: *HALIN GIRMA!* ®Hafsat Rano. FREE PAGES! (1) *_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_* *ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA* *_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_* *GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi* *JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE* *_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_* *_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_* *_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_* *_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_* *_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_* *DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL* 2👉🏾400 3👉🏾500 4👉🏾700 5👉🏾1000 *Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin* 6019473875 MUSAA ABDULLAHI SAFIYA keystone bank Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 08184017082 *IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU* 09134848107 *_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽 #team zafafa biyar (1) ***Komai na rayuwa na tafiya ne bisa tsari da kudurar ubangiji, komai ya faru da bawa dama tun fil azal hakan na cikin kaddarar sa, Wala kaddara mai kyau ko kuma akasin ta. Yarda da Kaddara me kyau ko mara kyau na cikin Imani!    A tsaye take gaban sink din cikin toilet din tana wanke kananan kayan da ya kasance mallakin Maama da Zeenat, lokaci zuwa lokaci tana cire hannun ta tana yarfe shi saboda sanyin da ake zugawa kasancewar karshen December ne a lokacin da ake zuga sanyi. Dauraye kayan tayi ta yi saurin fitowa ganin haske ya hudo ta window din toilet din. Karfe shida da rabi agogon falon ya nuna, tayi saurin karasawa kitchen din domin dora abin karin kumallo kafin ahalin gidan su tashi.   Tun kafin asubah take fara ayyukan gidan wani lokacin har karfe tara na safe bata kamalla wa, duk kuwa da tana iyakar kokarin ganin bata wuce taran ba saboda karatun ta na islamiya da take zuwa duk weekend, tana ganin shine kadai gatan da zata yi wa rayuwar ta a halin da take ciki a gidan mahaifin ta. Bata fatan wani ya shiga irin rayuwar da take ta kunci da tsantsar makirci, babu wanda ya san halin da take ciki balle ya kawo mata dauki, bata isa ta bud'e baki ba saboda kowa ganin kirki da karamcin Maman yake, mace ce me masifar kirki, me haba haba da saka duk wani abu nata gaba da na duk sauran yayanta a idon ahalin gidan,a badini kuwa bata da maraba da bola.    Kowa kallon mara dadin zama yake mata ko kuma mara godiyar Allah saboda rashin walwalar da take fama da har ya shafi kaso mafi rinjaye na rayuwar ta, zaka dauka bata dariya ko doguwar magana sai dai bata da sukunin yin kamar sauran yan matan gidan nasu.   Kowa kallon wadda tayi sa'ar uwar riko yake mata, ayi ta sakawa Maman albarka da yabo a gabanta tana amshewa amma a bayan idon mutane! Bakar wahalar da take sha ba zata misaltu ba.    Da tunanin ta kammala aikin ta dauraye hannayen ta sannan ta fito ta jera musu a saman dining ta dauko nata a dan plate ta wuce zuwa dakin su.    Bude kofar da tayi ya farkar da Zeenat, a zafafe ta dago ta watsa mata kallon banza gami da jan d'an karamin tsaki tana sake rufe kanta da katon duvet din da take kanannade a cikin sa. Cikin nutsuwarta ta karasa shigowa d'akin tana dora plate din saman d'an madaidaicin mudubin dake cike da kayan shafe-shafe ta soma gyara wajen data tashi. Katifar ta fara daukewa ta kaita chan store sannan ta dawo ta share dakin a hankali gudun magana taci abincin a tsaitsaye ganin lokaci na neman kurewa tayi saurin watsa ruwa a gaggauce ta fito.   Dogon hijabin ta ash colour daya kasance a matsayin uniform din islamiyar tasu ta saka bayan ta gama shiryawa ta dau yar madaidaiciyar jakarta me dauke da Al-kurani me girma da sauran littafan addini ta fito.    Habib na zaune saman dining da alamun zaman sa kenan ta gaishe shi a nutse sannan tayi masa sallama ta wuce islamiyyar dake chan kasan layin su inda take zuwa duk asabar da lahadi da safe sai sauran ranakun da yamma amma banda juma'ah.          *Babban gida ne irin wanda zaka kirashi da Family house, bangarori ne da dama a ciki wanda yake dauke da gidaje guda shida dake kunshe da mutane cikin su suna rayuwa irin wadda suka zaba ma kansu. Duk da kowanne bangare na da tsarin da yake tafiyar da rayuwar sa akai amma kuma suna tafiya ne da ra'ayoyin juna, daya baya taba zartar da hukunci be sanar da daya ba, sannan duk abinda suka zartar din dole ne ya samu amincewar mahaifiyar su Hajiya Fatima wadda suke kira da Gaji.    Gidan ta ne a tsakiya in da sauran gidajen ke kewaye da ita, galibin yan matan family din suna tattare ne a shashen nata da ya zama tamkar matattarar su, yanayin haihuwa a family din na tafiya ne kusa da kusa, inda zaka samu yawanci sa'oin juna a kowanne gida.   Duk da basu da tarin dukiya irin me yawan nan amma suna da rufin asiri daidai gwargwado, sannan ana damawa dasu a duk bangarorin ilimi na Islama dana bokon hakan ma bangaren kasuwanci da siyasa duk babu wanda basa tabawa.    Zamu iya cewa kowanne a cikin yayan Gajin yayi sa'ar abokiyar zama ta kwarai dan babu wanda yake kuka da abokiyar zaman sa, daidai gwargwado suna zaman su lafiya suna kuma mutunta juna suna girmana Gaji da duk wata bukatar ta.    Muguwar mace me kinibibi da kissa zai yi wuya ka gane alkiblar ta farat daya, komai su kayi daidai ne suna kuma da kokarin kyautatawa kowa, suna kokarin boye aibun su suyi amfani da hakan wajen muzgunawa wanda basu so, idan yayi korafi a bashi rashin gaskiya saboda kirkin su.    Alhaji Muktar shine Babban dan Hajiya Gaji bayan Babbar Yayar su mace da suke kira da Hajiya Babba dake zaune a Sheffield dake birnin London tare da family dinta , sai me bi masa Dr Ibrahim, sai Abba Usman sai Abba Musa sai dan auta Abba Kabir.    Dr Ibrahim dan boko ne sosai dan har ya kai matakin associate professor in da yake lecturing a halin yanzu. Matar sa daya ta aure Maama wanda zamu iya cewa kaf family din babu wanda baya kaunar ta saboda kirkin ta. Yaranta uku da Dr, Habib ne Babba, sai Zeenat sai karamin kanin su Marwan. Sai dai shi yana da ya daya daban wadda suke haifa da matar da ya aura a lokacin da yaje karatun sa na Masters a University of Michigan, anan suka hadu har sukayi aure suka haifi ya daya me sunan Gaji (Fatima-Iman) a lokacin ne kuma suka rabu saboda wata babbar matsala da ta taso tsakanin shi da family dinta, dan dama basa son auren, yana ji yana gani ya rabu da ita, ya dawo gida. Fatima na yin wayo suka kawo masa ita inda ya dauki rikon ta ya damka a hannun Maama wanda a lokacin take goyon Zeenat itama. Bata taba nuna masa komai ba ko a fuska kuma be taba ganin wani banbanci tsakanin Fatima da Zeenat ba, shiyasa ya kara bata mazauni me girma a zuciyar sa. ***Daidai layin su ta hangi Zeenat tsaye da Bashir, dan dam taji a zuciyar ta kasancewar ba wannan ne karo na farko ba, duk wanda yace yana son ta in sha Allah ba za'a dau lokaci ba zata same shi tare da Zeenat shikenan kuma ta ta maganar ta sha ruwa. Zeenat yar uwarta ce amma duk da haka tana jin babu dadi, sai dai bata bar hakan yayi tasiri a zuciyar ta ba, ta dau hakan a matsayin wata jarrabawar rayuwar ta. Daidai in da suke tsaye tazo zata wuce Zeenat din ta kira sunan ta "Iman!" Tsayawa tayi chak, ta kalle su kad'an sannan tace "Sannun ku." Murmushi Bashir din yayi mata sannan yace "Malamar islamiyya, sannu da zuwa." Bata amsa masa ba dan yadda yayi maganar taji akwai alamun rainin wayo "Ya akayi?" Tace tana kallon Zeenat. "Babu!" Ta dage kafadar ta. "Ok!" Tace tana cigaba da tafiyar ta, tana jin sanda suka kwashe da dariya, ta dan ji babu dadi a ranta amma ta danne, ta karasa gidan duk ranta babu dadi. Da gaske ta ji zuciyar ta, ta amince da Bashir farkon magana da yayi mata har tana addu'ar Allah ya tabbatar mata dashi, sai gashi tun ba'a je ko ina ba, ya koma wajen Zeenat wadda ko da ace da wasa yaje wajen Zeenat din toh babu ita babu shi har abadah. A gate taci karo da Maryam, a kalla ba kamar sauran ba, Maryam ta fuskance ta, shiyasa tasu tazo daya sosai, duk da ba wata doguwar hiraa ce ke hada su ba amma ta kan sake da ita fiye da kowa. Bikin su za'a yi su hudu a gidan. Maryam din sai Bilkisu, Aysha da Amina. Daga su sai ita da Zeenat da yar gidan Abba Musa Rabi'ah sune a layi, duk cikin su babu wanda bashi da me son shi amma banda ita da ta gagara samun wanda ma zai tsaya din. Bangaren Gajin suka wuce tana mata hira akan shirye shiryen bikin, rabin hankalin ta baya kan Maryam din har suka karasa, suna shiga ana kiran sallar magriba sai kawai suka wuce sukayi alwala. Bayan sun idar ne Gaji ta kalle su tana kan abun sallah kamar zatayi magana sai kuma ta fasa. Sai da ta gama ta tashi sannan tace "Maryama daga ina haka ke da alhuda-huda?" "Daga islamiyya Iman take ni kuma na fito zan taho nan muka hadu." "Toh ku tashi ku dubo min ko an gama tuwo dan cikina ya soma kiran chiroma." "Wai Gaji wasa wasa fa kina da ci wallahi." "Saukin ta ba kowa ke siyan kayan abincin ba 'yaya na ne, ko zaku hana su bani ne?" Rik'e baki Iman tayi tana dariya Maryam tace "Bamu isa ba ai Gaji, aci dadi lafiya lokacin ki ne." " Yafi muku sauki dai, kema alhuda-huda kin fara zama su balki ko? Kika biye musu baki da bakin da zaki iya karawa dani atau." Shiru tayi bata ce komai ba, suka zagaya kitchen din Gajin da ke baya suka hado mata abincin suka kawo mata sannan suka zauna suka ci tare, lokaci lokaci Maryam na tsokanar ta, ita dai Iman jin su kawai take har aka gama suka tattare kayan sannan Maryam ta tafi ta barta a nan, sai kawai ta zame tayi kwanciyar ta a saman doguwar kujerar ta fad'a kundin tunani kamar yadda ta saba. "Yaya Iman kizo inji Maama, zamu ci abinci kar ya huce baki ci ba, kiyi sauri." Muryar Marwan ta iso daidai kunnenta, da sauri ta tashi zaune, sai kuma ta mike da sauri tana jin sanda Gaji tace "Hajara ba dai kirki ba, yadda kike kula da yarinyar nan ubangiji Allah ya kula miki da naki yayan." Wasu guntayen hawaye ne taji suna neman zubo mata, tayi saurin maidasu ta kara sauri zuwa shashen nasu domin amsa kiran Maama. _*KASHI NA BIYAR*_ _*KASHI NA BIYAR*_ _*KASHI NA BIYAR*_ _*KASHI NA BIYAR*_ *_KASHI NA BIYAR_* _*SABUWAR SHEKARA, SABUWAR TAFIYA, SABON SALO*_ 🔥🔥. 🔥🔥. 🔥🔥. _*ZAFAFA BIYAR!! KASHI NA BIYAR!! SINADARIN ZAFAFA5 (BEST TOP 5)*_ _*INA MASOYA KUMA MAKARANTA, MABIYA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR? KU MATSO DOMIN NESA TAZO KUSA, KU SHARE HAWAYEN KU, ZAFAFAN NAKU SUN SAKE DANNOWA DA TURURUN SU, MASU ZAFAFAN FADAKARWA, NISHADANTARWA HAD’I DA ZAFAFAN KAUNA MARAR GAURAYE.*_ _*YAN BIYAR DIN NAKU KAMAR KO DA YAUSHE SUNE:*_ _*SAFIYYAH HUGUMA*_ _DABI'AR ZUCIYA_ 2-_*BILYN ABDULL*_ _TAKUN SAK’A_ _*3- MAMUH GEE*_ _DEEN MARSHALL_ _*4-HAFSAT RANO*_ _HALIN GIRMA_ _*5~NANA HAFSAT (MISS XOXO)*_ _SO DA ZUCIYA❤️_ 1 _DAGA TASKAR *SAFIYYAH HUGUMA* MARUBUCIYAR ZAFAFA DA TAYI; DAURIN BOYE, ALKAWARIN ALLAH, ALKIBLA, SIRADIN RAYUWA TA SAKE ZUWA DA WANI RANTSATTSE MAI SUNA:_ *_ƊABI'AR ZUCIYA_*😍 2 _DAGA ALKALAMIN *HAFSAT RANO* , MARUBUCIYAR ZAFAFA DA TAZO MUKE A BAYA DA, DAURIN GORO, ABINDA KE CIKIN ZUCIYA, SAUYIN KADDARA, MABUDIN ZUCIYA. WANNAN KARON TAZO DA WANI SABON SALON MAI SUNA:_ *_HALIN GIRMA_* 3 _DAGA SALON TAFIYAR *MAMUH GEE* ,WADDA A LITTATTAFAN TA NA ZAFAFA TAYI; MIN QALB, BURI DAYA, KAUNAR MU, UBAYD MALEEK. WANNAN TAFIYAR TAZO DA WANI DADDA’DA MAI SUNA:_ *_DEEN MARSHALL_*🥰 4 _DAGA TAFIYAR RUBUTUN *NANA HAFSAT (MISS XOXO)* WADDA A ZAFAFAN BAYA TAYI WASU KAMAR SU: KAI MIN HALACCI, KIBIYAR AJALI, DALAAL, IGIYAR ZATO. WANNAN NEXT LEVEL DIN TAZO DA WANI MAI TAKEN:_ _*SO DA ZUCIYA*❤️_ 5 _DAGA SALON RUBUTUN *BILYN ABDULL* MARUBUCIYAR ZAFAFA DA TAYI NA BAYA IRIN SU: WUTSIYAR RAKUMI, SARAN BOYE, MAKAUNIYAR KADDARA, GUDU DA WAIWAYE. WANNAN SABUWAR TAFIYAR TAZO DA WANI MAI SUNA:_ *_TAKUN SAKA🔥_* ☄️💫💥✨? _*KADA KU BARI AYI BABU KU, KUZO A DAMA DAKU A SABUWAR TAFIYA MAI TAKEN SABON SALO, SINADARIN ZAFAFA BEST TOP 5, MASU ZAFAFAN DARUSSA, NA RAYUWA, WANDA DUK WANI MAKARANCI BA ZAI RASA DARUSSAN DAUKA ACIKI BA.*_ _*GUDA DAYA: 300*_ _*BIYU 400*_ _*UKU 500*_ _*HUDU 700*_ *_BIYAR DUBU DAYA (1k)_* *_YAN TALLAH SAMAN SHAFI NAIRA 300, ‘KASAN SHAFI KUMA 200 NE_* _*YADDA ZAKU BIYA*_ *_ZAKU TURA KUDINKU ACIKIN WANNAN ASUSUN NA BANKI_*👇👇👇👇 *6019473875* *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai katura shedar biyanka ta wannan number*👇👇👇 08184017082 _*IDAN KATIN MTN NE, KO VTU SAI ATURO ZUWA GA*_👇👇👇👇 09134848107 _#TEAM ZAFAFA BIYAR_🔥🔥     1/2/22, 22:47 - Buhainat: *HALIN GIRMA!* ©®Hafsat Rano. FREE PAGE (2) ***** Takalmin Abban su da ta gani a kofar shiga falon yasa ta sauke ajiyar zuciya, ta bud'e labulen hade da sallama, idonta ya sauka a cikin na Mama da take kallon kofar, tayi mata wani kallo me cike da ma'anoni da ba kowa ne zai gane ba sai ita kadai da ta san manufar sa. "Abba barka da gida." Tace tana zamewa k'asa "Yawwa Uwata, kina ina haka mamanki na ta neman ki kinsan bata so kici abincin da ya huce ko? Ga yanayi na sanyin nan ba komai ne yake rik'e zafin sa ba." "Ina wajen Gaji ne." Tace tana sake yin kasa da kanta. "Toh dai a dinga kula ana abinda ya kamata kinji? Allah yayi muku albarka." "Amin." Tace tana mikewa ta shige dakin su da dan sauri tana avoiding idon Maman da ta rakata dashi. D'are-d'are ta tarar da Zeenat a saman gadon tana waya, wuceta tayi ta bud'e jakar kayan ta, ta sauya kayan jikin ta da wasu ta ninke Hijab din sannan ta dawo ta saka abun sallah a k'asa ta zauna ta ciro littafin da akayi musu a islamiya ta soma karantawa a hankali. "Malama kina distracting dina." Ta zare wayar daga kunnen ta tayi maganar a chunkushe. Banza tayi mata ta cigaba da karatun ta ba tare da ta daina ba. "Mtsww!." Ta ja dogon tsaki "Baby bari zan kiraka ina zuwa.* "Owk dear, ina jira." Katse kiran tayi ta zuro kafafunta daidai wajen da Iman din take zaune "Malama duk karatun da kikayi a islamiya be ishe ki ba, sai kinzo kin cika mana kunne mu san kina zuwa makaranta, bayan kowa yasan dalilin da ya saka kika nace da zuwa ko kya samu ya sayyadi ya ce yana so." Bata tanka mata ba, hakan ya sake kular da Zeenat din, ta saka hannu zata warce littafin tayi saurin janyewa ta mike tsaye, "Wallahi sai dai ki hakura da karatun ko kije chan kiyi, naga ma aiki ne gaban ki kin sani tsabar kinibibi so kike sai ya jiyo ki kina karatu. " " Kinga duk abinda kike yi bana taba tanka miki, ba wai don ina tsoron ki bane ko wani abu, kawai bana son tashin hankali ne da hayaniya. " " Toh ki tanka min ma mana, wallahi yanzu zanje na hado ki da Mama." Bata sake magana ba ta fice daga dakin dan ba karamin aikin Maman bane ta hanata zuwa makarantar na wani lokaci, sai kawai ta zarce kitchen ta tarar da kayan wanke-wanke tuli guda, ta nannade hannun ta tasoma wankewa. Abincin da ta gani a tukunya ta san nata ne, yayi mugun sanyi ita kuma a ka'idar ta bata cin abinci me sanyi, ko ruwan sanyi bata sha a rayuwarta balle yanzu da ake zuga sanyi sosai., gudun ta barshi bata ci ba gobe a hanata yasa ta samu leda ta juye a ciki ta wanke tukunyar ta goge gas da k'asan kitchen din ta gyara komai tsaf sannan ta fito da ledar ta zagaya ta kofar baya ta fita zuwa part din Gaji, ta samu me aikinta ta bata sannan ta dawo ta dauko katifar ta a store ta wuce dakin.    Har lokacin Zeenat bata gama wayar ba, toilet ta wuce ta dauro alwala tazo tayi shafa'i da wutri sannan ta kwanta ta rufe kanta gaba daya da dan yalolon zanin gadon da duk ya yayyage ta gefe da gefe ta kudundune da haka bacci ya dauke ta.    Da safe ta tashi kamar kullum tayi ayyukan da suka zama wajibi akanta, kasancewar litinin ce sai ta yi wanka kawai ta wuce shashen Gaji bayan ta tabbatar da fitar Mama tun sassafe, a chan taci abincin ta sannan ta kwanta bacci. Sai da rana ta soma dagawa sannan ta koma ta daura girkin rana,ta gama kafin lokacin tafiya islamiya, ta dauki na Gaji ta kai mata ta sake zama tana jiran lokacin ya cika. "Yaki takwara ta, zo nan." Gajin tace tana daga zaune a in da take "Me yake damun ki?" "Na'am?" "Fad'a min idan kina da wata matsala ne, na dade ina lura da yanayin rashin walwalar ki, sai dai na kan dauki hakan a matsayin halitta, amma kuma jiya sai abun yazo kaina, na dinga tunanin ko dai kina da wata damuwa ne? Da kika kasa sanar wa wani kika barta a ranki." "Babu komai Gaji, yanayi na ne a haka amma ni babu abinda yake damuna." "Kin tabbata." Daga mata kai tayi tana jin kamar ta saki kuka, ga dama ta samu amma bata da ikon furta wa, toh tace mene ma wai? Hakan ba shi zai hana Mama ta daina muzguna mata ba, Kai tsaye zata kare kanta da zarar Gajin ta tuhume ta karshe kuma abun ya koma kanta kowa ya cigaba da mata kallon marar kirki ko kuma wadda bata san halacci ba. Shiyasa ta zabi yin shiru kawai dan fadar ba zata sauya komai ba, su duka sun yarda da Maman yarda irin ta ban mamaki. "Ai nasan bangaren Hajara baki da wata matsala dama, na dai zata ko damuwa ce dai irin ta rashin maman ki kusa dake, duk da bani da haufi akan kulawar da kika samu iyakar abinda zaki samu kenan ko da ita mahaifiyar taki ce." "Haka ne." Tace a kasalance "Yawwa ki dinga dan daurewa kina shiga cikin yan uwanki kinji? Zaman shirun da kike babu dadi." "In sha Allah zan gyara." "Yawwa... Haka nake son ji." "Ya batun yajin aikin nan kuwa? Kun dauko karatu tiryan tiryan yajin aiki ya tsaidaku da tuni wata maganar ake ba wannan ba." "Wallahi shiru ba labari, muna dai ta addu'a Allah ya sa a daidaita." "K'asar nan kenan ai, dan karatun ma yanzu nema ake a hana dan talaka yin sa." "Wallahi." " Allah yayi mana maganin abinda yafi karfin mu." " Amin ya Allah!" " Shiyasa nace duk ku fidda mazaje kawai da zarar wadanchan sun tafi kuma azo ayi naku zaman haka nan ba zai yiwu ba." Shiru tayi gabanta ya fadi, bata son taji ana maganar auren su, gashi kuma taga alamar ba za'a dauki lokaci ba za'a ce su fidda mazaje, ya zatayi da ranta? Da ganin suna makaranta yasa maganar ta lafa amma yanzu yajin aikin da aka tafi da ba'a san ranar dawowa ba ya saka iyayen nasu yanke shawarar suma su aurar dasu kawai sai karasa karatun a dakin su.    Tashi tayi tayi ma Gajin sallama ganin lokaci yayi, taje tayi alwala ta saka Hijab dinta ta fito, a falo ta tarar da Mama tayi saurin tsugunnawa ta gaishe ta " Mama barka da gida." " Saura idan an tashi ki tsaya shiririta a hanya ko ki tsaya gidan Gaji karki zo kiyi abinda ya dace, jiya kam kinci darajar babanku yana nan." "In sha Allah." Tace sannan ta mike ta fice Maman ta rakata da harara. ****Sati biyu tsakani aka fara bikin gidan nasu, duk yadda taso gujewa wasu abubuwan amma Maryam bata barta ba, komai idan za'a yi sai ta sakata a ciki, haka kunshi da gyaran kai tare suka je da wata kawar Maryam din.   Alhamis suka fara bikin, a compound din gidan Anty Mabruka sukayi bridal shower iya su da kawayen su, juma'ah akayi kamu asabar aka daura aure hade da yini, lahadi aka kai kowacce gidan ta.    Ranar litinin suka tashi gidan da sauran bakin da basu riga sun tafi ba wanda yawanci dangin Gaji ne, a babban kitchen din gidan suka hadu aka hada breakfast Masa da miyar taushe, har rana tayi sosai basu kammala ba hakan ya sake haifar mata da wata irin gajiya bayan wadda take fama da ita, tasan halin Mama sarai idan ta makale taki fitowa ayi aikin da ita duk da akwai masu yi din amma dolen ta ne ta fito, duk da hakan ba karamin taimaka mata yayi ba wajen gogewa da kalolin girke-girke mabanbanta. Sannan uwa uba girkin mutane da yawa wanda ba kowa bane ya iya.    Da saurin ta, ta karasa dakin su, ta kwanta a gefen gadon saboda wani irin sanyi da take ji alamun zazzabi ne ke neman rafke ta, rawar sanyi ta fara hakoranta suka shiga haduwa waje daya, ta saka hannu da k'yar ta jawo bargon Zeenat din ta lulluba.    Shigowar ta kenan ta tsaya daga kofar "Kut! Lallai ma." Tace tana karasawa ciki, ta fuzge bargon da karfi "Dan Allah zee ki kyale ni bani da lafiya." Tace muryar ta chan ciki. Shiru Zeenat din tayi tana kallon ta, sai kuma ta sakar mata bargon ta juya ta fice daga dakin. Har dare zazzabin be sake ta ba, babu kuma wanda yazo neman ta. Tayi tunanin Zeenat din zata fad'a wa Maman ne duk da bata saka rai ba, amma jin shirun ya tabbatar mata da ta fad'a mata dan da ba haka ba da tuni Maman ta turo neman ta akan wani aikin.    Wajajen Tara Zeenat ta dawo dakin, ta kalle ta a zaune saman abun sallah ta kudundune, juyawa tayi ta fita ta dawo da paracetamol a hannun ta da ruwa ta mika mata. Karba tayi da sauri tayi mata godiya, bata amsa ba ta sake fita sai gata ta dawo da katifar Iman din, ta shinfid'a mata sannan ta dauko bargon ta, ta dora mata akai ta haye gadon ta kwanta ta rufe idon ta. Sosai Iman taji dadi a ranta, ko ba komai tayi mata abinda bata taba ba, tashi tayi da k'yar ta lallaba ta fita kitchen ta hado tea sannan ta dawo ta sha da k'yar ta sake komawa ta kwanta ta kudundune.    Kwanan ta uku a haka, har ta soma samun karfin jikinta, Mama ta shigo sau daya ta bata anti-malaria shima dan tasan Abban zai iya tambaya ne, shima da tasan zai shigo ya duba ta ne, tana jin sanda take ce masa sun je asibiti ma kuma jikin da sauki.    ***Karamin daki ne da yafi kama da shago, katifa ce karama irin ta yan boarding school sai jakar kayan sa a gefe, bayan haka babu komai a dakin sai wani dogon mudubi dake rataye jikin bangon dakin.    Tsaye yake a gaban mudubin yana duba fuskar sa dake cike da kasumba ko ina har baka iya ganin komai na fuskar tasa sosai, kansa rufe yake da katuwar hular sanyi, ya nannade wuyan sa da abu, kafar sa da hannun sa duk rufe suke cikin hular sanyi, idan ka cire fuskar sa da itama kasumbar bata wani bari a ganta sosai, babu wani abu na jikin sa dake a bud'e. Kayan jikin sa a wanke suke tsaf, sai dai sun tsufa sosai, har da wata yar bula a jikin hannun rigar.    A ko da yaushe yakan tsaya ne a daidai hanyar da take hucewa idan ta dawo daga islamiyya, amma kuma kwana biyu ya rabu da ganin ta, shiyasa ya yanke shawarar zuwa gida duk da yasan ba tsarar sa bace amma zai gwada sa'ar sa.    *_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_* *ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA* *_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_* *GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi* *JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE* *_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_* *_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_* *_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_* *_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_* *_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_* *DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL* 2👉🏾400 3👉🏾500 4👉🏾700 5👉🏾1000 *Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin* 6019473875 MUSAA ABDULLAHI SAFIYA keystone bank Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 08184017082 *IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU* 09134848107 *_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽 #team zafafa biyar 1/2/22, 22:47 - Buhainat: *HALIN GIRMA* Hafsat Rano 3 **** Tsaye yayi jikin gate din gidan yana kare masa kallo, tunanin ta yadda zai fara shiga yake musamman da ba sanin sunan ta yayi ba, ya dai saka mata suna da zuciyar sa kuma be taba yunkurin tsaidata balle yaji sunan ta ba.   Lekowa maigadin gidan yayi, ganin mutum a tsaye yasa shi fitowa gaba daya "Sannu." Yace masa yana kokarin daidaita muryar sa "Yawwa sannu, wa kake nema?" Maigadin ya tambaye shi yana kare masa kallon cikin rashin sani. Nan fa ake yinta, shiru yayi kamar me nazari shi kuma maigadin ya kafe shi da ido yana son jin abinda ya kawo shi. "Am... Amm nazo wajen..." "Malam Iliya." Zeenat dake fitowa ta kirashi tana leko wa. "Na'am ranki ya dade!" "Siyo min kati na 500 kayi sauri dan Allah." "Yanzu kuwa, ga wani bako nan bansan wajen wa yazo ba dai kin tambaye shi." Yayi gaba, kallon sa tayi tun daga sama har kasa a wulakanci ta yatsine baki tace "Wa kake nema kai kuma Malam?" "Yar uwarki nake nema dan Allah, wata me zuwa islamiya kasan layin nan doguwa haka fara." "Waye kai a wajen ta?" Kallon cikin ido yayi mata, ta ja tsaki tana juya fuskar ta "Ban fiye son kallo ba Malam, ka shigo ciki bari na tura maka ita dama ai sai dai ita din..." Gaba tayi tana cigaba da sababi "A kaf gidan nan wa zai kwaso mutum irin wannman dan Allah! Ji shi kamar wani mahaukaci." Sai ta kwashe da dariya tana sake daga kafa. A kwance ta tarar da Iman tana danna wayar ta da ba kasafai ta cika wani amfani da ita ba, yanzun ma wani labari ne yaja hankalin ta a Facebook take karantawa. " Kina da babban bako a waje da galleliyar ranar nan." " Waye?" " Idan kika je idon ki zai gane miki shi." " Owk."     Tace tana tashi zaune, har yanzu bata gama dawowa daidai ba amma haka ta karfafa jikinta tayi ayyukan ta. Hijab ta saka madaidaici akan doguwar rigar jikinta ta fito. Daga chan hanyar gate ta hange shi a tsaye ya rataye hannayen sa a bayan sa, kansa a kasa yana wasa da kafar sa.    Dogo ne na ajin farko, jikin sa ko ina a murje babu alamun rama ko kad'an, yanayin shigar sa bata dace da tsarin zubin halittar sa ba, kafin ta karasa ta gama ayyana shi a ranta. Da sallama ta isa, ya dago da sauri a lokaci daya kwayar idon sa ta sauka a cikin ta ta, gabanta ne yayi masifar faduwa, tayi saurin janye idon ta, ta russuna kad'an tace "Ina wuni?" Lumshe idon sa yayi ya bud'e, fuskar sa dake cike da kasumba ta dan yi fadi alamun farin ciki, ya tattaro dukkan nutsuwa da jaruntar sa yayi gyaran murya yace "Kina lafiya?" "Alhamdulillah." Tace a gajarce ta matsa wajen wasu kujerun roba guda biyu ta dauko daya ta kawo masa. "Bismillah zauna kana ta tsaiwa." Hannun sa ya dora a saman kujerar ta kalli hannun yayi saurin janye shi ya zauna sannan yace "Kefa?" Wani dan tudu a wajen ta nuna masa da hannu, ta zauna akai tana jin duk ta takura ganin yadda yake bin ta da kallo da wasu irin idanun sa da suka sake shiga ciki sosai. "Na same ki lafiya? Ya gida yasu Mama da yan uwa?" "Lafiya lou Alhamdulillah." "Ban gane waye ba amma?" "Me sonki ne, me kaunar ki da son duk wani farin cikin ki, yan kwanakin nan da na dauka banga wucewar ki ba, sun zame min kwanaki mafiya muni a rayuwa ta. Na kan zauna a duk yini ina dakon wucewarki, ban taba yunkurin yi miki magana ba, sai dai zuciya ta, ta gaza dauka har sai dana biyo bayanki, ina fatan ban takura miki ba?" Girgiza kai tayi tana jin wani bawai, wai ita ake karantawa wannan kalaman, idan har taji daidai wato ya dade yana bibiyar ta, bata ma sani ba. " Kinyi shiru!" Yace yana gyara zaman sa Shirun ta sake yi dan bata san me zata ce masa ba. " Nasan dama karambani ne irin nawa, ban kai ajin ko da me wanke miki takalmi bane, kiyi hakuri idan nayi miki shishigi a rayuwar ki." " A ah wallahi, ba haka bane ba, a kalla mutumin da yace yana son ka ai yafi makiyinka, nagode sosai da soyayyar ka gareni."  Tace da sauri sannan tayi murmushi, ji yayi kamar zuciyar sa zata fito daga kirjin sa, ya danne sosai ya maida mata murnushin "Nagode Nuryyy... Nagode sosai." Shiru ya biyo baya, ta dinga wasa da gefen Hijab dinta shi kuma yana satar kallon ta. Nutsuwarta tafi komai tafiya dashi. "Bari na wuce." Da sauri ta mike kamar me jiran kad'an, "Ka gaida gida." Tace tana saurin yin gaba "Ko zan samu number waya dan Allah?" Tsayawa tayi ta mika masa hannu, ya shafa aljihun sa dukka "Kinga garin sauri na manta wayar a daki, amma zan rik'e fad'a min." "Ok ." Tace ta karanto masa, " Nagode sunana Muhammad." " Fatima, ka gaida gida." Ta juya ta barshi a tsaye a wajen. Sake maimaita sunan Fatiman yayi, ya saki murmushi a hankali sannan ya juya ya fice daga gidan. ***A zaune a falo ta tarar da Mama na waya, zata wuce ta tsaida ta da hannu ta cigaba da wayar ta " Ba za dai ka bar maganar nan ba ko Khalil? Toh shikenan sai kazo din dai ma sake tattaunata, idan yaso ko a dangi ne sai ka duba sosai ba za'a rasa ba ai." Amsa ya bata daga bangaren sa, ta ja tsaki tace " Matsalata da kai kafiya wallahi toh sai anjima, sai kazo din." Ta kashe wayar ta dangwarar da ita a gefen ta " Na rasa shegen taurin kai irin na Khalil wallahi, sam baya kaunar ya ganni cikin farin ciki, mtsw." Ta sake jan tsaki a karo na ba adadi. " Daga ina kike?"ta jeho mata tambayar bayan ta riga ta san inda take. " Wani ne yazo dama." " Waye shi?" " Bansan shi ba nima, wai a bayan layi yake." " Toh kina jina? Idan zaki yiwa kanki kiyamullaili ki rik'e shi hannu bibiyu toh, idan kuma kika yi wasarairai da shi shima ya gudu kamar sauran, sai ki zauna muyi ta jerawa a gidan nan,tunda dai bakin hali ya hana samarin zama kowa yazo sai ya tafi." Bata dago ba, bata kuma ce kala ba, tana jin Maman tana kuma ajiye kowacce magana a mazaunin da ya dace, sai da ta gama yi mata cin fuskar sanann tace " Khalil zai zo gobe, babu ruwanki dashi da shiga harkar sa, ko falo bana so naga kina kaiwa da komowa har ya tafi, zan fi so ki tattara ki koma wajen Gaji da zama aikin ma na yafe miki, idan ya gama kwanakin ya tafi shikenan, bana son daukar magana dan shi ba kunya magana yake ji ba, kinji dai na gaya miki." " In sha Allah." " Jeki." Tashi tayi ta bita da kallo ranta na tafasa, da gaske take kishi da ita dukda bata zauna da mahaifiyar ta ba, amma duk sanda ta kalle ta sai ta tuno abinda ya faru. ****A guje suka taso ganin ya fito, ya nufi wajen da jerin motocin ke fake suna jiran sa, ransa a bace yake da kiran amma bashi da ikon kin amsawa, dole ya ajiye shirin sa a gefe ya kirawo su domin ba zai taba yarda da shigar masa shirin sa ba. Shiyasa su kansu basu da yakini ko masaniyar komai, dan ya tabbatar da zasu taimaka wajen lalata masa shirin sa. Dan su din basu da ikon kansu sai abinda aka gindaya musu. Bud'e masa bayan motar daya daga ciki yayi, ya russuna kad'an sannan yace "We are very sorry sir!" Be tanka masa ba, ya shige cikin motar ya jingina bayan sa da kujerar ya lumshe idon sa. "Oga Main house zamu?" Yayi tambayar yana tada motar "Lamido Crescent!" Yace yana sake rufe idon sa. Chan suka wuce direct, suna isa ya fito ya shige ciki, tun daga falo ya fara wurgi da kayan jikin sa, ya rage daga shi sai boxer da farar singlet, kallon kansa yayi a jikin tangamemen mudubin dake tsaye kikam a falon, ya juya ya sake juyawa sannan ya wuce zuwa cikin bedroom din sa. Wanka ya fara yi a gurguje sannan ya fito ya shirya cikin shigar babbar riga da jamfa da wando farare kal, sau cikin sa ya jawo ya ajiye a gefe ya fara saka farar socks a ciki sannan ya saka ya fito rik'e da babbar rigar a hannu. Zama yayi sannan ya danna remote din kofar, da sauri suka shigo su biyu, ya mik'a wa daya babbar rigar, karba yayi ya taimaka masa ya saka sannan ya dauki abubuwan da yasan zai bukata ya fita dasu. "Ka zauna anan zan kiraka da zarar na sauka." Yace da dayan sannan ya tashi ya fice cikin takun da yafi kama dana jinin sarauta. Motoci biyu ne suka fita daga gidan, shi yana cikin daya su kuma suna bin sa a daya har zuwa airport. *Muhammad Ahmad Santuraki* *(*Captain Moh*)* *_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_* *ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA* *_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_* *GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi* *JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE* *_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_* *_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_* *_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_* *_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_* *_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_* *DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL* 2👉🏾400 3👉🏾500 4👉🏾700 5👉🏾1000 *Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin* 6019473875 MUSAA ABDULLAHI SAFIYA keystone bank Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 08184017082 *IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU* 09134848107 *_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽 #team zafafa biyar 1/2/22, 22:47 - Buhainat: *HALIN GIRMA* *_Hafsat Rano_* 4 **** *Adamawa-Yola* Tun daga yanayin manyan motocin da suka cika harabar ya tabbatar da bakin dake cike da fadar, yana da yakini dalilin kiran Bubun kenan a kalla zasu ganshi sannan ayi masa maganar da tafi komai kona masa rai, maganar mulki da yake dukkan kokarin sa wajen guje mata. Be jira an bud'e masa ba, ya balle murfin motar ya fito bayan hango Aji da yayi yana nufar ciki tare da tawagar sa, da saurin sa ya cimmusu,domin ya samu su shiga a tare, ko ya gujewa idanun Bubun daga zuwan nasa. Yasan a cike yake taf dashi "Aji!" Ya kira shi da sunan da yake kiran sa "Hoo d'an nema, na dauka ba zaka zo ba ai." " Na isa naki amsa kiran ka ko na Bubu? Ai ban isa ba." " Dadin baki, idan har da gaske ne ai sai ka amsa kiran da muka jima munayi maka ko?" Sosa keya yayi ba tare da yace komai ba, suka karasa ciki. Da ido Bubu ya kafe shi tun shigowar sa, tabbas ya rame fiye da ganin da yayi masa kwanaki da suka wuce, sannan akwai wani yanayi a tattare dashi da be gamsu ba, a gabansa ya tare, ya kwashi gaisuwa ya cigaba da bin sa da idon ba tare da shi ya yarda sun hada ido ba, gefen Ajin ya samu ya rabe yana sake hade fuskar sa tamau, murmushi kawai Bubu yayi ganin da gaske Muhammad yake har yau yana nan akan bakan sa, ya rasa dalilin da ya saka shi baya son mulki ko kad'an, tamkar ba dan naga da ba, kamar wanda aka juyawa tunani kwata kwata akai, gashi da gaske yake jin ya kamata ace ya huta, yakamata ya karbe shi kamar yadda ya karbi Aji a lokutan baya. Sai dai d'an nasa sam be shirya hakan ba, abinda yasa yake dada jan lokacin sosai, burin sa kawai yasa a gaba tun bayan shigar sa jami'ah, in da ya kwallafa rai akan aikin tsaro, ya kuma samu cikar burin sa duk da ba hakan ne ya kasanci burin sa ba shi. Kamal ne ya shigo wajen, ya gaida kowa cike da girmawawa sannan ya samu gefe ya zauna yana fuskantar Muhammad din, kallon juna suka yi ba tare da wata magana ba, murmushi kawai Kamal din ya sakar masa wanda ya kasa maida masa domin ya san ma'anar sa, be damu ba ko kad'an, da ace Bubu zai ji shawarar sa da ya jima da yiwa Kamal din abinda yake muradi, amma shima kemaimai yaki, ya kwallafa rai akan Muhammad din, ko me yasa? Oho. Ya dage kafadarsa alamun baya da bukatar ya sani ma dai. Duk batutuwan da aka tattauna a wajen be tsinci komai ba, zuciyar sa ta lula chan zuwa in da ya baro, tunanin halin da take ciki ko abinda take aikatawa kawai yake har kusan kowa ya gama ficewa ya zama na daga shi sai Aji, da Bubu. "Muhammadu." Yayi firgigit sai kuma ya hau sosai kai yana murmushi "Barka da rana Bubu." "Kalli shigar ka fa Muhammad, kalle ka? Hakan ya dace a matsayin ka da gidan nan? Haka kaga dan uwanka Kamal yayi shiga irin ta masarauta?" "Wallahi Bubu garin sauri ne, kuma gashi ba wani iya nada rawanin nan nayi ba wallahi, infact ciwon kai wallahi yake sani, amma za'a gyara ba za'a sake ba." Murmushi Aji yayi me dan sauti, ya kalle shi yana sake fadada fara'ar fuskar sa. "Ayi hakuri ranka ya dade munyi kuskure ba zamu sake ba." A duk sanda irin hakan ta faru Ajin ne ke yin uwa yayi makarbiya ya hana ayi masa fad'a, hakan yasa ba kasafai Bubun ke korafi gaban Ajin ba, sai ya tsuke bakin sa kawai be sake cewa komai ba. Tashi yayi, ya dan russuna a gaban mahaifin nasa "Zan shiga ciki Bubu!" "Ka same ni a shashe na bayan sallar magriba." " In sha Allah. A tashi lafiya." " Aji sai na shigo wajen yar tsohuwa ta." " Tana nan tana jiran ka da manshanun ta da yajin daddawa." Murmushi yayi, ya fice suka raka shi da ido. Yana fita Bubu yaja tsaki " Na rasa me yake damun yaron nan wallahi, ace yaro ya taso a cikin abu amma sam ya tsane shi? Wannan wanne irin abu ne?" " Mu cigaba da hakuri kawai Ahmadu, komai zai wuce ne." " Allah yasa, kowa jira na yake, mutanen gari da manyan mutane kowa ya zuba ido yaga me zanyi akai, ga Kamal da gaske yake son mulkin nan, gashi sam be chanchanta ba, na rasa yadda zan." "Shima ka barni dashi kawai, ayi masa abinda yake so din, yanzu dai a zaman da zakuyi sai kayi masa maganar auren muji, a kalla auren zai taimaka masa ya zauna a cikin mu, kaga dole ya koyi komai." " In sha Allah, idan ma bashi da yarinyar da tayi masa ni zan nemo masa." " Kul, Muhammad ba irin yaran da za'a yi musu haka bane, mu da muke son amfani da soyayyar shi ga yarinyar, abi dai komai a sannu." " Shikenan in sha Allah, Allah yasa mu dace." " Amin ya Allah." ***Bangaren Ammin sa ya wuce, yana tafe yana amsa gaisuwar da ya tsana, ayi ta gaida mutum kamar wata tsiya, hakan na daya daga cikin abinda yake hada shi da gidan su, ya gwammace yayi guduwar sa waje daya kawai ba tare da hayaniyar mutane ba. Tana zaune ta dora kafarta a saman dan tumtum din dake falon, kafar na damun ta sosai shiyasa ko yaushe zaka ganta a mike ana dan mammatsa ta. Yana tura kofar duk suka mike, har rige rigen gaishe shi suke kowa yasan yadda Ammin ke masifar ji da tilon dan nata, mace me kirki da sanin yakamata, shiyasa ta karbe kowa a gidan daga ma'aikata har dangi kowa nata ne, wajen Bubu ma Itace star,itace kuma uwar gidan sa dan dai Allah be bata yawan haihuwa bane. "Barka da zuwa yarima, sarki me jiran gado, uban mara uba me uban ma kaine gatan sa, shalelen Gimbiya da maimartaba, ka tsare gaba ka tsare baya, Allah ya kara maka daukaka da girma, Allah ya ida nufi.. sai..." Da sauri ya dakatar da ita, sai ta juya sum-sum-sum ta fice, ya kalli Ammi yayi mata murmushi kafin ya zauna a daidai saitun kafafun nata ya tankwashe kafafun sa "Ashe zaka zo." Tace masa tana murmushi itama " Na isa naki zuwa Ammi? Barka da gida mun same ku lafiya?" " Lafiya lau Alhamdulillah , shiru daga cewa zaka je wani aiki Kano shikenan kamar an aiki bawa garin su, su ba labarin su da suka bika kaima ba labari, gidanka da kake sauka ma an ce min ba chan ka sauka ba." " Wani babban aiki ne ai Ammi, ki tayani da addu'a kawai in sha Allah zakuji labari me dadi." " Allah yasa toh, ya aikin naku?" " Alhamdulillah wallahi, muna ta fama, ba dadi amma haka dai za'a cigaba da lallabawa." " Tunda kana so ba." Tace. Dariya ya saka kawai be ce komai ba. Ya dan jima a tare da Ammin tasa kafin ya tashi ya yi mata sallama zuwa shashen shi, da yake kusa da na Bubu. Yana shiga ya tarar da kayan abinci a jere a falon nasa, sai kamshin turaren wuta dake fita ta cikin yar karamar burner din dake makale a jikin wani dan karfe. Wuce komai yayi zuwa bedroom dinsa, ya kwanta rigingine a saman gadon ya jawo woyoyin sa, ya shiga cikin contact dinsa, number farko da yayi saving dinta da emoji din heart da padlock ya danna kira ya kwanta sosai yana lumshe idanun sa lokacin da ta soma ringing... ****Da safe ta tashi kamar kullum tayi duk abinda tasan wajibin ta ne, har zuwa sanda rana ta fito sosai, kayan ta na wanki dana Marwan ta hada ta zagaya baya ta hau wanke su, daga gefe ta ajiye wayarta tana jin karatun alkur'ani me girma, tana wankin tana bi har ta gama tsaf, ta tattare su ta shanya sannan ta dawo ciki ta chanja kayan ta, ta fice zuwa shashen Gaji. Fitar ta kenan Khalil ya shigo, maigadi na bin sa janye da katotuwar trolly din sa a baya. Da Habib suka ci karo yana kokarin fita, ya bashi hannu suka chapke cike da murnar ganin juna "Welcome welcome." Yace masa yana juyawa suka shiga ciki. Da sauri Mama ta fito jin hayaniyar su.. "Wa nake ji kamar Khalil, inyee lallai yaron nan Ashe dai da gaske kake." "Gani dai, ai dama na gama shirin zuwa kawai ban sanar dake bane sai jiyan." "Maraba lalle da manyan yan jarida." Zama yayi a cikin kujerun falon, itama maman ta zauna tana gyara dan kwalin kanta. "Wai dama kinsan zaizo Mah?" "Nima sai jiya na sani, na zata kuma halin nasa ne Ashe da gaske yake shiyasa ma ban fad'a ma kowa ba." "Ina wuni Anty?" " Lafiya lou Khalil, yaso Hajiya da kowa da kowa?" " Duk suna nan lafiya, itama tayi mamaki da nace zanzo, gashi kuma zan dade sosai dan aiki ne ya kawo ni." " Ahaap ko da naji, Ashe zuwan dai da dalili, jairi dama nasan akwai abinda ya kawo ka." " Abubuwa dai Anty, karki manta da wannan maganar tamu hadda ita ma." Tsaki taja ta harare shi " Zaka fara ko?" " Nayi shiru." Yace yana dora hannun sa baki " Yafi maka dai." " Ina su Zeenat ne? Banji duriyar su ba." " Zaka ji su ne ai ba dai kananan ba, ka tashi ku shiga ciki ka huta kaci abinci, sannu da zuwa." Tashi yayi, yabi bayan Habeeb suka wuce dakin sa suna hirar yaushe gamo, idanun sa da kunnuwan sa na jiran yaji ta inda zasu bullo, he can't wait to see her beautiful face, ko me Anty zatayi masa kuwa ba zai fasa bawa zuciyar sa abinda ta dade tana so ba. Kishin ta daban soyayyar sa daban. Period! ****Zaman ta a bangaren Gajin yafi komai yi mata dadi, abu daya ne kawai yake dan takura ta yawan maganar Gajin, duk da haka take daurewa tana amsa mata, gashi ta manta wayar ta a kitchen bayan ta gama wankin nan, gashi taji alamar Khalil din yazo ta tabbata idan taje dauka zasu iya haduwa, ta kuma san me hakan ke nufi a wajen Mama. Zaman ta ta cigaba kawai har sanda taji ana kiran sallar, alwala tayi ta zauna ta jira a tayar, tana jin sanda za'a tada sallar ta fita zuwa bangaren nasu, lokacin tasan sun tafi sallah Maman ma kuma ta shiga ciki tayi sallar itama, ta baya ta bi, ta shiga kitchen din a daidai lokacin da ya saka wayar a kunnen sa "Waye?" Yace yana gyara rikon da yayi wa kofin hannun sa, tashi zaune Moha yayi da sauri, ya kalli screen din wayar ko be kira number daidai ba? Kai Anya? Daidai yadda ta fad'a masa ne "Fatima nake nema, ko tana kusa?" Yace jin me maganar ya sake tambayar waye a karo na biyu. "Fatima? Malam Waye kai din da kake neman ta?" "Sanin waye ni ba zai taba maka dadi ba, idan tana kusa ka bata zanyi magana da ita." " Ba zan bata ba, abun yar karfi ne kazo ka karba idan kana dashi, mtsw.". Yaja dogon tsaki hade da kashe wayar, kafar ta ta sako a kitchen din zata shigo domin ta karbi wayar ta da ya daga mata ba tare da izinin ta ba, muryar Mama ta dakatar da ita, ta juya da sauri ta bar kitchen din. " Kai kuma me kake anan kana jin an tada sallah?" "Ruwa nazo sha." Yace yana juyawa ya bar kitchen din, kofar bayan ta leka ta tabbatar babu komai a wajen, tayi kwafa ta juya bayan ta jawo kofar ta ciki. Wani irin tashin hankali ne ya ziyarce shi, ya tashi da sauri yana jawo dayar wayar tasa, cikin kankanin lokaci ya birkice ya koma Captain Moh din sa na ainihi, a yau ba sai gobe ba zai juya, dan ba zai taba daukar rainin hankali ba, ba dan ganin da zai wa Bubu ba, da babu abinda zai hanashi daukar hanya a yanzu, amma dole ya hakura zuwa lokacin da ya dauka masa duk da yana ganin yayi masa masifar nisa. Kaiwa da komowa ya dinga yi a tsakanin dakin, zuciyar sa tamkar zata hudo daga kirjin sa saboda tsabar kishi. _WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_* *ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA* *_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_* *GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi* *JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE* *_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_* *_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_* *_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_* *_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_* *_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_* *DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL* 2👉🏾400 3👉🏾500 4👉🏾700 5👉🏾1000 *Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin* 6019473875 MUSAA ABDULLAHI SAFIYA keystone bank Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 08184017082 *IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU* 09134848107 *_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽 #team zafafa biyar **** 1/2/22, 22:47 - Buhainat: *HALIN GIRMA* *_Hafsat Rano_*       *5* *_Last free page!_* **** Tana zaune ta idar da sallah, bata tashi daga kan abun sallar ba taji shigowar sa shashen Gajin, gabanta taji ya fadi, tayi kamar bata ji sallamar da yayi ba, tayi tsam a kan sallayar tana kallon gabanta. Da kallo ya bi bayan ta ya samu waje ya zauna a cikin kujerun falon yana kokarin daidaita yanayin da yake ciki. Gajin ce ta fito, "Wa nake gani kamar Ibrahim?" "Nine nan wallahi Hajiya." "Lale marhabin, barka da zuwa. Saukar yaushe?" "Dazu na shigo, mun same ku lafiya?" "Lafiya lou wallahi, yasu Hajiyan da yan uwanka?" "Kowa lafiya suna gaida ku." "Muna amsawa, sannu da zuwa." " Yawwa." Yace yana yawo da idon sa akan ta, " Iman ba magana?" Yace yana son Gajin ta tanka "Kaji sokonci, wai bata gaishe ka ba?" Tayi maganar da sauri "Ina wuni?" Tace a gajarce " Lafiya lou, kina lafiya?" Shiru tayi bata amsa ba, Gaji ta hau sababi tana mata fad'a, tashi yayi hannun sa cikin aljihu ya zaro wayar ta "Gashi na tsince ta a kitchen." Ya mik'a mata sannan yayi wa Gajin sallama ya fice yana raya ta yadda zai bulowa Iman din, ya gama gane yanayin ta ba irin nasa bane, shirun ta yayi yawa amma duk da haka shi ba damuwar sa bace, yadda ya shiga zuciyar kowa a gidan nan da hakan zaiyi amfani ya kafa kansa, ba zai wani ja lokaci ba zai gabatarwa Gaji da kansa, baya jin ma zai wuce gobe, zai sai fara tuntubar Yaya Hajara idan yaga ba ta goyi bayansa ba zai yi gaban kansa, iya ka tayi masa fad'a shikenan ya wuce.  Be koma shashen ba, sai ya fice daga gidan a kafa yana adana number da ya dauka a wayar ta ta, so yake ya saka number a truecaller yaga ko zai samu wani information akai.    Cikin call log dinta ta shiga ta duba amma bata ga number da aka kirata ba, taji babu dadi dan bata so yaga kamar tana sane ta bayar aka daga wayar tasa. Ko da tafiyar su ba zatayi daya ba, ba zata so yaji a ransa dan yana lacking wani abu bane shiyasa hakan ta faru. Kwantar da kanta tayi a saman hannun kujerar ta rufe idon ta tana tariyo zuwan da yayi wajenta, akwai wani abu me girma a muryar sa sai kuma abu daya da ya tsaya mata shine kamshin turaren da taji yana yi, wanda yayi kama da me tsada ne irin ajin farko, domin Allah ya hore mata kaunar kamshi, shiyasa ta kan yi saurin ganewa. Sai dai akwai irin tuurare yan durin nan da suke da kamshi me dadi har ka kasa tantance su, kila irin su ne, abunda ya kara burgeta dashi kenan, duk da yana cikin yanayin da zaka ce kai tsaye babu, amma be bar kansa a wulakance ba. Juya kanta tayi daya gefen ta dora wayar a saman cinyarta ta cigaba da tunani. ***Kiran sallar magriba ya sashi fita daga sashen nasa zuwa masallaci, achan yayi alwala ya shiga sahun farko sukayi sallar. Bubu na ganin shi yaji dadi sosai. Bayan an idar ya wuce bangaren nasa domin ya jira shi, yana zaune sai gashi ko ya shigo, ya tashi tsaye har sai da ya zauna sannan ya zauna shima a k'asa cikin girmamawa ya sake gaishe shi, ya amsa masa sake yana nazarin sa. "Muhammadu!" Ya kira sunan sa, gyara zaman sa yayi ya tattara hankalin sa waje daya cikin son ganin be yi wani abu a gaban Bubun ba "Kana ji na Muhammad?" "Inaji Bubu." "Madallah, Muhammad ka san dai a tsarin gidan nan kana cikin lokacin da ya kamata ace ka ajiye iyalin ka kaima, ka nutsu waje daya a kalla hakan zai taimaka maka wajen cikar kamalarka." Kansa a kasa yana jin Bubun yayi ta bayani yana gida kansa cike da gamsuwa, **A kofar ta tsaya tana kallon takalmin Muhammad din dake zube a wajen, ta samu labarin zuwan sa a wajen Kamal amma bata tsammaci irin wannan ganawar da Maimartaba ba, shiyasa ta kasa hakuri tazo ta nemi iso wajen Maimartaba din wajen sarkin kofa amma sai ya nuna mata ba zai yiwu ba, domin an gargade shi akan barin kowa ya shiga shashen maimartaba din har sai ya kammala ganawar sa da Muhammad din, ranta a matukar bace ta koma sashen ta tana jin wani irin tashin hankali, tana tsoron kar Muhammad din ya amsa tayin mahaifin nasa a wannan zaman da zasuyi. Safa da Marwa tayi tayi, har wajen sallar isha basu fito ba, tana hangen bangaren ta cikin nata shashen, ta kasa zama tana da yakinin ko menene suke tattaunawa haka me muhimmanci ne sosai. Tana tsaye jikin window taga fitowar su, fuskar Muhammad din a sake yana takewa mahaifin nasa baya. Tsaki taja ta saki labulen tana juyawa zuwa gefen gadon ta, ta zauna tana sake jan wani tsakin, tsakin haushin Muhammad din da ya zame mata ciwon ido shi da mahaifiyar sa. "Ranki ya dade, Maimartaba ya aiko yana da bukatar ganin ki bayan ya dawo sallar isha'i." Bata amsa ba, sai ma juya fuskar ta da tayi wani sashen tana sake sakin siririn tsaki. ***Bangaren sa ya koma, ya tattaro abunda ya san zai bukata ya fito, sai kuma ya tuna da maganar Maimartaba ta karshe da suka tattauna, yana son ganin sa da safe kafin ya fito fad'a, komawa yayi ba dan yaso ba, ya ajiye komai ya zauna yana kirga lokacin zuwa wayewar gari. Nisan yayi yawan da yake jin kamar yayi loosing idan har ya kyale shi tsawon wannan lokacin. Wayar sa dake ajiye a gefen sa ta dauki sowwa, ya daga ganin kiran da yake ta jira ne tun dazu, "Oga na duba maka number din, akwai bayanan sa da komai har da wajen aikin sa, hoton sa da kuma location dinsa a yanxu, na tura maka ta mail sai ka duba." "Ok! Thank you, zan neme ka. " Ya katse kiran ya shiga mail dinsa, ya hau kan message din ya bud'e. Hoton sa ya bud'e yayi zooming sosai, sai kuma ya fita ya karanta information din. Karamin tsaki yaja ya ajiye wayar yana jin a ransa wannan din karamin kwaro ne be kamata ya hana shi walwalar sa ba, abu daya zai masa ya kama shi a hannun sa, sai dai ba zai hakan ba har sai ya je ya tabbatar da zargin sa. ***Anan sashen Gajin ta shirya, ta wuce islamiyya tana tafe tana satar kallon hanyar ko zata ganshi tunda yace mata yana zama ne domin yaga wucewar ta, har ta isa makarantar bata ga ko me kama dashi ba, sai kawai ta share tayi abinda ya kaita. A dawowa ma haka ta sake yi shima bata ga kowa ba, ta dawo gida ta chanja kayan ta kenan aka shigo aka ce tazo inji Muhammad, Hijab ta dora a saman kayan jikinta ta fito. A tsaye yau ma ta hange shi wajen kujerar, ya rataye hannayen sa a bayan sa yana tsaye kyam akan kafafun sa. "Assalamu alaikum." Tayi masa sallama tana jan kujerar. "Sannu da zuwa, nan akwai rana bari na saka maka a chan." Taja kujerar zuwa k'asan wata yar bishiya ta ajiye, " Bismillah." Tace masa tana nuna masa kujerar, be zauna ba, ya zaro hannun sa daga bayan sa, ya dawo dasu gaba ya rungume su a kirjin sa, " Bismillah." Ya nuna mata kujerar da baki " Zauna babu matsala." Yace mata " A ah dan Allah ka zauna, be kamata na zauna kana tsaye ba, ance bakon ka..." " Kyale fadar hausawan nan, zauna dan Allah." Allah da taji ya ambata yasa ta zauna a kunyace, ya zura mata ido har sai da ta dan ji wani iri. " Na cika kallo ko? Kiyi hakuri." Yace mata yana murmushi,kallon ta kadai yayi jin sa yake kamar yafi kowa sa'a a duniya " Ba komai." Tace tana gyara wayar hannun ta " Ina wuni?" Ta gaishe shi yana dan zamowa " Lafiya lou, sai kika jini shiru, tafiya nayi zuwa kauye Baba ya kira ni, naso ma na zo kafin na wuce toh tafiyar ce tazo a gaggauce, sauka ta kenan ma." " Allah sarki... Allah yasa lafiya." " Lafiya lou, sai godiya. " " Ka baro su lafiya?" " Alhamdulillah. Nagode da kulawa." " Ba komai." Tace tana wasa da hannun ta. Turo gate din akayi, Habeeb na gaba yana bin sa a baya, wani irin daukewa yaji ganin sa na neman yi. Iman zaune tare da wani suna hira, a cikin gidan kuma? Be san sanda ya isa wajen ba, sai ganin mutum sukayi a gaban su. Wani kallo Moh yayi masa, yayi murmushi yana taune gefen lips dinsa na kasa "Yaya sannu da zuwa." Yace yana mika masa hannu, kin bashi hannu Khalil yayi, sai Habeeb ne suka gaisa, ya daki kafadar Khalil din " Muje ko?" " Yi gaba ina zuwa." Yace masa, "Ok." Ya wuce ya bar Khalil din a tsaye " Iman shiga gida." Yace a gadarance, ta dago ta kalle shi da sauri, ya hade girar sama data k'asa tamau irin ba wasa din nan. "My heart, ki shiga gida ki huta dama naji ba zan iya zuwa gida ban zo na ganki ba, shiyasa na taho nan kai tsaye, zan kira ki anjima ki ajiye waya a kusa dake kinji?" Kunya ce ta kamata ta noke, ta mike da k'yar tace "Ka gaida gida." Sannan ta wuce ciki, tana barin wajen ya hade fuskar sa sosai. " Da tsakar ranar nan ka taso yarinya, kazo zaka ishe ta da uban surutu, ku dama talakawa haka kuke, da kunga yar hanya sai kuzo kuce kuna so, kai kanka kasan ba sa'ar ka bace, ba sa'ar auren ka bace shishigi dai, toh ita din matata ce, ni zan aureta an gama magana, sai kaja tsumman kafafunka a koma in da aka fito, ka samu daidai da kai." " Zaka ga tasirin talaka da talauci kuwa, baka da ikon tsarawa kowa rayuwa, haka arziki ba wani abu bane face fitina, wadatar zuciya itace mutum..." Ya dan matso gaban sa " Mark my word, a gaban idon ka, right under your noses, talaka zai baka mamaki, mamakiin da har ka kare rayuwar ka zaka fita daga cikin sa ba, count down dinka ya fara daga yanzu." " 1,2,3!" Sai na jika. Ya juya ya fice daga gidan cikin takun da ya tsayawa Khalil a rai, cikin wani irin yanayi yayi cikin gidan yana jin yanzu ba sai anjima ba, zai yi abinda ya dace, gida be koshi ba, babu yadda za'a yi a bawa dawa. **A tsaye ya tarar da Habib yana ganin shi yace "Kaiko me ka tsaya yi ina ta jiran ka." "Abinda ka kasa yi, kana ganin kanwar ka da mutum a tsaye, kana ganin sa kaga mara gaskiya, wa ya sani ma ko dan boko haram ne da wannan uban kasumbar, amma baka damu ba kayi tafiyar ka, hakan ba daidai bane." Kallon sa Habib yayi, mamaki na kamashi, " Yaushe hakan ya zama ba daidai ba khalil?" " Habib, maganar gaskiya ina son Iman, son da ni kaina bansan adadin sa ba, zan iya komai akan na sameta, dan haka ba zan iya jure ganin ta da kowa ba, musamman mutum irin wannan da ya nuna alamun rashin gaskiya, gashi fakiri jibi shigar jikin sa, no ba zan iya ba, rakani wajen Gaji ayita ta kare." " Idan har kai din jinina ne, idan har na isa da kai babu kai babu Iman Khalil, na rasa kafiya irin taka, na rasa dagiya irin taka, bayan maganar nan mun dade da gama ta, na gaya maka ba zai taba yiwuwa ba." " Akan me? Dan Allah Anty ki gaya min hujja me karfi a musulunci da ya haramta min auren ta, na daya ni ba muharraminta bane tunda ita din ba ke kika haife ta ba, toh sai menene? Akan dalili mara tushe?" " Akan duk abinda zaka kira shi Khalil ka kirashi, amma idan har ina numfashi ba zamu hada jini ba wallahi, ga mata nan bila adadin, me yasa sai ita, wannan da yazo shi ya dace da ita, shine daidai da matsayin ta, inaso auren da zatayi ya zama sakayyar aure min miji da uwarta tayi, ta saka yayana samun yan Uba!." " Ohh shit! Kin kasa fuskanta ta Anty, kiyi hakuri wannan karon zabin raina zan bi, zanje na samu Gaji na sanar da ita, gwara kowa ya sani a san me yakamata ayi." " Khalil!" Ta k'wala masa kira, ya juya da sauri yayi hanyar fita, wayar sa tayi kara, ya tsaya chak jin layin da yake ajiye numbers din manyan mutanen sa ne, ciro wayar yayi sunan Sir ya bayyana a wayar, ya daga da sauri yana daidaita numfashin sa " Kana ji Ibrahim? Sako ne daga sama ba daga ni bane, an dakatar da kai aiki zuwa wani lokaci, za'a neme ka idan bukatar hakan ta taso." Be jira yace komai ba , ya katse kiran. Da sauri ya dafe bangon da yake kusa dan ji yayi jiri na neman kadashi, gaba daya rayuwar sa akan aikin ta dogara, yana da passion sosai a Kai sannan yana iyakar kokarin sa wajen aikin sa, maganar promotion dinsa ma ake idan har ya kammala wannan assignment din da ya kawo shi Kano, shikenan sai dakatarwa haka nan ba wani dalili? " Ya akayi?! Habib ya matso ya taba shi ganin kamar ya shiga coma 🔥🔥🔥🔥🔥 *_LAST BONANZA_* *_farincinku shine namu,ZAFAFAN DAI,sun sake amsa kokenku,sun sake rage muku kaso 20 cikin 100_* *_Daga yau 29 ga wata,har zuwa 31 ga watan nan,xaku iya biyan 800 a amadadin 1000 na kudin litattafai biyar_* *_za'a fara posting in sha Allah 1st January da yardar Allah_* *HANZARTA KI BIYA NAKI KAFIN RANAKUN SU QARE* *XAKI BIYA TA WANNAN ACCOUNT NUMBER DIN* 6019473875 MUSAA ABDULLAHI SAFIYA SAIKU TURA SHAIDAR BIYA 08184017082 GA MASU TURA KATIN WAYA KO KUMA VTU,SAIKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYANKU 09134848107 1/2/22, 22:47 - Buhainat: *HALIN GIRMA*   6 *Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107*  _ASSALAMU ALAIKUM BEAUTIFUL PEOPLE!! ZAFAFA BIYAR FAMILY💯💯🙌🏽❤️_ _MUNGODE DA ZABIN LITTAFAN ZAFAFA BIYAR. ALLAH YA KARA BUDI YA KUMA BAR ZUMUNCI_ _KAMAR KO DA YAUSHE, WANNAN KARON MA MUNZO DA KOKON BARAR YOUTUBE CHANNEL DIN YARON MU, SUDEIS MASOYI KUMA MAKARANCI, MAHADDACIN ALKUR’ANI MA GIRMA_ _WANNAN KARON MA DAN ALLAH A TEMAKA ADANNA WA CHANNEL DINSA KARARRWA DOMIN KASANCEWA DA MU A DUK SANDA MUKA DORA FEFAN BIDIYON SA, A TALLAFA A KALLA A KUMA DANNA MASA SUBSCRIPTION. HAKAN NA KARAWA SUDEIS KWARIN GWIWAR SAKE DAGEWA YA KUMA KARA KAIMI WAJEN YIN KARATUN SOSAI. MUNGODE KWARAI💯🙌🏽❤️_ _GA CHANNEL DIN DAKE YOUTUBE NAN👇🏾_ https://youtube.com/c/sudaiskura _Sudais is a young boy who has passion in recitation of the Holy Qur'an at a very young age._ _Please help him grow his YouTube channel by subscribing and liking his videos to encourage the little boy. Jazakumullahu khairan🙏🏻_ *** Girgiza kai ya hau yi da sauri da sauri. "Habib aiki na, innalillah wa inna ilaihi rajiun." "Me ya samu aikin naka?" Mama ta matso da sauri tana rik'e shi "Wai sun dakatar dani, babu wani kwakkwaran bayani kawai wai daga sama ne." "Innalillah wa inna ilaihi rajiun, zo ka zauna, rik'e shi Habib ya zauna." Zaunar dashi Habib yayi, yayi saurin dauko masa ruwa ya mik'a masa "Sha ko zaka ji sauki a zuciyar ka, ba wani abu bane babba in sha Allah, wata yar matsala ce zasu gyara da yardar Allah." Jujjuya kansa yake ya kasa magana, shi kadai yasan hakan me yake nufi, shi kadai yasan yadda yake ji a halin yanzu, tabbas idan suka hana mishi aikin nan sun yi masifar cutar sa, akan me? Me yayi haka da ya chanchanci wannan hukuncin? Bayan irin kokarin da yake ganin ya rik'e aikin sa, tsawon lokacin da ya dauka kafin ya samu aikin, da irin wahalar da yasha kafin ya kawo matsayin da yake, sai yanzu? Daga sama ta ka kawai ace an dakatar dashi? Innalillah wa inna ilaihi rajiun. Ya sake maimaitawa. "Kalle ni nan Khalil, karka ce zaka daga hankalin ka akan abinda kasan baka da iko dashi, kayi hakuri ka kwantar da hankalin ka, in sha Allah ba wata matsala bace, kaji?" Gid'a mata kai yayi kamar karamin yaro, ya kwantar da kansa yana jin kamar ya zubar da hawaye saboda bacin rai. Shiru sukayi kowa yana jimamin abinda ya faru, ya ma manta da abinda yake shirin aikatawa. Shigowa Zeenat tayi dauke da wasu manyan ledoji,uwar ta bita da kallo bata ce komai ba. "Daga ina kike?" Habib yace yana bin hannun ta da kallo "Bashir ne yazo." Kallon Mama yayi, yaga ta dauke kanta "Mama fa Bashir din nan naji wasu maganganu akan sa marasa dadi, ya kamata a duba sosai kafin a barta tana fita wajen sa." "Bana son maganar nan yanzu, dame zamu ji? Da abinda ya faru da Khalil din ko da naka zancen?" Tsuke bakin sa yayi be sake cewa komai ba, ya tashi ya bar falon ma, "Me ya samu Uncle Khaly din Mama?" "Babu komai, ki wuce ki bani waje uwar yan magana." Da sauri tayi gaba da ledojin ta, ta shige dakin uwar ta rakata da kallo kafin ta sauke ajiyar zuciya tana tuna abinda ya faru daren jiya ita da Abban su. *** "Ya ake ciki da yaran nan?" "Name fa?" "Akan maganar yaran da suke zuwa wajen su, Yaya yayi min magana akai yace ya kamata asan abinda ake ciki, kindai san tsarin gidan nan ba'a wani daukar dogon lokaci ana zance." "Eh toh, ita Iman akwai wani wanda yazo." "Zuwan sa biyu kamar ko?" "Ashe ka sani?" "Eh ina sane da komai ai, kinga alamun zasu dai-dai ta ne? Naga zuwan nasa biyu dududu." "Toh idan bashi ba waye? Babu kowa ai." "Khalil din fa?" Yace yana mata kallon mamaki "Wai Dr bar maganar Khalil din nan, ba da gaske yake ba wallahi." "Ana wasa a maganar aure ne Hajara?" "Shi dai yayi, gwara a tsayar da magana akan wanda yazo din dan da alama ba da wasa yazo ba." "Toh shikenan, Zeenatu fa?" "Eh ita ai Bashir ne dama." Tashi yayi tsaye yana girgiza kansa "Ban yarda ba sam, ban amince da yaron ba, binciken da nayi akansa be min dadi ba, kamar ance min ma kuma yana da mata duk da hakan ba zai hana a bashi aure ba, sai dai na samu labarin bashi da hali me kyau gaskiya, a wani labarin ma ance min har zaman prison yayi, sai ki fad'a mata nace banda Bashir ta kawo wani." Hankalin ta a tashe tace " Amma baka ganin sharri akayi masa? Don a hana a bashi?" " Akan me za'a masa sharri? Akan wanne dalili kenan?" Ya tsare ta da idanun sa, sunkuyar da kanta tayi bata ce komai ba, tsoron yadda za'a kwashe da Zeenat din take domin ta san yadda ta saka Bashir din a ranta, gashi babu laifi yana mata hidima sosai, hakan ya saka Maman sake yarda dashi da yar ta ta. "Bari na shiga ciki Anty." Khalil yace yana mikewa, ta daga masa kai kawai ya wuce ya barta tana cigaba da tunanin yadda zata bullowa al'amuran. ***Tana zaune a falon Gajin tana tunanin abinda ya faru tsakanin shi da Uncle Khalil, wayarta dake saman cinyarta tayi kara, ta kalli wayar ganin bakuwar number ya saka ta tashi, ta wuce zuwa bedroom din Gajin ta daga tana zama a gefen gadon ta "Assalamu alaikum." Tayi sallama cikin muryarta da tafi komai tafiya dashi, lumshe idon sa yayi ya bud'e a hankali ya amsa sallamar ta ta "Wa alaikisalam..." "Ina wuni?" Ta gaishe shi jin muryar sa "Lafiya lou Mi Love, na barki lafiya?" "Alhamdulillah." Tace a kunyace ganin shi kai tsaye yake maganar sa. " Kina jina Zahraaah na? " " Na'am?" Tace tana mike kafafunta " A zahirin gaskiya ba da wasa nazo ba, da gaske nazo neman auren ki ba kuma naso a dauki wani dogon lokaci in sha Allah, ni din dai ba wani bane kin dai ganni, bawan Allah ne me neman amincewar Fatima Zahra, ina fatan zaki bani dama dan Allah!" " Hmm..." Ta sauke ajiyar zuciya maganganun sa na taba ta, me zata ce toh? Da gaske take jin ya kwanta mata duk da taga alamun ba wani shi nne dashi ba, amma sai taji yadda yake abu kai tsaye ya birgeta sosai, babu karya straight kawai yake maganar sa, bayan haka da gaske take son matsawa daga wajen Mama, ko ba komai ta samu yanci itama. "Baki ce komai ba?" "Allah ya shige mana gaba, Allah ya zaba mana abinda zai zamar mana alkhairi gaba daya." Wani irin dadi yaji ya shige shi, ya rufe idon sa, ya dau yan sakanni yana jin sonta na sake ruruwa a zuciyar ta, yana tuna tsawon lokacin da ya dauka yana dakon soyayyar ta, a lokacin da shi kansa be san me ake nufi da so din ba.   