*KNKB2001* *Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 05521790550,ban da tsarin kati wannan karo a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488* Duka na tattara yaran muka bi Jamal zuwa gidan Mama hankali tashe,Har da Hafsah muka iske gidan cike da mutane,Kawayen mama da su Anty Binta,Anty mahma da sauran makotan abokan arzuka. Yadda naga Mama na kuka sai da ta karyamin zuciya ni kaina na shiga tashin hankali mai tsanani. na kasa dora wannan sabuwar kaddarar data bullo mana lokaci d'aya a kan mizani. abu d'aya na sani ina da yakana da yakinin na yarda da Allah sannan na aminta garesa kowani tsanani yake,kuma dukkan sauki daga garesa ne. Sai ban bi ayarin yan kuka ba. Na koma gefe ina hailala da yi ma Allah kirari da istigifari,domin nema ma Yaya ishaq mafita da salama acikin sabon halin da ya wayi gari acikinsa. Ganin ba wanda ya tuna da kiran mutanen karofi sai na Dauki wayata na fita daga falon Mama nayi nisa da Hayaniyar mutane,na kira Goggo na shaida mata abunda ke faruwa Allah Sarki dan'uwa rabin jiki sai Goggo ta Rud'e hankalinta ya tashi ta dinga Daukan Salati tana Direwa,mun rabu tace gatanan zuwa bari ta shaida ma su Yaya Isa halin da ake ciki. Ni da kaina na kira Yaya Asiya na gayamata Halin da ake ciki. itama tana ta salati tana Direwa,kowa in yaji abunda ya faru sai ya tambayi garin yaya..?mu kuma bamu da masaniyar yadda abun ya faru,abu d'aya muka sani ana Tuhumarsa da Batar wasu makudaden kudad'en gwamnati, lamarin akwai d'aga Hankali aciki. Zuwa yammah gidan Mama ya cika da jama'a yan jaje da masu zuwa kallon abunda ke faruwa suna komawa gefe suna dariya. Da yammah hatta Dangin Mama na yamai sun iso mazan su da matansu har da Hure,itama sai uban kuka take yi ba kiran sunan Allah ballatana Salati. Goggo ta iso tare da Yaya Isa da Yaya Salisu,basu jima da zuwa ba sai ga Hajiyar Dala ita da megidanta ashe yana gari duka an taru a falon Mama ana faman maida zencen,ni dai ina gefe sanye da Hijabi bazan ce ban yi kuka ba sai dai ban yi kuka na fitar Hayyaci da su mama suka dinga yi ba. ni nafi muka duka lamurana ga ubangijina, yara ma haka suke kuka tun ballatana ganin manya nayi Amir kad'ai ne bai yi kuka ba,sai Hawaye domin shi yazo wajena yana fadin"Umma da gaske yan sanda sun kama Daada.?shikenan bazai Dawo ba..? Sai na jawosa jikina na share masa hawaye Lokaci d'aya ina fadin"Basu kamasa ba sun dai rikesa suna masa tambayoyi,ka yi ma Daada addu'a da ikon Allah zai jibanci lamarinsa, Sannan ya warware al'umaransa ya Dawo gida lafiya" Sai ya dagamin kai Daganan bai kara kuka ba. na riga na cusamai yakinin Da sanin Allah komai ya faru sannan garesa ne dukkan wata mafita take. Mijin Hajiyar Dala babba ne a matakin gidan Soja yasan manyan mutane sosai sai bige bigen waya yake domin nemam makaman zencen,Ammh shuru kake ji har Dare sallah kawai ya fitar da mazan matan mu kuma muka gabatar da tamu acikin gida, A d'akin Badariya nake yada Saukata in nazo tana kwance sai kuka take yi, su Anty Mahma na bata baki da na idar da sallah ina azkar Lokaci d'aya bakina na motsi ban jirka daga inda nake ba sai da na Daga Hannunwana na rokar ma Yaya Ishaq sauki da salama acikin kaddaransa,na Roki Allah ya kubutar da shi cikin Aminci. Tare muka shafa addu'an da su Anty mahma ta kalleni tana fadin"Sannu Fa'iza kin fi mu karfin gwiwa,muma bari mu tashi mu yi sallar mu roki Allah sauki kan al'amarin yafi wannan koken koken da muke ta yi" Nayi yake ban ce komai ba,kamar bazan yi mgana ba ammh kukan Badariya ya Dameni sai na karisa kusa da ita na zauna na Dagota zaune ina Share mata Hawaye ta kalleni nima na kalleni, kafin ta kara saka kuka tana fadin"Anty Fa'iza Yaya ishaq bamu san wani Hali yake ciki ba..Mama nata kuka" Sai ta fada jikina ni kuma sai na riketa ina Lallashinta har sai da ta samu natsuwa sannan na kalleta ina Fadin"Kuka ba mafita ba ce Badariya.in mun yarda Allah ke da Kaddara sannan shike da sa'a da Aminci to mu mika masa duka Kukan mu, sai ya Dudemu ya share mana Hawaye.Tashi ki yi sallah ki rokar ma yayanki sassauci da warwarewar al'amarinsa,sai kiga da ikonsa komai ya Daidaita" Da ga alamu mganganuna sun shigeta nan take ko ta mike ta shige Tiolet Halisa na gefe tayi tagumi sai itama ta mike tana fadin"Madallah da wannan Tunatarwa taki Anty Fa'iza.Da su mama ma za'a samu mai Tunasar da su da sun bar wannan kukan sun koma ga Allah" Anty Mahma tace"Mai dakatar da kukan Mama abu d'aya ne sai in Ishaq din tagani a gabanta kila sai kukanta ya tsaya" Ni dai ina jin su ban ce komai ba,Dakin na bar musu na fita falo neman su Ahmad,Saboda Halin da gidan ya yini ko abinci ba wanda ya nema ni kuma naga in mu manya ne yaran fa..?sai na shiga kitchen na Dafa musu jallop din taliya na zubo musu ina bin yaran daya bayan D'aya ina ba su suci abinci,ashe Anty Binta na takaice dani,D'an wajen Anty mahma ke kusa da ita na nufesa da karamin Filet din na zubamai ina fadin''Anwar taho kaci abinci..". Ba zato kawai naji an yi sama da Filet din ya koma ya kife a kasa sai hankalin kowa ya koma kanmu Anty Binta na gani tsaye a kaina Tana faman Huci Idanuwanta sun kala sun yi jajir ta nuna ni da yatsa tana fadin"Acikin wannan halin da muke ciki ke har ta abinci kike..?ina lura dake tun dazu abunda ya faru bai Dameki ba, kamar ma murna kike da Faruwar haka me ake da auran mace irin ki Fa'iza macen kaddara macen da bata san mijinta ba" Sai na kame a tsaye na kasa mgana sai dai na Sadda kaina kasa Mama ta Dakata da kukanta tana kallona, sai kuma aka rasa me mganar mazan duk suna waje ana ta buge bugen waya domin samun mafita. Anwar ne yabi taliyar kasa yana ci,Alamun yana jin yunwa wata kawar Mama tace"yara fa najin yunwa, tayi Dubara da ta dafa musu in mu mun hakura saboda tashin hankali,su yara ne basu san komai ba" Goggo tace"To shi yaro ma me ya sani.?shi dai yaci ya koshi" Ganin ba'a bata gaskiya ba sai ta fara Borin kunya tana fadin"ku fa ganta wlh ko Damuwa ma batayi ba.kamar cewa ma take gwara da akayi hakan" Goggo ce ta shigar min cikin bacin rai tace"Assha.Haba Binta ta ya ya mijin ta uban ya'yanta na cikin wannan Halin kice bata damu ba..?ai ba kowacce damuwace ke nuna kanta ba, in mu muna nuna Damuwar da kuka ita sai ta fimu hankali ta nuna Damuwarta wajen Ubangijin komai da komai, kinga kenan tafi mu Dubara mai kyau" Sai aka fara fadin haka ne kuwa a wajen,ba'a bata gaskiya ba. ganin bata samu nasaran tozartani ba sai ta kalleni a wulakance ta juya ta tafi ni kuma sai na Dauki Anwar na tafi da shi domin na zuba mai wani abincin na basa yaci kada a Dauki alhakin karamin yaro da yunwa. Har dare ba wata mgana mai Dadi,Domin har alokacin mahaifin zainab yace basu bari an ga Yaya Ishaq ba, duk mazan nan suka kwana da Safe kuma suka hadu suka Dauki Hanyar Abuja har da mijin Hajiyar Dala da shi a Hotel ya kwana da Safe da shi da Tawagansa suka Dauki Hanyar Abuja. Nan kuma Yaya isa da su Jamal da Kawun Mama dake yamai da suka iso jiya,suka tafi tun a hanya ake ta kiransu sukace basu isa ba,bayan kuma sun isa sai suka daina Daukan wayoyin mutane hankula suka kara tashi Sai Dare sannan Hajiyar Dala tayi waya da megidanta yace shi ya wuce kano ma ammh yana ta kokarinsa abu ne da ya had'a da Gwammati, sunce zasu Tuhumesa ne kuma har Lokacin basu bari an gansa ba. Wannan labarin ya kara Tada Hankula cikin kwana Biyu ba'ayi barci cikin salama ba,Yaya Asiya tazo jaje ita da ya'yan Goggo na Karofi har da Yaya mariya nima makotana duk sun zo,yimin jaje abun duniya baya boyuwa Tuni mgana ta bazu a gari,Mutane na maau saran Zobo da kunin aya a wajena suna ta kirana bani da sukuni ga masu son Turaren kamshi har da masu biki na abinci, bani da sukuni hakuri nayi ta bama Mutane ina gaya musu halin da nake ciki na Mijina na Hannun masu Binciken Gwamnati a abuja. Goggo tunda tazo bata koma ba tana tare da Mama tana bata baki Hajiyar Dala data kwana biyu sai ta koma cikin kwana Biyar mama ta fita Hayyacinta su Anty Binta sun gaji da kukan sun hakura, Tuni wadanda sukaje Abuja sun dawo labarin bai Sauya ba, sai dai sun tabbatar da cewa Mahaifin zainab na iya bakin kokarinsa haka ma Mijin Hajiyar Dala ana ta shiga da fita. Ganin sai zama haka kawai muke yi,Sai nayi tunanin gwara na tattara yara mu koma gida mu cigaba da gayama Allah,tunda ko mun zauna anan gidan abunda Allah ya tsara shi zai faru kuma bamu isa mu sauya masa kaddara ba, sai dai in muna addu'a sai kaddarar tazo masa saukakkiya. Kwanan mu shida da Safe na samu Mama a dakinta ita da yan'uwanta na yamai bayan na duka na gaisheta ta amsa muryanta a shake kaina na kasa nace mata zan kwashe yara zamu koma gida, sai kawai tayi shuru batayi mgana ba,Hure na gefe sai ta tabe baki kafin tace"Ai ba sai kin gayamata ba ki yi gaban kanki kawai.Ai Anty ita ke da rashi saboda ita ke da D'a" Baki da asara ko da an rasa Ishaq" Sai mganganu ya fara tashi a tsakaninsu Mama ce ta katse da fadin"ku kyaleta ta tafi.." Muryanta a shake ni kuma ganin haka sai na sanyaya murya ina fadin"Mama naga zaman bai da amfani ne ga d'awainiya gwara mu koma gida sannan ga makarantarsu duk ya tsaya zamu cigaba da gayama Allah a duk inda muke da ikonsa komai zai warware" Wani kallo Mama tayi min kafin tayi tari ana mata sannu sai ta kara kallo kafin tace"Na dad'e da sanin baki da asara a komai Fa'iza, ki yi tafiyarki Domin zamanki bai da amfani ammh ki bar masa ya'yansa anan su d'in Dolensa ne saboda Mahaifin su ne, in suka rasa sa bazasu taba samun madadinsa ba" Daga haka sai ta koma ta juyar da kanta tana share hawaye, jin abunda ta fada yasa na tashi na fita ni ba haka ne nufi ba ganin ta min gurguwan fahimta sai na fasa gudurina. Goggo na sama na gayama yadda muka yi da Mama sai ta Dafa kafadata kafin tace"Da kin nemi shawara ta da baki yi mata mgana ba,me neman kuka ne fa aka jefe shi da kashin awaki.Ki rabu da ita ki zauna din har muga abunda Allah zai yi" Tun da Goggo ta fad'amin haka sai na bar mganar Tafiyar ashe na gudu ban tsira ba mgana ta ding yawo tsakanin Dangin Mama da kawayenta Anty Binta Kirkiri a gabana tace Daman ban damu ba so nake nakoma gida na cigaba da sana'ata tunda shine a gabana,naji haushin wannan mganarta kuma ban kyaleta ba sai da na kalleta ido cikin ido sannan nace"Ko ban damu saboda yana mijina kuma uban ya'yana ba.Zan nuna alhini na saboda yana matsayin Yayana wanda iyayenmu suke abu d'aya ballatana shi din Uban ya'ya na ne" Daga haka na huce na barta,sai ta fashe da kukan nayi mata rashin kunya mgana taki ci taki cinyewa Goggo ta kashe mganar da Fadin"Haba Binta mu bar wannan ceceku cen tunda ba shi ba ne a gabanmu.Mu ji da abunda ke gabanmu don Allah" Ammh Anty Binta batayi shuru ba sai da tace"Ai gani tayi tana kama kud'i sai ta dauka daidai muke da ita.Abunda bata sani ba komai lalacewar Daji bai kai in giwa ta mutu kiyasha ya jata ba, ko tana mace tana da Madaukakiyar Darajarta" Dakyar mgana ta mutu sai da Wata kanwar uwa take ga Mama ta tsawarta ma Anty Binta sannan mganar ta Dakata ammh tana ta kananun mganganu a kaina niko bansan tanayi ba ina Dakin Badariya. Washegari ya kama Sati daya kenan da labarin da iso mu,an yi an yi an shiga an fita duka labarin bai sauya ba,Hankula ko sun fara kwanciya sai su kara tashi jin ba wani labari mai Dadi. Sai a ranar muka yi waya da Zainab da yake muna da lambar juna sai dai mukam jima bamu yi mgana ba. sai in wani abu ya taso ko rashin lafiya,Ita ta kirani ni na shafa da ita ballatana ma na kirata, mun gaisa cikin Alhini muka yi ma juna jaje,Sai dai ban wani ji ta cikin wani yanayi ba,Ita take fad'amin mganar Yaya Ishaq sai manyan Gwamnati sun shiga tunda Fitar da kudi ne na ma'aikata kuma ta Office dinsa da saka Hannun sa komai ya fita ba yadda za'ayi ya fita,Tace Babanta ya samu ganinsa sau daya ammh har yanzu ba wani mganar su bada Belinsa,Mun dade muna mgana da ita nace mata ina gidan Mama tayi ta mamakin tace ita da yara sun koma gida sai dai bata bar zuwa wajen aiki ba,Saboda sun ki bata Hutu a raina nace Mama taji kuwa..?sai ga shi tana fadamin Ko da yaushe suna Mgana da su Mama,kuma susan tana zuwa wajen aikinta nan take na Fahimci abun,inda ake raina an fi kai Hari chan bangaran. Ranar da yammah sai ga Hajiyar su Raliya tazo,ni ina chan Dakin Badariya ban sani ba,Mama na ganinta da su Anty Binta suna ta Rawan jiki mama ta santa tunda kawancen Raliya da Badariya ba yau ba ne,Sai dai ita Hajiyar su Raliya ce bata zurfafa zumunci da Mama ba, sai kuma gashi ni jinina ya had'u da nata da zuru'arta. Bayan gaisuwa da jajanta abunda ya faru sai Hajiyar su Raliya ta nemi ganina Mama ta tabe baki kafin tace"Kila ma bata gidan domin tun jiya take son ta koma gida dayake bata damu ba" Hajiya batace komai ba,Da Badariya tazo gaisheta sai tace ta kira mata ni,Ina Dakinta tazo ta kirani ina jin tace Hajiyar su Raliya na mike na fita da Hijabi suna falo na duka na gaisheta cikin Fara'a ta amsa ni tana fadin"Haka ake yi Fa'iza abu ya faru haka bazaki kirani ki fadamin ba..? Sai dai naji a bakin Raly.? Kaina na kasa ban ce komai ba sai ta Cigaba da fadin"ba'a haka Fa'iza irin wannan sai ki kirani ki fadamin ko ba a Uwar kika Daukeni ba..?Goggon karofi ta karbe d'iyarta kenan.? Goggo na gefe tayi dariya kafin tace"Ba ruwana Hajiya ke da Diyar ki" Kaina na kasa na shiga bata Hakuri sai tace bakomai su Mama haushi duk ya cikasu kallona tayi tana fadin"Ya abun ya faru ne ina so na sani saboda naji in zan iya taimaka wa" Kafin nayi mgana Anty Binta ta karb'e da bayanin yadda ake ciki Hajiyar su Raliya,ta gyada kai kafin tace"Akwai Kanina yana aiki da Hukumar EFCC din achan Abuja, bari na nemesa naji ko zai iya taimaka mana" Nan da nan bakin Mama ya washe a gaban mu ta kirasa suka gaisa ta rattamai bayanin komai sai ya nemi sunansa da inda yake aiki Anty Binta ta fadamata sai ta turamai yace ta bashi nan da zuwa Dare zai bincika mata halin da ake ciki. Bata wani jima ba, tayi ma su Mama sallama,akan yadda akace in sha Allahu gobe zata dawo ita da sauran yaranta Mama godiya kamar zata kwanta mata Hajiya ta kalleta kafin tace"Bakomai kada ki damu babba ne a wajen zai binciko komai..Zan iya yin komai saboda Fa'iza kamar diya take a wajena Ahalina Ahalinta ne,zan iya bakin kokarina bazai gagara ba insha Allahu" Basa kaunar su ji an ambaceni kuma basa kaunar alfarma ta barayina har waje na rakata ni da Badariya,Direba ya zo da ita ta shiga mota tana ce min sai zuwa gobe,Ta tambayeni su Amir nace suna cikin gida,na dawo cikin gida naji ana ta maimaita zencen nidai a raina ina fatan Allah ya kawo mafita. Washegari da wajen yammah sai ga Hajiya ta dawo ita da Raliya da yayyin Raliyan suna zuwa ni suka nema daman suna zuwa gidana,Ita kuma Hajiya ta nemi su mama ta gayamusu halin da ake ciki,Hukumar ta na bincike ne,sannan akwai yuyuwar komai da ya fita da saka hannun Yaya Ishaq saboda haka in sun gama Bincikensu zasu yi mgana, sannan sun hana Belinsa saboda cases din na da girma Hankula sun kara tashi tace dai a Dage da addu'a komai zai daidaita. Wasa wasa har an shud'e Sati Biyu shuru dai mgana d'aya sai sun gama Bincike,Gajiya nayi da zama na Tattara na koma gida na da yara Goggo ma ta koma Karofi mama an barta da Anty Hure ne mutum yamai suma sun koma kowa ya Saduda yasan Allah ke yi,Mama ta saka ana ta Sadaka da Saukan Qur'ani ni kuma agida banzauna ba ni da yara muna ta kai ma Allah kukan mu,Ban kara bi ta kan Zobo da kunin aya ba,Saboda Halin da nake ciki ko makaranta yaran basu koma ba Hafsa ce ta koma makarantar ta tana zuwa. Wajen wata da'ya da Tsare Yaya Ishaq aka bama yan'uwansa Daman ganinsa Su Yaya Isa dai suka koma Abuja mgana ta tabbata ba yadda Yaya Ishaq zai fidda kansa saka hannunsa da yardansa aka fidda kudad'en,zai biya taran kudaden gabad'aya da tsabar kudi ko Kaddara. Lokacin da labarin yazo mana Sai murnan kowa ta koma ciki kudi ba kadan ba wajen Million 70,ina Yaya ishaq yaga wannan kudin ko Kaddara..?su Yaya isa sun dawo suna mganar ya lissafa abunda ya mallaka, gida biyu nan katsina d'aya sai na Abuja sai mota sai gidan mahafinsa,Sai tsabar kudi miliyan d'aya da rabi asusun bankinsa sai fili a nan katsina,Hukumar tace zata zo ta Duba duka kaddarorin zata kwace zai zama karkashinta. Sai naji na rude ina ta maimaita innalillahi acikin raina Hankali tashe na kalli Yaya isa ina fadin"Aikin sa fa Yaya isa..? Ya kalleni cikin Tausayawa kafin yace"Ba mganar aiki Fa'iza ya samu ma ya fito lafiya" Su mama sai kuka Daman a gidan ne ake maida zencen,Agidan muka kwana Dagani har yara saboda ana saka ran dawowar Yaya ishaq acikin Satin. Haka ko akayi hukumar tazo ta Duba Gidajen da Yace kada a saka gidan Mama,Mama ta saka kuka miye amfanin gidan in bashi a Had'a dashi,Sannan akwai tsabar kudi a wajenta na sana'arta miliyan uku Anty Binta ma ta saka miliyan Biyu,suka tura ta asusun bankin Ishaq,Saboda kudin su rage nauyi. muna ji muna gani Hukumar ta kwace gidan da muke ciki da gidan Mama da filin da ya siya acikin gari chan ma Abuja ta karbi wanda zainab ke ciki da motar hawansa, sannan sun bamu Notice Wata daya mu tashi Saboda wajen ya zama mallakin Gwamnati Lalle mun ga tashin Hankali mai suna tashin hankali,Wannan labarin sai dai mun Dauki Dangana tunda zasu sake sa,Bai amsa laifinsa ba ya riga ya rantse bai da hannu akan lamarin, zasu sake sa ammh ba su kyalesa ba in bukatar wani Binciken ya shigo zasu kara nemansa,Shima da taimakon manya acikin lamarin mijin Hajiyar dala da Kanin Hajiya dake hukumar tare da Mutanen Mahaifin Zainab Dr.Lawal bako. Mama ta tsine ma duk wanda ya saka Danta cikin bala'i tayi mugayen addu'o'i akan sa,Ta ce tunda ya jefa Rayuwar d'anta cikin bala'i shima bazai ga rayuwa mai kyau ba. Watan Yaya Ishaq biyu a Hannun Hukuma suka sakesa,Daga Abuja tare da Dr.Lawal da Zainab da yara, sai su Yaya Isa da su Jamal suka iso da shi katsina ko da suka iso karfe goman Dare ne an so ya kwana sai gobe yace Zai je yaga Mama yasan tana cikin Damuwa. duk da Dare ne, gida cike yake da masu dakon dawowarsa. Mama na jin Dirin motarsu ta Fice da gudu ita ta bude masa Mota ya fito Allahu akbar Duk wannan fafan da kyau da nasabar ta Yaya ishaq ta tafi cikin wata Biyu. ya rame ya fita Hayyacinsa sai sumar kai da kasumba ta rufe masa fuska, yayi duku duku kamar ba d'an kwalisa Ishaq Kabir Karofi ba. *03/07/2023* *Janafty* *KNKB2002* *Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 05521790550,ban da tsarin kati wannan karon. a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488* Mama ta rikesa cikin Fitan Hayyaci,da Dimaucewa ta furta"Ishaq.." Ashe zan sake ganin ka..? Sai ta rushe da kukan da ta Dade tana yin sa ammh na yau na Dabam ne, cike yake da tsantsan farinciki sannan hade da fargaba da fidda tsammani. Rumgumeta ya yi shima cikin wata murya mai cike da laushi da sanyi yace"Mama.." Sai ya kasa mgana gabad'ayan mu muna kansu,mu kanmu Tausayin ya kamani dole ka tausaya ma uwa indai ta bangaran abunda ta haifa ne. Dakyar Mama ta bari aka shigo da Yaya ishaq gida,ko kan kujeran da ya zauna tana kusa dashi kuka take yi tana Sharb'ewa fadi take yi"Duk wanda ya yi sanadiyar shigar ka wannan Halin Ishaq Allah ya Dai'Daita sa,ya hana sa zaman lafiya a cikin wannan duniyan" Sai ta kara fashewa da kuka tana cigaba da fad'in"Tsakanin mu da shi Sai Allah ya isa bazamu taba yafe masa ba" Shi ko yana ta faman lallashinta Fadi yake yi"Ba ga shi na dawo ba Mama? don Allah ki daina wannan kukan hakanan" Su Goggo kuwa sai sannu Ishaq kawai suke ce masa yana amsawa Hajiyar Dala tace"Sannu Ishaq ka auna arziki Allah ya kyauta gaba" Cikin yanayin Sanyi jiki yake amsawa Badariya da Anty Binta suka rumgumesa suna koke koke yana mirmishin karfin Hali yace"Kuka dai..?ba ku gani ina lafiya, Daddy ka fad'a musu ba wanda ya Dake ni fa" Dr.Lawal bako na zaune a gefe ya murmusa kafin yace"Tun muna Abuja nake fadama Jamal haka,ammh bai bar kuka ba kamar wani mace" Sai aka juya ana kallonsa yana ta sharban Hawaye Ishaq yamika masa hannu yazo kusa da shi Cikin karfin Hali yace"Kun gani ina lafiya basu dake ni ba in baku bar kuka ba,Mama ba zata bari ba" Ni ko ina gefe daya ban tusa kaina ba Farhan ne a sabe a Hannuna yana ganina ya kirani"Umma.." Ni kuma na Chabesa da yake har Hutu an taba kawosa wajena kuma indai suna garin to yana wajena sosai yaron ya saba dani. Sai dai nayi hamdala da godiya acikin raina da ya kubutar da shi Lafiya,duk da an rasa aiki da dukiya sai dai an gode Allah Yaran dake d'akin Badariya basu san abunda ke faruwa ba,suna tare da Halisa,Su na kyalla ido su ka gansa sai suka nufesa suna kiran sunansa "Daada.." Da sauri duka ya Tare su Anum ce akan gaba sai musty da Ahmad Amir dai a gefensa ya zauna yana fadin"Alhamdulillah Daada ya dawo" Mirmishi ya saki ya shafa kansa yana fadin"na dawo Baba na" Anum ta fashe da kuka su Ahmad na tayata Ishaq ya fara lallashinta sai ta tsagaita tana fadin"Daada.." Sai shesshekan kuka ya tareta sai ya rumgumeta yana fadin"Ina fatan baku yi kuka da baku ga Daada ba ko..? Anum tace"Bamu yi ba da mun fara Umma zata hanamu sai tace mu yi maka addu'an Allah ya kubutar dakai,mu addu'a muka yi ta maka" Amir ya karbe da fadin"Umma nata karatun Qur'ani ta d'aga hannu ta na ta maka addu'a Daada nima nayi maka sosai" Gabada'yan falon sai yayi tsit ana Sauraran yaran Yaya ishaq jikinsa ya karayin sanyi kaunar ya'yansa ya kara kamasa ya kamasu duka ya Rumgume yana Dagowa muna Had'a ido ina shirin na gaisheshi tare da barka da arziki karo na farko a Rayuwata tun da na san Yaya Ishaq da ya taba ambaton sunana cikin Tausasawa. "Fa'iza.." Idanuwana a bude na dago ina kallonsa shima ni yake kallo, ba ma shi kadai ba.kaf mutanen dake falon sai kallon su ya dawo kaina,mamaki da al'ajabi basu bar ni na iya amsa mai ba, sai ya kara shayar dani wani gumbar mamaki cikin karin Laushin da yayi ya sake fadin"Nagode..Nagode sosai da baki bari ya'yana sun yi kukan rashi na ba.ko achan in na Tunasu nakan shiga damuwa ammh da zarar na tuna kina nan sai naji sanyi a raina ina da yakinin zaki Kula da su fiye da yadda zan kula da su'" Ya karishe fada yana kallona da zurmamun idanuwansa da suka zurma Saboda wahala abun mamaki baya karewa har da mirmishi yayi min na Daskare a tsaye na kasa mgana Sabon Ishaq nake gani a gabana ko kuwa dai tsohon ne wanda na sani..? Ni kaina baki na yayi nauyi,Nauyin da dakyar na iya fuzgo mganar dake bakina sannu da arziki nayi masa, sannan na hada da Allah ya kyauta cikin yanayina nace"Allah ya baka ikon cin wannan jarabawar Allah kuma yasa a mizani" Cikin Muryansa mai cike da sanyi da Haiba ya amsa min da fadin"Ameen Fa'iza Ameen Ameen" Tare da su Goggo suma da suka amsa ni Ni dai tsabar mamakin da nake ci bai sakeni ba naji ana cewa ya kamata a barsa yayi wanka yaci abinci ya huta zuwa gobe da Safe. Mama da kanta ta rakasa har dakin Jamal ita da su Anty Binta,Mazan kuma fita suka yi Hotel zasu kama su kwana,Sai alokacin muka gaisa da zainab muna ma juna barka da arzikin Farhan na wajena ya makaleni tana Dariya ta bar min shi ta shige Dakin Mama inda ta saba sauka. Ni kuma daman ba ni da wannan gatan Dakin Badariya ne wajen saukata nan muka shige ni da yaran,basan ya suka kare ba ni dai daganan bayan na gama shirya yara sun kwanta nima na kwanta,Kafin nayi barci na dade ina tunanin Yaya Ishaq da Sabon Tausasawarsa gareni, wata zuciyar ta ankarar da ni da cewa kada na sakankan ce kada na manta Hukuma ce ta tsare shi na tsawon Lokaci yana cikin firgicin da bazai yin wani abu ba kada hakan ya rud'eki daganan na watsar da wannan Tunanin na kwanta barci,ammh sai da na tashi wajen uku na Dare na Dauro alwala nazo na yi nafilfilun godiya ga Allah. Washegari da na tashi,na riga na saba da aikin da jikina bazai iya zama haka ba,Hafsat bata nan tana Hostel wajen wata kawarta ta kwana tun jiya,Mun dai yi waya da asuba na fada mata Yaya Ishaq ya dawo sai tace ma ta gani a waya Badar ta saka,Sai da nayi sharan duka Dakunan na gyara nayi abun karyawa sannan na kama yaran nan duka nayi musu wanka, Goggo nata min sannu da kokari Su Anum nata Tambayan Daada Hajiyar Dala tace yana Hutawa ba'a so a damesa. Sai bayan na natsa na kira Yaya Asiya na gayamata sai da tayi hamdala,ta nuna alamun murnanta ammh Yaya Mariya ko ajikinta cewa kawai tayi Allah ya kyauta da nace ko zata zo ne..?sai tace min zaria zata tafi suna, kanwar mijinta ta haihu ban ja mganar ba, sanin bazata zo din ba Yaya mariya akwai kafiya da riko Daman sau d'aya tazo shima ba wai jaje tazo ba,Goggo ce ta dinga mata fada yasa tazo kuma har tatafi Allah ya kyauta bata iya ce ma Mama ba, Da Yaya Asiya ta mata fad'a bude bakinta sai cewa tayi"wani Jaje kuma Yaya Asiya..?Alhakin Fa'iza ne fa ke bibiyan Ishaq da danginsa" Bige mata baki Yaya Asiya tayi ta na mata fada sai bata kara mgana ba, kuma tunda tatafi bata Dawo ba. Chan da rana sai ga su Anty Nasara da mutanen karofi gida ya cika da yan Taya murna kamar Biki kawayen Mama har da yan'uwanta na yamai da suka yi sammakon tasowa da makota ammh Yaya Ishq din na barci har alokacin bai tashi ba, ana ta dai yi ma Mama barka da arziki bakinta Har kunne Hajiyar Dala tun safe ta bi mijinta suka koma Bayan Mama tayi ta Godiya,Kuma duk wanda yazo sai ta nuna Zainab tace ayi mata Godiya mahaifinta ne ya tsaya ma Yaya ishaq har aka sako shi,sannan sai ta zauna ta bada labarin sharri a ka kulla ma Danta,kawayenta na tayata mugayen addu'o'i ga wanda yayi sanadiyar haka. Ni dai ina gefe ban tusa kaina ba,Da kaina na kira Hajiyar su Raliya na fadamata tace sun yi mgana da kaninta ya fadamata an sakesa tace min zata shigo in ta samu sarari yanzu harkokin sun yi mata yawa ne,muka rabu bayan nayi mata fatan alheri da nasara,Yaya Ishaq bai tashi ba sai yammah ya rama Sallolin dake kansa yaci abinci Lokacim Tuni Goggo da iyalanta sun wuce Karofi sai ga Mama nayi mata godiya Goggo tace bakomai an yi ma zumunci ne. Ya iske Dangin mama da makota da kawayen mama da su Anty Binta,ana ta yi mai barka da arziki,yana amsawa kayan Jamal ya saka riga da wando sai naga yana yawo acikinta ahalin yafi jamal cikan namiji a baya sai dai zama waje d'aya da Tunane tunane yasa duk ya zabge. Ni aikina shine Saukewa da Dorawa da an yi baki Mama tace a kawo abinci da ance ya kare sai tace ina nake da bazan sake dora wani abu ba? ko meye amfani na.?daman nasan ba ni da amfani shiyasa ban damu ba Zainab kuwa yar gatace tun safe tana ciki tana hutawa tace min Kanta ke ciwo saboda tafiyar Mota Fadil ma ni ta bama shi nayi mai wanka na goyasa duk wanda ya ganni da goyo sai yayi mamakin sanin Tunda Ahmad ya girma ya wuce Goyo,Sai na juya aga Fadil ne,ni renon yara bai dameni ba kafin ma nasan zafin Haihuwa na iya kula da yara ballatana yanzu da na haifa nasan zafin su,Ni nake Dawainiya da yaran manyan da zasu iya cin abinci da kansu suci wadanda baza su iya ba na zaunar da su na basu,Zuwa Dare gidan ya watse sai na jiki jiki bayan sallar isha'i mahaifin Zainab ya iso daga chan inda ya kama yana Hutawa shima a falo aka taru har da ni ina chan gefe  fadil na Hannun kakansa yaran kuma suna jikin Baban su. Mgana yake akan gobe zai koma Abuja Mama da su Anty Binta suna ta mai godiya ya kada kai yana fadin"Bakomai Ishaq kamar Zeey na Dauke sa shima D'ana ne,Ina so na shaida masa kuma ku zama shaida,Na basu gidana na Abuja su zauna da Zeey Saboda bazata iya zaman wani waje ba in ba Abuja ba,nan ta saba sannan yaran nan sun fara rayuwarsu achan bazau yuyu a sauya musu muhalli ba sannan ta na aiki,Sannan kada ya damu nauyin komai ni zan Dauka kafin ya samu wani aiki zamu iya bakin kokarin mu bazai gagara ba In sha Allahu" Mama ta hau godiya har da Hawaye shi ko Yaya Ishaq mama ya kallah kafin ya kalli mahaifin zainab yace"Daddy ban ki mganarka ba,ba kuma don na raina kyautatawarka a kaina ba, sai don yanzu ba da ba ne.In a baya aiki ya kaini Abuja yanzu fa..?Ina ganin zamana a Abuja yanzu bamai yuyu ba ne" Kai tsaye batare da Damuwa ba yace"Why da bazai yuyu ba Ishaq..?ai auran soyayya kuka yi da Zeey, kai ka ganta kace kana sonta itama ta amince dakai na aura mata kai,kuma kai ka zabeta na tabbata zaka bita a duk inda take ballatana ma wannan ba abun damuwa ba ne kada kaji komai aikan ka ya kusa dawowa ko ba wannan ba wani zai samu kaji ko..? Zai sake mgana Mama ta Dake masa Hannu da kafarta ina lura da su ya Dago yana kallonta yana so yayi mgana ta hanasa har ga Allah sai da naku sa yin Dariya. Mama ta juya tana fadin'"Kai Alhaji mungode sosai Allah ya bar zumunci shirmen sa kawai yake yi me zai hana ya bita chan in ya zauna anan me zai yi..?mungode sosai Zainab ki tayamu godiya fa" Tana mirmishi tace"Bakomai Mama" Niko ina gefe araina nace wai me mata da iyalai ne ake cewa in ya zauna anan me zai yi..?ayi dai mu gani in tusa zata Hura wuta. Bai wani jima ba yayi ma su mama sallama da cewa gobe zai je kano ya bi jirgi zuwa Abuja.Yaya ishaq da zainab din suka fita rakasa jikokinsa na Hannunsa,ya dade yana Tattaunawa da yarsa kafin ta Dawo cikin gida har ga Allah naso mu koma gida sai naga ko shi kan shi Gogan bai yi mgana ba, kada nazo nayi mgana cibi ya zama kari sai nayi shuru da bakina ammh har ga Allah ina cikin Takura. Sai da muka shafe kwana Hudu a gidan mama yayi mganar komawar mu Gida Mama tace mutane na zuwa Jaje da murna ya zauna,Zainab kuma aranar Direba yazo ya Dauketa ita da ya'yanta ta koma Abuja saboda aiki a gabana a gaban su Mama tace ma Yaya Ishaq yaushe zai zo..?ina kallonsa ya gimtse fuska kafin yace bai sani ba sai ta wuce tana fadin zasu yo mgana ta waya Mama har bakin mota ta rakata kamar zata goyata saboda kauna. Mu kuwa sai da mukayi kwana Biyar naga zaman dai yaki ya kare na Tattara yara na nace zan koma gida,Sai yace mu tafi shi sai anjuma da Daddare jamal zai rakosa zasu karisawa Tattauna mganar da suka fara da Mama,naji dadi da bai hanani ba sannan itama Maman yan mutumcin na kusa batace komai ba ko da yake mai zugatan bata kusa Anty Binta kenan. Ina komawa gida duk yayi kura na zage na gyara ko'ina Amir na tayani shida Anum saboda na koya ma yara na aiyukan da basu da wahala saboda gaba,bayan mun gama muka yi sallar la'asar sannan na Dora girki Sa'adatu da Habiba sun shigomin daman sun je har chan gidan Maman sun min barka da arziki da su mukayi ta Hira sai yammah suka tafi,girki daman farar shinkafa ne Amir ke dubamin ya iya hae dafa indomie da, taliya kadan bamai yawa ba,Da miya nayi mana ina da komai na kayan cefane na saboda tunda na fara samun gumina na daina jiran ayi min komai,tsaye nake  a kaina kuma na tsaya akan ya'yana, ko yanzu din ma nace su kimtsa gobe sai makaranta fashin ya isa haka duk da sun koma karatun zango na farko akwai Laluran biyan kudin makaranta ga kuma abubuwa duk sun Chude ni dai na gama lissafina ko zan yini ina aikin sana'ata ne bazan gaji ba,Saboda ina so yarana su samu Ilimi bana fatan su rasa damar su kamar yadda na sara. Ina da Aiki da yawa na Hada Turaran wuta da Humra,sannan akwai masu Dilka wasu har kudin su sun turomin rashin natsuwa ne yasa ban ce musu komai ba sannan ga yan sarin Zobo da kunin Aya suna jirana,So nake sai hankula sun kwanta na Dawo da sana'ata kafin komai ya daidaita naga kuma inda Rayuwata zata kara Cillamu tunda sun bamu Notice nan da wasu kwanaki zamu tashi ashe da gaske zan tashi daga wannan Muhallin sai dai ba irin wanda na Kudiri niyya ba. Yaya Ishaq bai dawo ba sai washegari da Daddare muna zaune da yaran suna duba aikin da aka basu a makaranta,Ni kuma ina ta lissafin kudaden mutanen dake kaina acikin wani Littafi inda ban gane ba na Kira Amir ya dubamun suka shigo shi da Jamal,ya rakosa yaran suka mike suna Ihun ga Daada nima mikewa nayi ina musu maraba dukkansu nan falon suka yada Zango na shiga kitchen na kawo musu ruwa muka gaisa da Jamal shima na gaishesa ya amsa hankalinsa na wajen yaran. Jamal nayi ma mganar abinci yace sun ci abinci a gidan Mama sai dai ko In Yaya ishaq zai ci shi kuma sai yace sai dai zuwa anjuma, jamal bai Dade ba yayi mana sallama shi kuma ya nufi bangaransa yaran suka bisa yanzu har Ahmad ya Daina barci da wuri. Ni yaran suka bari da tattara musu littafan da suka watsar na kai musu Dakin su na adana musu nima na shige dakina, ina cigaba da lissafin abubuwa bani da wasu kayan Hadin sai na siyo sannan Kudina na Hannun Hafsah nake bama ajiya basa Hannuna. Ina so na kirata sai na Duburce na rasa ta inda zan latsa na nemo lambarta,Daman sun koyamin ba duka na iya komai a wayar ba,Sai na mike na leka shashen shi na gansu a falo suna da Budirin su na kira Amir sai dai ban ga baban nasu ba,Anum tace ya shiga wanka Amir na ba ma wayar shi ya nemo min Lambar Hafsah ya kiramin nayi mgana da ita tace min tunda na dawo gida gobe zata dawo nace yauwa gwara ta dawo din. Ina cikin Gyaran gado na Anum ta shigo da gudu tana fadin"Umma Daada yace ki hado masa Tea" Sai na amsa mata da Toh sai da na gama gyara gado sannan na fita na Dora ruwan zafi na saka mai citta da kanunfari,da Top tea suka Dahu tare na tace sannan na juye mai cikin karamin Fulas din da na siya,Tunda na siya sabbin kayan aikin Kitchen,su dai da suke nawa Tsoffin na Sadakar ne ammh na falo kam suna cikin wani Daki dake haraba kwashewa kawai nayi na sauya sabbi,nasan Halin sa tsab in yaji tijaransa zai ce ina kayansa Tunda shi ya saka komai na gidan kafin mu dawo. Da kaina na shiga na kai mai yaran dai ke ta duduma afalon shi bai fito ba na sauke mai saman Karamin Center table din dake falon na kalle su ina fadin"Dare yayi aje a kwanta gobe akwai makaranta" Anum sai ta dira baki tana fadin"Umma mu wajen Daada zamu kwana."sai na rike baki kafin nace"Da wajen Daadan kika saba kwana..?zaki wuce ko sai na mangareki" Nayi kamar zan kai mata Hannu sai ta goce ba zato kawai naji tace"To Umma Anty in tazo tana kwana anan ke ko baki taba kwana a dakin Daada ba.." Ta fada daidai Lokacin da ya fito daga cikin Daki yana sanye da jallabiya yaji kuma abunda tace ni ma mamakinta ya sandar dani na shiga tafa hannu Cikin mamaki ya kalleni nima na kallesa sai kawai na kauda kai na sukunci Ahmad da ya barci ina Fadin"Sai da safe..Amir riko Musty kuje ku kwanta" Daga haka na fice sum sum suka bi bayana Mazan na fara kula har suka kwanta sannan na dawo Daki mamakin Anum ya gama kamani na tashe ta tayi fitsari sannan ta koma ta kwanta araina nace yara ma kada a raina su,su na ankare da motsin kowa Allah mai iko har nayi barci da Tunanin Anum a raina. Haka muka cigaba da gungura rayuwar mu,Yaya Ishaq sai zaman gida ba inda yake zuwa sai ya bani tausayi magidanci ne fa da ya saba fita aiki da Zirga zirga yanzu ya Dawo sai dai ya kwanta in ya gaji ya zauna,Mutane na zuwa masa jaje cikin mutanen Mama,ko jamal yazo su wuni yana tayasa Hira,Hafsat ta dawo ita na Tura ta shiga kasuwa ta siyo min kayan da bani da shi na kunin Aya da zobo sai na Hada Turaruka ina da nayin Dilka na Halawa ne ta siyomin. Yaya Ishaq na da sati biyu da Dawowa na Fara sana'ata,yana shashensa bai fito ba sai dai komai ina yi masa,fita ko sai dai yaje gidan mama da daddare ya Dawo,tun Safe da na tashi ban koma ba ranar sau biyu nayi zobo Safe da Yammah Saboda yan sari ko da ya fito da yammah ya ganni ina ta Jera Robobin a katon Frezer na bai min mgana ba,nima ban yi masa ba yadai ce zai shiga gidan mama nace a dawo lafiya. Ina matukar Tausayamai Saboda akwai Tausayi ga wanda ya samu karayan arziki da kuma rasa aiki,Tunanin inda zamu koma nake yi, saboda ina lissafin saura Kwana goma Wa'adin da suka bamu ya cika yadda bai min mgana ba nima na zura masa ido ranar da yadawo yake fadamin abokan aikinsa daga Abuja zasu zo su yi mai Jaje akawai abincin da zan iya Dafa musu? nace muna da Cefane sai ya kalleni cikin mamaki kafin yace"Wa yayi muku cefanan..? Kai tsaye nace"ni mana" Cikin karin mamaki yace"ina kika samu kudi..? Ina Yar dariya nace"Baka ga ina sana'a ba ne..? Sai kuma yayi shuru bai kara mgana ba,washegari suka zo sun kai su goma Hafsah bata shiga makaranta ba ranar ita ta tayani muka yi musu abinci mai rai da lafiya na hada musu da Kunin Aya da zobo na da ke saidawa. Suka ci suna ta santi,Daganan gidan Mama ya kaisu sai dare ya Dawo,kwana uku tsakani yace min Mama ta kirasa kan mganar gida zai je yaji,da zai tafi na basa dubu daya nace yayi na adaidata sai yaki karba wai yana dashi ni nasan bashi da shi,bazai karba ba ne sai na kyalesa na cigaba da Harkan gabana. Daya dawo daddare karo na farko Tun aure na da shi ya taba zama ya yi shawara dani,sai ranar wai mama nata saida kayan gidanta na wuta da kayan katako tana so ta had'a kudin gida ne muma tace abunda zamu Dauka mu fara hade su waje daya Sauran sai a saida su. Ni ko sai naga kamar tsarin bai yi ba na kallesa nace"Ni ko da zaka bada shawaran da kudin da za'a siya gidan da zamu zauna me zai hana mu kama Haya na shekara daya..?kada ka manta akwai Hidima fa gata abinci gata yau da kullum ga na Makaranta da Dawaniyar yara ga Jamal yanzu yake aji Hudu Badariya wannan Shekaran zata gama ga Laluran Mama duka suna kanka ne shine naga sauran kudin in aka kama Haya sai a toshe wasu ramukan da su ko ya kagani..? Sai yayi shuru yana kallona kafin yace"Kuma fa Hakane Fa'iza ni sam ban yi wannan tunanin ba" Har acikin raina ni na fadi ra'ayina ne ban dauka zai ji mgana ba ta sai ga shi har su Maman da ya kawo mganar sai suka aminta,Mun fara shiryen shiryen tashi,na hada kayan da zamu Dauka wadanda kuma za'a saida aka fitar har da Tsoffin wad'anda na fitar duk aka saida su gabad'aya. kayan bangaransa yace a saida su duka,Katifa kadai yace za'a bar masa ta ishesa ni dai na ware gadona da na yara sai kujeruna sai kayan sana'ata da kayan amfanina na Kitchen, sauran kuma aka kira Dilallai suka yi musu kudi hakama gidan Mama kusan rabin kayan duk sai da su akayi abun akwai tausayi sosai Yan'uwa ma sun mana kokari Goggo ashe bata zauna ba ta saka ya'yanta suka hada kudi Dubu dari ta kawo tace a kara ita Hajiyar Dalan ma ba wanda ya kara jinta Ina gani Yaya Ishaq nata sunne kai kunya duk ta kamasa. Da kudin da Anty Binta ta hada da wanda mijinta ya taimaka harta Dangin mama suma sun taimaka aka Hada Miliyan Daya da rabi da su,aka samu gida acikin gari sai kuma Allah ya saukaka mana abun kusa da makarantan yara ne, ko ba abun hawa zasu taka da Kafarsu,Gida ne flat na daidai misali,Shashen Farko falo da Bedroom guda uku sai Kichen sannan kowani Daki akwai tiolet sai dayan Shashen Bedroom biyu da falo ba kitchen sai tsakar gida sai daga wajen Koridon kofar waje akwai wani Daki sai akace Jamal zai zauna anan. Tun kwana Biyu kafin Wa'adin ya cika kayan mu suka fara yin gaba mu zamu zauna a mai Dakuna uku, mama kuma da Badariya zasu zauna a dayan Shashen,Allah sarki Rayuwa Daman KANA NAKA ne shima Allah ya riga ya gamasa nasa,ranar da zamu tashi yara nata murna zamu tashi,har gwara Amir shi ya fi so wayau. Ni kaina sai da nayi hawaye inda ka saba da kewar yanayin rayuwa su Sa'adatu duk da su muka kwashe sauran kayana sannan nace don Allah ta gwada sana'ar zobo saboda mutanen dake barayin kada ciniki ya Gudu bayan na tashi,tace in sha Allahu zata jaraba. Su Mama su ma a ranar sukayi parking din komai,Goggo bata zo ba ammh Anty Nasara tazo ita da Yaya Asiya muna tare da su da Hafsat da makota na bangaran su mama kuma yan'uwanta da su Anty Binta. Yaya Ishaq da jamal su suka samo motocin da suka kwashe kayan suma sai da suka Chaji kudad'e masu yawa. *Janafty* *KNKB2003* *Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 05521790550,ban da tsarin kati wannan karon a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488* Kafin mu karisa chan gidan sai ga Matar Yaya isa tare da kanwarta,Yaya mariyasa nasan bazata zo ba.duk da ta bada uzurin bata jin dadin jikinta,ammh ni nasan dalilin ta. tare da su da makotana su Sa'adatu muka tare a daidaita zuwa anguwar Ajiwa,koda mukaje mun iske su Mama achan,Gidan mai kyau ne saboda sabon gida ne sannan wanda ya zauna agidan bai dade ba ya tashi. kuma basu lalata gidan ba,ammh dai yaya Ishaq ya sake fenti ya gyara bayika sannan an gyara glop din wuta in da suka samu matsala shi kan shi da'n wannan gyaran sai da ya ci kudad:e sosai. Mun iske su Anty Mahma har sun gyara barayin da mama zata zauna,bata dawo da wasu kaya ba Falon kujeru biyu aka saka sai cafet. sai Dakin Badariya katifa da Wardrope sai kayanta, Dakin mama ne aka jera mata gadonta da wadrope dinta,Da muka zo sai da muka shiga Shashen Mama muka ga waje muka saka albarka yara daman tuni Jamal ya taho da su nan muka iske su sun warware suna ta murna abun ka ga yaro Amir ne kadai muka zo tare da shi. Da taimakon Anty Mahma da su Yaya Asiya suka share bangaren da zan zauna suka gyaramin, sun maidamin kujeruna a falo da Cafet sai tibi. wanda naso a had'a a saida Yaya ishaq yace a barta tunda an saida na bangaransa,Duka kayan kitchen dina sun koma Saboda yana da girma har babban Freezerna,na kasuwanci ya samu waje da Buhu buhun robobina da sauran aya da ta ragemin sai Ganyen zobo da sauran kayan abincin da muka dawo da su, suka jeramin a Store din kitchen sannan suka gyara Dakin Yaya ishaq kusa da Dakin yaran ne da aka jerama gadajen su da wadrope din su,Shima katifa ce kadai sai akwatin kayansa sai Cafet karami na tsakar daki ni kuma suka maidamin gado na da sauran kayyakina kafin yammah waje ya fito ya yi kyau suka wanke tsakar gidan tas ya bushe gwanin ban sha'awa abun da yafi burgeni ta bangaran shashena akwai Daga gefe wani karamin Rumfa kamar na shan iska inda a raina nace zan rika hada hadar da sana'ata a wajen. Hafsatu ta yi abinci na saka aka dibar ma su mama,aka akai musu da shi,Saboda Dare dukkan nan suka kwana Anty Mahma ce ta koma gidanta har Anty Binta nan ta kwana Yaya ishaq kuma suka kwana Dakin korido shi da Jamal, sai da safe bayan an karya suka fara shirin tafiya. Yaya Asiya da Anty Nasara suna min fada da nasihan kan sai na ninka Hakura na wajen iya zama da mama, in a baya zama bai had'amu ba yanzu kuma ya had'amu sai na zama mai Taka tsantsan da kiyayewa. Ban ce musu komai ba. ammh ina ji a raina zan iya zama da mama a kowani Hali ai ni ba bakuwar cin mutumcinta ba ne  na riga na saba da Hallayarta na zauna da ita tsawon shekaru fin biyar naci wahalarta bayan kuma na auri Dan'ta ban tsira ba, to ban ga abunda zai bani tsoro akan hallayar Mama ba. Kafin azahar suka koma karofi narakasu har bangaran Mama suka mata sallama bamu fahimci yanayinta ba,sama sama ta amsa tare da yi musu godiya,sai da suka tafi naji wajen yayi min bambarakwai irin baka Saba ba Hafsah dai tana ta kara gyara dakunan,su Anum kuma suna ta Murna Musty har ce min yayi"Umma ina son sabon gidanmu' Nayi mai mirmishi kawai ban ce komai ba araina ina jinjina yarinta Amir ne kadai yasan halin da ake ciki Anum kuma uwar Shiriritace Dadi suke ji ganin har da Mama ta Dawo gidanmu da zama basu Dakinta basu Shashen da muke basu tsakar gida suna murna,Abu daya yasa gidan ya sakeni Burgeni akwai ruwa sosai domin akwai Famfo a tsakar gida, sannan suna da wuta kamar anguwan da muka taso,sai dai ita wannan anguwan tafi cika da mutane daidai misali ba kamar na masu  hali da dukiya ba. kwanan mu biyu a gidan sauran kud'aden da suka rage Hannun Yaya Ishaq ya yi mana siyayyan kayan abinci da su, da suka dawo siyo cefanen kayan abincin.Dakin Mama suka sauke komai ina cikin Dakin yaran ina gyara musu kayan da yake duk an hada kayan ne waje da'ya basu raba musu ba, ni kuma da na samu natsuwa sai na zauna ina ware ma kowa nashi ina saka musu a inda ya dace. Sai ga Anum tazo kirana in ji Daada na kalleta cikin mamaki sanin baya nan tun safe ya fita cikin yanayin mgana nace"Ina Daadan yake..? Kokarin hawa kan kayan da nake kan gyarawa tayi na hanata ina Hararanta sai ta juya tana Tura baki kafin tace"Yana Dakin Mama" Jin haka yasa na tsaida abun da nake yi na fita falo na Dauki Hijabina Hafsah na zaune a kasan cafet tana Duba Littafinta Amir na gefenta kamar yana gane me take rubutawa na Fice ina fadin"ina dakin Mama" Suka bini da toh da sallama na shiga,Na iske Mama zaune kan kujera jamal na gefenta yana danna waya Yaya Ishaq na nesa da ita ga kayan abincin nan a falon ta Badariya bata nan taje gidan Anty Binta da Safanan. Har kasa na duka na gaida Mama da gida ta amsa a Dake kafin ta kalleni tana fadin"Kayan abinci ne ya rikita da Sauran kudin da suka rage a hannunsa ya siyo.Shine yayi mganan za'a sauke a bangaran ki zaki rika Dafawa kina bamu nace ya kiraki gaki ga shi ga ni,ki fad'a da bakin ki in zaki iya dafa mana abinci kina bamu bana son abunda raina zai rika baci Daga baya" Kalamanta sai suka bani mamaki na Dago ina kallonta shima na juya muka Hada ido sai ya Dauke kansa nima sai na maida kaina kasa cikin Ladabi nace"Ai mama ko ba na auran Yaya Ishaq kina da hakkin da zan dafa abinci na baki indai muna zaune waje d'aya bakomai bazai gagara ba, da yardan Allah" Kai ta daga sama kafin ta karkace kai tace"Shikenan a kwasa a kai dakin ki" Har na mike zan fice tace"Sai a bi a hankali kin dai gani ba irin baya ba ne lokacin da akwai, yanzu babu. sai kiyaye da barna Ahto" Ban ce komai ba na fice a raina ina mamakin Mama yadda bata kaunar taga na zauna lafiya cikin Aminci sai ta Kirkire wata mgana da zata zama cin Fuska a gareni. Jamal ya shigo da kayan ina Dakina Hafsah ta leko tamin mgana nace ta gwadamai inda zai saka su,Ita ta nuna mai Store ya shiga ya jera komai ba wani abun sakawa a fridge sai kayan miya,sai kayan lambu da suka siyo ba su da yawa,Tun daga ranar ni nake abinci Safe da rana da yammah har Dakina nake  kai ma su Mama cikin wata Cooler mai girma yadda zai ishe su ita da jamal da Badariya,Ni kuma na ji da Yara sannan da Babansu kamar yadda wahalan komai nasa ya dawo wuyana yanzu tunda yana gida bai fara fita ko'ina neman aiki ba, kamar yadda yace zai fara fita ya gani ko za'a dace. Da kaina na shiga makotan mu gidajen da ke kusa damu muka gaisa na gabatar da kaina a matsayin makotan da muka dawo anguwan cikin Satin da ya gabata, na daina barin kaina Cikin Duhu tunda na san shiga mutane nada Dadi ban kara yarda na zauna agida ba. Duk kuma inda na shiga sai yi musu tallar ina Saida zobo da kunin aya, sannan ina hada Turarukan wuta na Daki da Humra da kwallacha sannan ina Dilkar Amare na gyaran jiki,Sai girke girken suna biki ko walima na kuma ce su min tallah wasu har suna tambayata ko akwai zobon nace ban fara ba tukunnah,sai mun natsa agidan, sannan sun tabbatar min da zasu siya Insha Allahu sai naji dadi kwarin gwiwa ya shigeni Duk daman masu sari ta wajena basu hakura ba sun ce duk inda nake zasu biyo ni su siya Saboda inganci zobo na da kunin Aya na. Su Anum sun koma makaranta ba nisa da safe ko Yaya ishaq ya rakasu su tsallaka titi ko Jamal,watarana har Amir ko Hafsah,Amir ne kadai ke gida shi da zai fara Junior section ga ba kudi ammh ina iya bakin kokarina ina so ya fara zuwa da wuri kafin wannan zangon karatu na farkon ya kare. Muna da Sati Biyu da dawowa Sabon Muhallin mu na cigaba da sana'ata Ranar tare da su Hafsah da Badariya suka taimakamin muka hada zobon da kunin Aya,ta waya na kira masu sara,bayan yayi sanyi chan da yammah suka zo suka Dauka Mama sau daya ta leko komai batace ba ta tabe baki ta koma ciki Sannu Sannu sai ga shi an fara ganeni ana zuwa Siya,ballatana anguwan akwai Dandali na matasa sosai tunda suka gane shikenan da yammah haka nake Ciniki sosai,Daga Mama har Uban gayyar basu taba ce min ba nima ban ce musu ba ina kokarin kiyaye abunda zai saka a tozartani. Jamal zai koma makaranta,ga kudin mota ga pocket money da kudin kayan abinci ga kudin makaranta Haka ma Badariya,Anty Binta tazo ranar sun dade a daki suna tattaunawa dukkansu sai dai har kwana Biyu ba wani mafita,Na lura shi kan shi Hankalinsa duk ya tashi a ranar suma su Anum aka basu takardan tunasarwan Biyan kudin makaranta Saboda damuwa abinci daren sa ma yadda na kai masa haka na koma na dauke sa bai ci ba,Da safe ma ruwan buni kadai ya sha ya fita ashe gidan Anty Binta yaje itama duk bata da wani kudi duk da su ta kwashe aka rufa asiri,Ammh tace ta ma mijinta mgana zai biya ma Badariya nata kudin makaranta sai dai a nemo na jamal ita zatayi kokarin nema mai na abinci kafin Lokacin tafiyarsa. Haka naji yana Mama bayani da Daddare da ya dawo ni kuma na shiga kai mata abinci.Mama tayi tagumi duk ta shiga damuwa kawayen nata da take takama da su,Duk sun janye daga gareta daman sai kana da shi ake yi da kai,Sannan itama babu jarin yin kasuwancin komai ya tsaya ita kanta duk ta rame ta Fige alamun ba natsuwa ba kwanciyar Hankali. Sai da yadawo bangarena na zubo mai abinci naga ya kasa ci yayi Tagumi sai naji ya bani Tausayi Namiji har namiji ammh lokaci kadan ya nemi ya susuce,batare da Tunanin komai ba ko shawara da wani ba,ina da kudi a banki na sun kai dubu dari da Hamsin daman shawaran Yaya Isa nabi da ya ce na tara wani abu ko Fili na siya kaddara ne saboda watarana,Washegari da Safe na bama Hafsah Atm dina zata tafi makaranta nace ta ciro kudin dake ciki Duka ita kanta tayi mamaki sai dai bata tanka ba. A hanyar dawowarta ta tsaya ta ciro kudin Dubu Dari da ashirin ta bani na adana su sai da Daddare da ya dawo Futu futu daman ya Dauki Takardunsa ya fita,Ko da ya dawo ya gaji salla ma acikin gida yayi ta ya kasa fita tun safe bai ci komai ba,Ruwan Citta da kunfari na Dafamai yasha cikinsa ya warware sannan ya Dora da abinci. Inda na fahimci damuwa ta masa yawa su Anum tana kiriniya bai bi ta kansu ba sai na saka Hafsah ta tarka su zuwa Dakin su nace su Dauko Littafan su,kafin su kwanta Sai da suka bar Falon sannan na shiga Daki na fito mai da kudin hannuna na basa da farko kin karb'a ya yi sai da nace ya karba sannan ya karba cikin mamaki yana fadin"Wannan kudin fa Fa'iza.? Ina zama nesa da shi nace"ka biya ma Jamal kudin makaranta shi da Yaran nan, zaman haka bazai yuyu ba tunda an fara sai a karisa" Sakin baki yayi yana kallona Lokaci daya yana kuma kallon kud'in bakinsa na rawa yace"Duka wannan kudin Fa'iza na waye..? Kai tsaye nace"Nawa ne dubu dari da ashirin ne Allah yasa zasu isa" Kai tsaye ya maidomin da kudin a gabana yana fadin"Bazan karb'a ba" Nima sai na turamai ina fadin"Kayi hakuri ka karba dukkanmu bamu da zabi ne" Sai yayi shuru ya kasa mgana,cikin wannan shurun ne wayarsa dake gefensa ta dau kara ina gani ya Duba yaja tsaki ya kashe haskenta ya mike daga zaune ya koma kan kujera yana fadin"Fa'iza duk ina kika samu  kudad'e haka? Cikin mamakin Tambayarsa nace"Ina sana'a ai ka sani" Yana kallona yace"wata sana'a kike yi haka da ta ke kawo miki kudad'e haka..? Ina yar dariya nace"Kunin Aya da zobon da kake sha kullum,to shine abunda nake saidawa" Ido ya zaro kamar bai sani ba ahalin nasan ya basar ne ban bari ya kara mgana ba,na tashi da kudin na karisa gabansa na sauke mai saman cinyarsa ina fadin"Don Allah ka karb'a" Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya Dauki kudin yana fadin"Zan karba ammh ba kyauta ba,bashi.In na samu aiki na warware zan biya ki kudin ki" Sai nace mai shikenan na amince nan ya zauna yana lissafin kudaden ya Dago yana cemin"Zai iya isa na biya ma su Anum kudin makaranta ammh Amir fa? Nazari nayi kafin nace'Shi ka kyalesa gaba sai a saka shi in an samu"sai ya jinjina kai yana fadin"Nagode Fa'iza" In yayi min godiya har mamakin sa nake yi tun ina mamaki har na daina adaran yaje ya fada'ma Mama kuma har aka bama jamal kudin ya koma makaranta ko mganar batamin ba nima don Allah nayi ban damu ba,daman  bana jiranta. Bansan cewa zaman Hafsah a gidan nan na damun Mama ba, sai da ta kirani a gaban Yaya Ishaq tace yanzu ba da ba ne nasan ba shi da shi ammh na kara kawo mai Dawainiya ina ganin suma suna fama da kansu,Ni dai har tagama mganar ta ban ce komai ba ina mamakin me zaman Hafsah ya tare ma Mama..?ban da abinci bata cin komai agidan nan,kudin mota da duka Dawainiyarta da Sana'ata nake yi mata Yaya ishaq ne ya tare mganar yasa Mama ta kyaleni sai abun ya dameni a cikin raina kamar Goggo ta sani tace Ko Hafsah zata nemi Dakin makaranta ne ta koma, ni ko naga ina garin kamar bai dace ba da ma ace bana nan ne,shine ammh Tunda ina nan ta zauna a wajena ai nima ina moranta ta bangaran sana'ata. Sai kuma korafi na biyu ne,mama ta fito da Tsirfan Masu zuwa a bani kunin Aya da zobo sun fara damunta ballatana da taga ina samun ciniki da yake akwai makarantar secondaryn Gwamnati ta mata dake kusa damu, tunda suka gane ni, shikenan arana sai na Dafa zobo fin sau biyu kunin Aya da yawa nake yi,Masu sari in basu zo da wuri ba sai dai su samu kad'an sai ta fara fadan ana damunta da Hayaniya sai na Fahimci bakincinta da na d'anta  take so na zauna ya kasheni ni ko nace araina, bazan miki Rashin kunya ba ammh kuma baki isa ki hanani sana'ata ba. Amir ne ke taimakamin tunda yana gida sai Hafsah in tana gida Badariya ma ba'a barta a baya ba, Kuma Maman tana sha kuma in tayi baki ina basu,ammh bata gani ba tamin mgana ban ce mata komai ba shima ta same shi ta mai mgana inaga shi ya kashe mgana bata kara tara ta da mganar ba. Ni dai na toshe kunnuwana na cigaba da sana'ata ganin wannan abun da tayi bai sa na dakata ba ko kuma shi Wanda take gani bai taka min Burki ba, sai ta fara fadin ina barinta da yunwa ina chan ina sana'ata sai rana ta take nake dafa abinci har da kwanciya ciwo sai da aka kai ta Chemist,ulcer ta kamata saboda zama da yunwa Anty Binta ta zo ta kirani dakin Mama ta na ta masifa Yaya Ishaq na jinta bai ce komai ba nima har ga Allah ban yi niyar mgana ba Saboda ni dai nasan ina dafa abinci akan Lokaci tunda na safe kafin tafiyar yara makaranta ne na rana kuma shi nake fara dorawa in na Dafa Zobon Farko na Dare kuma duk latti na bayan isha'i na gama abinci na kai mata ammh ban tsira ba. Sai da naji Anty Binta tace zan daina sana'ar da nake yi tunda Saboda ita zan kashe musu uwa da yunwa sai alokacin na dago na kalleta ban ji tsoro ba nace"Gaskiya Anty Binta ki yi hakuri ammh bazan daina sana'a ta ba.Domin banga ta inda hakan ya zama Takura ba" Sai ta saki baki tana kallona kafin ta kallesa tana fadin"Kana jinta dai ko..? Rashin kunya zata min a gabanka baka ce komai ba..? Sai ya muskuta kafin yace"Anty Binta mu bi komai a sannu in zaki ce mata ta gyara sai ki yi mata fada ammh babu Adalci mu hanata sana'arta" Mama na kwance ta daga kai tana fadin'"Ki yi shuru Binta ta siye shi da kud'i tunda yaga ta fara nuna tausayawa garesa shikenan bai iya tsawarta mata" Cikin mamaki ya kalli Mama kafin yace"Mama wannan wata irin mgana ce..? Mama ta zabura ta mike kamar daman chan lafiyarta kalau tana fadin"ai gaskiya na fad'a kada dai ta manta kafin tayi maka uban ka ya fara yi mata gata, sannan ya rufa mata asiri, kaima kazo ka rufa mata,ka zama gatan ta, in adalci kuma zatayi ai jarin  ba Ita ta ginama kanta ba kai ka gina ma ta shi" Da sauri yace"Aa wlh bani da hannun akan sana'arta ban san komai akai ba" Anty Binta ta koma ta zauna tana fadin"Shiyasa naso na dauke Mama ka hana ashe zaka bari matarka ta gana mata azaba ne ban sani ba..? Yaya Ishaq yace"Anty Binta ki bar wannan mganar matukar ina raye Hakkin kula da mama da su Jamal yana wuya na ne sai dai in ciwo ko mutuwa sun kwantar dani" Ina zaune ina jinsu so nayi na tashi na fita ammh kada suce na raina su,yasa na zauna kaina na kasa ina tsintar wasu mganganun su. Mama da ranta ya gama baci tayi Kyafci kafin tace"Ta gama da shi ne Binta shiyasa kiri kiri yaje ya Duba Zainab yaki zuwa itama ai tana da Hakki akansa wajen wata daya da rabi bai je ya ganta ba,wannan ai sai mahaifinta ya yi fushi da shi Tsakani ga Allah wannan bawan Allah babu abunda bai yi mana ba ammh nasara uban me ishaq ke yi acikin gidan nan da bai tafi ba" Mamaki ya kasheni wato Zainab ce matar so ni sanda yake tafiya sai yaga Dama yazo ai bata taba cewa ina da Hakki akansa ba takaici yasa nayi mirmishi mganar ma ta gundureni sai ya kashe zaman nawa da cewa"Je ki abun ki Fa'iza" Mikewa nayi na fice a raina ina fadin daman ya koma chan wajen zainab din domin da zamansa da akasinsa duk daya ne a wajen fa'iza ba abunda suke Tunani ba ne. Bansan ya suka kare ba ammh sun kai ruwa rana domin ina jin tashin muryoyin su shi da Anty Binta ina Dakina bansan tafiyar ta ba,mama bata so ta gansa yana zaune agida gani take yi kamar wani abu yake min ko zamansa wani Dadi yake yi min,Abunda bata sani ba ni mantawa nake yi ma yana gidan tun safe in yara suka tafi makaranta zan kama sana'ata Amir na tayani in Hafsah bata gidan ita a tunaninta na tsare shi a Dakina ne yana bani wani abu tunda ta Furtamin da na shiga gaisheta washegari ta kalleni sama da kasa kafin tace"Ki sakar min d'a Fa"iza na rasa me kike son ya baki bayan wanda ya baki a baya ke ko gajiya da nanikan namiji bakya yi ciki ko goyo ne baki gaji da yin sa ba ko me..? Mganarta sai ta bani Dariya sai da na Murmusa kai tsaye nace mata"Ko d'aya Mama haihuwa ai Fa'iza ta gama shi in dai a nan gidan ne na bar ma Zainab ita ya dace ta cigaba da tara miki Jokoki" Tasan mgana na gayamata ammh sai bata kara mgana ba,ai kunyan marasa kunya a sara sannan tsohon da bai ji kunyar hawa jaki ba shima jakin bazai nauyin yarfa sa da kasa ba. Hajiyar su Raliya bata san mun sauya gida ba,taje camoron kanwarta zata aurar da Diya su Raliya kuma sun je lagos hutu gidan Yayan mahaifin su,suna dawowa suka hadu a makaranta Badariya ta fadamata ranar tare suka suka zo,a shashena suka zauna tare da Hafsah,suka ci abinci suna Hira Raliya tace Hajiya bata sani ba ammh zata dawo kwanan nan zata gayamata. Mama taji Haushin shigar su Dakina da Raliya ta shiga mata sallama har da ni sai harara ta takeyi har tana fadin''Haka ake yi sai ki shigar da yarinyar daki ai ba wajen ki tazo ba sai ki bar ta da Badariya kawar tata" Daganan na Fahimci Kishi Tsagwararon shu Mama ke yi da ni a baya don bamu zauna waje d'aya ba ne yanzu kuma Abun nata na fitowa ,Cigaba na ne bata so tafi kaunar ganin na wulakanta ko na Tozarta to ai ba ita ke da Rayuwata ba,in ita tana nata ne shi Allah kankat ne ya riga ya gama nasa tsarin mutum bai isa ya hana faruwar kaddara da ya Riga ya zana ba. Ba'a rufe sati ba sai ga Hajiya Tazo Raliya ta rakota tayi ta min fadan meyasan ban kirata ba ni dai hakuri na bata,Tana ta kallon gidan cikin wani yanayi,da zata tafi ta bani Dubu Hamsi sannan taji dadin yadda sana'ata bai tsaya ba tace na cigaba da yi in sha Allahu watarana sai na bama kaina mamaki sai da zata tafi ta shiga Dakin Mama suka gaisa,Ta bata dubu goma mama nata godiya. Har waje na rakata tace min Direba zai kawo min sako ba yawa,Sannan tace akwai Bikin diyar kawarta da zasu yi a kaduna tana tunanin kwangilan Hada turaruka ni zatace a bamawa sannan tana tunanin Amaryan zata zo gidan sai nayi mata gyaran jiki ina ta Murna daman ta wannan bangaran ita kan kawo min Costumer,sau daya na hada Turaren Rushi da na Humra da muka dawo gidan nan shima na riga na karbi kudin aikin su ne tuni yana hannuna. Da Daddare naje kai ma Mama abinci sai da tambayeni a wulakance wai a ina nasan Hajiyar Raliya..? Kai tsaye nace mata"Su ne shugabannin kungiyar da suka bamu tallafi bayan sun koya mana sana'o'in hannu domin Dogara da kanmu" Sai ta tabe baki kafin tace"Ina ce sanadin Badariya kika santa? Sai na daga mata kai sai kawai tayi tsaki kafin tace"Aikin mur in ji tusa." Ban tanka ta na fice washegari sai ga Direba da kayan abinci shake da Mota Ishaq na gida Lokacin nayi mai bayani sai kawai ya kalleni yana fadin"ina fatan ba rokon ta kika yi ba ko..? Sai abun ya bani haushi na wuce sa na shige daki ina fadin"To ba dole fa a fada masa ya juya da kayan kawai" Daganan ko kara bi ta kansu ban yi ba, sai naga ana shigowa da kayan a raina nace abun ma iskanci ne sai da na natsa na kirata nayi mata godiya tace bakomai indai ina bukatar wani abu na kirata kamar uwa take gareni nace mata in sha Allahu. Muna da wattani biyu da kwanaki a sabon gidan da muke ciki,Yaya Ishaq ya tafi Abuja ranar wata asabar shima din Mahaifin zainab ya kira sa akan yazo yana nemansa ba shi ko da kudin Mota Mama ta kira Anty Binta ta bashi ya kama hanya sai da ya bar gidan nan Hankalin Mama ya kwanta. Kamar yau ya tafi washegari Goggo tazo ganin wajen da muka koma Yaya Isa ya kawota,shima Hafsah ya kira tayi mai kwatance Dakin Mama ta fara shiga suka gaisa anan Mama wai ke Tambayan Goggo ina Hajiyar Dala..? Goggo tace"Baki sani ba ta tafi raka mijinta kasar awaje a duba lafiyrsa" Sai Mama ta kasa mgana tunda da Yaya ishaq ya fito daga hannun jam'an tsaro Mama bata kara jinta ba tun tana kiranta ta na bata uzuri har dai ta daina samunta goggo mamaki ya cika ta  daman ana jin kan Saudatu da Fatima ne..? Da mamakin ta baro dakinta zuwa shashena ta iskemu muna ta Dura zobo a gorina,Goggo na zolayata fad'i take yi"A'a kaga Hajiya fa'i mai zobo da kunin Aya" Amir da Hafsah suka kwashe da Dariya Yaya isa na gefe yana taya su, shi sauran na jiya da yammah mai sanyi nace Hafsat ta kawo masa yana sha yana fadin"Goggo gaskiya Fa'iza ta iya hada zobo sosai yake da dad'i" Goggo ta kalleni kafin tace"Ke fa'i taso ki saka ma yayan ki waigi ya fara santi" Gabadayanmu muka fashe da Dariyan mganarta, shima Dariyan yake yi yana gyad'a kai kamar wani kadangare. *INGANTACCEN ZANCE*. *Akwai da INGANTATUN SAIWOWI na gyaran mejego ko amare*. *Haka uwargida ma ba'a barta a baya ba da irin nata tagomashin* *Kaya ne masu kyua ba garabiti ba, takanas ake kawo su daga chadi.