ne. Kasan darajar ɗan Adam. Gashi abinda kake bamu yana wadatamu da iyalanmu. Idan har kace baka san kulawar da muke baka bazamu tab'a samun wanda zai dinga biyanmu yanda ya dace ba.. Jan numfashi ADAMS yayi da cewa... "Toh naji. Kudai had'a kanku ranar lahadi kusameni. Sannan yanxu dai bani buqatar kuyimin rakiya. Toh suka cemai saiya shige motar Yusuf ya jasu.. Suna zuwa unguwar sukaga TAUDHAT ta fitto taci kwalliya ita da yarinyarta Haneepha. Waro ido ADAMS yayi ganin yanda tayi ƙiba komai na jikinta ya cika tam tam. Ta qara wayewa da ganinta kasan tana jin daɗin rayuwa.. ADAMS yace. "Wow Hankalinta akwance. "Kuma fa kwanan nan tafara qibar nan. Cewar Yusuf. Tsaki Adams yaja da cewa. "Karka wani kareta malam. Yana faɗin hakan ya fitto daga motar sosai jikinsa yake fudda qamshin turaransa.. ƙamshinne ya bugi hancin TAUDHAT ta ɗago da saurinta dan jin wane mahalukin ne ya mallaki ƙamshin ADAMS... Ai tana haɗa ido dashi tawancakalar da jakarta da wayarta kobi takan ƴarta Haneepha batayi ba ta daka wani tsalle saigata a ƙofar gidasu. Da sauri tashige cikin gidan nasu tana maida numfashi. Tunaninta gamo tayi. Dan yanxu tagama tunanin ADAMS d'in shiyasata tunanin ko wannan aljani ne. Murmushi ADAMS yayi danya lura ta tsorata dashi ne. Ahankali yaje ya kama hannun Haneepha tare da rage tsawansa yace da ita. "Haneepha kin gane ni. Shuru tamai tana me qarema fuskarsa kallo. Can tace. "Na ganeka kana kama da Dadyna na photo. Sai dai Dadyna ya fika fari. Murmushi ADAMS yayi da manna mata kiss a goshi. Yace. "Nine Dadynki kawai nayi rashin lafiya ne yasa nayi baqin. Amman Farin nawa zai dawo nan kusa kinji.. "Toh Amma me yasa ka gudu ka barni baka zuwa guna. Kullum mamana ce take kaini skull kai baka kaini. "Ba guduwa nayi ba. Nace miki bani da lafiya ne amma yanxu na samu sauqi kullum zaki dinga ganina kinji. ɗaga masa kai tayi. Alamar taji.. D'auko jakar TAUDHAT d'in yayi da wayarta yaba Haneephan yana cigaba dace mata Yanxu jeki gayama mamanki tafito.. Ai da gudu tayi cikin gidan tana cewa mamah mamah kifito ga Dadyna.. Kama hannunta TAUDHAT tayi da cewa. "Ya kama hannunki. "Har kiss yamin Dadyn. "Toh jeki gun mamah zanje ni gunsan. Toh Haneepha tace mata tanufi gun mama dake zaune kan taburma tana cin burabisko.. Da qarfin hali TAUDHAT ta fitto tana qara had'a ido da ADAMS ya galla mata harara. Sanda ta iso garesa yace mata. "Wai da ɗazu ina zaki kikaci wanka haka. Kallansa da sauri tayi yanxu ta tabbatar da cewar shine. Cikin matuqar Farin ciki sosai tace.. "Wayyo Allahna wai da gaske Kaine agabana. Harfa na cire tsammanin ganinka. Wayyo Allah abin godiya. Gaskiya naji mafificin daɗi da sanyi sosai. Kamar na rungumeka saidai gamu akan titi🙈. Murmushi yayi da cewa "baki dai so hakan ba. Yanxu kaimu muga Mamah idan naganta anjima idan Aka dawomin dake kyayimin yanda kikeso tunda yanxu kin kasa. Murmushi tayi da shigewa gaba tana cewa. "Muje kawai.. Haka tana gaba suna binta abaya har zuwa cikin gidan nasu. Mama murmushi tayi mai da nuna mishi Farin cikinta Sosai na ganinsan da akayi. Har take qaramai ai bata dad'e dayin waya da Dadynsa ba yake gaya mata bayyanarsa. Tana kyautata zatan anjima ma zaiso kan batun komawar TAUDHAT.. Murmushi ADAMS yayi suka tashi dayi mata sallama kan zasu shiga cikin gidansu NUFAISAT.. Nan taqara sakin fara'a dayi musu fatan alkairi. Bayan sunfita ne TAUDHAT taja tsaki dacema Maman nata.. "Ke dai mamah bazaki dena munafunci ba. In banda munafunci Ashe d'azu da Dadyn ADAMS d'in kike waya shine kika kasa sanar dani angansan sanda yazo sannan nake sani... Kallanta maman tayi kawai dan yanzu lamarin TAUDHAT d'in ya dena bata mamaki Sam... Su Adams ko gidansu NUFAISAT suka shiga... NUFAISAT ɗin na barandarsu ta sama da wani littafin AUNTYN LUV tana karantawa me suna *ABU KAMAR WASA FAH* jaruman cikin labarin suna burgeta hakan yasa take tare da nishaɗi.. Ji tayi ajikinta kamar ana kallanta. Saita maida kallanta inda tafi tunanin daga nan ake kallan nata... Aiko sai ganin masoyin nata tayi shida Yusuf jikin motar mummy ɗinta.... Nan tatashi da yar da littafin tana me murza idanta danta tabbatar da gaske mijin nata ne abin alfaharinta.. Murmushi ya sakar mata da dafa Yusuf dan ta tabbatar dashi ɗin ne.. Aifa ƙafa me naci ban baki ba. Nan tasheqo da gudun gaske ta sauko qasa mummy dake falo tana yankan farce fad'i take "ke lafiyarki kike gudu haka.. Sam batabi ta akanta ba sanda tayi waje lokacin yayi daidai da ware mata hannunsa da yayi alamar ta rungumesa. Dama itama niyarta kenan. Ai zafin nama taje ta rungumesa.. Fad'i take. "Mijina ka dawo gareni. Mijina ne wallahi. Mijina ne Yusuf ba kowa ba. Mijina ne na tabbatar. Mijina ne naji ɗuminsa. Mijina ne shine wallahi... Saka mata hannunsa yayi a bakinta alamar tayi shuru danin yanda take a rikice .. Aiko shurun tayi idanta cikin nasa. Cikin sanyayyiyar murya yace.. "Bazan iya rayuwa babu ke ba! dan ina tabbatar miki ko mutuwa ce tazo d'aukata rokwanta zanyi ta had'a dake. Saboda ina san kabarinmu suyi makwaftaka da juna... Tunda nadawo haiyacina farkwan tunanina kece my LUV. Dan haka ki nutsu da kyau matata danki qara gaya min naji sanyi araina. Madallah. Yanzu gaya min ya kikaji da kika ganni... Jan numfashi tayi "Komai ma naji mijina. Na rikice matuqa da ganinka. Dan Allah kayima zuciyata gata kada ka qara aikata wannan babban lefi agareta. Na shiga tashin hankali. Na shiga ɗimuwa sosai dana rasaka. Ashe da gaske kaine ganina. Dana rasa ganinka kowa haushin kallansa nake ji.. Ashe da gaske kaine jina. Dana rasa muryarka. Kowa jin muryarsa nake kamar maɗaci. Ashe da gaske kaine gangar jikina. Dana rasa ɗuminka rashin lafiya baibarni ba sai yanxu dana jini jikinka. Nayi missing abubuwa uku arayuwata. Wanda tunda ka ɓace har yau mummy da Dady wany'anda suka isa dani fama suke dani akansu. Sun kaini asibiti yafi sau nawa akan hakan. 1 Bana cin abinci yanda ya dace. B'cos idan nasaka agabana kai nake tunani. 2 Bana bacci yanda ya dace. B'cos idan na kwanta kai nake tunani. Bana cika magana da kowa. B'cos daikai kaɗai na iya hira.. Meyasa hakan ta faru dani. Saboda karigada ka ɓata masu tarbiyar ƴa... B'cos daka baka auranta kacanja musu duk wani abu da suka raineta dashi. ADAMS kaine rayuwata. Nayi alqawarin bazan tab'a bari wani namiji ya raɓar maka jikina ba idan har na rasaka arayuwa saidai na mutu babu aure... NUFAISAT takai ƙarshen zancenta da zubo da hawaye.. Ahankali yahau lashe mata su. Cikin matuƙar so da ƙauna "Ina sanki matata. Ina qaunarki matata. Ina fatan zarce kasancewa dake har agidan ALJANNAH.... Kai bakinta tayi cikin nasa ta aika masa da wani shu'umin kiss.... Cikin matuƙar buƙata yaso gyara mata mazauni a qirkinta wajen san su kasance da jin ɗumin bakin junansu. sai dai Yusuf ya katse musu jin dad'in nasu wajen cewa.... "Na farko agidan surukai kuke. Bacin nan saiku ɗan jin kirta agyara muku auranku... Denawa NUFAISAT tayi cikin jin kunyarsa. Sai dai duk da haka sanda ts qara bajewa a qirjinsa tana lumshe ido da kallan Yusuf tace.. "Dole surukan su mana uziri.. Murmushi yayi da cewa.. "Kimana iso wajen momy kawai mu gaisheta idan yaso kwaci gaba.. ɗago da kanta ADAMS yayi da cewa.. "Kiyi haƙuri matata ganin yanda ya katse mana qauna... "Da wani hali tace mai.. "Ba batun haƙuri kawai ka hukunta shine abun da zaifi. Murmushi yayi da faɗin "Yusuf ne fa.. Itama murmushin tayi da bashi amsa da. "Tona nayi hak'uri. "Yauwa masoyiya maza rakamu gun mummy itama taganni ta tabbatar. Murmushi ta qara mai... Hannunsa cikin nata haka suka shige gaba Yusuf na binsu a baya da murmushi akan fuskarsa dan Sosai suka birgesa. Har jin wani abu yayi aransa yadai yi addu'ar Allah ya kawo mai masoyiyarsa suma suyi rayuwa fiye da yanda ADAMS yake da NUFAISAT😄... Sun gaisar da mummy inda tanuna Farin cikinta sosai da bayyanar ADAMS ɗin.. Haka suka baro gidan zuciyar ADAMS cike da buqatar kasancewa da NUFAISAT. Da misalin qarfe takwas na dare iyayan nasu suka tattauna kan batun komawar su NUFAISAT d'in.. Bayan sunyi abin daya dace ADAMS yaso aranar akawo maisu. Saidai dole yayi haƙuri ya barma gobe. Aiko da misalin qarfe goma sha biyu TAUDHAT ta koma d'akinta. NUFAISAT ko sanda takai hud'u saboda shirye shiryen da mummy da Zainab suka tsaya yi mata.. Da misalin qarfe tara na dare ne yake tare dasu a falan nasa bayan ya gama gaya musu iya abinda yasani akan dukan da y'an iskan nan suka masa.. Nan yake tsokanarsu wai daga d'akin wayake ne kafin b'acewarsa. TAUDHAT tayi kicin kicin tace a ɗakinta yake. NUFAISAT ɗaure fuska tayi dan tasan kwanan shi d'aya a ɗakinta bai cikace mata na biyun ba yayi tafiyar. Dan haka saita ɗaure fuska batace komai ba. Ganin hakan saiya kalli TAUDHAT ɗin yace.. "Tunda yanxu sabuwar rayuwa zamu fara. Aisaina fara daga kan uwar gida nasan hakan duk bazai zama da matsala bako. Kunyarsa ce tasa TAUDHAT ɗin cewa. "La wasafa nakeyi. Dama ban gama shirya maka kaina ba. Dan haka har azuciyata na amince kayi ko kwana nawa ne aɗakin ƙawata.. Kallan qasan ido NUFAISAT tayi mata Jin tana san sashi nishaɗi da makirci irin yace ita ɗin nan me haƙuri. Sai kawai NUFAISAT ɗin tayi saurin cewa.. "Ai kinsan kece ƙarama dan haka naci girma nadai barshi ya fara yin kwana biyun aɗakinki dan nasan wannan ba wani abu bane.. Saidai zarcewane bazan iya jurewa ba. dan nayi missing abubuwa masu mahimmanci agaresa wanda duk baccin duniya idan zanyi idan banji shi ahannun damana yana yimin su ba bana samun wannan nutsuwar da kowace mace take samu idan ta rufe idanta dan san yin baccin... Harara TAUDHAT ta galla mata batare da ADAMS ya ganta ba. Itako NUFAISAT saita ɗaga mata gira alamar zamu ɗora daga inda muka tsaya... "Toh yanxu dai kowaccenku ta barma ƴar uwarta ni ko. Shikenan ni zan yanke hukunci. Zan fara daga kanki NUFAISAT. Idan nayi kwana biyun na koma ga TAUDHAT ɗin.. Dan haka hira ta ƙare zanje na watsa ruwa... Tashi TAUDHAT tayi cikin jin zafi aranta tace.. "Toh saida safe... Tana barin falan NUFAISAT ta gallama ADAMS hararar wasa tace.. "Ai daka bari ka kwana yau aɗakin TAUDHAT daba abin da zai hanani hukuntaka.. Murmushi ya sakar mata dasan kamota ta zille yace... "Aina gane yau kishi kike ji shiyasa nayi aiki da hankali.. Har takai ƙofa tajuyo da kallanta garesa tace. "Na baka minti biyar kacal kasameni a d'aki dan yau bani ba zuwa ɗakinka... "Yau ranarki ce sai yanda kikayi dani.. Ya faɗi hakan da tashi ya shige room nasa. Itako murmushi tayi da ficcewa daga falan.... Na gaida y'an hannuna🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻 [7/20, 10:05 AM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 22☆ Tana zuwa bed nata wanka tashiga bayan ta fito kayan bacci tasa na d'aukar hankali. Waƴanda suka fidda komai na tsarin halittarta. Tana gama sawa tafeshe jikinta da turare me sanyin qamshi sannan tatsaya tana tunanin takoma garesa ne kodai takwanta a bed nata tunda ta gayamai bata ba zuwa ɗakin nasa yau. Shiko ADAMS yana idar da wankansa bayan yasa kayan bacci sallar godiya ga Allah yayi daya dawo dashi cikin tunaninsa wanda ya sani. Sannan ya qara da rokwan Allahn daya bashi damar sanin wata rayuwa yayi tsawan wannan shekarun daya d'auka kuma a ina yayi. Bayan ya shafa addu'arsa da d'aukinsa yake niyar tashi dan nufar matar tashi wacce take da mallakinsa a wannan dare. Saidai yana juyowa yayi ido huɗu da ita jingine ajikin ƙofarsa da alama ta ɗan jima tana kallansa.. Kallanta yake daga sama har qasa yana me sakar mata murmushi daga bisani ya ware mata hannunsa tazo da gudu tashige jikinsa tana cewa.. "Dana ɗauka zan iya jurewa har sai kazo garenin kamar yanda nace. Saidai ashe nayi qarya in iya dakatar da zumuɗina. Wannan yasa nazo ahankali dan naga me kakeyi wanda yasa ka shanyani da yawa haka.. "Sallar godiya ga Allah na tsaya yi. Sannan tunda kikazo nima bani ba zuwa ɗakin ki. Murmushi tayi da ɗago da kallanta zuwa garesa tace.. "Yau jinake nafi kowace mace samun farin ciki da jin daɗin rayuwa. Mijina! Kai haskene agareni. Yanxu na qara tabbatarwa. Saidai ka bini ahankali dan naga har wani zumuɗi kake..😀 Ahankali ya hade bakinta da nashi yana bata wani kiss me tafiya da numfashin masoyi.. Bai barta haka ba dan aika mata da wasu sakwannni yake da hannuwansa wanda nan take tafara ɗauke wuta. Ta lura so yake ya hana qafafuwanta tsayuwa waje ɗaya. Dan haka saita fara kici kicin kwatar kanta cikin mutuwar jiki.. Nan tacikin kunnanta ya fara raɗa mata magana wajen faɗin.. "Bazan iya binki ahankalin ba my luv... Yaudai sai kinyi min haƙuri. Dan bazan iya controlling kaina ba idan har nakai inda kike jin tsoro.. "Wannan salan ya bambanta da sauran salan da kake amfani dasu adai dai wannan lokacin. Wakema hakan. NUFAISAT ta fad'i hakan cikin wani hali.. Bai dena mata abinda yake ba ya bata amsa da cewa. "TAUDHAT dai bata taɓa rikitani na mance kaina wajen bata wani salo wanda banrigada na baki shi ba. Karki ƙara tuhumata idan kikaga na canja miki dan ako yaushe so nake kwakwalwata tadinga bud'ewa dan na dinga baki salo me tsayawa arai.. "Fatan alkairi gareka masoyin asali. Zanso ka ɗaukeni dan kaga ina neman rasa nutsuwata... ɗaukarta yayi kamar yanda ta buqata bai direta ako ina ba sai'a kan gadansa. Sun samawa kansu nutsuwa da kwanciyar Hankalin da suka ɗauki lokaci me tsaho basu samu damar bawa juna ba.. Washe gari daga yanda suke breakfast kaɗai ya isa ya tabbatar maka suna tare da nishaɗi... Haka dai NUFAISAT badan taso ba tabama TAUDHAT ADAMS ran girkinta. Amman sanda tamai kuka.. Shiko ya shiga lallashinta yana me cewa tafito mishi da wani saban salo. Amsa dai ɗaya ce tabashi itace. Tayi missing d'in shi da yawa ne shiyasata yin kukan dan taso ace tajishi ko irin na wata biyu ɗinnan ne.. Da tsokana yake bata amsa da. To bara yaje gun TAUDHAT ya roqa musu hakan. Murmushi tayi da cewa. Wasafa take mai.. Eh da gaske daya tare da TAUDHAT yaji dad'inta sosai. Saidaifa NUFAISAT daban take agunsa... Kwana biyar da dawowarsa Amminsa ta had'amai walima ta nuna Farin cikinta na bayyanarsa. Y'an uwa da abokan arziqi ba wanda bai halarci wannan walima ba. Koya yaji dad'in tawowarsa sosai da sosai. A kwana na bakwai ne shida Yusuf sukaje can inda ake tsaran Ibrahim suka gano yana cikin mawuyacin hali... Yana ganin Adams ya durqusa da kama qafarsa yana rokwansa kan yayafe masa yayi nadamar abinda ya aikata masa arayuwa Wallahi yayi nadama... Kallansa ADAMS yayi da girgiza kai yace mai. "Sam banyi tunanin kaine mutumin da kake neman rayuwata ba. Kaje na yafe maka. Kuma bazan hanaka yin yanda kakeso da rayuwarka ba. Idan ma ka faɗin min hakan ne dan nasa asakeka kayima kanka. Dan ko baka roqeni ba zansa a sakeka. Sannan zan gaya maka har yanxu ina tare da masu tsaro. Dan naso nabarsu mahaifina yace bai aminta ba. Hakan yasa na ragesu. Yanxu mutum uku ne suke tare dani. Nasan wannan karan bazasu tsorataka ba bare su baka wahala wajen cimma burinka akaina. ADAMS na gama gayamai hakan ya tashi shida Yusuf suka barshi nan idansa na fidda hawaye.. Dan da gaske yayi nadamar abinda yayi masa. Sharrin shed'an ne kawai banda haka bega abinda Adams yayi masa ba arayuwa daya nufesa da wannan baqin halin. Sai yanxu ya gane d'aukaka ta Allah ce.... Su ADAMS na barin wajen aka ce an sallamesa. Da mutuwar jiki Ibrahim d'in ya shege motar mahaifin nasa dan ADAMS ne ya kira mahaifin nasa ya gaya masa yazo ya ɗaukesa ko yasa azo a ɗaukesa dan'an sallamesa yau... Bayan sati d'aya ne Adams ya koma duk wani aikinsa. Inda yaci gaba da ɗora aya aduk inda ya tsaya.. NUFAISAT ji take kamar yanxu tafijin dad'in ADAMS.. Kodan kullum zuciyarta qara sanshi take ne🤔 TAUDHAT har yanxu bata dena shege ayarta da malamin nata ba. Abin nata dai saici gaba yake. Dan lokacin da ADAMS ya b'ace Bama Alhazawanta dama tayi wany'anda tasansu tunkan auranta da ADAMS d'in.. Toh yanxu ma data koma gidan ADAMS d'in ji take aranta badena harka zatayi dasu ba. Saidai zatafi bama malamin nata mahimmanci saboda maganin matan da yake had'a mata. Sannan yace mata karta kuskura tayi ciki da wani idan bashi ba. Dan idan tayi asirinta zai tonu.. Wannan yasa take ankarewa da duk waƴanda take harka. ADAMS da aminin Dadynsa wanda ya tsinceshi sunje wajan daya tsinceshi sunyi binciken duniya mutanan qauyen dake kusa da d'an dajin sunce basusan ADAMS ba. Kuma baiyi rayuwa dasu ba. Atak'aice dai wata d'aya Dadyn Adams dashi Adams d'in suka d'auka suna zagaye kaf qauyukan dake makwaftaka da wannan waje da wannan direban yayar da ADAMS suna bincikesu akan koya tab'a rayuwa awajensu.. Amman sam basuci karo da Wanda Yace yasan ADAMS ba. Haka suka hak'ura suka barma Allah lamarin kan ya basu haske danshi kad'ai yasan meya faru.. ************ Abin ya dami MUSLEEMAT da YAWO ganin basuga dawowar ADAMS awannan ranah ba. Hakan yasa YAWO tafitta yawan nemansa ko wani abu ne yafaru dashi. Kasancewar ya faɗi baya jin daɗin jikinsa. Saidai neman duniyar nan ba inda YAWO bataje ba Amman kome kama da ADAMS bata gani ba. Hankalin YAWO dana MUSLEEMA ya tashi mutuƙa da'aka wayi gari still ba batun ADAMS Nan YAWO tayi gun Malam jauro takwashe komai tagaya masa. Yayi mamaki matuƙa dajin batunta. Hakan yasa liman yayi mai shela akan duk matan rugan suzo. Babu ɓata lokaci nan take kowa ya hallara a fadar malam jauro. Qarema jama'ar tasa kallo yayi tsaf yana nazarinsu sannan ya shiga basu labarin ba'aga ADAMS ba. idan da wanda yagansa yayi magana... Nanfa waje ya hargitse da magana. Kowa faɗin albarkacin bakinsa yake. Masu salati nayi masu gwalma nayi masu jajantawa nayi. Masu gwalma faɗi sukeyi.. Ai dama daga ganin Adams ba mutumin arziqi bane. Daga ganinsa wani abu yazo nema cikin rugar. Qila ya samu abinda yake nema d'in ne yasa shi gudu abinsa dan tsabar mugunta shi ba'asan inda yake ba. Ba'asan cikakken sunansa ba. Kawai dan gwaninta YAWO takama tabashi jikarta ya kunsa mata cikin yara uku aigashi ya tafi ya barta da tagumi.. Masu salati ko mamakinsa suka dinga yi dan basu zaci hakan daga garesa ba. Masu jajantawa ko gani suke kodai wani abu ne ya faru dashi. Ko wani ne yasace shi. Kowa dai da abinda yake fad'a.. Da Malam jauro yaga ba wanda yake da sani akan abinda yake san sani. saiya saka mutanansa kan suje su duba mai ADAMS d'in ko Allah zaisa adace.. Daga nan ya sallami kowa ya kama gabansa Anan yaba YAWO hak'uri kan takwanatar da hankalinta insha Allah za'a gansa. Da damuwa YAWO tadawo gida ta shidama MUSLEEMA yanda akayi.. Hawaye ne yaketa faman sauka akuncin MUSLEEMAN. Tana qaunar ADAMS tana san rayuwa dashi. Bata san wani abu ya rabasu. Haka tana fatan Allah yasa agansa..😭 Har sati biyu ba'aga ADAMS ba.. Wannan yasa duk MUSLEEMA tashiga tashin hankali da damuwa. Kullum kuka take babu dare babu ranah. Tun YAWO na bata baki hardai ta hakura tafitta daga harkarta. Dan ita YAWON ta d'auki zancikan da mutanan rugar suke fad'i nawai ya gudu ne ya barsu..Hakan ne yasa tanemi damuwar tata tarasa. Lamarin MUSLEEMA fa yanxu yafara ba YAWO tsoro. Dan duk ta fige tafita a hayyacinta. Kallo d'aya zaka mata kasan tana D'AUKE da matsananciyar damuwa... Bata da wani furuci saina Ahmad wato Adams YAYANTA. Musamman idan takalli kyawawan yaran data haifa dashi. Nan Zuciyarta take karyewa hawaye yata ambaliya afuskarta.. Yau ALHAMIS da misalin qarfe goma sha d'aya ne Iro ya nufi gidansu MUSLEEMA dan ya jajanta mata. Sannan ya d'an bar mata alama na har yanxu fa yana qaunarta. Aiko yana zuwa ya tarar da ita a tsakar gidan nasu. Takama Yaranta tsam ta rungumesu sai baccinsu suke. Ita ko sai zubar hawaye take. YAWO na gefe tana kwad'an latas.. Hankalin Iro yayi matuqar tashi da ganin MUSLEEMA. Baiyi tunanin zata saka damuwar ADAMS aranta haka ba. Ta fige ta lalace kamar ba MUSLEEMAN daya sani ba. Nan take zuciyarsa takarye. Tsoro ya kama zuciyarsa. Dan ya tabbatar idan taqara d'aukar lokaci ahakan ba makawa saidai azo a d'auki gawarta ta mutu.. Bakinsa na rawa ya gaisar da YAWO ta amsa da murmushi tana rayawa aranta dama shi MUSLEEMAN ta aura da yanxu duk wiya bazasu Shiga wannan tashin hankalin ba. Gaskiya tausayin MUSLEEMA ya kama Iro. Wannan shine karo na farko daya tab'a aikata wani abu yaji bai kyauta ba arayuwarsa. Dan haka Ahankali ya qara tsaida idansa akanta yace.. "Nayi miki lefi MUSLEEMA. Najefa rayuwarki cikin wani hali. Na cutar dake saidai kafin na gaya miki ina san kiyafe min... "Babu wani lefi da wani d'an Adam zaiyimin wanda bazan iya yafe masa ba. Iro koma me kamin na yafe maka. Dan ina ji ajikina nikam rayuwata tazo qarshe. Saboda nayi rashin abinda na kwallafa araina akansa. MUSLEEMA ta gayamai hakan da damuwa. Jan numfashi yayi cikin tausayawa yace.. "Nine silar jefaki cikin wannan yanayi. Nine na b'atar miki da mijinki uban y'ay'anki saboda na rikesa azuciyata tun lokacin dana bar mishi ke. Barin mishi ke danayi bana Allah bane awannan lokacin. Nan Iro ya kwashe komai na yanda yayima ADAMS ya gaya ma MUSLEEMA da YAWO.. Hankalin su yayi matuqar tashi sosai. Nan take YAWO tafashe da kuka wiwi. Dama ita MUSLEEMA tunda yafara koro mata bayanin hawayenta yaqi tsayawa.. Da sanyin jiki iro ya qarasa durqusawarsa ga MUSLEEMA yaci gaba da cewa.. Wannan shine abin daya faru. Kuma shine abu na farko dana aikata arayuwata yanxu zuwa gareki naji ban kyauta ba. Dan Allah MUSLEEMA kiyafemin. Rintse idanta MUSLEEMA tayi tace dashi. "Ka aikatamin abinda bazan iya yafe maka shi cikin sauri ba. Kajefa rayuwata cikin wani hali wanda bansan yazanyi ba. Ka tarwatsa min Farin ciki na. Ka b'ata tunanina. Yanxu har yaushe kake tunanin zanga mijina uban Y'ay'ana.. Lokacin daka tashi aikata Wannan aika aikan naka meyasa bakayi tunanin yaran nan nawa ba. Iro kacuceni karabani da FARIN CIKIN RUHINA. Ka rabani da LEEKITAN dake gyara ZUCHIYATA. Saboda dashi ne nake samun nutsuwar ZUCHIYAR. Yanxu ZUCHIYAR ta hargitse. Ta b'aci. Ta zaga zuwaga tunanina. Ta b'atamin tunanin. Kasan yanda nake ji araina kuwa.. Ji nake ZUCIYATA nayimin zafi. Tana yimin wani suya. Tana yimin wani raɗaɗi. Ina tabbatar maka bazata dena yimin hakan ba har saina gamu da Yaya Ahmad. Ya gyaramin tunani..