Mahaifiyar sa 'ya ce ga sarkin Kano kuma shi jika ne a gidan, hakan ya saka yake da alaka me karfi da garin na Kano duk da mahaifin sa da mahaifar sa Adamawa-Yola ne, rayuwar sa bayan ya tasa yayi ta ne tsakanin Kano da Adamawa, shiyasa babu in da be sanin a Kanon ba, yake kuma jin kamar yafi zama comfortably a Kanon, musamman da bashi da son hayaniya sosai sai nan din yafi zamar masa peaceful wajen hutawar sa.    Akwai ranar da ya fito shi da abokin sa Musaddik, suna tafe a mota hanya ta biyo dasu ta area din su Fatima, a lokacin ya ganta duk da lokacin ba ta kai yanzu ba, be kuma taba jin abinda yaji akanta, shiyasa ya nace a lokacin suka yi ta bin ta har suka ga gidansu, suka kuma yi tambaya akan ta da komai. A lokacin yaso ya shigo da karfin sa, sai dai wani labari da ya samu ya sauya masa tunani da shawara, ya kuma yanke ma kansa shawarar da yake ganin itace zata daga masa darajar ta, a ranar da gaskiya ta bayyana.   Musaddik be aminta da shawarar ba duba da gidajen da Muhammad din ya fito, amma haka ya kafe akan bakansa, shiyasa ma kawai Musaddik din ya kyale shi amma fa kullum cikin masa korafi yake.    Bangaren aikin sa zai iya cewa yana cikin yan gata da sai abinda suka zaba da inda suka zaba zasu zauna, kasancewar gaba daya k'asar babu in da kakan shi mahaifin Ammi zai nemi alfarma ba'a masa ba, sannan gefe guda mahaifin sa yayi sunan da zaka yi mamaki sosai.   Duk da hakan be daina aikin sa ba, sai dai babu wani matsi ko takura tun ma be kai matakin captain ba, balle yanzu da yake da rank me girma. "Kinsan me?" Yace yana gyara kwanciyar sa sosai, sanda Musaddik ya murda handle din dakin ya shigo bayan yayi knocking ya bashi izinin shigowa. "Ya Iman Abba na kira." Marwan ya fad'a mata yana tsaye a gefen ta, hannun sa ta riko shi kuma yace "Yaya Iman ki gaida min da Abba, idan kin dawo ki kira ni please, zan fad'a miki wani abu." Murmushi tayi me sauti yana jiyo ta "Ok bye." Ta ajiye wayar ta rik'e hannun Marwan din suka fito a tare.. "Yaushe Abban ya dawo?" "Be dade ba, yana falo yana cin abinci." "Owk." Tace suna karasawa. " Abba barka da gida." " Barka da Uwata, na dawo ban ganki ba, da zan fita ma ban ganki ba, shiyasa nace ya kira min ke." " Ina wajen Gaji Abba." " Eh haka maman ku tace, amma ai na ganki dai ko?" K'asa tayi da kanta Mama ta karbe " Tafi son zaman chan yanzu ai." " Kuna shan hira da Gaji kenan ko?" Yace yana murmushi " Ko kuma tafi jin dadin tayi wayarta a chan ba, ko 'yata?" Maman tace cikin son a sako zancen Moh, shiru kawai Iman tayi Abba ma ya girgiza kansa kawai "Allah ya kyauta, kinci abinci dai ko? Nasan ki da wasa da cikin ki." " Naci Abba." " Toh karbi nawa ki kara, nasan ba da wani yawa kika ci ba." Ya tura mata plate din gabanta "Maza kirawo min zeenatu Marwan." Gaban Mama ne ya fadi, ta zamo daga kujerar tana sakin salati a ranta. Tana gyara daurin dankwalin kanta ta shigo falon, ta zauna a kusa da Iman ta gaida Abban. "Abinda yasa na kiraku ke da yar uwarki, akan maganar yaran da suke zuwa wajen ku ne, duk da shi wanda yake zuwa wajen Uwata bansan shi ba, inaso ki sanar dashi yazo yaga Yaya kafin ya cigaba da zuwa." Abincin da ta diba ta hadiye da k'yar gabanta na dukan uku uku. "Ke kuma..." Ya nuna Zeenat "Ki kawo wani daban ba yaron nan Bashir ba, ki sake dubawa a cikin sauran ki nemo wanda ya dace da nasabar gidan nan, me Halin Girma mutumin kirki, kinji na fad'a miki." Waro ido tayi cikin tashin hankali ta kalli Abban " Hakan shine abunda ya kamata muyi a matsayin mu na iyaye, dan haka kiyi hakuri." Tashi yayi, ya kalli Iman da tayi tsam a wajen, ya juya ya kalli Mama yayi mata alama da ido sannan yace " Na fita!" Da k'yar Mama ta bud'e baki tace " Adawo lafiya." " Allah ya kiyaye Abba." Iman tace yana kokarin fita " Amin." Ya amsa kafin ya fice gaba daya. Wani kallo Mama tayi mata, tayi kwafa ta mike sannan ta kalli Zeenat da ta soma kuka wiwi tace " Ki same ni a daki." Kamar wadda zata fadi saboda kuka haka ta tashi, ta kusan fadowa Iman din aka, a ranta tana jin babu abinda zai hana ta auren Bashir, duk tashin hankalin da za'a yi sai dai ayi shi, amma babu wanda zai hanata abinda zuciyar ta take so. ***Cikin wani yanayi bayan ya gama jin komai ya gaida Abban da ya fito, yayi masa adawo lafiya sannan ya juya zuwa wata hanyar ya fasa shiga dakin. Idan har abinda yaji gaskiya ne, wannan me zubin yan boko haram din aka bawa damar turowa kenan, ba zai taba yarda yayi biyu babu ba, ba aiki ba Iman, shi zai fara isa wajen Yayan idan yaso ayi wacce za'a yi, yasan ba zasu taba hanashi ba, domin shi ya chanchanta ba wani bare ba, da ba'a san daga ina yazo ba. *** Tashi zaune yayi zaune bayan ya ajiye wayar, ya kalli Musaddik da ya zauna a gefen sa "Ya akayi ne?" "Na shigo kana ta waya" "Eh wallahi, ni da Wifey ne." "Wifey kuma? Yaushe kayi aure ba labari?" "Bana son iskanci, kasan wa nake nufi ai." "Toh ai sai kace aljanar ka da ka nacewa, amma kace wifey bayan bamu shafa fatiha ba." Jefa masa dan pillow din da yake kusa dashi yayi "Dan iska, ka jira ka gani ai." "Wai karo maka yaran ka akayi ne? Naga gate din naka ya sake cika ga wani uban iyayi kamar basu san mutum ba?" "Sai hakuri kawai, ya ake ciki ne?" "Normal, shiru ne ko ina, ya ka baro su Ammi?" "Lafiya lou wallahi, Bubu yayi min maganar aure ai, nace zan zo musu da magana in less than a month, kafin nan mun gama daidaitawa da Wifey." " Ya zakayi toh idan aka ce ka turo?" " Shine matsalar wallahi, amma zan san yadda zan dai." " Toh Allah ya sa muji alkhairi angon Fatima." " In Sha Allah." Yace yana dafe saitin heart dinsa, dai-dai lokacin kiran ta ya shigo wayar, yayi saurin dora hannun sa akan baki alamun Musaddik yayi masa shiru, wurga masa pillow da ya jefe shi dashi yayi ya fice yana cewa " Ka same ni a kasa idan ka gama zan kalli laliga." Da kai ya amsa masa yana kara kiran a kunnen sa " Nagode sosai da kika kirani, na zata ba zaki kira ba." " Haba! Zan kira ai." " Nagode sosai, bari na kira ki toh." " A ah ba komai, muyi magana akwai kati kar a cinye maka naka kai kadai." Murmushi yayi me sauti " Kinga kuma 200 nasa dazu har ta kusa karewa, bari na fita sai na sake siyo ko na 100 ne sai na kiraki." " Allah ba sai ka fita ba, ga sanyin nan da ake yi ma." " Shikenan Nagode." " Me kikayi a wajen Abba." " Abinci naci." " Iyeeeee, yar gata! Har abinci abba ke baki? Allah sarki ni." " Kaima ai dan gata ne." " Ni din? Tab ni ba dan gata bane, gashi ke har abinci Abba yake baki, niko kin ganni a dan shago na sanyin nan duk a kaina zai kare, babu me tausayi na ya bani abinci." " Allah sarki." Tace cikin tausayawa, da ace sun saba sosai da tace yazo ya karbi abinci, ta hada masa har da abin rufar ta idan yaso ita sai ta samu wani wajen Gaji, amma ba zata iya ba, sai kawai tayi shiru tana tunanin ta yadda zata fad'a masa Abba yace yazo ya samu yayansa. "Dama... Dama...Abba ne yace." "Me?" Yace cikin zakuwa "Wai ka fara zuwa ka samu Abba (Baban yayansu) ka nemi izinin zuwa kafin ka cigaba da zuwa." "In Sha Allah zanzo, yaushe ake samun sa a gida?" "Kamar da yamma haka zuwa bayan Magriba." " Ok in sha Allah zanzo, nagode sosai da wannan karamcin na Abba, duk da ni din ba kowa bane, amma har aka bani wannan damar, nagode Sosai." " Ni dai dan Allah ka daina cewa kai ba kowa bane, a islamiyya an fad'a mana, babu wanda yafi wani sai wanda yafi tsoron Allah." " Haka ne, wai kinga ina nufin ni din ba kudi ne dani ba, amma..." " Kudi ba sune farin ciki ba ai, wadatar zuciya itace mutum, dan Allah ka daina wannan maganar kana sani jin wani iri." "An daina ta daga yau, ba zaki sake ji ba, kiyi hakuri idan na bata miki rai." " Babu komai." " Yawwa, kiyi min murmushi naji toh." Shiru tayi " Kinji mana, pleaseee." Yace sai kuma yayi saurin daidaita kansa ganin zai zarme da yi mata shagwaba har ta ranfo wani abu "Nayi fa, ai baka gani na." "Tam shikenan, idan naje na nemi izini wajen Abban mu, zanzo na gani a zahiri." "Uhum." Tace tana jin zuciyar ta na sake nutsuwa dashi, ko ba komai ta samu wani da yake dauke mata damuwar ta da kadaici "Bari na barki haka kar na cinye miki kudi..." "Goodnight, sweet dreams of meeeee." "Allah ya tashe mu lafiya." Tace tana yin dariya k'asa k'asa "Amin ya Allah, bye inji turawa." "Bye." Tace mishi ta ajiye wayar. "Yess!" Yayi tsalle ya dire kafin ya fice yana saka hannun sa cikin aljihun dogon wandon sa. A falon ya tarar da Musaddik da tea yana sha, ya zauna ya diba shima yana murmushi. _"You don make me fall in love, you don make me fall in lov, Baby I love you."_💕 Dariya sosai Musaddik ya saka " JJC kawai, zaka cika mana kunne da wata wakar ka." "Idan fitsari abin banza ne, kaza ma tayi mana?" "Okh haka ne, shikenan ai.Wait and see. Ni yanzu ba wannan ya kawo ni ba, me yasa ka saka aka dakatar da gayen nan ne?" Tashi yayi rik'e da cup din yana bata fuska "Kaga dacewar ya nemi irin abinda nake nema?" "Kamar ya?" "Ba'a takara da Sarki, be chanchanci karawa dani ba, bashi da qualities din da zai iya neman auren ta, cika bakin sa ya saka na nuna masa iyakar sa, anyways warning ne kawai, zan sake gwada hankalin sa , idan yayi hankali fine, idan be ba kuma sai muje a haka, sai a karbi application din wasu." Gid'a Kai Musaddik yayi be sake cewa komai ba, yasan waye Moh, yasan bashi da matsala ta kowanne bangare, amma bashi da dadi idan har kayi crossing din sa, zai nuna maka shi din babba ne a cikin manya! "Ka fahimta dai ko?" "Yes Captain!" Ya mike sannan ya sara masa. "Aje waya!" Yace masa suka kwashe da dariya a tare. HALIN GIRMA Hafsat Rano WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_* *ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA* *_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_* *GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi* *JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE* *_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_* *_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_* *_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_* *_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_* *_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_* *DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL* 2👉🏾400 3👉🏾500 4👉🏾700 5👉🏾1000 *Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin* 6019473875 MUSAA ABDULLAHI SAFIYA keystone bank Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 08184017082 *IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU* 09134848107 _*HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽 #team zafafa biyar . ___________ 1/6/22, 17:52 - Buhainat: *HALIN GIRMA*             7 *Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107*  I'm on Instagram as @zafafabiyar5. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *** Kukan ta ne yake karuwa Mama na tsaye a kanta, ta ja tsaki tace "Bana son shirman banza kina ji na? Akan namiji zaki zauna kina rafka wannan kukan kamar uwarki ce ta mutu ko ubanki?" "Mafita nake so mu samawa kanmu, saboda anga zaki huta shine aka shiga aka fita ake so ayi mana bakin ciki, idan ba haka ba, me ya kawo wadannan zantukan?" Cikin kuka tace "Wallahi Mama nasan Iman ce taje ta samu Gaji da maganar tunda dama ita yace yana so ai, shine dan taga wanda yazo wajen nata talaka ne shine zata min bakin ciki, toh wallahi babu wanda ya isa ya hanani auren Bashir, naji na gani kowanne hali ne dashi." Shiru Maman tayi tana kallon yar ta ta, idan har ta bari maganar ta sha ruwa akwai matsala, sanin cewa Zeenat din ba wani farin jini bane da ita, dama dai jamaar Iman din ne tun farko take sanin yadda zatayi, dole ta san abinda ya kamata amma duk da haka ba zata nunawa Zeenat din komai ba " Kina jina? Ki tashi ki tafi dakin ku, ki daina wannan kukan tunda ba ubanki bane ya mutu, zan san yadda zanyi komai ya daidaita." Da bayan hannun ta ta goge kukan, ta fice tana rangaji, tana sake kudurewa a ranta babu gudu babu ja da baya a auren ta da Bashir din.   Tana isa daki ta tarar da missed calls din sa, ta bi kiran da sauri tana sake daidai ta kanta. " Gani a waje." Yace tana dagawa. " Mu hadu a bayan layi akwai matsala karka zo gida." " Me ya faru?" Yace a kidime. " Babu komai gani nan zuwa." Kashe wayar ta, tasan zai ta tambayar ta menene gwara kawai taje suyi magana su sama wa kansu mafita dan ba zata iya hakura dashi ba.   Ficewa tayi ta kofar kitchen bayan ta gyara fuskar ta, ta bar gidan cikin sauri tana tsoron haduwa da Ya Habib ko wani.   A chan bayan layin ta hange shi jikin motar sa, a tsaye yake yana ta jijjiga jikin sa daga gani baya cikin nutsuwar sa, tana isa ya juyo da sauri. " Lafiya baby?" Yace yana riko hannun ta. Kuka ta saka da sauri yace " Na shiga uku, me ya faru?" " Abba ne yace wai na rabu da kai, wai yayi bin..." " Shisshsh..." Yace da sauri yana dora hannun sa a saman bakin ta " Kinsan dai hakan ba gaskiya bane ko? Sharri akayi min ko menene akace domin a hana mu aure, duk wanda ya yi min wannan sharrin na bar shi da Allah kawai." Yace yana girgiza kansa " Shikenan yanzu rabuwa zaki dani? Nasan rayuwata shikenan ta kare, idan har zaki iya yarda mahassada su shiga tsakanin mu, bakya so na baby, rayuwata shikenan ni." " Ni ban yarda da duk abinda akace ba ai, kawai sharri ne na sani, amma ya zanyi da Abba? Bayan shi din kaifi daya ne akan maganar sa." " Dan Allah Zeenat karki yarda a raba mu, wallahi Ina sonki , bansan ya zanyi da rayuwa ta ba idan har baki aure ni ba." Hawaye ya fara yi tayi saurin sa hannu ta goge masa "Zanyi duk yadda zanyi, ba zan bari a raba mu ba..." " Da gaske? Kinyi alkawari?" " Nayi maka alkawari." " Dan Allah karki saba alkawari dan Allah, ki taimaka wa rayuwa ta, kinji?" " Karka damu." Tace tana jin wani karfin zuciya, " Ba zan taba yarda su yi min abinda bana so ba, Kai nake so kuma duk yadda kake ina son ka a haka.* "Nagode nagode baby, in sha Allah ba zakiyi dana sanin amincewa dani ba." Zatayi magana wayar sa tayi kara " Sorry." Yace mata kafin ya daga yana rage volume din wayar sosai " Malam tun dazu nake jiran ka, ka dawo min da mota zan fita, wai ina ka tsaya ne?" " Gani nan yanzu in sha Allah." Ya kashe kiran ya ce " Baby bari naje, urgent call daga Baba, zamuyi waya kinji?" " Tam shikenan." Tace a sanyaye " Yawwa ga sakon ki..." Ya bud'e murfin motar ya fiddo da ledoji, hannu tasa ta karba tayi godiya, ta juya ta soma tafiya shi kuma ya shiga motar ya tada ita da sauri ya bar wajen, yasan ba zasu kare kalou ba da ita, amma kuma hakan shine kadai zai kankaro masa mutuncin sa. ***Daki ta koma ta ajiye ledar bayan ta bud'e taga ice cream ne da Pizza, sai charger waya da yake ta lalace ta ta, sai wasu tarkachen alawoyi. Bata taba komai ba sai charger din ta jona wayarta a jiki sannan ta fice zuwa bangaren Gaji dan ta samu Iman a yi wacce za'a yi.    Iman din ce kuwa kadai a falon tana karanta hisnul muslim. Sai ganin mutum tayi a kanta, bata tanka mata ba ta sauke kanta ta cigaba da karatun ta kawai. "Saboda kina bakin ciki kin samu fakiri talaka shine zaki kai munafurci kice Bashir bashi da hali ko?" "Wacce irin magana ce wannan Zeenat?" " Malama karki pretending kaman baki sani ba, idan bake kika fad'a ma Gaji wata magana akan Bashir ba waye ya samu Abba ya fad'a masa Bashir bashi da hali me kyau?" Tashi tayi zaune tana kallon ta, ta girgiza kanta kawai kafin tace " Kinsan bani da lokacin batawa akan irin wadannan maganganun, dan haka please bana son maganar." " Zaki ce bakya so mana kina min bakin ciki, toh wallahi sai dai ki mutu da bakin ciki amma aure na dashi babu fashi, kije chan kiji da wanda zaki aura, mutum kamar shi ya kawo talauci duniya." Tashi kawai tayi ta bar falon zuwa bedroom din Gaji dan ba zata iya irin wannan shirmen na Zeenat ba, sai dai da gaske maganar ta taba ta, har taji ta rasa gaba daya walwala da farin cikin ta, kwanciya kawai tayi ta rufe idon ta tana hasaso rayuwar ta nan gaba! ***Cikin shigar Khaki pants da wata jibgegiyar rigar sanyi da ya saka a saman armless rigar sa ya fito, kansa da yake a kwance yasha gyara ya tsaya yana sake dubawa a katon mudubin da yake ajiye a falon, yasan Takawa zai saurare shi ya kuma bi abinda yake so sai dai baya son ko kad'an karya ko wasa ya shigo a cikin maganar auren sa. Kallon kafar sa yayi, sai ya koma ya sauya takalmin zuwa wani daban sannan ya fice yana tura hannun sa cikin aljihun dogon wandon nasa.    Suna tsaye k'yam suna jiran fitowar sa, kowanne su cikin shigar da take nuna shi din waye, bud'e masa motar akayi da sauri ya fad'a yana makala bakin glass din sa yasan yau zai same shi a wajen hutawar sa, in da ya dace da maganar da zasu tattauna, shiyasa ma yayi shigar sa da yasan Takawan bazai masa surutu ba, dan ya riga ya san shi, ko yace kowa ya san shi da tsanar manyan kaya musamman a lokacin zafi sai yace wai takura masa suke.    Da yake sun san in da zasu, kai tsaye suka wuce dashi Family house din, in da Takawan ke hutawa a duk ranaku irin wannan ba tare da shigowar wani shaani na mulki ba. Iyakar abinda ya shafi kansa da iyalin sa kawai yake tattaunawa a rana cikin saukakakkiyat shiga da ba zaka taba cewa sarki bane duba da ko yaushe yana nannade cikin rawani da manyan kaya.    A kofar wajen motocin nasa suka tsaya, ya balle murfin tare da me bud'e masa ya fito yana kallon ko ina na harabar gidan. Kansa sanye da hular sanyi ya cire glass din idon sa ya shiga takawa zuwa ciki. Gaisuwar da ya tsana ya dinga kokarin kaucewa har ya dangana da inda takawan yake ya hange shi a zaune a cikin wajen yayi matashi da pillow yana kallon yadda yan yaran da suka kasance jikokin sa ke wasa a wajen.    Sarkin dogarai ne ya fara ganin shi,ya washe cikin farin cikin ganin shi yace "Maraba da Yarima!" "Sarkin dogarai..." Muryar sa ta saka takawa d'agowa, ya gyara daga gishingid'ar da yayi, ya fad'ad'a fara'ar fuskar sa da tayi ma Moh iso har gaban kakan nasa. Russunawa yayi cikin girmamawa ya kai gaisuwa, hannu ya mik'a masa ya matso kusa dashi sosai, ya shafi saman kansa " Sai yau kaga damar leko ni ko Muhammadu?" " Tuba nake Takawa, ayyukan ne suka yi min yawa." " Toh madallah, naji kace kana son gani na, toh gani ya akayi?" " Dama magana ce akan abinda Bubu yayi maka magana." " Auren ka? Jairi toh sai akayi yaya?" Dariya ya saka sosai " Toh kunce sai nayi aure yanzu kuma nazo da maganar kuma, sai na fasa auren ma gaba daya." " Fasa mana, waya yayi asara? Kaji dan nema." Dariya suka saka a tare, kafin Takawa yace " Toh sai ka fadi a inda yarinyar take ko? Idan yaso sai a nemi iyayenta." " A ah ni dai Takawa, ayi min aikin gafara a bari a samu wasu suje su nema min auren ta." " Wasu?" Yace yana kallon sa " Eh a dangi haka ba, ba manya sosai ba, Ina nufin ba cikin manyan masarauta ba, yan chan kasa kasan dai." " A wanne dalili?" " Kawai ni bana so suji tsoro su ga kamar mun fi karfin su." Girgiza kai Takawa yayi " A neman aure babu boye boye Muhammadu, a sak dinka zaka je, kai ne fa jika na farko a gidan nan, sannan a wajen mahaifin ka, wanne irin tunani ne haka ya shiga kanka?" Sosa kai Moh yayi yana marairaice fuska "Ni dai dan Allah takawa, a bar wasu suje." "Sam sam kaima kasan hakan ba mai yiwuwa bane, dole ne su san kai din daga gidan da ka fito." Shiru yayi yana jin kamar ya daure kansa da ya budewa Takawa zuciyar sa, yasan shi sarai da tsayawa akan ra'ayin farko, amma yayi tunani zai fuskance shi duba da irin son da yake masa, dama Musaddik ya gaya masa, babu me yarda da shirmen sa kamar yadda yake jaddada masa a kullum, babu me biye masa ko bashi goyon baya. Tun daga lokacin yasan sarai babu me tsayawa ya saurare shi, balle ya yarda da tsarin sa. Ammin sa ce kadai itama bata ja da maganar Takawa, ballantana Bubu da baya iya aiwatar da komai sai abinda Takawa din yace.    "Kana jina Muhammadu, maganar da kazo da ita bata kamawa bace. A tsari na gidan nan ma zamu iya aika musu suzo nan din domin muna da damar bada diyar tasu, sai dai ba zamuyi haka ba, zamu basu girman su da darajar su in Sha Allah, za kuma musu duk abinda Muhammad yake so amma banda shiririta." Ya karashe yana murmushi, murnushin shima yayi kawai ba tare da yace komai ba. Suka cigaba da hira irin wadda suka saba har be san iya adadin awoyin da ya bata ba, sai da suka ci abinci da Takawar sannan ya lallaba ya shiga gidan ya gaida matan gidan ya kare a dakin kakarsa ya tarar da yan matan family din sunzo suna da wani get-together da suka shirya sannan suyi maganar tsari bikin Abidah guda daga cikin jikokin gidan.    A kaidar sa baya sakar musu fuska ko kad'an domin suna da rainin hankali sosai, duk da shi basa yi masa neman ma ya kula su suke amma shi sam baya tsayawa shirmen su, da gaske suka shakkar shiga shirgin sa hakan yasa yana shigowa shashen suka dinga yayewa da d'aya d'aya.   Dan tsiririn tsaki yaja sanda suka gama ficewa ya zauna yana muzurai a dole baya son raini shi. Mutane da yawa na fad'a masa yadda yake abubuwan sa kadai ya tabbatar da shi din jini ne na sarauta amma shi sam be san ma yana yi ba ma.    Ya dan jima a wajen nata kafin ya tafi yana jin zai dan dade kafin ya sake waiwayo su duba da tafiyar dake gaban sa akan aikin sa. ***Yana zaune a gate din gidan yana dakon shigowar Abba Babban, a kan idon sa ya dawo ya tashi da sauri ya tare shi ya bud'e masa kofar mota. "Sannu da zuwa Abba." "Yawwa Ibrahim, kaine yau a gate din kenan." " Wallahi kuwa Abba, sannu da dawowa, ya aiki?" " Alhamdulillah mun gode Allah, ya naka aikin?" " Alhamdulillah." Yace yana tuna abinda ya faru dashi. " Allah ya taimaka ya bada sa'a." " Amin Abba." Yace yana bin sa rik'e da jakar sa a baya. " Mika jakar ciki bari na fara gano Gaji." Yace yana bin hanyar da zata kaishi bangaren Gajin, da sauri Khalil din ya kai masa jakar ya dawo ya zauna yana jiran ya fito. Ya dan jima a wajen Gajin kafin ya fito sai dai ganin Khalil ya saka shi mamaki, abunka da Babba nan da nan ya gane akwai wani abu. " Ya akayi Khalil? Kana son gani na ne?" " Eh Abba." Yace yana sosa kansa " Haba ko da naji, toh zan turo a kiraka kaji?" " Toh Abba Nagode." Girgiza kai Abban yayi ya wuce bangaren sa. Maimakon ya koma gida sai yayi zaman sa anan yana jiran kiran Abban. Yana zaune kuwa yaga fitowar Sadik ya tashi da sauri ya tare shi "Yawwa wai kazo in ji Abba." Rik'e hannun sa yayi suka koma yana jin wani iri a ransa, bakin sa dauke da addu'a ya shiga falon ya tarar Abban ya chanja kaya yana zaune da alama abinci ya gama ci. A chan gefe ya zauna yana jin kunya. "Yawwa ina jin ka Ibrahim, ya akayi?" Shiru yayi yana tsara yadda ya kamata ya ce, sai da ya dau sakanni yana hado maganar kafin yace "Dama Abba akan maganar Fatima ne." "Uhum ina jinka. Ya akayi?" "Dama... Dama so nake dama a bani dama kamar yadda tsarin gidan nan yake." Murmushi Abba yayi cikin jin dadi yace "Masha ALLAH naji dadin wannan abu matuka, Allah ya tabbatar mana da alkhairi kaji? Allah yayi muku albarka." " Amin Abba." Yace a ciki-ciki farin ciki na kamashi, " Kaje ku daidaita idan Allah yayi mu haka muke so, an riga an zama daya ai in sha Allah babu wata matsala." " Nagode Sosai Abba, Allah ya kara girma." " Amin." Yace yana chanja tasha a tv, shiru Khalil din yayi kafin ya mike " A huta lafiya Abba." " Yawwa Ibrahim." Yana fita ya daka tsalle a wajen yace "Yes!!" Da sauri ya bar wajen yana jin kamar ya same ta ya gama ne, zai nuna wa fakirin saurayin ta cewa dan gida yafi bare. ***Sabon yadi ne me saukin kudi sosai, dinkin ma irin dan 1500 din nan ne, a rayuwar sa be taba hasashen saka ire-iren kayan da yake sakawa a yanzu ba, wani kallo Musaddik yake masa yana jin kamar ya kamashi yayi ta bugu. "Yanzu Moh irin kayan da zaka saka kenan zaka ganin sirikin ka?" "Wait and see." Yace yana kawo wata leda a kusa dashi, ya wurga masa yana cigaba da kallon kansa a mudubi "Ka chanja mu tafi idan yaso muyi sallar magriba a hanya sai mu karasa." "Na saka me?" Musaddik yace da sauri yana bud'e ledar. "Wait what! Kana nufin ni zan saka wannan kayan." "Mu nawa ne a dakin nan?" "You must be kidding me, haba haba an fad'a ma kowa ma irin ka ne." "Allah su zaka saka mu tafi, kayi sauri karka batan lokaci I'm dying to see my love." "Aiko sai dai ka tafi kai kadai wannan karyar ba dani ba." "Da wa toh? Wa nake dashi bayan kai? Kasan da ace ban samu kanta ba dole kaima ka tattaro ka dawo sabon shagon nan dana zauna mu zauna tare. Allah dai ya taimake ka wallahi." " Ai wallahi babu yarinyar da ta isa nayi mata irin wannan son, the whole you, Captain Muhammad Ahmad Santuraki, dan ga sarki jikin sarki sannan kuma babban soja, ko da yake fa dama ance ku sojoji baku iya soyayya ba, musamman idan allurar ku ta motsa." Daina abinda yake yayi ya matso kusa dashi " Idan bansa an saka min kai frog jump ba, kace ba suna na Muhammad ba." Dariya maganar ta bawa Musaddik, " Ni zaka saka frog jump?" " Sosai, ka cigaba da batan lokaci kaga." Tashi Musaddik yayi ya sake daga kayan, kafin ya fara sawa yana cigaba da mita. " Kanka akeji wallahi." Moh yace yana cire agogon hannun sa. " Ka cire watch dinka please, anything da zai sa ta zama suspicious, I don't care idan kowa na gidan su yasan ni waye, amma ita? Da marikiyarta will be the last da zasu sani, surprise ne me kyau nake son basu dukka, sai dai kowanne da yadda surprise din zai zo masa." " Wicked soul." Musaddik yace yana jefar ta watch dinsa akan mirrow " What ever!" Yace yana yin gaba yabi bayan sa yana jin dadin kayan jikin sa, babu nauyi shawai shawai amma kuma ba zai yarda Moh din yasan ya ji dadin kayan ba. A daidai shagon aka daajiye su, yace su je chan in da suka saba jiran sa su jirashi zai kirasu. Duk da basu so ba amma haka suka tafi suka barsu, Musaddik ya dinga jan tsaki suna tafiya a k'asa har suka isa kofar gidan. Wayar sa ya ciro ya kira ta, tayi ta ringing bata daga ba, " Bata daga ba." " Da ka kirata tun kafin muzo ai." " Wannan ba matsala bace, bari kaga." Ya kwankwasa gate din kafin ya dan tura shi suka shiga, dai-dai lokacin Khalil ya taho zai fita sukayi kichibis, wani kallo ya bisu dashi irin na sama da k'asan nan, kafin ya tuntsure da dariya sosai, hakan yayi bala'in bata ran Musaddik da dama chan baya daukar nonsense. " Malam lafiya zaka kalle mu kayi dariya?" " Lafiyar kenan, sai dai kun makara, dan gida ya shiga ya fita ya gama tabbatar da komai akansa, sai abi wani sarkin dan an riga an gama magana kuma su din ba kananan mutane bane da zasu sauya maganar su." " Kana nufin?" Musaddik yace a zafafe " Ina nufin kamar yadda na fada mishi ne a baya, Iman matata ce an riga an gama magana rana kawai ake jira a saka mana." Wani kallo Moh yayi masa da ya saka Khalil shan jinin jikin sa, amma sai ya dake ya cigaba da gaggayawa musu magana. Muhammad be ce komai ba har ya gama, ya juya ya fice ya barsu a tsaye kamar mutum mutumi. " I have no option than to show him my real identify, idan yaso duk abinda ya biyo baya yayi kuka da kansa ba da kowa ba, karfe nawa ne appointment dinsa?" " Da safe ne, goma kamar." " Owk Allah ya kaimu." " Amin." Musaddik ya amsa ransa na sake baci akan abinda Khalil din yayi musu HALIN GIRMA Hafsat Rano WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_* *ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA* *_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_* *GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi* *JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE* *_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_* *_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_* *_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_* *_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_* *_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_* *DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL* 2👉🏾400 3👉🏾500 4👉🏾700 5👉🏾1000 *Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin* 6019473875 MUSAA ABDULLAHI SAFIYA keystone bank Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 08184017082 *IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU* 09134848107 _*HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽 #team zafafa biyar . ___________ 1/6/22, 17:52 - Buhainat: 08 *zafafa biyar na kudine,tuntubi wadan nan numbers din don samun naki copy din ki karanta cikin aminci* 08184017082 Ko 09134848107 *_follow us @ instagram_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1h9y2qgfg67x5&utm_content=nj79azb Or facebook https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share ___________________________ Dan kwantar da kujarar yayi kana ya miqe sosai Samanta yana jin yadda gajiya take bin jikinsa,don gaba daya wunin yau bai shirya fita ba,ya shirya zama ya huta sosai a gida,saboda satin gaba daya cikin aiki ya yisu,babu dare babu raba,har inda ma a tsarinsa babu schedule na zuwansa sai daya ratso masa a sannan din. hannayensa saman kansa yayin da idanuwansa suke a rufe,yayi nisa a tunaninsa sosai,busy busy ne dashi irin wanda mutane da yawa ke mamakinsa,sam bai bawa kansa hutu ba. a qalla ya kusa minti ashirin a zaune a haka,wanda hakanan yaji zaman yayi masa dadi,ko ba komai ya dan samu break na wasu mintuna. Dan waiwayawa yayi gefansa,a sannan ya hango tahowar professor shi da wasu mutane hudu,saiya miqe ya gyara zamansa,ya kuma kunna motar yana jiran qarasowarsa. yana jin sanda ya shiga yana sallama da mutanen,suka maida murfin motar suka rufe masa,don haka saiya tashi motar,dai dai sanda professor ya furta "alhamdulillah"yana sauke ajiyar numfashi. A nutse yake tuqin har suka fita daga airport din,a hankali professor rashid yace "lawan....ko ka sake koyon sabon salon tuqi ne?"raba idanu samir yayi hagunsa da damansa,saiya lanqwashe murya yace "eh alhaji"dan jim professor yayi sannan yace "to yayi kyau"daga haka bai sake cewa komai ba,zaman shuru yaci gaba da ratsawa a tsakaninsu. "Daka sani ai baka wahalar da kanka ba samir....."yaji abban nashi ya fada bayan tsahon wani lokaci,ya ganeshi kenan,qyaleshi yayi kamar bai gane ba,qaramin murmushi ya subuce a kuncinsa,jerarrun fararen haqoransa suka bayyan,har yayi kamar bazaice komai ba sai kuma ya tanka "yau daya dai abba....ai nima na samu ladan yau din"wayar hannunsa professor ya ajjiye,ya tsurawa gaban motar idanu,kamar anan fuskar samir din take,baisan me yasa a kullum shi da tilon dan nasa komai nasu yasha banban ba,komai nasu ba iri daya bane,abinda yake sam ba cikin tsari da burinsa ba,ya jima da sanin cewa ba haka yakeso ya kasance ba,ba haka tsarinsa yaso ya zama ba,to amma duk ta inda yake tunanin zai gyarota babu wani sauran dama data rage masa,don haka a maimakon yayi magana,saiya buge da hade yatsunsa waje daya,yana maida tunaninsa wani waje daban. Duk sanda yayi tafiya irin wannan ya dawo iyalansa dama ma'aikatan gidan kan cika da murna,kamar yanzun,da samir ke biye dashi dauke da wata qawatacciyar qaramar jaka mai zubin akwati,yana biye da professor har zuwa cikin qawataccen falon gidan,mai yalwa da kuma burgewa,wanda ya wadata da dukkan wani nau'in kayan alatun rayuwa. mutum uku ne ke dakonsa zaune cikin falon,biyu daga cikinsun matasan yammata ne,daya tafi daya tsaho da haske,kamar yadda daya tafi daya shekaru da basu wani taka kara sun karya ba,don dukkansu ba zasu gaza shekara sha tara da ashirin ba. Daga wata kujera kuma mai mazaunin mutum biyu,macace xaune itama wadda ta mallaki shekaru ɗai ɗai har shekara hamsin,saidai idan har kai mai kallo xa'a qyaleka kayi mata ƙiyasin shekaru,to ba shakka zaka ce dauka cewa bata wuce shekara talatin da biyar ba. Tun a kallon farko xaka bata sunan HAMSHAQIYA saboda ta cancanci sunan,fara ce sol,shekarunta sam basu boye hasken fatarta ba,tana da matsakaicin kyau wanda ya cakuda da tarin ado da qawar da take qawata kanta dashi kullum kwanan duniya,kallon farko zai gaya maka ta saba da ado ya zame mata jiki,salon irin abun nan da hausawa suke cewa WANKA YABI JIKI,tun daba hannayenta zuwa wuyanta kayan ado ne na mata,fuskarta wadace take da murmushi kamar bakinta zai yage,idanunta qur bisa saman fuskar wadan nan halittu guda biyu,wato samir da professor,tana dubansu da wani irin kallo me nauyi da zurfi. Dukkaninsu suka miqe kowanne fuskarsa na nuna tsantsar farinciki,daya daga cikin matasan yammatan nan wadda da alama batakai shekarun daya ba ita ta tako da sauri zuwa inda professor yake "Abba.....sannu da dawowa"ta fada da 'yar siga ta shagwaba,da alama kuma hakan habit dinta ne,tana dora kanta saman kafadarsa,kamar marayan daya samu tallafi,murmushi ya saka yadan dora kansa saman kanta "barka kadai auta....na sameku lafiya?" "lafiya qalau abba,saidai munyi missing dinka"murmushin yakuma saki "gani na dawo ai jauhar,duk wata kewa ta qare ko?"kai ta gyada,sai dayar itama ta matso,tasa hannu kadan tana gyara eye glasses dinta,fuskarta itama murmushinne kwance "barka da zuwa abba" "barka kadai lelen abba.....na sameku lafiya?" "lafiya lau abba ya hanya?" "alhmdlh,ya karatu?"saida ta saki wani ni'imtacce murmushi,tana jin wani dadi na ratsata,ta daga idanun a hankali ta maida gashi,samir.......wanda har yanzu yake tsaye a bayan abban nasu tamkar wani dogari,hannayensa zube cikin aljihun wandonsa yana kallon dukkan abinda ke faruwa, inside him yana jin tsaiwarsa a wajen cikin abubuwan da suke gundurarsa nan da nan,ya qagu duka a gama wadan nan gaishe gaishen. dauke idanunta tayi ta maida kan abban,a duniya tana jin dadi tana alfahari abban nasu ya tambayeta karatunta,tana jin wani qwarin gwiwa yana shigarta aduk sanda ya tambayeta wani abu daya danganci karatunta,takanji burinta kwadayinta da qwarim gwiwarta yana daduwa "alhmdlh abba....komai lafiya" "ma sha Allah"ya fada yana maida dubansa xuwa gareta,har yanzu bata matsa daga inda take tsaye ba,amma hankalinta idanuwanta da hankalinta dukka yana kansu "sarautar mata.......yada tsaiwa a nan?"murmushi ta saki "to ai naga hankalinka duka yana kan yaranka,kaga gwara na barku ku gama tukunna.....barka da dawowa" "barka kadai.....na sameku lafiya?" "alhmdlh"ta fada taba jifansa da wani murmushin,saita tako a hankali ta raba ta gefansa,idanunta saman fuskar samir,suna hada idanu ya kauda kansa ya miqa mata jakar professor dake riqe a hannunsa,hannu ta miqa zata amsa tana cewa "ka kyauta samir"ya fahimci abinda take nufi,saiya saki qaramin murmushi yana juyawa kadan zai fita "ya da haka son...ka bari daddy ya kintsa muci abincin rana tare mana"ta furta cikin nuna zallar kulawa,kansa ya girgiza yana sosa kan mashi da tsinin key din mota,shida yakeson tsallakewa fadan professor,yayi imanin idan ya zauna suci abin tare zai tono laifin da shi yaketa qoqarin bunnewa ne "akwai abubuwa da yawa dana bari,zanje na rage wasu,bazan jima yau a waje ba zan dawo gida" sanda yake maganar shima professor ya nufi hanyar da zata sadashi da sassansa da suka qunshi bedrooms manya guda biyu,da.katafaren falo guda daya "da zaki daina wahalar da kanki wajen tsaidashi,ki barshi ya tafi kawai, saboda haka yakeso,hakan ya tsarawa kansa kamar ko yaushe" sarai samir yasan magana ce mai harshen damo yayi masa,sai data waiwayo ya kalli samir "ohk....saika dawo,Allah ya tsare" kansa ya gyada sannan ya juya zai fice,itama ta rufawa professor baya. "ya saraki"kiran da aka masa shine abu na biyu daya shiga kunnensa daga hirar professor da matarshi,sai yaja tunga ya tsaya sannan ya waiwayo a hankali sanda take tasowa a shagwabe ta riskeshi. Idanuwan najwa tar bisa fuskar jawahir sanda take nufar yayan nasu,saita sanya hannunta ta cire airpiece guda daya cikin biyun dake maqale a kunneta,tana jin wani abu na tokare zuciyarta,ta tsani taga tana magana dashi sam,tana son taji yanzun me zatace da shi ne. "ya saraki.....please,alqawarinmu fa" ajiyar zuciya yayi hade da lumshe idanu,lokaci guda kuma ya furzar da iska daga bakinsa,baice komai ba saiya cusa hannunsa cikin aljihunsa ya fiddo sabbin 'yan dari biyar biyar masu dama ya miqa mata,wani dan tsalle ta saki bayan ta amshu kudin "thank you so much,am proud of you my yaya"murmushi kawai ya bita dashi sannan ya taka ya fice. kudin na hannunta tana juyasu,fuskarta a wadace da murmushi ta koma kujerar data tashi akai ta zauna,duk abun nan da ake idanun najwa a kanta,tana binta da wani kallo da zai nuna maka zallar tkaici da haushinta daya cika mata zuciya,sam jawahir batasa me take ba tana irga kudinta hankali kwance,ganin cewa da gaske jawahir batasan tana yi ba,lissafin kudinta kawai take,saita miqa hannu ta fusge kudin a tare tana furta "banza"da qarfi,hakan yaja mata hankalin jawahir din yadda takeso,dubanta take baki bude "me na miki ya najwa" "banza"ta sake maimaitawa tana hararta,idanuwanta kamar zasu fado akan jawahir din "wai me na miki?" "ke wai.me yasa baki da zuciya,kuma baki da kishin kanki?,na meye zaki tambayesa kudi,momi ba zata baki bane da ba zaki tambayeta ba?"sosai jawahir ta bata fuska tana kallon najwan,ranta a dan bace "amma shi da momyn ai duk daya ne ko?,kuma ko ita ai taga ina tambayarsa,kuma bata ce komai ba"baki najwa ta tabe 'bakya ganewa,kuma ba zaki taba ganewa ba....." "nidai koma meye bani kudina"ta furta tana miqa mata hannu "naqi na bayar din"najwa ta fada tana cusa kudin a gefan cinyarta,sai jawahir din ta sake gimtse fuska sosai "kinga ki bani kudina ya najwa,ko momy tace ki daina shiga harkata ko?" "idan kina da qarfi ki danne ni ki qwata,sarai dai kinsan babu abinda zanyi da kudin nan.....". A hankali ta buda qofa ta dawo ta cikin falon,idauwanta ya sauka a kansu sanda jawahir ke sake maimaita wa najwan ta bata kudinta "lafiyanku?"momyn ta jefa musu tambayarsu,wanda banda tayi magana babu wanda yaga fitowarta cikinsu "momy....ya saraki na tambaya kudin ankon yasmin tun rannan,to ya bani shine ya najwa ta karba ta hanani,tana masifar wai don me zan tambaya ya saraki"jawahir tayi caraf ta gaya mata,sai data tabbatar ta aikawa jawahir saqon harara sannan ta maida dubanta ga mony da nufun yin nata bayanin "momy wai ba....."wani kallo momyn ta aika mata,sannan ta daga hannunta kawai ba tare da tabi takan qorafin da takeso. sako.mata ba tace "bata kudinta"fuska ta bata "momy...." "nace ki bata kudinta ha'an...?"ta fada da dan zafi zafi yanzun a muryarta,fuskar najwa a cunkuse,ta zaro kudin ta jefawa jawahir,ya fada saman cinyarta,bata damu ba ta dauki kudinta taci gaba da irgawa,momyn ta kalleta "ajjiye kudin nan kizo kitchen ki hadama daddynku drink" "to momy"ta amsa mata tana miqewa da kudinta a hannu tabi bayanta,yayin da najwa ta bita da harara,tana jin kamar ta shaqeta,saita gyara glass din fuskarta,ta kuma gyara zaman qaton littafin dake ken cinyarta taci gaba da dubawa,can qasan ranta abubuwa da yawa na mata yawo,inda tana da qarfin iko da sai ta canza abubuwa da dama cikin gidan nasu,abubuwa masu tarin yawa da basuyi rayuwarta yadda takeso ba,basu zauna kuma a gurbi da muhallin da takeson ganinsu ba. *_9:30 am_* *_DARMANAWA HOUSING ESTATE_* *_PROFESSOR RASHID USMAN AZARE RESIDENT_* Daya ne daga cikin jerin qawatattun gidaje dake gine cikin unguwar,,wanda suka qawatu aka kuma ginasu bisa basira da kuma kyakkyawan tsari. Gini ne na alfarma mai cike da qayatarwa da ban sha'awa,kamar yadda akasan ire iren gidajen masu sukuni suke da kuma unguwaninsu. A hankali momy ta daga kanta,fuskarta na fidda wani irin murmushi mai haske tunda ta jiyo sautin muryarsa,tun gabanin ma ya iso inda suke din,yayin da ta tsaida dukkan abinda takeyi,ciki harda cin abincinta,da kuma hira da take da 'yammatan dake gefanta su uku,najwa jawahir da kuma ramla da take 'yar ruqo a wajenta. Dukkaninsu sunsan meye ta baiwa hankalinta haka gaba daya,ba wacce bata saba da ganin tarin kulawa da qauna daga gareta ba zuwa ga samir,wadda ta banbamta da ta kowanne da dake cikin gidan. Kallo daya professor yayi mata yaci gaba da cin abincinsa a nutse,don shi din ma hakan ba baqon al'amari bane a wajensa,illa dai ya kada kansa sannan ya maida hankalinsa ga farantin gabansa. Cikin sakanni da basu kai goma ba ya bayyana cikin falon dab dasu,matashin saurayi muhammad samir me laqabin saraki,ma'abocin tsaho,wanda murjewar jikinsa ta hana bayyanuwar tsayin da Allah yayi masa yadda za'a fahimta,ya mallaki kalar fatar da hausawa suke kira da wankan tarwada amma irin wankan tarwadan nan dake da haske,taqi kadan zai dada ka kirayeshi da farar fata,matsakaicin kyau gareshi,saidai abubuwa guda biyu sun taru sun qarawa siffarsa kyau da cikar haiba KWARJINI da yake dashi,da kuma wasu lumsassun idanuwa masu kama da na me jin bacci. Yana da sanyin murya,irin sanyin da bai hana bayyanar cikar mazantakarsa gami da jarumtarsa ba,sam ba miskili bane,kamar yadda wasu mutane da yawa suke masa kallon haka,abubuwa ne guda biyu suka sanya suke masa wannan kallon,baya shiga sabgar da bata shafeshi ba,bashi da shishshigi sam,hakanan bai fiya magana kan abinda yasan yana da qarancin muhimmanci,koma kwata kwata bashi da muhimmancin,yana da kamewa da wata irin nutsuwa mai jan hankali,yana da zurfin ciki a yawancin lokuta,komai nasa bisa tsari da dacewa yake tafiya,shi yasa wasu ke ganin abune mai wuyar gaske iya zama dashi,abunda basu sani ba shine,zama dashi din wani abune mai dadi ga duk wanda ya soma mu'amala dashi. Akwai boyayyun halayyensa da ba kowanne ya sanshi dasu ba,ciki kuwa harda makusantansa,yana da tausayi yana da taimako,a wasu abubuwan ba zaka taba tsammanin cewa ya fito daga gidan girma da arziqi irin wannan ba,rayuwa sassauqa da yakan gudanar....saidai,matuqar kazo lokacin da yake kan tsininsa,zaka dauka baida kirki ko kadan. Muhammad samir,da namiji guda daya tilo da Allah ya mallakawa professor rashid usman azare,wanda tarin banbamce babancen halaye da zabi na rayuwa yaso ya zama babban shinge tsakaninsa da mahaifinsa da samun dukkan wata yarda da qauna tashi. "welcome son.....na tsammaci yau ba zaka fita ba?,naji shurun yayi yawa,duk da na kira wayarka taqi shiga....saina zabi na barka ba tare dana aika ba,wala'alla kana bacci ne kada a katse maka shi" hajiya jidda wadda auke kira da mommy ta fada,dukkan kulawarta tana tare da samir din,fuskarta na fidda wani kalar murmushi dake nuna farincikin dake tattare da ita na ganin fitowar samir din,kamar yaune lokaci na farko data fara ganinsa,ko kuma wani gari yayi tafiya mai nisan zango ya dawo a yau din. Washewa fuskarsa tayi da wani murmushi mai aji,ya soma qoqarin jan kujera daya don yiwa kansa mazauni sannan ya amsa mata "A'ah anna....bani da wani abu da zan aiwatar ne da safen....shi yasa na zabi na huta kafin na fita yau,don jiya ban samu zama yadda naso ba" ya qarashe maganar yana duqawa zuwa qasa gefan mahaifinsa,muryarsa cike da tsantsar ladabi ya furta "Barka da asuba daddy" kallo daya yayi masa ya maida kansa ga abincinsa yana amsa masa da "Ka tashi lafiya?" "Lafiya alhmdlh" sai ya maida dubansa ga mommy wato hajiya jidda "Barka da asuba mommy" "Barka kadai yarona....da fatan ka tashi lafiya" "lafiya qalau alhdmdlh" "To ma sha Allah" ta amsa masa fuskarta na nuna jin dadin samunsa lafiya da tayi kamar kullum,saita miqe da kanta ta fara bude dukkan wani kwano dake saman teburin sanda qannensa ke gaisheshi daya bayan daya yana amsa musu,kamar yadda ta saba tanayi kullum kwanan duniya matuqar ya halarci wajen cin abinci,zata bude masa dukka ya zaba abinda yakeson ci,don wani lokaci ma abinda ya zaba yana so shi za'a dafa kowa da kowa,koda ba zabinka kenan ba,tun suna yiwa mommy mita da qorafi har ya zame musu jiki. "Me zakaci a ciki samir?,Allah yasa akwai wanda ya dace da ra'ayinka" mommy ta fada tana murmushi kamar kullum,wanda baka rabata dashi saman fuskarta,sai a sannan alhj mukhtar yayi magana tun fitowar samir din,idanuwansa saman fuskar mommy,wani abu na yawo saman zuciyarsa,wani abu mai nauyin daya wuce a aunashi a mizani "Ki kalleshi mana da kyau,ba yau ko jiya ko shekaran jiya aka haifeshi ba,amma kullum kina kallonshi ne kamar ranar nan da aka miqo miki shi cikin tsumman goyo,a qa'ida ya isa aure,a kuma qa'idance kamata yayi ace a gaban matarsa yake" kanta ta langabe tana duban professor "Haba daddy.....kai kake ma samir kallon yayi girma har haka,ni kam a wajena har yanzu kamar yaron goye nake kallonsa.....bugu da qari ma daddy idan ba'a kula da samir ba...wa zamu kula dashi?,karka manta shi kadai Allah ya bamu...." "Abbaaaa"sautin muryar jawahir tayi kutse cikin maganar mummy,sautin daya fito a narke,kamar me shirin sakin kuka,waiwayawa suka dukka suna kallonta,sai daddyn ya daga hannayensa duka biyun kafin yace "You see.....su kuma daughters dina ki kaisu ina?" Murmushi ya saki,wani abu na lilo can qasan ranta da zuciyarta "Dole dukkaninsu subi bayan samir a wajena" a nutse tsaf daddyn ya waiwaya ya dubi samir din sosai kuma kai tsaye,duk da idanun samir din na kai kawo ne tsakanin yan uwansa,fuskarsa tana fitar da wani murmushi me sanyi mai kuma cike da nutsuwa "Gwara da kika ce a wajenki,ta ina yaronkin zai kama qafar yarana?,yaron naki da ba jin magana yake ba,wanda ya sarayar da alqiblarsa,babu wanda ya gane har yau inda yasa gaba" samir ya gama fahimtar qorafinsa na jiya da yaketa gujewa shi yakeson sokowa a yau din,saiya dan sunkui da kansa,kana ya daga kan nasa,yana muradun rushe wannan maganar,don baida sha'awar ci gaba da yinta,don haka cikin girmamawa yace da ita "Kome akayi yau din zanci mommy,ki zauna ki huta....zan zuba da kaina,ina sauri ne ma,jiya akwai taron da zanyi da ma'aikata,ban samu zama ba nasa aka maidashi yau"ya fada yana miqa hannu zai hada tea. jawahir ce ta miqe da hanzari ya dauka cup din ta soma hada masa,mummy tadan kalleta saita dauke kanta "yi a hankali sarkin rawar kai,kada ki zuba masa a jiki"mummyn ta fadi sanda jawahir ke aje masa tea din,murmushi yayi ya dauka yana.kaiwa bakinsa,shi yasa yakeson autar tasu,sosai take nuna kumawa kan dukkan wani abu daya shefeshi,ba kamar 'yar uwarta ba,wadda har yanzu bai fuskanci inda ta sanya gaba ba,shegen sin jiki gayunbanza,izgili da yiwa.mutane kallon banza hadi da rashi iya magana dukka najwa ta hadasu,abu daya da yasa bata iya wani kyakkyawan abu a gabansa ko a kansa shine,baya daukar raini,kamar yadda baya raina kowa,tafi kowa sanin ainihin wayeshi,wannan shine ya ke mata waigi a kansa. miqewa prof yayi yana yagar tissue "idan ka dawo yau din bayan sallar isha'i,ka sameni zamuyi magana dakai" "ok daddy"ya fada da muryarsa mai dadi,sannan yaci gaba da kurbar tea din a nutse. cup din ya ajjiye bayan ya gama amsa wata waya,mummy ta dubeshi "bakaci komai bafa samir?" "mommy,am late" "a maka packaging ka tafi dashi mana,ya zaka fita aiki babu cikakken abinci a cikinka" "ba komai mommy,zan nemi wani abun naci idan na samu break" "a'ah..,.najwa......maza,shiga kitchen ki cewa baraka ta baki warmers qanana"fuska tadan bata "Mommy.....yace a barshi fa"idanu ta fitar mata gaba daya "ni kuma nace ki dauko....."tuni ta miqe ma kafin mummyn ta qarasa bayani,saboda wani kallo da samir din ya jefeta dashi,harta soma takawa tajishi yana fadin "dawo ki zauna,jawahir.....jeki dauko,guda daya ma is ok"taf tsoro ya cika cikinta,saboda ba kasafai yake bi takanta ba,tana tsoron irin wannan kallon nasa,saita ci gaba da tafiya ta miqe zuwa kitchen din,wata tsawa ya watsa.mata wadda ta sanyata tsaiwa,ta kuma kasa juyowa,har jawahir tazo ta wuceta da saurinta kuwa kamar yadda ya umarceta bata motsa ba har sai dataji fitarsa yana cewa idan an zuba jawahir din ta miqa masa yana cikin mota. koda ta koma harara Mommy ta bita da ita,sannan ta rufeta da fada,tana kallon fuskar jawahir,da alama taji dadin yadda mummyn ta balbaleta da fadan,sai tayi sakato,mamaki fal ranta,me yasa mummy ke mata fada da zafi har haka?,bata tanka ba har jawahir ta fice daga parlour din,saita dauki jakarta dake gefe wanda dama shirin makaranta tayi,kawai ta fice a falon. yana daga zaune a driver seat ta buda gidan baya ta sanya warmer din sannan ta rufe,saita zagayo inda yake zaune din,fuskarta da murmushi "a dawo lafya yaya" "Allah yasa"ya amsa yana shirin rufe murfin motar,saidai jawahir din bata matsa ba tana tsaye still a wajen,kansa ya daga bayan ya sauke glass din motar yana dubanta "ya akayi auta?"murmushi ta sakeyi "kayi haquri yaya da abinda ya najwa keyi....ni kaina bansan meya canza ba"qawataccen murmushin gefan baki ya saki "karki damu, she's still my sister.....ina tunanin tana da damuwa,but we will talk later"kaita gyada kawai kana taja baya,ya tada motar a nutse,ya qarasa bakin gate ya danna horn,idanunsa saman fuskar mai gadinsu da yaketa marmashe gyada yana zubawa cikin jiqaqqen garin kwaki,ya taso da hanzari ya durfafi qofar zai budeta,sai samir ya yafitoshi da hannu,don haka yabar bude qofar ya iskoshi da sauri ya iso bakin window inda samir ke zaune "Allah ya taimaki saraki" "an tashi lpy baba" "lafiya qalau dana" "abinda aka dafa ne yau baba bai maka ba,na ganka da garinka harda gyada?"samir ya tambayeshi yana dan murmushi,murmushin shima yayi,a ladabce yace "ko daya mai gida,yau dai bamu samu abun karin bane"fuskarsa cike taf da mamaki bayan yadan yamutsata yace "kamar yaya?,kune baku da sha'awar ci?"da sauri ya girgiza kai "ko daya,Allah ya taimakeka wazaiqi abinci irin na gidan professor?,inajin dai yau da gobe ne irin ta bahaushe,wani lokaci ku samu,wani lokacin kuma saidai kowa ya siya abinda yake dashi"baice komai ba saiya duba agogon hannunsa,bashi da lokaci da cikin gidan zai koma,bai zaci wasu cikin gida dake rayuwa tare dasu ba'a basu abinci ba,saiya bude aljihun gaban motarsa ya aciro yan dubu dubu guda biyu ya miqa masa "gashi,ka ajjiye wancan ka siya wani abun me dumi kaci"hannu bibbiyu yasa ya amsa kudin yana zabga masa godiya,sannan ya tafi qofar ya dage masa gate din,yaja motar da dan hanzari ya fice. 1/7/22, 08:18 - Buhainat: Halin Girma     9 *Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107*  I'm on Instagram as @zafafabiyar5. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1ft46u5twk6r3&utm_content=nj79azb *** Yana jin sanda motar ta tsaya, ya juyo da sauri ya kalle shi, hankalin sa na kan wayar sa yana dannawa, fuskar sa a hade tsaf babu alamun wasa ko kadan, tsoro ne ya sake shigar Khalil din sosai, yaji kamar yayi ta kurma ihu yana neman taimako, amma kuma ya san babu wanda zai taimaka masa musamman idan aka zo aka ga wanda yake tare dasu.   Ji yayi an murda handle din bangaren sa, yayi saurin matsowa sai gashi a tsakiyar motar, daf da Moh, wani banzan kallo ya watsa masa da ya sakashi saurin komawa inda yake zaune. "Come ou!" Wani murdadden soja yace matsa bayan kofar ta gama budewa, idanu ya soma rabawa tsakanin Moh da sojan fuskar sa ta nuna matukar tashin hankalin da ya shiga "I said come out!" Ya daka masa tsawa da ta saka shi saurin fitowa "Dan Allah Oga kayi hakuri, wallahi sharrin shaidan ne da rashin hankali, duk abinda na farfada ba wai har zuciya ta bane wallahi." Ya hau magiya yana kallon Moh da yayi kamar baya wajen, damtsen hannun sa sojan ya kama ya shiga jan sa har zuwa wata kofa in da ya hangi sojoji sun fi su ashirin suna tsalle tsalle a wajen. "Oga dan Allah ka bawa oganku hakuri Dan Allah!" "Kasan waye oga kuwa?" Da sauri ya girgiza kansa "Ban sani ba wallahi, rashin sani ya jawo nayi masa abinda nayi amsa amma dan Allah na tuba yayi hakuri." Dariya sojan ya saka sosai " Baka da hankali amma, ka zo har nan wajen kayi tunanin zamu kyale ka, ka tafi free? Nah sai mun dan sassamaka yadda gobe ba zaka kara ba. " " Dan Allah nace fa? Ka tayani bawa ogan hakuri. " " Naka wasa ne. " Yayi gaba yana rik'e dashi, yanayin rikon da yayi masa da yanayin jikin Khalil din zai baka dariya sosai, dama bashi da wani jiki sosai gashi kuma a hannun manyan maza, wani daki ya kaishi sannan ya sake shi yana masa dariyar mugunta "Zaka kwashi kashin ka hannu yau, wallahi Oga zai iya sawa a batar da kai a k'asar nan, kasan waye kuwa? Tab." Jawo masa kofar yayi ya rufe ta har da key yana kwasar dariya.   