* *Idan kina da kannen da za'a aurar, ki zo ki yi musu tanadi na mussaman*. *SAIWOWIN itatuwane da basu da illah* *Da sau'ki zaki same su, amma aikinsu yawa ne dasu.* *Kawai ki tuntu'bi Surayya HALIN YAU a wannan lambar dan samun gamshasshen bayani* *08032773332.* ✍️. *Janafty* *KNKB2004* *Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 05521790550,ban da tsarin kati wannan karon a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488* Itama cire hijabi tayi ta shige cikin mu. tana tayamu zuba zobon a sabbin Gorunan da na siya,muna yi muna hira cikin Annushuwa lokaci d'aya muna darawa in abun dariyan yazo,Yaya Ishaq ne bayan ya gama shan na shi zobon zai shiga cikin gari ya mike yana fadin"Fa'iza zan dawo daukan Goggo dole na tafin ma da Madam zobon nan domin itama tana min labarin sa" Hafsah na gefe tace"Yaya isa har da kunin Aya.." Da sauri yace"Eh har da kunin Aya a had'amin dashi" Gabad'ayanmu muka kara kwashewa da Dariya yana sosa kunnensa da key din motar dake hannunsa yace"Goggo kin jamin yara na min dariya ko.? Goggo tace"Kayi abun dariyan ne.Ke Hafsah bisa ya kwaso min tsaraban Fa'iza kafin ya tafi" Har zai fice daidai lokacin yaji Goggo na tambaya ta Yaya Ishaq sai nace mata ya tafi Abuja sai ya koma ya zauna cikin mamaki yana fadin"Daman bai daina zuwan Abujan nan ba..? Goggo tace"Kaji wata mgana shi da yake da mata da ya'ya kake fadin bai daina zuwa ba" Yaya isa yace"Haba Goggo.In a baya ya je yana aiki ne yanzu kuwa ba ya aiki ga wahalan rayuwa in a baya yana da motar kansa, yanzu ko babu ko na motar da zai rika zirga zirga ai wani abu ne mai zaman kansa shima ya kamata ya zauna yayi ma kansa Tunani haba.." Ni da goggo kamar had'in baki ba wacce ta tankansa ya cigaba da fadin"In har tana son shi ta baro chan ta dawo nan, ai gidan nan shima ban ga laifinsa ba inda rayuwa ta juya dakai sai ka juya kai ma ka fuskanceta" Goggo tace"Ya za'ayi ta dawo bayan achan take aikinta a kace" Yaya isa yayi tsaki yana fadin"Mganar banza ne Goggo in dai tana son shi kuma ya isa da ita duk inda yake zata bisa.ammh gaskiya wannan tsarin bai yi ba, duk wanda yaji haka sai ya raina ma wayaun Ishaq. baisan zama ba aikin yi ba ne, yana ganin kamar abun wasa ne sai rayuwa ta fara kwallo da shi zai Fahimci Shayi ruwa ne" Dariya ta kusa subucemin da mganarsa ta karshe ya mike yana fadin"Ita Fa'izan ba mutum ba ce, ba ga ta nan ta biyo sa inda yake a kuma yadda yake ta zauna da shi ba, sai ita yar gwal wahala ce bata ishesa ba Allah ya ba da sa'a" Daga haka ya mike bayan yace Hafsah tazo ta shigo da kayan ni kuma sai nace Amir ya bita ya tayata bayan fitan su ni da Goggo bamu tada zencen ba sai muka shiga wata Hiran na Dabam Goggo ta kalli falon ta kara kallo kafin tace"Nan din ma ba laifi sai ku lallaba kafin muga Abunda zai yi" Na gyad'a ma Goggo kai ina fadin"Ai anguwan nan tayi Goggo sosai nake samun Ciniki" Goggo na dariya tace"Dakyau Allah yasa albarka Allah ya tunkud'o ciniki Fa'i ta biyamin hajji da kudin zobo da kunin Aya" Ina dariya na rika fadin Ameen Ameen Goggo har da Umra ma goggo na Dariyan jin dadi tace'"Allah ya ida nufi Fa'iza" Hafsah ne suka dawo da kaya Nasan Goggo da Dawainiya bata zuwa Hannu Rabbana tace su garin kuni ne mu lallaba ina ta godiya har da Taliyar yar muji garin Danwake garin Tuwo da tsakin masara kubewa danya,kuka daaddawa,da bushashiyar Zogala da rama sai gyada mai bawo da Mai gishiri da ta kawo ma yara Tsaraba Dadi ya cikani sai cewa nake yi"Allah ya saka da alheri Goggo na zama yar gatan ki" Goggo tace"Daman ke yar gata na ne tuni zaman ki ne kawai bai yuyu a Hannuna ba" Nasan haka domin duk wata kauna Goggo ta nuna mana barin ma ni,Su Hafsah tuni sun ja gyad'a gefe suna ci ita da Amir na balla musu Harara ina warce ledan Lokaci d'aya ina fadin"Wannan na sauran yara na ne yan makaranta" Amir yace"Umma wannan yayi musu yawa fa..? Na bude ledan ina gani sai naga da yawa sai na debo a hannu na zube a gabansu na boye sauran ina fadin"yara kun ci rabon ku" Goggo na mana Dariya naji Dadin wannan zuwan na goggo muka yini muna Hira,Hafsah tayi abincin rana bayan ta gama nace ta dibar mama da Badariya da taje kai mata sai tace sai yanzu aka ga daman bata abincin..? Ita dai Hafsah bata tanka ta ba sai da ta Dawo daki take gayamin Ban ce komai ba Goggo tace"Sai kin kara Hakuri daman fa'iza yanzu Saudatu zatayi ta tsiro da abubuwa saboda ta kuntata miki, to kada ki biye mata Har a gobe uwa take gareki" Kai na jinjina ina fadin"Goggo ni ban da Lokacin wannan kina ganin bama zaune nake ba" Goggo tace"Ba shakka Sana'a ai mganin Damuwa ne da sha'anin Duniya," Sai da muka yi sallar la'asar sannan Goggo ta yi shirin tafiya daman da La'asar Ya Isa yace zai dawo shima daga ma'aikatar su ta nepa dake Dutsemah ne aka turo su meeting babban Headquater su na katsina da ya gayama Goggo tace zata Biyosa. Aiko sai ga shi hudu da wani abu sai faman hon yake yi ma Goggo tunda yaki shigowa na zuba ma Goggo kunin Aya da zobo mai yawa shima Yaya isa na bashi na shi Goggo sai fada take yi tana fadin"bai yi yawa ba Fa'iza? kada mu karya fa jarin" Ina Dariya nace"Cikin Riba ne fa Goggo" Sai ta karba tana fadin"To Allah ya yi albarka Allah ya sanya miki nasibi da karama acikin Kasuwancin ki da sana'arki" Na dinga amsa mata da Ameen na rakata Dakin Mama tayi mata sallama ni da Hafsah da Amir har kofar gida muka rakasu Yaya isa ya zaro dubu biyu ya bani naki karba sai ya harareni yana fadin"Kyauta na baki ni ba kudin zobo ba ne" Jin haka yasa nayi dariya na karb'a ina masa Godiya Hafsah na ganin haka tace"Yaya isa kada ka manta yar makaranta marainiyar Allah" Dagowa yayi yana fadin"Data zaki saka ko..? Da Sauri tace"Eh Yaya ai muna Browsing sosai" Sai ya yi dariya ya zaro dubu ya bata yace a saka data ayi ta browsing ta karba tana godiya sai kuma ya bama Amir dari biyar yana fadin"Kai baka fara zuwa makarantar ba ne..? Da Sauri nace"Bai fara ba sai zangon karatu na biyu Yaya isa" Sai ya jinjina kai har Goggo ta shiga mota sai ta leko ta window tana fadin"Kinga na manta Maman isuhu tazo da kanta ta kawo min goro da mintin biki Isuhunta zai yi aure tace kada a yada zumunci don Allah" Fatan alheri nayi kafin nace"Da wahala zuwa na Goggo kinga ga Mama ina fita sai kiji ance ban kyauta ba" Goggo tace"Hakane ki yi zaman ki ni da mariya sai mu leka" Da haka muka yi sallama suka tafi muna Daga musu hannu sannan muka koma cikin gida,Danwake nayi mana da Daddare Hafsah kuma sai ta hada kunin Aya zobo ma bamu yi na yammah ba nagaji nace ta bari da Safe yan sari ma basu samu ba duk a gida ya kare. Aiko Mama tayi ta fad'a wai danwake ne abinci da daddare kamar a gidan yari..?yarda aka kai mata haka Hafsah ta Dauko kulan da safe da zatayi wanke wanke, Badariya bata dawo ba kila gidan Anty Binta ta kwana,haka na cigaba da Hakuri da Mama ammh Allah ke da kullum da Sabon korafin da take tashi da shi sai dai bana biye mata,Yaya Ishaq tunda ya tafi bai kirani ba nima ban damu ba sai dai nasan suna waya da Mama. Sana'ata na maida hankali bani da wani Hutu sai dare ya tsala wani Lokacin Saboda kada ayyuka su Chudemin karfe uku na Dare nake tashi na Dafa Zobo a tsakar gida tunda na koma amfani da gas na kasa 4kg,Sai na siya babban murhun gawayi ina amfani da shi wajen Dafa zobo,har girki ina yi akai saboda gas din ya rika yi mana auki sosai. In na tashi ukun nan kafin asuba na Dafa zobon,sai naji da saka ruwan wanka. wani Lokacin Hafsah ke abun karin Safe in zata fita da wuri in kuma tana gida sai nayi in ta tashi sai ta Hada zobon ta kuma share gidan da Dakunan in kuma bata gidan duk ni nake had'awa nayi kunin Aya saboda yana Saurin Lalacewa nafi hadasa da yammah saboda an fi samun Wutar Dare kafin safe yayi sanyi. Hakan ma bai burge Mama ba, duk yadda nake taka tsantsan sai da ta fito tace min wai warin ganyen zobo na tayar mata da zuciya ni ko sai nace sai dai ko ki yi ta sheka amai bazan daina wannan sana'ar ba,kuma duk kushen mai kushe da Hassada ta Allah ba tashi ba. Duk yadda nayi sai tace kaza kaza ita dai kada ta ganni cikin ni'imar Allah sai dai na zauna ta rika tusamin Haushi da tozarcinta nan kuwa bata isa ba,yanzu ba irin da ba ne an samu Sauye sauye da dama. daman haka Rayuwa ta gada Kifi na ruwan sanyi sai ya iya juyawa ya gansa ana zafi kamar yadda ya faru da ita. Na toshe jina da ganina na cigaba da sana'ata ina rufa ma kaina da ya'yana asiri,har da ita kanta Mama muna da kayan abinci ammh bamu da Cefane da Riban sana'ata nake mana komai Dawainiyar yara na makaranta na yau da kullum Badariya ma ina bata na mota har da wata matsalan in ta taso in dai tamin mgana ina da shi zan Dauka na bata. In da na biye mata na koma na zauna yadda ta matsa Yaya Ishaq ya tafi Abuja da ta gane bata da wayau.Anty Binta take takama da ita itama bata da komai yanzu sai karya da Girman kai da tijara fal cikinta domin ban ga abun arzikin da take kawoma Maman ba,Da farko da Mama tace Ucler ya kamata kayan Tea ta siyan mata da suka kare bata kara siyan ba na Tabbata bayan Yaya ishaq ba mai iyawa da Dawainiyar Mama. Sai da ya shafe fin sati biyu a cikin na uku ya dawo na zata zan gansa da abun arziki ne niki niki yadda Mama ke fadin sun musu komai babu abunda yazo da shi daga shi sai kayansa kamar ma a kidime yake ba wani kwanciyar hankali sai ramar da ya karayi, ashe wai takardunsa yasa yaje mai da shi ko za'a dace yasaka shi yayi zama ba wani labari mai Dadi gajiya yayi da zaman ya dawo ina Tsakar gida ina shara naji Mama nata mai fad'an meyasa bai jira ba ya Dawo dayake Mama ta iya mgana a sama sama. Yayi mgana sai dai nashi ne yayi kasa ban ji abunda yace ba, ni dai ba gulma ba na cigaba da aikina,Yadda bai ce min kanzil ba nima ban ce mai ba sai na tambayesa ya ya baro su Farhan..? Sai yace min Farhan ya fara zuwa makaranta Fadil kuma gidan su zainab ke kaisa in zata fita aiki Daganan bai kara mgana ba, nima na kama bakina fadan da ba ruwan ka ai Dadin kallo ne da shi. Sai ranar da yayi kwana Biyu da Dawowa yana zaune afalo ni kuma ina safa da marwa aiki ya had'e min Hafsah da wuri ta shiga makaranta ga aikin zobo ga girki,Amir ne ya taimaka yayi min sharan Dakuna da Tsakar gida,gajiya yayi da ina wucesa ko barayinsa bana kallah yasa ya kirani nazo gefensa na tsaya yana kwance ne ya mike yana fadin"Nagode bisa Dawainiyar da kika yi da yara da su Mama bayan ba na nan" Sai kawai na wuce ina fadin"Ba damuwa daman kasan kula da yara aikina ne Mama kuma itama kamar uwa take gareni, kada ka godemin domin na yi mata Hidima" Daga haka na wuce kitchen na Dauki Abunda zandauka nayi waje achan nake girki gas ya kare Hafsah nace taje ayi Refiling bata samu zama ba ne. Har na fice yana bina da kallo nasan a ransa yana mamakin yadda na sauya ne bakina ya bude fiye da yadda yayi tsammani,Haka muka cigaba da Rayuuwa yau dadi gobe Tsumma,ahakan ma ni nake tallafe da kananun Lalurorin gidan nan ammh Mama bata gani take yi komai nake yi alfarman da suka yi min ne nake rama musu. Ni ko Don Allah nayi abunda take yi bai Taba Damunaa ba,Ba inda Yaya Ishaq yake zuwa yana gida sai dai in masallaci in ya gaji da barci ya fito falo ya kunna kallo in yagaji ya kwanta,ko ya shiga Shashen Mama,duk yadda baya so damuwa ta samu zama a jikinsa sai da ta samu duk yayi baki ya rame hatta na katin waya gagaransa yake yi,kuma yana da girman kai da Fafa bazai yi tambayata ba ni ko bani da masaniya kananun matsalolin da na gani ne nake mgancen su. Ana cikin Haka jamal ya yo masa waya Kudin hannunsa ya kare sannan kayan abincin sa ma sun kare Bai fadamin ba sai ya shiga bangaran Mama ya fadamata kai tsaye mama tace"Sai kayi ma matarka mgana nasan bazata rasa ba,gidan nan yini ake shiga da fita saboda sana'arta" Kai tsaye yace"Mama ni bazan iya taba tambaya Fa'iza kud'i ba" Mama tayi karamin Tsaki kafin tace"Kiramin ita ni zan gayamata" Amir ya kwalama ya kira da ya shigo sai yace ya kirani ni kuma ina Falo na Dukufa da littafin, ina ta lissafin kudi so nake wannan karon daga rabin Solon Ganyen zobo na siya Solon buhun ina tattara Riban hannuna sannan Aya ma tiya goma nake so na siya,da yawa da Dabino na ijiye kwakwa kuma tana lalacewa kadan zan siya sanda Amir yazo ya kirani shine a raina so nake nayi kokarin na biyasa masa kudin makaranta ya fara zuwa zamansa ya fara Damuna,so nake na fara ji da Hidimarsa kafin su kuma a fara mganar na su Anum Ijiye komai nayi na saka Hijabi na tafi Dakin Mama da na shiga a kasa na duka ina gaisheta da lafiya ta amsa kafin ta daga murya tana fadin"Jamal ne yayo waya bai da kudi a hannunsa nasan kina da kudi ki bada ko dubu ashirin ne sai a sakamai ya lallaba" Sai mamakin Mama ya kamani kamar ita ta tarfamin jarin cikin sanyina nace"Sai dai Dubu goma baza'a samu ashirin ba" Mama ta saki baki kafin tace"Wlh karya kike yi ba za dai ki bada ba ne, meye amfanin samun naki in dai bazaki taimaki mijinki naki ba" Ina jinta ban yi mgana ba shi ya katse mganar da cewa na tashi na tafi haka na koma Dakina ina jinjina karfin Halin mama shikenan lissafina ya Sauya daman yan riban da su nake Hidiman yau da kullun kudi fa ana zaran su basa zama,Sai na cire dubu goma na ware kayan da nace zan siyo na ijiye bazai samu ba saboda kudin sun yi gibi,ko da ya dawo dakin bai tada mganar ba sai ni da kaina na dauko kudin na basa ya karba Jikinsa a sanyaye lokaci daya yana fadin"Ki rika Rubutawa Fa'iza zan biya ki kudin ki da zarar na samu aiki in sha Allahu" Ko kulasa ban yi ba sai dai na dago na kallesa kamar bazan yi mgana ba sai kuma nace"Kai dai baka na lissafe da abunda ka karba ba?ai shikenan." Daganan sai bai kara mgana ba ya saka takalmi ya fita yaje ya tura ma Jamal kudin,ya dawo Yaya Ishaq na bani mamaki ko irin ya dan fita waje ya zauna bai iya ba yana gida koda yaushe dole damuwa tayi masa yawa,kamar zan yi masa mgana sai wata zuciya ta kwabeni na kama kaina. Zainab na kiransa ko da yaushe ni ban san Halin da suke ciki ba sai wataranar asabar da Safe na shiga kai masa abun karyawansa naji yana waya ya daga murya sai fada yake yi Cikin kaukkausan murya yake fadin"Zeey na fada miki bazai yuyu nazo abuja na tare ba,bani da aikin yi ba wajen zuwa ke ba zaman gida ba ki fice tun safe ki barni da mai aiki, Fadil ma ki bar mun shi ya Debemin kewa gida kike tafiya da shi gwara na Dawo gida na zauna nan din ma ina da uwa da wata matar da kuma yara" Ni dai daga haka na sauke abun hannuna na fice yayi nisa a mganarsa bai ma san na shigo ba. Da na fita acikin raina sai abun ya fadomin sai naga Zainab na da gaskiya abunda ya zabar mata tun farko ne meyasa yanzu zai sauya..?ai yasan da akwai rashi da samu akwai rayuwa akwai mutuwa kuma ya zabi hakan duk wanda ya siyi rariya yasan zata zubda ruwa yadda ba wanda ya sani cikin mganar nima nayi kamar ban ji komai ba, na cigaba da Sabgan gabana. Ina ta buga bugan  yadda zan had'a kudin makarantar Amir saboda su Anum sun kusa hutu sannan ga kudin makarantar Tahfez din su yanzu sun ciresa a kudun makaranta Daban za'a biya hakuri na bada wanchan Team din ba'a biya ba yanzu kuma baamai karban uzurin mu,Shiyasa nake aiki ba rana ba Dare rana na Dafa zobo sai Uku,saboda zafi da nake tunkara da Wahala yasa kaina ya fara ciwo da ganin Jiri ina jin haka nasan jinina ne ta haye sama bana samun Hutu ga amfani da Hutu nasan in ya kwantar dani abubuwa ba zasu tsaya sai naje kemist aka auna ni aka ga jinina ya Hau sai aka bani mganguna,Dalilin haka yasa kwana Biyu nayi baya da Wutar Sai dai Hafsah ta Dafamin kafin tatafi makaranta sai ta barmun na hada,kunin Aya bai da matsala da kaina nake yin ta tadawo da wuri sai ta sake Dafa na yammah ni kadai araina ina fadama kaina Fa'iza bi sannu Sannu zafin nema baya kawo samu. Allah maji rokon bayinsa domin ban daina rokon mafita daga garesa ba,kawai sai ga kiran Hajiya tana fadamin bikin da ta fadamin na kaduna saura sati biyu,In na samu Lokaci nazo gida na sameta ina jin haka ko ban yi wasa ba,Allah yasa Ranar Hafsah na gida sai na bar mata komai Yaya Ishaq na dakin Mama da na shiga ciki na shiga na gayamai zan fita Hajiyar su Raliya ta kirani kan wani aikin Turaren wuta bai ce komai ba yace a dawo lafiya Mama kuwa sai da ta tofa kallona tayi tana fadin"Da zaki kwashi kafafu ki fita abinci wa kika bari ya dafa ya bamu..? Kai tsaye nace"Hafsah zata dafa ai ba jimawa zan yi ba zan dawo" Baki ta tabe kafin tace"Wanki na ya taru wannan satin naga baki zo kin kwashe kin wanke ba ko kin gaji ne..? Yadda tayi mganar kamar wata baiwar ta ko yar aikinta Tunda muka Dawo gidan nan ni nake kwashe kayan Mama in sun yi Datti na wanke mata.   kuma na zauna na goge mata,ba kayan Mama ba Har na Yaya Ishaq ni nake wanke masa wani lokacin saboda bai saba ba,Sai dai in aiki yayi min yawa sai nace yakai wanki da guga zan ba da kudin. wannan satin da ban ji dadi ba ne ko na yaran Hafsah ta rage musu nasu ammh ji yadda take min mgana kamar tana biyana. Kaina na kasa nace"Banjin dadi ne wannan satin ban yi wanki ba, ammh za'a wanke in sha Allahu" Yaya Ishaq mamaki ya kamasa cikin mamakin yace"Mama bata jin dadi yanzu ko Badar baza ki saka ta wanke miki kayan ki ba..?baki ga ayyuka sun mata yawa ba ne..? Sai Mama ta fara bala'i tana fadim"Kaga Badar din ne a gidan..?da makaranta zataji ko da aikin gida ba zaune take ballatana kace" Kai tsaye yace"Ai ba kullum ake makaranta ba Mama ita Hafsah ai karatun take yi kuma bai hanata ta taya yayarta aiki ba." Mama ta cika tayi fam ta faara fadin"Na lura ai yanzu yarinyar nan tafini Daraja a idon ka saboda tana Dauke maka wasu laluron,har Abada bazan so Dangin jaraba da cin Amana ba'" Naga cin mutumci zai yi yawa sai na tashi na fice sai yi take yi ban bi ta kanta ba, na dauki pos dina da na siya da kudi aciki nayi tafiya ta, adaidaita na hau har anguwan su Hajiya kusa da jami'ar alkalam. Nasameta a gida da tana shirin fita ne ma sai gani,sai ta fasa bayan mun gaisa tamin bayanin komai zan had'a Turaren rushi da na Humra sai kwallacha sai zan yi ma Amaryan gyaran jiki,duka zasu bani dubu dari biyu,Naji kudi sai na rude cikin Firgici nace"Hajiya duka nawa..? Hajiya na dariya tace"Eh kudin aikin ki da ladan ki ba' Sai na hau mata Godiya sai ta bata rai tana fadin bata so na koma na zauna araina ina Hamdala,Nan take ta bani dubu dari a hannuna sauran tace zata Turamin ta banki ta karishe da fadin"Sati mai shiga amaryan zata zo nan zaki zo ki yi mata ko sai dai ta biyo ki gida..? Cikin Ladabina nace"Hajiya sai dai gida kinga ga yara sannan ga Mama bazai yuyu na rika Dadewa a waje ba" Hajiya tace"Eh hakane shiyasa da suka yi mganar girki nace su dauki wata kawai zuwan ki kaduna da wahala" Na jinjina mata kai sai tace ba Damuwa fita zatayi duk abunda ake ciki sai mun yi waya,tare muka fita da ita bayan ta bani kyautar atamfa da Mayafi,sai turare da lotion mai kyau,tare muka taho Direban ta ya Daukoni sai da suka saukeni a gida sannan ya wuce da ita in da zataje. Bakina kamar gonar auduga haka na shiga gidan cikin murna naja Hafsah Daki na zayyana mata komai na nuna mata kudin cikin Farinciki tace"yaya Fa'iza Hajiya tana da kirki tana son ki da arziki" Ina jinjina kudin hannuna nace"Bari Hafsatu Allah dai ya biya ta kawai" Aranar bamu je kasuwa ba sai washegari mukaje da Hafsah ta tayani na sissiyo abunda zan bukata ina Dawowa na Dukufa na fara aikin Hada Turaruka,araina ina jin duka matsalolina zan kauda su in na samu wannan riban aikin,Aikin zobo sai ya koma sau daya a rana kunin Aya ma sai da yammah Lokaci na bada kacokan kan hada Turarukan nan ban rufe kwana hudu ba, na gama su duka,Kwallachan ne ma ta bani wahala ita sai da nayi kwanaki ban gama ba,inagamawa na kira Hajiya sai tace na ijiye komai a Hannuna in su Laila sun gama gyaran jiki in zasu tafi sai su tafi dashi. Haka ko akayi satin bikin Amaryan Laila mai kyau da ita yar gayu ga ilimi ga nasaba ga kudi,ma'aikaciyar banki ne a kaduna suke Raliya ta dinga rakota kullumn da yammah muke farawa sai shida,A tsakar gida nake bazamana Tabarmana a rumfar nan Ishaq na Daki baya fitowa ga Hafsah wani Lokacin harda Badariya sai abun ya kara armashi,Laila ba ruwanta ga sakin fuska Anty Fa'iza kasa da sama take kirana kamar yadda Raliya ke Kirana,Sannan jininta ya shaku ita da Anun ta dinga rokona in bar ta su Tafi Bikin ta kaduna da ita Amana Hajiya zasu dawo da ita ban yi mgana ba sanin Halin Babansu da Mama ba lalle su bari ba. Sati daya nayi ina mata sai ga shi ta fito shar da ita abunka ga farar fata,ga jiki lawai lawai sai tashin kamshi take yi,Da naga ta matsa da mganar Tafiya da Anum sai nayi ma Yaya Ishaq mgana da kaina nayi mamaki da ya barta ammh yace kada ta Dad'e a dawo masa da yarsa. ranar Litini Laila taji Dadi tana ta Godiya Direba yazo ya kwashe su ranar karshe da kayan su aranar kuma Hajiya ta Turomin sauran kudina, na daka tsalle ina murna nayi sujuda na gode ma Allah. Batare da sanin Yaya Ishaq ba,naje na yi ma Amir komai har Uniform an basa na Biya musu kudin Tahfeez sannan na shiga kasuwa na siyo mai takalmin makaranta da jaka da littafai,yanzu nima sana'a ta Budemin ido nasan sirrin shiga kasuwa lungu da sako. *INGANTACCEN ZANCE*. *Akwai da INGANTATUN SAIWOWI na gyaran mejego ko amare*. *Haka uwargida ma ba'a barta a baya ba da irin nata tagomashin* *Kaya ne masu kyua ba garabiti ba, takanas ake kawo su daga chadi.* *Idan kina da kannen da za'a aurar, ki zo ki yi musu tanadi na mussaman*. *SAIWOWIN itatuwane da basu da illah* *Da sau'ki zaki same su, amma aikinsu yawa ne dasu.* *Kawai ki tuntu'bi Surayya HALIN YAU a wannan lambar dan samun gamshasshen bayani* *08032773332.* ✍️. *Janafty* *KNKB2005* *Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 05521790550,ban da tsarin kati wannan karo a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488* Ranar monday da safe bayan yaran sun shirya Hafsah tayi musu abun karyawa,Musty sai tura baki yake yi shi bazai je makaranta ba yau. Na kallesa ina kokarin saka masa safa yana Turje kafa cikin haushi na mangarar da kansa ina fadin"Zaka tsaya ko sai na dake ka..? Sai ya fara kokarin sakin mun kuka na ko zare mai ido ina fadin"Na dake ka ne da zaka min kuka..? Amir na gefe da ya shirya Tsaf yau zai fara zuwa makaranta yace"Umma cewa yayi bazai je ba, saboda Anum bata nan yau" Na kallesa da mamaki sai abun nasa ma ya bani dariya na jawosa jikina na Rumgume ina fadin"Haba babban mutum na Umma.Anum din ai yau zata dawo yi hakuri ka saki ranka kaji" Cikin muryan kuka yace"Da gaske yau zata dawo..? Da sauri na amsa mai da Insha Allahu sai ya saki ihu Ahmad na tayasa Amir na gefe an saka hannuwa aljihun wandonsa kamar wani babba na kallesa ina Dariya Hafsah ta fito daga Daki tana fadin"A'a yan jss ba zama ne yau..?a tsaye zamu tsaya..? Fuska yayi bai yi mgana ya Dauki Sabuwar Jakarsa ya rataya yana fadin"Umma yaran nan su zo mu tafi" Na bisu da Allah ya kiyaye hanya bayan na rike ma Ahmad jaka zan rakasu kofar gida Hafsah ta daga murya tana fadin"Amir shine ba mgana..?zaka zo ka same ni ne.." Muna gabda fita daga falon naji muryan Yaya Ishaq a sama yana fadin"Yaushe Amir ya fara zuwa makaranta ban sani ba..? Su sun riga sun fice sai na mikama Hafsah jakar Ahmad tabi bayan su ni kuma sai na Dawo tsakiyar falon, yana daga kofar Dakinsa alamun yanzu ya fito sanda zamu fita daga falon zuwa waje. Cikin sanyi na, na gaishesa ya amsa a gajarce yana sake fadin'Ko ba shi ba ne nagani da kayan makaranta ya fita da su Ahmad ba.? Kai tsaye nace"Shine ni naje nayi biya komai ranar jumma'a yau suka ce ya fara zuwa tunda karatu yayi nisa" Sai kawai ya tsaya yana kallo na Fa'iza ta sauya sauyin dake basa mamaki bai isa in zata yi abu ta nemi shawaransa ba, ance mai hali baya fasa halinsa kawai sai ya fara fada yana fadin"Meyasa kika raina ni ne Fa'iza kin ware ni kan sha'anin ya'ya na ban isa ki fadamin Amir zai fara zuwa makaranta ba sai dai ki rika yin komai kanki tsaye..?sai yanzu na yarda da mganar Mama, kina ganin yanzu kina samun kudi kina Dauke laluran kanki da na gida shine kike ganin zaki iya yanke hukunci kan ya'yana to baki isa ba,ba na so.." Ya karishe fad'a har yana nuna min yatsa kawai sai na saki baki ina kallonsa na kwaso gauron numfashi zan tare sa da mganar ya wuceni Fuu kamar kabubuwa ya fice sai Dakin Mama na bisa da kallo hannuna sabe da Haba na a fili na furta"Yau naji karfin hali ko na gani zencen ni Fa'iza" To in ba karfin hali ba sai yanzu kasan da ya'yan ka ne?a baya da kake banzar ta dasu ka zabi wasu akan su ba'ayi maka mgana ba sai yanzu ne kake da bakin mgana..? Kawai sai nayi tsaki na cigaba da Harkan gabana abun karyawansa ma sai Hafsah ya ma mgana ta basa, ni Daki na shige na kwanta a raina nace bazan sake yarda ka rika sakani Damuwa ba. Daman da kullatan fad'an safe ya shiga kuma Dakin Mama ta kara ma Wutar fetir, da yammah sai ga Direban Hajiya ya kawo Anum da sha tara na arziki kaya akwati guda nata ga kayan wasa har da karamar Ipad na game din yara,da Sabuwar jakar makaranta da littafai da kayan biki cike da Jakar bikin ga Hoton Amarya da ango nan sannan ga kudi dubu goma Sabbin yan Hamsim Hamsin a Cikin wata farar takarda,Harda takalma masu kyau sai sweet da chaculate na su musty,Anum da shigem kaud'i sai murna take yi bakinta ya tsinke da Labari har Yaya Ishaq dake ciki sai da ya fito,Yana kallon kayan Anum na ganinsa ta nufesa ta rikesa bakinta yaki yin shuru an bata kaza sun je kaza sun je kaza. Fuskarsa ba fara'a ko kad'an,kamar ta Fahimta ne yasa ta bar ta batunsa ta kwashe kayan taje ta nuna ma Mama Hafsah taso ta hanata nace ta kyaleta ta shiga ba dad'ewa sai gata tazo kiransa in ji Mama, ya tashi ya tafi ba jimawa sai ga shi ya shigo ina faman tattara sauran kayan da Anum ta watsar ya daga murya yana fadin"Daga yau ya'ta bazata kara zuwa wani gida kwadayi ba" Sai na Dago ina kallonsa ni yanzu ya Daina bani mamaki a baya sai nake ganin Rayuwa tasa yayi sanyi ammh daga Safiyar yau na Fahimci lambo yayi. Kamar zan yi mai mgana sai na fasa na zata shikenan kawai sai naji yana fadin"In ke zaki je kije, ammh kada ki kara tura ya'ata wani gida da sunan kwaad'ayi." Sai na sake dagowa ina kallonsa ban yi nauyin baki ba nace"to ai in dai kace naje kamar kace itama taje ne.Saboda ni ya'yana na zaba akan ka.Kai kuma ka manta ka zabi Zainab da iyalanta a kaina da ya'yanka..? Tsuramin ido yayi nasan yana mamakin kalamai na ne ni kuma ganin yaji mganata yasa na juya nayi shigewata Daki na barsa nan bansa ya yakare ba, Anum ta dawo da kayan ba jimawa su Amir suka dawo da ga makaranta sai Ihu ya tashi Anum ta Dawo labarai ta rika basu na abunda ya faru a chan har da abunda taci ta kwaso musu kayan suka yi min Baja baja da falo sai da na fito nayi musu fad'a Amir ya hau taya Anum tattara kayan yana fadin"Kiyi hakuri Umma zamu kwashe" Sai na Sassauta ina fadin"Lokacin sallah yayi ayi alwala ku tafi masallaci Anum tazo muyi namu a gida" Da haka suka kwashe kayan suka maida Dakinsu mazan suka fita alwala Babansu na dakin Mama ya tarasu suka tafi masallaci mu kuma mukayi namu agida ba abinci sai Hafsah tayi Taliya jallop,ta sa ka kazan da Anum tazo da shi na biki aciki,ita muka ci da Daddare kafin mu kwanta na raba ma yaran kayan Fulawan da Anum tazo da shi na Bikin harda lemuka na kuma aika ma Mama nata,ta kuma karb'e ko kunya, sai da safe na Kira Hajiya nayi mata godiya. Daga wannan lokacin sai ya Dawo sak Yaya Ishaq din da na sani mara ragowa sannan mai tsanani sai na Fahinmci,wani abu har da zafin Talauci ya sake firgitasa sai dai bai min tijaran da ya saba da agaban mama ko mutane, saboda yaga bakina ya bude yanzu zan maidasa mganar da bazai so ta fita wani yajita ba. Duk nayi biris da shi domin har ga Allah ba ina zaune saboda ina son sa ba ne,babu wani birbishin so a cikin zuciyata in a baya na so shi Saboda yana Uban ya'yana yanzu ko wannan Darajan bana dubawa,abu d'aya na sani ina zaune ne saboda ya'yana ba saboda shi ko jiginannen auransa ba. Shiyasa nake kama kaina ina chan ina Hidimar sana'ata da ga shi Har maman bana ta kansu,Anty Binta ma ta rage zuwa akai akai su Anty Mahma ma sai dai su leko mu ni kuma ban fasa abunda na yi niyya ba,Kananun lalurori har manyan ma ina Daukan su da sana'ar da nake yi,wannan zafin ran da na Talauci ban yarda na zauna ya saukemin ba,Ya saba in ya gama min Tijara na rika basa Hakuri ammh yanzu da ya fara in bana jin mgana zan bama banza ajiyarsa ko na bar masa wajen. A cikin wannan takun sakan da muke yi ne, kayan abinci suka kare dole ni na fidda kudi na siya Mama da gadara duk abunda take bukata zatace na bata kaza kamar ita nake yi ma wahalan,sai dai ban taba biye mata ba, ina ganin ta a matsayin uwa shiyasa ban taba Daga kai akanta ba. shi kuma komai nayi sai yace na rubuta in ya samu aiki zai Biyani ni ko nace shi ya Lissafa da kansa mana Muna cikin haka zazzabi ya Sarke sa kamar wasa ya kwantar da shi Ranar kwance ya yini Dakin mama,Yadda bai fad'amin ba shi da lafiya ba, nima ina da Miskilanci ko lekawa Dakin Maman ban yi ba ballatana nayi mai sannu Abakin su Amir naji Daada bai da lafiya, Mama ce ta leko da kanta Dakina da bata taba shigowa ba, sai dai ta tsaya daga bakin kofa tana ce min na bada kudi Amir ya raka Ishaq kemis  bai jin dadi,kamar nace bani da shi sai kuma ban ce ba na ba ma Amir dubu biyu suka tafi a ka mishi allurai da mganguna ashe maleria ce ta kamasa,ni iya dakina da dakin yara nake siyan ma mganin Sauro na kunna sai Dakin Mama ban yi tunanin yana jin cizon sauro ba ma. Abu kamar wasa daga zazzabi sai zawo cikin dare haka ya kwana zagayawa,da safe har da Amai duk  karfinsa ya kare,washegari daga zuwa bayi sai dai na je na daukosa duk ya bata jikinsa da amai da zawo duk yadda nake kauce ma wata mu'amalan ganin sirin juna tsakanina da shi sai da na yaye wannan Hijabin ranar,Tun kafin auran sa da Zainab ko Hannuna sai da kuskure yake gegata ballatana ganin juna a yanayin da bai dace ba,Sai ranar ni nayi masa wanka Maman dai bata yi masa rana ba,Ina yi ina kauce kauce shi kuma jiki yayi lakwas duk yayi laushi sai abun yayi min wani barambaram kwai namiji da suna Hajara. Bayan na yi masa wankan na koma na wanke bayin da kuma kayan shi da ya bata, sannan na fita baya damu kad'an inda Chemist yake na kira mai zaman wajen yazo ya gansa ya dora masa karin ruwa da allurai abu kamar wasa nan take sai da ya chajeni dubu Hudu,kada mutum ya raina ciwo komai kankantarsa,Yara sai dai suka Dawo makaranta suka iske sa rashe rashe ana masa karin ruwa,sai duk jikinsu yayi sanyi sai da nayi ta lallashin su sannan suka saki jiki yasha wahala rana zuwa dare duk ya fada abinci ma,ya kasa ci sai da Anty Binta tazo mai da Ferfesun kayan ciki ya samu ya ci kad'an yace bakinsa D'aci ga zazzabi ga amai da gudaawa. Anty Binta bata neman zaman lafiya sai da tayi korafin wai meyasa ba'a kaisa asibiti ba? Mama tace mugunta ta ta ce ta tashi kuma ina da kudin naki kaisa asibitin,ni bana biye musu sai na nuna ma ban jisu ba Mama fa sai ciwon d'anta ta taba shiga bangarena ita kuma Anty Binta in asibitin banza ne meyasa bata Dauke sa ta kai sa ba..? Wlh na yarda da maganan Hausawa da sukace in kana da abun yi,ba komai ke damunka ba. a baya ne in Mama ko Anty Binta sun min wani abu yake damuna nayi ta kuka yanzu na manta rabo na da kuka akan su,To ayyukan gabana ma sun isheni inaga naga Lokacin sauraransu ko suna yi baya Damuna, kamar irin na riga na zama Jan wuya a lamarin ballatana yanzu da nake yawan samun masu son Turaruka ta bangaran Hajiya sai ayyukana suka yi min yawa. Ashe sun raina kulawar da nake basa balle da suka ga kurajen baki sun fito mai yaba yaba na alamun wucewa Mura, sai Mama ta saka Anty Binta ta kira Zainab na ta fad'amata wai tunda bazan iya kula dashi ba,yana da wata matar zata zo ta kula da shi,Sanda akayi ma bana gidan naje kasuwa da na Dawo Hafsah take fadamin sai nayi mirmishi ban ce komai ba. Ashe ko sun kirata sun zuzuta abun Hankali tashe ta d'au alfarma a wajen aiki ta taso,ita da Fadil Farhan saboda makaranta ina tsaka da Hidiman Zobo na ta shigo,Direba na binta da kayanta A karamar a kwatinta kwata kwata ban yi mamakin ganinta ba, na tsallake komai na tarbeta sai dai Mama bata bari ba,ta janyeta zuwa Dakinta chan ta sauka a fili nace a gayyas. Na koma dakina na cigaba da aikin da nake yi,Chan ba jimawa sai gasu sun shigo ita da Mama,Zainab na rike da Fadil sai alokacin muka gaisa kallo na take yi tana kare ma falon kallo Mama tayi mata Jagora har dakin Yaya Ishaq ni dai ban bisu ba saboda ba wanda ya gayyaceni sun dan jima aciki sannan suka fito sai ta kalleni tana fadin"Maman Amir zobo kike saidawa yanzu? Ina yar dariya nace mata'"Eh wlh muna tabawa ya hanya..?ina Kika baro mana Farhan..? Kai tsaye tace"Yana wajen mommy saboda makaranta" Mama sai jiranta take yi daga waje ganin muna ta mgana yasa ta Dago labule tana fadin"Zainab muje ki yi wanka ki yi sallah sai ki ci abinci" Sai ta amsa mata kafin ta fitan sai da tace min"Ashe Honey haka yayi ta rashin lafiya..? Sai na gyada mata kai ina fadin"Ai yama ji sauki yanzu' Cikin jimami tace"Ayya Allah ya basa lafiya" Na amsa mata da Ameem sannan ta fice zuwa Dakin Mama ni ko sai da na gama zuba zobo na sannan na shirya ma zainab abinci daman da rana Shinkafa da miya nayi mana da Salat har dare saboda na gaJi bazan iya wani girki ba,har dakin Mama na bita da shi har da zobon na zuba mata Bata a falo kila tana ciki Mama sai Hararata take yi ban bi ta kanta ba na sauke abincin hannuna na fice abuna. Sai da na had'a kayan wanke wanke bayan yara sun dawo makaranta ni nace su shiga Dakin Mama su gaida Antynsu suka shiga gabadayansu suka gaisheta daganan bayan sun ci abinci suka shige Dakin babansu Fadil na Hannunsa suna ta wasa Amir ne kadai ke falo yana duba Littafansa na makaranta. Da kaina na shiga zan dauko kololina da wanda na kai ma Mama nata,na iske zainab na zaune tayi wanka ta sauya kaya waya a hannunta tana ta Dannawa sannu da gida tamin na duka ina kwashe kwanukan da suka yi amfani da shi Mama na gefe nasan hira suke yi da na shigo ne Maman ta Dauke mganar ammh saboda salon cin Mutumci sai ta gyara zama tana fadin"Zainab nace ba.." Sai ta Dago tana fadin"Na'am Mama" Mama tace"Daman so nake naji ko zaki d'an kwana biyu kafin ki koma..? Zainab ta yamutsa fuska kafin tace"Anya? hutun kwana biyu suka bani a wajen aiki" Mama ta kalleni ta gefen ido tana fadin"Gaskiya gwara ki tsaya ki kula da shi.ita wannan baya gabanta ta sana'arta take yi tunda ta fara wannan sana'ar nata bata kallon kowa da Daraja kema matarsa ce shiyasa nace Binta ta kiraki kizo ke kila kya kula da shi yadda ya kamata" Sai tayi Dariya batace komai ba ni kuma ina cigaba da Tattara kwanukana ina jinta daman tayi mganar ne saboda naji. Ganin Zainab batayi mgana ba yasa Mama ta cigaba da fadin"Ni dama in kin tashi tafiya zaki tafi dashi chan Abujan,zan fi samun kwanciyar Hankali zamansa anan bai da wani amfani" Na mike kenan Zainab tace"Mama naga Maman Amir fa na kula da shi"sai Mama ta wani yarfa Hannu tana fadin"Wlh bata kula da shi, wannan da kika gani ai muguwa ce ta sosai" Tafad'a Lokaci daya tana nuna ni da baki kamar zan fita na barsu sai na fad'a kamar an min wahayin mganar na Tsaya ina kallon Mama kafin nace"Aiko baki ce ta tsaya ta kula da shi ba tunda tazo, na sakar mata komai Tunda itama matarsa ce, kamar yadda yake da Hakki a kaina itama yana da Hakkin akanta" Daga haka na juya nayi ficewata Mama ta rakani da fadin"babu abunda ta iya yanzu sai rashin kunya har shi ta raina" ni dai bansan ya suka kare ba ina wanke wanke abun na dawomin ni kaina ina mamakin yadda bakina ya bude wani Lokacin na yarda ba shawara ko nuniya ke saka mace tayi baki a gidan mijinta ba Wuya ce mutanen duniya ke chanzata,batare da tama sani ba kamar yadda yake faruwa dani domin ban taba kawowa ma kaina zan iya maida ma Yaya Ishaq mgana ba ko shi ko Anty Binta ba sai ga shi shakkar da nake ji da yanzu wlh bana gani,wani abun ma ina raga musu ne saboda wasu Dalilai. Tunda Mama ta raina kokarina ni ko a raina nace sai na bata mamaki na tsame hannuna a kula da shi ai daman ba hakki na ba ne, ita da bai jingine auranta ba,yafi zama Dolenta ta kula da shi nifa daman taimako ne da Darajan ya'ya sai ta wani Fanni in na Duba zumumci. Sai ana mangariba na gama wanke wanken nan sai lokacin Hafsah da Badariya suka dawo,Amir da su musty sun bi babansu zuwa masallaci daya fara rarrafa d'azu,sannu da gida suka yi min kowacce ta shige inda tafi wayau. Ina komawa Daki daman na Dafa ruwan zafi nayi wanka,Hafsah kuma nace in tayi sallah taci abinci taje makotan mu ta Dauko min ninkan Ayan da dazu yaron gidan ya shigo Siyan zobo na bashi sai ta amsamun na shige Dakina nayi wanka nayi sallah na zauna ina azkar,ina ga sai da sukayi sallar isha'i suka dawo shi Uban Gayyar Dakin Mama ya shige yaran kuma suka dawo Daki Hafsah da ta dawo dauko nikan na saka ta raba sauran abinci nace ta diba ta kai Dakin Mama da yawa Saboda Zainab sauran su ci su da yara. Akace Namiji ya iya munafunci nidai tunda na shiga ban fito ba Hafsah na bari da hada kunin Aya,Ashe da ya gama zamansa Dakin Mama tare da Zainab suka dawo Dakinsa sai suka bar Fadil wajen Mama bakinta washe,Adakin nasa ta kwana ni ban sani ba ko da na tashi da asuba ban lekasa ba ina ma yara shirin tafiya makaranta,muna falo da ni da yaran suna cin abinci sai gata ta fito tana mika sanye da rigar barci Riga da wando masu taushi gashinta kanta ya bazu wata hula ce ta saka ana ganin kanta,sau daya na kalleta ban kara ba ita ta fara gaisheni na amsa ta cikin Sakin Fuska har ga Allah ban ji Haushi ba, to me zai dameni ai ba yau aka fara ba an dade ana haka. Abun karin ma na aika Dakin Mama basu ci ba Zainab ta basu kudi suka siyi kayan tea Badariya tazo kitchen dina ta soya musu kwai, ni ina Dakina Hafsah ke fadamin nace saji da shi dai. Sai da chan rana na shiga na Duba sa yana kwance sun yi kaca kaca da Dakin,daga nesa na tsaya na gaishe shi da jiki ya amsa sai naga yana karemin kallo sai na Tsargu da Sauri na kalli kaina Riga da sikat ne a jikina Atamfar ni na siyeta da kudina na Dinkata sai dai dinkin yayi min Cif a jikina ganin yadda ya kuramin ido ne yasa kawai na juya zan fice da Sauri ya yunkura ya mike yana kiran sunana na Juyo ammh ban karisa gabansa sai yace"Fa'iza kariso mana bana jin dadin yadda kike maida Dakina kamar bakon ki" Sai kalamansa suka bani mamaki kai tsaye nace"ai bakon ne a wajena.." Bai damu ba sai ya dan kalli D'akin yana fadin''Haba Fa'ita kwana biyu ba'a zo an gyaramin Dakin ba. sannan kuma ga kayana duk sun yi Datti wlh ko na sawa bani da shi" Na kura masa ido ina Dariyan sunan da ya kirani wai Fa'i ta abunda ban taba ji ba ko acikin mafarki har da wani lankwasa wuya yake yi na yaudara sai kawai nayi Dariya kafin nace"Ai wannan ba Hurumina ba ne Hurumin Matarka ce ka kirata ta gyara dakin sannan ta kwashe kayan naka ta wanke" Kai tsaye yace"Saboda me sai zeey.?ai ke kika saba yi Fa'iza kada ki bata ladan ki don Allah" Karfin Halinsa ke bani mamaki cikin gajiya da mganar na juya ina fadin"Ba bata lada ba ne, Itama Hakkin ka na kanta ta kula dakai tunda tazo ta amsheni daman ni taimako nayi ba Hurumina ba ne" Har zan fice ya kwalamin kira "Fa'iza..' Sai na juyo ina fadin"Wlh bazan yi ba ka kire Zeey din taka mana, inace ita ma Matarka ce" Sai kawai ya koma ya zauna yana fadin"Fa'iza yaushe na fara mgana kina min gaddama sannan yaushe na fara mgana kina sa'in sa da ni..? Kai na tsaye nace"Tun ranar da ka furtamin da kanka ka zabi wata matarka fiye da ni nima tun ranar na zabi rayuwata da ya'yana sama da kai.Komai kaga ina yi maka don Allah da taimakon zumunci ne" Daga haka na fice na barsa da sanyin jiki Hidmar hada zobo na fara satin nan Hafsah karatun Safe suke yi,Allah yasa tamin shara da Safe wanke wanke kadai nayi sai na share tsakar gidan na wanke ina wajen Zainab ta shige bata fito ba, ni ko dakin ban koma ba Fadil ne ya dinga kuka a Hannun Mama ta kasa lallashinsa sai na shiga na karbesa sai na Fahimci yunwa yake ji ina da Sauran garin kuni nan da nan na dora ruwan zafi daya tafasa na Damamai na Duramai tas ya shanye sai barci,naja zani na goyesa ram a bayana na cigaba da ayyukan gabana Mama daman tagaji da renon ta shige Daki tayi kwanciyarta Tunda baiwarta ta Dauke komai. Da rana Danwake nayi da salat,aiki duk ya Chudemin Zainab kam da uban gayyar sun shige daki ba mai jin motsin su, Fadil na Dakina yayi barci da ya tashi nayi mai wanka nima nayi ban san fitan ta ba ta koma Dakin Mama tayi wanka ba,sai da ya tashi ya fara rigima na lekata sai na ganta na mika mata shi ina fadin"Ya tashi yana rigima" Ta karbe tana fadin"Daman tunda naji sa shuru nace yana Hannun ki" Mirmishi nayi mata na fice,ina komawa Daki na ci karo da shi ya fito Daga kitchen da ya gani sai yayi Turus ni kuma sai nayi kamar bangansa ba zan wuce dakina yace"Dama..dama kuna da ruwan zafi ne..?garin ai ko sanyi zazzabi bai sakeni ba kada na Dawo da shi da wanka da ruwan sanyi" Da nayi niyyar na yi wucewa ta ne sai wata zuciyar tace ashe ya Dameki..?sai na juya ina"Ka kira Zainab ta saka maka mana" Sai ya bude ido yana kallona,na ganin na juya yasa yasha gabana yana fadin"Don Allah Fa'iza don Allah nace.Zeey bata shiga kitchen achan komai ma'aaikata ke yi mata" Rashin kunya ba Halina ba ne yasa na juya na koma kitchen na kunna gas na Doramai ruwan zafin na fice na barsa nan falon inaga da yayi zafi ne ya kashe gas din ya juye,yau alhamis ne da la'asar yara suka dawo makaranta Amir ya taimakeni ya tayani Dura zobon a gorina Anum na shirya mana nayi na Safe har ya kare wannan na yammah ne,Addu'a nake yi Allah ya dawo da Hafsah ta dora girki sai biyar da wani abu ta shigo tana shigowa Amir yace'"Umma ga Antyn Hafsan ta dawo" Daga ganinta ta gaji ta sauke jaka tana fadin"Da Antyn Hafsah tayi me..? Ina Dariya nace'Yaji ina ta cigiyarki ne aiki yayi min yawa ban dora girki ba" Sai ta ce"Bari naci abinci na dawo hayyacina"Da sauri nace"Yauwa yar albarka mu in mun gama sai mu had'a kwanuka mu yi wanke wanke" Da Sauri Anum tace"Umma ni zan yi" Ina dariya nace"Ko baki ce ba tare zamu yi kafin nan gaba ki iya na sakar miki,ammh kafin sai kin share inda muka bata" Musty yace"Ummi ni zan share" Nace"To ya'yan Umma yan albarka" Ahmad na gefe yace"Umma zan wanke miki robobi" Amir yace"Kadai samu na wasa" Gabadayanmu muka saka Dariya gabadaya bani da damuwa indai ina ganin Dariyan ya'yana su nafi damuwa da su bangaran su Mama tunda zainab tazo ta bud'e musu bakin aljihu suna cin dadin su yau nama gobe kaza ni dai ya'yana suna daki basu gani ba,ballatana su saka rai ammh fa Fadil na wajena ni nake mai komai har wanka uwar tana nanike wajen miji ana shan soyayyah. Washegari da Safe bayan yara sun tafi makaranta na fada ma Hafsah yau zobo Sau daya zamu yi,sai kunin Aya shiyasa da Safen bayan yara sun tafi makaranata na samu kujera na kwanta sai barci Hafsah ke dafa zobon awaje basu da shiga makaranta yau,ai naji dadin zaman Hafsah a wajena tana bala'in taimakamin kan sha'anin gida da sana'ata wani lokacin ba domin ita ba,bansan ya zan rika yi da wasu ayyukan ba. Na fara barci sama sama na rika jin Hayaniya na gyara kwanciyata saboda ban ji hayaniyar ko ta macece ba,Sai da Mama ta shigo har Falona ina kwance kawai naji ta Dakamin duka na Bude idanuwana da suka yi ja Saboda barci sai naga Mama a saman kaina Tsakani ga Allah ina gajiya saboda aikin Hannu nake yi komai sai na sarrafashi da kaina. Ina kokarin tashi zaune kawai ta hau ni da fad'a nama kasa gane in ta dosa sai da nace"Lafiya Mama..? Cikin wani kallo tace min"Bansani ba.Kya ce lafiya mana kina kwance kina barci,shi kuma ga shi chan bai da lafiya shi kika bari da wankin kayansa" Sai taga na mike kawai zan shige cikin D'akina kai tsaye ta saka hannu ta fizgoni na dawo gabanta tana zare min ido tace"Don ubanki ina mgana kina wucewa,ni sa'arki ce.? *INGANTACCEN ZANCE*. *Akwai da INGANTATUN SAIWOWI na gyaran mejego ko amare*. *Haka uwargida ma ba'a barta a baya ba da irin nata tagomashin* *Kaya ne masu kyua ba garabiti ba, takanas ake kawo su daga chadi.* *Idan kina da kannen da za'a aurar, ki zo ki yi musu tanadi na mussaman*. *SAIWOWIN itatuwane da basu da illah* *Da sau'ki zaki same su, amma aikinsu yawa ne dasu.* *Kawai ki tuntu'bi Surayya HALIN YAU a wannan lambar dan samun gamshasshen bayani* *08032773332.