😭 "Zaki gamu dashi MUSLEEMA. Dan garin KANO na tura shi. Kuma na gaya miki Sunansa LEEKITAN ZUCHIYA. Dan haka naji waƴannan matan sun faɗi... Iro ya katseta da faɗin hakan hawaye na zubar masa. Jan numfashi tayi dace masa.. "Kaje nayafe maka. Tunda kabani sheda d'aya na sunansa. Badai kace sunansa LEEKITAN ZUCHIYA ba. Yace "eh haka naji matan sunce.. "Kaje kawai.. Dan Wallahi d'aukewar numfashi ce kawai zata hanani zuwa garin KANO neman mijina.. MUSLEEMA ta faɗi hakan da goge hawayenta.. Dan sanyin jiki Iro ya tashi yabar gidan.. Yana zuwa gidansu ya gayama Malam jauro mahaifinsa shinefa silar b'acewar ADAMS. Ya kwashe komai ya gaya masa. Ran malam jauro yayi matuqar b'aci... Dan har yaso yayima Iro d'in baki liman ya Shiga tsakani... Dama shi malam jauro sam zuciyarsa bata yardar mishi ADAMS guduwa yayi ba.. Gashi ko gaskiya ta bayyana.. Nan ya taka qafarsa yaje ya tarar da YAWO da MUSLEEMAN ayanda Iro ya barsu. Sai subar hawaye suke. Yaba YAWO hakuri sosai har sanda taji kunyarsa. Ganin babba dashi yana qoqarin durqusa mata. Haka dai suka bar gidan shida liman zuciyarsu babu daɗi. Wannan dare MUSLEEMA tattara kayanta tahauyi anufinta gobe idan Allah yakaisu zata cale zuwa garin na kano dan neman mijin nata... Kallanta YAWO take kawai dan tausayinta ne ya kama zuciyarta. Washe gari YAWO tasa aka kira mata Malam jauro ta gayamai zasu garin kano neman Ahmad. Nan yahau cemata tayi hakuri zaisa mutane suje su bincika mata shi. Tace bazai yuhuba. Tana san farin cikin jikarta. Dan ita kad'ai tarage mata arayuwa dan haka ita yanxu so take yasiye shanunsu sutafi da kuɗinsu danzai temaka musu sosai wajen nemansa. Saboda talura ma tunda suka rasa Ahmed d'in shanun sai mutuwa suke..🙂 Nan Yace mata shi bashi da kud'in dazai iya siye shanunsu kaf Dake Hankalin yawo ya tashi ita buqatarta subar rugar dan kwata kwata tunda taga MUSLEEMA tayi yimma ita kano take san zuwa. Sai taji duk rugar tafitan mata arai. Dan haka cemai tayi yabata muliyan d'aya kawai ita tabar mishi shanun. Murmushi Malam jauro yayi dan ganin hankalinta baya jikinta. Tabbas yasan shununta sunfi karfin kud'in data fad'a. Dan haka kallanta yayi cikin tausayawa Yace.. Zai bata muliyan d'ayan Amman badan iya kud'inta kenan ba.. Dan haka tabashi kwana uku ya had'a mata kan kud'in Haka YAWO taba MUSLEEMA hak'uri sujirasa zuwa nan da kwana ukun. Haka ko akayi dan malam jauro ya had'a mata kud'in. Yace idan tadawo saiya ware nasa yabar mata sauran shanun dan tasan shanunta sunfi qarfin kud'innan daya bata.. Nan YAWO tamai godiya shi kuma ya musu fatan alkairi akan Allah ya had'asu Ahmad wato ADAMS cikin sauri idan kuma sun rasasa su dawo karsu zauna ako ina.. Toh YAWO tace mai Dake da yamma ya kawo musu kud'in hakan ne yasa suka bari sai gobe sabar rugar Nan YAWO tama makwaftanta sallama da iyayan Hasiya mahaifan uwar MUSLEEMA Sannan ta qara had'a kayan su a gana masgo tabama makwaftan nata sadakar kayan aikinta. Washe gari ko dake Dr Usman yazo ajiyan anan yaji komai daya faru. Shine ya fitar dasu daga rugar zuwa kan titi da motarsa. Haka yabarsu zuciyarsa da jin takaicin yanda bai Adana hotan ADAMS ba lokacin da yake tare dasu. Daya d'auka ya Adana da yanzu yayi musu amfani dan baza susha wahala wajen nemansa ba. Toh koma dai miye yana musu fatan alkairi. *Saidai me😳* Bayan sun samu motar dazata kaisu garin na kano. Kafin su fitta daga garin gwamben Y'an fashi suka taresu. Anan suka samu nasarar amshe mak'udan kud'in nan da malam jauro yabasu. Sauqinta d'aya dama YAWO taware dubu d'ari dansu fara amfani da ita. To Allah cikin ikwansa da wannan d'arin suka tsira. Sauran dubu d'ari taranko y'an fashin sun amshe. Kuma sun sami nasarar amshe kud'in ne sakamakwan harbe wani da sukayi a qafa dayace bashi da kud'i. Toh Hankalin YAWO ya tashi shiyasa tabasu dubu d'ari taran tunanin d'arin data warene tabasu. Sanda suka samo nasarar tafiya lafiya sannan tagane me yawan tabasu. Sam YAWO bata wani damu ba dan tafi buqatar rayuwarsu akan kud'in... Suna shiguwa garin na kano sai suka fara raba ido ta'ina zasu fara neman ADAMS wanda suka laqabawa Ahmad. Tun a tasha MUSLEEMA tafara yima y'an tashan kwatancen ADAMS.. Wani ya kalleta cikin raini Yace... "Ke kin ishemu da kwatance. Idan zaki fad'a mana sunansa kifad'a kozamu iya ganewa.. Cikin sauri YAWO tace "Sunansa Ahmad.. MUSLEEMA ta girgiza mata kai da rungume Y'ay'anta tace. "Yawo wannan sunan da kuka rad'a masa ne. Kuma kinji abinda Dr Usman yake cewa. Zai iya yuhuwa dukan da Iro yayi masa ya iya sawa tunaninsa na ainihi ya dawo. Kuma idan hakan tafaru ba shakka nufar inda ya fito zaiyi. Bazai waniyi tunaninmu ba. Idanko haka ne dole muyi amfani da sunan da Iro ya gaya mana wanda yace matan nan sun fad'i wato LEEKITAN ZUCHIYA. MUSLEEMA takai qarshen zancenta da kallan mutumin tacigaba da cewa. Sunansa LEEKITAN ZUCHIYA dan Allah ka temaka min mijina ne shi. Yana nan wani fari kyakkyawa haka me yawan murmushi dasan tsafta... Sheqe mata da dariya mutumin yayi tare da way'anda suke wajen. Nan ran YAWO ya b'aci ta kallesu da takaici tace.. "Haba yaran nan daga tambayarku sai kuhau yima mutane dariya. "Mutumin ya kalle da cewa. "Kema tsohuwa da girmanki zaki tsaya biyema shirman jikarki. Fisabidillahi a'ina zamusan wani waishi LEEKITAN ZUCHIYA. Kuma gashi wai kyakkyawa me san tsafta da murmushi. Yanxu idan ke mukama wannan tambayar fisabidillahi zaki bamu amsa. "Me zaisa bazan baku amsa ba yaran nan. Idan nasan shi gaya muku zanyi idanko ban sanshi ba banga dalilin da zaisa na tsaya yi muku dariya ba. Dariyar suka qara bushe musu da ita. Kana ya bata amsa da.. "Tomu bamu san wani waishi LEEKITAN ZUCHIYA ba. Kuje can gaba wala'Allah zakuci karo da Wanda ya sanshi.. Hawaye ne ya zuboma MUSLEEMA. Nan YAWO tatab'ata tana meyi mata nuni dasu qara gaba.. Afuwan masoyana LEEKITAN ZUCHIYA naku ne.. 😍kuci gaba da bibiyata akansa [7/23, 10:30 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 23☆ Haka suka qara gaba inda suka had'u da wani masifaffan tsoho ya kalli Yawo kallan wani iri haka yace. "LEEKITAN ZUCHIYA kowa kuke cewa. Yanxu ni a'ina zan sanshi. Da Allah ku qara can gaba qila kwa gansa. Haka YAWO da MUSLEEMA suka dinga yawo suna neman ADAMS da bashi suna LEEKITAN ZUCHIYA amma basuci karo da wanda yace ya sanshi ba. Duk sunsha ranah. Musamman kunsan garin kano da zafin ranah. Haka suka zauna bakin shagwan wani mutum me saida kayan provision dan ganin akwai wani me soya indomie da kwai. Haka suka bashi kud'i ya had'a musu yanda zai ishesu. Bayan sun gamaci ne suka fara tunanin inda zasuyi sallah. Bama wannan ba a'ina zasu samu wajen kwana. Wani saurayi ne yazo wuccewa Yawo takirasa take tambayarsa dan Allah a'ina zasu samu d'akin haya na sati biyu. Su baqi ne suna neman wajen kwana ne. Kallan tsaf saurayin yayi musu kana yace suna da kud'i ne. Nan YAWO tace mishi eh suna da shi. Ai dajin hakan saurayin yace suzo zai kaisu wajen Hajjiya ladi tana da d'akuna acikin gidanta sannan tana bada haya yana tabbatar musu sun sami gidan haya me kyau dan ko'ina a gidan me kyau ne sosai Haka YAWO da MUSLEEMA da yaranta sukabi bayan mutumin nan yakaisu gidan Hajjiya ladi dake unguwar bacirawa. Hajjiya ladi shahararriyar shed'aniya ce. Kaf way'anda suke haya a gidanta gogaggun y'an iska ne karuwai. Shi dai wannan mutumin shiyake kawoma Hajjiya ladi mutane musamman way'anda idan ya lura basusan kan gari ba. To idan ya kai mata su yakan dawo da daddare yayima mutunan dai daya kawo mata sane wato sata. Sam bashi da wani aiki sai hakan. Dan haka da suka isa gidan Hajjiya ladi kallansu tayi da kyau taga dai basu da fuskar mugayan mutane sai tace subata dubu talatin.. Ai nan YAWO ta zaro ido tace. "Haba keko baiwar Allah kiji tausayinmu mu baki dubu goma saboda muma bada hakan mukazo ba. Munzo da kud'i da yawa saidai munci karo da y'an fashi sun yashe mana me yawan. Nan YAWO takwashe komai tagayama Hajjiya ladi. Azahirin Gaskiya Hajjiya ladi ta tausayama MUSLEEMA dan ganinta qaramar yarinya. Saidai taji haushin YAWO over dan inda itace bazata tab'a Aurama ADAMS jikarta ba. Saboda bata san waye shi ba. Bata san daga inda ya fito ba. Haka kawai dan gwaninta saita kama ta bashi jikarta dan toshewar basira.. "Toh ai shikenan. Allah ya rufa asiri. Kidai bada dubu Ishirin kiyi wata d'aya. Idan wata d'aya yayi saiku fitta kubani d'akina idan kuma zaku qara biya saiku qara zama har Allah yasa kusami shi LEEKITAN ZUCHIYAR naku.. Hajjiya Ladi tafad'i hakan da wani tab'e baki. Godiya YAWO tamata ta fito da kud'in ta qirga tabata. Sannan tamaida kud'in cikin y'ar lalitarta cikin wani d'an qaramin buhu duk wannan mutumin yana kallanta. Haka Hajjiya ladi tayi musu jagora zuwa wani d'aki haka. Eh dai bashi da wani matsala. Dan akwai ledar d'aki cikinsa da wata yololuwar katifa da fillo.. Haka MUSLEEMA ta share d'akin tas tasaka musu kayansu a gefe sukayi sallah kana suka fara tunanin me zasuci na dare. Anan kusa da gidan Hajjiya ladi akwai wata mata Yalwa me saida abinci safe da rana da dare tana da ma'aikata da dama. Matar ta'iya abinci sosai shiyasa mazaje masu aji daji da kansu da mata masu aji suke zuwa wajenta cin abincin nata. To gurinta Hajjiya ladi ta nunama su MUSLEEMA da suka tambayeta inda zasu sami abinci. Kallan farko da Yalwa tama MUSLEEMA taji aranta dama tazama meyi mata aiki. Dan taga yarinyar tana da diri sosai zata qara ja mata Hankalin maza kwastamomi. Gashi ta mallaki duk wani abu da mazan suke so agun mace. Dan haka da fara'a ta kalli MUSLEEMA tace.. "Daga ina kike yarinya. Nuna mata gidan Hajjiya ladi MUSLEEMA tayi tace.. "Daga nan gidan nake.. "Ikwan Allah. Meya kawoku gidan. Dake MUSLEEMA ahannu take burinta mutane su dinga sakewa da ita dan tadinga fad'in musu buqatarta na neman ADAMS ko Allah zaisa wani yace mata yasanshi. Nan tabata labarin abinda ya kawosu gidan. Sosai Yalwa me abinci ta tausayama MUSLEEMA tace. "Aiko nayi mamaki danaji kince daga gidan Hajjiya Ladi kike. Ganin da nayi kamar kina da nutsuwa. "A nazarce MUSLEEMA tace.. "Meyasa ki fad'in hakan. "Eh gani nayi gidan karuwai ne. Waro ido waje 😳 MUSLEEMA tayi da cewa. "Gidan karuwai. Toh aimu ba karuwar bane. Meyasa wannan mutumin ya kawomu gidan. "Nima mamakin danaji kenan. Karfa wani abu ya dameki dan zaman naku ai na wani d'an lokaci ne. Murmushin yaqe MUSLEEMA tayi mata. Da miqa mata kud'i ta had'a musu abincin da MUSLEEMA tace mata tanaso.. Aiko MUSLEEMA na dawowa ta gayama YAWO agidan karuwai suke. Ran YAWO baiyi mata dad'i ba. Amma data tuna zaman nasu na d'an wani lokaci ne sai Kawai ta share. Kula dai da yaran MUSLEEMA zatayi sosai dankarsu b'ata musu tarbiya. Sosai yawo tayaba abincin Yalwa Cikin dare da misalin qarfe goma sha biyu na dare wannan mutumin daya kawo su YAWO ya lallab'a ya tura d'akin dasu yawon suke yashige. Dake sun kashe kwan wuta da d'an hasken wayarsa ya dinga lalubar inda zaiga inda yawo tasa sauran kud'in nan. Aiko yaci sa'a. 😳 nan cikin kayan su Khalit yagani. Ahankali kamar yanda yake tafiyar da motsin nasa ya d'auke kud'in gabaki d'aya. Har zai fitta saiya dawo ya sakama musu d'ari biyar a inda dai ya d'auki kud'in. Kana ya ficce daga d'akin ahankali cikin jin dad'in yanda basu sakama ƙofar sakata ba kamar yanda yayi zato. Washe gari da safe YAWO ta tambayi Hajjiya ladi kan inda zasu samu ruwan wanka. Hajjiya ladi ta cokaro d'an kwali gaba tace da ita Hita zaku sayo da d'an bokati da soso dakomai na buqata. Harda furko da gawayi kudinga yin abinda kukeso. Kamar yanda kukaga kowa nayi. Dake ku baqi ne kikawo kud'in naba almajirin gidan nan yaje ya suyo muku Toh YAWO tace mata da dawowa d'akinsu. Anan tahau neman kud'in nasu tanema sama ko qasa babu ko sisi sai d'ari biyar. Hankalin YAWO dana MUSLEEMA ya tashi nan suka fara hargitsa kayansu waiko zasu gani. Amma babu kud'in nan nasu ba dalilinsa. Hawaye ya zuboma MUSLEEMA ta d'ora hannu aka tace "YAWO mun shiga uku. Yanxu waye zai bamu kud'i. Can y'an fashi sun amshe manyan kud'ad'an. Nan kuma gashi an yashe mana Sauran. Sam YAWO bata iya ba MUSLEEMA amsa ba. Dan hankalinta ya tashi matuqa. Da muguwar damuwa taje tana gayama Hajjiya Ladi sufa basuga kud'insu ba. Dariya Hajjiya Ladi tasheqe musu dashi tace. "Ban gane bakuga kud'inku ba. Kun bar ƙofar taku a bud'e ne. "Eh abud'e muka barta saboda nayi nayi na kulle na kasa.. YAWO tabata amsa da damuwa. Qara dariya Hajjiya Ladi tayi tace.. "Shege d'an malam. Ai gaya muku ne banyi ba na sha'afa. Wannan mutumin daya kawoku jiya ai tantagaryar b'arawo ne. Idan ya kawamin mutane irinku way'anda basu san gari ba. Zuwa yake daga baya yayi musu sane wato sata. Dan haka sai kuyi hakuri. YAWO ta waro ido tace. "Muyi hakuri muci me kenan. Yanxu tunda kin sanshi nezai hana ki had'amu dashi yabamu kud'inmu Kallan raini Hajjiya ladi tayi mata da cewa. "Tabd'ijan. Ai sai dai kuyi hakuri dan Wallahi tunda d'an malam ya sace muku kud'in ban yatafi kenan har abada. Toni yanzu ma a ina zanga d'an malam. Dama idan ya aikata irin wannan nemansa ake a rasa sai ya daidaici mutanan sun tafi yake dawowa yaban labarin yanda yayi satar. Kinga tsohuwa kibar batun d'an malam yanxu kikama abinda zai fishsheku "Innalillahi-wa'inna'ilaihirraji'un. Shine abinda YAWO ta fad'i. MUSLEEMA ko sai hawaye take tana hararo mezai faru dasu gaba yanzu tunda ba kud'i. Da d'ari biyar d'in MUSLEEMA taje tasiyo musu hitar d'ari da hamsin da buredin d'ari biyu. Da Lipton na ishirin da sikarin arba'in dake da sauran canji ahannunta na jiya data siya musu abinci saita had'a tasiya musu soso da sabulu harda man shafawa tadawo gidan lokacin akwai wuta. Hajjiya Ladin ce dai tanuna musu yanda ake amfani da hitar har tabasu aran bokatin ta da kofuna. Kafin almajirin data aika ya kawo musu nasun. Dan MUSLEEMA tabata sauran kud'in dan taba almajirin yasai musu bukati d'aya da kofuna uku harda lokali d'aya da buta. Shine taba almajirin yasiyo musu. Haka YAWO tayi wanka MUSLEEMA ma tayi tayima yaranta. Sannan suka sha ruwan Lipton d'in da buredin. Suna gama sha ko MUSLEEMA tasaka yaranta agaba YAWO na binsu dama Hajjiya ladi ta had'asu da wani almajiri dan haka nan suka Shiga gari neman ADAMS. Duk inda sukaje sai ammusu dariya. Wasu su tausaya musu Wasu kuma suga ganganci irin na Yawo data ba ADAMS MUSLEEMA bayan tasan bata san kowa nasa ba bata san waye shi ba. Haka suka dawo gidan lilis da gajiya. Gajin yunwa gashi basu da ko sisi. Abin gwanin ban tausayi. Suna gani Hajjiya Ladi tasaka abincinta agaba ta zauna a tsakar gidan tacinye ko kwad'an batayi musu tayi ba. Dan tasan idan tayi musu tayin wallahi ci zasuyi dan tasan sarai yunwa sukeji. Khalil ya kalli MUSLEEMA yace. "Mama yunwa nake ji. Khalit ma yace "nima yunwa nakeji mama. Hawaye ya zuboma MUSLEEMA tace.. "Kuyi hakuri Yanxu zan nemo muku abinci. YAWO ta share hawayan da itama ya zubo mata tace. "Gwara musan yanda zamuyi mu basu abinci MUSLEEMA. Tunkan wannan acicin tatashi kinga dai yanda tayi baccin da kukan yunwar. "To yanzu YAWO ya zamuyi. "Muje wajen me abincin nan na roketa tabamu bashi mubasu daga baya masan yanda zamuyi. Haka ko suka nufi gun Yalwa me saida abinci suka gaya mata buqatarsu har suka qara mata da cewa sace musu kud'insu wani yayi. Yalwa tayi murmushi tace. "Hmm yanxu idan na baku ya zakuyi anjima. Kawai dai ga shawara idan kunga zaku iya. "YAWO tace idan tayi mezai hanamu iyawa "Yauwa tsohuwa temakwanku zanyi. Kinga ke saiki dinga min wanke wanke da shara. Ke kuma MUSLEEMA saiki dinga zuwa kina bama mazage abinci. Amma cikin nutsuwa yanda zakina jan ra'ayinsu kamar yanda akeyi. YAWO tace.. "Yanxu idan muka yarda da hakan yaushe zamu samu lokacin dubawa shi LEEKITAN ZUCHIYAN. Yalwa taja numfashi tace. "Sai MUSLEEMA tadinga zuwa da safe nemansan har zuwa ranah. Daga lokacin da yamma tayi saitazo tajimin da kwastomumina har zuwa sha d'aya na dare. Idan kun yarda to zan dinga baku abinci safe da ranah da dare sannan zan dinga baku naira d'ari. ammafa ba batun biyanku albashi kamar yanda nake bama y'an aikina duk sati.. Danku nayi muku babban temako ne.. Saidai idan zaman namu ya d'ore nan da wata uku zan iya baku kud'in da zaku koma garin na gwambe Da sauri sukace mata sun yarda. Aiko nan tacika musu abinci suka dawo gidan sukaba Khalil da Khalit sukaci Suma sukaci sannan suka ragema Rahma kan tatashi.. **** Sai rayuwar tasu ta kansance haka. Kullum idan sun tashi wanka sukeyi YAWO tana tasa Khalit da Khalil zuwa gun Yalwa me abinci su hau yimata aiki kamar sauran ma'aikatan nata. MUSLEEMA Kuma tashiga gari neman (ADAMS) LEEKITAN ZUCHIYA.. Safe da ranah MUSLEEMA neman ADAMS tasaka agaba. Kullum cikin kuka take musamman idan tatambayi wasu mutanan suka sakata a gaba da dariya. Duk sallar da zatayi addu'a take tana kuka kan Allah ya had'ata da LEEKITAN ZUCHIYA. Ayanxu dai satinsu d'aya kenan Yau tun asuba kan MUSLEEMA yake mata ciwo. Lokaci lokaci kuma takanji qirjinta nayi mata zafi musamman wajen da ZUCIYA take amsar sak'o. Haka daddafa tashirya qarfe tara ta fitta kamar yanda tasaba ita da almajirin dake mata rakiyar dan neman LEEKITAN ZUCHIYA. Sunyi tambayoyin da dama bataci karo da wanda yace ya gane kwatancen nata ba. Sai kawai tazauna kan wani dakali tad'ora hannu aka tarushe da kuka. Fad'i take a bayyane. "Meyasa kamin haka Abban Khalit. Meyasa kamin haka baban Khalil. Meyasa kamin haka YAYANA. Meyasa kamin haka LEEKITAN ZUCHIYA. Kamanta cewar ka b'ata tunanina. Kamanta cewa kadasamin qaunarka azuciyata. Kamanta cewa bana ji bani gani akan sanka da qaunarka. Meyasa kake wahalar da ruhina. Meyasa kake wahalar da tunanina. Meyasa kake wahalar da zuciyata. Harshena. Gangar jikina. Kafafuna. Ya dace kaji aranka kayi rayuwa dani. Ya dace kaji aranka ina nemanka. Ya dace kaji aranka kana da yara dani. Ya dace kaji aranka akwai wata meyi maka wani SO wanda yafi qarfin akirashi da MASIFAR SO. Haka tadinga sambatu tana kuka wiwi mutane na kallanta wasu suji tausayinta su tsaya tambayarta idan tayi musu shuru su qara gaba. Wasunsu ko koda sunji tausayin nata basa mata magana suke wuccewa. Wani tsoho ne ya nace saiyaji abinda yasata kuka haka. Nan tagaya masa. Ya tausaya mata nan ya bata shawara tunda sunan ya had'a dangantaka da likita mezaisa bazataje asibitoci taga ko zata ganshi acan ba. Aiko taji dad'in shawarar daya bata. Haka suka dawo gida tagayama YAWO. Washe gari yawo tabata d'ari biyar irin d'ari d'arin da Yalwa take basu. Haka suka tari kekenafaf zuwa asibitin Aminu kano. Taci sa'a wata doctor salma taji tausayinta dataji labarinta. Dan haka nan tasadata da hotunan doctors Amman bataga ko me kama da idan Adams ba. Tunkan tabar asibitin tafara kuka. Washe gari haka Yalwa ta ranta musu dari biyar ta nufi asibitin murtala. Nan kam tad'an sha wahala kafin wani Dr Ahmad ya fahimceta. Shima ya nuna mata manyan doctors nanma ko me irin qeyar Adams MUSLEEMA bata gani ba. Still haka tabaro asibitin da kuka. Haka akwanakin nan tadinga ziyartar asibitoci amma shuru kake ji. Haka ta tabari tadena bin asibitocin badan ta hak'ura ba. Saidan babu kud'in zuwa gunsu. Dan Yalwa tace bazata qara ara musu ko sisi ba. Tunda kud'inta yakai duba biyu da d'ari biyar akansu. Gashi MUSLEEMAN ba dawowa take da wuri ba. Sai kusan bayan isha. Dan haka idan zata tsaya tayi mata aiki tatsaya tayi mata aiki. Sannan tasan inda zataje ta biyata kud'inta. Yawo ce tace tayi hak'uri zata dinga dawowa akan lokaci batun kud'i kuma tadinga cirewa aduk rana cikin d'arin da take basu. Wannan yasa Hankalin Yalwa kwanciya.. Toh MUSLEEMA tadena dadewa wajen yawan neman ADAMS saboda dukar Yalwa. Saidai yanxu tafara fuskantar wata matsala kamar haka wajen aikin nata. Idan tazo kawowa Mazajen abinci saisuta kallan qirjinta da qugunta. Suna janta da hira. Sam bata san hakan b'cos tana ganin ita matar aure ce. Duk da cewar hijab take sawa amman hakan baya hanasu qin kallan way'annan abubuwan biyun ba. Gashi duk da saida dare take dawowa hakan baya hana mazan dake suwa wajen karuwan gidan Hajjiya Ladin binta da mayataccen kallo Itadai jifansu take da addu'a dan tasan itace makaminta Dan akwai ranar da wani ya tab'a fad'o musu d'akin nasu yana me san fad'ama MUSLEEMAN haka dai Allah ya kare Saidai daga ranar suka koyi iya rufe d'akin nasu.. ________ Yau tun safe Hajjiya Ladi tabasu notis kan kud'insu ya qare wata d'ayan da sukayi da ita ya qare dan haka su tashi mata daga d'aki zatasa wata budurwa aciki. Dan gashi tabata kud'inta cif cif dan haka su tattara inasu inasu su qara gaba Kuka MUSLEEMA tasama Hajjiya Ladi tace.. "Dan Allah ki temaka mana kiqara mana lokaci zamu biyaki kud'inki. Tace.. "Bazai yuhu ina ganin kud'i ahannu nabar budurwar nan ta tafi da kud'inta bayan ku babani zakuyi yanxu ba Wallahi Saidai kuyi hakuri inda ace d'akunan basu cika ba dana qara muku lokacin. Ba irin magiyar dasu MUSLEEMA basuma Hajjiya ladi ba kan ta barsu tace basu isa ba. Haka suka d'an kwashe kayansu sukaje gun Yalwa me saidai abinci. Anan Yalwa tace idan sunga zaku iya kwana cikin y'an aikin da suke mata aikatau a shagwan abincin nata to ga waje nan su ajiye kayansu. Idanko sunga bazasu iya ba. To ita bata da wani waje da zata sasu. Dan gidanta d'aki d'aya ne tayimai rufi daga shi sai bayan gida ai gashi nan dai sunga gidan ajikin shagwan nata. Shuru sukayi mata dan a y'an aikin nata harda maza almajirai. Kuma duk balagaggu ne. Amma da sukaga gefan matan daban na mazan daban dansu mazan a barandar waje suke kwana. Matan ne aciki Suma irin yaran nan ne way'anda iyayansu suke koransu kai da duhun jahilci ko yaran da basu da yanda zasuyi. Haka dai YAWO tacema MUSLEEMA su yarda. Haka suka yarda tunda ba yanda zasuyi. Sunyi kwana