Chan karshen dakin yaje ya tsugunna yana jin dana sanin barin zancen da yayi, dama a maida baya da ya goge duk abun da yace ma Muhammad din cikin rashin sani. Ji yayi cikin sa na kara alamar ya lalace, ya tabbatar bala'in tsoro da firgicin da ya shiga ne ya saka cikin nasa lalacewa. Mikewa yayi da sauri ya hau zagaye a dakin yana maimaita "Innalillah wa inna ilaihi rajiun." Ji yayi ana murda key din dakin, ya tsaya yana kallon kofar cikin tsoro. Captain Moh ne ya shigo sojoji biyu na biye dashi a bayan sa, daya rik'e da kujera yazo ya ajiye masa ya zauna yana wa Khalil murmush "Alhaji Khalil barka da warhaka." "Dan Allah dan Allah kayi hakuri, wallahi sharrin shaidan ne da yarinta wallahi amma ba zan sake ba." "Haba Khalil, so soon haka? Ka sani ko sojan gona ne ni, kasan fa talaka da samun wuri." "Wallahi ni dai ba zan sake ba, kayi min rai, mahaifiyta da ni ta dogara, dan Allah." "Calm down magana zamuyi, ka nutsu ka saurare ni, warning ne me hade da dokoki, ina fatan zaka bud'e kunnuwan ka kaji ni sosai." "Ina ji wallahi." "Babu kai babu abinda ya zama mallaki na, Ina nufin Fatima, ko a hanya ka hadu karka taba nuna ka santa balle har magana ta hada ku, a da nayi niyyar barka ka gwada sa'ar ka akanta, amma kuma a yanzu na gama yanke wa, baka kai na nemi abu tare da kai ba, dan haka ko son ta zai kashe ka sai dai ka hakura... " " Na biyu, a yau ba sai gobe ba zaka wuce in da ka fito, ba tare da ka bud'e bakin ka kace wa kowa komai ba, ina nufin, bakin ka ya zama kanin kafar ka, kar naji zancen a wajen kowa ciki har da ita yayarta ka da bata tsoron Allah. " " Last but not the list ka koma bakin aikin ka, ka rik'e mutuncin ka sannan bakai ba wulakanta kowa. " " Duk abinda ka fad'a wallahi zanyi, nayi alkawari, ni dai kar ka raba ni da mahaifiyata wallahi bata da kowa sai ni. " " I'm done with you, gashi nan take him back, ku tabbatar ya bar Kano kafin karfe shida na yamma. " Juyawa yayi cikin wani irin taku ya fice daga wajen, yana fita sukayi kansa " Ai wallahi ba zaka shigo nan a banza ka fita bamu ci ladan ka ba. " Wani soja yace yana kai masa rankwashi. " Tashi kayi frog jump. " Dayan ya daka masa tsawa yana zaro belt dinsa. Da sauri ya hau yi yana hada zufa su kuma suna tuntsura dariya, sai da suka gajiyar dashi sosai sannan suka fito dashi suka sashi a mota suka maidashi har kofar gidan suka ajiye sannan suka tafi. ***Abba na zaune yaji text message ya shigo wayar sa, tunanin sa ma ko alert ne ya bud'e sai yaga sako daga bakuwar number da be sani ba, bud'e message din yayi ya soma karantawa _" Dr. barka da warhaka, ya aiki? Allah ya taimaka. Dama wata magana nake son yi akan fatima, ina rokon alfarmar daka saka ido sosai akan abinda yake faruwa a cikin gidan, in sha Allah zaka gano wani abu da ya dade yana faruwa ba tare da sanin ka ba. Sai anjima a huta lafiya. "_    maimaita karanta sakon ya dinga yi yana kokarin daidaita tunanin sa waje guda, waye ko wace wannan? Me sakon yake nufi? Me ya faru da Fatima din? Duk wadannan tambayoyin ne suka shiga yi masa yawo aka, be san me yasa ba, kawai sai yaji hankalin sa ya kasa kwanciya da abinda ya karanta. Tashi yayi ya fito zuwa falon gidan, ya k'wala kiran Iman din. Zeenat ce ta fito " Ina Ummi? " " Ina ga tana wajen Gaji. " " Je ki kira min ita. " Fita tayi shi kuma ya cigaba da tsaiwa awajen har suka shigo a tare. " Ki same ni a daki na. " Yace yana juyawa tabi bayanshi, dariyar mugunta Zeenat tayi a tunanin ta wani laifin Iman din tayi dan sosai yanayin Abban ya nuna bacin rai. A gefen gadon sa ya zauna, ta samu chan gefe daga kasa ta rakube tana tunanin dalilin kiran. " Kina jina Uwata? Kina da wata matsala wacce ban sani ba? " Girgiza kanta tayi " A ah Abba babu. " " Kalle ni nan, ni ne mahaifin ki, baki da wanda yafi ni bayan mahaifiyar ki, ki fad'a min gaskiya idan akwai wani abu da yake damunki." Zuciyar ta ce tayi rauni, taji kuka na taho mata, ta k'asa rike shi kawai ta fashe da kuka. Dafe kansa Abban yayi, ya shiga tunanin me yake faruwa? Wanne irin abu ne haka da har shi ya kasa ganewa? "Fatima..." Ya kira ainihin sunan ta a karo na farko a rayuwar ta "Na'am." Ta amsa cikin muryar kuka "Kowanne bawa da irin yadda rayuwa take zuwar masa, kiyi hakuri zanyi bincike, sannan akwai shiri da nake yi na kaiki wajen mahaifiyar ki da zarar maganar bikin ku ta tabbata, nayi mata alkawarin kai mata ke da zarar lokacin auren ki yayi, mahaifiyar ki na son ki fiye da yadda take son kanta, ki rik'e wannan." " Tashi kije kinji, ki daina kukan haka." Tashi tayi bayan tace " Nagode Abba." Ta fice ya bita da kallo yana jin kamar be kyauta mata ba. Dakin su ta wuce ta tarar da Zeenat na waya har da shewa, juyawa tayi zuwa store ta zauna a gefen katifar ta, tayi kuka sosai har sai da taji babu abinda yayi saura a zuciyar ta. Tsawon lokaci ta sauka a ciki har sai da taji maganar Mama tana fad'a a waya anan ta gane ta dawo dan dazu bata gidan. Tashi tayi ta fice ta kofar baya bayan ta gyara fuskar ta a sink din kitchen. ***Zama Mama tayi tana sababi akan tafiyar Khalil din babu sanarwa, sai dai a k'asan zuciyar ta taji dadin hakan domin a kalla hankalin sa zai dauke daga kan Iman din har a gama magana da shi dayan da yazo. Abba ne ya shigo ya sameta tana zaune , ya zauna a gefenta sai tasha jinin jikin ta musamman da ta gama sanin halin sa tsaf. "Me yasa kika ce min Ibrahim ba da gaske yake akan maganar Ummi ba, sannan shi kuma yaje ya samu Yaya da maganar." Yadda ta zabura yaso bawa Abban mamaki. "Khalil din ne yaje wajen Yaya? Yaushe akayi haka? Me yayan yace masa?" "Duk ba wannan na tambaye ki ba, baki bani amsa ta ba." "Toh toh ai gani nayi shi Khalil ba yanzu zai yi aure ba, su kuma yaran nan yanzu ne muke so mu aurar dasu, bana so Zeenat ta tafi da bar Iman tunda kaga tare suke komai, shiyasa nace gwara wanda ya shirya." "Haka ne kuma." Yace yana mata wani irin kallo da ya sakata tunani sosai "Toh hakan yayi ai, Ina fatan dai zeenatu ta sallami yaron nan Bashir ko? Dan ina nan akan bakana ba zan bashi ba." "Dan Allah Dr ka bar wannan maganar, tunda tana son shi kayi hakuri kawai ayi tunda an wuce zamanin da za'a yi wa yara auren dole." Girgiza mata kai yayi yana dakatar da ita "Wannan maganar taki shirme ce, musulunci mu ya bawa damar zaba wa yayanmu mazaje na gari, dan haka ban yarda da Bashir ba, idan akwai wani ta kawo shi." Ya tashi ya fice ransa na baci da yadda maganar Bashir din taki karewa, sam Hajara bata shirya gane abunda yake hango musu ba, eh hango musu tunda duk in da aka je aka jawo ita uwa sai tafi cutuwa da abinda zai samu yarta. ***Text message biyu ya tura a lokaci daya, address din sa da Abba yace ya tura masa ta message sai kuma message din da yayi wa Abban Iman din, wanda yake ganin shine kadai hanyar da zai bi wajen hana Maman sanin duk wani abu akan Iman din, ya tabbata daga lokacin Abban zai saka ido sosai, ba kuma za'a dau lokaci ba zai gano komai, shi kuma sai yayi amfani da wannan damar ya nemi alfarmar barin komai ya zama sirri a tsakanin su iyaye maza, domin dama su iyaye maza baa sansu da ratatin zance ba, ba kasafai ma suke zama suyi ta magana anyhow ba, ya tabbata idan har hakan ta yiwu toh zai samu abinda yake so, zai kuma tabbatar da Fatiman sa ta samu gatan da bata taba tunani ko hasashen samun sa ba. ***Tunani Abba ya fad'a ganin address din da Muhammad ya turo masa a matsayin in da yake,Emir Palace Kano, Emir Palace Adamawa-Yola, me hakan ke nufi? Kiran Abban su Fatiman yayi yazo ya same shi a part din sa, ya nuna masa message din sannan ya kira sauran yan uwan su Abba Musa suka hau tattaunawa akan abinda ya kamata su yi. Dama chan Abba Musan yana siyasa sosai, sai sukayi shawara akan shi ne zai wuce gaba wajen binciken waye Muhammad din a cikin kwana uku kachal. Haka kuwa akayi, washegari ya same su da maganar da ta yi matukar basu mamaki. A yadda suka sani idan wani daga cikin irin wannan yaga yarinya yana so, kawai aikawa ake iyayenta suzo ayi magana a fadar sarkin, a matsayin shi sarki dama uban kowa ne, sai suga ga banbanci inda Muhammad din yazo kai tsaye ba tare da ya nuna shi din waye ba, ba kuma tare da ya nuna karfin iko na mulki ba, hanyar da ta dace da kowa yake bi wajen neman aure shima ita yabi.   A cikin su babu wanda be yi amanna da maganar ba, musamman binciken da Abba Musan yayi da irin yabon da Muhammad din ya samu daga wajen mutane da dama musamman mazauna masarautar.     Shiru Abba yayi bayan kowa ya gama tofa albarkacin bakin sa, aka bashi dama a matsayin sa na mahaifin Iman din, "Bakwa ganin idan iyayen yaron nan suka san in da yazo neman aure zasu kyale shi, duba da mu din ba wasu bane akan irin girma da nasabar gidan da ya fito." "Idan har a yadda bincike na ya nuna min ne, iyayen sa basu da matsala masu son talakawan su ne, dan haka muyi addua kawai in sha Allah alkhairi ne." "Shikenan, Allah ya tabbatar mana da alkhairi,." "Yanzu kayi magana, Amin ya Allah." " Ina neman alfarma daya, da mu bar maganar nan a tsakanin mu zuwa muga abinda Allah yayi." " Hakan yayi, Allah ya shige mana gaba." Suka hada baki a tare, sai kuma suka shiga wata hirar tunda daman su dan dade basu yi irin wannan zaman ba, anan duk suka ci abinci a tare sannan kowa ya tafi zuwa sabgar sa. Aka bar Yaya a zuwan zai kira Muhammad din da daddare ya sanar dashi ya bashi izinin yazo yaga Fatiman su daidaita, da daddaren bayan ya gama komai ya turawa Muhammad din text message akan ya cigaba da zuwa. Muhammad na zaune shi da Musaddik suna kallon video da ya saka akayi wa Khalil suna kwasar dariya text din ya shigo, tashi yayi ya daka tsalle kafin yace "Yess!!! " Ya akayi?" " Karfe nawa yanzu?" Yace yana kallon agogon falon " Opss Ashe dare ya fara, ba dan ba dan ba da yanzu zanje na ganta, amma ba komai kafin na wuce Abuja zan tsaya na fara ganin ta." " Me faru wai." " Karanta!" Ya mik'a masa wayar " Ah congratulations angon fatiti, Allah ya tabbatar mana da alkhairi." Rik'e k'ugu yayi yana hararar sa " Allah ka sake bata mana suna sai na saka frog jump, kaji ma na ratse." " Kut! Allah fa ka raina ni Moh, komai sai kace zaka sani frog jump an fad'a ma nima kamar wadanchan dogs din naka ne na bakin gate." " Ka dai kula, kana magana ne da Captain Muhammad Ahmad Santuraki, Captain Moh!" " Whatever, ni dai muhammadu na sani, ba wani bragging da zaka min." " Zaka gane ne idan na dauke ka na je na jefa wa mayunwatan zakunan nan na barack, ba zaka sake kiran sunana gatsal ba." " An gaya ma kowa irin khalil ne? Lusari!" Dariya suka saka Muhammad ya shiga gwada yadda Khalil din yake, suka sake tuntsurewa da dariya suka tafa " Ashe farar kura ce a wajen, sai uban cika baki dan iskan yaro, gobe ma ya sake, naso ka dan saka su sun sassama masa jiki wallahi,." " A hakan ma nasan sai sunci zalinsa ai." " Wicked soul!" Yace yana dariya " Naji, bari naje na kira Baby na, naji voice dinta me dadi kafin gobe naje na ganta, dan yanzu ina da license, na matsu na ganmu tare, muna yawo a garin nan cikin mota my hands in to her's, ga cool music na tashi Malam, wow love in the air." " Toh Mr Romeo, Allah ya kaimu dai zamuyi kallo, yadda kake son ta Allah yasa tana maka ko rabin sa ne." " I don't care, as long as munyi aure, zan koya mata yadda zata so ni." " We shall see." ***Ruwan zafi ne a katon bawo, Khalil na zaune a gaban ruwan hajiyar su na danna masa bayansa, gaba daya jikin sa ciwo yake kafarsa kamar zata cire yake ji, babu irin tambayar da batayi masa akan me ya same shi ba amma yaki fad'a mata, haka Mama ta bugu tana fad'an tafiyar Khalil din hajiyar ta fad'a mata a yadda ya dawo, kuma yaki cewa komai. Yana jin su har suka gama ya tashi ya koma dakin sa ya kwanta yana tariyo abinda ya faru cikin tausayin kansa. Shi ya jawo yana takama da shegen bakin sa ya je ya kaishi ya baro, dama an fad'a mutum ya kiyayi harshen sa, akwai hadisi guda da akayi magana akan harshe da kiyayar sa, yaga izina a kansa, gashi bashi da damar fadawa wani abinda ya faru domin yasan shi za'a yi wa dariya, ko da muhammadu a iya soja ya tsaya matsayin da yake kai ya isa ya taka shi son ransa ba kuma wanda ya isa yace dan me? Balle ganowar da yayi waye Muhammad din, anan ya gane bakin rijiya ba wajen wasan yaro bane, shi din ma ganganci ne da kuruciya. Eh toh kuruciya mana tunda dai yasan a girme Muhammad din zai girma shi dole ya fishi hankali da komai. Abu daya ne zai hana shi walwala, yadda zai yi da tarin soyayyar ta, gashi yayi masa kashedin ko a hanya babu shi babu ita, ya kuma tabbatar idan har ya kuskura yayi wani abu, za'a iya neman shi ma baki daya a rasa, dan masu kudin nan yasan ba wani abu bane a wajen su su batar da mutum bat, har abada a daina jin labarin sa.    Tagumi ya rafka yana jin kamar yayi ta kurma ihu ko yaji sassaucin radadin da zuciyar sa ke masa. Allah sarki Khalil 😂 1/9/22, 10:17 - Buhainat: Halin Girma     10 *Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107*  I'm on Instagram as @zafafabiyar5. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1ft46u5twk6r3&utm_content=nj79azb ***Be ji sallamar ta ba, sai ganin ta yayi kawai a dakin bayan a zahiri tayi sallamar amma saboda baki daya hankalin sa na ga tunani shiyasa be ji ba sam. "Ya Khalil wai a kawo maka abinci..." Ai kafin ta karasa ya daka mata uwar tsawa "Uban abincin, dallah Malama karki dame ni." "Toh... Me yayi zafi? Hajiya ce ta aiko ni ai." "Fitar min daga daki!" Yace yana tasowa, da gudu ta juya tana dariya, sai da ta ga ta fice sannan ta daga murya tace "Bani na kar zomon ba..." Ransa ne ya sake baci, ya bigi kofa yana komawa ya fad'a saman katifar sa yana jin kamar yayi ta cizon kansa. A falo ta samu Hajiya ta zauna tana haki "Allah ya taimake ni na kusa cin duka, daga tambaya kawai ya hayayyako min Hajiya." "Toh wai ko dai Khalil tsokana yayo ne aka tattaka shi, kinsan fa Khalil ba dai tsokana da cika baki ba." "Alamu dai sun nuna Hajiya, fad'a ya takalo da yafi karfin sa wallahi, gashi nan yaki fad'an abinda ya faru." "Toh Allah ya kyauta " Hajiyan tace tana tashi ta fita zuwa dakin nasa. ***Tana tsaye a bayan kitchen dinsu, wanki ta gama tana ta sauri saboda kwana biyu bata maida hankali zuwa islamiyya saboda abubuwan da suka sako kai, tana wankin tana tunanin maganar da sukayi da Abba da ta zama tamkar bitar karatu haka take yin sa, takun tafiya taji, ta juyo sai taga Abban a tsaye yana duban ta, da sauri ta dan russuna, "Abba sannu da zuwa." "Wanki ake ne?" "Na'am.?" Tace tana zaro ido sanin cewa ba da sanin sa take wankin ba, musamman ya samu almajiri yake wanke musu kaya ita da Zeenat da Marwan yake biyan shi ta hannun Mama, duk da yasan dole zasuyi wanki irin kayan ciki da abubuwan da ba za'a iya bawa me wanki ba, amma kuma tarin kayan da ya gani a wajen da ya gane na Marwan ne sai wasu na Maman ya saka ransa mummunan baci, har a jiya sai da Maman ta karbi kudin wanki a wajen sa da zumar yau me wankin zaizo karbar kudin sa ya kuma bata babu musu. Yanayin sanyin garin zai yi wuya wajen wanki musamman da tun da dadewa yasan fatar Iman din bata son wahala idan tayi wanki hannun ta kanyi ja sosai, shi kuma Allah ya hore masa son yaya Kuma gasu ba wai yawa ne dasu ba shiyasa duk wani aikin wahala baya son siyi duk da ba wai kwata kwata ba zasuyi komai ba, amma kamar wanki yana ganin be kamata shima a saka shi a cikin aikin mata ba, mata na wahala da aikin gida kula da yara da girki wankin aka dauke musu zasu samu sassauci. Matsowa yayi ya sake leka kayan kafin ya girgiza kansa ya juya bayan yace "Ki bar wankin nan kizo ki wuce ciki." Sakalo tayi a tsaye tsoro na kamata "Bakya ji ne?" Ya daka mata tsawa, da sauri ta bi bayansa har cikin gidan, dakin su taga ya wuce ya kwankwasa sannan ya tsaya "Waye?" Zeenat tace tana daga kwance cikin rufa, a yadda tayi maganar zaka gane knocking din ya takura ta, sake kwankwasa wa yayi sannan ya tura kofar da sallama, be shiga ba, ya tsaya a kofar yana karewa dakin kallo, gadon zuwa katifar dake shinfid'e a kasa da ta tabbatar masa da ta Iman din ce. Tuna lokacin da ya bada kudin gadajen nasu yace a siyawa kowa nasa amma sai Mama tace daya ya ishesu me dan girma saboda hakan zai sake shakuwa tsakanin su,da wannan yayi amfani a ganin sa hakan ne ya kuma dauki hakan a matsayin soyayyar da Maman ke wa yar tasa. A yadda yake jin zuciyar sa a lokacin zai iya yin komai, sai kawai ya fice daga gidan gaba daya ba tare da ya koma daki ba. Tsoro ne ya kama Iman musamman da bata san me zata ce wa Maman ba akan wankin, shiryawa tayi cike da fargaba ta tafi makarantar tana fatan koma menene ya taso ya zama daidia kafin ta dawo dan a rayuwar ta, ta tsani tashin hankali ko kad'an. Rabi da kwata bata gane kan karatun ba, haka dai ta taho gidan tana ta zulumi, tana shigowa ta ganshi a tsaye ya harde hannayen sa a gadon bayan sa yana kallon kofar shigowar. Shigar jikin sa ta bi da kallo zuwa gyaran da yayiwa fuskar sa, murmushin da ta gani kwance a fuskar tasa, ya saka ta samun nutsuwa har ta karaso wajen da yake a tsaye. "Ashe kina kusa da shigowa, naji a jikina." Murmushi tayi kafin tace "Sannu da zuwa." "Yawwa, ya hanya?" "Alhamdulillah wallahi.* " Akwai wanda ya kalleki da kina tahowa? Idan akwai fad'a min naje na same shi." Sosai ya bata dariya, " Kai... Babu kowa fa, ya gida yasu Mama?" " Mama? Ammi muke ce mata, tana nan lafiya tace ma na gaishe ki, na gaida wacce ta kwace mata yaronta kafin tazo haka tace." Rufe fuskar ta tayi tayi yar dariya " Allah sarki, ina amsawa nagode." " Itama ta gode, tace ta matsu ta ganki." "Watarana zata ganni in Sha Allah." "In Sha Allah, very soon." "Abba Babba yace idan kazo ka shiga ciki." " Da gaske? Kice na zama dan gatan Abba." Dariya tayi " Naga alama kam, Abba ya yarda da kai sosai." " Allah sarki, ai yana da kirki sosai." " Sosai." Tace " Bari na bud'e maka, chan ne seat room din sa." " Owk." Yace ya harde a jikin ginin yana kallonta, har ta bud'e ta dawo sannan ya bita a baya yana admiring steps dinta zuwa ciki. A kofar dake farkon kofar ya zauna ita kuma ta shiga ciki, yana zama Aliyu ya shigo da ruwa a tray, ya ajiye ya gaishe shi sannan ya fita, ruwan ya dauka ya sha sosai sannan ya kalle ta, gefe take kallo tana wasa da jikin kujerar da take kai. " Zahraah, tafiya ce ta kamani, ba zan iya wucewa ban sanar miki ba, ba wani dadewa zan ba in sha Allah, inaso kafin lokacin da zan dawo mu sake fahimtar juna sosai, idan na dawo sai a shigo da magana me karfi, bana so a ja lokacin." " Allah ya kiyaye ya tsare, ya dawo da kai lafiya." " Amin ya Allah, Amin Amin Zahraah Nagode" Shiru ne ya dan shiga tsakani, shi yana kallon ta yana sake ganin ainihin kyawun ta, ita kuma ta tafi tunanin Allah yasa ya dawo din kar taji shiru idan ya tafi, har zuciyar ta bata son tafiyar tasa, amma kuma ya zatayi? Ba zata hanashi ba ai. "Ina wannan yayan naki da muka hadu ranar nan? Har ya korar min ke?" " Uncle Khalil?" Tayi dariya " Auw sunan shi kenan." " Eh kanin Mama ne, a nan gidan ya taso kafin ya koma gida." Gid'a kansa yayi kamar be sani ba " Shiyasa ya nuna min iko kenan." " Uhum." Tace kawai bata ce komai ba. "Yana ina kuwa?" "Kamar dai ya koma, naji dai mama na fad'an ya tafi be sanar ba." "Ai be isa ya sanar." "Na'am?" Tace tana kallon sa "Sorry ba komai." Ya maze kamar be ce komai ba, be san maganar zata fito ba shima. " Bari na gudu, kar nayi rana." Mikewa tayi " Daga nan zaka wuce?" " Eh gaskiya, idan na koma gida na koma baya." " Ok ina zuwa." Ta fita ya tashi ya dan zagaye falon yana observing komai na ciki, yana tsaye jikin wani frame ta shigo dauke da leda ta mika masa tana dan russunawa " Gashi ka kaiwa Ammi, ina gaishe ta." Rik'e ledar yayi yana kallon ta, tayi saurin dauke kanta k'asa ta sakar masa ledar gabanta na faduwa. " I love you." Ya samu kansa da whispering cikin muryar da tayi masifar shigewa ciki, wani irin feeling taji, sarai ta jishi sai tayi kamar bata ji ba, ta ja baya sosai tana diriricewa, shi kansa wani iri yake ji, be taba tunanin haka daga gareta ba, da tasan yadda Ammi take a wajen sa, da kuma yadda sakon nan yayi nasarar kara masa son ta ninkin ba ninkin, da tun ranar da ya fara zuwa tayi, kasa matsawa daga in da yake yayi, sai murmushi yake shi kadai. "Nagode sosai, Ammi ta gode." "Ba komai." Tace tana jin nauyi da kunyar yadda yayi "Zan tafi, ki kula da kanki kinji? Karki yarda wani ya bata miki rai, kin fi karfin haka, ke din ta daban ce, ta musamman ce." "In Sha Allah." Tace tana jin dadi , a kalla idan tana tare dashi tana jin cewa itama tana da yanci, sannan takai matsayin a so ta. Ta cikin idon sa yake ta kokarin aika mata da sakon sa, sakon da yake so ya tafi ya bar mata, irin me zafin nan da zatayi wuyar dauke shi daga tunanin ta, sau daya ya samu nasarar aika mata da sakon, ya kuma je a yadda yake so, sai ya marairaice mata fuska yana jijjiga kansa. "Allah ya kiyaye Allah ya kaimu lafiya." Tace da sauri ta bud'e kofar kuusa da ita ta fice ta bar shi a ciki, dariya sosai ya saka, ya sake rik'e ledar hannun sa gam gam, ya fice yana jin sa tamkar yana yawo a cikin gajimare. A kafa yake tafiya rik'e da ledar, iska na kada shi, sam baya jin komai baya ganin kowa sai tsadadden murmushin sa, shi kadai yasan yadda yake ji a lokacin, shi ya saka shi tafiya kawai ba tare da ya neme su ba. A chan bayan layin da suka saba haduwa suna tsaye tana masa mitar kwana biyu be zo ba, hakuri yake bata akan wata tafiya ce ta taso masa Muhammad din yazo wucewa "Kaga saurayin Iman." Tace da sauri tana nuna masa shi. Wani kallo Bashir yayi masa daga nesan kafin yayi saurin juya bayan sa, yayi saurin bud'e motar ya shiga ciki, yayi kamar yana neman wani abu a ciki "Baby me kake nema? Fito ku gaisa da Malam mana." Kin fitowa yayi ya cigaba da bud'e dashboard yana rufewa, "Assalamu alaikum." Moh yayi musu sallama yana karewa motar kallo. A wani yanayi Bashir ya fito bayan nacin da Zeenat din tayi masa, ya diririce ganin Moh din "Sannu ko?" Moh yace masa yana mika masa hannu "Sunana Muhammad, kaifa?" Yace masa, a sakale Bashir ya miko nasan hannun kamar me tsoro cikin rada rada yace "Bashir." "Yayi Bashir, sai anjima." Ya wuce ba tare da yace komai ba. Dariya Zeenat ta saka "Shi wannan din kika ce shine zai auri Iman?" Yace da sauri " In Sha Allah, baka ga sun dace ba? Ko baka ga yanayin su daya bane?" " A haka yake tun zuwan sa gidan kuma? "Babe me ta faru?" "Noo noo babu komai." "Naga duk ka damu ne, me ya faru?" " Ah babu komai, kawai na ganshi haka haka ne." "Dan ma baka ganshi sanda ya fara zuwa bane, tab!" Ta sake kwanshewa da dariya "Abun mamaki." Ya furta ba tare da ya sani ba. "Abun mamakin gaske , mutum kamar wani mahau." "Keee." Yace mata yana zaro ido, sai kuma ya waske da sauri "Bari naje, ya kamata mama tayi tayi ya shawo kan Abba ina so na turo manya." "Ka turo kawai, ka bar komai a hannu na, bbu me min auren dole, wanda nake so zan aura babu me hanawa." "Toh shikenan." Sallama sukayi ya tafi itama kuma ta koma gida, tana shiga ta tarar da Abba a compound, ya tasa ta a gaba ransa a bace. ***Wani kallo da Maman tayi wa Iman lokacin da ta shigo ya saka ta shan jinin jikin ta, ta wuce bayan ta gaishe ta bata amsa ba, ta ajiye jakar ta sannan ta fito ta shiga kitchen ta sha ruwa ta dora ruwan abinci sannan ta fito falon, tana tsaye ya hade ran ta sosai, ta tsaida ita "Uban waye ya baki izinin ajiye min wankin da na sakaki? Ka tafi?" "Ubanta ne!" Abba da suka shigo tare da Zeenat yace, da sauri Mama ta juyo sukayi ido biyu dashi ***Ba karamin matse kaina nayi ba saboda na cika alkawari, kuyi hakuri babu yawa 1/11/22, 15:42 - Buhainat: Halin Girma     11 *Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107*  I'm on Instagram as @zafafabiyar5. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1ft46u5twk6r3&utm_content=nj79azb _*Mierah's dukkan_* _*Mierah’s dukkan_* _*Mierah’s dukkan_* _(Palace of exotic scent and more)💯❤️_ _MD: is ur plug! Muna siyarda kaya kala2 kamar jaka da takalmi kamfanin lamis,Dior,vellabela da dkny da sneakers 'yan yyi dominku da yaranku,Muna order kaya dga kasashe daban-daban,Muna siyarda da kayan decors,plated gold,da turaruka kala-kala Hadi dna tasa (oil perfume) dga kamfanin naseem hr suratti,Muna da room fresh da turarukan wuta Dan gangaria. Muna adashe na yargata(kaya) Dana kudi ku tuntube mu awannan nmbr kamar haka wa.me/07039773001 Muna turawa ko Ina afadin Nigeria da wasu kasashen ketare ngd_ *** A wani yanayi Maman ta dago, gabanta ya fadi ganin Abba a tsaye a kofar Zeenat na rakube a gefe kamar munafuka "Dr, Sannu da zuwa." "Kinsan daga ina yarinyar nan take?" Ya nuna Zeenat yana jin kamar ya rufe ta da duka. "Aiken ta ne nan baya gidan Amarya me koko." Tace bayan tasan ba hakan bane. Kwafa yayi cikin kada Kai yace "Yaron da nace babu ita babu shi take zuwa suna haduwa a bayan layi, na fad'a miki na kuma bana son yaron domin ba yaron kirki bane, amma a bayan kunnenku." "Idan har ta dage ba zata ji magana ta ba, zata dinga fita suna haduwa a wani wajen ba da izini na ba ko na yan uwana, zan sallama masa sai tace ya turo,amma..." Ya nuna ta da yatsa "Idan har wani abu ya je ya dawo, kar ku kuka da kowa, ta kuka da kanku!" Shiru Maman tayi taki cewa komai, haka Zeenat din da ya zaci zata bashi hakuri sai yaji tayi shiru " Kin amince da Bashir din, kin yarda zaki aure shi?" Daga kanta tayi da sauri babu kunya ba tsoron Allah, wani irin faduwa gaban Abban yayi, yaji tamkar zai fadi saboda wani jiri da ya nemi zubar dashi, be zaci haka daga gareta ba, sam ba tarbiyyar da yayi wa yaransa bace, sake maimaitawa yayi cikin danne abinda yake ji yace " Kinji kin gani, kin Amince?" " Dr ka bar maganar nan idan muka shiga ciki sai mu..." Dakatar da ita yayi da hannu, ya dakawa Zeenat din tsawa " Ki bani amsa!" " Eh Abba." Tace tana nokewa idon ta fes tamkar an soye gyada " Shikenan, shikenan." Ya maimaita " Kice dashi ya turo magabatansa, suzo wajen Yaya." Sai ya juya wajen Iman da tayi kamar ta bud'e kasa ta shige saboda kunyar abinda Zeenat din tayi yace " Kema ki ce masa ya turo dan ba zan bata lokaci ba." Daga kanta tayi da sauri, ya wuce su yana jin wani irin tashin hankalin abinda Zeenat din tayi, tabbas laifin Hajara ne, ita ce bata tankwarata ba, bata nuna mata daidai da akasin haka ba, abinda ma ya lura Itace take son abin, ba zai yarda wani abu ya faru ba a dalilin hana ta auren Bashir din, dan yaran yanzu zasu iya komai akan soyayya, shiyasa kawai ya yanke shawarar aura mata shi din idan har ta kafe, da azo ana wallahi tallahi. Abban na barin wajen itama Iman tayi saurin ficewa dan tasan sarai Mama zata huce akanta, tana juyo fad'an da take wa Zeenat din sama-sama, ta kara sauri ta zagaya ta baya ta shiga ta kitchen ta wuce dakin su kawai. Tsawon kwanakin Abba bashi da walwala sam, ita kanta Mama ta kasa gane kansa, da ya shigo zai wuce dakin sa kawai sai kuma gobe, a da tayi tunanin fushin ba zai nisa ba, sai taga abin yana neman zarcewa, takanas ta same shi da maganar da ban hakuri amma sai ya share ta yama yi ficewar sa ya barta, haushin hakan ya sakata share shi itama ta san dole zai gama fushin sa ya dawo ko da Anyi auren yaji su kalou zai ajiye komai ya dawo, tasan ta fishi gaskiya shiyasa taki goyon bayan sa, dan tasan zugashi akayi dan an ga Zeenat din zata huta. ***Bayan tafiyar Muhammad basu yi magana da ita ba, sau biyu tana kiran number sa bata samun sa, hakan ya saka ta damu sosai, gashi tasan Abba zai sake mata magana akan abinda yace ta fad'a masan, gashi bata sameshi ba, tsoron ta daya Allah yasa ba guduwa yayi ba, dan har ga Allah zuciyar ta, ta yarda dashi. Har tana jin son sa na shigar ta, koman sa daban ne hatta maganar sa, ta kasa gane komai akansa musamman a fagen da zata ajiye shi, yanayin sa da koman sa yasha banban da shigar sa, tana bukatar sanin sa sosai kila ko bayan sunzo da iyayen sa an daidaita, a lokacin zata bijiro masa da tambaya akan sa, ko da ba komai ba, a kalla ya bata labarin wani abu da ya shafe shi. Fitowa tayi falo ta zauna bayan ta gyarawa Gaji daki, maman su Maryam ce ta shigo, ta gaishe ta tana tashi ta kira mata Gaji, tare suka dawo da Gajin ta gaishe ta sannan suka soma hira akan abubuwa da dama. Ita dai Iman na zaune tana jin su tana duba wayar ta. Maganar Maryam suka shiga ya sakata d'agowa tace "Umma Ya Maryam din ce bata da lafiya?" "Wallahi Iman, wai har kwananta uku a asibiti amma basu fadawa kowa ba, bari tayi an sallameta dazu amma, shine nake tunanin wanda zai je mata ya dan taimaka mata ko na sati daya ne." "Allah sarki, Allah ya kara sauki." " Ko ke zaki je ne takwara?" "Toh..." Tace har cikin ranta bata so ba " Iman bata son mutane ai, zata iya zuwa kuwa? Maman su Maryam din tace tana murmushi "Idan ta kamata ya zatayi?" Gaji tace "Wai kar a takura ta dama." "Haba kinji wani zance, yar uwarta ce fa? Idan batayi mata ba wa zatayi wa?" "Haka ne." "Zance Umma, ba komai ai." "Toh shikenan, anjima sai wani cikin samarin ya mik'a ki." "Ai ba sai anjima ba, yanzu zata shirya sai su wuce, ki shiga sai ki sanar da Maman tasu, idan yaso sai ta fadawa Ibrahim din duk da nasan babu abinda zaice." "Toh shikenan bari na shiga wajen nasu." Ta tashi ta fita,ita kuma Iman ta wuce ciki ta dauko charger ta tazo ta fita. A zaune ta tarar da Umman suna maganar da Mama, tana shiga tace "Ki shirya zaki je gidan Maryam kiyi kwana biyu, Allah ya kara sauki." "Toh." Tace ta wuce ciki, ta dauki wata karamar Jakarta, ta saka kayanta kala biyu sai undies da hisnul muslim, da dan abinda tasan zata bukata ta fito, bata ga su Maman a falo ba, sai ta nufi dakin ta rataye da jakar a kafadarta, ta kwankwasa kafin ta shiga "Mama na fito." Tace daga kofa, jakar ta dake kan gado ta dauko ta ciro dubu daya ta mik'a mata "Sai kin dawo." Hannu biyu tasa ta karba mamaki na kamata, tayi godiya ta fito still tana jin kamar mafarki, magana me dadi daga Mama har da bata kudi? Akan me? Sam sai taji hankalin ta be kwanta ba, taji kamar ta koma ta tambaye ta dalilin action dinta amma babu hali. Ita kadai ta dinga juya dubun har suka isa gidan Maryam din, ta fito rik'e da jakar ta shiga gidan. A falo ta tarar da ita da mijinta sai sister dinshi wata babba haka. Wani farin ciki ne ta gani a fuskar maryam din, ta tashi zaune tana mata sannu da zuwa. Gaishe su ta fara yi suka amsa dukka sannan ta nufi wajen Maryam din tana mata ya jiki, "D-D bari naje na kai Yaya gida tunda ga Maryam tazo." "Ok tam." Tace "Nagode sosai Anty Saliha, ku gaida gida." "Gida zaiji Maryam, Allah ya kara sauki ki kula da kanki sosai kinji? Ki dinga cin abinci sosai saboda kiyi saurin dawowa dai, Allah ya kawo wani rabo me albarka." " In Sha Allah zanci, nagode." Tace a kunyace, sukayi sallama suka fita " Sa mana key din a kofar." Tace wa Maryam din tana gyara zaman ta. Key din Maryam ta saka musu ta dawo ta zauna kusa da ita "Ashe ke zaki zo, naji dadi da ba'a turo wata cikin yaran chan ba wallahi." "Wallahi, ya jikin naki? Naga kinyi fari sosai." " Toh ba dole ba, kin ga uban wahalar da nasha kuwa? Kai Iman aure- aure akwai wahala wallahi." " Sannu, Allah ya kara sauki." " Amin ya Allah." " Ya gida yasu Mama, Gaji da kowa da kowa?" " Kowa lafiya lou, duk suna gaishe shi." " Ina amsawa, amma zasu zo su dubani ai ko?" " Eh toh nasan zasu zo, dan baki ga ma fad'an da Umman tayi ba, kwana uku a asibiti baku fad'a ba." " Ina na sane, hankali na baya jikina, laifin D-D ne, shi ne be fad'a ba wallah. Anty Saliha ma baki ga fad'an da tayi ba." " Ai dole, wani abun kana bukatar Babba kusa da kai." "Aikuwa." " Allah ya kara sauki ya kiyaye gaba." " Amin addu'ar kenan." " Sai naji labari kuma, Ashe su Abba sun fara maganar ku, Umma tace min ma ke kamar su abba sun gama bincike akan shi har ma sun tabbatar da shi din zasu bawa, Umma tace bata taba ganin Abba ya damu da wani a cikin masu zuwa neman yayan gidan ba kamar yadda ya damu da wannan din, ko dai wani Babban kika samo mana ko wani basarake?" Tace cikin zolaya " Kai Ya Maryam, bafa kowa bane hasalima dai ba wani me kudi bane kawai dai inaga ko Abba ya gamsu da halayen sa ne." " Eh toh haka ma Umma tace, nima tsokanar ki nake, ke yanzu ka samu miji na gari me son ka me son farin cikin ka shine, ba yalwar arziki ba, da wani arzikin gwara rufin asiri." " Haka ne." " Allah ya kaimu lokavin, musha biki." Dariya tayi kawai dan ita jikinta a sanyaye yake da rashin jin sa har tsawon kwanaki hudu, ta damu sosai sosai har ta kan zauna tayi ta tuna moments din da sukayi tare, wani lokacin tayi murmushi ita kadai wani lokacin kuma ta ji kunya ta kamata. _"I love you."_ Kalmar da yadda ya fade ta take ta tunawa, har yadda lips dinsa suka hade waje daya yayin da yake furtawa, cikin muryar da take yawan yi mata amsa kuwwa a cikin kunnenta "Dan Allah dafa min danwake, shi kawai nake sha'awa baki na babu dadi wallahi." Maryam ta katse mata tunanin da take, ajiye wayar ta tayi a gefen Maryam din, ta tashi zuwa kitchen din, minti kad'an ta leko "Toh ai bansan Ina kayan naki suke ba." Tasowa Maryam din tayi, tazo ta dauko nata komai ta nuna mata sauran sannan ta dawo falon ta jona wa Iman din wayar ta a charge kusa da ita ta kunna tv ta koma ta zauna tana kalla, jefi jefi tana yiwa Iman din hira daga nan. Wayar Iman din ce tai kara, alamar shigowar kira, tana daga kitchen din amma sai da ta ji gabanta ya fadi, saboda tsabar jiran kiransa har ringing tone ta chanja masa nashi shi kadai saboda da ya kira yadda zata fi saurin ganewa, "Ana kiran ki Iman." Maryam tace tana jawo wayar ta kalli screen din "M ne yake kira, M M M waye Ma? Sirikin nawa?" Tace tana murmushi, maimakon Iman din ta fito ta karba sai kawai ta cigaba da aikinta tana jin Maryam din na mata sababin zata katse, kamar ba kiran da take jira bane, amma kuma a kalla yanzu hankalin ta ya kwanta, tasan cewa da gaske be manta da ita ba. Sake kira akayi karo na biyu, "Bana son wulakanci Iman, bari na daga kizo ki karba." Dagawa tayi ta saka a kunne "Sweetheart." Ya furta cikin rada yana sauke ajiyar zuciya, da sauri Maryam tayi gyara murya tana cire wayar kafin ta mayar tace "Yayarta ce maryam, tana kitchen ne." "Anty Maryam, Ina wuni?" "Lafiya lou wallahi, ya aiki?" "Alhamdulillah." "Dama tana kitchen ne, amma yanzu zata zo zata kira." "Owk nagode sosai." "Nima Nagode." Ta katse kiran tana tashi, zuwa tayi kitchen din da daddage da d'aka mata duka a baya "Dan wulakanci kina ji yana kira ko? Wannan irin hot guy din ba'a musu jan aji wallahi, kinji kuwa? Haka yake kashe ki da soyayya? Hmmm lallai yau ga wanda yafi D-D na." Banza Maryam din tayi mata tana murmushi, ta karbi wayar ta ajiye a gefe ta karasa kwashe danwaken ta zuba a flask ta zuba ruwan zafi akai ta rufe, ta soya man ta hada komai a babban tray ta dora Maryam din na tsaya a akanta tana mata hirar Moh din ita a dole sai taji wani abu daga iman din amma tayi mata fumfurus "Mara lafiya ba'a cika son shi da yawan magana ba, muje na kai miki abincin falo." Dukan ta kara kai mata ta goce tana dariya, suka jero Maryam din na rik'e da bottle water ta ajiye mata komai a falon ta zuba mata sannan ta dauki jakarta tace "Ina ne dakin?" Da baki Maryam din ta nuna mata lokacin ta cika bakin ta da dan wake. Dakin ta nufa ta shige ta rufo kofa sannan ta cire hijab dinta ta ajiye a agefen gadon ta zauna tana kallon wayar, kunya da nauyin kiran sa take amma kuma tana bukatar kiran nasa, tayi missing dinsa da muryar sa gaba daya. Kiran nasa tayi tana tashi tsaye lokacin da ta soma ringing, be daga ba, amma kuma tana katsewa ya biyo kiran a take. "Assalamu alaikum." Tayi sallama wayar a hannun ta bata saka a kunne ba "Wa alaykisalam." Ya amsa sai yayi shiru, itama shirun tayi tana saka abinda zata ce "Shine baka kirani ba?" Ta samu kanta da fad'a ba tare da tayi tunani ba. Abinda dama yake son ji kenan, tayi missing dinsa in dai har tayi korafi akan rashin kiran, murmushi yayi wanda taji sautin sa ta cikin wayar "Kinyi kewa ta kenan ko?" "Um um." Tace da sauri "Kawai dai na kikkiraka bata shiga, kuma Abba ya bani sako shine kawai dama." "Ohh, sakon Abba ne yasa kika kira ni ba don kinyi kewa ta ba?" Shiru tayi dan a zahirin gaskiya ba hakan bane, tana bukatar ji daga gareshi, tana bukatar comforting words dinsa, tana bukatar shi kawai ma in short. "Ni kuma kinga nayi kewar ki, sosai sosai komai ma da nake anan din yinsa kawai nake ba don naso ba, kiyi hakuri kin kirani, ina wajen da dole na kashe waya, shiyasa har kika jini shiru haka." "Ok." Tace a ba tare da tasan me zata ce ba "Ya gida ya kowa da kowa?" "Alhamdulillah, yasu Ammi? Ka samesu lafiya?" "Lafiya lou, banje gida ba, yau nake shirin zuwa in sha Allah." "Ok tam, karka manta ka gaishe ta." "Ba zan manta ba, zance mata sirikarta na gaishe ta, zan kira sai na bata kuyi magana." " Um um ba zan iya ba." " Kunyar ta kike ji? Irin kunyar surkutan nan ko?" Ya kyalkyale da dariya " Ni dai bance ba." " Ni kuma nace." " Uhum." " Wacece Maryam?" " Yayata ce da akayi bikin su, nazo gidan ta bata da lafiya zan kwana biyu na dan taimaka mata." " Owk ayya, ki duba ta, Allah ya bata lafiya." " Amin zataji." " Baki fad'a min ba, me Abbanmu yace?" " Na zata ba zaka tambaya ba ai?" " Na isa? Ina sane kawai dai." " Dama cewa yayi, a turo." " Me!!! Alhamdulillah, Alhamdulillah Alhamdulillah! Kina nufin Abba yace na turo magabatana ayi magana? Kenan Abba ya yarda ya bani ke? Kai mAsha Allah, Alhamdulillah." " Wannan murnar haka." Tace cikin mamaki " Ba zaki gane ba, ba zaki gane ba Zahraah, Nagode sosai, Allah ya sakawa da Abba da alkhairi. Nagode nagode, wannan ranar ta shiga cikin ranaku masu matukar muhimmanci a tare dani, Alhamdulillah." " Allah ya tabbatar mana da alkhairi." " Amin Zahra nah, Amin Amin. Bari kiga na tashi, banga ta zama ba a yau zanje na same su da maganar, in sha Allah a kwana daya zuwa biyu magabatana zasu zo, ayi komai a gama, Allah yasa Abba ya saka mana lokacin kankani, bansan irin farin cikin da zan ba, Alhamdulillah." " Uhum." Tace dadi na kamata, a kalla ta samu wani da yake son ta sosai, irin soyayyar da ta rasa tun tana yar kankanuwar ta. " Zan kiraki anjima, ki kula da kanki." " In Sha Allah. Ba-bye." Fadawa tayi saman gadon tana jin farin ciki matsananci " Ya Allah ka sa ya zama alkhairi a rayuwa ta, Allah ka tabbatar mana da alkhairi." Ta furta tana jin kamar bata da saurin bakin ciki. ***Da karfin sa da kwarin guiwar sa ya isa masarautar su, wannan karon shigar da yasan Bubu yafi so yayi, shigar Manyan kaya da rawani, yayi masifar kyau ya fito a basaraken sa na ainihi, duk wanda yaci karo dasu sai sun kalle shi sun sake kallon sa, kai tsaye bangaren Aji ya nufa, domin wanchan karon be samu ganin Hajjan sa ba, shiyasa ya fara tachan dan tasan sai tayi korafi. Tana ganin shi kuwa ta hau murna, ta rasa in da zata sakashi, mace ce me jin mulki sosai domin mulkin a jinin ta yake dan har tafi Aji, amma kuma a duk abinda ya hada da muhammad bata hada shi da komai da kowa, da kanta take masa komai duk abinda yake so kuma shi take so ko da kuwa kowa ba zai goyi bayan sa ba. Sai da ya gama mata shagwabar sa son ransa sannan ya gabatar mata maganar auren da yake so aje a nemar masa, murna a wajen ta kamar ta dauke shi ta goye haka taji, karshe ta dinga tsokanar sa da sauran idan amaryar tazo ya manta da ita, da tsohuwar zuma dai ake magani. Da haka ya wuce fada in da yasan zai samu Bubu wanda tuni labari ya riga ya kai masa, ya shirya yana dakon karasowar Muhammad din. Ganin sa ya saka Bubun farin ciki, musamman da ya ganshi cikin shiga irin ta gidan sarauta! ***Abba na zaune ya gama karatun alkur'ani me girma Maman ta shigo, ta zauna a gefen sa yayi kamar be ganta ba "Dr wai fushin ne har yanzu? Be kamata ace abu irin wannan ya bata maka rai ba, yara hakuri ake dasu." Daga mata hannu yayi "Bana son maganar nan, idan har ba zaki iya tankwara yarki ba, kuma ba zaki nuna mata dai-dai ba, shikenan, abinda kuke so kuka zaba zanyi muku." "Allah ya huci zuciyar ka, da anyi auren ma.in sha Allah zaka sauko, musamman idan kaga zaman nasu lafiya lou." "Allah ya taimaka." Yace yana kokarin mikewa "Dama magana nazo muyi, gida zanje." "Allah ya tsare hanya, ya kiyaya" yace kawai cikjn halin ko in kula "Kwana uku zuwa sati nake son yi." "Duk yadda kika ga yayi miki." Ya karasa ficewa. Kwafa tayi ta mike tana jin haushin sa. Ko me zaiyi ba zata hana Zeenat abinda take so ba, an wuce zamanin auren dole. Zai gaji dan kansa ya sakko. 1/12/22, 08:56 - Buhainat: Halin Girma     12 *Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107*  I'm on Instagram as @zafafabiyar5. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1ft46u5twk6r3&utm_content=nj79azb ***Kai tsaye ya wuce zuwa chan gaban Bubun, fadawa na aika masa da kikari, kirarin da yake jin sa har cikin kansa, sai dai baya taba bari yayi tasiri a gareshi, hasalima yi yake tamkar be san me suke cewa ba. Dukawa yayi kamar yadda yake a al'adah ya gaida Bubun, ya amsa masa da ka ba tare da yace komai ba, a irin wannan zaman Bubun baya magana sai ta kama, sanin haka ne yasa Muhammad din ya koma daga bangaren dama ya zauna kafin sauran yan fadar su shiga kawo masa gaisuwa. Amsawa yayi duk a jimlace, ya hakimce a gefe yana sauraron zaman yake wakana. Kasancewar zaman na gab da tashi ne yazo, shiyasa yayi tunanin ba za'a wani ja lokaci ba, sai yaga an dauki lokaci ana maimaita abinda aka fad'a a baya, ya sani sarai hakan tsarin bubu ne, kila kafin ya iso ya shirya hakan saboda shi, murmushi yayi yana satar kallon Bubun da shi din ma shi yake kallo. A karon farko yaji tausayin mahaifin nasa ya kamashi, yadda yake kokarin ganin ya damka mulkin a hannun sa bayan shi kuma bashi da ra'ayin hakan, amma kuma be tursasa masa ba, ya cigaba da bin sa a hankali zuwa lokacin da yake ganin ya dace. Be san ta yaya zai fahimtar dashi ba, amma yana da dalilin sa babba da ya saka shi tsayawa akan bakan sa, akwai babban kalubale a gabansa idan har ya amince da muradin Bubun , amma ta yaya zai iya gujewa hakan? Bayan babu wanda yasan dalilin sa? Yana jin sanda zaman ya kare, ya sauke ajiyar zuciya me nauyi ya daga idon sa sama yana kallon tsaruwar fad'ar, komai na ciki me tsada ne da kawa, haka duk wani abu da yake ciki me muhimmanci ne ga masarautar. Tunanin Bashir ne ya fado masa, da ganin da yayi masa da fitsararriyar yarinyar nan, Bashir yana direbobin Masarautar Kano wanda ya sanshi sosai saboda kaudin sa da hayaniyar sa, kafin ya auri wata mata wadda ake kyautata zaton auren jari yayi, tun daga lokacin kuma ya bar masarautar sai jefi jefi yakan je ya gaida Fulani idan ta kama. Yayi mamakin ganin sa da zabgegiyar mota amma da ya bincika ya gane komai, sai yaji hakan yayi matukar yi masa dadi, yayi Kuma daidai da tsarin da yake son dora su akai. Dawowa yayi daga tunanin jin kamar an taba shi, ya kalli wanda ya taba shin sai ya fad'ad'a fara'ar fuskar sa, "Aji!" "Tunanin me kake haka Muhammad?" " Babu komai, mun same ku lafiya?" " Lafiya lou, ya aikin? Amma kazo kenan ko? Zaka dade?" " In Sha Allah!" " Sannu da zuwa." Yace yana mikewa " Zuwan ka dana ji ne ya sakani zuwa , Ina fatan idan ka huta zaka shigo, akwai batutuwan da nake so mu tattauna." " Muje na taka maka, dama nima akwai maganar da nake so muyi." " Toh toh madallah." " Muhammad." Bubu ya kira sunan sa yana daga zaune " Na'am Bubu!" " Naji dadin ganin ka da shiga irin wacce ta dace da kai, Ina fatan dorewar hakan." " In Sha Allah Bubu, zan kokarta." " Madallah da kai." " Allah ya kara girma." Tashi yayi suka fice tare da Aji, hannun su cikin na juna, Maimartaba ya jinjina kansa yana mamakin tarin kaunar da suke wa juna, har suka bacewa ganin sa sannan ya sauke ajiyar zuciya yana tafiya tunanin abubuwan da aka tattauna don cigaban al'umma. Sai dai yana fara tunanin, tunanin ta ya shigo ya katse masa duk hanzarin sa, ya rasa dalilin da ya saka a duk sanda ya tuna da maganar yake jin duk wata walwalar sa da farin cikin sa ya ragu, musamman a dan tsaikon nan, sai yake jin tamkar ana dakatar dashi da yin wani yunkuri. Shi din mutum ne me riko da addini matukar gaske, baya taba bawa maganganun da za'a zo a fad'a masa muhimmanci ko kad'an, sai dai a duk abinda ya shafi Muhammad baya wasa, yana ji a ransa kar fa abinda tsohuwar matar ta sanar masa ya zama gaskiya, tsoron hakan ya hanashi gabatar da komai cikin sauri yake bin komai a hankali, ba kuma wai dan ya gasgata maganar ta dari bisa dari ba, sai dan yana ji da tsoron sharrin masu sharri, be san me suke shirya wa dan nasa ba, sai dai be gaza ba, babu dare babu rana kullum cikin nema masa kariya yake a wajen ALLAH, ko ma menene tabbas zai zo masa da sauki. ***A falon Ajin ya same shi yana zaune fuskar sa kamar gonar auduga, da kansa zai je amma sai Bubun yace ya bari yazo kawai ya huta. Bayan ya zauna ne fadawan suka fice suka jawo musu kofar. "Na matsu na sanar da kai wannan albishir din, abinda muka dade muna jira ne, Muhammad dai yazo da magana, har yana neman aje ayi masa tambaya!" Fuskar Bubu ta fad'ad'a,farin ciki ya mamaye shi " Masha ALLAH! A kanon ne kamar yadda Takawa yace?" " Eh har binciken da mukayi, nan din ne in Sha Allah." " Sai a sanar wa Takawa babu jira, in Sha Allah gobe duk abinda ya kamata ayi sai ayi, jibi sai aje musu da magana, da tsayayyiyar rana domin Takawa ya bukaci ayi komai a cikin kankanin lokaci." " Madallah...Hakan yayi." Tattaunawa suka shiga yi har dare yayi sosai,kafin ya koma bangaren sa cikin jin dadin labarin auren Muhammad din. ***Jifa tayi da kofin hannun ta, ya fashe a wajen gaba daya kwalbar ta wawwatsu a dakin, wani irin bakin ciki take a duk lokacin da taji wani abu da ya danganci Muhammad din. Yau Itace a turakar Bubu amma tasan ba zata taba samun kansa ba, idan ma ta zafafa zai iya cewa ta bar masa dakin shiyasa ta yanke wa kanta hukuncin ko da yadawo daga wajen Aji ba zata je ba zatayi zaman ta tayi tunanin menene mafita a gareta. "Ranki ya dade, Yarima Muhammad yana waje yana neman iso." " Uban me zai min!!" Ta daka mata tsawa tana huci, sai kuma ta hau kokarin daidaita kanta " A shigo dashi babban falo gani nan." Da sauri baiwar ta fice tana mamakin uwar dakin nata. Zaman sa yayi yana karewa falon kallo, an sabunta komai ba kamar zuwan sa na karshe ba. Murmushi ne a fuskar sa, yana da yakinin bata da bukatar ganin shi, ko da gilmawar sa ne balle har ya kai ga zama a falon nata, yana sane yazo domin ya kara tabbatar da abinda ya sani tun tuni. A yadda ta fito, da yadda ta zauna kadai ya isheshi amsar abinda yazo nema, yana kallon yadda take satar kallon sa cikin kallon da yasan na tsantsar tsana ne tun da ya riga da ya dade da sanin bata kaunar sa ko daidai da minti daya ne " Barka da gida, mun sameku lafiya?" Ya fad'a da yanayin da yasan zai sake tunzura ta. " lafiya, ya aikin naku?" "Babu dadi, na gudo ma na dawo gida cikin yan uwa!" "Ka kyautawa kanka." Tace a gajarce Mikewa yayi yana zuba hannayen sa cikin aljihun sa, ya yi mata kallon cikin ido tace "Bari na koma." "Baka Sha ko ruwa ba." Tace tana daga zaune "Na yafe, bani da bukata." Ya dage gira yana juyawa, da kallon bakin ciki tabi bayansa har ya fice daga falon, ta yarfe hannunta tana jin kamar ta kamo shi ta tayi ta jibgar shi har sai taga ya daina motsi. "Ciwon Ido, zanyi maganin ka!" Ta furta tana tashi ta koma ciki ***Daga nan bangaren Ammin sa ya wuce, yana jin kansa kamar sabon ango, farin ciki yake ciki shiyasa ma be wani damu da abinda ya faru ba. Dama yasan kafin ya isa ta samu labarin ko ta wajne Hajja ko Bubu, aikuwa yana shiga ta tare shi da murnar ta, ya zauna ya tankwashe kafarsa a gabanta tana jin yadda take lissafo masa abubuwan da za'a bukata na zuwa gidan su Fatiman. A farkon farko be so wani abu na sarauta ya shigo ba, amma kuma da ya tabbatar hakan ba zai yiwu ba, shiyasa yayi amfani da damar nan wajen hadawa Mama gadar zare, dalilin tafiyar ta da shine ya assasa bayan ya kira Khalil a waya ya karanta masa yadda duk yake so ayi, babu musu ya amsa kuma ya tabbatar masa da zai yi komai daidai. Dazu Kuma ya kira shi ya tabbatar masa da Maman ta iso tun wayewar gari. Da wannan ya yi gaba wajen aiwatar da saura shirin sa da ya tabbata zasu yi matukar girgiza kowa ba Maman kawai ba. Har dare sosaii yana shashen Ammin, ta hada komai abubuwan da ya tabbata zasu dace da tsarin fatimar sa, shi din ma akwai tanadin da yayi mata amma ba yanzu ba, sai ranar da dubban mutane suka shaida, ya zama ita ta zama shi, a ranar zai nunawa duniya kalar gatan da take dashi a wajen sa. Da sassarfa ya karasa part dinsa, Kai kace wani uban aiki yayi saboda yadda yake jin sa a gajiya. Kwanciya kawai yayi bayan ya aika mata da cool night text message ya kashe wayar sai bacci, baccin da yake yi a duk lokacin da ya samu kansa a dakin sa na cikin gidan. Zai iya cewa ya jima beyi bacci me dadin na ranar ba, ko dan abinda ya faru a ranar ne? Ko Kuma dai dan ance gida daban yake, dama bahaushe na cewa kowa ya bar gida... wanka ya soma yi, ya fito domin ya karya dan yasan komai na kammale a ajiye yana jiran sa. Zaman karyawa yayi, yayi dialing number dinta yana kallon plate din da ake zuba masa abinci, da hannu yayi masa alamar ya isa, ya karba ya soma ci jin bata daga ba, a yar mu'amular da yayi da ita, ya lura tana da bawa kowanne abu muhimmanci idan har shi ta saka a gaba, misali idan tana aiki takan ajiye wayar ta waje daban ta kammala aikin, haka idan tana wani muhimmi abun bata hada shi da komai har sai ta gama. Tunanin sa ne ya katse lokacin da kiranta ta ya shigo nasa. Murmushi yayi yana jan tissue ya goge bakin sa, yayi rejecting kiran sannan ya bi bayan yana kishingid'a a jikin lallausan tumtum din dake kusa dashi. Da sallamar ta, ta daga kamar ko wanne lokaci, ya amsa mata shima kafin ta dora da gaisuwa "Ina kwana?" "Lafiya lou, kin tashi lafiya?" "Lafiya lou, yasu Ammi? Ka same su lafiya?" "Kalou kowa, ya sister Maryam da jiki?" "Gata ta samu sauki, inaga ma na tafi gida tunda naga ta warke sosai. " " A ah kiyi zaman ki! " Yace da sauri " Me yasa? " " Amm kin gane, kinga tana bukatar ki, ki dan kara mata ko da kwana biyu ko uku ne, zata ji dadi. " " Owk tam. " " Yawwa. " " Ina kika shiga dazu na kira no answer, kitchen? Ko shara? " " Ya ka sani? Ina kitchen. " " Na sanki ai, nasan bakya wuce wuraren nan biyu. " " Lallai, kasan abubuwa da yawa akaina, amma ni bansan komai ba. " " Zaki sani, karki damu zaki sani fiye da sanin da kowa ma yayi min. ". Ya karashe maganar cikin sigar tsokana, bata ce komai ba, yasan kuma ba zata ce din ba, shima ba dan tace wani abu yayi maganar ba "Zan zauna takanas, kiyi min duk tambayoyin da zaki yi min, zan amsa, amma kafin lokacin ina so ki san, nifa soja ne!" "Soja!" Tace gabanta na faduwa sosai, bata son aikin soja ko miskala zarratin, bata kuma taba tunanin auren soja ba, dan tasan yadda suke very busy da aikin su "Eh ni soja ne, amma fa irin kurtun nan." "Soja dai ai duk soja ne, sunan daya ne." "Amma rank din daban daban ba." "Uhummm. " Ta ja ajiyar zuciya, ya sammace ta, kenan dai zaman kadaici be rabu da ita ba, dan sojoji basu da lokacin kansu balle na matan su, yanzu ita kenan... " Karki damu, ba zan dinga nisa ba kinji? Zan zama ko yaushe kika bukace ni Ina kusa, nayi miki alkawari." "Allah yasa, dan da gaske bana son aikin soja wallahi." "Saboda me? Aikin taimakawa kasa ne fa, aikin lada ne idan har ka yi yadda ya dace." "Na sani, ni kawai bana so ne, basu da time din kansu ballanta na ..." "Na matan su? Haka ko yaushe aka cewa dama, toh ni dai Ina da time dina Ina kuma da na matata, har sai kin gaji kin koreni daga gidan ma wataran." "Shikenan." "Zaki gani ai, ki zuba ido." Shigowar Ya Maryam ya sakata yin shiru "Ki fito falo ya tafi wallahi, ni kadai kamar mayya." Tace mata tana rik'e kofar, tun dazu tace tazo falo taki sboda maigidan yana nan, shiyasa Maryam din tazo kiranta da ya tafi, ko yar hira sa yi "Kice ina gaishe ta, ya jikin nata." "Da sauki." Tace tana janye wayar daga kunnenta. "Ashe waya kike shine kika yi luf, toh ki gaishe shi, in kin gama Ina jiran ki." Ta fita ta ja mata kofar "Bari na barki kuyi hirar ku, zan sake kira anjima." Kamar ta tambaye shi maganar zuwa gidan amma ba zata taba iyawa ba, sallama tayi masa ta ajiye wayar ta fita wajen Maryam. Yana sane sarai yake ce mata komai, baya so tasan komai sai anyi komai ya kammala, ba zai ma gaya mata zuwan nasu ba, Abba kawai zai wa text ya sanar masa, idan yaso sai ya turo Musaddik ya sameshi ya sake fad'a masa Incase ko be ga message din ba. Haka kuwa akayi, yana masa text din ya gani, yayi saurin kiran kowa ya sanar dasu zuwan bakin, anan suka fara tunanin abinda ya kamata suyi, baki daga irin wannan babban gidan dole ne ayi abinda za'a fita kunya. Sun dade suna shawarwarin su kafin su tsaida matsaya, nan da nan suka shiga shirin tarbar su cikin tsarin da suka san ba zai zama wani iri ba. Abba na zaune kiran Mama ya shigo wayar sa, shi kadai ne a gidan sai Habib ta tafi da Zeenat da Marwan, shiru gidan babu kowa kallon tv yake a zahiri amma a badini tunanin masu zuwa neman auren Iman yake a gobe, yaso ya sanar wa mahaifiyar ta zuwan nasu da komai akan maganar sai dai baya samun ta a waya wajen kwana uku kenan, yasan tana business sosai kamar ma tana fita kasashe saro kayayyaki shiyasa yayi tunanin ko kila bata k'asar ne. Kallon wayar tasa yayi, har lokacin haushin Maman yake ji musamman abubuwan da ya gano akan irin rikon da tayiwa Fatiman tsawon lokaci be gane komai ba, har Marwan ya titse ya tambaya ya kuma gaya masa komai abinda ya sake daga masa hankali sosai kenan. Kiran ne ya sake shigowa ya daga ba dan yaso ba, dan dai kawai be san ko wani abu bane emergency ya taso, sallama tayi ya amsa ciki ciki. Dama tasan za'a rina shiyasa kawai ta tafi kai tsaye akan dalilin kiran "Dama Zeenat ce ta ce na sanar da kai iyayen Bashir zasu zo gobe idan Allah ya kaimu." "Su bari jibi gobe Yaya yana da abinda zai yi." Yace mata kai tsaye "Amma da ka barsu sunzo goben ba dole sai wajen Yayan ba ai." "Haka tsarin mu yake tun farko, babu Kuma dalilin da zai saka na chanja yanzu dan anzo auren nawa yayan, idan har ba zasu iya bari sai jibin ba sai ki nema musu wanda zasu gani a goben." "Abin be kai haka ba ai, Allah ya kaimu jibin." "Amin." Yace ya katse kiran yana Jan tsaki, wato duk dadewar ka da mace ba zaka taba sanin wasu daga cikin halayen ta ba har sai abu ya faru, lallai. Shi kadai yake ta wannan tunanin har lokacin da zai kwanta yayi, ya kwanta da addu'ar Allah yasa komai ya tafi dai-dai goben. ***Duk cikin su babu wanda ya makara, suka tashi aka hau gaggayara gidan harabar da lungu da sako su Habib suka taimaka aka tsaftace ko ina, dama dai a gyara yake saboda takanas aka dauki me aikin kula da wajen amma duk da haka idan suka tuna bakin da zasu zo sai suga ya kamata a sake gyara ko ina. Wajajen sha biyu cikin jagorancin Musaddik suka iso, cikin manya manyan motocin alfarma da aka rubuta Emir Kano 1 guda biyu sai guda biyu dauke da tambarin Adamawa Palace. Cikin kankanin lokaci unguwa ta dauka, mutane suka dinga lekowa daga gidajen su dan tabbatar da abinda yaran su suka je suka fad'a musu, kowa ya leko sai ya rik'e baki cikin tunanin abinda ya kawo irin mutanen gidan. Cikin matuakr girmamawa Abba suka karbe su, sai dai sunyi tunanin zasu gansu a matsayin mutanne da basu kai ba ko kuma level dinsu ba daya ba, amma sai suka ga akasin haka, cikin girmamawa, karamcin da dattako suka zo musu, suka nuna Halin Girma, halin babban gida babu fariya ko nuna su din wasu ne, cikin tattautasa harshe da girmamawa suka nemarwa dan su kuma jikansu Muhammad auren Fatima. A take Abba yace an bashi. Su kuma nan take suka gabatar da ranar da suke so a saka, babu musu nan ma Abba ya amince suka tsaida wata daya kachal, shi din ma saboda Muhammad din ne ya bukaci haka, amma idan sune toh sati biyu zasu saka. Babu wani bata lokaci abinka da manyan mutane, masu Halin Girma, suka yi komai cikin sauki sannan da zasu tafi suka gabatar da kyaututtuka daga iyaye da kakannin Muhammad din da yake cikin al'adarsu idan za'a zo neman auren. Tarin kayan da suka kasance mota guda sai da suka bawa su Abba mamaki, a gefen Abba aka ajiye mukullin motar nufin su har da motar da duk abinda yake ciki kyauta ce ga sirikar Sarki Ahmad Santuraki, da iyalan gidan sa kafin zuwan ta, sannan suka yi musu sallama suka tafi. #HafsatRano #ZafafaBiyar2021 Not edited Ignore typos Masu sharing sannun ku da kokari kunji? Allah ya shirye ku idan masu shiryuwa ne, idan kuma ba masu shiryuwa bane toh... Kun san sauran dai😀 1/12/22, 21:41 - Buhainat: Halin Girma     13 *Zafafa biyar na kudi ne, idan kina so ki karanta ki tuntubi 08184017082 or 09134848107*  I'm on Instagram as @zafafabiyar5. Install the app to follow my photos and videos. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1ft46u5twk6r3&utm_content=nj79azb ***Sai da suka ga tafiyar su sannan suka dawo ciki, kowa da abinda yake cin sa a zuciya. Tabbas sun amsa sunan babban gida, haka sun nuna Halin Girma da dattako na irin manyan mutane da suka san mutunci da yakana. Fadar irin tarin kayan da suka zo dashi ba abu bane me sauki, hakan ya dan tarsa tsoro a zuciyar Abba, yake jin tamkar siyar da Iman din zai yi, wannan uban dukiya a matsayin tambaya, ina ga idan aka zo auren? Basu da talaucin da arziki zai tsorata su, sai dai dole ne suyi mamaki ganin uban dukiyar da aka lafto da sunan na Iman din ne, tun daga kan sutura zuwa kayan kawa na mata, da kyautata gwala-gwalai tamkar ba'a san darajar su ba. Haduwa suka yi suka tattauna yadda zasu adana komai saboda yadda rayuwar yanzu ta zama ta rashin tssro, shawarar farko shine su bar maganar tsakanin su domin mata akwai sakin baki musamamn idan abun da ya sha musu tunani ne, yanzu zasu yi ta kwazozotan sa har wasu dake waje su samu damar aiwatar da mummunan kuduri akan su. Tabbas shawarar tayi dan da gaske komai na iya faruwa idan maganar ta fantsama shiyasa kawai a take aka fita da motar da duk abinda yake ciki daga gidan zuwa in da zai fi zama safe kafin bikin yazo kusa sosai sai ayi abinda ya dace dasu, ko bata kayanta ta tafi dasu tunda dama su chan babu wani tsoron rashin tsaro ta ko ina zagaye suke da Jami'an tsaro. Karshen magana kuma ma shi Muhammad din kansa, su ne tsaron ma baki daya. Da wannan shawarar suka tashi bayan Abba ya sanar musu da zuwan iyayen Bashir a gobe kamar yadda Mama ta shaida masa. Sake gwada kiran Maman Iman din yayi bayan ya koma gida, cikin sa'a kuwa kiran ya shiga, bata wani jima tana ringing ba ta dauka a nutse cikin sallamar ta da muryar da yake jin ta kullum a bakin Iman din, maganar da sak ta mahaifiyar ta, hatta nutsuwar ta irin ta uwarta ce shiyasa yake jin ba zai iya mantawa da ita ba ko da shekaru sun ja, duk da yanzu babu batun soyayya a tsakanin su tun da be riga yasan matsayar da take a yanzun ba ko da aure ko babu, a dai kwanakin baya ya samu labarin tayi aure har da albarka Yaya a tsakanin su. "Ina wuni Abban Iman?" Ta gaishe shi jin yayi shiru bayan amsa sallamar ta "Lafiya Lou Maimunatu, ya gida ya kowa da kowa?" "Kowa lafiya Alhamdulillah, Iman fa?" "Tana nan lafiya." Shiru sukayi baki daya, kowa da kalar tunanin sa a ransa, shine ya katse shirun ta hanyar cewa " Inaso zan kawo miki ita kamar yadda nayi miki alkawari idan auren ta ya tashi, ta samu miji har an tsaida rana wata daya, in sha Allah a tsawon wata dayan nan zata zauna a wajenki, a matsayin ki na mahaifiyar ta sai kiyi duk abinda ya dace, kiyi hakuri da Kaddara, kiyi hakuri!" Wani irin yar taji har cikin kanta, Iman dinta har ta girman da zata yi aure, rayuwa na gudu sosai, tana tuna lokacin da ta dawo masa da ita, da irin tashin hankalin da ta shiga a rashin ta wanda bata taba tunanin zata dawo daidai ta cigaba da rayuwa ba, a lokacin tunani take rayuwarta ta kare gaba daya, amma kuma sai gashi ta cigaba da rayuwa duk da babu ranar da zata fito ta fadi bata tuna yar tata ba, amma ya zatayi? Mutane na fifita al'ada akan addini. Ta sani sarai uwa ce taka da ikon rik'e yarta har zuwa aurenta, tare da sharadin kula da duk wata bukatar ta daga mahaifin ta, sai dai idan anji tsoron tarbiyyar da zata samu a wajen uwar, toh amma a lokacin wa take dashi da zai tsaya mata? Bayan iyayenta da take ganin su a matsayin gatan ta sun kekashe kasa sun ki amincewar da rikon nata a wajenta? A lokacin da akwai karancin shekaru a tare da ita, amma da ace yanzu ne, babu me raba ta da yarta kuwa, duk yadda zatayi zatayi ta tabbatar da ta rik'e ta a wajen ta. Ta bata kulawa da dukkan gatan da take bukata. "Allah ya sanya alkhairi, ya nuna mana lokacin." Kawai tace dan bata kuma san me zata ce masa ba, taji dadi da ma ya cika alkawarin sa, zatayi kokari a dan zaman nan ta koya wa yarta kaunar ta da sabawa da ita da yan uwanta, sannan ta nusar da ita rayuwa da yadda zata kula da auren ta. Sallama sukayi da alkawarin ana gobe zai kawo ta, zai kira ya sanar mata. Godiya tayi masa dan har gobe tana ganin kima da mutuncin sa, mutum ne shi na gari, me kirki da son iyalin sa. Bayan gama wayar da sukayi ne zuciyar sa ta gwada masa kiran Zeenat ya sake gwada tankwarata, idan Allah ya taimake shi ta hakura sai yafi kowa murna, dan yanzu bashi da babban tashin hankali kamar auren zeenatun da yake da yakinin zai iya zamar mata wani Babban tashin hankali a gaba. Kiran nata yayi, tana dagawa yace ta matsa daga wajen kowa zai yi magana da ita, da ido ta kalli Mama dake zaune ana maida maganar auren Zeenat din da Hajiya ta fice zuwa tsakar gidan. "Abba na fito." "Yawwa zeenatu, magana nake so muyi a matsayi na, na mahaifin ki, kin san dai ba zan taba zabar miki abinda zai cutar dake ba, ba kuma zan ga cigaba a gareki na dakushe ki ba, ina neman alfarma, kiyi hakuri da Bashir ki kawo wani ba shi ba,nayi miki alkawarin tsaya miki kinji?" Gabanta ne ya fadi, a tunanin ta an gama wannan babin, sai gashi Abban ya dawo da shi yana kuma kokarin daure ta da jijiyoyin jikinta. " Kina jina zeenatu?" Ya sake fad'a cikin yanayi me wahalar fassarawa Shashekar kuka yaji, ta fashe da kuka cikin muryar kukan tace " Dan Allah Abba kayi hakuri?" "Ai ba laifi kikayi min ba Zeenatu, alfarma kawai nake nema a matsayi na, na mahaifin ki." "Abba dan Allah kayi hakuri, wallahi ba zan iya hakura da Bashir ba." Kamar saukar aradu haka Abba yaji, ya dafe kansa ya shiga karanto innalillah wa inna ilaihi rajiun, babu babbar jarrabawa irin yayanka suyi rashin sa'ar miji, duk abinda yaje ya dawo dole kana ciki, kamar ka saida akuyar ka ne tazo tana ci maka danga, baya fatan hakan ta faru ga ita, shiyasa tun farko ya hakurkurtar da zuciyar sa be ga laifin ta ba sai na Mama, amma yanzu ya tabbata abinda Zeenat din take so shi Maman take goyan ba, dama mafiya yawan lokuta uwa na tafiya ne da ra'ayin yarta. "Shikenan zeenatu, duk abinda yaje ya dawo karki kuka da kowa, ki kuka da kanki." "Abba dan..." Kafin ta kai karshe ya katse kiran, Jan kafarta tayi ta koma ciki tana jin a ranta tayi abinda ya dace, a kalla ta yi kokarin kare soyayyar ta ko ba komai idan akayi auren Abban zai hakura ya sakko. "Lafiya?" Mama tace tana kallon ta. "Ya kukayi da Baban naki? Maganar dai ce ko?" Da kai ta amsa mata da eh, tsaki Maman taja "Shine kike kuka ko me? Ni wai Zeenat asiri Bashir yayi miki ne? Da bakya ganin kowa da komai sai shi?" Kanwar Maman Atika ta fad'a cikin bacin rai " Ni banga wani abun naci a Bashir din nan ba, tunda mahaifin yarinyar nan baya so toh a hakura mana? Iyaye maza sun fi mu tunani da hangen nesa." "Toh Atika ya za'a yi? Shi ma fa duk zuga ce wallahi, ai da be san da hakan ba sai bayan yaga mijin da yar lelen tasa ta samu, shikenan kuma sai kananan maganganu bansan daga ina ba, amma ina kyautata zaton daga wajen Gaji ne, dan ita kadai ce take sauya musu tunani da raayi dukkan su, ita kuma na tabbata munafurcin Iman ne dan ko yaushe tana wajen ta." "Duk wannan ta tunani ne Yaya Hajara, bamu da tabbas din hakan, kinga dai yadda Dr ya dage ya kamata ace kin bashi dama kinji ta bakin sa akai." "Kyale shi kawai, zai sakko ne." "Me yace miki?" Ta tambayi Zeenat din tamkar abin be dameta ba. "Cewa yayi nayi masa alfarma na hakura da Bashir." "Ehen kinji? Har ya saukar da kansa a matsayin sa na mahaifi yace yana neman alfarma kema Yaya Hajara kinsan da matsala." " Me kika ce masa ke kuma?" Taki amsa atikar ta tambayi Zeenat din. " Hakuri na bashi." Tace tana rakubewa a gefen Hajiya da tunda aka fara maganar bata saka musu baki ba sai lokacin " Gaskiya da kun hakura kun bi zabin Ibrahim, a kalla shi namiji ne yafi mu dukka tunani da hangen nesa." " Hajiya toh ya za'a yi? Lokaci ya riga ya wuce bata kula kowa sai shi, yaushe zata fara daga farko kafin ma ta samu saurayin su fuskanci juna a zo maganar aure." " Duk wannan me sauki ne akan ka dauki dan ka, ka kaishi inda zai Sha wahala." " It's better to marry late than to marry wrong." Atika tace tana girgiza kafarta " Khair in sha Allah, babu abinda zai faru." Maman tace a kasan zuciyar ta tana jin tsoron abinda zai je ya dawo, ita kanta ta fara tsoron yadda Abban ya kafe ta tabbata akwai babban dalili, amma kuma ta Ina Zeenat din zata fara? Hasalima bata da farin jinin samarin duk asalin su Iman suke so sai ita maman tayi amfani da wannan a juya mata kansu zuwa Zeenat din dan ba zata iya gani Iman din tayi aure musamman auren babban gida ita kuma Zeenat din na zaune a gida. ***Da sauri ya karasa part dinsa yana jin kayan na masa nauyi sosai, yau tun safe Bubu ya Aiko masa da kaya sannan ya bukaci ganin sa a kofar part dinsa dan shiga tawagar sa zuwa Fada, haka ya tashi ya shirya ba dan yaso ba ya fita. Tun lokacin sai yanzu ya samu dawowa part din sa, yana shiga ya hau cire kayan yayi wurgi da rawanin yana jin shi sakayau. Allah Allah yake ya samu feedbacks din aikin da ya saka Musaddik sai gashi kuwa ya kirashi adaidai lokacin, dagawa yayi yana rage daga shi sai singlet da boxer kasancewar zafi ya fara hurawa kadan kadan ba kamar kwanakin baya da ake sanyi sosai ba. "Gani fa ga mutumin ka." Musaddik yace yana dagawa "Da gaske? Sharp sharp haka? Ok bari na kiraka Video Call." Ya katse sannan ya kira video call, a daidai saitin fuskar Bashir Musaddik ya saka wayar yadda yana dagawa Moh zai fara ganin sa. Yana durkushe tamkar me neman gafara, wata dariya ce ta zowa Moh, yayi murmushi kawai yace "Oga Bashir barka da warhaka." "Dan girman Allah ranka ya dade kayi hakuri, wallahi bansan gidan da kaje Neman aure bane nima naje, wallahi kuskure ne kawai amma kayi hakuri." "Ai ba laifi kayi ba Bash, ni hakan yayi min dadi sosai, kuma ina tayaka murna, kaga ni da kai mun zama yan uwa tunda zamu auri yan uwa." "Tuba nake ranka ya dade!" Yace yana kasa da kansa "Dago kanka bash, bafa wani laifi kayi ba, aiki nake so na baka, bana son kuskure ko kadan a ciki, idan har kayi min yadda ya dace akwai babban tukuiwaci." "Hakan shi yafi komai sauki a wajena ranka ya dade, fadi ko menene ." "Yaushe za'a je tambyar maka auren?" "Gobe ne ranka ya dade, amma idan kace a fasa na fasa wallahi." Girgiza kai yayi " Ba za'a fasa ba, Ina so idan sun je su nemi a saka musu wata daya!" " Wata daya!" Ya zaro ido " Wata biyar nace ko shekara, ban shirya ba wallahi,dan dai bana son na rasata ne." " Ba zaka taba rasata ba, ni zan maka komai na auren tun daga lefe har gidan zama zan baka, ni dai kawai kayi duk abinda nace kayi." Dukawa yayi jiki na rawa " Nagode nagode Allah ya kara girma, zanyi duk abinda kace, ba zan yi komai ba sai da sanin ka." " Good, yanzu aikin me kake?" " Buga buga kawai, sai kuma aiken Hajjaju idan ya tashi." Dariya sosai Moh yayi, ya hangi tsantsar mutuwar zuciya da son zuciyar a tattare da Bashir din, mikar da yan yatsun sa yayi baya, ya dawo dasu gaba suka bada sauti kafin ya katse dariyar yana zama so serious. " Abinda nake so kayi min, zaka ji daga bakin Musaddik, bana son kuskure ko kadan, komai Ina so ya tafi cikin tsari , Ina so gobe ka dauki hanyar Katsina, zan aiko maka da sako ka kaiwa Gimbiya Zeenatu, hakan zai sake goge shakku ko wani tunani akanka." " Nagode ranka ya dade, nagode nagode." " Karka damu, kai dai kayi abinda nace, bana son kuskure ko kadan!" " Da yardar Allah zaka same ni da bin duk umarnin ka. " Daga masa kai Moh yayi sannan yace " Guy!" " Yeah Captain!" Musaddik yace yana matsawa daga wajen da Bashir din yake "Ka kula dashi sosai dan dan iskan kansa ne, duk da be isa ba, amma dai bana so a samu matsala har zuwa ranar daurin auren, watch him and report anything da be maka ba." "Karka damu, babu ma abinda zai faru. " " Yau nayi zaman fad'a, kamar nayi kuka wallahi, wannan yazo ya fadi yayi gaisuwa, wanna yazo ya ce makwafcin sa kaza, wannan suzo maganar aure, wannan ta kawo karar mijinta wannan ya kawo karar matar sa, maganar gado, kai abubuwan da mugun yawa, kamar na gudo nake ji, nasan iya zaman da zan Bubu ba zai raga min ba wallahi, har na fara ramewa. " " Haka zaka hakura kayi abinda yake so, iyaye dole a bisu ayi musu yadda suke so. " " Haka ne dama, shiyasa na matsu nayi auren nan nima na zama me yancin kaina, kasan aure fa yanci yake siyo ma da martaba ba komai Bubu zai dinga matsa min ba da zarar yaga nima na zama dan gari a harkar. " " A harkar me? " " Harkar auren mana, ina fita daga novice zai yanta ni, kwana kad'an kaji nima ana Daddy, Daddy! Wayyo I can't wait. " " Kaifa yanzu baka da magana sai ta aure ko? Wannan sanyin ne ba komai ba. " " Sanyi ai ya wuce kuma, ba zan kara yarda na sake wani sanyin a gauro ba wallahi, haba Malam ai an ji jiki kawai. " " Dan air. " Musaddik yace yana dariya " Yan air dai, Wa ma ya kaika ne? Gwara ni wallahi kowa yasan uztaz. " " Nima haka ai. " " Fadawa wanda be sani ba toh. " " Toh ai idan har Moh uztaz ne toh tabbas ni sai da shehin malami, kai din? Ina dai tausayin yar mutane da zata shigo hannun tuzuru irin ka wallahi. " " Naji karka bata min tunani, jeka zan neme ka anjima bacci zan." " Hahaha, shikenan sai na jiki, angon Fatiti. " " Musaddik.!!! " Ya furta da karfi " Sorry sir, angon Fatima. " " Zaka shigo hannu ne wallahi, sai na saka an samin kai frog jump. " " Idan wannan ne ai na gaji da yi, a chanja wani punishment din dai Captain. " Kashe kiran Moh yayi, yasan ya biye Musaddik sai su cinye lokacin suna abu daya, wurgi yayi da wayar gefe ya kwanta dan rama baccin da Bubu ya katse masa. 1/18/22, 19:54 - Buhainat: Halin Girma      15 _*Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._* *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw _________________________ •••••••••? Kasa fitowa tayi, tana taraddadin yadda zasu karbe ta, ji tayi an bud'e kofar bangarenta, taji muryoyinsu a lokaci daya suna mata sannu da zuwa "Yau ga Fatima,sannu da zuwa dota, sannu da zuwa." Wata farar mata da a kalla zatayi sa'ar Mama ta fad'a tana riko hannun ta. Da wani irin yanayi take kallonsu su dukka, kowannen su kokari yake ya nuna mata kansa, mutum daya dage gefe tsaye ta harde hannayen ta a kirjin ta ta daga kai ta kalla, tun isowar su wajen ita kadai ce bata yi magana ba. Wani irin shock taji ta furta Mommy a tsakanin lips dinta, gyada mata kai matar tayi da sauri ta isa gareta ta rungume ta tana sakin kuka, bata chanja ba ko kad'an daga yadda take a hoton ta da take dashi tun na zamanin yan matantaka, duk da ganin ta da ita a zahiri kadan ne amma ko yaushe zuciyar ta na manne da hoton mahaifiyar ta.    Tafi sukaji an saka daga bayan su, duk Kuma sai suka saka dariya har Iman din da kunya ta kamata ta sake shigewa jikin mahaifiyar ta tana jin wani irin son ta da kaunar ta. "Muje ciki ko?" Babban namijin ya fad'a yana nuna musu hanya da hannun sa. Sakin Mom din tayi, matar farkon nan ta kama hannun ta zuwa ciki hanyar da ta ga sun fito dazun.    A falo suka yada zango, kowa a cikin su kokari yake yaga ya nuna mata soyyayyar sa, da kallo kawai take binsu cikin mamakin dalilin da ya saka basa neman ta tsawon lokaci haka duk kuwa da soyayyar ta da ta hanga a tattare da family din. Tana da bukatar amsa saboda tasan yadda kowacce uwa take kulafucin danta musamman ita da aka dauke ta da karancin shekarun ta, tabbas a farko farko ta kan zo ta ganta tare da wani babban namiji duk kuwa da karancin shekaru basa barin ta tuna komai amma tabbas ta san anyi haka kuma Abba da kansa ya kara sanar da ita a wani lokaci da ta tambaye shi.    Kamar an jeho su suka shigo su biyu, suka yo kanta da gudu macen ta rungume ta tana sakin ihu, namijin kuma ya durkusa a kusa da su yana dariyar farin ciki "Welcome sister!" Yace bayan macen ta saketa ta zauna tana maida numfashi "Welcome sis!" Tayi saurin fad'a itama tana hararar sa "Sannun ku." Tace tana murmushi tana mamakin su, "na riga shi ganin ki, na rigashi yi miki magana dan Allah ni kadai zaki so kinji? Dama kullum ina jin haushin bani da big sister sai wannan coconut head din , sai gashi na samu yanzu, I'm so happy wallahi, da k'yar na bari aka gama islamiyya yau wallahi." "Amaani kin cika surutu wallahi, ai sai ki barta ta huta ko?" " Tell her Mamma, wallahi kamar na bugeta yau din nan ta bani haushi." " Kaifa ya sunan ka?" Ta tambaye shi " Amaan." Amani tayi charaf ta rigashi fad'a sannan ta dora "Nice hassana, shine husaini, na girme shi so nice babba."    Murmushi Iman tayi, so adorable yaran, "Oya ku wuce kowa ya cire uniform dinsa kuzo muyi dinner, nasan Iman ta gama gajiya tana so ta huta" Mamma tace tana mikewa " Zayd, Ya Mubarak dinner na table." " Ni sai nace gida gaskiya, I'm full." Ya Mubarak yace yana gyara zama sosai. Kama hannun Iman Mamma tayi, suka wuce dining din tare da Zayd yana mata tambayoyi. Mommy na jinsu bata saka baki ba, dama kuma ita haka take da kara sosai, komai nasu Itace akai amma bata taba nuna musu iyaka akan nata, shiyasa suma duk wani abu da ya shafe ta toh sune a gaba gaba, sai ta koma gefe ta zama yar kallo. Bata da hayaniya kamar dai Iman koman ta a nutse takeyi musamman kuma abun da ya hadu da arziki sannan ga ilimi both boko da islamiyya. Kujera taja gefen Iman din da suka bar mata ta zauna daidai lokacin Amaan da Amaani suka dawo kowa ya sauya kayan sa zuwa na zaman gida. Amaani na kokarin fara surutun ta suka hada ido da Mommy, kallon da tayi mata kadai yasa taja bakin ta tayi shiru har suka gama babu wanda yayi magana.    Falon suka dawo, a lokacin Ya Mubarak da Zayd suka yi musu sallama akan zasu dawo gobe kowa da family dinsa, har bakin mota Mommy ta rakasu ta dawo sai kawai ta wuce dakin ta, ta bar Mamma da yaran suna hira, ta lura da yadda Iman din ke jin kunya da rashin sabo amma kuma tasan wace Mamma ba zata taba barin ta ba har sai ta tabbata ta sake dasu, balle uwa uba iyayen magana su Amaani su kadai ma sun isheta.    Kwanciya Mommy tayi farin cikin zuwan yarta na ratsa ta, wayar ta ta dauka ta kira number Abba, lokacin ya gama cin abinci kenan yana kokarin duba wasu papers dinsa a computer yaga kiran nata, tsaywa yayi da abinda yake yi ya daga. "Nagode sosai IB, naga Iman fiye da yadda nayi tunanin ganin ta, hankali na ya kwanta dan na tabbatar da tarbiyyar ta, kayi ma maman tasu godiya dan Allah. " " 'yaya amana ce a garemu da dole mu kula dasu da tarbiyyar su, domin dole ne Allah ya tambaye mu a ranar gobe kiyama, banyi komai ba face abinda ya zama wajibi na." Ya fad'a yana jin chan kasa zuciyar sa da zata samu labarin abinda ya faru a zaman Iman din da Maman daku tabbas za'a iya samun matsala, abu daya ya hanata yin wani katabus akan maganar Iman din, tabbatar mata da yayi akan bata da matsalar komai, kuma tana hannu na gari.     Sallama sukayi ta runtse idon ta, hasashen irin shirye shiryen bikin da zatayi kawai take, ba zata bari ta koma ba har sai tayi mata nata kalar gatan da zata tabbatar da ita din yar gata ce.    Turo kofar akayi, ta daga kai ta kalli Iman din cikin rakiyar Mamma. " Sai ki gudo ki bar mu? Gamu toh mun biyo ki." " Na zata wajen Hajiya kuka yi ai." " Munje chan din ma." " Ok." Tace tana mikewa zaune. " Bari na duba yaran chan, ina ga daga haka zan kwanta, sai da safe Iman." Murmushi Iman tayi ta amsa sannan mummy tace "Sai da safe Yaya." Fita tayi ta ja musu kofa cike da farin cikin kwanan da ya da uwar zasuyi yau. "Dawo kusa dani." Dawowa tayi ta zauna daf da Mummy din, ta jawota ta dora kanta a saman cinyar ta, cikin tattausan lafazi tace "Kin girma sosai Iman, nayi mamakin yadda kika kara chanjawa akan last da Dr. Ya tura min hoton ki, amma kuma naga baki da walwala sosai, ko rashin sabo ne? Ko kuma hakan halitta ne?" Murmushi tayi me sauti, nutsuwa ta saukar mata, taji da gaske she's safe fiye da yadda ta taba ji a rayuwa ta, a hankali ta furta "Babu komai Mummy." "Shikenan, ki kwanta idan kika huta duk maganar da zamuyi sai muyi kinji?" Ta shafa kanta tana murmushin. Daga kan ta tayi ta ajiye a saman gadon ta fita daga dakin. Wajen kayan ta, ta nufa ta ciro wayar ta, tasan ya mata magana a WhatsApp bata samu sukunin dubawa ba. Misscalls ta gani ta whatspp call sai messages dinsa da ya turo mata. Sakon ta fara dubawa ta,tabi kowanne tayi reply ta bar daya da yake tambayar ta size din undies dinta kunya na kamata. Godiyar kudin da ya bata tayi masa hade da addu'a tana turawa sai gashi yazo online, maimakon ya amsa sai taga yana kiranta, kasa dagawa tayi kunyar tambayar da yayi mata na dawo mata _" Baby menene size din B da P?"_ Haka ya rubuto mata fa, kin dagawa tayi har ta katse ya sake kira ta kara bari ta katse, _" Please dan Allah ki daga, kwana nawa banji muryarki ba? Sam na manta zan iya kiran ki ta whatspp call sai daxu, please ki taimaka ki daga inaso naji muryar ki wallahi."_ _" Ni dai muyi chatting."_ _" Ni dai ki daga, zan sake kira. "_ Kafin tayi reply sai ga kiran sa, ta daga da k'yar tanayin nesa da wayar. Ajiyar zuciya ya sauke da karfi " Kin iya rigima wallahi, haka kawai sai anyi punishing dina ko? " " Um um. " "Toh naji, ya hanya? Ya me ya faru?" Cikin zumudi tace " Ina cikin farin ciki yau, komai ya tafi yadda ya kamata, kowa so na yake kamar zai goya ni. " "Mum fa? " " She's just like me, kamar ni take har I don't care attitude dinta, amma deep down she's super happy, na gani a idon ta. " Dariya ya saka " Alhamdulillah, nayi miki murna sosai sosai, Alhamdulillah. " " Nagode sosai. " " Yau kwana zakuyi nasan da Mum kuna magana. " " Anya? Kila ko sai an kwana biyu. " " Bari ki gani dai. " " Uhum tohm shikenan. " " Baki min replying dayan chat din ba, abinda na tambaye ki. " Dauke wuta tayi gaba daya kamar bata ji ba, ya sake maimaitawa yana rik'e dariyar sa, ya gano kunya taji tunda taki daga wayar sa, bata san halin sa ba lallai, rage murya yayi sosai yace " Dan Allah ki fad'a min Aunty zata yi min fad'a gobe idan nace ban tambaye ki ba, dan Allah. " Shiru tayi masa " Please ki fad'a min, ko da yake ma zan iya chanka ai, bari muga... zasu kai size..." " Innalillahi. " Tace tana zare wayar gaba daya ta kashe ta. Tuntsurewa yayi da dariya kamar zai fado daga gado, yayi saurin komawa chat din ya hau rubuta mata "Sorry matar Muhammad, daga wasa sai ki yanke min waya? Toh ai ban gama jin muryar ki ba wallahi." Tick daya ya gani alamar ta ma kashe datan gaba daya, gwada kiran ta yayi aikuwa yaji switch off. Tsaki taja ta wurgar da wayar , ta rasa me yasa me maxa sam basu da ta ido, zata dade kuwa bata yi waya dashi ba. Samun kanta tayi da yin murmushi sai kuma ta hade fuska ta sake jan tsaki. Ya ma bata haushi gaba daya. Har ta gama shiryawa ta jona wayar a charge amma bata kunna ba har lokacin Mum din bata shigo ba, gefen gadon ta kwanta cikin lallausan zanin gadon da yake kamshi sak irin kamshin da mummy din take, tana rufe idon ta, ta shigo rik'e da cup a hannun ta. " Iman, kinyi bacci?" " A ah." Tace tana mikewa zaune " Yawwa ungo karbi kisha, fresh milk ce nayi miki warming dinta." Karba tayi, tayi godiya ta kafa kai ta shanye tas, ta tashi da cup din rik'e a hannun ta " Ajiye shi anan zan kira azo a fita dashi." A saman fridge din jikin kofar ta ajiye ta dawo ta zauna tana so abinda tasha ya dan yi settling a cikin ta. "Zo ki tayani duba wannan kayan." Tayi maganar tana bud'e profile dinsu a cikin system din, gefenta Iman ta zauna suka hau duba wasu jewelries, duk wanda Iman din tace yayi kyau sai tayi starring dinsu, sai da suka gama tsaf sannan suka dawo kan wanda akayi starring din suka sake fidda guda biyar masu kyau sosai, biyu gold biyu azurfa sai daya fashion ne daga wani babban company, a take mummy tayi payment din da komai sannan tace Iman din taje ta kwanta zata karasa wani aiki.       Tana kwanciya bacci ya dauke ta  dama ta gama kurewa sosai tana lura da Mummy din bata so ta matsa daga kusa da ita ne. Cikin bacci tayi juyi ta jita a bayan ta, daga nan bata sake farkawa ba sai da aka kira sallah. ***Gaba yayo ya bar su a chan su karasa siyayyar abinda zasu siya dan yaga abin nasu bana kare bane, a Kano ya dira domin su karasa abinda zasu karasa da Bashir saboda yadda lokacin yazo sosai. A gidan sa ya same shi, suka jira Musaddik ya karaso suka fita zuwa wata unguwa da tafi kama da a kirata da unguwar talakawa kai tsaye, tunda suka shigo layin Moh ya tabbatar da zai samu yadda yake so, lallai Musaddik mugu ne na gaske, idan ba haka ba ya rasa unguwar da zai samo ya siya gida sai irin wannan unguwar. A daidai wani kofar gida karamin gaske suka tsaya, suka fito a tare wanda zasu gani yana tsaye yana jiran su, yana ganin su ya karaso bakin sa cike da murna ya gaishe su, sannan ya bud'e musu gidan yace su shigo.    Siminti ne gaba daya tsakar gidan sabo yana ta kamshi, bashi da girma tsakar gidan sosai dan be fi yaci tabarma days da rabi ba, a gefe yar karamar rijiya ce saboda rashin ruwan unguwar.    Dakunan guda biyu da suka kasance falle-falle ya bud'e musu suka shiga nan ma ko ina an masa fenti yana ta kamshi, babu abinda ba'a saka ba hatta karamin gado da kujeru an saka,da yar karamar tv babu batun fridge ko cooker gas balle azo maganar su AC da sauran kayan more rayuwa, kitchen din babu komai dama sunyi da nufin daga gida sai a kawo mata kayan kitchen suyi amfani dashi. Kitchen din karamin gaske ne dan mutum biyu ba zasu iya aiki a ciki ba saboda kankantar sa, balle a samu sukunin cika shi da kaya.    Fitowa sukayi ya rufe gidan yana sake washe baki "Ranka ya dade gidan yayi ko?" "Yayi sosai yadda nake so, sai ka sanar musu ba sai an kawo kayan gida ba ,iya kitchen ya isa shima karsu matsawa kansu duk abinda babu zaka saka musu." "An gama ranka ya dade, sai maganar lefe." "Ana gobe daurin aure za'a kai, an gama hada komai ina tunani." " Nagode Allah ya kara arziki." Be amsa ba, yayi gaba ya fad'a motar yana kallon tsarin gidan, murmushi ne ya kwace masa, ya girgiza kansa yana ayyana yadda zuciyar Mama zata buga ko kuma ta kusan bugawa,yayi alkawarin shayar da ita mamaki irin wanda bata taba tunani ko hasashe ba.   Kai tsaye wajen gym suka wuce, ya kwana biyu be motsa jikin sa ba, yana bukatar hakan saboda tafiyar da sukayi be samu lokaci ba. Dariyar shakiyanci Musaddik ya dinga yi masa, ya tsaya daga abinda yake yana hararar sa "wai dariyar menene haka? Uhum?" " Naga yadda ka dage kake ta faman daga karafu nan nan ne wallahi, kar dai ka illata musu yarinya wallahi, kasan dai kai din tsohon tuzuru ne da yaki auruwa. " Robar ruwan da ya gama sha ya jefe shi dashi, ya goce ta fadi kasa yana sake tuntsurewa " Ka kiyaye ni wallahi. " " Anki din, daga fadar gaskiya?" " Zan kamaka ne, naga kafarka a gida na wallahi. " " Gidanmu dai. " Towel ya ja ya goge gumin fuskar sa, ya biye wa Musaddik zai dauke hankalin sa ne ga abinda yake shirin yi. Wayar sa ya dauka akan dan table din wajen yayi dialing number ta, sai da ta kusan katsewa sannan ta daga. "Huh!" Ya furzar da iska yana jan numfashin "Ranki ya dade an gama jamin ajin ne?" "Ina wuni?" Ta kautar da maganar ta hanyar gaishe shi "Lafiya lou, ya gida ya kowa da kowa?" "Alhamdulillah." "Masha ALLAH, yaushe Abba yace zaki dawo?" "Be fad'a ba, amma naji Mummy tace ba zan dawo ba sai ranar." "Ranar? Yaushe kenan?" " Ka cika tsokana wallahi, nima ban sani ba." "Ke kuma kin cika kunya ba, sai kici sai ranar auren mu kawai." " Allah zan kashe wayar." Ta fad'a tana turo baki, dariya yayi yace da sauri " Allah ya baki hakuri Matata." Shiru tayi tana wasa da album din hotunan da Mamma ta bata bayan ta mata bayanin kowa da yake jiki. "In sha Allah ana gobe za'a kai lefe, kinsan sha'anin rayuwar, Allah yasa be makara ba." " Be makara ba, Allah ya saka musu albarka." "Amin Matata, nagode sosai da bani dama da kikayi, in sha Allah ba zaki yi Dana sani ba." "Kullum godiya? Ni me nayi?" "Ai wai kinga dai yanayin yadda abubuwan suke." "Babu komai Allah ya tabbatar mana da alkhairi." "Amin Amin amarya ta." Yar karamar dariya tayi, shima ya tayata kafin suyi sallama. Mamma ce ta shigo dakin rik'e da jaka babba, sai me aikin gidan dake biye da ita da wasu kayan suma da yawa, ajiye su sukayi a gefe me aikin ta fita kafin ta sake dawowa ciki dauke da tray da aka doro chicken pepper soup da wani cup shima cike da abu kamar kunu, sai wani da akayi ma hadin fruits aka saka madara. Dora shi tayi a saman drawer ta fita ta barsu. Da hannu Mamma tayi mata alamar ta taso, ta taso ta zauna a k'asa in da Mamma din ta nuna mata, tray din ta sakko mata dashi tace maza ta cinye naman tas, idan ta gama akwai bakuwar da zata shigo wajenta, Itace me jakar chan. Tun zuwan ta gidan take faman shan abubuwa, a dan lokacin tayi masifar chanjawa, tayi kara fari da kiba jikinta ya sake murjewa sosai. Ita kanta tana jin da gaske ta kai mace, tana jin zata iya karawa da ko ma wace amma a dah, bata da wannan confidence din. Bata kyuwar cin duk abinda aka bata dan da bata samu wanda zai dubeta ba balle har ya bata abinda yasan zai amfane ta. Shiyasa ta bada himma take yin duk abinda za'a sata. ***A bangaren gidan su Iman kuwa, bayan dawowar Abba sai da suka sake wani rikicin da Mama, wanda ya saka kowa ji har aka dinga ganin baiken Maman, amma kishi ya rufe mata ido matar Abba Musa na zugata tayi masa tijara son ranta, be kula ta ba don a yanzu baya sakata cikin jerin masu hankali, yana mata uzurin kishi ne ya sakata yin wasu abubuwan. Bayan kamar kwana biyu da dawowar sa ta same shi har daki ta bashi hakuri abinda ya bashi mamaki sosai, hakura yayi ya sakko amma ba wai don ya hakura da maganar Iman ba, yana nan sai ya yi mata hukunci daida abinda ta aikatawa yar sa. Shirye shirye ya kankama sosai, mama babu zama kullum tana hanyar kasuwa tun da ta samu labarin cewa Bashir yace iya kitchen kawai zasuyi, hakan yayi mata dadi shine ta maida hankalinta sosai wajen kawata kitchen din dan ta tabbata gidan ba karamin gida bane, dole ne su fita kunya ta hanyar hada mata kitchen din yayi sosai. Duk abinda ta tambaya Abba bata yake dan baya son wata doguwar magana, hankalin sa gaba daya yana kan maganar auren Iman, da yadda daurin auren zai kasance domin yasan za'a yi taro ne irin wanda ba'a taba yi ba, manyan mutane zasu halarta da yan siyasa da manyan sarakunan k'asar nan da ma na ketare. Duk abin nan Mama bata san komai akai ba, bata taba tambayar shi game da Iman din ba ko yadda nata tsarin yake, shiyasa kawai shima ya rufe ta ruf ya barta da abinda take yi. A yadda tsarin bikin yake, alhamis za'a yi kamu, juma'a a daura aure sai asabar dinner kamar yadda Zeenat din suka zauna suka tsara ita da Bashir bayan ya sanarwa Moh da tsarin ya kuma bashi go ahead. Tsarin bikin da su kuma chan masarauta suke shirya wa biki ne gagarumi za'a yi a Kano da Adamawa, kowanne kuma kwanaki za'a dauka anayi tun daga asabar din washegarin bikin, na Kano za'a fara kafin a koma adamawa in da za'a kai amarya. Kamar yadda yake a tsari, ranar alhamis za'a karbi lefe, lefen Zeenat da Iman, wanda Mama tayi gayya, gayya irin ta ban mamaki, tana Kuma sanarwa mutane suzo suga lfen Zeenat dan ta tabbatar za'a ga kayan da baa taba gani ba. Yan uwa da abokkan arzikin Mama su suka cika gidan, aka shirya kaya na mamaki, aka gyara gidan. Wata sister Mama ce tazo ta sameta tana zaune cikin kawayenta ana shewa, ta jata gefe hankali a tashe tace "Yaya, wani labari naji fa, dangin mijinki na hirar basu san Ina wajen ba, naji suna cewa Iman tayi goshi ta samo jinin sarauta, ana ma tunanin dan sarki ne duk da Basu tabbatar ba ana boye zancen ne amma kamar hakan ne." Wata irin dariya Maman ta saka, har da hawaye " Kinji ki Fatima da wani zance, su fa basu san kan zancen ba, maganar Zeenat ake ba Iman ba, na ji wannan zancen tun bayan zu ba ai, kawai na kyale mutane ne yadda abun zai kada su, ba dai anjima kadan zasu iso ba? Zamu gani ai." " Allah yaya? Kin Kuma tabbatar da hakan ne?" " Zaki gani ai." Tayi gaba tana murmushin mugunta, ba karamar kunya tasan za'a sha ba a lefen Iman din ba. Hmmm ***Assalamu alaikum sisters fatan alkhairi ga kowa da kowa. In Sha Allah hutun mu zai kama asabar da lahadi, domin kowa ya samu damar aiwatar da wani abu me muhimmanci a rayuwar sa, sannan mu kula da gidajen mu da iyalan mu dukka, mu bawa yaranmu da mazajenmu lokacin da suke bukata daga garemu. In Sha Allah Monday to Friday za'a samu posting in sha Allah, sai dai wani uzurin ya gifta. Sannan masu korafin ba'a basu page biyu ko uku a rana, wani page dayan yayi wasu pages din guda biyu, so idan hakan ne gwara dayan me tsawo mu tafi a hankali har Allah ya bamu ikon kammalawa. Zafafa biyar na godiya da zabin su da kuke a kowanne lokaci, dan Allah mu cigaba da yi ma juna uzuri kuma mu kyautata lafazi a tsakanin mu domin magana me kyau ma sadaka ce. Masu sharing novels group group una weldone kunji? Dan Allah ku daina babu kyau, ka sowa dan uwan ka abinda kake sowa kanka hakan na cikin cikar imanin mumini. Rano 1/18/22, 19:58 - Buhainat: Halin Girma 14 _*Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._* *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw _________________________ *_MACE SAI DA GYARA_*💃🏻💃🏻 _GYARAN MA NA KAMFANIN TURAREN:_     *YERWA INCENSE AND MORE* *Ƴar uwa ta hanyar gyara ne kawai zaki cigaba da amsa sunanki mace hamshaƙiya a wajen miji ba tare da ya ga kin tsufa masa ba.* _Maza garzayo ki gyara jikinki da kayan ƙawatattu kuma nagartattu irin namu na gida da suka sami haɗi na musamman da babu cutarwa a ciki. hadin bornu/chadian na kamfanin turaren YERWA INCENSE AND MORE_ *_Muna da haɗin_* _Turaren wuta kala kala na gidah_ _khumrahs_ _Kullaccham_ _Turaren wanka_ _Turaren Kaya_ _Turaren wanki_ _turaren mopping_ _Dukkanil al’ajab (Turaren tsugunno na Matan aure kad’ai)_ _khumratul al’ajab (khumrah ta jiki ta matan aure_ _Muna Gyaran jiki_ _Na amare_ _Da masu jego_ _Da sabulai masu gyara fata_ _Turaren tsugunno_ _zumar goran tula_ _Scented hair cream and spray (man kamshin gashi da gyara gashi_ _Akwaisu kujeran tsugunno _Dilke and halwa set_ _Burners da igniters da tong_ _turaren fesawa dana ruwa._ _wardrobe balls_ _scented pebbles_ _cotton wooly oudi incense_ _kabbasas_ _Da sauran kayayyaki da yawa da bamu ambata ba_ _Akwai ragi na musanman ga yan zafafa fans❤️_ _Muna bada sari, Ko sayi ‘dai ‘dai akan farashi mai sauƙi da rahusa. Ga mai buƙata sai ya nememu tanan 👇🏼_* _EMAIL:yerwaincenseandmore@gmail.com ko INSTAGRAM PAGE d’inmu:yerwaincense_and_more dama nambR mu:08095215215_ _MUNA TURAWA KAYAN MU KO’INA A FADIN NIJERIYA DAMA KASASHEN KETARE. 100% TESTED AND TRUSTED_ •••••••••? ***** Azahar sosai ya tashi, ya mike yana salati, daga curtains din dakin yayi yana mamakin tsawon lokacin da ya dauka yana baccin, wayar sa dake saman gadon ya dawo ya dauka ya bud'e ta, misscalls ya gani ya duba sannan ya ajiye ya fito zuwa falo in da yatar da abincin sa a jere cikin manyan warmers sai kuma wani dan basket da aka rufe shi da jan kyalle me kyau dake dauke da hoton heart, matsawa yayi gabansa yana kallo, "Menene wannan?" Yayi maganar yana rik'e kugun sa da sauri wani bafade ya shigo, ya rissina yace "Sako ne daga shashen Kilishi, inji gimbiya Laila." "Laila?" Ya furta cike da mamaki "Yaushe ta zo?" "Tun da safe, lokacin baka nan." "Dauke shi a kai sashen Ammi, ace ta ajiye." Sake dukawa yayi cikin girmamawa yace "An gama ranka ya dade." Juyawa yayi ya koma ciki, yayi wanka sannan ya shirya yana tunanin dawowar Laila a irin wannan lokacin da yasan suna tsakiyar karatu ne. Fitowa yayi ya tsattsakuri abincin ya fita wajen ammi dan be samu ganin ta da safe ba. A gabanta ya tarar da sakon nasa, ta bishi da kallo sannan ta kalli kwandon da yake na Kaba. Sai da ya zauna ya gaishe ta sannan ya saka aka miko masa basket din "Ammi kinga ko? Menene ma'anar haka?" "Ni kaina nayi mamaki, amma kuma kasan dama hakan zata faru idan har ta samu labarin auren ka." " Bana son wata matsala gaskiya, zan aika da sako wajen Kilishin dan ba zan dauki rainin hankali ba." " Ka rabu dasu, karka yarda su bata maka rai har kayi tunanin biye musu, ka cigaba da addu'a nima kuma ina tayaka mahaifin ka ma,.ba zasu taba samun nasarar abinda suke so ba." " Shikenan Ammi, dan Allah aje a kona basket din nan dan bana son ko ganin sa." " Shikenan, ka cigaba da walwalar ka karka yarda makiyinka ya gane weakness dinka." " In Sha Allah Ammi." " Allah yayi maka albarka." " Amin." Ya amsa yana jin tamkar dawowar Laila akwai wani babban dalili " Yawwa na kira Fatima akan lefen ka, zata hada komai in sha Allah, idan yaso sai su tafi ita da kai da wata dai cikin su, Takawa ma yace shi zaiyi komai, amma duk da haka Fulani tace yayi nasa itama zatayi nata mu ma nan sai muyi namu." "Wayyo ni dan gata." Yace yana murmushi "Ammi gatan kar yayi min yawa ai." "Ba zai ba, Allah yasa ayi damu kawai, amma dole sirikata taga gata." "Uhm.. Allah sa idan tazo karta kwace min wajena." " Dole ne ai, kasan dai yadda nake son ya mace ko?" " Shikenan sunana sorry wallahi." Dariya Ammi ta saka " Aikam ka shirya tun yanzu." " Shikenan, Muhammad kana ji? Kayi hakuri da duk abinda zaka gani." Ya fad'a cikin yanayin kalar tausayi, dariya sosai ya bawa Ammi tayi sosai, kallon ta ya dinga yi cikin tsantsar son ta, yana son Ammi da duk wasu halayenta, babu abinda yake so irin yaga tana farin ciki sosai, hakan yake sashi jin zai iya komai dan ganin ya faranta mata, ya dawwamar da farin ciki a kan fsukar ta, hakan kuma ba zai yiwu ba sai dole yaki karbar muradin Bubu, dole ya hakura da mulkin ko da yana so, saboda farin cikin Ammin Sa! ***Satin Mama daya cif a Katsina, ranar da zasu dawo ranar Bashir ya iske su a chan da dalleliyar mota da sha tara ta arziki, murna wajen Mama da Zeenat ba'a magana aka dinga turashi gida gida na dangi dan aga irin mijin da zeenatun ta samo, aikuwa nan da nan magana ta karade ko ina cikin family din Maman, anan wasu da yawa suka samu labarin bikin Zeenat din wanda aka saka wata daya kachal bayan Bashir din ya tabbatar musu da zaiyi komai basa bukatar komai hatta da kayan gida duk shi zai zuba, hakan ya sake fasawa Mama kai ta dinga hura hanci a lallai zeenatun ta ta dallo miji na kere sa'a, tausayi da farin cikin halin da ta tabbata Iman zata shiga idan har ta auri fakirin nan take, gashi dai su kam Allah yayi musu gam da katar dan yadda aka dinga maganar Bashir din a dangi kadai ya ishi Mama tutiya da alfahari. A motar ya kwaso su Zeenat na gaba gida na tashi cikin taken soyayya Mama da Marwan na baya har Kano, Zeenat ji take kamar tafi kowa sa'a a duniya dan da gaske take jin wani irin son Bashir din na ratsa ta. Sanda suka isa gida magriba tayi saboda basu taho da wuri ba yana faman zaga dangi, alwala aka kawo masa ruwa yayi, ya zauna Zeenat din ta shiga ta fito suka dasa sabuwar hira irin ta yaushe rabo. Cikin hirar ne yake fad'a mata lefe in sha Allah za'a kawo cikin upper week, zai sanar mata da ranar sai ta fadawa Mama, hakan yayi mata dadi har tana hasashen uban kayan da za'a kawo mata dan taga Bashir din me bajin ta ne sosai. Ranta fes ta koma ciki bayan ya tafi, ta labartawa Maman lokacin Matar Abba Musa ta shigo wajen Maman yi mata sannu da zuwa. "Haba ni nayi mamakin da aka ce manyan mutane ne suka zo neman aure gidan nan na tabbata dama wajen Zeenat ne, yarinya kakarki ta yanke saka wallahi." Tace tana dariya, murmushi mama tayi " Kice manyan mutane ne suka zo? Bani labari Binta." " Ai Maman Habib baki gani ba, wallahi manyan mutane ne kamar ma daga wata babbar masarauta, yadda naga mazan gidan nan sun rikice kadai zaka gane ba kananun mutane bane, na zata ma na Iman ne ashe na Zeenatu ne, Baban Walid be min bayanin da zan gane ba kinsan wajen lokaci daya suka zo dukka." " Aikuwa sune, kai kice dai manyan mutane ne, masarauta fa? Kai masha ALLAH abu yayi kyau wallahi." " Ai Maman Habib ba karamin dace Zeenat tayi ba wallahi, Allah dai ya kaimu bikin nasan za'a ga lefe na ban mamaki." " Bari kawaii, sai muzo mu tanadi kyautar girma da zamu fita kunya, na gode da kika sanar dani dan Dr ba lallai ya fad'a min ba muna yar tsama dashi." " Ai haka suke, basa fadar cikin su wallahi, itama kuma Gajin ba zaka ji daga bakin ta ba tunda komai suna fad'a mata ai." Tabe baki Mama tayi " Ai ni baki sani ba, so akayi a yi min bakin ciki." Sai ta rage murya " So akayi fa a hana Zeenat auren Bashir din nan, kuma ina kyautata zaton akwai saka hannun Gajin a ciki, toh in ba haka ba yadda Dr ya rikice akan maganar lokaci daya zaki gane zugashi akayi." Kama baki Matar Abba Musa tayi " Allah? Tab ashe an so yi miki tsakiyar da ba ruwa." " Ke dai bari, shiyasa na tsaya kai da fata, kinsan mutane basa son ka cigaba ko aga danka ya cigaba ko zai huta." " Zahiri, toh Allah ya kyauta, ban yi zaton hakan daga gareta ba." " Ai ba laifin ta bane, itama yadda aka dora ta haka zata tafi akai." " Eh kuma gaskiya, tunda kinga ai bata cika saka ido akan al'amuran mu ba." " Shine, koma waye kansa yayi wa, aure kam babu fashi." " Assalamu alaikum." Iman tayi sallama ta shigo, gimtse fuska Maman tayi,ta gaishe su matar Abba musa ta amsa a sake tana tsokanar ta da amarya amarya, murmushin yake kawai tayi tana satar kallon yanayin fsukar Maman, zuwa tayi ta fad'a mata anjima zata tafi wajen dangin Mamanta amma ganin Matar Abba Musa ya saka ta fasa ta wuce kawai daki ta karasa hade koman ta waje daya. Bayan tafiyar Matar Abba Musa ne ta fito ta samu Maman a kitchen tana rarrabe kayan da tazo dasu dangin su kuka kubewa da daddawa waje daya "Mama dama yau zan tafi gidan su Mamana." Tsayawa da abinda tayi, tayi ta kalle ta a mamakance tace "Yau? Yaushe aka yanke maganar tafiyar taki ban sani?" "Dama tun ranar da na dawo daga gidan Ya Maryam Abba yayi min maganar." "Toh! Shi zai kaiki kenan? Ko turowa za'a yi kije? Ko da yake mutanen da basu damu dake ba yaushe zasu turo? Wannan din ma nasan dan Dr yayi magana ne." "A ah tare da Abban zamu je." "Kutmar Uba!" Da sauri Iman din ta ja baya dan yadda ta ga Maman ta birkice lokaci daya " Ni za'a yiwa munafurci? Wato yace zai ganki saboda yaga tsohuwar matar sa ko? Dan an raina min wayo an maida ni wata sakarai. " " Dama... " " Dallah rufe min baki, wato gani shashasha an dauko raino an bani shine yanzu za'a nuna min bariki ko? Toh wallahi ba zata sabu ba wallahi kinji na rantse, ko ya barki ki tafi ke kadai ko ya hada ki da wani cikin yan uwansa ko Hafiz ne ma. " Shiru Iman tayi kamar ruwa ya cinye ta, tana jin sababin da Maman take kanta na kasa ita dai bata ce komai ba,me zata ce ma? " Bari yazo naji abinda yasa zai munafurce ni wallahi, bayan duk kokaarin da nayi wajen rik'e ki amma sam yanzu baya gani, dan kawai yar matsala ta ratsa tsakanin mu shikenan sai ya rufe ni. " " Uwata zo ki wuce, kije waje kina da bako. " Abba da yazo a lokacin yace yana kallon Maman, sum sum Iman ta fice kafin Abban ya dubi Maman cikin bacin rai yace " Kin bani mamaki Hajara, ban zaci haka daga gareki ba." " Dama ai haka ne, duk abinda mutum yayi ba gani za'a yi ba musamman aka ce da ba naka bane, amma ai Allah ya gani. " " Bakya tsoron Allah kuwa in dai haka ne, har kece zaki ce Allah yana gani? Kina tsoron haduwar ku kuwa? Bayan wahalar da kika bawa yarinyar nan har kina da bakin magana? " " Wahala? Ita tace maka na bata wahala kenan ? Oh shine ka shirya zaka kaita wajen uwarta kenan bayan na gama cin wahalar ta, duk abinda nayi baka gani ba. " " Kiki tsoron Allah, na gano duk irin rikon da kika yi wa Ummi, kinci amanata kin ha'ince ni, Ashe ke din fuska biyu ce dake ban taba sani ba." " Da yake yanzu hankalin ka ya koma wajen tsohuwar matar ko, ko nace tsohuwar karu... " A wani irin bacin rai ya daga hannu zai Kai mata mari, fasawa yayi yaji kamar an rik'e hannun zuciyar sa na tafasa, ba ya cikin mazan da zasu daki matar su,baya kuma fatan hakan duk da irin yadda Maman ta bata mishi rai. "Dukana zakayi Ibrahim? Dukana? Akan na fadi gaskiya, waya san auren da kukayi na gaske ne ko kuwa? Tunda mu dai babu wanda ya shaida, shine zaka dauki hannu ka dake ni akanta ko?" Ji yayi kansa yana sarawa, be taba tunanin tashin hankalin mAman ya kai haka ba, juyawa yayi da nufin barin kitchen din amma sai yaji ta rik'e masa riga ta baya "Wallahi ba zaka je wajen ta ba, wallahi ba zan yarda ba." Tsoro ne ya kamashi jin ta daga murya sosai, da sauri ya fizge rigar sa ya daga kafarsa wajen ficewa daga gidan ma gaba daya, ba zai biye mata ba, har a jisu a gidan abinda zai zamar masa abun kunya a wajen yan uwan sa . Shashen Gaji ya wuce da ya hango Iman tsaye da Musaddik a chan wajen gate din. Sako ya kawo mata daga Muhammad ya juya ita kuma ta koma cikin gidan. Tana shiga Mama dake tsaye a falo tana huci ta fisgota, saura kad'an ta fadi amma ta tsaya akan kafarta, kallon Maman take a tsorace dan bata dauka abin nata ya kai haka ba "Zan ga uban da ya isa ya fita daga gidan nan wallahi, wato kece munafukar kina so ki hada uwarki da ubanki ko? Toh wallahi baki isa ba na gama cin wahalar ki." Matsawa baya tayi ganin kamar dukanta Maman zatayi, kamar daga sama sai ga Habib kaamr an jeho shi, yayi saurin shiga tsakani yana wa Maman magana, " Lafiya Mama? Me tayi?" Bata jira amsar Maman ba ta yi saurin ficewa. Abinda Abba ya guda sai da ya faru, magana har gaban gaji, mama ta dage ba zai tafi ba shi kuma yace bata isa ta hana shi ba, haka sukayi ta kai ruwa rana karshe ya je da kansa ya dauko kayan Iman din ya bawa Habib ya saka masa a mota sannan suka tafi tana kallo ta cigaba da haukanta. ***Jingina tayi ta rufe idonta a lokacin da suka shiga jirgin, karon ta na farko kenan shiyasa take jin tsoro tsoro amma ta dake dan da wuya kaga abinda zai sa kaga weakness dinta, rashin tsaron da ake fama dashi a k'asar ya saka Affan yi musu booking flight kawai zuwa Abujan dan ba zai yi risking tafiya da Iman din a hanya irin wannan ba. Lokacin ma da Moh yaji labarin tafiyar tata sai da yaji tsoro Allah yasa ba a mota zasu ba, dan har ya gama shirya yadda zai siya musu ticket din kawai ya aikawa abba amma kuma baya so a san shine sai kuma tace masa a jirgin zasu, hakan ya saka shi samun relief. Tafiyar su Dubai ya saka basa waya sai dai chatting dan kar tayi saurin gano shi. Da zata tafi ya saka Musaddik kai mata dubu biyar a cikin envelope, sai da ya jinjina kudin kafin ya aika, kyautar sa ta farko kenan amma sai yake jin kunyar kai mata, tana bukatar manya manyan abubuwa a wajen sa amma akwai sauran lokaci. Tunawa da tayi da envelope din ya sakata cirota a cikin handbag dinta ta bud'e, murmushi tayi ganin kudi ne sai wani dan karamin note an rubuta I love you da shape din heart a k'asa. Sosai taji dadin kyautar tayi ta kallon note din tana jin dadi sosai. Cigaba da rikewa tayi a hannun ta har zuwa sanda zasu sauka sannan ta maida cikin handbag dinta tana jin wani irin feeling, she's nervous bata san wanne irin tarba zata samu ba. Tana ganin sanda Abba ya dauko waya bayan sun sauka yayi kira. "Mun sauka." Taji yace sai kuma yave "Owk tura min number shi." Suna tsaye ya sake duba wayar, number aka turo ta text message ya ciro ta ya kira ya fad'a masa yadda zai gane su kafin ya kashe yana cewa "Ummi muje gashi chan ma." Matse jakar hannun ta tayi, taja akwatin ta zuwa wajen wanda yake nufo su. "Welcome Sir." Yace cikin girmamawa, ba bahaushe bane jikin sa sanye da wasu uniform navy blue an saka number 5 a daidai aljihun. "Thank you." Karbar kayan su yayi ya zuba a booth sannan ya budewa Abba gaban motar ya zauna ita kuma Iman ya bud'e mata baya sannan ya jasu suka fita daga airport din. A daidai wani hotel suka tsaya Abba ya juyo bayan ya kalli Iman yace "Zanzo da safe in sha Allah, ki gaishe su, idan kina bukatar wani abu ki kirani." "In Sha Allah Abba, Nagode sai da safe." "Allah ya kaimu." Ya fice ya rufo kofar ya tsaya daga gefe yana kallo suka bar wajen. Ta cikin dark tinted glass din motar Iman take karewa garin kallo tana admiring ko ina musamman da dama magriba ta kawo kai dan wasu masallatan suna kokarin fara kiran sallah. A wani babban gida cikin jerin gidajen Babbar unguwar nan ta Maitama yayi horn, a hankali gate din ya shiga zugewa har ya karasa budewa gaba daya. A gefe daya yayi parking kafin ya gama daidaitawa wasu mata su uku da wasu maza biyu suka fito ta wata kofa suka nufo su dukkansu fuskar su dauke da farin ciki mara misaltuwa. 1/21/22, 12:57 - Buhainat: Halin Girma 16 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ***************** Yana zaune a daki kiran Aunty Faty ya riske shi, dagawa yayi yana tashi dan yasan dalilin kiran "Mun shirya tafiya kawai zamuyi kana ina ne?" " Ina cikin gidan bari nazo." Yace yana cire wayr, takalmin sa ya zura ya fito falon, fadawan dake wajn part din suka yunkuro jin motsin sa, da hannu yayi musu alamar kar su bi shi ya shiga takawa zuwa shashen Fulani da ya san a chan zai same su. Babban falon ta ya nufa in da ya tarar da su da yawan su, daga gefe akwatuna ne masu yawan gaske, da ido ya bi kayan kafin ya zauna suka hau tsokanar sa da ango ango, yawancin su yan uwan Ammin sa ne,sai dangin Bubu da matan abokan sa da badu da yawa sosai, komai Takawa yace sai Bubu yace masa ba sai an zo ba, ayi komai a nan din kawai. Yanzu ma dan dai abun kamar al'ada ne, shiyasa kawai Takawa yace ya kyale su idan yaso sai ya zama ba kowa da kowa ba. Anty Faty ce ta tashi ta hau nuna masa yadda kayan suke "Wannan saitin na Takawa ne, gasu nan 12 ne cip, kaya ne na alfarma komai da kasan ya kamata a saka an saka ciki, sai wannan masu pink din su kuma saitin Ammi ne, suma Sha biyun ne kamar na Takawa, wadannan kuma masu purple din na Hajja ne da dan tsohon mijin ta Aji, guda shida ne gasu nan ko? Sai masu maroon din nan na karshe, namu ne dan muma ba za'a bar mu a baya ba, suma guda 6 ne idan ka hada set nawa kenan? " " 36!" Yace yana sake bin kayan da ido. " Wadannan kwandunan kuma, gasu nan guda 24 kowanne da ka gani, abokin Bubu Maimartaba sarkin Ghana ne ya aiko dasu." " Allah sarki." Yace yana murmushi " Kilishi fa?" " Auw kaga na manta ko? Gasu chan fito dasu Harira." Tayi wa daya daga cikin bayin dage tsaye daga gefen kayan magana, " No a barsu bana bukatar su, a barsu anan zan duba su daga baya, akwai kayan da za'a kai na rabon da zasuyi a dangi, suna cikin Ford 2 nasa an saka su, zaku duba kafin ku wuce, komai yayi in sha Allah." " Owk shikenan, kaga wadannan boxes din da kasa aka yi musu design a dubai da hoton ku?" " Na gani aunty sunyi kyau sosai, su nake so a fara fitowa dasu, dan Allah aunty ayi duk yadda nace." " An gama karka damu." " Shikenan, Musaddik zai shige muku gaba, ya za'a yi tafiyar?" " Eh da wai kamar motoci goma haka, sai wanda za'a zuba kayan Hilux din Takawa masu rufin bayan nan, idan yaso sai su biyo baya ko?" Murmushi yayi me aji, ya girgiza kansa yana ayyana kalar tsiyar da ya shuka yana kuma jinjina abinda zai faru nan da wasu yan awoyi. Bed room din Fulani ya shige, ya sameta da yan uwata da suka zo, ya zaune tsakanin wasu tsofaffi biyu ya dinga tsokanar su ya hanasu sakat, kowa ya ganshi yasan yana cikin farin ciki mara misaltuwa, yanayin sa kadai zaka san ba karamin murna yake da auren ba, su kuwa basu san harda murnar hawan jinin da ya tabbatar zai kama Mama, dama ita hassada ga mai rabo taki ce, idan kuma zaka gina ramin mugunta toh ka gina shi gajere baka san ko kai ne zaka fad'a ciki ba. ****Mama babu zama tun da taga yamma tayi ta tabbata suna hanya ko sun kusa zuwa, tayi nan tayi nan duk farin ciki ya hana mata sakat, karar tsayawar manyan motoci a kofar gidan ya saka kowa nutsuwa aka hau sake gyara wajen, kowa ya zauna ana dakon shigowar su. Gate din gidan me gadi ya bud'e da sauri, aka shigo da motocin da akwatunan suke ciki, sauran aka bar su a waje saboda babu wajen da zasu shiga dukka. Sauke akwatunan aka fara yi a harabar wajen, kafin su gama sauke su dukka guda talatin da shida, sai baskets din suma. Boxes din da Anty Faty tayi masa magana akai suka riko kowacce mace ta rik'e daya a hannu dama yan kanana ne, matan da Mama ta wakilta da idan sun zo su tare su ne suka karaso kowanne fuskar sa dauke da fara'ar suka tare su sannan suka yi musu jagoranci zuwa ciki, Mama na zaune an sha lullubi da kayan alfarma suka shigo, ta bisu da kallo ta kasan Ido, mata ne hamshakai wanda suka amsa sunan su mata, hutu da jin dadi ya kama jikin kowacce kai ba sai an fad'a maka ba. Rawar jiki jamaar Mama suka fara su a lallai an zo wajen su, dangin su Abba na gefe sun zama yan kallo, akwatunan aka dinga shigowa dasu Mama ta hadiye wani yawu me karfi, cikin al'ajabin uban kayan da ake ta shigo dasu, gaba daya ma sai ta bata lissafi suka dinga yi mata gizo, kamar ta tashi ta hau bubbudasu taji, wani farin ciki na ziyartar ta. Duk gaishe gaishen da ake tsakani bata wani fahimta saboda yadda ta tafi tunanin kalar hutu da gatan da Zeenat zata shiga, gashi alamu sun nuna dangin mijin nata masu karamci ne, basu da nuna kyama ko wulakanci ko kadan. "Baki ne daga gidan sarki, mun kawo lefen dan mu, jikan Maimartaba sarki, sannan d'a ga sarkin Adamawa Alhaji Ahmad Santuraki,Ina mahaifiyar amaryar tamu take?" Mama tayi firgigit sanda taji wata cikin matan na tambaya, murmushi ta yi tana sake kama kanta ita a dole akwai surkutar nan. Aunty Faty ce ta tashi tsam, ta isa gaban Maman ta mika mata akwatin hannun ta, dake dauke da hoton Moh da Iman da ita kanta Iman din idan ta gani zatayi mamakin yadda ya same shi, hoton yayi masifar kyau zaka rantse tare suka dauka, yana sanye cikin shigar babbar riga da rawani, yayi wani murmushi da zaka kalla ka sake kalla. Wani irin shock Mama taji lokacin da ta karbi akwatin a hannun ta hoton da yake jiki ya shiga cikin idon ta ya aikawa da kwakwalwarta sako a take. "Wannan itace kyauta ta farko ga yar mu Fatima, akwai sauran kyaututukan da bazasu kirgu ba, amma dai ita wannan din ita ce zamu iya cewa ja gaba ga sauran." Kamar mutum mutumi haka Mama ta dinga kallon matar da take mata wani yare da sam kwakwalwarta ta gaza dauka balle ta fassara mata abinda matar take cewa. "Wadannan kayan kad'an ne daga cikin abubuwan da muka tanadawar Fatima, in sha Allah ba zata taba dana sanin amincewa da dan mu Muhammad ba. " Dan sarki jikan sarki kuma sarkin gobe idan me dukka ya kaimu." Wata mata tace daga gefe, duk suka amsa da in sha Allah. Guda aka saka a wajen, gudar da Mama taji kamar an saka allura ne ana chacchaka mata a tsakiyar kanta, kokarin sakin box din hannun nata take, wata kanwar su Abba da take lura da ita tuntuni ta taso da sauri ta karbe tana ma yan uwan Maman kallon banza. "Masha ALLAH, lallai mun ga Halin Girma da karamci na wannan babban gida, mun kuma tabbatar da yar mu ta shiga hannu na gari" Ta fad'a bayan ta koma wajen zaman ta, ta kuma mikawa wata babba a dangin box din. Murmushi matan sukayi dukka, sannan aunty Faty tace " Sai a bude kayan ko?" Da karfin guiwar su dangin Abba suka tashi, aka fara bud'e box din farkon nan, kowa ya shiga mamaki, mukullaye ne wajen guda uku na mota, sai mukullin gida da takardun su, sai kuma wani babban set of gold masu girman gaske. Wata irin guda da tafi ta dazu aka sake saki, jira ya soma dibar Mama, ta kasa gane komai sai hajijiya da take ji kamar zata kayar da ita daga zaunen da take, me yake faruwa? Me yake shirin faruwa. Daya bayan daya aka dinga bud'e kayan, tun mutane na irgawa har kowa ma ya gaji aka zuba ido ana kallon tarin dukiya, dukiya me sunan dukiya, dangin Abba da Mama ta dinga dagawa kai sai suka zama kamar sune kawai a wajen, farin ciki suke dama kowa yaji haushin abinda Maman tayi a dan tsakanin gabatowar bikin, sai kuma yadda ta dinga yada habaici a ranar da za'a kawo kayan wanda suka tabbatar dasu take shiyasa suka ji haushin ta sosai, amma yanzu da haka ta faru sai suka hau murna suka dinga yin abu da gayya dan su kara haukata Maman. Tashi sukayi bayan an gama ganin kayan, aka damka duk wasu abubuwan da suke da muhimmanci sosai kamar golds da takardun gida da keys a hannun kannen su Abba sannan suka yi musu sallama, abubuwn da aka shirya da sunan Zeenat suka je suka dauko aka saka musu a mota, basu ma so karba ba amma yadda suka dinga insisting yasaka suka karba dan kar suga kamar sun raina musu ne. Suna gama fita daga gidan masu kawo kayan Zeenat ta shigowa, mata ne kwantsam masu mugun yawa, masu goyo ne, gasu nan harda wanda suka ciko bus suka zo. Ana kokarin daga Mama a maida ta cikin daki sanarwar zuwan su ya katse su, a sanyaye suka dawo suka zauna, suka shigo bayan an matsar da kayan Iman an tura wasu dakin Abba da dakin Maman. Da kallon bakin ciki Mama take bin su, kamar ta tashi ta hau bugun su haka taji, yaran da suka zo dasu suka dinga ihu na goyen sai da aka sakko su, na hannu kuwa suka hau wasa a falon. Gaisawa akayi suka gabatar da kansu, kafin ma su dire sunan Zeenat din Mama ta ja numfashi da take jin kamar zai fice daga jikin ta. "Kuyi hakuri asthma ce da ita nema take Kuma ta tashi tun dazu, tashi Yaya mu shiga ciki ki huta." Aunty Maimuna kanwar Maman tayi saurin rufawa ta janye Maman dan ta hango matsala babba, kamar ma kokawa take da numfashiin ta. Suna shiga dakin ta kurma ihu, ihun da kowa ya ji shi, da tayi sauri ta saka hannu ta rufe mata baki "Haba Yaya Hajara, ai sai aji kunya, dan Allah kiyi hakuri." "Kutmar uban hakuri, kike ce min nayi hakuri? Bayan kinga abinda ya faru? Kinga yadda Ibrahim ya munafurce ni da yan uwansa? Bayan duk halaccin da nayi musu ? Amma kike cewa nayi hakuri, ke kinsan me nake ji? Innalillah, wayyo Allah na." " Ni dai kiyi hakuri, ko ma menene ki bari a gama taron nan, kinga mutane zasu tafi dake a baki." " Taro? Ke kina ganin za'a cigaba da taron nan?" " Toh me za'a yi Yaya?" " Ba zai yiwu ba, wallahi sai dai a fasa auren, amma ba zan bari bakin ciki ya kashe ni ba a banza." Sai ta sake fashewa da kuka, kuka irin wiwi din nan da kana gani zaka tabbatar da ba karamin kuka mutum yake ba. Duk yadda Aunty Maimuna taso ta bata baki tayi hakuri ta kasa, sai kawai ta fito ta rufo mata kofar ta dawo wajen bakin, lokacin har an soma bud'e kayan, akwatu na guda hudu sai kit daya, da kayan ta masu kyau daidai da tsarin akwatunan, amma ganin da mutane sukayi wa kayan Iman ya saka zasu ga na Zeenat din kamar bola, a daddage kowa ya kalla, suka dauko dubu ashirin suka ce gashi nan ta kai dinki ba'a samu an dinka ba saboda kurewa lokaci. Daga haka sukayi musu sallama aka je dakin Mama a dauko ragowar kayan da suka rage ta ce idan an basu ko ruwa ba'a za'a basu ba, da k'yar Aunty Maimuna ta bata hakuri aka saka musu ruwa da lemo a bayan mota suka tafi. Daya bayan daya yan uwan Abba suka zo suka kwashe kayan iman suka maida su bangaren Gaji a cewar su kar bakin ciki da kishi ya saka Mama ta saka wuta ta kona su. Hauka hauka Maman ta soma da suka shigo, kowa yayi mata banza suka dinga dariya suna yada mata da magana, suka kwashe komai suka yi tafiyar su. Jiki a sanyaye kawayen Mama suka dinga sulalewa suna guduwa kowa burin sa ya isa gida ya bada labarin abinda ya faru. Zeenat na wajen saloon suna ta waya da Bashir kiran Maman yake ta shigowa tana kin dagawa, da dai taga kiran ya ishe ta sai tace ya bari ta daga wayar Maman, katse nasa kiran tayi ta daga na Maman. "Kina gidan uban wa wai?" "Mama kinsan fa ina saloon." "Toh ki bar komai kike ki taho gida, kizo yanzu ki same ni." "Mama ban gama ba, kuma kinga zamu je mu siyo head din da zan saka da dinner da Bashir daga nan..." "Bashir din yaci abu ta kaza uban sa, na rantse da Allah kika bari man da awa guda baki dawo gida ba, sai kinga yadda zan miki" tana kaiwa nan ta katse kiran, saroro Zeenat din tayi rik'e da wayar cike da mamakin Maman. "Me ya faru kuma?" Ta Tambayi kanta cike da mamaki. Safa da Marwa Mama ta dinga yi a daki tana jiran Zeenat, ko sama da kasa zata hade ba zata yarda ayi auren nan ba, tasan idan ita kanta Zeenat din tazo taga abinda ya faru zata ce ta fasa ne, shege matsiyaci dama munafurtar su yayi kenan. " Yaya Hajara da kin zauna kin nutsu, tashin hankali ba zai gyara komai ba." " Ba zaki gane halin da nake ciki ba, ba zaki gane ba, ina cikin tashin hankali, bayan kunyar da nake ciki." Ta fad'a tana cigaba da zagayen, idanun ta ya kada yayi jajur taci kuka ta godewa Allah. Jugum sukayi kowa da abinda yake rayawa a ransa. A haka Zeenat ta shigo ta same su, Mama tayi kanta da sauri ta fizgo hannun ta da sauri. " Kika ce min talaka ne, kayan jikin sa ma a yayyage, daga gani bashi da komai." "Waye? Wai Mama menene ya faru?" " Ubanki, bake ce kika ce min wanda yazo neman auren Iman talaka bane?" " Eh Mama, dan baki ganshi ba." Dundu Mama ta kai mata ta goce cikin bacin rai tace " Toh dan ubanki dan sarki ne." " Sarki!!!" Zeenat ta fad'a da karfi tana zaro ido *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _1aHALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 1/21/22, 12:57 - Buhainat: Halin Girma     17 Hafsat Rano *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw **************** "Sarki!" Ta zaro ido cikin tsananin kaduwa "Laifin ki me, duk laifin ki ne, da baki yi min karya ba, da baki boye min abinda kika gani ba, da nasan abinda ya kamata nayi tun a lokacin." "Haba Yaya Hajara, komai fa da kika gani ya faru toh dama chan haka yake a rubuce." " A ah Maimuna, wannan kam sakaci na ne, ni ce duk na jawo komai, gashi yanzu bansan yadda zan ba, komai ya kwabe min." " Hakuri kawai zamuyi mu tayasu da addu'a, kudi ba shine kwanciyar hankali ba,rufin asiri  shine, idan har Bashir din zai kula da ita ai shikenan, a hankali sai suyi kudin su." " A ah, ba zai yiwu ba, shegen yaron nan da har zai iya yaudarar mu, ya ha'ince mu ke kinsan ba mijin kwarai bane, dole Dr yazo a sake sabon zama, wallahi ba zan bawa yata mayaudari ba." " Toh wai yama akayi? Kika ganshi a fakiri sannan kuma ya koma dan sarki? Ta yaya hakan ta faru? Bayan babu wani abu da ya nuna hakan tun farkon zuwan sa?" " Salamu alaikum." Habib ya yi sallama kafin ya shigo dakin, su i su ne a ciki shiyasa ya shigo kai tsaye, ya gaida sisters din Mama sannan ya kalli Zeenat dake gefe tana matsar kwalla, yayi kwafa ya zauna akan kujerar gaban mudubi yace "Kiyi hakuri Mama dan Allah, amma ni da kaina na fad'a miki Bashir ba mutumin kirki bane, yanzu dai hakuri kawai za'a yi tunda lokaci ya riga ya kure, dan Allah karki yiwa Abba wata magana kinsan dai ba zai saurara ba, dan Allah ki kwantar da hankalin ki, kiyi musu addu'a arziki ai na Allah ne. " Wani kallon banza Mama tayi masa, kafin ta nuna masa kofa " Fice ka bani waje bana bukatar maganar ka. " Mikewa yayi, yana jin babu dadi abinda Maman take yi, tun daga irin rikon da tayi wa Iman din wanda sun sha haurawa sama a kai idan yayi mata magana, daga baya sai ya daina kawai ya watsar amma kuma ya kan yawan yiwa abokin sa sadeeq maganar ta akan zai bashi Iman din saboda yadda yaga zaman da take yana so yaga ta samu yanci, akwai ranar ma da hira ta saka ya kwashe komai ya sanar wa sadeeq din duk da yasan kamar tonawa mahaifiyar sa asiri yayi amma kuma ya zai? Baya jin dadi sam.   Kofar ya ja musu ya bar gidan ma gaba daya dan ba zai zauna ya cigaba da kallon bacin rai ba. A waje suka hadu da Abba ya aike shi karbo wasu kaya sai kawai ya biya ya dauki sadeeq suka wuce tare.    ***Har dare Abba be shigo ba, idon Mama kamas tana jiran sa, Zeenat ma idon ta biyu sun shirya samun Abban ita da Maman ayi magana dan da gaske take ba zata kuma auri Bashir ba yanzu, musamman bayan taga kayan da aka ce wai nata ne, toh wai mana, dan bata saka rai ko hasashen irin su ba ko kad'an.    Kamar Abban yasan za'a yi haka yaki shigowa da wuri har sai da suka soma kosawa, gaba daya duniya bata musu dadi sam, Bashir sai kiranta yake amma sam taki dagawa dan bata da lokacin sa balle ta wayar sa.    Wajen sha biyu Abba ya shigo bayan ya gama kallon kayan iman din a bangaren Gaji duk da be iya kallon komai ba sama-sama shima don sun matsa masa ne, Gaji ce ta kirashi daki tace ko me Maman zatayi kar ya yarda ya biye mata, ayi a gama komai lafiya shine kawai.    