* ✍️. *Janafty* *KNKB2006* *Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 0552179550,ban da tsarin kati wannan karon, a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488* Ba nufina in yi Mama rashin kunya ba ne, saboda a uwa na Dauketa sai na Sadda kaina kasa ina fadin"Naga fad'an bai shafeni ba ne Mama" Sai ta saki baki tana kallona lokaci daya tana fadin"Wato bai shafe ki ba? ko ni ki keso na kwashe kayan nasa na wanke mai ishashiya Dangin Jaraba? Sai na dago kai kamar zan yi mgana sai na fasa na kama Hanya na fita Tsaakar gida yana Zaune kan kujerata ta tsuggunon Tsakar gida, ga kaya a gabansa ya saka Hafsah ta taran masa ruwan famfo Har ga Allah Dariya sai da ta kusa kamani yadda yayi kamar mai ko wankin,Karisa fitowa nayi ina fadin"wanki da kanka ina Zainab din..? Ko kallo na bai yi ba nima sai na juya ina kallon Mama da ta zata da na fito zan karbesa ne, sai taga akasin haka kafin tayi mgana na tare ta da fadin"Mama kada kiga laifina ba ga Zainab ba, ai itama matarsa ce. kince tana da Hakki a kansa kamar yadda nake dashi daman kuma kin kirata tazo ta kula dashi tunda kin ce ni ba takansa nake bi ba,Ki kirata tana ciki ta fito ta karb'i kayansa ta wanke shima ai yana daga cikin Hakkokin da kika mgana" Ina gama fad'in haka na kama Hanyar Dakina Mama ta rakani da kallo cikin mamaki tace"Fa'iza yanzu ni kike fadama wannan mganar..? Kafin nayi mgana ya katseta da fadin"Don Allah kyaleta Mama tun jiya na roketa ta rantse bazatayi ba" Sai mama ta shiga tafa Hannu tana salallami ni ko nayi shigewata Dakina na kwanta a gado na,ban san ya suka kare ba sai wajen sha d'aya na Safe na tashi na iske Hafsah ta gama Had'a zobon tana jiran ya huce ni ita ke bani Labarin yadda suka kare Zainab din ta fito tana wani yamutsa fuska tace a kwashe kayan aka kai wanki da guga zata bada kudin wai har tana fadin"Honey sai da nace kayi zaman ka achan ka ki inda kana chan wani kuma wanki ne sai kayi da kanka..? Dariya ma abun ya bani Hafsah tace"Yaya fa'iza wlh kin burgeni gwara da kika fara nuna ma Mama abunda take yi bata kyautawa" Mirmishi kawai nayi ban ce komai ba,ni ba mgana na maida mata ba Abunda ta bukata nayi mata daman na rantse bazan kara yi masa komai ba indai matarsa na nan,ba ni sun raina nawa ba? to yar masu da shi tazo tayi musu su gani. Ashe mgana bata mutu ba mama ta rika yawo dani wai Ishaq bai da lafiya bani da Tausayi da Imani na barsa zai wanke kayansa da kansa, da Mama tamin mgana nayi mata rashin kunya da Yammah sai ga Anty Binta tare da Anty Mahma har Dakina Anty Binta ta biyoni tana gayamin duk mganar da tazo bakinta cin mutumci sai wanda ta manta,Kamar na sani nace Hafsah ta tafi da Anum da Amir gidan nik'an Aya Ahmad da Musty ne kuma suna Dakin Mama wajen Fadil. Ko daga kaina ban yi na kalleta ba,sai da naga ta Dage wai in nace zan cigaba da yi ma Mama rashin kunya zamana ne zai kare a inda aka rufamin asiri sai alokacin na Dago ina kallonta kafin nace"To ko a yanzu din ma me ya rage..? Adai yi sha'ani an cuci na kauye" Bata Fahimci mganata ba ta cigaba da fadin mganarta ta dauka irin da ne har tana kokarin kamamin kunni nako mike nayi baya ina kallonta cikin Hargowa tace"Zaki dake ni ne Tattaciya..?bar ganin kin fara wannan sana'ar ta biyar goma dama bamu san asalin balbela ba ne sai ta gaya ma da ga kasar masar ta fito.." Na lura suna adawa da samun Cigaba na, a raina ko nace sai dai ku mutu sana'a yanzu na fara shi wlh. Ganin ta fara isata da mgana ga Musty ya shigo ya tsaya yana kallon mu yasa nace"kiyi hakuri Anty Binta ni fa ba rashin kunya nayi ma mama ba. Cewa tayi ta kira zainab ne saboda tazo ta kula da shi,Tunda ni ba na kula dashi. nayi laifi domin na sakar mata komai tunda gata tazo.? ai acikin kula dashi har da yi masa wankin kayansa.." Kawai sai ta kalleni bataji kunya ba tace"Lalle kin cika mara kunya Zainab din sa'arki ce ko Matsayin ku da'ya da zaki rika had'a kanki da ita..? Sai na dago ina mirmishi kafin nace'Tabbas ba matsayin mu d'aya ba, nasan wannan tun kafin ya aurota ya raba mana matsayi kuma kuka rabamananwannan matsayin. sannan ni nasan ba sa'ata bace saboda ni marainiya ce ban aje ba sannan ban ba wani ajiya ba, sannan ni ba yar gata bace kuma ba yar boko irinta ba, ni yar gargajiya ce da wahala da komai na ke rayuwata kin ga ni kaina nasan tazaran dake tsakani da ita kamar tazaran sama da kasa ne ku yi hakuri na manta ne ammh daga yau zan kiyaye zan kuma tsaya a iya matsayina" Sai ta kad'a kai tana fadin"Da kin ma kanki kiyamullaili" Ta juya ta fita Musty ya rugo da gudu ya rikeni yana fadin"Umma zagin ki take yi..?. Da sauri nace"A"a hira muke yi Musty" Yaro da Fahimtar abu sai yace"Umma naga fa fada take miki" Nasan sa da surutu su Amir na Dawowa zai gaya musu sai nace"Waya fad'a maka..? Hira muke yi baka gani ba.? Sai yayi shuru ya kasa mgana ni kuma sai na daga sa sama ina juyi da shi sai ya fara bangalan dariya. Har Anty Mahma sai da suka kitso mata zencen ta shigo Dakina tana fadin"Gaskiya Fa'iza baki kyauta ba,ban san ki da haka ba,Bai kamata bai da lafiya ki barsa da wanki ba. kuma ina ruwanki da Zainab ita da ba mazauniya ba, dubiya tazo yi zata koma inda ta fito ke dai kiyi aikin ladanki kada ki manta duk abunda kika yi na lada agidan mijinki za'a ninka miki ne kin karanta na kuma san kin san haka" Gani nayi in na tsaya mata bayani ma bata Lokaci sai kawai nace"In sha Allahu baza'a kara ba" Sai taji dadi ta dafani tana fadin"Yauwa ko ke fa Fa'iza in anjuma ki shiga ki bama Mama Hakuri shima ki basa Hakuri" Sai na gyad'a mata kai araina ina jinjina al'amarin wannan rayuwar. Sai ta gyara zama tana fadin"Hajiya Fa'iza mai zobo da kunin aya naga fa alaman kin fara samun kasa da wannan sana'ar kin zama big madam" Sai ta bani dariya na dara ina fadin"Kai Anty mahma da zoyala" Agabanta Hafsah ta had'a kunin Ayan da zasu tafi na bata harda zobo ta karba tana fadin"Kada mu zama karya Jali fa..?. Sai nace"Kada ki damu bazaku karya ba" Sai tamin godiya ta fice zuwa Dakin Mama ina jin tafiyar su ita da Anty Binta Gogan daman dakin Mama ya yini shiyasa Tun safe bamu hadu da Zainab ba sai da Daddare muna falo ina ma yara karatun Hadisi suka shigo ita da shi,Yaran sun riga sun sani in suna karatu ba na barinsu su tashi sai ba su tashi ba Ahmad ne ya mike da gudu ya nufesa sai ya Dagasa sama yana fadin"Kai ma fa ka fara zama Lukuti irin musty" Saukesa yayi ko sauraran gaurancin da Ahmad ke masa bai yi ba Zainab kuwa kala batace min ba,gani nayi kamar ranta yana bace ne sai nima na kame kaina haka suka shige ko sannu Daga shi har ita ba wanda yace min. nima ban damu ba na cigaba da yi ma yara karatu bayan mun gama nayi musu Tarihi sannan nace su je su kwanta. Ni da Anum da Hafsah muke kwana adakina Hatta Ahmad na maida shi tare da su Amir da Safiyar asabar suna da Tahfezz karfe Takwas na tafi kaisu da kaina Saboda Amir ya shiga ajin yan Hadda akwai littafan da zai siya sannan ina son naji karin bayani,na jima a makarantan suna ta gayamin kokarin yarana musamman Anum da Amir malamin Qur'anin su Anum yake min godiya lokaci d'aya yana Fadin"Saudatu ta fadamin Ummansu ke musu karatu agida sosai na yaba miki kin yi kokari kuma hakan da kike yi ya kara taimakon yara wajen hazaka da maida Hankali da ace iyaye mata da maza zasu san amfanin koyar da yaro kad'an daga abunda ka sani agida da yara da yawa sun zarce Tunanin iyayansu" Na jinjina kai ina yarda da mganarsa Saboda ban zauna ba ko na bangaran Bokon da ban iya ba ina sawa su koyama junansu na addinin kuma da na kwarewa ban ta gajiyawa ba domin shi kadai gareni da zan basu su godemin watarana. Sai wajen Tara na Dawo gidan na iske Rigima acikin gidan Tsakanin Zainab da Yaya Ishaq,Allah ya taimaka Hafsah bata nan na aiketa kasuwa ammh Badariya na gidan,Suna Dakinsa ne ammh fad'an nasu yayi kamarin da gabadayansu suke daga muryoyin su,da na dawo na kasa karisawa Dakina kamar zan shiga na gani wata zuciyar ta kwabeni tana fadin"Ke fa'iza ina ruwanki.? Aiko sai na kama kaina na kama Sabgan gabana dakin yaran na fara gyarawa na fito falo kenan Sai ga shi ya fito har yana Tureni bai sani ba nayi Saurin yin gefe kamar kububuwa haka ya shige Dakin Mama itama sai gashi ta fito tabi bayansa tana fadin"Wlh baka isa ba Ishaq" Itama tabi bayansa Fuu kamar zata tashi sama,sai gani rike da baki ina binsu da kallo ina nanata sunan Ishaq din da naji ta ambata, tunda nake ban taba jin ta kira sunansa gatsal ba sai dai Honey, ashe su Honey an jiki yau din nan. Domin duk rashin karfin jina haka na rika jiyo tashin muryoyin su Mama nayi suna yi kamar ta kasa tsawarta musu ne sai ga Badariya ta shigo da Fadil tana Lallashinsa yana ta kuka na ijiye tsintsiyan Hannuna na karbesa ina fadin"Me ya same shi? Badariya sai ta koma ta zauna tana fadin"Rudewa yayi da hayaniyar iyayan.Ni kaina barci nake yi sai da na tashi a firgice" Kamar zan tambayeta sai kuma na fasa,Daman nasan zata koramin yadda akayi Kitchen na shiga na Dauko Purewater nazo na zauna ina basa yana karba da sauri alamun kishi yake ji cikin alamun Tausayi nace"Allah sarki bawan Allah kishi yake ji" Badariya tace"Komai ma zai ji tun safe an fara fada,Daman ni nasan sai haka ya faru yadda Yaya Ishaq ya gina auransa ba kan turba mai kyau ba ne Anty Fa'iza" Sai na kalleta ina fadin"Hala me ya ke faruwa..?. Sai ta gyara zama tana fadin"Nima ban san kan mganan ba ina dai jin Kan tafiyar Anty zeey ne.Babanta ya Turo mata Mota tuni Direban ma ya iso zata koma Abuja to ina ga shine Yaya yace wlh bazata tafi ba sai dai in ta tafin ta fara shirin dawowa nan gabadaya ku zauna tare. shi bazai rika binta ba tunda baya aiki achan yanzu ita kuma ta Daka Tsalle tace bai isa ba sai ta tafi kuma bai isa ta ijiye aikinta ta Sauya rayuwarta Saboda shi ba,in bazai Bita ba sai dai ya bar shi" Sai na jinjina kai jikina duk yayi sanyi Badariya tace"Ta wani fanni fa tana da gaskiya abunda ya zaba mata ne Tun farko rana tsaka ba shi da Hujjan da zai ce a'a duk wanda ya siya rariya yasan zata zubda ruwa" Kafin nayi mgana Zainab ta shigo Dakin tana kiran Badariya ta kawo mata Fadil na mike na mika mata shi ta fita dashi nima sai na bita Daidai Zainab din ta fito da karamar akwatinta ta kalli Badariya tana fadin"muje mota da shi" Taci gayunta ta yafa mayafinta abun nasa ya shafeni ko sallama batamin ba ta juya ta fara tafiya kenan Ya fito Daga Daki cikin Daga murya yace"Wlh Zainab in kika saka kafa kika fita daga gidan nan batare da izinina ba kin tafi kenan" Dam!naji mganar nasa na d'ago ina kallonsa ita ma sai ta tsaya cak kafin ta juyo tana kallonsa Mama ta fito daga Daki hannunta a saman kai tana fadin"Na shiga uku ni Saudatu me zan ji haka..?Don Uban ka ka janye kalaman ka ko ranka ya baci" Idanuwansa sun sauya launi yace"Bazan janye ba Mama haka nace.Wlh bazan zama jani talau ba..Ni ke auranta ko ita ke aurena..? Mama ki duba fa wannan mgana taya za'a kafa min sharadin zuwa Abuja ina naga ko kudin mota.?zirga zirgan kansa ina naga kudin yinsa..?in a baya ina da aikin yi na dauki wannan Dawainiyar yanzu ta sani bani da shi To meyasa bazata zo ta zauna da ni a inda nake da shi ba in dai har da gaske tana so na? Yafad'a cikin bayyana bacin ransa,Mama kuwa ta kasa mgana Ni kaina ban ce komai ba ni da Badariya muna tsaye cirko cirko,kamar wasu zakaru,ita ko Zainab sai batayi mgana ba ta jawo akwatinta ta shige Falona ta fito da waya tayi kira sai ta sauya Harshe turanci da Fillanci. Shi kuma Mama ta shigar da shi Daki bansan me take fadamai ba,chan kuma sai ga Anty Binta suka sake kulewa Daki itako Zainab tana falo na kafa d'aya kan daya tana girgizawa karamar akwatinta na gefe sai hura Hanci take yi bini bini ana kiranta a waya tana mgana yadda batamin mgana ba nima sai na kama kaina na fito ina harkan gabana. Zuwa azahar ina waje ina Dafa zobo na sai ga Mahaifin Zainab ya fad'o gidan kamar daga sama ashe jirgi ya shigo ya iso kano,Direban da yazo daukan Zainab yaje ya Daukosa Kai tsaye ya shigo cikin Hanzari ina gaishesa ko amsani bai yi ba cikin Kaushi da Dagawar murya yace"Ina Ishaq din..? Muryansa ya fito da Zainab Daga dakina tana ganinsa ta nufesa da Sauri ta fada jikinsa ta fashe da kuka tana Fadin"Daddy wai ni Ishaq zai ce in na fita a bakin aure na..?ni Daddy Ishaq fa..? Sai ta kara saka kuka,Cikin Kakkausan murya yace"Shi..Am here bai isa ya fad'a miki wannan mganar ba,Who is he.? Mganarsa da kukan Zainab ya fito da Ishaq da Mama da Anty Binta suna ganinsa suka fara kame kame Mama ke fadin"Alhaji sai da ta taso ka? Kallonta kawai yake yi bai yi mgana ba Ishaq ne ya nufesa yana fadin"Daddy k.." Hannu ya d'agamin cikin tsawa kafin yace"Kayi min shuru Butulu kawai." Sai ya tsaya ya kasa gaba ballatana baya Su Mama sai ido yayi kasa,Hannun Zainab ya kama kafin yace"Ina son mgana da kai domin ba zama nazo yi ba" Da Sauri Mama tace"Mu shiga daga ciki Mana Alhaji" Wani kallo ya watsa mata Lokaci d'aya yana fadin"Ba ni da wannan lokacin.Nazo ne Ishaq ya maimaita abunda zeey tace ya gayamata.." Yafada yana bin su da wani kallo ni dai ina gefe ina kallon ikon Allah. Ishaq ya sausauta murya yana fadin"Daddy da ka shigo ciki don Allah" Cikin Tsawa yace"Ina da Lokacin shiga ciki ne ballatana naji shirmenka?nace ka maimaita abunda ka fad'amata so nake naji da kunnena" Ishaq sai ya gyara Tsayuwa yana fadin"Daddy gaskiya na fada mata nace baan iya juran binta Abuja ba sai dai ta dawo nan mu zauna tare" A wulakance yake kallonsa kafin ya nuna gidan cikin Yatsina yace" A wannan kejin gidan zata zo ku gamutsu da iyayanka da matarka..? Yafad'a yana masa wani kallo lokaci daya yana kare ma gidan kallo a wulakance,Gabadaya su Mama sun daskare sun kasa mgana Yaya ishaq kuma sai ya sunkuyar dakai ya kasa mgana cikin kakkausan murya ya cigaba da fadin"Na ce a wannan a kurkin gidan kake tunanin y'ata ta bar komai nata ta dawo ta zauna dakai saboda kai ne autan maza ko? Yaya Ishaq ya dago yana fadin"ammah Daddy.." "Dakata min shashasha butulu a irin wannan gidan ka ganta ka aureta..? Nace a irin wannan gidan ka ganta ka aureta da zakace hakkun Dole sai tazo ta zauna da kai a haka..? Ya fada bayan ya katsesa,cikin Fusata da Bacin rai. Ya nuna Zainab cikin Daga murya yana fadin"Lokacin da ka y'ta kace kana sonta acikin rayuwar hutu da jin Dadi ka ganta.cikin iliminta da tarin gata ka ganta kaji sha'awanta ka nemi auranta na aura maka ba domin ka chanchanta ba, sai domin nayi maka alfarma ina kallon ka kamar D'ana ashe baka da mutumci ban sani ba..?yar tawa kake so ka saka ka maidamin ita bazawara..? Yaya Ishaq yace"ni ban ce zan saketa ba"Ya taresa da fadin"Ba ka ce ba kalaman ka me suke nuni..?kace in ta fita kada ta dawo..?so kake ta ijiye rayuwarta da Aikinta da komai nata tazo ta tare a wajen ka, to ka ba ta mene..?Kada kaa manta ko da ka ganta chan ta fara gudanar da rayuwarta bazata iya zama a ko'ina sai a inda ta saba.Bazan lamunci wannan rainin da iskancin ba,in ba ma kana Butulu ba an dauke maka nauyin ya'yanka na Dauke ma nauyin gida da zirga zirgan ai duk hakkin ka ne sannan na Dauke maka nauyi ita kanta Zainab din hakan ma baka gode ba kawai naka ka shiga mota ka rika zuwa kana dubasu ne zai zame maka matsala..?batulci zakamin ko kuwa zafin Talaucin ne yasa ka fara Nuna min akan ya'ta..? Ya fad'a yana kallonsa cikin fusata,Sai wajen ya Dau shuru Mama bakinta yayi nauyi sai Anty Binta ta rika ma alama da tayi mgana itace tayi karfin Halin cewa"Alhaji ayi hakuri duk mganar bata kai haka ba a zauna a warwareta" Ko kallo bata ishesa ba yace"Zan iya warware mganar ko wata iri ne ba sai na zauna ba,Kan ya'yana zan iya shari'a da ko waye na lura D'anku baisan  mutumci da Hallaci ba,duka abunda nayi mai bai gani ba in na barsa da Dawainiyar Zainab din zai iya Dauka ne..?to bai isa ba ku fadamasa bai isa ba.ba haka na aura masa yata ba kuma bai isa ya dawo min da ita haka ba, zan tafi da ya'ta kuma ya zama Wajibi ya janye kalamansa a kanta,Domin shima yasan hakan bazai taba yuyu ba ni ba sakaran Uba ba ne kan ya'yana sai nayi shari'a dakai wlh." Abun mamaki Yaya Ishaq sai gashi ya kasa mgana Har da mama,Anty Binta ne ke bada Hakuri yace sai Ishaq ya janye kalamansa,Mama ta kallesa tana fadin"Kana ji ana mgana kana banza da mutane shashasha kawai" Ransa bace yace"Na janye kalamai na" Da sauri Mama tace"Ya janye Alhaji don Allah kayi hakuri Zainab kema ki yi hakuri don Allah" Bai ko saurare su ba ya kalli yarsa yana fadin"Ina fadil.? Sai ta juya tana neman Badariya ita ko daman tana dakin Mama tana ji ta fito da Sauri yako karbesa ko kunya yaja hannunsa yarsa ya dago yana kallon su Mama da suka yi Tsumu tsumu,Lokaci daya yana fadin"Zan tafi da y'ata zata kuma zauna ta jiraka.Hajiya ki gayamsaa duk bayan Sati biyu zai rika zuwa yana ganin matarsa da yarsa in kuma yaki jin mganata wlh tallahi zan saka Hukuma aciki saboda tun farko yasan Da Tsarin ya amince da haka sai yanzu zai sauya mganaa..?ina ruwan aikin Zainab da rashin aikinsa..?da zai wuce a kanta..?to zan kai kararsa bai isa ya tozartamin ya' ya zauna lafiya ba.in kuma bai ji mgana ba zan nuna masa waye lawal bako dan mutanen Adamawa" Daga haka yaja hannun yarsa ita kuma ta dauki Jakarta suka fice Daga gidan,Sai aka rasa tsakanin Mama da Anty Binta ko Yaya Ishaq wanda zai motsa ni ko Allah ya kyauta nace araina na cigaba da duba dahuwar zobo na,Mama da ranta ya gama baci da Ishaq ta kallesa tana fadin"Ka kyauta ga abunda taurin kanka ya jawo ma ka nan, kaje in ya cire hannunsa a kanka sai ka duka ka Dauka." Anty Binta tayi tsaki kafin tace"To me ma ya kawo mganar ta ijiye aikinta ta dawo nan ta zauna..?in ta Dawo kana da wajen da zaka ijiyeta ne..? Sakarci kawai achan ya baku gida ya Dauki dawainiyar su Farhan da komai nasu ammh baka gode ba sai ka Tsiro da wata mgana Saboda kada a zauna lafiya.? Idanuwansa jajir ya dago yana fadin"Don Allah ya isa.Ya isa nace.." Mama ta saki baki tana kallonsa Anty Binta tace"To dake ni don na fada maka gaskiya Ishaq dake ni nace" Gefe ya koma yana numfarfashi Kafin yace"Bazan dake ki ba ammh bazan fasa fad'a muku wannan ba gaskiya muka taka ba.Ta yaya wannan abun zai yuyu Mama duk bayan fa Sati Biyu ina naga kudin motar..? Bude bakin Mama sai cewa tayi"Ba ga matarka nan na sana'a ba. tana da kudi sai ta rika baka Lokacin da kake da shi taci gajiyanka yanzu sai ta rama ma kura aniyarta" Ina duke ne sai da na dago ina kallon mama tako zabgmin harara tana fadin"Munafuka ta saka shegen kurman kunnuwanta tana ji tana Dariya" Sai na maida kaina kasa na cigaba da aikin Gabana shiko a fusace yace"Sai kawai saboda ina jani talau saboda zuwa na ganta sai na rika karban kudin mota wajen fa'iza wannan wani irin mutuwar zuciya ce?Haba Mama ki ma bar wannan mganar bazai yuyu ba wlh na jawo ma kaina bansan haka abun yake ba" Yafada cikin kosawa Mama tace"Da auran Zainab din ka jawo ma kanka..?kada ka manta sun maka komai..? A fusace ya katse Mama da fadin"Basu min komai ba Mama don Allah ki Daina fad'in haka me suka min.?da girma na ya ganni aikina Bashi ya nemamin ba,Auran yarsa da nayi nawa ya yafe min komai sai nayi Mama Dawainiyarta da yake mgana yaushe ya farayi..?ko da take aiki duk watan duniya 100+ nake tura mata nata da na Hidiman yara in adalci zan yi kudin zasu isheni..?nawa nake turo miki ke da Fa'iza da Dawaniyar yara sai kuma don yanzu Kaddara ta hau ni sai afini nuna iko Kan matata da ya'yana wannan wani irin kaddararran aure ne..? Ya karishe fad'a kirjinsa na Dagawa alamun bacin rai ganin ya birkice yasa Mama ta fara lallabasa tana fadin"Taho mu shiga ciki" Kin shiga yayi ya cigaba da fadin"Meyasa kuna ganin gaskiya bazaku bi bayanta ba.?In adalci zai yi bazai min uzuri ba..?ko bai san bani da aiki ba ne yanzu zaune nake nima lalurorina Dauke min su ake yi bai taba Duba Lokacin da nake wata biyu har uku a Abuja ya taba  ko sau d'aya ya yi min fad'a cewa na rika zuwa gida akai akai ina da wata matar da ya'ya..?bai taba ba yana jin dadin haka sai yanzu don kaddara ta fad'amin na rasa aikina sai yace Dole duk bayan sati biyu sai naje na Duba yarsa..?bazan iya ba Mama wlh bazan iya ba gwara na zauna anan ko banza ina ganin gilmawar ya'yana da mahaifiyata tare da Matata,achan kuwa ban ma ganta ba yaran kuma basa yini a gidan ni kad'ai kamar maye ina musu gadin gida.wlh ban taba jin abunda nake ma Fa'iza Laifi ba ne sai yau kuma na Tabbata Hakkinta ne ya fara Bibiyata, na Danne mata tarin hakkokinta daya rataya a wuyana, ko da sau daya ban taba duba hakan ba nasani akwai hakkinta dake Bibiyata na sani har da Hakkin Fa'iza Mama" Ya karishe fad'a kamar zai yi kuka ban taba ganinsa cikin rauni haka ba inaji ajikina kallona yake yi ni kuma sai naki Dagowa sai ma na mike na Sauke tukunyar zobon na shige Daki Hawaye suna cika kwarmin idona. Rana ta farko da Yaya Ishaq ya taba Furta ya zalunceni ashe yana sane da abunda yake aikatawa..? Maganganun sa ya sanyaya ma su Mama jiki shi dai ina ji ya shuru takalmansa ya fice daga gidan, su mama kuma suka shige Daki jiki ba kwari. Ranar gidan haka ya yini ba walwala nice ma na dinga zirga zirgan girki da Hada zobo har na gama abincin na zuba ma su mama na sakamai na kai Dakinsa bai shigo ba,yara suka Dawo makaranta kusan Lokaci da'ya suka shigo da Hafsah daman aiki aka basu taje kaiwa sai kuma na fara Damuwa da rashinsa suna ta tambayan ina Daada sun leka baya dakin mama haka ma baya Dakinsa sai nace musu ya fita. Wasa wasa Yaya Ishaq bai shigo gidan nan ba sai Dare,kafafunsa Futufutu daga gani tafiyar kasa ya sha abunda yasa ya warware da ya dawo Jamal ya iske ya dawo shiyasa ya saki ransa. Ruwan wanka ma Amir ya aiko yace wai Daada yace don Allah Umma ki saka mai ruwan wanka. Sai ya bani Tausayi na tashi na saka mai na kai mai har Tiolet din dakinsa na aika Amir ya kirasa,sai da na baro  ya shiga wankan nazo na gyara Dakin da Matarsa ta gama bata sa ammh bata gyara ba,araina in naji kamar tausayinsa zai yi min tasiri a raina,sai nayi Saurin na kauce ma haka sai wata zuciyar tace saboda su Amir bazan bar Babansu a wulakance ba. Koda ya fito dakin Tsab ya ganshi  ga abincinsa a gefe,sai ya zauna gefen katifarsa yana fadin"Anya ban yi wauta ba..? Ko dai dai bakin Baba ne ya fara kamani..?. Ya tuna Baba yasha fad'amai ya rike Fa'iza Amana in ya wulakantata bai yafe masa ba,sannan yana tausayamasa ranar dazai san amfaninta lokacin kuma tayi masa nisa..' Tuna haka yasa yaji hankalinsa ya tashi bayan fitansa bai san ina ya nufa ba shi dai yasan yayi ta gagari a gari inda yaga masallaci ya tsaya yayi salla yasha a ruwa karon farko da ya tsaya ya fara Tunanin kuskuran da ya tafka a rayuwarsa tun farkon auransa da Fa'iza har zuwa yau..?sai a yau yake jin tabbas zai iya yuyuwa girman hakkin Fa'iza ko Bakin Baba ne sune suka yi Zaren Dabaibayi suka fara taba Rayuwarsa. lalle ko in hakane ya zama Dole ya fara gyara mu'alamansa da Fa'iza ya roketa ta yafe masa kila Furucin Baba zai sake sa. Yana cin abinci hawaye sun cika kwarmin idanuwansa Ya tuna burinsa na auran Zainab da ra'ayinsa sai gashi Burinsa bai masa komai ba, yau ta kawo Fa'izan da ya raina ya hantara ya wukalanta itace komai nasa ta dauki laluransa har da ta kannensa da ta mama daman Laluran ya'yansa tun yana da aikinsa ya bar ma Fa'iza ragamar komai kaicon sa" Cokalin hannunsa ya sauke abincin kamar yana cin mgani kansa ya Dafe dake juyamin cikin Fitan Hayyaci yace"Innalillahi yanzu ya zan yi..?ta wata Hanya zan gyara kuskurena..?duk da tarin laifukana a wajen Fa'iza zata iya duba na ta yafe min..? Tuna haka yasa yaji hawaye masu duni sun zubo masa yayi wauta rud'in duniya da Irin Tarbiyan Mama sun kai shi sun rabo duniya da mutanen cikinta sun saka ya hau keken bera ta kaisa tsakiyar kasuwar nadama ta gungurar da shi me Fa'iza tayi masa da ta chanchanci Tozarcin da ya shafe shekaru yana yi mata..? Da wani ido zai kalleta sannan da wani yare ko harshe zai fara bata Hakuri ta sauraresa..?Anya Lokaci bai kure masa ba kuwa..? *12/07/2023* *8:00pm* *Janafty* *KNKB2007* *Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 0552179550,ban da tsarin kati wannan karon, a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488* Gabad'aya sai yaji abincin da yake ci ya koma masa mad'aci sai ya ture komai kawai ya koma ya kwanta rigingine,idanuwansa na kallon rufin dakin Lokaci d'aya rabin jikinsa da kafafunsa suna kasa ne daga kasan katifar. tunani ya farayi tunda ga zaman Fa'iza a gidansu har zuwa Had'a auran su da Baba ya yi shi da Hajiyar Karofi abubuwan da suka faru,Zaman auren su da Fa'iza yadda ya tafiyar da ita da kyara hattara tozarci da cin mutumci,sai ya koma yana tambayan kansa me ye illah Fa'iza da ya tsaneta..?ko miye laifinta da yaki karb'anta a matsayin matarsa meyasa bai darajata ya karb'eta ya daidaita sahun ta da matan maza nagari masu takwallali da sanin ya kamata ba.?Sai yaga bata da wani laifi Fa'iza mai Hakuri ce Fa'iza mai biyayya ce Fa'iza mace tagari ce, burin kowani Namijin kwarai zamowarta baka ko mara kyan fuska wani abu ne na bangaran Halitta in da ya jata ajiki ya sota ya tattaleta ya tattali lafiyanta da jikinta sai Fa'iza ta Daukemin Tunanin kowata mace duniya. sai bai yi ba yayi fatali da Umarnin Allah ya toshe kunnensa da furucin Baba a kansa ya zauna da Fa'iza cikin Takura iko,Umarni da Bauta cikin Tozarci da cin mutumci har da wulakanci ya tuna yadda yake barinta da wahala kan cikinsa da kuma ya'yan da shine Silan fitowarsu duniya. Ya tuna yadda ya kwallafa rai wajen ganin ya samu cikar Burinsa na auran mace mai kyau da gata da ilimi da nasaba, bai taba rokan zabin Allah ba shi dai kawai ya auri mace mai wadanan abubuwan sai Kuma ya basa,Domin ya jarraba imaninsa ya kuma sa ta haifa masa ya'ya daidai da Zabinsa sai kuma ya nuna masa ikonsa tunda ya auri zainab ba ga wani abu na armashi a auran shi da ita ba,sai dai eh! ya cika burinsa na auran mace mai kyau da nasaba ammh ba mutumci aciki ba ganin Darajan juna kamar yadda yake ganin yayi ma Fa'iza alfarma haka Zainab da Ahalinta suke ganin sun masa alfarma ya tuna yadda yake yi ma Fa'iza iko akan komai hatta akan ya'yan data Haifa ya tuna ya rabata da Danginta da yan'uwanta duk bata taba dagaa kai ba ,ya mu'amalanci yan'uwanta ta mummunan siga ba ta taba d'aga kanta ba,sai ya tuna Zainab gabadaya rayuwar auran su Mahaifinta ke jan ragamar shi sai abunda yace da shi Zainab take amfani in kuma yace a'a shi din banza bazata taba yin wani abu batare da cewar mahaifinta ba ko sanin ba,kan ya'yansa ma iko yake nuna mai babu shakuwa ta uba da ya'yansa tsakaninsa da su Fadil suna gidan iyayanta sai an ga dama ake kawosu ya gansu ko da yana garin in yayi mgana sai Zainab tace Daddy yace wajen sa zasu zauna gidan ba kowa Zuzu bata nan,A komai shi ke da ta cewa shi ya zama Hoto,yana Tuna sanda yake da kudi Fa'iza bata dora komai daga samunsa ba,ammh yau gashi ya rasa komai na shi biyar ma sha'awa take basa ta zauna da shi ahaka tana kuma Dauke da Laluransa ita wacce yake ganin ta fita ta kuma yi daidai da shi ta gujesa saboda bai dashi,bazata iya baro aikinta tazo ta zauna da shi ba sai dai shi ya bita,ta nuna mai daman ba sonsa take yi ba. Ta aure sa ne saboda kyansa da wani kyalkyalin duniya kamar yadda shima ya gina nasa auran ashe ba'ayi ma Allah Wayau..? Ishaq yana da taurin zuciyar da ko abu ya damesa ba dai kaga kukan sa ba.ko mutuwa akayi sai dai yayi kukansa a boye ammh sai ga shi kwance Hawaye suna sauka ta gefen kunnuwansa duka biyu,suna jika zanin gadon dake jikin katifarsa zuciyarsa ta yi wani irin nauyi kamar ana yi mai wahayi haka abubuwan daya aikata suka rika dawomai Daki daki acikin kasan ransa fad'i yake yi"Allah na tuba. Allah na tuba ka yafemin" Kansa yake girgizawa yana ji a ransa in ma Fa'iza bata yafe masa ba, bazai ga laifinta ba ammh baya raba d'ayan Biyu duk bala'in dake bibiyansa akwai Hakkinta,ya tuna sanda ya wulakan ta Mariya da kalaman data furta masa alokacin, ya tuna ta fadamai ko ba Hakkin Fa'iza ba,sai hakkin Zumunci ya tambayesa watarana. Ga shi tun ba'aje ko'ina ba ya fara gani rana tsaka aka samu saka Hannun Fidda makudan kudad'e bai san hawa ba bai san sauka ba,ya shiga matsala karshe bayan ya rasa aikinsa sai da ya rasa duk abunda ya mallaka Allah ya barsa da ransa ne saboda ya gane kuskusransa in da yaso gidan yari za'a kaisa ya kare rayuwarsa a banza. Sai hankalinsa ya dawo jikinsa ya tuna ko abokansa yanzu da suka san ba shi da aiki sun gujesa tunda bai da shi bazai iya ma kansa komai ba ballatana su.hatta abokan aikinsa nachan Abuja bamai kiransa sun ma fara mantawa da shi, daman haka Duniya ta gada in yau mune to gobe fa wasun mu ne. Bai taba daukan furucin Baba a matsayin wani bakar sarka mai wuyar warwaruwa a garesa ba,ya dauka tunda bai saki Fa'iza ba ya fita daga Furucin sa abunda bai sani ba Shi Furucin iyaye kan ya'yan su yana tasiri har mutuwar su Baba ya bashi Amanar Fa'iza sannan ya kakkausa mgana kan in ya wulakantata bai yafe masa ba shi ko adadin sau nawa ya wulakanta Fa'iza bazai iya sani ba..? Zumbur ya mike kamar an tsikare shi da ya Tuna da shirmen da ya tafka na Jingine auran sa da Fa'iza tun kafin ya auri Zainab bazai manta ba tun a wannan Lokaci wani abu na auratayya bai kara shiga tsakanin su ba,Shekaru Biyar kenan Innalillahi ina zai kai girman hakkin Fa'iza daya Dauka..?bai taba Tunanin ita ma Mutum bace mai lafiya..?bai taba Tunanin zata shiga masifa da bala'i saboda jinginarsa ba..? Ya tuna Zainab macece mai yawan bukata har tama fisa shi wani lokacin,yana da Hakuri wani Lokaci ammh ita bata da Hakuri ta wannan Fanni shiyasa bazata yarda ya yi wata D'aya bai je ya ganta ba. Mahaifinta yasan zata cutu shiyasa ya Tsaya mata Ita Fa'iza wa take da shi da zata kai masa kukan ta ya tsaya mata..? Sai kamar ana gayamasa da kansa yace"Allah.." Shi ya tsaya mata" Hannayensa duka biyu ya saka ya Tallafe fuskarsa yana jin kamar ya fashe da kuka,Sai dai duk abunda ya faru da gudummuwar Mama yasan ita din uwa ce garesa da bai da kamarta ammh ta bada gudummuwa wajen kara karkatar da Rayuwarsa zuwa hawa kan keken bera in da tana ankar da shi ko in yayi ba daidai ba ta yi masa Fad'a da bai kai haka Lalacewa ba.Sai ya tuna Baba lokacin yana gabda rasuwa yake mai fad'an ya zama adali sannan magidanci mai kyautata ma iyalansa,Kada ya biye ma Mahaifiyarsa wajen kuntata ma Fa'iza kada ya manta marainiya ce bata da kowa kada ya wulakantata domin mace ce tagari ce in ya rasata ba lalle ya samu mace kamarta ba. Kamar karamin yaro haka ya dinga rera kuka yana fadin"Ka yafe min Baba..Ka yafe min Baba na Tafka kuskure ka yafe min" Shi kad'ai haka ya dinga sambatu  Daran nan barcin sa rabi da Rabi ne da asuba Dakyar ya iya tashi fuska da Idanuwansa sun kumbura saboda Damuwa da suka dawo masallaci sai da Jamal ya tambayesa ko zazzabin ne.? yace ya warware saboda Mama ta sanar da shi lokacin da yayi rashin lafiya. Daki ya sake komawa ya kwanta yana Sake saken yadda zai fara gyara mu'amalan sa da Fa'iza sai dai ba shi da wannan kwarin gwiwa yana tunanin bama ita ba ko waye yaji abunda ya faru zai yi tunanin Saboda yanzu ba shi da shi ne yaga amfani Fa'iza ammh har ga Allah daga daran jiya zuwa wayewar gari zuciyarsa ta cika da Fa'iza sunanta alherinta,Sanyin ta,Ladabinta da Hakurinta kaunar ta Kunyar ta,had'e da nauyinta sun hade masa waje d'aya sun ki barinsa yayi wani sukuni tunda ya dawo masallaci bai bari sun hadu ba ya shigo Daki,Wajen Mama kadai ya leka suka gaisa. Gani yayi har bakwai ta gota kuma yaji hayaniyar yara afalo suna ta shirin Tafiya Makaranta,Sai ya mike Dakyar yana rawan jiki ya kwashi kular abincin jiya da ta kawo mai da Kofin ruwa,ya fito falo ya iskeni ina Ta fama da Musty wajen saka masa Rigar makaranta Hafsah  Lahadi ne tana gida ita ke Kitchen ta na yi musu abun kari Amir ya shirya tuni shi yake taimaka wajen shirya Ahmad Anum kuma ta shiga Daki neman Hijabinta bata gani ba ,Dagani har yaran Hankalin mu yayi gaba bamu san fitowarsa ba sai da Anum ta fito daga Dakin su tana ganinsa ta bude murya tana fadin"Daada ina kwana" Muryanta yasa duk muka Dago muna kallonsa Amir ma ya saki Ahmad yana gaida shi ya amsa yana ta sakin fuska kamar an saka shi Dole sau daya na kallesa na kauda kai na,Musty na saki ina fadin"kullum kai ne rigimamme ko Ahmad ya daina rigima ammh kai babban kwabo baka daina ba" Ina shirin nace Amir ya karbi kayan hannunsa sai naga yaje ya karba ya wuce kitchen shi kuma ya kariso falon yana fadin"Musty na ne Umma ke ce ma Babban kwabo..? Ya fada yana daukan sa,Ahmad na ganin haka shima ya fara zillo sai ya koma ya zauna yana fadin"To karfin Daada kuma ya kare" Duka suka hayesa ya dauke su yana Nishi suna Dariya ni kuma sai na Duka ina kwashe kayan da suka cire ina shirin gaishe shi Saboda na Dauka zan gansa cikin wani yanayi sai naga ya ware kamar jiya baya cikin Damuwa ba zato kawai naji muryansa yana fadin"Ina kwana Fa'iza.." Dankari makari mamaki ya cikani sai naji kamar ban ji daidai ba,na juyo ina kallonsa kai tsaye ya sake fadin"mun tashi lafiya ya kwanan yara..? Yadda ya kafeni da ido ne yasa bakina na rawa nace"la.lafiya ina kwana" Da Sauri na wuce dakin yaran har ina cin Tuntube wajen waigensu to Allah na Tuba abun ne naji sa wani bambaramkwai namiji da suna Hajara ban gama mamaki ba sai da naga Hafsah ta zubo musu taliyar data dafa musu ya zauna kasa a cikin su yana bama Ahmad da Musty a baki in Anum ta bude sai ya saka mata Amir kuma sai yace"Daada kai ma bude baki na baka" Sai ko ya bude baki ya basa,mamaki ya sandar dani wani abu ne da ban taba gani ba ko a baya,zai dai dauke su yayi musu wasa ammh wahalar su kan bai sani ai abun mamaki na gaba sai da suka gama,Shi ya tarkata su yace zai kai su har makaranta,Saboda Halin Rayuwa yaran ma sun koyi hakuri ba kullum suke tafiya da abinci ba watarana ruwa ne sai ranar da na samu ciniki sosai har da Lemu ina siyan musu, yau ma nayi niyya ganin shi zai kai su sai na bashi naira Dubu nace ya siya ma kowannen su Lemu da biskit. Bai yi min gaddama ba ya karba yana fadin"Ni kar na siya ma kaina Umma? Sabon salon nasa ne ya girmeni sai na wuce kitchen ina fadin"Kaima ka siya" To fadan da yafi karfinka ai sai ka maida shi wasa,ina cin abinci ya shigo nayi mai sannu da zuwa na bude baki na ce abincin nasa na Dakinsa sai kawai naga ya tankwashe kafa a gabana ya zauna ya tsoma min hannu acikin Farantin da muke ciki ni da Hafsah ta tashi taje ta Dauko mana Ruwa ne. Baki na saki hade da Hanci ina kallonsa shiko ko ajikinsa Hankalinsa kwance ya fara ci a baya nasan Halin Fafansa,Ko abinci ban taba gani yaci da Hannu ba, sai da cokali ammh yau da Hannu yake ci har yana sude hannu,ganin haka yasa na tsame hannuna zan yi mgana yayi saurin tare ni da fadin"ki ci mana Fa'iza. ko baki son ci da ni ne.? Kai na girgiza ina fadin"Aa tare da Hafsah muke ci" Kafin yayi mgana ta fito Dauke da Ruwa itama ina gani ta saki baki taga bakon abu,yana ganinta ya Dago yana fadin"kin ji Hafsah jeki zubo naki kici ki barni na samu Ladan cin abinci da Matata yau" Kalmar Matata din ne na rika nanatawa kaina ya yi wani dum sai ya kasa Dauka duk da yaso na sake naci abinci da shi,sai na kasa saboda abu ne da ban saba gani ba. Kai ranar naga abu ni Fa'iza Shigowar Jamal ya ceceni suka zauna afalo suna Hira ammh Fita goma shiga goma in na dago idonsa na kaina mamakinssa ya cikani kamar wamda yayi gamo..? Ashe wasa farin girki tundaga ranar Yaya Ishaq ya sauya daga Ishaq din da na sani ya koma wani mai sanyi mai kula mai tallali,yanzu ya daina zama in dai yana gidan komai zan yi sai ya taimakamin yara ko da nayi musu wanka shi zai shirya su ya basu abinci ya kuma kai su makaranta,Ko gyaran Daki nake yi sai yazo ya amsa ko ya fara tayani tun yana bani mamaki har yazo ya daina bani. Sai wani kafa kafa yake yi dani wanda sam wannan Sabon dabi'an nashi bai burgeni ba domin nafi sabawa da wanchan Ishaq din,Ranar kwana Biyu Tsakani na fito da wankin yara kawai shima ya fito yace zai tayani jikina ya fara rawa kada Mama ta fito ta gan shi na shiga uku.na fara Hada sa da Allah ya bari yace bazai bari ba, sai kawai na sakin masa wankin na koma gefe ina kallon sa. Ganin haka yasa sai jikinsa yayi sanyi ya ciro hannuwansa a ruwa yazo kusa dani yana fadin"To na bari shikenan..? Ajitar rai na sauke ina fadin"Kana so ka jamin fad'an Mama ne in ta fito ta ganka kana wanki..? Na fada cikin fargaba har ga Allah yanzu ina gudun abunda zai sa a tozartani. Sai kawai ya koma ta bayana bakinsa gabda kunnena yana fadin"Ina ruwan Mama don ishaq ya taya Fa'iza wankin kayan ya'yan su" Jikina ya fara rawa nayi gefe ina Haki,sai ya bini da Dariya kafin ya shige Daki ya juyo yana fadin"Yau ba zobo ne da kunin aya kuma..? Ina zama kan kujeran tsugunno nace"akwai sai na gama zan Dafa kunin Aya kuma sai Hafsah ta Dawo" Ni dai har na gama wankin nan Ina auna wasu abubuwan a fili na furta"kamar wanda akayi ma wahayi'" Jamal Sati daya yayi mana ya koma makaranta, ni na basa kudin mota,da na kashewa Anty Binta ta hadamai yan kayan abinci,Ya tattara ya koma makaranta yanzu kam ina samun ciniki sosai,Har ta Badariya ni nake bata na mota da na laluran makaranta,Da dawaniyarmu na yau da kullum ba domin sana'ar na ba da Tuni asirin mu ya tonu. Yanzu in ina aikin Zobo haka Yaya Ishaq zai fito yace sai ya tayani ko nace ya bari bazai bari ba.sai na basa wani aikin zai kyaleni,sannan yanzu ya samu wata banzar Dabi'a ya rika shigemin yana so mu rika hada jiki da juna to banzan dabi'a mana yaushe jikina ya zama abun sha'awa a wajen sa da zai zo ya na rab'ata,da na ga haka sai na rika kauce masa ammh sai naga kamar bai Damu ba sai ya nuna kamar bai gane ba,yanzu ko Hafsah bata nan yana tayani zuba zobon a gorina ko ya wanke min Aya Mama dai bata taba gani ba sai ranar aiko tayi ta fad'a daga karshe ta fashe da kuka tana fadin"Shikenan Fa'iza kin asircemin D'a ya zama bawanki.Allah ya isa tsakanina da Dangin Sidi da tamadina sai mun yi shari'a da su ranar gobe kiyama" Raina ya baci saboda ta kira iyayena a Kabarin su sai na kallesa Idanuwana sun ciko da kwallah ina fadin"Kagani ko sai da nace ka bari.nasan Halin Mama ga shi yanzu ka janyo ma iyayena Zagi suna kwance a kabarin su" Ba zato kawai naji ya mike ya rikoni ban tsinci kaina a ko'ina ba,sai akam kirjinsa ya Rumgume ni dukkan mu sai da mukaji wani abu kamar wuta ya jamu Mama daman tana gama fadin mganarta ta shige daki tana cin mutumcina,Tuni naji na gigice na fita Hayyacina,da gaggawa na turesa na fizge jikina ina numfarfashi sai naji abun yazo min kamar daga sama wai Yaya Ishaq ni ya Rumgume..? Hawaye suka zubo bisa kumatuna sai ya miko hamnu zai share min,na matsa baya ina fadin"Me ye haka..? Bai damu ba,sai yayi mirmishi yana fadin"Hawayen da na yi sanadiyar fitar su zan goge miki" Wlh sai mganarsa ta bani dariya,har sai da na dara ganin ina dariya sai shima,ya biyemin yana Dariya ni ko baisan shi nake yi ma Dariya ba Sabon acting din nasa ne naga bai Dace da shi ba. Acikin Satin sai ga Hajiyar Dala tun da muka yi Hijara bata taba zuwa ba har muna neman wattani shida Mama ta jata Daki ana ta Labarai,duk yadda suke da Mama bata kwana ba,Sai yatsina take yi,Ta shiga har Dakina ta gani duka sai wani yamutsan fuska take yi,ishaq na gida ta kallesa tana fadin"Shikenan Ishaq ka dawo zaman gidan aiki dai shuru..? Yana zaune kan kujera yace"Wlh Goggo a cigaba da tayamu da addu'a" Mama na daga gefe ita ta rakota ta tabe baki tana fadin"Ba shiyasa nake masa fad'a bai ji ba,Mahaifin zainab wlh tsab zai sake nema masa aiki ammh ya Tsaya yana shiririta ko da yake an mallakesa ya zama mai Duran zobo da kunin Aya" Hajiyar Dala tace"ke ko ta ga yana gida sai zaman kashe wando mana. Ya koma chan Abuja ya zauna nan din ai kina nan sai kiga in ana ganin idonsa an fi saurin sama masa aiki" Mama tace"Gayamai kila yaji ki" Hajiyar Dala ta wuce tana fadin"Ishaq kayi ma kanka fada dai" Daga haka ta fice Mama tabi bayanta shine naga ya Damu ammh ni ko agefen gyalena guga daman suka tarar ina yi sai na zama kurma na nuna musu kamar ban ji su ba,shine bayan fitar su ya zabga tagumi. Na zata wani abun arzikin Hajiyar Dalan ta kawo maman,ashe kwalin Taliya da macaroni ne sai kudi da ta bata naji tana fada ma D'anta,Tundaga Lokacin sai na daina Bashi Fuska,da ya fito zai karbeni aiki zan yi tuku tuku da rai sai jikinsa yayi sanyi shi da yaransa dai sai son barka ya maida kansa kamar wani kaninsu, ya Lura sun fi shakuwa dani fiye da shi,sai yake neman shima su fara wannan Shakuwar da shi ni baisan adadin Shekarun da na kwashe ina bama ya'yana Lokaci ba ne. Alhamdulillah da duka ni'imarsa gareni Domin kasuwar Turarukaa sun bud'emin Sanadin Turaren da Hajiya ta saka na hada ma Diyar kawarta Laila ta Kaduna,sai mutane suka rika gani suna suna yaba kamshi ina ta samun ciniki ba abunda zan ce ma Hajiya sai godiya ta aikomin da kayan sawa ni da yara na dauka Gogan zai yi fada sai naga har da shi ake duba kayan ana murna,na kirata nayi mata Godiyan kayan da kuma Godiyan Yayan mijin Laila da sanadin laila taga Turaruka na,suka burgeta ta aiko na had'a mata na Dubu hamsin kwallacha da Humra,kuma na samu alheri sosai da ita naji dadi ko da yaushe in nayi sallah sai nayi ma Allah Godiya sannan na gode ma Hajiya tare da wadanda suka yi sanadiyar tsayuwana da kafafuwana. Ishaq ya kafe bazai rika bin Zainab Abuja ba,mama ta kasa tankwasa shi ga shi mahaifin zainab ya kara kiran mama yayi mata gargadi mgana har Yamai sai ga kanin Mama da kanwarta Hure sun zo shi ya yi ta ma Ishaq Fad'a akan meyasa zai bijire ma mganar Mahaifiyarsa Dalilin daya sa ya yarda zai je kenan ammh sai yace bashi da na mota kamar Dole aka Turo mota tundaga Abuja tazo ta Daukesa. Ina Daki ina gyara kayan Dirowa ya shigo da Jaka a hannunsa daman tunda naga zuwan su kawun yamai nasan za'a rina. Kusa dani ya zauna ni kuma sai na zame na sauka kasa bai damu ba yace"Zan tafi Abuja fa'iza" Kai Tsaye yaji nace"Allah ya kiyaye hanya a gaida zainab da yaran" Sai yayi shuru ya kasa mgana ni kuma bana son muna kebewa a daki mu kadai sai na dakatar da abunda nake yi na mike zan fita karaf ya riko Hannuna. Sai naji wani iri na ratsani na juyo da Sauri ina kokarin kwace hannuna sai ga shi ya mike gabda ni yana fadin"Ki kula da gida da yara" Ina kwace Hannuna da ga rikonsa nace"In dai wannan nan ba sai ka bar min Sallahu ba kaima kasan aikina ne" Ina shirin fita ya kira sunana ina Juyowa,har ga Allah bansan ya taso ba sai ji nayi ya sakar min sumba a kumatuna na gefen dama Lokaci d'aya yana fadin"Fa'izan Ishaq ki kulan min da kanki" Har ya fice ina binsa da kallo Gabadaya sai da gabban jikina suka yi sanyi zuciya bata da kashi,sai ga shi na yini ina tuna yanayin da na shiga da ya sumbaceni sai da wata Zuciya ta ankar da ni da fadin"A kul din ki Fa'iza ki tsaya iya matsayin ki" Sai nayi kokari na yakice wannan Tunanin Lokacin Hafsah taje korafi ta kwana Biyu sai ni kadai sai yara suma sun ji ba Dadi da baya nan Anty Hure kuma ta nan tare damu Badariya yanzu tafi zama gidan Anty Binta. Azumi ke gabato mu ina ta kokarin na siya kayan zobo da kunin aya masu yawa tunda nasan in Allah ya Budamin zan samu ciniki sosai a raina na guduri niyar ba Jamal ba Har Yaya Ishaq sai nayi ma kayan sallah ko guda D'ai d'ai ne ya'ya na ko sai na gwangwaje su da ikon Allah. Yaya Ishaq sai da yafi sati uku sannan ya Dawo,Namiji kenanbyana baya son zuwa sai gashi ya shantake har da kiba yayi,Sai da ya dawo yana min dadin bakin cewa mganar neman aikinsa ce ta taso shi shiyasa ya tsaya,ni ko bi ta kansa ban yi ba,tunda ba sabon abu ba ne, Ba laifi wannan karon yazo da kudi har ya siya mana kayan abinci,ya rage rabin kudin makarantan yara daman na biya musu rabi sai ya cikasa. Watan azumin Ramadana yazo,ba laifi albarcin watan alfarma mun samu tallafi Goggo ta aiko mana da Buhun shinkafa da taliya da su garin Danwake garin kuni,taliya yar murji,Ni kuma da abun da nake da shi na shiga kasuwa nayi mana kananun Cefane Mijin Anty Binta ma ya bamu gero da shinkafa da siga,Bamu da matsalan abinci a lokacin sai godiyar Allah, Anty Asiya ta aiko min da yaji da kori da Shadda na Ahmad kala biyu,Ganin mun samu rufin asiri bangaran abinci sai na maida hankali ga sana'ata da azumi na chab'a ciniki sosai Hafsah ke taimakamin tare da yara saboda basa makaranta da azumi. Da kudin ciniki da na tara na azumi. na siyan mana kayan sallah da ni da yara nayi ma Hafsah kala da'ya da ita da Badariya na yi ma Jamal shadda shi da yara sai kuma Yaya Ishaq na siya masa nasa shi kad:ai daga gidan Hajiya aka aiko mana da Naman sa mai yawa ana gobe salla da Sakon kudi dubu Hamsin muyi Hidiman Salla kamar nayi kuka ni da ya'yana mun zama abun son mutane ban tsinke ba sai da Raliya ta kawo kaya masu kyau na mata na Anum in ji Laila Daga kaduna. Sai ga Mama bakinta Gum ba karofi Tunda taga an rufa asiri har da ita ake cin arzikin,Anty Hure ma tana nan a wajen mu tayi azumi har ta zobo da kunin aya suna sha har suyi kyauta dashi, daga karshe ce min tayi zan koya mata,tana so ta siya komai anan in taje chan ta gwada nace mata toh. Ana gobe sallah na ba ma Mama kayan sallarta da Jamal har Anty Hure nayi ma Turmi,Mama ta karba a reni ko saka albarka bata yi ba,Jamal har daki ya biyoni yana godiya Yaya ishaq bayan ya gama ganin nasu Mama da yara bayan ya shiga daki na Dauko nasa na bashi duka an dinka,Hafsah ta ba wani dan ajin su yana dinkin maza ya dinka musu,suna mutumci da mai dinkin ne. Sai kawai Ya rumgumeni yana fadin"Nagode Fa'iza Nagode kwarai. Madallah da Fa"iza..Fa'iza matar Ishaq" Da wayau na zame jikina daman ina so nayi mai mgana kan Zainab Saboda ina jinsu tana ta kiransa baya son daukan wayarta, kan mganar zuwansa da azumi bai je ba Mama kuma tamai mgana bazai saurareta ba. Sai nayi amfani da wannan damar na sako mai mganar shuru yayi yana kallona kafin yace"kina so naje da sallah ne ke kuma fa da ya'yana..? Sai na jinjina kai ina fadin"itama ai matarkace tana da hakki akan ka, sannan itama tana da ya'ya suma kuma suna da hakki a kan ka" Kawai sai ya kuramin ido yana kallona kafin ya kama hannayena duka biyu ya rike lokaci daya yana fadin"Wata irin zuciya Allah ya yi ma Fa'iza..? Sai nayi mirmishi kai tsaye nace"Zuciyar hakuri da Takwali ne" Sai ya girgiza kai yana fadin"Da kuma zuciyar  Diomod wanda samun mai macen aure irinta acikin maza dubu sai mai sa'a Fa'iza" Sunkuyar da kaina nayi ina jin jikina na yam yam! saboda yadda yake murza yan yatsuna,sai kawai naji Tattausan muryansa gabda kunnina yana fadin"Zuciyar Fa'iza me hakuri ce zuciyar Fa'iza mai biyayya ce da yafiya Allah yasa zata iya yafe ma Ishaq gigimemen laifin sa a gareta? Dagowa nayi ina kallonsa muka yi ma juna kir,kallo ne yake min cikin wani yanayi dake kassara zuciyar ko wata lafiyayyar diya macen da aka zaunar da ita, ana yi mata irin wannan kallon da Ishaq Kabir karofi ke bi na dashi" *Janafty* *KNKB2008* *Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 0552179550,ban da tsarin kati wannan karon, a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488* Ba iya kallon dake narkar da zuciya ba,Sai da ya had'a da langon Matso da jikinsa yana gogan jikina lokaci d'aya da Numfashinsa yana sauka a dokin wuyana,sai suka taimaka wajen fitar dani daga Hayyacina har ina shirin manta matsayina?ballatana da naji yadda hannayensa ke kara kaina acikin Hannayena. Ban dawo Hayyacina ba sai naji mganarsa a dokin wuyana gabda da bakina yana fadin"Fa'iza zaki iya yafe ma Ishaq.?zaki iya basa rayuwarki a karo na biyu..? Kamar an dawo dani cikin Hayyacina haka na zabura na mike jikina na rawa,yana shirin riko ni na fizge hannuna na fice daga Dakin da Sauri zuwa Dakina,bai biyo ni ba ina tunanin Saboda ganin yara ne,ni ko gado na na fada ina kokarin daidaita kaina Sai kuma daga baya naga wautata na manta matsayina ne da zai rudeni na saki jiki..? Meyasa sai yanzu yake tunanin yayi min laifi yake neman gafarata..? Ko ya manta nice dai Fa'izan da ya sani yar gargajiya kurma mara ilimi da gata baka mummuna ko ya manta wad'anan nakasun a tare da ni ne..? Sai naji bana son na fita mu kara haduwa,Na shige daki duk hayaniyar yara da buruntun su naki fitowa ina jin su afalo yana ta sha'aninsa da yara da Hafsah sai washegari Ranar idi muka had'u shima gaishe shi kawai nayi sai ya amsa yana wani kafe ni da ido nayi saurin kauce ma kallonsa. Da shi da yaran suka shirya gabadaya har da Jamal,sai a ranar naga ya Dawo da gayunsa sai dai ba kamar da ba,da zasu tafi masallaci muna tsakar gida muna tuwon Shinkafa miyar agushi ni da Hafsah ban sani ba naji ya karkato wajen kunnena yana fadin"Ishaq na jiran wankan sallar Fa'iza domin ya tanadar mata babban Tukwaici" Sai na tsorata garin juyowa saura kad'an na fada tukunyar miya ya saka Hannu ya tareni yana fadin"Ki kula da kada ki yi min asara" Sai na sunkuyar da kai ganin Hafsah na Dariya sai ya bi bayan su jamal yama Fadin"Hafsty ki kular min da matata kada ta fada cikin miya ta ragemin kara'in da na shirya mana da sallar nan" Har ya fice ina kara jinjina mamakinsa,Hafsah ma ta kalleni tana fadin"Naji dadi Yaya fa'iza yaya Ishaq ya sauya kamar ba shi ba" Saboda bana cikin yanayin mgana yasa ko tankata ban yi ba. Ba su jima da fita ba muka gama komai ni na wanke tsarkar gida Hafsah tayi wanke wanke,Ni nace taje tayi wanka na fara gyaran Dakin data gama ta shirya sai tazo ta karbeni itama Goggo ta aiko mata da kayan salla na kala Biyu. Ba domin ya roka ba sai domin daman nayi ra'ayin cin kwalliyata da gumina sai na saka wata karamar super waz din da na siya ta Dubu Goma sha biyu,mai kalan ja da fari dinkin riga da zani ne ammh rigar fited ce ta kama jikina Dam na saka Sabbin Dan kunne da sakarna da abun Hamnu,Ban yi kitso ba sai dai na wanke kaina na tufke Hafsah ce zata min kitso kuma bata samu damar min ba, saboda layin yan lalli taje karofi tayi gabda sallah ta dawo wajena Anum kad'ai tayi ma kitso,ni kuma aiki yayi min yawa ballatana daman ni ba yar kwalliya bace. Ko kafin su dawo na aika ma da Mama nata tuwon da naman salla sannan zobo na musamman nayi saboda gida da sallah,Na kuma shiga da kaina har daki na gaishe su nayi musu barka da sallah Anty Hure ta amsani da fara'a Maama ko sama sama tana kallona tana tabe baki ban damu ba,na fita ko ba soso da sabulu sannan na sauke nauyi. Suna dawowa suma abincin na kasa musu suka ci,shi ko sabon mijin nawa sai kallona yake yi,to sabon mijina mana Tunda komai ya sauya,ashe ban sani ba Hoto ya dinga Daukana sai da naji Anum na fadin"Laa Umma zo ki ganki a wayar Daada" Sai na juya ina kallonsa sai ya basar yana dagamin gira jijjiga kaina nayi a raina ina tambayan kaina wannan chanjin duk na menene..? Duk yadda yaso ya samu kebewa dani naki basa daman hakan,washegarin sallah da kwana Biyu na samu ya tafi Abuja kudin mota ma ni na bashi ya tafi bayan ya jaddamin in ya dawo yana so zamu yi mgana nace Allah ya Dawo da shi lafiya. Ya bamu izinin tafiya yawon sallah Shiyasa ban zauna a gidan ba, muka sha yawo ni da yara da Hafsah har gidan Anty mahma mun je da gidan Hajiya,na leka har anguwan da muka taso mun yi zumumci da makotan arziki su Sa'adatu yini zir mukayi sannan muka dawo ita kuma Mama tana gida ita da ya'yanta su Anty Binta washegari da wuri muka gama girki shinkafa da miya nayi da Salat na saka a babban cooler sai karofi da na shiga gayama Mama chan zamu kwana sai gobe zamu dawo sai ta kalleni tana fadin"To in kin tafi da yunwa kike so ki bar ni kenan..? Zan yi mgana kenan Anty Hure,ta karbeni da fadin"Kyaleta taje baka ga ni ba, zan yi mana girkin" Ba dai a son ran Mama muka tafi karofi ba,Chan ko naga yan'uwana har Yaya Asiya nan tayi sallah ita da iyalanta ga Yaya mariya da sai dai mu hadu a karofi har yau ina jin takaicin wannan abun in na tuna. Kowa ya ganni sai yace na sauya kamar bani ba ni kaina nasan na samu kwanciyar hankali ba kamar baya ba sannan sana'ata ta taimakamin wajen inganta rayuwata mun sha ziyara a karofi ni da yara da su Yaya Asiya mune har gidan kakanin mu Baba ati na gidan muka gaisheta tare da yi mata barka da sallah ko alokacin sai da muka mata mganar dan'uwan Tamadina ko an ji Labarinsa tace har yanzu shuru. Duk aranar mukaje har Cikin garin Dutsemah muka gaishe da abokan zaman Tamadina kuma sun ji dadi sosai suna saka albarka ballatana da Yaya Asiya taje musu da Nama da cincin din da tayi suna saka rika albarka su da megidan da ya'yan su. Daga kwana daya sai ga shi sai da nayi Biyu Shima sai da Goggo ta yi fad'a sannan muka koma,aiko Mama ta cika Fam kamar zata fashe,Sai kananun mganganu take yi wai an barta ita kadai a gida,mamakinta ya kamani wani irin ita kad'ai..?ina jamal ina Badar..?ga Anty Hure ga Anty Binta da iyalanta nasan nan suka yi bidirin su,ammh saboda korafinta a kaina baya karewa sai da ta tofa ni dai ban ma yi lokacin ta ba shi kuma wanda ta saba zaunar da shi tayi din har ya yi lokacin nata baya nan dole ta kama bakinta tayi gum. Muna dawowa na cigaba da sana'ata saboda yan makaranta da masu sari,Ranar da Yaya ishaq ya cika sati da Tafiya da Daddare sai ga zainab ta kirani a waya daman da Maman Fadil na saka akayi mata Saving wayar na Hannun Anum ta kafa mata kahon zuka duk ta saka Hafsah ta cika min waya da game game gwara ma Amir shi karatun Qur'ani yaje aka turo masa saboda Haddansa ammh Anum Sai shiririta ko na hanata Dauka sai tayi dubara ta dauka,Ga shi kamar aljanna ko ni ta fini sanin kan wayar in an gama game ayi ta daukan Hotunan banza duk ta cikamin waya. To ranar ma wayar na hannun su ni kuma ina kitchen ina gyara aya na kunin Ayan gobe saboda Ayan Hafsah bata duba ba,duk akwai datti ajiki sai ya samu gyara. Anum ce ta rugo ta zo ta kawo min wayar tana fadin"Umma..umma ana kiran ki" Karba nayi ina kurama sunan ido,yanzu na kan iya karanta suna naga maman fadil sai na rasa ma wajen Dauka,Anum ya kallah ina fadin"Anum matsa min wajen daukan" Sai ta karba tana dariya Lokaci d'aya tace"Umma ni fa nasan bazaki iya dauka ba tunda naga kina Zare ido" Kanta na mangara ina fadin"Gidan ku Anum" Dariya take yi lokaci daya ta Daga kiran bayan tace"Umma a saka a amsa kuwwa ne? Hararan ta nayi ina fadin"in baki saka ba tare da kunnuwan ki zan ji wayar" Dariya ta kyalkyacemin da shi Anum Ai shakiyace ta maidani kamar kakarta. kab'ar wayar nayi ita kuma sai ta fice tana dariya ashe ta jima da Dauka ni kuma ina amsa jin ba'ayi mgana ba yasa na yi sallama lokaci d'aya ina fadin"Maman Fadil kina jina.? Kawai sai naji muryansa cikin sanyi da zati yana fadin"Ba maman Fadil ba ce,Baban Fadil da Anum ne" Sai nayi kasake ina jinsa da waya a Hannuna nama kasa mgana jin nayi shuru yasa yace"Kin yi shuru Fa'iza..? Dakyar na tattaro yawun bakina sannan na iya samun mganata ta fita gaishesa nayi ya amsa yana fadin"Ya gida ya yara na..?ina fatan komai lafiya..? A gajarce nace komai lafiya,kawai sai yayi kasa da murya yana fadin"Nayi kewarku Fa'iza na kosa na dawo wlh" Kam na kame da waya a hannuna ina kifkifta ido kamar nan ne nake da Raunin ganin ba kunnuwana ba. Har yana kara lankwashe murya wajen fadin"Ko baki yi kewaata ba ne Faa'izaaa!"? Yadda yaja sunan nawa ne sai da Tsikar jikina ta tashi yar abunda na Dade ban ma san yanayin shi ba,Ganin yana neman kwace min yar natsuwata yasa na basar da tambayansa ina fadin"Ya su Zainab da yara..? Kasa kasa yace"Suna lafiya..Gata ma ta shigo ku gaisa" Na dauka fad'e kawai yake yi sai da naji mganarta tana fadin"Honey waye hala..? Kai tsaye naji yace mata"Karbi mana..Fa'iza ce' Sai ta karba da murnanta muka gaisa ta tambayi su Anum nace suna gaisheta cikin yanayin mganarta tace"Na zata tare da su Honey zai taho sallah sai na ganshi shi kad'ai Maman Amir"ina yar dariya nace"Shine bai bukaci yazo da su ba ne,ammh ki bari da Babban sallah. Nima ai ina binki bashi zuwan su Farhan ko..? Da sauri tace"Zasu zo ina so sai na yaye Fadil ne na tattaro miki su gabadaya Fadil ai d'an gidan Umma ne,ko wannan zuwan yana ganin Honey ya fara gauranci yana kiran sunanyensu Anum Umma ko Rad'am a bakinsa" Dariya nayi ina fadin"Ina ruwan Farhan" Cikin mganarta ta cigaba da fadin"Daddy ne ya hana da wannan hutun ma kin gansa,ammh zan kara tuntubansa in ya bari zaki gansu" Kai tsaye nace"Allah yasa ya bari din" Bamu jima muna mgana ba muka yi sallama ina ji tana cewa"Honey ga shi"sai nayi saurin latsan dan jan abun nan alamun kashewa bazan iya da sababbin kalaman da Yaya Ishaq ya koya a kaina ba,Bani da wajen sauke su ballatana su samu muhalli sai ga shi ya kara kira sai na kwalama Amir ya kira yana zuwa na mika masa wayar ina fadin"Baban  ku ne,jeka ku taru da yan'uwanka zai yi mgana da ku" Da Murna ya karb'a suka fita falo ina jinsu suka Dauki wayar suna ta Bidirinsu gajiya yayi ya kashe wayar ko kudin ne kila suka kare, tunda ya Fahimci ni din ne bana bukata jin mganarsa sai ya shafa ma kansa lafiya. Bai dawo ba sai da ya kwashe kwana Goma tsakanin miji da mata daman sai Allah,har ga Allah bana son auran Zainab ya kare saboda haka,ance ba'a son kishiya ammh ni Fa'iza ina kaunar Zainab da zuciya d'aya ta karbeni ta mutumtani fiye da yadda wanda ya ijiyeni ya mutuntani,bawai don tana ma ya'yana Hidima ba a'a ance Halin mutum ka fad'esa bata da wulakanci bata da girman kai,tunda nake da ita bazan ce ta taba min wani abu da ya sosa min raina ba. tana kaunata tana kaunar ya'yana nima shiyasa nake kaunarta da ya'yanta bana fatan kuma auransa ya samu matsalan ina addu'an ya kauda dukkan Fitina ya Dauwamar da su har abadan saboda sun fi dacewa da juna. Zainab ta aiko ma da yara Tsaraban kayan sallar da tayi musu yan kanti harta Amir yan kanti ta siya masa ni kuma sai ta aiko min da Takalmi da Jaka da mayafi,Mama kuma Atamfa da leshi har da kud'i Badariya ma da nata Jamal ma boyel da takalmi shima uban gayya sabbin kaya ya Dawo da su fin kala Biya Mama an samu Duniya sai washe baki take tana jin dadi fadi take yi"Kaga to in da abun arziki yake zaune da digadigansa Ishaq ammh ka zauna kana wani shirme,in da ka zauna wazai biyo ka da wannan kayan arzikin..? Shuru yayi bai mata mgana ba,yasan shi da Zainab akwai kauna da Fahimtar juna matsalan ilmin addininta Ragagge ne batasan miji yafi ubanta iko da ita ba, gani take yi da ita da miji duka suna karkashin ikon Mahaifinta ne shi kuma Daman haka yake so,kada ikon ya'yansa ya tashi Daga Hannunsa har Abada yana son komai ya'yansa zasu yi cewarsa ne da ikonsa,Ko wannan zuwan ya sake zuwa ya basa hakuri sai da ya gama gayamaasa mgana har yana fadin bai kai ba,bai kuma isa ba, kaunar da yake masa ne yasa ya aura masa Zainab ammh shi ai ba sa'an auranta ba ne Daganan yasan Allah ne ya kai shi inda za'a koya masa Rayuwar duniya indai bai santa ba. Mama nata mgana ko jinta bai yi ya fada kogin Tunani sai da Jamal ya tabashi sannan ya dawo Hayyacinsa Mama tace"Ka daina wannan zurfin Tunanin fa" Anty Hure da bata koma ba har Lokacin tace"Kuma hawan jini yafi kama yara yanzu ba". Shi dai shuru yayi bai yi mgana ba Sai da Mama ta tambayesa ya mganar aikinsa sannan yayi ajiyar zuciya yace"Mganar aiki ana ta nema Mama ni ma ban zauna ba in da naji ana neman masu karatu irin nawa ina Tura Cv dina ko za'a dace.." Mama tace"Yanzu shikenan ka rasa wanchan aikin naka.?. Kai tsaye yace"Sai dai fatan samun wani Mama ammh wanchan sai babban Rabo kad'ai ne zai iya dawo min da aikina, shima bayan Hukuma ta wankeni daga wannan zargin" Mama ta jinjina kai kafin tace"bakomai muna gayama Allah ko waye ya yi maka sanadin barin ka aikin ka da ikon Allah shima bazai taba samun kwanciyar hankali ba" Aransa ko sai yace"Ba wani bane Hakkin Fa'iza ne. Allah ne yaso ni ma da Rahma ba sai na mutu ranar lahira na tashi da bari d'aya na jikina na Rinjaya na ba.Subhanallah Allah ya Tsaremu" Sai jikinsa ya dau d'imi ya tuna wa'azin da yaji lokacin dayaje Abuja na wani malami ya na fadin azabobin da Allah ya Tanadar ma mai kuntata ma matarsa da wanda ya kara aure bai kwantanta adalci a tsakanin matansa ba ,sai yaga kamar malamin yasan shi,kamar da shi yake yi wa'azin jin wannan wa'azin ya sa tsoron Allah ya kara kamasa. wannan azumin ya Dawo da kudirin niyar bama Fa'iza hakuri su Fuskanci Sabuwar rayuwa ammh ya kasa kwarjini Fa'iza take yi mai,sannan bata sakar mai fuska, kuma bata yadda su kebe inda ba Mutane kamar bata son ma taji dame yazo ya Lura da ita tana da'ri da'ri da shi. Ni ko ta bangare na bansan yana yi ba, duk da ai ya fad'amin in ya dawo zamu yi mgana ammh sai na rika kauce ma haduwa dagani sai shi ko bana wani abu,in Hafsah na makaranta da yara bana yarda nayi zaman daki ina Tsakar gida ina tsiro aikace aikace sanda Sakon Zainab ya iso da kaina na kirata nayi mata godiyan Dawainiyar tayi yawa sai ta yi dariya kafin tace min"'Haka Honey yace. Ammh sai da yayi korafin ban siya ma Uwargida nata Leshin ba" To na dai ce a bini bashi zan biya in sha Allahu"har muka gama waya ina mamakinsa wai uwargida..?lalle abunda ya baka dariya wata rana shi zai saka kuka gashi ina gani akan Ishaq kabir karofi. Duk neman Hanyar da zai samu kaina yayi bai samu ba,na kauce ma wannan haduwar tamu,kwatsam sai ya Tsiri shigewa dakina ya kwanta saman gadona Hake hake Allah na tuba ko a zamanin baya, baya shigowa Dakina iyakarsa in kira ne ko mgana daga bakin kofa ballatana yanzu da komai ya sauya. Ni ban ma san yana shiga ya kwanta ba,Saboda in yara sun tafi makaranta ni kuma ina waje ina aiki Dakina sai dai in nazo daukan wani abu nakan shigosa,ranar ma Zobo aka zo siya na Dubu d'aya naje neman ledojin da nakan tara acikin dirowa ta, har ga Allah ban gansa ba ina ta duba ledan sai ji nayi kafa daga bayana tana zungurin Bayana na tsorata na juyo a firigice sai kawai naga Namiji kwance a kan gadona ban ko ga fuskarsa ba saboda ya rufe kansa a tsakanin Filo gefe nayi gabana na fadi jikina ba inda baya rawa ammh bakina bai yi ihu ba sai naji nace"Subhanallah waye anan..? Ashe yana ji sai ya Dago kansa yana Dariya ido na zaro ina kallonsa kafin nace"kai ne..? Mikewa zaune yayi yana fadin"To da waye zai shigo miki daki ya kwanta in ba mijin ki ba..? Sai na jinjina kai mamaki ya cikani,Ban ce masa koomai ba na koma na cigaba da neman ledata,Saboda yanzu kuma sha'aninsa nasa yafi karfin Tunanina kawai ban ankaraba sai ji nayi ya chachumeni ta baya ya rumgumeni ya hadani da kirjinsa,tudun kuguna na dukam bayansa Hannayensa Cak ya dadumo kirjina kamar ya samu wani abun har da sauke ajiyar zuciya nan da nan jinin jikina ya daina aiki ya Tsaya cak! sai na rasa ina zani tun ballatana da Bakinsa ke saitin wuyana ya na fesar min da Numfashi ko a lokacin da rabon ya'ya ke giftawa tsakanina dashi bai san wadan'an abubuwan ba. shi dai bar sa ya biya bukatarsa in ya Damesa. Ba domin ya damu da ni ya nawa Bukatan ba.?shiyasa tun a wanchan Lokacin bazan iya dora komai akan bukatawata ba, na dai san ni bakuwa ce a harkan bansan komai ba. Yanzu da yake yi min wad'anan salon sai nake neman rasa hankalina, a yanzu ma Hannayensa suka fara kasa zuwa wajen cikina yaraf na saki hannayena jikina na rawa ban dawo Hayyacina ba sai da ya daga riga ta,ya dafa haannunsa saman marana Fatar Hannunsa ta had'u da nawa lokaci daya muka gwama Numfashi Hmmmm!!!!!" Bai kyaleni ba,sai ma bakinsa da ya kai saman kunnena ya lasa sai da naji ji kamar na shid'e na sake dawowa,Lokaci d'aya da ya yi amfani da wata irin karuwar murya yana fadin"Fa'ii...ki zo ki tayani barciii..'" Lokaci da'ya yana matseni a jikinsa inaji ta baya abu na dukan bayana na rikice iya rikcewa kamar wata gaula,Yana shirin ya kai hannunsa akasan zanina na shammacesa nayi kasa bai zata ba sai ya koma kan gado ya zauna Dabas ni kuma kamar wata yarinya sai na saka gudu na fice Daga Dakin, Allah yasa masu siyan zobon suna tsakar gida da sun sha kallon yadda na fito a razane,Kitchen na shiga ina Sauke numfashi har Lokacin Salon sa da Sautin muryansa basu bar jikina ba sai da na Huta sannan na samu ledan Aya na juye cikin wani Bokiti na zuba musu zobon na fita na mika musu shima ganin na gudu sai bai biyoni ba,Ranar wasan buya na rika yi masa bana son ma mu had'u,Da daddare dukkanmu muna falo shi yake koyama Amir lissafi ni kuma ina Rubuta ma Ahmad Huruful Hija'iya a wani Takarda inda zai ta maimaitawa Saboda ya iya rubutawa da karantawa,Dagowa goma sai naga idonsa kaina Lokaci da'ya yana