d'aya lafiya lau dai. Ayau na biyun ne MUSLEEMA tazo kawoma wani alhaji abinci kamar yanda yasaba zuwa kullum ci qarfe tara na dare.. Yana d'aya daga cikin mutanan da suke bin qirjinta da kallo. Hakan ne yasa ta tsane shi. Harta juya zata tafi ganin ta shirya mishi duk abinda yake buqata dancin. Sai ya kirata yana tambayarta a ina take kwana. Kallansa tayi dakyau tana nazarinsa can tace mai miye had'insa da inda taje kwana Murmushi yayi mata idansa qir akan qirjinta yake bata da cewa. Kawai yana san sani ne. Idan bazata gaya masa ba yaje gun Yalwa tagayamai. Sanda ta galla masa wata muguwar harara kana tace mai ashagwan taje kwana. Yaji dad'in hakan sosai dan b'aro b'aro taga ya saki dariya yace mata zai dawo wajenta anjima. Bata gane me yake nufi dazai dawo d'inba haka tashige abinta ta barsa. YAWO jikinta kwana biyu babu lafiya komai daurewa kawai takeyi saboda aikin datake bana wasa bane Hakan yasa yau qarfe goma:pm ta kwanta. MUSLEEMA ko sai sha d'aya da rabi tasamu kanta. Qarfe d'aya na dare kowa yayi bacci cikinsu. Almajiran suna tacan waje suna baccinsu Ammanfa ahakan gadi sukema Yalwa na kaya. Su Yawo ko suna tacan ciki. Amma dan tabar shed'ananci haka shegen mutumin nan ya ratsa kowa yaje har inda MUSLEEMA take yahau shafata. Dake baccin ya fara cin qarfinta sam bata fara jin wani abu ajikinta ba. Motsinsa ne ya Rahma tashi dake tana kusa da MUSLEEMAN ganin mutumin saita hau jan rigarsa tana mama kitashi ga wani yana tab'aki Sam MUSLEEMA bataji ba. Sanda shegen yayi nasarar damke na fulaninta ya fara cirosu tare da daneta iyakar qarfinsa sannan MUSLEEMA tafarka da wata shegiyar qara. Ai sanda dukkansu suka farka. Ganin abinda yake faruwa sai Matan sukaja tsaki kowaccensu takoma baccinta dan Wannan su aganinsu ba bakwan lamari bane. Mazan dake wajen ko tunaninsu d'aya daga cikinsu ne ya afkawa MUSLEEMAN kamar yanda idan wani cikinsu yaji lalurarsa yake afkawa duk wacce yaso amatan kuma komin ihunki saiya biya buqatarsa sannan zai barki. Toh tunaninsu ko hakan ne. Duk da kowa acikinsu idansa akanta yake. Ganin Yanxu tafara bunqarowa. YAWO taya MUSLEEMA ihun tayi. Amma sai taga kowa cikinsu ya sharesu. Nan tanufi inda kayan aikin Yalwa suke ta rarumo muciya aiko tasauke masa a baya. Lokacin bakinsa nakan san Shiga kan na fulaninta. Aiko jin hakan afurgice ya saketa YAWO ta qara shinfid'a mai a kafad'a ainan ya taso da zafin nama ya mangare YAWON tazube qasa sannan ya taka hannunta da qarfin tsiya ya fuzze muciyar. Sannan ya qara nufar MUSLEEMA ganga ganga wacce tayi nasarar gyara rigarta. Aiko nan ya kwasheta abinka da ririya. Nan tazube qasa tim. yako bita ruf ya rufeta kamar matarsa yana kici kicin lalle saiya cinmma burinsa akanta. Kuka wiwi MUSLEEMA take yi tana yimai ihu da yakushinsa da cizansa amma ina burinsa dai yacimma burinsa. Daqer YAWO ta qara tashi kasan cewar ba qaramar mangare yayi mata ba. Haka tadaure taje ta qara rarumo farantin tangaras ta rutsa masa aka.... Wannan karan yayi qarya wajen cigaba da aiwatar da kudirin nasa Dan haka ba shiri ya tashi ganin yanda kansa yake fitar da jini. Sanda ya qara mangare YAWO kana ya ficce daga shagwan.. Sai a lokacin almajiran suka gane ba d'aya daga cikinsu bane. Matan ko mita suka dingama MUSLEEMA wai tashiga hakk'insu ta hanasu bacci miye danta barshi yayi amfani da ita. Ai wannan ba wani abu bane. Amma dan tsabar mugunta ta wani hanasu bacci bayan ba lokaci suke samu nayin baccin ba. Dan wasu acikinsu da qarfe hud'u na asuba suke tashi d'ora abincin safe. Tomiye danta barsa yayi abin aina d'an wani lokaci ne. Ba kunyar YAWO ba jin tsoran Allah haka suka dingama MUSLEEMA Wannan masifar.. MUSLEEMA ko tattara kan y'ay'anta tayi ta rungumesu tana kuka suna tayata abin tausayi. Itama Yawon hawaye takeyi Wannan dare dai basu iya rintsawa ba. Washe gari da kuka MUSLEEMA tace da YAWO.. "Dan Allah yawo mubar wajen nan. Dan suna shirin ketamin hakk'in aureta. Sun kulla aniyar cin mutuncin aurena. Zasu wulaqanta min igiyata. Wallahi YAWO ina san mijina ina san ya ganni batare da wani yayi masa illa cikin Soyayyarsa ba. Kimin rai ki amincemin mubar wajen. "Toya zanyi MUSLEEMA. Ai barin wajen nan ya zamam mana dole dan zan iya jure wahala amma bazan iya jure aci mutuncinki ba. Jin hakan yasa hankalin MUSLEEMA kwanciya. Yalwa na fitowa qarfe takwas na safen wata qawarta Hajjiya batula tazo gareta karb'ar kud'inta da wata mata takawo mata jiya danta ajiye mata. Nan Hajjiya Batula tayi ido hud'u dasu Khalit da Khalil & Rahma. Nan tagigice ta kalli Yalwa daniyar cewa wani abu saiga MUSLEEMA da YAWO sun iso wajen. MUSLEEMA ta durqusa da cewa. "Dan Allah Aunty Yalwa kimana hakuri zamubar aiki anan. Saboda abinda ya faru jiya damu... Nan YAWO takwashe komai tagaya mata. Ta qara da cewa "Kiyi hak'uri Yalwa ki yafe mana kud'in da kike binmu bashi wanda bamu qarasa aikin dan biyanki ba. Nan hankalin Yalwa ya tashi. Danta gane kamar yanda tayi harsashe idan tamallaki MUSLEEMA zata qara samun kwastamomi. Toh haka abin ya kasance. Dan MUSLEEMA nafara bama munan nata abinci saita lura wasunsu jikin MUSLEEMAN ne yake sasu dawowa washe gari ko basuyi niyar dawowa ba. Tunaninsu ko zasu cimma burinsu. To tayaya zatayi ta rabu dasu haka cikin sauqi. Dan haka cikin b'acin rai ta kalli yawo dakyau tace... "Ke tsohuwa ba inda zaku har sai kunyi min aikin kud'ina. Dan ba haka mukayi daku ba. Tayaya zan ciyar daku da way'ancan yaran naku masu cin tsiya sannan na baku aran kud'i yanxu kuzo kuce min wai inyi hak'uri zakubar aiki nayafe muku kud'ina. To wallahi baku isa ba. Dan sai kunbiyani kud'ina. Saboda lokacin dake kikazo kikamin y'ar murya akan na ranta miki kud'i zakiba MUSLEEMA taje can gari nemo mijinta ba wanda yasani dan haka babu batun hak'uri ko yafiya anan zaku zauna kuyimin aikin kud'ina iyeeee... Galla mata harara MUSLEEMA tayi da cewa. "Lallema matar nan baki da imani. Kina gani za'aci mutuncin aure. Za'aci mutuncin soyayyata. za'aci mutuncin shinfid'ar mijina amma kike magana akan wai saimun zauna hakan tafaru dan kawai munci kud'inki wanda bai taka kara ya karya ba.. Kallemu sama daga qasa muba matsiyata bane. Qaddara qaddara qaddara ce tasa kika gammu nan cikin garinku gabanki muna sunkuyar dakai dan muyi miki aiki kibamu abin zamuci. Banda haka ba abinda zaisa muyima wata mata kamarki aikatau. Dan haka kwantar da hankalinki ina dai dubu d'aya ce Yanxu saura kud'in da kike binmu. Zan biyaki kafin fad'uwar rana kwana ne dai bazamu qarayi cikin wannan akurkin naki ba... Ba Yalwa ba hatta YAWO sanda tayi mamakin maganar da MUSLEEMA tagayama Yalwan. Dan aqalla Yalwa ta haifi MUSLEEMA. Yalwa gyad'a kai tayi tace.. "Hmm d'an Adam butulu. Tokije duk inda zaki kije ki nemomin kud'ina sannan kizo ki kwashi y'ay'anki da kakarki kubarmin akurkin nawa tunda ke matsiyaciya ce. Girgiza kai Hajjiya batula tayi cikin jin dad'in faruwar yanayin. Yanxu take da damar dazata cuka maganarta ko zatayi tasiri. Dan haka salta kalli MUSLEEMA tace "Y'ata zonan ba haka za'ayi ba. Zo nan kigayamin wacece ke... Da kuka MUSLEEMA ta qarasa gareta takwashe komai tagaya mata. Duk da cewar Hajjiya Batula shed'aniya ce sanda ta tausayama MUSLEEMA. Saidai duk da haka zataso burinta ya cika akan yaran MUSLEEMAN dan haka saita kalli YAWO tace... "Ayya ai mutanan kirki sun mutu a garin Kano. Dakin sani daba nan kike nufo ba. Sannan gaskiya Baba kinyi kuskuran bama shi LEEKITAN ZUCHIYAN jikarki MUSLEEMA. Yanxu shawarar dazan baku d'ayace. Shine zai iya yuhuwa shi direban ba garin kano ya kawosa ba. Dan haka ku canja gari ko Allah zaisa ku dace. Amma idan kunga zaku iya bina ni ina garin KADUNA ne da zama. Kuma kunga zai iya yuhuwa direban garin kaduna yayi dashi ba nan garin kano ba. Tunda kunga duk hanyar d'aya ce. Idan kun yarda dama ni nazo nan Kano siyan kaya ne jiya. Idan kunga ba damuwa kuzo muje garin Kadunan kuyi sati d'aya a gidan nawa lokacin kun huta. daga nan saiku fara neman LEEKITAN ZUCHIYAN. Tunda kunga likitocin zuciya sunfi yawa a garin Kaduna. Ina kyautata zatan zaku samesa acan d'in Kunga shikenan saina bama Yalwa kud'inta wannan na bata fisabidillahi ne na temakeku. Saidai zaku dinga min aikin gidana har lokacin daza kuga LEEKITAN ZUCHIYAN shikenan fa idan kun amince. Danni nayi niyar temakwanku ne tsakani da Allah ganin likitocin zuciya sunfi yawa a garin na Kaduna... Ai dajin hakan MUSLEEMA tace. "Na amince Aunty Allah yasaka. Haka YAWO mah tace ta amince. Jan numfashi Hajjiya Batula tayi da cewa. "To kuje ku had'a kayanku da kan yaran ga motata can kusaka kayanku kafin na gama da Yalwan. Aiko kicin jin dad'i suka koma ciki dan aiwatar da abinda tace musu. Yalwa takalli Hajjiya Batula tace "Nasan dai badan Allah kike san zuwa dasu garin na Kaduna ba. Tace "Eh magana ta gaskiya naga yaran MUSLEEMAN zasuyi daraja da yawa ne. Sannan daga ganinsu basu da hankali. Banda haka me zaisa kakar tata tabama wanda bata san daga Inda ya fitoba jikarta. Sannan dan rashin dabara sukama suzo garin kano batare da sunsan inda zasu dosa ba. Kawai magana ta gaskiya anan naga zanyi kud'i sosai da yaran nan idan na siyarma da Ahaji bala su. Murmushin mugunta Yalwa tayi da cewa.. "Dan Allah albarkacin rashin kunyar da MUSLEEMAN tamin ina rokwanki da ALLAH kuna zuwa kisa a fiffille musu kai🤣 Dariya Hajjiya Batula tayi da fad'in.. "Kai Yalwa baki da mutunci. Ai ki kwantar da hankalinki tunda sukacemin su fulani ne naji na tsanesu. Kin manta kishiyata bafulatanace ta kwacemin miji. Aitun daga lokacin natsani duk wani bafulatan mutum dan babu mugu kamarsa. Yanxu dai ga dubu ishirin kiyi harkar gabanki da ita. Idan mun had'u na qara miki wani abun koda yake kema ai kin kusa fad'owa hannu adinga damawa dake. Yalwa tace. "Eh duk da haka wallahi baki isa ba. Koki bani duba hamshin ko yanxu na tona miki asiri agunsu. Sanin halinta shiyasa Hajjiya Batula qara mata sukayi sallama. Motar tata kad'al idan ka kalla ta'isheka tabbatarwa Hajjiyan me kud'ice. Cewa tayi MUSLEEMA takoma gaba tabar YAWO da yaran a baya zasufi sakewa. Aiko hakan MUSLEEMA tayi. Hajjiya Batulan tashiga mazaunin direba tajasu da gaske garin na kaduna tanufa dan acan d'in gidan nata yake... By AUNTYN LUV😍😍😍 [7/26, 1:00 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ® http://hausafulaniwriters.blogspot.com ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 24☆ Sun d'an sha tafiya sannan suka iso wani katafaran gida. Tun daga bakin get YAWO da MUSLEEMA sukasan hajjiyan tajik'u da naira. Nan ma'akatanta biyu mata suka hau zube mata suna masu yimata Barka da dawowa. Tunda MUSLEEMA da YAWO suke aduniya basu tab'a zatan zasu Shiga gida irin wannan ba. Duk da cewa bawai gidan ya taka kara ya karya bane. aa gida ne dai me kyau amma ko kwatan kwatan kyau baiyiba a irin jerin gidajen masu kud'i. Yanxu dai gasu afalan gidan sai raba ido suke inda ɗaya daga cikin masu aikin takawo musu abinci me rai da lafiya. Shinkaface da miya da had'in salat da nama manya manya. Ga drink da ruwa susha duk wanda sukaga dama. Haka sukayi nak Hajjiya Batula takallesu da murmushi tace bara tayi musu jagora I zuwa inda zasu dinga kwana. Da murmushin godiya sukabi bayanta har takaisu wani d'aki me kyau da tsari. Gadone lafiyayye ad'akin da durowarsa sai toilet. d'akin dai ba lefi yayi kama dana saukar baqi. Haka su MUSLEEMA sukayi sallah tayima yaranta wanka da canja musu kaya suka d'an kwanta saboda gajiya. Basu suka tashi ba saican kusan magrib. Haka sukayi salati da godema Allah daya kawosu hannun wannan mata me kirki. Dan tunda suka baro Rugar malam jauro basu tab'a baccin kwanciyar hankali cikin lokaci kad'an haka ba. Haka da sukayi sallar isha haka me aikin nan taqara basu abinci har cikin d'akin da suke. Sukaci suka qoshi kamar d'azu suka qara meqewa suka kwanta. Sam Hajjiya Batula Bata bi takan su cikin daran da udirinta ba. Saboda tana so susake da ita tayanda zata aiwatar da udirin nata da hikima. Haka yasa tadinga kyautata musu. Ba dare ba ranah harna tsawan sati d'aya kamar yanda tagaya musu saisun huta saboda jikin YAWO da bata jin daɗinsa kana saisu fara fitta neman ADAMS dan idan suka fitta ne take da damar cimma burinta akan yaran. Ayau d'inne kwanansu bakwai dan haka sai murna Hajjiyan take tana Allah Allah gobe tayi dan agoben ne su MUSLEEMA da YAWO zasu fara fitta neman ADAMS LEEKITAN ZUCHIYAN nasu. Hafsat sunan d'aya daga cikin y'an aikin Hajjiya Batula itace taji tausayin su MUSLEEMA data nemi yau subata labarinsu sukako bata. Taji tausayinsu matuqa musamman ma datasan k'udirin Hajjiya Batula akansu. Saboda itace idan hakan tafaru ma'ana idan Hajjiyan tazo da mutane irinsu irin hakan. itace take jan hankalin yaran takaisu can bayan gidan Hajjiyan wajen wata k'ofa da aka fitar da yaran da Hajjiya Batulan take siyarwa. Sai wani alhaji bala yasa yaran amota yayi gaba dasu. Shikenan duk bala'in duniya da za'ayi yaranka sun tafi kenan. Dan ita Hajjiya Batula zata nuna ai tana tare daku masu y'ay'an. Kawai dai yaran sun fitta waje ne wasu suka sacesu. Dama garin Kaduna ai garin mayune.🤪 yanxu ne dai abin yayi sauqi. Ahankali Hafsat ta kalli YAWO da MUSLEEMA tace dasu.. "Zan gaya muku wata gaskiya saboda yanda naji tausayinku araina. Hak'ik'a da kunsan wajen wacce kuke hannunta ayanzu. da baku yarda kun biyota ba. Hajjiya Batula wata shahararriyar shed'aniya ce. Bata da aiki saina sato yaran mutane tana saidama manyan mutane suna kud'i dasu. Ta gayamin gobe zaku fara fitta neman LEEKITAN ZUCHIYA dan haka agoben naja hankalin yaranki ke MUSLEEMA nakaisu wajen Alhaji bala. Idan kuka dawo sai nace muku ai kuna fitta yaran suka saka kuka shine na bud'e musu get suka biyo bayanku dan atunanina tunda naga bakuyi nisa ba nasan zakuji motsinsu a bayanku. Kai batama yanda za'ayi kuna fitta na bud'e musu get kuce baku gansu ba.. Idan kunqi gamsuwa da wannan hujjar Hajjiya Batula tasan abubuwan da zata gaya muku dole sai kun yarda kun gamsu yaranku b'ata sukayi. Sannan zata b'ata muku tunani wajen yad'awa gidajen rediyo da talabijin wajen cikiya sam bazaku kawo cewar itace tasace muku yara ba. Idanfa kuncire zoton ba itace tasace muku y'ay'aba. Idanko kunsaka mata gaba kan itace tasace muku y'ay'a Wallahi makaku zatayi agun bokanta ya rufe muku baki. Waro ido waje😳 MUSLEEMA tayi jin abinda Hafsat ke faɗi. Ai ba shiri tararumo yaranta ta rungumesu cikin matuqar tsoro kamar ance mata yanxu ne za'a rabata da yaran. Cikin kuka ta kalli Hafsat d'in tace.. "Yanxu ya za'ayi mu ficce daga gidan nan. Wallahi ina san yara na ina san yaruwa dasu ina san ubansu ya gansu ina san rayuwa dasu da ubansu.😭 Jan numfashi Hafsat tayi da cewa. "Agaskiya yanxu kuna cikin bala'i. Saboda yanxu kuna tashi kuna cewa zaku fitta daga gidan nan da yaran nan wannan saurayin me bama fulawa ruwa bazai tab'a barinku kufitta ba. Dan yasan nufin Hajjiya akanku. Nan zaiyi babakere a get yace saiya kira Hajjiya idan tace abarku ku ficce toh. Idan yaji sab'anin hakan bazai barku ba. Kuma Hajjiyan na zuwa farko tambayarku zata farayi mezaisaku tafiya batare dakun gaya mata ba. Daga lokacin da kuka fara mata kame kame daga wannan lokacin kunjefamu nida abokiyar aikina a bala'a. Saboda zatace mungaya muku wani abu Wallahi daga yau mumbar numfashi aduniya. Dan kashemu zatasa ayi. Saboda da mu uku ne masuyi mata aikin. Sai d'aya data gane me take aikatawa saita gudu garinsu dan acewarta a imani irin nata babban kuskure ne dasa hannunta adinga kashe yaran mutane. Wallahi ina gaya muku har garinsu Hajjiya Batula tasa wasu sukaje suka kashe Balkisu bazamu tab'a mantawa ba dan agabanmu tayi waya tana jinjinama way'anda sukayi kisan. Sannan taja kunnanmu wai muma idan muka fad'ama wani abun da takeyi bama muba har iyayenmu saitaga bayansu.. Wallahi nima raina basan wannan aikin yake ba. Lokuta da dama idan ina aikatawa kuka nakeyi cikin dare kan Allah ya fitar dani daga gidan nan lafiya😭 Dan ni aikin su wanke wanke nazo mata kuma haka iyayena suka turoni nayi. Saidai basu san abinda nake aikatawa ba. Hafsat takai qarshen zancenta da zubda hawaye Goge gumi YAWO tayi da tashi arikice take cewa. "Bar kuka y'arnan yanxu ba lokacin kuka bane. Innalillahiwainna'ilaihirraji'un. Wannan ba gidan zama bane. Keko yarinya meyasa baki fad'in mana hakan tuntuni ba. Goge hawayenta Hafsat tayi da cewa.. "Kwantar da hankalinki YAWO zan fitar daku daga gidan nan ta k'ofar da ake fitta da yaran da take satowa. Amman sai cikin dare yayin da qafa ta d'auke. Dafatan kingane. "Nagane y'ar nan. "Toh yanxu kusake karku nuna kunsan wani abu bare tagane. "Insha Allah bazamu nuna wani abu wanda zaisa ta ankare damu ba. MUSLEEMA tagaya mata hakan da qara qanqame yaranta. Godiya sosai YAWO tama Hafsat. Kana Hafsat d'in ta fitta daga d'akin nasu cikin sand'a takoma nasu. Kasancewar tara har da rabi tayi:pm. Su MUSLEEMA ko sam basu kwantar da haqarqarinsu ba. Dan tsoro ya cika zuciyarsu. Haka suka had'a kayansu gefe d'aya jira kawai suke dare yayi Hafsat tayi musu dagoran fitta. Har qarfe biyu na daran idansu qir yake. Rahma na bayan yawo. Yayin da Khalil yake bayan MUSLEEMA. Haka d'auki Khalit ma tarungume duk da sun fara nauyi da wayo. ita dai awannan lokacin bataji nauyinsu ba. Aiko Ahankali Hafsat tatuto ƙofar tasu tayi musu nuna da hannunta su biyota. Cikin sanda haka Allah ya basu sa'a suka ficce ta k'ofar da Hafsat tagaya musu. Sanda suka fitta. YAWO takama hannun Hafsat tace "Yanxu bazakizo mu gudu dake ba. Murmushi Hafsat d'in tayi da cewa. "Kiyi hakuri YAWO nafiki san nabar gidan nan. Ina san iyayena araye wannan yasa nake har yanxu agidan. Indai addu'a na magani insha Allah zan fitta daga gidan. "Tome yasa bazaku kai qararta gun hukuma ba. MUSLEEMA tace da Hafsan hakan Murmushi Hafsan tayi da bata amsa da.. "Wata rana wani mutum ya tab'a zuwa da y'an sanda yace tasace miki d'a. Haka tarufe idanta tace ita bata sace mishi d'a ba. In takaice muku tunda tamaka mutumin akotu wai yayi mata qage da sharri akan abinda bata jiba bata gani ba. Har yanxu yau kusan shekara biyu kenan ba'a sake mutumin ba. Yana can gidan yari ana ganamai azaba. Kudai Allah ya temake ku sai kuyi Maza kuqara gaba. Dan yanzu lallabawa zanyi na mayar mata da kin k'ofar nan karta gane. Ga number na wata nasan wata ranah zaku nemeni. Karb'a MUSLEEMA tayi. Sannan YAWO tayi mata godiya sosai suka d'auki hanya. Ita kuma Hafsan takulle ƙofar da komawa cikin gidan da sand'a Sam su MUSLEEMA basu san inda suke jefa qafarsu ba. Sudai saibin titi suke suna tafiya da addu'a. Ahaka sukaga wani layi suka Shiga. nan sukaga wani gu da alama wajen me saida balangu ne. To wajen yad'anyi duhu anan suka shinfid'a zaninsu suka zazzauna da rungumar yaran dansu bacci ne a idansu. Har aka kira sallar asuba idansu YAWO garau yake. Suna ganin mutane suna wuccewa zuwa masallaci har aka sauko akan idansu. Haka sanda gari yayi haske har mutane sun fara yawa sannan suka tashi daci gaba da tafiya. Rahma ce tasa musu kuka ita abata abinci. Nan suka tsaya wajen wata mata me saida koko da k'osai. YAWO ta durqusa taroketa taba yaran kokon da k'osai d'in basu da kud'i idan tana buqatar sumata aikin kud'inta zasu mata. Kallansu sosai matar tayi kana ta tab'e baki tace Nanawa zata basu YAWO tafad'a mata sannan tabasu. Haka suka ibi ruwa a gun matar suka wanke musu baki da burushinsu da makilin Suma suka wanke nasu. sannan suka ba yaran koko da k'osan kana suka roketa dan Allah tanuna musu gidan da zasu Shiga suyi salla.. Daqer matar tanuna musu wani gida ba nata ba. Dan bataji aranta tayarda dasu ba. Matar gidanku me kirki kuwa. haka tabasu ruwa sukayi sallar sannan suka fitto lokacin harsu Rahma sun gama cin k'osan da kunun. Sai suka tambayi matar wane aiki zasu mata na kud'inta. Tace ita kawai tabasu dan Allah ne. Dan haka su d'auki yaransu su qara gaba. Haka suka mata godiya suka tasa yaran agaba suka fara tafiya suna tambayar mutane LEEKITAN ZUCHIYA.. "Dan Allah malam katemaka idan kasanshi. Sunan damu muka rad'a mishi shine Ahmad. Amman sunanshi na Ainihi LEEKITAN ZUCHIYA. Ance mana likitocin zuciya sunfi yawa anan garin na kaduna ne shiyasa mukazo ko Allah zaisa adace. YAWO tafad'ama wani mutum hakan da suka taresa.. Kallansu yayi a nazarce kana yace.. "Gaskiya ban sanshi ba. Kuma garin kano yafi cikin garin nan likitocin zuciya. kawai wanda ya gaya muku ya fad'in muku hakan ne danya baku wahala.. Yana fad'a mata hakan ya wuccesu. MUSLEEMA ta zauna kan wani d'an dandamali anan kan titi bakin wani layi tana me kallan YAWO tace da ita. "Wallahi nagaji YAWO. Yunwa nakeji. Gashi qirjina zafi yake min. Yana min wani abu kamar soya haka ga zafi kamar ZUCIYATA zata fitta.... Itama Yawo zuwa tayi gefanta tazauna yaran suka tsaya gabansu tace. "Hak'uri zakiyi MUSLEEMA mu qara gaba ko Allah zai had'amu dame saida abinci kici ko yunwace Shuru MUSLEEMAT tayi. jin yanda yanxu gabanta ya shiga bugawa fat fat fat... Aiko dai dai lokacin ADAMS ya faka motarsa agefan titin. Amman tatsallakensu MUSLEEMAT d'inne. Yana tare da Yusuf ne Wanda yaje har office d'insa ya d'aukosa dan ya duba masa kakarsa Hajjiyansu. Yusuf d'in yayi yayi da ita Hajjiyan nasu kan tayarda yakaita asibitin kamar yanda ya saba kaita tace ita sam yau batasan yakaita yaje dai ya d'auko mata ADAMS d'in tasan zaibar duk abinda yake yazo ya dubata ai. Shine fa Yusuf yanxu yaje yasa ADAMS d'in agaba kan suje ya dubata. Ahankali ADAMS ya kalli Yusuf yace.. "Kayi hak'uri d'an uwa. Yau dai d'aya na tsaya gefan titi dan amsa waya. Murmushi Yusuf yayi da cewa.. "Haka tsarin yake ai. Dama ai ganganci kakeyi da kake d'aga waya kana tuqin. Fatana dai Allah yasa ba maiyarka bace takiraka taja mana lokaci. Murmushi ADAMS yayi da cewa "kamarko kasan Ita d'ince. Yafad'a yana me d'aga wayar daci gaba da cewa... Ina cikin k'oshin lafiya my luv. NUFAISAT dake tsaye a kitchen d'inta tana yanka kub'ewa dan yau ADAMS d'in yace mata tuwo yake san ci da ranah. kasancewar yau itace dashi ma'ana tashiga girkinta. Ajiye wuqar dake hannunta tayi tare da tab'e baki tace.. "Nasan kana cikin k'oshin lafiya mijina. Tunda tunkan kafita nake binka da addu'a. Kuma nasan bazata fad'i qasa banza ba. Kawai haka kawai naji gabana yana fad'uwa yanxu. Shine na kira ka dan naji lafiyar zuciyarka. babu mamaki ko zuciyar taka tana dab da karb'ar wani saqo ne shine nake san jan kunnanka dan Allah karka bari ta amshi sakwan soyayyar wata y'a mace... Hak'ik'a ADAMS yana jin NUFAISAT da kalamanta amma idansa nakan MUSLEEMA yana me qare mata kallo from up down. Kallo na qurilla. Tunda idansa yakai kanta wasu jijiyoyi acikin kansa sukaso fara aiki. Saidai dake yana jin muryar NUFAISAT d'in sai hakan yaqi ba jijiyoyin damar aikin yanda ya dace. "Kamar nasanta. Ya faɗi hakan a bayyane batare da yasan ya fad'i ba Cikin nutsuwa NUFAISAT tace.. "Ita wah🤔.. Ahankali yacire wayar tashi daga kunnansa yamaida kallansa kan wayar.. Shi sai yanxuma ya tuna Ashe waya suke da NUFAISAT. Dan haka cikin sauri ya maida wayar kunnasa da cigaba da cewa. "Kiyi hak'uri my LUV na Shiga wani yanayi ne. Waro ido😳 NUFAISAT tayi da cewa. "Na Shiga uku ni NUFAISAT. Kardai har zuciyar taka ta karb'i sakwan. Murmushi ADAMS yayi da faɗin. "Kwantar da hankalinki matata. Dan ba wani sak'o da zuciyata zata karb'a imba naki ba. "Naqi yarda da abinda kace min a wannan lokacin. B'cos baka tab'amin qarya ba. "Haka ne my LUV. Kuma bazan fara miki yau ba. Zan gaya miki idan nadawo gida. "Yanxu bazaka gayamin ba. "Muna kan hanya ne nida Yusuf zanje duba Hajjiyansu. Pls ki barni kar kisa kaina ya kulle na kasa komai dan Allah. Murmushi tayi da cewa "Kanka bazai kulle ba mijina bare yasaka kasa komai. Na Barka saika dawo luv u.