Yana shigowa ya gansu a falon Zeenat na rakube a k'asan kujera tana cigaba da matsar kwalla, yi yayi kamar be gansu ba, yayi hanyar dakin sa Mama tayi saurin tare shi "Dr." "Kinga dai a yadda na shigo kinsan akwai gajiya, ki bar duk wata magana zuwa gobe da safe idan ALLAH ya kaimu." "Ba zai yiwu ba, idan na bari aka kai gobe na samu matsala, yanzu zamuyi ta mu san abinda muke ciki." Kada kansa yayi ya dawo ya zauna sannan yace "Ina jinki." "So nake a fasa auren Zeenatu, ba zata auri Bashir ba." Wani banzan kallo Abban yayi mata, kafin ya hade rai sosai yace "Ashe ma ke mahaukaciya ce ban sani ba Hajara, Ashe baki da tawakkali ma, ashe ma baki san komai game da rayuww ba, bari kiji." Ya juyo yana kallon ta "Dama shi sharri dan aike ne da kike ganin sa, duk in da yaje sai ya dawo, dan haka Wallahi, Wallahi kinji ma rantse ko?" " Ba zan karya alkawari na ba, ba kuma zan zama mutumin banza ba, sai dana jaddada muku ke da ita gata nan, nace kunji kun gani? Sai yanzu da ya rage yan awowi shine zaku zo min da maganar banza? Saboda bansan me nake ba ko?" " Idan kana kaunar Allah Dr ka rufa min asiri a fasa auren nan dan Allah!" " Lallai Hajara kin haukace, wallahi babu abinda zai hana auren nan sai dai idan cikin mu biyu babu wani, ko ni na mutu ko ita Zeenat din ta mutu, amma in dai da ranmu da lafiyar mu wallahi sai an yi, kinji ma na gaya miki." " Abba dan Allah kayi hakuri, wallahi zan iya mutuwa." " Allah ya jikan ki." Ya tashi yayi shigewar sa daki ya saka key kar ma ta samu damar biyo shi dan a yadda ya hangi tashin hankali a idon ta, zata iya jure su kwana a tsaye akan maganar da babu komawa baya. Wani irin marayan Kuka Zeenat ta fashe dashi, bata san ba son Bashir take ba, kwadayin abun sa da kuma kishin Iman ya sakata ganin kamar son nashi take, sai yau ta gane kawai bakin cikin da take wa Iman ne ya sakata amince dashi.   A zaune suka kwana, babu kalar tunanin da Mama batayi ba akan washegarin, har da tunani ko ta dauki Zeenat ta gudu da ita? Kafin gari ya gama haske tuni hayaniyar gidan ta cika ko'ina wanda ta tabbatar da gangan suke yi don a kular da ita.    Da k'yar taayi sallah ta saka Zeenat ma tayi lokacin yan uwa har sun tashi sun fara gyara shashen Maman.    Dakin Abba Mama ta shiga, ta same shi ya fiddo sabbin kayan sa da zai saka ya ajiye a saman gado, yana waya da Maman Iman, duk da ta shigo amma be daina wayar tasa ba, ya cigaba da yi mata bayani "Masu zuwa daurin auren su taho da ita, kinga anan dinma za'a so a ganta, in yaso daga nan sai a wuce kawia da ita." "Owk shikenan." Ta amsa sannan ta kashe wayar. Haushi ya sake turnuke mama amma ta share dan ba abinda ya dameta bane a yanzu, matsalar da take ciki yanzu tafi wannan. "Ina kwana?" Ta durkusa a k'asa ta gaishe shi, "Lafiya lou." Ya amsa a gajarce yana cigaba da duba sakwannin wayar sa. "Dan Allah Dr kayi hakuri, hannun ka baya taba rubewa ka yanke ka yar, kar ka hukunta yar ka akan laifin da ni na aikata, naji duk hukuncin da zaka yi min kayi min amma dan Allah a fasa auren nan." " Kinsan Allah?" Yace yana ajiyewar wayar hannun sa " Ba zan fasa auren nan ba, iyayen yaron nan sun zo na karbi maganar su nayi komai har sun kawo lefe sai yau ranar kawai kice a fasa? Nace musu me kenan? Tun farko ban fad'a muku ba? Ban nuna muku illaar abinda kuka nace akai ba, kuka nuna min ku ba zaku fasa ba, har kika saka zeenatu ta watsa min k'asa a ido ina mahaifin ta, ko da ace Bashir yaron kwarai ne idan nace ta hakura dashi ba zaki taimaka wajen ganin ta yi min biyayya ba? Amma me kikayi? Sannan sai yanzu, sannan zaki zo min da maganar banza, ya kike so nayi?" " Dan Allah nidai kayi hakuri ka yafe mana,dan Allah ka taimaka." " Wallahi Hajara babu abinda zan iya akai, kinji ma na rantse, ki barni dan Allah." Zama tayi dabas a k'asa, sai kuma ta tashi da sauri ta fice ta nufi shashen Gaji, ta same su a falon yan uwa ana ta shewa, ta wuce su zuwa ciki kamar wadda ta zare. A k'asa ta tsuguna ta gaida Gaji wanda rabon da tayi haka an dade. " Dan Allah ki taimaka ki saka baki Dr ya fasa auren nan, wallahi idan akayi auren komai zai iya faruwa, nasan ke kadai yake jin magana dan Allah." " Yana ina?" " Yana gida, dan Allah ki taimaka min." " Kije kice idan ya gama ina neman sa, Allah ya kyauta ya rufa asiri, sai a hakura kawai." Tashi tayi da sauri, ta manta ko godiya bata yi ba, ta fice kowa ya bita da kallon mamaki cike da jin haushi. Ko da ta fadawa Abban be ce mata komai ba, da ya fito ya shiga wajen Gajin bata yi masa maganar ba, ya gaisa da kowa sannan yayi breakfast da masa ya wuce wajen yan uwan sa.    ***Daren ranar Moh be runtsa ba, duk wasu bakin da zasu iso sun gama isowa a lokacin kowa an sama masa masauki na alfarma. Abokan sa da sukayi karatu tare suke kuma aiki tare sai dai kowa wajen da take daban ne suka sauka a cikin gidan a bangaren Moh din, kafin a daura auren su wuce adamawa sannan su sake dawowa Kanon saboda events din da za'a yi a Kanon.    Raba dare sukayi ana hira, anan suke fad'a masa suma fa sun shirya masa kayataccen bikin sword crossing amma a abuja saboda suna so manyan su na wajen aiki su ma su zama sun samu halarta. Abubuwan sun so suyi ma Moh yawa saboda shi dai tsakanin sa da Allah zai fi so ace da an daura auren kawai su yi tafiyar su shi da ita,amma kowa kokari yake ya shirya wani abu da zai sake rik'e su, shi dai kawai dan kar ya fito fili yace baya so ne, amma har ga Allah da kowa ya hakura.    Da suka tashi da safe ma wasu suka dora da hirar in da Musaddik da wasu ciki suka tafi karasa abubuwan da basu samu gamawa ba, duk da sai bayan sallar juma'a za'a daura auren kuma komai da ya kamata su yi an ma riga an gama amma suma zasuyi nasu kokarin ko yaya ne.     Tun wajen sha biyu Takawa ya saka aka kira masa Muhammad, ya same shi da manyan mutane har da Mr President sai Bubu da tasa jama'ar. Aji dan tsoho ma ba'a barshi a baya, yaji dadin ganin su musamman Aji da be saka ran zuwan nasa ba. Bin su yayi daya bayan daya ya gaishe su dukka, kowa ya kawo kyautar bangirma ya damka masa, harda masu blank cheque duk dan a birge Takawa.    Godiya yayi musu dukka ya koma wajen jama'ar sa, suka dauki duk abinda zasu dauka suka wuce gidan Moh din dake Lamido Crescent yadda zasu fi yin komai a tsare.    ***Wanka na wajen uku kenan idan tayi ta gama da wannan hadin ruwan sai Mamma ta sake bata wani, gaba daya wani irin sulbi fatar jikin ta take yi, tayi wani irin haske me kyau fatar ta sai glowing take kamar fuskar ta taji labari.    Tun da aka soma mata gyaran jiki ta tabbatar da komai nata ya sauya, hatta lallen da aka yi mata da gyaran gashi na daban ne, bata kara tabbatar da gatan da take dashi ba sai a event din da aka yi jiya taga tarin mutanen da suka zo domin ita, kowa don ya ganta kawai. Tasha kyaututtuka daga kawayen Mummy da yan uwa kowa burin sa ya yi mata abinda zai burge mummy din.   Sosai kuwa Mummy taji dadi ba kad'an ba, duk kuwa da miskilancin ta amma sai da yanayin ta ya sauya sosai.    Bayan an yi taron an gama ne da daddare take bawa Iman din labarin yadda akayi suka rabu da mahaifin ta. "Kinsan aure rai ne dashi, idan lokaci yayi sai an rabu, amma har gobe ina son mahaifin ki, kaddara ce kawai ta raba mu, a lokacin alhajin mu yayi fushi sosai akan auren da mukayi ba da sanin kowa ba. Alhajinmu me kudi ne sosai kuma dan siyasa ne, yana matakin senate president a lokacin, hakan ya saka dole Ibrahim ya sake ni akan kar abinda mukayi ya shafi mutuncin sa, dan wasu ba zasu taba yarda da cewa munyi aure ba, ko bayan an haife ki nan ma yace a dole dole sai ya karbi yarsa, ya rik'e ta dan baya son ko kad'an mutuncin sa ya tabu. Hakan ya saka Ibrahim yin fushi, ya karbe ki ya kuma yi alkawarin ba zai bani ke ba, nasha kuka nayi ta rokon sa ina masa magiya karshe yayi min alkawarin idan da rai da lafiya zai kawo ki idan kin isa aure." " Amma fa ko bayan nan Alhaji yazo daga baya yayi regretting abinda yayi har ya nemi Ibrahim din da kansa ya kuma roke shi ya bashi ke, dan a lokacin girma yazo gashi yana son gyara, Mamma ce babbar mu gashi har lokacin Allah be bata haihuwa ba ,amma sai Abban naki yaki yace yayi hakuri ba zai iya ba." " Ni banga laifin shi ba dan nasan shi da Zuciya idan har aka taba shi,karshe dai nima nayi aure bayan na kammala wani course da nake na auri wani dan siyasa Babba, na dade sosai a gidan kafin karshe Allah ya bamu haihuwa daya, na haifi yan biyu Amaan da Amaani, daga nan kuma sai muka rabu." Shiru Iman tayi tana harhada maganganun. "So kinga kowanne bawa baya wuce kaddarar sa, ni dake haka kaddarar mu take, dole ne kuma mu karbe ta hannu bibiyu mu gode wa Allah." "Haka ne mummy, wallahi na zata so Amaan yaran Mamma ne." Murmushi tayi "Yaranta ne kam, tunda dai ni ban wani san komai akan su ba, Itace komai dinsu, Allah be bata haihuwa ba shiyasa ta dauki son duniya ta dora akan su." "Hajiya fa?" "Step Mom dimu ce,itace ta haifi Zayd." "Allah sarki tana da kirki." " Sosai, kirkin ta yayi yawan da karyar mutum ya shigo gidan nan yace ba ita ce ta haife mu ba, ita ta kula da koman mu, Itace kuma a matsayin mahaifiyar mu har gobe." " Ashe akwai step moms masu kirki?" " Akwai su da yawa Iman, ba dukka aka taru aka zama daya ba, wasu kuma zaki ga yaran ne basu da kirki sam, sun takura mata sun hana ta sakat, komai dai da kika gani akwai good side dinsa akwai bad side haka rayuwar take." " Haka ne." Tace tana tuna Mama da Zeenat Shirya ta aka yi cikin wasu yan ubansu kaya, kayan da ta tabbatar ba kananun kudi aka kashe wajen samar dasu ba, komai na jikin ta unique ne, me kyau da ya dace da ita. Sarkar gold din da Mummy ta siya mata Mamma ta saka mata, sannan ta zaunar da ita a gefen gado ta dauko mata abinci, ta zauna da kanta ta taimaka mata ta ci dan ta tabbata idan suka tafi babu batun cin wani abinci a wajen amarya. Ci tayi sosai sannan ta dauko wayar ta tana duba misscalls ko ya kirata, be kira ba, ajiye wayar tayi akan cinyar ta har lokacin tafiyar su yayi, text message ta tura masa ta saka wayar a jaka suka fito gaba daya, wajen Hajiya aka kaita tayi mata nasiha sosai kafin su nufi airport da su Ya Mubarak da sauran jama'ar da zasu halarci daurin auren, sai kuma su Amaani, Mamma da yan uwan su da zasu je a karasa bikin da su a matsayin dangin Mamanta.    Mintuna kad'an suka isa dasu Kanon, dan ma basu taho da wuri ba, Abba ne ya saka aka je aka taho dasu daga airport din, aka sauke su a bangaren Abba babba, ita kuma Iman aka wuce da ita ta gaida Gaji sannan suka shiga wajen Mama.    Gabanta ya fadi tun shigowar su, ko wanka bata yi ba, duk da ta dan samu nutswa bayan ta samu Gaji, tana da yakinin zata hana Abban kuma ya hanu, amma kuma jikin ta duk yayi sanyi tana dai zaune ne tana kallon kowa, masu kaya-kaya ma a cikin yan uwan ta haushin su take ji, gani take ai kamata yayi su tayata alhini. Kawayen ta kuwa da sun kirata take dagawa tace an daga bikin zata neme su, abinda bata sani ba zance ya gama zagaya ko ina wasu ma da gayya suke kiran dan su tabbatar. Gaishe ta Iman take amma ta tsura mata ido ta kasa amsawa, tsabar bakin ciki ta kasa boye shi, mamakin yadda yarinyar ta sauya take, Ashe haka take da kyau bata sani ba? Ko Kuma dai yanzu ne kyawun ya fito. Kayan jikin ta kawai ta kalla tasan an kashe kudi, idon ta ya sauka akan sarkar wuyan ta, tana ta sheki da kyalli kana gani zaka gane zallar gold ne. Tari ne taji kamr zai sarke ta, duk suna lura da ita da suka ga kamar bata hayyacin ta sai kawai suka tashi suka koma in da aka sauke su. Lokaci lokaci Iman na kallon wayar ta, ta matsu suyi magana ta san halin da ake ciki, ba zata kirashi ba dan tasan yana cikin hayaniya amma taso ko yaya ne ya kirata.    Daidai lokacin da aka saka na daurin auren yayi, ta kwanta kawai lamo tana jin faduwar gaba, wani iri kamar tace ta fasa, ba'a gidan ake daura auren ba, a babban masallacin Kano ne da yake kusa da gidan sarki shiyasa basu san abinda yake faruwa ba.    Ji tayi gidan yayi tsit, kamar babu mutane, ta dinga jin wani tsoro tsoro yana shigar ta, Mamma ce ta taba ta, tayi mata murmushi tace "Kowacce mace ta kan ji irin haka idan za'a daura mata aure, kiyi addu'a kinji yata?" Da kai ta amsawa Mamman, ta soma karanta hasbunallahu wa ni'imal wakil, a hankali taji nutsuwa na saukar mata. A daidai lokacin suka ji karar tsayawar motoci, kafin gidan ya kaure da wata irin guda me karfin gaske.   Wani maroki ne me muryar tsiya, ya shiga kirari cikin muryar sa da ta shiga har kwakwalwarta, ta tsaya chak da tunanin abinda kunnen ta yaji "Alhamdulillah, Allah mun gode maka, an daura auren Yarima Muhammad da amaryar sa Gmbiya Fatima, dan sarki jikan sarki, kuma sarkin gobe idan Allah ya kaimu." Farin ciki ne ya kama su Mamma suka hau murna, bata fuskantar komai, a daidai lokacin sakon sa ya shigo wayar ta, "Duba whatsapp dinki amarya tah." Da sauri ta shiga whatsapp din har ta mantawa bata kunna data ba ,kunnawa tayi messages din suka shigo tayi saurin bud'e nasa. Hotuna ne masu yawa, ta hau bud'e su tana kura idon ta, hoton farko ya saka numfashin ta tsayawa na dan sakanni "Capt Muhammad Ahmad Santuraki." Yayi captioning hoton, yana sanye da nadi irin na sarauta, da kunnuwan sa guda biyu a sama da yake nuna yadda tsarin sarautar take, gaba daya gani tayi an sauya mata shi,shine sai wasu abubuwan da yawa da suka dauke ta zuwa wani tunani na baya tana kokarin alakanta abubuwan da tayi ta shakku akan sa. Kwanciyar fatar sa, da yadda yake magana yana bata mamaki matuka. Sauran hotunan ta shiga bubbudewa, duk akwai shi aciki tare da manyan k'asar da ma ketare, hoton sa da Takawa da yadda Takawan ya rik'e shi says alot. Ji tayi gaba daya ya goge mata hadda, ya bar kanta blank bata ma san wanne irin tunani zatayi ba. Wasu mata ne suka dinga shigowa, wanda kana ganin su zaka san su din hadimai ne daga gidan sarauta, duk suka taru waje daya cikin girmamawa suka hau gabatar da kansu. Kayan hannun su Mamma ta saka suka ajiye a gefe sannan ta aika wata bangaren Gaji akan wasu suzo a cikin dangin Abban, hakan ya bawa Iman damar sulalewa ta shige dakin Umma, sannan ta kira Ya Maryam ya waya tace dan Allah tazo dakin Umma. Sai gata tazo har da saurin ta, murna fal fuskar ta dan suma ba karamin mamaki suka shiga ba. Hotunan ta soma nuna mata, sannan ta hau mita kamar zatayi kuka, katse ta Ya Maryam tayi, "Yarinya kad'an ma kika gani, sai kin ga uban lefen da aka kawo miki, wallahi Iman Allah ya baki miji, miji na kere sa'a me sonki tsakani da Allah, kinyi sa'a, halin ki ne ya jawo miki amma." "Amma me yasa zai rufe ni?" "Haka tasa salon soyayyar yake, kin ganshi kuwa? Salo,aji kyau ga kudi." Turo baki Iman tayi, ta rasa me ma zatayi, Itace zata shiga gidan sarauta? Sarauta ma babba irin ta Kano? Katse mata tunani yayi da wani sakon nasa "Meet me a seat room din Abba, na matsu na ganki, I want to feel you right close to me." Da sauri ta kife wayar,. Maryam da taga komai ta kyalkyale da dariya "Su Iman an shiga sahun manya, jeki dan Allah yaji duminki, halal dinsa ce ke yanzu ehe." Duka ta kai wa Maryam din ta manta ma basa yar haka da ita, ta sake kwanshewa da dariya tana tsokanar ta "Saura kije ki dinga wannan nuku nukun naki, tashi ki sake gyara jikin ki, bari naje na karasa jin drammer da ake a gidanku, Zeenat na chan ta tada aljanu wai ba ta yarda ba, kinsan an riga an daura itama." "Kamar ya?" Tace cikin mamaki "Jeki ke dai wajen aikin Allah, bari zan baki labari in details." Ta juya da sauri ta fice bayan ta sanarwa da Mamma cewa Iman zata je yarima na seat room suyi hotunan tarihi. Rano💕💕 #Note edited *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _1aHALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 1/21/22, 12:58 - Buhainat: Halin Girma     18 Hafsat Rano *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ************** Shigowa Mamma tayi, ta same ta a tsaye ta ma rasa abinda zatayi. Hannun ta, ta kama ta zaunar da ita, ta bud'e jakar da suka zo da ita ta ciro turare me dadin kamshi na daban ta fesa mata, ta duba fuskar ta sannan tace "Ki kwantar da hankalin ki dan Allah,bari na duba kayan da yan matan nan suka kawo, ba za'a rasa alkyabba ba. " Fita tayi sai gata ta dawo tare da daya daga cikin yan matan, ta russuna har k'asa ta gaida Iman din da gabatar da kanta da sunan ta Ummimi sannan ta matsa daga gefe, " Tashi ta taimaka miki ta saka miki. " Mamma tace tana murmushi, wani banbarakwai Iman taji, ta tashi cikin sanyin jiki yarinyar ta hau saka mata alkyabbar cikin k'warewa. Ji take tamkar mafarki, kamar zata farka taga komai yana yadda take. Har ta gama gyara mata, ta kawo sauran kayan ta sassaka mata ta fito sosai a gimbiyar ta mamaki be bar ta ba.       Khadija da Zahra ne suka shigo, kusan sa'annin Iman din ne a family, doki ya saka su zuwa suka Iman din suma su bawa idon su abinci, suna shigowa dakin suka ganta cikin shigar da tayi masifar mata kyau, shigar alfarma.    Hoto Zahra ta ciro waya ta hau daukar ta, kala kala har da videos dan dole ne yau followersa dinta na Instagram su kara kiyayarta.    Kiran ta ya sake yi dan da gaske ya matsu ya ganta, irin matsuwar ba don idon sirikai ba, da dumbin jama'a da sai dai kawai ta ganshi a duk ma in da take.    Mamma ce ta dakatar da hotunan haka, tace suyi mata rakiya zuwa in da Muhammad din yake, ko tace Yarima Muhammad dan sunan kam be chanchanci a dinga fadar sa haka nan kai tsaye ba.     Kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki, haka ta tashi tana turo baki. Tare suka fito da biyu daga cikin hadiman yan matan nan, suna daga bayan ta suna take mata baya, domin da gaske Ammi tayi musu gargadi akan surukarta ta, su kula da ita da komai nata     Suna zuwa daf da seat room din suka soma jin hayaniyar maza,amma ba irin hayaniyar da zaka ji ba irin ta wasu mazan marasa aji da tsari. Hayaniya ce ta nuna farin cikin su da taya murna cikin ilimi da wayewa. Ji tayi kamar ta koma da baya, dan yadda ta tsani taro na maza har ya zama tana ciki, bata san kalar kunyar da zata sha ba, dan da alama dukkan su masu surutu ne. Bata dai ji muryar uban gayyar ba, ta kamo addu'a ta soma yi har ta samu nutswar ta "Iman." Ya kirata yana karasowa wajen, tare suke da Habib da abokin sa Sadeeq. Murmushi tayi masa "Uncle Khalil, ashe kazo." Murmushin yak'e ya maida mata, ya tuna da warning din da Moh ya kada masa, duk da yayi kokari matuka be saba ka'ida ba, yanzu ma dole ce ta sakashi zuwa tun da dai ba zai ki zuwa daurin auren Zeenat ba. "Nazo Iman, Allah ya sanya alkhairi ya baku zaman lafiya." "Amin." Ta amsa a ciki tana jin babu dadi, lokaci daya yanayin sa ya sauya, yayi saurin barin wajen yana yin gaba, suka gaisa da Sadeeq da Ya Habib sannan suka wuce zuwa in da zasu.    Sallama Ummimi tayi daga kofar, ta sanar da zuwan Iman din kamar yadda yake a tsarin masarauta, murmushi Moh yayi me aji, ya mike da kansa yana hararar su Ja'afar "Amaryata tazo dan Allah muna bukatar privacy." Dariya suka kwashe gaba daya, ya hade rai da gaske ba da wasa ba,su ka hau tsokanar sa amma yayi fumfurus yace wallahi sai sun fita. Musaddik ne yace "Ai ka bari ta shigo mu gaisa ko? Sai mu fita daga baya." Da kai ya amsa ya koma ya zauna yana jin rawanin da ke kansa ya soma gundurar sa. Shigowa sukayi bayan sun saka Iman din a tsakiya, idanun ta da tayi kokarin saukar dasu k'asa sosai suka shiga cikin nasa, da sauri ta dauke idon ta, ta zauna su Zahra suka sakata a tsakiya. Gaishe su sukayi suma suka amsa sannan suka gaisa da Iman din da take amsa musu ciki ciki dan ji take kamar ace fit ta fice saboda tsoro. "Capt. Lets snap please." Wani abokin sa Gbenga yace yana kallon sa "Ok sir." Yace yana tashi, taimaka mata Zahra tayi, ta isa wajen da yake a tsaye, daga gefen sa ta tsaya, sai taji kamar ana saka abu ana bubbuge mata kafafunta. Hannun ta taji yana laluba ta cikin babbar rigarsa, ta daga kai da nufin kallon sa, shima a lokacin kallon ta yake, Ja'afar yayi sauri ya dauki scene din, hoton yayi masifar kyau, duk suka hau yabawa.    Masifaffiyar kunyar da take ji ta hanata sakewa sam, duk da haka an dauki hotunan sosai sun fita, banda camera man suma wayoyin su duk babu na banza.    Wani irin laushi hannun sa da yake cikin nata taji,ta tuna kullum cikin safar hannu yake zuwa mata, duk sanda zata ganshi hannun sa da kafar sa, na sakaye, sai yanzu ta gani dalilin nasa na yin hakan.   Mammatsa mata hannun ya dinga yi, ya hanata sakat ya sakata a  wani irin yanayi me wuyar fassarawa, gashi ya saka shi cikin rigar yadda ba wani wanda zai lura, sai da aka gama hotunan tas sannan suka fita suka barsu da nufin idan sun gama gaisawa sai su fito a shiga cikin gidajen ayi sauran hotunan a cewar Musaddik.    Kamar me jiran kiris kuwa, suna gama ficewa ya saka dukkan karfin sa, yayi hugging dinta kamkam yana sauke tagwayen ajiyar zuciya.    "Alhamdulillah." Ya furta yana murmushi "Mrs Muhammad Ahmad Santuraki." Ya rada mata a kunnenta, ture shi tayi tana turo bakin ta gaba, ya tsaya yana kallon ta dan be taba sanin ta iya shagwaba ba sai yanzu "Me yasa kayi haka?" Tace cikin dan daga murya ita a dole ya bata mata rai, riko ta yayi da sauri ya dora hannun sa akan lips dinsa yace "Shssh... Ba'a dagawa miji murya babu kyau." Kokarin ture shin ta cigaba da yi amma sam ya hanata damar hakan, sai ma sake manne ta da yayi sosai da jikin sa suna shakar kamshin juna. Luf tayi ta daina motsawa kowa na sauraron bugun zuciyar dan uwan sa. Wajen minti daya suna a haka kafin ya saketa yana jan ta suka zauna a saman kujerar, ya rik'e hannayen ta yana kallon cikin idanunta "I promise you ba abinda kike tunani bane, zan miki bayanin komai amma ba yanzu ba, yau ranar farin ciki ce, let's not discuss duk wani abu da be shafi ranar ba kinji matata? " Turo bakin ta sake yi, ya saka hannu ya shafa yana murmushi " I love that. " Saurin rufe fuskar ta tayi kunya na kamata " Itama kunyar duk ina so, komai ma ni so nake kinji? Amma dai ki ajiye mana zuwa sanda zamu tare a gidan mu, ko nawa ne zan biya na siya. Bana so a samu matsala dan zai iya yin abinda ban shirya ba. " Da sauri ta gyara bakin ta, ta kuma gyara zama tana matsawa kadan, matsowa yayi ta sake matsawa ya sake matsowa kafin ta samu damar sake matsawa ya saka hannu ya tokare ta, ya matso da fuskar sa daf da tata, tayi saurin runtse idon ta tana jin kamar zata saki fitsari. Light kiss taji yayi mata a saman idonta dake a rufe.     A hankali ta bud'e idon ta, tayi saurin rufewa ganin yadda nasa ya sauya sosai. " Amm.. amm muje kaga su Mamma da yan uwan mummy, sai Gaji da sauran yan uwan Abba ko? " " Hmm. " Yace yana jan ajiyar zuciya " Tohm bari na kira Musaddik yazo. " Tashi yayi tsaye, ita kuma ta dukar da kanta k'asa, murmushi ta samu kanta da yi, tayi saurin katse shi ta sake saukar da kanta dan kar ya gani. Dawowa su Musaddik sukayi, su Zahra da aka samu sabbin samari suka shiga ciki don sanar da shigowar su Mubamamd din.    Ta bangaren Gaji aka fara, akayi hotuna sosai da kowa da kowa, sannan aka dawo in da su Mamma suke nan ma akayi musu, sai sauran mstan gidan da jikoki da sauran yan uwa da abokan arziki har ma da makwafta da suka shigo ganin kwaf.    ***Yadda Zeenat ta koma zaka rantse tayi shekara tana jinya, gyaran gashin ma da aka yi duk ya hargitse kamar ba'a yi ba, ta tada aljanu yafi kala biyar duk da muryoyi kala kala akan suns gargadin in dai aka sake aka kai ta gidan sai sun kashe ta.    Ko da Mama ta kira Abba ta fad'a masa cewa yayi karya ne, ya kashe kiran dan yana cikin mutane ne, amma kuma sai ya dinga jin babu dadi yana kuma tausayawa Zeenat din sosai, amma ya zai yi? Su suka jawa kansu duk da ba irin muna musu da be yi ba.    Kayan kitchen su Aunty Maimuna suka dauka, suka kira Bashir din dan ba ma a samu damar zuwa an yi jeren kitchen din ba. Cewa yayi zai aiko a tafi dasu, ba'a dade ba kuwa sai ga wani saurayi yazo a golf irin ta hayar nan, dole suka saka Habib bin bayan su da wasu kayan bayan ya dauko yar kurkura dan yawan kayan kadai sun isa a yiwa wasu amaren biyu amfani dasu bayan Zeenatun.    Sanda suka shigo unguwar gaban kowa ya hau faduwa, basu gama shiga masifa ba sai da suka ga kofar gidan da aka tsaida, katuwar kwatar dake kwance a kofar gidan ce ta fara tsorata su. Haka suka daure suka fito ya bud'e musu gidan suka shiga.    Babban tashin hankali sanda suka shiga gidan suka tarar da kayan da suke gidan da Bashir din yace ya saka mata kaya kar ayi komai, su kansu kujerun bayan yadda aka daina yayin su, ba set bane dan babu three seater ko kankantar falon ya hanata shiga ko kuma ba'a yi da ita ba oho.    Sanda suka shiga kitchen din sai da suka kusa kurma ihu, kwatan kwatan abinda Maman ta siya ba zai shiga kitchen din ba. Babu wanda yake wa wani magana a cikin su, suka saka abinda zai iya shiga kitchen din da ko kitchen cabinets babu, sauran na amfanin suka saka mata a cikin sip dan wannan ba za'a kirashi da wardrobe ba sai da sip😢😂 ragowar kayan suka juya dasu cike da tunanin yadda za'a kare da Mama. Babu maganar uban kayan turaren wutar da ta siya wajen hadaddiyar me turaren wutar nan*yerwa incense and more.*      Shigowar su kenan suka tarar ana ta hotuna da Iman, jiki a sanyaye suka wuce bangaren Maman suna taraddadin yadda za'a kwashe. Mama ma jin ance sun dawo ta yi zumbur ta tashi, sai dai tun kan su gama zama ta san da matsala.    Aunty Maimuna ce ta jata daki tayi mata bayanin komai sai ragowar kayan da tace an loda su a motar Aunty Muhibba dan kar a shigo dasu saboda yan saka ido.    A k'asa dirshan ta zauna, ta cire dan kwalin ta da take jin yayi mata nauyin gaske saboda yadda kanta ke masifar sarawa "Amma Bashir ya cuce mu, ya cuci rayuwata, yanxu dan Allah wannan abun kunya da me yayi kama? Na shiga uku." Ta jefar da hannun ta gefe, "Be kyauta ba gaskiya, ha'inci ne wannan kuma, sam be kyauta ba." Aunty Maimuna dake kokarin bata baki ta fad'a duk babu dadi " Allah ya isa ban yafe ba wallahi,shege macuci. " "Kiyi hakuri Yaya Hajara, cuta dai Bashir ya riga yayi mana ita sai dai muyi hakuri, mu lallaba a kai ta idan yaso daga baya idan hankalin kowa ya dauke sai musan abinda ya kamata. " Wani kallo tayi mata, kamar ma ta rufe ta da duka take ji " Sai bayan an kai ta ya gark'ama mata ciki sannan ne kike tunanin zai rabu da ita? " " A ah Yaya, kinga wai ai dai yanzu daga daure aure yau ai ba za'a ce ya saketa ba, kinga hakan ai kema zai iya baki matsala da Dr. " " Matsala ta nawa kuma? Ni yanzu ya riga ya fita daga kaina, ta yata kawai nake, dole na bata farin ciki ko ta halin Kaka. " Shiru kawai Aunty Maimuna tayi dan ba kuma tasan yadda zatayi ta bawa Maman hakuri ba. Aunty Muhibba ce ta shigo, tace maman ta tashi ta gyara jikinta Iman da mijinta zasu shigo. Kamar ta danna ma Aunty Muhibban ashar taji dan dai akwai kunya tsakanin su kasancewar ta matar babban wansu, dole ta tashi ta wanko fuskar ta a bathroom ta shafa mai da yar hoda ta saka kwalli sannan ta fito. ***A zaune take ta tankwashe kafar ta akan dan carpet din da yake jikin gadon dakin, ranta a bace yake tun bayan da ta samu labarin auren da Yarima Muhammad zai, taso ta tada hankalin ta amma Kilishi ta hanata, yanzu gashi tana ji tana gani an daura.   "Laila!" Ta kira sunanta tana daga zaune a gefen makeken gadon ta, da ido ta kalle ta ba tare da ta amsa ba, ta mike tsaye. Sanye take da doguwar gown ja, sai gashin ta da yake a tattare a waje daya da yasha gyara na musamman. "Yaushe zaki koma?" Ta ta da tambayar bayan tasan amsar da zata bata. Da ido ta sake dubanta, ranta na sake baci tace "Na dawo kenan." Da sauri ta mike daga gishingid'ar da tayi, ta dauka zata ce mata soon zata koma kamar yadda take bata amsa a ko da yaushe idan tayi mata maganar komawar. "Kinsan me kike cewa? Ba zaki koma ba? Me yasa?" "Ba zan koma ba har sai na samu cikar burina. Ni ce na chanchanta da zama a wajen da aka bawa yar talakawa, wadda bata da komai da kowa. Yarima nawa ne ni kadai babu kuma wanda ya isa ya dakatar dani." "Har ni?" Tace tana zaro ido cikin mamaki "Duk wanda yayi kokarin shiga hanya ta, ko waye kuwa, ko da Bubu ne!" Tsam kilishi tayi a in da take tsaye ta kasa cewa komai. Tana son Laila tamkar yadda take son Kamal,sai da tafi son Kamal ya gaji ubansa akan yadda ita Lailan take so. Sai dai idan taga da gaske Kamal ba zai samu sarautar ba, toh zatayi duk yadda zatayi ta samu Laila ta shiga rayuwar Muhammad din.    Juyawa Lailan tayi cikin takun ta na isa, ta bar dakin. Da kallo Kilishi ta bita ta girgiza kai "Ba zan taba barin ki da tsarin ki ba har sai na ga da gaske plan dina ba zai yiwu ba, wanda bani da shakku, Kamal shine zai gaji  ubansa a ranar da suka shirya bawa dan gatan dan nasu. Maimartaba da kansa zai yi fushi dashi, fushi irin wanda be taba yi ba!" Dariya ta saki ta koma ta zauna tana harda kafarta, indai tana numfashi Muhammad ba zai taba sarauta ba wannan alkawari ne da tayi wa kanta. ****     A gajiya Bubu ya dawo, shiyasa be samu ganin kowa ba ya shige turakarsa. Tun da wuri Ammi ta shirya tana jiran sa dama,aiko yana dawowa ta tafi dan tana so su karasa maganar da ya fara yi mata ranar basu samu damar gamawa ba    Har ta karaso ta zauna be bar kallon ta ba, babu wani babban chanji akan sanin da yayi mata a dah da nayi yanzu, jikin ta me kyau ne zaka rantse bata ajiye garkamemen saurayi kamar Muhammad din ba. "Barka da zuwa gimbiya a fad'ar Ahmadu." Yayi mata kirarin da ya saba mata tun zamanin kuruciyar su. Dariya tayi ta zauna tana dora tray din da ta shigo dashi a saman table. "Sannu da zuwa, kun sha gajiya. An rabu da taro lafiya da kowa?" "Lafiya Alhamdulillah, Takawa yayi matukar kokari sai dai muci Allah ya saka masa da alkhairi." "Ai dama yace shine uba, kuma shine kuma kaka, mu yan kallo ne kawai." Murmushi Bubu yayi yace "Gaskiya kam ga zahiri nan mun gani ai." "Allah ya basu zaman lafiya, har na matsu su tawo nan wallahi." Hannu ya kai saman hancin ta ya lakace mata fuska yace "Ko kunya, dan farin." "Kuma dan auta ba." Sai suka saka dariya a tare. "Allah dai ya basu zaman lafiya da zuria dayyiba, kwanan nan zaki ga yan duguiw duguiw suna yawo a tsakiyar masarautar nan, lokacin na dawo gida nima na huta kamar Aji, kinga sai kawai na dinga kallon su ina jin dadi."  " Allahu ya sa, Allah ya nuna mana. " " Amin. " Yace yana hasaso lokacin idan da rai da lafiya " Ka gama yanke shawarar nad'in ranar juma'a din? " " Haka muka tsara da Aji kuma na sanar da Takawa shima yayi na'am da hakan. " " Kana ganin babu matsala? " Rik'e ta yayi a jikin sa, yasan me take tsoro take gudu kuma " Babu komai in sha Allah, babu abinda zai faru. " " Aikin sa fa? " " Ajiye shi zai kinga ba zai yiwu a hada ba ai. " " Amma... " " Ki tayashi da addu'a har ma dani din ma, idan ban ajiye mulkin nan ba hankali na ba zai taba kwanciya ba. " " Allah ya nuna mana, Allah yasa ayi lafiya a gama lafiya. " " Yawwa ko kefa, addu'ar kenan. " #Rano💕 *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 1/25/22, 10:41 - Buhainat: Halin Girma       19 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ************** Ta cikin ido Moh ya kalli Mama da ya lura kamar tsaiwar na neman gagarar ta tunda aka fara daukar hotunan, gashi sai dauka ake an ki dainawa itama a cikin yanayi take da saura kad'an ta zube a wajen idan aka cigaba da daukar hotunan. Sai da ya tabbatar da tayi masifar kaiwa karshe har tana neman fito da abinda yake zuciyar ta ne sannan yace ya isa haka, tayi saurin fadawa daki babu ko magana, hannun Iman din ya kama a gaban kowa, suka juya suka bar part din yana jin a kalla Mama zata yi hankali, a kalla zata san rayuwa da yadda take juya wa bawa.     Tafiya sukayi bayan sun yi sallama akan zuwa magriba za'a zo a dauki Iman din. Sake chanja kaya tayi zuwa wasu kayan na daban, suka zauna cikin yan mata da sauran yayan da aka ma aure a family aka dinga hira cikin farin ciki. Bata saka musu baki sai dai tayi murmushi musamamn da ya zama kusan rabin maganar akan zaman aure ne wanda take jin kamar wasu maganganun sun girmi kanta.    Gabatowar la'asar ya sake saka Iman din a cikin yanayi fargaba, irin wanda ake ji idan za'a rabu da gida. Tashi tayi ta ja Khadija suka fita zuwa shashen su, tana son ganin Zeenat sannan tana son daukar wasu abubuwan a dakin su.    Shigowar su ya saka kowa na falon bin su da kallo, kai tsaye dakin Mama ta wuce Khadija na binta a babu yadda zatayi. Kusan zabura mama tayi ganin ta, ta tamke fuska tamau tana jin haushin shigo mata da tayi a halin da take ciki. Har kasa ta duk'a, ta gaida Maman sannan ta gaida su Aunty Maimuna. Duk sun amsa banda Maman da tayi kamar bata ji ba, tashi tayi bayan nan ba tare da wata magana ba ta wuce zuwa dakin su. Tayi mugun mamakin ganin Zeenat din, sai taji tausayin ta ya kama ta, ta durkusa a gabanta tana tuna lokacin da ta taimaka mata da bata jin dadi. "Zeenat?" Ta kira sunan ta, sai a lokacin ta san sun shigo dakin ma. Da ido tabi Iman din kamar taga sabuwar halitta, "Iman?" "Na'am, baki da lafiya ne? Kin ganki kuwa Zeenat?" "Bani da lafiya Iman, bana jin dadin komai, wallahi bana son auren nan gashi an riga an daura, tsoro ma nake ji kar naje na aikata wani abu mara kyau." " Me ya faru? Me yasa bakya so?" " Bashir karya yayi min, babu gaskiya a maganar sa, bashi da komai fakiri ne wallahi." Shiru Iman din tayi dan bata san me zata ce ba, tunanin yadda akayi hakan ta faru take, sai dai bata san yadda zata dauki maganar ta kuma ajiye ta ba. Kuka Zeenat din ta sake fashewa dah, kuka dacin da take jin sa a chunkushe a makoshin ta. Baki Iman din ta dinga bata, ta samu da k'yar tana maida numfashi. Tashi Iman din tayi ta duba wajen da ta ajiye jakar islamiyyar ta, ta dauka sannan ta sauki abubuwan da tasan zata bukata ba kaya ba. Khadija ta bawa ta tafi kai mata wajen Mamma sannan ta dawo ta cigaba da kwantar wa da Zeenat din hankali.    Kamar ba Zeenat ba da take taka Iman din tayi mata duk wulakancin da ta ga dama, tayi laushi sosai,har tana dora kanta a kafar Iman din.    Wayar hannun ta ce tayi k'ara,  Moh ne yake kira, dagawa tayi tana tashi daga gaban Zeenat din "Amaryata." "Umm." Ta turo baki, dariya yayi sosai kafin yace "Ki cigaba da turo bakin nan, babu ruwana aka samu matsala wallahi" Murmushi ta samu kanta da yi, ta jujjuya kanta tace "Kaiko?" "Me nayi?" "Ba komai." "Sharri kawai zaki min dan kin ganni bawan Allah." "Nima ai baiwar Allah ce." " Na yarda kuwa, are you ready?" " Mefa?" " Shigowa fadar Moh." " Ummm." " Get ready kinji? Yanzu zasu zo, kwana biyu zuwa uku zamuyi anan sai mu wuce adamawa." " Adamawa?" Tace tana zaro ido " Calm down, zan miki bayanin komai." " Shikenan." Tace a sanyaye " That's my wife, Allah yayi miki albarka." " Amin." Ta amsa tana sakin murmushi a hankali. Kashe kiran yayi, Zeenat ta bita da kallon sha'awa, tana hango tsantsar dacewar da Iman din tayi, gashi ita ta tashi a tutar babu. "Zeenat bari na tafi, zamuyi waya in sha Allah, kiyi hakuri dan Allah ki kwantar da hankalin ki." Jumbur ta mike, ta rik'e jikin rigar ta tana goge kwallar da ta zubo mata " Dan Allah Iman karki tafi ki barni, wallahi ba zan iya zama da Bashir ba." " Me yasa? Bakya son sa ne wai dama?" " Wallahi bana son shi, ko kad'an wallahi laifin Mama ne." " Iman!" Taji muryar Mamma a kofar dakin tana kiran ta, juyawa tayi ta fita tana kallon Zeenat din cikin tausayawa " Ke kuma daga zuwa daukar abu sai ki zauna? Kinga ai lokaci yayi ko?". Bata ce komai ba sai kawai tabi Mamman suka bar bangaren, ranta babu dadi ko kad'an.    Wanka mamma ta sake sata tayi, kayan da zata chanja ta tarar a dakin, an turara mata su da turarurruka masu dadin kamshi. Tana shiryawa tana tunanin halin da Zeenat din take ciki, yadda ta firgice ta shiga tashin hankali zaka gane akwai wani abun a k'asa, ba wai kawai dan Bashir din bashi da hali bane kamar yadda ya Maryam ta bata labari.    Duk shirin da tayi da taimakon su Harira, aka kuma kawo wata sabuwar alkyabbar aka dora mata, tayi kyau ainun, babu make-up babu komai amma yadda fuskar ta take sheki kadai zaka gane ba karamin gyara tasha ba.      La'asar likis sai ga jama'ar gidan su Bashir, motoci goma ne gaba daya har data amarya , yadda za'a samu kowa ya je har mutanen unguwa, a lokacin babu irin kiran da be yiwa Zeenat din ba akan gasu nan amma bata dagawa, shiyasa kawai ya kyale ta domin shi a yanzu ba ta ita yake ba, yadda zasu kwashe da hajiyar ce kadai matsalar sa, labari ya riga ya kai mata ya kuma san gamon su bazai taba yin kyau ba, gashi akwai wasu kudade da ya ta bashi da nufin zai mata wani aiki ya bi ta kansu.    Hankalin Mama ne ya kara tashi sanda suka iso, ta tabbatar da gaske Zeenat dai sai ta tare gidan Bashir, kiran Abba tayi, kafin ma ta fadi komai yace "Ina falon Yaya idan kun gama ki turo min Zeenatun." Daga haka ya kashe kiran, cikin sanyin jiki Mama ta nufi dakin su Zeenat din, ta tarar da Aunty Maimuna na ta fama da ita akan ta tashi ta shirya, ganin shigowar Mama ta saka ta saurin tashi ta nufi wajen Maman. "Jeki shirya Zeenat, kiyi sauri Mahaifin ku yana kiranki." "Mama?" "Ya zanyi? Ya zanyi? Aure an riga an daura ba kuma zan je na chakumi wuyan Bashir nace lallai sai ya sake ki ba, tunda kuma an daura ai dole ki tafi, dole ki bishi shine mijinki, ya zanyi." Fashewa tayi da kuka, tayi saurin fadawa toilet din ta rufo kofar, danne zuciyar ta sosai Mama tayi, ta juya ta bar Aunty Maimuna a dakin ta kuma jaddada mata kar su bata lokaci. Mamaki sosai Aunty Maimuna tayi da yadda Maman ta dake, amma kuma ta hango tsantsar tashin hankali a tattare da ita.    Da k'yar ta taimaka mata ta fito ta shirya har lokacin kuka take, kaya kawai ta saka sai turare babu batun powder ko makeup. Lullube mata fuska Aunty Maimuna tayi suka fito, kai tsaye aka wuce da ita wajen Abba. Su uku ne a dakin daga shi sai Abba kabiru sai Abba (Babba) nasiha suka soma mata, me shiga ciki akan rayuwar da zata shiga sabuwa, yawanci magana daya ce hakuri wanda Zeenat din ta kasa fahimtar su, bata gane me suke cewa balle ta san a wanne mazauni zata ajiye maganganun nasu ba, har suka gama bata fuskanci komai ba, hankalin ta ma baki daya baya wajen su ta tafi tunanin kalar rayuwar da zata fara a gidan Bashir din. Sadakin ta Abba ya dauko a aljihun ta ya mik'a mata "Gashi zeenatu,Allah ubangiji yayi miki albarka ya baku zaman lafiya." K'asa karba tayi, ta fashe da kukan da take ta rikewa, mikewa Abba yayi ya fice daga dakin zuciyar sa na tabuwa, yana jin kamar ya dawo da hannun agogo baya a lokaci da ya dinga nunawa Zeenat din illar abinda take shirin aikatawa.     Abba Kabiru ne ya karbi kudin a hannu Abba yace "Barshi Yaya, bari wani cikin yaran nan sai yaje ya saka mata shi a account, idan yaso bayan komai ya lafa sai ta ciro tayi amfani da abinta." "Hakan ma yayi, shikenan zeenatu kudin ki za'a saka miki shi a account kinji? Ki daina kuka." Tashi tayi da k'yar tana gid'a kai kamar gadangaruwa ta fita, daga nan ne kuma kowa ya firfita dan zuwa kai ta gidan Ango Bashir. Sai dai duk mutane suka gama shiga mota sannan aka fito da ita aka sakata a mota, tana kuka Mama na yi haka aka tura ta a motar. Dangin Bashir din sukayi ta mamakin abinda yake faruwa dan kowa ya ga kukan yasan ba kawai na rabuwa bane akwai wani abu daban.     Shiru kake ji a motar babu motsin kowa kamar ba ma mutane a ciki. Wata Yayar su Abba ce da Aunty Maimuna suka sakata a tsakiya, hannun ta na damke ana Aunty Maimuna tana cigaba da kukan ta a ciki ciki. Har suka karaso bata daina kukan ba. Sauran jama'ar motar ne suka fiffito, kowa tayi cirko cirko suna jiran a nuna musu gidan Zeenat.    ***Text message ne ya shigo wayar Bashir din, ya duba yana sauri sauri dan yana so yaga Moh kafin tafiyar da zai yi, _"Ina jiran ka kaida kanwar tawa a gida, na saka an gyara muku daya daga cikin dakunan nan. Sai kunzo." _ Gaban sa ne yayi mummunar faduwa, yayi sakale rik'e da wayar yana tunanin mafita, be shi da niyyar hada Zeenat da Hajiya Layuza gida daya, amma kuma be isa ya ki kai ta ba dan komai zai iya faruwa. Kiran ganin sa Ghali yayi ya tabbatar da sun karasa, yace idan kafa ta dauke ya kirashi ya sanar masa. Yana kashewa yayi mata reply da an gama hajjaju sannan ya saka wayar a aljihu ya fita yana sauri     Yadda dakunan suke kananu ya saka gidan ya chunkushe, kowa so yake yaga abinda zai samu na dorarwa a gaba, masu bud'e kitchen masu bud'e toilet har da masu bud'e rijiya dan tabbatar wa.     Aunty Maimuna ce tace kowa ya fita za'a koma gida saboda zuwa kai Iman, mutane suka hau saurin fita dan kowa ta kama motar da taxo amma suna fita suka ga wayam babu ko mota daya duk sun gudu,. Nan fa waje ya rude kowa ya hau tofa albarkacin bakin sa, yan uwan Mama suka shiga tashin hankali dan babu abinda yafi ciwo a debo mata a kawo su gidan amarya a watsar dasu, komawa cikin sukayi aka tilastawa Zeenat kiran Bashir din, be daga ba har aka gaji da kiran sa suka hakura suka fita, aka fara tunanin yadda za'a yi kowa ya koma gida.. saukin ta ma dama duk cikn garin ne dan tuni wasu ma sun dade da tafiya sun tari napep. Wanda suka rage ne dole su Aunty Maimuna suka san yadda sukayi kowa ta samu abin hawa. Sai yada habaici da bakar magana suke musamman yan uwan Abba da Mama ta bata wa rai tun a farkon fara bikin.    Sanda suka gama dawowa gida magriba ta kawo kai, a lokacin ne kuma motocin masarauta suke jere kansu a cikin layin wanda ya kasance tun daga farkon layin har karshen sa. Motar da za'a dau amarya daban take ta gaji da haduwa, anyi decorating dinta tayi kyau.    Gashi nan na biya bashin na ranar Friday.    #Rano💕 *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 1/25/22, 10:41 - Buhainat: Halin Girma       20 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ************** Gaban Iman din ne ya dinga faduwa sanda taji tashin algaita da bud'a a lokaci daya, rik'e hannun Mamma tayi tamau bayan sun dawo daga wajen su Abba da wajen Gaji. Zaunar da ita Mamman tayi tace tana zuwa Amaani tayi saurin dawowa ta manne kusa da ita hakan ya saka ta dan ji dama dama. Mukullin motar da Abba ya damka mata a hannun ta da wasu abubuwan ya sakata shiga yanayin da ta shiga, har yanzu bata bar mamakin yadda abubuwan suka sauya salo ba, wanda bata taba tunani ko hasashen hakan zai faru da ita ba.     Bayan kamar minti biyar sai ga Mamma nan ta dawo ta kalli sauran tace "Matar nan bata da kirki sam, bansan me yake damunta ba, amma ni dai na fad'a mata lallai ta shirya tazo ta kai Iman dakin ta, idan ma wani abun ne yake damun ta ko hassadace ita ta sani, na dai bata girmanta." "Toh ai Mamma kina gani kinsan bakin ciki take, dama kin kyale ta kawai mu kadai mun isa." "Ai ba haka ake ba, mu muka zo muka same ta kuma duk tsiya dai itace marikiyar Iman din." " Toh yanzu zata je din ko yaya?" " Ban san mata ba wallahi, na dai fita ai ni dai,ruwanta taje ruwanta taki zuwa, babu abinda za'a fasa." " Wallahi kuwa, Allah ya kyauta." " Amin." Tace tana zama.      Kayan Iman din aka gama fitarwa, aka saka a booth din motocin, sannan suka shigo da kansu su uku, suka ce sun zo daukar amaryar su, akayi barkwanci dai tsakanin su da su Mamma sannan suka fita su kuma su Mamma suka fito da Iman din.     A harabar gidan suka hadu da Mama, ta yafa mayafi ita da Aunty Muhibba, kallo daya Mamma tayi mata ta dauke kai suka fice, bayan su suka bi, suka tarar an gama tsara mutanen kowa ta samu mota ta shiga, kowacce mota da kayyadadden mutanen da za'a saka kuma kowa ya samu an shirya komai yadda ya kamata.    Motar amarya ce kawai ta rage sai guda daya da tazo a karshe, wasu ne suka shiga dayar tare da Aunty Muhibban sai Mamma da Mama suka shiga ta amarya suka sakata a tsakiya kamar yadda ake yi. Chan jikin kofar motar Mama ta makale taki yarda ta rabi Iman din, jawo ta sosai Mamma tayi jikin ta ta dora kan Iman din a saman kafadarta ta kwanta sosai.     Lamido Crescent suka nufa in da nan ne ainihin gidan Iman din, sojojin da ke zube birjik a gaban gidan ya saka mutane sake jinjina lallai Babba ne Muhammad din, gida ne hadadden gaske wanda dama chan a nan Muhammad din yake amma an masa gyara sosai da ba zaka taba cewa ba a lokacin aka gina shi ba. Tsaruwar gidan da yadda aka kawata faluka da dakunan gidan da kaya na alfarma ya kusan saka Mama shan k'asa, ta rik'e hannun Aunty Muhibba dan da gaske ta tsorata da yadda taga gidan. Falo biyu ne daya sama daya k'asa sai dakuna biyu a sama, uku a k'asa kuma kowanne Masha Allah kaya ne aka zuba na alfarma, kar Azo batun kitchen wanda duk yadda Mama ta kai ga kure siyayyar ta sai taga ta raina kanta, komai na ciki unique ne ga wasu shegun electronics wasu ma bata san menene amfanin su ba. A daddafe ta daure ta shiga ko ina dan yadda kowa ya zura ido a kanta kowa so yake ya ga yadda zata shiga dimuwa ko ma ta kasa rik'e bakin cikin ta har ta nuna a samu abin fad'a.    Basu wani jima a gidan ba suka fito, dama saboda dai su san gidan Iman din tunda yanzu ba anan za'a fara kaita ba, masarauta zash dan suna da shagalin bikin da zasuyi su ma.     Kin yarda Mama tayi ta koma motar amarya ta fad'a wajen Aunty Muhibba dan komai zai iya faruwa idan ta zauna gata ga Iman din. Bata taba tunanin kalar wannan daukakar ga Iman din ba. Sai gashi in da Iman din taje ko zata je nan gaba bata isa ta taba kai wa wajen ba har abadah. Tayi mata nisan da za'a iya cewa ya kai tsakanin nisan sama da kasa.     Bata kara raina kanta ba sai da ta gansu a cikin masarautar, babbar masarauta irin ta Kano, da bata kawo kanta a ciki ko da wucewa tazo yi kuwa bata taba hasashen kasancewar ta ba.     Wani tsari akayi na tarbar su, wanda ya sake bawa mutane mamaki, kana kallon fuskokin kowa zaka tabbatar da yadda suke ciki. Sanda suka isa bangaren Fulani kakar Moh din da kanta ta taso ta rungume Iman a jikinta, ta kuma zaunar da ita a kusa da ita, jikokin ta sauran suka hau dariya suna tsokanar ta, ta biye musu suka dinga yi kamar ba matar sarki ba,  duk da ba kowa ne aka bari ya shiga wajen ba, iya makusantan Iman din ne daga Mamma sai Mama sai dangin Abba su biyu sai Amaani da take makale da Iman din, sauran mutanen a wani babban falo aka ajiye su aka shiga gabatar musu da nau'ikan abinci kala-kala na gida dana kasashen ketare.     Sun dan jima a shashen Fulanin mutane daban daban manya wanda suka zo bikin suka dinga zuwa suna ganin Iman din, kunya kamar ta nutse ta dinga boye kanta wanda hakan ya saka suka kara son ta kowa ya dinga yabon ta yana yaba sa'ar da Moh din yayi.     Rakasu bangaren Moh din Fulani ta saka akayi, wanda dama chan aka ware wa Iman din da wanda zasu tayata zama kafin gobe yan uwan ta su dawo shagalin da za'a yi a babban Hall din gidan da tun a ranar an gama tsara shi an kawata shi.    Two bed room ne sai falo da kitchen, tuni masu kula da shashen sun gyara komai, daya daga cikin dakunan aka kaita, sannan su Mamma sukayi mata sallama aka bar mata Amaani, khadija, Zahra sai su Amira, duk dai yan matan aka bari a zuwan su Mamma sai su dawo gobe. Kamar zatayi kuka haka taji da zasu tafi amma kasancewar ta me dakiya ta daure kawai tayi shiru tana cigaba da kallon komai tamkar almara.     A falon su Amira suka zauna bayan sun raka su Maman sun dawo suka dasa kallo da hirar gidan Iman din da irin yadda aka karbe su a masarautar. Tana jin su sama sama bata fito ba sai ma tayi kwanciyar ta saman gadon dakin tana shakar kamshin da ta tabbatar da kamshin sa ne dan shine kamshin da ko da yaushe take jin sa yana yi.    Tana kwance taji kamar motsi, ta daga kai ta duba, sai taga kofa a jikin karshen bangon dakin wanda sai ka lura sosai zaga gane don ta saje da kalar curtains din dakin. Budewa taga kofar tayi, ta mike daga kwanciyar da tayi da sauri kafin ta gama daidatuwa har ya shigo, cikin shigar bakin dogon wando da riga armless, cikin mamaki take kallon sa har ya shigo cikin dakin gaba daya. Mikewa tayi tsaye lokacin da ya karaso daidai in da take. Ya saka hannu ya shafi gefen fuskar ta. "Wai tsoro kika ji?" Da ka ta amsa, ya rik'e ta ya zauna a gefen gadon sannan ya zaunar da ita a daidai kusa dashi, k'asa kallon sa tayi, ya zuba mata ido yana kallon ta kamar a ranar ya soma ganin ta. Farin cikin da yake ciki a yau din mara misaltuwa ne, ba zai iya tafiya adamawa be sake ganin ta ba shiyasa kawai ya hakura da zuwan sai da safe.    D'agowa tayi da nufin ta ga abinda yake, tayi saurin sake maida kanta k'asa ganin yadda idanun sa sukayi k'asa sosai. Hannun ta ya kamo ya rik'e a cikin nasa yana murzawa, yana kokarin danne abinda zuciya da gangar jikin sa ke wassafa masa. Yadda yake murza hannun nata da yadda suka samu kusanci sosai ya saka ta a yanayin da bata taba samun kanta ba, shi din ma hakan ce, dan yadda yake ji yayi imani idan aka dauki lokaci me tsawo baa bashi matar sa ba toh komai zai iya faruwa. Lissafin ta yaji sunayi ya saka shi jin gaskiya ba zai iya bari har tsawon kwanakin da su Ammi da nan Kano kowa ya diba na shagalin da zasuyi ba. Kwana daya ya isa anan ko biyu chan kuma daya idan yaga zasu ki yarda zuwa zai ya samu Aunty Fatima ya karanta mata komai a taimaki dan maraya a bashi matar sa ko kuma yayi musu aika-aika.    Turo kofar akayi, su dukka suka kalli kofar, da sauri Khadija ta juya tana fadin "Dan Allah kuyi hakuri." Tashi yayi tsam bayan ta fitan, ya sakawa kofar key ya dawo ya mikar da ita, ya cire mata alkyabbar da take jikin ta har lokacin, saurin runtse idon ta tayi saboda yadda dinkin fitted gown din jikin ta ya kamata sosai dan sai da suka kusan haurawa sama da Mamma kafin ta yarda ta sakaa. A abuja aka mata duk dinkunan nata kuma kaf babu wani dinkin arziki a duk kayan da Maman ta bayar akayi mata tace idan tazo kayan lefen ta sai ayi mata wasu na fita amma ita nata duk na zaman gida ne ayi wa Moh kwalliya. Dogon numfashi yaja, a karo na farko ya ganta haka babu hijabi balle mayafi. Kayan su zauna das a jikinta,ta wajen hips din sun zauna kamar a jikinta aka dinka su. Idon sa ya shiga rarraawa daga tsakanin kirjinta zuwa kasan hips din ta, yabi flat tommy dinta da kallo wanda zaka rantse ba'a saka masa abinci saboda shafewar sa. "Masha ALLAH!" Ya samu kansa da furtawa, kunyar da take ji kamar ta haka rami ta shige gashi ya hanata sakat ya rik'e ta babu damar ta zauna. Sai da ya more kallon ta tsaf sannan ya dawo samar fuskar ta ya matso daf da ita har tana jin hucin numfashin sa a saman fuskar ta, tayi saurin runtse idon ta ya kura wa lips dinta ido, ya kai bakin sa daidai kan nata ya shiga kissing dinta passionately ba tare da ya shirya ba.     Jikinta ne ya hau rawa tayi kokarin hanashi amma sai ya sake matso da fuskar ta sosai, ya tallafo ta ta baya ya sakata a jikin sa ssosai ya cigaba da aikin sa. Ta saman bayanta taji yana neman abu, har ya kai wajen da zip din ta yake, ya shiga jan shi zuwa k'asa, da sauri ta rik'e hannayen nasa tana girgiza masa kai hawaye har ya fara sauka a idon ta. "Pleaseeeeee." Ya furta cikin muryar da taji kamar ba tasa ba, ta shige ciki sosai. "Dan Allah kayi hakuri." Tace tana sake rik'e hannun nasa, dan taga kamar ma baya gane me take cewa.    Wayar sa dake cikin aljihun wandon sa ce tayi kara, ya janye ta yana murmushi ya ciro wayar yana daidaita kansa. "Zan kira ka Bashir." Kawai yace yana kashe kiran. Lokacin ta koma ta zauna tana kokarin daidaita kanta dan ba karamin yanayi ta shiga ba.    A gabanta yayi kamar kneel down, ya tallafo fuskar sa yana mata kallon tsantsar kauna, turo baki tayi ta harare shi ya tuntsure da dariya "Pretender kawai." Ya saka hannu ya lakaci gefen hancin ta, murnushin ita ma tayi ta juyar da kanta daga kallon sa abinda ya faru yana cigaba da haskawa a idon ta. "Kaje anan kiran ka." Tace ganin yaki tashi ya kuma hanata sakat da kallon sa da idon sa da suke sake bata tsoro a game dashi. "Kora ta kike? Wallahi sai naki tafiya na kwana anan din dama ai daki na ne." " Ya hakuri ni dai dan Allah." " Matsoraciya, kin fiye tsoro wallahi." " Tsoro ai halak ne." Tace tana dariya "Inyee kinyi baki haka? Yarinya zaki maimaita maganar nan ne, for now zan barki amma gaskiya zan dawo, kice ma su Amaani su kwana dayan dakin ke kadai zaki kwana anan, kinga dama akwai secret door dita kawai sai na shigo mu sha soyayyar mu." " Tab!" " I'm serious       #Rano💕 #Rano💕 *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 1/31/22, 19:12 - Buhainat: Halin Girma       21 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ************** Ta kofar ya koma ya fice bayan ya tabbatar da ya isar mata da sakon da yake son isarwa, yana kallon yadda tayi laushi sosai ta bishi da kallo har ya fice gaba daya.    Kai tsaye wayar sa ya dauka ya kira Bashir, ya daga yana tafiya zuwa shashen Takawa dan yana son ganin shi "Ya akayi Bashir?" "Barka da warhaka Ranka ya dade" " Barka dai, ya taro?" " Mun gode Allah, an kawo amarya yallabai." " Yayi kyau, Allah ya baku zaman lafiya, ka kula da ita sosai kar naji wani abu mara dadi, karka kuma taba yarda mahaifiyar ta ko wani yace zai taka ka akan matar ka." " In Sha Allah ranka ya dade, hakan ba zata faru ba." "Yayi kyau, sakon ka na wajen Musaddik." Godiya ya hau yi dan dama abinda ya saka kiran kenan. Cilla wayar yayi a aljihu sanda ya isa sashen Takawan da ya zata ya jima da isa a adamawa. ***A tsorace take tun bayan da mutane suka yaye, yan matan biyu da aka barta dasu suma basu wani jima ba suka cikawa wandon su iska dan ba zasu iya zaman ba, babu kalar ma da bata yi musu ba akan su zauna amma suka ki, a cewar su idan suka zauna basu san uban da zai maida su gida ba su ba samari masu mota ba ga unguwar da shegen nisa kafin kaje titi. Haka tana ji tana gani suka yi tafiyar su suka barta. Tasha kuka kuwa kamar ba zata mutu, ta dinga tsinewa Bashir albarka taji kamar ta gudu ta bar garin ma baki daya.    Tana nan a zaune cikin duhu taji ana saka mukulli a kofar gidan, tashi tayi da sauri tana zaro ido,a duhu take dan dama da wayar ta, ta haska kuma babu charge ta mutu tun dazu.    Shigowa yayi yana haske gidan da wayar sa, ya shigo ciki ya dalle ta, tayi saurin kare fuskar ta tana cewa "Waye!" A tsorace "Amarsu ta ango." Wani abu ne ya tokare mata a makoshi jin muryar sa, tayi kansa da sauri ta hau kai masa duka tana kuka "Allah ya isa ban yafe maka ba, Allah ya isa." Rik'e hannun nata yayi da karfi ya juyar da ita ta dawo tana jingina da bayan sa "Ni kike wa Allah ya isa? Lallai ma yarinyar nan." "Allah ya isa na fad'a mugu, macuci maha'inci." Juyo da ita yayi ransa na soyuwa amma ya danne kamar be ji komai ba, ya dalle mata baki da bayan hannun sa, yayi murmushi yana sake haske ta "Duk abinda ma zaki ce ki fad'a amaryata." Kuka ta shiga rusa wa da karfi, ganin zata iya jawowa a jiyo su a makota ya sakashi jawota ya shiga sumbatar ta, ta dinga dukansa tana harbin sa a kafa amma ko a jikin sa, sai da ya gajiyar da ita sosai sannan ya saketa yana murmushin, a kalla ya rage zafi dan yasan ba lallai Hajjaju ta yarda ta barshi ba.    A wajen ta duk'a tana kuka, ta dinga jin kamar ta mutu ta huta da abinda take ji, tana jinshi yana waya har ya gama kafin ya dagata tsaye ya rik'e hannun ta a cikin nasa su shiga barin gidan.    Mota ce a kofar gidan irin wadda yake zuwa wajen ta zance, bud'e mata gaba yayi ta shiga ya rufe sannan ya zagaya ya shiga mazaunin driver ya tada motar suka bar unguwar.    Tafiya sukayi da dan nisa har suka iso unguwa, gangarawa taga yayi zuwa wata doguwar hanya suka dinga tafiya kafin su isa kofar wani babban gida, horn taga yayi da sauri me gadin ya bud'e gidan ya shiga da motar ciki. Tunanin ta ne ya tafi wani waje daban, ko dai Bashir gwada ta yake yana so yaga yadda zatayi idan ya kaita wanchan gidan shiyasa ya kai ta? Ko kuma dai duk shiri ne. Murmushi ya sakar mata ta cikin hasken da ya hasko cikin motar bayan ya tsaya a gaban ginin gidan.    Sauri taga yayi ya bud'e motar sanda wata babbar mata hamshakiya ta nufo su cikin wata irin kwalliya, ta sha ado sosai tana walwali, katuwar gaske ce dan zatayi biyu ko ma ukun Bashir din idaan aka hade shi da Zeenat din waje daya.     Kafin ta kai ga garasowa Bashir din ya isa wajenta. Yayi kamar zai zube a k'asa a gabanta, ta riko shi tana masa murmushi, ware ido sosai Zeenat tayi tana tunani toh ko Maman shi ce? Karasowa tayi daidai kofar da Zeenat din take ciki ta bud'e mata tana sakar mata murmushi "Amarya." Ta kira ta tana sakin hannun Bashir din ta kama na Zeenat din tana jawo ta daga ciki. "Sannu da zuwa kanwata, sannu sannu." "Kanwata?" Zeenat ta maimaita sunan tana bin Bashir da kallon neman karin bayani amma sai taga ya fuske kamar be ganta ba. Takawa suka shiga yi har zuwa cikin gidan wani babban falo da yasha kawa sosai. Wasu mata ne hamshakai suma kamar matar farkon suka tarbi Zeenat din suna tafi, ita dai Zeenat gaba daya kanta ya kulle jira take su samu kebewa da Bashir ta tambaye shi me yake faruwa. Zaunar da ita matar tayi ta ja hannun Bashir din sauran mstan suka hau shewa da dariya, bin su Zeenat tayi da ido har suka haura sama, zuwa anjima kad'an sai gata ta sakko ita kadai babu Bashir din cikin shigar kayan bacci ta karaso falon ta kalli sauran matan tace "A rakata dakin ta ko?" "An gama Lay, an gama." Suka tashi gaba daya, daya ta kama Zeenat din suka nufi wata hanya da take a bayan kafar benen dake falon, wani dogon corridor ne suka bishi har zuwa bayan dakunan gidan, sai wani daki guda daya a wajen da kofar sa tana kallon kofar da suka fito, nan taga an bud'e, sannan sun shiga gaba daya ciki.    Katifa ce a k'asa karama kamar ta yan boarding sai wata karamar kujerar roba fara, suna shiga kamar jira dama suke matar da ta shigo da ita ta wurgar da ita a saman kujerar har sai da kanta ya bugu da bango, tayi kara saboda zafin da taji kafin wadda suke kira da Hajiya Lay (Layuza) ta rankwafo akanta tana mata kallon tsana tace "Ke dan yar iska ce ke, har kin isa mu hada miji daya? Kin isa nayi sharing dake? Karamar yarinya da bata fi sa'ar yata karama ba, kece kishiyata ko? Toh ni ko a zamanin kuruciya ban zauna da kishiya ba balle yanzu da nasan ciwon kaina nasan abinda nake so, dan haka nan dakin da nake ajiye masu aiki nane kuma na sallame su dan yanzu basu da amfani, sai ki cigaba daga in da suka tsaya, shara wanke wanke, wankin undies dina da girki, komai ma dai da kika sani." Gaba daya kwakwalwar Zeenat ta gaza gane me matar take cewa, ji tayi kamar wani yare take mata na daban da bata sanshi ba, ta dinga jujjuya kanta tana son gasgata abinda taji akan Bashir din, yana da mata dama? Mata babba kamar wanna da ta yi sa'ar uwarsa? Abba ne ya fado mata, sanda ya kirata yake mata magiya kamar ba Mahaifin ta ba, ya kaskantar da kansa yana rokon ta akan ta rufa masa asiri ta hakura da Bashir amma ta shafawa idon ta toka, ta kekeshe kasa tace taji ta gani, yanzu ta yaya hakkin Abban ta zai barta? Tun a ranar farko ta fara fuskantar wannan tashin hankalin.    Firgigit tayi sanda taji saukar abu kamar ruwa asaman fuskar ta, ta saka hannu ta shafa da sauri tana daga kanta "Kinji abinda na fad'a miki ko?" A hankali ta daga kanta alamar eh, ta daka mata tsawa tace "Baki zaki bud'e kiyi min magana bana son rainin wayo." "Naji." Tace tana barin kwallar da ta taru a idonta ta shiga sakkowa saman fuskarta. Dariya suka kwashe da ita, suka juya suka fita suna cigaba da zantuttukan su mara sa dadi ji. ***Bangaren amarya Iman kuwa komai na tafiya daidai, ta dade batayi bacci ba tana tunanin Moh da kalar soyayyar sa me tsayawa a zuciya, koman sa abin so da birgewa ne tun daga maganar sa har yadda yake tafiyar da ita. Da k'yar ta samu bacci ya dauke ta bayan ta gama tunanin nasa. Tun asubah da suka farka basu koma ba, kana jin yadda hayaniya take tashi a masarautar kasan akwai gagarumin shirin da ake yi. Shiryawa suka hau yi ita ta fara wanka sannan su Khadija suka yi. Suna fitowa falon suka tarar da abinci a jere na alfarma yana jiran su, nan suka hau kai suka ci suka yi nak, sannan aka turo tafiya da Iman din shashen Fulani. Alkyabba aka sake saka mata sannan suka fito kanta na k'asa tana jin yadda take shan gaisuwa kamar ta tsaya ta amsa amma yan matan nan sunce mata ksr ta tsaya amsawa haka sarautar take.    