dagamin gira da na Fahimci haka sai na daina yarda ina dagowa na yi kamar bashi ma afalon da zamu kwanta yayi ta tsiro da sani aiki ni kuma sai na saka ya'yansa daga karshe sai ya kalleni yana fadin"Fa'iza ina jin zafi ina so nayi wanka" Ban kallesa ba nace"Amir tashi kaje famfo ka tarar ma baban ka ruwa in ya cika Hafsah sai ta Dauko" Sai ya bata rai har Amir ya mike sai yace"Kai koma ka zauna. ke na saka in kuma baki yi shikenan" Ina kallon rubutun gabana nace"To Abban Anum baka ga aiki nake yi ma yara ba..? Amir ko sai ya mike yana fadin"Daada bari na cika maka" A chunkushe ya mike yana fadin"yi zaman ka zan yi da kaina" Dariya ta kusa kamani sai na Danne da kansa ya fita ya Debi ruwan yazo ya kai tiolet din Dakinsa, chan kuma ina Murnan na rabu da k'aya sai ga shi ya leko yana fadin"Baki shimfid'a zanin gadon da kika wanke ba ne Fa'iza..?daman yasan nayi wanki jiya kuma har da kayansa na wanke da zannuwan gado saboda bana so na shiga Dakin ya Ritsani ne yasa naki shiga na maida zanin gadon, sai kawai na kalli Amir ina fadin"Yana nan saman Dirowa dauko ka kaje ka shimfid'a masa" Ai ban gama Rufe baki yace"Bar shi bana so' Daga haka ya koma Daki sai da nayi Dariyan data kawomin Amir ya kuramin ido ina Dagowa muka had'a ido sai na Dauke kai ammh yaron nan sai cewa yayi"Umma Daada ne ya saka ki aiki fa..? Sai na ware mai ido ina fadin"Eh Daadan fa sai akayi ya ya..? Sai ya kasa mgana araina nace ji yaro da iyayin tsiya to dai har muka shiga barcin ban kara ganinsa ba ni kadai in tuna yadda ya yi jiya sai naji Dariya tazo min,Washegari da safe da ya fito na gaishe sa a dake ya amsa kayan karyawansa kuwa yana fita rakasu makaranta na shiga na ijiye mai na fito. sai da ya dawo ya iskeni ina karyawa a falo yana ganina sai ko ya zo ya zauna karshe dai tare muka ci ni dai ban sake ba sai da muka gama ne ya kalleni yana fadin"Yanzu abunda kika yi jiya kin kyauta kenan..? Ido na waro kafin nace"Me nayi..? Sai ya yi wani kamar maraya kafin yace"Au baki ma sani ba ko..?jiya nace ki gyaramin shinfid'a kika saka Amir ko..? Sai na dukar da kaina ina fadin"Ai lokacin ina ma yara a karatu ne" Ban dire ba ya tareni da fadin"Ko kina menene in na kira ki na sakaki aiki zaki ijiye kizo ballatana gyaran Shimfidar miji. Kin ga jiya kin kwana mala'iku na fushi da ke" Mamaki ya bani na kallesa sai yace"Eh mana ai kin fini sanin haka tunda Lokacin kina gaban Mama a kwai ki da son zuwa islamiyan nan ta la'asar" Araina sai nace ashe ya sani ganin ya nace da mganar ne yasa nace"To kayi hakuri" Nan da nan yaji dad'i ya washe baki yana fadin"Yauwa ko kefa yar albarkata. Ina fatan in nakara kiran gyaran Shimfid'a baza'ayi min gaddama ba ko?.sai na gyada mai kai saboda ya kyaleni aiko bai barni ba. sai ya rika jana da Hira yana shigemin ni ko ina baya baya labarai har da wad'anda basu Shafeni ba abun mamaki har yana tambayata yaushe zamu je karofi mu gaida su Goggo..? Sai kawai nace ranar da ya shirya sai yace sai weekend saboda yara. Ban ko tsaya mamakin sa ba domin yanzu ya daina bani mamaki in dan yayi wata mganar ko ya yi wani abun. Jamal ya yi shirin komawa makaranta acikin kayan abincin mu na dibar mai Taliya da shinkafa da man girki sai na bashi Dubu goma, biyar yayi pocket money, biyar yayi na mota nace in na samu zan bama yayansa ya Tura masa ya karba yana ta godiya har yana fadin"Allah ya kawo babban Shago Matar bro.' Ina yar dariya na amsa mai da Ameen haka ya tattara ya tafi to yayan bai da ko sisi yana nema nema. itama kanta Maman bata da shi kawayenta duk sun gajeta ba wacce tafi bani mamaki sai Hajiya Barira bata zo ba tun bayan da Yaya Ishaq ya fito Sannan Mama ta shirya taje gidanta bata sameta ba,Kuma bata biyo sahu ba kuma bata Hakura da binsu ba shine da yagaji ya yi mata mgana fadi yake yi"Mama yanzu rayuwar nan ba irin da ba ne. In kana da shi ayi dakai daga Lokacin daka rasa bamai son rabarka ka zame masa wahala Mama.ni kaina alokacin da nake dashi abokai har da na banza kuma ai mun taimaka musu ammh yanzu ko kare bana gani ballatana kira an san bani da shi kowa Tsoron haduwa dani yake yi kada na gayamasa matsalata" Ko nace ya taimakeni" Mama ta gyada kai tana fadin"Uhm nagani,ammh na Dauka ko kowa zai gujeni ban Dauka harda Hajiya barira ba, ta bani mamaki kamar mafa blooking dina tayi fa"Dariya yayi yana fadin"Shi yafi komai sauki Mama bazata yarda ku hadu ba, tasan baki da shi yanzu zaki yi Tunanin samun wani abu daga barayinta, a baya kina da shi kuna nima ina dashi kinga dole ta rab'eki ki kama kanki da kowa kawai ki Rumgumi kaddaranki Mama kina gani ko a yan'uwa sai wanda yaga Allah ne yake tunawa dakai in ka shiga Halin babu, sai kuma wanda ma kake tsammanin zai tsaya maka ranar da baka da shi, sai kiga shine ke baya baya dakai. wanda ka gujema Lokacin da kake da shi shine in ka shiga Halin Rayuwa zai taimake ka" Mama na hawaye tace"Hakane wlh nagani Ishaq" Tana tuna Hajiyar Dala ko wayarta bata son dauka yanzu. Ammh Goggo ko bata zo ba zata aiko da Sakonta tabbas Lokacin da suke da shi basu mu'amalance ta da kyakyawan mu'amala ba,ammh ita bata rike su ba ta Duba zumunci ta kuma bi Umarnin Ubangijinta.. Nan ya fice yana fadin"to haka halin mutanen duniya yake Mama Lokacin da kake da shi ayi da kai, in kuma baka dashi ayi da wanin ka" *Janafty* *KNKB2009* *Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 0552179550,ban da tsarin kati wannan karon, a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488* Haka muka cigaba da lallab'a Rayuwarmu yau fari gobe Tsumma. abunda aka samu aci agode ma Allah ba domin ina samun,masu son Turaruka ba,da tuni jarin Zobo da kunin aya sun Dargane da Hidiman gida na yau da kullum,To riban da nake samu na turarukan,sun fi na su auki. da shi nake had'awa muna rufa ma juna asiri sannan Allah ya sanya ma kasuwancina Nasibi komai na yi sa sai ya kare kuma ana nema,Shi kan shi Yace min ya gaji da zaman gida ba abunda yake yi ranar har ce min ya yi ko zan fara doramai zobon da kunin Aya ne yana zuwa tasha ya zauna min..? Sai da naji kwallar Tausayinsa na kallesa yana bakin kofa zaune duk ya rame ya lallace ba wannan farin ba kyau ba fafa ba,kwanbo rayuwa kenaan. A lokacin ban ce mai komai ba sai da ya karamin mgana sannan nace mai"Ko fita da shi baka ga inayi ba, a gida ake siye shi. Kai ma da wata mgana ka ke" Cikin bayyana yanayin dayake ciki yace"Bazaki gane ba ne Fa'iza wlh na gaji ne ko Dako zan je na fara ne..? Na kallesa ina maimaita"Dako..? Sai ya gyad'amin kai yana fadin"Shima sana'a ne kuma akallah zan rika samun wani abun da zan rika taimaka miki da shi" Da sauri nace"Aa ka bari dai mu yi Tunanin wata sana'ar tukunnah" Da haka ya bar mganar tunda muka yi wannan mganar sai ta Dameni sai naga yana da gaskiya shi magidanci ne,zama agida kad'ai ya isa yasa bawa Damuwa na yi ta tunanin sana'ar da zai fara ban samu mafita ba, yanzu fa ko wata sana'a ta kudi ce sai kana da shi,ni kuma d'an jarin nawa kad'an ne Riba kuma agida muke cinye su don ma yan'uwa suna ta tallafawa. Babban sallah tazo tana matsowa bani da matsala tuni na wanke ma yara kayan su na goge ga kuma na wajen Zainab, daman basu saka ba,ni daman bani da matsala in dai ya'yana zasu saka su fita cikin tsara Allah ya gama min komai Mama bata nan ta tafi Yamai da Hure zata koma sai ta bita,tafi wata achan ina jin Yaya Ishaq na fadi'n kila chan zatayi sallah Sai kuma naji gidan ba Dadi ba Mama ko yaya mutum yake  Rahma ne haka ma yaran su yi ta fadin"Daada yaushe Mama zata dawo..?sai yace"Zata dawo in sha Allahu" Ga Hafsah ma sun yi Hutu ta koma korafi tayi ma su Goggo Hutu, Badar kuma tana gidan Anty Binta suna ma Jarabawar Fita ne bayan sallah zasu gama makarantar gabada'ya ita da Raliya tun nesa da kofa tazo ta sameni tace min"Anty Fa'iza zamu gama makaranta akwai kudin riga da zamu yi na graduation din mu, wajen dubu ashirin ake so kowannen mu ya bada kinsan ba ni da shi Mama bata da shi ko da ta na nan Yaya ne kuma kina gani kece komai nasa yanzu,Anty Binta kuma bata ta kaina da na fara mata mganar kudi zata fara masifan itama bata da shi ke kad'ai gareni Anty Fa'iza don Allah ko rabi kika ragemin bakomai nagode".Sai ta bani Tausayi wane ni na manta da Badariya da Sanadinta na samu Rufin asiri, batare da sanin kowa ba na bata Dubu goma nace zan cika mata in na samu shima Dubun goma Sa'adatu ce chan inda muka taso ta samo min wata mata mai son Turare Humra,to da yake ina da Sauran kayan amfani sai nayi mata amfani da shi na samu ba laifi,Sai na koma ina Fafutukar yadda zan sama mata cikon sauran ga shi kuma salla ya matso,Allah ya taimakeni na samu aikin zobo da kunin aya na masu son da yawa da sallah dakyar na had'a mata dubu biyar na kara mata godiya har da kuka ta Rumgumeni tana fadin"Nagode miki Anty Fa'iza yadda kike jin kanmu Allah ya baki wanda zai ji kank'i watarana Allah ya Dauwamar da farinciki da arziki da wadata acikin rayuwarki gabad'aya" Na amsa mata cikin fara'a ina Fadin"ke meye na kuka share hawayen ki ko sai na kira miki Ya'yan ki ne..?jin haka yasa ta goge Hawayenta,ni na hanata nace ko yayanta kada ta fad'amawa ana saura kwana Hudu sallah tazo da murna tana Fad'amin Hajiyar su Raliya ta biya mata kudin sannan ta bata dubu goma tayi dinkuna sai tace zata maidamin da kudina na riga nayi niyya sai na karbi biyar din da na bata Daga baya na barta mata goman nace tana da bukatu tayi amfani da shi,Badariya ta yi murna tayi murna kamar bakinta zai yage addu'a kam na shata ni ko tana da Muhimmancin da bazan manta da alherinta gareni ba. Atamfa taje ta siyo da less sai mayafi da takalmi da jaka,Sai kayan shafa ina D'aga kayan ina fadin"Ehee! kaga yan mata." Tana Dariya tace"To Anty Fa'iza mace sai da kwalliya mazan nan, kuma suma kyale kyalen suka fi so" Na aminta da mganarta yasa nace"Hakane Allah ya kawo miji nagari"ta amsa tana rufe fuska ni kuma ina binta da Dariya sai da Yaya Ishaq yaga kayan ne ya tsareta sai ta fad'amai gaskiya kallo na yayi yana fadin"Lalle kina da d'aure ma karya gindi ke baki bukatar kayan kwalliyan sai ita..? Ina dariya nace"Me Fa'iza zata yi da kayan kwalliya ai wannan sai irin su Badar mata masu kyau da nasaba" Ita Badariya bata gane mganata ba sai ta karb'e da fadin"Kai Anty Fa'iza wlh kwalliya bata zaba bace.Mu mata kowa yasan yan ado ne da kwalliya" Shi kuma da yasan kan mganata sai yayi gum ya koma yana kallona ni ko na basar da shi,Daga ni har shi bamu san Zainab da yara zasu zo mana sallah ba,Mun samu tallafi shinkafa da naman sallah Daga gidan Hajiya Daga Korofi kuma Goggo ta aiko mana da kaji da kayan miya mangyada su maggi da sauran Cefane,an yi idi lafiya an sauko ranar nayi mana  shinkafa da miya sai nayi mana cowslow,Sai zobo da kunin Aya Saboda Sallah Jamal ma ya dawo da da bai da kudin mota, yayan yace ya zauna chan yayi sallah nace hakan bai kamata ba na hada dubu hud'u aka turamai nace ya taho gida yayi sallah cikin yan'uwansa. Ranar idi da yammah sai ga Direba ya kawo zainab da yara,Gida sai ya Rud'e da Murna su Anum nata tsalle da Murna ganin kannensu Farhan na ganina ya Nufeni bakinsa har kunne yana fadin"Umma.." Na daukesa na daga sama yaro kamar balarabe wajen kyau yana bangalamin Dariya nace"Farhan d'an Umma" Tazo da naman sa an soya tare da naman kaza anyi pepe dinsa ga su cake samosa da su sprill role, ta zo da kantan kantan na lemuka da biskit, ta ce min Saboda sallah ko kuma in mun yi baki,Nace mata"Angode. Sai dai gaskiya sai kunin aya da zobo ya kare tukunnah" Tana dariya tace"Ga abun arziki wazai bi ta na kwalayen bature masu shegen zaki" Ishaq basa gidan shi da jamal sai dai suka dawo suka ganta kuma daga alamu uban gayyar yaji dadin ganin matarsa, Dakin mijinta na Sauketa,Yaran kuma suna tare dani Direban daya kawo ta bai koma ba. tace zai tsaya sati d'aya zasu yi zai maida su sai aka sauke sa Dakin Jamal. Sosai wannan sallar tayi mana Dadi,babu abunda yafi kwanciyar Hankali Dadi ni nake hidiman abinci na gida da na yara, Zainab sai da tana tayani da Hiran duniya,Farko da na sauke Zainab a dakinsa samu na yayi yana min mgana wai meyasa sai Dakinsa na sauketa,dakina fa..? Na kallesa ina fadin"Saboda mene?sai mu gamutsu da ni da ita da Anum kamar ba bu wani da'kin..? Kuma nan din ta saba sauka in tazo a Dakin naka shi yasa na sauketa anan" Sai kawai ya juya yana fadin"Ki bude dakin Mama ki sauketa anan mana" Mamaki ya bani Namiji sai a barsa da gulma ya gama wannan borin kunyan, sai ga shi suna kulewa a daki bamai jin su ammh yazo zai min dad'in bakin su na maza. A gida muka cinye sallar mu sai ranar washegarin sallah da kwana uku Zainab ta matsa sai na shirya mun fita. da zamu tafi,na saka atamfata da Hajiyar su Raliya ta dinka min,Zainab tace ban isa ba ta dinka mana Less mai kyau iri d'aya,har dinki daga Abuja aka dinko ta matsamin sai na saka Saboda kada tace ko ban karb'i kyautar nata ba ne,yasa na saka Doguwar riga A shape dinkin ya fita haka ya fitar min da Shape dina in kika ganni a lokacin bazaki taba yarda na haifi Yaro dan shekara sha biyu kamar Amir ba. Ina nan da kuruciyata sai dai kowa yasan Fa'iza yar gargajiya ce,ammh zainab bata barni haka ba,Hijabi na saka tace ban isa ba Dole na Dauko mayafin data aikomin da shi da Takalmi da jakata na saka,sai gani na fito ras dani na yarda da Hausawa da sukace kowa ya gyara ya sani ni kaina sai nake ganin kamar bani ba. Zainab ta kalleni sama da kasa kafin tace"Komai yaji ban da abu d'aya" Ina dariya nace"Ban yi kyau ba ko..? Sai tace"Aa fa.Lalli ne yayi miki cikas" Sai kawai na wuceta ina fadin"Lalle ai naku ne na fararan mata yan gayu" Domin tayi nata Hannu da kafa, abun ka ga farar fatar kamar don ita aka fito da zanen jan kunshi tana bi na a baya muka fito daga daki Lokaci daya tana fadin"Wlh ko ke kika yi ba karamin kyau zai yi miki ba Maman Amir" Ina jinta ban ce mata komai ba, ina jan abu zai fito a wannan bakar fatar tawa ina fitowa yaran na Falo suka dago suna kallon mu sai kawai Anum da Amir suka hada baki wajen fadin"Laa! Umma kin yi kyau wlh.." Musty da Ahmad ma suka karb'a Farhan na jin haka shima yace"Umma jin yi kyau" Fadil na gauranci yace"Chauu.." Gabadaya muka saka Dariya,Ni na sabe Fadil na rike yaran duk sun ci yan kanti mazan kaf iri d'aya Zainab tayi musu Anum kuma an cakare da Doguwar riga da takalmin yan gayu Badariya ta kaita akayi mata jan kunshi da kitso da yake bata dauko suma na ba,tana da gashi an yi kitson gaba yaji bit sai yanga take da farko ma kin saka Hijabi tayi sai da nayi mata jan ido,Zainab ta hana sai ta Dauko mata wani karamin mayafi ta nad'a mata, muka fita daman ta fad'ama megidan zamu fita gari gidan Anty Binta mu gaisheta yace to. Ban kulle dakin ba tunda suna waje da Jamal jakata na Hannun Amir na Zainab na hannun Anum ta kama ta rike in ka ganmu bazaka taba cewa muna cikin wani hali ba,ko mijin mu bai da aiki ba kila in an fad'a maka ma bazaka yarda ba. Suna tsaye suna mgana da Jamal yaran suka fara fitowa ganin su shar da su yasa yafara washe baki Jamal ne yace su  jere a dauki Hoton Tarihi ko da muka fito har Baban duk suna ta Hotuna Zainab ce a gaba sai ni a baya ina rike da Fadil zainab nata min Tsiyan na nad'a mayafi a kaina,nace mata ban iya saka shi a saman kafad'a ba ne. Tunda muka fito idonsa ke kaina kallo kamar zai fad'i,har yana wani bude ido sai ji nayi kawai ya kira sunana"FAA'IZAAA...! na dago ina kallonsa Fadil dake ta mika masa hannu alamun ya Daukesa bai ma gansa ba ya saki baki da hanci yana kallona Ya nuna ni yana fadin"Fa'iza ke ce.? Sai dariya ta kamani nace"Ba Fa'iza ba ce Wannan Uwar Fadil ce" Sai nan ya gano abun da yayi sai ya fara sosa keya Jamal yayi dariya yana fadin"Matar bro ba bro ba,koni ban gane ki ba da farko". Hararansa nayi ina fadin"Uhm ka manta ne" Karaf ko Anum tace"Daada yaga Umma tayi kyau ya saki baki yana kallonta"Zainab ta kwashe da Dariya tana fadin"Yes my Daugther" Sai kunya ta kamani na sadda kaina ya matso ya karbi fadil daga hannuna ammh sai da ya gogi jikina Lokaci daya yana fadin"kin yi kyau,Sannan kamshin yayi dad'i" Sauran Humran da nake hadawa ce in ta ragu sai na ijiye ban ma cika shafawa ba yau ma Zainab ce ta matsamin sai da na shafa,da sauri nayi baya ina yake sai ya basar ganin Zainab kusa dani sai ya kalleta yana fadin"Matan Abuja sun yi kyau" Hararan soyayya tayi masa tana fadin"Ai yanzu ta zama matar katsinawa" Dariya mukayi gabad'aya Fadil ne ya fara kuka yana mika hannu muna juyawa muka ga yara har sun rigamu shigewa mota nayi dariya ina fadin"Dole fadil yayi kuka yaga za'ayi masa kan ta waye" Mikamin shi yayi yana fadin"Sai kun dawo, kada kuyi dare jamal fita zai yi ni kad'ai ne agidan" Zainab ta wuce tana fadin"Honey sai fa mun zaga gari ka ma yi hakuri kawai" Ni dai ban ce komai ba muka shige mota wata bakar Jeep ce kaf ta Daukemu su Anum an kame agaba kamar motar gidan su dariya ma tabani,Gidan Anty Binta muka fara zuwa mun iske har su Anty Mahma,suna gida sun yi mamakin ganin mu dukkanmu a tare sannan cikin shiga mai kyau Anty Binta haka take ta kallona kamar idonta zai fad'o ina gaisheta ta amsa min cikin wani yanayi.Anty mahma ko ihu ta Buga tana fadin"ku zo ku sha kallo wajen Hajiyar Zobo da kunin Aya" Badariya na gidan tace"Kin manta harda Turaran humra da kwallacha" Dariya suka bani Zainab tace"Maman Amir yadda kika san bata haifi Amir ba" Anty mahma tace"Fa'iza nada jiki mai kyau gaskiya" Mun dade agidan kafin mu yi sallama Anty Binta dai sai kallo na take har muka tafi, sun yi mgana da zainab tace yaushe tazo tace shekaran jiya Daga gidanta Badariya ta biyomu muka taho tare da ita,jin nace har gidan hajiya zani mata yawan sallah. Ba gidan Hajiya mukaje ba da muka fita ba,sai da muka fara zuwa anguwan da muka tashi. Allah sarki gidanmu an buge sa ya zama sai Filin gwamnati Sa'adatu da Habiba sun yi murnan ganin mu sosai,na kullo musu nama da lemu da Zainab ta zo mana da shi, duk wanda yayi maka mutumci kada ka manta da shi, gidan Hajiya sai yammah muka je bata gidan sai su Raliya da yayyinta da suka zo sallah, ammh sun kirata a waya nan muka yi sallar mangariba muka ci abinci sai gata ta Dawo tana shigowa su Anum suka nufeta suna oyoyo Hajiya ta tarbesu tana fadin"Oyoyo Ya'yan Hajiya" Zama tayi muka gaisa Zainab ta gaisheta ta amsa sai na gabatar mata da ita sai ta kalleta tana fadin"Maraba da Fa'iza da Zainab naji dadin wannan ziyaran Allah ya hada kawunan ku" muka amsa da Ameen ta karbi Fadil tana fadin"Wannan ne kama da yan sudan di'n fa..? Ina dariya nace"Kanin Farhan ne" Tana dagasa sama tace"Naga kaman su da Amadin ki". Hajiya ba ruwanta tana da sakewa muna ta Hira da ita tun zainab bata saki jiki ba har ta saki yaran kuma tuni su Raliya sun jasa su cikin gida,duk yadda muka so mu tafi kafin isha'i sai da ta hanamu shi ko Babansu sai kira yake yi Zainab nace mai muna Hanya sai da muka yi sallar isha'i muka yi shirin tafiya ta bamu kyautan atamfofi super guda biyu,yaran kuma kudi sabbin yan Hamsin kowannen Bandir d'aya Badariya kuma tace ta dawo ta karb'i nata Sakon har haraban gidan ta rakomu ita da ya'yanta da sai tambayan Hajiya suke itace Fa'iza me Turare da dilka..?.Sai Hajiya tace itane sai kiga wad'anda basu sanni ba suna gaisheni cikin girmamawaa. Sai da muka kamo hanyar gida sannan Zainab tace min"Yar'uwan ku ce Hajiyar nan..? Na girgiza kaina ina fadin"Aa sune shugabannin wata kungiyar taimakon mata da marayu,wad'anda suka koya mana wannan sana'ar da nake yi. sanadin haduwar mu kenan sannan Raliya diyarta kawar Badar ce" Sai ta rausayar da kai tana fadin"Tana da kirki sosai" Na jinjina kai ina ba'a mgana,hirar ta muka rika yi har muka isa gida,Badar na fad'in irin kudin su ya'yan Hajiya manya maza duk ma'aikan gwamnati ne,matan ma suna auran manyan manya a garin katsina,itama aiki take sannan suna da manyan kungiyoyin mata na taimakon mutane" Ko da muka koma Gogan ya cika saura Kiris ya fashe sai hararan mu yake yi,Zainab tace"Honey mun dawo" Yana kwance kan kujera yace"Na ganku,sannan ku da zuwa sai a tube a sama min abunda zan ci" Ina kwantar da Fadil da yayi barci akan kujera nace"Yunwa kake ji.?ina abincin da na bar maka a kula..?. Yana daga kwancen yace"Ban yi ra'ayin ci ba,sabo nake so" Ni da zainab muka kalli juna sai ta zauna wajen kafafunsa tana fadin"Maman Amir barayin ki ne wannan, ni bari naji da lallashi" Ban damu ba,na shige dakina na sauke mayafina da kayan hannuna na shige kitchen. yaran kuma suna ta murna da Budirin kudin da aka basu suna nuna mai ya karb'a yana fadin"Tunda kun zama masu kudi kowa sai ya bani goron sallah" Suka fara Dariya yana taya su bansan ya suka kare da Amaryansa ba, ni dai Shinkafa na sake dafamai sai nayi mai miyar albasa da naman kaza na kawo mai da maltina na iske suna hira da matarsa sai na shige daki nayi wanka na Sauya kaya na gaji ga barci yaran ma da kansu nace suyi shirin kwanciya,Fadil kawai na karb'a mukaje muka kwanta Farhan tare da su Amir zai kwana Anum kuma sai ta gama iyayinta zata shigo ta kwanta. Mun so washegari mu je karofi ya hana,Sai da aka kara kwana sannan muka tafi gabadaya har da shi da Badariya da Jamal,sai dai su Goggo suka ganmu kamar daga sama mamaki da murna ya hana Goggo sakat sai fad'i take"maraba da bakin alheri. ni kadai da zaratan masu gida haka,Allah yasa kun zo da cefanen ku" Amir ya zaro mata kudi yana fadin"Nawa kike bukata Tsohuwa..?. Ta ko warce kudin tana fadin"Duka nake so" Sai ya fara fadin'Ke ko goggo baki san wasa ba" Gabadayanmu sai da muka yi Dariya Yaya Ishaq dai duk yaji kunya,Kansa na kasa yana gaida Goggo ita ko a Fuska bata nuna masa wani abu ba,Su Anty nasara duk suna gida aka gaisa sai fa alokacin wasu suka san Zainab da su Farhan,mune har gidan su Yaya Isa achan muka sallar la'asar daganan muka isa gidan Yaya mariya tayi mamakin ganin mu sai kallo na take yi cikin gatse tace min"To su Fa'iza dai akwai ki da son a sani yawo da kishiya" Allah yasa zainab ta shiga ciki tayi waya,da Yaya mariya tamin baramb'arama a gabanta,ban bata amsa ba ta kara kallona tana fadin"Naga kin yi wani d'anye ne ko dai ciki kika kunso ne..? Dariya na kwashe dashi ina fadin"Ciki? ai mun bar ma masu mazaje a hannu" Dariya ta yi lokaci d'aya ta daki kafad'ata tana fadin"Oh Allah! ji yadda Fa'iza ta koma shekaru biyar bqya, wazai ce Fa'izan nan ce mai shuru shuru da an yi mgana ta hau kuka tana kuyi hakuri" Tafad'a tana kwaikwayon mganata ni dai ina ta Dariya Hafsah na gidan daga barci ma ta taso na kalleta ina fadin"Sannu yar hutu gidan Goggon kenan..?tana sosa ido tace"Yau fa nazo chan hayaniyar yara" Yaya mariya tace"To ai ga hayaniyar nan Fa'iza ta tattaro miki har da gayyar sod'i ba katin gayyata" Sigina na rika yi ma Yaya mariya ammh ta nuna kamar bata gane ba,Allah ya taimakeni da Zainab din ta fito sai ta gyara bakinta sai dai Taki sakin jiki da ita sai ma had'e rai da tayi shiyasa bamu dade ba muka tafi sai ko ta rakomu har gidan Goggo nan suka had'e Da Yaya Ishaq akayi kallon kallo ta Dauke kai abun mamaki ammh shi sai yace"Mariya ba gaisuwa..?to ni bari na gaisheki tunda ta wani fanni ni kaninki ne an yi salla lafiya ne  ? Ba ita ba har su Goggo sai da suka yi mamaki sai dai ba wanda ya nuna hakan,Yaya mariya ko da lafiya ta amsa mai kafin ta Dauke kai, daman taji labarin sa a wajen Hafsah kafin ta tafi sai da tajani gefe tana fadin"Ke naga wannan wawan mijin naki na wani rawan kafa akanki saboda yaga yanzu ba shi da komai, kina sana'a kina yi mai wahala to in kika sakar masa ke kika sani,kada dai ki manta da abubuwan da suka faru a baya wlh kada naji kin sakarmai ki bari sai ya samu aiki yi in har chanjin na gaske ne sai ki gani" Ban ja da nisa ba nace mata toh kawai nasan halinta yanzu ina ta wata mgana sai ajimu daga waje, Kafin mangariba muka tafi,da Tsaraban su gyada da aya,Sannan na taho da ayan na da ganyen zobon da Goggo tace na bada kudi ayo min Sautin su a kauye anfi samun sauki,To shine na ba ma Hafsah da zata zo ta zo mata da kudin, shine na dauko kayana ita dai Hafsah tace sai ta kara kwana biyu zata dawo. Tunda muka dawo bamu sake fita ba muna gida muna warware gajiya,Zainab sati daya tayi ta koma Abuja ni kaina sai da naji kewa ballatana yara da suka saba da kannensu,shi ko Yaya ishaq ranar da ta tafi har ce min yayi yaji dadin tafiyarta kila na sauraresa yanzu kai namiji sai a barsa, nan yake shigewa daki da ita fa yana amfana ammh baazai yarda ba sai ya yi dadin baki. An gama Hutun salla yara sun koma makaranta Mama dai taji dadin yamai bata dawo ba,Hafsat ta dawo saboda makaranta,Badariya kuma na gidan Anty Binta tsakani da sallah ba Dadewa suka yi graduation na gama makaranta,Raliya har walima Hajiya ta shirya mata agida,an yi waliman ko sati ba'ayi ba Hajiya ta aiko min da Kayan saka ranan Raliya,nayi murna sosai Badariya itama tazo tana fadamin har da na Halisa itama an saka,yar wajen Anty Binta zatayi aure a kano dan'uwan mijin Hajiyar Dala ne,ita kuma Raliya chan wajen bikin Laila suka hadu da shi,Yaron yayar wanda Laila ta aura ne. Bansan me ya faru ba sai gani kawai nayi Badariya ta had'o kayanta tazo ta Bude dakin Mama ta share ta dawo,kamar bazan mata mgana ba sai naga tana cikin damuwa ranar bayan fitan yara makaranta na bita har Dakin sai na isketa tana kuka. Na tsorata na zauna gefenta ina tambayanta me akayi mata take kuka..? Sai ta mike zaune tana cemim"Don Allah Anty Fa'iza aure na waye..? Kai tsaye nace"Aure na Allah ne Badar me ya faru ne..? Sai ta sakamin kuka tana fadin"ba na fada miki an saka ranar auran Halisa ba? Na daga mata kai sai ta cigaba da fadin"Shine shine fa tunda ta samu ssurayin nan take min gani gani har Anty Binta tana gani Halisa na min wulakanci don ina zaune a gidan su,Gori kala kala take min wai bani da Tsayayyen saurayi sai shirme shine fa a Shekaranjiya Salisun da zata aura yazo daman ya sanni don yace ta kirani mu gaisa muna gaisawa muna hira sai zuwa tayi ta cemin wai don Allah na fita tana so ta gana da saurayinta nayi kane kane kamar ina so nayi mata sinacin" Ta karishe fada cikin kuka cikin wani yanayi nace"Miye sinacin? Kai tsaye tace"Wai zan kwace mata shi Haba Anty Fa'iza ko Hali na ne ai bazan yi ma Halisa ba,mamanta uwa daya uba d'aya muke da ita ballatana ba Halina ba ne" Sai na rike hannunta ina fadin"To miye na kuka tunda kinsan ba haka ba ne..? Sai ta kalleni tana fadin"Na shiga damuwa ne anty Fa'iza na kai minzali nima kawayena duk da muke tare sun yi aure,ga Raliya itama an saka mata rana,ni kuma gaskiya Halisa ta fada bani da wani Tsayayyan Saurayi, sai ka samu kana murna sai ka nemi mutun ka rasa ga halin da yaya yake ciki akallah dai nima na kauce sai wata Lalurar ta Dauke muku Anty Fa'iza" Sai kawai ta kara saka kuka ni ko na Dage ina ta lallashinta sai da tayi shuru sannan na kalleta ina fadin"Saurareni Badar.shi aure da kike gani na Allah ne,Sannan mutum bai isa yayi ma kansa aure ba. shi kamar zanen kaddara ne irin na mutuwa da haihuwa ne lokacin da Allah yace kun ya fakum ba wanda ya isa ya hana Faruwarsa,kada kice zaki saka damuwa don wance tayi aure wance batayi ba ki dai ki bar ma Allah zabi ki kama kanki ki Tsarkake mu'amalan ki da Allah da Mutane kina Zaune Allah zai kawo miki miji nagari kiyi auranki. kada Surutun mutane ya Dameki ita kuma Halisa ki kyaleta in dai namiji ne ai d'an Babansa ne kina zaman zaman ki sai nuna mata kalan da zata gane tayi kuskure ki kwantar da Hankali Allah na sane da bayinsa masu takawa da Hakuri" Sai da na Tabbatar da mganata ta shigeta kuma ta aminta da mganganu sannan na fito daga Dakin ni kad'ai a Tsakar gida ina aiki Tausayin Badariya ya cikani kowaani bawa da nashi kabulen Rayuwar in kana gida baka yi aure ba, ace kaki aure shi kuma mijin ba Tukunya ba ne balle ka tantance na gari,sai ga shiga gidan wani auran kaji gwara zaman ka agidan ku ma,ammh duk lalacewar aure yana da Daraja saboda Ibada ce ta Ubangiji. Nayi alkawarin a duka Khamsin Salawatul di'na zan saka Badariya aciki,domin Allah ya sama mata mafita alokacin ma sai da na daga Hannayena sama nace"Ya Allah ga Baiwar ka nan Badariya ka fi ni sanin Damuwarta a cikin zuciyarta Allah ka kawo mata mafita daga cikin kyawawan mafitan da kake bawa bayin ka Salihai,Allah ka turo mata miji nagari wanda zai share mata hawayenta" Sannan na shafa a raina ina jin Wani iri,rayuwa kenan kowa da irin tasa kaddaran. *Janafty* *KNKB2010* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000* *09069067488* Har ga Allah na taya Badariya damuwar halin data ke ciki,Saboda ina aiki in abun ya fad'o min a rai sai na tsaya nayi mata addu'a acikin raina ballatana da naga tafi kwana biyu kafin ta warware sai nayi amfani da wannan damar na kara jawota a jiki ina kara nuna mata in dai tayi yakini da Allah ke yi to ta saki ranta mun rokesa kuma shi Allahu Rahimun ne,yana share ma bayinsa hawayensa da haka na samu ta saki jikinta. sai ya kasance in yara sun tafi makaranta Hafsah ta fita zata fito  taimaka min da aikin gida,wani Lokacin har da na sana'ata muna yi muna hira hakan sai ya rika debe mata damuwa. Ba'a fi sati da dawowarta ba ranar sai Yayan nata ya kirata,ina falon lokacin na shigo da bahon da na jera gorunan zobo zan shiga kitchen na jera a frezer ta ma shigo ta tayani ne ya kirata,Kasa kunne ba Halina ba ne ballatana da nake da raunin ji da nasan ko na kasa kunnen ba lalle bukata ta biya ba,sai ban damu da naji abunda yake tambayanta ba, na shige na cigaba da aikin gabana sai ita ne ta shigo bayan ya sallameta tana cemin"Anty Fa'iza kiji Anty Binta" Sai na dago ina fadin"Me ya faru da Anty Bintan..? Cikin yatsina Badariya tace"Wai yaya Ishaq ta kira tana fad'an wai daga mun yi hatsaniya da Halisa ko sani batayi ba na hado kayana na dawo gida"Mirmishi nayi kafin nace"To shi yayan me yace?baki ta tabe bakin tace"Me kuwa.?fad'a ya yi min wai na rika hakuri da rayuwa" Sai na cigaba da aikina ina fadin"Ya fada miki gaskiya. Ke uwa kike ga Halisa bamai sauya wannan sunan a wajenta har abada" Daga haka bata kara mgana ba illah hmm!da tace min ta zo ta kama min muna jera gorunan tare ganin haka nima sai na saki mganar muka kama wata,Yadda shi ma bai min mganar ba haka nima nayi kamar ban sani ba ni nasan ina da miskilanci kuma abun nawa ya had'u ne sanadin mijin da nake aure da irin yadda ya tafiyar dani wajen zamantakewarmu,shiyasa na zama ba komai nake mgana a kai ba.ballanta na nuna na sanin din na koya ma kaina ga duk abunda ba'a ce Fa'iza zo kiji ba, ko zo ki gani ba. na fahimci bawa zai fi zama lafiya in ya bar abunda ba ruwansa hadisi ne guda kan haka. Fargaba na d'aya shekara ta na neman kare mana acikin wannan gidan akwai Karin Dawainiya na kudin Haya,kudin makarantan yara,ga jamal da sai wannan shekaran zai gama ga abinci da Hidimdimun yau da kullum,har takai ga mun fara awon abinci saboda komai namu ya kare sai abunda ba'a rasa ba,da na rasa mafita sai na auno masara aka nika nayi Tsaki da gari yau tuwo gobe fate jibi dambu sannan na kira Goggo nace ta saka ayi min garin Danwake da Taliyan murji ,Hafsah zata zo satin karshe ta taho min da shi ban fito na gayamata muna cikin wani Hali sai dai hikimarsu ta manya yasa sai ta Fahimceni,sai tace ba sai na aiko Hafsah ba,Yaya Isa zai shigo katsina Ranar jumma'a zai taho min da shi Da haka muka rabu saboda na lura komai in baka Tsara ba sai ka kwana aciki,a kwana a tashi na fara yi ma dan jarin nawa Rugu rugu ga masu siyan zobo da kunin aya sosai ammh kuma ba da yawa nake yin sa sosai yanzu ba,Nafi son ma a bani aikin Had'in Turaruka nafi samu sai dai shi zobo da kunin Aya sana'a ce ta cikin gida da zata tallafi Hidiman da bata gaza dubu goma zuwa kasa ba,duk yadda Yaya Ishaq nake ganin yana cikin Damuwa iya wanda na gani ne acikin Ransa bansan zafin da yake ji ba koda yaushe cikin fad'i yake yi"Kiyi hakuri Fa'iza na barki da wahala.Kiyi hakuri" Ammh duk da haka ban barsa ya zauna bai je ya duba Zainab da yara ba,tun bayan tafiyarta yafi wata bai je ba ni na matsa mai sai kawai yace min"Kina ta matsamin naje naje..To ina naga ma na motan zuwa ko a kasa kike son na tafin..? Sai na kallesa kafin nace" A bun bai kai haka ba,Ko ita ka fad'ama baka da na mota ai zata turo maka ka tafi din" Wani kallo yayi min kafin yace"Sai na gayamata bata fiki sanin bani da shi ba ne..? Ina jin ya harzuka sai na kama bakina ni kadai nayi kulla kulla na, na had'a cinikina na kwana Biyu, dubi biyar nabasa nace yayi na zuwa na dawowa bazai gagara ba,Ranar naga fad'a kamar zai dageni ya watsar da kudin yace na kwashe su bazai je ba, naki jin mganarsa na barsa masa su a tsakar daki na fice. ina jinsa yana fadin"Fa'iza ki dawo ki kwashe kudin ki nace,Haba matar nan so kike hakkin ki ya kamani.?gabad'aya kin Lullube rayuwata da alherin ki,so kike na mutu Allah ya sakani a wuta ko Fa'iza ai shikenan kin kyauta" Ina jinsa sai da nayi dariya wai ina so ya mutu ne ya shiga wuta Allah na Tuba daga taimako ni bana so auran su ya samu matsala ne sannan na dandana rashin miji a kusa bana fatan itama ta dan'dana duk da rayuwata ba irin nata rayuwar ba ne, ita tana da gata gaba da baya ba irina bace da gatan kalilan ne. Bansan ya akayi ba bayan kwana Biyu ya shirya yace zai tafin duk da bani da Tabbas nasan Mama ce zata matsa mai tana chan ne ammh na tabbata hankalinta na nan gani take yi yanzu tunda bata nan to sai a hankali,da ya tafi kwana goma yayi ya dawo. Sai dai yazo da kudad'e sun kai dubu hamsin yace Mahaifin zainab ya basa sannan ana ta dai kokarin neman aiki a ma'aikatu Dabam Dabam a bangaran da ya karanta wato na'ura mai kwakwalwa, ni ko a raina da fili sallata da zama na ina rokar masa Allah ya kawo masa aikin da zai amfanesa da kasa bakid'aya. Da kudin da ya samo ya siya mana kayan abinci,duk da Goggo ta aiko mana har da shinkafa da Yaya Isa ya kawomin sakon nan kuma na bashi kudin yaki karba yace tace kada ya karbo na kirata ina ta godiya sai tace"Babu godiya tsakanin mu Fa'iza da ina da shi abunda yafi haka ma zan miki shi"na aminta da mganarta yanzu Goggo ba irin da ba ne mijinta Tuni yayi Ritire yana gida sai kudin Fashion yaran ne ke kula da komai harta kudin makaranta Hafsa sune ba abunda zamu ce da goggo sai godiya,Sauran kudin kuma ya ijiye amfaninsu zai iya zuwa kwanan nan sai yabi shawarana ya bar min kudin a hannuna na adana. Tunda ya dawo na lura ya dawo da Dama daman da yake yi dani,Sai na fara shan jinin jikina,wani abun ma Saboda Badariya na gidan ne yasa yake ragamin,daya fara shigemin nake zaraf na shige dakin Mama ko na fito Tsakar gida na kirkiri aiki,haka kurum bana so mu kadaice saboda gudun kada ya ruguzamin shirina. Da daddare kuma baya samun dama Saboda yara ina yi musu karatun Qur'ani saboda Anum ma ta shiga ajin Hadda Baban ma yana yi musu na boko duk dare in mun gama su yi shirin kwanciya,ko yana son mgana dani sai nayi saurin jan Anum mu shige Daki mu kwanta ba Halin kuma wani abu saboda idon yara,da kuma idon Hafsah tunda tare muke kwana da ita. Yau muna zaune bayan mun gama cin abinci da ni da yaran duka muna kasa ne ina musu karatun Qur'ani Anum tana izifi goma ne Amir kuma ya wuce ashirin,su Ahmad kuma suna kasa kasa izifi biyu,shi yana kishigid'e saman kujera yana kallon mu har muka gama,Sai Amir ya mike yana fadin"Daada yau ba zaka koya mana karatun ba ne,? Yana daga kwance murya a shake yace"Ban ji dadi Amir sai gobe..yau ka famshe ni ka koya ma kannen ka" Sai Amir ya amsa mai yace su Anum su dauko littafan makarantan su,sai suka dauko ya fara duba musu,ina gefe har na fara gyangyad'i saboda gajiya Hafsah daman in yana falon bata cika zaman falon ba,sama sama naji Anum na kiran sunana"Umma..Umma! Sai na yi Firgigit na farka ina hamma cikin,lokaci daya nayi mika ina fadin"Nagaji ne menene kuke kirana..?.Amir yace"Umma kema ki zo mu yi karatun tare" Wata Hamma ta kara kwace min cikin kasala nace"Amir nagaji wlh ka bari gobe"Amir ya ware ido yana fadin"Umma yanzu kin daina karatu fa?kila ma kin manta na baya" Nace"in ji wa..?ban manta ba kawai Hidima ce ta sha kaina ammh zan dawo makarantar nan ayi hakuri dai yau mallam Amir" Su Anum suka yi dariya ina tayasu yana daga kwance yace"Amir kai ne malamin Umman taku..? Kafin yayi mgana fadi ba'a tambayeka ba ta mike ta isa garesa ta fara basa labarin Anum akwai shigen Surutu kamar wata aku,tana bashi Labari yana kallona yana mirmishi Lokaci daya yace"Kice Umma ta fara jin Turanci" Anum ta kyalkyace da dariya tana fadin"Sosai Daada" Gani ya yi ina mika bayana duk ya sake kawai sai ya mike yana ce ma Anum"Je ki ku cigaba karatun ku" Sai ta koma wajen zamanta shi kuma sai ya taso da ina shirin mikewa ne sai naji mganarsa a kasa kasa daidai kunnena yana fadin"Naga duk kin gaji muje dakina na tayaki da Tausa, duk zasu sake kiji dadin jikin ki" Ai ina jin haka na koma na zauna ina Kifta mai ido sai ya kuramin ido sai na zame masa kurma nace"E he..me kace..?mirmishi yayi kafin yace"Kinji ai me nace zaki iya tashi ne ko sai na Dagaki..?ya fada Lokaci d'aya yana dagamin gira sai na juya ina kallon yaran bakina sake shima sai ya kallesu hankalinsu baya kanmu alamun in tashi yayi min sai naki tashi sai kawai naga ya mike yana gyarawa ai ban san lokacin da na mike a guje na shige daki ba,tsayawa kawai yayi yana kallona yaran suka Dakata da karatun suna kallon sa Anum tayi farat tace"Daada me ya faru da Umma take gudu..? Yana shafa kansa ya juyo yana fadin"ta gaji ne kafafunta sun sake, sai tayi gudu saboda su sauka'' Tana daga ido Lokaci daya tace"Exercise kenan Daada" Yana zama kan kujera yace" yauwa my Anum" Amir dai bai ce komai ba ammh sai Hararan Anum yake yi ta cika Kaudi da fadi ba'a tambayeta ba sai da ya mata mgana sannan ta daina damun Dadan nasu da mgana wanda ya shiga Zurfin Tunanin in fa ya tsaya biye ma Fa'iza to bazai samu daman gyara kurakuransa na baya ba, har sai nagaba sun zo sun iskeshi a ransa ya shiryamata wani wayau da bata isa wannan karon ta tsallake ba. Da safe bani da masaniyar abun da ya kulla yara sun tafi makaranta Hafsah ma kusan tare suka fita Badariya na Daki bata fito ba, ni kuma na gama kaye kayen daki kafin na fita Tsakar gida sai na koma Daki ina lissafin kudin da suka Rage a hannuna na bama Hafsa kudi kafin ta fita zata shiga kasuwa ta siyo min aya da zobo na wajena bai wuce yau ba zai kare, sai kayan maggin gida da man girki da nace ta Siyo min ko ba da yawa ba. siyan kullum duk baka gane masa kayi ta ganin kudi na narkewa ka rasa ina suke zuwa. Na dukufa ina kirga kudin Hannuna har ga Allah ban ji motsinsa ba sai kawai naji mganarsa yana fadin"Hajiya Fa'iza mai zobo da kunin Aya ana ta lissafi ne..? Sai a lokacin na dago na gansa ya Coge a kofar shigowa dakin yana kallona yana min mirmishi,Sai nima na maida masa martanin mirmishin nasa ina fadin"Ka manta baka cike mai Turaren wuta da kwallacha ba" Sai kawai ya karisa shigowa Dakin yana Fadin"sana'a goma da ashirin wai Fa'iza yaushe kika zama yar kasuwa haka..? Dariya nayi ban yi mgana ba na zata zai zauna ne sai naga ya coge yana miko min hannu Lokaci daya yana fadin"A bani in taya kirgawa mana." Kai na girgiza ina fadin"ina kudin suke balle ka tayani kirgawa? riban wannan satin ne duka duka dubu hudu ne da yan chanji" Sai ya gyada kai yana fadin"Ina laifi ai motsi yafi labewa Allah dai ya kara Rufamana asiri" Na amsa da Ameen ina kallonsa sai ya yarfa Hannu yana fadin"Na gaji da zama ne waje da'ya shine zan dan fita na mike kafa" Sai na jinjina masa kai ina fadin"Ya kamata to a dawo lafiya" Har ya kama hanya zai fice ni kuma na mike sai kawai ya juyo yana fadin"Fa'iza na manta" Sai na juyo ina kallonsa Lokaci daya ina sauraransa kai tsaye yace"Taimakawa zaki yi ki shiga ki gyaramin Shimfid'ata da daki na duk yayi kura kafin na dawo" Yadda yayi mganar ba wasa ne yasa kaina Tsaye nace"Shikenan za'a gyara in sha Allahu" Sai kawai ya fice yana fadin"Allah yayi miki albarka FA'I TA.." A fili na amsa da Ameen  har ga Allah a raina ban kawo wani abu ba Sai da na gyara Dakina da dakin yara,na falo daman na kimtsa shi,sai na shiga Dakin nasa na fara gyara masa,Tiolet na fara shiga na wanke na fito ina gyaran Daki na kakkabe Shimfid'a na gyara har ina sauya masa zanin gado naga nasa yayi datti sai na kudiri a raina zan hada da wankin yara na wanke masa da sauran kayansa da suka yi datti. Ina cikin gyaran gado,ya shigo ban ji ko shigowarsa ba har ya samu nasaran rufe kofar damam abunka ga wanda ke da raunin ji,sannan gabad'aya hankalina yana ga abunda nake yi na duka ina saka zanin gadon jikin katifar na gama na mike kenan sai ji nayi an rumgumeni ta baya kam! Lokaci d'aya ana saki karfaffan ajiyar zuciya ni kuma har ga Allah na tsorata ban Zaci ganinsa ba gabana ya yanke ya fadi ras sai da kaina ya sara min jiri na neman kada ni, jinin jikina cak ya tsaya ya daina gudu ga shi ta baya ya rikeni sai na fara kokarin kwatan kaina ina fadin"Wa...ye..? Cikin rawan murya hannayensa duka Biyu yasa ya zagaye cikina da karfin da na kasa motsi kawai sai na Dage iya karfina zan yi ihu zaraf ya juyo dani ina fuskartarsa Saboda yadda yaji ina zufa ne,ga haki Lokaci da'ya Fuskata ya tallabo da Hannayensa duka Biyu Lokaci d'aya yana fadin"Fa'iza..Fa'iza ni ne fa" Sai da naji muryansa naji Numfashina na daidaita,Abun ka ga mai hawan jini abu kadan ke haye mana sai na sauke ajiyar zuciya ina kallonsa cikin mamaki shima kallona yake yi na bude baki nayi masa mgana cikin mamakin ganinsa kawai Dif! Kamar an kawo wutar lantarki an Dauke haka naji Jikina ya amsa ya koma kuma ya saki Lokaci da'ya, sakamakon bakin Yaya ishaq da na tsinta dumu dumu acikin nawa bakin yanayin da ban san yadda zan kwantata muku ba.ni dai da Hankalina Yaya Ishaq bai taba sumbatata baki da baki ba,ban ki in muna cikin auratayya yana bukatar natsuwa yana yi shima ba cikin soyayya ba ko natsuwa ba. cikin Tilastawa da neman biyan bukatar sa. Shiyasa sai na rude na gigice na fita daga Hayyacina ban kara Dimaucewa ba sai da naji Hannayensa na kara kaina ajikina da zafi zafi duk inda Hannunsa yakai a jikina sai ya taba,tsayuwa ce ta nemi gagaranmu sai kawai ya bini muka zube bisa Katifar da na gama gyara masa ya kasance ina kasansa shi kuma yana sama na,bazan iya fassara yanayin ba abu d'aya na sani yayi nasara motsa sha'awata da nayi shekaru da Binneta yayi nasaran yayyafa mata ruwa data Farfad'o batare da sanina ba,Doguwar rigar yadi ne ya jikina daga sama ya zage zif din yayi kasa da ita,ba san da wani lokaci hakan ya faru ba na dai san naji hannayensa suna kai da kawo saman kirjina sannan hancinsa na shinshino duka fatar jikina tare da Game numfashinsa da karamin Nishin dake fita da kofofin Hancina. Na fita daga duniyar da muke ciko ko nace ya taimaka wajen fitar dani daga Hayycina har yayi nasaran raba ni da Rigar jikina hannayensa dumu dumu acikin maraata,Fatar jikinsa tana gogar fatar jikina numfashi na ya sarke sai wani Uhmm...! Kawai nake saki,wani irin tafiya ya dinga yi dani tafiyar da tunda nake bantaba sanin ana iya kai macen wannan bangaran ba,Ban kawo ma kaina abunda yake shirin faruwa dani ba sai da naji bakon al'amarin da bayan shudewar mintina Arba'in yana kokarin kwace natsuwata kamar almara naji wani bakon al'amari na kokarin Ratsani Ratsawar da na manta ya yanayinta,kansa na tsakanin wuyana cikin Shakar Nunfashi naji yana karanto addu'ar da sai in zaka kadaice da matarka kake karantata kamar irin an buga kaina Gaf!yayi gaba sai yayi baya sai naji ni Tsamo Tsamo na dawo duniyar da ya tafi ni ina Dago idanuwana da suka yi min nauyi na kallesa a saman kaina daga ni har shi mun rasa suturun jikinmu,shi kokarinsa ya kai ga inda yayi alkawarin jinginewa na har abada ai kamar an sako min wani karfi bansan Lokacin da nayi wani yunkuri d'aya ba sai ga shi na barar da shi a gefena har keyarsa na bugun bangon Dakin na tabbata ba karfina ba ne Ya riga yayi laushin da bazai iya moran ma kansa wani abu ba. Kafin ya dawo hayyacinsa nayi gefe ina Raruman kayan na,daga inda na turesa ya Dafe keyarsa dishi dishi yake ganina Tsabar Halin da yake ciki cikin muryan da ta shige ba'a ko jinta ya kira sunana"Faaaa...izaaaa" Naji dai jan sunan nawa ammh ban tsaya bin ta kansa ba,na rarumi zanin Gadon da na cire zan wanke na nade jikina da shi ba inda jikina baya rawa,kuka kawai naji ya Sarkeni kawai sai na fashe da kuka har da Shessheka. Da rarrafe da jan jiki ya kariso gabana sai ji nayi ya rikoni nayi saurin kwace kaina cikin ihu nace"kada ka sake ka tab'ani..' Kada ka sake..". Na fad'a cikin ihu lokaci d'aya da kuka sai ya kasa kara tabanin ya koma gefe yana kallona,da kafarsa ya ja gajerun wandonsa ya saka kaina na maida kasa ina kuka,kamar ana dawomin da komai haka abubuwan da suka wuce suka rika dawomin na Dade bana fama da Kuncin zuciya tunda Allah ya samamin mafita ammh yau sai naji kamar komai anan yake faruwa kirjina yayi nauyi bakinciki ya cikani da na kasa sarrafa kaina agabana ya Durkusa kamar jaririn dake neman nono wajen uwarsa,yana shirin kara tabani nayi gefe da sauri ina kara rike zanin gadon dake hannuna gudun kada ya rabu da jikina,Sai ya Daga hannu cikin kasala da sanyin jiki,idanuwansa sun sauya Launi Jijiyoyin kansa sun mike gabad'aya cikin alamun Sararawa yace"Na bari naji bazan taba ki ba,ammh kiyi ma girman Allah ki bar kukan nan ki tsaya muyi mgana Fa'iza" Sai a lokacin na dawo hayyacina na Fahinmci gadar zare ya hadamin Allah na sona da Rahma da na Rufta acikin shirinsa da na shiga uku. Bani kuma da sauran mgana burina da na dad'e dashi acikin raina zai mutu batare da na cika sa ba. Rokona ya cigaba da yi ganin naki daina kuka ganin yana magiya kamar zai yi kuka yasa na saurara da kuka na, sai dai ban daina jan Numfashi ina Jan majina ba,zaman dirshan yayi a gabana cikin wata irin muryan da bazaka taba cewa Ishaq kabir karofi gaye dan kwalisa ne ya mallaketa ba murya ce da zata iya kasaara jikin ko wacce d'iya mace mai lafiya in dai ta jisa da muryan ya fara mgana cikin karyayan sautin da ni kadai zan jisa yace"Haba Fa'iza haba fa'iza meyasa..?kin san halin da kika sani Tsawon wannan lokacin..?ki dubeni kiga yadda na koma a gabanki don Allah ki kara bani dama na gyara kuskurena na yarda na amince ni mai laifi ne ammh kada ki horani ta wannan bangaran na amince ki min duk abunda kika ga dama,ammh ba ta wannan bangaran ba ki bari na samu natsuwa daga gareki koma menene sai ya biyo baya.." Sai da ya Dire mganarsa na Dago jajayen idanuwana na wurgasa masa wani harara da mamakin jin kalamansa na karshe,cikin karya wuya yace"Don Allah Fa'iza.." Har da kokarin sake rikoni na ko kara matsawa baya shima yana kara matsaoni da karfi nace"Ka na matsowa wlh zan yi maka ihun kwarto wlh" Cak ko ya tsaya yana kallona cikin mamaki yace"Kwarto fa,kwarto fa Fa'iza..? Kai tsaye ina kuka nace"Eh Kwarto nace. kuma ka kara matsowa kusa da ni kasha mamakina" Sai ya koma gefe na ya zauna yayi Tagumi kamar wani maraya Lokaci daya yana fadin"Ina cikin wani Hali don Allah Fa'iza ki bar ni na samu natsuwa daga wajen ki don Darajan don Allah Fa'iza ki ji tausayina" Banza nayi da shi ina ta sharan hawaye ya kara kwaso magiya har ya gama ban ce masa komai ba, sai ya matso kusa dani na zaro mai ido sai ya koma da baya hannunsa a sama yana fadin"Wlh bazan taba ki ba..ammh in kika min haka kin min adalci kenan Fa'iza.?zina kike so naje nayi ko kuma kina so na fad'a wata Halakan ne..? Idanuwana suna fitar da kwalla na Dago ina kallonsa cikin Muryata nace"Adalci ka ke mganar ban yi maka ba..?kai kasan menene adalci kuwa..?kuma  da kake mganar ka da ka fad'a zina ko halaka, au sai yanzu kasan Ana iya fad'awa wannan halakar.?ammh baka taba Tunanin matar daka jingine Shekaru Biyar baka taba waiwayanta da sunan bata hakkinta na aure ba.Ita baka taba Tunanin wata Halaka zata fad'a ba..?ko ita ba Mutum bace..?ko ita bazata iya fadawa zinar ba ne..? Na fada cikin wani yanayi Lokaci kamar alokacin yake fadamin ya zabi Zainab sama dani sannan ya jingine aurena fiye da shekaru biyar ammh Saboda Namiji bai da kunya har zai iya nema na da wani abu..? Wani irin kallo nake bin sa da shi kallon tarin takaicinsa da bakincikin da yayi shekaru yana kunsamin Hawaye suna kwarnya a saman fuskata. Kansa ya dafe cikin wani yanayi lokaci d'aya yana fadin"Na sani..nasan ni me laifi ne Fa'iza kiyi hakuri ki yafemin nasan nayi miki tarin laifukan da bazasu yafu lokaci d'aya ba, ammh ki duba ki gani wlh nayi nadama nayi nadama ki bani dama na gyara kuskurena" Cikin kuka nace"Ina nadaman da kayi..?yaushe ka fahimci Fa'iza mutum ce kuma macece kamar zainab..? Sai ya kasa mgana ya fara mgana cikin kame kame yana fadin"Tun tuni Fa'iza,Wlh tuni na gane kuskurena. nayi nadama kema kin sani" Kai tsaye nace"Babu abunda na sani.Abu d'aya na sani cewa baka sona baka taba kaunata ba.ka zauna dani ne saboda Baba..ka ce bani da amfani kace ni ba matar kwarai bace, ni ba matar rufin asiri  ba ce kace ni  Fa'iza ban dace dakai ba,Alfarma kake yi min,ka manta ka sha fad'amin baka Daukeni a bakin komai ba..?ka manta da kanka ka kirani ka nemi alfarman na barka ka yi rayuwar aure da Zainab ni kuma ka jingine aurena ba.?ko ba kai ba ne ka zabi wata macen sama dani ba?meyasa sai yanzu kake tsammanin komai zai zo maka da sauki..?. Na karishe fad'a ina tsiyayan hawaye,wani Turiri da hayaki na fitowa daga kasan raina,Hannuwana ya riko jikinsa na rawa yace"Na sani ki bar tuna baya wlh a wanchan Lokacin bansa me ya shiga kaina ba ne,Ammh wlh na dawo hayyacina na gane kuskurena na fahimci sakacina da laifina na fahimci sakacin da nayi Wlh na tuba na tuba..nabi Allah na biki Fa'iza na dade da sanin kin fiyemin kowacce mace amfani a Rayuwata kuma na dade da sanin nayi kuskuran furta kalaman jingianan auran mu fa'iza,ki bani Dama mu sake gyara rayuwar auran mu a karo na biyu don Allah Fa'iza.." Yafad'a lokaci d'aya yana jimke hannuwana cikin nasa sai kawai nayi Dariya lokaci d'aya da kuka kamar Mahaukaciya kafin nace"Fa'iza ce fa,kurma diyar Bebiya,Baka mummuna,Mara ilimin boko,mara gata mara kyau da nasaba,macen da bata chanchanci namiji kamar Ishaq kabir karofi ya so ta ba.Ni ce fa Fa'iza yar gargajiya nan,ina nan ban sauya ba.Ni ce dai wacce ka ke ciyar dani Saboda ina zaman kula da ya'yan ka, Fa'izan ne da ka ke tafiya wajen wata macen kafi wata biyu baka kirata a waya kaji yaya lafiyanta ba, Fa'izan da da bata san komai ba, sai ibadar aure da kula da ya'yanta da aka bar mata amanar su Fa'izan da ka rabata da kowa nata ciki har da mahaifiyarta marainiya da bata dukan wani gata, bata da uba bata da wani babban yayan da zai Tsaya ma rayuwarta ita ce dai wannan Fa'izan da Mama da Anty Binta suka maida abar wulakantawan su da cin mutumcin su, wannan fa Fa'izan da baka san ganinta Fa'izan nan ce da kake jin kunyar nuna ta amatsayin matarka, ita ce wacce kake jin kunyar duniya taga ya'yan da kuka Haifa tare ita wannan Fa'izan bata d" Ban karisa ba ya rufemin baki da Hannunsa ina kuka,hawaye jage jage,da majina shima idanuwansa Jajir kamar zai yi kuka yace"Fa'iza ki bar tuna baya..Na rantse da zatin Allah na gane kuskure na,Wlh kin fiyemin kowacce mace a wajena yanzu.Ki yi min aikin gafara ki yafemin laifuka na nayi miki alkawarin zamowa mijin da baki taba jin Labarin kamarsa ba' Don Allah Fa'iza ki yi hakuri" Kauda kai nayi kada kalamansa su sakani rauni cikin shakewar murya nace"Saboda yanzu ka rasa komai yasa nake da amfani a wajen ka..? Da Sauri yace"Wlh Talllahi ba haka ba ne. Allah ne ya dubeni da idon Rahma..Ya ganar da ni da wuri ba sai na mutu kasa ta kasa karb'ana Saboda bazan zamo adali gareki ba,Wlh Fa'iza in baki yafe min ba to Baba ma dake chan kabarinsa bazai taba yafemin ba" Kiran sunan Baba da yayi sai rauni ya kamani cikin kuka nace"Allah sarki bawan Allah mai son zumunci da son ya'yan yan'uwa. Allah ya jikan baba da Rahma" Da rawan jiki ya amsa da ameen Lokaci d'aya yana fadin"Ki yafe min Fa'iza ko don darajan Baba.Ki yafemin ki kuma bama Rayuwar auran mu Dama ta biyu don Allah.." Sai kawai na kallesa ina fadin"Ta ya ya zaka Zauna da wacce baka taba so ba..? Da Sauri ya Rumgumeni yana fadin"Wlh INA SON KI FA'IZA..wlh ina sonki" *Janafty* *KNKB2011* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Kalaman Ina sonki Fa'iza. Sun shiga jikina sun kusa kassarani sai nayi masa kuri da ido kawai,bawai don na yarda da mganarsa ba,Ba kuma don na taba rikesa a raina ba,so nake ya kyaleni yasa na yi saurin cewa"To ka sakeni mana"kara kamkameni yayi yana fad'in"Sai kin ce kin yafe min. kuma kin amince ki bama rayuwar auran mu Dama ta biyu" Cikin Sarkewan numfashi nace"Na yafe maka ban taba rike ka a raina ba Yaya Ishaq,a komai in kayi min bana ganin laifinka. alfarman da kayi min da kake zaune dani baka taba korana ba,shima wani abu ne,na yafe maka duniya da Lahira" Sai kawai ya kara kamkameni yana Dariya cikin farinciki yake fad'in"Thank you so much Fa'iza.Na gode nagode.." Lokaci d'aya yana sumbatar bakina nayi saurin kwace jikina ina fadin"Na yafe maka ammh kuma ina da Sharad'i na" Sai jikinsa yayi sanyi ya koma yayi min kuri,yana kallona bakin sa na rawa yace"Me ne sharad'in Fa'iza.? Yana bani mamaki sunan Fa'iza a bakinsa kamar shi ya rad'amin. Ina kallon cikin idanuwansa nace"Na yafe maka duka abubuwan da kayi min. Sai dai indan har kana so na kara bama auranmu wata Dama, sai dai kayi min alkwarin bani Lokaci har zuwa sanda naga dama sai nayi maka mgana" kamar ya had'iye wani abu sai da naji karan miyan da ya wuce ta makogwaronsa mukut. Ban damu ba, na cigaba da fadin"in kuma  ka matsa min to zan fasa yafe maka.sannan kuma bazan iya cika muradinka na bama auran mu wata Damar ba" Da Sauri yace"Aa to to na amince.ammh Fa'iza har zuwa wani lokaci?kada ki dauki Lokaci kinga fa Halin da nake ciki..? Kai Tsaye nace"Ba ruwnka da Lokacin da zan d'auka  alkawari shine kada ka takuramin in kuma ka takuramin zan fasa gudirina" Da Sauri yace"To bazan takura miki ba" Yafad'a harda daga hannu,Hawayena na Share ina kara rike zanin gadon hannuna kada ya subucemin,a marairaice ya kalleni kafin yace"Fa'iza ki yi ma girman Allah ki barni na rumgumeki ko na samu saukin abunda nake ji" Ido na sakarmai cikin mamakin kalamansa kafin na daure fuska nace"Sai yau ne ka fara shiga wani Halin Saboda ni ko yanzu ka fara di'n..? Ban basa damar mgana ba nacigaba da fadin"kuma kada ka fara karya alkawarin ka,nima zan karya nawa" Da Sauri ya matsa baya yana fadin"Na bari.Wlh na bari bazan kara tab'aki ba,sai kin ce na tabakin" Sai ya kusa bani Dariya sai da na murmusa,kokarin mikewa nake yi ya mike zai riko zanin gadon na balla masa Harara da Sauri ya juya yana Raruman kayana ya mikomin yana fadin"Dama..dama kayan ki zan d'auko miki" Ban yi musu ba nasaka hannu na karba,da sauri ya bani Hanya yana fadin"Ranki ya dad'e ki huce lafiya". Ban tankasa ba na fara tafiya ina Tattare zanin gado yabi ni da kallo har na fice ya koma ya zauna saman katifar yaraf kamar an sauke kayan wanki kansa ya dafe yana fadin"Allah na tuba..Allah ka yafemin..Ya Allah ka lallashi zuciyar Fa'iza ta sake bama auran mu wata damar" Ban kara ganinsa ba,tunda na koma dakina naci kukana sai da na koshi sannan naje nayi wankar Tsarki na Tsabtace jikina, ranar ko Kunin aya ban yi ba zobo kawai na Dafa,Shima Daki ya yini sallah kawai ke fitar dashi ,sai da Hafsah ta dawo ta kai nikan kunin ayan,abinci kad'ai nayi mana sai gyaran gida,ko da Daddare kwanciyata nayi a daki ban fito karatun dare ba, Anum tazo na korata bace bani da lafiya ba jimawa sai ga shi ya shigo har gadon ya zauna yana Taba goshina da Sauri na jaye kaina ina bata rai da wata murya yace"To taba goshi ma sai ya zama laifi..? Saurin matsawa nayi ina fadin"Ai a shari'a ma yanzu kai ba mijina ba ne,in nace bazan zauna dakai ba,ba wanda zai matsamin na zauna dakai" Ina gani jikinsa yayi sanyi cikin wani yanayi yace"Fa'iza wata shari'ar ce ta ce haka..? Kai tsaye nace"Baka sani ba..?ai musulunci yace Haramun ne ka yi wata Hudu baka kusanci matarka ba. Sannan jinginan aure a musulunci kamar sakin aure ne" Kafin na karisa yayi saurin tareni da fad'in"Ba saki ba ne Fa'iza wlh ban sake ki ba. kuma har abada kinsan auran mu ba saki in sha Allahu" Ina jinsa ban tankasa ba na koma na kwanta shi kuma sai ya mike yana fadin"Da alamu dai lafiyan ki lau yau laifina ya shafi ya'yan Umma kenan..?. Baya na juyamai ban kara masa mgana ba ina jinsa har yana gyaramin bargo ya fice yana fadin"a huta lafiya Fa'in Ishaq" Tun daga ranar bai kara matsamin ba da ya fara na d'ago na ballamai harara sai ya koma gefe yace"Yi hakuri". Ko Allah ya baki hakuri,Daganan sai na samu lafiyansa,ko bakomai na daina fargaban zai ritsani ko zai mamayeni irin na ranar,ammh duk da haka