💋 Murmushi kawai yayi da ajiye wayar ya qara maida kallansa ga MUSLEEMAT tare da tab'a Yusuf wanda yaketa danne dannan waya yace dashi... "Kaga wata Baby mekyau🧕🏻. Nutsu dakyau ka qare mata kallo tatara duk wani abu damu maza muke buk'ata agun mace.. Murmushi Yusuf yayi idansa nakan MUSLEEMAT d'in yace. Saidai hannunta na dafe da zuciya. "Eh nanma na lura kamar tana da matsala da zuciyartata. dan idan kaqara kallan gefan wiyanta dakyau zakaga alamar tashin wata jijiya wacce nake kyautata zatan akowane lokaci ciwan zuciya zai iya kamata. Dan wannan jijiyar alamace tafara bayyanar ciwan Jan numfashi Yousuf yayi da cewa "Wai dama waya kakeyi d'azu ko kallan yarinyar mutane. Dan naga kayi saurin gane komai atare da ita cikin lokaci k'ank'ani.. Murmushi ADAMS yayi da bashi amsa. "Kasan ko'a skull nafika gane abubuwa cikin sauri. Kuma karkace na shagala da yawa. Dan kasan san mata ba d'abi'ata bace. Juyowa Yusuf yayi yana harararsa da cewa. "Wato magana zaka gayamin. ADAMS ya qara yin murmushi da cewa. "Harma na gaya maka mai ai. In banda iskanci kasan dai neman mata baya gabana Kaine dai wahalalle daka dami zuciyarka saika had'u da wacce tacika sharid'anka.. "Naji dan Allah. Wannan d'inma dan tayi yarinya ne. Bazata isheni watayawa da yaw ba. Da Wallahi yau saina baka kunya na nemeta da aure in kashe bakin gorin da kakemin akoda yaushe. Tada motar ADAMS yayi yana cewa. "Dako ka huta wallahi.. Daidai nan kamar ance MUSLEEMA tad'ago kanta saiko tasauke akan gefan fuskar ADAMS... Azarane tatashi har tana mangare Khalit dake gabanta ta kwalla ihu tana nunama Yawo ADAMS faɗi take "Wallahi shine. Shine YAWO. Shine acikin motar can. Wani saurayi ne yazo wucce yaji abinda take fad'i. Sai ya kalli motar ADAMS dake tafiya ya dawo da kallansa kan MUSLEEMA da galla mata harara yace.. "Shine wah. Da sauri MUSLEEMA ta qarasa gun saurayin tace. "Shine mijina Wallahi mujina ne dan Allah kasan shi ne. Kallan raini yayi mata da qare mata kallo daga sama har qasa yace. "Gaskiya ke y'ar rainin hankali ce. ADAMS LEEKITAN ZUCHIYA ne mijinki. Ke kinsan waye shi afad'in garin nan kuwa. Wani babban mutum ne me arziqi. Gashi Doctor gashi d'an kasuwa. Kafin ki gansama kuzanta sai kina da hanya. Dan yau baki gansa da masu tsoro ba shine zaki wani ce mijinki ne. Mijinki a ina kina kicaka dake haka. Dubeki fa kamar wata almajira. Ke idan kikaci karo da Matansama kikace ke matarsa ce wallahi sai sun sa and'aureki d'aurewar dahar ki mutu bame kunceki. Shashasha wawiya almajira kawai... Ai MUSLEEMA bataji qarshen zancensa ba hannunta dafe da k'irji tafad'i sumammiya sakamakwan qara ganin motar ADAMS da tayi tana nufosu.. Dama zagawa ADAMS yayi da motar tashi dan cikin layin dasu MUSLEEMA suke zaune zai Shiga kasancewar nan ne layinsu Hajjiyansu Yusuf d'in da suke san zuwa dubata. Jan tsaki saurayin yayi da wuccewarsa abinsa yana tafiya yana sambatu daga ganinsa kasan akwai abinda yake damunsa kamarma dai abuge yake. Hankalin YAWO ya bala'in tashi. Nanta jawo MUSLEEMA jikinta tana mata fifita da fad'in. "Ki tashi MUSLEEMA kinga halin da muke ciki dan Allah ki tashi. Dai dai nan ADAMS ya qaraso da motarsa dan yin kwana ya Shiga layin. Ahankali ya tsaya da motar tare da zuge gilashin b'angaransa ya kalli YAWO da cewa.. "Sannu Baba meyasameta. Ai da sauri YAWO takallesa tana had'a ido dashi tunaninta ya tsaya cak.... San da ADAMS ya qara maimaita tambayarsa Sannan tunaninta ya dawo. Hawaye ya zubo mata tace dashi. "Yanxu tafad'i d'an saurayi. dan Allah katemaka min ita kenan gareni.. ADAMS ya kalli MUSLEEMA dake hannunta kamar bata da rai. Kana ya kalli yaran nata da suka zuba musu ido shida Yusuf. Saiya fitta daga motar Yusuf ya biyo bayansa. Ahankali ADAMS ya d'auki MUSLEEMA Yusuf ya bud'e mai gidan baya yasata. Sannan ya kalli YAWO da cewa. "Kushiga muje asibiti. Da sauri yawo tashige ciki da yaran. Yusuf ya koma wajen zamansa yana cewa. "Mujuya kawai adubata ma dawo ka duba Hajjiyan namu.. "Toh. ADAMS yace mai jiki babu kwari dan haka kawai yaji jikinsa ya mutu da ganin yaran MUSLEEMA. Shi idanma idansa ba gixo yake masa ba zai iya cewa yaran na kama dashi. Shima Yusuf yaga kamar amma sam wani abu bai dirsu a zuciyarsa ba. Suko yaran kallan ADAMS kawai suke zuciyarsu na raya musu ayya basu san wannan mutumin ba. Yawo ko gabanta fad'uwa yashiga yi. Yayinda hankalinta duk ya tashi da ganin Adams d'in. Dan ganin ya qara kyau sosai. Ga wani kwarjininsa daya maketa. Ita tsoroma taji tace tasanshi bare har takaita da cewa ya Auri jikarta harda yara uku. Wayyo Allah ya kawo mata sauki cikin lamarin.. Awannan lokacin TAUDHAT na tare da malamin nata sun gama tsula tsiyarsu. Dan cema ADAMS tayi ya sauketa agidansu tana da maganar da zatayi da mamanta. Toh shinefa daya tashi fitta office d'azu da safe ya sauketa. Shine yana tafiya tayi wajen malamin nata karb'ar maganin mata. Shi kuma yace mata saiya jita. "Dan Allah kamin had'i na musamman. Dan naga kan ADAMS bai dena rawa akan NUFAISAT kwanan nan ba. Ka duba yau zai Shiga girkinta sai wani nishad'i yake. Ina jinsafa yana cemata tayi masa tuwo ta turamai office shi zaici yau da ranah. Kumafa karka manta idan da nice nayi masa tuwo sam bazaici ba.. TAUDHAT ta fad'inma malamin nata hakan da damuwa. Murmushi malamin nata yayi da shafan gefan fuskarta yace.. "TAUDHAT kina da futuna. Nina rasa me kike gani agun wannan kishiyar taki da kike kishi da ita. "Kai bazaka gane bane. Yanxu dubamin kaga me yake tafiya a tsakaninsu. "Toh.. Yace mata da wargaza qasarsa yana Zane Zane cikin gwanancewa. Can ya d'ago ya kalleta a furgice. Sai kuma yaci gaba da zane zanen nasa. Sanda ya gama tsaf ya ture farantin qasar tasa gefe yace da ita.. "Tabd'ijan.. Lalle ambar baya da qura.. "Ban gane me kake nufi da ambar baya da qura ba. "Ina nufin NUFAISAT da ADAMS ba wani abu na tashin hankali agaresu. Qara san junansu suke kamar yanda kika sani. Baya da quran da kikaji nafad'i ko shine Wallahi ga wasu yara nan kyawawa na mijinki ADAMS har uku. wata qaramar yarinya ce tahaifa masa su. sam shi bai samma yaransa bane.. Haka ita yarinyar ayanzu bata cikin hankalinta. 😳😳😳 Inda ace kawunan TAUDHAT uku ne ba shakka da saita waro dukka idanunta dasu. A razane. A furgice. A haukace tadafe qirji da cewa.. "Kutumar uba. Ban gane me kake nufi ba. Ka fahimtar dani na fahimta. Wallahi kwakwalwata ta hautsine.. Isma'in ina san nayi haukafa.. "Ki kwantar da hanlinki yanxu ki koma gidan naki ki gano mana komai. Danni nayi bincike akan nasan komai. Saidai banga komai d'in ba. Yanxu saikin gano mana wani abu zan iya baki haske. Da sauri TAUDHAT tatashi da saka kayanta ta d'auki yajarta ko sallama batayi masa ba taficce daga d'akin nasa hankalinta amatuqar tashe... 🤔🤔🤔🤔🤔 na gaida y'an hannuna [7/28, 4:18 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R http://hausafulaniwriters.blogspot.com ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 25☆ Koda ta iso gidan bataga kowa ba alamu sun nuna ba wani ma abinda ya faru. Nan takira malamin nata tace bataga kowa ba. Yace tabari Adams d'in ya dawo tukunna... Su ADAMS ko bayan sun isa asbitin duba MUSLEEMAT yahauyi. Inda ya tabbatar tana d'auke da ciwan zuciya. Sosai yashawo kam matsalar yana me mamakin yanda tana qaramar yarinya haka takamu da ciwan ZUCIYAR Ahankali ya kalli yawo dace mata. Bara suje ya duba kakarsa. Yana nufin Hajjiyansu Yusuf. Bayan sun dawo ne yana zaune kan kujerarsa a office d'insa sai kawai ya shiga tunanin meyajama MUSLEEMA ciwan ZUCIYA tana qaramar yarinya haka. Shuru yayi dajan numfashi ya kira ma'aikaciyarsa yace takira masa kakar yarinyar daya duba d'azu. Cikin ladabi ta amsa mai da kiran YAWO. Bayan YAWO tazauna ya kalleta anutse da cewa.. "Baba ina san nasan sunanki. "Sunana YAWO.. "Wannan yarinyar dana dubata y'arki ce ko jikarki. "Jikata ce. "Ina iyayenta. "Atakaice dai yanxu ita marainiyace. Danni yara biyu gareni. Rahma da Musa. Kuma duk na rasasu. Yazu haka dai ita kad'ai taragemin da yaranta. Waro ido ADAMS cikin mamaki yace da ita. "Kina nufin way'ancan yaran ita ta haifesu. YAWO ta d'aga mai alamar tabbatarwa hawaye na zubamata tace. "Y'an uku ne su. Wata ranah wani yazo rugarmu da matsalar d'aukewar tunani. Ita ce tafara ganinsa. Sai me rugar nawa yasa d'ansa doctor yayi mai binciken lafiyarsa. Bayan yagane yasamu d'aukewar tunani. Sai muka saka masa suna Ahmad kasan cewar bamu san sunansa da inda ya fitto ba. Bayan d'an me Rugar namu ya dawo dashi daga asibitin nashi. Sai jikar tawa tanuna qauna agareshi. Zai zauna wajen me rugar tamu. saitace ita tana san nakawosa gidana yazama yayanta. Haka na yarda da abinda tace dan baqaramin so nake mata ba. Ahaka ahaka soyayya tashiga tsakaninsa da ita. Taqi wanda suke da alk'awarin Aure. Tace shi take so. Nan banyi cikakken tunani ba. Banyi tunanin bansan daga inda ya fitoba. Banyi tunanin waye shi ba. Banyi tunanin ko sunansa bamu sani ba. Kawai saina duba nutsuwarsa da kyawun halinsa. Da ladabi da biyayyar da yake min. Kawai saina aura masa ita. Watansu tara tasamu ciki. Shine tahaifi way'annan yaran y'an uku.. Bayan wasu lokaci sai wanda yake da niyar Auranta dafarko wanda suke da alqawarin Aure dashi saiyaja shi wannan mijin nata daji ya makeshi da sanda. Anan dai muka nemesa muka rasa.. In takaice maka shidai wanda ya makesan shine wanda yazo ya bamu labarin shine sanadin b'acewarsa. Shine mukaxo garin kano nemansa dan nan yace mana ya turasa. Gaban ADAMS ne ya fad'i sakamakwan tunanin dayazo masa kwakwalwa amma danya tabbatar da tunanin nasa saiya kalleta a nazarce yace da ita.. "Yanxu ina ne rugar taku. Kallansa yawo tayi da tunanin tagaya masa gaskiya ne kodai tad'an jinkinta taga iya gudun ruwan lamarin. Gaskiya ita tsoran ADAMS takeji. Sam bata tab'a tunanin ganinsa da zatayi akaro na biyu zai kasance mata haka me matuqar kwarjini da kamala ba. Idan tace zatayi saurin gayamai lamarin qila yaqi yarda da ita. Koma yayi mata wata fassarar. Gaskiya bazata gayamai yanxu ba. Saidai zatasan yanda zatayi su rayu dashi. Daga nan idan ya fara sakewa dasu saita gaya mai gaskiyar lamarin. Dan haka gyara nutsuwarta tayi da cemai. "Rugarmu nacan garin JOS basa. Jan numfashi ADAMS yayi da cewa. "Gaskiya kinyi kuskuran bashi jikarki bayan kinsan baki san daga inda ya fito ba. Sannan kuskure na biyu da kikayi shine na baro Rugarku da kukayi kuka fito yawan nemansa. Yanxu dai ina buqatar sanin wata damuwa ce tasa ita jikar taki shiga cikin wani hali dahar ya haifar mata da ciwan ZUCIYA haka... "Sanshi da qaunarsa ne ya haifar mata da hakan. Tana matuqar sanshi da qaunarsa. Dan kowane lokaci zancenta shine. Kullum cikin kuka take. Jan numfashi ADAMS yayi da cewa "Toh nidai yanxu nayi niyar temakwanku. Inasan naji wane irin temako kikesan nayi muku. "YAWO tashere hawaye cikin matuqar Farin ciki tace.. "Kayarda damu kan bazamu cuceka ba. Kakaimu gidanka matsayin y'an aiki ga matanka. Sannan dan Allah kabama yaranta kulawa kamar kaine mahaifinsu. Dan bani san sutaso da rashin soyayyar mahaifi agaresu. Shuru ADAMS yayi da tunanin shi tunda yaga yaran qaunarsu tashigesa. Gaskiya wannan karan saidai Dadynsa yayi hak'uri dashi yabarsa ya raini yaran daba nasa ba. Ahankali yace da ita. "Indai wannan ne insha Allah bazai zama da matsala ba. Zan nemi amincewar mahaifina yanxu naji tabakinsa. idan ya amince min shikenan. Godiya YAWO tamai sosai.. Anan yakira Dadyn nasa a waya yace dashi. "Dan Allah Dady kamin afuwa ina san rainan wasu yaran wata yarinya da kakarta. Ina san basu kulawata. Dan Allah Dady karkace aa. Shuru Dady yayi. Lokacin yana wajen shaqatarwar gidan nasa yana karanta jarida. Ahankali yace mai.. "Na amince amma ka kula dakyau. Dan kasan yanxu mutane babu yarda... "Insha Allah Dady zan kula. damma naji ajikina basu da niyar cutar dani. Murmushi Dadyn yayi da cewa.. "Kadai ka kula da kanka da matanka. "To nagode Dady sainazo. Yana fad'in hakan ya kashe wayar da kallan YAWO yana cigaba da cewa. "Yace ya amince min. Sosai YAWO tanuna Farin cikinta da qara yimai godiya. Kana ya bata umarni kan taje can waje wajen jira idan yaje ya duba MUSLEEMAN yaga tafarfad'o zai gaya mata.. Toh tace mai da matuqar jin dad'i... Qarfe biyu NUFAISAT ta aikomai da tuwansa datamai. Kad'an yaci yabama YAWO sukaci da yaran. Sai kusan qarfe biyar da rabi MUSLEEMA ta farfad'o.. Dake YAWO ta roqi Adams lokacin daya kawo musu tuwo tace mai yabarta tazauna a d'akin da MUSLEEMA take dan tana san ta farfad'o akan idanta. Ya amince mata da hakan badan suna yin hakan ba. To shine lokacin da MUSLEEMAN ta farfad'o Yawon tana d'akin. Dan haka cikin sauri YAWON tabata labarin yanda akayi bayan sumewarta. Sannan taqara mata da cewa karta tab'a gayama ADAMS cewa ita matarsa ce koda ya tambayeta yanxu. Ita dai duk abinda zaice mata tajishi kawai. Dan tana san tasan yanda yake rayuwarsa kafin subashi gaskiyar labari.... Kallanta MUSLEEMA tayi da cewa. "Indai zan qara rayuwar Aure dashi akaro na biyu zanyi duk abin da kikace. Sannan na godema Allah daya baiyana mana shi cikin sauqi.😀 Kan yawo tabata amsa saiga ADAMS d'in ya shigo d'akin.. Nan YAWO tashiga gayamai yanxu tafarka. Murmushi yayima YAWON saita futa daga d'akin shi kuma yaja kujera Ahankali ya zauna daf da MUSLEEMA yana qarema fuskarta kallo yace.. "Mema sunanki. Cikin sanyin murya gabanta na fad'uwa tace.. "Sunana MUSLEEMA. " MUSLEEMAT. Ya maimaita sunan da cigaba da cewa.. Suna me dad'i. Yanxu me yake damunki. "Ba abinda yake damuna. "Har tunanin mijin naki. Kallansa tayi da d'aga masa kai hawaye ya zubo mata tace.. "Eh har shi. "Zan iya roqar wata alfarma agareki... D'aga mai kai tayi alamar eh... Yaci gaba da cewa. Zan d'auke ki matsayin qanwata idan har zaki iya cire damuwar mijinki aranki. Dan ina san naci nasarar bama zuciyarki kariya.. Murmushi tayi dinful nata ya losa tace.. "Nayi maka alqawari idan har ka'iya rik'eni da gaskiya. Ka'iya bama zuciyata kulawa da amana. Zan cire duk wata damuwa daga zuciyata na fuskanci sabowar rayuwa. "Mijinki ya tab'a gaya miki cewa muryarki na dadad'i. "Bashi da abin fad'a wanda ya wucce yaban duk wata halitta tawa. "Toki kula da kanki. Dan yanxu zaki fara sabowar rayuwa. Bani fatan naqara ganinki kwance a wannan gadan dan matsalar ZUCIYA. Zan riqeki da gaskiya da amana qanwata. Zan baki kulawa fiye da yanda Yaya yake bama qanwarsa.. Ahankali ta sakar mai murmushi shima ya sakar mata. Sannan yace tatashi taci abinci ga toilet nan tayi sallah yanxu zaizo su tafi. Sunansa ADAMS.. Toh tace mai. Zuciyarta nasan tajita jikinsa. Ga qamshinsa me gyara tunaninta. Tana matuqar san mijinta.. Har yakai qofa tace da shi.. "YAYANA baka temaka min natashi ba. Ahankali ya dawo da tsayawa gabanta yace. "Ba cemin kikayi yanxu baki jin ciwan komai ba. Gabanta ne ya fad'i. Bata fatan ya futa batare dajita jikinsa ba. Gaskiya qauna da SO da zafi suke azuci... A shagwab'e kamar zatayi kuka tace mai.. "Na faɗin maka hakan ne kafin nagane qafata tana da matsala.. "Kina nufin bazaki iya takawa ba. "Idan dai naganni a bayi na sakama qafar tawa ruwa me sanyi zata tashi. Dan dama tasaba yimin hakan... Takai qarshen zancen nata da shagwab'ewa. Abin gwanin ban wani iri haka👌🏻. D'aukarta yayi ahankali yakaita toilet d'in sannan ya fito dajin dad'in yanda tafara saurin sakewa dashi. Murmushi yayi aransa yana fad'in koma waye mijinta sosai yake shan fama da shagwab'arta..😂 Bai wani dad'e a office d'in nasa ba. ya kulle dan shidda har ta gota. Nan yasa masu tsaransa su kwashi kayansu MUSLEEMAT susa a shara... Haka su MUSLEEMA sunaji suna gani aka saka kayansu a shara. Saidai suna cikin tafiyar tasu suka biya wani saban biotic d'in Adams d'in daya bud'e anan ya ibamma MUSLEEMA kaya sunkai 20. Haka Khalit da Khalil ma & mamansa Rahma. Dan harya fara kiranta da mamansa. Dayaji sunan Amminsa take da shi. Haka direct suka iso gidansa. NUFAISAT taci adonta cikin riga da wando jajaye. Tayi kyau sosai. A nazarce take qarema su MUSLEEMA kallo dayi musu sannu da zuwa. Sanda takawo musu ruwa da drink kana ADAMS ya mata nuna data biyosa shashinsa.. Dan haka saita cema su MUSLEEMAN tana zuwa. Da mamaki akan fuskarta take tayasa rage kayan jikinsa dace mai... "Mijina suwaye way'an nan. Jawota jikinsa yayi ta zauna kan cinyarsa saiya shiga bata amsa da... "Wasu y'an uwanki ne my luv. Dan Allah kiji tausayina ki tayani cika alqawarin danayi musu. "Na kasa gane inda zancenka ya nufa. "Bini Ahankali mana my luv aizan gaya miki komai.. Shuru tayi zuciyarta na bugawa. Ahankali ya qara jawota jikinsa dakyau ya kwashe komai ya gaya mata.. Sanda ta nutsu sosai kana ta kallesa da cewa. "Nayi alk'awarin zan tayaka cika alk'awarinka mijina. Saidai bazan b'oye maka ba. Gabana ya fad'i lokacin dana d'aga ido na kalli MUSLEEMAT. Jikina ya bani zuciyarta tana d'auke da wani sak'o.. Jan hancinta ADAMS yayi da fad'in "Kawai ki gayamin mekikejin tsoro. "Ina jin tsoran kar nasake da ita tazo ta auremin kai. Kamar yanda TAUDHAT tayimin. "Kina san dawo da hannun agogo baya my luv. Kince min kin gane manufata na auran TAUDHAT danayi. Ya kamata kibar batun TAUDHAT. Sannan batun da kike akan wannan Babyn tayimin qarama ASO. Tayaya zan fara iyawa da ita idan na auretan. Ya dace ki gane kece da ZUCHIYAR ADAMS har abada. Kece me iyawa dashi har abada Kece wacce ya fara so da qauna arayuwarsa.... "Kaga naji naji. Takatseshi da fad'in hakan. Tana me cigaba da cewa. Saidai katabbatar duk ran danaga MUSLEEMA tazama mata agareka zan d'auki hukuncin daya dace akanka. Sannan duk abinda nace awannan lokacin saika yishi.. Murmushi yayi da manna mata kiss💋 yana cewa "Na yarda... "Ba yarda kad'ai ba. So nake ka d'aukimin alqawari. "Na d'aukar miki alqawarin bani ba Auranta... Tashi NUFAISAT tayi daga jikinsa fuskarta cike da murmushi ta manna masa kiss da cewa. "Idanko ka kuskure zaina yanka kowa ya rasa🙅🏻‍♀.. Waro ido ADAMS yayi😳 da cewa. "Yankawa fa kikace. Da dariya sosai tace mai. "Eh. Kuma sai kana bacci zan yanketa fil🙈 Murmushi yayi dan ganin yanda taqarashe maganar tata da rufe idanta alamar taji kunyarsa. Kana ya tashi da qarasowa gabanta. Ya zare hannayanta daga fuskar tata yace... "Idan kika yimin hakan kinsan bani ba qara rayuwa. Magana ta gaskiya my Luv. tunda nake arayuwata ban tab'a d'aukar alqawari na tsinci kaina cikin fad'uwar gaba ba sai yau. Gaskiya wannan alama ce na akwai kuskure cikin alqawarin dana d'aukar miki yanxu.. Dan Allah kiba zuciyata nutsuwa kiyi hak'uri da wannan alqawarin. kiciresa daga zuciyarki kisa aranki tamkar ban d'aukar miki shi ba dan Allah.. Kama fuskarsa tayi da hannu biyu tana cewa. "Ai tunda naganta nasan akwai wani abu Wanda zai faru dani akanta nan gaba. Walau ni ko wani nawa. Ina ganin akanka ne abin zai faru shiyasa naji araina. Kawai na share nabarma Allah ikwansa. Zan kuma karb'i duk qaddarar dazata sameni sanadinta. Zan karb'a da hannu bibbiyu... Tana kawowa nan azancenta tarungumesa. shima rugumeta yayi cikin matuqar MASEEFAR SONTA.. Daqer ta kwaci kanta agunsa takoma wajensu YAWO. Nan takaisu wani shashi na baqi agidan. Falo ne da bedroom me toilet acikinsa Ba komai a falan saisu TV da kafet da kujeru. Sai bedroom d'in shi kuma set d'in gado ne. Bayan sun saka kayansu a durowa abinci me rai da lafiya NUFAISAT takawo musu Nan YAWO tama NUFAISAT d'in godiya sosai. Haka kawai NUFAISAT taji tana san YAWO da MUSLEEMA da yaranta Nan tarungume yaran tace tara tabasu abincin nasu da kanta. Murmushi MUSLEEMA tayi mata dan itama taji santa aranta sosai. Ahankali taje ta durqusa a gabanta tace da ita. "Aunty dan Allah zaki d'aukeni matsayin qanwarki. Wallahi tallahi haka kawai naji ina sanki. Sanda NUFAISAT tagama ba Khalit abincin da takai mai baki Sannan ta kalli MUSLEEMAN tace da mata. "Kawai kin rigani fad'a ne. Zan d'aukeki kamar qanwata idan har kika sakemin way'annan yaran suka zama kamar nice mamansu... Murmushi taqarayi da qarasa matsowa kusa da ita tace.. "Aunty na baki su. Dama yaranki ne. Kawai ni na Haifa miki sune.. Ahankali NUFAISAT ta kalleta. Nan take taqara jin qaunarta aranta Amman tashare da cewa. "Idanko haka ne zanyi saurin y'antaki cikin ZUCIYATA. Musamman idan kika kasance meyimin ladabi da biyayya.. "Aunty na d'auki alqawarin zanyi duk abinda kike cemin.. idan dai bazai sab'awa Allah da manzansa ba. "Yauwa my sister yanxu kiyi wanka bara na kawo miki kayan bacci kisa dan kifi samun nutsuwa. YAWO ma tayi. kiyima yaran Sannan ku kwanta. Na tabbatar zakufi samun nutsuwa... "Toh MUSLEEMA tace mata. Nan NUFAISAT taje ta kawo mata kayan bacci. Kana tayi musu sallama takoma shashin mijinta. Lokacin bata samesa ba. Da alama yayi shashin TAUDHAT ne Eh yana falan TAUDHAT dan duba lafiyarsu kamar yanda yasaba idan ya dawo yake shiga d'akin wacce bata da girki dashi dan duba lafiyarta. Haneepha na jikinsa tana murnar ganinsa yake ba TAUDHAT labarin su MUSLEEMAT. Da yanda ya d'auki aniyar temakwansu. Gumi ne yaketa tsattsafoma TAUDHAT. Hankalinta ya bala'in tashi da labarin da yake bata. Duk sai tanemi nutsuwarta tarasa... "Wai meyake damunki ne naga kikata had'a gumi. Da alamama kamar kina cikin damuwa. A furgice ta kallesa da gyara nutsuwarta tace da shi.. "Bansan me zance maka ba. Haka kawai naji hankalina bai kwanta dasu ba. D'aga Haneepha yayi daga kan cinyarsa ya zaunar da ita kan kujera sannan ya qarasa gaban TAUDHAT da kama hannunta yace.... "Kar wani abu ya dameki. Hankalina ya kwanta dasu dari bisa dari. Dan haka kema ina san hankalinki ya kwanta dasu. Dan bazasu cutar miki da miji da qawarki da y'arki ba.