Da murna Fulani ta tarbe ta yau din ma, ta saka aka kaita har uwar dakin ta in da mutane suka dinga shigowa suna ganin ta wanda suke da kusanci da gidan. Ta jima sosai anan har suka soma jin tashin kidan kwarya in da adaidai lokacin su Mamma suka iso sai dai babu Mama, gaisuwa aka sake kafin a rakasu in da ake kidan kwaryar aka nuna musu wajen zaman su, kafin daga bisani a rako Iman din wajen itama.    Da yamma kuma aka dawo ciki aka sake shiryawa in da aka nufi hall din dan gabatar da bikin da kuma kyaututtukan da aka shiryawa Iman din.   Sakon Maimartaba ne ya samu Fulani akan yana son ganin Matar Muhammad din dan a yau zasu wuce komai dare, mamaki ya kama Fulani dan a yadda suka shirya kwanaki uku zasuyi a nan din kafin su tafi adamawar, bata sani ba Muhammad din ne da kansa yaje ya samu Takawan ya roke shi akan a rage bidiar dan shi kam ya gaji sosai, take kuwa ya amince har ma ya sanar da Bubu tun a daren jiyan.    Maimakon a wuce da ita hall din sai aka fara kaita wajen Takawar. Kanta a k'asa sosai kwarjinin sa ya cika wajen ta yadda kowa ya kasa sakewa, nasiha ya soma yi cikin maganar sa da ta saka jikin kowa mutuwa, yayi musu fatan alkhairi sannan ya kare da sake jan hankulan mutane akan yadda rayuwar ta zama, basu dade a wajen ba, suka fito kowa na yaba karamci na Maimartaba da ya karbe su hannu bibiyu ba tare da nuna banbanci ko wani abu ba.    A gaggauce akayi taron, saboda tafiyar da zasuyi, sosai iman ta samu kyaututtuka masu tarin yawa a yan awowin da basu gaza biyar ba, kowa so yake ace shine yafi, kowa so yake ya burge Fulani da Maimartaba, dan kowa ya san yadda muhammad din yake a zukatansu. ***Motoci ne guda uku suka dauke su zuwa airport din daga su Mamma sai wasu yan uwan Abba su uku shikenan wanda zasu adamawar, shima saboda bikin da zasuyi ne suma badan haka ba da babu me zuwa. a lokacin Moh sun dade da isa suna zaune dasu Musaddik ana hira a wani kebantaccen wuri.    Zuwan su da aka dan suka dauki hanya babu wani bata lokaci. Ita kadai ce a wajenta, babu kowa a saman duk suna k'asa sai ita kadai kwal har ta dinga tunanin dalilin da ya saka aka kawo ta nan din ba abarta wajen su Mamma ba. Kamshin turaren sa ne ya amsa mata tunanin ta, ya karaso ya zauna kusa da ita yana kashe mata ido. Kayan jikin sa ta kalla wanda suka kasance na sarauta, sai takalmin kafarsa da akayi da fatar zaki yayi kyau sosai shigar gidan sarauta, babu hula akan sa ya rik'e ta hannun sa, sumar sa ta fulani ta sha gyara ya fito a bafulatanin sa sosai.    Shi din ma shigar ta yake kallo, yana kuma yaba yadda komai ta saka sai yaga ya karbe ta yayi dai-dai da ita. "Ba magana?" Yace bayan ya gama kallon nata Mirgina kanta tayi gefe tayi masa murmushi tace "Sannu da zuwa toh." "Yawwa." Yace yana jingina da kujerar jirgin sosai, be sake magana ba sai dai yanayin sa ya nuna mata kamar akwai damuwa, tasan yadda yake mata dan haka yau din sai taga kamar bashi ba, bata sani ba ko sarautar ce ta motsa. Satar kallon sa ta dinga yi sai taga ya kulle idon sa yayi kamar me bacci. Duk sai taji ta takura ta kuma damu, taba shi tayi kad'an, ya motsa amma be bude idon nasa ba, sai kamo hannun ta da yayi ya sakalo shi ta tsakanin nasa hannun ya harde su waje daya, kusan rabin jikin ta ya sauka a nasa, bata sake attempting komai ba har zuwa sanda suka iso jirgin ya sauka suka fito still hannun sa na sarke da nasa.    ***Kafarta a mike take tana sauraron bayanin da take mata, ko motsi batayi ba, kamar bata jin me take cewa har ta kai karshen bayanin tayi shiru tana kallon ta. Sai da ta dauki lokaci me tsawo kafin ta gyara zama, ta bud'e hannun ta, ta mik'a mata shi, jikinta na rawa ta ciro kwalbar da take nannade a gefen zanin ta, ta saka mata a cikin tafin hannun ta. Jujjuya shi tayi tayi a hannun nata tamkar me son gano wani abu. "Turare ne ranki ya dade, a jiki kawai ake shafa shi bayan haka babu wani abu." "Kin tabbatar da abinda kika ce?" "Allah ya taimake ki, yadda nayi miki bayanin haka yake, yace kar ayi wasa dashi, sannan kuma kar ayi sakacin da za'a samu matsala." "Rik'e." Ta mika mata, da sauri ta karba tana damke wa a hannun ta sosai. " Kin tabbata babu wani abu da ya faru tsakanin su?" " Na tabbatar, sai da ya nuna min komai kafin ya bani, yau zasu iso sai kiyi kokari kafin su tare a sabon bangaren su dan naji rad'e rad'in bikin ba zai dau kwanakin da aka tsara ba, bisa umarnin Sarki." Murmushi tayi me kyau, ta dawo ta zauna bayan ta ciro wata karamar riga ta karata a jikin ta,sai kuma ta ajiye tana mikar da hannun ta baya. " Kinyi kokari, kina da kyauta me tsoka idan har na samu biyan bukata." " An riga ma an samu gimbiya, ki kwantar da hankalin ki." "Tukunna dai." " Me yayi saura? Yan awoyi ya rage miki ki samu abinda kike so gimbiya ta." Jikin tagar dakin ta karasa, ta daga labulayen tana kallon harabar gidan da yadda hadiman gidan ke kaiwa da komowa a tsakanin bangaren Moh din da na Ammi, tasan duk shirin tarbar bakin ake, hankalin kowa ya riga ya koma chan dan haka zatayi amfani da damar ta isa bangaren Moh ta yi zaman jiran dawowar shi! Rano💕 *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107   1/31/22, 19:14 - Buhainat: Halin Girma       22 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ********** Tamkar rana haka harabar masarautar take, komai an shirya shi an tsara saboda shirin tarbar su. Tafiya sukayi doguwa a ciki kafin su kai wajen manyan gine-ginen cikin masarautar.    Ba mota daya suka shigo daga airport din dashi ba, shiyasa ma bata ganshi ha a sanda suke fitowa daga mota. Cikin rakiyar hadiman shashen Ammi da na gidan ma baki daya suka isa babban falon nata, da aka kawata shi matuka ana jiran isowar su. Kamar yadda suka samu tarba ta musamman a Kano haka aka karbe su anan dinma. Hakan ya kara bawa su Mamma nutsuwa da tunanin irin yadda Iman din zata samu kanta a gida irin wannan wanda yake cike da abubuwan da ba lallai ta iya dauka ba.    Bayan sun huta an gabatar musu da abinci ne Ammi ta saka aka rakasu masaukin su, wanda aka ware musu tun kafin isowar su. A gajiya kowa yake dan haka suna zuwa kowa ya mike aka shiga maida maganar yadda aka karbe su da irin sa'ar da Iman din tayi.    Tana jin su bata tanka ba, hankalin ta ya tafi sosai wajensa tana son jin yadda yake dan ta tabbata da akwai wani abu da ya rage masa walwala. ***Tun isowar su ta samu labari wanda dama abinda take jira kenan, ta shirya tsaf babu Kuma abinda zai hanata aiwatar da abinda tayi niyya shiyasa ma bata bari Kilishi ta sani ba balle har ta hanata.    Shigar sa shashen nasa bayan ya bar wajen Bubu hadimar ta, ta sanar mata wanda dama ta saka ta ne ta saka ido tana ganin ya shiga ta fad'a mata.    Tashi tayi tana gyara gashin kanta da ta saka ribbon din tayi sako-sako dashi, ta daura babbar Alkyabba akan kayan da suke jikin ta da ya kasance karamar riga ce mara hannu iyakar ta guiwa kawai, sai dogon wando a k'asan da ta saka saboda yadda zai zama ko ina na jikinta ya rufe.    Turaren da yake cikin Jakarta ta ciro, ta dunkule shi a hannun ta, ta fita ta kofar bayan cikin rakiyar amintacciyar hadimar ta. Tafiyar dake tsakanin bangaren Moh din da nasu da akwai tazara dan haka yasa suka bi ta baya har suka isa. Idon ta, ta daga ta dubi bangaren bedroom dinsa amma sai taga dakin babu haske sai sauran dakunan. Zagayo wa sukayi zuwa gaban ginin masu kula da kofar suka tashi ganin ta, da ido sukayi magana da daya, ya girgiza mata kai alamar eh sannan yace "Yarima na jiranki gimbiya Lailah." Jin haka ya saka dayan saurin bud'e mata kofar, ta kutsa kanta ciki kai tsaye tana jin kamar anyi an gama ta samu cikar burin ta.    Tafiya ta ke a cikin falon tana kallon komai, yadda aka sauya komai kamar ba part din da take shigowa a duk sanda ta ga dama ba, babban hoton da ke manne a jikin bangon dakin ta kurawa ido tana matsawa gaban sa. Iman ce a jiki, ita da Moh ranar da aka daura aure, sunyi masifar kyau kamar kayi musu magana su amsa. Wani bakin ciki ne yazo ya tokare mata a makoshi, taji kamar tayi wurgi da hoton ya tarwatse a wajen amma sai ta daure, ta maida hannun ta baya tana nufar bedroom din nasa in da tasan zata same shi.    Kafin ta karasa ta hango glass cup a k'asa a farfashe, ta durkusa ta dauki ragowar tana kaiwa hancin ta, murmushi tayi tana da yakinin komai ya zama daidai, everything is in order kamar yadda ta tsara. Hakan ya saka ta wucewa Kai tsaye ta murda kofar dakin ta kutsa kanta ciki tana zare alkyabbar da take jikin ta, ta zame a wajen ta fadi.    Muryar sa da ta soma bacewa yayi kokarin cewa "Waye!" Yadda yayi maganar ya saka ta sake tabbatar da komai yayi daidai, basu yi mata shirme ko shiririta ba. Karasawa tayi jikin gadon, ta kai hannu ta taba shi ta hasken bedside lamp da ke kunne, take kallon sa, idon sa yayi masifar komawa ciki yana lumshe su tamkar wanda yake shirin yin bacci irin baccin da yafi karfin sa yake neman kai shi k'asa. "Waye?" Ya sake maimaitawa da k'yar kansa da yake juya masa ya shiga kai masa sakon mayen kamshin da yaji ya karad'e dakin,kamshin da ya dauke shi zuwa wata duniya ta daban, a take yaji komai ya hargitse masa, ya mike da k'yar yana duban ta cikin ido, gaba daya komai ya chanja masa,ta juye masa Iman dinsa gaba daya. Hannu ya kai zai taba ta, ta saka karbi ta tura shi baya ya fad'a saman gadon! ***Text message ne ya shigo wayar ta, ta bud'e da sauri tana fatan ya kasance daga shi, kamar yadda tayi tsammani, shi din ne kuwa, _"A rako ki shashe na."_ Haka kawai sakon ya kunsa, kifa wayar tayi tunanin yadda zata fara fadawa Mamma yace a rakota bangaren sa. Da kunya sosai bata kuma jin zata iya,shiru tayi tana wassafa abun a ranta, zuciyar ta na ce mata kawai ta kira mamma ta fad'a mata ai ba wani abu bane, wata zuciyar kuma na ce mata a ah. Ta na nan zaune har aka dau tsahon wani lokaci, sakon ya sake shigowa irin na dazu a karo na biyu, sai dai banbancin lokaci. Amaani ta kira suna zaune suna cin snacks da juice, ta bata wayar tace ta kaiwa Mamma. Sai ta kifa kanta tana jin nauyin Mamma. Tana jin sanda Mamman tazo kanta, tana sababi "Yanzu haka ake gaya miki anayi Iman? Mijinki yana kiranki tun dazu kika yi shiru. Kunyar me? Zamani ya chanja kinji? Tashi maza ki gyara jikin ki, ga masu kula dake nan da yawa daya sai ta rakaki, tashi maza kina kara bata lokaci." Tashi tayi kunya na nukurkusar ta,ta dinga sunne kai taki yarda su hada ido da Mamman, tana kallon ta, ta fito mata da wasu kayan tace ta sauya, sannan ta kawo mata wani abu a cup da madara ta bata ta shanye, ta faffesa mata turarurruka masu kamshi sannan suka fito in da yan matan ke zaune, da sauri suka tashi su biyu, suka sakata a tsakiya suka nufin bangaren Moh din da yake da dan tazara da wanda aka sauke su.    Babu kowa a kofar, kai tsaye ta shiga su kuma suka samu waje daga wajen suna jiran ta dan tace musu ba jimawa zatayi ba, babu kowa a falon babu motsin komai, dakin farko ta bud'e da sallamar ta, baya ciki, sallama take amma ba da karfi sosai ba, a tunanin ta ko ya shiga toilet ta zauna jiran shi, shiru shiru babu alamar sa, ta kasa kunne ko zata ji karar ruwa a toilet sai taji kamar shesshekar kuka, sake kasa kunnen tayi sosai ta tabbatar da abinda taji, sai ta fara tunanin aina take ji, dakin da yake karshen falon ta kalla, babu alamun haske a ciki amma kuma tabbas da ga nan ne sound din yake fitowa. Tashi tayi ta nufi dakin tana taraddadin abinda zata tarar. A hankali ta tura kofar, ta leka da kanta kafin ta shiga da jikin ta gaba daya, tana gama shiga wutar dakin ta kawo, kwakwalwarta ta dauke kamar yadda ake dauke wutar nepa, idanun ta suka sauka akan Moh yayi ruf da ciki a saman gado yana bacci cikin kwanciyar hankali, boxer ne kawai ajikin sa dgaa shi babu komai. Da sauri ta maida kallon ta kan matar dake zaune a kasan tiles din dakin, kanta babu dankwali gashin kan nata da ya hargitse ya barbazu har zuwa saman fuskar ta, shigar jikin ta kawai ta kalla tayi saurin dauke kanta tana kokarin barin dakin, sai dai bata kai ga barin wajen ba dan ko taku biyu batayi ba, taji sanarwa shigowar Maimartaba, bayan sanarwa ne taji shigowar sa.    Karuwar kukan Laila ya sake sakata cikin yanayin da ta shiga, har Maimartaba ya karaso bakin dakin tana tsaye kamar an dasa ta, bata san me zatayi ba. kallon ta yayi kafin ya maida kallon sa cikin dakin, yayi musu kallo daya wani abu me dacin gaske yana tokare shi a goshi. Juyawa yayi sai a lokacin kwakwalwarta ta kai mata sakon waye wanda ya shigo din, da sauri ta zube a wajen ta gaishe shi cikin muryar ta da take rawa sosai.    Be amsa mata ba, sai daga mata kai da yayi ya juya ya fice yan rakiyar sa suka bi bayan sa cikin tunanin dalilin zuwan Bubun shashen Moh.     Kasa daga kafarta tayi daga wajen, ta jingina da bangon dakin tana karanto duk addu'ar da tazo bakin ta, ji tayi kamar ana mata magana, ta dago tana kallon cikin dakin "Amarya! Kinyi farin gani ko?" Me zata ce? Shiru tayi tana maida idonta ta rufe shi ruf tana kokarin ajiye abinda ta gani din da kuma abinda zuciyar ta take haska mata waje daya. "Anya? Anya kuwa? Muhammad? Me ya faru? Me yake shirin faruwa? Wacece wannan din?" "Karki wahalar da kanki tunanin wacece ni, sunana Laila, gimbiya Lailah." Yawu me karfi ta hadiye, ta hau kokarin daidaita kanta waje daya, shigowa taji an sake yi, ta daga idonta da sauri wannan karon wata babbar mata ce ta shigo a hargitse, tayi saurin yin kan wadda ta kira sunan ta da Laila tana rik'e ta, tana kallon yadda Lailan ta cigaba da rusa kuka kamar Allah ya Aiko ta, matar na bata baki jikin ta na rawa sosai. Daga ta tayi da sauri, ta yafa mata mayafi ta rik'e hannun ta, suka zo daidai in da Iman din take tsaye, matar tayi mata wani mugun kallo, ita kuma Laila tayi mata murmushin da ta tsaya mata a rai. Fita sukayi tayi saurin zuwa ta sakawa kofar key, ta dawo ta durkusa a k'asan falon ta shiga kuka, kukan da take ta kokarin rikewa dan bata son su ga weakness dinta, dama chan ita mutum ce me taurin zuciya da wuya kaga weakness dinta, shiyasa yanzun ma ta daure har suka fita.    Sai da tayi kuka sosai sannan ta tashi ta share hawayenta, a kalla zata so taji ta bakin shi, kar ta yi judging dinsa da abinda ko a musulunci babu hujja, dan bata gansu suna aikata wani abu mara kyau ba. Duk da ta na kokarin karfafa jikinta da zuciyar ta akan ta bari taji komai, amma kuma jiki da zuciyar ta ta sunyi sanyi, sanyin da take jin kamar komai ya kare mata, kasan zuciyar ta tana jin zafin sa, tana jin haushin sa amma kuma bata da damar yanke masa hukunci.    A yan awannin da tayi a cikin gidan nasu ta fuskanci akwai wani Babban al'amari da ya shafi Moh dinta. Tana jin kamar gadar zare aka hada masa har ma da ita. A nutse take duk da abin ya kadata, dan babu matar da zata ga wata mace a dakin mijinta cikin yanayin da taga Laila ba tare da taji komai ba, sai dai ta yarda da addu'a dan haka ta dage sosai har ta soma jin nutsuwa na saukar mata.    Bata san dadewar da tayi a wajen ba, taji kamar motsi a dakin, ta tashi ta dubo cikin rashin sa'a ta cire takalmin ta, ta taka glass din da yake fashe a wajen, kara tayi hakan ya farkar da Moh gaba daya, ya mike da sauri kansa yayi wani irin sarawa da be taba jin irin sa ba, jiri yaji yana neman kayar dashi yayi saurin komawa ya zauna yana dafe kan, bayan kamar sakan goma ya mike a hankali ya fito.    A durkushe ya ganta tana rik'e kafarta da har ta fara jini, da sauri ya karaso ya durkusa a gabanta yana kama kafar "Me ya same ki? Me kika taka." Kokarin janye kafarta tayi, ya sake kama kafar ya rik'e yana kallon kafar cikin tausayawa. "Cika min kafata." Tace ba tare da tasan me yasa ba, kawai ganin sa ya sakata jin haushin sa. Kin cika mata kafar yayi, sai ma daukar ta da yayi gaba daya duk da yadda yake jin sa babu kwari, ya ajiye a gefen gadon ya dauko first aid box din sa yazo ya durkusa a gabanta ya gyara mata kafar Allah ya taimaka kwalbar bata shige ba. "Yaushe kika zo nan? Ya akayi nayi bacci? Me ya faru aina aka samu kwalba a wajen nan har kika taka? Ina masu kula da wajen?" Ya jero mata tambayoyin cikin son tuna wani abu, da Ido kawai yake bin sa kamar me son karantar sa, sai dai bata ga komai ba sai tsantar gaskiyar sa a yadda yake maganar. Janye kafarta tayi ta mikar da ita a saman gadon, ya dawo ssman gadon ya zauna yana jan kafar ya dora akan cinyar sa. "Bacci ne ya dauke ni bayan na sha juice daga nan kuma bansan me ya faru ba, kin dade kina jirana? Da baki tashe ni ba?" "Bana so na katse maka barci ne." Tace ganin duk ya damu, ajiyar zuciya ya sauke yana matsowa ya gyara mata kafar yadda zata ji dadi, ya mannu a jikinta. " Kiyi hakuri, kaina ne naji yana min ciwo sosai shine kawai nazo na dan huta bansan zanyi bacci ba." " Ba komai." Tace tana rufe idon ta " Bacci?" " Umm." Tace a gajarce dan bata son doguwar magana tana son tattara bayanan da ta samu ta hade su waje daya kafin wayewar gari. Tashi yayi ya fita bayan ya maida rigar sa,  ya hau k'wala kiran ma'aikatan wajen, da sauri ya shigo yana raba ido, masifa ya fara yi masa akan dalilin barin kwalba a hanya, hakuri yayi ta bashi yayi saurin gyara wajen sannan ya fita.    Ji yayi duk jikin sa yana masa ciwo, chan k'asan zuciyar sa kuma wani irin feeling ne da be san dalili ba, ji yake kamar idan har be samu abinda yake so ba zai iya rasa ransa, yana wanka yana tunani har ya kammala ya fito daure da towel iya ka guiwar sa, kallon in da take kwance yayi, ta dunkule waje daya kamar me jin sanyi.    Kaya ya saka sannan yayi sallah ya duba wayar sa yaga misscalls da yawa, ganin dare yayi ya saka shi ajiye wayar ya hawo gadon yana juyo da ita tana kallon shi. Hawaye ya gani a saman kuncin ta, ya saka hannu cikin mamaki yace "Kuka?" Kamar wadda take jiran kiris ta shiga rera shi sai dai babu sauti, rikicewa yayi ya hau tambayar ta menene, bata amsa masa ba, ta cigaba da kukan ta wanda ita kanta bata san me yake sake tunzura ta take kukan ba, da farko ta zata zata iya daurewa sai daga baya ta gane duk dauriyar ta wannan ya wuce in da take tunani, kishin mijinta ne ya sakata kuka. Magiya ya cigaba da yi mata akan ta fad'a masa dalilin kukan ta amma taki, rungume ta yayi a jikinsa yana lallashin ta amma kamar kara ingizata yake, ya rasa yadda zai, ga wani irin abu da yake jin yana taso masa. Kasa daurewa yayi ya hade bakin su waje daya, da karfi tayi kokarin turashi ta amma ta kasa! Rano💕 *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107   1/31/22, 19:15 - Buhainat: Halin Girma       23 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ******* A hankali ya shiga bin ko ina na jikinta yana aika mata da sakonnin shi, kukan da take na taba shi, yana jin har cikin kansa, sai dai ba zai iya controlling kansa ba, abinda yake ji yafi karfin ikon sa, ba kuma zai iya tsere masa ba.    Da fari ta dauka babu wani abu da zai mata sai son ganin ya rarrashe ta, amma daga baya sai taga abin yana chanja salo. Jikinta ne ya hau rawa ta ko ina, ta sauya akalar kukan nata zuwa magiya da rokon sa, baya jin ta, idan ma yaji ta baya tunanin zai iya yi mata abinda take so din.    Juyo ta yayi ta zama a saman sa, ya sake hautsina ta zuwa kasansa , ya ajiye mata dukkan karfin sa, ji tayi kamar numfashin ta na janye wa daga jikin ta, ta dinga jansa tana kuka tana kiran sunan sa, yadda yake kissing dinta kamar mayaunwacin zaki ya sake tsorata ta,shi kansa jikin sa rawa yake,ga wani karfi da yake ji ya zo masa wanda be taba jin irin shi ba. Kayan jikin ta ya shiga janyewa yana wurgi dasu ta kowanne angle, har yayi nasarar rabata da komai. Idanun sa da suka rine sosai ya zuba mata yana kallon ta, wani abu yana kaiwa da komowa a tsakanin wuyansa. "I'm so sorry." Ya furta mata da k'yar kafin ya shiga aiwatar da abinda yayi niyya.    Sama sama yake jin ta, cikin muryar da ta shige ciki saboda kukan da ta sha,  kamar mafarki haka yake jin abun, juyowa yayi da k'yar ya dune ta, tana kwance agefen sa taci kuka har ta gode Allah. "Subhanallah!" Ya furta yana tashi, abinda ya faru ya shiga dawo masa akai, ya akayi haka? Bayan yayi ma kansa alkawarin zama so gentle, yadda yasan ba zai bata wahala sosai ba, what has gotten in to him? Me yayi mata?   Rik'e ta yayi yana kokarin daidaita kansa ya samu damar kwantar mata da hankali "I'm so sorry dan Allah, dan Allah kiyi hakuri ki yafe min, bansan me ya hau kai na ba, this is not me, bani bane ba." Bata da karfin da zata kwaci kanta, sai kawai ta lafe a jikin sa tana jan numfashi. Kanta ya dinga shafawa a hankali a hankali, yana jin wani irin son ta, na saka shigar sa. Idan har abinda kwakwalwar sa ta dawo mata dashi gaskiya ne, toh lallai sai yaci uban Lailah, dole ne yayi mata abinda ko a hanya ta hadu dashi ba zata nuna ta sanshi ba.   Idonsa a rufe yana tariyo abinda ya faru, tabbas ya ganta a tsaye a kansa, lokacin da baccin da be san na menene ba dauke shi da sauri. Tunanin sa ne ya koma baya, zuwa sanda ya shigo ya tarar da juice akan table din da ake ajiye masa, a gajiya yace amma ya tsaya ya sha daga nan ne ya fara jin wani abu me karfin gask yana taso masa, sai wani irin bacci me nauyi da be taba jin irin sa ba. "Desire pills?" Ya furta yana kokarin tashi, k'ara tayi mara sauti ya tuna tana jikin shi, yayi saurin komawa ya zauna yana sake gyara ta. " I'm sorry." Ya saka hannu ya goge mata hawayen da suke sauka a fuskar ta. Tsawon minti talatin yana a haka yana tunanin abubuwan da suka faru a daren, tabbas koma menene an shirya masa abu ne, be san ya akayi ya bada kafa ba, har aka yi galaba akansa. Tashi yayi bayan ya gyara mata kwanciya, ya shiga toilet ya gyara jikin sa, sannan ya fito, ya taimaka mata, ta tashi tana ciccijewa sai dai taki yarda su hada ido, ta hade fuska sosai a dole haushin sa take ji, haushi biyu ne suka hadu waje daya, ta kasa manta abinda ya faru farko da na karshen.   Toilet din ta shiga sai taga ya biyo ta, ta dube shi tana tsaye gaban bathtub din, ta marairaice fuska, yi yayi kamar be ganta ba, ya rufe kofar ya karaso ya durkusa yana taba ruwan. "Ka fita." Ta fad'a muryar ta babu karfi, banza yayi kamar be ji ta ba, ya ciro towel a cikin jerin sabbin towels din dake jere a cikin wata drawer, sannan ya dauko brush da toothpaste ya saka mata a jiki ya ajiye a gefe ya hau nannade hannun rigar sa. Kamar ta rusa ihu haka taji, ta rasa yadda zatayi ta hanashi, bata ga alamar ma zai hanun ba, sai kawai ta hakura ta zubawa sarautar Allah ido, bata san rashin kunyar namiji ta kai haka ba. Sai da ya gama abinda yayi niyya ya tabbatar yayi mata yadda zata ji dadin  jikin ta sannan ya kyale ta ya fito yana jawo mata kofar.    Kwanciya ta sake yi a cikin tub din ruwan na ratsa ta, gefe tana tuna abinda ya wakana tsakanin su. Murmushi tayi, duk kalaman sa na dawo mata daki daki, abu daya ne ya tsaya mata har take kokarin alakanta shi da abinda ya faru kafin nan, idan har shi din ba mutumin kirki bane, idan har wani abu ya faru tsakanin sa da Lailah, ba zai sha wahala wajen neman hanya ba.    Saurin kawar da tunanin tayi kunyar kanta na kamata kamar yana wajen, da wanne idon zata koma wajensu Mamma ma wai tukunna, da wanne idon? Kwankwasa mata kofar yayi ganin ta dade, sai ta tashi tana karfafa jikin ta, ta dauro towel din bayan ta goge jikinta ta fito kanta a k'asa. Ajiyar zuciya taji ya sauke bayan ya kare mata kallo, hankalin sa yaki kwanciya tunanin sa ko yayi mata illa ne, sai yaga akasin haka, be sani ba ko duk cikin dauriyar da ya gane tana da ita bane. Lokacin sallah ake kira a cikin masallacin cikin Masarautar, daga jikin kofar ya tsaya be fita ba, yana kallon ta har ta gama ta saka doguwar jallabiyar sa daya ajiye mata a gefen gadon, murmushi yayi ya fice kansa sanye da farar hula da ake kira da tashi ka fiya naci ya dora doguwar riga irin wadda ya dauko mata.    A sahun farko ya samu Kamal, daga liman sai shi, hakan ya bashi mamaki amma ya share, bayan an idar suka gaisa a tsattsaye ya fice yana son komawa ya ga halin da take ciki. Sun hadu da Bubu amma be masa magana ba, ya dai ce masa ya sameshi idan garin ya gama wayewa, sai dai yanayin fuskar Bubun ta saka shi tunanin akwai wani abu me girma.    A saman sallayar ya tarar da ita, ta kwanta akan hannun ta ta mik'ar dashi, karasawa yayi ya daga ta, ya maida ta saman gadon yana zama a gefen ta. Rufe idon ta tayi da sauri jin ya matso da fuskar sa daidai saitin tata. Iska ya fitar me zafi, ya tashi ya kashe wutar dakin ta dawo ya hawo gadon ya kwanta. "Me ya faru?" Yayi mata tambayar kai tsaye, yadda yayi sounding zaka gane daga muryar sa, maganar yake so suyi, shiru tayi bata ce komai ba, dan bata san me zata ce ba, tace masa ta same shi da wata a daki ko me? Ta yaya ma zata fara? "A lokacin da kika zo dakin part din nan, wani ya shigo? Ko kinga wani a ciki?" Nan din ma shiru ta sake yi masa, kasan zuciyar ta na ce mata kar ta yarda,kawai zai yi amfani da innocent dinta ne ya nuna mata kamar be san komai, daga gefe kuma wata zuciyar na ce mata ta fad'a masa watakila be sani ba, watakila so ake a hada su, tunda har yanxu bata san komai akan sa ba, ba zata iya dorar da wani abu ba balle har ta iya judging dinsa, kawai dai a matsayin ta na mutum me tunani , tana kyautata masa zato.    Birkitota yayi da karfi muryar sa na fita da dan karfi akan dazu yace "Tell me, me ya faru? Wani abu ya faru? Kin samu wata ko wani da kika zo? Wani ya fad'a miki wani abu ne? Me ya faru!" Kuka ta samu kanta da fashewa da, ya tashi da sauri yana kunna wutar dakin, ya dawo ya tashe ta zaune suna fuskantar juna, zuwa lokacin ya ji yana neman loosing temper dinshi. "Kalle ni, look at me! Menene? Me ya faru da ban sanshi ba? Tell me, waye yazo? " Maimartaba ne yazo." " Maimartaba!?" Ya furta da dan karfi cikin yanayin dake nuna tsantsar mamakin sa "Me yazo yi a part dina? Me yace? Me ya faru? Wani abu ne ya faru while i'm sleeping?" " Eh." Ta daga masa kai, tsugunawa yayi a wajen yana tattaro dukkan nutsuwar sa, gabansa na faduwa da abinda zata ce dan yasan ba karamin abu bane zai kawo Bubu part din sa. " Believe me, bansan komai ba, kamar yadda babu alkalami akan me bacci, na rantse miki bansan me ya faru ba." Goge fuskar ta, tayi da hancin ta a jikin sa, ta dago tana kallon kasa tace " Naga wata Laila a nan." Ta nuna wajen da Lailan ta zauna " Lailah!? " "Eh." "Ehen, sai me?" "Tana zaune a wajen tana kuka sosai, daga nan sai Maimartaba ya shigo, sannan ya tafi sai kuma wata mata ta shigo ta daga ta suka fita    Abu ya hadiye me karfi, ya yi kokarin ganin be yi wani abu ba, a hankali yaji kamar ana masa rad'a _Be calm Moh, be calm."_ Kamar wanda aka saka abu aka bubbuge ma guiwa haka ya zube a wajen, zai tolerating komai amma banda fushin Bubu, shi za'a wa wannan kazafin? Abinda be taba tunani ko shaawar aikatawa ba, Zina? Shi Muhammad shi aka yiwa wannan sharrin? Saboda yayi kamar be san wani abu yana faruwa ba, shine har aka samu damar yi masa wannan kullin?   Tana ankare da yadda ya shiga kaduwa, tana kuma ganin yadda Adam apple dinsa ke hawa da sauka tsakanin makogwaron sa, idon sa kadai zaka kalla ka tabbatar da ransa yayi masifar baci.    Sai da yayi kusan minti goma be ce komai ba, ba dan bashi da abinda zai ce din ba, sai dan yadda mamakin Iman din ya hanashi komai, be zaci haka daga gareta ba, idan wata ce, ba zata iya daukar abinda ta gani ba, har ta tsaya jiran shi, ya ga kokarin ta sosai kuma ya jinjina mata, hakan ya kara mata matsayi a zuciyar sa.   Girgiza mata kai yayi yana kama hannun ta "Kin yarda dani?" " I don't know." Tace tsakanin ta da Allah "Bansan yadda zan dauki abun na ajiye ba, all I know shine I'm hurt, more than yadda nayi tunanin I ll be." Folding hannun nata yayi a cikin nasa ya damke. "I promise to make everything right, koma menene we will over come it, in sha Allah, together we will build tomorrow, I promise you that!" Shiru sukayi babu wanda ya sake magana, ko be ce ba, ko be ba ita zata gano komai, zata gane kafin ma ya gane, tana da kaifin tunani, sannan tana karantar komai kafin tayi judging din mutum.    Kwanciya tayi ganin suna zaune kowa da abinda yake tunani, ganin ta kwanta sai ya mike ya fita, ya nufi part din Ammi duk da lokacin garin ke karasa yin haske. Ya san tana zaune har lokacin tana azkar kamar yadda ta saba a ko da yaushe.    Yadda ta ganshi ya shigo jikin ta, ya bata babu lafiya, katse abinda take tayi ta mike tana kallon sa har ya karaso "Lafiya Babana?" "Ina kwana Ammi?" Ya duk'a k'asa ya gaishe ta, kafin ya amsa mata tambayar ta "Ba lafiya ba Ammi, yarinyar nan Laila tayi abinda zan nuna mata ko ni waye, ganin kamar ban san me take ba ya bata damar aikata abinda ta aikata wanda zai zame mata dana sani, dama chan Ammi kece kike hanani, saboda zumunci amma not anymore." "Me ya faru?!" "Bubu be sanar dake komai ba?" "Be ba, me ya faru?" Iyakar abinda ya sani ya sanar da ita, jikinta yayi sanyi, ta kuma san Bubu zai iya daukar kowanne mataki akan muhammad din, tun da be taba sanin wani abu daya danganci Laila din ba da shi, ita kawai da Muhamamd din ne suka sani sai Kilishi. "Babu abinda zai faru, kai dai ka rike gaskiya, zatayi halin ta." "Shikenan, zanje naga Bubu, zanji me zaice." "Allah ya taimaka, zanyi magana dashi nima in sha Allah." Fita yayi ita kuma ta zauna a wajen tana hango abinda zai je ya dawo. Kasancewar safiya ce, shiyasa ya shige kai tsaye wajen Bubun, a lokacin ya fito wajen shashen bayan sallah yana duba wasu littattafan sa. Sai dai yau ya kasa yin komai, tunda aka fito masa da littafan ya kasa taba ko guda daya, balle har ya karanta, abinda ya gani jiya yayi masifar girgiza shi, ya kada shi sosai, har yayi furucin da yake jin idan har Muhammad be wanke kansa a tsawon kwanaki biyar ba, ko da yana da gaskiya ya zama dole ya auri Lailah tun kafin maganar ta fito waje, a jita a ko ina.     Aji ya samu da maganar a lokacin dan ji yayi yana neman faduwa k'asa, sai dai yadda yayi tunanin maganar zata taba Aji sai yaga akasin haka, yana zaune kem fuskar sa bata chanja ba ko kad'an, har sai da Bubun ya kasa daurewa ya tambayi Aji dalilin da be ji abun ba, murmushi yayi yace. "Ahmadu kenan, da Muhammad da Laila su dukkan su nawa ne, ni na haifi iyayensu na kuma san kowa a cikin su, na san abinda kowa zai aikata da wanda ba zai aikata ba, duk da yanzu ance baa shaidar mutum, amma ni zan shaidi Muhamamd ko aina ne, lallai akwai wani al'amari bayan abinda kai din ka gani." "Amma kuma komai ya nuna, a yadda na ganshi naga Lailan, bani da hujjar kare shi ko yarda dashi, idan har nayi haka sai naga kamar banyi wa Yaya adalci ba, mutane zasu ce ko dan babu shi. " " Duk abinda zakayi karka tuna mutane dan dama su baa raba su da abin fad'a, kayi gaskiya kawai. " " Toh ta yaya zan yarda da Muhamamd be aikata ba? Da wacce hujja zan yarda dashi? " " Ka bashi lokaci, ya kare kansa, idan har ya amsa laifin sa shikenan, idan kuma ya kawo hujja gamsasshiya toh." " Idan har muhammad ya kasa kawo hujjar bai aikata abinda ni da mahaifiyar Laila muke tunanin ya aikata ba, nayi alkawarin aura masa ita a tsakanin kwanaki hudu! "   Dawowa yayi daga tunanin yadda suka kwashe da Aji yayi, ya bata rai sosai sanda Moh ya dire a gabansa, cikin girmamawa ya gaishe shi, amma sai yaki amsawa, ya kausasa murya yace " Ban kiraka nan dan ka gaishe ni na amsa ba, ban kuma kiraka nan dan muyi doguwar magana ba, me ya faru tsakanin ka da Lailah? " " Babu komai Bubu. " Yace kai tsaye dan dama ya riga ya shiryawa tambayar " Babu komai? " " Eh babu, duk abinda ka gani sharri ne, bansan komai akai ba. " " Waye shaidar ka? " " ALLAH! " Ya fad'a kai tsaye, shiru Bubu yayi, ya dauki wani lokaci kafin yace " Ka dauki alaka ta da kai ta d'a da mahaifi ka ajiye a gefe, ka kalle ni a matsayin alkali da aka kawo min kara ka, na baka nan da kwana hudu ka kawo min kwakkwarar hujja, idan har kwana hudu ya wuce babu komai, nayi maka alkawarin aura maka Laila! " " Aure?!!! " " Aure, tashi ka bani waje." Jikin sa a sanyaye ya tashi, ya fice cikin sauri sauri ya nufi part din Lailan, yana tafiya yana huci, ji yake kamar ya dauko bindiga ya harbe ta, mutanen da suka fara fitowa wanda suka kasance masu aikace aikace a tsakanin parts din suka hau mamakin ganin Moh a irin lokacin shi kadai babu wani tare dashi. Be same ta a bangaren nata ba, tana bangaren Kilishi,juyawa yayi zuwa bangaren Kilishi yana ayyana kalar rashin mutuncin da zai yi musu.      Sai da ya kusa zuwa sai kuma zuciyar sa tace yaje yayi musu me? Yafi karfin haka, ba girman sa bane, dan haka sai kawai ya koma nasa part din yana lissafin kwanaki hudun da Bubu yace, yasan zai iya yin komai ba kuma sai karya alkawarin sa ba, idan kwanakin suka cika bashi da wata hujja. Abu na karshe da zai iya shine auren Lailah, gwara ya hakura da komai akan ya aure ta.     Bacci ya sameta tanayi, baccin da yasan na wahala ne, duk tausayin ta ya kamashi, shi da yaso ta huta sosai kafin ta fara sanin komai amma sai gashi daga shigowar ta gidan ta fara da karo da abinda yafi komai muni. Peacefully take baccin,fiye da wanda tayi jiya, a kalla yanzu ta samu kwanciyar hankali bayan ta sanar masa da abinda yake damun ta, yasan tayi dauriya sosai.    Kissing goshin ta yayi, ya gyara mata kwanciyar ya koma dayan side din ya kwanta da tunanin kwana hudu Rano *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/1/22, 10:25 - Buhainat: Halin Girma       24 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw Sai da rana ta daga sosai sannan ta farka, da sauri ta mike tana mamakin dadewar da tayi tana bacci ita da ya kamata ta koma wajen su Mamma. Sakkowa tayi tana jin jikin ta da dama-dama, ta shiga takawa a hankali zuwa toilet din dakin,ta wanko fuskar ta, ta fito ta gyarata sannan ta cire jallabiyar tasa ta maida kayan ta, ta ajiye masa a gefen gadon ta fito zuwa falon. Tunanin yadda zata iya komawa wajen su Mamma take da kuma yadda zatayi da kunyar da take ji daga zuwa ta dawo sai kwana bayan ba haka ya kamata ba a ganinta. Abin takaicin ma bata dauko wayar ta ba balle ta kira, tana tsaye tana tunanin yadda zata fita taji maganganu a kofar part din,wajen window ta isa, ta daga curtains din tana son ganin komai. Gabanta ne ya fadi, tayi saurin cika window din a daidai lokacin da taji suna karasa maganar su. Kyakkyawa ce ajin farko, kana ganin ta kaga bafulatanar adamawa, yau ba kamar jiya da ta soma ganin ta ba, tana cikin shiga me kyau harda Alkyabba, tayi kyau fuskar ta fes alamun tana cikin farin ciki. Kokarin daidaita kanta tayi sanda taji an turo kofar an shigo, idonsu ya hadu lokaci daya, wani banzan kallo Lailan ta watsa mata tana karaso wa ciki a gadarance, ta samu saman daya daga cikin kujerun falon ta hakimce baiwar ta,ta gyara mata k'asan rigar sannan tace ta fita ta basu wuri. Tana fita ta kalli Iman irin kallon sama da k'asa kafin tace "Barka da rana amaryarmu." "Sannu." Kawai Iman din tace ta juya zata bar wajen amma sai ta dakatar da ita "Nace ba, ya kika ji da kwanan bakin ciki? A ranar farkon ki a dakin mijinki?" "Bakin ciki kuma? Na me kenan?" Ta tambaya Kai tsaye kamar bata gane me Lailan take nufi ba "Na abinda kika gani mana, bakin gani, kinga true color din so called mijinki ko?." " Ohh, wannan wasan kwaikwayon wai? Yayi kyau sosai ya kuma tsaru yadda ya kamata, sai dai shi actor din be san kan wasan ba dan be ma san me yake faruwa ba, shine kawai matsalar film din amma yayi kyau." "Me kike nufi?" Tace a hasale tana mikewa tsaye " Abinda kika sani shi nake nufi, kin dauka zan yarda da banzan plan dinki? I'm not an illiterate, I can tell when someone is lying, beside mijina ba zai taba aikata abinda kika ikirarin ya aikata, and i trust him yadda bakya tunani." "Wow! Wow!! Wow!!! Sannu da kokari, I love your confidence, amma wanne irin sani kikayi masa haka? Da har zaki bashi irin wannan yardar? Kinsan waye namiji kuwa?" " It doesn't matter yaushe na sanshi, all that matters now shine, miji na ne, kuma nayi trusting nashi, dari bisa dari." " Shikenan, sai muga yadda zakiyi depending mijin naki at this critical condition, let's see how far you can go...." " Kwana hudu kachal kike da, idan har baki samu way out ba. Ki shirya karba ta a matsayin kishiyar ki, sannan na fitar dake ta karfin gaske, dan baki da waje a gidan nan, captain nawa ne right from the start kuma he will always be mine." Murmushi Iman tayi mata, tana jin wani irin tsana da haushin Lailan, tana jin zata iya komai, idan tace komai tana nufin komai domin taga ta fitar da shi daga koma menene, akwai babban kalubale a gabanta, amma ba zata karaya ba, duk wanda ya rik'e Allah da addu'a ya gama, da ikon Allah sai tayi galaba akan duk wani makiyin su. Ta daina shiru, duk wanda yace mata kule! Zata ce masa chas! Ita kanta bata san tana da courage din da zata iya maida mata martani ba, sai gashi. Juyawa tayi ta koma bedroom din dan ba zata cigaba da bata lokaci akan wadda bata tunanin tana da hankali ko kad'an. Wayarta ta gani ajiye a saman chest of drawers ta dauka ta kira Mamma da k'yar, sukayi magana ta ajiye ta zauna tana lissafin rayuwar da zatayi a irin wannan gida, tuna sanda ake mata fad'a irin na bankwana tayi, wata Babar su Abba tana ta jaddada mata hakuri da kuma shirya wa duk wani kalubale na gidan sarauta, karta bari a takata kar kuma ta cuci kowa, akwai makirci sosai wanda zata gamu dashi amma idan ta nutsu tayi hakuri da karfin addu'a Allah zai bud'e mata komai.    Bata jima a zaune ba taji ana mata knocking, ta tashi ta bud'e ta fito, russunawa tayi har k'asa da sauri ta gaishe ta, kunya ta kama Iman din ganin Matar da zata yi kusan sa'ar Mama tana gaishe ta a haka. Kaya ta mika mata cikin girmamawa tace ta chanja zata rakata bangaren Fulani (Ammi) juyawa tayi ciki, dan dama kayan jikin ta sun dame ta sosai. Sai da ta shirya tsaf  sannan ta fito, ta lura Laila ta jima da barin falon sai dai mayen kamshin da take yana nan a falon. Kai tsaye shashen Ammi suka wuce wanda sai a sannan ne ta sake karewa fadar gani sosai. Anan suka tarar da su Mamma da wasu mutanen wanda da yawan su kana kallo zaka gane alakar su da gidan saboda yanayi na kama da suke da juna. Shigowar su ya saka kowa maida hankali kanta kowa na son ganin amarya, tunda jiya babu wanda ya samu ganin ta saboda dare. Kanta a k'asa taki yarda ta dago saboda yadda take jin kamar ta nutse, a tunanin ta duk sun san daga in da ta taho, bata san Mamma bata fad'a ba sun dai barshi a zuwan sun barota ne tana shiryawa. Sai da duk suka lafa ne aka zazzauna sannan ta gaida Mamma da take kallon ta da murmushi, murmushin da ita kadai ta san ma'anar sa, hakan ya sake saka Iman din cikin jin kunya.   Sanda ta shigo Ammi bata falon, tana zaune suna magana da Amaani ta dawo, da sauri Iman din ta zamo daga kujerar ta gaishe ta, ta rik'e ta, ta mik'ar da ita tsaye tana amsawa a sake sosai, sannan ta saka a raka Iman din part din Kilishi.    Hannun ta cikin na Amaani suka shiga, babu kowa a falon farko sai wata baiwa guda tana goge-goge,wadda ta rako su ce tace su zauna sannan ta nufi kofar ciki don sanar da zuwan su. Jim kad'an ta dawo ta tsaya a gefe, zuwa wani lokaci Kilishin ta fito, fuskar ta kadaran kadahan ba zaka gane komai ba, Iman bata kalle ta ba, ta gaishe ta cikin girmamawa ta amsa a yatsine bata ma zauna ba. "Hari wannan din itace sirikar tamu?" "Itace ranki ya dade." "Lallai sannu yarinya, shi ko Muhammad ya rasa wa zai dauko mana sai yar karamar yarinya haka? Ko da yake ra'ayin sa ne ai, ba kuma a san ya akayi ba dai, ko da yake dama dai yaran talakawa sai a hankali, idon su idon me arziki sai in da karfin su ya kare, sannu kinji? Allah ya bada zaman lafiya." Sai ta juya " Hari naga amarya, ki gaida uwar dakin naki." Wani abu ne ya tokare wa Iman a makogwaro, idan har ta fahimci maganganun matar tana nufin asiri tayi ta aure shi kenan, a fakaice ta ci mata mutunci babu gaira babu dalili, bayan bata san ta ba, idan banda jiya sai yau ne karo na biyu da ta taba ganin ta. Ajiye ta tayi a daidai mazaunin da da ajiye Laila, ta kuma kuduri aniyar zama dasu daidai da yadda suka zaba.   Daga nan sai suka wuce bangaren Aji da Hajja, amma a mota saboda tazarar dake tsakanin bangarorn biyu, sosai taga karamci da girmamawa dan Adam, Hajja kamar ta goye ta saboda murna, ta dinga tsokanar ta da ta kwace mata miji da rana tsaka, murmushi kawai Iman din take, hakan ya janyo suka dade sosai a bangaren har zuwa sanda taji sallamar sa, ta dago suka hada ido sanda yake shigowa ciki, jamfa da wando ne a jikin sa kalar sararin samaniya, ya tsaya iya kar guiwar sa, kansa sanye da hula me kalar duhu, yayi kyau sosai, da sauri ta janye idon ta kunyar abinda ya faru daren jiya na hasko mata, murmushi yayi me kyau ya karaso ya zauna kujerar dake fuskantar ta. Hajja dake nade a saman wani cushion me laushi ta tabe baki tana dubanss "Saboda rashin kunya shine ka biyo bayanta ko?" "Toh ya zanyi? Kin rik'e min ita kin hanata tafiya." "Ah lallai, shine ka biyo baya kazo kaga ni, toh ba zan cinye ta ba ai." "Kai yar tsohuwar nan kin fiye rikici wallahi, kishi ne nasan yake damunki ba wani abu ba." Dariya tayi tace " Ai na bar mata kai tuntuni, kuje ku karata nima Amadu na ya ishen." A tare duk suka yi dariya, ya kashe mata ido daya tayi saurin dauke kai kamar bata ganshi ba. " My wife!" Yayi kiranta a hankali karaf sai a kunnen Hajja, ta banka masa harara ya sosa kai "Dan nema, kin hadu da aiki kinji Fatima, mijin nan naki bashi da kunya sam, bari kiga na tashi, taso yan mata muje na baki wani abu ki bar wadannan." Tashi Amaani tayi tabi Hajjan, suna shigewa yayi saurin komawa kusa da ita. "Ka ganka ko?" "Me nayi?" Ya tsare ta da ido yana marairaice fuska "Gashi nan ka kori Hajja." "Rigimar tace kawai fa, mun saba irin haka da ita." "Toh ka koma chan ka zauna." " Wai kunya ta kike ji? Ko kunyar Hajja?" " Both!" Tace tana kauda kanta Murmushi yayi kawai " Kinsan me? Bubu ya bani kwana hudu na kawo masa gamsasshiyar hujja, idan ban kawo masa ba, zai aura min Laila." Sak tayi, duk da Laila ta riga ta fad'a mata amma ji daga bakin sa ya sakata shiga yanayi, " Karki damu, hakan ba zai faru ba, I promise you that!" " Allah ya bada sa'a." Tace a sanyaye " Zan je Abuja anjima ko gobe da safe zanyi kwana biyu, na dawo" " Tafiyar ba zata bamu matsala ba?" " In sha Allah." " Shikenan, Allah ya kaimu ya dawo da kai lafiya." Tayi shiru tana tunanin yadda zata taimaka masa ta taimaki kanta dan ba zata taba iya zama da Laila ba a yanayin ta. ***Idan tace tayi bacci a ranar tayi karya, tun bayan fitar matar gidan da kawayenta bata sake nutsuwa ba, kuka take tun tana yi da hawaye har ya zama babu hawayen sai suya da zuciyar ta, take kamar zata fito. Da asubar fari taji ana buga kofar dakin amma a hankali, tashi tayi da k'yar tana jin jiri jiri saboda yunwar da ta kwaso ta zare sakatar dakin. Da sauri ya shigo ciki ya maida kofar ya rufe yana kallon ta, matsawa tayi baya tana masa kallon tsana "Karka matso nan wallahi zan iya illataka, ka maida ni gidan mu wallahi ba zan zauna anan ba." "Rage muryar ki dan Allah, kar taji, kiyi hakuri zan yi kokari naga na lallabata ta bar mu, mu koma gidan mu dan wallahi a matse nake, kinsan dai mutum da sabuwar amarya." "Wallahi bazan koma ko wanne gida ba, gidan mu zaka mayar dani ka sake ni kuma, ba zan zauna da kai ba na tsane ka." Saurin damkota yayi, ya toshe mata baki yana hade jikin su waje daya "Idan kina daga murya wallahi zamu dade a haka, idan ta gano na sato hanya nazo ni dake duk ba zamu fita ba, yanzu ki kwantar da hankalin ki, ki bita duk yadda tace zan dinga shigowa nan din da asubah tunda bata tashi da asubah sai gari yayi haske sosai." Fizge kanta tayi tana masa mugun kallo "Na tsane ka, na tsane ka Bashir har bansan iya adadin tsanar da nayi maka ba, Allah ya isa cutar dani da kayi, kasan dama kana da mata amma shine ka auro ni, wallahi sai ka sake ni ko na jawo maka abinda zaka dade kana dana sani." "Baby!" Yaji muryar hajjajun tasa tana k'wala masa kira, jikin sa ne ya hau rawa yayi hanyar fita hankalin sa a tashe,kafin ya karasa ta turo kofar cikin shigar kayan bacci masu shegen kyau, tayi musu wani kallo kafin ta kama hannun sa tana murmushi "Kana nan ashe, toh wuce muje ko?" "Toh;" yace yana yin gaba. "Ke kuma, ki fito ki fara min aiki kafin gari ya gama wayewa, akwai menu na kalolin abincin da nake son gani kullum a saman dining bana kuma so ki wuce karfe goma baki gama komai ba." Ta juya tana karkada mata mazaunanta ta buga kofar. Hawayen bakin ciki ne suka sakko mata, ta share tana shiga dan kurkutaccen bandakin da ke gefen dakin ta dauro alwala da k'yar sboda yadda yake wani shegen wari ta shinfid'a dankwalin ta, tayi sallah akai sannan ta bi ta hanyar zuwa kitchen din dan ta tabbata idan har ta sake muguwar matar ta dawo bata fito ba zata iya nada mata shegen duka babu abinda ya dameta gashi babu me kwatar ta dan shi kansa Bashir din ba abakin komai yake ba.   Menu din ta dauka tana kallo, babu abu daya daga cikin kalolin girke-girken guda biyar da ta iya a ciki, tasan dai tabbas Iman tana yi musu dukka a gida amma ita bata taba ko da sha'awar gwadawa ba, daga indomie sai tea sune kadai take yi, sai yar taliya ko macaroni shima ba kullum ba, duk wani girki me wahala kamar su tuwo da sauran su. *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/1/22, 10:25 - Buhainat: Halin Girma       25 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ***Ta dade a kitchen din tana jujjuya yadda zata yi, gashi lokaci na tafiya dan har kusan bakwai ce zatayi, barin kitchen din tayi ta wuce ta fara gyara falon, duk da ba wani datti da yayi amma sai da ta sake share shi ta bubbuge kujerun ta tattare komai ta ajiye a gefe har da rigar baccin da ta gani a jikinta dazu. Daga nan ta sake komawa kitchen din kawai ta yanke shawarar tayi abinda zata iya, ta dauki indomie ta dafa da egg sannan ta dafa ruwan tea ta jera musu akan dinning din ta wuce dakin da yake a mazaunin nata da tunanin yadda zata samu waya ta kira gida, ko kuma ta samu hanyar da zata bar gidan dan bata ga alamar Bashir zai kyaleta ta sauki ba.   Tana zaune tana sak'awa da warwarewa aka turo wata yarinya kiranta, kamar ba zata tashi ba, sai kuma ta mike tabi bayanta tana taraddadin abinda zata tarar. Matan jiya ne jere akan dinning din, sai uwar gayyar daga gefe ta hade rai sosai tana mata mugun kallo, tun kafin ta karaso ciki ta hau surfa mata ashar "Saboda tsabar ke yar iska ce, abinda nace ki dafa daban abinda kika dafa daban ko? Zo nan." Kin zuwa tayi, ta k'ame a wajen tana kallon su "Ji yadda ta tsare mu da ido Hajiya Lay, amma dai yarinyar nan bata da kunya." "Ku barta, bata san wacece Layuza ba, zan koya mata hankali." Bud'e baki Zeenat din tayi, tace. "Ke nake aure ne wai ko shi?" "Kutmelec! Ni kike wa wannan tambayar?" "Toh ai naga dai iyaye na Bashir suka aura min ko? Me yasa kike nuna kamar ni din me aiki ce a gareki, ni bansan ki ba, bansan wacece ke ba kawai zaki dinga nuna iko akaina " "Lallai yarinya, kinyi babban kuskure da har zan fad'a ki mayar, toh dake da Bashir din duk a karkashi na kuke, kuma baki isa ki hada miji dani ba wallahi, kinyi kad'an ace kece kishiyata, dan haka yanzu baki da maraba da me aiki a gidan na, kuma dan ubanki dole kiyi duk abinda nace, na samu labarin komai da yadda auren ya kasance, shegen kwadayi da son zuciyar uwarki dake ya jawo miki, dan haka ki wuce ki yi abinda na saki kafin na taso na yi miki mugun dukan da zaki kasa tashi wallahi." " Ai da kawai daidaita mata shegen bakin nan nata akayi gobe ba zata sake fad'a ki fad'a ba." " Barta, zata gane kurenta." Zumburo baki tayi, ta ki barin wajen ita a lallai basu isa ba, ganin haka ya saka Hajiya Layuza tasowa aikuwa tana ganin haka ta kwasa da gudu bata tsaya ba sai data kai dakin tayi saurin saka sakata tana maida numfashi. ***Tagumi Mama ta rafka, duniyar gaba daya ta daina mata dadi tun bayan da ta tabbatar da babu wani abu da zata iya dan Abba sai da ya sake jaddada mata akan duk wani abu da ya samu auren Zeenat toh ta tabbatar da mutuwar nata auren, ada taso suyi duk wacce zasuyi amma daga baya sai tayi wa kanta fad'a ta hakura ta zuba wa sarautar Allah ido, gashi ta kikkira wayar Zeenat din amma ko da yaushe bata shiga, takanas ta tura Habib ya je har kofar gidan amma sai ya tarar a rufe, abinda ya kara daga mata hankali kenan, ta saka Abba a gaba tana kuka dole ya dauki waya ya kira Bashir din, ya kuma yi mata handsfree dan taji. Maganar an je an ga gidan a rufe Abban yayi masa nan ya shaida masa ai suna family house dinsu sai sun danyi kwanaki zasu dawo gida haka al'adar gidan su take, addua Abban yayi musu daga nan ya kashe yana kallon Maman da tayi tsuru tana ji har suka gama. "Kin dai ji ko? Ko kuma address din gidan nasu zan baki?" "A ah." Tace a sanyaye tana mikewa. Cigaba da aikin gabansa yayi dan be ga dalilin da zai saka ta tada hankalin ta ba, bayan sun riga sun aurawa Bashir din basu da ikon bibiyar in da duk zai kaita. ***Zuwa yamma masarautar ta cika sosai, duk wanda Ammi ta gayyato sun hallara, yan mata ne kyawawa masu aji suka fi yawa sai manya tsirari wanda Ammi ta barsu sai ranar nadin dan kar ya zama an takure mutum, Ba'a dau lokaci aka shiga gabatar abinda ya tara su, saboda a ranar su Mamma suke so su wuce. Tsarin daban ne da duk wani taro da akayi na bikin, Muhammad da be niyyar attending ba, amma ganin abinda ya faru ya sakashi shiryawa cikin shigar da yasan zai burge Iman dinshi, wanda be san iya adadin yan matan da suka sake faller masa ba a ranar. Yana zaune kusa da ita daf ya dan karkace yana fuskantar ta, yana mata magana k'asa-kasa, tana jin sa sarai amma ta fuske dan ta gama gane shi so yake suyi abin da zata sha kunya dan taga kamar shi be san kunya ba sam. Daga nesa ba zaka gane yanayin da suke ciki ba, zaka dauka yanayin zaman nasa na mulki ne, sai ka matso sosai zaka gane kan abun. Shigar da Laila tayi a wajen ta kusan fin ta Iman din, babu laifi Allah ya hore mata kyau ba kad'an ba, dan sanda ta shigo wajen sai da gaban Iman ya fadi ganin uwar kwalliyar da taci kamar wata dawisu, kai tsaye wajensu ta nufo tana tafiya tana karkada kowanne lungu da sako na jikin ta, kamar bishiyar da iskar rani ke kadawa haka ta dinga karkada jikin ta har ta karaso wajen fuskar ta a washe ta matsa daidai saitin Capt Muhammad ta rankwafo tana nunawa camera man sign din ya dauke su.   Da ido Muhammad yayi masa alamar idan ya dauki hoton sai dai wani bashi ba, sum-sum ya bar wajen hakan ya bata wa Laila rai tace "Capt wanne irin wulakanci ne wannan?" "Baby kinga waccar da ta shigo yanzu?" Yayi kamar be ji ba, ya matsa jikin Iman din yana nuna mata wata, "Kanwar Ammi ce, itace Aunty Fatima." "Ok wadda ka bani labarin ta ko!?" "Yea ita." "Allah sarki, she's nice." "Sosai." Sai ya sake kai fuskar sa jikin ta sosai "Baby perf din nan akwai kamshi, i just love it, yayi dadi." "Thanks dear." Tace tana smiling Bakin ciki ne ya tuke Laila, tayi saurin barin wajen kafin zuciyar ta, ta buga. Tana barin wajen sukayi wa juna murmushi. A gajiye suka koma cikin gidan bayan an gama taron, su Mamma sun jima da tafiya dan haka part din Ammi aka maida ita, daga nan Ammi ta saka mutane da yawa suka yi mata rakiya zuwa nata part din da ta riga ta tare tun a jiya ba tare da Ammin ta sani ba, sai gobe za'a rakata wajen Bubu idan ta huta shi ma baya nan yau sai goben zai dawo.    Masu kula da bangaren da duk wani abu da ya shafe ta Ammi ta nuna mata, suna isa kuwa suka shigar da kayan su dakunan su dake bayan part din suka shigo suka fara aikin gyara shashen, suka gama suka saka masa turaren wuta sannan aka jere musu abinciccika masu rai da lafiya. Sai da suka tabbatar babu wani abu da zata bukata sannan sukayi mata sallama suka tafi.    A gajiye take sosai amma kuma dole tayi wanka dan sosai Mamma ta jaddada mata muhimmanci wanka da gyara jiki, cire kayan jikin ta tayi, ta zari towel daya ta daura ta nufi toilet din, wanka tayi ta hado da alwala ta fito tana sharce kanta. Wayarta ce tayi kara ta dauka tana dubawa, Mommy ce ke kiranta, tunda aka fara bikin basuyi magana ba, sai dai ta jisu da Mamma suna yi, zama tayi tana daga wayar dadi na cikata "Mummy barka da dare." "Iman... Kuna lafiya?" "Lafiya lou mummy, dama yanzu nake so nazo na kira." "Ko? Toh gashi na kira ni ai, ya sabon waje?" "Alhamdulillah." "Mamma ta sanar dani duk yadda abubuwan suka kasance, nasan kuma duk abinda ya kamata ki sani ta sanar dake, dan haka ita rayuwar aure yar hakuri ce, sannan duba da irin gidan da kika samu kanki, sai kinyi hakuri kin kuma zama me lura sosai." "In Sha Allah mummy." "Yawwa, ki kula sosai da mijinki da duk abinda kika san yana so, karki ga tarin ma'aikata ki sakar musu kula da mijinki, duk wani abu da ya danganci mijinki ki taske kiyi shine hanyar samun ladan ki, kuma hanyar aljannar ki." " In Sha Allah Mummy, nagode sosai." "Ki ajiye kunya ki kula da mijinki sosai, banda sanyin jiki da lalaci." A kunyace tace "Toh mummy." Turo kofar akayi, yana sanye da 3quarter wando babu riga a jikin sa, saurin dauke kanta tayi tana amsawa mummy bayanin da tayi mata akan wasu magunguna da ta saka mata a bag dinta. Gabanta yazo ya tsaya k'yam yana karewa cinyoyin ta dake bayyane saboda kankantar towel din. Tsugunawa yayi a gabanta ya saka hannu ya shafa saman cinyar ta ta, tayi saurin janye su tana jan numfashi, "Kina ji na Iman?" Mummy tace jin kamar attention dinta ya tafi wani wajen. "Am.. am ina ji Mummy." Ta amsa a firgice ganin ya kai hannu jikin towel din ya janye, da sauri ta saki wayar bayan ta danne power button din, ta mike tana rik'e towel din. Idonsa a shanye yake kallon ta "Zanyi wanka." Yace yana shigar da idonsa cikin nata, kasa matsawa tayi daga wajen, sai jan towel din take a dole sai ya sauka ya rufe bayanta. Bata taba jawowa zai shigo a lokacin ba, ta yi tunanin ma ya tafi, sai ganin shi tayi. Dariya ta bashi,yadda ta hakikance a dole sai ta saukar da towel din. "Zanyi wanka." Ya sake maimaitawa yana folding hannun sa, kamar ta dora hannu a ka tayi ta kurma ihu ta shiga takawa zuwa toilet din tana cigaba da jan towel din. Ji tayi an rungume ta, ta baya ya dora kansa a saman kafadarta. "Me kunya, kunyar me kike ji?" "Ba komai." "Shine kike ta jan towel din bayan halal dina ne, sai a barni na more kallon kayana ko?" "Uhum". " Emana. " Ya sake tura kansa wuyan nata sosai,yana jujjuya kan, hakan ya haifar mata da kasala, ta dinga kokarin zamewa amma ya hanata, a dole ta kyaleshi yayi budurin sa. Sai da ya tabbatar da tayi laushi sosai sannan ya jata zuwa toilet din. Mamakin rashin kunyar sa take, shi ko a jikin sa babu abinda ya dame shi, ita kuwa kamar ta shide idan ta kalleshi a hakan sa, da k'yar ta samu ya barta bayan ya kara tattabe ta, ta samu ta fito ta barshi a ciki, a gurguje ta shirya ta saka kaya ta tada sallah ko da ya fito tana sallah sai kawai ya shirya shima ya fita falo dan cikin sa ya fara kiran yunwa. Zaman jiranta ya dinga yi jin shiru bata fito ba ya leko ya kirata, dan baya so a kara kwana be bata labarin komai ba, a kalla hakan zai saka ta sake yarda dashi ta kuma taimaka masa dan ita kadai ce ta fara ganin Laila sanda ta shigo part din. Tsattsakurar abincin tayi tace ta goshi dan da gaske tsoro take ji, tsoron kar yace zai sake yi mata irin abinda yayi mata jiya, ba zata iya dauka ba, shiyasa tana gama ci ta sulale ta gudu ta kwanta ta kudundune a dole tayi bacci. Sai da ya gama komai sannan ya biyo ta dakin ya yaye abinda ta rufan yana shigewa jikinta. *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/2/22, 18:24 - Buhainat: Halin Girma       27 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ******* ? Matsowa Limamin yayi ya zauna, sai wambai da zai karbi auren shima ya matso zuciyar sa fes shirin su ya tafi yadda ya kamata. Dakatar da su Aji yayi, ya bada umarnin a fara gabatar da nadin sarautar kafin daurin auren ya biyo baya, babu wanda yayi magana dan babu me ja dashi, sai dai kuma sam manyan fadar sun ki amincewa da nad'in Muhammad saboda abinda ya faru, Bubu na zaune be tanka ba, suka shiga tattaunawar gaggwawa in da kaso saba'in cikin dari suka amince da nad'in Kamal, sai kaso talatin suka nun Muhamamad din, idan aka samu irin haka toh dole ne a dauki ra'ayin bangare mafi rinjaye, a take aka gabatar da Kamal a gaban fadar, aka kuma shiga yi masa nad'in cikin yanayin da ya saka Bubu a matukar tashin hankali, be gamsu da karbar mulkin Kamal din ba dan akwai gyara sosai a rayuwar sa, ganin da gaske idan yayi wasa komai na masarautar sai ya rushe, sai kawai ya dakatar dasu. Duk kowa yayi zuru yana jiran bayanin sa, be san me zaice ba, duk kuwa dashi ne shugaba amma kuma idan har aka zauna tsakanin manyan fadar aka zartar da hukunci toh shi ma dole ne yabi. Shiru ne ya biyo bayan dakatarwar da Bubun yayi, kowa na jira yaji abinda zai sanar.    Magatakarda ne ya shigo, ya fadi yayi gaisuwa sannan ya mik'a sakon rubucacciyar wasika daga fadar kwamnatin adamawa akan sabuwar dokar da aka zartar a daren jiya, aka kuma kayyade shekarun da ake so duk wani sarki ya cika su kafin zamtowar sa sarki, ajiyar Zuciya Bubu ya sauke ganin ko kusa da shekarun Kamal be kai ba. A karshe kuma gwamnati ta jaddada lallai Sarki Ahmad Santuraki ya cigaba da zama akan kujerar sa kafin a samu wanda zai gaje shi da irin shekarun da yake a rubuce, da kuma cika duk sharadin da aka gindaya.   Hayaniya ce ta dauka a cikin fadar, masu kushe abun nayi masu nuna farin cikin su nayi, shi dai Bubu sai yayi shiru yana duban kowa, sai a lokacin ya kara tabbatar da masu son sa tsakani da Allah a cikin manyan masarautar da kuma wadanda da gaske suke son ganin bayan sa.    Sai da kurar ta lafa, kowa yayi shiru bisa umarnin Sarki Ahmad din, dan gani yayi abun nasu na neman ya zarme shi kuma bashi da katabus akan dokar da taxo a rubuce daga gwamnati wadda take da dama da ikon sakawa ko sauke duk wani Sarki. Jawabi ya soma yi cikin son ganin ya kwantar da hankalin kowa, da kuma kokarin nuna bashi da masaniyar komai akan sakon gwamna, duk da dole ne sanar da gwamnati kafin dora sabon sarki kuma sunyi hakan amma be san ainhin dalilin gwamnati na fito da wannan dokar ba.   