ina taka tsantsan da shi Saboda naga da gasken yake yayi nadama,kuma na karb'i nadamarsa ammh ba domin zan iya karban bukatansa na sake basa wata damar ba. Mama ta dawo bayan tayi kwarari wajen wata biyar a yamai, yan'uwan ma sun so tayi zamanta achan ne Mama taki sana'o'i suka dinga yi a chan ita da Anty Hure kuma sun had'a mata yan kudade kafin ta dawo da su aka samu aka biya kudin makarantan yara,aka siyan kayan abinci tunda yan kudad'en hannuna mun cinyesu wajen siyan abinci sannan ya turama Jamal shima wani abun,Ga Badariya itama suna shirin zuwa bautar kasa ne ita laluranta kad'an ne babban abu shine kud'in haya da kud'in makarantar Jamal tunda shi ajin karshe zai shiga ya maimaita aji hud'u,yana karatun Software enginearing ne. Kudin Hayan nan da shi nake kwana araina,kud'i ba yan kad'an ba wajen dubu Dari hudu ne wannan gidan,Shi kan shi ya damu tunda mai gidan ya fara mganar kudinsa tun watan daya gabata sai ya bashi hakuri yace ya karamai Lokacin,mai gidan daman ba shi da kansa ba ne,Komai na Hannun babban d'ansa ne,kuma ba wani kirki da ya cika ba,Don ma yana ganin mutumcin Yaya Ishaq da Tuni ya fara yi mana sallama. Zagayowar wannan shekaran sai dai Godiyar Allah jamal ma gida ya Dawo,Anty Binta kuma da an yi mgana sai tace tana da biki a gabanta,bata da kudi shi bai ma nemanta,Mama ce ta kan kirata a waya tana fad'a mata sai ta fara korafin itama akwai hidima agabanta,Abuja ma yanzu sai yafi wata bai je ba,Ita Zainab din ne ma,takan turo masa kudin ya tafi yayi sati ko kwana goma ya dawo nima ta kan kirani lokaci bayan Lokaci mu gaisa auran nasu har mamaki yake bani kamar Dole,to ita tana son mijinta kuma mahaifinta yasan haka, shiyasa bazai yarda auran ya lalace ba shima Ai yana son matarsa da baya sonta da Tuni ysan mafitarsa. Tun mai gidan nan na d'aga mana kafa,har yazo ya daina Sauraran ban hakurin Ishaq ranar da Safe yayi mana Dirar makiya Allah yasa yara suna makaranta da abun bai yi dad'i ba,Da kakkausan murya ya ce mana ya bamu nan da sati daya in bamu biya ko rabi ba sai dai mu bar gidan. Hankalin mu ya tashi bamu ijiye ba,ba kuma mu ba wani ajiya ba. Yaya ishaq ko barcin kirki ba yayi duk ya bushe a tsaye gashi yana ganin Jamal a gida shima ba kudin abinci da pocket money ballatana ya koma makaranta har shi da kansa yayi ma Anty Binta mgana tace bata da kudi ta shiga adashe ne,ni kuma jarin hannuna duk yayi kasa sai na Bukatun cikin gida. Mama ma duk hankalinta ya tashi,Mama a baya datake yar gayu yanzu wahala duk yasa ta tsufa kamar ba ita ba,Sai dai ya shiga D'aki yana Tufka yana warwara ba mafita Hafsah mganar kudin makarantar Jamal ta sani shi kadai takai labarin Karofi wajen Goggo,sai ga shi ta kira Jamal yaje wajenta ita da ya'yanta sun had'amai dubu sittin tace ya biya kudin makaranta,bayan ta hadamai kayan abinci,haka yazo mana da kayan arziki Mama sai kunya ya kamata har da kuka sai gashi ta Biyoni har daki tana cemin"Fa'iza ke kika yi ma Goggon taku mganar jamal hala..? Ina zaune nace"Aa Mama inajin Hafsah ne da taje wannan satin" Sai mama ta kasa mgana ta fita ta koma Dakinta abun mamaki sai ga Mama da shiryawa ta tafi karofi yima Goggo Godiya sai da ta kwana Biyu ta Dawo tana fad'in irin alherin Goggo da ya'yanta a raina nace da ba Hajiyar Dala ce kad'ai yar'uwar mijin ki ba,ashe kin san da Goggon,Hajiyar Dala da take ganin tana tare da ita ko jinta ma ba'a yi. Yanzu naga Mama ta daina Takura min,ba kamar baya ba. Kuma bata shiga harkata,  naga ma alamun Ta koma wata shuru shuru a d'aki kamar bata nan,Aranar da satin d'ayan da mai gidan ya bamu,zai cika kasa barci muka yi,a daran ranar har ce ma Yaya Ishaq nayi"Me zai hana ka yi ma zainab mgana ko akwai taimakon da zatayi maka ta bangaran su..? Kai Tsaye yace"Aa bazan roki kowa ba Fa'iza ai susan ina bukata kuma basu Dauko sun bani ba. In sun bani zan karba in basu bani ba, bazan taba rokan su ba" Sai ya bani Tsausayi daganan ban kara masa mgana ba, sanin da nayi tunda yace bazai yi mgana to bazai yin ba,Da Sassafe bayan ya raka su Amir makaranta gidan Anty Binta ya tafi,yana chan bai dawo ba sai ga yaron megidan da wasu matasa majiya karfi har gidan suka shigo Hafsa na makaranta Badariya ke gida tunda sunanta bai fito a bath A ba. Tijara ya fara yima sannan yace watsi zai saka ayi mana da kaya,Mama ta fito nima na fito ni ke basa Hakuri Mama ko cikin gadara tace"Ka dad'e baka sa an yi mana watsi da kaya ba, ban da yanayin rayuwa kai har ka isa ka wulakantamu. shekaran da ta wuce kai baka isa kazo kana mana barzanar banza ba,rayuwa ce ta maida mu haka" Ta fad'a cikin baci rai,ido cikin ido ya kalleta kafin yace"Tsohuwa ina daraja Furfuranki ammh ke baki gani ba ko..? Kai Tsaye Mama tace"in kana Daraja Tsufana ai da baka tsaya ina fad'a kana fad'a ba" Kai tsaye yace"Gidan nan ai ba na tsoho ba ne ko?to in dai bana Tsoho ba ne sai kin fita daga gidan nan,yau na zata abun naku na mutumci ne. kuma Darajan d'anki kikaci wlh da yau sai kin raina kanki ina ruwana da rayuwarki a baya  wama ya sani ko a lokacin baya d'in da kike da arzikin ba alheri kika shuka ba tsiya ce shiyasa kika ga karshen ki? Ai sai Mama ta saka kuka tana fadi'n yayi mata rashin kunya na riketa ina fadin"Haba Mama ba girman ki ba ne ki Tsaya kina tanka tanka da shi" Sai mama ta kasa mgana nan na saka Badariya ta shiga da ita ciki D'aki sai kuka take yi. Wani Lokacin masu gidajen haya kalilan ke da burb'ishin mutumci saboda nasan bamu da gaskiya Kuma a maganar Gaskiya Mama ta zak'e da yawa ne shiyasa. Hakuri na rika basa ina fadin"Kayi hakuri don Allah ,ya fita ne ya dawo yanzu zai shigo" Kai tsaye ya kalleni ba wani babba ba ne, bazai wuce sa'an Yaya Ishaq d'in ba kawai dai irin ya'yan masu kudi'n nan ne, kallo na yayi yana fadin"wanchan tsohuwar ai ta bata komai Hajiya.Kai ashiru ku shiga ku fara fito musu da kayan su waje" Sai na durkushe a gabansa na had'a hannayena ina fadin"Kayi wa girman Allah kayi hakuri.In kayi mana watsi da kaya ka tona mana asiri ina zamu..?ka da ka manta mu musulmai ne kuma duk inda musulmi yake dan'uwan musulmi ne,In ka rufamana asiri ka suturtamu sai kai ma Allah ya Suturtata taka ranar gobe kiyama. kayi hakuri don Allah zamu biya ku kudi'n ku da zarar mun samu" Na fad'a cikin magiya sai kawai ya Tsaya yana kallona cikin Tausayi kafin ya ce na mike sai na mike ammh ban sauke hannayena ba cikin Tattausan murya yace"bakomai naji rokon ki na yi muku lamani ku zauna ammh kuyi adalci ku biya da zarar kun samu" Da sauri nace"Wlh zamu biya.In sha Allahu" Daga haka ya gyad'a kai ya yi ma samarin mgana suka fita tare  ajiyar zuciya na sauke, na koma kan kofa na zauna ina kuka ahaka Yaya Ishaq ya shigo futu futu kafafunsa, dani ya fara cin karo ina kuka cikin tashin Hankali yace"Kuka Fa'iza me ke faruwa..? Ya fad'a yana zama kusa da ni da Sauri na Share hawayena ina kallonsa Daga sama har kasa ganin yadda yayi Futu futu kamar wanda yayi tafiyar kasa cikin mamaki nace"A kasa ka tako..? Bai bani amsa ba ya kara fadin"Me ya faru ne..? Sai nayi masa shuru yana shirin kara mgana ba sai ga Badariya ta fito ita ya tambaya ta maida masa yadda akayi har yadda na duka ina rokon su sannan ya amince ya d'aga mana kafa cikin d'aga murya ya kalleni yana fad'amin"kika duka mai Fa'iza..?kika dukamai fa..? Saboda wani dalili..? Yafad'a cikin bacin rai sai kawai na mike ina fadin"Ba dukawa bace roko ne da neman alfarma, in ban duka ba da yanzu kazo ka ganmu a kofar gida an fara yi mana watsi da kaya" Daga haka na shige daki sai kawai ya bini da kallo ga takaicin yaje bai samu Anty Binta ba, sun fita da mijinta a kasa ya tako tunda batagwarawa har Ajiwa,sai kuma yazo ya iske wannan tashin Hankali D'akin mama ya shiga ya isketa tana kuka dakyar ya Lallasheta tayi shuru tana fadi'n wai mai gidan ya zageta yasan halin Mama shiyasa ya kalleta yana fad'in"Mama bafa kowa ya ke da ragowa ga manya irin ku ba. Sannan kema Mama me ya kaiki sa'in sa da shi.?mu ne fa bamu da gaskiya hakkinsu ne a kanmu bamu biya ba kuma sun yi mana Hallaci bai kamata ki nemi zaginsa ba" Ganin ya rufeta da fad'a yasa ta sauya mganar da cewa"Ka samu Bintan? ya kuka yi..? Kai tsaye yace"Bata nan sun fita da megidanta a kasa na dawo duk nagaji" Mama ta yi tagumi kafin tace"Allah ya warware mana ko zakayi ma Zainab mganar ne..? Da Sauri yace"Aa Mama Allah zai kawo wata hanyar" Sai bata kara mganar ba,sanin halinsa Tunda yace a'a to bazai kara bi ta kanta ba,Batare da sanin kowa ba, ta Kira Zainab ta fada mata komai ita Zainab d'in ne ta kirani tana fadin"Haba Maman Amir sai ki boyemin wannan abu haka..? Sai nayi mamakin a ina taji nadai san bashi ya fad'a mata ba,sai da naji tana fadin Mama ta kirata ta fad'amata sannan nayi mata bayani sai tace bari ta kirasa to bansan ya suka kaya tsakanin su ba, ta dai turo masa kudin kuma ya biya mana kudin Hayan ranar da ya Tura ma mutumin kudin har sai da yace mai"Gaskiya kayi sa'an mata mai hankali da iya mgana." Da ko ya dawo gida tasani yayi agaba da masifa da fad'a wai na fito ina ma wani gardi magiya kallonsa kawai nayi kafin nace"Yaushe ka fara kishin Fa'iza..? Kai tsaye yace"Ke Fa'iza ki fita daga idona. ko a baya bana barin ki sakakaka.nasan abunda nake yi kada ki kara batamin  rai da mganganun ki na banza" Daga haka ya barmin wajen yana ta masifa a raina nace topah Sabon Salo Tusa a lasifika. Hankalin mu ya kwanta tunda Allah ya Rufa mana asirin duka,Badariya Sunanta ya fito a Bach B, an tura ta Camp yola Raliya kuma Abuja suka barta,Hajiyar su Raliya ta bata kudin mota da kudin kashewa na har ta dawo,Hajiya ta Dauke mana wannan nauyin ta tafi da tarin nasihan yayanta da mama akan ta kula da kanta,Sati uku tayi ta dawo gida,Sai kuma cuku cukun yadda zata dawo kusa gida tayi bautar kasarta. Haka muka cigaba da Rayuwa yau fari gobe Tsumma Goggo na lekomu ita da su Anty Nasara nima nakan lekasu,Makota na su Sa'adatu basu manta dani ba,Nima ban manta da su ba, ina leka su wani Lokacin sana'ata ne baya barina fita har kuma yau Yaya mariya bata kara takowa gidana ba.sai dai mu yi mgana da ita ta waya. Hajiyar Dala ko ba wanda ya kara jinta ko garin ta shigo bata zuwa Anty Binta kuma ta maida hankalinta wajen Shirin Bikin Halisa daya rage Saura wattani bata cika zuwa ba ma. Ina zuwa gidan Hajiya gaisheta Lokaci bayan Lokaci anan ne har tace Yaya Ishaq ya kawo takardunsa daga barayinta tagani ko za'a dace da murnanta nazo nayi mai magana sai kawai ya kalleni kafin yace"Ina fatan ba zuwa kika yi kikace kina so ta nema min aiki ba..?. Wani Haushi ya bani, ba ka da ko sisi sai shegen girman kai hararansa nayi ina fadi'n"Sanarwa na bada a masallaci baka ji ba..? Sai ya maida abun wasa ya taso zai rikeni na matsa baya kafin nayi mgana yayi saurin tareni da fadin"Kai na bisa wuya afuwan na manta ne" Sai kuma ya bani Tausayi yadda yayi mganar,ni da kaina naje na kai ma Hajiya Takardunsa,a amsa da yakinin acigaba da addu'a za'a dace. Ana cikin haka Badariya ta samu aka ijiyeta kano inda zatayi bautar kasarsta sai Mama tace ta zauna gidan Hajiyar Dala Badariya tace bata son zama,Maman ta had'a ta da Yayan nata yayi mata fad'a Nima nayi mata nasiha sosai ina fadin"Kiyi hakuri kije ki zauna ke mace ce yafi ki zauna a inda baki sani ba,duk tsiya ke yarta ce bazata ce zata kore ki ba" Da haka Badariya ta amince ta tattara kayanta ta tafi kano Bayan,Maman ta samu tayi mgana da Hajiyar Dala Anty Binta dai sama sama take da Badariyan acewarta ta mata rashin kirki,tunda abun da ya faru tsakaninta da Halisa da har yanzu ita da Badariyan basu koma Daidai ba, ba sa gaba suna mgana da juna,ammh sama sama. Raliya kuma kaduna aka ijiyeta,Sai ta zauna gida kawar Hajiya gidan su Laila kenan. Tafiyar Badariya ba jimawa sai ga waya daga Abuja akan wani kamfanin Sarrafa fattu da Mahaifin zainab ya taba kai takardunsa sun nemesa,Dole ni nayi murd'a murd'a na basa kudin mota ya tafi,bayan tafiyar sa mun yi mgana da shi sau d'aya ya samu sun yi interviuw sai jiran kiran su bai dawo ba ne saboda baya so bayan ya koma su sake kiransa,To yana zaman jiran kiran nasu ne,Zainab ta fara rashin Lafiya har da kwanciya a asibiti,Ashe ciki gareta da sauran rabo a Tsakaninsu. Daya kirani ya fad'amin ne bayan suna asibitin da ita nace in ta farka ya bata waya na gaisheta sai dare ya samu ya Had'amu na gaisheta bai fadaminciki gareta ba, ita ce tace min"Maman Amir bakin ki dai ya amsu,zai zo miki da Farhan ki yaye min shi tunda Honey yaki bari na huta hakanan" Daganan sai na d'ago mganarta nayi murna sosai da Fatan alheri da ta basa wayan nayi masa murnan karuwa sai kawai sai yayi yar  murya yana fad'in"Saura ke. kema na kusa har ba miki alluran.." Da Sauri na katse wayar ina mamakin a gaban matarsa yake fadin hakan?a fili na murmusa,sannan acikin raina nace haihuwa ai na bar ma, matan so ba irin mu da rabo kan rantse ba. Kamar cikin na bata wahala ne an dawo da ita gida kwana biyu jikin ya rikice sai da aka kara maidata ita asibitin shiyasa bai dawo ba,Kuma har yanzu basu kirasa ba kuma yace an kira Mutane biyun da suka je interview tare,ni dai na lallashe da cewa Allah ne mai yi kuma shi ke ba da aiki in alheri ne Allah ya basa in kuma ba alheri ba ne, Allah ya musanya masa da wanda yafi alheri. Ya shafe kusan wata a Abuja ba yara ba ni kaina ina kewarsa kaji Fa'iza da Samun waje wai ina kewar mijin aro.?da Sauri na cire tunaninsa a raina na cigaba da Sabgan gabana ni nake rike da karfin gidan duk da muna da sauran kayan abinci, sannan daga Gidan Hajiya ma ta aiko mana da shi,Sannan na samu aikin yin Humra da kwallacha da kudin nake ta riritawa muna cefane da Hidiman yara.. ****** Wata ranar asabar data kama kwanan Yaya Ishaq Talatin da hud'u da tafiya Abuja mun yi waya da shi a daran jiya har da yara suka gaishe da Antyn nasu tana gida an bata Bedrest,Da gaske yake da yace yayi kuskure kuma yayi nadama zai gyara kuskuransa,yana kokarin kirana in dai baya garin sannan zai ji ya gidan yake tafiya mganarsa kenan"Nagode Fa'iza Allah yayi miki albarka" Safiyar ranar sai da na zane Musty sannan yaje Tahfezz da shirin sa bazai je ba,ya zauna yana min rigima na shiga jikinsa da Bulala,Daman tun jiya nake jin jikina ba dadi,da Safe kuma sai fama da sanyin jiki Hafsah ta shiga makaranta zasu su yi wani aiki ita da Sauran yan ajinsu tunda ta fita ina kwance afalo ban yi komai ba sai dai in masu siyan kunin aya da zobo sun yi sallama na mike na basu, Tunda jiya nayi da yammah shiyasa yau da Safe nace bazan yi ba sai da yammah. Wayata na cikin Dakina na baro ta ana ta kirana ban ji ba,barci ne ya kwasheni nan saman kujera acikin barci sai na ganni a gari Dabam ba karofi ba kuma ba katsina ba,bakon wajen da mutanen da ban sani ba,Kamar kuma acikin barci naji ana kiran sunana a firgice na mike ina Salati sai naga Mama a saman kaina, na mike zaune ina raruman da'nkwalina da ya fad'i saboda barci lokaci d'aya  ina fadin"Mama.." Kallona tayi cikin nazarina kafin tace"lafiyarki kuwa.?Isa tun dazu yazo yana  ta sallama baki ji ba..? Sai gabana ya fad'i na zare ido ina fad'in"Wani Isan.?Yaya isa." Kafin na karisa ya d'ago labule ya shigo a gaggauce yana fad'in"Fa'iza maza dauko hijabin ki Karofi zamu tafi yanzu" Gabana ya fad'i ras! Cikin Dafe kirji nace"karofi..?me ya faru ne..? Na fad'a ina wuce Mama zuwa gaban Yaya Isa itama Mama sai tabi bayana tana fadin"Isa lafiya kuwa.? Cikin natsuwa yace"Lafiya lau kada ku damu.Goggo tace na dauko su ita da Hafsah akawai wanda zai gan su ne" Dagani har Mama sai muka bisa da kallo zan yi mgana da sauri ya tare ni da cewa"Ki sako hijabi muje sauri ake yi Fa'iza" Jikina na rawa na ruga daki na Dauko Hijabi na fito ina fad'in"Mama su Amir" Da mamakina sai kawai tace"kuje ko taliya zan dafa musu,tunda akwai komai kafin ki dawo" Sai kawai nabi bayan Yaya isa da gudu daya riga ya fice gabana na fad'i jikina na rawa a raina nace kodai Goggo ce..?da sauri nace"Aa ba haka ba ne" A mota na same shi na bud'e gidan gaba na zauna cikin Sauri yace"na kira hafsa tana makaranta zamu biyu mu dauketa" Sai kawai na Sadakar Mun rasa goggo,kawai sai ji yayi na fashe da kuka cikin kukan nake fadin"Allah Sarki Goggo" Tsawa ya dakamin yana fadin"Wayace miki wani abu ya samu Goggon.? Cikin hawaye nace"To me zai saka kazo da gaggawa ka daukemu zuwa karofi..? Hankalinsa na wajen tuki yace"To ba mutuwa ba ne abun farinciki ne, Dan'uwan mahaifiyarku ce ya bayyana, shi da mahaifiyarsa yau a karofi" Na ji dai kalmar dan'uwan mahaifiyarku a kunnena sai na Dafe kirji ina fadin"Ta madina..? Kai ya gyad'amin yana fadin"Shifa..Sauri suke yi shiyasa Goggo ta tasoni daga gun aiki tace na dauko ki keda Hafsah" Daganan ban kara bi ta kansa ba farinciki da wani irin zumud'i ya sarkeni hannuwana na da'ga sama ina fadin"Alhamdulillah..Allah abun godiya" Har muka isa makarantan su Hafsah bakina yaki rufuwa a waya ya kirata ta fito a gaggauce itama kamar ni duk ta Rud'e sai da yayi mata bayanin da yayi min sannan itama ta rud'e da Murna tana fad'in"Yaya Isa ya ka gansa? yana kama da Tamadina..? Mirmishi yayi yana fadin"Tsammanin abunda baku yi tsammanin ba. muje dai zaku gansa labari bazai gamsheku ba." *Janafty* *KNKB2012* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Har muka isa karofi ban sani ba, na lula cikin wani irin farinciki da zakwad'i abun da ka dade kana hasashensa bai faru da wuri ba sai yanzu. Wani irin farinciki ne ace yau ga wani naka daka jima kana jin labarinsa baka taba ganinsa ba, kafin isar mu gidan Goggo a cikin zuciyata na wasaafa yadda zan ga Dan'uwan Tamadina bansan iyaka ba nadai san bakina yaki zama waje d'aya na kasa natsuwa har Hafsah tafini mallakan kanta. Tunda Muka iso kofar gidan Goggo sai kuma jikina yayi sanyi maimakon na zama ta farkon shiga gidan sai na kasance ni ce ta karshe na koma na rab'e bayan Hafsah kamar wacce tayi karya, gabad'aya sai naji gabbaina sun saki na fara tunanin wani irin tarba ko maraba zai yi damu alhalin bai taba ganin mu ba? sannan meyasa ya kai wad'anan shekarun batare da ya waiwayemu ba?har sai da Allah ya Dauki ran Tamadina basu gana ba? Ya ya zamu gansa..?mu ma ya ya zai gan mu..?yadda ya zata ko ba yadda yayi tsammani ba? Duk wad'anan tunanin suka taimaka wajen da dakushe murnanta a fili har Yaya Isa yayi sallama kofar falon Goggo Ya shige Hafsah tabi bayansa nice karshen shiga falon, sannan sallamata ma a saman bakina ta makale idanuwana suka fara wurgawa cikin falon ina neman bakon fuska naga Goggo da megidanta,Sai Baba Ati da wasu Tsofaffi maza daga gidan su Tamadina ne,Sai wata Dattijuwa mai natsuwa da Haiba zaune kan kujera cikin shigar alfarma kallo d'aya zaka yi mata kasan ta samu dukkan gatan duniyan da suka Boye shekarunta. Gefenta a kasa wajen kafafunta wani kamilin megidanci ne baki sai dai bakinsa ya hade da hutu da jin dad'i da Fatarsa ta sauya,yana Sanye da Shadda Mai ruwan kasa har da babban Riga tana maiko kansa da Hula zanna na mutanen maiduguri,yana duke ne ammh ina iya ganin yadda yake saka karamin farin kyale yana Tsane ruwan Hawayensa,Yaya mariya na gabansa itama a duke kamar kukan take yi, Dattijuwan nan ta rike mata hannu alamun lallashi. Daga sama naji murya Goggo tana fadin"Alhamdulillah ga Fa'iza nan da Hafsatu nan sun iso.." Kamar an zabure sa haka ya mike cikin Haibarsa da muryansa da ta dakeni yace"Ku matso nan ya'ya na ku matso naji dumin ku..Ku zo ga Abban ku" Yake fad'a cikin nuna tsananin murnansa sai alokacin na kara kallonsa ba shakka jini ba karya ba ne ina ganin kama ta jini Tsakaninsa da Tamadina Hafsat ne ta nufesa zata duka ta gaishesa sai kawai ya Rumgumeta,hawayensa na zuba ni kuma ya miko min hannu sai na sulale kasa a gabansa idanuwana sun ciko da kwalla,Dattijuwan nan ta kallemu ta kara kallon mu musamman ma ni sai kawai ta fashe da kuka tana fadin"Allahu akbar daga ganin wannan na shaida jinin Lauratu ne" Sai kawai ta rikice tana rusa kuka Goggo ta matso tana fadin"Haba Hajiya zuwaira ashe kukan naki bazai isa hakan nan ba..?. Cikin kukan take fadin"Dole nayi kuka, Dole na koka na yi sanadiyar da na yanke ganawa Tsakanin yan'uwan juna.?kaico na.." Tafad'a cikin wani yanayi da sauri ya tareta da fadin"Inno ni ne kika yi ma wannan laifin kuma nace na yafe miki ba shikenan ba..? Ni dai naji ciwon rashin ganawa da yar'uwata guda d'aya da nake da shi,Ammh nayi murna daya kasance ta barmun zuru'an da bazan jima ina kuka ba, in na kallesa zan tuna yar'uwata ta bar min su ne domin kada in na zo nayi kukan rashinta" Gabad'aya kalamansa sai suka sakani rauni bansan Lokacin da na fashe da kuka ba ganin haka yasa sai Hafsah ta d'auka Yaya mariya ma daman mun sameta tana kukan ta ne.Wacce aka kira da Inno ta sauko kasa tana neman Durkusa mana cikin kuka tace"Ku yi hakuri ku yafe min ya'yan nan na zalunce ku na yanke ganawa tsakanin mahaifyarku da dan'uwanta" Da Sauri ya saki Hafsa bayan ya zaunar da ita ya karisa gareta ya rikota ya maida ta saman kujera yana fadin"Inno ki daina wannan kukan don girman Allah" Sai ta ji mganarsa ta koma tayi shuru tana sharan kwallah kasa ya zauna a gabanta yana kallonmu d'aya bayan d'aya kamar yadda muke kallonsa. Lokaci da'ya yana Dauke Hawayensa da Farin hanky din dake hannunsa. Cikin Kayattaciyar Muryansa ya dago yana kallon su Goggo kafin yace"Cikin su wacece tafi kama da yar'uwata..? Har Baba ati da goggo suna had'a bakin wajen fad'in"Gata nan a gabanka Fa'iza kamar Tamadina ta tsaga kara yadda ka ganta haka mahaifiyarta take. sai dai ita bambamcin Tamadina bebiya ce ita kuma Fa'iza jinta ne yake da rauni" Kawai sai ya kuramin ido Lokaci d'aya yana fadin"Naji dadi da akwai fuskar da zan rika ganin yar'uwata a ciki, baku da Hoton yar'uwata ku nuna min ya'yana..?. Ni dai na kasa mgana Hafsah ce tayi karfin Halin cewa"Yaya Asiya na da shi a wajenta"da alamun karin bayani ya ke kallon mu Yaya mariya ta jinjina kai tana fadin"Itace babbarmu wacce su Goggo suka ce tana kano tana aure" Sai ya jinjina kai yana fad'in"Rashin sani ne ai kano gida ce a wajena chan na girma nayi karatuna kuma chan nayi aure,kafin chanjin aiki ya Dawo dani nan kaduna,yanzu komai ya kare tunda Allah yasa nazo kuma na ganku nayi alkwarin bazan kara sakacin da zaku rasani ba" Sai ya fara sharan kwallah ya cigaba da fadin"Yau yau din nan Inno ta fad'amin ina da yar'uwa bayan ta sanar dani inda dangin Babana suke,a gaggauce na taho ko iyalaina ban zo da su ba suna kano ana auran kanin Mai dakina,yaran duka suna chan,ni kaina Tafiya gareni zuwa porthercourt gobe akwai Taron da muke dashi daga wajen aikin mu aka turamu,ammh nace bazan zauna ba sai nazo na ga ahalina ina zuwa kuma sai na samu labarin dangi duk sun kare itama yar'uwan nawa Allah ya yanke ganawa tsakanin mu da ita" Inno na sharan kwallah tace"Allah ya jikan Hafsatu ina kallon fuskarta ranar da zan bar garin Lokacin bata wuce shekara Biyar ba" Aka amsa da Ameen Ameen mu dai sai kuka muke yi muna sharban hawaye Shi ma kukan yake tayamu ammh nasa bamai sauti ba ne,yana dai yi yana tsane hawayensa,da farin Hanky din dake Hannunsa.. Baba ati ta gyara zama tana fadin"Zuwaira wani dalili ne yasa tunda kika tafi baki kara waiwayomu ba sai yau.?Sannan wannan yaron baki taba sanar da shi komai game da mahaifinsa da Danginsa ba..? Inno ta fara kuka kasa kasa tana fadin"Ba laifin Usman duka acikin abun da ya faru kada ku manta na bar garin nan yana da kananun shekarun da bazai iya tuna komai ba! Duka abunda ya faru laifina ne shiyasa nace ku yafemin" Hannayenta ya rike cikin Lallashi yana fadin"Inno ashe kukan nan ban ce ya isa haka ba..? Da jajayen idanuwanta tace" USMAN rashin kuka na ba zai sa laifina yaki bayyana ba,da gaske na zalunceka na tafi dakai na raba ka da Dangin mahaifinka gashi karshen karshen sai da na kawo ka gare su" Sai ya kasa mgana Saboda bata kiran sunansa sai dai tace mai BABAN Nana kamar yadda matarsa ke kiransa. Gyara zama tayi tana kara gyara zaman mayafin dake kanta tace"Bani da wani kwakwaran Dalilin aikata abunda na aikata Sai dai nace rashin son da ban yi ma mahaifin Usman ba aka aura min shi,alokacin ina da wanda nake so ammh Mahaifina yayi min Dole,ya aura min shi aka kawo ni wannan garin kada ku manta tun Lokacin da aka kawo ni,ban yi zaman Dad'i da kowa hatta da kakarku da ta haifi mahaifiyarku Lauratu,Sannan ban saki jiki da kowa ba,bani da aiki sai kuka sai zama cikin Damuwa Ko Usman Rabo ne ya rantse tsakanina da mahaifinsa  aka same shi,ko da zama ya kare tsakanimu da shi bayan rasuwarsu zuciyata bata Rusuna ba. gani nake yi in na barsa a wajen ku bazaku barsa ya zauna dani ba, shiyasa tunda kuka amince na tafi da shi a raina nakudiri niyyar zan Nisanta shi da abunda ya shafi wannan nahiyar,Tsakaninsa da mahaifiyarku bai fi shekaru uku ba yana gabanta domin neman irin haihuwan yakai mallam ga aurena sai bayan na haifi Usman sannan Lauratu ta Haifi Hafsatu tabbas nasan an haifeta da laluran rashin ji da mgana,Sai dai bamu zauna da lauratu ba,Duk da mun yi zaman kishi na mutanen na wanchan lokacin,Ni ba kishi nayi da ita ba, ni tsanar duk abunda ya shafi mallan nayi shiyasa itama ban yi mu'amala mai kyau da ita ba,Ita kuma tayi kishi dani a matsayin wacce ta auran mata miji duka duka zamana ko shekara goma ban yi ba na bar karofi na koma karaye gidan mahaifina ba jimawa shima ya rasu.sai yayana ya Daukeni zuwa cikin Hukumar Dala ta kano inda yake zaune da iyalansa yana kasuwanci. Shi ya rikeni ya rike Usman har ya zama abunda ya zama,A baya shi ba mai arziki ba ne,d'an kasuwa ne mai karamin karfi ammh daga baya ya samu arziki har mun koma cikin garin kano a anguwar mandawari da zama,A hannunsa Usman yayi karatu,tun bayan dawowarmu kano Usman na yawan son ya tuna yar'uwansa da Dangin mahaifinsa,Sai dai ina kokarin shafe Tunanin acikin ransa a hankali a hankali sai abun ya shafe a ransa,Da kuma girma ya kamasai sai dangina suka zame masa komai yaya na shi ya bashi auran Diyarsa Azizatu ya aura a shekarun baya har sun tara zuru'a a tsakanin su,Daga baya Usman ya so ya san wani abu kan Dangin mahaifinsa ni nayi masa iyaka da hakan nayi masa Kaushin muryan cewa in ya kara tambayata garin mahaifinsa ko abunda ya Dangance shi sai na Dagamai Nono, daga Lokacin Bai karamin mganar ba.sai naji dadin haka ammh a raina ina jin ba dadi kamar wani abu mai nauyi ya zauna a kirjina,har ga Allah kiyayyar mallam ce da na sakama raina ta Haifarmin da haka na dad'e ina mafarkai marasa kyau har barci bana samu a Lokacin Dalilin haka yasa na zauna sai nayi Tunanin wannan shine babban laifin dana aikata wanda Allah bazai yafe min ba,nayi mafarki da mallam yana fad'amin na ki had'a kan ya'yansa Allah bazai barni ba.yau da Safe na kira Usman na fad'amai komai a kansa sannan na shaida masa yana da yar'uwa a garin Korafi inda na Haifesa" Ta karishe fad'a cikin kuka Lokaci daya tana fadin"Ku yafe min ya'yan nan wlh sharrin dokin zuciya" Ba wanda ya iya mgana sai ajiyar zuciya na mutanen dake falon Mu ko sai kuka muke kamar yanzu akace Tamadina ta rasu,Baba ati ta gyara zama tana fadin"Ashhha.Shiyasa dokin zuciya ba dadi..Yanzu ina amfanin wannan..?lauratu dai da mallam Hashimu sun bar duniya itama Tamadina Allah ya karbi abunsa ba domin wad'anan yaran data bari ba da yau kin jefa d'anki cikin Damuwa saboda bazai ga wani abu daya Danganci yar'uwansa ba" Goggo tace"Koma dai menene yanzu ya wuce daman chan Allah bai kaddara saduwa tsakaninshi da Tamadina ba,Mu yi hamdala tunda muna da sauran rayuwa.Ga ya'yanta nan data bari shiyasa nace a dauko su su ganka kaima ka gansu Asiya ce kadai bata nan saboda tana nesa" Yana duke a gabanmu kansa na kasa yana sharan kwallah cikin Raunin murya ya dago yana fadin"Naji dad'i da na iske zuru'ar yar'uwata.ku kalleni nan daga yau ku masu gata ne.Bazaku kara kukan maraici ba" Yaya mariya ta dago tana sharan kwallah Lokaci d'aya tana fadin"Kawu.." Da Sauri yace"Ba sunana kawu ba. ABBA zaku rik'a kirana kamar yadda y'yana ke kirana.nayi shekaru da nauyin kirji ina tunanin akwai wani abun da ban isa garesa ba acikin wadanan shekarun ba,na samu wadatar Rayuwa da cigaba nayi karatun addini nayi na boko har matakin Masters,na fara aiki da Hukumar wutar lantarki na jahar kano. kafinMakotan su Baffa sanadiyar gidan kakanin megidana shi chairman ne na babban Headquater refinering and petrochemical,Limited Edo state,Sanadinsa na samu aiki a Nageria National petroleum corporation NNPC,na kaduna wato Kaduna Refinaring and petrochemical company,Nayi auri da Diyar Baffa Azizat,mun haifi yara Hudu babban su shine Abdul'Ahad ma'aikaci ne hukumar sadarwa ta layin Mtn,zai yi aure wattani kad'an masu zuwa sai Nana Fadila tana Lagos tana aure sai Nana Fatima tana Dutse tana aure,Sai Nana khadija dake gabanmu yanzu tana aji daya ajami'ar kaduna ina zaune a anguwan NDC kaduna ina da gida da motar hawa sannan Ina da Rufin asirin da na Dauko mahaifiyata Gata nan Inno muna zaune tare da ita da. Bikin ma da ba ta tafi tare da su Maman Nanah ba,Tana faman da matsalan ido,jiya ne ranar zuwanta ganin likita yasa nace ta tsaya in na kaita ajiyan yau sai na wuce kano da ita sai kuma muka wayi gari cikin wannan al'amarin nan take na kira Direba nace mu Dauki Hanyar katsina bazan iya sukuni ba sai nazo naga Ahalina" Ya karishe fad'a yana kallon mu gabadaya su Goggo suka amsa da Masha Allah. Cikin yanayinsa yace"Ya'yana ku fadamin a inda kuke aure da adadin yaran ku..?ina mazajen ku..?ko dai yake nima ban zo da iyalaina ba. ammh da zarar na dawo daga Tafiyar da zan yi zamu zo gabad'ayan su ku gansu suma su gan ku" Cikin yake Yaya mariya ta fara fad'in sunanta da adadin ya'yanta sannan ta fad'i yaya Asiya sai ni muryata a shake nace"Fa'iza ya'yana hud'u Kabir Amir,Saudatu Anum,Musty da Ahmad Ina aure a katsina" Hafsah kuma karamar mu ce tana wajena shekaran nan ta fara karatu a jami'ar katsina" Cikin gamsuwa ya gyad'a kai yana kallonta kafin yace"Aa Transfer zan yi mata zata koma kasu su yi karatu tare daa yar'uwanta Nana khadija,bazan bari ku yi nesa dani ba bangaran karatu fa baku gayamin inda kuka tsaya a karatun ku ba..? Sai na kasa mgana Yaya mariya tace tayi Nce cikin gamsuwa yace"Meyasa baki cigaba ba Mariya..? Sai ta sunkuyar da kanta sai yayi mirmishi kafin yace"Zaki cigaba insha Allahu ilimi shine mace zan dauki Nauyin karatun ki da komai,su Nana Fatima kowacce sai da ta gama Degree tayi aure Nana Fadila Nurse ce tana aiki da aibitin Gwamnati na garin Lagos" Ni dai na riga na zama mutum mutum ina jin sunayen wasu ahalin namu da bamu taba sani ba,ni ya kallah kafin yace"Ke fa Fa"iza..?a ina kika tsaya a karatun ki..?. Sai na kasa bashi amsa kaina na maida kasa kafin nace"Ban yi karatu ba ni" Cikin mamaki yace"Bangane ba..? Da Sauri Goggo tace"Fa'iza batayi karatun boko ba sai dai na addini,kasan Lokacin rasuwar mahaifin su mun raba su ne a Tsakanimu ta zauna hannun Kabiru ne kafin rasuwarsa D'ansa ma take aure yanzu Haka mai suna Ishaq" Kai Tsaye yace"Aa wannan ba Hujja ba ne. Da za'a barta batayi karatu ba,Ai ilimi ginshiki ne ga y'a mace Dole Fa'iza zata koma makaranta domin ta sake inganta rayuwarta" Cikin rauni nace"ko primary fa ban yi ba,sannan ina da raunin ji" Cikin yar dariya ya Dafa kaina Lokaci d'aya yana fadin"Kada ki damu girma baya hana neman ilimi lesson Teacher za'a sama miki ya koyar dake kafin ki fara shiga makaranta,Mganar raunin ji kada ki damu makafi ma sun yi karatu kuma sun zama wani abu indai ni ina Raye y'ayan yar'uwata bazasu taggayara ba,na ji takaici da ban sameta a raye taji gajiyan dukiyata ba,ammh bakomai tunda ga ku, kamar wani nauyi ne a wuyana kamar yadda Nauyin su Nana khadija ya rataya a wuyana" kai tsaye yake mganarsa Kuma babu tsoro ko shakka,Nan ya rika mana Tambayoyi kan Rayuwarmu muna bashi amsa ya tambayemu muna sana'a ko kasuwanci ne muka gayamasa ni na fad'amasa ina zobo da kunin aya ina Turarekan kamshi. Mirmishi yayi cikin jin dadi yace"Good ina son naga mace da ta iya sana'o'iin hannu.Dakyau Fa'iza zamu inganta wannan kasuwan cin naki' Ban san Lokacin da nayi mirmishi ba,Sai Hira ta tsinke a tsakaninmu shi kuma sai kiransa ake yi a waya ya koma gefe ya sauya harshe zuwa Turanci yana ta mgana mu ko Inno tajamu jikinta tana fadin"Ya'yan nan ban ji kun ce kun yafe min ba..? Dukkanmu muka ce mun yafe mata tana dariyan jin dadi tace"Nagode. Daga yau kun tashi daga marasa kaka kun koma yan gatan Inno.Daga yau ni kakarku ce Baban Nanah Kuma Uba yake gareku Aziza kuma uwa take gareku su Nana fadila kuma yan'uwan ku ne" Wani farinciki ya Lullub'eni daman zan ga wannan ranar..? Ashe mu ma muna da gata bamu sani ba..?Nan Yaya mariya ta kira Yaya Asiya ta fad'amata haka ta dinga Tsallen Murna aka bata Inno suka gaisa Lokacin Abban ya gama wayar aka bashi suka yi mgana mutum ne mai barkwanci da son yan'uwa Yaya Asiya ta kirasa da kawu yace"Sunana Abba.Ya'yana haka suke kira kuma ya'yana ne haka zaku rika kirana. An ce kina kano ai yan'uwanki da maman ku duk suna kano sun je sha'ani nima daganan ni da Inno kanon zamu je zan sauketa ni kuma zan hau jirgi zuwa Porthercourt,muna da Taro ammh da zarar na dawo zan kawo su dukkansu su gan ku,kuma kuga sauran yan'uwan ku" Cikin murna Yaya Asiya tace"Na kosa Abba don Allah ku zo da wuri" Cikin Dariya yace"Kada ki damu ba domin kuna gidan mazajen ku ba, da duka Gidana zan maida ku.ko o a yanzu kowacce da mijinta zata zo da ya'yanta ina son ganin iyalan ku gabad'aya" D haka suka yi sallama da Yaya Asiya duka duka ko awa uku bamu yi ba tare ba, ammh mun saba da juna ji muke yi kamar in ya tafi bazai dawo ba,kamar bazamu kara ganinsa ba,Sai dai ana ta kiransa jirgin karfe hudu da rabi zai hau a kano shiyasa suka yi shirin Tafiya idanuwan mu ya ciko da kwallah ya rike Hannayen mu yana fadin"Kada ku damu da zarar na Dawo daga tafiyar da nayi zamu zo sai kun gaji da ganinmu kuma zan tafi daku gidana kuje ku yi min sati d'aya na san komai akan ya'yana suma susan komai a kaina" Bai zo da komai ba Saboda tafiyar Gaggawa ce kud'i ya zube mana da bamu san nawa bane Direba ya kawo su da wata bakar Jeep dankareriya,Su Baba ati ma ya cika su da kudi da Sallaman yana dawowa daga tafiya da shi da iyalansa zai dawo,Inno ma tana ta sallama da alkwarin wannan karon zumunci an fara kenan har Abada,kafin ya tafi ya karb'i lambobin mu har da na Yaya Isa,mune rakiya har bakin mota da zai shiga mota ya dafa kan Hafsah yana fadin"Auta sai na dawo ko.?domin kece auta Nana Khadija zata girme miki,Zamu dawo in sha Allahu bayan Abba har Babban Yaya ma kuna da shi" Da haka muka yi sallama suna d'aga mana hannu muna daga musu hannu,Cikin gida muka koma ana ta maida zence Goggo ta kallemu tana fadin"Kunga abun Allah ko..? Allah ya nufa ganawar sai a wannan lokacin ne" Yaya mariya tace"Naji dadi Goggo naji Dadi yau naga wani ahali daga Ahalin Tamadina murna kamar zata kasheni" Ta fad'a cikin farinciki Hafsah kuma ta Daka Tsalle tana fadin"Abba yace ni ce auta kuma muna da Big bros muna irin na ya'yan yan gayu" Ni dai sai faman washe baki nake yi farinciki ya gama cikani Yaya Asiya ta kasa zama sai kira take muna bata labarin abunda ya faru,Murna kamar me tace itama cikin  Satin nan tana Tafe su Baba Ati sun koma gida da Tarin alherin Abba garesa muma kudi ne sun fi dubu dari ya zube mana,Goggo ko kwandala bata Dauka ba sai muka raba a tsakanimu,nan mukayi azahar da la'asar saannan muka tafi ni da Hafsah muna masu Farinciki ko da muka koma gida yara sun dawo makaranta Mama abun mamaki ita ta dafa musu Taliya Jallop muna shigowa Musty da Ahmad suka zo suka makaleni suna kiran Umma Umma daman nayo musu Tsaraban su Chaculate,Dakin Mama na fara shiga na gayamata na dawo ganin yanayi na fara'a yasa ta kalleni kafin tace"Ina fatan su Goggon lafiya..? Cikin Tsananin Farinciki nace"Lafiya lau Mama. Daman Abba ne yayan Tamadina ya zo yau shine goggo ta saka aka daukomu" Mama sai ta kasa gane kan mganar Cikin Mamaki tace"Bangane ba Wani Yayan tamadinan..? Cikin zakwad'i na fara bata labari Cikin karin mamaki Mama tace"Ikon Allah ashe tana da dan'uwa kuma shima yana da iyalansa..?. Kai tsaye nace"Sosai ma don ma tafiya ta kamasa yanzu, iyalan nasa kuma suna kano biki ammh yace da zarar ya Dawo zasu zo gabad'ayan su ganmu mu gansu muma..," Sai Mama ta kasa mgana mamaki duk ya cikata Dakina na shiga Anum ta tare ni tana fadin"Umma nayi miki wanke wanke." Amir kuma ya amsa min da cewa"Umma nayi miki shara" Ina dariya nace"Allah yayi muku albarka ya'yan Umma" Ahmad ke dane kafata yana neman kadani na murde kunnensa ina fadin"Umman zaka kada ko..? Sai ya fara Dariya Musty na tayashi,Kan kujera ta na fada ina Sauke Hijabin Jikina Hafsah ta shige Daki Amir har ya shiga kitchen ya zubomin abincin Ya kawo min kenan yana fadin"Umma ga abinci na kawo miki ruwa..? Kafin nayi mgana Anum ta Ruga taje ta Daukomin ruwan na karba ina fadin"Amun di'na ta zama yan mata fa" Sai ta rufe fuska wai kunya ina ruwan Anum,Mama ce ta kwalama Amir ya kira ya fita sai ga shi ya Dawo da kudi wai cinikin zobon da akayi bayan ba na nan mamakin Mama ya kamani itace har da siyar min da zobo..?ban dai ce komai ba sai da na Huta naci abinci na leka nayi mata Godiya bata amsani ba,Ranar cikin Farinciki muka karishe yini,Yaran har sun Fahimci ina cikin farinciki sai da Amir yace"Umma kina ta dariya ko kin samu kudi ne..? Dariya na saka ina mamakin wayon Amir yasan dariyata yasan Bacin raina,Kansa na shafa ina fadin"Sosai Amir, ammh ba kudi na samu ba abunda yafi kudi Daraja da Tsada na samu"Amir na mirmishi yace"Umma menene shi..? Cikin bayyana Murnata nace"Zan gayamaka kaji" Daganan sai ya bar mganar,Bamu yi mgana da Yaya Ishaq ba,sai washegari ban gayamasa ba ammh yanayin murna na sai da ta bayyana a waya sai da yayi min mgana yace"Fa'iza hala yau an kwashi cinikin zobo da kunin Aya ne kwasha kwasha naji jiki cikin Fara'a.? Dariya ya bani har sun Fahimci in na samu kud'i ina murna sosai ban gayamasa ba na bari sai ya Dawo kwana Biyu Tsakani sai ga shi ya Dawo,ban kai ga ma gayamasa ba Har Mama ta rigani sai da daddare yake min mganar na kallesa ina da'gama masa kai alamun hakane cikin kallona yace"Na tayaku murna.." Cikin farinciki nace"Mungode..Yace ai in suka zo har kai yana son gani" Cikin mamaki yace"Ni kuma..? Lafiya kuwa..? Sai na girgiza kai ina fadin"Ban sani ba ya dai ce dukkan mu yake son ganin mazajen mu" Daganan sai bai kara mgana ba,nima ban kara cemai komai ba kudin hannuna Jarin zobo na da kunin Aya na kara,Sannan nayi Humra makotan mu wata Amarya ta bani na yi mata,har da kwallacha. Kwana Takwas da zuwan Abba Ya kira Hafsah yace gobe shi da duka iyalansa,Daman su Nana Fadila Daga biki basu koma ba ya Tsaida su yace sai sun zo anyi zumunci Yaya Asiya daman ta kwana Biyu a karofi,Murnan kamar zan zuba ruwa a kasa nasha,Har chan karofi ya kira Goggo ta saka aka gyara bangaran Hajiya na gidan Yaya isa inda za'a sauke su,sai kuma mganar abinci Matan Yaya isa da Yaya Salisu zasu ji da komai,Ga Yaya mariya da itama mun yi waya tace zata shirya musu abinci mai da rai da lafiya ni kuma nace zan yi zobo da kunin aya na Taho dashi a goben dani da yara da Yaya Ishaq da sai da Daddare na fadamai. Yayi shuru kamar bazai yi mgana ba sai chan yace"Allah ya kaimu goben" Mun yi zencen da Badariya da yake ta dawo shekaranjiya tace itama zata je kawai da Safe sai Yaya Ishaq ke fadamin Mama ma tace zataje ban yi mamaki ba araina nasan zataje ganin komai ne,kenan duka gidan zamu tafi,Itama Yaya Asiya mijinta aranar zai kamo Hanya da sauran yaran ni ma dani da iyalaina,Har girki sai da nayi jallop din shinkafa mai rai da lafiya da taji kayan lambu da nama nayi zobo da kunin Aya mai yawa,Na daukan mana kaya tunda dawowa badai ranar ba Kulle gidan mukayi,Tashar Mota Ishaq ya samo mana har kofar gida,Karfe d'aya da wani abu muka tashi Hafsah suna ta mgana da Yaya mariya har da Abban sun yi mgana yace Tafiyar ta su ta Motace,suna hanya sun Tsaya su yi sallah ne ammh sun kusa karisowa Mun isa karofi Biyu da wani abu na rana, gida cike su Anum nata murna sun zo Karofi,har alokacin basu iso ba ammh sun ce sun shigo katsina suna gabda karisowa. Yaya Asiya ta fimu murna saboda ita basu taba Haduwa ba ammh mu kanmu murnan ya cikamu,Yaya Isa da su Yaya ishaq da mazajen su Yaya mariya suna kofar gida,mu kuma muna cikin gida muna Dakon zuwan su. *Janafty"* *KNKB2013* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Wajen misalin karfe uku na rana mukaji diran motoci da Hayaniya daga kofar gida,mu muna cikin gida sai muka kasa zama muka mimmike kan kafafun mu,muna masu kurama kofar falon Goggo ido domin ganin masu shigowa. Yara ne almajirai daga waje suka fara shigowa da jakunkuna da akwatina, sai kuma bayan su wasu fararan yara kyawawa mace da namiji suka shigo mace iyakar ta sa'ar Anum namijin kuma kamar Musty ne,Da gudun su suka shigo daidai Lokacin suma su Anum sun kwasa aguje zasu fita waje sai suka had'e da yarinyar nan,Tsayawa suka yi suna kallon juna kamar susan juna sai kuma dukkansu suka washe baki suna Dariya Anum tace"Laa..Ke.." Itama yar yarinya sai tayi dariya sai da Kumatunta suka loba kafin tace"Kema kinsan Gidan nan ne..? Sai gabad'aya mamakin su ya kamamu kafin mu samu mu fita daga mamakin Ina Anum ta san wannan yarinyar mai kyau da ita,sai ga wasu mata Farare yan gayu sun biyo bayansu,da yi sallama sun shigo d'ayar Babar itace ke dauke da karamin yaro a Hannunta sai d'ayan da bata kai ta Tsawo ba tana rike da jakunkunansu na Hannu da wayoyinsu dukkansu Bakin less ne mai adon pink ajiki da mayafansu, a kallo farko in kayi musu zakasan yan gayu ne sannan masu ilimi ne da Nasaba mu dai muna ta bin su da maraba ji kawai ka ke yi ana"Maraban ku." Sannunku da zuwa" Goggo kuma ita ke faman fadin"Maraba da baki maraba da bakin mu" Suna amsawa cikin sakewa lokaci daya suna kallon mutanen dake falon bayan su kuma wata matashiyar yarinya ce tsawon Hafsah inaga itace Nana Khadija itama kayanta iri Daya da na yan'uwanta,tana tafe da wata karamar jaka ta mata a bayanta,Daga ita sai ga wata Farar Mata ta bayyana Tare da Inno dukkansu cikin Fara'a mu dai bakin mu bai daina kiran musu sannun su da zuwa ba. Gabadaya waje suka samu suka zazzauna,Yaya Asiya tayi ma Inno barka da zuwa data zauna a kasan Cafet ta mike kafa Saboda gajiyan zaman mota.ta kalleta lokaci d'aya tana fadin"Mariya ce ko.? Kan Yaya Asiya na kasa tace"Aa Asiya ce" Sai Inno ta rike baki tana fadin"Asiya..Sannu Asiya kece bamu had'u wanchan zuwan ba,ba shakka Allah ya jikan Hafsatu da rahma" A ka amsa da Ameen Nana khadija tace"Don Allah ina so zan shiga toilet"ina kusa sai na kalli Hafsah ina fadin"Hafsah rakata" Sai Hafsah ta mike tace tazo ta rakata ta mike suka shige bedroom kowa ya bisu da kallo gwanin sha'awa. Yar farar matar nan tace"Inno lalle Jini d'aya ba wasa ba, kinga Nana khadija kamar ta da wannan yar sa'arta ta ta, hala tana cikin ya'yan da marigayiyar ta bari ne..? Inno tace"Itace Auta Hafsatu kenan. Ga Asiya nan itace Babban su sai Mariya sai Fa'iza gasu nan kun gansu ku bari Shi Baban Nana ya shigo shi da Abdul'ahad zaku ji sauran bayanin" Daganan Goggo tace ko zasu yi sallah sukace sun tsaya a bisa hanya sun yi sallah,Sai dai aka fara kokarin gabatar musu da abinci Farar matar nan da daga ganinta itace mamansu tace"mu fa ba baki ba ne mun tsaya a inda muka yi sallah mun ci abinci zamu ci anjuma mu da mun zo kenan sai mun gama Zaga dangi gabad'aya ai abinci sai kun gaji da Dorawa kuna saukewa ko Inno..? Tafad'a cikin barkwanci Inno tace"Kwarai kuwa" Goggo tayi Dariya kafin tace"Ina shi Alhajin bai shigo ba..? Inno tace"Ya tsaya da mazan dake waje" Bata ma gama rufe baki ba sai ga su sun shigo,Yaya Isa ne yayi musu jagoranci,Abun mamaki da zugan yaran nan su Amir kamar sun san shi Bayan shi kuma wani zankaded'en Saurayi ne kamar shi, sai dai shi Saurayin fari ne sannan ya fishi jikin Murjewa,suna shigowa yaran na biye da su zuga guda Maman Nana tayi dariya tana fadin"Baban Nana baban yara kenan" Baya ya juya yana fadin"Ina ya'yan nawa..?ku shigo mana ku ai ba surukanta zamu yi ba,Duk ya'yana ne ku ku shigo nan ai duk mun zama Daya" Sai ga su Yaya ishaq sun shigo da mijin Yaya mariya da na Yaya Asiya sai Yaya Salisu waje aka basu suka zazzauna aka shiga gaisawa da tambayan Hanya,sannan muka tashi dukkammu muka durkushe a gabansa muna gaisheshi ya amsa bakinsa har kunne ya saka hannuwansa Biyu ya Dagomu yana fadin"Ku tashi ku zauna ya'yan Abba" Gabadayamu muka zauna a gabansa yabi mu da kallo kafin ya yi mgana Yaya Asiya ganin yana kallonta yasa tayi Saurin cewa"Asiya ce Abba' Gabadaya sai da akayi dariya shima Dariyan yayi yana fadin"Zan kama sunan sai kika rigani Ase ase ya gida da yaran..?kanta na kasa ta amsa mai sai ya fara waige yana fadin"To ni jikokin nawa yawa ne dasu kai yara maza kowa yaazo wajen mamansa mu gani"Kamar suna jira kowannen yazo ya rabe jikin uwarsa Anum har da kwantomin saman wuya rad'a take so tamin a kunne ban jita ba. Abba ya kallemu ya kara kallonmu sai ya juya yana kallon Inno Lokaci d'aya yana fadin"Alhandulillah yar'uwata ta bar min zuru'a inno" Inno ta gyad'a kai tana fadin"Ba shakka nima ai duk ta kara min yawan magidanta da kishiyoyi" Abba na Dariya yace"Inno Maman Nana sai dai tayi hakuri Kishiyoyo gareta Rututu ba adadi" Maman Nana ta washe bakinta fararan Hakoranta suka bayyana Lokaci daya tana fadin"Bakomai ban damu ba dad'in abun ma duk na Roba ce nice dai uwar Nana ta karfen" Gabadaya dariya akayi daga ganinta itama akwai barkwanci su Mama na gefe suna Dariya Saurayin ya dago ya kallah yana fadin"Babban yaya ta kanka zan fara fa" Mirmishi yayi mai kayatarwa kafin yace"Girman ka ne Abba" Badariya ta kara kallonsa ita tun shigowarsa taga kamar ta san shi, sai dai ta kasa tuna a ina shi kuma bai ma Lura da ita ba D'aya bayan d'aya ya fara Gabatar da mu kafin ya karishe da fadin"Duka wad'anan kannenka ne nauyi ya kara hawa kanka Babban yaya.kamar yadda kake tafiyar su da Nana Fadila haka zaka tafiyar da su ya'yan yar'uwata da na baku Labarin bamu had'u ba har Allah ya Dauki ranta wad'anan sune iyalan data bari" Cikin gamsuwa yace"In sha Allahu zaka sameni mai kulawa da kannena kamar ko yaushe" Jinjina kai yayi kafin ya Kallemu yana fadin"Fa'iza Asiya,Mariya da Auta ga yayan ku nan sunan sa Abdul'Ahad zai yi muku Jagoranci kamar yadda zan jagorance ku, ku gaisa da shi" Daya bayan d'aya muka rika gaishe shi yana amsaawa cikin Sakewa kafin Abba ya yafito Nana Fadila ta matso kusa da shi Tana fadin"Na'am Abba." Cikin Dattakonsa ya nuna mu yana fadin"Ga yan'uwanki nan.Kinga Asiya itace kamar age mate din ki to ki riketa Amana ku zama kamar yadda kike da Nana Fatima" Cikin gamsuwa tace"In sha Allahu Abba"Nan itama muka gaisa ya yafito Nana fatima ya gabatar mana da ita yana fadin"Ga age mate din ki nan Fa'iza ki kula da ita kamar yadda zaki kula da Nana khadija tana da raunin ji Hallita ne haka aka haifeta ki kula da ita"Da sauri ta rike Hannuna tana fadin"Ni daman Abba ina ganinta naji ina sonta"gabadaya sai akayi Dariya Abba ya Kira Nana khadija da Hafsah ta Dawo rakata Tiolet ya had'a su da Hafsah sai Yaya mariya taga an wareta Cikin damuwa tace"Abba ni wa zaka damka ma Amanata? Yana dariya yace"Amanarki tana hannu nagari D'iyata. Maman Nana ga wata amanar na kara miki Dukkansu ya'yanki ne kamar su Nana fadila ki zama uwa tagari garesu kamar yadda na sanki kada ki kara bari suyi kukan maraicin rasa uwa" Da Sauri ta Gyada kai Lokaci d'aya tana jawo Yaya mariya ta Rumgume tana fadin"In sha Allahu Baban Nana,Mari babban kifi rabu da wad'anan yaran ke da uwa kika samu sukutum ga Abdul'Ahad da zan saka yafi shagwabaki" Yana dannan wayar sa yace"Itace fv sister di'na ma daga yau Ammi" Nana Khadija ta shagwabe fuska tana fadin"Kai yaya ni din fa..?. Yana tabe baki yace"Kin zama tsohon yayi"Sai dariya gabadayanmu Farinciki ya samu muhalli a zukatanmu Abba ya gabatar da su Baba ati ne a matsayin Goggon su kad'ai data rage mu su sannan ya gabatar da Maman Nana a matsayin matarsa uwar su Fadila sai su Goggo a matsayin Dangin mahaifin mu. Badariya ya gani ya nunata yana fadin"Wannan fa ban ganeta ba..? Da Sauri nace"Kanwar mijina ne Badariya Abba" Cikin gamsuwa yace"Itama ya'ta ce sannu Badariya"kanta na kasa ta amsa tana gaishesa sai lokacin Abdul'ahad ya lura da ita ammh shi karon farko ya gane ta,har Hoton wayarsa ya Dauko yana gani to ai dolensa ya ganeta duk kan Hoton Raly dake wayarsa rabin sa tare da wannan kawar nan tata take yi, in bai manta ba sunan  kamar Badar sunan ta, in suna tare wani Lokacin har gaisawa suna yi ta kalleshi shima ya kalleta ammh ganin kamar bata ganesa ba sai shima ya basar. Yaran duka Abba yasa muka yi masa bayaninsu,muma muka tara su wajen shi muna fada musu Abba ne su gaisheshi Amir ya karisa ya gaishe shi ya Dagosa yana fadin"An ya Fa'iza bazaki bani abokin nan nawa ba yaron ya burgeni akwai natsuwa sosai' Ina dariya ban yi mgana ba Da Sauri yace"Kada ki damu in dai bangaran megidan  ne ke da shi Duka ya'ya ne ina da iko a kanku da ya'yan ku gabadaya"Nana Fatima na gefe tace"Allah ya bar mana Abba" Nana Fadila da Inno na tayata Dariya shi bai ma jinsu ba Hankalinsa na wajen Anum kuke tana faman tambayansa"Kai ne Abban Umman mu.?ya gyad'a mata kawai sai ta kalleni tana fadin"Umma ba kin ce Baban ki ya rasu ba har muna addu"a ba? kafin na samu amsar bata ya amsata da cewa"Wani Sabon Abba ta samu ke kuma kin samu sabon megida ko bakya so na..?.sai su Anum aka noke kai ana dariya kafin tace"Ina sonka mana ammh sai na girma zamu yi aurre"Gabadayanmu muka saka Dariya Ammi tace"Kaji min yarinya Daga haduwa sai fashin miji"Abba ya Dora t saman cinya yana fadin"Maman Nana dai ana ta kishi"Sai dariyan barkwancin su muke yi, Sai yarinyar da suka fara shigowa naji Nana Fadila na kiranta Falaq,ita tayi ma mamanta Rad'a a,kunne sai ta Dago tana kallon Anum kafin ta kalli Ammi tana fadin"Ammi Kin ji Falaq tace Anum tazo bikin uncle Junaid ta ganta a gidan Anty Laila" Sai kallo ya koma kan Anum tana jin haka jikinta na rawa tace"Nima na ganta"Sai mamaki ya kamani Ammi tace"Haba ni fa ina ta yi ma yarinyar nan kallon Sani sai da Falaq ta fad'a na tuna kunga yara da rashin mantuwa ko..? Nana Fadila tace"Ko ita ce Anum d'in da kika Dameni da zencenta da kika koma gida.?sai yarinyar ta Daga kai sai mamaki gabadaya ya kamamu Abba yayi mirmishi kafin yace"To yara dai sun san juna sai aji ta ina aka haihu a ragaya" Ammi ta kalleni tana fadin"Fa'iza ko har dake aka zo bikin Lailan ne bamu hadu ba.?Laila ta kaduna..? Sai alokacin na tuna bayan Amir yayi zaraf yace"Umma Anty Laila da take zuwa ita da Anty Raliya" Da Sauri nace"Laila..Oh na tuna ta Aa Anum kad'ai taje bikin ita ta roki babanta ya barta suka tafi da ita"Sai da ake mgana Badariya ta tuna inda tasan Abdul'ahad da Sauri ta kallesa tana fadin"Abdul'Ahad right.? Sai ya jinjina mata kai yana fadin"Yes Badar ko..? Sai ta fara Dariya kallo ya koma kansu ta kalleni tana fadin"Anty Fa'iza kinsan waye..?wanda zai auri Raly ne fa."sai na bude baki ina fadin"Raliyar ki.?sai ta gyada min kai sai na kasa mgana Ammi tace"ikon Allah kusan Raliyar da Abdul'ahad zai aura kenan..?kusan Hajiya Aisha Saulawa kenan? Kai tsaye nace"Nasan ta sosai akwai zumunci a tsakanina da ita da ahalinta. Raliya kuma yar gidana ce Aminiyar badariya ce, kanwar mijina" Sai mamaki ya kama kowa,Ammi ta bude baki kafin tace"Ke Fa'iza ba dai ke bace mai Turaran kamshi na Katsina ba..? Sai ta bani dariya na gyad'a mata kai lokaci daya sai na Tuna da Sauri nace"Ba dai ke ce yayar mijin Laila da na hada turare humra da Kwallacha wajen ki ba..? Sai ta fara Dariya tana fadin"Baban Nana diyar taka fa sananniya ce. Ba shakka ina turaren da nace maka naga Amaryan junaid dasu masu kamshi na tambayi inda akayi mata tace Daga katsina kawar mamanta Hajiya Aisha ta bada akayi mata?ka manta har kana min tsiya shegen son kanshi bazan iya siya a kaduna ba sai na lula har katsina..? Sai ya daga mata kai yana fadin"Duk na tuna"Da sauri tace"To ai di'yar kace mai hadawan Allah mai iko sannu Fa'iza" Sai kallo ya koma kaina Nana Fatima tace"Ammi wai turaran da na sace din nan da nazo duba Inno..? Dakuwa tayi mata tana fadin"Asirin ki ya Tonu kaga barauniyar gidan ka Baban Naana ina fad'an an dauke min Turare kace baka da barawo a gidanka to wannan fa..? Gabadaya dariya muke cikin Had:e rai yace"Yayi mata kamshi ne ta ara ko Nana Fatima..? Da sauri ta daga kai Lokaci daya tana fadin"Fa'izata zata sake had'amin nawa Ammi na dibar miki" Dakuwa ta sake yi mata tana Dariya AbdulAhad na dariya nace"Nana Fatima kamar itace mujaheed d'an sandan farin kayan wajen Lauya mgana" Abba yace"To Za'ayi mata taron dangin abun kuma ma nasu ne.daman haka abun yake ba gashi da aka had'u ba yara suka fara shaida da juna ba" Nan fa falo ya kaure da Hira suma basu da bakunta sun saki jiki suna ta Hira damu,Ammi ko ta shige cikin mu ba ruwanta Inno dai Goggo tajata Daki don ta Huta Mama ba baka sai ido ta zama kamar mujiya afalon da na gabatar da ita a matsayin uwar miji na, cikin girmamawa Abba ya gaisheta sau taga ba ma raina gorin asalin datake yi min sai da ta raina kanta da taga Abba da Ahalinsa. Abdul'Ahad kuma na gefe ya Kira Raliya sun yi mgana da yace ga wata su gaisa sai ya bata Badariya tayi matukar mamakin inda suka Hadu sai Badariya ta bata labari tuni ta bazama Dakin Hajiya tana gayamata yadda komai ya wakana Daman tun a satin Abdul ya gayamata zasu zo katsina wajen dangin mahaifinsa tana ta mamakin daman su ba yan kano ba ne..?sai yace eh asalin Babansa haifaffan garin karofin katsina ne. Abba da shi da yara aka barsu suna ta Budiri da kuma mazan su Yaya Ishaq kowannen ya gabatar da kansa garesa,Duk rashin sakin jikin Yaya Ishaq ya saki jiki da Abba Saboda yana da Dadin zama sallar la'asar ya fitar da mazan zuwa masallaci mu kuma muka yi namu acikin gidan yaran kuma tuni sun hade kansu suna wasa. Bayan an dawo sallah ne aka zauna zaman cin abinci,su Abba a kofar gida suka baza musu tabarma suka zauna mu kuma muna cikin gida,Girkina aka ci daga karshe zobo da kunin Aya har ana Fada da Nana Fatima da Nana Khadija Goggo na Dariya tace"sai kun gaji da sha duk sana'ar yar'uwan ku ce gatan  nan Fa'iza" Ammi ta saka salati tana fadin"Allah mai Hikima sannu Fa'iza kai masha Allah"tana sha itama tana santi hakama abinci da akace ni nayi ta kalleni Lokaci d'aya ta kalli goggo tana fadin"Goggo Fa'iza yar baiwa ce gaba da baya fa ba'a sani ba" Nana Fadila ne ta kara mata jaka a baya da sunan waigi ta ko mako mata Dakuwa suka koma gefe suna Dariya,ashe suma mazan sun yi santi sai da Daddare bayan an sake Taruwa a tsakar gida ciki zafi ga ba wuta ana Hira Abba yace"wacce cikin ya'yana tayi shinkafar nan mai dan karen dadi? Da sauri Nana Fatima tace"Abba Fa'iza ta ce"Nana fadila tace"Ji bakinta Fa'izan mu dai malama ai bataki ke kad'ai ba ce" Sai suka fara gaddama muko murna da Farinciki yaki barin mu,Abba ya  raba rigiman da fadin"Naji fa'izan kowa da kowa ne shikenan" Daganan sai ya kashe mganar ya kalleni yace"Fa'iza komai da ruwan ki kenan..?masha Allah Allah yasa albarka" Aka amsa da Ameen sai ya kalli Ishaq dake dauke da Ahmad Lokaci da'ya yana fadin"Ishaq ka yi dace gaskiya zaka karamin Sadaki saboda wannan girkin da zobon data kware akwai cikon Sadaki" muka saka dariya gabadaya Ammi tace"Baban Nana zaka zama surukin zamani ne..? Da Sauri yace"Daman nace miki ni surukin da ne..? Yadda yayi mganar ne ma Dole sai da mukayi Dariya Allah Sarki Rayuwa daman haka Allah ya kan shirya lamuran bawa, sai kusan sha Biyu su Abba suka tafi masauki bangaran da aka  gyara musu ,Mijin Yaya mariya gida ya koma ya kwana kuma shi ya sauki su Yaya ishaq a gidan iyayansa Dakin kaninsa shi da mijin Yaya Asiya muko duka nan gidan goggo muka kwana har da Mama da Badariya mu da yan'uwan mu raba Dare mukayi muna Hira kamar mun shekara tare Nana Fatima na zama Fa"izanta abu kad'an sai kiji tace"Fa'ina kaza kaza" Ita ya'yanta Biyu,Jidda da jalil kanana ne,Saboda sai da tagama Service dinta tayi aure Nana Fadila ke da uku FalaqFahad,Da Fairuz,Yadda kuka san mun dade da sanin juna saboda yadda muka shaku daga Dare zuwa Safe suma suna da Tarbiya daidai gwargwado Ammi ta basu tarbiya itama irin Abba ne akwai barkwanci. Da Safe ni suka yi ma chaa na shiga kitchen nayi musu abun karyawa da su Yaya isa suka jifgo cefane,ko wajen karyawan har sai da akayi santi Tunda nan mazan suka zo gidan Goggo aka had'u aka karya gabadaya. Yaya Abdul'Ahad na shan ferfesun kayan ciki da nayi musu ya kalleni yana fadin"Ina fatan kina koya ma Raly irin wannan girke girken ko? Sai Falon ya kaure da Dariya Ammi