😀 Murmushi tayi mai da d'agamai kai. Ahankali ya sakar mata kiss a goshi da sakin hannunta ya sakarma Haneepha ma sannan yabar d'akin.. Ai yana futta TAUDHAT tatashi a rikice takira malamin nata da gaya masa komai.. Sannan taqara da cewa "Pls kasan yanda zakayi yanxu kajefemin bakinsu dukkansu. Tayanda bazasu tab'a gayama wani komai ba. Sannan ina san ganin bayan yaran. Dan Wallahi idan suka taso tawa taqare. Pls kayi wani abu akai yanxu.... "To ki kwantar da hankalinki kibani minti biyar zan kiraki yanxu.. "Toh tace mai da kashe wayar. Tana me safa da marwa cikin matsananciyar damuwam. Canko bayan ya gama binciken nasa nan ya kirata dace mata.. "Gaskiya akwai matsala TAUDHAT.. Dan ainiyin fulanin daji nesu. Ba wani abu dani zan iya yimusu. Saboda ita kakar tata tarigada ta dafa kanta da maganin tsari kala kala. Hakama tajiqa jikar tata da maganin bana wasa ba. Sannan suma yaran tunda sukazo duniya ta wankesu da ganyayyakinsu irin na fulani Wanda duk maseefar me jifa da matsafi da maye bai isa yaci yaran nan ba. Sannan ita kanta uwar tasu yarinyar tana da ibada.. Sosai takema yaran nata dan Allah ya kare mata su. Agaskiya TAUDHAT kifita daga harkar muta nan nan. Dan duk inda zakije bazaki samu galaba akansu ba. Iya gaskiyar kenan dazan gaya miki itace tunda kikaga basu gayamai gaskiyar lamarin ba. To kibarsu ahakan. Ki dinga yimusu kirsa da kisisina yanda zasubar gidan wannan itace mafuta agareki... "Kaga da Allah malam dakata. Naji duk abinda kace. Harsai yaushe zanta zama da maqiyana kana gayamin nabarsu bazan samu nasara akansu ba. To bari kaji... zanje wajan bokan dayayi sanadin aurena da Adams yayimin maganin wannan matsalar "Ba wajen boka ba. Kowajen wa zakije bazaki samu nasara akansu ba. Kuma na gaya miki iya gaskiyar ne kasancewarki uwar y'ata bani san kije kisha wahala. Tsaki TAUDHAT taja da kashe wayar tayi jifa da ita. Ranta abala'in b'ace. Haneepha na kallanta tace.. "Momy malaminmu na islamiya yace babu kyau zuwa gun boka.. Galla mata wata muguwar harara TAUDHAT tayi da cewa. "Dan ubanki angaya miki gunsa zanje. Shuru Haneepha tayi. (Kar me karatu ya manta Haneepha bata wucce shekara shidda ba idan ma takai. Amma take gayama uwar tata hakan.) Shiko ADAMS rungume matarsa NUFAISAT yayi sukaji dad'insu abinsu. Sam basu da wata matsala. Washe gari da safe NUFAISAT taje suka gaisa dasu YAWO. MUSLEEMA tace zata raka NUFAISAT kitchen tatayata aiki. Aiko NUFAISAT taji dad'in sake irinna MUSLEEMA. Dan haka tare suka had'a kayan breakfast d'in. Taba MUSLEEMA nasun takai nasu dining tajera ita da gwanin nata. Suna breakfast d'in ne ta kalli ADAMS da cewa. "Saidai kamin afuwa. Dan MUSLEEMA tatayani had'a wannan breakfast d'in. Fatan kayafemin. "Nayafe miki matata. Kuma dama tunda kika bata matsayin qanwa agarki dole nayi hakuri da duk wani abu dazan samu daga gareki naci Dan nasan dole tatemaka miki. "Nagode mijina. Dafatan komai yayi zamzam. "Sosai mah. Dan karna yaba ne ki zargeni shiyasa yin shuru. Dannaga lokacin da kuke aikin tare. "Yabi abinka ai qanwa ce agareni. Murmushi yayi mata da shafar gefan fuskarta.. "Ina sanki da yawa matata "Gaskiya da fahimtar juna ce takaimu har iyanxu a SO Mijina. Nima ina san ka.😍 Koda yaje gun TAUDHAT dansu gaisa har a lokacin bata tare da nutsuwarta. Nanma sanda ya qara tabbatar mata Bafa wani matsala mutanan arziqi ne. Sannan ya nufi gunsu MUSLEEMAT d'in... Bayan sun gaisa da Yawo Ahankali ya kalli MUSLEEMA ya amsa gaisuwar da take masa a shagwab'e. shagwab'ar tata tana shigansa da zafi fah😒.. Da sanyin jiki yake cema YAWO "Zan turo salim qanina yakai yaran nan skull da islamiya anjima. dan bani san ganin yara haka ba karatu. Godiya yawo tamai sosai sannan ya kalli MUSLEEMA tasakar mai murmushi shima ya mayar mata kana ya ficce daga d'akin zuwa motarsa. Nan masu tsaran nasa sukayi gaba dashi.. Bayan NUFAISAT tagama komai na gyaran d'akinta saka Asiya tayi takira mata MUSLEEMA. Bayan MUSLEEMAN tazo janta wani d'aki tayi suka zauna takira sunanta a nutse. Nan MUSLEEMA ta kalleta da amsawa. "Ina san kigayamin ainiyin labarinku. Dan zuciyata taqi gamsuwa da labarin da kakarki YAWO taba ADAMS akanku. Idan har kina san zama dani na amana to kiban labarinku na gaskiya.. Shuru MUSLEEMA tayi mata. Ita dai tun ganin farko taji tana san NUFAISAT d'in. Kuma taji aranta zata iya gaya mata komai na rayuwarta.... Qara kallan NUFAISAT d'in tayi da fashewa da kuka tace.. "Aunty kiyi hak'uri dajin labarinmu. Komai gaskiya YAWO tagayama Adams. Kawai dai ta boye wasu abubuwan ne. "MUSLEEMA ina san sanin labarinku. Bazan iya hak'uri dashi ba.. Sanda MUSLEEMA tayi kukanta san ranta NUFAISAT bata hanata ba. Sannan takwashe labarinsu kaf ba abinda tarage tagayama NUFAISAT d'in.. Sannan taqara ta cewa.. "AUNTY MIJINKI ADAMS SHINE MIJINA UBAN ƳAƳANA. Wallahi Aunty ina matuqar laba'in sanshi kiyi hak'uri.. "Innalillahiwainna'ilaihirraji'un. Shine abinda NUFAISAT tace kanta na tsarawa. Nan tatashi taji jiri na ibanta. Ai MUSLEEMA bata ankareba sai ganin NUFAISAT tayi ta zube qasa sumammiya.. Nan hankalin MUSLEEMA ya tashi. Gashi ba abin takira yawo YAWO ba. YAWO tasan tagayama NUFAISAT d'in komai. Dan haka kitchen ta nufa ta ibo ruwa tadinga yayyafama NUFAISAT har Allah yasa NUFAISAT farfad'o.. Nan NUFAISAT taja numfashi duk da haka kanta bai dena Sara mata ba.. Nan hawaye ya shiga zubo mata. MUSLEEMA da itama hawayen takeyi takama hannun NUFAISAT d'in tace.. "dan Allah Aunty karki nunama YAWO na gaya miki komai dan Allah.. Murmushi NUFAISAT tayi dace mata.. "Karki damu MUSLEEMAT. Albarkacin qaunar da kika nunama ADAMS zan sadaki dashi cikin hikima. zakiji dad'insa fiye da yanda kikaji a rayuwar da kukayi a Ruga.. Saidai kimin alqawarin zaki kiresa amana. Kiza kik'eni amana. "Aunty wallahi bani da mugun hali. Auntyna zakiji dad'ina. Aunty kece nake san kiriqeni amana. Aunty idan kin rikeni kamar qanwa zanji dad'in rayuwata. Bazanyi rashin uwa ba. Bazanyi rashi a maraici ba. Rungumarta NUFAISAT tayi na d'an wani lokaci. Kana tace mata.. "Yanxu zaki fara sabuwar rayuwa. Zan fara gyaraki kafin nagayama Adams d'in komai. Idan kuma YAWO ta rigani shekenan kinga saidai kawai a gyara muku auranku. "Aunty ina sanki Wallahi... "Nima ina sanki Qanwata. Sanda suka qara fahimtar juna sannan MUSLEEMA taje shashinsu. NUFAISAT tayi murmushi da sakawa aranta zata riqe MUSLEEMA tsakaninta da Allah. Koda kuwa zata cutar da ita. Dan santa na hak'ik'a ne yayi ram da zuciyarta... Follow me on wattpad @Rahamatnalele Sadaukar da wannan shafi gareki ummu bashir nagode sosai da qaunar da kikemin cikinmu MARUBUTA. Ina sanki daji dake.. luv u 2 sister Nagaida y'an hannuna🙏🏻 [7/31, 1:04 AM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018 Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ *© REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄* ☆We the best ☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R *Yanxu zaku iya following nawa a wattpad.* @Rahamanalele ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 26☆ Ga TAUDHAT ko MUSLEEMA na komawa shashinsu. tafito daga part nata dayi nasu MUSLEEMAN.. Da mutuntawa YAWO take gaishe tana amsa mata daqer kamar ansata dole. Dama ita MUSLEEMA kallan farko datama TAUDHAT d'in nan tagane itace matar Adams d'in ta biyu.. Da izgilanci TAUDHAT take qare musu kallo musamman MUSLEEMA da yaranta. Sai zuwa can taja tsaki tace. "Dama kune y'an aikin da Adams ya kawo jiya. Murmushin yaqe YAWO tayi mata da cewa.. "Eh mune y'ar nan. Kina buqatar muyi miki wani abu ne.. "Ba Sunana y'ar nan ba Baba. Kamar yanda kukazo aiki da Hajjiya ya dace kikirani. "Toh Hajjiya kiyi hak'uri. Tsaki taqara jah. Kana tace. "Amma wannan shine karanku na farko azuwa aiki ko. Shuru YAWO tayi mata. Saiko MUSLEEM ta karb'e maganar cikin sauri da cewa. "Eh wannan shine karanmu na farko. Allah yasa ba lefi mukayima Aunty NUFAISAT matar gidan ba... Harara TAUDHAT ta galla ma MUSLEEMAN da faɗin. "Ce miki akayi NUFAISAT ita kad'aice matar gidan. Murmushi MUSLEEMA tayi mata da cewa. "Ai mun d'auka ita kad'ai ce matar gidan. "Toh mu biyu ne. Ita NUFAISAT ni kuma TAUDHAT.. Dan haka daga gobe zaku fara yimin aiki.. YAWO tace.. "Toh Allah ya kaimu darai da lafiya... Tsaki taqara ja batare datace komai ba ta ficce daga d'akin zuciyar cike da baqin cikin ganin yaran MUSLEEMA. Nan tahau safa da marwa afalanta tana cewa.. "Shegun yara sai idanuwa kwala kwala kamar na mayu. Ga fari kamar y'an shan jini. Ga kyau kamar d'awisu.🤣 Haka tadinga sambatunta kamar tab'abb'iya. daga qarshe dai tayanke shawarar zuwa wajen bokanta kan adawo da Haneepha daga skull.. Ko qaryar data saba shararama Adams idan zata wajen malaminta batayi ba tazari gyale da iban kud'i tahad'a da kin motarta sai daji.. Tana fitta ko wani saurayi yazo ya kwashi su Khalit yakaisu skull d'in da Haneepha take zuwa. Dake had'e da madarasa ce skull d'in nan da nan komai ya kammala na zuwa skull d'in su Khalil d'in. Dan nan take skull d'in tabayar da uniform nasu har na madarasa ad'inka musu. Nan saurayin ya dawo dasu daba YAWO tabbacin gobe idan yazo d'aukar Haneepha zai tawo da uniform nasu asa musu ya tafi dasu. Dan agoben akesan sufara zuwa. Godiya YAWO da MUSLEEMA sukamai.. NUFAISAT tayanke shawarar gobe zataje kasuwa da MUSLEEMA dan tafara aiwatar da udirinta akanta. Nan taqara duba account nata taga tana da wadatattun kud'i sai tayi hamdala ga Allah tana rokwansa daya bata damar aiwatar da komai cikin nasara. Sannan yacire mata jin kishi da baqin hali ko hassada. Kana tashafa addu'arta dajin wani shauqi me saka zuciyata cikin sukuni.. TAUDHAT ko tasamu bokan nata yana da baqi sosai. Amma haka ta fad'a turakar tashi kuma ya saurareta dan shima dama yayi missing nata.. Sanda ya gama surkullansa ya d'auko wani magani ya bata yace tasama MUSLEEMA a abinci ita da yaranta. Yana tabbatar mata idan sukaci nan zasubi duniya ba Wanda zai qara ganinsu bare ya kawo labarinsu. Aiko nan TAUDHAT ta karb'a da bashi kud'i yace sam tariqe kud'inta yafi buqatar jikinta akan kud'in.. Nan dai takwanta yayi yanda yaga dama da ita kusan awanni. Asannan ne yabarta tasamu dawowa gida.. Ai tana dawowa gida tadafa had'add'iyar jalof da kifi ta barbad'e maganin aciki. Da nufin takaima su MUSLEEMA.. Saidai kan takai musu sanda takira malaminta da farin ciki take cewa... "Toh naje gun bokan nawa har yabani magani nasama su MUSLEEMAN a abinci yace suna ci zasubi duniya kuma ba Wanda zaisan inda suke har qarshen rayuwa. Jan numfashi malamin nata yayi da cewa. "Dama nasan sai kinje wajensa. Bazaki tab'a hak'uri ba. Toh wallahi nayi bincike basu bane zasubi duniya kece zakibi duniya. Dan haka ina shawartarki kafin ki aiwatar da udirin kije ki nemi yafiyar mahaifiyarki dan Wannan asirin da kika mata ya karye d'azu d'azun nan ajikinta. Sakamakwan temakwan da maman kishiyarki NUFAISAT tabata. Dan taje tagaya mata matsalarta tsaf. Ita kuma tasa wani malami ya b'ata abinda kika mata shekara da shekaru. Yanxun nan naga hakan nake qoqarin kiranki sai gashi kinkirani. Sannan ki kawomin yata. Karsai kinbi duniyar nazo karb'a yazama hajadi.... "Me kake san cewa. Kana nufin idan sunci abincin ni zambi duniya su suzauna saboda nice naci abincin.. "Ina nufin kome zaki musu bazai kamasu ba. Idan kuma kika matsa komai dawowa kanki zaiyi. "Ban yarda ba. Dan ina ji ajikina nice dacin galaba akansu. "Haba TAUDHAT. Ya kamata ki gane qaunar ki nake har cikin zuciyata. Wane malami ne yake gayama miki gaskiya tsagwaranta imba niba. Wallahi abin dana gaya miki idan har baki bishi ahankaliba haukacewa zakiyi.. "Haukacewa. Haukacewafa kace. Waini d'in kake cema zan haukace. To canja tunaninka. Dan ba wani asirin dazan yima wani ko wata dazai dawo kaina har nayi hauka. "Ba mamaki qila akan MUSLEEMA da yaranta qarshenki yake san zuwa TAUDHAT.... Saboda haka kiyi duk abinda kike sanyi kiyi na barki lafiya. Amma kafin nan kikawomin y'ata da hannunki dan Wallahi yanda banyi auran nan ba ko sama da qasa zata had'e saina karb'i yata agun mijinki Adams. Danko gawarki nagani saiya bani y'ata b'cos kinfi kowa sanin yanda nake qaunarta. Shiyasa nake qara jaddada miki daki kawomin y'ata tun da wuri.... "Da Allah dakata Isma'in. Kama dena batu akan Haneepha. Dan Haneepha y'ace ga ADAMS. Kaima kasan muslinci ya bashi ita... "Wato TAUDHAT baki sanni bane. "Zan sanka tunda ina darai da lafiya.. Tana faɗin hakan takashe wayarta da mamakin yanda asirin da tama mamanta ya qarye.. Ahankali ta d'auki abincin tanufi shashinsu MUSLEEMA. Lokacin NUFAISAT na tare dasu. Tana nunama MUSLEEMA yanda ake dressing d'in kayan yara. Da nutsuwa TAUDHAT ta'ajiye musu abincin agefe ta harari inda NUFAISAT d'in take tace da Yawo. "Gashi abinci nakawo muku kuci kuji irin nawa girkin.. Da murmushi yawo tace.. "Toh angode Allah ya saka.. Har takai ƙofar fitta tajuyo da qara kallan YAWO tace.. "Kuci fa. "Insha Allah zamuci yanxu kuwa. YAWO taqara bata amsa da kulawa Sanda NUFAISAT tatabbtar tatafi Sannan tace da MUSLEEMA. "Kar kuci kuzubar a shara. Badan ina zarginta ba. Saidan hankalina bai kwanta da abincin ba.. Ba musu MUSLEEMA tajuye a baqar leda kana taje tasaka a sharar...😁 ADAMS ko daya tashi daga office gidansu ya nufa. Kasancewar jiya baisamu yaje ba. Anan yake qara gayama Dadynsa ya kwantar da hankalinsa yayaba da hankalinsu YAWO. Alamu sun nuna mutanan arziqi ne. Sanda ADAMS ya tabbatar Dadyn nasa ya gamsu sannan yaje gun Amminsa itama ya kwashe labarin komai ya gaya mata. Da jin daɗin temakwan da yayi musu Ammin nasa ta kallesa da cewa.. "Gayamin sunansu. "Ita dai yarinyar sunanta MUSLEEMAT sai kakarta YAWO. Sai yaran MUSLEEMAN Khalit da Khalil & Rahma.. Shuru Ammin tayi cikin tunani. Can taqara cewa. "Kuma kace fulani ne ko. "Murmushi yayi da bata amsa... "Eh fulani ne. Saima kinga yaran ita MUSLEEMAT d'in suna kama dani sosai. Wallahi saikace nine ubansu. Bara naje gida dare yayi kuma gashi ina jin yunwa. Jan numfashi Ammin tayi da cewa.. "Kona zubo maka abinci ne. "aa barshi. Karki had'ani fad'a da ita😄 Murmushi tayi da cewa.. "Wacece acikinsu. Tashi yayi da sakar mata kiss ahannu yace. "NUFAISAT.. "Wato har tayi nesa yanxu a girki dazaka k'i cin nawa ko.😀 "aa wasa nake miki Ammina. Kingama na zauna zubomin naci kawai😃. Murmushi tayi da cewa. "Nagodema Allah data kware yanxu. Allah ya qara had'e kanku maza jeka bana san kana yawo da yunwa. Murmushin shima yayi mata da sallama ya fitta daga falan nata suka d'auki hanyar gida.. Suna isowa shashin su MUSLEEMAT yayi. Nan yaga MUSLEEMAN da Rahma suna kallo. Da alama YAWO da su Khalit sunyi bacci. Ahankali takemai sannu da zuwa da gayamai YAWO dasu Khalit sunyi bacci. Dajin dad'in yanda tasake da gidan nasa yayi mata sallama daniyar ficcewa daga falan.. Ai cikin sauri tatuna tana san yimai godiya dan haka cikin sanyin murya tace... "Nagode da cika maganarka da kayi d'azu da safe YAYANA. Juyowa yayi da kallanta ya d'aga mata gira alamar me take nufi.. Ganin hakan sai tacigaba da cewa.. Ina nufin wajen sakasu amakaranta dakayi. Murmushi yayi da harararta yace... "Idan kika qaramin godiya akan wani abu dazan miki ko nayima yarana saina sab'a miki. Cikin shagwab'a tace.. "Afuwa YAYANA. Wallahi na tuba bazan sake ba. "Idan kika sake fah. Shuru tamai. Sai yaci gaba da cewa.. Ke da kanki nakesan kigayamin wane hukunci ne yadace dake. Jan numfashi tayi da cewa "Saika dena kulani. "Shikenan. Yanxu saikin sake ki gani a kwaryarki. Gud9t Yana faɗin hakan ya ficce daga falan... _Wallahi Yayana ina MASEEFAR SONKA_ tafad'i hakan aranta tare da tashi takulle musu kofa... Ya samu NUFAISAT kamar yanda yasaba ganinta cikin tsafta. Bayan sunyima junansu wlcm part na TAUDHAT ya nufa. Ba lefi yaga tasake ba kamar yanda yabarta da safe ba. Anan yasakarma Haneepha kiss ya koma shashinsa yayi wanka dama NUFAISAT tashirya masa komai na abinda zaici. Dan haka yana yin sallah yahau cin abincinsa. Anan NUFAISAT take gayamai gobe zataje kasuwa da MUSLEEMA.. TAUDHAT har kwanciyar bacci taji shuru su MUSLEEMA na tare da lafiya. Dan bala'i haka takasa nutsuwa qarfe goma sha d'aya da rabi taje ta bugama su MUSLEEMA kofa. Nan taga MUSLEEMA ce ma tabud'e mata kofar dan har alokacin basuyi bacci ba ita da rahama.. A rikicewa take tambayar MUSLEEMA waiko sunci abincin data basu d'azu. Nan ko MUSLEEMA ta bata tabbacin sunci har suna Santi.. Da mamaki ta dawo d'akinta tana tunanin ita dai tunda take da bokan nata bai tab'a bata abu tayi taga sab'anin abinda yace mata ba. Nan alokacin takira malaminta tace bataga komai daya faru dasu MUSLEEMAT ba. Kodai zancenshi haka yake. Murmushi yayi dace mata TAUDHAT kinqi gane gaskiya nagaya miki. Dan duk inda zaki saidai kawai suci kud'inki. Shuru tayi bayan ta kashe wayar. Tunani tashiga kodai taqara komawa wajen bokan natane. Sai wata zuciyar tace mata tadai d'an jinkirta taga gudun ruwan lamarin Washe gari haka MUSLEEMA taqara taya NUFAISAT had'a breakfast.. bayan ADAMS ya fitta NUFAISAT saurin gama shirya d'akinta tayi. Saita tasa MUSLEEMAT agaba sukaje kasuwa inda tazab'an mata kayan make-up dasu kayan gyara jiki irin na mata kala kala masu kyau. kana suka nufi wajen atamfofi fashion masu kyau tasai mata kusan kala talatin tare da su les material. Daga nan wajen telanta suka wucce ya gwada MUSLEEMA tace mai tana san kayan dukka su kammala nan da sati d'aya. Pls ya rabama yaransa aikin dan suyi sauri. Nan ya tabbatar mata insha Allah zai kawo mata kayan bazai qara ko kwana d'aya ba. Nanko NUFAISAT tabasa kud'in d'inkinsa cif bata rage masa komai ba suka dawo gida. Godiya ba irin Wanda MUSLEEMA batama NUFAISAT ba. Ganin akwalla kud'in data kashe mata yau zaikai dubu d'ari biyu. Duk da cewa dama kana kallan NUFAISAT kasan taci tatada kai amma abin a jinjina mata ne wannan siyayyar datai mata ai.. Haka yawo ma tadinga gode mata. Sanda NUFAISAT tanuna musu b'acin ranta kana suka hak'ura suka dena yimata godiyar.. Alokacin NUFAISAT d'in tafara koyama MUSLEEMA yanda ake make-up na zamani. Aiko dake kwakwalwar MUSLEEMAN abud'e take nan tafara gane komai.. Zuciyar TAUDHAT ko tayanke mata shawara kan taqara komawa wajen bokan nata. Dan hausawa nacewa kanufi cimma burinka da zafi zafi yafi kabishi da sanyi sanyi .. Still yau d'inma haka taficcewarta batare data gayama Adams ba.. Saidai koda taje gun bokan shima bata tabbaci yayi kan tayi hak'uri Kawai da lamarin. Idan kuma tana ganin bazata iya hak'urin da lamarin ba. Toh ta lura da lokacin da MUSLEEMA take al'ada. Tasan duk yanda zatayi takawo masa tsumman da take amfani dashi alokacin kota kawo masa wani dai abu dayake da jinin al'adar tata.. Da damuwa TAUDHAT tadawo gida.. Tana saqa tataya zata gane MUSLEEMA tana al'ada bare takawoma bokan abinda ya shaifi jinin nata.. Dan dai tayanke shawarar zata sakama MUSLEEMAN ido sosai har tacinma borinta.. _________ Bayan sati biyu zanso me karatu yaga yanda MUSLEEMA tacanja. Tacanja kamar ba MUSLEEMAN ruga ba.. Dan mayukan da NUFAISAT tabata dan tadinga amfani dasu sun goge fatarta sunmai da ita gwanin ban sha'awa. Dama yanxu take kan cikowa dan haka data fara samun gyara dacin abinci me gida jiki nan taqara murmurewa. Haka yaranta ma gwanin ban sha'awa. ADAMS san yaran yake kamar me. Wannan ma ya qara baqanta ran TAUDHAU. Musamman yanda taga NUFAISAT tana zagewa akan lamarinsu. Yanda ta maida su y'antattu kamar tasan yaran ADAMS d'in ne.. Wannan abu na k'ona ran TAUDHAU matuqa.. (Batasan NUFAISAT tasan komai fiye da saninta ba😂) Dake yau LAHADI ne ADAMS yana dawowa gida da wurri. Dan haka sai NUFAISAT tasa MUSLEEMA tayi wanka tayi makeup. bayan tafito daga wankan wasu riga da siket na atamfa NUFAISAT ta d'auko mata. Kayan yana d'aya daga cikin wanda tad'inka mata. Ba qaramin karb'arta atamfar tayi ba. Dan ita kantama NUFAISAT santa taji sha'awarta. Nan tabata turare me sanyin qamshi d'aya daga cikin way'anda take sawa. Nan MUSLEEMA ta saka... NUFAISAT takalleta da nutsuwa tace.. "Yauwa yanxu bazai wcce minti goma ba zai shigo. dan haka ina buqar kisan duk yanda zakiyi ya ganki. Na tabbatar zaiji wani abu aransa. pls kifa nutsu dakyau dan bani san asamu matsala. Murmushi MUSLEEMA tayi dace mata. "Karki damu Auntyna. Insha Allah komai da kika tsaramin yana nan a kwakwalwata.. "Masha Allah. Yanxu ni zanyi wajen shaqatawar gidan nan. Nasan komai zai faru akan idona. Danta k'ofar baya zai shigo. Dan Allah ki ankare dan Adams daban yake acikin maza. Murmushi MUSLEEMA taqara yimata da d'aga mata kai alamar taji.. Aiko NUFAISAT na barin wajen saiga Adams ya dawo.. Da nutsuwa ya fitto daga motarsa yana mejin dad'in yanda NUFAISAT ce dashi. Shi kawai yana rayuwa da TAUDHAT ne badan tana gamsar dashi abubuwa da dama na rayuwar aure ba. Dan nesa ba kusa ba NUFAISAT tafita sanin abubuwan da suka dace.. Yana wannan tunanin ne yaci karo da MUSLEEMA.. "Subhanallah.. Shine abinda yace. Dan sunbigi goshin juna. Ahankali cikin sanyayyiyar murya MUSLEEMA tace.. "Dan Allah kayi hak'uri YAYANA bansan kana tawowa ba daban tawo gabaki d'aya ba.. Lumshe ido ADAMS yayi. Shifa ya lura kwana biyun nan MUSLEEMA na canjawa. Dan fatarta ta goge ga wani kyau da take qarawa. Sannan uwa uba Shifa yana jin wani iri sosai idan magana tana shiga tsakaninshi da ita Yau kuma gashi yaji qamshin d'aya daga cikin turaran da NUFAISAT take sawa ajikinta.. Wai me yake faruwa ne.. Ya tambayi kansa.. Bud'e idansa yayi ahankali ya sauke akan dara daran idanunta kamar madara yana me cigaba da qare mata kallo daga har qasa. Tayi mai kyau sosai ga gashinta yasha gyara. Wallahi jiyayi kamar ya rungumeta.. Cikin wani hali yace. "Na hak'ura.. MUSLEEMA najin hakan taratsa tagefansa ta wucce. Saiko yabi bayanta da kallo cikin mamakin had'uwar datayi... "INA SANTA.... Ya fad'i hakan abayyane ba tare dayasan ya fad'i ba... Yana juyowa danci gaba da tafiyarsa kawai sai yaga NUFAISAT tsaye!!! nannad'e da hannu tana kallansa. Nan yahau kame kame yana cewa.. "Umm amm dama... Kasa cewa komai yayi dan haka sai kawai ya nemi wucce NUFAISAT d'in dan Wallahi wata kunyarta ce ta bala'in kamasa..