Shigowa Muhammad yayi, ya samu gefe ya zauna suka hada ido da Bubu yayi masa murmushi yana tuna haduwar sa da gwamna a daren shekaranjia, ya kuma je masa da bukatar sa ta son sauya baki daya dokar, ya bashi kwararan hujjoji masu gamsarwa wanda dama chan mutumin sa ne tun kafin zamowar sa gwamna, babu abinda Muhammad din zai nema be masa ba in dai be saba ka'ida da doka ba.    Babu wanda yasan da wannan shirin nashi, babu kuma wanda yayi tunanin hakan zata kasance, makasudin tafiyar tasa kenan da be shirya karbar mulkin ba, ba zai kuma bari Kamal ya samu ba, yana da bukatar morewa rayuwar sa da Fatiman sa, idan har ya sake ya karbi mulki toh dole akwai abubuwa da yawa da be isa yayi wa kansa ba, ko ita.    Bayan gama bayanin Bubu ne, kowa yai shiru masu tattaunawa da zuciyar su nayi, masu tunanin mafita nayi amma kuma babu me sake furta komai dan an gama maganar sai kuma wani lokaci idan me dukka ya kaimu.   Liman ne ya sake dawowa gaba, domin gabatar da daurin auren tunda an gama da wanchan babin, wambai da fuskar sa ta kasa boye damuwa da bacin ransa ya matso bayan yayi wa Muhammad din wani kallo da shi kadai ya san dalilin sa.    Kamar yadda addini ya koyar, ana aure ne bisa doran abubuwa guda uku, sadaki, siga da kuma shaidu, wanda duk sun hallara a wajen, liman ni ya soma magana da gabatar da abinda ya tara su, kafin ya kai karshe Muhammad ya katse shi, ya taso daga wajen da yake zaune ya iso gaban su ya durkusa, ya mikawa wambai wayar sa yana komawa ya zauna daga gefen wamban bayan ya tankwashe kafar sa, idon sa fes akan wamban yana karanta yanayin fuskar sa. Da farko tsayawa wamban yayi chak da kallon video din, sai kuma ya saki wayar ta fad'a saman cinyar sa jikin sa a mace ransa y kai kololuwar baci.   Hannu Muhammad ya saka ya dauke wayar sa,ya mikawa Malam Liman ya kunna video ya kuma karo volume din sosai yadda duk wanda yake kusa da wajen zaiji. Muryar Laila ce take magana ita da baiwar nan tata, a daren da za'a kawo Iman, a lokaci da suke maganar turaren, tun daga farkon hirar su har karshen ta. A fuskar Bubu zaka hangi tsantsar farin ciki, amma kuma rawanin kansa ya boye, sai ta kwayar idon sa kadai zaka gane, be ce komai ba dan dama ba zai ce ba.    Karbar wayar Muhammad yayi, ya mikawa sauran dake wajen suma suka kalla, sannan ya kunna na karshe wanda yake nuna Laila sanda take shiga part dinsa, bayan ta bawa masu tsaron kofar wani abu a cikin envelope, wannan kadai ya isa hujja, hujja me karfi.    Girgiza kai kawai Aji yake, dama yasan gaskiya zatayi halin ta. Laila da Muhammad duk su din nasa ne kuma yana kaunar su amma kuma ba zai taba goyon bayan karya ba.    Wata hayaniyar ce ta sake kaurewa, aka hau Allah wadai da hali irin na Laila, kuma ko babu hujjar nan Laila Itace mara gaskiya, babu yadda za'a yi idan har cutar da ita Muhammad din yayi a sameta a bangaren shi, idan har hakan ce ta kasance toh lallai shi za'a samu a nata bangaren amma sai aka samu akasin haka.   Aikawa Bubu yayi aka taho da baiwar nan, hade da masu tsaron shashen muhammad din, tun kafin aiken ya je sun samu labari, sun shiga matukar tashin hankali dan basu yi tunanin za'a gane gaskiya adan kankanin lokaci haka ba, basu san cewa duk wanda yace Allah, toh ya gama komai. Jifa tayi da dankwalin kanta da shahararriyar me kwalliya da ta taho kafa da kafa tun daga Abuja tazo ta tsara mata shi, ihu ta saki ta hau jifa da kayan dake saman dressing mirror dinta, ta riga ta gama duk wani shirin ta, ya akayi haka ta kasance? Wacce irin sa'a ce da yarinyar da har komai zai kasa tasiri akanta? Me take takama dashi? Me take ji dashi? Kanta ta hau bubbugawa a jikin bangon kafin ta fashe ta kuka, ba zata dauka ba, bata san ya zata iya rayuwa babu shi ba, bata sani ba.    Aikowa Bubu yayi a tafi da ita, lokacin Kilishi na wajenta, tana bata baki, bata san me zata ji ba, da fasa nad'in Kamal din ko da abin kunyar da Iman din ta jawo musu? Kamar mahaukaciya haka ta nufi bangaren Bubun. Shi kadai ne a turakar sa, bayan an tashi daga zaman ne ya dawo gida dan yana so ya huta, tension din da ya shiga a kwana biyun nan ba kad'an bane shiyasa yace babu zaman fad'a har sai bayan kwana biyu idan ya huta sosai, be ga muhammad ba tun bayan an tashi daga zaman, bayan ya saka an aika da bayin nan gidan gyaran hali sai kawai ya zarto nan ya kuma bada umarnin a kawo masa Lailan, sai gashi sun shigo ita da mahaifiyar ta, kan Lailan tsaya ta shigo sai dai kamar wadda aka bubbugewa guiwa haka ta koma, kwarjinin Bubun ya sakata shiga hankalin ta, fuskar sa a daure take tamau babu ko digon fara'a hakan ya sakata shan jinin jikinta, dan bata taba ganin sa a haka ba, sosai yake sakewa da ita har suyi hira, yana son ta sosai tamkar shine ya haife ta,sai gashi yau ta kasa kwakkwaran tsaiwa a gaban sa, ta makale daga gefen wata kujera tana leken fuskar sa.   Be bi ta kan Kilishi ba, dan ba ta ita yake ba, ya kira sunan Lailan da kausashshiyar murya, bata iya amsawa ba, sai matsowa da tayi da jan kafa ta gurfana agaban sa.    Sanarwar shigowar Muhammad ta dakatar da maganar da Bubun yayi niyyar yi, ya shigo kansa tsaye zuciyar sa fes ko babu komai yasan ya wanku tas a wajen Bubu, dama kuma babban tashin hankalin sa ace Bubun na fushi dashi.   Ganin su ya saka shi juyawa, amma sai Bubun ya dakatar dashi, ya dawo ya zauna a gefe yana jin kamar dakin yayi musu kad'an, kamar idan ya cigaba da zama yana shakar iska daya da Laila zai iya nakasta ta. Ammi ce ta shigo tare da Iman tana bin ta a baya, fuskar Ammi fes ba zaka taba gane halin da take ciki ba, daidai saitin kafarta Iman ta zauna kanta a k'asa sosai kwarjinin Bubun ya cika ko ina na dakin, ganin su ya saka muhammad din sakin ransa, ya dinga satar kallon Iman din cikin so da kauna.   Gyaran murya Bubu yayi, ya shiga bayani da harshen da yake tunanin duk zasu fuskanta, muryar sa na fitar da amo me tsoratarwa, babu wasa ko digo a cikin maganar sa, ta in da yake shiga bata nan yake fita ba, yayi wa Lailan tas, ya kuma tabbatar mata da sai ta karbi hukunci daidai da abinda ta aikata, gaba babu wanda zai yi sha'awar aikata irin abinda ta aikata, karshe kuma yace y haramta mata karatun nata baki daya, ta dawo gida kenan ba zata koma ba, tunda babu abinda ta sake daukowa sai mugun hali.   Ko gezau batayi ba, dama kuma babu wanda ya saka ran zata girgiza ko ta tsorata, kanta dai yana k'asa dan bata isa ta hada ido da Bubun ba, amma tana zaune kekam har ya gama ya kuma juya kan Muhammad da Iman ya sake basu hakuri musamman Iman da ta shigo gidan ta kuma fara da karo da irin wannan abun, kachokam ya dora laifin Lailan a akansa, ya sallame su ya zama daga shi sai Kilishi.   Gaba Ammi tayi zuwa bangaren ta, tare da Iman dan bata bukatar sake jin komai hakan ma ya isa, Allah ya kawo komai cikin sauki, ba zata kuma bata lokaci a abinda ya riga ya wuce ba, shi dama sharri dan aike ne, duk in da yaje sai ya dawo.    Sauri-sauri yake ya isa gida a tunanin sa Iman chan tayi, ya matso yaji yadda akayi ta samu evidence din, a lokacin da ya riga ya cire rai, tsaida shi Laila tayi, ya tsaya yana juyowa, "Ni ka wulakanta ko cap..." Ai bata kai karshen maganar ta ba, ya dauke ta da wani gigitaccen mari, marin da ya dauke mata ji da gani na wani lokaci "Ni ka mara?" "Shine kawai abinda nake ganin zan miki na huce, duk da addinin musulunci ya hane mu da dukan mace, musamman ma a fuska, amma bani da zabi, nayi duk kokarin da zanyi nayi avoiding dinki, amma saboda ke jaka ce sai da kika saka ni aikata abinda nake gudu, idan kika cigaba da shiga rayuwata ko? Wallahi sai na miki abinda baki taba tunani ba." Hannun ta dafe da fuskar ta, ta kasa cewa komai har ya juya da nufin barin wajen, cikin daga murya yadda zai ji tace "Sai dai idan kashe ni zakayi, amma nayi maka alkawarin sai ka aure ni, ko kana so ko baka so!" Be tsaya ba, dan bashi da lokacin batawa, yana kyautata zaton Laila ta haukace, ko kuma tana shaye-shayen kayan maye, idan ya biye ta zai iya mata illa, dan yadda yake ji kamar ya saka hannu ya shake mata wuya har sai ta bar numfashi.   Sababbin masu kula da kofar ya tarar, suka gaishe shi ya amsa musu da kai, har ya wuce ya dawo ya nuna su da yatsa "Idan har na samu wani abu daga gareku, wallahi tallahi sai kun yabawa aya zakinta." Ya wuce su yana juyo su suna bashi hakuri da alkawarin ba zasuyi komai ba, kofar ya buga da karfi, ba zai cigaba da zama a cikin gidan nan ba, idan ma ya zauna toh fa ba zai iya da tsarin su ba, tafiyar sa zai wata k'asar ya huta sosai, ko da zai dawo amma sai ya tabbatar da ya samu enough time da matar shi, ba zai yiwu wasu banzaye su nemi hana shi morewa ba,daga yin auren sa.   Abincin dake saman dinning ya kalla, ya wuce ya hau bubuda dakunan yana neman ta, bata cikin ko daya, ya dudduba toilets nan ma bata nan, ya zata nan zata wuto be yi tunanin Ammi zata bi ba.   Dawowa yayi falon ya kwanta rigingine ya rage volume din tv ya rufe idon sa. Bacci ne ya soma daukar sa, yaji kamar ana taba shi, bud'e idon yayi ya ganta a tsaye a wajen kafar sa, kallon kayan jikinta yayi daga sama har kasa, doguwar rigar material ce me budadden hannu, sai kanta dake rufe da inner cap, murmushi tayi masa ya mayar mata yana mika mata hannu ta daga shi, make kafada tayi alamun a ah, ya sake mika mata ta noke, marairaice mata yayi yana sake mika mata hannun, karba tayi da nufin dagashi amma sai ya saka karfi ya jawo ta, ta fado kansa ya saka hannu ya zagayeta a jikinsa. "Dama na san haka zakayi, shiyasa naki." "Toh laifi nayi? Mutum da iyalin sa halaliyar sa." "Zuhr ake kira toh ai." "Don't tell me azahar tayi." "Tayi, har ma nayi sallah ta." "Ohh... Ya Salam rayuwar nan tana gudu." "Wallahi, tashi toh kayi sallah." Tace tana kokarin daga shi, maida ita yayi yace "Zan tashi, amma sai kin min tausa, I'm weak kwana biyu ban fita exercise ba." Gefen kadarsa ta danna masa, zuwa saman chest dinshi "Gashi nan na gama." "Ojoro, wannan ai ba tausa bane, danna ne." Dariya ta saka "Menene banbancin?" "Tausa daban danna daban, ji fa yadda kika danna min kafada kamar wani katako." Dariya ta kwashe da ita sosai, irin wacce be taba ganin tayi ba, tsayawa yayi yana kallon ta yana admiring dinta, komai idan tayi burgeshi yake sosai, sai da ta lafa sannan ta ga irin kallon da yake mata sai kuma taji kunya, ta dora fuskar ta a saman kirjinshi tana dannawa. "Sarkin kunya." Ya mike yana dagata, zama sukayi akan kujerar ya rik'e hannun ta cikin nashi "Thank you so much, kin taimaki mijinki a lokacin da yake cikin tsananin bukatar taimako, dama mace ta gari itace me taimakon mijinta idan ya shiga matsala, I'm very proud of you, bari nayi sallah nazo ki bani labarin yadda akayi, I hope baki saka kanki a matsala ba ko?" Girgiza masa kai tayi " Ko daya, kayi sallah ga abinci na shirya mana da kaina" "Really? Kece kika girka?" " Nice." Tayi folding hannunwanta a kirjinta tana murmushi "well-done, hakan yayi min dadi, bari na zo naci girkin amarya ta." Dariya tayi ya shige ciki ita kuma ta zauna tana jin dadi sosai. ***Cikin dare ya tashi, ya kalli Hajiya Layuza dake shirge kamar kayan wanki, bayan ta hanashi sakat da zalamar sa ya samu ya bata maganin bacci shine tayi bacci, sadaf-sadaf ya sulale ya fice yana kallon hanya sai dakin da Zeenat take. Tura kofar yayi yaji ta a rufe, ya shiga kwankwasawa a hankali kamar barawo, cikin baccin wahala Zeenat din ta farka taji kamar ana taba kofar, tsoro ne ya kamata ta, ta makale a wajen daya tana zaro ido, " Zeenat kina ji? Bashir ne dan Allah bud'e min. " " Ba.. bazan bude ba." Tace tana sake makalewa a jikin ginin dakin " Dan Allah ki cece ni, ki bud'e muyi magana akan tafiyar ki gida, na samo hanyar da zaki koma gida cikin ruwan sanyi, dama naji an ce an janye yajin aikin da jami'oi suke, bud'e kiji." " Da gaske kake? " " Da gaske nake, bud'e dan Allah kafin ta gane bana nan ta biyo ni tazo ta tafi dani. " Tashi tayi ta bud'e kofar, tana gama budewa ya fado daga shi sai gajeren wando, wani iri taji tayi saurin dauke kanta, kamar wanda yasha wani abu kawai taga mutum yayo kanta, ya dakume ta yana kokarin rabata da kayan jikin ta, dukan sa ta shiga yi amma kamar ingiza shi take, toshe mata baki yayi sosai ta hanyar saka abu ya daure bakin yadda ihun da zatayi ba zai fito ba. Duk yadda tayi kokarin ganin ta hana shi amma sam be hanu ba, sai da ya karbi sadakin sa, ya kyaleta yana maida numfashi, kamar wanda yayi tsere da zaki. Bayan kamar minti goma ya tashi da sauri ya fice daga dakin ba tare da ya kalli in da take ba.    Tun tana kuka har ta daina ta galabaita sosai, ko hannun ta bata iya dagawa balle tayi wani kwakkwaran motsi ko ina na jikinta ciwo yake balle uwa uba chan kasanta da take jin kamar zata mutu dan tsabar azabar da take ji _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/2/22, 18:35 - Buhainat: Halin Girma       26 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ******* ? Sai da ya gama komai sannan ya biyo ta dakin ya yaye abinda ta rufan yana shigewa jikinta "Kinyi bacci?" Yace yana leka ta kin motsi tayi a dole tayi bacci, fuskar sa ya matsar jikin ta ta, ya taba saman idon ta, motsi yaji idon nayi yayi dariya yana cewa "Stop pretending ki tashi, nasan ba bacci kike ba." "Uhum..." "Yawwa, hira zamuyi, zaki iya tambaya ta koma menene akai na, zan sanar dake." _"Farko  dai sunana Muhammad Ahmad Santuraki, kamar yadda kika gani, mahaifi na shine sarkin Adamawa, sannan Mahaifin Ammi shine sarkin Kano, na taso tsakanin Kano da adamawa in da zama na yafi yawa a Kano saboda yadda Maimartaba ya kwallafa rai a akai na. Nayi karatu na both na addini dana boko har na kai matakin captain a yanzu a bangaren aikin soja. Ni kadai Ammi da Bubu suka haifa,bani ne dansu na farko ba, kuma bani ne na karshe ba amma ni kadai ne Allah ya raya musu. Aji shine Mahaifin Bubu da sauran yan uwansa su hudu, shine na biyu akwai babban wansa wanda Allah yayi masa rasuwa, shine Mahaifin Laila da Kamal, bayan rasuwar sa ne Bubu ya auri matar wan nasa wadda ake kira da Kilishi,a lokacin kuma rikon su ya dawo hannun Bubu tunda dama chan gida daya muke baki daya. Daga nan ne kuma Aji ya sauka ya nada Bubu domin ya huta shima. Tun farkon dawowar Kilishi gidan mu, daidai da sakan daya bata taba kauna ta ba, infact idan za'a bata wuka ace wa zata kashe toh tabbas ni zata kashe, bata kaunata ko kad'an duk akan sarautar da take ganin Kamal dinta ne yafi dacewa ya karbi kujerar tunda Mahaifin su shine gaba da Bubu. Tun da na taso bani da ra'ayin sarauta ko kad'an, mutane da yawa na min kallon wanda be san abinda yake ba,. abubuwa da yawa sun faru wanda ni kadai na san su, wanda suka kara taimakawa sosai wajen ganin ban karbi tayin bubu ba, tsawon lokaci ya dauka yana bibiyata da maganar amma sam ban taba nuna masa zan iya ba, illa iyaka sai ma na nisanta kaina da duk wani abu da ya shafi gidan da sarautar baki daya. Wannan dalilin shine ya saka ni zama lafiya har wannan lokacin. Akwai abubuwa da yawa na ban mamaki a gida irin na sarauta, wanda sai wanda yake cikin ta ne kawai zai iya ganewa, babban kalubale shine tsantsar makirci da nake kyautata zaton dashi ake haifar da yawa yawan yayan sarauta. Amma duk da haka akwai mutane na gari a ciki wanda basu da matsala ko kad'an sai abinda ba za'a rasa ba." Shiru yayi kamar me nazari, kafin daga bisani yace " Laila ta jima tana so na, tun bayan da ta taso ta san menene soyayya ta kwallafa rai akaina, sai dai nayi ma kaina alkawarin ba zan auri jinin saurata ba, sannan ba zan iya auren mace me irin halin Laila na rashin sanin darajar hatta mahaifiyar da ta kawo ta duniya, a sangarce ta tashi ganin duk wani abu na duniya ta same shi, kyau kudi mulki sannan uwa uba gata, sai ya zama na bata san komai ba sai kanta, bata son talaka da duk wani da zai rabe ta, she's very selfish, mutum ce ita da zata iya komai dan ganin ta samu muradin ranta. Mafiya yawan lokuta takan aika min da sakonni, na kyaututtuka ko wani abu, amma ban taba nuna na gane me take nufi ba, har tazo ta tarkata ta bar k'asar don karatun ta na Masters, hakan ya saka ni samun sauki, sai gashi ta dawo a lokacin da maganar auren na ta kai mata, bansan da wanne shiri ta dawo ba, amma nasan ba zata hakura ba." " Humm..." Taja numfashi tana jin shi, kanta a saman chest dinshi yana wasa da gashin kanta, dagota yayi, suka kalli juna, "Nayi alkawari zan kula dake da dukkan karfina, gatan da kika rasa zaki same shi yanzu har sai kin ce na gaji Muhammad dina." Ya karashe cikin kwaikwayon muryarta, dariya tayi tana dora fuskar ta a saman tasa. "Baka fad'a min dalilin da ya saka ka boye identity dinka ba." "Saboda step mom dinki ne, na samu labarin komai ta wajen Sadeeq abokin yayanki Habib, shiyasa na zo a haka dan na tabbata ba zata taba hutawa ba har sai ta tabbatar da auren mu, wanda na tabbata da nazo a ainihin identity dina da ba lallai ta bari ba." " Haka ne." Tace a sanyaye cikin son kauda tunanin Maman da zaman da sukayi. " Na tambaye ki..." " Ummm." Ta daga mishi Kai " Did you love me?" Da sauri ta kalle shi " I'm serious, inaso na sani, ko tausayi na baki kika taimaka min kika aure ni!" " Inji wa?" " In jini, haka nake gani, tunda ni banga wata alama ba, baki taba furta min ba, ni kadai nake kida na nake rawata." Sauka tayi daga jikin shi, ta kwanta tana juya bayanta. " Ni dai goodnight bacci yazo." Da sauri ya jiyota " Ai baki isa ba, sai kin fad'a min." Sake juyawa tayi tana jan duvet ta rufe kanta, ya shiga ja tana ja, ganin zata bashi wahala ya saka shi dagata gaba daya, ya mike da ita a jikin shi zuwa doguwar sofa din dake chan gefe a dakin, zaunar da ita yayi akan cinyar sa ya warware duvet din daga jikin ta, yunkurawa tayi zata gudu ya riko waist dinta ya dawo da ita. "Sai kin fad'a min, ko kuma na miki irin abun jiya." "Na shiga uku." Danne dariyar sa yayi ganin yadda ta firgice "Allah kuwa da gaske, tell me you love me or else..." Ya rad'a mata a kunne "Me zance toh?" "Abinda nayi ta ce miki, I love you Zahraah, Iman, Fatima, Baby, sweetheart duk dai." "Ni dai... Ni bansan me.zance na." "Kice I love you baby, ki hada da hot kiss a nan." Ya turo bakin sa gaba, hannun ta tasa akan bakin ya dan cije ta, tayi saurin janye hannun ya maida shi baya. "Oya ina jinki, say it, inaso naji muryar ki tana fad'a " Shiru tayi kunya na kamata, kunyar sa take ji sosai ta yaya zata fara furta masa wani I love you right in front of him, ai da kunya tunda ba sabawa tayi ba, gashi har da wani hot kiss shi ko kunyar nan ma babu. Rufe idonsa yayi ya sake turo mata fuskar tasa " I'm all ears." Minti kad'an yaji shiru ya bud'e idon, lokacin har sun sauya zuwa wani abu daban, saurin dauke kanta tayi tana turo baki. Kamar daga sama taji hannun sa a cikin rigarta, ta juyo da sauri tana rik'e hannun " Dan Allah tsaya zan fada, wallahi zan fad'a." " Oya ina ji, don't waste my time." " I lo...ve... You." Tace a rarrabe " Ban yarda ba, ki fad'a kai tsaye daga chan k'asan zuciyar ki, in a romantic way., Kice I love you Muhammad. " " I love you Muhammad. " Tace da sauri kamar wadda tayi gudu ko tsere.  Murmushi yayi mata ganin yadda ta fitar da maganar, yana son komai nata, har kunyar ma, ya san in dai suna tare toh har wanka ma sai ta yi masa wataran, zai koya mata komai, yadda yasan yana so rayuwar auren su ta kasance.   Zaka rantse wani babban laifin ta aikata ganin yadda take jujjuyar da fuskar ta gefe, zaunar da ita yayi ya fita, tashi tayi da sauri ta haye gadon ta kwanta, shigowa yayi dauke da cups akan tray da vacuum flasks dake dauke da black tea, dorawa yayi akan table ya zuba ya mika mata, sannan ya zauna a gaban table din ya shiga kurbar nasa da zafin sa. First time na shan black tea dinta kenan amma sai taji yayi mata dadi sosai, sai dai bata shanye ba ta ajiye a gefen nasa ta dawo ta sake zama, sai kuma ta tashi ta nufi toilet din ta daurayo bakin ta, ta fito ta haye gadon ta kwanta. Kallon ta yake har ta gama ta rufe idon ta, sai da ya gama shan tea din tas, ya wanko bakin sa sannan ya kashe hasken dakin ya barshi k'asa k'asa, ya kwanta rigingine yana kallon sama, yana tunanin yadda zai bulowa al'amarin Lailah don baya son a samu matsala, gashi har lokacin bashi da wata hujja da zai kare kansa. Ganin zai cigaba da bata lokaci wajen tunanin abinda bashi da iko akai yaga gwanda kawai yayi abinda zai karu ya kuma samu dumbin lada, duk da yasan duk gudun sa take amma ba zai iya hakura ba.   Ji tayi an matso ta sosai, tsoron ta ya karu zuwa sanda taji yana jujjuyata, kuka ta saka masa bil hakki da gaskiya dan tayi masifar tsorata da abinda ya faru, "Dan Allah kayi hakuri." Ta hau bashi hakuri ganin ya dauki hanyar da yar kwakwalwarta ta gaza dauka balle ta gane karatun. Tsayawa yayi chak da abinda yake, ya soma lallashin ta cikin kalamai masu dadi da kwantar daa hankali, a hankali ta dinga samun nutsuwa har ta dawo da nutsuwar ta, ta saduda ta saddakar ta mika wuya, domin dama ance shi aure yakin mata ne, toh tabbas wannan yana daya daga cikin manya manyan yakin matan. Ba zata iya cewa ga kalar wahalar da tasha ba, duk da yayi matukar kokari wajen ganin bata sha wahala sosai ba, amma kuma dole ne, sai dai a hankali a hankali komai zai daidaita haka rayuwar take haka kuma kowa yayi har ya saba. Ita dai bata san sanda wani baccin wahala ya kwashe ta ba, a hakan ba tare da ta gyara ba, sai chan cikin dare ta farka ta zame jikin ta, ta wuce toilet ta gyara kanta sosai sannan ta dawo dakin ta kwanta tana shigewa jikin sa, sake rungume ta yayi tsam a jikinsa bacci ya sake awun gaba da ita.    Da yake tafiyar wuri zai saboda ogan sa da yake son gani, ya saka yana sallar asubah yayi mata sallama ya tafi, kamar ta hanashi tafiyar haka taji amma bata nuna ba, dan ta lura da muhimmancin tafiyar tasa shiyasa ma bata nuna damuwar ta ba, bayan gari yayi haske sosai Ammi ta aiko aka tafi da ita chan shashen ta, daga nan kuma aka kaita ta gaida Bubu, ya saka musu albarka sannan ya hada da nasiha akan rayuwar zaman aure wadda ba zaka taba iya gane ta ba sai ka shiga cikin ta.   Sai dare ta dawo bangaren ta, tayi wanka ta dauki waya da nufin kiranshi sai ga kiran nashi ya shigo, sunyi exchanging text message amma basuyi magana ba tun da ya tafi, whatspp yace ta hau ya kirata video call suka dade suna waya, kamar kar su rabu da k'yar suka hakura suka kwanta. Kwana biyu da tafiyar sa, babu wani abu da suka samu daga ita har Muhammad din, duk da yace yana kokarin sa daga chan din ma amma sam hankalin ta ya gaza kwanciya, gaba daya bata cikin hayyacin ta kwata kwata dan ko sunyi waya korafin ta kenan. Duk shirin da ya kamata Laila tayi taa gama, ta saddakar dole ne ya aure ta, dan bashi da wata hujja duk wata hujja ma bata bar mishi ba, shiyasa take shirin ta hankali kwance kuma shiri gagarumi dan biki zatayi na kece raini, ita kanta Kilishi sai ta zama yar kallo, amma kuma ita kanta tana son auren ya yi wu, dan rashin samun mafitar Muhammad din shi zai taimaka sosai wajen cikar burin ta, dan ta riga ta gama aikawa duk wasu manyan masarautar sakon abinda muhammad din yayi, ta kuma san ba zasu taba bari a zaba musu muhammad din a matsayin shugaba ba. Ana gobe wa'adin da Bubu ya gindaya masa ya dawo, shi kansa ba a nutse yake ba amma yayi kokari sosai wajen kwantar mata da hankali. Takanas yaje ya samu Aji sukayi magana be baro wajen Ajin ba sai dare sosai, yayi tunanin ma zai tarar tayi bacci amma sai ya ganta a zaune tana jiranshi. Tsokanar ta ya hau yi har sai da ya tabbatar ta manta, suka kwana cikin farin ciki sai dai asubah nayi duk jikinta yayi sanyi, duk abinda take yana kallon ta, ya kuma kara tabbatr da da gaske tana son shi tana kuma kishin shi sosai, sai dai bata son ta nuna kishin nata a fili, ta barshi a zuwan kawai tana tayashi ne. Da wuri ya shirya ya fice ta biyo shi har kofa kafin ya fita, ta rik'e shi sai hawaye, janta yayi zuwa falon ya rarrasheta ya samu da k'yar tayi shiru ya fice yana waya da Musaddik. Kasancewar ranar ne ranar da Bubu ya shirya ranar da zai sauka ya bawa muhammad mulkin duk da shi Muhamamd din bashi da masaniya, sai ya zama na gaba daya masarautar ta cika sosai da manyan mutane, tun a daren jiya wasu suka iso. Hakan ya jawo bubu ya shiga busy sosai, sai da suka hadu da muhammad din a masallaci yace ya same shi karfe takwas na safe a bangarensa. Shiyasa ya shirya ya fita da wuri, ya kuma same shi yana shiryawa,. Kai tsaye Bubun ya tambaye shi idan yana da wata magana akan abinda ake tuhumar sa? Kai tsaye yace bashi da wata hujja da zai kare kansa, amma yasan be aikata abinda ake zargin sa ba, shiru Bubu yayi dan yadda maganar ta karade ko ina har kunyar fita yake a yau, sallamar sa yayi kawai ba tare da yace komai ba. Fitowar Bubu ya saka kowa nutsuwa, fadar tayi tsit bayan ya zauna, wanda suka sanshi suna kallon shi zasu gane ransa a bace yake,limamin babban masallacin Masarautar ya saka aka kira masa shi gaba, ya matso gaba, Bubun ya bada umarnin za'a daura auren Muhammad da Laila. Nan da nan fad'ar ta dauki hayaniya, kowa na kokarin tofa albarkacin bakin sa! *_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/3/22, 21:11 - Buhainat: Halin Girma       28 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ******* ? Jan kafa ta dinga yi har zuwa wajen da jakar ta ke ajiye, ta hau zazzage ta ko Allah zai sa taga wayar ta, tun da tazo gidan bata sake ganin wayar ta ba, gashi tana matukar bukatar tayi magana da Mama, ji taka kamar mutuwa zatayi saboda azabar wahalar da take ciki. Bata ga wayar ba, sai yan kayan ta da Bashir din ya dauko mata daga wanchan gidan da yafi mata nan sau dubu duk kuwa da rashin haduwar gidan amma chan a kalla zata samu yancin ta, ba kamar nan da take xaune karkashin matar Bashir din ba.   Kwanciya tayi a tsakiyar dakin, tana cigaba da rera kukan ta, har zuwa lokacin da taji ana taba kofar, kafin ta bud'e ta zuro kanta "Uban me kike wai har yanxu baki fito kin yi ayyukan ki ba?" Ta tsinkayi muryar ta har cikin kwakwalwarta, matsawa tayi amma bata tashi ba, shigowa tayi a fusace ta mik'ar da ita, ta k'wala ihu cikin azaba tace. "Dan girman Allah kiyi hakuri bani da lafiya." Da sauri ta saketa, ta ja baya tana kare mata kallo "Kutmar U! Ni Bash zai munafunta? Kan bala'i amma wallahi sai na yi masa rashin mutunci, dan wulakanci duk yadda nake kaff-kaffa amma sai da ya zagayo ya taba yarinyar na? Ni xai zawo wa raini!" Kamar wadda ake hankadawa ta fice da sauri, Zeenat na jinta tun daga kofar ta fara k'wala masa kira, baya kasan da ta barshi haka kuma baya sama ya riga yasan abinda ya aikata shiyasa ya bar gidan. Sake dawowa tayi dakin ta tashi Zeenat din tsaye da karfi " Tunda har kin iya kwana da miji sai ki fito kiyi aiki, babu wani langabewa da zakiyi wallahi sai kin min aiki." "Dan Allah kiyi hakuri wallahi zazzabi nake ji, jikina duk ciwo yake." "Hehehe..." Ta saki shewa tana mata kallon banza gami da tafa hannu "Idan kinga na kyale ki sai dai idan mashasharar mutuwa naga kina yi, amma wallahi tunda kika kwana da miji sai kinyi min aiki." Kuka Zeenat din take da gaske ba da wasa ba, kuma da gaske take zazzabin take ga wani irin ciwo da ta kasa gane wanne iri ne, a lokacin ne ta tuna wtaa rana ana ruwan sama, haka Mama ta tursasawa Iman wanke mata wasu kaya masu yawan gaske,sannan tana wankin tana girki duk kuma a bayan, har aka kare ruwan nan tana kaiwa da komowa ba tare da Maman ta tausaya mata ta duba halin da zata shiga ba, a lokacin ita tana kwance a daki tana karatun wani littafin hausa, sai bayan an gama ruwan ne ta fito ta sakawa cikinta abinci ta sake komawa.    Tulin kayan wanke-wanken da yake gabanta ta kalla, ta sake fashewa da wani sabon kukan, a hankali ta zauna a gefen dandamalin ta shiga wanke su tana yi tana kuka shabe-shabe.    Sai da ta gama komai ta gyara gidan tas sannan ta samu ta sakawa cikinta ruwan tea da take jin shi kadai zata iya sawa a cikin, ta koma daki ta kudundune tana jin sanda Hajiyar ta bar gidan cikin rakiyar kawayenta. Bayan kamar minti goma sha biyar da tafiyar ta, ta tashi ta dauki jakar hannun ta, da mayafi ta fito ta nufi hanyar gate din gidan, fatan ta kawai ta bar gidan idan har ta fita toh babu ita babu auren Bashir ko me za'a iya sai dai ayi amma ta gama auren. Har taje gate din bata ga kowa ba, haka babu me gadi a wajen tayi saurin isa kofar ta kama ta bud'e ta, sai taji ta a rufe, ta ja da dan ragowar karfin ta amma still ko motsi kofar batayi ba, tana haka ne sai taji alamun ana saka key ta waje, kafin ta iya barin wajen har Bashir ya shigo sanye da sabuwar shadda kunnen sa makale da waya yana magana yana dariya sai dayan hannun nasa rik'e da wayar ta da leda me tambarin sahad stores. "Zan kiraka oga, nagode sosai." Ya katse kiran yana dubanta "Ba dai guduwa zakiyi ba?" "Ban sani ba." Tace tana matsawa gaba tana cigaba da kokarin bud'e kofar dan da ya shigo rufe tayi yayi "Muje ciki kiji." "Babu in da zani, na gama zama a bakin gidan nan, da muguntar matarka, wallahi gidan mu zani ba zan iya ba." "Naji toh, amma kizo muje kinga na siyo miki chocolates masu kyau da gasasshiyar kaza, da yogurt." "Da yake ka samu mayya ko? Toh ba zan koma ba wallahi." Sai ta fashe da kuka da karfi, da sauri ya toshe mata baki, ya sungumeta tana ihu be ajiye ta ba sai da ya kaita dakin, sannan ya dire ta, gani yayi idan ya biye mata zata tara masa mutane. Yana ajiyeta ya zauna a gefe yana bud'e ledojin " Nasan kinsha wahala jiyan nan, taso kisha fresh yogurt din nan zaki ji dadi." Banza tayi masa ta cigaab da gursheken kukan ta. Ci ya hau yi yana kallon ta, yana jin da zata yarda da ya sake zuwa karaye, amma yasan yadda ta sha wahalar nan zai yi wuya ta amince masa, yaga kiran Hajiya wajen sau goma amma be daga ko daya ba, dan yasan kwanan zancen yanzu ma sai da ya tabbatar ta bar gidan sannan ya shigo, da ace Zeenat din zata amince masa da lafiya lou, shiyasa ma ya tsaya yayi mata siyayyar yasanta da shegen kwadayi, amma sai yaga ko kallo be isheta ba daga shi har kayan hannun nasa. Sai da ya kusan cinyewa sannan ya tuna ya rage mata, ya mike zai fita ta tsare shi " Bani wayata." "Hauka nake? Kije ki kira min ruwa kenan, ai kinga na baki wayar nan ko? Toh nasan me na taka in da ko kinje sai kin dawo da kafarki." Matsar da ita yayi ya fice yaje ya dora ruwa, yayi zafi ya juyo mata a wani babban bawo ya kai mata toilet ya dawo ya sake sungumarta tana dukansa da komai ya kaita, ya danna ta ciki ta dinga ihu tana tashi amma sai da ya daddanne ta har ta hakura ta zauna, sannan ya fito ya barta a ciki, ya nufi gate ya samu me gadi ya dawo ya ja masa kashedi akan kar ya kuskura ya barta ta fita sannan ya fice daga gidan da baya saka ran dawowar shi sai dare yayi sosai saboda Hajjajun sa da yasan ta tama zata kare masa tanadi tsaf dan ba abinda ta tsana kamar tarayya ita da wani akan abu guda! ***Tana zaune ya dawo daga sallar, ya chanja kayan jikin sa zuw doguwar jallabiya maroon colour me kyau, bata kai masa har k'asa ba, tashi tayi suka hadu a hanya sannan suka karasa tsakiyar falon, ta wuce zuwa dining area din ta dauko warmers din ta dawo ta jere su a k'asan bayan ta ciro table mat ta shinfid'a akan carpet din "Me yasa zaki bawa kanki wahala bayan duk wannan aikin kina da wadanda zasuyi." "Ban iya zama haka nan babu aiki ba wallahi, ni nama sallame su tun dazu nace su je zan neme su." Jinjina kai yayi yana yaba mata, tashi yayi ya tayata suka karasa sakko da sauran kayan, sannan yayi serving nasu a plate daya, da spoon daya, debowa yayi ya nufo bakin ta yace "Oya, it's my duty bud'e bakin ki." Dariya ta saka ta bud'e bakin a kunyace ya saka mata, sannan shima ya diba ya ci dadin girkin ya ratsa shi, lumshe idon sa yayi ya bud'e yana ware su akanta "Da gaske kice kika yi abincin nan?" "Da gaske!" "Wow... Alhamdulillah Ya Allah, I'm blessed ta ko ina, Allah nagode maka, abincin nan yayi dadi sosai,Allah yayi miki albarka." "Amin." Ta amsa tana jin dadi sosai, babu abinda mace take so irin idan tayi abu a yaba, tana fatan ya dore har gaba, hakan yana karawa mace karfin guiwa wajen kyautata ma mijinta. Cikin nishadi suka gama cin abincin, ya sake tayata suka tattare kayan zuwa kan dining din, in da masu aikin zasu kwashe daga nan zuwa kitchen. Falon suka dawo suka zauna, ya matso kusa da ita ya ajiye kansa a saman kafarta, yace "Ina jinki, bani labarin yadda akayi." Dan muskutawa tayi ya gyara shima, tayi murmushi me sauti ya maida mata yana jan kunnensa "Na matsu naji!" "Abinda ya faru bayan ka fita, na dawo daki na zauna ina tunanin mafita, duk tunanin da zanyi nayi babu wani abu da nake ganin zamu iya rik'e shi a matsayin hujja, duk da haka ban karaya ba, inaji da yakinin Allah ba zai bata nasara ba, hakan ya saka ni tashi na dauro alwala, nazo nayi nafila, na sake rokon Allah akan ya taimaka ya bayyana gaskiya, bayan na idar ne kawai nayi deciding bari na shiga kitchen na ga abinda yake wakana, domin a rayuwa ta kitchen na daya daga cikin wuraren da ya zama tamkar daki na, domin nayi masa sabon gaske. Na tarar da ma'aikata da yawa suna ta hada-hadar hada girki, shine na karbi aikin namu, nace su ji da nasu. Muna aikin ne sako ya iso, a cikin envelope din nan..." Ta nuna masa tana mika masa " Flash ne a ciki, wai inji wata mata sanye da nikaf tace a bani, a haka sakon yazo." Jujjuya envelope din yake a hannun sa, tambarin gidan ne a jikin envelope din, wanda ba kowa ne yake samun ta ba sai jinin gidan... Cigaba tayi "Shine nazo na saka a jikin Tv, abinda na gani ya saka ni rawar jiki, nayi sauri na nufi daki na dauko system dinka da kayi amfani jiya, naci sa'a na sameta a bud'e, na saka flash din a jiki nayi copying komai a wayata sannan na tura maka, na kuma kiraka da nufin nace ka duba amma kuma har ta gama ringing baka daga ba, a lokacin babu irin tashin hankalin da ban shiga ba, na dinga kaiwa da komowa a tsakani ina fatan ka daga wayar ko kuma ka duba sakon kafin lokaci ya kure. Ganin shiru shiru babu alamar zaka daga, sai na yanke shawarar zuwa da kaina, har fadar dan ba zan iya jurewa ba, har na dauki abinda zan dauka na fito na kuma kira wadda zata rakani, sai ga kiran ka." Zaune ya tashi ya jere da ita akan kujerar, yana cigaba da jujjuya envelope din, yana son gano wanda zai aiko da sakon, duk iya tunanin sa be samu amsa ba, sai ya ajiye a gefe ya rungumota jikin sa yana murmushi "Thank you so much Baby, nagode sosai da kokarin ki." "U welcome." "Ashe dai Ashe ana so na tunda har ake kishi na." "Kishi kuma?" "Ehen menene? Kishi ne mana, hadda kuka fa daxu da zan tafi, kamar wanda zai tafi filing daga!" Sai ya tuntsure da dariya yana gwada yadda ta riko shi, turo baki tayi tana tashi daga kusa dashi "Tayaka jimamin abun nake fa, aiko ba zan kara tayaka ba." " Fadi gaskiya dai, kinga za'a kwace miki handsome mijinki, hankali ya tashi." " Na shiga uku." " Ba haka bane? Kinga hanci zur har baka, yarinya taga handsome guy tace idan bani ba sai rijiyar kusugu." " Allah kaiko?" " Ai gaskiya ne, ki rantse ba kishi bane." Shiru tayi ta kyale shi, ta lura yana da so wasa da tsokanar ta, is like kamar ma yafi jin dadin sakata a gaba yayi ta tsokana, amma ka ganshi da sauran mutane kamar bashi ba.    Bayan yayi sallar la'asar ne ya sake chanja kaya ya fita, lokacin yaran sojojin sa sun iso, dama sunyi waya akan suna hanya, yazo ya baza su a kofar shashen sa in da babu shegen da zai sake gigin shigar masa, balle har wani abu ya faru, duk da ma ba wani zama zai ba, sati daya zasu kara ya tattara yayi tafiyar sa Kano daga nan kuma yana tunanin ma k'asar zai bari, ya rasa yadda zai da abokan aikin sa da suka ce sun shirya masa kayataccen bikin sword crossing gashi har date din ya wuce sun sake rescheduling wata ranar, dole ya yarda dan sun kashe kudi sun kuma gayyaci manyan mutane, shiyasa kawai ya hakura yace zasu zo, daga nan sai suje su ga mahaifiyar Iman din daga nan suyi tafiyar su Kano Adamawa sai an Baba ta gani. Akwai tafiyar da zasuyi akan wani babban assignment daga wajen aiki duk da ba'a saka rana ba, amma baya so tafiyar ta zo nan kusa, yafi so sai sun je sun dawo ma, amma zai sake tuntuba yaji, yaji kuma iya dadewar da za'a yi idan yaga za'a shiga rayuwar sa zai iya fadawa dan baya son abinda zai saka shi yin nisa da Iman din, musamamn ya barta a gidan su ita kadai, be yarda da kowa ba, haka nan be yarda da duk wanda ya aiko da flash din nan ba, akwai wani hidden bayani a k'asa, ya riga yasan gidan su, ya san abinda za'a iya da wanda ba za'a iya ba,be kuma san iya adadin mutanen da suke son ganin bayan sa ba, duk da ya nuna bashi da ra'ayin saurata ko kad'an, amma ya tabbatar da akwai wadanda suke tsoron sauyawar ra'ayin sa, wanda suke gudun wani abu ya faru ba abinda suke fata ko suka tsara ba.    A wajen Bubu ya shantake dan tare sukayi har sallar magriba yayi masa tas akan abinda ya aikata dazun akan sakon gwamna, duk da yaji dadi a kasan ranshi amma be nuna masa ba, sai ma fad'a da yayi masa akan kar ya sake, ya amsa da toh ba zai sake ba, sannan suka cigaba da hirar su irin wadda suka dade basu yi irin ta ba.   Ana magriba Ammi ta aiko kiran Iman din, ta tashi cikin rakiyar hadiman ta suka nufi wajen Ammin in da ta tarar da wasu baki wanda daga gani masu muhimmanci ne ga Ammin, gaishe su tayi a ladabce bayan ta gaida Ammin, sannan Ammi ta gabatar da ita a matsayin matar Muhammad suma ta gabatar dasu ga Iman din, matar gwamnan Adamawa ce da yarta wadda Iman din ta lura da girman kanta, dan tun shigowar Iman din ko daga kai batayi ta kalle ta ba, tana ta danna waya tana cin chewing gum. Share ta ita ma Iman din tayi, suka cigaba da zaman shiru bayan tashin Ammi da matar suka shiga ciki suka barsu. Wayarta ta kara a kunne, tana yatsine kafin tace "Moha gani a part din Ammi fa." "Wallahi tun dazu ma, zaka shigo?" "Owk ina jiran ka." Satar kallon ta Iman tayi suka hada ido, sai ta dauke kanta kamar bata gane me take magana akai ba. Suna zaune a haka har wajen minti talatin kafin kofar part din ta bud'e, ya shigo yana kokarin daidaita kallon sa akan Iman da take zaune ta dayan bangaren. "Ina chan ina jiranki ashe kina nan kin ma manta dani ko?" Yayi maganar yana zama a hannun kujerar da take kai "Nazo gaida Ammi ne, sorry na maka text baka gani ba?" "Sai yanzu na gani fa, shine nayo nan da sauri na." Dariya tayi, ta dan taba shi alamun kai ko? Gyaran murya suka je, ya kalli wajen "Samha! I'm so sorry na manta munyi magana kince kina nan, gaba daya hankali na yayi gaba wallahi,." "Uhm ba komai, ai kana tare da Madam." "Yes yes wallahi kin ganta, Baby ga Samha my classmate." "Allah sarki sannu." " Sannu." Tace a gajarce tana dauke kai "Samha this is my wife, baki zo biki ba zamu ciki tara." Yak'e tayi "Bana k'asar time din, naga Amarya Allah ya sanya alkhairi, Laila ta fad'a min ai." " Kin gama mu wuce?" Yace yana bagarar da zancen jin ta sako maganar Laila " Ai bance ma Ammi zan tafi ba." " Owk bari na fad'a mata." Ya tashi shiga ciki, ya barsu su biyu, murmushi ne a fuskar Iman, a kalla taji dadi da yadda muhammad din yayi dan ta gane sarai so tayi ta kunsa mata haushi shine har da kiran sa a gabanta. Be dade da shiga ba ya dawo yace ta tashi su tafi, suka fice suka barta da bakin ciki. Suna fita ta dauki waya ta kira Laila " Wai baki dawo ba?" " Na kusa shigowa ki jirani." " Ina nan ina jiran ki, ashe rabon zanga kayan bakin ciki, haka Muhammad yake rawar kafa akan yarinyar nan?" " Me yayi?". "Kinga yadda ya narke mata kamar bashi ba, kinsan dai tsaurin sa ko? Toh wallahi a gabanta kamar ruwan sanyi haka ya koma, ni kaina baki ga yadda ya amsa min a sake ba wallahi, kamar fa bashi ba." " Toh an fad'a miki haka ta barshi? Bari kawai na karaso muyi magana." " Shikenan kiyi sauri please." Suka ajiye wayar, jefar da tata Laila tayi a gefen ta, ta shiga jan tsaki a jere cikin bacin rai. _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D’aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/7/22, 09:08 - Buhainat: Halin Girma       29 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ******* ? Tana daf da shigowa ta kira Samha tace ta wuce part dinta dan ba zata iya zuwa wajen Ammi ba, tashi tayi ta fita bayan ta saka wayarta a cikin purse dinta, taja kofar ta nufi wajen Laila din da ya kasance nata ita kadai kusa da na Kilishi. A waje suka hadu ita tana fitowa daga mota ita kuma tazo daidai bangaren, sallamar driver tayi yaran suka dauko mata kaya suka biyo ta, suka hadu suka rankaya ciki tare da Samha. Bayan sun zaune ne Lailan ta tuge mayafin kanta da yake dan yalolo da ta yane kan, ji taka kamar iska bata ratsa kan nata sosai shiyasa duk take jin ranta a jagule babu dadi, ga haushin abinda ya faru ga na karatun ta da take jin kamar ta rasa komai a yanxu. "Kin ganki kuwa Queen, ya akayi haka?" "Menene ma ba zaki gani ba, hmm wallahi bansan waye yayi min zagon k'asa ba, amma ko waye toh tabbas baya kaunata ko kad'an!" " Kin binciki Hadimar nan? Ba kince ita kadai tasan da plan din ba." Girgiza kai tayi " Ba ita bace ba, someone very close to me ne, dan yadda ba kowa ke shiga part din nan ba, toh lallai wanda yake da direct access da part din ne." " Lallai, gaskiya ko waye be kyauta mana ba, yanzu ya ake ciki?" " Wai hakuri? Wallahi ban ba,kinsan yadda nake son Capt tun muna school haka shima kinsan kaunar da yake min ba kad'an bace, ba zan iya rayuwa da kowa ba sai shi, bayan haka kinsan matsala ta da Dr. Bryan Ford." " Haka ne, toh shikenan yanzu menene next move dinki?" " Har yanxu ban dawo daidai ba, I need time to recover nasan me zanyi." " Shikenan, duk abinda zakiyi dai kiyi informing dina, zan baki shawara yadda ya kamata." " I know I can count on you, Nagode Bestie!" "DM!" Tayi murmushi yana relaxing sosai akan kujerar, tana tunanin yadda zatayi amfani da Laila ta samu cikar burin ta! Sai wajen tara sannan suka tafi, bayan Maman sun gama zantawa da Ammi, babbar aminiyar ta ce sama da kowa a kaf adamawa dan da ita ta fara sabawa lokacin da aure ya kawota, sannan yaransu ma tare suka taso ita tana da yara biyar compared to Ammi da take da guda daya tal... Zuciyar ta fari kal sanda suka isa gida, ta san ko babu komai zata dinga samun duk information din da take so ta bakin Laila, tunda tayi masifar yarda da ita fiye da yadda ma ta yarda da uwarta mahaifiya. Bata da kirki ko kad'an idan har ka shiga gonar ta, amma kuma tana masifar ganin mutuncin Samha din, dan itace tafi mata kowa a yanzu, gani take ma babu me kaunar ta sai Samha din kawai. Ko Kilishi ta san ta Kamal kawai take yi ba tata ba, shiyasa itama bata wani sanar da ita idan zatayi abu sai dai daga baya, daga Samha sai amintacciyar hadimar ta guda daya wadda zata iya bada ranta fansa ga Laila din saboda tsabar biyayyar da take mata. Wurgi tayi da tarkacen da ta debo daga mota tayi a saman gadon ta, ta kwanta tana kallon sama ba tare da ta cire dogon takalmin kafarta ba, murmushi take ita kadai duk kuwa da abinda Muhammad din yayi ya bakanta mata rai, amma kuma ta raina yarinyar da ya kira ta da matarsa, a shekaru ba wata babba bace haka ma wayewar rayuwar duniya sam bata cikin sahun amma kuma tana da nutsuwa a yanayin ta, da kuma iya handling abu dan yadda tayi da taji da wanda take waya ya matukar bata mamaki, kamar bata fahimci komai ba bayan sarai ta gane, kuma bata ko bi takanta ba ,ko ta tuhume shi ko ta chanja masa fuska sanda ya shigo, sai ma ta tarbi mijinta da fara'ar da ta mantar dashi komai da kowa. Tashi tayi tsaye ta soma zagaye a tsakanin dakin tana jin kamar taje ta jawo ta da karfin gaske ta fidda ta daga gidan, duk yadda suka kai da wayewa amma ya tsallake su ya dauko wadda bata kai ko rabin ajin sa ba, adah Laila kawai take jin haushi amma yanzu na Laila ya daina damunta, dan tasan babu wani abu da zatayi sai da sanin ta, yarinya karama ce yanzu take neman zame mata ciwon ido. ***Suna shiga part dinsu tun daga kofa ya daga ta sama, ta saki siririn ihu tana kankame shi, da gaske taji tsoro dan bata yi tunani ba, sai ji tayi anyi sama da ita, kin ajiyeta yayi sai da ya kai karshen falon sannan ya zaunar da ita ya bita ya zauna a gefenta yana dariya "Kin fiyaa tsoro Allah!" "Ai it was unexpected shiyasa." "Ba wani, tsoro dai kawai, ki yarda, you have to be strong, kinsan dai ance a wife of a soldier is a soldier!" " Wasa suke suma wallahi." Ta saka dariya " Haka dai aka ce." Yayi dariyar shima "Yawwa... Dazu na gani a WhatsApp wai anyi calling off strike?" " I can't say, bari na kira naji, amma zaki koma ne? Ko a samu wata school din daban?" " Duk yadda akayi yayi." " Owk toh bari naji." Yace yana ciro wayar sa daga aljihu, yayi dialing number wani lecturer abokin sa, suka gaisa sannan ya tambaye shi, baa gama daidaitawa ba amma dai akwai yiwuwar komawar nan kusa. Ajiye wayar yayi ya fad'a mata yadda sukayi "Matsalar k'asar nan kenan, yanzu fisabilillahi fiye da 9month ana strike amma gwamnati tayi shiru? Shikenan karatun yara ya lalace akan wani dalili mara tushe, it's so unfortunate gaskiya." "Wallahi har sai mutum ma ya gaji da zaman, babu dadi sam." "Dole ai, Allah ya kyauta." "Amin." Tace sai sukaayi shiru, chan kuma yace "Bari muga idan basu daidaita ba, kawai sai mu chanja ko Base ne, ko kuma wata private uni din na Kano." "Owk Allah ya zaba mana mafi alkhairi." " Amin Matata!" *** Tare suka shiga ciki bayan sun kammala duk abinda ya kamata su kammala a falon, zama yayi ya kunna system ya shiga aiki ita kuma ta wuce toilet dan ta watsa ruwa tazo ta kwanta. Sharp sharp tayi wankan ta fito sanye da rigar da ta cire , be kalle ta ba, har ta isa gaban wardrobe ta dauki wata mara nauyi iyakar ta kasan guiwa, dan duk sauran kayan da take dasu anan ba zata iya kwanciya dasu ba, idan ma ta saka tasan shi, zai iya yin karfa karfa ya hanata yayi amfani da damar yayi mata wayo. A gajiye take jin ta yau din ba wai don tayi wani aiki ba, bata san dalili ba gaba daya jikin ta ciwo yake mata, wankan da tayi take saka ran zai dan saka taji dama-dama. Kallon ta yayi bayan ta sako rigar, yayi mata alamar tazo, ta taho ta zauna agefen sa, ya cigaba da aikin da yake na hada kan wasu takardu masu muhimmanci sosai, yana lura da ita yadda jikinta yayi sanyi sosai, jawo ta yayi bayan ya dan matsar da system din, ya kwantar da kanta a jikin shi "Goodnight sweet dreams." Ya rankwafo yayi mata peck a kunci, lumshe idon ta tayi bacci na cin karfin ta sosai. Be san iya adadin awoyin da ya dauka a wajen ba, ya dade sosai har sai da ya fara jin bishi-bishi, sannan ya rufe system din, ya gyarata a hankali sannan ya tashi yana mika, alwala yayi yazo yayi sallah raka'ah biyu, ya lura da ko shafa'i da wutri da ta saba yau bata yi ba, be san wanne irin bacci take ji haka ba, dan har ya gama aikin sa ya tashi ko motsawa batayi ba. Taimaka mata yayi zuwa gadon ya kwantar da ita ya lullube mata iya kafarta, sannan ya kwanta bayan ya rage kayan jikin sa ya rage daga shi sai boxer kawai. Cikin dare sosai taji ishirwa, irin wadda bata taba jin irin ta ba, tashi tayi ta lallaba ta fito bayan ta duba fridge din dakin ta tuna babu ruwa a ciki, ta manta kuma bata kawo ba dan bata bar kowa cikin masu aikin sun taba shigar mata dakin ba, iyakar su falo shima dan babu yadda zatayi ne amma ko yaushe suna BQ sai wani abu me muhimmanci sannan take kiran su. A kitchen ta samu ruwan, tasha sannan ta dauko karamin katan na ruwan ta taho dashi. Falon yayi dim amma kuma akwai dan haske kadan da ya hasko ta corridor din kitchen da yake a kunne, kafarta take sawa a hankali tana tafiyar har ta kai tsakiyar falon, da yake falo ne katon gaske da sai kayi tafiya tsakanin kitchen da corridor din bedrooms din, motsi taji kad'an kad'an, tana matsowa yana karuwa har ta kusa kai wa corridor din abinda ta gani a wajen ya sakata daskarewa a wajen. Chak ta tsaya ta kwalla wata irin kara da ta tashi Moh daga bacci, ya mike a firgice yana kiran sunan ta, sai kuma yayi hanyar fita daga dakin da sassarfa kirjin sa na bugawa da karfi! BIYAN BASHI ⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️😂😂😂😂😂 2/7/22, 19:06 - Buhainat: Halin Girma       29 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ******* ? Tana daf da shigowa ta kira Samha tace ta wuce part dinta dan ba zata iya zuwa wajen Ammi ba, tashi tayi ta fita bayan ta saka wayarta a cikin purse dinta, taja kofar ta nufi wajen Laila din da ya kasance nata ita kadai kusa da na Kilishi. A waje suka hadu ita tana fitowa daga mota ita kuma tazo daidai bangaren, sallamar driver tayi yaran suka dauko mata kaya suka biyo ta, suka hadu suka rankaya ciki tare da Samha. Bayan sun zaune ne Lailan ta tuge mayafin kanta da yake dan yalolo da ta yane kan, ji taka kamar iska bata ratsa kan nata sosai shiyasa duk take jin ranta a jagule babu dadi, ga haushin abinda ya faru ga na karatun ta da take jin kamar ta rasa komai a yanxu. "Kin ganki kuwa Queen, ya akayi haka?" "Menene ma ba zaki gani ba, hmm wallahi bansan waye yayi min zagon k'asa ba, amma ko waye toh tabbas baya kaunata ko kad'an!" " Kin binciki Hadimar nan? Ba kince ita kadai tasan da plan din ba." Girgiza kai tayi " Ba ita bace ba, someone very close to me ne, dan yadda ba kowa ke shiga part din nan ba, toh lallai wanda yake da direct access da part din ne." " Lallai, gaskiya ko waye be kyauta mana ba, yanzu ya ake ciki?" " Wai hakuri? Wallahi ban ba,kinsan yadda nake son Capt tun muna school haka shima kinsan kaunar da yake min ba kad'an bace, ba zan iya rayuwa da kowa ba sai shi, bayan haka kinsan matsala ta da Dr. Bryan Ford." " Haka ne, toh shikenan yanzu menene next move dinki?" " Har yanxu ban dawo daidai ba, I need time to recover nasan me zanyi." " Shikenan, duk abinda zakiyi dai kiyi informing dina, zan baki shawara yadda ya kamata." " I know I can count on you, Nagode Bestie!" "DM!" Tayi murmushi yana relaxing sosai akan kujerar, tana tunanin yadda zatayi amfani da Laila ta samu cikar burin ta! Sai wajen tara sannan suka tafi, bayan Maman sun gama zantawa da Ammi, babbar aminiyar ta ce sama da kowa a kaf adamawa dan da ita ta fara sabawa lokacin da aure ya kawota, sannan yaransu ma tare suka taso ita tana da yara biyar compared to Ammi da take da guda daya tal... Zuciyar ta fari kal sanda suka isa gida, ta san ko babu komai zata dinga samun duk information din da take so ta bakin Laila, tunda tayi masifar yarda da ita fiye da yadda ma ta yarda da uwarta mahaifiya. Bata da kirki ko kad'an idan har ka shiga gonar ta, amma kuma tana masifar ganin mutuncin Samha din, dan itace tafi mata kowa a yanzu, gani take ma babu me kaunar ta sai Samha din kawai. Ko Kilishi ta san ta Kamal kawai take yi ba tata ba, shiyasa itama bata wani sanar da ita idan zatayi abu sai dai daga baya, daga Samha sai amintacciyar hadimar ta guda daya wadda zata iya bada ranta fansa ga Laila din saboda tsabar biyayyar da take mata. Wurgi tayi da tarkacen da ta debo daga mota tayi a saman gadon ta, ta kwanta tana kallon sama ba tare da ta cire dogon takalmin kafarta ba, murmushi take ita kadai duk kuwa da abinda Muhammad din yayi ya bakanta mata rai, amma kuma ta raina yarinyar da ya kira ta da matarsa, a shekaru ba wata babba bace haka ma wayewar rayuwar duniya sam bata cikin sahun amma kuma tana da nutsuwa a yanayin ta, da kuma iya handling abu dan yadda tayi da taji da wanda take waya ya matukar bata mamaki, kamar bata fahimci komai ba bayan sarai ta gane, kuma bata ko bi takanta ba ,ko ta tuhume shi ko ta chanja masa fuska sanda ya shigo, sai ma ta tarbi mijinta da fara'ar da ta mantar dashi komai da kowa. Tashi tayi tsaye ta soma zagaye a tsakanin dakin tana jin kamar taje ta jawo ta da karfin gaske ta fidda ta daga gidan, duk yadda suka kai da wayewa amma ya tsallake su ya dauko wadda bata kai ko rabin ajin sa ba, adah Laila kawai take jin haushi amma yanzu na Laila ya daina damunta, dan tasan babu wani abu da zatayi sai da sanin ta, yarinya karama ce yanzu take neman zame mata ciwon ido. ***Suna shiga part dinsu tun daga kofa ya daga ta sama, ta saki siririn ihu tana kankame shi, da gaske taji tsoro dan bata yi tunani ba, sai ji tayi anyi sama da ita, kin ajiyeta yayi sai da ya kai karshen falon sannan ya zaunar da ita ya bita ya zauna a gefenta yana dariya "Kin fiyaa tsoro Allah!" "Ai it was unexpected shiyasa." "Ba wani, tsoro dai kawai, ki yarda, you have to be strong, kinsan dai ance a wife of a soldier is a soldier!" " Wasa suke suma wallahi." Ta saka dariya " Haka dai aka ce." Yayi dariyar shima "Yawwa... Dazu na gani a WhatsApp wai anyi calling off strike?" " I can't say, bari na kira naji, amma zaki koma ne? Ko a samu wata school din daban?" " Duk yadda akayi yayi." " Owk toh bari naji." Yace yana ciro wayar sa daga aljihu, yayi dialing number wani lecturer abokin sa, suka gaisa sannan ya tambaye shi, baa gama daidaitawa ba amma dai akwai yiwuwar komawar nan kusa. Ajiye wayar yayi ya fad'a mata yadda sukayi "Matsalar k'asar nan kenan, yanzu fisabilillahi fiye da 9month ana strike amma gwamnati tayi shiru? Shikenan karatun yara ya lalace akan wani dalili mara tushe, it's so unfortunate gaskiya." "Wallahi har sai mutum ma ya gaji da zaman, babu dadi sam." "Dole ai, Allah ya kyauta." "Amin." Tace sai sukaayi shiru, chan kuma yace "Bari muga idan basu daidaita ba, kawai sai mu chanja ko Base ne, ko kuma wata private uni din na Kano." "Owk Allah ya zaba mana mafi alkhairi." " Amin Matata!" *** Tare suka shiga ciki bayan sun kammala duk abinda ya kamata su kammala a falon, zama yayi ya kunna system ya shiga aiki ita kuma ta wuce toilet dan ta watsa ruwa tazo ta kwanta. Sharp sharp tayi wankan ta fito sanye da rigar da ta cire , be kalle ta ba, har ta isa gaban wardrobe ta dauki wata mara nauyi iyakar ta kasan guiwa, dan duk sauran kayan da take dasu anan ba zata iya kwanciya dasu ba, idan ma ta saka tasan shi, zai iya yin karfa karfa ya hanata yayi amfani da damar yayi mata wayo. A gajiye take jin ta yau din ba wai don tayi wani aiki ba, bata san dalili ba gaba daya jikin ta ciwo yake mata, wankan da tayi take saka ran zai dan saka taji dama-dama. Kallon ta yayi bayan ta sako rigar, yayi mata alamar tazo, ta taho ta zauna agefen sa, ya cigaba da aikin da yake na hada kan wasu takardu masu muhimmanci sosai, yana lura da ita yadda jikinta yayi sanyi sosai, jawo ta yayi bayan ya dan matsar da system din, ya kwantar da kanta a jikin shi "Goodnight sweet dreams." Ya rankwafo yayi mata peck a kunci, lumshe idon ta tayi bacci na cin karfin ta sosai. Be san iya adadin awoyin da ya dauka a wajen ba, ya dade sosai har sai da ya fara jin bishi-bishi, sannan ya rufe system din, ya gyarata a hankali sannan ya tashi yana mika, alwala yayi yazo yayi sallah raka'ah biyu, ya lura da ko shafa'i da wutri da ta saba yau bata yi ba, be san wanne irin bacci take ji haka ba, dan har ya gama aikin sa ya tashi ko motsawa batayi ba. Taimaka mata yayi zuwa gadon ya kwantar da ita ya lullube mata iya kafarta, sannan ya kwanta bayan ya rage kayan jikin sa ya rage daga shi sai boxer kawai. Cikin dare sosai taji ishirwa, irin wadda bata taba jin irin ta ba, tashi tayi ta lallaba ta fito bayan ta duba fridge din dakin ta tuna babu ruwa a ciki, ta manta kuma bata kawo ba dan bata bar kowa cikin masu aikin sun taba shigar mata dakin ba, iyakar su falo shima dan babu yadda zatayi ne amma ko yaushe suna BQ sai wani abu me muhimmanci sannan take kiran su. A kitchen ta samu ruwan, tasha sannan ta dauko karamin katan na ruwan ta taho dashi. Falon yayi dim amma kuma akwai dan haske kadan da ya hasko ta corridor din kitchen da yake a kunne, kafarta take sawa a hankali tana tafiyar har ta kai tsakiyar falon, da yake falo ne katon gaske da sai kayi tafiya tsakanin kitchen da corridor din bedrooms din, motsi taji kad'an kad'an, tana matsowa yana karuwa har ta kusa kai wa corridor din abinda ta gani a wajen ya sakata daskarewa a wajen. Chak ta tsaya ta kwalla wata irin kara da ta tashi Moh daga bacci, ya mike a firgice yana kiran sunan ta, sai kuma yayi hanyar fita daga dakin da sassarfa kirjin sa na bugawa da karfi! BIYAN BASHI ⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️⛹️😂😂😂😂😂 2/7/22, 19:06 - Buhainat: Halin Girma       30 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ******* ? A durkushe ya ganta tana kuka ta rik'e kanta, saurin durkusawa yayi a gabanta yana janye hannun nata "Menene?" "Miciji!" Tayi maganar tana nuna masa wajen, saurin kalla yayi amma be ga komai ba, ya yunkura zai tashi ta kankame shi sosai tana fashewa da kuka. Hannun ta ya kama zuwa wajen switch din falon, ya kunna haske ya bayyana a ilahirin falon, wurwurga idonsa ya dinga yi a gaba dayan falon amma be ga komai ba, "Aina kika ganshi?" "Adaidai nan zai shiga dakin chan!" "Tsaya ." Ya tsaida ita yana sake dubawa amma babu komai. Riketa yayi ya kaita daki, tayi saurin rikeshi ganin zai fita " Dan Allah karka fita ka barni." " Kinaji? Calm down babu abinda zai faru, yanzu zan dawo.". Sakin sa tayi, ya fita ya taso securities din a gaba, suka zo suka hau bincika falon da ko ina na part din,ciki ya koma ya sameta ta kudundune a saman gadon still jikinta be bar rawar da yake ba, tana addu'a kasa kasa, daga gani kasan ta tsorata sosai dan bata taba ganin shi haka a zahiri ba. Jawota yayi jikin sa, ya mannata da kirjinsa yana shafa mata baya kad'an kad'an. " Babu abinda zai faru kinji? Ki kwantar da hankalin ki." Da kai ta amsa masa, zuwa lokacin ta fara dawowa nutsuwar ta, sai wani uban juyi da taji cikin ta nayi,ta dora hannun ta a saman cikin yana yatsine fuska, kallon hannun nata yayi, ya dauki nasa ya dora a saman nata yana tayata shafa cikin, "Ciwo?" "Eh." "Sannu zai daina, bari na dubo ko sun gama dubawar." Ya kwantar da ita ya fita, a tsaye ya same su rik'e da abu me kama da maciji, matsawa yayi yana dubawa cikin son karin bayani "Macijin roba ne ranka ya dade!" "Roba?" Yace cikin yanayin mamaki "Me ya kawo shi nan? Me yasa bamu ganshi ba tun da rana sai yanzu..." "Waye da waye suka shigo part din nan?" Ya fad'a yana daure fuskarsa tamau. Rantse rantse suka hau yi, kowa na son kare kansa, wata uwar tsawa ya daka musu, duk suka nutsu suka kame suna masu saukar da kansu k'asa "Kwana daya tal na baku, ku gano wanda ya shigo part din nan har ya ajiye wannan shirmen, koma waye sai ya fuskanci hukunci me tsanani!" " Yes sir!" Har ya juya sai kuma ya tsaya. " Get ready, we are leaving tomorrow in the afternoon!" " Yes sir!" Suka kara hada baki wajen fad'a sannan ya juya ya bar su a wajen da sassarfa. Dayan dakin ya shiga, ya hau bincike wasu kaya da sauri da sauri, ba zai yarda a taba masa ita ba, idan har ba zasu iya tsayawa iya kansa kawai ba, toh zai yi abinda zai girgiza su matuka. Ya dan dau lokaci a dakin, sai da ya tuna ya barta ita kadai ya kuma san tsoro take ji, sannan ya koma da sauri, ya tarar bacci ya dauke ta, ta takure waje daya tana fitar da numfashi kad'an kad'an. AC din dakin ya rage, zuwa low ya dawo ya gyara mata kwanciyar, ya kura mata ido yana jin son ta na kara ruruwa a zuciyar sa, ba zai bari banzar al'adar gidan su ta taba ta ba, zai yi duk abinda zai yaga ya kareta da dukkan karfin da yake dashi.    