tace"Baban Nana saka ma d'anka waigi shima Cikin Dariya yace"Ammi ba fa santi nake yi ba" Abba na gefensa yace"My son yi santin ka dadi'n abun ba kai kad'ai ba ne har da Baban Nana shima yayi santin"Kai Abba akwai ban dariya Ammi tace"Baban Nana kasan wa na ke tunawa in na samu abinci mai dadi haka..? Yana shan tea ya zuka ya dawo da mug din yana fadin"Engr.mana" Cikin gyad'a kai tace"Wlh shi ke fad'omin rai kasan shi da son abincin Hausawa na gargajiya da na zamani." Abba yace"Ki bari musamman ace ya samu zobon nan na Fa'iza da shi da Maltina ko coke har abada,kinsan ya tsani lemukan ba gwamgwani ko da yaushe korafinsa Baban Nana duk kayan basir ne zakin su ya yi yawa" Ammi tace"Allah sarki Engr kamar ba Jinin yarbawa" Abba yace"To ai kinsan ya sirka ta bangaran Hajiya Shukra shiyasa zaki ga rabin sa bahaushe rabinsa bayarbe ba, ba domin ma ya tashi cikinsu ba sai in akace miki ya had'a iri da yarbawa sai ki karyata"Ammi tace"Nima ka manta ganin farko da nayi masa sai da na karyata" Abdul'Ahad na gefe yace"Abba kana ji da Engr nan Sosai" Abba yace"Mutum ne har da rabin mutum..Ya yi min abunda bazan taba mantawa ba yayansu.Engr ya goya mutane Dabam dabam irina da yazama madubin su kirkinsa nake fada'maka sai ka zauna da shi zaka san hakan" Abdul'Ahad ya jinjina kai bai ce komai ba,Abba da Ammi suka cigaba da mganganunsa kan Engrn da su,suka  san shi. Haka dai muka gama karyawa cikin Nishad'antarwa da Annshuwa,ranar a gida muka yini ana ta hira sai yammah muka fita Lokacin Yaya Ishaq ya koma gida shi da Mama da yara wanda Dakyar na samu Anum tabisa da ta saka rigiman bazata ba nace bata isa ba makaranta,Badariya na tare dani sai gobe zamu koma katsina Tunda suma Jibi zasu tafi saboda ayyukan su Abba su, suNana Fadila kuma zasu koma gidan mazajen su. Da yammah Karofi muka zaga har gidan su Tamadina da yazama duk ya rushe Abba yace zai saka a bige shi a gyara zai zama nan zasu rika sauka in suka zo,Baba Ati kuma da ita zasu tafi zata zauna tare da Inno a gidan Yaya mariya muka kai wajen goman Dare,Muna ta Hira, washegari kafin mu wuce Katsina sai da muka biya Dutsemah gidan da Tamadina tayi aure har da Abba akaje sun gaisa da mutan gidan da shi kanshi megidan suna ta fadin irin Hallayar ta madina Abba ya cika su da kudi muka bar su,suna kwallah muma muna yi Daganan muka rabu da Abba,ya koma karofi,mu kuma Direban Abba ya kaimu har katsina da Abdul'ahad shi ya rigamu yin gaba wajen Raliya yaje ,Gidana muka sauka Nasan ko ban fad'a ba sun ga yanayin gidan susan muna da karamin karfi,Nan muka ci abinci mukayi sallah mun iske Anty Binta a gidan sai kallon su Nana Fadila take da ya'yansu taga ba ma raina a wajen su,sai la'asar na rakasu gidan Hajiyar Raliya har da Ammi,inno na gidan goggo tace bata iyawa kafa ciwo Hajiya taji Dadi ta karbemu hannu goma kamar yadda ta saba. Ammi ta kalleta tana fadin"Hajiya ashe ya'ta ce ma ke turarukan kamshi bansani ba..? Hajiya na dariya tace"To ba gashi yanzu kin sani ba! Ammi tace"Wlh ai naji dadi kamshi har karkashinn Gadon Baban Nana insha Allahu" Gabadayamu sai da muka Dara Raliya nata kunyana nace"Ni daman ai Antyn Raliya ce, ba kunya Tsakanimu Hajiya nata mamakin lamarin na zauna nayi mata bayani atakaice tace ikon Allah kenan itama Raliyan a bikin Laila suka had'u da Abdul'ahad duk da daman an san suna sanadin Iyayan Laila.sai dare muka baro gidan Hajiya da Sha tara na arzikin da ta hada mana, adaran suka koma karofi Washegari kuma suka koma gida Saboda a ranar Nana Fadila da Nana Fatima zasu koma gidajensu. Kafin rabuwar mu Abba ya Tattauna damu kan abunda muke bukata sai muka kasa mgna sai yace bakomai Ko mazajen namu da bai samu zama Sosai da su ba, saboda ba Lokaci ammh zai gayyace su har gida su Tattauna mun raba ma junanmu Lambar wayanmu,Kwana uku muka yi tare kamar mun shekara tare Basu kyamace ni ba, duk rashin son mutane na, na shaku da su Nana fatima mutane ne masu karamci ilimi waye kudi da nasaba da sanin ya kamata.yaya Asiya ita yar gida ne Ammi yar kano ce Haifaffiyaa Dala ta kano,kuma daman ga bikin Raliya dake gabatowa mun zama iyalai D'aya kaduna zata yi diban manyan baki. Badariya da Raliya sun fi kowa murnan wannan al"amarin,Ko Yaya ishaq sai da ya yabi kirkin Ahalin Abba gabadayansu. Kuma kowa ya gansu yasan suna da kudi kuma sun taki gwamnati,Abba kamar yadda ya fada tare da Baba Ati suka koma Inno nata jin Dadi ta samu abokiyar zama tuni har Abba ya damka ma su Yaya Isa kwangilan gini an fara baje gidan ana sake sabon Faundation. Sai da nafi sati ban koma da sana'a akan zobo da kunin aya na ba,Saboda rashin zamana waje d'aya,Muna yi da waya su sosai barin ma Nana Fatima har megidanta data koma sai da ta bani muka gaisa,Kowa ya ganni yasan na samu natsuwar zuciya da kwanciyar Hankali muma mun zama yan gata abu kad'an Abba yace me muke so..?Hafsah ta zama auta kowa ita yake riritawa yanzu haka ta kosa su samu Hutu ta gudu kaduna gidan Abba tayi Hutun ta achan. Sati daya tsakani da zuwan su Abba ranar da Daddare muna zaune Yaya Ishaq yakalleni yana fadin"Abban ku aikin me yake yi? Tunani nayi kafin nace"Na manta kamar ko a NN Me naji su Yaya Asiya na mgana? Sai Yace"NNPC dai ko..? Sai nace"To kila nan din ne".kai ya jinjina kafin yace"Akwai kudi gaskiya babban ma'aikatan matatar mai ne fa" Ni dai ban ce mai komai ba, ammh kowa yaga Abba ai yasan ba karamin mutum ba ne. Acikin watan Abba ya kira kowannen mu a waya kowa ta fadi abunda take so ni dai jari nace ya karamin yana Dariya yace"To Fa'iza aammh ai ni burin gina miki katon gidan abinci nake da shi, tare da shagon gyaran jiki da kayan kamshi"Sai na Bushe da Dariya ina fadin"Allah ya amsa Abba" Dubu dari biyu ya turamin yace na rike a hannuna kafin yaga abunda Allah zai yi Dukkammu haka yabimu ya bamu kuma yace zai kira duka mazajemmu ammh sai yaje warri ya Dawo  warkshop din da zasu je suyi na wattani biyu in ya Dawo zai nemesu,Sannan ya aiko mana da kayan sawa dukkanmu mu da yaranmu da mazajen mu,abun sai wanda ya gani da wad'anan kudin na cigaba da Rufamana asiri,sannan gefe daya muna waya da su Nana Fatima muna tsara shiryen shiryen Bikin Raliya da aka matso da shi kusa,Da sai bayan wata hudu za'ayi yanzu kuma an maido da shi bayan wata biyu Saboda Yaya Abdul'ahad zai tafi kasar waje karo karatu kuma da matarsa zai tafi. Mama dai kam kamar bata gidan ko motsinta ba'aji ta daina shiga duka Hurumina,sai dai bansan tsakaninta da Da'nta ba,Anty Binta kuma tana ta Hidiman auran Halisa ba'a cika ganinta ba,Mganar aiki kuma shuru kake ji sannan har Abujan Mahaifin zainab ya kirasa ya koma ammh ba wani Labari. Sai daga baya na Fahimci Saboda kawai ya rika zuwa yana zama da zainab ne,ammh tuni sun san akin bazai samu ba,tuni har ma'aikatan da aka dauka sun fara aikin su. *Janafty* *KNKB2014* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Zukata tuni sun kwanta,gabbai sun samu natsuwa hankula sunyi ruku'u sun rusuna. Ta kowani bangare na juya na irin shafukan kaddara da kan bud'e ma bawa to ta kowani tsanani daman Allah yayi alkwarin sauki,hakan ce ta kasance dani duk lokacin da naga rayuwa ta chude'min ko tamin zafi da ikon Allah sai wata kaddara ta bude ma rayuwata sabon shafi da zai zama bango ko majingina gareni Bayyanar Abba garemu daga Allah ne, sannan zamowarsa makwafin Uba garemu shine jin dadin mu,Sannan har makwafin uwa ya Dauke mana Ahalinsa kuma sun Dauke mana makwafin yan'uwa da Dangi,sai alokacin muka san muma ya'ya ne,Abba ko tari bai yarda mu yi ba tare da yasan Dalilin yin sa ba,Yace duk abunda muke bukata kiransa kawai zamu yi a waya mu gayamasa,to mu saka aran mu komai muke so mun samu,Yaya Asiya tuni har ta je gidan su Ammi a kano tasha karamci ta tabbatar mana da cewa Duka Ahalin Abba masu karamci ne,Tace sai nuna ta ake yi ana fadin"Diyar yar'uwan Baban Nana ne na kaduna"Ko'ina aka kaita sai an karramata duk da Ammi bata garin tana kaduna,Direba aka saka yakai ta har gida,Sannan sun karbi lambar wayarta da alkawarin zasu rika zuwa suma. Ammi suna da yawa a gidan su matan Mahaifinta hudu ne kuma duka sun haiyayyafa,Sannan tana da kanne maza sosai wasu duk suna garuruwan da suke aiki da matansu kamar mijin Laila Uncle Junaid Staff ne a kasu Kaduna State University. yana chan sai dai lokaci bayan Lokaci suna zuwa ganin gida shi da ita. Azumi ne ke kara gabato mu ma wannan karon,Zainab saboda ban samu zama ba bamu kara mgana a waya ba tunda na gaisheta kwanaki da jiki,shi kuma Gogan bai min zencenta ba.  Ni ma kuma ban cika Tusa kaina inda ba'a sakani ba, tunda muka yi alkawarin da shi ya daina matsamin ammh fa bai daina Takurani da kallo ba,ko kuma ya rika shigemin jikinsa na gogan jikina bana son haka nayi mai mgana sai kawai ya kalleni yace"Ba kyau Fa'iza wlh ba kyau. Ki bari kada Allah yayi fushi da Da ke" da naji haka sai ban kara mai mgana ba,sanin gaskiya ya fada,Tunda bai sakeni ba har yanzu yana da Hakki a kaina kuma shi Allah ba ruwansa da wannan,mganar jinginan auran mu kuma wannan wani zama ne mai zaman kansa. Sai na rabu da shi tunda na samu ya daina sakani gyaran Shimfid'a yana Rutsani sai na gode ma Allah,Abba Dubu Dari uku ya kara turo ma kowannemu mu yi siyayyan azumi har da su Goggo suma bai kyalesu ba,bakina yaki rufuwa Kana naka daman Allah ya gama nashi kuma nashi Tsarin shine daidai na zata Yaya Ishaq zai yi fad'a sai naga bai ce komai ba ya dai ce"Abban nan naku naji da ku Fa'iza"Sai na samu kaina da yin kayattacen mirmishi,Hajiya ma ta aiko mana da kayan abinci,Domin ita a di'ya ta daukeni ba kowa ba,Alherin Hajiya gareni mai girma ne da bazan taba iya mantawa da ita ba. A satin za'a fara azumi yara sun yi Hutun makaranta suna gida da Safe muna waje ni da Anum da Amir muna wanke wanke Ahmad da Musty na fad'a kan shara nagaji da yi musu mgana ne na kyalesu sun ki bari ina jira na tashi ne yaro yaji a jikinsa,Hafsah na makaranta jarabawa suke yi ta kosa su gama ta gudu kaduna,Badariya na kano ammh suna chan suna ta shirin Biki ita da Raliya ta waya. Daga Daki ya fito kamar an jehosa Fadi yake yi"Bazai yuyu ba. Wlh bazai yuyu ba in kika bari aka cire cikin nan na rantse da Allah Zainab aure na dake ya karem Bazan iya ba Nagaji haba.." Yake fad'a cikin Tsawa da Daga muryan da sai da Mama ta fito daga Daki zani a hannu cikin wani yanayi ni kaina sai da na saki aikin da nake yi na mike gabana na faduwa. Mgana yake a waya kamar kuma da Zainab yake mgana sai kara shan wallahi yake in aka cire cikin nan sai ya rabu da ita cikin bacin rai yace"Me kuka maidani daga ke har mahaifin naki.?sakarai shashasha ko sai yadda akayi da shi ko.?to wannan karon ba Kotu ba Allah yasa majalisar Dinkin Duniya zai kaini wlh sai kin yi zawarci ni bazan iya wannan auran naku ba da kuka fifita yahudanci Fiye da Islama acikin lamuran ku" Kokarin yi mai bayani take ya Daka Tsaki ya katse wayar yana Huci,Mama ta kallesa tana fadin"Meke faruwa ne Ishaq.? Sai ya kalleta Har idanuwansa sun cika da kwallah cikin wani yanayi yace"Mama ki duba fa ki gani,wai cikin yarinyar nan babanta yake so a zubar..'" Sai ya kasa karisawa saboda yadda ransa ke Tukuki,Mama tace a zabure"Cire ciki kuma Saboda mene. ?Kamar zai yi kuka yace"Saboda Hujjar su na banza wai yana wahalar da ita, hala ciwo take ko kuma wani abun ne ya sameta ana raba mai ciki da laulayi ne mganar banza kawai,Mama ne Zainab da Mahaifinta suka maidani jani talau..?wannan wani irin kaddararren aure ne..? Mama zatayi mgana kenan wayarsa ta fara kuka yana dubawa yace"Babanta ne"Yau ko arzikin Daddyn bai samu ba,kamar bazai Dauka ba Mama tace ya Dauka mu dai mun ga yana mgana Yaya Ishaq na cika ya bude baki yace"Daddy.." Kamar katsesa ya yi yana mgana kamar kiftawan ido sai ji mukayi K'aras,ashe wayarsa ce ya buga da bango sai da ta dargargaje,A firgice muka yi baya har da yara da suka yi Tsuru tsuru basu saba ganin haka ba. Mama ta firgita ta rikesa da karfi tana fadin"Kai Ishaq ka natsu mana" Haki yake yi kamar wanda yayi gudun mutuwa cikin hakin yake fadin"Shi ke auranta ko ni Mama.? A shari'an ce na fi shi iko da ita meyasa komai shi zai zartar da shi.?Rabon da wasu suke nema da kudin su,mu mun samu shine zai yi sanadiyar zubarwa saboda bai da Hankali yana Uba ammh uban banza wanda baisan ya kamata ba..? Mama ta kara rikesa tana fadin"Kwantar da hankalinka ka natsu." Cikin Hargagi yace"Wani  iri na natsu mama..?Har ce min yake sai an zubar nayi abunda zan yi, wai akan ya'yansa zai yi iya yin komai wlh Mama indai aka zubda min jinina ba shege ba,d'an sunna wlh sai Zainab sai tayi zawarci aurena da ita ya kare har Abada,in ya'yana ne zan karbo kayana Fa'iza ta had'a da su Amir ta rike min su" Mama ta yi saurin tareshi tana fadin"Abi komai a sannu Ishaq" Ni dai nayi tsuru ina kallon ikon Allah Amir yaje ya tattaro wayar baban nashi ya had'ata ya miko min yana Fadin"Umma ga wayar Daada" Sai na saka Hannu na karba ban kallesa ba nace ya had'a kan kannensa su shiga Daki,Anum sai da yayi mata jan ido ta tafi ta tsaya tana Kura ido da Daukan komai sai anjuma kaji tana maimaitawa. Sai da suka shige ne na kallesa Mama ta Dake sai faman bashi Hakuri take yi,tana ya kwantar da Hankalinsa shi kuma yana kara rantsuwar Wlh matukar Zainab ta yarda Mahaifinta yasa aka cire cikin nan auran su ya kare. Kai Tsaye nace"Saboda me zaka ce zaka Saketa..? Sai duka suka dago suna kallona, ni ko na gyara tsayuwa a raina nace yau ce ranar maida martani Mama ce tace"Haba Fa'iza ai suma abun nasu ba su saka Tunani aciki ba" Kai Tsaye nace"Zainab ce fa Mama. Zainab matar so yar Dangi,yar gata masu kudi da nasaba" Sai ta kasa mgana ta Tsaya tana kallo na,Shi ma haka sai ko na kara fadin"Eh ai Zainab ce mai kyau ce ba Mummuna ba, sannan yar asali mai ilimin zamani yar gata yar masu kudi yar dangi mai cikakken gata,matar nuna wa duniya,wacce zata haifa maka ya'ya farare masu kyau ba irin ya'yan Fa'iza ba,matar da kuka zabeta sama da kowa matar da kuka fifita ta fiye da kowa matar da kuke so da kauna. Meyasa saboda wannan matsalan kace zaka saketa ke kuma Mama baki Tsawarta masa ba..? Na karishe fad'a ina tsareta da ido kunya ya kamata sai ta kasa mgana shiko Tsawa ya dakamin bai so na kara mgana na warware komai ban kulasa ba na cigaba da fadin"Ita fa ka zaba sama da ni. Ka fifita ta sama da ni,Ka fifita zuru'arta sama da tawa zuru'ar, sannan ka fifita ya'yanta sama da nawa ya'yan,to ta ina kake Tunanin zaka hanata abunda take so.?ai tun farko a haka ka ganta, kuma ka ji ka gani kana sonta.." Cikin hargagi yace"Ya isheki Fa'iza..Ya isheki haka nace" Ya karishe fad'a kamar zai Dakeni sai nayi baya na tsorata kada yakaimun duka,Cikin wata murya yace"Ki bari Fa'iza ba kyau irin haka. don Allah ki bari kada ki kara Tunzarani" Sai da na tabbatar da nayi baya sannan nace"To ka daina mganar Sakin nan  bai dace ba gaskiya, ai ku ba yara ba ne, kun fara tara kyakyawan zuru'a a tsakanin ku" Sai kawai ya Dafe kansa ya koma kasa ya zauna Dirshan yana kara Dafe kansa,Mama na gefe jikinta yayi sanyi da kunya yasa ta kasa mgana,ni ko sai naji zuciyata wasai ko banza na gasa musu mgana sannan na maida musu martani. Yana girgiza kansa yake fadin"Nayi Nadama Fa'iza nayi nadama ba tun yau ba.wannan auran bai amfaneni da komai ba sai bacin rai da Nasani,ban bi Turban Annabi ba wajen auran nan sai Allah ya barni da zabina,ya bani mace tagari ban gode masaa ba,na rika Hange hange ina ganin na wuce da ajin Fa'iza,Sai ga shi na bi auran kyau da nasaba da ilimi daga karshe hakan bai amfaneni da komai ba.." Da Sauri nace"Ya amfaneka mana Zainab na sonka sannan kuma ta fara tara maka irin zuru'ar daka ke so" Idanuwansa Jajir ya d'ago yana kallona kafin yace"Bata so na, in da tana so na,da bata fifita ta mganar mahaifinta akan nawa ba. Tana ganin tana da kyau alfarma tamin data aureni,Tana ganin tana da ilimin da Taimakona tayi ta aure ni,tana ganin tana da Gatan da ban isa da ita ba. kaico na da nabi Rudin duniya da Rudin Shed'an,ga shi yanzu ina Nadama Shiyasa duk wanda bai bi Turban Annabi ba, tun a duniya zai Tabe Annabi ya fad'ama mu auri mai addini domin itace mafi kyawun cikin su" Dagani Har Mama ba wacce tayi mgana ita kunya da Sanyi ni kuma na shiga wani yanayi mara Dadi a lokacin. Shuru yayi yana sauke Numfashi kafin yace"Mahaifinta bai Daukeni a bakin komai ba,gani yake taimakona yayi alfarma ya yi min don ya bani auran yarsa shiyasa yake takani yadda yaga dama har cikin gidan nan ya tako ya ci zarafina na, kasa komai ammh wannan karon wlh bai isa ba. sai na nuna masa na fisa cikakken iko da yar tashi ta zubar da cikin ta gani Sai dai kuma a bi wani Sarkin" Da haka ya shuru takalmansa yayi waje Mama na kiransa bai ko Juyo ba,Ni dai nace Allah ya kyauta na koma ina cigaba da wanke wanke na, Mama na Tsaye ta kasa gaba ballatana baya har ga Allah ba wai dadi naji ba ammh raina bai baci ba,Gwara su fara gani Tun yanzu ban ga laifin su ba,Irin Rariyan da ya siya ne kuma don tayi zubar ruwa shatata bai kamata yayi korafi ba. Ina gama aikina na shige Daki abuna,Na fara wata Hidiman yaran kuma karatu na iske su suna yi,Duk da nasan suna jin tashin mganar Baban nasu daga falon,tsakar gida na fito zan Dafa zobo na,Sai naga Mama an kwashi kafafun da sanyin jiki ta koma Daki Ranar sai dare ya shigo gidan ajaran majaran a falo ya fadi kan kujera yana sauke Nunfashi ina mai sannu da zuwa ya amsani a Dake kafin yace na sama mai ruwan wanka. Sai da ya rarrafa ya shiga Dakinsa na bisa na kai masa wayarsa da ya fasa da tawa ina fad'in"Ga shi matarka nata kira, tana son mgana dakai" Domin tun bayan La'asar Zainab ke kirana tana tambayansa nace mata ya fita ta Dameni ta kira yafi sau goma Daga gani bata cikin natsuwarta ne. Yana cire rigan jikinsa ya d'ago yana kallona ina shirin ficewa yace"Dawo ki Dauki wayarki" A kausashe nako ki dawowa na fice ina jinsa yana fadin"Lalle itama ko zan fasata wlh" a fili na furta"Kana fasamin waya zaka biyani kayana" Daganan na fita zuwa kitchen sai da ruwan yayi zafi sannan na juye mai na ba ma Amir ya kai mai ban koma Dakin ba, abinci ma Anum ta shigar mai da shi yaran suna falo suna karatu ni kuma ina Daki,Hafsah na gefe na muna mgana sai ga shi ya shigo daga gani yanzu ya fito wanka ga kansa nan na digar da ruwa yana shigowa yace"Hafsah jeki falo wajen yara zan yi mgana da yayarki" Ba musu ta fice ya kariso gabana yana fadin"Ki ka bama Amir ruwan zafi in ya kona sa fa..? Sai na kallesa kafin nace"Ba yau ya saba dauka ba, zai iya ne" Sai ya kuramin ido kafin yace"Ba kyau Fa'iza na horu fa don Allah ki yi hakuri".ganin ya fara sauya mganar yasa na mike na fice,na bar masa Dakin jiki a sanyaye ya koma Dakinsa ya shirya abincin ma afalo ya fito ya ci,Ina gefe sai kallona yake yi ni ko nayi kamar ban gansa ba. Wayata sai washgari ya aiko Anum da ita, ban ko Duba  ko sun yi mgana ba. ammh naga an kirani Hafsah ta Dubamin tace Abba ne da Nana Fatima daman sune rana bata fitowa ta fadi basu kirani sun ji lafiyata ni da yara na ba,Har ga Allah ina kaunar Nana Fatima kamar yadda take kaunata,Sai da na natsa sannan na kirata muka gaisa sai tace measurement din yara da nawa take so na Rubuto mata sai nace ta bari sai Hafsah ta dawo zata turo mata,mun cigaba da mgana duk akan Bikin Yaya Abdul'Ahad ne da Raliya bayan sallah Tana fadamin Nana Fadila ta fitar mana da anko imu imu gabadayanmu,Na lura suna ji da Bikin nan ko don shine na farkon da zasu fara na Namiji, barin ma Ammi kamar Abdul'Ahad ba yaron ta na fari ba,ba ruwanta da kawaici da ita ake shiryawa komai.  Abba kuma daman ba mazauni ne ba ne tafiya na yawan kamasa Ammi ce akan komai. Da Hafsah ta dawo na saka ta tura mata har da na takalmaa,Ban san cewa Yaya Ishaq bai yi mgana da Zainab ba, sai da ta kara kirana bayan na Dauka mun gaisa sai ta sakamin kuka na rud'e na zata ma ko wani abun ne ya faru cikin Kid'ima nace"Lafiya Maman Fadil..?. Cikin kuka tace"Maman Amir ki saka baki Honey ya daina fushi dani wlh ba laifina ba ne. Daddy ne ya matsa kuma ni nace mai bana so tunda Honey baya so kuma ba'a cire cikin ba. wlh nayi ta kiran sa wayarsa a kashe bana samun sa" Sai shesshekan kukan ta, na fara lallashinta kafin nace"Daman jiya baku yi mgana ba ne da na kai masa wayar ..? Da Sauri tace"kashewa ya dinga yi Maman Amir yaki ya saurareni ma, Daddy fa har fushi yake yi dani saboda naki amincewa da mganarsa Maman Amir don Allah ki basa hakuri wlh ban cire cikin ba, yana nan kada yace zai sakeni wlh ina son mijina" Sai ta bani Tausayi cikin sanyi na nace"Kiyi hakuri ki daina kuka in ya Shigo zan mai mgana" Da haka muka rabu sai mganarta ta Tsayamin arai, tana son mijinta har ga Allah nice shaida,ammh Mahaifinta ne ya riga ya saba da juya al'amarin ya'yansa,Ni kuma na kudiri niyar daidaita Tsakaninsu saboda itace Dahir dinsa,Da ya shigo Dakin Mama ya tsaya,sai da ya jima sannan ya shigo Dakina yara suka mike suna mai Sannu da zuwa Dakinsa ya shige Saboda ina da mgana dashi da kaina na tafi kai masa abinci,yana zaune ya yi Tagumi ammh yana ganina sai ya cire Tagumi,sannu da zuwa nayi masa na sauke mai abincin a gabansa ya jawo yana fadin"Me muka samu ne..? Ina zama nesa da shi nace"dambun Shinkafa ne da zogale" Cikin yanayin sa yace"Salon ya shake mu Fa'iza"ina Dariya nace"Tuwo naso nayi ban samu gyad'a ba,sai yara sukace Umma ki yi mana Dambu" Bai ce komai ba sai da ya tashi ya wanko hannunsa ya fara ci sannan yace"Ko bakomai zamu dora da zobo mai sanyi" Yafad'a yana kashe min ido sai nayi dariya yana ci muna hira,Sai da ya gama ya kuma dora zobo mai sanyi kamar yadda yace sannan na sako mai mganar Zainab kici kici yayi da Fuska kafin yace"Ina ruwanki da wannan mganar Fa'iza..? Na rausayar dakai nace"Da ruwana mana ai yar'uwata ce musulma kuma shi ai sulhu alheri ne" Sai kawai ya mike yana fadin"To ki cire bakin ki a ciki ba ruwanki ahto.." Sai naga daga taimako kawai sai na tattara kwanukan daya bata na fice ina fadin"Allah ya kyauta" Da gatse ya amsamin da Ameen sai abun ya bani Dariya a raina nace mata da miji sai Allah sai su shirya ma ban sani ba. Kuma saboda Zainab din yaki kai wayarsa ya gyara. ya gwammace ya zauna ba waya nidai tunda yace ba ruwana na cire bakina data kara kirana,sai nace mata nayi mgana yace zai kirata in ya gyara wayarsa Da dai taga ba Nemanta zai yi ba an fara azumi Takwas sai gata ta iso,ita kadai ko Farhan bata zo da shi ba, ta yayesa yana gidan su Tace ko Daddy bai son ta taho ba Shari'a har Falon Mama ammh Gogan ka yace shi fa ya gaji kowa yayi ta kansa baiwar Allah sai kuka take yi a raina nace ita kuma nata Jarabawar kenan na soyayya Allah yasa mu dace. Yadda yake yi mata ban dauka zai iya kallonta ba, ammh dayake Namiji sunnsa Namiji sai ga shi sun shirya an shiga kurya an yi lamo,Daganan na san sha'anin mata da miji sai Allah Shi da har masifa ya rikamin wai na ce ta tafi nace dayake ni na kawo ta ba,Bata koma ba sai da suka Daidaita da juna kwananta Biyar ta koma Abuja,motar Haya ta shiga abunda bata tayi ba ammh ga shi Namiji ya sakata acikin wani Hali. Ni daman tunda yace na cire bakina na kama kaina, ko da tazo ta zaunar dani tana gayamin har abunda ma bansani ba iyakata da ita hakuri kawai Domin kamar yadda yace ba ruwana to ba ruwana din. Mun yi azumi sha biyar Hafsah suka samu Huta,Washegari Yaya Abdul'Ahad yazo wajen Raliya shi ya wuce da ita Tare da Anum da Laila ta matsa sai an zo mata da ita haka kurum Allah ya hada kaunarta da Anum da taji ma dagantarkar dake Tsakani sai tace daman ba haka kawai take kaunar Anum ba ashe jini d'aya muke da mijinta. Musty har da kuka akan sai ya bi Anum Dakyar Babansa ya Lallashesa akan zamu je da sallah sannan ya Hakura,Azumi nada ashirin da Biyar sakon Abba na kayan sallarmu ya iso karofi aka kai,Yaya Isa ya kawo min nawa har gida duka da ni da yara. Har da Babansu,kala biyar biyar,harda na Anum data ke chan Da na Hafsah kenan wasu za'a sake dinka musu Yaya mariya haka aka kai mata nata ita da Yaya Asiya,Bakina yaki Rufuwa na kira Abba ina masa godiya sai yace"Ba godiya tsakanimu Fa'iza duk abunda nayi muku ba komai ba ne, ku ya'ya na ne kamar yadda zan yi ma Nana Fadila haka zan yi muku" Sai na kasa mgana,Saboda farinciki ya gamamin komai ganin ba na Mama aciki sai na saka kudi na siya mata kala uku har da Hijabi da takalmi ta karba Karo na farko da Mama ta taba godemin bayan nayi mata wani abun alheri.. Shi kuma Yaya ishaq da nace ya kira Abba yayi masa godiya sai yace"Ba kin kira shi ba?sai na Dagamai kai cikin basarwa yace"Ya wadatar kin hada da godiyata da naki godiyar"daganan ban kara mai mganar ba,na lura ba duka halinsa ba ne ya sauya wani Lokacin rashin Mutumcinsa na nan bai tafi ba,Wannan karon dai mun yi sallah cikin Farinciki da wadata Jamal ya Dawo gida sallah shima nayi masa kayan sallah har da Hula da takalmi,Badariya a kano tayi sallah Tace Hajiyar Dala ta mata kala Daya nima na tura mata kudi tayi guda Biyu ta kara da shi Saboda yanzu ina samun kudi sosai tunda bana taba kudin sana'ata tunda Abba ya karamin jari abubuwa suka daina Cushemin ga shi muna da kayan abinci sosai,wannan sallar ko Anty Binta bata kawo mana komai ba ganin bana neman komai,Naman salla kuma Abba sa ya saka aka siya aka yanka a karofi aka raba mana Nama,Ni kuma na siya mana kaji,sai bayan na siya ma Hajiya ta aiko mana da shi,Sai dai ma muka rika kyautarwa,Ranar sallah na uku naje Karofi ni da yara muka kwana Daya muka Dawo sai kuma washegari naje Gidan su sa'adatu nima tazomin ranar Sallah na biyu,Daganan na sauka gidan Hajiya ana ta fentin gida saboda Biki bayan salla da Sati Biyu ne. Hajiya tace wajenta zan zauna kaduna sai za'a tafi da Raliya sai na bisu mu tafi ina Dariya ina fadin"Hajiya su da suke jiran mu tun ana sauran Sati daya..? Hajiya tace"Aa su mariya su je ammh ke kina gidan nan ai Raliya kanwarki ce, ke zaki mata gyaran jiki da Hadin Turaruka'"Na dauka Hajiya wasa take yi sai da Ammi ta kirani tana fadin"Fa'i shikenan sai Hajiya ta mana Haka.? Ina uwar d'iya ammh ana min fin karfi akan ya'yana". Nidai dariya na dinga yi ban yi mgana ba ina jin Abba na gefe na fadin"D'anki zata gyara ma Amarya fa Maman Nana" Sai tace"Kuma fa hakane to na d'aga kafa. ammh da sharad'in a Turaran Amarya za'a dibarmin nayi ma Baban Nana kwalliya da shi" Abba yace"Shikenan kuwa na uwar miji da matar d'a ba" Ni dai sai dariya nake yi in ka Biye ma Abba da Ammi sai cikin ka ya Kulle Tuni muka shiga shirin Biki,Biki ne na manyan mutane,Balle Abba wannan ne na farkon da zai aurar da Namiji,an aiko da katinan Daurin aure kayattu Abba yace duka jama'ar Karofi yan'uwa na kusa kusa yana gayyatarsu,Har Hajiyar Dala Yaya Asiya ta gayyata ita da suke ta shirin su ita da yan gidan su Ammi ga Nana Fatima a kusa da ita, tunda har gidan juna sun je ina Dutse ina kano. Hajiyar Dala taga bikin na irin nasu ne tace zataje har kaduna,sai mamaki take yi yadda Lokaci da'ya Gata ya Lullube rayuwarmu yanzu babu abunda ya'yan gata zasu nuna mana muna. Nima a barayina na gayyaci su Anty Binta da su Anty mahma,da mama ni daman ina gidan Hajiya kamar yadda ta fad'a,Hajiya tamin dinkunan ankon Biki,Kala hudu har da na Lonching din da zata hada na mata zallah,achan kaduna ma su Nana Fatima sun ce duka kayana sun zama Ready na fitar Biki achan zasu yi Dinner din su gabad'aya. A na saura sati daya biki Badariya ta Dawo suka fara shirye shiryen saboda gyaran jiki sai suka tare a gidana nan suke kwana,gefe daya kuma ina hadin Turaruka ga zuwa gidan Hajiya ba na ko zaman gida,Abba ya kirani yace na turo yara suzo tunda ni sai ranar Daurin aure,sannan a kaduna za'a Daura auran Raliya gidan kanin babanta Hajiya tace ayi chan yafi sauki kawai,su Goggo duk zasu tafi kaduna ana gobe biki sai na had'a su da yaran suka fara yi min gaba da su Mama su goggo tabi Anty Binta kuma ita da Anty mahma da Halisa direban Anty Binta zai kai su, su Yaya mariya da su Yaya Asiya tuni suna kaduna ana sha'ani da su sai kirana suke yi naji kamar nima nayi tsuntsuwa na ganni achan. Tun ana gobe biki na tare gidan Hajiya,gidan ba kowa sai Yaya Ishaq da jamal,zasu Daurin aure gobe domin Abba yace yana son ganinsa,mota guda Hajiyar su Raliya ta basu zasu bi tawagan mazan da zasu tafi daga nan katsina. mu ko muna chan muna ji da Lonching,na hadu da manyan mata sosai kawayen Hajiya,Amarya bazatayi walima ba sai ranar Lahadi da yammah bayan an kaita gidanta,Hajiya da ya'yanta ni suka saka kan abinci akwai ma'aikata ammh ni nake nuna musu yadda za'ayi. Ranar asabar daya daga cikin asabar din karshen mako aka Daura auran Raliya Kasim Saulawa da angonta Abdul'Ahad Usman karaye a garin kaduna a masallaci sultan bello,Ana gama Daurin aure ango da Tawagansa suka nufo katsina inda akayi pinic party dasu da kawayen Amarya adaran Ranar,Washegari sai shirin kai Amarya tun Safe aka shirya Daman tuni an je an yi mata Jere a gidanta acikin garin kaduna zai zauna anguwan Sarki chan yake da gidansa mai kyau. Amarya su suka fara yin gaba ita da kawayenta da angwaye,mu kuma sai da muka Tsaya muka shirya wasu kaya muka tafi da su,Sai yammah muka isa kaduna,gidan Raliya muka fara sauka chan na iske su yaya mariya da su Nana Fatima sun zo tarban Amarya muka Rumgume juna muna murnan ganin juna, sanye nake da Less din da Hajiya ta dinkamin na yinin ta nayi kyau duk da ban yi kwalliya ba,Da anan za'ayi walima sai aka sauya akace Ndc za'a koma gidan Abba achan za'ayi,gabadaya muka tattara muka koma chan,Hafsah sai wajen walima na ganta ita da Nana khadija sun ji kaya iri daya kamar yan biyu su Anum kuma an saje cikin su Falaq sai dai naji ana fadin Umma haka su Ahmd sun ci gayu suma suna ta wasan su cikin yara sa'aninsu. Su Yaya ishaq da mazajen su Yaya Asiya Abba ya hanasu tafiya suna nan tare da shi,Sai bayan isha'i aka tashi Daga walima,aka kuma fara shirin Tafiya Dinner ni dai ina ganin in da ake bikin yan gayu,sai ga shi duniya juyi juyi na gaba ya koma baya. Sai ga shi su Anty Binta da Mama ne a rab'e mu kuma mune amara kirjin biki. *Janafty* *KNKB2015* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Kuma daidai gwargwado ba'a wulakantasu ba,an kula da su sosai duk abunda suke so shi suke yi,ba mai hanasu. Balle kuma ga Badariya da sune manyan kawaye,Raliya ta mata komai na kayan fitan biki,kawancen su ba irin na sauran kawaye ba ne hatta duka ankunan biki duk Hajiya ta siya ma Badariya,Sai dai kunya ce da nauyi yasa suka koma gefe suna kallon abunda ke gudana. Sanda muka zo naga Abba muka gaisa shima wajen Ammi yazo suna mgana,Baya gidan suna Hotel inda bakin sa suka sauka har da su Yaya Ishaq suna chan suma,Abba sai da yayi min tsiyan ido na kenan..? Ina dariya nace"Abba kanwata na tsaya nayi ma rakiya" Ammi tace"kuma matar yayanki ba" Mukayi dariya gabadaya Ammi bata manta ba sai da tamin mganar Turaranta nace nazo mata da shi sannan tace na fita ko ba soso da Sabulu, abunda na lura da shi Ammi macece wayayyiya mai son kamshi da gayu,domin yar gayu ce ta Bugawa a jarida in ba an fad'a maka ba,baka isa kace itace mahaifiyar Yaya Abdul'Ahad ba,Tana ta shiga tana fita ko a jikinta damu da yaranta duka D'aya ta Daukemu. Da ita da kawayenta da yan'uwanta suma suna ta shirin zuwa Dinner din Shashen Ammi aka sauke Amarya da Tawaganta,mu kuma shashen Abba gida ne ba ni da gida ba wajen Haduwa da kayan more rayuwa,babban gida mai shashina ba adadi harta Yaya Abdul'Ahad yana da shashensa a gidan.  Da zai iya zama da matarsa basu takura juna da su Ammi ba,nan su Nana khadija suka zauna da Kawayensu,dasu Hafsah da aka zama yan matan kd,su Goggo kuma suna Shashen Inno ita da su Baba Ati suna nasu sha'anin. Muna shashen Abba sai shirin Tafiya ake yi Kaya iri d'aya Suka dink'amana Dukkanmu har da Nana khadija da Hafsah,wani uban su material mai ja da baki,yayi kyau matuka dukkammu dinkin Dogayen riguna suka yi mana,Irin na zamani Fitted,sai head ja,da zamu nada da takalmi ja da Karamar pos har da mai yi mana kwalliya na musamman. yaran kuma daga mata har mazan su shadda Fara aka dinka musu sai akayi amfani da zare ja wajen aiki da kwalliya,Ina kallonsu suna ta shiryawa tuni har an fara yi ma su Nana khadija kwalliya,Da farko kayan naga kamar baza su yi min ba, sai da Nana Fatima ta saka nata ta matsamin nima na sake yin wanka na shirya sai ga shi kayan yayi min cif a jikina kamar an gwadani,na juya na kara juyawa na kalli Nana Fatima ina fadin"Wannan ba irin namu ba ne Nana, sun matseni fa dinkin yanmata ne" Harara na tayi tana fadin"Ni juya na zage miki zif din riga. Ba wanda yace ga dinkin yanmata da matan aure kaji matar nan"Ina dariya na juya ta zage min,na ja head din ina shirin Daurawa ta Fizge tana fadin"Meye haka.?kai tsaye nace"Daurawa zan yi mana"Da karfi tace"Daurawan ta. Mai kwalliya zata daura miki bayan ta gama miki kwalliya" Sai na Bude ido Lokaci d'aya ina fadin"Ni za'ayi ma wannan fenten fenten haba Nana mana wannan sai su Hafsah" Dariya tayi Lokaci d'aya tana fadin"Har su fa'i yau sai sun yi kwalliya"na zata wasa take sai gashi tamin Taron dangi Nana Fadila tace"Muma nan kwalliyar zamu yi fa'i banga abun damuwa ba' Na marairaice ina fadin"Anty Fadila ban fa taba yi ba, na dauka kwalliya na masu kyau ne da yan gayu" Sai suka kalleni suna Dariya Nana Fatuma tace"Kaji wani Tunani kuma. kwalliya da gayu na macen data san kanta ne Fa'i,kuma yau ko zaki suma ne sai kin yi kwalliya" Taruwa suka yi suna ta gayamin amfanin kwalliya ni jinsu kawai nake yi, ko kunshi da gyaran kai da nayi Hajiya ta matsamin da na rakata gyaran kai tace sai an yi min, sannan da mai kunshi tazo tace na zauna ayi min gaskiyan mganan hausawa da suke cewa duk wanda ya gyara zai ga dakyau ni kaina nasan nayi kyau a baya ina Tunanin bakin Fatata  bazai saka lalli ya zauna ba sai gashi ya fito ras da shi,Tabbas na yarda ko kana da kyau ka kara da wanka ni kaina da yanzu na samu sauyin rayuwa Fata ta fara gogewa. Ban gama mamaki ba sai da naga har su Yaya Asiya sun sha kwalliya an buga musu Dauri ita da Yaya mariya na kallesu na kwashe da Dariya ina Fadin"Yaya Asiya wai kema ahaka zaki Dinner din.? Fari tamin ido tana fadin"Kwarai ma kuwa Fa'i bari ma na kira baban Usaini yace min Abba yace suma sai sunje fa" Ta wuce tana wani juya jiki gabadayammu muka saka Dariya mamakin yadda ta sauya kawai nake yi Yaya mariya ko sai faman duba madubi take yi na kalleta nace"Yaya mariya mata a gidan Manaja" Ta juyo tana fadin"fad'i ki kara kuma dagani ba kari" Kawai sai Nana Fatima ta saki guda suka tafa da Yaya mariya chaa sukamin Dole bayan an gama ma Nana Fadila na zauna nima akayi min kwalliyar zamanin da a baya na Dauka sai a Fuskar mata masu kyau ake yinta,kuma yayi kyau ba irin mu munana kuma bakake ba. Fuskata naji duk ta Daure,har abun ido aka karamin ina bana so ba na so Nana Fatima tace sai an sakamin,Ina tura baki tayi dariya tana fadin"Sai fa kin zama yar gayu kema Fa'i ga mijin ki na ganshi dan gayu da shi ammh ke baki son gayu" Yaya Mariya ta tabe baki tana fadin"in dai Fa'iza ne abun haushi yanzu kika fara gani, gabadaya ta maida kanta baya shiyasa har miji ya raina ta ya yi mata kishiya' Sai Nana Fatima ta Tsaya tana kallona cikin mamaki tace"Fa'i daman kina da abokiyar zama ne shine ban sani ba..? Sai na kauda zencen da cewa"Kun san fa kari ba kyau a addini" Yaya mariya tace"Allahu akbar Sayyada" Da na Dake bana so ne sai Nana Fadila tace kada a sakamin a barmin ido na haka,Sai da aka gama na duba madubi sai naga kamar ba ni ba gabadaya Fasalina ya Sauya na sake kallon kaina na koma na kalle su kafin nace"Wai fuskata ce haka..? Sai suka kwashemin da Dariya,Nima kaina sai da nayi dariya,ko wajen saka Takalmi an sha Fama dani yayi min Tsini Nana Fadila tace"Ke da ma baki da tsawo fa'i ai na irin ku ne" Kamar zan yi kuka nace"Ban saba sawa ba. Kuma ban iya tafiya da su ba"Nana Fatima tace"Zaki koya yanzu malama"Haka ta sakamin shi mai igiya,ina tafiya ina neman fad'i Suna min Dariya. Ammi ta shigo tana fad'an ga motoci chan a waje ana ta Daukan mutane goma ta kusa dare yayi sai taga ina tafiya ina Tangad'i salati ta saka Tana fadin"Me zan gani haka Fa'i..? Ina matse ido nace"Ammi bazan iya tafiya da shi ba don Allah kicesu kyaleni"Ammi tace"To bari kada ki yi kuka ki bata kwalliyan ki.." Tafiya kuma da takalmi ya zame miki Dole ana mganar gayu fa'i ko ni kalleni Da wanda ma ya fishi" Tafada tana d'agamin kafarta mamaki ya kamani nata baki ne mai igiya kalan leshin jikinta a bunka ga farar Mace Less din data saka baki ne sai ya haskakata na zata Ammi zata Sassautamin  ne,itama fad'a ta kama min tana fadin"Saki jikin ki ki yi tafiya ba zaki fadi ba. In baki koya ba sai yaushe Fa'i? yanzu in Tafiya ta kamamu na shiga Villah haka zaki je kina yi mana? Suka ko kwashe da Dariya Nana Fatima tace"Sai mu tafi mu barta"Ammi tace"Aa fa da ita zamu rika shiga ko'ina bame barinta a baya" Dole zata koya yadda baki da Tsawon nan ai irin takalman ki kenan yarinya"Ina ji ina gani suka hanani cirewa Yaya mariya tace"'Fa'iza fa sai a hankali komai na gayu bata iya ba" Ammi tace" Zamu ko b'ata da ita.Ko ni da nake sauke ku ina gayu na ina Dalili. Shiyasa ban jita tana tashin kamshi ba,kamata yayi yadda kike sana'ar kayan kamshi da jikin ki da Dakin ki sai sun kama kamshin ki, ammh ba ko d'aya"Sai kunya ta kamani na Sadda kaina kasa ammh ita ko ajikinta ta cigaba da min fad'a tana fadin"Mace sai da gyara Fa'iza muma fa duk burga ce,Adon ne ke cetan mu"Tafad'a tana fari gabadaya muka saka Dariya Nana Fatima tace"Ammi to har kishiya fa'i fa gareta..? Ammi ta saka salati kafin ta mangare ni tana fadin"Ba fad'an yanzu ba ne zama zamu yi,mu yi mata  na musamman wuce muje" Saboda kada Ammi tayi mgana yasa ban ce komai ba, da naga zamu fita dagamu sai wani karamin mayafi,ance Tuni Yaya Asiya da Nana Fadila sun tasa yara sun yi gaba,Mun fito Falo sai ga ango yasha kamshi sai Nana fatima ta fara kirari yayi Tsaki yana fadin"Ku daman baku tafi ba..? Tana dariya tace"Tawagan ango zamu bi"Kai tsaye yace"To ku cigaba da jira. Ammi wai ina Abba sai kiran wayarsa nake tana kashe" Ammi tace"ban san to ina ya tsaya ba. Dazu dai ya kirani yace ga Engr ya sauka daga a kaduna daga Lagos yazo masa murna, bai samu zuwa Daurin aure ba" Abdul'Ahad yace"Engr din yazo ne Ammi? Tace"Baka ji me nace ba ne, yazo ammh inaga ya wuce domin Baban Nana yace min Karfe goman daran nan jirgin su zai tashi daga abuja zuwa London zai raka kakarsa ganin Likita" Kasan tana fama da matsalan koda"Abdul'Ahad sai ya fice yana fadin"Ammi in kin same sa kice ya tabani" Mu dai waje muka fita motoci sai kad'an tunda duk sun wuce sai Amaryan da tawaganta su kuma angwaye zasu bi,Allah sai ya jeho mana Mijin Anty Laila uncle Junaid yaje ya kaisu Laila ya dawo Nana Fatima ta Dafe mana shi ya kaimu ni da ita da Yaya mariya Ammi agida muka barta tace za'a kawota. Wani Hadadd'en wajen Event ne mai girma da fad'i goma ta wuce ammh kamar rana chan muka iske su Anty Binta da Mama sun je suma,su Goggo dai na gida sun ce a raba su da zuwa wani shegantaka da Daddare. Amir na ganina ya taso yazo kusa dani ya kama Hannuna yana fadin"Umma kin yi kyau" Nayi dariya ina shafa kamshi nace"Kai ma haka Amir dina." Su Anum suna tare dasu Hafsah da Nana Khadija kowa ya kama bangaran da zai zauna muna sai muka kama Tebur d'aya dukkanmu mu Bakwai har da su Hafsah su Laila suna nasu bangaran,Gabadaya ji nake yi a takure saboda shigar jikina ga uban Takalmi Kallon da su Mama suke min ne yayi min yawa na tashi naje na gaishe su Allah ya taimakeni ban Turgud'e ba. Anty Binta haka take kallo na kamar na Sauya mata har sai da tayi mgana da cewa"Lalle Fa'iza kece haka..? To kada dai ki manta kina da aure ba Budurwa bace ke'" Ban ce mata komai ba, sai ga Nana Fatima tazo tajani muka yi gaba tun ina Dari Dari har dai na saki jikina ina ganin zuwan su Yaya Ishaq shi da Jamal sai mijin Anty mariya,da wasu da ban sani ba,kuma a Tebur din bayan mu suka zauna ina da Tabbacin basu gane ni ba. Ammi tazo ita da tawaganta daga ita sai Tawagan amare da angwaye. Matuka wajen ya hadu bazaka ma gane Dare ba ne,an ci an sha an sha rawa sannan an yi nishadi,Badariya ta bada Tarihin Amarya wani daga cikin abokan ango shima ya ba da Tarihin ango. An kira kannen ango mun fita mun yi liki Daman Ammi ta bamu yan Dubu sabbi muka  zubda da su,ana bikin Duniya in da ake yi jama'a haka muke taka kudi,Sannan an bamu fili mun rausaya Nana Fatima in na yi kokarin Sulalewa ta rikoni,ni na samu na yafa mayafin su basu yafa ba a Hannu suka Rike. Mun koma wajen zaman mu sai igiyan takalmina ya warware na duka in gyara ina Dagowa muka hada ido da Yaya ishaq sai naga ya kauda kai kamar bai gane ni ba,sai na mike na isa gabansa cikin wani irin takun da bansan na iya ba kuma abun mamaki Tsab na saba da tafiya da takalmin kafata ina zuwa gabansa nace"Hy.." Ina mai kura masa ido na make murya yasa bai yi Saurin Dagoni ba. Jamal baya wajen ya koma chan Teburin gabammu.kauda kai yayi yana wani basarwa zan kara mgana sai ga Amir yazo yana fadin"Umma.." Yaron nan shi ya Tona min asiri a Firgice ya Dago yana kallona yana kuma kallon Amir kafin yace"Bangane ba..Wata Umman..? Amir yace"Daada Umma ce fa baka ganeta ba ne..? Yadda ya saki baki da Hanci yana kallona ne yasa na bushe da Dariya ina Talle ma Amir keya Lokaci daya ina Fadin"ji yaro ya batamin shiri na" Amir shi kanshi Dariyan yake yi ganin yadda Babansa yayi daga sama har kasa yake kallona,daman shi bai so zuwa ba Abba yace sai sun zo tunda suka zo yake ganin yan mata kenan har su Yaya Asiya bai gane ba, tunda ya Dauka yaran yara mata ne kawai a wajen. Kirjinsa sai duka yake yi yana kallona Amir da ya ga haka sai ya Sulale ya barmu kujeran gefensa naja na zauna ina fadin"Samari." Sai kawai ya miko hannu ya kama Hannayena duka Biyun yana Fadin"Fa'iza wai don Allah da gaske ke ce..? Sai na kara saka Dariya kawai ban tsammani ba sai naji saukan sumba a saman bakina cikin wani yanayi yace"Kin yi kyau Fa'iza ashe ke mai kyau ce ban taba sani ba.."? Ina shirin bashi amsa naji Tafi a bayana ina juyawa Naga Nana Fatima da Sauri na kwace hannuna ina Hararanta karisowa tayi gabanmu tana Dariya Lokaci d'aya tana fadin"Allah ya kamaki wato kina nan kin zo gwada ma miji kwalliya ammh nan ina fama dake kin ki Tsayawa ayi miki,Ranka ya dade a biya ladan kwalliya domin sai dakyar ta amince akayi mata" Ba musu ya saka hannu a aljihu ya zaro kudi ya damka mata,suma Abba ne ya basu yace na liki ne,Tako amshe Abunta tana fadin"To yanzu sai ka mora kallon ka..Fa'i." Ina juyowa ta kashe min ido tayi gaba na bita da dariya,kai tsaye nace"Ina ka samu kudin tukwaici..? Cikin wata murya yace"Abba ya bamu wai na liki ni ai ga babban liki na nan"yafad'a har yana wani lashe baki yar Dariya nayi cikin yangar da wlh bansan na iya ba,kai wani lokacin bakin mutane na taimakawa wajen Dakushe tasirin da muke da shi a Rayuwa, yanzu da na samu masu yabani da Daidaitani da Sauran mata har na fara tunanin to dame suka fini..? Kiri kiri Yaya Ishaq yaki barina na matsa ko'ina har yana fadan na saka karamin mayafi,rai bace ya kalleni yana fadin"Wato kyale kin da nake yi yasa kika maidani sauna ammh bari mu koma gida zaki shiga hannu" Ina jin haka na shiga Taitayina,Sai da za'ayi Hotuna Anty Fadila Dakyar tazo ta jani shima sai da tasha korafinsa sai bina yake da kallo barin ma takalmin kafana a ransa bai san sanda ya furta"Jar uba.." Fa'iza fa ta tashi kan sa ,ya so yayi wauta da farko ballatana da kayan suka kamani,gabadaya Shafe dina ya bayyana kamar ban haifi yaran nan ba Tuni kishi ya kamashi muna Hotunan kamar ya fizgoni ya rumgume haka yake ji bamu muka bar wajen ba sai Dayan Dare Shima ba'a tashi ba nan muka bar Amarya da sauran mutane Yaya Ishaq bai sauke ajiyar rai ba sai da muka tafi ba shi kadai ba duk wanda ya ganni sai yace Fa'iza kin yi kyau barin ma Badariya juyi goma sai tace"Kai matar yayana tafi kowa a wannan bikin" Bamu san yaushe suka dawo ba sai da Safe su Hafsah sukace sai uku na Dare araina nace lalle kaduna bariki. A ranar  muka raka Raliya dakinta Dangin Hajiya da kawayenta suka wuce bayan sun damka amanarta ga Ammi da su Inno,Mama da Anty Binta a ranar suka tafi bayan Ammi ta hada musu sha tara na arziki tare da Jamal suka Tafi Abba dai ya Tsaida Ishaq yace yana so zai yi mgana da shi. Domin yadda ya samu labarin a bakin Goggo Mijina baya aiki yanzu nice duka hidomomin gida shine yake so ya gansa su Tattauna. Kuma in dai ba wannan Lokacin ba bai kuma da Sauran hutu in aka gama Bikin. Hajiyar Dala bata zo ba rasuwa akayi mata, Yayan megidanta ya rasu dole ta Tsaya ammh taso ta zo ta bama idanuwanta abinci,sai dai tagani a waya tunda Badariya nata zuba Hotuna yaran ta na Nuna mata,Hajiyar Dala tayi mutuwar zaune da taga Hotona da Badariya ta saka a kasan Hoton ta saka"Matar yaya na tafi ta kowa. Anty Fa'iza" An ce har Jamal ya Dauka shima ya saka a Status d'insa, gogan bai da waya bai san wainar da suke toyawa ba,Hajiyar Dala aranta sai da tace kamar an yi min wankin in ji nice na koma wata classis haka a baya tasan ni yarkace yarkace kamar yar Gudun hijira,ammh yanzu kuma taga na zama wata mai aji da Daraja. Inaga ta wayar Jamal Zainab tagani ta tambaye shi yace ina kaduna muna Biki sai ta kirani tamin Allah ya sanya alheri kai tsaye kuma tace min"Ashe kuna da yan"uwa a kaduna.?ni ko sai nace mata eh na kara da fadin"Kanin Mahaifiyarmu ne mai rasuwa"Sai ta jinjina kai tace"Allah sarki" ba mu jima muna wayar ba,bayan tambayan yara da gida muka yi sallama. Zuwa talata kaf gida ya watse hatta Goggo ta koma karofi sai mu har Yaya mariya tanan sai gobe zata tafi Yaya Asiya kuma aranar suka tafi da yammah tabi yan gidan su Ammi daman tare suka iso,Amarya na gidanta suna hutawa ita da ango Badariya na gidan tare dani zamu koma da yara. Wasa wasa ina neman yin Sati a kaduna Gida duk ya watse,Nana Fatima ta koma Dutse,hakama Anty Fadila ta koma lagos,Abba ne ya Tsaidamu ni da Yaya Ishaq shiyasa bamu koma ba shima kanshi ya koma Office sannan ga wannan Hayaniyar Biki shiyasa bamu samu zama ba. ammh nasan Ba domin Yaya Ishaq na ganin girman Abba ba,bazai zauna ba,sai korafi yake min shi ya gaji da zaman wuri d'aya da cewa yayi zai tafi ya barni sai na Taho daga baya nace ya dai Tsaya yaji me Abban zai ce masa. Sai Ranar Alhamis da Daddare suka samu zama da Abba. Tunda bikin ya watse ni nake yin girki,Umarnin Abba ne har kayan hadin zobo da kunin Aya an siyo da sauran lemuka ina ta Shagwabasu da cimata. To ranar ma daddaran Lemun abarba nayi musu,sannan na soya musu kaji nayi pepe din su sai tashin kamshi yake yi,daman Tuwon shinkafa nayi miyar agusi da naman rago an kai musu sai Ammi tace na bi su da wannan su dora daga baya. Sanye nake da Hijabi mai ruwan kasa har kasa Nana Khadija ta Dauko min Voul din kazan muka shiga Falon Abba sun ware suna ta Hira da Yaya Ishaaq Abba ne fa da ba ruwansa. Har kasa na duka ina gaida Abba ya amsa yana fadin"My Dota me muka kara samu ne.? Ina mirmishi nace"Abba pepe chikchen ne sai lemun abarba" Abba ya bude kamshi ya Dakesa sai ya lumshe ido yana fadin"Gaskiya Ishaq kayi hakuri ku kara ko Sati d'aya ne nima na Mori yata da girken girken nan nata masu dadin Tsiya" Yana mirmishi yace"Sai ayi haka Abba? Abba ya kalleni kafin yace"Fa'i Allah ya kawo kudi Abba ya bude miki katon gidan abinci.." Ina Dariya na amsa da Ameen khadija na gefe tace"Abba ga Vacany na farko kun fara samu nasan albashin zai yi tsoka"Abba yace"Aa sai mun yarda da kwarewarki bama son masu son jiki"Sai ta fara dira kafan Shagwaba da Sauri yace"Ni fa ba da nake ba" Yadda yayi ne yasa muka Dara mikewa muka yi muka fice yana sakamana albarka. Bayan sun taba kazan sun sha Lemun Abba ya koma ya kishingida yana fadin"Fa'iza ta shagwabani da abincinta gaskiya Maman Nana ta kara koya kafin tatafi in baso take na rika barin mata kayanta ba" Ishaq yace"Baza'ayi haka ba Abba" Abba yace"To a san yadda za'ayi dani Allah" Haka dai suka yi ta barkwanci. Abba baya so ya fara mai mganar kai Tsaye kada Ishaq din ya Dauka da wata manufa sai ya fara sako mai mganar aikin Gwamnati suna hira cikin Hiran ne Abba ke tambayansa ina yake aiki kansa na kasa yace"A baya dai nayi aiki da Hukumar Tattara Haraji ta kasa ammh yanzu bana aiki da su bisa ga wani abu da ya faru"Sai Abba ya gyara zama kamar bai sani ba yace"Subhanallah me ya faru..?kai Tsaye kuma Ishaq din ya warware masa komai, Abba ya jinjina kai ko ni bai yi mganar dani ba. Yaya isa daya fadamai sai ya Tattauna da Goggo ta kara yi mai bayani ammh yanzu yaji wasu a bakin Ishaq din. Kai Tsaye Abba yace"A abuja kace kayi aiki da su ko..? Kai ya gyada yana fadin"Eh Daga katsina chan suka maidani nafi shekara Bakwai ina aiki dasu a wajen"Sai Abba ya muskuta yana Fadin"Nako san chairman din ku na wajen. Dr.Lawal Bako zan kirasa ko zai iya yin wani abu akai,ai bai kamata a bar shi haka ba, sai a tsananta Bincike har a gano gaskiya" Da Sauri Yaya Ishaq yace"Kasan shi ne Abba? Abba yace"Yes Tare muka yi Mastering Degree din mu a Buk kano Shekarun baya" Sai Yaya Ishaq ya murmusa kafin yace"To ai surukina ne. Ina auran yarsa Zainab" Abba ya ware ido kafin yace"Au daman kana da wata matar ne bayan Fa'i.?sai ya gyad'a mai kai cikin Mamaki Abba yace"Ikon Allah to tana ina ban taba ganinta ba..? Kai Tsaye yace"Tana chan Abujan Abba.." Abba sai ya kasa mgana ya Dauko wayarsa yana fadin"Ammh kuma duk da wannan dangantarka bai saka an tsananta bincike ba? domin daga gani kamar Trap ne aka had'a maka acikin kuma ma'aikatan naku ne" Yaya Ishaq yace"Gaskiya ba'ayi ba. Lokacin dai an ta fad'i tashi Saboda Shigar EFCC kan mganar" Abba yace"Suma EFCC din ina da wanda zan kira kan mganar ammh bari na fara kiran Dr.Lawal din ina da lambarsa mukan taba juna Lokaci bayan Lokaci" Kai tsaye ko ya lalubo lambarsa ya Doka masa kira ya kuma sakata a amsa kuwwa kira uku ana hud'u ya Dauka cikin Dariya Dr.Lawal yace"Kaga Matatar mai da kanta ba Sako ba. Allah ya taimaki Engr" Abba yayi mirmishi yana Fadin"Dr bako kana lafiya..?ya iyalai..? Shi Dr.Lawal yaje ya karo karatu ne har yazama Dr,shi kuma Abba bai yi ba,aammh dukkansu Chemical Engerniaring suka karanta a makaranta. Bayan sun gaisa Abba yace"Kai ashe mun hada suruki d'aya bamu sani ba..?Dagachan Bangaran Dr.Lawal yace"Suruki wani surukin nawa kenan..? Abba yace"Suruki nawa gareka..? Dr.Lawal yace"D'aya mijin Zeey ne, Ishaq dan katsina ne" Abba ya yi dariya kafin yace"Shi fa. Nima ai yana auran y'ata" Sai Dr.Lawal ya mike daga kishingid'en dayake yana fadin"Wata y'ar taka Kuma Engr.? Abba yace"Sunanta Fa'iza abokiyar zaman ita yar taka kenan" Sai ya mike tsaye a razane yana fadin"Dama yar ka ce ita..? Abba yace"Diyar kanwata ce mai Rasuwa. Ga ni ga Ishaq din sun zo Daurin auran Abdul'Ahad ne muna Hira sai muka tabo bangaran aiki, To yana gayamin a office din ku na Abuja ya taba aiki nace na sanka shi kuma yace ai surukin sa ne kai" Dr.lawal ya share zufa yana fadin"Ikon Allah.." Abba yace"Kaji fa." Dr.Lawal yace"To ai baka gayyace ni bikin yaron namu ba".? Abba yace"Kaina yayi zafi ne kuma kasan mun jima bamu yi mgana ko ta waya ba" Daganan suka cigaba da Hira Abba ya Sako mganar Ishaq da Tunanin a saka Kwamitin Bincike a gano bakin zaren mana Dr.Lawal yace"Ai hukumar EFCC ke cikin mganar Engr shiyasa" Kai Tsaye Abba yace"Kada ka damu ni dai ka nad'a kwatimin bincike ta bangaran ka, ni kuma zan yi mgana da megidana Engr mahaifinsa Shine Chairman na EFCC a yanzu haka so nasan zai taimaka mana insha Allahu" Dr.Lawal a ransa yace aiki ga mai kare ka,Sun dad'e suna mgana yace zai nada masu binciken tunda zai shiga mganar nan take ya kira Megidan nasa bai same shi ba sai ya kalli Ishaq yana fadin"Zan kirasa kuma ina gayamai Cikin Satinan za'a dauko Fayel dinka a Sabunta bincike da ikon Allah za'a wanke ka" Yaya Ishaq nata godiya,ni bansan me suka Tattauna ba. washegari Direban da Abba ya bamu aka maidamu gida a jeep dinsa ni da yara da Badariya da Hafsa da zata koma makaranta booth din mu cike da kayan Biki. Bai fad'amin yadda suka yi da Abba ba, sai bayan kwana Biyu da muka natsa sannan yake gayamin nayi murna sannan nasan tabbas tunda Abba yace zai shiga mganar an yi an gama. Har Mama ya fad'amawa sai addu'an Allah yasa adace take yi,da fatan a gano gaskiya. Ko da aikinsa bazai dawo ba,ammh yana da kyau kada sunanka ya zauna a matsayin barawon Gwamnati. *Janafty* *KNKB2016* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Wannan shekaran data zagayo. bamu sha wahalan rayuwa ba,saboda Abba ya tsaya mana,shi ya biya kudin makarantan yara da sauran bukatumu na yau da kullum.  hatta da kayan abinci ya cike mana wannan bangaran,Yace komai muke bukata mu kirasa bamu da damuwa Ishaq kuma daman ya fad'a masa shi a D'a ya dauke sa ba suruki ba, shima uba yake garesa kamar yadda yake uba gareni Shikenan shima sai ya saduda yana karban komai da girmamawa,Mama ma haka tana ta min godiya,ni ko nace mata bakomai,Badariya ta koma kano wajen Hidimar kasarta Jamal ma ya koma makaranta sun shiga Semister karshe a makaranta. Gefe daya ina cigaba da sana'ata ban Dakata ba,Sannan ayyuka sun karu min yanzu saboda akai akai nake hada Turaruka yanzu daga chan kaduna da kano ko'ina akayi mganar Turare sai Ammi tace Fa'in mu tana Had'asu masu kamshin Dadi,in nayi sai dai na bama Hafsah ta kai tasha a saka a mota kuma kudin aikina cas a Hannuna,Allah yasa ma Anum na gida ta gama primary zata shiga JSS Section. Muna waya da su Nana Fatima kusan kullum muna sanin Halin da juna ke ciki,Yaya Ishaq yaki ya gyara wayarsa sannan yaki ya siya wata. Matarsa sai kirana take yi ni na zama alkali a Tsakaninsu wani Lokacin sai ta kira baya gida sai ya barni da gayamata ya fita,gajiya nayi ranar muna zaune da Daddare shi ya gama yi ma yara karatu sun kwashi Littafan su zuwa Daki,Hafsah na kitchen tana Dafamin zobo wanda zan yi na safe da shi,ni kuma ina gefe zaune a kasan cafet,shi ko har ya koma ya kwanta a saman kujera. Dagowa nayi ina kallonsa kafin Nace'"Na manta. matarka ta kira d'azu baka nan" Yana ji na bai yi mgana ba sai na tura masa wayar gabansa ina fadin"Gaskiya ka siya waya. ko ka gyara taka, nagaji da Damuna da matarka take yi, kana kuma barina da bayani in baka gida" Sai alokacin ya bud'e ido yana kallona cikin shakewar murya yace"Ba zan siya ba sannan ban yi ra'ayin gyarawan ba" Ban yi mamaki ba daman nagansa yau sai a hankali yana jin yan tsiyan nasa, sai na rabu da shi aiko ko tashi bamu yi a wajen ba sai ga kiranta na leka naga itace na mike na fice daga Falon zuwa tsakar gida ina faman kaye kaye ban sanin masa ba ko sun yi mgana.  