🙈 Ainan cikin sauri NUFAISAT tasha gaban sa da cewa. "ɗan jini kaɗan mana malam.. Tsayawa yayi batare daya kalleta ba. Ganin hakan saitaci gaba da cewa. Kace kana santa ko.. Kallanta yayi ahankali da girgiza mata kai alamar aa... Murmushin yaqe tayi mai daci gaba da cewa.. Hmm. Kasandai y'ar d'akina ce. Dan haka yanxu saika bada dubu d'ari saboda wannan furucin da kayi... Cikin marairaicewa ya had'a hannuwansa biyu 👏🏻 alamar tayi hak'uri bazai sake ba. Tab'e baki tayi dacigaba da cewa.. Bayan kabada kud'in daga baya sai muyi ciniki kawai nabaka auranta. Cije bakinsa yayi cikin matuqar jin kunyar yace.. "Zan bada. Amman kafin nan muje falanki kiji wani abu. Gyad'a masa kai tayi alamar suje... Bayan sunje sakata yayi kan kujera da durqusawa gabanta ya kama dukkanin hannayenta yace.. "My luv wallahi akwai matsala babba.. Dan tunda nayima yarinyar nan kallan farko naji wani abu ya minsini zuciyata... Magana ta gaskiya zuciyata na tsumuwa idan magana tashiga tsakanina da ita.. Gashi ita matar aure ce. Bai dace naji hakan akanta ba... Kawai ni yanxu na yanke shawarar zan kaisu gidansu momy dan kare kaina ga fad'awa ga halaka.. Saboda yanxu haka da naji qamshin wani turaranki ajikinta jinayi kamar na rungumeta.. Waro ido NUFAISAT tayi😳.. Cikin sauri yacigaba da cewa.. Wallahi gaskiya na gaya miki dan kinsan ban iya yimiki qarya ba.🙂 Shuru NUFAISAT tayi tana tunanin tagaya masa gaskiya ne yanxu kodai tabari sai nan gaba. Idan tagaya masa yanxu gaskiya tatemakesa da ita kanta dan bazai kwashe mata su ba. Idan kuma taqi gaya masa tasan tunda ya furta zai kaisu wajen su Dady to saiya kaisu. Dan haka Ahankali taqara rike hannunsa fiye da yanda shi ya riqe matan tace.. "Ka godema Allah ya Mijina daya had'aka dasu MUSLEEMAT har yabaka ikwan temakwansu kakawosu cikin gidanka. Kasan da cewa MUSLEEMA matarka ce ya Mijina Kasan da cewa yaran MUSLEEMA yaranka ne ya mijina Kasan da cewa ganinka da MUSLEEMA tayi shiyasata sumewa har katemaketa Kasan da cewa sanadin sanka da qaunarka shine silar kamuwa da ciwan zuciyarta Kasan da cewa labarin da YAWO tad'an gutsira maka da cewa wani ne ba wanin bane kaine wanda tunaninka ya d'auke har tabaka auran MUSLEEMAN.. Cikin zubar hawaye NUFAISAT takwashe komai ta gayama ADAMS kamar yanda MUSLEEMA tagaya mata.. Shuru ADAMS yayi saboda jin yanda kansa yake juyama.. Ahankali yasaki hannun NUFAISAT ya tashi da komawa kan kujera hankalinsa tashe. Lalle Allah shine Allah. Bai tab'a tunanin hakan zata faru dashi arayuwa ba. Wai ya rayu a ruga. Sannan har kiwo yayi. Sannan yayi Aure har da raban y'ay'a uku... sannan tunaninsa ya dawo baisan yayi hakan ba. Wannan kad'ai ya isa mutum ishara... Sosai yayi nisa cikin tunani. sam baiji abinda NUFAISAT take cemai ba. Naya ya kwantar da hankakinsa.. Sanda tatab'a shi da miqa masa madara me sanyi sannan ya dawo daga duniyar tunanin daya fad'a.. Jiki asanyaye ya karb'i madarar yasha kad'an da tashi da niyarsa nasan ficcewa.. Shan gabansa NUFAISAT tayi da riqe qugu tayimai fari da ido tace dashi.. "Sam bazaka fitta ba saika gayamin me zuciyarka tashirya maka. Dan bamuyi da MUSLEEMA zan gayama kowa ba.. Murmushi yayi da rungumarta yace... "Kinyi kyau sosai matata.. Sannan kinyi arayuwa.. "Ba wannan na tambayeka ba. Kawai kabani amsata. "Dama part nawa zanje nayi wanka daga nan saina fara shawarar da zuciyar tawa.. "Nifa ban yarda ba. Kawai ka gayamin.. "Wallahi NUFAISAT kina da futuna. To dama zuwa zanyi na kwashe yaran naje asibiti ayimin gwajin jininsu da nawa. Idan naqara tabbatarwa saina Nazo wajen YAWO na tuhumeta kan meyasa tab'oye min komai tunda farko... Murmushi NUFAISAT tayi da kallansa tana cewa.. "Gud... naji dad'i sosai. Saidai yau lahadi baku zuwa asibiti kai da doctor Aryan. "Zan kirasa yanxu muhad'u ai. "Bara naje na d'auko gyalena to saina rakaka.. Jan hancinta yayi cikin matuqar santa da qaunarta. Yace "idan bake bazan iya rayuwa ba. Kiss tasakar mai da cewa. "Wayace maka nima idan bakai zan iya rayuwa... Murmushi ya sakar mata.. Bayan tad'auko gyalan nata direct shashin su MUSLEEMA sukayi... ADAMS ya qara kallan MUSLEEMA mamaki cike tam azuciyarsa wai ita d'in matarsa ce.. "Kuzo muje kumana rakiyar unguwa.. NUFAISAT ta katse masa tunani da faɗin hakan gasu Khalit.. Murmushi ya sakarma YAWO yace.. "Unguwa zasu rakamu. Itama YAWON murmushin ta mayarmai da cewa... "Toh kudawo lafiya... Har sun shiga mota saiga Haneepha tafito da sauri daga part d'insu tana cewa.. "Dady ina zaku nima zan biku.. Murmushi yayi mata dayima masu tsaransa nuni dasu bud'e mata motar itama ta shiga. Aiko tana shiga Adams yaja motar dan yacema masu tsaran nasa subari basai sunyimai rakiya ba yanxu zai dawo.. Tun ahanya ko yakira abokinsa doctor Aryan yabashi tak'aitaccen labarin dacigaba da cemai pls su had'u yanxu a asibiti ya gwada mai jininsa dana yaran.... Jan numfashi doctor Aryan yayi da cemai ai yanama asibitin tun d'azu sakamakwan matarsa tatashi da naquda tun da safe. Dan haka ya qaraso kawai zai samesa.. Bayan sunkai Nan Doctor Aryan ya ibi jininsu Khalit da Khalil da Rahma dana ADAMS yahau binkice. Masha Allah bincike ya nuna Khalit Khalil Rahma ƴaƴan ADAMS ne..😀 Nan ADAMS yaja numfashi da rungumarsu kamar zai cinyesu haka yadinga sakar masu kiss.. Cikin tausayawa NUFAISAT ta goge hawaye. Doctor Aryan ko murmushi yayi da bama ADAMS hannu yace.. "Na tayaka murna d'an uwa. Dan samun uku a lokaci d'aya ba qaramin abu bane.... Kan ADAMS ya bashi amsa saijin kukan Haneepha kawai sukayi. Tana cewa itama ayi mata abunda akayima su Khalit dan Dadynta yayi mata kiss ya rungumeta itama..😟 Dariya sukayi dukkansu da rarrashinta kan bakomai aka musu ba tayi hak'uri basai anyi mata ba. Saidai fur Haneepha taqi yarda saima qara volume na kukan nata da tayi..😳 Sam ADAMS baya san kukan Haneepha Dan haka sai kawai ya biye mata yace doctor Aryan ya ibi nata jinin ya gwada da nasan. Aiko Cikin rikicewa NUFAISAT ta goge gumin daya wanke mata fuskar tace... "Haba my luv kabarta basai ammata ba. Ai Haneepha najin hakan taqara tab'arb'arewa da kukan... NUFAISAT taja numfashi haka kawai taji gabanta na fad'uwa. Saboda tasan idan doctor Aryan yagwada jinin Haneepha dana ADAMS gaskiya akwai matsala.. 😒 Murmushi ADAMS yayi dace mata.. Karki damu my luv. bari yayi mata kinsan Haneepha da rikice idan ba'a mata ba har dare kuka zatata mana yau.. Gyad'a masa kai NUFAISAT tayi dacigaba da goge gumi.. Haka tana ji tana gani doctor Aryan ya ibi jinin Haneepha ba abin ta hanasa ba.. Shi kansa doctor Aryan ya girgiza da ganin sakamakwan da binciken ya nuna masa na Haneepha ba jinin ADAMS bace😊.. Dan haka Sanda yayi gwajin sau uku yaga duk abu d'aya sakamakwan yake basa. Sannan ya hak'ura da fitowa daga wajen gwajin jikinsa a sanyaye ya miqama Adams takaddar gwajin nasa da Haneephan.. Tunda Adams ya fahimci Haneepha ba y'arsa bace ya zuba Haneephan ido zuciyarsa na bugawa. Canko sai ganinsa a qasa sukayi.. NUFAISAT da doctor Aryan sukayi kansa suna masu kiran sunansa.. Bashi da damar amsawa dan yarigada ya sume.. Minti goma tsakani Adams ya farfad'o da kallan NUFAISAT yace... "Wannan ma kina da sani akai.. Saurin girgiza masa kai tayi alamar aa hawaye na zubo mata tace.... "Banda da sani akan wannan sam Shima hawayen ne yazubo masa yace.. Nagodema Allah daya saka mukazo da Haneepha har hakan tafaru.. NUFAISAT taudhat tacuceni.. Ta ha'inceni.. Duk halaccin danayi mata sanda ta munafunceni. Ashe abinda tagayamin ranar farkon amarcina da ita qarya ne.. Allah Kasan nakamu dasan wannan yarinya Haneepha Allah ka sassautamin. "Amiin.. NUFAISAT da doctor Aryan suka ce. Ahankali ya tashi da saukowa daga gadan da doctor Aryan yasashi sannan ya karb'i makullin motarsa gun NUFAISAT yace su tashi suje gida.. Haneepha ta kalli ADAMS tace.. "Dady baka rungumeni kayimin kiss d'in ba.. Rintse idansa Adams yayi cikin wani hali ya rungumeta dayi mata kiss d'in.. Doctor Aryan ya dafa kafad'arsa yace.. "Kayi aiki da hankali abokina. Tunda kaga lokacin dakasan hakan akan Haneepha lokacin ne kake da arziqin su Khalit harsu uku.. Dan haka pls kanutsu sosai wajen yanke hukunci... Murmushi kawai Adams yayima masa da ficcewa daga d'akin yana cema NUFAISAT susamesa a mota.. Haka da damuwa NUFAISAT sukabi bayansa.. Tuqi kawai Adams yake amma hankalinsa ya tafi kan tunanin wane hukunci ya dace yayima TAUDHAT.. Ahaka suka iso gidan jiki a sanyaye.. Direct part d'insa Adams yayi ya d'auki takadda da biro ya rubutama TAUDHAT saki har uku.. Itako tana zaune a falan nata zuciyarta cike da mamakin ina Adams ya d'auki NUFAISAT sukaje.. Saiji kawai tayi wayarta na ringing.. Bak'uwar number ce. Dan haka saita d'auka a yatsine.. "TAUDHAT nice me magana.. "Wake nan. "Hajjiya Rukayyat kishiyar sirukarki. "Ayya. Sannu Hajjiya. Dafatan dai Alkairi ne yasa kika kirani.. "Ai tunda kikaga ban tab'a kiranki ba. Yadace kigane wannan kiran ba alkairi bane agareki "Ko. "Kwarar "To ina jinki.. Murmushi Hajjiya Rukayyat tayi da qara bajewa kan kujerar falanta tace.. "Dama na gaya miki saina baqanta rayuwarki kan abinda kika min ko. Toh yau ranar tazo dan ba abinda zai katangeki ga haukacewa yanxu... Murmushi TAUDHAT tayi da faɗin.. "Lalle kanki ya kulle. Dan ina tabbatar miki har qarshen rayuwata bazan tab'a yin hauka ba. "TAUDHAT kenan. Zaki gani yanzu a kwaryarki. Danni Hajjiya Rukayyat ban tab'a d'aukar alqawari naqi cikawa ba. Dan haka kibaza ido yanxu d'an zukuluzu zai baiyana agareki.. Hajjiya Rukayyat na fad'in hakan ta kashe wayarta da sheqewa da dariya.. Sororo TAUDHAT tayi da wayarta a hannunta. Kuma daidai lokacin ADAMS ya shigo falan nata.. Ahankali ya miqa mata takaddar hannunsa me d'auke da sakin dayayi mata. Tako karb'a cikin sauri da wareta dan taga me ta kunsa.. Agigice tatashi da kallansa tace... "Wai ni TAUDHAT kasaka ADAMS.😳 Murmushi yayi mata da cewa.. "Eh. Na sake ki saki uku TAUDHAT. Sannan ki tattara kayanki a yanxu ki barmin gidana. Sannan nasan kinsan muslinci yaban Haneepha ko.. Dan haka ke d'aya zaki fitta batare da ita ba.. Cikin matuƙar gigicewa tace "Kan uba. Kutumar uba. Durin uwa.😊 NUFAISAT ce ta gaya maka Haneepha ba y'arka bace ko.. Lalle tunda tayi sanadin datse igiyar aurena tsakanina dakai Wallahi sainayi mata abinda har tamutu bazata tab'a mantawa dani ba... ɗauketa da wani matsiyacin mari ADAMS yayi.. Kanfin tadawo daga hayyacinta ya qara bata wani.. Nan take ta kwalla wata muguwar qara sakamakwan ganin wani jibgegen aljani da tayi a gefanta yana zaro mata ido kamar zai cinyeta. Sannan ya watsa mata wani abu kamar qasa ajikinta. Ai nan take taji kamar an zuba mata wuta. Wannan shine yasata kwalla qara ba marin da Adams yayi mata ba.. Nan tafara cire d'an kwaninta tare da fara cizge gashin kanta tana cewa shikenan na haukace. Zuba mata ido ADAMS yayi ganin kamar da gaske abinda take fad'a na shirin faruwa da ita.. Daidai nan NUFAISAT tashigo falan saboda ihun da TAUDHAT d'in tayi.. Ai NUFAISAT naganin abinda takeyi cikin rashin fahimta tace... "TAUDHAT kidena cizgar gashinki mana. Kokinyi hauka ne.. Kallan NUFAISAT d'in tayi idanta ya juye ya zama ja tace. "Nayi hauka NUFAISAT.. Na haukace. ADAMS ya sakeni bayan baqar wahalar dana sha wajen bin malamai da bokaye akansa... Sannan Hajjiya Rukayyat ta haukatar dani dan nayi mata asiri takwanta jinya tsawan shekara biyu. Yanxu kema zokimin naji dad'i dan kema nasaka malamina ya bata miki ni'ima dan kawai Adams ya tsaneki.... Takai qarshen zancenta da nufo NUFAISAT d'in.. Ai cikin sauri NUFAISAT tayi tsalle d'aya ta maqalqane ADAMS tana ihun wai ya kalli idan TAUDHAT tazama mayya😁... Afuwa sis hajjaju🙏🏻 ga LEEKITAN ZUCHIYA kema naki ne. Ki gaidamin da Habibat kice ina santa... Nagaida y'an hannuna🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻luv u ❤❤❤❤ [8/2, 7:13 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018.. *Viawattpad@rahamanalele* Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 27☆ Qara qalqale NUFAISAT d'in ADAMS yayi cikin matuqar mamakin abinda TAUDHAT d'in take fad'a.. Itako NUFAISAT Yanxu tagane cikin hauka TAUDHAT d'in tayi maganar. Cikin tsawa ADAMS yace da TAUDHAT d'in.. "Idan kika kuskura kika tab'amin mata Wallahi saina miki dukan mutuwa.. Ai TAUDHAT najin hakan sai tatsaya cak da fashewa da kuka... Da sauri NUFAISAT tasake ADAMS tayi waje da gudu ADAMS yabi bayanta da kulle TAUDHAT d'in.. Hankalin NUFAISAT atashe yake matuqa... Nan tahau safa da marwa a d'akinta tana mamakin abinda yasami TAUDHAT d'in. ADAMS ya bata labarin shidai yana bata takaddar saki tahau yimai sambatu. Sannan ya qara dace mata takwantar da hankalinta komai zaizo da sauri. Nan NUFAISAT tabashi labarin abinda tasani tsakanin Hajjiya Rukayyat d'in da TAUDHAT d'in.. Sannan taqara mai da janta wajen boka da ita TAUDHAT d'in tayi... Sosai ADAMS yayi mamakin wannan lamari. Anan ya rungumi NUFAISAT d'in dajin qarin sanda da qaunarta aransa.. Nan yakira mama Mahaifiyar TAUDHAT dasu Dadynsa ya gaya musu gafa abinda yake faruwa.... Koda sukazo gidan Hankalin Dady dana Amminsa ya tashi matuqa. Mamah ko mahaifiyar TAUDHAT d'in sam bata wani damu ba. Cewa tayi dama haka qarshen mutane irinsu kenan yake zuwa.. Dan haka ADAMS yasata amota akaita gidan mahaukata. Karya wani saka lamarin aransa bare ya damesa. Dan alhakin mutanan dake kanta koyasa ayi mata wani temako cikin gidan nasa baza awani ci nasara ba. Dan haka maza yanxu yasa akaita can gidan mahaukata.. Aiko ADAMS yabi abinda maman nata tace... Dan haka saiya dubi TAUDHAT d'in yace.. "Duk da na sakeki TAUDHAT kije ki qarasa rayuwarki nayafe miki duk abinda kikayi min. NUFAISAT ma ta kalleta da hawaye tace.. "Nima na yafe miki TAUDHAT Allah ya baki lafiya.. Mamanta ma tace "Nima haka.. Abin gwanin ban tausayi. Dan Sai dariya TAUDHAT d'in take musu alamar haukar tagama shiga jikinta..😭 Haka ADAMS yasa masu tsaransa sukaita can gidan mahaukatan sannan su tsaya tsayin daka su cika komai na abinda masu kula da lafiyar irinsu suke buqata suyi musu kana su dawo. Nan suka amsa masa da ladabi suka taficce da TAUDHAT tana ihu da kiran sunan Hajjiya Rukayyat da ADAMS d'in da mamanta harda NUFAISAT.. Kalamai masu dad'i da sanyaya zuciya Ammin Adams take gayama maman TAUDHAT na tayi hak'uri ta rungumi qaddarar da Allah ya aiko mata akan yar tata tilo... Murmushin yaqe kawai maman TAUDHAT d'in tayima Ammin da cewa bakomai ai rayuwa haka take. Aduk yanda ka d'auketa haka zata zo maka. Jan hankalin da zatayi shine dan Allah idan da masu hali irin na TAUDHAT suyi gaggawar komawa ga Allah tunkan rayuwarsu ta wulaqanta idan sukazo gangara. Wallahi rayuwar bata da tabbas. Idan yau mune gobe bamu bane. Gashi dai kowa yaga farkwan TAUDHAT kuma kowa yaga qarshenta. Wannan kad'ai ya ishi mutum ishara. Bokaye da malaman tsubbu ba abinda suke iya yima mutum sai kaishi ga halaka. Wallahi jama'a boka da malaman tsubbo manyan maqiyinku ne dan jefaku suke ga halaka suna baku biyan buqatarku nad'an wani lokaci. Ni wannan abun ma yana bani mamaki.🤔 Tayaya zakaje wajen annamimai irinsu neman biyan buqata bayan ga ALLAH wanda yayika.. Wanda ya halicceka yayi maka komai na rayuwa sannan yace karoqesa zai biya maka buqatarka amma ka bijirema maganarsa kaje wajensu sannan kace qarshenka zaiyi kyau.. Lala lala🙁. Wallahi qarshenka-ki bazaiyi kyau ba Yanxu ku duba NUFAISAT... Bata zuwa wajen irinsu neman biyan buqata ita Allah kawai tasa agaba... Ya hanata Haihuwa😭 amma hakan baisata kauce masa ba. Tana jin dad'in rayuwarta. Tunda ya bata lafiya ya bata kwanciyar hankali. Ya bata soyayyar miji. To itako mezaisa tayima Allah budulci taje wajen waninsa neman wani abu bashi ba. Mutane wallahi muyima kammu tanadi agidan lahira. Mudena biyema san duniya muna jefa kammu ga maseefa. Tun anan gidan duniya bamu tare da kwanciyar hankali hakama agidan lahira bamu ba samun rahamar ubangiji..😭😭😭😭😭 Haka maman TAUDHAT tatafi gidan nata zuciyarta da sanyi dan taji d'ad'in sanyayyun kalaman da Ammin Adams tagaya mata.. Maman TAUDHAT d'in na tafiya Dady ya kalli Ammi dace mata suma ai saisu koma gida ko.. ADAMS ya gyara zama a falan TAUDHAT d'in dake duk anan suka taru yace da Dadyn nasa... "Dama ina san nagaya muku wani batu kuma.. Ammi tace "yauwa bamuji dalilin sakin da kayima TAUDHAT d'in ba tunkan tayi haukan.. Kama hannun Ammin tasa yayi ya kwashe duk abinda NUFAISAT tayagamai akan MUSLEEMA na matarsa ce kuma su Khalit yaransa ne. Sannan da sanin da yayi na Haneepha ba y'arsa bace. Da sakin dayayima TAUDHAT d'in sanadin hakan.. Dady Ammi sun girgiza dajin wannan batu... Sunji mamaki matuqa. Nan Dady yasa yaje ya kira masu su MUSLEEMAN su gansu. NUFAISAT tace aa ya zauna bara taje ta kirasu.. Aiko nan taje shashin dasu MUSLEEMAN suke Tagansu jugun jugun da alama sunfahimci wani abu na farawa agidan.. Su Khalit da Kahlil Rahma da Haneepha ko sai wasansu suke. Nan NUFAISAT tasakar musu murmushi da gaya musu iyayan ADAMS nasan ganinsu yanxu a shashin TAUDHAT.. NUFAISAT na fad'in musu hakan tahad'a kan yaran tace subiyota tabasu minti. Nan suka bi bayanta da murna. Suma su MUSLEEMAN bayansu sukabi da tunanin Allah yasa ba wani abu sukayi ba.. Dake MUSLEEMA ce a gaban YAWO tana shiga falan YAWO tabiyo bayanta.. Nan YAWON idanta ya sauka akan Ammin Adams.. Ai a furgice Ammi tatashi da nuna YAWO tace.. "YAWO.. 😳 Cikin sarqewar murya da mamaki itama YAWON tace.. "RAHMA..😳 Ainan Ammi tazube qasa sumammiya.. ADAMS yashiga zuba mata ruwa cikin tashin hankali.. Shiko Dady zubama YAWO ido yayi yana tuna itace mahaifiya ga Ammin Adams.. Wacce sukasha nema ashekarun da suka gabata.. Bayan Ammi ta farfad'o kuka tasaka da tashi ta rungumi YAWO tana cewa.. "Haba mahaifiyata menayi miki arayuwa kika gujemin. Kin hanani ganinki. Sannan kin hanani sukuni. Kwanciyar hankali nutsuwa duk na rasasu sanadinki. Sanda nasaka araina baki raye sannan na samu nutsuwa.. Share hawayenta YAWO tayi da bata labarin dalilinta na barin BASA garin Jos sukazo gwambe. Anan take cigaba da bata labarin mutuwan yayanta Musa da samuwar y'arsa MUSLEEMA da sukayi. Sannan taqara mata da labarin Auran ADAMS da MUSLEEMA data musu.. daidai wahalar da suka sha kafin su qara ganin Adams d'in akaro na biyu..😭 Jan numfashi Ammi tayi dace ma Yawon... "Wahalar ku taqare YAWO. Dan MUSLEEMA d'an uwanta ta Aura. ADAMS D'ANA NE YAWO.. Da mamaki YAWO ta kalli ADAMS da sakar mai murmushi tace.. "Ashe ba banza ba naji qaunarka da sanka a zuciyata. Sannan MUSLEEMA takafe kan kai take so. Murmushin shima ya sakar mata da kallan MUSLEEMA wacce tayi saurin sunkuyar dakanta qasa tana wasa da awarwaran hannunta.. Yace.. "Nima ganin farko dana muku kan titi naji zuciyata tana san rayuwa daku. Wannan dalilin yasani tambayarki meyake damun MUSLEEMAN lokacin da take a sume. Nagodema Allah dayasa mutanan nan suka min dukan dana rasa tunanina na fad'a hannunki kika bani Auran qanwata har hakan tafaru Sannan ina qara godema Allah dayasa nake rayuwa da matata NUFAISAT.. Wacce ta kasance daban acikin mata.. Wallahi YAWO idan har MUSLEEMA bazatabi NUFAISAT a zamansu da zasuyi ba zan iya barin MUSLEEMAN na rungumi yarana na rayu ni kad'ai da NUFAISAT d'in.. Murmushi YAWO tayi dace mai.. "Wallahi baka nan Allahn ka nanan bamu da abin yabo sai matarka NUFAISAT.. Tunda nake arayuwata ban tab'a tunanin zanso wata y'a mace har cikin jinina bayan MUSLEEMA sai NUFAISAT.. ADAMU ina san NUFAISAT kuma ina bayanka kayanke duk wani hukunci dazaka yanke akan MUSLEEMA idai har zata takawo ma NUFAISAT d'in wani wargi.... Murmushi NUFAISAT tayi da zuwa wajen MUSLEEMA takama hannunta da cewa.. "Zan rayu dake qanwata rayuwa irinta yaya da qanwa.. Ina sanki saboda san da kika nunama ADAMS a Ruga. Ina qaunar y'ay'anki dan Allah badan san da nake miki ko nake ma ADAMS ba. Saboda idan naso su dan ADAMS wata rana baya nan. Idan naso su saboda ke wata ranah bakya nan. Yau naqara ganin ishara agun abokiyar zaman TAUDHAT.. Dan haka dan Allah ina rokwanki daki saka Allah azuciyarki mubama mijinmu Farin ciki da kwanciyar hankali... Kallanta MUSLEEMA tayi hawaye ya zubo mata ta rungumi NUFAISAT d'in tace... "Aunty zan biki. Wallahi zan biki. Ke uwace agareni yanzu. Sannan abokiyar zama. Auntyna. Wacce zanna gayama damuwata.. Haka kawai naji sanki azuciyata. Haka kawai naji qaunarki azuciyata. Haka kawai naji ina san nayi rayuwa dake.. Uwa uba nasan bazan tab'a samun wani Farin ciki tsakanina da mijina ba idan har ban biki nasaka azuciyata zan rayu dake da amana da gaskiya ba. Aunty ina sanki dan Allah kiyarda aranki haka ne.. Murmushi NUFAISAT tayi da cewa.. "Nima ina sanki MUSLEEMA. Allah ya shige mana gaba akan dukkanin al'amuranmu.. "Amiin.. Dukkansu sukace.. Sannan Dady yaqara sakama NUFAISAT albarka. Ya rungumi yaran MUSLEEMA jikokinsa yayi musu addu'a sannan suka d'an tab'a hira kad'an inda Ammi take cewa yanxu Adams yasa masu kwasar kaya suzo su kwashe kayan TAUDHAT sukaima Mahaifiyarta ayau. Sai gobe ayima MUSLEEMA d'an gyare gyare ya saka mata komai na rayuwa saita koma d'akinta. Tunda ba wani batun gyara Aure tsakaninsu dan har yanxu tana nan a matsayin matarsa dan bata kai iya adadin da za'ayi musu gyara ba... Nan ya amsa mata da to insha Allah zaiyi yanda tace... Da MUSLEEMAN su Dady suka tafi gidansu.. Dan Ammi tace tana san tad'an tab'a hira da ita kafin tashiga d'akin nata.. Sai gidan ya kasance daga NUFAISAT sai Haneepha da Adams sai masu hidima.. Anan ADAMS yasa masu kwashe kaya sukazo suka kwashe kayan TAUDHAT tas ko tsinke basu gari ba sukayi gidan maman nata dashi . Tun alokacin aka fara gyaran shashin TAUDHAT d'in... Komawar su Ammi gidansu ko abin daya faru shine. Dady nayin ido hud'u da Hajjiya Rukayyat ya danqara mata saki uku.. Ai yana danqara mata nan tafad'i sumammiya.. Dama lokacin qanwarta na gidan. Nan Dady yace tafitar masa da ita daga gida.. Sannan zai turo musu da kayanta tas.. Aiko hakan ce tafaru.. Dan qanwar tata na tafiya da ita asibiti Dady yakira masu kwashe suka kwashe kayanta tas zuwa gidansu.. A asibitin cewa sukayi b'arin jikinta ne ya shanye. (Rahama nalele tace Toh ALLAH ya bata lafiya✋🏻) NUFAISAT rungumar Haneepha tayi awannan dare suka sha baccinsu. ADAMS na kallansu yace da NUFAISAT tasan fa bai iya kwana shi kad'ai ba. Tace yau dai saidai yayi hak'uri dan bata tab'a jin qaunar Haneepha aranta irin nayau ba. Shuru yayi mata.. Dan abin gwanin ban tausayi ne.. Yasaka aransa zai riqe Haneepha kamar yanda ya faro.. Dan dama yana santa yana qaunarta.. Dan haka bin bayan NUFAISAT yayi ya kwanta tana jinsa taqara rungume Haneephan a gabanta. Saiya sakar mata kiss awiya da cewa "Ina sanki matata... Murmushi tayi batare da tacemai komai ba.. Washe gari komai ya kammala.. Na d'an gyare gyaren da akama MUSLEEMA na shashin TAUDHAT.. Dan haka tun a ranar ADAMS ya turama da NUFAISAT kud'i ta account nata yace tafara tunanin abinda zata siyama MUSLEEMAN. Zainab yayar NUFAISAT yazo NUFAISAT d'in ta kwashe komai daya faru tagaya mata Zainab qara godewa Allah tayi da bai bama NUFAISAT d'in muguwar zuciyaba Tayima TAUDHAT da Hajjiya Rukayyat Fatan samun lafiya. Har tsawan Sati d'aya tunda ADAMS yake zuwa gidansu baya cin karo da MUSLEEMA.. Gashi zuciyarsa tana buqatar ya ganta kawai magana tashiga tsakaninsu.😂 Matsalar ba daga kowa bane daga ita MUSLEEMAN ce. Dan wata kunyar ADAMS d'in takeji tunda taga yasan komai daya faru tsakaninsu.. Shiyasa tana jin zuwansa gidan take shigewa can bedroom na Ammi tayi kwanciyarta har saiya tafi take fitowa.. Toh yau Allah yayi yau Ammi tace MUSLEEMAN zata tare a gidan nasa.... Dan haka takwas da rabi na dare dayaje gaisar dasu anan Ammin take CE mai yau zai tafi da MUSLEEMA. tunda tayi waya da NUFAISAT ta tabbatar mata tagama yimata siyayyar komai na rayuwar a mace a d'akinta.. Murmushi ADAMS yayi dace mata toh.. Aiko yana tashi tafiya nan MUSLEEMA tafito cikin riga da saket na material me mayafi d'inkin yayi mata kyau sosai Nan suka yima su yawo sallama.. Dan Ammi tace saidai akawo Haneepha dan Khalit da Kahlil Rahma sai sunyi wata agunta. Dan haka akawo Haneepha ma dan idan direban da yake kaisu makaranta yazo yadinga tafiya dasu kawai lokaci d'aya.. Sannan Dady yace Yawo ma bazata koma gidan ADAMS da zama ba. Dan Akwai wani shashi nan cikin gidan nasa ya mallaka mata nan d'in anan zata dinga rayuwarta. Sannan shashin Hajjiya Rukayyat zaisa a canja mishi fasali Salim ya zauna aciki shida matarsa idan anyi auran. Dan yazo da wata Iyami yarinyar me hankali yacema Dadyn ita yake so.. Kuma koda dadyn yayi binkice yagano gidansu yarinyar gidan mutanan arziqi ne.. Dan haka sai kawai suka tsaid'a magana za'ayi bikin dazaran yarinyar ta kammala karatunta.. Tuƙi ADAMS yake Ahankali shuru ba me magana tsakaninsa da MUSLEEMA.. Saima satar kallansa da MUSLEEMAN takeyi.. Tana tunanin yau ta'ina zata fara da mijin nata.. Ahankali ya kalleta da cewa.. "Wai miye ne kiketa wani satar kallona. "Naga YAYAH aiba lefi bane idan na kalle ka ko. "Toni aini naga ba Kallanki nake ba. "Alamu sun nuna kamar kana fushi dani.. Murmushi yayi da cewa. "So nake naji dalilin dayasa kika hanani ganin kanki tunda kika bar gidana kika dawo gidansu Ammi.. "Kayi hak'uri bazan sake ba insha Allah. "Nafa lura bada hak'uri ya zamar miki jinin jiki.. Cikin shagwab'a tace.. "Toh YAYA mezance maka bayan hakan.. "Kawai yanxu idan kinyi min lefi hukuntaki kawai zan dinga yi.. "Ban saba da hukuncinka ba YAYAH dan Allah ka rangwanta min.. Wani kallo ya watsa mata da cewa.. "Zaki saba dashi nan kusa.. Shuru tayi mai dan Kallan yashigeta sosai.. Ahaka batare da sun qarama junansu magana ba suka iso gidan.. Direct falan NUFAISAT suka shiga tana tare da Haneepha suna kallo.. Ai MUSLEEMA na ganinta taje da gudu ta rungumeta tana cewa.. "Aunty nayi kewarki sosai. Murmushi NUFAISAT tayi da faɗin.. "Nima haka my sister.. Dafatan kina lafiya.. "Na daɗa samun lafiyar ne dana ganki Auntyna.. "Toh yayi kyau yanxu muje kiga shashinki idan komai yayi miki to. idan kuma akwai abinda kike buqata saimu barma gobe idan Allah ya kaimu na qarasa aikin ladana.🙁 "Aunty dukfa abinda kikayi kawai yayi.. Bani buqatar abinda baki buqata. Murmushi NUFAISAT taqara yi. Wallahi ita dai tana san MUSLEEMA.. Yauwa Aunty.. Zan fara kawo miki qarar YAYA tun yanxu...🙁 Wai zai hukuntani idan naqara yimasa nefi. Wai yana fad'in bazai qara hak'ura da duk abinda zanyi masa ba.. MUSLEEMA takai qarshen zancenta da turo baki.. Waro ido NUFAISAT tayi da Kallan ADAMS wanda yake zaune a dining ya zubo musu ido kawai yana kallansu Kallan sha'awa. Tace.. "Dan Allah ajanye wannan hukuncin.. Dan nasan kowane iri ne akwai cakwakiya acikinsa. Sam bazata iya d'aukarsa ba.. Murmushi ADAMS yayi da tashi ya qaraso wajen nasu ya mannama NUFAISAT kiss a kumatu yace.. "Na janye uwar gida. Duk abinda kikace shi za'ayi.. Itama murmushi ta mayarmai da cewa "to nagode da bani wannan matsayi muje kuga gyarana.😀 Haka ADAMS yasasu a gaba yana me qare masu kallo a halittarsu da fatan ya rayu dasu rayuwa me tsawo.. Shi kansa ADAMS ya yaba da komai da NUFAISAT tasaka a falan da bedroom harda kitchen.. Dan dama bawai yana bibiyan shashin bane lokacin da NUFAISAT take saka kayan d'akin. Gaskiya yayaba da komai 100 Bare kuma MUSLEEMA dabata tab'a ganin tsari irin wannan ba.. Komai na falan da kitchen da bedroom d'in lemon green ne.. Sanda MUSLEEMA ta magantu tace da NUFAISAT.. "Aunty gaskiya banyi tunanin zanyi rayuwa a irin wannan waje dasunan matar wajen kuma mallakina ba.. Magana ta gaskiya Aunty kin had'u. Bani da bakin gode miki.. Jan numfashi ADAMS yayi dasan cewa wani NUFAISAT tatareshi da cewa.. "Bani san kace komai... Kawai na baku kwana bakwai kadawo min d'akina. Sannan ga abincinku can bisa dining nasan zakuji dad'in abinda na had'a muku.. Murmushi yayi mata da d'aga mata hannu alamar yaji.. Tana ganin hakan tama MUSLEEMA sallama da Murmushi tabar falan.. Ahankali suka had'a ido shida MUSLEEMAN.. Saiya qaraso inda take da rungumota jikinsa yana mece mata.. "Na dad'e ina sha'awar rungumarki.. Shuru tamai sakamakwan dad'in daya rufe zuciyarta yau gata a jikinsa kanta bisa qirjinsa. Gashi cikin shauqi da murad'i.. Cikin nutsuwa ya fara d'ago da fuskarta suka had'a ido. Nan yakai bakinsa cikin nata yana aika mata da me zafi.. Nan da nan qafafunta suka fara rawa jin hakan da yayi ne yasa shi barinta da d'aukar ta ya direta a dining.. Duk yanda taso akan karta sake suci abinci tare amma abin ya gagara. Dan kafeta yayi da ido yace saitaci komai da NUFAISAT ta girka musu.. Bayan sun gama cin komai dama shi ya rigada ya gama kintsa kansa tunkan yaje gidansu Ammin.. Dan nan gidan ya fara zuwa yayi wanka da sallah ya canja kaya kana yaje gidansu Ammin tasa. Dan haka tambayarta yayi kotayi sallar isha'i. Nan tabashi tabbacin tayi.. Saiya nuna mata shashinsa dace mata idan ta canja kaya tabiyosa yana jiranta.. Jiki a sanyaye ta'amsa masa. Shiko part na NUFAISAT ya nufa sam tamanta tabar k'ofar a bud'e sanda ya kunna mata wutar bedroom nata sannan tagane abud'e tabarta... Harararsa tayi da cewa. "Katafi kabar amarya ko.. "Eh.. Nazo qara ganinki ne dan bazan iya yin missing d'in rungumarki ba akullum.. Murmushi tayi da tashi daga gadanta ta rungumesa.. Tana cewa dan Allah.. "Kabimin qanwa a hankali.. "Wai wayace miki zanbi takanta ne yau.. "Koma yaushe katashi bin takan nata ina san kabita ahankali. Dan zan iya jure komai amma bazan iya jure jinya irin wannan ba... Dan nasan halinka ne sarai. lalurace kawai ke hana ka jin mace yayin bacci.. "ƙin kulata yayi danya lura neman magana takeji.😀 Dan haka dataji yayi mata shuru sai kawai tayimai kiss daci gaba da cewa. "Toh yanxu kaji rungumata.. Dan haka maza kabarmin d'aki. "Dama yasani dole kumallan matan ya motsa ko kad'an ne😂 Dan haka simi simi ya bar mata d'kin da Murmushi akan fuskarsa yana fad'i a zuciyarsa Allah ya barsa da ita... Hmm🙁 Yana fittan ko bayan ta kulle kofarta. Sai kawai taji kuka yazo mata.. Tana matuqar san ADAMS amma dole tayi hakuri da nuna kishi akansa dan bazai tab'a zama nata ita kad'ai ba.. ALLAH yasa Haneepha tayi baccin saitaci kukanta bame rarrashinta tashare hawayenta tana me fad'i a bayyane.. "Wallahi kishi da zafi yake.. Duk yanda kaso danne zuciyarki dole kajishi ayayin da kana kallo mijinka zai tsallake yaje wajen waninka.. Yanxu fa abinda yake yimin shi zaima wannan yarinyar qarama da ita..😀 Yanxu fa duk abinda nasani akansa itama tasani. Yanxu zai raba san da yake min yana bata rabi yabani rabi.😭 Ai tana kawowa nan a zancenta tara fashewa da kuka tana meci gaba da cewa.. Allah ka rage min kishin mijina araina. Allah ka haneni nunama abokiyar zamana kishi akansa. Allah kayima zuciyata gata ka hana idona ganin wani abu dazai mata agabana wanda zanji haushi na nuna kishi agareta.. Allah kasan ina santa ina qaunarta ina san kasan cewa da ita matsayin kishiyata amma Allah karka barni da wayona wajen zaman nawa da ita. Nidai fatana Allah kasa mijina yasoni fiye da San dazai mata arayuwa.. Nidai fatana Allah ka rufamin asiri ka kwantar min da hankalina kasa naci jarabawar da zaka d'auramin akowane lokaci ne. Allah ina san mijina.. Idan ya kasance shine mijin qarshen rayuwa toka barni dashi da ita murayu rayuwa taban sha'awa. Idan kuma ya kasance bashine mijin qarshen rayuwa ba Allah ka zab'amin abinda zai zama alkairi agareni.. Haka NUFAISAT taqaraci baya nanta ta hak'ura da komawa bedroom nata ta rungumi Haneepha bacci me qarfi yayi awan gaba da ita... Shiko ADAMS yana komawa part nasa MUSLEEMA na shigowa bedroom nasa cikin shigar bacci da hijab a jikinta.. Nan ya tashi ya tareta da cewa.. "Bara naga wankan naga ko yayi kyau.. Shuru tamai.. Yacire mata hijabin yana me cigaba da cewa.. "Yanda nayi miki cikinsu Khalit haka nake san kiyimin duk abinda nake miki cikin dare dan yau ina san kidawo min da tunanina Wanda nayi missing nashi dake.. Kallansa tayi da sauri.. Shiko ya d'aure fuska😌... Sosai tagane ba wasa yake mata ba da gaske yake mata.. Dan haka bayan yayi nasakar kaita bed nasa ya rabata da komai na jikinta nan takai bakinta cikin nasa tana aika masa da salan da yake mata amfani awannan lokacin.. Sosai ADAMS yayi mamakin lamarin danya tuna wata rana yayima NUFAISAT amfani da salan tatambayesa wayake yima.. Sosai ADAMS yaji dad'in harkar da MUSLEEMA danji yayi kamar karya barta.. Sam bai damu da ihun da take mai ba danya gane ihun bana kuka bane ihun dad'ine... Ya gane yarinyar ta had'u da yawa dan ko nafalaninta bazu zube ba. Basuma nuna alamun anwani shasu ba. Hakan ne yasa shi nuna mata zalamarsa akansu. Dan sosai ya nuna mata qauna wajen shansu.. Washe gari tana zaune a kan cinyarsa yake bata breakfast d'in da NUFAISAT tayi musu.. Zazzab'i ne yake damunta sosai.. Da tausayawa ya kalli fuskarta da cewa.. "Ko dama haka ne yake faruwa idan muka had'e da juna.. Qara lefewa tayi ajikinsa cikin shagwab'a tace.. "aa kawai ina ganin ciwan yazo ne.. Kiss ya sakar mata dajin santa arai.. cikin kulawa ya bata magani tasha.. Dayazo ma da NUFAISAT da batun bata jin daɗin jikinta sanda ta hararesa da cewa.. "Ai dama nasani.. To yanxu miye kawani zo gaya min... Sosa qeyarsa yayi da rungumarta cikin jin kunyarta da qaunarta yace.. "So nake tunda bakiyi jinyar TAUDHAT ba kinga sai kiyi nata dan Allah karkice aa.. Wallahi na wahalar miki da ita da yawo tunda na gane tayi missing nawa da yawa. Gata shagwab'abbiya. Duk da cewar bayau bane na farko Amma ai kinsan dole taji da bambamci da salan da taji a Ruga ko... Kai Allah ya tsine wannan fad'ar gaskiya irinta Adams🤦🏻‍♀ NUFAISAT yau tafad'i hakan aranta dan sosai taji zafin gaya mata hakan da yayi😆 Aiko kallansa tayi cikin masifa tace.. "Wallahi bazanje jiyar tata ba.😭 Ganin da gaske tana san saka mai kuka sai yahau lallashinta da cewa.. "Dan Allah karkimin kuka. Kawai mubarta ta mutu dama nafisan yin rayuwa dake ke d'aya y'ar matata. Y'ar cafai y'ar me kyau😀.. Ya faɗin mata hakan cikin wayo da hikima.. Aiko nan tace.. "Hmm umm.. Lalle ma. Toni bazan iya barin qanwata ta mutu ba. Dan kasanfa ina santa kawai dai kasan ba kowace mace bace take iya d'aukar jinya irin wannan.. Amma zan kula da ita insha Allah wannan ba zai zama da matsala ba. Daidai tamutu koya kagani.. Murmushi yayi ganin yau yarinta tazo kwakwalwarta yace.. "Kuma fah.. Haka ya tafi office ya barta da jinyar MUSLEEMA.😂 Akwana bakwan da NUFAISAT tabasu MUSLEEMA taji jiki sosai agun ADAMS.. Dan gaskiya fa yana jinta kamar NUFAISAT d'in ne Hakan yasa ya yaqi saurara mata.. Saidai daya dawo d'akin NUFAISAT sai yaji ina da bambanci..😌 Eh gaskiya NUFAISAT tad'anfi MUSLEEMA dad'in kusanta kad'an. Amma zai iya rayuwa da MUSLEEMA ahakan batare daya damu da rashin NUFAISAT ba.. Ma'ana dai yanxu ADAMS yana jin dad'in harka da matansa cikin nutsuwa fiye da yanda yake tare da TAUDHAT.. Idan yana tare da NUFAISAT yana qara qaunarta Sosai.. Idan kuma yana tare da MUSLEEMA yana ji kamar yarya barta dan shagwab'arta na tafiya da zuciyarsa matuqa har yadinga jin dama ace karya barta. Ya zauna kawai shida ita tana zubamai shagwab'ar.. Saidai kuma inda ace NUFAISAT tagane ADAMS yana matuqar san shagwab'a a rayuwarsa tafara yimai ba makawa saidai MUSLEEMA tayi zaman hak'uri agidan dan komai na Adams d'in tattarewa NUFAISAT d'in zatayi dan zaiji kawai da ita kad'ai zai iya rayuwa. Wannan shine abinda NUFAISAT bata sani ba ajerin abinda ADAMS yake so arayuwarsa.. Kuma duk randa tasani tafara yimai zai iya juyama MUSLEEMA baya.. Da gaske hakan tafaru.. Dan wata ranah NUFAISAT tagane ADAMS yana shagaltuwa da MUSLEEMA idan tana zuba mai shagwab'a.. Dan haka sai itama ranar tashagwab'e akan duk abinda yake shiga tsakaninta dashi.. Duk maganar da zata mai sai tamai a shagwab'e.. Aiko awannan ranah taga rikicewar ADAMS akanta. Dan qarara taga ya nuna mata kulawar da tunda suke ita dashi bai tab'a nuna mata ba.. Talura da MUSLEEMA da yanda take mishi magana aranar ya wani fitta daga harkarta. Wannan shine dalilin dayasa NUFAISAT bata qara yimai irin wannan shagwab'ar ba dan bata san wani abu ya shiga tsakaninsa da MUSLEEMAN na rashin jituwa.. Saidaifa tana d'an tab'amai kad'an kad'an..😄 _________ Ran nan malamin TAUDHAU yazo wajen ADAMS ba kunya yake gayamai wai yazo karb'ar y'arsa Haneepha ne. Nan ADAMS ya zuba mai ido har yakai qarshin shirin kunyarsa. Sannan ADAMS d'in ya kira jami'an tsato yace su kulle shi karku tab'a barinsa ya fito dan zama da irinsu masifa ne acikin al'uma... Ai malam isma'il yayi dana sanin tunkarar ADAMS da yayi da batun ya bashi Haneepha Dan yanxu Gashi a kurkuku yana aikin wahala cikin nadamar abubuwan daya aikata arayuwarsa... ... ******* Wata shidda da tarewar MUSLEEMA tasamu ciki. Inda bai wani zo mata da wani laulayi ba har takai watan haihuwanta.. Inda tasamu y'a mace kyakkyawa san kowa in wanda ya sara.. Yarinya taci NUFAISAT.. Aiko NUFAISAT tayi tsalle tayi murna na Farin cikin takwarar da mijin nata yayi mata.. Haka MUSLEEMAN tatayata farin ciki sosai sam babu wani abu aranta.. Sati biyu da haihuwan MUSLEEMA akayi Auran salim qanin ADAMS inda salim d'in ya tare da amaryarsa Iyami acikin gidan Dady shashin mahaifiyarsa.. Inda ita Mahaifiyar tasa Hajjiya Rukayyat take gidansu ana cigaba dayi mata magani amma kamar ba'ayi mata... Haka TAUDHAT hauka ba sauqi. Sai dai kawai muyi mata fatan samun sauqin nan gaba.🙁 YAWO da MUSLEEMA da Adams harda NUFAISAT da Ammi sunje rugar malam jauro sunyi mai godiya da kulawar da yaba ADAMS. inda yaji dad'in Sosai dan yaci gaba da ciwata ma Yawo dabbobinta.. Daga qarshe dai haka yawo. Tace ya riqe shanun sun bar mishi Har kukan dad'i sanda Malam jauro yayi musu. Mutan Rugar ko sunyi mamakin ganin Adams da tunanin dama haka yake babban mutum... Haka dasu dawo MUSLEEMA bata manta da Hafsat wacce tatemaka musu a gidan Hajjiya Batula ba Dan takanas ta kano Adams yasa jabi'an tsaro dasuje su akama Hajjiya Batulan Abin yayi kyau sosai dama idan kaji irinsu suna cika bakin bata yanda za'ayi a kamasu to sai dai idan basu tab'o yaran manyan masu kud'i ba.. Hafsat tayi murna sosai da irin karamcin da MUSLEEMA tayi mata.. Dan kud'i me yawan gaske ADAMS ya bata kan tayi aure taja jari karta qara zuwa aiki wani gida.. Anan MUSLEEMA take tambayarta yanda suka kaya bayan tafiyarsu. Sai Take bata labarin ai ba yanda tayi amma tayi mamaki sosai dan tayi bincike kowa ya tabbatar mata baiga fitansu ba... _*Wata ranah*_ ******************************** _*Wannan ranah itace mummunar rana gareni ni MUSLEEMA*_😭😭😭😭😭... (Rufe Diaryn da nake karanta wa nayi ni Rahma nalele da kallan Junior Ramadan nace.. "Tun kan naji wannan rana naji gabana ya faɗi da ita... Pls gayamin mezai faru.. Murmushi junior yayimin da cewa... "Duk nasan abinda ya rafu a wannan ranar bazan iya gaya miki ba. Kawai bud'e diaryn kici gaba da karantama masoya LEEKITAN ZUCHIYA.. Jan numfashi nayi da bud'ewa kamar yanda yace min naci gaba da karatu kamar haka...) 👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Yau MUSLEEMA tun da safe takejin gabanta na fad'uwa. Tarasa meyasa takejin hakan.. Dan haka kasa hak'uri tayi tatashi tanufi shashin NUFAISAT dan ta gaya mata.. Lokacin qarfe takwas dai dai na safen. Dan harsu Khalit sun tafi skull.. Anan falo taganta ita da adams kanta na bisa kan cinyar ADAMS d'in. da alama ADAMS d'in ya gama breakfast ne yake dan hutawa kan takwas da rabi tayi ya ficce zuwa office... Da damuwa MUSLEEMA tazauna gefansu tace.. "Auntyna yau narasa me yake min dad'i a duniyar nan.. Gabana sai fad'uwa yake. Kamar wani abu zai faru da wanda nake so... Murmushi NUFAISAT tayi mata da tashi tadawo kusa da MUSLEEMAN tace.. "Ki kwantar da hankalinki.. Insha Allah ba wani abu dazai faru. Tashi ADAMS yayi da zuwa kusa dasu ya kama hannun MUSLEEMAN yace... "Babyna ki kwantar da hankalinki kamar yanda Auntynki tace insha Allah ba abinda zai faru kinji.. Kuka MUSLEEMA tasa musu da cewa... "Wallahi bakuji yanda nake ji bane araina ji nake kamar zan rasaka Ya ADAMS.. Kamar zan rasaki AUNTYNA.. Kamar zan rasa YAWO.. Kamar zan rasa YARANA.. Kamar zan... ADAMS bai barta ta qarasa ba ya rufe mata baki da cewa .. "Ya isa haka... Shuru MUSLEEMA tayi cikin zubar hawaye saita kalli NUFAISAT ta kallesa.. "Bana san kiyi yin irin wannan maganar Babyna. Koda ace kina jin hakan kamata yayi kifara gayama Allah kafin ki gaya mana... Adams ya fad'i yana me janye hannunsa daga bakinta.. Ita dai MUSLEEMA shuru tamai dan bazasu gane me takeji aranta bane.. Itako NUFAISAT murmushi taqara sakar mata da goge mata hawayen dake zubo mata Tace.. "Bafa komai dazai faru K'anwata.. Kidena kuka bana so.. Murmushin yaqe MUSLEEMA tayi mata da janye hannunta daga na Adams takama hannun NUFAISAT d'in tace.. "Auntyna ina san kigayamin wani abu dan Allah.. "Toh ina jinki MUSLEEMA.. "AUNTY kimin alqawarin bazaki tafi ki barni ba.. "Haba MUSLEEMA.. Idan nabarki inyi rayuwa dawa. "Yauwa AUNTY dan Allah karki barni kinji... takai qarshen zancen nata da qara zubo da wani hawayen.. ADAMS baya san kukan d'aya daga cikinsu dan haka tayar da MUSLEEMAN yayi da rungumarta yace.. "Kije d'akinki kiyi sallah raka'a biyu kiroqi Allah yasa koma menene kike tunani yasa yazama alkairi.. Yana gaya mata hakan ya saketa dayi mata nuni da hannu akan taje kartaji komai.. Har takai ƙofar fitta tajuyo da kallanta garesa tace.. "Dan Allah YAYANA karka barni kaima Wallahi ina sanka.. Kallan junansu sukayi shida NUFAISAT kana suka maida kallansu gareta yace da ita.. "Toh bazan barki ba shikenan.. Yana gaya mata hakan taficce daga falan.. ADAMS ya rungumi NUFAISAT da sakar mata kiss da cewa.. "Naji ajikina kamar wani abun nasan faruwafa. Kinga bata tab'a rikice mana irin nayau ba.. Qara lafewa a jikinsa NUFAISAT tayi da cewa.. "Aini tun jiya gabana yake fad'uwan nan kamar za'ayi mutuwa.. Ai ADAMS na jin hakan ya d'ago da fuskarta zuwa ga kallansa cikin tsoro yace.. "Wa kike tunanin zai mace.. Hawayene ya zubo mata tace.. "Nima ban sani ba mijina. kawai dai nafijin fad'uwan gaban yana qara yawaita yanxu..... Innalillahiwainna'ilaihirraji'un shine abinda ADAMS ya fad'i da qanqame NUFAISAT kamar ance mishi itace zata mutun.... 