ni dai da nadawo naga wayata nan saman kujera na Dauki kayana na wuce Daki. Abunda na lura Zainab da mahaifinta sun sauko suna neman sulhu da Ishaq shi kuma yaki basu wannan damar Saboda bayan kwana Biyu ta sake kirana baya nan domin yakan d'an fita ya mike kafa ina ji a gefenta tana mgana tana fadin Daddy wai baya nan ya fita sai naji an yi mata mgana kafin tace min in ya dawo nace ya Kirata Daddy zai yi mgana dashi. Da ko ya dawo na bi shi har Daki na Fad'amasa sannan na bar masa wayan a wajensa sai gashi ya biyoni nima har Daki ya mikomin wayata yana Fadin"Ki daina kawo min wayar nan Fa'iza wai sau nawa zan fad'a miki ne.? Sai na bude baki ina kallonsa cikin mamaki nace"To in ta kira sai nace mata me..?kai tsaye yace"ki fad'a mata gaskiya bana son mgana da ita" Nima kai Tsayen nace"Tace ka kirata Daddy na son mgana dakai" Yadda ya wurgamin wayar ya fice a Fusace ne yasa sai da nayi Dariya Allah yasa wayar kan gado ta fad'a,Na dauki wayata ina fadin"Bani na kar zomon ba" Zainab bata barni ba, ta rika addabata da kira kunya sai na rasa me zan ce mata sai taga kamar ni ne bana son had'asu,Gajiya nayi nace gwara na fito nayi masa mgana Tattara yaran nayi zuwa Dakin Mama harda Hafsah saboda chan yafi kusa da tsakar gida yafi iska,Kayan sa da na wanke masa na ninke masa basu kawo wuta ba,ballatana na goge masa,Sai na Tattara na kai masa Dakinsa tun da ya shigo ya shige ciki sannu da zuwa ma dakyar ya amsamin Abincin sa Anum na bama ta kai masa ko da na shiga yana wanka domin naji karan saukan Ruwa a makewayi. Sai na sauke kayan Hannuna saman katifarsa na zauna gefen katifar ina jiransa bai jima ba ya fito da Dogon wando a jikinsa,Kansa na digan ruwa yana gogewa da karamin Towel,Sai da ya tsaya yana kallona alamun yayi mamakin ganina ni kuma ganinsa ba kaya yasa na mike ina fadin"in ka shirya sai na dawo' Ban jira cewarsa ba na fice shima bai Dakatar dani ba,Na koma Falo ina yan kaye kaye yara dai ba'a rabasu da Lalata waje ko sau goma zaka gyara shi kuwa,ba jimawa sai ga shi ya fito da jallabiya da farantin abincinsa a nan falon ya zauna ya ci abincin ya sha ruwa,sai ya koma ya kishingid'a yana Hamdala ni kuma falon na Tattara domin ina taka datti Musty ne yayi sharan,ba domin ya share dakyau ba. Ina ta jira ko zai ce me nake son fadamai sai naji yayi kamar bai ma ganni a falon ba,Sai na samu gefen kafafunsa na zauna ina fadin"Mgana fa nake so mu yi" Kai Tsaye yace"kunne ke ji ai" Sai na bude baki zan yi mgana sai na Rufe saboda ina tunanin bazai karb'i mganata ba Sai ya dago yana kallona kafin yace"Uhm ina jin ki" Sai na dukar da kai ina Fadin"Tsakani ga Allah baka kyautawa abunda kake yi"kai tsaye yace"Da na yi me kuma..? Ina gyara mganata nace"Kan mganar Zainab mana ka barni ina mata karya. Haba don Allah baka je bafa tun zuwan nan da kayi kafin azumi,Itama ai tana da Hakki a kan ka, kuma Allah zai tambayeka akan hakan ka dauki waya ka kirata ku yi mgana don Allah" Kamar bazai ce komai ba har sai da nace"Kaji.." Sai ya gyara zama kafin ya mike ya zauna dakyau yana fad'in"Kina bani mamaki Fa'iza wai wani hakki kike mgana..?ke sau nawa ina zuwa wajenta na tare kuma tasan hakkin ki na shiga ammh bata taba min mganar naki Hakkin da ke kaina ba, sai ke ki bi ki dameni Haba." Ya karishe fad'a yana Tsareni da idanuwansa da suka fara shigewa Ciki,sai na sunkuyar da kai ina Fadin"ni ba ruwana da wannan. Abunda na sani ne nake gayamaka kai ma nasan ka sani,Tunasar dakai nake yi ciki fa gareta tana Bukatar kulawarka" Kai Tsaye yace"ke ciki nawa kika Dauka kika haifeshi batare da kulawata ba..? Sai na kasa mgana kafin nayi mirmishin takaici nace"Ni sunana Fa'iza ni ba yar kowa ba ce. sannan ni ba yar gata bace Fa'iza ba Turanci komai nata zero ne Zainab kuma mai kyau ce yar gata yar Dangi tana da ilimi tana jin Turanci sannan kowa na sonta, kaga kenan Tsakanina da ita akwai Tarin bambamcin da ko a wajen Daidaito na miji bazamu zo Tsara d'aya ba". Ina kallon cikin Idanuwansa na fadamai haka sai kawai ya rausayar dakai yana fadin"Ashe bazaki bar wannan mganar ba Fa'iza..?baki manta komai ba kenan..? Ko daman kin fad'ane kawai baki yafe min ba..? Da Sauri nace"Wlh na yafe maka duniya da Lahira" Da Sauri ya Tareni da fadin"To me kike son nayi ne ki daina damuna da wad'anan mganganun ne" Kai tsaye nima nace"ka Saurari zainab sannan kaje ka dubata tana bukatar kulawarka" Sai ya kankance ido ya mike yana fadin"To bazani ba. Nace bazani ba,Sai ki sani naje dole..Haba mata kin bi kin dameni..?zaman ki nake yi a gidan da zaki rika min kora da Hali.?na riga nayi rantsuwan da bazan kara bin Zainab ba, in tana so na tasan inda nake zata Biyo ni. kuma kin ji ma na rantse bazaki sakani yin kaffara ba. Ba ruwanki in ta kara kiranki kada ki sake d'aga wayarta Umarni ne na baki ba Shawaran ki nake nema ba Fa'iza" Ya karishe fad'a yana kureni da ido,na bude baki zan yi mgana ya saka min yatsa a saman bakina yana fadin"Shii..Mu rufe babin wata zainab mu yi mganar mu Fa'iza ina mganar mu ta kwana..?baki ga duk na galaibata ba ne saboda rashin ki..? Kai Tsaye nace"Shiyasa nake so kaje inda zaka samu abunda kake muradi" Sai kawai ya mike tsaye yana Nuna ni da yatsa cikin bacin rai yace"Rashin kunya zaki yi min Fa'iza don kinga ina Lallaba ki ko..?ko karfi na saka miki Bani da laifi Saboda ke Halaliyata ce. ina binki a Hankali ne Saboda nayi miki laifi ba domin kin fini iko da kanki ba" Mamaki ya kamani kamar zan yi mgana sai na fasa sai kuma ya Saussauto ya koma ya Duka gabana ya Riko Habana ya dago fuskata yana Fadin"Don Allah Fa'iza ki manta komai mu bama auran mu wata Dama nayi miki alkawarin bazaki kara kuka dani ba don Allah. Wlh na wahala na fara susucewa" Ya fada lokaci d'aya yana langwabe min kai kamar karamin yaro,sai nayi wuf na kwace fuskata na mike shima sai ya mike zan gudu ya rikoni kafin nayi wani motsi ya kamkameni a jikinsa duk mutsu mutsu na na kasa kwace kaina sai na Saduda kaina ya Dago yana kallon cikin Idanuwana yace"Saboda kin ga ina kyale ki ko..?ni kuma sai na bude baki zan yi mgana, sai kawai naji ya Had'e bakina da nasa waje daya ya fara sumbatata lokaci daya yana kara kaina da Hannayensa a cikin jikina. duk iya kokarina na kwace kaina na kasa tun muna Tsaye har muka zube saman kujera yana Jagwalgwalani fargabana D'aya kada wani cikin yaran nan ya shigo gashi yaki barin bakina ballatana na yi masa magiya sai da ya maidani Tubus ko yatsana ban iya dagawa, Saboda yadda Hannayensa suka Ladaftar dani,Mganar Ahmad muka ji daga kofar daki yana kiran"Umma.."Umma" Shi ya ceceni zaraf ya tashi daga kaina Daman doguwar rigace ajikina ya Dagemin ita har wuya,saboda bala'i shi ya saukar min da rigan yana kallona takaici da bakinciki suka tasomin,Kallona yayi cikin yar dariya kafin yace"mganin ki kenan. na lura ni nake kyaleki" Daga haka ya wuce dakinsa yana Dariya sai hawaye suka zubomin nayi Saurin sharewa,saboda shigowan Ahmad yana fadin"Umma barci nake ji"Cikin kasala ina share hawayena nace"je kayi fitsari ka kwanta" Daga haka na mike na shige Dakina ina share kwallah kamar wacce aka daka kan gado na fada ina cigaba da kukana abu d'aya ya tsayamin a rai in ya cigaba da min haka watarana zai karyamin lagona kuma faruwar haka kamar rugujewar Burina ne. Kuma ni bazan bari hakan ya faru ba,Wannan kudirin nawa ya Dade a raina cika shi tamkar wajibi ne. Bansan adadin da na dauka ina kuka ba sai da naji shigowar su Hafsah naje na wanko Fuskata,nazo na kwanta Na rufe ido da suka shigo sai suka yi tsammanin nayi barci nan ko idona Biyu,Har suka yi shirin kwanciya suka kwanta,ni kuma na kasa barci ina Tunanin yaushe ne mafitan da na Dad'e da neman ma kaina zai cika..? Shin zan iya yin abunda nake hasashe ko ba zan iya ba..? A haka har barci ya kwasheni,Sai chan wajen ukun dare na tashi nayi alwala na fara Nafila bayan na idar na Daga Hannuna ina addu'ar Allah ya bani juriya da kwarin gwiwa sannan kada yasa ya'yana su zama raunin da zai sa su shiga Tsakanina da Burina. Washegari Fuskata a Had'e na tashi shi kanshi ya ganni ko gaishe shi ban yi ba shine yace"Ina kwana Anty Fa'iza" Kallonsa nayi na basar na cigaba da aikin gabana sai ya kwashe da Dariya yana fadin"Wai fushi kika yi..?zaki yi ma mai Dalili yarinya" Ina jinsa nayi masa banza Da rana Zainab nata kirana sai na rasa ya zan yi da ita.?Sai kawai na dauki wayar na tafi Dakin Mama yana ko kwance kan kujera Mama na zaune a kasa suna Hira yanayin yadda na shigo yasa Mama ta kalleni tana fadin"Fa'iza lafiya..? Shima sai ya sakamin ido yana nazarina Gabanta na duka na ijiyemata wayar ina fadin"Mama ki masa mgana kila ke yaji mganarki" Matarsa ke damuna da kira shi kuma in na kai masa sai yak'i mgana da ita. Har ga Allah mama bana so Zainab taga laifina,sai taga kamar ina mata Tsakani da mijinta ne" Mama sai ta kallesa tana fadin"Shi ina wayarsa ne..? Kai tsaye nace"Bai gyara ba kuma yaki siyan wata. saboda yasa matarsa ta rika jin Haushi na" Sai Mama ta Rausayar dakai kafin tace"ka kyauta. Tashi kije Fa'iza zan yi mai mgana" Na ko mike na ficewata ban ko kallesa ba,inaga Mama tayi mai fad'a yasa ya dauki wayar suka yi mgana,washegari kuma da Safe wajen sha daya sai gata Direba ya kawosu ita da yara,Na karbeta hannu biyu kamar yadda na saba kai Tsaye wannan karon Dakin mijinta ta sauka yana dakin tana zuwa ya shuru Takalminsa ya fice ya'yansa kawai ya Kula ga cikinta har ya fitio ta kara kiba kamar ba ita ba. Bayan na gama abincin rana munci muka zauna zaman Hira a manganunta na fahimci ita kaddaranta Soyayyan Yaya Ishaq ne shine Rauninta Kuma mahaifinta na kaunarta bazai so abunda zai sosa mata rai ba. Kai Tsaye ta kalleni tana fadin"Maman Amir Honey yaki ya yafemin laifin da ban ma aikata ba. Daddy mu kad'ai ya Haifa Dagani sai zuzu komai muke so a duniyan nan yana bamu shi baya so yaga muna wahala ganin yadda kwanakin chan nayi ta fama da Laulayi ne yasa yace a cire ciki ammh da nuna bana so ai bai kara mganar ba. meyasa shi Honey bazai sauko ba Har Daddy fa ya so yaje chan su yi mgana yaki ya Saurareni,yanzu haka Daddy na chan ya kafa kwamitin Bincike a ma'aikatarsu kan Case dinsa ammh duk bai gani ba yanzu nazo ko kulani bai yi ba" Sai Hawaye sharr sai ta bani Tausayi,Ashe an fara binciken ni bama mu yi mganar da Abba ba. Tunda yace min bai samu sun yi mgana da Engr din ba har yanzu saboda baya kasar bai dawo ba,Ina kallonta tana kuka,sai a raina nace ita kuma nata kaddaran kenan..?tana son shi Kuma Dole Mahaifinta ya barta ta biyo abunta take so in har shima yana son abunda yarsa ke so. Lallashinta na dinga yi ina bata baki ta kara kallona tana fadin"Wlh maman Amir ina cikin wani Hali Cikin nan sani Son kasance da shi yake yi. ammh yaki Saurarena a kwanakin baya kamar zan yi hauka haka nakeji,saboda yanayin jikina yasa sai da na samu sauki na taho" Na Tausaya mata saboda haka nayi fama da wannan sha'awan Lokacin cikin Ahmad ammh ban samu ba,Domin Yaya ishaq bai saurareni ba akwai ranar da har kuka nayi masa yace shi baya cikin mood din ya gajiye ya Dawo bazai iya min wani amfani ba, ranar kamar zan yi hauka naji kamar na Mutu da addu'a da Taimakon Allah sai da cikin yayi kwari komai ya lafa tsakani ga Allah na Tausaya mata matuka shiyasa na Rike mata Hannu ina fadin"kada ki damu zai sauko in sha Allahu" Tana sharan kwallah tace"Yaushe zai sauko..?ko fa kallona bai yi ba..? Don Allah ki yi masa mgana ki tayani basa Hakuri"Sai na kasa mgana kawai ina kallonta ina zan kara mgana nima ta kwabemin Saboda na lura da yadda nake masa mganarta alokacin yake kokarin nuna min nima ai matarsa ce. Ni dai ina ta bata baki ina fad'amata zai sauko cikin hakane yasa nace"To kiyi masa abunda yake so ki bar aikin nan Maman Fadil sai ya sama miki anan ki dai dawo kusa da shi hakan zai fi"Sai tayi shuru kafin tace"Daddy ne ya hana fa. Ammh wlh naso haka tun da na Fahimci bazan iya zama nesa da shi ba" Ni ko sai naga na samu damar da zan gayamata gaskiya sai na gyara zama ina fadin"Mahaifa suna da iko a kanmu ne idan muna gabansu. ammh da zarar sun aurar damu mun bar karkashin ikon su mun koma karkashin ikon Mazajen mu,Ki gane wani abu shifa miji ba abun wasa ba ne yana da cikakken iko akan ki Zainab. Yafi mahaifinki iko akan ki, in yace kada kiyi abu kika yi Allah zai yi Fushi dake in ransa ya baci,ko da mahaifinki kika sabamawa dalilin Umarnin mijinki Allah bazai kamaki da laifi ba,a ko'ina Umarninsa na saman na kowa in dai a kanki ne" Sai tayi shuru tana kallona alamin bata san haka ba ni ko sai na cigaba da Fadin"Annabi muhammad Salallahu alaihi wasallam ya fad'amana in da Allah zai wajabta Sujudda Tsakanin mutane da ya wajabta Sujuda ga mata zuwa ga mijinta.Saboda a nuna Daraja da girman miji ga matarsa"Sai ta waro ido tana fadin"Yanzu duk ina cikin Fushin Allah ne Maman Amir..? Sai na girgiza mata kai ina fadin"Cikin Rashin sani ne. Shi kuma Allah bai kama mutum da laifin da bai sani ba,Ni dai shawaran da zan baki ki yi kokari ki gyara zamantakewar dake Tsakanin ku,Sannan ki daina Fifita mganar Mahaifinki saman tasa baki kyauta ba ki bashi hakuri ki nuna masa zaki bi Umarninsa sannan zaki Girmama duka muradansa akanki sai a zauna Lafiya"Sai ta damke hannuwana Tana fadin"Nagode sosai Maman Amir.Ban taba ganin kishiya mai kyakyawan zuciya kamarki ba" Sai kawai nayi mata mirmishi sai gashi na zake ina gayamata yadda zatayi ya sauko,ni nace ta sake wanka ta d'au gayu yau a sha soyayya. Sai Dariyan jin dadi take yi,Mama na Dakinta tana jin mu bata ko leko ba naga yanzu ta daina ma Zainab din Rawan jiki,yara suna dawowa makaranta suka fara Murnan ga Anty ga su Farhan,ko Dakin nasa ma ni na shiga na gyara shi Saboda bata iya ba. Da Daddare tuwon shinkafa nayi mana miyar ganye,da gyad'a sai Dare ya Dawo ina ta mamakin shi ko ina yaje haka? Ruwan wanka ma da yace na sakamai yana zafi na juye na bama Zainab nace ta bisa Dakin dashi ta karba ta wuce to bansan ya suka kare ba,Saboda afalo muka hadu muka ci abinci gabad'aya. ina kallo sai kallonsa take yi shi kuma yana basarwa kamar an matsi bakina nace"Wai ina kaje yau tun Safe ne.? Kamar yana Jirana kawai sai ya harareni kafin yace"masallaci naje na zauna ina kai kararki wajen Allah. Ki nemi yafiya ta. wlh in ban yafe miki ba, bazaki yi albarka ba Fa'iza" Sai na saki baki ina kallonsa kuma agaban yara ga Hafsah. zaraf Anum tace"Umma me kika yi ma Daada..? Kafin nayi mgana yace"Tambayeta dai Anum.." Zainab na gefe tace"Kema fushi yake yi dake Maman Amir..? Kawai sai ya kai mata Harara yana Fadin"Ina ruwanki..? Sai ta kalleni nima na kalleta nayi mata signa da ido sai ta mike nima na mike ina fadin"Amir ka kwashe kwanukan nan ka kai kitchen. Anum ki share falo Hafsah ki yi ma yaran shirin kwanciya Fadil dina taho muje mu kwanta"Yaro ko ya taso daga wajen Uban ya nufoni na Daukesa na kalli Zainab ina fadin"Ki shiga ki gyara masa shimfid'a. Sai da Safe" Sai ta amsamin da Toh,ta wuce nima na wuce da kallon mamaki ya bimu da shi kuma muka ki basa damar mun Fahimcesa yaran kuma suka rika fad'in"Umma sai da Safe,Anty Sai da Safe" ni dai tunda na shige Daki kamar Allah ya aikomin da barci ina Kwantar da Fadil nima nabi gefensa na kwanta sai barci sai asuba na tashi,Da Safe basu ma fito da wuri ba. Sai chan rana tunda naga ta fito tana Annushuwa na kalleta ina fadin"Ya ya.? Sai ta bani Hannu muka tafa Lokaci daya tana fadin"Komai ya daidaita. Ammh fa yace sai na ijiye aikina na Dawo nan sannan zai san ina son sa" Kai Tsaye nace"Sai ki nema wani anan ba Shikenan ba" Kai ta gyada min kafin tace"Haka za'ayi. Nasan zamu sha rigima da Daddy ne" Ina shirin mgana kawai daga bayanmu mukaji muryansa yana Fadin"Fa'iza wlh kiji Tsoron Allah. Ki kuma Tubar masa saboda abunda kike yi sam bai dace ba." Kafin nayi mgana tayi zaraf tace"Honey laifin me Maman Amir tayi ita kuma..? Sai ya harareni yana fadin"Tambayeta ita ai tasan komai" Sai ta juya tana kallona kafin tayi mgana na tare ta da fadin"Kada ki biye masa bansan abunda yake mgana ba"Saboda kada ya kara mgana na yi wuf na fice ina sauke Numfashi,shikenan ma'auratan suka Daidaita kansu,Sati daya tayi mana sannan ta koma ta kuma ta tabbatar min zata yi kokarin ta ijiye aiki sannan ta Lallabi Daddy ko gida ya siya mata a nan ni ko araina nasan Yaya Ishaq bazai yarda ba. kuma Tsakani ga Allah wannan gidan yayi mana kad'an ace mata Biyu da yara ga Mama shima ai sai ya Duba ammh yadda bai sakoni aciki ba nima ban Tusa kaina ba.. Maganar auran Halisa ya taso Anty Binta ana ta shirye shirye ni dai nace zan gyara amarya ta bangaran jiki da kamshi,kuma Anty binta na fad'amawa sai gashi tana min godiya sannan tamin mganar zatayi Zobo da kunin aya ranar walima tana so nayi mata,girki ma in ba damuwa na shige gaba ban nuna mata komai nace duk zan yi,mun yi waya da Badariya tace bazata dawo ba,ni na bata baki tace zata dawo ana gobe Daurin aure tunda kano za'a kawo amarya sai ta biyo su ta dawo abunta nace shikenan kuwa. Da kudina na siyo kayan hadin Turaruka na had'ama Halisa da na Rushi da Humra da kwallacha sun kai na Dubu ashirin,sannan ga na gyaran jiki tun ana saura sati daya biki take zuwa kullum da yammah ina mata Gyaran jikin. Ranar da muka kwana uku muna yi sai dare na gama mata,ita da wata kawarta suka zo,kuma tare suka tafi a dakin Mama nake yi mata ita tunda ta gidace,Mama sai mamaki take yi tana fadin"Ikon Allah.." Ranar na gaji,ko zobon yammah ban Dafa ba Hafsah na makaranta,bata dawo da wuri ba,Ban iya ko yin abincin Dare ba saboda bayana ya rike sai nayi wanka na gasa jikina da Ruwan zafi nayi sallar mangariba ina zaune ina lazumi Hafsah ta shigo ina ta mata fadan ina ta Tsaya sai tace min bata samu abun hawa ba ne da wuri, sai na Sassauta nace in ta huta ta Dafamana ko Cousscouss ne. Tace to bari tayi sallah Yaran kuma suna Falo Yaya Amir na biya musu karatu ina jin tashin muryoyin su daga Falo,Chan sai ga Hafsah da wayarta ta kawo min Abba ke son mgana dani bayan na dauka mun gaisa yacee"Kuna lafiya ina matata da megidan naki..? Nace"Duk suna lafiya Abba" Sai yace"To madallah kan mganar Binciken da nace za'ayi kan Case din mijinki ne,Engr ya dawo nayi mgana da shi yace ba matsala sai dai zamu kara jira Tunda mahaifin nasa yana London Mahaifiyarsa ke chan za'ayi mata Dashen koda. hankalinsu duk ba'a kwance yake ba shiyasa har yanzu bai yi masa mgana ba" Sai nace"Ayya Allah ya bata lafiya Abba"Sai ya amsamin mud'an taba Hira har ya bama Ammi muka gaisa tana min Tsiya"Hajiya Fa'i mai turaran kamshi" Dariya nayi ina fad'in"Kai Ammi" sai kawai tace"Abban ki ma yace y'ata ta iya had'a Turaren kamshi" Kunya suka bani su ko ba ruwan su Abba da Ammi sai su,mun gama wayar kenan naga mutum tsaye a kaina ina dagowa cikin mamaki nace"Sannu da zuwa" Sai kawai yace"ina son mgana dake. ki sameni a dakina" Daga haka ya fice mamaki ya kamani na rike haba a fili nace"Topha..! Ina shirin tashi aka fara kiran sallar Isha'i sai na mike nayi salla na idar kenan na mike ina ninke Darduma Anum ta leko tana fadin"Umma Daada na kira" Sai na gyada mata kai ban ko cire Hijabin jikina na fita zuwa Dakinsa ina Shiga sai faman safa da marwa yake yi har sai da nace"Lafiya..? Kai tsaye yace"Ina jin yunwa ina abincina.." Kai Tsaye nace"Aiki nayi nagaji sai da Hafsah ta shgo nace ta dafa mana ko Taliya" Sai kawai naga ya karisa ya rufo kofa da Sauri nace"Ya da rufe kofa..? Yana juyowa yace"Yau zamu yi ta kare Fa'iza hakki na zaki bani nagaji" Gabana ya fadi na kwalolo ido waje hakkina..? Na maimaita a raina. na shige su ga shi in nayi wani ihu yara na falo suna jin mu. bakina yayi nauyi ina ji ya ja har hannuna bakin katifarsa ya cire min Hijabin jikina cikin rawan murya nace"Abincin fa..? Kai Tsaye yace"Zamu ci in mun gama. Fa'iza bazan iya jira ba" Bakina naji yayi wani Dif. Jikina kuma Kamar mara Lakka, kamar rakuma da akala haka yafara bi da ni a gaggauce kamar daman ni yake jira. *Janafty* *KNKB2017* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Saboda yanayin da zuciyata take ciki yasa kwata kwata gangan jikina bai karb'i sakonnin dayake aika min da shi cikin zafin nama ba,Doguwar riga ce a jikina har ya samu nasaran Rabani da ita,ammh na kasa wani motsi na riga na Sadakar bani da wani Tsumi ballatana Dubara a lokacin. Bakina ne yayi min wani irin nauyi, ina ji kamar ya kumbura saboda irin yadda Yaya Ishaq ya rika sumbatata a raina sai cewa nake yi daman haka Sumbarta take..? Sharaf nayi masa ko hannuna ban yarda na motsa ba,kwance nayi masa kamar ruwa ya cinye ni,Ina jinsa yana gwama Numfashi,sama sama sannan Lokaci d'aya yana sauke ajiyar rai chan naji yana kiran sunana fad'i yake yi"Fa'iza ki rikeni. Ki rumgume ni don Allah"Ya fad'a cikin wani irin yanayin da ba kowa zai iya sanin yanayin ba. Nayi masa banza kamar ban ji ba, kuka ne ya taho min daga karkashin Zuciyata sai hawaye sharr sannan na saki Shesshekan har yana jina. Sai naji kamar an zare masa lakkar jiki ya koma ya kwanta a gefe yana maida numfashi. ni kuma ina ta kukana sai ya mike zaune cikin yanayin Sarkewar murya yace"Yanzu Saboda zan karbi Hakkina ne yasa kike wannan kukan Fa'iza.? Shuru nayi masa ban yi mgana ba sai dai ina cigaba da kukana kamar karamar yarinya sai kawai ya mike Kaina na juya gefe har ya gama Suturtata jikinsa,ina daga kwance kawai naji ya yi wuf ya tadani zaune yana fadin"Tashi ki saka kayan ki" Sai na bisa da kallo ina Tunanin ko ya fara samun matsala ne ganin yana komai a gaggauce. Mikar dani Tsaye ya yi ya na kokarin sakamin rigar na rike hannunsa muryata a shake nace"Bari zan saka da kaina"Kamar wacce zan gudu ina gama sakawa ya jawo hijabi ya zuramin Saboda Sauri kamar zai ciremin kai, nayi baya ina kallonsa da Tarin mamakinsa Maikon hawaye sun cikamin ido ban samu damar mgana ba. kawai ya finciki hannuna ya isa ga kofa ya Bude yana jana muka fito Falo yaran duk suna falon suna ganinmu suka bimu da ido ganin yana kokarin Fita daga Dakin yasa na Turje ina fadin"ina zaka kai ni..?. Bai ko Saurareni ba ya fincikeni zuwa waje sai kawai naga mun shiga Dakin Mama Lokaci d'aya yana fadin"Mama kin kwanta ne..? Mama na zaune saman kujera da waya a hannunta kamar ta ma gama wayar ne muka fad'o dakin yadda ta ganmu ne yasa ta mike a firgice tana Fadin"Kai lafiyan ku kuwa..? Gabanta ya zaunar dani yana Fadin"Mama gata nan ta fad'a miki meyasa take hanani Hakkina..? Ki tambayeta meyasa take guduna bata kaunar na rabeta. Mama Fa'iza na gudu na a Shimfid'a" Shi yake mganar nan ammh ni kunya da bakinciki sun rufemin ji na da ganina na wani Lokaci,Tsabar yadda na kad'u na girgiza da wannan wulakancin na Ishaq .ashe shi yana da bakin mgana ban sani ba..?ni shekarun da ya kwashe a jingine da aurene wajen wa na taba kai karansa.?sai shi ne yake da bakin mgana." Kaina na dunkule a kasa ina kuka kamar na mutu haka nake ji Saboda kunya ita kanta da Mama sai da ta kasa zama kunya duk ya Rufeta ta kasa mgana tana mamakin d'an yau. Kallonta yayi a rikice yana fadin"Baki ce komai ba Mama..? Sai Mama ta juya baya tana fadin"Fa'iza ki yi hakuri don Allah.Kada ki kara gudun mijinki a shimfid'a. kai kuma ka bita a hankali kada ka matsa mata." Wannan mganar ku ce Tsakaninku ne, don Allah kada ku kara sakani" Daga haka ta shige uwar Dakin ta tabar mu nan zaune,shi yana Tsaye ne kamar wani Saraki. Kafafuwana sun yi min zafin da na kasa tashi sai da na ganshi Durkushe a gabana yana fadin"Kin ji dai abunda Mama tace ko..?kada ki karamin Gaddama in dai na kira ki a Shimfid'ata" Sai kawai na Dago Rinannun Idanuwana na sauke a kansa cikin wata irin murya mai cike da Takaici nace"Meyasa ka kawo k'ara na wajen Mama..? Sai hawaye ganin kukana sai kuma ya Rud'eni ya fara kokarin son rikoni yana fadin"To ke ne Fa'iza duk yadda zan yi dake kin ki ganewa shiyasa na kawo kararki wajen Mama" Ture hannunsa nayi dake kokarin rikeni na mike Dakyar ina fadin"n ban taba kawo kararka ba. Ban taba fad'ama kowa halin da nake ciki ba,ko da yan'uwana ne. sai kai ne da bakin ka yafi nawa Tsini..?. Na karishe fad'a a Fusace cikin kuka Sai shima ya mike yana kallon Dakin da Mama ta shige Lokaci daya yana Fadin"haba mana.." Kuma wai yana kokarin rikoni Saboda bai da kunya a fusace na make Hannunsa ina fadin"Tunda kaso a fasa komai za'a fasa kowa yaji" Ganin ina nufar dakin da Mama ta shige yasa ya rikoni da karfi yana Fadin"Don Allah a'a Fa'iza don Allah" Daman ba fad'a zan yi ba sai na Turesa na kama Hanya na fita Daga Dakin mama,zan shiga Dakina ya Taremin Hanya yana faman marairaicemin sai kawai na juya da gudu nayi hanyar waje saboda naji hayaniyar yara har lokacin suna falo kamar abinci suke ci bana so su Fahimci abunda ke faruwa. Shima da gudun yabi bayana yana kiran sunana gaba na ya sha yana Haki yace"Ke ke ina zaki..? Cikin duhun Korodin dakin Jamal na balla masa Harara ina fadin"Tafiya zan yi..Zan tafi ne wlh bazan zauna dakai ba" Na fad'a masa cikin Tabbacin mganata sai ya Rude ya fara fadin"Ban gane ba. Wani irin tafiya kije ina kuma..?. Kai Tsaye nace"In da baza'a takurani ba sannan inda nima zan kai kararka.Nima ai ka jingine shekaru ina maka gadin ya'yan ja wa na taba kai ma kararka..?sai ni Zaka kai ma Mama karar na hanaka kaina ina ce ba kai ka ce na kyaleka ba..? Ba kai kace na barka kayi Sabuwar Rayuwa da wacce ka zaba ba .? Meyasa sai yanzu zaka matsamin na gayamaka aurena dakai ba aure ba ne yanzu,Jingina ne.." Na karishe fad'a cikin Tsawa lokaci daya ina kuka sai ya kasa mgana Saboda yadda na ke ture hannunsa in yakai min zai rikeni Cikin fitan Hayyaci yace"Ke ba ki Afuwa ne Fa'iza..?wlh na yi nadama na tuba na bi Allah na biki kiyi ma girman Allah ki saurareni" Da Sauri na daga masa hannu ina Fadin"Bazan saurareka ba. Na fada maka ka daina cewa aure aure, auren mu a jingine yake in ka cigaba da matsamin na rantse da wanda raina ke Hannunsa zan bar gidan nan Daman ya'yan ka ne kuma sun yi girman da zasu kula da kansu. Ahmad ne matarka ta had'a da na Hannunta da wanda zata haifa ta rike maka ammh in dai na tafi to Har abada BAZAN DAWO BA" Na karishe fad'a ina Tsaida kallona a kansa Cikin Firgici yace"Eh. A'a kije ina.?Fa'iza kina son ki kasheni ne..? In kika tafi to na zauna da uban wa.?.kai Tsaye nace"Ka zauna da Zainab wacce ka zaba sama da ni" Kara girgiza kai yayi yana fadin"Aa ba inda zaki.Ba zaki tafi ba Fa'iza in ba so kike na laalace ba" Cikin kuka nace"To wlh in ka kara matsamin sai na tafi kuma nayi Rantsuwan in na tafi bazan dawo ba. Sannan in ka kara kai karata ba ma wajen Mama ba,wlh ni kuma sai na Fallasa ma duniya komai, tasan Tsakanina Dakai auran jingina ne" Kamar na watsa mai ruwan zafi haka yaja baya yana fadin"Na shiga uku don Allah kiyi hakuri Fa'iza, eh naji Wlh naji na yarda bazan kara matsa miki ba ammh kimin rai kada ki fad'i wannan mganar wani yaji don Girman Allah.." Kukana na Tsagaita kafin nace"To naji bazan tafi ba. kuma kamar yadda nayi maka alkwari tun a baya sai dai kai ka fadi mganar da bakinka ammh ni nayi maka wannan alherin kamar yadda ka Rokeni,kada ka kara cewa zaka Takuramin ba wani hakkin ka dake kaina, domin tun kafin auran ka da Zainab ka rokeni da nayi maka adalci na kyaleka kayi rayuwa da wacce ta dace Dakai a lokacin ban yi maka korafi ba.  sannan ban taba maka gaddama ba har Tsawon yau din nan To nima bana son kayi min Korafi abunda ka zaba ne, nake yi maka kada ka kara damuna ni bani da jikin da zan baka ka mora sannan ban chanchanci wannan binbinin daga gareka ka ba. kyaleni don girman Allah. "Na karishe fad'a cikin Kuka ina Had'a Hannayena jikinsa a Sanyaye yace"Duk naji na yarda mu koma cikin gida kuma ki daina kuka ga yara chan kada su dauka na Dake ki ne" Ban yi musu ba na daina kukan na Share hawayena na kama hanya na koma yabi bayana muna Zuwa Tsakar sai ga Hafsah ta fito daga Dakin Mama abinci ta kai mata tana ganin mu tace"Fita daman kuka yi..? Da Sauri yace"Eh eh.." Dagaji bai da gaskiya ni dai daga shi har ita rabasu nayi na shige ciki Suna cin abinci yaran Anum har ta mike taga nayi Zaraf na shige Daki har da banko kofa,sai suka yi wani shuru Baban nasu na shigowa suka sakamai Ido duk sai ya Daburce Anum ne tace"Daada me ya samu Umma..? Da sauri yace"Umma.." Ya kasa mgana Amir ne ya kwace sa da Fadin"Kila bata da lafiya ne" jin haka yasa yace"Eh eh bata jin Dad'i kuci abincin ku" Daga haka ya wuce Dakinsa yana Zufa yaran suka bisa da kallo harda Hafsah da ta zargi wani abu na faruwa sai dai bata ce komai ba ta kira Amir ya Dauki abincinsa yakai mai,sai gashi ya Dawo dashi yace bazai ci ba. nima kuma sun kawomin nace su Dauke bazan ci ba,da suka shigo ma sun fara min Hayaniya na koresu nace kaina na ciwo,Su kansu sun san an tabani gabad'aya har wayewan gari suma duk sun yi wani iri ban ma fito ba Hafsah ta musu komai Hatta zobo ita ta Dafa ta barmin na hada ta wuce makaranta shara da wanke wanke kuma Anum tayi shi ban fito ba sai da rana Saboda zuwan dangin Mama daga yamai dole ta sani na Dora girki,Yaya Ishaq na dakinsa in ji Anum ammh ban ko duba barayinsa ba,Da yammah Halisa tazo nayi mata Dilka washegari da Safe muka hadu na gaisheshi ya amsa sannnan na gayamai yau zan je gidan Anty Binta akwai Walima ba gaddama yace a dawo lafiya, ni kadai na tafi yara suna makaranta Anum kuma tun safe tabi Anty Hure suka tafi. Sai Dare muka dawo chan Badariya ta iskemu an yi walima ni nayi zobo da kunin Aya sannan tare da ni akayi cake din Rabo,Da Sassafe kuma na koma Saboda girki duk da ta Dauki ma'aikata ammh ni zan rika nuna musu komai yara basu je makaranta ba Hafsah da ta shiirya ita da Badariya ta taho da su,Hajiyar Dala ta zo ita da Suwaiba,Yaya Asiya ce bata samu zuwa ba Yaya mariya ma tazo abun mamaki har da su Anty Nasara,gida cike da baki na nesa da na kusa, aranar za'a Daura aure,sai washegari Lahadi da safe a wuce da Amarya mun yi waya da Nana Fatima da farko ban fad'a mata zan zo kano ba saboda nayi Tunanin in na tafi wazan bar ma gida? ammh Daga baya sai na fasa nace sai naje shi ya zauna ya kula da gidan da ya'yan sa. ban yi anko ba saboda bata nuna ma kowa ba,ammh nima na yi shigar alfarma cikin kayan da Hajiya ke dinkamin ne super wax na saka,Da Daddare gida na muka dawo da su Anty Nasara yaya mariya dai chan muka barta daman nasan bazata Biyoni ba. Amir na aika nace ya gayamasa zan raka Halisa kano,kai Tsaye yace Allah ya kiyaye hanya,Da yake shima da Safen ya shirya ya fita saboda Daurin auran Safe ne Na fad'ama Mama zanje kano sannan zan bar yara Saboda makaranta Ga Hafsah ga babansu tace ai daman ya kamata naje ni ko bata sani ba gidan ne da D'anta suka isheni. zan yi musu yaji na kwana Biyu. Kaya kala Biyu na dauka da abunda zan Bukata,Anty Nasara ce zataje Goggo gida zata koma Hajiyar Dala Daman yan gida ne suna cikin masu tafiya. Karfe goma da rabi aka Daura aure zuwa sha biyun rana an fara tafiya Saboda kada ayi dare ni mota D'aya muka hau da Badariya da Anty Nasara,Yaya mariya bata je ba megidanta bai barta ba. Anum har da kukanta sai taje sai da nayi mata Jan ido Amir daman bai da damuwa sauran kuma suna wajen Babansu. Ban taba zaton zan iya tafiya na bar ya'yana ko da na yini d'aya ba sai ranar, na gwada ne daman naga ko zan iya sai dai muna tafiya ne ina jin kamar na bar baya da kura.?wazai kula da su..?Hafsah tana zuwa makaranta shi kuma bai iya komai ba ballatana ya Kula da su, sai dai hankalina ya kwanta da na Tuna na Horar da ya'yana Musamman Amir da Anum zasu kula da Sauran kannensu. Dama already an yi ma amaryan jerenta gidanta mai kyau ita kad'ai,da muka isa abinci muka ci sai sallah sai kuma dan Saura gyare gyare kawayen Anty Binta sun kama komai yasa mukayi musu sallama sai gidan Yaya Asiya. chan muka kwana muna Hira harda Badariya,washegari Litini muka shiga kasuwa na raka Anty Nasara nima har na siya ma Anum takalmi mai kyau na mata, da muka dawo har da Yaya Asiyan muka leka gidan Amarya chan muka hadu da ya'yan Hajiyar dala sai dare Direban da zai maida su gida ya Saukemu gidan Yaya Asiya ranar Talata Anty Nasara tace mu tafi sai nace ta tafi zan taho bata Damu ba ta wuce karofi a ranar,ni kuma bansan Dalilina nakin komawar ba Yaya Asiya kuma tasha Ishaq ne ya barni Har tana jin dad'i. Tun da muka zo bai kirani ba sai ranar Laraba da Daddare ina Dakin Yaya Asiya ita kuma tana wajen mijinta naga kiransa sai nayi mamakin sanin bai da waya bayan na Dauka mun gaisa sai yace"yaushe zaki dawo.? Yara sun damu fa" Sai na basar da tambayar sa,ina ya samu waya na tambaye sa,kai Tsaye yace"Zainab ta aikomin daga chan" Sai na yi shuru ban yi mgana ba ganin haka yasa sai ya mika ma yara wayar duk dai korafin Umma yaushe zaki dawo ne? nace zan dawo kada su damu ina Tunanin har da shi ya Dinga matsa musu su ji yaushe zan dawo ni ko a raina nace ba yanzu ba,ko zan dawo .har ga Allah ba da niyyar zuwa Dutse nazo ba sai da Yaya Asiya ke min Tadi'n ba nisa fa daga kano to Dutse gidan Nana Fatima kamar almara sai  ko nace zani na kirata na Fad'amata ta daka Tsalle da Ihu tace in na hau mota da nazo tashar Dutse na Kirata zata zo ta Daukeni nan da nan naji Kwadayin zuwa na yi ma Yaya Asiya karya da ta tsareni da tambayan shin an bar ni..? Nace mata eh mana ya barni sai ta kyaleni mijinta yarakani na hau Mota ranar jumma'a gabana na fad'i hakan nan na Daure bayan na roki Allah ya yafe min na yi doguwar tafiya mijina bai sani ba, Sai ko gani a Dutse ina kiranta sai gata tazo ta Daukeni har tasha muka Rumgume juna. Sai gani a kayattacen gidan Nana Fatima mijinta babba ne Aikinsa D'an sanda farin kaya ne,Ita da mijinta kamar zasu goyani yana Dawowa a gaba na suka rumgume juna yana da fara'a kamar ita yana ganina Tun kafin na gaishe shi yace"Sannu da zuwa Fa'in mu maraba da zuwa Dutse" Ina mirmishi na amsa masa duk yadda zan baku labarin gidan Fatima da Ahalinta sun wuce haka,Ya'yanta Jalil da jidda tun saba dani kamar sun sanni daman gani da son yara, Daki guda Nana Fatima ta ware min kuma har ta Kira chan gida ta fesama su Abba zuwana. Ammi tace kafin na koma Nana Fatima ta rakani har kano na gaida Hajiyar su tace in sha Allahu zata kaini,gani nayi dai ban kyauta ba, ranar da na kwana na yini na kirasa na fad'amasa ina Dutse gidan Nana Fatima. kai tsaye yace"Kika tafi har Dutse baki fad'amin ba Fa'iza..?ai naga dai duk lalacewar aure sunansa aure" Sai na kasa mgana nasan ban kyauta ba yasa nace"Kayi hakuri.." Bai ce komai ba illah yaran da ya mika ma wayan muka yi mgana Duk sun damu da in dawo daman mun yi waya da Hafsah ta fad'amin Ahmad nata rigiman bana nan,sai na fara Tunanin komawa gida kwana hudu nayi a Dutse kamar kar in dawo,Nana Fatima macece mai kirki ita da mijinta sun fita dani naga gari sannan zama da fatima yasa na kara sanin ita mace mai Daraja ce sannan yar kwalliya ce. A na gobe zamu tafi kano da ita ni dagachan zan wuce katsina take kara min mganar Zainab kai Tsaye nace"Ina da abokiyar zama ammh tana Abuja chan take zaune" Cikin karin mamaki tace"kuma tana da ya'ya..? Ina dariya nace"Sosai biyu har da cikin na uku ma" Sai ta rausayar dakai tana fadin"meyasa ita tana Abuja ke kuma kina katsina..? Ganin Nana Fatima ce akwai yarda Tsakanina da ita yasa na gayamata kadan daga abunda ya shafeni sai dai ban gayamata irin zaman da nayi da Ishaq da jinginar aurena  dashi ba,sai dai na gayamata Dalilin da ya sa zainab ta zauna abuja ni ina katsina. Cikin mamaki tace"Tab kuma tana zuwa gidan ki na katsina ki sauketa a Dakin ki..? Ina Dariya nace"A'a dakin dai megidan" Sai ta bude baki tana mamaki Dariya ta bani na kwashe da dariyan ina fadin"Rufe bakin Mana" Sai ta rufe lokaci d'aya tana Fadin'"Lalle kina da karfin zuciya wlh bazaki kwanar min a shashe ba..Tabdijam" Dariyan yadda take jinjina abun nake yi a raina nace don ma bataji ni ke Dawainiya da su ba da sai ta zageni,a kwana Hud'un da nayi da ita na kara sanin wasu abubuwa na kuma kara yarda kwalliya da ado  na duka mata ne,ba na bambamcin Fata ko kyawun Fuska ba. Na kuma kara sanin ko kana da kyau to ka kara da wanka sai kafi haka kyau gata dai mai kyau da ita ammh kwalliya da gyara bata rabo da shi har mgana nayi mata nace"Nana baki gajiya da kwalliya da gayu..?me zaki gyara ke da komai Allah ya baki mai kyau a jikin ki" Dariya tamin kafin tace"Ko kana da kyau Fa'i ka kara da wankan sannan ki yi shuru kawai ba komai Allah ya bamu ba. muma duk barazana muke da kwalliya da gayun yana karamana kwarjini" Kuma na yarda da mganarta,Domin naga gayu in da ake kiran gayu a wajenta tana fadin Ammi yar gayu ce sannan bata shiri da wanda bai son gayu,nace tabbas na shaida haka Sai naji nima ina so na fara gayun nan na shiga Sahun manyan mata Cikkaku. Washegari Direban mijinta ya kaimu kano har gidan Yaya Asiya tare da ita muka dumguma zuwa gidan su Ammi,sun yi murna sosai sai nuna ni suke yi suna tambayan ita ce Fa'in Azizat mai turaran kamshi sai Nana Fatima ta gyada kai wasu daman mun Hadu Bikin Yaya Abdul'Ahad,Balle kuma daman Yaya Asiya ta zama yar gida,Duk yadda naso na wuce katsina a ranar bai samu ba saboda mun jima muna Hira a gidan su Ammi ita kanta Nana Fatima tayi yammh don dai motar gida ce. Mun fito gidan su Ammi Nana Fatima ta nuna mana wani katon gidan Bene tana fadin"ina Engr din da zaku ji Abba na yawan mganarsa..? Sai muka d'aga mata kai Saboda duk wanda yasan Abba yasan Labarin megidansa Engr. Cikin Nuna mana gidan Nana Fatima tace"Ga gidan kakaninsa ta bangaran Uwa.nan aka haifi mahaifiyarsa dalilin makotansu da gidan su Ammi ma Suka hadu da Abba." A tare da Yaya Asiya muka jinjina kai ina kallon gidan daga gani masu gidan suna da kudi sosai,irin kamar fasalin gidan da Abba ke ginawa a karofi sai dai wanchan ba gidan ba Bene ba ne. Muna tsaye jikin motar da zata maida ta gida muke mganar Yaya Asiya ta ce"To ina masu gidan..? Nana Fatima tace"Hajiya Tafisu ce mahaifiyar Hajiya Shukra ce kadai a gidan sai ya'yan yan"uwa Datake riko megidan ya rasu da jimawa daga ita sai yan aiki a cikin wannan gidan" Na  jinjina kai ina kara kallon gidan da akace mace d'aya ce aciki Nana Fatima ta cigaba da fadin"Shi Engr babansa bayarbene mutumin Beneu ne, Hajiya Shukra ce bahaushiya suna Abuja da zama. Sai dai dangin su kaf suna Beneu har kakansu tana chan da ciwo ya kamata ne ma ta koma hannun Hajiya Shukra,Engr kuma shi a Edo yake aiki" Ni dai har gajiya nayi da labarin Engr Nana Fatima ko ta zage har Yaya Asiya na tambayan"Tab.To ya"yansa nawa..? Nana Fatima tace"Tab. Bai da ya'ya fa, ya taba aure sau da'ya sati biyu matar ta kone da gas shikenen bai kara aure ba. kuma fa Abba ya girmesa, matashi ne sai dai yana da kirki sannan ya taka matsayi mai girma da kananun Shekarunsa" Gani nayi sun bud'e hirarsa da Sauri na katsesu da fadin"Nana kada ki yi Dare" Sai da nayi mgana ta farga Mukayi sallama Ta shige mota suka tafi,Dole na kara kwana gidan Yaya Asiya washegari motar asuba na hau sai katsina,Ance in mace mai ya'ya ta fi sati bata a gida sai abunda ta gani nima haka na tarar,kudin zobo da kunin aya sun ci ubansu,Hafsah sau Daya take yi a rana watarana ma in bata da Lokaci batayi,sannan kudin kuma suna tabaawa in zasu siya wani abu ,sannan yara wlh sun yi kewata ranar da na dawo yini Ahmad yayi Tsalle acikin gida,Shi kan shi Gogan bakinsa har kunne har da fadin"Mutanen kano da Dutse maraba"a Tsime na amsa masa nazo musu da Tsaraban Dutse da Nana Fatima ta bada a kawo masu,nafi kwana Biyu,gidana da kasuwancina bai Dawo daidai ba,Na yarda mace itace gida ranar da bata to sai kame kame har Mama tayi murnan Dawowata.. A satin kuma naje Karofi,Matar Yaya isa ta haihu naga ginin Abba an kusa gamawa a raina nace komai in da kudi an yi an gama,ammh duka duka yaushe aka fara ginin nan har an kusa gama shi..?ban kwana ba na dawo gida Hafsah chan na barta zatayi weekend,ina kuma Dawowa na iske wani sabon salo ban sani ba ko Mahaifin zainab ko ita wanda ya kirasa kan zainab zata baro aikinta ta biyo shi katsina ammh sai ta fara neman wani anan sannan zata zauna agidanta ne ita kad'ai in ya amince shi ko yace bai amince ba sai dai tazo mu zauna tare a wannan gidan. Yana gayamin takaici ya kume ni na kallesa nace"To gidan da zata zauna wazai Dauki nauyin sa..? Kai Tsaye yace"Daddy ne mana" Nima kai tsayen nace"To meyasa bazaka barta ta zauna inda zata Sake ba.?Mganar gaskiya gidan nan yayi mana kad'an ban ga inda ita da yara zasu zauna ba abun kuma yayi yawa" Hade rai yayi kafin yace"To wai haukatani zaku yi ne..? Nace Haukatani zaku yi ne..? To anan zata zauna nace" Sai na bude ido kafin nace"Ba damuwa ta zo mu zauna din na d'an Lokaci ne, kowa zai san matasayinsa" Mgana na gasa masa ammh bai gane ba,Ya gimtse bakinsa nima na kama kaina ina ji har Mama sai da tayi  masa mgana tace gidan yayi mana kad'an ammh bai jita ba. Har Anty Binta sai da mama ta kira ta shaida mata, itama fad'a ta hau yi masa na gidan ya yi mana kad'an,shi kuma yace ba ruwanta shi ya yi alkwarin bazai kara yarda a rika juyasa ba. Karfin Hali kenan baka da ko asi sai bakin rai da isa,tab zan ko ga yadda wannnan zaman zai kasance. Sai dai na roki Allah kafin hakan ya faru Allah ya bani mafita. *Janafty* *KNKB2018* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Magana fa taki ta kare,Saboda Yaya Ishaq yayi rantsuwan Zainab bazata zauna a ko'ina ba sai gidan nan tare da mu,kuma bazai amince Mahaifinta ya kama mata gida ba. Kowa yayi mishi mgana ammh bai ji ba,daman yana da Taurin kai wani Lokaci sannan rashin aikin nan nasa yasa zafin zuciyarsa ta karu,Mama gajiya tayi da mai mgana ta kyalesa har da kaninta Dake yamai ta had'a shi ko zai ji mganarsa ammh yace matsayarsa kenan. Ni tunda nayi mai mgana yace nan din zata zauna ban kara masa mgana ba,na cigaba da Harkokin gabana. Ammh ganin ya dage da gaske yake yi yasa naji kamar nima in kai k'aransa wajen Abba ko Yaya Abdul'Ahad da kan kirani shima duk bayan kwana Biyu yaji lafiyata,Sai kuma na fasa saboda kai kara ba Halina ba ne sannan bayyana sirrin aurena ba Halina ba ne shima,ammh mganar gaskiya Yaya Ishaq zai tauyemin hakkina,Kuma gani yayi ya saba shiyasa yake so ya gwamatsa mu acikin wannan gidan. Ni ban ma jin kaina nafi jin yarana Saboda komai daman nake yi saboda su ne, an saba tauyemin hakki na Hakura saboda su daman. Sai nafara tunanin in Zainab ta dawo gidan nan a ina zai sauketa..? Dakinsa dai falle d'aya ne,Sai bayi rayuwar mace bazai yu yu acikin wannan Dakin ba,bansani ba ko Dakin yara zai sauketa ko kuma ni yake so ya fitar dani daga dakin ya sakata ban yi dai mgana ba na zura ido ina ganin ikon Allah. Ban sani ba ko sun yi ta ja'in ja da Zainab din ne,kan mganar sai kuma Kwana Hud'u da fara mganar sai ga Mahaifinta Dr.Lawal ya diro gidan Dakin Mama ya sauka sannan,sun jima suna mgana da Mama domin da kan shi yace shi Ishaq din ya basu waje zai yi mgana da Mama, daman wajenta yazo sai ya koma Daki yana cika yana batsewa ina tsakar gida ni dai ina Harkokina ban bi ta kansa ba. sai bayan awa D'aya da wani abu Mama ta leko ta kirasa,ya shiga shima ba jimawa sai ga shi ya fito ya kirani Lokacin kuma na gama Dafa zobo ne, sai na bar ma Anum ta kular min da shi kafin na fita na koma Dak'i na sanya Hijabi nayi sallama Dakin Mama na shiga. Mama da Dr.Lawal ke zaune kan kujera shi kan shi Uban gayyar yana zaune a kasa nima sai nabi ayarinsa na zauna a kasa dagachan bakin kofar cikin Ladabi na kara gaisheshi, sai naga ya amsa cikin kulawa ba kamar sauran Lokutan da in na gaisheshi yake amsani a wulakance ba. Mama ce ta kalleni tana fadin"Kan mganar Dawowar Zainab nan ne. Yazo mun yi mgana yace a kira ki  Saboda mganar ta shafeki" Tana rufe baki yayi gyaram murya ya cigaba da fadin"Ai itama y'ta ce Hajiya. Engr Usman karaye mutumin kwarai ne mun yi zumunci sosai da shi Lokacin muna masters a Buk bayan mun gama shi sai bai cigaba ba,ni kuma sai na tafi nayi Phd dina,nayi mamaki da ya ce min ke y'a kike a wajensa" Kaina na kasa ban yi mgana ba sai yanzu nasan wato Dalili kenan da ya fara sakemin Tunda yasan Abba, kai wannan rayuwar sai Allah wa ka sani waya sanka ne. ya manta nan ya taba cewa zai batar dani har da Dangina akan yarsa ammh yanzu ko kunya ya zauna yana fadin nima yarsa ce' Ina jinsa sama sama yana cigaba da bayaninsa Ishaq yake yi ma fad'a akan ya nemesa yazo ammh yaki zuwa. Mama ce ta karb'esa ta basa Hakuri da Fadin"Ayi hakuri Alhaji ni kaina bansan meke damunsa ba kwanakin nan" Mirmishi yayi kafin yace"Rashin aiki ne Hajiya kuma ina nan ina masa kokari. yanzu haka kwamitin Binciken da na kafa ya fara nisa kuma da yakinin insha Allahu za'a samu mafita" Mama ta amsa da karfin Gwiwan Allah yasa a dace da mafita na Alheri,suka amsa da Ameen nima sai na amsa acikin raina Yaya Ishaq kansa na kasa bai ko Dago ba,Sai da shi da kansa ya kira sunansa sannan ya Dago yana amsawa,Cikin mirmishi Dr.Laawal yace"haka ake yi sai kayi fushi da Baban ka.?ni har Abada a D'a na Dauke ka. Kaunar da nake yi maka yasa na baka auran yata mafi soyuwa gareni. Wlh tallahi ba domin kai ba ne bazan taba yarda Zainab ta baro inda ta saba rayuwa zuwa wani wajen ba,Sai dai tana sonka sannan ta shirya ta zauna dakai,ammh sai nace ga Sharad'ina zan nema mata gida inda zata zauna domin bisa adalci ban ga wajen da zata zauna anan ba,Kuma ga Dawainiyar yara achan duk na Dauke ma kasu gata nayi maka sai kuma naga baka gani ba,kana Tunanin ina maka iko ne da matarka,Sannan nace zan nema mata aiki a nan garin,da aikinta ka sameta baka kuma da ikon da zaka hanata. Ammh sai naji kace baka yarda ba,Sai dai ta zauna anan tare da ku kai kanka kayi ma kanka Adalci,Ta yaya zaku zauna awannan gidan kalli fa gidan ga yara ga ku haba sai kace akuyoyi zaka saka ba Mutane ba..? Ya fad'a cikin zolaya da yanayin mganarsa zaka san sulhu yake nema Saboda yarsa shi kuma nashi Jarabawar kenan,ammh duk wad'anan mganganun bai shiga kunnen Yaya Ishaq ba. yana dagowa sai cewa yayi"Gaskiya ni Daddy bazan amince kace zaka kama ma Zainab wajen zama ba, nan din zai ishemu muma aciki muke zaune me ya ci mu..?Fa'iza nan take zaune da su Amir kuma akwai ishasshen wajen da zata zauna bazata Takura ba, idan ma har zan raba musu gida sai dai in ni na kama Hayar da kudina ko na siya gidan. ammh alfarman ne Daddy bana so, ba domin kuma na raina kokarin ka a kaina ba,a'a wlh nagode sosai bisa Dawaniyar ka gareni" Ya karishe fad'a cikin Ladabi Dukkanmu shuru muka yi ni sai satar kallonsa nake yi ina ganin mamakinsa mutum ka Dage baka da ko asi lalle zan ga yadda za'ayi wannam zaman. Mama ranta ya baci ta taso mai tana fadin"Kai dai ka cika Taurin kai meyasa baka jin mgana ne..? Kai tsaye yace"Mama ki bar ni kawai akwai abunda nake dubawa ne. Indai tana so na to zata iya zama dani a duk inda rayuwa ta kaini. kamar yadda Fa'iza ke zaune dani" Ya fada yana kallona sai na kauda kai nace ji wannan zai jazamin bakinjini Daman sunan Abba ne ya wankeni,To yana ambaton sunana tsakani ga Allah,Shi ko Dr.Laawal jinjina kai yayi kafin yace"To duk naji zencen ka, nuna min in da in Zainab d'in ta Dawo zata  zauna..? Kai Tsaye yace"ko ta zauna ad'aki na akwai Tiolet aciki. ko kuma dakin yara sai su koma Dakin Mama tunda Badar na kano duk inda ta zaba duk D'aya ne" Baki na bude galala ina kallonsa yako hade rai yasha mur,Mama tace"Wannan wani irin lissafin banza ne..?Kai ya girgiza ma Mama yana fadin"Ba lissafin banza ba ne Mama. Mganar su Fadil kuma Fa'iza zata rika kula da su" Jar uba bansan haka mutumin nan ya raina ni ba sai yau, wato mganar yara Boyi boyi yar reno zata kula da su kuma bai ji kunya ba,Saboda daman baisan adalci ba kuma bai san yadda ake yi ba,Kamar zan yi mgana sai kuma na fasa saboda gani nayi ko nayi mgana babu amfani ammh na rantse da Allah in ya fitar min da ya'yana daga bangarena to sai dai mu fita tare da ni da su,domin  bai isa ba. Dr.Lawal dariya yayi kawai. Tsakani ga Allah uzuri ya yi masa talauci ai bone ne,Yana saka zafin rai da tunani masara kyau Mama zata fara fad'a ya Dakaatar da ita da fadin"kyalesa Hajiya na Fahimce sa. Shikenan zata Dawo ammh sai aikin nata ya samu,Ina kan nema mata ne,kai dai ka gyara mata muhallin da kasan bazata Takura ba tunda a inda ka Daukota ba'a Takure ka ganta ba" Kai Tsaye yace"Daddy gidan iyayena Dabam gidan aure dabam. Ba lalle sai ta samu abunda ta ke samu a gidan su ba,in ina da shi zan yi mata abunda yafi wanda take samu a gidan su, in kuma bani da shi zan kwantata daidai misali" Kai ya jinjina yana fadin"Gaskiya ne'" Ni kaina nayi mamakin yadda yau ya yi laushi,ammh ba'a san yadda ransa ke bace ba ne. Saboda Zeey yake komai ta rokesa tana kuka kada ya yi Fad'a da Ishaq she love her Husband kuma ta shirya zama da shi a ko'ina. da ya nuna bai amimce ba, sai dai a raba auran sai Hajiya Halima tayi masa Bore ta tafi Chan rugar adamawa ta kai karansa wajen iyayensu akan zai kashe ma zainab aure,Kiransa suka yi suka yi masa Fad'a sannan da ikirarim Zainab akan in ya kashe mata aure to zata shiga Duniya sai ya rud'e zai iya juran komai ammh ban da Nesa da ya'yansa sannan zai iya rasa farincikinsa akan na ya'yansa ba haka ya Dauka yaron yake ba ya Dauka yadda ya rika Juyasa a farko yanzu ma haka zai juyasa. Sannan bai taba zaton Reshe zai juye da mujiya ba,ya dauka shi ne zai so zeey kamar ransa ya rika binta a daidai wannan Lokacin basu ne zasu rika lallaba shi bashine zai rika Lallabasu sai ga shi komai yana Faruwa ba yadda ya yi zato ba shiyasa yayi kokarin Daidaita Fushinsa. Sannan yana mamakin kamar Engr Usman da ya sani mara d'aukan reni da Tsage gaskiya shine Diyarsa ke zaune in da bata Daraja,Tun farkon had'uwarsa da Ishaq  yasan Fa'iza bata da wani Daraja a wajen sa. balle in akayi duba da abubuwan da suka yi ta faruwa,Sai dai yayi tunanin kila ra'ayinsa ne ammh shi kam bazai iya barin yarsa cikin wannan Wahalan ba Allah na gani. Bai jima ba,suna gama mganar su ya tafi Daman jirgi ya shigo daga Abuja zuwa kano sai ya Dauko tashar Taxi zuwa katsina kuma yana jiransa zai maidasa,ni dai tun a matsayar farko ya sallameni na fito na cigaba da aikina ammh mamakin bawan Allah nan bai fita kaina ba wai yara su koma Dakin mama..?lalle bai taba ganin Haukana ba ne zai gan shi kwananan kuwa karyan Iskanci ma yake yi wlh raina ranar yini yayi a bace,ko fara'a ban yi ba shima kila hakan ya gani sai bai min mgana ba,Sai washegari yaran sun tafi makaranta Anum na tsakar gida tana shara basu fara daukan yan Jss1 ba ne wannan karon da wuri ba shiyasa. ammh komai nata Abba ya riga ya Turomin kudin Sakata kawai za'ayi. ina D'akina ina had'a kudaden hannuna Hafsah zan kira akwai wasu kudi a hannunta ta biya kasuwa in ta Dawo ta siyomin siga na ya kare. Kamar Daga sama naga ya fad'omin cikin daki a kaina ya tsaya a gabana kere kere,Sau d'aya na kallesa ban kara ba na cigaba da had'a kudina sai naji ya zauna gefena yana fadin"Fa'iza baki ganni ba ne..? Kai tsaye nace"In na ganka me zan yi maka..?kai ka shigo min Daki ko Sallama baka min ba" Sai ya gyara zama yana fadin"To Salamu Alaikun shikenan" A tsime na amsa masa daganan na bama banza ajiyarsa na lura yana so yayi mgama ya kasa sai kame kame yake yi har da tashi yana leka band'aki da kara Duba Dakin na d'ago ina kallonsa cikin mamaki kafin nace"Hala kayi ajiya ne kake nema.?. Sai ya fara sosa kai yana fadin"A'a ina duba dakin ne sai yau na Lura yafi Dakin yaran nan girma ashe.." Sai na yi kasake har kofafin hancina na budewa na shaki iska a kasan makoci na kafin nace"Uhm" Kai tsaye kuma yace"Shine sai nayi wani Tunani me zai hana ke ki koma Dakin yaran nan ita kuma Zainab sai ta zauna anan tunda yafi girma kinga ita ba rayuwar mu da'ya da ita baa,akwai Danne hakki in na ce ta zauna Dakin yaran nan yayi mata karami kinga Dakinta na Abuja? Wlh yayi biyun wannan Fa'iza.." Daman nasan za'a zo wajen mai Hali bazai fasa halinsa ba. meyasa nake Tunanin Ishaq zai iya daidaitani da Zainab.?har abada ta fini a wajensa matsayina bazai taba zamowa d'aya da nata ba,Nagode ma da ya sa Rud'add'en kalamansa basu Rud'eni na sake bashi kaina ba.da yanzu na fi kowa nadama. Maganar bata D'akina ce ma ta tsaya min arai,na bude baki yafi sau biyar ina rufewa sai kawai na maida Hankalina kan kirga kudin hannuna kama kansa ya yi,sai ya durkusa a gabana Lokaci d'aya yana fadin"Kin gane Fa'iza ki Fahimceni wlh ba da wata munafa nayi wannan mganar ba. Nasan ke zan iya sakaki komai kiyi min sannan zaki zauna dani ko a dakin Bukka ne,ita kuma ba kamar ke ba ce shiyasa kikaji nace haka don Allah kada ki Daukeshi a wani abu" Ya karishe fad'a yana min uban magiya sai kawai na mike idanuwana ne suka ciko da kwallah me na zama ne.?na tabbata har abada in dai a Rayuwar Ishaq kabir korofi ne ni Fa'iza bazan taba samun daraja ba. Gaban Wadrope d'ina na tsaya kawai na rasa me zan yi ma saboda takaici,Ina jinsa ya mike yana fadin"Kin ji Fa'iza baki ce komai ba..? Juyowa nayi bayan na Saita kaina Lokaci d'aya nace"Me kake so nace.?ai ba shawarata kake nema ba Hukunci ka yanke sai kuma ka ke bani Umarni,ba komai kada damu ni daman ban taba had'a kaina da matarka ba nasan tafini Daraja. Zan kwashe kayana kada ka damu ka fad'amata zan bar mata Dakina na har Abada" Na fada Lokaci daya ina kokarin wucesa na fita Daga dakin kawai sai ya Riko hannuna a fusace na juyo ina kallonsa irin kallon da na sakar mai ne yasa ya sakeni da Sauri a Shake nace"Nace maka zan bar mata dakin nawa har abada daman ai D'ofane nake kada ka damu. Hafsah daman ba zama zatayi ba Abba na nema mata Transfer zata koma kaduna yara kuma ya'yanka ne ko a soro ka zaba musu su zauna bazaka samu matsala da Fa'iza ba" Ina gama fadin haka na fice daga d'akin domin ji nayi iskar Dakin tamin kad'an,na rasa ina zan shiga sai kawai na shige kitchen na fara safa da marwa Anum ta shigo kawo kwanuka ban ma ji shigowarta ba sai ji nayi tace"Umma lafiya..?Da sauri na goge kwallar da suka kawomin,na juyo ina kirkiro mirmishi kafin nace"Bakomai kin gama wanke wanken.? Kai ta dagamin kafin tace"Yanzu zan wanke tsakar gidan ko Umma..? Sai na jinjina mata lokaci daya ina fadin"Gama ki tayani zuba zobon nan in ya wuce kada su kawo wuta bamu saka ba" Sai ta amsamin da toh Umma,Falo na koma shi kuma daidai ya fito ina ganinsa sai na juya na fita wlh bana son ma ganinsa,a kwanakin baya sai naji kamar Burina zai samu Rauni na fara Tunanin sauke kudurina,ammh yanzu na ji na samu karfin gwiwan da zan iya tunkaran komai menene tabbas ina Bukatar Sabuwar rayuwa ina son na shaki iskar yanci nima. Gabadaya yini yayi son kara min mgana ni kuma ban yarda mun had'u ba,ga shi dai nace na amince ammh kuma Fuskata ba fara'a Da Daddare na kira Abba muka gaisa sai na masa mganar Hafsah cikin barkwancin sa yace"Ina ta kokarin nema mata Transfer Fa'i..Wlh tallahi ko kuma ba domin aure ba,da gabad'aya zan tattaraku a gidana"Sai nayi dariya ina Tambayansa Ammi yace"Tana chan ta na kwalliya kinsanta gayu gayu dai Mamam Nanah taki ta bar ma yara"Da Sauri nace"Abba ta bar ma yara ka kyallo wata yar caras" Sai ya fara Dariya yana fadin"Fa'i Laala..aiko baku isa ku hanani kara aure ba.ku gama shafa dai jan bakin da hoda sai nayi ehe" Ni dai sai Dariya nake yi tuni Abba ya mantar dani Damuwar da nake ciki mun jima muna mgana,Sannan muka yi sallama,Mun gama wayar kenan sai ga Kiran Nana Fatima itakam sai da taji yanayina ba Dadi tace"Fa'in mu ya ya ne.?naji ki wata so silent ne" Sai nayi saurin ce mata kaina ke ciwo sai tace na sha mgani na kwanta da Safe zamu yi mgana da haka muka yi sallama sai kawai na kira Goggo ita har ta Tsorata cikin Tsoron tace"Fa'iza lafiya kuwa.?goma saura na Dare fa" Ina dariya nace"Lafiya lau Daman na kiraki mu gaisa ne naga kwana biyu kin manta da D'iyarki"Sai goggo tayi dariya kafin tace"Kina raina Fa'i nasan kina lafiya ke da yaranki,hidima tayi miki yawa Fa'iza kinsan sana'ar hannu tana da wahala nasan sai hankali yanzu"Gyada mata kai nayi kamar tana ganina kafin nace"Na saba goggo ba matsala ga Anum kinsan tana gida sannan in Hafsah na gida tana taimakamin,haka ma yaran ma in sun dawo. Amir kinsan san shi sarkin aiki su shara har girkin su taliya ya iya Goggo"Sai goggo taji dad'i har sai da ta bayyana min cikin Murnan ta tace"Masha Allah Dakyau.Dama iyaye su rika tunani irin naki Fa'iza su rika koyama yaransu, aikace aikacen gida tun suna da kananun shekaru, saboda taimakon iyaye da kuma taimakon kansu a duk inda Rayuwa zaata kai su Allah yayi albarka Allah ya shirya miki yaranki,Allah ya Daukaka su alfarman Annabi muhammadu salallahi alaihi wasallam" sai na samu kaina da Hawaye sun cikamin kwarmin idanuwana, ina amsawa da Ameen Ameen cikin jin dad'in da ya bayyana har a murya ta. kafin nace"Goggo Baba ati tana kaduna abunta..? Goggo tace"Tana ko chan Fa'iza ta samu hutu,Inno tace bata son ta dawo ta samu abokiyar zama ai ma ginin Abban naki an kusa gamashi kila in ya kammallu ta dawo" Kai tsaye nace"Kila ta dawon to.nima Hutu nake son nazo miki Goggo "Dariya tayi ina jin ta Dauka Zolaya ce sai tace"Ina maraba da Fa'iza Allah ya kawo ki lafiya"na amsa mata da Ameem daganan ta tambayeni megidan da Yanayin zaman mu da Mama nace lafiya lau kamar bata gidan. Goggo tace'"Nima naga duk tayi sanyi.Rayuwa ta gara Saudatu daman na fad'amiki watarana sai tafi ruwa sanyi a wajenki"na jinjina kai ina Tunanin yadda Mama ta zama kamar kankara yanzu,Duniya ce da mutanen cikinta suka maida ita haka. Bayan munyi sallama da Goggo na jima ban yi barci ba,Hafsah tana Dakin yara tana karatu sun kusa fara Jarabawa Ni da Anum me muke kwance ita har tayi barci ni kuma ina faman sake sake a daran nan na yanke ma kaina abunda zai fissheni bayan na roki Allah kada ya barni ni kad'ai ya yi min jagoranci. Da Safe wasai na tashi,Duka aikin gidana ni nayi abuna. Abun kari kawai Hafsah tamin,Sai aya data wanke ta mikamin nika kafin ta fita,ni kuma sai ta barni da Dafa zobo,Ganin yadda nayi ne ko da Safe saboda a gaban yara ne muka gaisa na Sakar mai Fuska suna watsewa na had'e raina gim ko fara'ata bai gani ba. Mama ta aiko Anum ta kirani ina zuwa na durkusa na kara gaisheta ta amsa cikin kallona Lokaci d'aya tana fadin"Ishaq ya same ni da wata mgana. Wai zaki koma Dakin yara Zainab zata zauna a dakin ki  nace kin amince ne yace eh! shine nace sai na tambayeki" Kai tsaye nace"Eh Mama yau zan fara ma Tattara kayana. yaran kuma duk inda ya ijiyesu daidai ne a wajena" Sai ta muskuta tana fad'in"yaran ba matsala ga daki nan su zo mu zauna damam xaman kada'ici ya isheni kece bana so mu kara yi miki wani rashin adalci kamar yadda muka yi miki a baya,Shiyasa nace sai naji ta bakin ki,ki fad'amin in hakan bai miki ba to bai isa ba" Sai nayi mirmishi takaici kafin nace"Bakomai Mama na amince ni daman ba mazauniya ba ce.Dakin daman ai jingina ne, Zainab ce ke da wajen zama na har abada" Nasan bata gane kan mganata ba, sai dai nauyin baki yasa ta kasa min mgana har na fice,ina komawa Daki bayan mun gama hada zobo mun zuzzuba agoruna Anum ta jera a Frezee,kunin Aya ne zan had'a shi jira nake nepa su kawo wuta. Anum na bar ma sharan Falo da gyaran kitchen, ni kuma na shiga Dakina na fara had'a kayana a waje daya duk abunda nasan nawane na Daukosa babban ghana d'aya gareni itama sakon kayan sallar yara aka kawo aciki daga kaduna kuma tamin kad'an sai na kira Hafsah nace in ta shiga kasuwa ta siyomin manya guda biyu Kafin dare wardrope dina kaf ba kayana aciki Hafsah ta siyomin manyan ghana guda biyu sun isheni na dura komai nawa,aciki akwai wasu kayan da ko di'nka su ban yi ba. na Ishaq ne ban kara dinka kayan da ya siyamin ba,tun bayan auransa da zainab hatta kayan da Anty Binta ta bani na Fad'an kishiya suna nan suma na Had'a masa kayansa waje daya. Gadajen yara daman duk ya b'abb'alle,sai nayi tunanin na basu na Dakina da wardrope din ya ishe su saka kayan su,nasu  kuma a gyara ma Anum tunda ita macece ni ba zama zan yi ba,so kayan basu da amfani a wajena. Da dadadre suna falo da shi yana musu karatu,na fito ina kallon Amir kafin nace"Amir ku fara had'a kayanku waje daya,ka taya kannen ka su had'a nasu .Anum na fara had'a miki naki kema kije ki karisa in kun gama" Da mamaki suke kallona ammh sai na juya zuwa kitchen ina ji suna tambayanta Umma ina zamu..? Sai na bar mishi ya basu amsa sai kuma ya kasa ina kitchen din ya Biyoni yana fadin"Fa'iza bafa yanzu ba ne naga kina ce ma yara su had'a kayansu' Ina juya tumatur din da Hafsah ta Dora Tafashensa akan wuta nace"Eh gwara su fara had'awan tun yanzu kada sai lokacin yayi kuma basu samu sararin had'awa ba. gwara tun yanzu kowa yasan matsayinsa" Na fad'a ina kokarin rab'asa na bar kitchen din sai ya bake hanyar yana fadin"Fa'iza.." Kai Tsaye na kallesa ina fadin"Na'am Ishaq" Sai mamaki ya hansa mgana,Girata na Daga ina fadin"Bani hanya na wuce" Ba musu ya matsamin na fice ina jin wani irin Tukuki acikin kaina Amir ne ya taso yana fadin"Umma ina ZAMU KOMA..?Ko zamu yi tafiya ne.? Ban kallesa ba nace"Ku yi abunda nace Amir kaji" Sai ya amsamin da Toh ammh sai jikinsu duka yayi sanyi,nan na barsu na shige Dakina ina Sauke numfashi,Adaran na saka Hafsah ta taimaka musu suka had'a kayansu itama ban bata ikon mgana ba sai dai ta tambayi yaran Anum tace"Umma bata ce mana komai ba" Sai itama bata kara mgana ba, ammh ta kara tsorata da ganin na kara had'a kayana a karo na biyu wannan karon bata san kuma me zai iya Dakatar dani ba. Lalle kana naka Allah na nashi Washegarin jumma'a da Safe Ishaq ya samu wayar Dr.Lawal inda yake sanar da shi an gano saka hannun nan ba nasa ba ne, kwaikwayo ne na wani abikin aikin su.Mr James mutumin osun State ne Daga office din sa sai na Ishaq,da shi aka had'a baki aka kwaikwayi saka hannu Ishaq Daga office dinsa aka fitar da wad'anan kudaden,yanzu Mr james din ya tafi gida chan Osun,abu d'aya ya rage bangaran Cibiyar Bincike ta EFCC ita zata ba da umarnin a kamo James ya fad'i gaskiya sannan ta wanke shi Daga zargi. Da murna ya fito yana fad'a mana,ni da Mama da muke tsakar gida ita tana shan iska ni kuma ina Dafa zobo,sai na manta da abunda ke tsakanina da shi na mike ina fadin"Alhandulillah. Ka kira Abba kira Abba ka fadamasa" Mama ko sai da tayi sujuda tana godema Allah sai kuka shi ko Jiki na rawa yace"Shima Daddyn haka yace na kira Abba..yayi ta kiransa bai same sa ba' Kiransa yayi sau biyu bai Dauka ba nima na Ruga daki na Dauko wayata na kirasa bai Dauka ba. Sai na Kira Ammi bayan mun gaisa na tambayi Abba tace ya tafi Office ina fad'ama Ishaq yace"kila ya shiga meeting ne. mu basa Lokaci" Anum na gefe tace"Daada me ya faru..? Cikin farinciki ya dagata sama yana Fadin"An gano gaskiya Anum.angano bani da hannu a satar kudin ma'aikanmu"Sai itama ta washe baki tana fadin"Congratulation Daada" Sai da yagama juyi da ita sannan ya sauketa yana kallona Lokaci da'ya yana Fadin"Fa'iza kinga abun Allah ko..? Sai na jinjina kai ina fadin"Allah yasa karshen wahalan kenan"Mama ta amsa da ameen ta mike tana fadin bari ta kira Binta Yaya ishaq ya hanata da fadin"ki bari mu yi mgana da Abba tukunnah" Da sauri nace"Eh Mama gwara labarin ya kamallah Tukunnah"Sai ta gyada kai yini mukayi Duba waya ko Abba zai kira sai Dare ya kira Yaya Ishaq,kafin shi yayi masa mganar ya fara yi masa. yace sun yi mgana da Dr.Lawal yanzu nan ya kira Engr sun yi mgana shima ya ce Mr ABDULGHAFFAR ABDULBASIT BABATUNDE ya dawo Office satin daya gabata,zuwa gobe ko jibi ya sauraresa" Nima Abban ya kirani yayi min bayanin komai ya karishe da fadin"Last friday ai muna Abuja da ni da Maman Nana mun je duba Hajiya Kudirat olamide,itace kakar Engr sun dawo gida bayan an yi mata Dashen koda,da mukaje mun samu Engr din a gida sai na kara tunasar da shi mganar aiko yana masa mganar yace a tuna masa in ya shiga office sai fara Duba Case din,balle da Engr ya fad'a masa Ishaq Inlow ne a waje na,ya  tabbatar min da ba matsala mu jira cewarsa kawai" Da wannan labarin mai Dad'i muka kwana sai dai na Tsananta addu'a na Allah ya kawo mafita da karshen al'amarin. Har yara na saka suka yi ta addu'an Allah ya kawo ma Daada mafita shima nace yayi ta addu'a da ikon Allah sai an wanke sa daga wannan zargin. *Janafty* *KNKB2019* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Allah maji rokon bayinsa kwana Biyu Tsakani. ranar Litini da misalin wajen sha biyu na rana ya samu wayar Abba in da yace maza ya taho kano yanzu zai had'u da Abdul'Ahad a Airport din Aminu kano zasu hawo jirgi zuwa nan Abuja. A na nemansa a Office din Chairman na EFCC,daganan bai yi mai wani karin bayani ba. shiyasa sai ya Rude,ya fito daga daki yana fad'amin cikin wani yanayi kafin ya kara da cewa"Gaba na ta fad'i Fa'iza. Allah yasa ba wata matsalan ce ta sake kunnowa ba" Cikin son kwantar masa da Hankali nace"Haba ba komai abunda muke fata ne jeka ka fad'a ma Mama,bari na saka maka ruwan wanka ka shirya kada ka b'ata Lokaci" Bai min gaddama ba ya wuce Dakin Mama ya fad'a mata ni kuma na je na kunna gas na saka mai ruwan wanka Tuna murhun gawayina yana waje girki na d'ora akai,sama sama ruwan yayi zafi na sake mai nice har bayi sai da na kai masa.  