🙂🙂🙂🙂🙂 yau ba dariya y'an hannuna.. Kawai dai Ina gaisuwa. Danni naga abinda nagani a page d'in gaba LEEKITAN ZUCHIYA saura page guda ya rage muku masoyana😭 [8/5, 10:18 PM] ®🔳◾◼▪official Auntyn Luv.: `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• ❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠ *LEEKITAN ~ZUCHIYAH* *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´- ☆“˜•☆• ¸☆“☆ª☆_☾`☆• {Zoka Gyara Tunanina} A true life story April.. 2018.. *Viawattpad@rahamanalele* Labari da rubutawa zuwa ga tsarawa.. ☾•Rahma Muh'md Rufa'i Nalele..☆ https://mobile.facebook.com/Real-Hausa-Fulani-Writers-forum-RHFWF-173984973194167/?refid=52&ref=opera_speed_dial&__tn__=H-R ” بسم الله الرحمن الرحيم realhausafulaniwriters@gmail.com ☆page 28☆ qarshe😍 Lumshe idanta NUFAISAT tayi cikin jin wani iri ajikinta haka... Shima ADAMS d'in yaji hakan dan haka saiya zaunar da ita kan kujera cikin rikicewa yake qare mata kallo da cewa.. "Koma miye zai faru ina rokwan Allah daya barni da matana.... Murmushi NUFAISAT tayimai hawaye ya qara zubo mata da cewa.. "Na tsinci kaina dasan binka asibiti yau mijina. Dan Allah karkace aa. Ina san kawai naganni dakai ne. Saboda naji wani mafificin tsoro araina yanxu kamar idan katafi wani abu zai faru dani.. Kallo d'aya zakama ADAMS kagane ya qara rikicewa.. Dan haka tashi yayi da shiga bedroom nata ya d'auko mata gyalanta yayafa mata da cewa. "tashi muje matata.. Dan nima ayanxu yanda nake ji araina bazan iyama tafiya nabarki cikin wannan yanayin ba.. Kan tabashi amsa kiran YUSUF ya shigo wayarsa.. Cikin sauri ya d'auka inda Yusuf d'in yake cemai dan Allah ya tawo asibiti da sauri yanxu ya kawo Hajjiyansu yau kam jikin nata ba sauqi.. Dan har aman jini takeyi.. Amma Dr Ibrahim ya bata temakwan gaggawa har tasamu bacci. Amma duk da haka Shidai kawai yazo dan yafi gane aikinsa fiye dana Dr Ibrahim d'in.. Rintse idansa ADAMS yayi dacemai Gashi nan zuwa.. Haka suka fito masu tsaransa suka bud'e masu kofar mota suka ficce sam kotakan MUSLEEMA Adams baibi ba.. Dan haka MUSLEEMAN najin fitarsu tashiga wanka sama sama da d'aukar y'arta little NUFAISAT tayafa gyalanta tafito da cema direban gidan yabi mata bayansu Auntynta NUFAISAT ina yasan inda suka nufa. Yace mata ba mamaki asibiti suka nufa. Tace mai to maza yakaita gunsa... Dake ADAMS yana baya direbansa ne me tuqasu dan haka NUFAISAT na jikinsa tayi lef da ita kamar matacciya.. ADAMS yana jin wucin zafin da jikinta yakeyi. Nan ya fahimci zazzab'i ne yake shiga jikin nata.. Ai ba shiri ya d'ago da fuskarta arikice yake cewa.. "NUFAISAT ke NUFAISAT wai meyake daminki ne.. Shuru tamai dana me lumshe ido da bud'ewa kad'an kad'an.. Iya rikicewa ADAMS fa ya rikice.. Dan haka cikin tsawa yake cema direban nasa ya qara gudu.. Sam NUFAISAT baki ya rufe dan bata cewa umm bare um um.. Suna isowa ya kwantar da ita kan d'aya daga cikin kujerun office d'in nasa. Yusuf Yace mai.. "Lafiya meya sameta. "Wallahi YUSUF yanxu fah kamar wasa zazzab'i ya kamata. Bara na kira Dr Aryan ya duba min ita. Nan ya kira Dr Aryan yahau duba masa ita... Aiko Dr Aryan ya gane zazzafan zazzab'i ne ya shigeta nan take.. Dan haka suje su kwantar da ita kan gadan asibitin dan bata cikakken temakwan daya dace da ita.. Nan ADAMS ya d'auki NUFAISAT dan kaita d'akin dake da gado. Aiko yana kwantar da ita sai yaga kamar bata numfashi.. Arikice yakai kunnansa setin qirjinta dan yaji tana numfashin ko batayi..😳 Ai dai jin ADAMS yaji bata numfashi. Dan haka cikin wani yanayi me tafe da tashin hankali yahau girgizata yana cewa.. "NUFAISAT ke NUFAISAT ke matata.. Dan Allah kitashi.. Dan Allah na roqeki daki tashi pls.. NUFAISAT NUFAISAT. Haba NUFAISAT.. Ina shuru NUFAISAT bata da alamar amsa ma ADAMS... Dan haka saiya saketa yaja da baya hawaye na zubo masa tunaninsa tamace ya kalli Dr Aryan da YUSUF dake waje jikin window yana Kallan abubuwan da suke faruwa yace dasu... "NUFAISAT tatafi Tamutu ta barni. Zan iya rayuwa kuwa.. Yana fad'in hakan ya zube qasa sumamme agun... Nan Yusuf ya shiga d'akin da matuqar rikicewa ya temakama Dr Aryan suka sashi kan wata kuje dake d'akin.. daqer da sid'in goshi Dr Aryan yasamu ADAMS ya farfad'o.. Lokacin ko a akan idan NUFAISAT ya farfad'o dan haka suna had'a ido tasakar mai murmushin yaqe da cewa.. "Na d'auki kwanaki uku mijina ina jin wani yanayi ajikina da fad'uwar gaba. Hak'ik'a MUSLEEMA ita taji abinda taji yau aranta mijina. Ina san rayuwa daku amma hakan bazai yuhuba. Saboda lokacina yayi. haka dole natafi na barku. Takai qarshen zancen nata da zubo da wani hawaye me d'umin gaske. Sannan tacigaba da cewa.. Nagode ma Allah dayasa kakeda MUSLEEMA mijina.. Ina san kariqeta amana ka.... ADAMS bai bariba ta qarasa zancenta ba!!! ya katseta wajen cewa.. "Waya gaya miki idan babu ke zan iya rayuwa.. Banyi zatan abinda nake gaya miki akullum zai kasance awannan ranar ba. Nima gasu sunzo da fararan kaya suna san d'aukar rayuwata NUFAISAT.😭 Dan haka Ina yima MUSLEEMA fatan alkairi a rayuwarata.. dan zatayi rashi biyu a lokaci d'aya.. MUSLEEMAN na jikin window tana jinsu tana kallan abunda yake faruwa dan tun sa'adda YUSUF ya shiga d'akin tafahimci ba mamaki kosu NUFAISAT d'in suna ciki. Danta duba office d'in ADAMS baya nan. hakan yasata isowa wajen da tsayawa gurus jikin windown d'akin. Ganin NUFAISAT kwance ADAMS kwance... Qara tsaida kallanta NUFAISAT tayi akansa.. Tace. "Zata zama abin tausayi mijina. Ina san MUSLEEMA tasamu Farin ciki me d'orewa. Takai qarshen zancen nata da maida kallanta zuwa ga MUSLEEMA wacce fuskarta tawanku da jiqewar hawaye. Sai Kawai NUFAISAT ta sakar mata murmushi da cewa La'ilaha'illallahu-muhammadarrasulullahi-sallallahu a laihiwasallam. Tana fad'in hakan ADAMS ya rintse idansa da Kallan Yusuf yace.. "Kagani tatafi ko. Kamar yanda tatafi haka kaima zaka tafi. Ina rokwanka da Allah daka Auri MUSLEEMA kabata kulawar data zarce wacce nake bata. Dan nima... Bai qarama YUSUF zancen ba😭.. ya b'ige da cigaba da faɗin.. La'ilaha'illallah muhammadan rasululla sallallahu'alaihiwasallam. "NUFAISAT tatafi.. ADAMS abokina wanda ya zama d'an uwa gareni abokin hira abokin wasa da dariya. Abokin kasuwanci na. Me gaskiya me amana me kirki. Wanda yasan abinda ya dace ya bita.. Yusuf ya fad'i hakan da zubewa qasa sumamme... Aiko MUSLEEMA batasan sanda tayi wurgi da little NUFAISAT ba... Ta kwalla qarar da duk asitin sanda suka jita... Hankalin kowa yayo kanta.. ALLAH yaso wata ma'aikaciyar wajan na tsaye gefe ita ta cab'e little NUFAISAT d'in amatuqar tsorace dan jifan da MUSLEEMA tama little d'in bana wasa bane... Da wani shegen gudu MUSLEEMA tafad'a d'akin tarasa kan wazatayi cikinsu.. ADAMS ko NUFAISAT.😭😭. Ai kawai sai tayi kan NUFAISAT... Fad'i take.. "Aunty dan Allah kitashi.. Dan Allah Dan annabi Aunty kitashi.. Aunty kinyimin alqawarin bazaki tafi ki barni ba. Kinyimin alqawarin kina tare dani.. Na shiga uku ni MUSLEEMA. Tafad'i hakan da komawa kan ADAMS tana meci gaba da cewa. Ya ADAMS kaima katashi. Dan Allah Dan soyayyarka da manzan Allah katashi kacema Auntyna tatashi muci gaba da rayuwa.. Wallahi ina sanku ina qaunarku ina fatan qare kowace rayuwa daku.. Kuka MUSLEEMA take bana wasa ba. tana zuwa wajen NUFAISAT tajijjigata taje wajen ADAMS ta jijjigasa tana rokwansu dasu tashi suci gaba da rayuwa.. Kaf doctors d'in asibitin da ma'aikatan asibitin ba wanda bai tausayama MUSLEEMAT ba... Sannan sun tsinci kansu da mummunar fad'uwar gaba da suka fahimci DR ADAMS LEEKITAN ZUCHIYA ne da matarsa tafarko NUFAISAT sune suka rigamu gidan gaskiya. Anan wasunsu masu raunin zuciya suka fara kuka wiwi... Suna fad'i dole MUSLEEMA ta shiga tashin hankali dan sunfi kowa sanin waye ADAMS. Haka suna samun labarin matarsa NUFAISAT da kirkinta da haƙurinta kamar yanda duk abinda kakeyi idan mutane na kanka.... Aqarshe dai bayan Dr Aryan ya samu daidaituwar numfashin YUSUF sai yasa ma'aikatan wajen dasu kaisa wani d'akin. Kana ya kalli MUSLEEMA da zubar hawaye dan mutuwar ADAMS d'in tashigesa sosai shida matar tasa NUFAISAT.. Cikin wani hali ya kama hannun MUSLEEMA da cewa "kiji hak'uri MUSLEEMA.. *Amma kin rasa NUFAISAT da ADAMS rasawa irin wacce ba'a dawowa* Tsayawa cak MUSLEEMA tayi da kallansa cikin matuqar qarin shiga razana tace.. "Da gaske... D'aga mata kai yayi alamar tabbatarwa... Aiko tana ganin hakan tafad'i qasa luuuu sumammiya... Mahaifan ADAMS Mahaifan NUFAISAT Mama Mahaifiyar TAUDHAT YAWO Y'an uwa da abokan arziqi Jama'ar gari.. Ba wanda bai zubda hawaye akan mutuwar ADAMS da NUFAISAT ba..😭 Mutanan azziqi.. Masu gaskiya da amana. Masu san mutane. Masu ruk'o da addini. Masu yarda da qaddara.. (Ina san nidake dakai me karanta wannan littafi nawa na LEEKITAN ZUCHIYA muyi koyi da kyawawan halaye irin nasu.. Dan muyi mutuwa irin tasu. Irin mutuwar da kowane musulmi yake so. Wato cikawa da kalmar shahada. Bacin hakan jama'ar gari da yan uwa suyi kukan rashinmu. Suta fad'in alkairin mu. Suna binmu da kyakkyawar addu'a irinta fatan alkairi agaremu.) Ammi da Dady sunyi kukan rashin ADAMS da NUFAISAT kamar ransu zai fitta.. Haka mommy na NUFAISAT da Dadynta da ƴar uwarta Zainab sunyi kukan rashinta kuka bana wasa ba.. Haka Yusuf bai tab'a tunanin zai rasa ADAMS nan kusa... Dan qaunar ADAMS yake har cikin b'argwansa.. Komai jiyayi ya tsaya masa cak dan ganin yayi babban rashi arayuwarsa. Ya saka a zuciyarsa zai rayuwa da MUSLEEMA rayuwa irin ta gaskiya da rukwan amana.. Haka MUSLEEMA ta bala'in fitta daga harcinta ganin rashinsu da tayi. Ta kamu da ciwan ZUCIYA dan akwalla ya ibeta shekara d'aya kafin aka samu kanta da lafiya.. Kullum tunaninta YAYANTA ADAMS da AUNTYTA NUFAISAT sun tafi sun barta... Ni akayima mutuwa ba kowa ba. Hakan take fad'i dazaran an sakata agaba dan taci abinci ko ana mata fad'a kan tatsaida tunaninta... Itama Haneepha shekara biyu tsakani tabi bayan NUFAISAT da ADAMS.. Sakamakwan amai da gudawa da tayi.... _________ ************************ Dake Yusuf ya saka aransa zai rayu da MUSLEEMA zai aureta. Sai kawai yaji aduniya ba macen da yake so kamar ita.. Dan haka bayan rasuwar Haneepha da wata biyu yaje gun Ammi yace mata shifa yana san a d'aura masa Aure da MUSLEEMA.. Lokacin MUSLEEMAN tana falan alokacin da yake maganar.. Dan haka Ammi tace mata to taji abinda Yusuf d'in yace shin ta'amince.. Kallan Ammi tayi hawaye ya zubo mata da cewa.. "Wallahi na amince tun sanda Ya ADAMS yace mai ya Aureni.. Murmushi Ammi tayi da sunkuyar da kai tashare hawayenta dan bata san taji an ambaci ADAMS d'in.. Yanxu yanxu sai qewarsa ta dameta..😭 Daurewa YUSUF yayi da qarasa wajen MUSLEEMAN ya share mata hawayen.. Da cewa.. "Gobe nake san a d'aura mana Aure Babyna.. Kallansa da sauri MUSLEEMA tayi dan aduniya bata ba mance duk wata kalma da ADAMS ya kirata dashi.... Dan haka Ahankali tace.. "Ko yanzu ne INA san a d'aura Ya Yusuf.. Qara share mata hawayen yayi da fad'in.. "Kin tabbatar.. Da sauri ta d'aga masa kai alamar tabbatarwa.. Saiko ya tashi da kallan YAWO yaci gaba da cewa. "Zamma Dady magana yanxu YAWO. Tunda gobe jumma'a ne za'a d'aura Auran namu bayan idar da sallar jumma'a.. Dan Allah YAWO kar kibi tasu Ammi kan saisun sharyamin ita kafin akawota. Kawai idan dai dare yayi akawomin ita haka. Danna shirya mata komai.. idanko kunyi zanzo da kaina na d'auki abata... Yana fad'in hakan ya ficce daga falan ya nufi wajen shaqatawar gidan dan ganawa da Dadyn.. Murmushi ammi tayi cikin matuqar qaunar YUSUF.. Dan tunda suka rasa ADAMS ya qara shige musu yana nuna musu idan sun rasa adams ai suna dashi shi da Salim.. Wannan abu yana yima Ammin dad'i.. Haka YAWO tasa ammi tasaka aje wajen masu saidai maganin gargajiya anemo mata wasu saiwa ta had'ama MUSLEEMA maganin manta da bazawa kake tare. Kawai kalleta a budurwa..😂 Aiko nan Ammi tasa y'an aikinta sukaje suka samoma yawo duk abinda take buqata.. Sannan ta daka na dakawa tabada na dafawa a dafa mata.. Nan tahad'ama MUSLEEMA me zafi🙈. Ita kanta MUSLEEMA duk da a ranar tafara amfani da had'in amma sanda taji canji ajikinta.. YAWO fad'i take dama saboda y'ar albarka NUFAISAT naqi yimiki had'in mallakar miji. Saboda nasan idan nayima NUFAISAT d'in haka ban kyauta mata ba. Amma yanxu tunda Allah ya d'auke su Yusuf ya shiga uku..😂 Murmushi MUSLEEMA tayi Kawai tana qara tuna NUFAISAT da mijin nata ADAMS.. Nan hawaye ya zubo mata. Itama YAWON hawayen ne ya zubo mata tayi saurin sharewa wai dan karta qara karyarma da MUSLEEMAN zuciyata.. Aiko a washe garin ranar aka d'aura Auran YUSUF da MUSLEEMAN.. Auran daya tara manyan mutane.. Dan abokan takar YUSUF da ADAMS ba qaramin qarama YUSUF d'in Farin jini tayiba agun jama'a.. Hakan yasa aka san YUSUF d'in kamar yanda aka san Adams d'in.. Haka kuma kunga Dady ne yaba YUSUF d'in Auran MUSLEEMAN Wannan yana d'aya daga cikin abinda yasa Auran ya samu Albarkan matane masu mugun yawa.. Aranar ko aka kai MUSLEEMAT gidan YUSUF.. Gidan da YUSUF ya d'au shekara da shekaru yana tsari akansa... MUSLEEMA tayi kuka tayi kuka kamar ranta zai fitta.. Sakamakwan tunawa da tayi ashe zamanta da ADAMS da NUFAISAT na d'an wani lokaci ne..😭 Kafin akaita gidan sanda YAWO tace mata karta kuskure tabari YUSUF ya tare da ita awannan rana tadai bari sai bayan tagama shanye maganin tunda na sati d'aya ne.. Toh MUSLEEMA tace mata sannan suka mata nasiha sosai aka kaita gidan YUSUF d'in.. Salim qanin ADAMS ne kawai ya rako YUSUF d'in gidan nasa.. Dan yanxu shine wanda YUSUF d'in ya yarda daya shiga al'amuransa.. Kasancewar yayaba da Hankalinsa Tsiya Salim ya shiga yima MUSLEEMA akan wai takula mai da yayansa akaro na biyu kamar yanda takula mai dana farko imba haka ba zai hukuntata.. Murmushi Kawai MUSLEEMA tayi kanta na cikin mayafi kamar dai yanda amarya me kunya takeyi idan ankaita d'akinta.. Bayan Salim d'in ya tafi kulle makeken gidan nasa YUSUF yayi da dawowa gurin MUSLEEMAN. Ahankali ya d'ane gadan da yaye mata mayafin kan nata yana cewa.. "Haba Babyna. Wannan rufe kai haka aisai zafi ya illatarmin dake.. Murmushi tasakar mai.. Saiya kama hannunta taji wani zirr shima yaji amma yayi fuskar daci gaba da cewa.. "Mu biyu iyayanmu suka Haifa Baby. Daga ni sai qanwata.. Ina matuqar santa da yawa dan haka ina san kema ki sota dan Allah da gaskiya dan yanzu bata kowa saike.. Kinga Hajjiyanmu me kula damu bata nan. Tabi bayansu ADAMS.. Dan Allah matata karki saka wani abu aranki akan qanwata wanda zaijamin matsala dake.. Ina sanki MUSLEEMA Sannan ina san qanwata.. Ina san kizama uwa agareta tun daga yanxu duk da cewar zama ta iya girmanki Kinji.. Qara kafeshi da ido MUSLEEMA tayi da cewa.. "Wallahi zan rayu da qanwarka lafiya da gaskiya da amana har izuwa ranar da zamu kaita gidan mijinta kai har qarshen rayuwarmu mah. Dan banci karo da wani mugun hali ba azamana da kakata YAWO. Sannan na qara samun wata tarbiya agun Auntyna NUFAISAT.. Haka na samu adalci aso tsakanin zamana da YAYANA ADAMS.. Ina tabbatar maka bazakayi dana sani azamana dakai ba.. ____YUSUF ayanxu ya girma sosai dan zaikai shekara talatin da tara ko arba'in a takaice.. Amma idan ka kallesa zakayi tunanin d'an ishirin da takwas ne. Saboda yanda Hutu yake tare dashi sam bashi da wata matsala a rayuwarsa.. Yana matuqar buqatar mace me Hak'uri me kyau wacce tatara duk wani abu da namiji yake buqata agun mace.. Sannan yana buqatar mace shagwabb'iya wacce tasan salo kala kala na shwagwab'ar... Tunda ADAMS ya mutu YUSUF ya tabbatar MUSLEEMA tatara dukkan way'annan abubuwan da yake so agun macen Auransa____ "Yauwa Babyna nagode sosai da bani Wannan tabbaci da kikayi.. Ina san yanxu kije kiyo alwala muyi sallar godiya ga ALLAH... Cikin sauri MUSLEEMA tace.. "Bana sallah ina al'ada.. Waro ido YUSUF yayi cikin damuwa yace.. La'ilaha'illallahu.. Murmushi MUSLEEMA tasakar mai da cewa.. "Muhammadan rasulullahi sallallahu alaihi wassallam. Meya na saurin sakar salati haka.😀 "Baby bazaki gane ba. Ina cikin wani hali yau. Wallahi buqatarki nake da gudu... Murmushi tayi da fad'in.. "Kaga dama fa wasa nake maka duk da dama YAWO tace min wai... Saita rufe ido da hannayenta taqi qarasawa.🙈 Murmushin jin dad'i yayi da zare hannuwanta daga fuskar tata Yakai bakinsa cikin nata ya fara aika mata dame zafi. Saura kad'an ya shid'ar musu da ƴar mutane.. Yadai barta sun gabatar da sallar godiya ga Allahn.. Yayi mata tambayoyi akan addini. Ta bashi amsa gamshashshiya.. Kana ya ciyar da ita abubuwan da kowane ango yake ciyar da amaryarsa adaidai Wannan lokacin. Wato kaza da madara.. Kana ya fara b'ata tunaninta bayan ya d'auketa ya kaita shashinsa.. Nan ya fara Sarrafata kamar na'ura... Saidai fa qarshen tafiyar kuka YUSUF yasakarma MUSLEEMA da girmansa yana harkar yana godema ADAMS daya bashi wasiyar Auran MUSLEEMAN.. Itama kukan take mai dan taci wiya ba d'an kad'an ba. Tayi qoqari ma dabata sume masa ba. dan sosai Yusuf ya juye mata abubuwan daya d'auki shekara da shekaru yana tattalinma wacce taci nasarar mallakarsa.. Washe gari bayan yadawo daga masallaci daninta yayi zaune a gefan gado da alama fitowarta kenan daga wanka... Haka ya durgusa a gabanta da kama hannuwanta yace da ita.. "Wallahi Babyna ban tab'a tunanin dake zan faro rayuwa ba... "Nima haka mijina. Ban tab'a tunanin zanyi rayuwa dakai ba.. "To yanxu ya jikin naki "Da sauqi kawai zance maka mijina.. Dan kasan ka juye min da yawa.. Murmushi yayi da fad'in.. "Yanxuma zan qara juye miki dan bana jin zan iya dena juya miki idan har zanyi ido hud'u dake.. "Wayyona Allah🙆🏻‍♀ wallahi Ya YUSUF zaka kashe matarka nan kusa.. "Idan na kasheta nayi rayuwa dawa..😳 "Toh kawai kadaure kana juyewa bayan kwana uku uku.. "Wannan ne kuma bazan iya.. Tukunna ma!!! Gayamin. "Me kakeso kasani mijina.. "Lokacin da kike tare da Adams yana barinki har na tsawan kwana uku... "Toh ai lokacin mu biyu ne. Kaga dole na dinga samun hutu.. "Toh shikenan zan qara tabiyu kawai dan kidinga samun hutun.. "Ai mijina kishiya idan irin Auntyna ce ina santa ina qaunarta har agidan aljanna. Magana ta gaskiya ayanda najika adaran jiya bana fatan ka kahad'a da wata y'a mace dan tazama kishiya agareni.. Zanji ba dad'i sosai araina idan taji abinda naji akanka daran jiya.. Dan Allah mijina kabarni na rayu dakai ni d'aya.. Badan ina qin kishiya ba. Saidan bani san irin TAUDHAT datasa AUNTYNA kuka da YAYANA. "Idan ko haka ne. To ki'iya ibewa idan na juye miki. Zan rayu dake ke d'aya babu qari.. Wallahi tunda nake arayuwata ban tab'a san wata y'a mace kamarki ba MUSLEEMAT.. Kuma hakan ya farone daga lokacin da ADAMS ya danqamin wasiya akanki. Sannan na qara jin hakan a daranmu na jiya... Murmushi MUSLEEMA tayi da cewa.. "Nagodema allah dayasa kaine kazama miji agareni akaro na biyu.. Saboda nasan zakaji da komai nawa. Ina baka tabbacin baka da matsala dani dan sai yanda kayi dani.. Sannan nifa Har na kwad'aitu dakata juyewa akowane lokaci dadai kamin kishiya..🙈 Murmushi yayi da sakar mata kiss yace "Bayan ji dake har da ƴaƴanki bazan bari suyi kukan rashin mahaifinsu ba. Dan qaunar ADAMS ajinina yake... ALLAH ya raya min Khalit da Kahlil & Rahma da little NUFAISAT.. yakai qarshen zancen nasa da tashi ya tasar da ita dakai hannunsa ga ware towul d'in dake jikinta.. Aiko cikin sauri ta rungumesa wajen shigemai da cewa.. "Ya dace kidena karanta labarin namu AUNTY RAHMA.. Dan kinji sirrinmu da YA ADAMS.. Yanzu ina rokwanki daki bar mana namu sirrin nida YA YUSUF haka.... Qara rungumeta YUSUF yayi cikin so da qauna yace.. "Barta kawai my Baby. Kedai bani nutsuwa nasamu kwanciyar hankali Kawai.. D'ago da fuskarta tayi zuwa ga kallansa takai bakinta cikin nasa bayan ta aika masa da zafi. Tace zan baka dukkan Farin ciki mijina... Saurin d'aukarta yayi niyar Kwantar da ita.... Sai kawai ta dafe qirjinta daci gaba da cewa wayyo ZUCIYATA.. Arikice YUSUF ya kalleta da cewa.. "Me yadami ZUCIYAR.. Tace "zafi take min yanzun nan.. Da matuqar tashin hankali yace da ita... "Dan Allah ki rufamin asiri dan LEEKITAN ZUCHIYAN ya mutu... 😂😂😂dariya MUSLEEMA tayi da dukan qirjinsa tace... "Toh kazama shi mana.. Yace. "Hmm Amma dagaske babu ciwan zuciyar ko.. Gyad'a masa kai tayi da cewa "Kwantar da hankalinka mijina idan ina tare dakai bani ba ciwan ZUCIYA.. Bare mufara tunanin inda zamu samo *LEEKITAN ZUCHIYA...*😍 Alhamdulillah *Ni Rahama Nalele Auntyn luv nasan dacewa na b'ata tunaninku*😍 Fatan Allah ga MASOYA LEEKITAN ZUCHIYA Ina tare daku akone yanayi da kowane lokaci.. Amatsayinku masu makaranta Wannan littafi LEEKITAN ZUCHIYA. Miyafi birgeku awannan littafi Miyafi saku nishaɗi Meyafi baku dariya Meyafi b'ata tunaninku Meyafi tafiya da tunaninku Meyafi baku tausayi Meyafi b'ata muku rai.. Wata jarumace tafi birgeku Wane jarumi ne yafi birgeku A cikin ƴaƴan rajuman wa kukafi so.. Shin rahama Nalele tabaku zafi har kun iya abewa😍😍😍 Alhamdulillah nagode ma Allah daya kaini qarshen wanga novel lafiya.. Dan Allah sister n brothers duk wanda a tsinci kansa cikin wani yanayi acikin dukkanin littattafaina ina rokwansa rokwanki daku yafemin. Allah ya qarama marubuta y'an uwana masu bin wannan noven nawa basira da fasaha.. Y'an mata way'anda suka karanta ina muku fatan samun mazaje na gari Haka matan aurema ina muku fatan Allah yasa mazajenku su soku fiye da yanda ADAMS yaso NUFAISAT fiye da yanda YUSUF yaso MUSLEEMA.. Na sadaukar da wannan littafi nawa ga dukkanin way'anda suka so shi.. Dan haka idan ya miki ina jiran comments daga gareku😍😍😍😍😍 1 *DAGA WASA ƘARAMAR MAGANA TAZAMA BABBAH* 2 *YA FARU AKAN KAI NAH* 3 *MATAR ƳAƳANA* 4 *MATAR KAMAL* 5 *HAYATUDDEN* 6 *AURAN DA A ƘAUYEN FAGO* 👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻👆🏻SUNE MASU FITOWA DA IZININ ALLAH INA KUMA ROKWAN ALLAHN DAYA BANI DAMAR RUBUTA MUKU SU CIKIN LAFIYA NA ƘARE DA NASARA. Yanxu naku zanyi y'an mata.👍🏻👍🏻👍🏻👍🏻 By AUNTYN kamar yanda kuka rad'amin😍😍😍luv u 🙅🏻‍♀..