Da kuma ya shiga wankan na Lalubo masa kayan da zai saka,yana wankan sai ga yaya Abdul'Ahad ya kirasa ni na d'auka muka yi mgana yace yana kano yana Jiransa, daman ya kawo Raliya ta gaida su Hajiya ne, sai ga kiran Abba so in ya taso ya kirasa yadda zasu hadu a Filin jirgin kawai. Ko da ya fito wankan mun gama wayar,Sai rawan jiki yake yi ya kasa natsuwa fad'i yake yi"yanzu a chan kano zamu hadu da Abdul'Ahad din? Kai Tsaye nace"Eh mana yanzu ma ya kira wayarka na d'auka muka yi mgana,yace in ka taso ka kira sa" Sai ya amsamin da toh fita nayi na basa waje ya shirya nasan ba shi da kudi cikin kudad'en sana'ata na kirgo Dubu Biyar na bashi Saboda nasan in dai suna tare da Abba bazai rasa kudi ba in yaje koda na dawowa ne, har ya shirya cikin shadda fara riga da wando,Sai Hula daya sanya ina shigowa yace"Ba sai na dauki wasu kaya ba ko.? Kai Tsaye nace"Me zakayi da kaya kuma? in ma kwana ya kama ka kana da Muhalli da wasu iyalan achan ka manta ne"Sai ya sauke ajiyar rai kafin yace"Wlh duk na Rud'e ne Fa'iza" Ina mika masa kudin Hannuna Lokaci daya ina fadin"Ka kwantar da Hankalinka babu abunda zai faru ai Yaya Abdul'Ahad yace Abba na chan shima in kaji zuciyarka bata natsu ba kayi ta ma Allah kirari da Hailala, yafi ka zauna kana wannan zullumin" Cikin gamsuwa ya gyad'a min kai kafin ya karbi kudin da nake mikamasa Lokaci d'aya yana fadin"Wannan fa na menene..? Nasan ya rude ne, kila ya Dauka haka zai tafi ba kudi sai na juya ina fadin"a kasa zaka je kanon.? Sai ya Dafe kansa yana fadin"Shaa..Fa'iza wlh na manta"ina jinsa yana bin bayana har Tsakar gida Inda Mama ke jiran fitowarsa. Sallama yayi mana ya tafi mama na sakamai albarka da fatan Allah yasa mu dace. ni kuma mun rabu kan sai ya kirani naji yadda ake ciki. Mun yi masa fatan sauka lafiya tare da Fatan Allah ya tsaresa ni da mama Anum bata san tafiyarsa ba taje kai min nikan Aya,sai da ta dawo nace tayi ma Daada addu'a ya tafi Abuja. Tafiyarsa ba Dad'ewa Yaya Abdul'Ahad ya sake kirana na fad'a masa ya kama Hanya sai yace ya yi ta kiransa bai Same shi ba,yana ga network ne, bari ya Saurareshi. Mu dai ya tafi ya barmu da zullumi,bayan ya isa kanon mun yi waya yace suna Filin jirgi yanzu zasu tashi zuwa Abuja . Daganan shuru bamu kara jinsa ba,Dagani har Mama muna ta zullumi ni kuma kunya ta saka na kasa kiran Abba ko Yaya Abdul'Ahad kada suga kamar na damesu shiyasa na daure Ammh ko Mama bayan mintina sai ta leko d'akina tana fadin"Fa'iza shuru Ishaq bai kiraki ba ko..? Ni kuma sai nace mata"Mama in ya kirani ai zan gaya miki. kuma nasan in sha Allahu zai kiramu" Daganan sai muka koma muka Nad'e hannaye,muna jiran tsammani sai wajen karfe goma sha d'aya saura,ya kirani lokacin yara har sun kwanta Hafsah ce kadai a falo tana karatu,saboda sun fara jarabawa,ni kuma ina dakina sai dai ko da na Dauka bana jinsa har sau biyu,daga baya sai ya kira Wayar mama da ita suka fara mgana kafin ta leko da kanta ta kawo min waya bayan mun gaisa sai kawai ya bige da cemin"Wato Fa'iza ki ji tsoron Gwamnati da kuma in kana da Kafa a Gwamnati. kinsan  24hrs ya yi yawa Efcc ta saka an kamo Mr James tun jiya kuma yayi mgana. Dalilin dayasa ma aka kirani kenan ma" Cikin son jin ya aka haihu a ragaya nace"To ya kuka yi da su yanzu..? Cikin Farinciki yace"Ya amsa laifinsa Alhamdulillah an wankeni daga wannan zargin. ashe da wani suka had'a baki,kinsan kana zaune da mutum bakasan ya tsaneka ba ni wlh lafiya nake zaune da kowa,Yanzu haka dai an yi cike ciken Takardu an tura chan ma'aikatanmu,kuma Efcc ta bani Hakuri tare da alkawarin zata maidamin da kudina da ta karb'a sun rike Mr james a hannunsu suna kara Bincikensa. ammh ni nace na yafe masa Har abada" Cikin jin dadi nace"masha Allah. Alhandulillah gwara daka yafe masa, ammh shi miye riban abunda ya aikata..? Kai Tsaye yace"Matsayina ya ke so. Kuma ya samu tunda bayan Dakatar dani shi aka d'aura akan kujerata" Cikin mamaki nace"Ikon Allah daman ai abun duniya fararre ne kararre ga shi yanzu komai ya kare masa"Cikin jimami yace"Wlh kuwa. Muna chan har karfe Takwas na dare da ni da Abba da Daddy da Abdul'Ahad,da wasu cikin ma"aikatan mu, sai shi chairman na Efcc din da Sauran ma'aikatan su da wanda suka ja Ragamar case dina a hannunsu.Wh Fa'iza Abba yayi min kokari ke kinga yadda Chairman din nan ya dinga bama Abba hakuri.?gaskiya mutumin nan yasan karamci kuma ba fa ba Bahaushe ba ne, Fa'iza Bayarbe ne. abunda na Lura dashi Megidan Abba da yake kira Engr na ji da Abba sosai. tsakani ga Allah cikin gaggawa akayi komai aka gama,kuma Engr ma ba shi a wajen,naji Abba yace yana Edo ki tayani godiya Don Allah" Ajiyar rai na sauke kafin nace"Alhamdulillah Allah ya kara Tsarewa yanzu kana ina ne.?ko kuna tare da su Abba ne..? Da sauri yace''Ina wajen zainab nan zan kwana zuwa gobe. Abba daganan jirgi ya hau zuwa warri suna da taro gobe Abdul'Ahad kuma ya hau jirgin kano" kai na tsaye nace"Ba damuwa ai kana gida kayi zaman ka mu nan ba mu da matsala"Shima kai Tsayen yace min"Aa zan dawo ai ba wajenta nazo ba, itama" Ban tsaya jan mgana ba tunda ba Hurumina ba ne,in ba wajenta yaje ba, me ya hana yabi yo  Ya Abdul'Ahad su dawo tare ya tsaya nan zai kwana?shine zai zo yana min wata mganar banza jin nayi masa shuru yasa ya kira sunana sai na amsa sai kuma ya kasa mgana sai kawai ya bige da Fadin"Sai dai na dawon" Yara ya tambaya nace sun kwanta yaso yajani da mgana nace mai barci nake ji duk nagaji cikin Dariya yace"Ai ina samun wani babban aiki duk zaki daina sana'ar nan ta wahala Fa'iza" Sai ya bani dariya har sai da na Dara kafin nace"To ai ko ni ce da kaina na samu babban aikin ban ji zan dakatar da wannan sana'ann tawa, domin tamin komai a Rayuwa sai dai na nemi Hanyar ingantata kawai' Da sauri yace"Eh hakane kam.."ina ji sama sama ana mgana ta gefensa ban Tsaya ji ba na kashe wayata na yi kwanciyata sai dai har ga Allah na tayasa murna sai naji kamar komai dake faruwa Mafitan da na Roki Ubangiji ne ya sama min ne. Zuwa washegari mgana ta watsu a Dangi Mutanen karofi dai Hafsah ta Fada musu su jamal kuma duk mama ta kira su ta fad'a musu abunda ke Faruwa. sannan sai ta kara da fadin wlh duk sanadin Kanin mahaifiyar Fa'iza shi ya tsaya har aka wanke Ishaaq,Har daki mama ta biyoni Tana min godiya ta kuma saka na kira Abba ta kwararamai godiya. Abba yace"Hajiya kada ki damu.Da Fa'iza da Ishaq duk d'aya suke a wajena duk abunda nayi kamar nayi ma Abdul"Ahad ne"sai kimar sa ta karu a idon Mama,sai da yaya Ishaq ya kwana Biyu sannan ya dawo ranar kuma Anty Binta tazo ita da Anty mahma,sun zo yi ma Mama barka da arziki,Shima din yana samun wayoyin yan'uwa da abokan arzuka harda abokan aikinsa da suka Dad'e ma basu yi mgana, suma labarai yakai headquater din su tunda EFCC ta tura Takardan wanke Ishaq din daga dukkan zargi. Su Goggo duk sun kirani hatta ko da Yaya mariya,ta kirani su Nana Fatima ma duk sun kirani tace Abba yace su kira su yimin barka da arziki,Har da Ammi kuma naji dadi sosai masoyin ka ne Zaka yi rashi ya janjanta maka sannan in kasamu shima ya tayaka Murna,su Amir nata murna domin ce musu yayi da kansa kud'in Daada ya Dawo ya'yan Umma nan suka Biye masa suna ta tsallen Murna. Allah shi ke ba  da samu da rashi kuma shi ke da Daukaka da Nasara shu kuma ke da Fad'uwa da Tashi,kwana Biyar Tsakani da EFCC ta wanke Yaya Ishaq ya samu kiran gaggawa daga Headquater dinsu na Abuja aranar ya tafi sai dai mota yabi,bai kirani ba ina ta neman wayarsa a daran a kashe sai da asuba kawai zainab ta kirani ina Dauka tace"Congratulation to us Maman Amir kinga Kuduran Allah ko..?. Mamaki ya kamani bansan kan mganar ba,ina shirin tambayanta sai kawai ta zarce da fadin"Jiya da Honey yaje ma'aikantan su upper ce suka basa ta maida shi aiki da matsayi mai girma,sun mai da shi office din su na Lagos zai fara aiki nan da wata D'aya" Karfaffan ajiyar zuciya na sauke a Fili na furta"Alhamdulillah! Cikin Farinciki tace"Wlh ai tun jiya nayi ta neman wayarki ni da shi bamu samu ba, yanzu haka ya tafi masallaci ne,shi nace bari na kiraki na fara yi miki albishir" Ciki jin dadi nace"Masha Allah. Allah ya sanya albarka,ya sa alheri a cikin aikinsa damu gabad'aya" Ta amsa min da ameen ameen bamu jima,muna mgana ba muka yi sallama,Daganan sai na tashi na shiga Dakin Mama na isketa tana azkar bayan mun gaisa na fada'mata abunda Zainab ta fad'amin Mama ta washe baki tana Hamdala ta daga hannu sama tana yi ma Allah godiya. Daganan dakin yaran na koma na iske sun idar da salla,Amir da Musty suka hada baki wajen fadin"ina kwana Umma"ina mirmishi na amsa ina fadin"Daada ku ya samu aiki a lagos"Sai suka fara murna har da tsalle Ahmad kenan. Fita nayi na koma falo sai ga Hafsah ta fito na gayamata, Anum na bayanta ta Daka tsalle tana fadin"Eyyee zamu koma Lagos ehyee.." Sai tsalle take yi ina kallonta ina mirmishi,sai da gari yayi shaa Yaya Ishaq ya kirani cikin Tsananin murna yace"Fa'iza albishirinki" Ba da niyyar gwasale shi ba nace"Zainab ta riga ka. Har na shaida ma Mama da yara"Sai naji kamar gwaiwarsa tayi sanyi duk da haka bai nuna ba nan take na tayasa murna ya amsa yana fadin"Wlh ban taba saka rai aiki nan zai dawo gareni ba,Ammh sai ga shi sun kirani sun bani takarda har da karin girma da kuma sauyin wajen aiki"sai na tare sa da fadin"Haka Allah ke lamarinsa. Sai ya baka ya kwace in kuma yaga dama sai ya maida maka mafiyinsa" Cikin gamsuwa ya gyada kai yana fadin"Hakane wlh. Allah ya datar mu" Na amsa mai da Amen mun yi sallama yace zuwa anjuma zai kamo hanya ina shirin nace sun yi mgana da Abba?sai na sha'afa sai ga shi ma Abban ya kirani da kansa ina Dauka yace"Congratulation Dougther yanzu na samu labari wajen Dr.Lawal" Cikin mirmishi nace"Daman yanzu nake shirin kiran ka Abba" Kai tsaye yace"Gashi ni na rigaki,Duk na kira sauran yan'uwaki na shaida musu. Allah ya tayasa riko Zaki koma kusa da yar'uwanki Fadila tana ta jin dad'i da na shaida mata" Sai mirmishi na ya Dauke da yake da cijewa muka gama wayar nan,yinin ranar sai amsa waya nake yi har mamakin yarda mganan ta Je, kunnen kowa nake yi,Yaya Asiya tace min Goggo ta fad'amata sai ban yi mamaki bam Saboda ni na kira ta da kaina na fad'a mata. Ranar ya dawo da Daddare,yana shigowa ni ya fara cin karo dani a Tsakar gida ina kaye kayen kaya sai ji nayi ya Daukeni Caraf ya dagani sama yana juyi dani cikin Firgita nace"Innalillahi ka sauke ni don girman Allah"bai saukenin ba sai da yaji muryan Mama sannan ya saukeni Tana fitowa ya sakeni ya nufeta yana Fadin"Mama.." Cikin jin dadi tace"Na'am Ishaq naji abun arziki Allah ya sanya alheri" Ya amsa mata cikin fara'a ta dafa kansa tana sakamai albarka,mganarsa yaran sukaji suka firfito suna masa oyoyo d'aya bayan d'aya ya dinga dagasu yana saukewa Anum sarkin mgana tace"Daada yanzu Lagos zamu koma..?cikin shafa kumatunta yace"Sosai chan zamu koma." Musty yace"Daada dukkan mu? Ya gyad'a masa kai Lokaci d'aya yana fadin"Dukkan mu mustapha.." Amir ne ya kalleni yana fadin"har da Umma da Mama..? Kai tsaye ya bashi amsa da"Eh har da Anynku dasu Farhan" Sai suka saka Ihu,yana biye musu da Dariya ni dai sau daya muka hada ido na kauda kaina,Daki na koma shi kuma da yaransa suka shiga Dakin Mama sai chan ya fito Hafsah tayi mai Fatan alheri ya amsa bakin nan har har kunne. Garin ana d'an zafi zafi da ruwan Sanyi yayi wanka na kai masa abinci yana ci yana bani labarin abubuwan da suka faru cikin hirar nasa ne yake ce min"Sai zuwa gobe zamu yi shawara Fa'iza. nan da wata d'aya suka ce zan fara shiga office bana so na kara raba iyalaina Waje d'aya zan had'eku bari kudi su shigo kawai" Ina kallonsa nace"Yaushe su sukace zasu maida maka kudaden na ka..? Yana lomar shinkafa yace"Ko wani Lokaci zan iya gani suka ce" Ni dai ina jinsa yana ta Tsara abubuwansa nayi masa gum sai in ya sako sunana ne zan daga kai nace tom ko Umh,naja bakina na tsuke ni dai gajiya nayi naje na kwanta shi da yaran sa falo suka Dawo suna ta Shagalinsu tun ina jinsu sama sama har barci ya Dsukeni. Tun daga washegari muka yi samun bakin Taya murna wad'anda basa kusa sun yi mana ta waya Goggo tazo Yaya isa ya kawota tayi mishi Murna,Anty Binta baki har kunne,ita da Mama,Jamal yana makaranta suna Jarabawa Badariya dai sai ta zo gida ta kwana Biyu,ranar da ta dawo zuwa tayi ta Rumgumeni tana fadin"Ina murna matar yaya. Allah ya sanya alheri" Na amsa mata da mirmishi sai ta fara zolayata da fadin"Har mun fara kewa Anty Fa'iza yanzu chan ikkon zaku koma.? Kai Tsaye nace"Za dai ku koma Badariya" Cikin jimami tace"Ni ina kano kin manta,ban gama hidimar kasa ba" gyada kai nayi ina fadin"Duk da haka dai. in kika gama chan zaki koma indai ba aure kika yi ba" Daganan muka cigaba da Hira duk akan mganar aikin ne,ni da kaina na Kira Hajiya na sanar da ita,tace zata zo taya murna abun mamaki har da kawayen Mama da suka gujeta a baya har da su a masu taya murna. Hajiyar Dala bata zo ba ta dai kira mama a waya da dashi da Uban gayyar ta masa murna nima su Nana Fadila duk sun kirani ita har ta fara murnan zan dawo kusa da ita. ban ce mata komai ba sai yake a raina ko nace kiyi hakuri Fadila hakan bazai tabbata ba. Baki muka yi ta samu ta ko'ina abun har mamaki yake bani,shi kan shi yace wasu wlh sun manta ma dashi Lokacin da ya rasa ammh sai ga shi har da su a sahun masu murna,mganar da yace zamu yi duk bamu samu mun yi ba. nasan kan mganar tafiya lagos ne tuni mutane har sun gama daukan zencen Lagos zamu koma gabad'ayanmu har da yara. Yaya mariya bata zo ba. A waya ta kira ni bayan mun gaisa tace"Ashe kuma abun alherin da ya samu kenan..? To Allah ya sanya albarka.Goggo ke tad'in Lagos zaku koma daa ke da yaran gabad'aya"sai kawai na ce mata haka yace,yaya mariya bazata sauya ba sai ta karkace baki tana fadin"itama yar abujan fa?ina fatan chan zai barta domin Lagos ke kad'ai zaki zauna kamar yadda ki ka bar mata Abujan ita kad'ai" Sai nayi dariya kafin nace"Ya ce gabad'ayanmu zamu koma har da Mama"sai ta tabe baki kafin tace"A na nan dai jiya iyau" Ban biye mata ba shiyasa bamu dad'e muna mgana ba muka yi sallama. Bamu samu zama ba sai da mutane suka Tsagaita,Ranar ma da daddare,Dariyan Musty muka sha wai har yayi ma yan ajinsu sallama su zasu koma Lagos gabad'aya.ina Dariya nace"kaji yaro da zakewa. " Yaya Ishaq na gefe yace"Ba wani zakewa ya fad'a musu gaskiya da ya tafi ba sallama fa..? Amir yace"Umma da Anum na zuwa makaranta da tuni kowa ya sani" Ita muka kallah yadda tayi yasa muka kwashe da Dariya,kowa yasan zata aika da bakinta kamar na aku,har fa gidan da muke kai nika da taje sai da tace lagos zamu koma zamu tashi Daga gidan nan kamar an tambayeta,Amir ke fadin da yaje kai nika suka tambayesa,kallonta nayi ina fadin"To wa ya aike ki gwana..? Cikin Shagwaba tace"Umma sallama nayi musu kada suga min daina kai nika"Sai ko muka kara saka Dariya sai ta fara kokarin kuka Ya jawota jikinsa yana fadin"manta da su mamana ki fad'a ma kowa lagos zaku koma sannan ki kara da fad'a musu a jirgi zaku tafi"Da sauri ta waro ido tana fadin"Daada jirgi fa mai tashi sama..? Ya daga mata kai kawai sai ta fara Tsalle tana murnan zasu hau jirgi Ahmad da Musty na tayata,Amir dai na zaune yana bin su da kallo. Yaro shi yana son sauyin muhalli,Amir ne yayi hankalin cewa'Daada in muka koma chan wata makarantar zaka sakamu? Yana dariya yace"Amir d'an makaranta. Kada ka damu makaranta mai kyau zan saka ku in sha Allahu" Daganan ya cigaba da biye ma yaran suna masa tambayana yana amsawa. Ni har zan shige daki yace yana son mgana dani,dole na hakura sai da yaran suka yi mana Sai da Safe suka shige Dakin su,sanin in yace muje Dakinsa bazani ba yasa muka zauna afalo ya fara da gayamin EFCC ta dawo mai da kud'insa kimanin Naira miliyan Sitti,Tunda ba lalle kudin mutum su dawo duka ba. Shine  ya ke ce min yanzu ya yanke shawaran zai fara yin gaba yaga yanayin garin da komai,zuwa ya sama mana inda zamu zauna tunda Abba yace zai had'asa da mijin Nana Fadila. Ban yi mai musu ba nace shawaran shi tayi sai ya cigaba da fadin"gida nake son siya babba wanda zai wadace mu. In bai samu yanzu ba, sai na kama Haya zuwa gaba in na samu a hankali a hankali sai na siya na kaina" Kai Tsaye nace"Gwara ka mallaki naka zai fi. Kuma mganar ka siya babba kada ka yi asaran kudin ka,ka siya daidai zaman mata d'aya da Dakunan yara,kana da maza sannan mace Daya gareka Anum,Ga mama ga su Badariya duk da ita tace sai ta gama hidiman kasa tukunnah" Cikin mamaki yace"Bangane wajen mace da'ya ba.?ina miki bayanin itama Zeey na gayamata ta fara shiri,kila ku zaku fara yin gaba ita sai daga baya zata same mu achan" Mirmishi nayi kafin nace"Ka gane mganata mana. ni fa bazan bika Lagos ba" Sai ya yi karamin Tsaki kafin yace"To sai ki zauna a ina.?kai tsaye nace"A nan mana"harara ya sakar min kafin yace"kina Hauka ne.?ina wata Duniya kina nan?wazai barki di'n? kafata kafarki, kafar yarana Fa'iza" Sai ban ce komai ba na kauda kai bai Damu ba ya cigaba da fadin"Abba yace na siya mota saboda zirgan zirgan  zuwa wajen aiki da sauran dai Bukatu"jin sa kawai nake yi ina tunanin ya dauka wasa nake yi sai na kara gyara zama nace"Da gaske nake yi. ni bazan bika Lagos ba" Sai kawai ya mike yana fadin"Bina ko kamar kin gama shi Fa'iza meyasa zan barki.?ba mai kara rabamun hankalina yanzu iyalaina duka waje d'aya zan had'asu" Kai Tsaye nace"Yanzu kuma.? Ni fa kada ka manta na saba zama ni kad'ai a baya ma kana Abuja ina katsina, kuma na zauna lafiya sai don ka koma Lagos..? Kallon sai ki yi yayi min ya shige Dakinsa ya bugo kofa sai ya bani Dariya ya Dauka wasa ne?lalle ko zai ga wasa alokacin da bai yi tsammani ba. Ya samu mun fara tattara kayanmu,ni daman ma na had'e nawa na yara ne ba'a gama had'awan ba,yace bazai saki gidan ba sai in ya siya wani inda zamu rika sauka inda munzo,tunda dagamu sai kayan sawa zamu tafi sauran kayan gida Sabbi za'a siya kawai,har sun yi mgana da megidan ma ya bashi kudin Shekara,Hafsah kuma daman bata da matsala Transfer dinta ya samu kaduna zata koma,ranar muna tattara kayan kitchen waje daya Anum tace"Umma shikenan kin daina zobo da kunin aya..? Kai tsaye nace"In ji wa..?zobo da kunin aya yanzu na fara" Na tuna ko ranar da Hajiya tazo min murna na fad'a mata lagos aka kaisa tun kafin na yi mata bayani tace duk inda naje kada na saki sana'ata domin sana'ar hannu abu ne mai kyau da amfani kuma na aminta da mganarta na Jaraba kuma naga riba,kuma dayake nima baama Lagos din zani ba ballatana ya dameni, inda zan koma da zama na tabbata zan rika yin ciniki sosai. Kuma ko da muke tattara kayan ina sana'ata ban fasa ba,Mama ma nata shiri tunda yace in yaje ya dawo har da su Anty binta za'a tafi saboda suga waje,Sati hudu Tsakani ya tattara ya tafi,jirgi ya bi daga kano zuwa Abuja,bayan ya isa headquater din su ya saka hannu sun bashi accepted letter,Daman yana zuwa ya kira mijin Nana Fadila shi Costume ne,gidanta ma ya sauka yaci abinci ya huta sannan suka fita duba gida,sun duba inda yafi kusa da ma'aikatan su anguwan Apapa lagos,ya siya apartmemt,gida ne mai girma ba sosai ba,Falo hud'u mai Dauke da bedroom da Tiolet guda takwas,yana da girma gidan tunda akwai Haraba sosai,sai kudi wajen miliyan Ashirin gidan tunda Sabo ne shima mijin Nana Fadilan wani kaninsa ke harkan gidajen shiyasa suka samu da sauki,Ya siya gidan sannan kuma yayi oder din gadaje da kujeru da sauran kayan bukatu da ya Kirani ya fad'amin sai nace"ka san kana da yara a siya musu kananun Gadaje. Ga uku anan ga biyu Farhan da Fadil,Anum kuma ko ita da Badariya sai ka had'asu,Mama kuma tana Dakinta ita kadai sai jamal kada ka manta da shi" Cikin gamsuwa yace"ban manta da shi ba wajen zai isa ba takura fa. na Dauko muku hoton gidan in na Dawo zan nuna miki"Da haka muka rabu sai da yayi sati sannan ya Dawo da shirin zai tafi damu gabadaya Zainab kuma sai daga baya zata biyomu ita. Sallama yace duk mu yi da abokan arzuka da yan'uwa da makota,Ranar a karofi muka yi yini,washegari kuma da muka dawo na zaga cikin gari naje nayi ma Sa'adatu da Habiba sallama saboda  sabo har suna kwallah,makaranta yara daman tun kwanaki naje na sanar da su suka ce zasu yi kewar hazikan Dalibai. Hajiya ma naje mataa sallama,ta bani kyautan kaya da su Turaruka da mayama mai na gyaran jiki muka rabu cikin mutumci,Abba dai shi ya hana naje yi masa sallama duk da ko ba inda suke tunani zan tafi ba, yace shi zasu je har lagos suga muhallina. Anty Binta da da Mama sai Anty Hure da tazo zasu tafi daga bangarena yace a samu mutum biyu sai Goggo ta wakilta Anty Nasara da matar Yaya Isa tunda Yaya mariya tace bazata samu zuwa ba,Yaya Asiya kuma yaronta bai da lafiya yana fama da kyanda. Tafiyar jirgi yace zamu yi,zamu je kano daga katsina kenan,Ya siya mana Ticket gabadayanmu zamu tashi karfe uku na ranar talata,damu da kayan sawan mu,ana gobe Tafiyar na had'a komai nawa na kayan zobo na da kunin aya. Sannan na cire soket din Freezer di'na,duk kulle kullen da Goggo ta aikomin da shi na had'a cikin kayan yaran nasa zai musu amfani. Na zata ina da Dauriya sai ga shi na fara raunanaa, in naga yadda yaran ke Tsallen Murna ina Tunanin ya ya zasu ji gobe in har na ce musu ba Tafiyar mu d'aya ba..? *Janafty* *KNKB2020* *Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.* *09069067488* Ko yaran ban bari sun fahimci Halin da nake ciki ba,daki na shige ina kokuwa da yanayina. Nace kada su dameni da Hayaniya Hafsah bata nan daman tun jiya ta wuce karofi daganan Abba zai turo mota a Dauketa zuwa kaduna. Yaran ne kad'ai da babansu ke ta Budurin su da murnan gobe zasu hau jirgi,sannan zasu koma Lagos da zama,kayan su dai masu muhimmanci na hada musu saboda tafiyar jirgi ce yace ko shi daga baya zai saka a taho mana da komai gabadaya,Badariya tana kano sun kusa gama Hidimar kasa bata da Lokaci sai dai zata taho daga baya. Kwana nayi ina kuka Sai dai ban kwanta ba ina sallah hawayena sun kasa tsayawa sai kuma naji kamar abunda nake shirin yi bai kyautu ba.?kamar in nayi haka na karya raunin zukata da dama ciki har da ta yarana. da suka fi kowa shakuwa dani ammh sai wata zuciyar ta tunasar da ni Babban Dalilina da yasa naji na kara samun karfin zuciya. Sai dai a komai in zan yi ba ma yin gaban kaina Allah nake fara sawa cikin Duka al'umarana,Shi na daga hannu na roka da kyawawan sunayensa sannan na yi masa magiya na yi masa naci ina kuka ina fadim"Ya Allah kasan damuwar dake damuna acikin zuciyata, sannan kasan wahalwahalun da nayi ta fama da su yayin biyayyan auran da kai ka Umarcemu da yin sa. Sannan kasan komai da ya faru tunda kai mai ji ne kuma mai gani ne na yanke wani Kuduri a raina ya Allah in har ba alheri acikin Tunanina, Allah ka hanani aikata wannan kudurin nawa in kuma Hakan shine alheri a gareni da Duniyata gabad'aya Allah ya bani Hakuri ka sanyamin juriya kada kuma ka barni ni kad'ai kayi Riko da Hannayena sannan ka yimin Jagoranci a duka al'murana,sannan ya'yana Allah ka tallafe su,  kayi musu albarka, ka kara shiryamin su cikin addininka" Ina addu'an kukana yaki Tsayawa sai na kife kaina a kan hannayena ina ta rafzan kuka,ni da barci sai wajen hud'u na asuba shiyasa na makara sallar asuba sai da naji sa a kaina yana Tab'a kafafuna na bude idanuwana jajir da suka kumbura saboda kuka,na sauke a kansa cikin mitsike ido na ce"An yi sallah ne..? Kai Tsaye yace"Har mun dawo masallaci ni da yara kina kwance ashe baki tashi ba..? Jin haka yasa na yunkura Dakyar na mike ina fadin"Ban yi barci da wuri ba ne" Kai tsaye na wucewa zuwa Tiolet sai ya bini da kallo yaga idanuwana sun tasa ammh ganina a kan darduma sai yayi tunanin sallar Dare nayi,Ficewa yayi falon wajen yaran har Anum ta kunna gas ta Dora ruwan zafi saboda wanka,Amir kuma ya saka a Heater tunda akwai wuta. Sai da idar da sallah na fito falon ina ganin an saka ruwan zafi nasan Anum ce uwar zumud'i ban dora abun kari ba sai da duk sukayi wanka har da Baban nasu,sannan na fere dankalin Turawa na soya musu sai ruwan Tea muna da sauran kayan ciki sai nayi mana Ferfesu da yawa saboda Mama da Anty Hure,su Anty Nasara suna Karofi sai yau zasu taho ammh ina Tunanin zan Dakatar dasu. Saboda tafiyar dake gaban mu yasa suna gama karyawa suka fara shiri ni dayake ban iya saka komai aciki na ba gabad'aya komai baya min dadi. Yaya Ishaq yana dakin mama shi da yaran zainab ta kirani bayan na Dauka mu gaisa tace"Maman Amir yau sai kwanan Lagos ko? Sai nayi yake kafin nace"Uhm ke bakin k'i mu je mu gyara gidanmu tare ba.?tana dariya tace"Wlh ba haka ba ne zan tsaya shirye shirye ne Daddy wannan karon bai bani matsala ba,da Full yes din sa zan koma ai ko Sati biyu baza'ayi ba zan same ku achan in sha Allahu"Jin haka yasa nace"To Allah yasa" Ta amsa da Ameen mun taba Hira sama sama na tambayeta yara tace suna makaranta,mun yi sallama cikin girmama juna kamar yadda muka saba,har ta kashe sai na sake kiranta tana dauka nace"Maman Fadil ga amanan yaran nan. Don Allah ki kula da su sannan kiyi hakuri da su,Amir da Anum sun girma nasan zasu yi miki kokarin kula da sauran kannensu. In sun yi ba daidai ba ki tsawarta musu ki yi musu fad'a ki Tsaya kan tarbiyan su don Allah, in sun fi karfin ki ki had'a su da Babansu shi sai ya yi musu hukumci" Bata gane kan mganata ba yasa tace"yaran da duka nakin da nawan kike hadawa ki rike Maman Amir..?kinsan bani da juriyan kwarammiya yara fa..?kina ma wata mgana muna komawa ai su Farhan daman ya'yan ki ne"Sai nayi mirmishi kafin nace"Ki rike mganata zaki tuna da abunda na gayamiki watarana"ban tsaya sauraran mganarta ba na katse wayata ina maida numfashi anya zan iya kuwa.?sai wata zuciyar tace min zaki iya in sha Allahu Fa'iza. Anty Nasara na kira tana Dauka sai tace min gasu nan gidan Goggo yanzu zasu taho kai tsaye nace"Ku yi zaman ku nima ganinan tafe" Cikin mamaki Anty nasara tace"Ga ki nan zuwa..?ban gane ba.?kun fasa tafiyar ne..? Kai Tsaye nace"Aa.." Anty nasara tace cikin mamaki"Bangane a'a ba ki bude baki ki yi min mgana Fa'iza"Bana son mgana alokacin sai kawai nace"Sai dai nazo" Da sauri na katse kiran,ina jin kaina yana saramin ban zauna ba na mike na rika fito da jakunkunan kayana na zuwa falo,Sai ledan kayan da ba cikin kayana zan hada shi ba. Ina cikin aikin ne sai ga shi ya shigo yana ganin haka sai yace"Yauwa daman mganar da na shigo nayi miki ne,bari naje tasha na yo tashar Ko Sharon ne yadda zasu daukemu da kayanmu duka" Kai na gyad'a mai kafin nace"ni ma ka yo min tashar Ko karamar Golf ne don Allah" Cikin mamaki ya juyo yana kallona lokaci d'aya yana fadin"bangane ba..?sharon fa zata ishemu in na yo tashar ta" Kai tsaye nace"Aa ina so zan aika ma Goggo wannnan Frezer din karofi ne, in na barsa anan ba'a amfani da shi zai lalace. shiyasa nayi mgana da ita zan aika mata da shi" Kamar zai yi mgana sai ya fasa ganin zai fita yasa nace"Kayi ma su Amir mgana su zo su fitar da kayan su" Ya amsa min da toh ina ji ya leka Dakin Mama yana musu mgana,sai da suka zo nace su fito da kayan su tsakar gida daman tun jiya nagama duka kaye kaye muka kwashe komai muka adana cikin rawan jiki suka fara fito da kayan suna murna suna jin Dadi kallon su kawai nake yi ina zaune ko wanka ban yi ba Anum ce tace"Umma ke bazaki shirya ba ne..? Sai na Rausayar da kai ina fadin"Zan yi wanka yanzu Anum" Nan suka fice suka barni,ina sake sake ganin zaman bazai amfaneni ba yasa na mike na shiga daki,tubewa nayi na shiga wanka,kokarin daidaita kaina nake yi saboda in na rasa kwarin gwiwa bazan iya aiwatar da kudurina ba. Na fito wankan kenan ina Shafa mai,naji dawowar Yaya Ishaq da maganan su Mama sai hayaniyar yara kamar suna fita da kayan ne waje da Sauri na Zura Doguwar rigar leshi,daman kwalliya ba aikina ba ne,Dankwali kawai na dora na zura Hijabi,na fito da sauri duk suna Tsakar gida har su Mama yana ganina yace"Ga motar chan a waje." Nasan wanda nayi masa mgana ne kai Tsaye nace"akwai yara a waje ne..? Juyawa yayi yana fadin"Bari na duba" Ba jimawa ya Dawo,da wani Saurayi tare suka kama suka fita da Babban Frezer din da Starplezer,Anty Binta da ta shigo kenan ta ci karo da su suna fita da shi shine ta shigo tana fadin"Ina za'a je da wannan frezer din.?ba dai Lagos ba..? Dayake na gayama su Mama karofi zan kaisa sai itace ta bama Anty Bintan amsa ni dai muna gaisawa na koma daki na shirya a gurguje saboda kada na bata Lokaci,hijabina na saka Dogo har kasa ni na kulle sauran Dakunan gabad'aya na fito da jakar hannuna na,karama na duba duk sun gama fita da kayan suna  jidan sauran zuwa waje ne, har da Baban nasu ina kulle dakin na juyo ina kallon Amir da zai Dauki karamar ledar da na fito da ita da Sauri nace"Kai bani ledan nan" Ba musu ya mikamin na karba ina fadin"ina kayana.?kun kai waje ne..? Cikin natsuwarsa yace"Daada ya saka a mota"ina shirin mgana sai ga shi ya shigo yana fadin"Ku hanzarta fa Goma ta wuce mu isa kano akan Lokaci,ke kuma ga mai motar nan yana mganar lambar wanda zai kira in ya isa karofin..? Anty Binta har ta fice,Mama ce da Anty Hure ban damu ba nayi karfin halin yi masa mgana ganin zai sake fita cikin Dakiya nace"Ina son mgana dakai" Ba shi kad'ai ba har Mama sai da tayi mamaki gabad'ayan su suka kuramin ido,Sai nayi saurin Kauda kai ina juyawa na koma na bude dakin na shige daidai Lokacin da yake fadin"Fa'iza zamu makara fa kinsan jirgi ba jiranmu zai yi ba" Ina kokarim daidaita yanayina nace"In sha Allahu bazaku makara ba" Biyo bayana yayi muka Tsaya a Tsakiyar falon,na juya bayana ina maida hawayena a bayana ya tsaya yana fadin"Kin kuma juya.?wata mgana ce..? Sai na juyo cikin karfin hali,idona yake son kallo saboda ya Fahimci yanayina ni kuma sai naki basa Dama,jikina ne ya kara yin sanyi Sabida ba jimawa mun yi mgana da Anty Fadila tace ita da mijinta zasu zo Filin jirgi daukan mu sai min je gidanta mun huta sannan su rakamu Sabon muhallin mu,da ita taje jiya ta kara gyara shi bayan kamfani yazo ya saka kayan Furnitures. Har muka gama waya ban samu abunda na gayamatabba, ina jin kunyar gayamata cikin masu sauka a Lagos ba Fa'iza a ciki. Ledan hannuna na mika masa sai ya saki baki yana kallona cikin sanyin jiki yace"Meye wannan kuma..? Kai Tsaye nace"Duba ka gani mana" Sai ya amsa ya bude yana gani Lokaci d'aya yana kallona da mamaki da alamun karin bayani da sauri nace"Kayan ka ne. Tun daga lokacin da ka jingine aurena da kai na daina amfani da duk wani abu naka,Abinci dai naci sannan ka bani wajen kwana Darajan ya'yana nagode kwarai Ishaq." Na fad'a ina kallonsa ido cikin ido yadda ya kafeni da ido ne yasa nasan karin bayani yake so sai na yi ta Mazan cewa"Kayi hakuri Ishaq. Bazan iya binka Lagos ba." Cikin Daga murya yace"What..?wannan wata irin mgana ce Fa'iza don Allah ki bar wannan wasan bana so.." Ya fad'a har yana d'agamin hannu,sai nayi mirmishin takaici kafin nace"Ba wasa nake yi ba. Da gaske nake yi, daman na fad'a maka ka bani Lokaci naga ko zan iya bama auran mu wata Dama ko ba haka ba..? Kamar gaula haka ya gyad'amin kai sai ya bani Damar cigaba da mgana ina fadin"To abunda na Dad'e da yankewa kenan,rasa aikin ka da abunda ya faru yasa na dakatar da kudirina,ammh yanzu tunda ka samu aiki komai ya wuce zama na dakai ya kare daman auran ka jingina ne,  shine nake rokom ka ka karisa ballesa daga wannan jinginan ma'ana ka Furta min SAKI da kan ka" Na gama fad'a ina maida hawayena lokaci daya ina jin karfin gwiwa na shigata shi ko ledan hannunsa ne ta kubce ta fadi kasa cikin Tsananin Firgita kamar kiftawan ido na ji sa ya Damki kafaduna duka Biyu yana fadin"Fa'iza ki daina irin wasaan. Wani irin saki.?ki yi tunani mana kina tunanin zan iya sakin ki ne.?so kike na rabu dake wai Fa'iza..? Kai Tsaye na gyad'a masa kai cikin idonsa nace"Kwarai haka nake nufi ka Sauwake mun auran ka domin bazan so ka cigaba da zama da matar da baka so ba. Ka auri zab'inka a wanchan Lokacin kace nayi maka adalci in barka ka yi rayuwa mai Dad'i da matarka. ni ma a wannan karon ina neman wannan adalci nima a wajenka kayi hakuri ka sakeni, daman a jingine nake kamar yadda ka fad'a" Ban ko gama mgana ba kawai naga ya sakeni da karfi yana fadin"Ina. Wasa kike Fa'iza har fa mun shirya jirgi na jiranmu fa ?kowa yasan yau zamu tafi sai yanzu ki sauya mgana..?ga yara chan na murna sai na fita nace musu me..?su Mama na Tsakar gida me zan gaya musu..?to wai kina nufin na tafi ni kad'ai dagani sai yara.?wa zai kula damu Fa'iza rayuwar mu ta fara tare dake kuma Dole mu karisa tare Fa'iza har Abada babu saki ko yaji Tsakanin aurena da ke" Nima cikin Tsawa da Daga murya na taresa da fadin"Ammh akwai jingina acikin auran namu ko..?sannan akwai Tozarci da wulankanci duk aciki ko.?kayi hakuri na riga na yanke hukunci bazan iya cigaba da zama dakai ba.." Sai ya juyo yana kallona cikin Fitan hayyaci yana fadin"In sake ki na Lalace Fa'iza?kin manta abunda Baba ya fad'amin?yace in na rabu dake na rasa mata tagari sannan bazai taba yafemin ba in na barki,don girman Allah ki bar wannan mganar ki bari in muka isa chan na yarda mu zauna da Mama ki fad'a mata komai tayi mana Sulhu, ammh zuciyata bazata iya Daukan wannan mganar ba. plz ki bari don Allah" Ya fad'a har yana hada hannayensa alamun roko gabadaya tsoro da firgici sun bayyana a saman fuskarsa gabadaya,jikinsa kuma sai rawa yake yi,ina kallonsa kamar zan yi rauni sai  kawai na tuna da irin zaman Tozarcin da nayi da shi na Tsawon shekarun auran mu,kuka ya kwace min na juya baya na ina fad'in"Kayi hakuri ba zan iya ba.." Sai kuka shabe shabe,Ban sani ba ashe duk'amin yayi sai ji nayi yana jan Hijabina Lokaci d'aya yana fadin"Ki yi ma girman Allah Fa'iza ki yi hakiri ki bar mganar nan. Hankalina tashi yake yi in naji kina fadin saki da kuma cewa bazaki bimu ba.?Ta yaya kike so na fara rayuwa a in da baki..? Bansan Lokacin da na juyo,har ina bangajesa cikin daga muryan da bansan ina da shi ba nace"Zaka iya. Nace Ishaq zaka iya.." A baya ka zauna da wata macen inda bani kuma baka mutu ba. Na fuskanci Kaskantattaciyar rayuwa a gidan auranka,na fuskanci tozarci a wajen ka da wajen dangin ka a karkashin auran ka,ka rabani da kowa nawa ciki har da mahaifiyata ka rabani da yan'uwana duk wani mai so na baka kaunarsa,baka son ganin Dariyata sai kuka na Ba a macen aure ka Daukeni ba,ka Daukeni a baiwa,mara gata,jahila wacce bata da ilimin zamani,sannan mummuna baka wacce ka ke zaune da ita Saboda alfarma,wacce tayi ma rayuwarka karan Tsaye Fa'izar dai da tayi ma mafarkin ka kutse, Fa'izar da ka zaunar da ita kana rokonta da ta taimaka tayi maka adalci ka zama na mace Daya,Matar da ka fifita a kan Amaryan ka,Fa'izar da baka san ciwon ta ba,baka san cikin ta ba,baka san zafin nagudar haihuwar ya'yanka da ta dinga yi ba, itace dai wacce ahaka ake kiranta kamar akuya ta cika Haihuwa Fa'izar da ka nemi datse mata Haihuwa saboda baka kara kaunar Zuru'a da ita,Ni ce dai Fa'izan da kasa nuna ma duniya ni matsayin matarka kana jin kunya,Nice Fa'izan da ka ke barina wata da wattani Saboda wata mace ni ce Fa'izan da na dauki dukkan Tozarcin yan'uwan ka har da na Dangin matarka saboda Fa'iza bata da gata,Fa'iza ba kyakyawa bace. Sannan bata da ilimin zamani ba wayayyiya bace ba kuma yar gayu ba ce,sannan ita ba fara bace bata kuma iya haihuwan Fararan ya'ya ba,ni ce Fa'izan da kake kirana mara amfani Fa'izan da auran ta bai amfana maka komai ba ni ce dai Fa'iza nan wannan mai raunin jin,wacce ka ce ka tsani mgana da ita saboda tana saka ka ihu ko ka manta ne..? nice fa nice fa kake kiran bazaka iya Rayuwa a inda bani ba..?karya ka ke yi..Wlh karya ka ke yi.." Na karishe fad'a cikin Tsawa Lokaci daya da kuka sai kawai na zube saman Cafet din ina wani irin kuka mai cin rai ban sani ba ihu na da mganata yasa su Mama rugowa Dakin,duk a gabansu na rika amayar da abunda ke cikina. Su kansu jikinsu yayi sanyi sannan sun kasa gane wasu abubuwan Shi bai ma gansu ba sai ya rarrafa cikin Fitan hayyaci ya na kokarin rikoni nayi maza nayi baya da jajayen idanuwana ina fad'in"Kar ka kara tabani. Kar ka kara in ba haka ba wlh zan sharara maka mari" Na fad'a ina nuna sa da yatsa cikin bacin rai da bai taba ganina aciki ba Sai ya kasa karisowa gabana,cikin rawan baki da na murya yace"Fa'iza ba kin ce kin yafemin ba..? Me ya sa..? Kai Tsaye nace"Eh da gaske na yafe maka,.ammh ba shi zai goge tabon da kayi ma rayuwata ba. Dalilinka aure ya fita kaina na Tsani duka maza sannan nake Tausaya mata ire ire na da Tunanin wata irin Rayuwa su kuma suke fuskanta a gidan nasu auran..?ka taba Tunanin ko sau d'aya kayi min adalci? Nace ka taba wannan tunanin.? Sai kawai na kara fashewa da kuka ina fadin"A  gabana ka kori yar'uwata uwa d'aya uba d'aya,Har kana ikirarin in ka kara ganinta a gidanka zaka had'a ta da Hukuma?ashe ko bata ci darajan aurena da kake yi ba, bazata ci Darajan zumunci ba Ishaq..? Mahaifiyata ta rasu bata san Dadina ba. Har ta koma ga Allah ban taba zama da ita na yini d'aya ba. Ranar da zata rasu ma baku barni na kwana da ita ba,ta rasu ban sani ba. Na rasa uwata ammh ko gaisuwa baka zo min ba, kana wajen wacce ta fini muhimmanci a wajenka.Sai da ka dawo baka iya ce min Fa'iza ya hakuri ba sai Duba na kayi kana ce min ashe wai kuma babarku ta rasu..? Wai ne ma baka Tabbatar ba.?shine kake so na manta..?ko kuwa yadda ka ware ni daga cikin sauran mata a dalilin auranka yasa nayi shekaru ina fama da Gulit din mata masu kyau da gata ne suka chanchanci ado da kwalliya,a gidan ka na fuskanci mata ire irena basu dace da samun soyayyar miji irin Ishaq kabir karofi ba. Shiyasa na yanke shawaran karshen zama na dakai yazo daga yau.Na rantse da Allah bazan bika ko'ina ba. Daganan karofi zan koma daman ranar da Baba yace zai had'a aurena dakai Mama ta koreni sannan tayi alkawarin bazan koma mata gida ba,Karofi na koma wajen Goggo kuma chan aka daukoni nan duniya bani da gatan da ya fi gaban Goggo gabanta zan koma na zauna Domin Fuskarta Sabuwar rayuwata" Na karishe Fad'a ina share hawayena lokaci Daya na mike da Sauri ina fadin"Zainab zata iya kula da kai. Yara kuma Amir da Anum sun yi girman da zasu iya kula da kansu. Ahmad da mutsy ba su da matsala zasu kula da su. Ba lalle ba ne don na faro rayuwata dasu na karishe ta da su ba..Haka Allah ya kaddara Labarin ya kare daga wannan Lokacin" Na fad'a Lokaci daya ina Daukan karamar jakata,Mama na gefe sai sharan kwallah take Anty Hure ta sha gabana tana fadin"Haba Fa'iza ku ba yara bane. yi hakuri mu tafi in mun je chan sai a zauna a fahimci juna' Kallonta nayi kafin nayi mirmishin takaici na tuna har da ita a masu biye ma Mama suna cin zarafina,sai kawai na kad'a kai ina fadin"Bakin alkalami ya riga ya bushe Anty Hure.." Na kad'a kai na zan fita waje,Ishaq ya yi kukan kuran shan gabana yana rike Hijabina na balla masa harara ina fadin"Cikani kafin raina ya baci" Yaki ko sakina fad'i yake yi"Fa'iza ina zaki.?Fa'iza kada ki yi min haka..?me zan ce ma yaran chan..? Fa'iza..Fa'iza" Sharr sai kuka abunda ban taba gani ba,kai na kauda abubuwan suna dawomin kamar yanzu komai ke faruwa,kwace hijabina nayi ina fadin"Na fada maka kuma zan kara fad'a maka na gama zaman aure da kai. Na tsani aure na tsani kowani zamantakewa,Ka sauwak'e min Ko kuma ka k'ara Turgud'e shi daman jinginanne ne" Na turesa zan wuce sai ya makale kafafuwana yana fad'in"Kada ki yi min haka Fa'iza,Kada ki yi min haka" Kasa kwace jikina nayi sai kawai na juya ga Mama tana kuka nima ina Hawaye nace"Mama ki fad'a masa ya cikani don Allah" Sai Mama ta sunkuyar dakai shi ko,sai alokacin yaga su Maman sai ya sakeni ya Rumtuma wajenta ni kuma sai na kwashi Sauri na fita Daga Falon ina Fitowa sai nayi Turus ganin yaran duk Tsaye suna jin abunda ke faruwa ga Anty Binta itama. Cikin mamaki tace"Fa'iza meke faruwa ne har kofar gida ana jin Hayaniyar ku..? Ban bata amsa ba Ishaq ya fito rike da Hannun Mama ya kawota gabana yana fadin"Mama ki gaya mata wlh nayi nadama.bKi gayamata abunda Baba ya sha fada'min,Yace in na rabu dake zan lalace Fa'iza ko so kike kada nayi albarka..? Komai ban ce ba kaina na kallon kasa ina Digar kwallah,Mama ma sai sharan hawaye take yi Anty Binta ta kalli Anty Hure tana fadin"Anty meke faruwa ne..? Anty Hure cikin Damuwa tace"Fa'iza ce tace bazata bisa lagos ba. Tana neman saki ne da wasu mganganun da ban gane ba.." Sai ta waro ido kamar yadda yaran suka yi cikin wani yanayi tace"Fa'iza yanzu kuma?kika ma zauna dashi a bai da shi sai kuma yanzu da Dadi yazo sai kice haka.?aa ku bari muje chan sai mu zauna mu tattauna kin ji ko..?tafad'a gabanta na fadi domin bata san ya wannan al'amarim zai kare ba. Jallonata nayi ina tuna Yadda tayi Tsawon shekaru tana Tozartani har da ita masu saka bakin na zauna sai kawai na share hawayena ina fadin"lokacin da bai da aiki wannan yanayin da mata ire iren Fa'iza ya Dace shiyasa ban tafi ba tun a wanchan Lokacin,sai yanzu kuma da komai nasa ya dawo sai nayi Tunanin Lokacina ya kare daman kema kin sha Fad'a jin dadi bai dace da mata ire irena ba,wahala ce da bauta ta Dace dani kamar yadda Mama ta sha fada. Shiyasa zan tafi zainab itace ta Chanchanci zama da shi Tunda ita ta tako kashin arziki sannan bata yi kama da matan bauta ko wahala ba.." Dukkansu Tsaye suka yi an kasa mai mgana ina gani Anty Binta na zaran ido sai kawai nayi Dariyan takaici kafin nace"Na kwashe fin shekara goma ina bautar aure kuna ganin komai ammh baku taba zaunar da shi kin fad'amasa bai kyauta ba..?sai ni yau don a shekaru goma sha Biyar da auran mu na yunkuro sai ku nemi Danne ni.?wannan karon ba wanda ya isa ya hana Fa'iza tafiya. Zan tafi kuma tafiya ta har abada" Ina gama fad'in haka na ratsa Mama zan wuce sai ta riko Hijabina tana kallona,yanayinta zai sakani rauni sai na daga kaina sama cikin wata murya tace"kiyi hakuri Fa'iza. Ba domin na isa ba..Ki yi hakuri ki Duba yara nan kada ki bar su yi maraicin uwa" Ta fad'a tana nuna su Amir,Anum har ta fara kuka da su Ahmad zuciyata ta karye ammh ban damu ba Hawayena na Shatata saman fuskata nace"Ke kan ki shaida ce Fa'iza bata dace da D'anki ba.,yaran nan kuma rabo ne Allah ya sa na same su,maraici kuma baza su yi maraici ba Mama kina nan ga Zainab,sannan shi ma babansa zai kula da su tunda ya'yansa ne sune Dolensu bazan ce a zama da shi bai Tabamin wani abun alheri ba,yayi min Tunda dalilin sa yasa yau nake amsan sunan uwa,ammh mganar na Duba yaran nan bai taso ba. Nima a lokacin da yake tozartani ko sau d'aya bai tab'a Duba darajan ya'yana ba.." Na fad'a ina kallon su, bana so na cigaba da mgana a gabansu kada su ji,kamar ma Amun da Amir tunda suna da wayan su. Na tuna Lokacin da Anty Binta tazo ita da Mama suna min watsi da kaya akan sai na bar gidan,meyasa yau don nace zan tafi sai su damu..? Wani tukuki ya taso min dayasa har jiri na fara gani cikin Duhun ido na juyo ina fadi'n"daman kuna so na tafi,Aurena ba alheri ba ne ko ba haka kuka fad'a ba..?meyasa don yau nace zan tafi kuke magiyan kada na tafi..?Wlh kaina tuni ya Dauki Dumi kuka na kara Fashewa dashi na juya ga ya'yana da suke kallona cikin rauni hatta Amir da ba kasafai ake ganin kukan ba yau har da majina,Ahmad kuwa da gudu ya nufeni ya rumgume ni yana fadin"Umma zan biki ni dai" Musty ma ya kariso yana kuka ya rikemin Hijabi gam yana fadin"Nima Umma ke zan bi na fasa zuwa Lagos din"suna mgana kukana na karuwa Anum ma ta rugo ta makalemin jiki ta fashe da kuka tana fadin"Umma nima ke zan bi" Ina Kuka suna kuka Amir na Tsaye shi bai zo ba na dago ina kallonsa cikin kuka nace"Amir ku yi hakuri ka zo ka taimaka min ka lallashi kannen ka" Sai kawai shima ya rugo da gudu ya Rumgumeni yana fadin"Umma zaki tafi ki barmu?don Allah kada ki tafi Umma kada ki tafi ki barmu" Sai kuka yadda suke kukan ne yasa naji gabbaina sun yi sanyi in na tafi na barsu yaya rayuwarsu zata kasance?sai na juya ina kallon Ishaq da idanuwansa suka kad'a jajir,sai kawai naji Duhu ya rufeni da Hanzari na yakice su a jikina na duka Bisa gwiyoyina dukkansu na rike hannayensu cikin nawa sannan na Dauki na Amir na rike ina fad'in"ba inda zan je ina karofi gidan Goggo zan koma,In ina bukatar ganin ku zan zo ko ku kuzo wajena,sannan zan rika kiran ku a wayar Anynku muna gaisawa kun ji ko? Ahmad ya makale kafada yana Fadin"ni dai umma zan biki" Musty ma yace haka Anum Sarkin kuka tace"Umma ki tafi damu chan gidan goggon mana" Ina girgiza kai hawaye na zubomin nace"Bazai yuyu ba Anum. ku kuna da Baba sannan ga kakar ku nan bazai yuyu ku bini ba,ni kuma bani da uwa ba ni da uba,Goggo itace gata na shiyasa zan koma wajenta ku kuma Babanku na da mata Antynku ga kannen ku su Farhan,ku zauna lafiya da junan ku ku zama masu jin mgana Amir kai ne Babba ka rike kannen ka Amana ka ja su ajikinka a matsayinka na Babban Yaya,ku zama masu jin mgana da Tarbiya Anum ki kula da Ahmad kin ga shine karamin cikin ku kada ku takurama Antynku komai tace ku yi kuyi kun ji ko..?.sai suka kasa dagamin kai ina kokarin Dauriya na saki Hannayensu na rika bin su daya bayan d'aya ina share musu hawaye ina fad'in"kada ku ce zaku rika saka Anynku mgana,Amir karatu ka rika duba na kannenka,Karatun Qur'ani ku rika bita kada ku manta da azkar din safe da maraice,ban da abokan banza sabon waje ne bakusan kowa ba,kada ku manta da Tarbiyan da na baku Anum kece mace ki rika taimaka ma Antynku da ayyukan gida kuna ji ko..? Sai gabadayansu suka bare min baki Amir jikina ya fad'a yana fadin"Umma mu ba ma a son Antynmu ke muke so.." Hawaye suka kwaranyomin na kamkamesa ina kuka Anum ta ruga wajen Babansu tana fadin"Daada kaje ka ce Umma kada ta tafi.." Tana fada tana jan Hannunsa,sai ya biyota har gabana shima dukawar yayi,yana fadin"Don Allah Fa'iza ki duba yara nan" Ban ko amsa mai ba na hada ya'yana na Rumgume gabad'ayanmu muka saka kuka,Mama na gefe sai ta juya kawai ta fice tana kuka Anty Binta ma duk jikinta yayi sanyi in Fa'iza ta tafi ya kuma abubuwa zasu tafi?Zainab wannan yar son jikin da bata iya komai ba, ta ina zata yi da Dawainiyar yara?akwai matsala babba kuwa. Suna kuka ina kuka da na ga bazai Fissheni ba na rarrashi kaina na koma ina ba su hakura suka makaleni suna kukan sai sun bini Hon din masu mota ne ya ankarar damu suna jiranmu,Ishaq ya marairaice yana fadin"Na siya mana Ticket Fa'iza asaran kudina kike so nayi..? Kai tsaye nace"Ai ban ce ka siya har dani ba. Tunda ban ce maka zan bika ba" Cikin wani yanayi yace"To dukkanmu mun fasa bazamu tafi ba, mu tattara muje karofi a warware komai" Cikin yak'e nace"Kada ka biyoni Karofi Ishaq ka lallaba ya'yanka ku tafi,kada ka manta aikin. ka fara ba jimawa rashinka a office zai iya zame maka matsala sannan meyasa bayan ka kashe kudin jirgi zaka fasa? Na fad'a ina kuramai ido gani yayi kamar na fara saukowa yasa da Sauri ya rikeni yana fadin"Fa'iza zuwan bashi da amfani idan baki kin sani ko? Kai tsaye nace"Bazan bude baki nayi mgana ba.ka lallashi yaran nan ku tafi in kuma kace zaka bini karofi zaka Fallasa kanka da kanka. Daman na Fada maka da bakina bazan fad'i komai ba,sai dai in kai ka fad'a da kanka" Shuru yayi yana ajiyar zuciya a Firgice kamar wanda yayi karya,Ban damu ba naja hannun su Ahmad da Musty,su Amir suka biyo bayana muna zuwa kofar gida masu motoci na jiran mu sawa nayi aka Fitomin da akwatina da jakunkuna na,nace a sakamin a karamar Golf din nan,Mama na gefe tana sharan kwallah,su Ahmad nata kuka har Lokacin sai na Daure saboda bazan bari su hanani Tafiya ba,key din gidan na isa gaban Ishaq na Damka masa ina Fadin"Key din gidan nan, ne Sauran kayana in ka sauwakemin zan zo na kwashe" Makullin fad'i ya yi a kasa,ya kasa amsa ni kuma na juya ina goge kwallah na bude bayan mota na shige,Su Amir sun yinkuro zasu shiga na rufe kofar da karfi ina kuka ina ganinsu suna kuka suna dukan jikin mota ammh na kasa motsi,Direba ya shigo yana fadin"Hajiya yaran nan zasu hanamu tafiya fa" Kai tsaye ina kuka nace"Glass.! d'agamin" Ba musu ya d'agamin na Leko da kaina da sauri suka nufeni Ahmad sai fadi yake Umma nima zan biki shi da Musty,Amir na share ma Hawaye Na rike hannun Anum ina fadin"ba na ce ku lallashi kannen ku ba..? To in dai kuna kuka bazan dawo na Dauke ku ba"jin haka yasa suka daina kukan Amir yace"Umma to kizo mu tafi tare"kai tsaye nace"Aa ku fara yin gaba, ni zan zo daga baya..Ka kula da kannen ka kaji ko Amir" Sai ya gyad'amin kai dukkansu na Shafa kansu ina fadin"Allah ya yi muku albarka"Sai kuka yaci karfina cikin kukan nace"Direba muje" Lokaci daya na maida glass din na zuge,mun fara tafiya na juyo ina daga musu hannu Ahmad ya kwace yabi motarmu yana kiran sunana har yana Fad'i ina gani Baban yaje ya daukesa,Anum kuma Mutsy ta rike tana kuka Anty Binta ta rike Amir kasa Daurewa nayi na juya ina kuka kamar in ce Direba ya Tsaya sai kuma wata zuciyar tace"Fa'iza ki sani ko kin koma baki da wata daraja. Ishaq Zainab kadai yake so ke alfarma yake miki" Ammh ya'yana fa..?basu saba da kowa ba sai ni wazai kula da su..?zasu fara sabuwar rayuwa a inda bani ya ya zasu tafiyar da rayuwar su.?Zainab bazata kulamin da yarana ba bazata iya ba,yar gatace bata saba da wahala ba ,yaranta ma yan aiki ke daukan mata su,Tarbiyan su da na dauk'i shekaru ina ginawa in ta rushe fa..? Kuka nake yi da karfina har sai da Direba ya juyo yana fadin"Hajiya ki yi hakuri,In bazaki iya tafiya ba sai mu koma ko kuma ki taho da su naga yaran basu son tafiyarki hala rabuwa kuka yi da Baban nasu,duk da shima naga kamar bai so tafiyar ta ki ba..? Irin dirobobin nan ne masu fad'i ba''a tambaye su ba. murya shake nace"Karofi..Karofi zaka kai ni" Na katse mganarsa lokaci d'aya ina cigaba da kuka zuciyata na Zafi kaina ya fara Dif Dif ga jirin danake ji. alama ce ta jinina ya haye sama. Har mun yi nisa sai naji bazan iya wannan jarumtar ba ya'ya na,ya'yana kawai nake tunani. Sai kawai na ce ma Direba"Tsaya mallam.." Sai ya juyo yanaa fad'in"In tsaya..? Sai kawai na gyad'a mai kai da sauri ina fad'in"Mu juya mu koma..! mai dani da sauri' Ina haki na fad'a,Tunani na da zullumi na,kada kafin mu koma mun iske sun tafi. Na fasa bazan iya nesa da yarana ba. tunda na iya kwashe tsawon shekaru goma sha, cikin tozarci na jure me zai hana yanzu bazan jure ba..?kuma yayi nadama zan karbi Tubansa zan bisa naje na zauna tare da yarana. Muna tafe ina fadin"Kayi gudu don Allah ka yi sauri." Yadda nake mganar zaka san bana cikin Hayyacina. *K'arshen littafi na Biyu,Littafi na uku zai zo in na samu natsuwa insha Allahu,Ammh ba gabadaya zai zo ba,zai zo kamar yadda muka fara daga farko.* *Nagode..Nagode da Soyayyarku Allah ya bar zumunci Ameen* *Janafty* *19/17/2023*