Da asubah ya tashe ta, sukayi sallah a dakin, sannan ya fita ya shigo mata da micijin robar yana mata dariya "Matsoraciya, nina fa na shigo dashi jiya by mistake, abun wasan yaran chan ne suka bani, ashe sai na yar dashi ban ma lura ba." Shiru tayi tana kokarin daidaita maganganun nasa da abinda ta gani, idan har ba gizo idon ta yayi mata ba, toh tabbas tafiya ta ganshi yana yi, har ya kai kofar dakin kafin ta daina ganin sa. "Common!" Yace yana son dauke tunanin ta "Babu komai fa I promise you." "Amma na ganshi fa yana motsi!" "Imagination ne kawai nothing else, karki damu ki kwantar da hankalin ki." Shiru tayi tana kallon sa, yanayin sa yayi mata kama da na wanda yake so ya dauke hankalin ta, amma idan ba haka ba babu yadda za'a yi taga abu yana tafiya da idonta ya zama imagination kuma, hore mata idon yayi yana jawo ta jikinsa "Karki yi ta tunani kinji? Anjima zamu wuce ma, Abuja zamu fara zuwa na gaida Mummy, daga nan muyi tafiyar mu gidan mu mu sha soyayyar mu." "Da gaske?" "Da gaske mana, are you happy?" "Naji dadi sosai, bari na fara hada kaya na, da wuri zamu tafi ko? Ko sai da yamma." "Yamma!" Komawa tayi ta zauna tana jin kamar yamman ya mata tsayi "Zanga Aji ne, sannan bana son kowa yasan mun tafi sai Ammi kawai, shiyasa ba zamu dauki yaran chan ba, i mean ma'aikatan gidan, akwai screening da za'a yi musu kafin su biyo mu." " Owk Allah ya kaimu." " Amin my beautiful wife." Murmushi tayi, ya dauko musu al'qurani me girma suka shiga karantawa, ya dinga admiring muryarta da yadda take bawa kowanne harafi hakkin sa, cikin nutsuwa da fitar da tajweed a duk in da ya dace. Sai da rana ta fito, sannan sukayi wanka, suka shirya a tare suka fita don karyawa, bud'e warmers din yayi, ya kakkala sannan ya saka aka kwashe masa su daga wajen, ya aika part din Ammi aka karbo musu breakfast din, taso ya barta tayi amma ya hanata, ya kuma ki gaya mata dalilin da ya saka shi sawa a kwashe abincin da aka girka a part din, bata ce komai ba, ta barshi a zuwan kawai zata ji koma menene daga baya, dan ta lura yadda ya boye masa kanta kafin aure akwai abubuwa da yawa da yake boyewa a yanzu ma, duk da haka ba zata zarge shi ba, zata bashi lokaci sosai ta kara fahimtar shi, jikinta na bata akwai wani abu da shi kadai ya sani, sai ko Aji da take ganin kusancin su yafi na kowa hatta mahaifiyar sa da mahaifin sa.   Bayan sun gama breakfast din ne ya fita, cikin shigar kayan sojoji da suke masifar yi masa kyau, cikin rakiyar yaransa ya nufi part din Kilishi, wanda tun kafin ya karasa sakon zuwa nasa ya ishe mata, tana zaune ta gama karyawa, tashi tayi da sauri ranta na baci, tasan zuwan sa babu abinda yake jawo mata sai bacin rai. Daki ta shiga ta chanja kaya, ta zauna tana jiran sanarwar isowar sa. Tana jin sanda ya shigo, dan har falon ta na ciki ya shigo, ya zauna fuskar sa fes dauke da farin ciki, idonsa na kan kofar da zata fito, ya dan dauki lokaci a zaune har ya fara tunanin ko ba zata fito ba, agogon hannun sa ya kalla, ya daga kai ya kalli na jikin bangon dakin, a tare suke tafiya dakiya daya, sauke idon sa yayi yana murza agogon nasa, takun tafiya yaji, yaki d'agowa amma yasan itace,sai da ta zauna sannan ya dago yana dubanta, yayi murmushi cikin salon girmamawa yace "Barka da gida ranki ya dade." "Barka dai, ya iyali?" "Lafiya kalou kalou, kamar yadda kike fata a kowanne lokaci." Yak'e tayi, tasan magana ya fad'a mata, dan ya saba gasa mata ita dama, murmushi ya sake yi yana lankwasa hannayen sa baya " Haka ake so ai, sai a sake kula sosai." " In Sha Allah, za'a kula kulawa me kyau, duk wani me sharri Allah zai maida masa kansa ma, saboda addu'a itace makamin mumini, kuma matakin duk wata nasara." " Haka ne!" Tace tana gid'a kanta. Mikewa yayi cikin salo na burgewa, ya dan rankwafa yace " Na barki lafiya!" " Nagode!" Tace tana danne zuciyar ta, bayan sa tabi da kallo har ya fice gaba daya, "Ahhhh!" Tayi kara tana jifa da trow pillow din dake kusa da ita,kamar ta shako shi haka taji, gashi kamar masifa yasan duk wani shirin ta, ta rasa yadda zatayi dashi ya zame mata tamkar kadangaren bakin tulu! Ya kuma zame mata ciwon ido, da za'a bata makami ace ta kashe mutum daya toh tabbas shi zata kashe, bata son ko ganin wulgawar sa.    Laila ce ta shigo, ta tarar da ita cikin halin da take ciki na bacin rai, bin ta tayi da kallo har ta dauki jakar ta, ta bud'e ta dauki ATM cards din Kilishin, ta juya zata bar dakin. "Laila!" Tsayawa tayi ta juyo "Ina zaki? Me kuma zakiyi da Atm dina?" "Haba Mah, tunda har na dauka ai amfani zan dashi." " Shine ba zaki iya fada min ba?" " Da ma fa na saba dauka kuma bana fad'a miki, why now?" Sai ta juya ta cigaba da tafiyar ta " Zan dawo dashi wani payment kawai zan." Sai data kai karshen kofar sannan ta fad'a, ta saka kai tayi ficewar ta, kwafa Kilishin tayi ba tare da ta sake cewa komai ba. ****Bayan fitar sa ne tana zaune da waya a hannun ta suna chatting sama-sama da Ya Maryam,rabin hankalin ta na kan Tv sai tana duba sakon lokaci zuwa lokaci, ta kira Abba bata same shi ba, kila ko ya fita ko kuma baya kusa da wayar. Kara wayarta tayi a tunanin ta Abban ne, sai taga number Ya Maryam ce, dauka tayi tana tashi zaune "Ina ta magana a whatspp kin sauka, yanzu aka kira ni a gida Aunty Bilki ta haihu!" " Dan Allah!" " Wallahi yanzun nan kuwa ta haihu." " Masha ALLAH, me aka samu?" " Ina ma na tsaya tambaya? Murna ta saka ni kiranki, kinga al'amarin Allah, bayan ta cire rai, dama ba'a cire rai da  rahmar Allah." " Wallahi, kai Masha ALLAH, nayi murna sosai Allah ya bata lafiyar shayarwa." " Amin ya Allah, zuwa kano ya kamaki." " Gaskiya, dama yau zamu bar nan din, amma Abuja zamu wuce daga nan zamu dawo Kanon." " Ah shikenan ma, ki kirata toh kafin nan, bari na kira Amira itama na fesa mata." " Owk ki tura min number ta, Inaga kamar bani da ita yanzu." " Ok tam, zan ajiye miki a WhatsApp." " Yawwa." Ajiye wayar tayi farin ciki na kamata, after all a karshe dai itama ta samu nata babyn, shekara ashirin da aure amma bata taba ko batan wata ba, sai yanzu Allah yayi, dama dai sunji kishin kishin din ciki ne da ita musamamn da bata zo bikin da akayi ba, sai mutane suka kara tabbatar da zargin su, boye labarin sukayi sun fi so kawai aji haihuwa daga sama. Duk da bata da yawan magana amma tana masifar son kananan yara, musamman jarirai zuwa 4years haka, ko magana sukayi sai taji dadi, shiyasa take son kaninta Marwan ba kuma tajin komai idan Mama ta sakata aikin sa.    Daukar number aunty bilkin tayi, ta kirata tayi mata murna sosai, suna wayar kiran Abba ya shigo, ta katse na Aunty Bilkin ta daga nasa suka gaisa, anan yake fad'a mata labarin haihuwar ta nuna kamar bata sani ba tayi farin ciki sosai, bayan sun gama wayar ne ta kira Mamma take fad'a mata zuwan su, amma bata san ko a yau din zasu iso ba ko sai gobe dai, murna tana jiyo su Amaan ta wayar kamar zasu shigo ciki saboda karadin su.    ***Tana idar da sallar la'asar sai gashi ya shigo, ba kayan da ya fita dasu bane a jikin sa, wasu ne daban da sukayi mata kama da sababbin da ba'a taba sakasu ba, gaishe shi tayi a ladabce tana daga kan sallayar, ya amsa yana zama, yanayin sa ya nuna a gajiye yake, sai ta tashi ta ninke sallayar ta ajiye ta nufi kitchen ta dauko masa ruwa da soft drink, akan tray ta doro ta dawo falon ta ajiye masa tana rissinawa, saurin tayata yayi yana hadawa da hannun ta da tray din, sukayi dariya a tare ta zauna a gefen sa tana zuba masa ruwan. Karba yayi yasha, sosai saboda tunda ya fita be saka komai a cikin sa ba, gashi sam baya jin yunwa so yake kawai su tafi. "Ga abinci akan dinning ko na kawo maka nan?" "Waye yayi?" "Nice." "Owk zanci, amma ki zubo min a plate ba da yawa ba, sai ki taimaka min da fruit please,." "Ok." Ta mike bayan ta karbi cup din ruwan ta ajiye, taje ta zubo masa abincin ta kawo ta koma ta yanko fruits din ta kawo, yana kwance ya mike kafafunsa, har sai data zauna a gaban abincin sannan ya sakko yana saka spoon din a gaban sa ya soma cin abincin hankalin sa a kwance, sosai yaci dan beyi tunanin zai ci kamar haka ba, sannan ya sha fruits din kadan, bayan ya gama yace "Thank you...Abincin yayi dadi." Blushing tayi cikin jin dadin yabon da yayi mata, ta hau tattare kayan zata kwashe ya rik'e mata hannu "Ki barshi yaran chan zasu gyara idan mun tafi." "Ai ba wahala, bari na kwashe kawai." Sakin hannun nata yayi, ta dauki tray daya, cikin takun da bata san tana dashi ba, ta shiga takawa zuwa kitchen din, kallon ta yake har ta kule kafin ya dawo hayyacin sa, yana kallo ya sake dawowa ta kwashe sauran ya sake bin steps din nata da kalllo, ba zai iya hakura ba, musamamn idan ciki ya dauka, ga kuma abunka da sabon angon da be san ya isa ba, tashi yayi har da dan saurin sa, ya sameta a kitchen din tana tattare dattin plates din, sam bata ji shigowar sa ba, sai ji tayi an rungume ta, ta baya. Ta juyo a dan tsorace kafin kamshin turaren sa ya mamaye ilahirin kitchen din.    Manne bayan su yayi waje daya, ya dora kansa saman gadon bayanta, ya shiga goga mata bayanta da kan nasa. "Ba... Bari... Na karasa gyara kayan." "Barshi, ai dama ba aikinnki bane, ga aikin lada me yawa." Ya sake chusa kansa sosai, tsam ta dauke hannun ta, sanda taji hannun sa na yawo a daidai tsakiyar cikin ta, yana shafawa har zuwa kasan rigar ta, rik'e jikin kitchen cabinet din tayi dan ji tayi kamar zata fadi, Allah yaso ta dafe wajen. Daga ta yayi sama chak, ya wuce falon zuwa bedroom dinsu, ya dire ta yana mata murmushin mugunta,  a matukar tsorace take dashi amma kuma ba zata hanashi ba, dan ba zai taba bata damar da zata hanashin, yabi ya kanainayeta da salon kaunar shi me tsayawa a makoshi!    Sai da suka bata lokaci sosai, dan har wani dan guntun bacci yayi bayan nan, da k'yar ta tashe shi yayi wanka ya shirya, suka fita a mota zuwa wajen Ammi, daga nan suka fice daga masarautar da magribar fari! *** Tun bayan fitar sa bata tashi daga wajen da take ba, sai da taji yunwa na neman kai ta k'asa, ta tashi ta jawo ledar da ya bari ta cinye ragowar,tasha ruwa ta kwanta a wajen.    Har wajen takwas na dare Hajiyan bata dawo ba, turo dakin akayi, ta dago tana kallon sa, tashi tayi zaune da sauri tana kare jikin ta, murmushi yayi ya zauna a kusa da ita, ya ciro wayar sa a aljihu ya rik'e a hannun sa yace "Zan kira miki Mama,dan ta kira tana son magana dake nace mata wayarki ce ta lalace, idan kika kuskura kika fad'a mata wani abu sai ranki ya baci." Banzan kallo tayi masa, ta warci wayar lokacin da taji tana ringing, bata jira Maman tayi magana ba ai tana jin ta daga ta rushe da kuka, "Lafiya Zeenat, wannan kukan fa?" Tace a kidime tana saka handsfree dan Habib yaji shima "Mama dan Allah kice wa Abba yayi hakuri na tuba, dan Allah!" " Ki nutsu ki fad'a min abinda yake faruwa, menene?" " Bana son auren nan Mama, dan Allah kizo ki tafi dani wallahi zan mutu!" " Mutuwa? Me yayi miki Bashir din?" Shiru tayi ta rasa me zata ce, dan bata isa ta fadi abinda ya faru tsakanin ta da Bashir din ba, a sanyaye tace " Mama yana da Mata, kullum sai ta sakani aikin wahala babu dare babu rana, ga tsangwama, karshe ma Mama a BQ nake wallahi." Sai ta sake fashewa da wani kukan,salati Mama ta saka, ta kama zagaye a dakin tana jin bayanin Zeenat din " Yana ina, bashi wayar." Tun kafin ta bashi ya karba yana mata murmushi, " Hello Mama." " Kana ji? Wallahi tun muna shaida juna da kai ka dawo min da 'yata, wannan ai wulakanci ne, wallahi ka dawo min da ita kafin kasha mamaki na." " Kiyi hakuri Mama, amma Zeenat matata ce,a yanzu nine nake da iko da ita,dan haka kiyi hakuri dai." " Kan bala'i, ni kake fadawa haka Bashir?" " Ayi hakuri Mama, gaskiya ce, sai mun sake kira mu gaishe ki." Kafin ta sake magana ya kashe kiran, ya kuma kashe wayar gaba daya ya jefa ta aljihun sa, yayi gaba zai bar dakin ta chakumo shi ta baya " Na rantse da Allah sai ka rabu dani,sai ka sake ni wallahi ba zan zauna ba, na tsane ka bana son ganin ka." Maganganun ta sun masa zafi kwarai, amma sai ya danne ya jawota ya hadata da bangon dakin, ya dalle mata baki sannan ya bi ta da kiss me zafi. "Idan kika sake yi min ihu wallahi sai nayi fata-fata dake, aure na dake babu saki ko yaji, auren mutukaraba kenan, ko nace miki auren zobe, idan bakiyi wasa ba sai na tabbatar miki da haka a yau din nan, ta hanyar zuba miki ajiyar da baki isa ki guje min ba." Tofar da yawu tayi ta durkushe a wajen tana sakin kuka gwanin tausayi. Tsallake ta yayi, yayi ficewar sa yana dariyar mugunta, yana son Zeenat din da gaske, amma kuma ba zai dauki rashin kunyar ta ba, ko kuma ya kyale iyayenta su taka shi ba, sai abinda yaga dama zai yi da ita tun da dai shine me iko da ita a yanzu. _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/8/22, 07:39 - Buhainat: Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._* *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb _________________________ 31     ×××Ya fada a can 'kasan zuciya yana yamutsa fuskar sa. Yanayin yadda ya yamutsa fuskar tasa ne hakan yasa Zaraah sake matse tata fuskar. Ta wulkita idanu ta dankara masa harara. Hade da kokarin bude murfin motar cikin fushi da takaicin sa. Ledar ya dora mata akan cinya. Tare da sake rufe murfin motar . "Budemun. "Ta fada a hankali. Hade da kaudar da fuskar ta zuwa kan murfin motar. Don sam batason kallon fuskar Maheer. Domin tamkar sudeis yayi kaki ya tofar. Saboda tsananin kamar da suke. "Tsiwar ki ta bude miki" Ya fada cikin muryar umarni . Ya kuma bata rai don karta dauka da wasa yake. ‘Kunkuni ta fara yi ahankali . Maheer ya saki siririn tsaki, “Dauka ledan ki fita. Kuma this should be the very last time da zaki tsallake dokata kinji na gaya miki.? Ya karasa ransa a matukar bace . Cikin zuciyar sa na masa zugi. “Toh ina ruwanka da rayuwata.? “Ni kike gayawa haka?? Yana kokarin jefa mata wani kallo mai dauke da kalamai. “Ni dai ka budemun na fita…? Ta karasa fada tamkar zatayi kuka. . Hade da sake kiciniyar bude murfin motar. Hannun sa d’aya ya dora akan nata da zummar hanata kokarin fitar da take. Wani Irin electric shock ne ya ziyarce ilahirin jikin su da kwakwalen su. Da sauri ya janye itama ta dauke nata hannun. “Dauki kayan ki fita . Kuma su zaki dinga amfani dasu wajen fita unguwa da sauran su. Kar ki kuskura ki kawo wani abun a zuciar ki. Amanar da dan uwana ya bani nake zartarwa.? Ya karasa hade da jan kasan leben sa ahankali . Lock din ya cire, Ta fice da sauri har tana tuntube. Ya sauke zuciya kawai hade da girgiza kai. Ya ja motar zuwa bangaren sa. Ya sha mamaki kwarai matuka wajen ganin masu aikin gidah nata rushe rushen bangaren nasa ana sake kawata shi. Zai yi magana kenan sai ga fitowar Addayo daga ciki. Fuskar ta kumshe da murmushi. Gayar da ita Maheer yayi ya na mata kallon karin bayani game da gyaren bangaren nasa. “Addayo? “Na’am na ikko dan albarka. Kaga bangaren ka ya fara sauyawa ko?? Ya daga kai alamar eh hade da susar keyar sa. “Toh me zaa jira, Aure an rigada an daura, Sai tariya kadai ta rage. Ina ita kishiyar tawa ne.? “Ta shiga sashen su.? “Yauwa inason ganin ku an jima da yardar Allah.? “Tohm Addayo! Saukar yaushe?? “Tun dazu fa nazo. Dan na tsaya gidan Harisu ne.? “Okay Masha Allahu.? “Allah ya maka albarka, Allah ya jikan mahaifan ku da dan uwanka.? Ta karasa fada tana mai goge hawayen dake tsiyaya a idanunta “Aaamen Addayo? Ya bata amsa yana runtse idanun sa. “Muje bangare na nan aka mayar maka da kayan ka kafin a kammala nan din.? “Toh Addayo.? Tana gaba da yar sandar da take dogarawa, Shi kuma Maheer yana biye da ita a baya yana tunanin yadda zasu kwashe da Zaraah idan suka tare. Dubada ganin su duka biyun ba kaunar junan su suke ba. Gwara gwara ma shi yakan ‘daga mata kafa awasu abubuwan saboda amanar ta da Sudeis ya bashi. ••?. ••?. Tana shigewa parlorn nasu bakinta dauke da sallama ta ajiye ledar hannunta akan kujera. Hadi da kwaye hijabin dake jikin ta, Ta ajiye a kusa da ita. Dadaa dake daki tafito tana jijjiga baby sudeis daya tashi a bacci. “Dadaa barka da yammaci.? “Barkan mu..? “Love of my life? Zo nan.? Ta karbu baby sudeis a hannun ta tana kallon sa. Har cikin bargon jikinta take kaunar baby Sudeis. Idan ta dauke shi ji take nutsuwa da kwanciyar hankali ta dabaibayeta. Dadaa na hankalce da ita, Ta zauna akan kujera hade da janyo ledar da Zaraah ta ajiye. “Wannan kayan fa?? “Yaya Maheer ne ya sayo? “Na waye?? Dadaa ta tanbayeta tana dudduba hijaban da su safa hadi da sabuwar wayar. “Wai nawa ne? ta karasa cikin kasa da murya. “Yauwa zo ki zauna anan Zaraah. Ki bani hankalin ki da nutsuwar ki. Abunda zan gaya miki abune mai muhimmanci a rayuwar ki. Kinga saura kwanaki kalilan ku fara jarabawar kare makaranta ko? Dan haka inaso kafin lokacin ki samu nutsuwa ki kuma sa aranki hukuncin da aka zartar akan ki shine mafificin alkhairi agare ki.? “Tohm Dadaa. ? Ta fada, Hadi da zama a gefen kujera . Tuni hawaye suka shiga reto a idanun ta. “Allah yasa ba laifi nayi ba Dadaa da aka yankemun hukunci? “Aa wallahi ko d’aya! Hasalima nina bada hadin kai wajen yanke hukuncin. Illa dai kiyi hak’uri na rashin neman yarjewar ki da bamu yi ba. Kina sauraro ko?? “Toh Dadaa. Ina ji? “Ba wani abu bane fyace daurin auren ku da akayi da Maheer. Maheer dai yayan Sudeis marigayi…? Dadaa na karasa fada, Maheer ya doka sallama ya shiga parlorn. Don sanarwa Zaraahn nema su da Addayo take? Zaraah ta daga idanunta da suke zama tamkar garwashi saboda tsananin yadda suka rine sukayi ja. Ta sauke akan Maheer. Hawaye d’aya na bin d’aya suka shiga kwarara a fuskar ta. Unedited Sorry for the late post Thank you ❤️❤️ *_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_* *ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA* *_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_* *GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi* *JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE* *_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_* *_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_* *_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_* *_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_* *_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_* *DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL* 2👉🏾400 3👉🏾500 4👉🏾700 5👉🏾1000 *Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin* 6019473875 MUSAA ABDULLAHI SAFIYA keystone bank Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number 08184017082 *IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU* 09134848107 *_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽 #team zafafa biyar XOXOWRITES🤩 2/9/22, 20:30 - Buhainat: Halin Girma       31 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ******* ? Lokacin da suka isa Abuja dare yayi dan basu suka bar Yola ba sai wajen karfe takwas na dare, sun dan samu delay ne shiyasa, direct Hotel suka nufa ta dinga masa magiya akan ya kaita gida amma fafur yaki, yayi mata kunnen uwar shegu har suka huta bata bar mitar ba, yi yayi kamar be ji ta ba, shima akwai gidan Bubu da suke sauka duk sanda suka zo ko shi yazo kawai akwai dalilin sa na zuwa nan din. Waya taga yana ta faman yi, da mutane daban daban duk akan maganar zuwan nasu, sai da ya gama tas wajen takwas da rabi sannan ya tashi ya nufi kofa ya bud'e, ya karbi sakon ya rufe ya dawo yana ajiye ledar a saman makeken gadon hotel din. "Tashi ki shirya akwai dinner da Chief of Army Staff, da sauran manyan soldiers na k'asa, a madadin wanchan event din kawai aka hada wannan dinner din kowa da family nasa." " Owk." Tace tana mikawa, ya nuna maya ledar da hannu yana shigewa toilet. Daukar ledar tayi me dauke da tambarin wani babban Mall, ta bud'e doguwar riga Abaya ta gani me kyau, ciro ta tayi tana ware ta, sosai tayi mata kyau ta ajiye a gefe ta ciro sauran tarkacen kayan hadda wata kar karamar jaka da tafi kama da purse sai takalmi hills amma ba chan ba. Shiryawa ta hau yi tana yi tana kallon toilet din har ta gama be fito, ta matsa wajen yar trolley dinsu da ciro perfumes ta faffesa sannan ta zauna tana dauko wayarta da take haske alamun kira ne ya shigo, Mamma ce, tasan cewa zatayi taji su shiru,ita kanta batayi tunanin nan din zasu zarto ba dan tasan an gama shiryar su kada ma Mamma taji labari tasan ba zata huta ba har sai sun iso. Dagawa tayi daidai lokacin da ya fito daga shi sai gajeren wando, faffadan kafadarsa ta kalla da take a mummurde, ta sauke kanta tana jin wani yanayi da bata san na menene ba, a gabanta ya tsaya yana rik'e k'ugu, yana, hannun sa daya rik'e da karamin towel, ganin ta dauke kai kamar bata ganshi ba, ya saka shi yarfa mata ruwan da yake hannun sa a fuska, yi tayi kamar zata tashi amma da daure ta cigaba da wayar, ta bawa Mamman hakuri yana ji ta gama ta ajiye wayar tana tashi da sauri. "Kinyi kyau Matar Muhammad." "Nagode." Tace a kunyace bubbude hannayen sa yayi, ya ja baya yana tattare fuskar sa. "Shirya ni..." "Na'am?" "Eh ki shirya ni, ki shafa min mai ki saka min kaya..." "Kamar dan baby?" "Toh da mene? Ai babyn naki ne ni." Dariya ta saka tana sake gyara zaman ta "I'm serious fa, kinga we are running late, kar suyi ta jiranmu." Ganin da gaske yake, ya sakata tashi ta dauko man, ta shiga shafa masa yana lullumshe ido, da gangan ya dinga sata komawa baya yana cewa be yi ba, nan fa. Da dai daga alamun so yake ayi tayi sai ta tattara man ta mayar, ta dauko masa suits din da ta gani tare da abayar ta, ta mika masa ya noke yana sake bararrajewa. Girgiza kai tayi, ta shiga saka masa, yana sake narke mata kamar wani karamin yaro a gaban mahaifiyar sa, sai data gama tas ya rage saura necktie sannan ya karba ya karasa sawa a gaban mirror, ya kalli kansa yana hango ta ta cikin mirror din,da hannu yayi mata alamar tazo, ta tako ta tsaya daga kuibin sa, ya matso da ita jikinsa yana kara kansa a jikin fuskar ta. "Perfect!" Yace yana dariya, wayar sa dake kusa da wajen ya dauka, yayi musu hoto me kyau a gaban mirror din, sannan ya daga kiran da George yake masa. "We are on our way." Kawai yace ya katse kiran, ya rik'e hannun sa cikin nata suka fito, duk da suka hauro reception din suke shan kallo, tana jin shi yana jan tsaki k'asa-k'asa har suka shiga wajen da yake a cikin hotel din ne dalilln da ya saka ma suka sauka anan din kenan saboda already an riga anyi booking dakin tun kafin ranar ma. Duk in da suka wuce sojoji ne a tsaitsaye sun yi shirin ko ta kwana, cikin girmamawa suke gaida su, har suka kai babbar kofar shiga wajen.        Wata iriyar kunya ce ta dabaibaye ta lokacin da suka shiga wajen, mutane ne masu yawa kai kace wani gagarumin biki ake, kowacce kofar shiga wajen dankare take da jami'an tsaro, ji tayi ido yayi mata yawa, gashi duk sun tashi da shigowar su. Mafiya yawancin su ba hausawa bane, sai yan daidaiku da tayi hangowa daga in da take. Wajen zaman su waitress dake tsaye a wajen ta nuna musu, basu wuce chan ba kai tsaye sai da suka je wajen manyan kusoshin, suka kwashi gaisuwa in da taga yayi wata irin gaisuwa tasu ta daban, sannan suka samu wajen zama suka zauna sai a lokacin ya sakar mata hannu. "Sannu Amarya!" Wata bahaushiya a kusa da ita tayi mata magana, amsawa tayi tana maida mata murnushin da tayi mata, sai kuma suka gaisa da sauran matan wasu hausawa wasu ba hausawa ba, kafin kuma a fara gabatar da abinda ya hada su.   Captain Is'mail ne a gaba gaba akan komai shi da George, su ne ma organizers din event din shiyasa ko zama sun kasa yi, har sai da lokacin cin abinci yayi sannan suka zauna shima na wucin gado,ana gama ci aka cigaba da gudanar da event din. Sun sha kyaututtuka sosai har sai da Iman ta gaji da karba, idon ta yayi nauyi kwanciya take so kawai yayi, yana lura da ita, yasan ba karamin aikin su bane su kai fiye da biyu a wajen babu kuma wanda zai damu, ita kuwa akwai rashin sabo, tashi yayi yana zura hannunsa cikin aljihun wandon sa, ya nufi wajen da Is'mail yake ya jashi gefe, yayi masa magana kana ya dawo wajen zaman sa ya zauna. Sai da aka kara kamar mintuna ashirin sannan isma'il din ya bada sanarwar amarya bata jin dadi zata je ta huta, da haka suka samu suka sulale daga wajen suka nufi masaukin su. Dukkan su a gajiye suke dan haka babu abinda suka kara bayan sauya kayan jikin su sai bacci, cikin kankanin lokaci bacci yayi awon gaba dasu.     Da wuri ta tashi, ta shirya ta zauna tana duba lokaci, baccin sa yake tsakanin sa da Allah tun bayan dawowar sa sallar asubah gashi ta matsu ta ganta a gidan, gashi babu alamun zai tashi har past 10, an kawo musu breakfast daga reception din taci kad'an ta ajiye masa sauran ta cigaba da zaman jiran sa. Wasa wasa lokaci ya dinga ja, babu abinda yake sai chanja kwanciya da juyi daga nan ya koma nan cikin jin dadin baccin. Ganin da gaske ba zai tashi ba, ya sakata zuwa daidai saitin kansa, ta dan rankwafa da niyyar tashin sa, hannu takai kan sajen fuskar sa, ta taba kadan, juyi taga yayi ya sake maida kansa dayan barin, sake durkusowa tayi ta bayan nasa ta kai hannun ta jikin sa, kam taji ya riko hannun ya makale shi tsakanin hannun sa da jikin sa, ja tayi taji ya makale shi kam, gashi sauran kad'an ta fado kansa gaba daya, dayan hannun ta saka ta taba shi, "Please ka tashi zamu makara." "Uhum..." Yace cikin muryar dake cike da nauyin bacci, ya sake kankame hannun nata a jikinsa wanda ta jawo mata fadawa kansa ta gefe daidai saitin bayan sa.    Sun jima a haka tana jin shi yana fitar da numfashin bacci, kafin yayi motsi ya bud'e idon sa da suke cike da bacci sosai, ya juyo bangarenta yana sakin hannun nata. "Ka tashi dan Allah." "Um um..." "Ka manta zamu fita?" Da kai ya amsa mata da eh, kokarin tashi tayi zaune ya daddanne ta, ta hanyar dora kafarsa a jikin ta "Kinsan fa jiya bamuyi wani bacci ba, please muyi bacci idan muka tashi sai mu fita." "Past eleven fa, please please please." "Ohhhh! Ni dai gaskiya, gaskiya bacci nake so nayi, anjima sai muje idan mun tashi, bari kiga." Ya sake kadannade ta da kafafun nashi da sukayi mata nauyi ta kasa janye su,gani tayi yana maida idon sa zai rufe tayi saurin rik'e fuskar sa "Dan Allah!" "Shikenan." Yace yana sauke kafarsa, ta samu ta mike tana murmushi "Amma da sharadi, ke zaki min wanka ki shirya ni, ki kuma bani abinci a baki." "Ahhhh." Ta bud'e baki cike da mamaki "Fine, bari na koma bacci na sanda na gama mun fita." Da sauri ta rik'e blanket din da zai sake rufa "Zanyi." "Good girl."   Yace yana mata murmushin mugunta. Janye blanket din tayi, ya zuro kafafun sa k'asa yana mika mata hannu, kama hannun tayi ya tashi, yayi kamar zai fadi ya fado jikin ta, nauyi sosai taji, amma ta daure dan taga take taken sa zai iya cewa ya fasa, a haka suka isa toilet din, ya zauna a gefen bathtub din ta hada ruwan, ta dauko masa brush da toothpaste ta matsa masa ta bashi, kin karba yayi ya bud'e mata bakin wai tayi masa, sake mika masa tayi ya noke yana tashi alamun zai bar toilet din, da sauri ta riko shi, ya koma ya zauna ta fara yi masa, dariya ce take kamashi amma ya kanne, yadda ta daddage kawai zai baka dariya, hannun sa ya dora a saman nata ya karbi brush din, ya karasa, ya bata ta cilla shi a dustbin din toilet din daga nan tayi hanyar fita "Kina fita zan fito nima." Tsayawa tayi ta dawo tana tura baki, ya hau cire kayan sa a gaban ta, tayi saurin juyar da kanta, murmushi yayi ya shiga ruwan da yayi masa daidai da yadda yake so, sai data tabbatar ya shiga ciki sannan ta juyo tana cigaba da dauke kanta ta dauko sponge da sabulu ta bud'e ta ajiye a dan wajen da aka tanada, zama tayi a gefen bathtub din,  taki kallon gefen sa ta juyar da kanta gaba daya hanya, bata yi aune ba taji ya jawo ta cikin ruwan, ta saki kara, ya hade bakin su waje daya ya hana karar tata tasiri.    Sai da suka bata lokaci mai tsawo a ciki sannan suka fito, ta dinga turo baki tana jin kamar tayi masa kuka, ta riga ta gama shiryawa tsaf har kayan da ta saka dama su tayi niyyar sawa amma ya jawo sai ta sake sabon shiri, a wajen shiryawar ma haka tayi ta fama dashi da ya janye mata towel ta nan sai ya janye mata ta nan haka dai yayi tayi har sai data gama cika fam, zata fashe kafin ya kyaleta su shirya a nutse.    Kasancewar ciki da falo ne dakin, sai tayi ficewar ta, ta barshi a ciki yana karasa shiryawa ta hada masa breakfast din ta ajiye da yazo ci kawai zai yi su tafi. Da waya a makale a kunnen sa ya fito, yayi zaman amsa wayar da ta fuskanci da Musaddik suke magana, sai da ya gama wayar tsaf sannan ya jawo abinci ya soma ci a yangace kamar ba jiran sa take ba, bata dai ce komai ba, ya gama duk bata lokacin da zai yi, sannan ya tashi yana goge bakin sa da tissue. Tashi tayi itama dama tayi ready har da jakarta a kusa da ita, gaba yayi ta bishi a baya, ya murda kofar sojan da yake jiran sa a wajen ya karbi Notepad da wayoyin sa, shi kuma ya zuba hannuwan sa a aljihu suka shiga takawa zuwa wajen da aka tanadar domin parking motoci.    Bud'e mata kofa yayi, ta shiga ya rufe sannan shima aka bud'e masa nasa bangaren ya shiga suka fita daga harabar hotel din! Bashin Jiya....so sorry banajin dadi ne _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/12/22, 11:07 - Buhainat: Halin Girma       32 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw *******? Address din drivern ya dinga bi har suka isa gidan, tun kafin motar ta gama daidatuwa a harabar gidan take kokarin fita, chapko ta yayi yana bata fuska "I'm jealous!" Da mamaki dake kallon sa "Yes I'm jealous, I want my share of love too, inaso naga same action na murna anytime mukayi nisa da juna, inason soyayya, inaso a gatata ni, aji dani sannan a damu dani please." Dariya ma ya bata, ya saki hannun ta yana sake bata fuska shi a lallai yayi fushi, girgiza kanta tayi cikin muryar lallashi tace "I'm so sorry toh, kawai I'm eager ne, ban wani zauna dasu sosai ba, shiyasa kawai." "Shikenan reason din?" "Shikenan, ko baka so naga Mama ta? Kullum fa kai kana tare da Ammi fa, nifa?" "Ba haka bane, banda Mummy ai nake nufi, Mamma, Amaani, Amaan and rest, su nake kishi dasu." Dariya ta sake yi, ta rik'e kofar ta bud'e, ya zuba mata ido kamar bashi da niyyar fitowa, sai da tayi masa alamar da hannu sannan ya bud'e ya fito ta dayan side din, yana karewa gidan kallon.    Kofar shiga part din suka nufa, yana biye da ita a baya hannun sa sakaye a cikin aljihun sa, daf da zasu kai kofar ta bud'e, Amaani ce a gaba da shegen gudu, tayi kanta tana ihun wallahi itace, kamar zata kada ita, sai da k'yar ya nutsu tana numfarfashi, hango shi da tayi a baya sai kawai tayi wajen sa , ta rik'e masa hannu ta fara zuba masa surutu kamar tayi shekara da sanin sa. Cike da sha'awa yake duban ta, ta rik'e shi gagam har ciki tana bashi labarin da be gane kan sa ba.   Mamma ce ta fito daga wani corridor, tana sanye da lullubi akanta, fuskarta cike da farin cikin ganin su, "Sannun ku da zuwa." Tace sanda ta karaso falon, idon ta akan Iman dake zaune da Amaan a kusa da ita. Russunawa yayi cikin ladabi ya gaida Mamma din, a daidai lokacin Mummy ta fito itama, ya gaishe ta a kunyace dan kallo daya yayi mata yaga tsantsar kama da Fatin sa, amsawa tayi ita din ma a yanayin kunya irin tamu wadda aka gada tun iyaye da kakanni. Iman ce ta gaishe ta,  ta amsa daga tsaitsaye ta juya ciki, murmushi kawai Mamma tayi dan tasan yadda ta matsu da zuwan nasu, amma ba zata taba nunawa ba, yadda tayi zaka dauka ma bata damu ba sam,nan kuwa tsantsar kara ce irin tata da har take nema tayi yawa.    Abinci aka shiga jere musu, yayi mata alama da ido akan tafiya zai, ya dauki bottle water guda daya ya mike yayi musu sallama akan zai dawo, mamma ce ta hau korafin me zai sa ba zai tsaya yaci abinci ba, hakuri ya bata akan zai dawo akwai wanda yake jiran sa ne. Shikenan tace ya fice ta harari Iman "Haka ake wa miji? Tashi mana kije kiji." Tashi tayi tana dariya, ta bi bayan sa ta same shi har ya kai wajen mota, tsayawa yayi ganin ta fito ya choge jikin motar sai data karaso sannan ya shiga, ya sauke glass din motar yana kallon ta "Kwana zanyi ko?" "Inji waye? Da yamma zan dawo zuwa magriba." "Dan Allah..." Girgza mata kai yayi tun kafin ta karasa. "Zaki dawo next time, sai na dawo bye." Ya daga glass din ta dan ja baya tana kallon motar har ta fice daga gidan, kamar zatayi kuka haka taji, taja kafarta a hankali ta koma ciki ta samu Mamma ta zuba mata abincin mummy kuma ta dawo falon ta zauna tana wa Amaani fad'a akan rawar kanta.    Taji dadin zuwan ta gidan sosai, kamar tayi ta zama haka taji, amma tasan tun da yace zai dawo toh zai dawo din, amma taso ya barta ko zuwa da safe ne sai yazo su tafi ko ya turo a dauke ta.   Ta idar da sallar magriba kenan a dakin Mummy, Amaani ta shigo tace ya dawo, har ga Allah taji babu dadi, ta tashi ta nannade sallayar ta ajiye a gefe ta zauna a saman sofa tana ciro wayarta. Tana zaune har wajen minti talatin babu wanda yazo kiranta, har ta kishingida sai ga Mamma ta shigo, tace ta tashi su tafi yama fita, "Na zata zai barni na kwana." "Kul... Dududu yaushe akayi auren? Kar ma ki soma yi masa maganar kina ji na? Watarana da kanki zaki zo ma" " Wuce muje kar suyi ta jira." Tace tana sakata a gaba suka fito falon, uban kaya ne jibge a gefen falon dangin su shinkafa kayan abinci dai masu yawa, Mummy na zaune tana juya kudi a hannun ta " Kinga wahalar da yayi ko? Kiyi masa godiya nace ba za'a karba ba amma ya dage dole." Tayi maganar tana ajiye kudin a saman center table, bin kudin Iman tayi da ido wanda a kalla zasuyi hundred thousand, sai kayan abincin da yake a dankare awajen, jinjina kanta tayi cike da mamakin sa, ko alama be nuna mata ba balle ta gane shirin sa, dadi ne ya kamata ta fito bayan sun yi sallama da Mummy tana zuba masa ido ta cikin hasken compound din gidan, duk da motar tint ce, amma tana iya hango inuwar sa, cike da karsashi ta karasa wajen motar, dai-dai lokacin da kofar ta bud'e, ta shiga da sallama tana dagawa su Iman hannu.    Suna fita daga gidan ya matso kusa da ita cikin lallashi yace "I'm sorry na hanaki kwana, kinga gobe da wuri zamu tafi amma next time da kaina zan kawo ki har sai kin gaji." "Laa ba komai fa, dama wasa nake yi, su Mamma ma ba zasu barni ba ai, wai dududu yaushe akayi auren?" "Haka suka ce ko?" "Eh..." "Yawwa kin gani." "Babu komai fa, ni nama manta ma ma na tambaya, I'm sorry." Ta kama kunnenta, zare hannun nata yayi yana jawo ta jikinsa. " Thanks dear." **** Washegari suka dauki hanyar Kano, tun kafin su isa an gama gyara musu gidan su, dama dai ba wani baci yayi ba saboda akwai masu aiki da kula da gidan banda sojojin da suke waje suna gadi, suna isa ya fice tare da Musaddik, anan ta tarar da uban kayan lefen ta, tayi zaman kallon su cike da mamaki, idan kaya na yawa toh ita dai sun mata mugun yawa, ya zatayi dasu? Shine kuma har da siyan mata wasu kayan saboda dai ba'a san wahalar kudin ba. Gajiya tayi da kalla ta saka masu aikin suka kwashe su, suka maida su wani daki guda kafin ta kira Mamma taji abinda ya kamata tayi dasu da mutanen da ya kamata a bawa.    Slippers ta zura ta zazzagaya gidan nata, wanda yasha kaya na alfarma, har da wani babban garden a baya da pool daga chan gefe shima, gidan yayi kyau amma yayi girma ace mutum daya kwal dan ma ma'aikata masu yawa wanda yawanci daga masarauta suke sai wanda aka turo su daga adamawa. Daki ta koma ta haye gado tayi kwanciyar ta dan bata jin yunwa tasha cornflakes suna zuwa sai kawai ta kwanta da niyyar ta tashi wajen azahar ta dafa masa simple dish dan wata gajiya take ji na nukurkusar ta.    Ta jima batayi irin baccin da tayi ba, ga sanyin AC da kamshin fresheners masu dadin kamshi da ya cika dakin, hakan ya kara taimaka mata jin dadin baccin sosai har sai da taji ana mata knocking sannan ta tashi bakin ta dauke da addu'a ta yane kanta ta fito ta bud'e kofar, daya daga cikin masu aikin ce Atine, ta russuna ta gaishe ta sannan tace tayi baki ne a falo. Ok tace ta rufe kofar ta koma ta gyara fuskar ta, ta fesa turare ta dauko wayarta ta fito. Yan mata ne su biyu kyawawa dasu masha ALLAH, suna zaune suna kallon TV ta fito, "Sannun ku da zuwa." "Yawwa." Suka amsa a sake, suka gaishe ta sannan suka gabatar mata da kansu "Fulani ce ta aiko mu, kayan gara ne dangin su alkaki dasu bakilawa da dublan, sai gireba da sauran su, tace gashi nan zaku iya tayin baki tunda kun dawo." "Kai mun gode sosai, Allah ya saka da alkhairi." Ta tashi ta bubbude, ta dawo ta zauna tana murmushi ta sake godiya, aikin gidan mace ne kayan gara amma basu bari anyi mata ko daya ba, dama tasan dai ko za'a yi sai dai a gayawa su Mamma suyi mata sai gashi sunce ba sai anyi ba,itama yar su ce kamar Muhammad din.    Hira sukayi sosai tun tana nokewa har ta saki jiki dasu dan suna da hira ga faram faran kamar sun saba. Tare suka ci abincin da suka zo dashi alkubus da miyar taushe, suka bita kitchen da zata yi ma Moh dan abincin sa, suka tayata sai yamma suka tafi, bayan sun mata alkawarin zasu dawo basa so ya dawo ya same su dan tsaf zai kore su, jin su kawai tayi dan batayi tunanin zai aikata ba, bata san yadda yake tsare musu gida da daure fuska bane shiyasa har yake mamaki dan sun ce ba zasu zauna ya same su ba.    Suna fita kuwa sai gashi ya shigo, yaga fitar motar su amma basu tsaya ba suka kara mai. Bud'e hannun sa yayi ya tsaya daga jikin kofa, ta tafi a sanyaye ta fad'a jikin sa, ya rungume ta yana shafa kanta. "Sannu da zuwa yallabai." Ta karbi rigar hannun sa suka rankaya cikin falon, sai da ya zauna sannan ya amsa mata sannun ya dora da "Baki kikayi?" "Su umaima ne, daga chan gida aiko su." "Yan rawar kai, tun yaushe suka zo?" " Wajen twelve din rana." " Ah kice kin samu yan hira ko nace yan surutu dan bakin su sam baya shiru." " Naji dadin zuwan su kuwa, sun tayani hira ai." " Sun kyauta da suka tafi kafin na dawo, dan tsaf zan saka yarinya frog jump ba abinda ya damen." Ya fad'a yana kai cup din ruwan da ta zuba masa bakin sa, " Da gaske wai?" " Da gaske mana, suma sun sani ai, kila ma sun fada miki ko?." " A ah." Tace tana dariya " Ya yau din? Ya gidan naki?" " Alhamdulillah, komai yayi Masha ALLAH, Allah ya kara arziki, thanks for everything, " Amin Amin, I'm glad you like it." Yace cikin jin dadin addu'ar ta " I love it!" " Masha ALLAH." ***Tun ranar farko da Bashir ya samu damar shigowa dakin har yayi abinda yayi, tun daga lokacin duk dare sai ya lallabo, ranar farkon tana jin su suka haura sama da uwargidan tasa suka fado, sai da k'yar suka daidaita dan shima jan wuya yayi mata ganin idan ta biye masa zai iya cewa su rabu yasa ta kyale shi, taga kansa rawa yake ya samu yarinya karama shiyasa ta kwantar da kanta ta cigaba da bin sa tana so taga iyakar limit din iskancin nasa, tasan sarai yana zuwa dakin da dare amma ta share bata taba nuna masa ba, wani zubin ma akan kunnenta komai yake faruwa amma ta daure dan plan dinta akansa ba na yanzu bane, shigo shigo babu zurfi tayi masa sai ya gama sakankancewa zatayi maganin sa.    Ranar ma kamar yadda ya saba kawo mata waya suyi magana da Mama haka ya kawo mata, ta karba tana daga kwance da babu wani aiki da takeyi yanzu matar gidan ta rage takura mata, dattijuwar me aikinta da ta tafi gida ta dawo shiyasa aikin ya rage mata sai dai taci ta kwanta ga uban kasalar da take fama dashi ga shegen nacin Bashir da yake hanata sakat, tana shan wuya sosai a hannun sa dan baya daga mata kafa ko kad'an, tun tana masa rashin kunya har tazo ta kyale shi yayi uwar da zai yi, ranar da zata samu hanya kawai take nema wallahi ta tafi ba zata dawo ba ko me za'a yi mata kuwa.   Wayar ya mika mata bayan ya gama amsawa da toh, suka gaisa da Mama ta take fad'a mata haihuwar Aunty Bilki, tayi murna sosai ana take jin gobe suna kuma a gidan su za'a yi sunan saboda akwai fili sosai "Ki lallaba shi ya kawo ki na dai gaya masa." "Toh shikenan, zan kira." Ta katse wayar ta mika masa "Dan Allah ka barni naje suna gidan mu gobe." "Ki shirya da safe zan mika ki sai na wuce garari na, idan na gama sai nazo mu dawo." Yace ya sa kai ya fice da bishi da kallon mamaki, bata taba tunanin zai yarda haka kai tsaye ba, murna ta hau yi ta dinga zagaye dakin tana jin kamar wahalar ta, ta kare kenan dan ko giyar wake take sha idan taje gida ba zata dawo ba sai dai Abba ya kashe ta.   Murmushin mugunta yayi yana barin dakin, shi kadai yasan tsiyar da ya shirya ya kuma tabbatar da ko taje gidan toh sai ta dawo da kanta ko Maman ta sakota gaba ta dawo da ita. ***Waya suka gama yi da Ya Maryam ta cigaba da shiryawa a tsanake saboda safiya ce, sannan yace ta jira shi ya fita toh dole sai ya dawo zata tafi, tana so taga Abban ta da Marwan da Gaji da sauran yan gidan, shiyasa ta tashi tun wuri ta hau shiryawa yadda zata samu zuwa da wuri ta dade kuma.    Tana zaune taji shigowar motocin sa, ta yaye curtains din dakin ta ga wasu motoci guda biyu da bata san su a gidan ba, sakin labulen tayi, ta sake fesa turare ta fito suka hadu a falo.    Tafi ya shiga yi mata dan ba karamin kyau tayi ba, lace ta saka me orange da black yayi mata kyau ya dace da kalar ta, zaunar da ita yayi ya dauke ta hotuna masu kyau sannan yace idan ta gama ta ga driver nan idan yaso zai zo da daddare su dawo tare. Jakar ta, ta dauko ya rakota har wajen motar ya bud'e mata ta shiga, sannan suka fita daga gidan yana tsaye yana kallon su. Tasa motar ya fad'a shima ya bar gidan dan yana da important abun da zai yi. A daidai lokacin Zeenat suka fito da Bashir, ya kunna machine din da ya aro a wajen abokin sa dan Hajiya ta fita da motar ta, kamar tace ba zata hau ba, sai kuma ta hau dan bata da ko biyar din da zata dauki adaidata sahu, tunanin idan taje gida ta karbo masa sam be zo kanta ba.   _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/12/22, 11:31 - Buhainat: Halin Girma       33 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw *******? A kusan jere suke tafiya da motar Abba da Habib ke ciki shida mama, kasancewar tint ce ya saka basu gane Iman din bace a ciki, suna shigowa layin su Habib ya sake kallon motar yace "Ina tunanin fa Iman ce a motar nan." "Wacce motar? " Mama tace tana waigawa, gabanta ne ya fadi ganin dalleliyar mota a bayan su, " Ta ya akayi ka sani?" " Number na duba. " Ya amsa mata yana tsayawa a daidai kofar gidan, daidai lokacin motar Iman din itama ta tsaya, yayi daidai da isowar Zeenat a saman machine din Bashir. Mutuwar zaune Mama tayi ta kasa bud'e murfin motar balle ta fito, idon ta yana kan motar da ta gama gane wacece a ciki, ta saitin ta Bashir ya zagayo bayan ya faka machine din, ya leko yana cewa " Sannu da zuwa Mama. " Wani abu taji, ta kalle shi a kaikace kamar ta falla masa mari, tayi dauriya ta danne zuciyar ta ta amsa tana jan kofar ganin yana kokarin bud'e mata, matsa wa yayi ta fito idon ta akan Zeenat da tayi wani irin haske, hasken da tana kallon ta, ta gane na menene, kamar wadda aka sage wa guiwa haka ya shiga jan kafarta zuwa cikin gidan, suka rufa mata baya a jere Iman din na magana da Zeenat da take ta kokarin maida hawayen da take jin zasu zubo mata wanda bata san dalilin su ba "Ashe zaki zo?" Tace a sanyaye "Wallahi, ya gida? Ko waya bamuyi ba." "Wayata ta lalace ne. " " Ayya." Kawai tace suka karasa ciki, nan da nan mutanen dake harabar gidan sukayi kan Iman, kowa so yake ya ganta, duk sun rude babu wanda yabi ta kan Zeenat, ganin haka yasa ta sulale ta gudu bangaren su, ta samu Mama a zaune tana kuka wiwi, kukan bakin ciki, kukan dana sani da aka ce keya ce wadda bata da amfani, ta tuna watarana da aka zo akayi sallama da Iman, ranar ce ta farko da aka fara zuwa kuma wajen Iman din, tun basu kai yanzu ba, da kanta ta saka Hijab ta koreshi irin korar wulakanci, ba tare da kowa ya sani ba sai Habib, wanda bayan ta kore shi ne Habib yake gaya mata waye shi, da kuma gidan da ya fito,. Tun daga lokacin ta dauki alwashin dakushe Iman din, ta kara maida ita mara yanci cikin rashin sanin cewa gata tayi mata, babu in da zata shiga rayuwa ta bata wahala musaman irin abubuwan da suka shafi kula da gida.    Taba ta Zeenat tayi ganin sai sallama take amma bata amsa ba, firgigit tayi tana dawowa tunanin ta, suka rungume juna Zeenat din ta fashe da kuka, bata hanata ba, sai da tayi me isar ta dan tasan kukan zai rage mata abinda take ji, gwara ace kishiyar uwa ke gallaza maka akan ace kishiyar ka ce zata hanaka sakat da sukuni, abinda tayi ne ya juyo kanta amma ta siga ta daban, sigar da bata taba tunani ko tsammani ba.   Yan uwan Abba ne suka biyo Zeenat din har cikin gidan nasu, da mitar me ya faru zata shigo ta wuce su babu ko gaisuwa, Mama na jinsu bata ce komai ba, dan tasan da biyu suka zo maganar, tana jin Zeenat din tace suyi hakuri, wanda ya saka su jin nauyi da kunya kuma, suka tafi cike da borin kunya.   Suna fita Iman ta shigo, ta russuna har k'asa ta gaida Mama kamar yadda ta saba, ko ba komai ita a uwa take kallon ta, dan itace tayi mata komai na mahaifiya idan aka cire shekarun haihiwa zuwa yaye, ita ta sani, ko ma menene dai tayi mata wani abu.   A chunkushe ta amsa, har yanzu akwai haushin Iman din a zuciyar ta, wanda bata jin zata daina sai ko ranar da ta bar duniya, har gobe tana kallon Iman din ta tuna cin amanar da akayi mata, wanda take ganin da gaske Itace baa kyautawa ba.    Ta dan zauna a bangaren nasu, babu me magana a cikin su, sai jefi jefi da suke magana tsakanin ta da Zeenat wadda take cike da mamakin sauyawarta, tayi sanyi sosai kamar ba ita ba, ta kuma hangi wani abu a idon ta, da take da yakinin damuwa ce. Tashi Mama tayi ta barsu a falon tayi shigewarta daki, domin ta samu damar yin tunanin abinda ya kamata tayi akan auran Zeenat din.    Bin ta Zeenat tayi, ganin haka ya saka Iman ficewa ta koma bangaren Gaji in da anan me jegon take, ta shiga yan uwa aka cigaba da kuranta ta da yaba ta, kowa yana so ya samu ya kafa kansa ganin cewa yanzu ta wuce duk wani matsayi ta kai in da basu taba tunani ba, shiyasa kowa yake kokarin chusa kansa dan idan wata dama ta taso ko da ta aikin Hajji ne, toh Iman din zata tuna da mutum.    Wajen azahar sai ga Yaya Maryam tazo, sai da ta biya ta asibitin da take ANC sannan ta tawo shine dalilin rashin zuwan nata da wuri. Jan Iman tayi suka koma gidan su, suka zauna su isu matasa aka hau hirar aure da yadda rayuwar auren take ma baki daya, sosai Iman take daukar haske, tana karuwa da wasu abubuwan tunda sun fita jimawa, bata saka musu baki ba, a tunanin Yaya Maryam ma bata jin su, nan kuwa ta haddace komai akanta.    ***Tare suka shigo da Musaddik, wanda kallo daya zaka yi musu kasan a gajiye suke sosai, babu wanda yayi magana sai da suka huta sannan ne Musaddik ya mika masa wayar sa da ake ta faman kira tun suna hanya, karba yayi ya daga yana kishingid'a a saman kujerar "Ya akayi? Kun duba yadda abun ya samu kansa a cikin part din?" "Mun duba dukka CCTV footage na gaba daya area din, bamu ga kowa ba a kusa da wajen ma, har zuwa kofar shiga shashen, falon kuma babu CCTV kasan, time da za'a saka kace baka so. " " Na sani, shikenan ba damuwa. " Yace yana zare wayar daga kunnen sa, ya ajiye yana murmushi wanda ya saka Musaddik kallon shi " Akwai wanda yake so yayi wasa da hankali na, ko ma waye yasan babu cameras a ciki, target din su iya na wajen ne kawai. " " Me kake tunani? " " I can't say exactly, amma dai akwai wani abun daban ba sarauta ba, ko ma waye yana da matsala da aure na, ba sarauta ba. " " Laila fa? " " Ba ita bace. " " Toh me zasuyi benefiting anan, ban gane komai ba. " " Guy, baka san wanne irin mutane ne suke zagaye da gidan nan ba, da kuma kudurin kowa, zaka sha mamaki amma. " "Ka sansu? " " Almost.. " " Then why are you allowing them to walk over you? Bayan kana da duk damar da zaka yi musu abinda zakayi to get rid of them. " " Ba zai yiwu ba, this is not a military war, wannan fad'an ba ma makami bane, ko na gwajin kwanji ba, sai ka zama very very careful da duk moves dinka, akwai bakin ciki a gidan sarauta, akwai kyashi, da hassada. Masu son kujerar ba mutane bane yan kad'an, suna da yawa kuma kowa zai iya komai domin ganin ya samu abinda yake so" Gid'a kai Musaddik yayi yace " It's harder than i thought. " Murmushi Moh yayi, ya hade hannuwan sa waje daya, suka fitar da sauti me dan kara, ya mike yana zuba hannayen sa cikin aljihun sa "Muje naga Takawa." "Owk." Yace ya mike suka fita ***Be samu ganin Takawar ba kamar yadda ya saka rai, ya zauna zaman jiran sa dan yana so ya nema masa alfarma akan tafiyar da za'a yi akan wani aiki gashi har da sunan sa, baya son yayi nisa da gida dan a kalla zasuyi wata guda cif, yasan idan ya samu Takawar ya kira waya za'a iya cire sunan sa, duk da tun daga last yace ya daina nema masa alfarma, tun da shi yaji ya gani dole ne yabi dokar aiki, sai gashi ya dawo yanzu be kuma san yadda zata kaya musu ba, shi kansa kunyar neman alfarmar yake amma kuma baya son tafiya ya bar Iman ita kadai bata gama sanin komai ba.    Har sukayi la'asar suka dawo Takawan be dawo ba, cigaba da zaman jiran sa sukayi Muhammad har da dan baccin sa,ya bar Musaddik yana kallo dan dama shi mayen kallo ne. Sai goshin Magriba sannan suka ji dawowar sa, alwala suka daura suka fita zuwa masallaci aka yi sallah,.    Yadda ya dawo da irin wannan lokacin dama babu wani zama da zai kara direct ya wuce gida dan yana bukatar ya huta sosai.    Shawara sukayi akan kawai su dawo gobe da wuri kafin ya fito zaman fada. Da wannan shawarar sukayi amfani suka tafi, suka wuce kai tsaye gidan su Iman daukota. A ransa ya kuduri zai kaita ya nuna mata dakin da ya zauna har ya kwana aciki saboda ita! ***Akwai Yayar su Abba da take turai tare da iyalin ta, sukan dade basu zo ba yawanci sai dai waya suke yi, akwai dan ta Mahfuz zai yi sa'an su Habib ko ya dan d'ara su da kadan, duk ciki shine me zumunci me son dangin sa, tun da ya girma idan ya samu lokaci ya kan zo yayi wata biyu ko daya ya koma, karshen zuwan da yayi ya jima sosai be dawo ba, sai wannan lokacin da yazo. Yaso ya samu bikin da aka ce masa za'a yi, duk da ba wani sanin su yayi ba saboda yawansu sai kuma aka samu yar matsala da ta dakatar da zuwan sai yanzu. Yana da wasa sosai da sakin fuska , abu daya yake hada shi da kowa shine yadda dabi'un sa da al'adun sa suka sha banban da na Malam bahaushe, gashi dama bahaushe ko yaya ka kuskure wajen al'ada wadda ba irin tasa ba be kuma karbe ta ba,toh fa zaka samu matsala dashi. Hakan ce ta kasance ga Mahfuz, yadda yake mu'amular sa tasha banban da tamu, dole ne za'a ga banbanci wanda shi tsakann sa har ga Allah ba da wani abu yake ba   Tun da ya shigo falon ya dora idon sa akan Iman ya kasa daukewa, be kawo matar aure bace sam, gefen ta yaje ya zauna daf har sai data dan matsa, suka gaishe shi dukka ya amsa idon sa na kanta. "You are beautiful." Yace mata kan sa tsaye, gabanta ne ya fadi, ta kalli Yaya Maryam ta kalli sauran yan dakin, sai kawai ta mike tana tattare jakar ta. "Bari naje wajen Gaji kafin ya zo." Bata jira amsar su ba tayi gaba, ya tashi da sauri ya bi bayanta ya jera da ita yana yi mata surutu, da hausar sa da ba wani ganewa take ba, tana shiga part din Gajin text din Moh ya shigo wayarta, "Muna waje." Yace a text din kawai, sallama tayi wa Gaji kawai dan kuma babu zama, ta juya zuwa nasu gidan ta tarar da Zeenat a zaune tana cin tuwo, nan ma tayi wa Maman sallama tace ta gaida gida. Fitowa tayi rik'e da hannun Marwan, ta koma wajen su Yaya Maryam tayi musu sallama, suka firfita zasu rakata, anan suke ganin ana sauke kayan abinci a irin motar da Iman din ta gani dazu a gida, ranta ne ya bata lallai aikin sa ne, tana jin su Maryam suna maganar sai dai idan shine ya aiko dan cikin surukan gidan babu wanda zai aiko da kayan abinci haka masu yawa. Har gate suka rakata sannan suka juyo,  Mahfuz na ganin zata bita ya tashi ya sake bin ta suka rankaya zuwa waje, kamar tace masa ya koma amma sai ta kasa tana jin nauyin sa. Tun da suka fito idon Moh akan su, ya gama tabbatar da ba Habib bane, ba kuma Khalil bane dan ba zai kara gangancin da yayi a baya ba.  Ransa ne ya baci, ganin yadda suke jerawa yana mata magana da yanayin yadda yake maganar. K'asa hakuri yayi, ya balle murfin motar ya fito daidai lokacin da Mahfuz yake kokarin kai hannu ya bud'e mata kofa, gashi yayi kusa da ita sosai. "Dalla malam baka da hankali ne?" Ya daka masa tsawar da ta saka Iman sakin yar jakar hannun ta, tsayawa Mahfuz yayi yana kallon sa yace "Pardon?" Wani banzan kallo yayi masa, ya zagayo ya kama hannun ta, ya jata zuwa dayan side din motar ya turata ciki, be lura ba sai data bigi ya rufe kofar da karfin sannan ya dawo wajen Mahfuz din dake tsaye rik'e da jakar Iman din da ta fadi cikin mamakin abinda ya harzuka gayen. "Wannan shine last warning dinka akan matata, ko waye kai komai alakar ka da ita, kar na sake ganin ka haka kusa da ita, idan ba haka ba wallahi sai na balla kafarka, nonsense." Be jira abinda zai ce ba, ya bud'e motar a fusace ya shiga ya rufo, Musaddik dake gaba ya juyo zai magana yaga yanayin sa, sai kawai yayi shiru, yace ma driver ya ja, jan motar yayi suka bar wajen. _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/14/22, 19:05 - Buhainat: Halin Girma 34 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw *******? Tun da suka dauki hanya babu wani wanda yayi magana a cikin su, ransa a bace yake matuka. Manne da jikin kofar take, cike da mamakin dalilin fushin sa haka, a kalla ya tsaya ya fuskanci abinda yake faruwa kafin ya yanke hukunci haka, abun ma dariya ya so bata, yadda ya jata zuwa cikin motar, lallai da gaske sojoji akwai su da temper, idan ba haka ba, menene abun tashin hankali anan? Tana jin sanda suka sauke Musaddik yana masa sai da safe ya amsa da k'yar, suka ja motar sai gida.    Motar na gama tsayawa ya balle murfin motar ya fice ko bi ta kanta be ba, jiki a sanyaye ta fito itama, ta bi bayan sa cike da mamakin sa. Bata same shi a falo ba, kai tsaye ta wuce bedroom dan rage kayan jikin ta da suka dame ta, baya dakin kamar yadda tayi tunani, kuma be shigo ba har ta gama sauya kayan ta fito falon ta zauna tana bud'e wayarta. Ta jima a zaune a wajen, sannan ya fito sanye da kajaren wando babu riga a jikin sa, wuceta yayi ya dauki abu a cikin wata drawer a falon ya koma dayan dakin da ya fito. Ya sake dadewa sosai dan har tayi tunanin ta bishi ta gani sai gashi ya fito ya doro gajeriyar jallabiya a jikin sa, yana kamshin turaren sa na hugo boss. "Abincin nan za'a kawo maka ko achan zaka ci?" Ta tambaye shi bayan ya zauna "No ba zan ci ba." Sak'alo tayi tana duban sa, yaki ko kallon sashen da take sai ma fito da waya da yayi yana daddanawa. Tashi tayi ta bar falon ta koma daki cikin rashin jin dadin abinda yayi mata, wannan ai wulakanci ne, me tayi haka? Ji tayi hawaye na kokarin zubo mata,  kokarin maida shi tayi tana daga fuskar ta sama.    Tana tashi kiran Takawa na shigowa wayar sa, ya daga yana mikewa tsaye "Barka da wannan lokacin Takawa." "Barkan ka dai, kuna lafiya ya iyali?" "Alhamdulillah wallahi." "Toh madallah, alfarma akayi min akan tafiyar da zakuyi, dalilin da ya saka sunanka ya fito saboda ana bukatar jajirtattun mutane kamar kai, kuma kai zaka jagoranci tafiyar,  sannan akwai alkwarin karin girma akan ka bayan an dawo, dan haka nake so ka ajiye komai ka tafi, Allah ya baku sa'a ku dawo lafiya." " Amma..." Yace a firgice "A'ah fa! Bana so naji komai Mohd, na jima ina neman alfarma irin wannan akan ka, komai idan har baka so toh fa an barshi, waya kawai zan, wannan kuwa takanas ya kira ni mukayi magana na kuma bashi tabbacin zaka je, toh kayi hakuri kaje." " Shikenan Nagode Allah ya kara girma, zanyi duk yadda akace." " Yawwa, Allah ya taimaka ya baku sa'a, Allah yayi albarka." " Amin." Ya amsa a dunkule zuciyar sa na wani irin suya, wato sai DG ya riga shi samun Takawa akan maganar ya kuma nemi alfarma yasan Takawa dole ya amsa masa, me ma ya saka shi wai kin tsayawa yaga Takawan a dazu ya tafi? Ai da duk haka bata faru ba. Wani abu me ya tokare masa makoshi, ya jefar da wayar a saman kujerar yana barin falon da sauri zuwa daki.   Tana zaune a gefen gadon tana tunani ya shigo, ya wuce wajen da jakar sa take ajiye ya ciro flash din, ya dauki system ya sake barin dakin. Hada su yayi da dayan na wajen Iman, ya kunna kowanne yayi copying dinsa akan system din, sannan ya saka su a envelope ya mayar jakar. Tafiyar da zai yi Itace zata basu kafa wanda har za'a iya samun matsala be samu dukka bayanan da yake son samu ba, yanzu dai zai damka wa Musaddik flash din guda biyu, ya ajiye a wajen sa dan sune manyan evidence dinsa idan ya tashi yin abinda ya jima yana shiryawa.   Wayar sa da ya jefar dazu ya dauko ya kira Musaddik din, sukayi magana sannan ya ajiye yana dafe kansa. Zai iya jure komai amma banda abu biyu, iyayen sa da matarsa, idan har aka samu matsala zai dauki matakin da ba zai ma kowa dadi ba.    Tun tana jiran shigowar sa har ta gaji ta hakura, ta kwanta tana matsar kwalla, bata ga abin fushi ba sam, bata kuma san ta yadda zata fara bashi hakuri ba, ba wai dan tana ganin ai bata yi laifi ba me yasa zata bashi hakuri, sai dai ta rasa fuskar da zata iya bashi hakurin.    Chan cikin dare ta farka bayan bacci ya dauke ta da k'yar, ta ganshi a gefen gadon yana bacci hankalin sa kwance, ya riga ya saba mata tun farko tare suke kwanciya, cikin bargo daya amma sai gashi yau, akan abinda bata da laifi akai,yana fushi da ita. Baccin ne ya kaurace mata gaba daya, ta dinga tunanin wai dama haka auren yake kenan? Sai wajen asuba sannan ta samu baccin ya kwanshe ta bayan ta sha kuka ta gode Allah.    A kanta ya tsaya yana kare mata kallo, yadda ta kwanta sai ta bashi tausayi sosai, be san me ya hau kansa jiya ba, amma ba wai haushin ta yake ji ba, bayan ma wayar da yayi da Takawa zai iya cewa ya manta abinda ya faru, tunanin abinda zai faru idan baya nan shi yafi daga masa hankali har ya hanashi zuwa ya kwanta sai dare sosai.   Hannu ya kai ya shafi gefen fuskar ta, ta bud'e idon tana salati a hankali, ganin shi da tayi a tsaye akanta yana mata murmushi ya sakata tashi da dan sauri tana gyara jikin ta "Good morning Baby,." Yace kamar babu wani abu da ya faru, bata amsa ba, sai zuro kafarta da tayi ta sakko, ta wuce shi zuwa toilet dan ta makara daga ganin yadda haske ya cika dakin. Hijab ya ciro mata ya shinfid'a mata abun sallah, ya zauna yana jiran fitowar ta. Ko da ta fito bata kalle shi ba, ta tada sallar ta, da ta idar ma sai kawai ta kwanta a wajen tana janyo hijab din ta rufe fuskar ta dashi. Tasowa yayi tsam yayi zaman dirshan a gaban ta, ya janye hijab din yana dagota, hawayen da ya gani a saman fuskar ta yayi mugun bashi mamaki "Innalillah, kuka? Don't tell me kuka kikayi tayi the whole night..." "Ya Salam...Look at your eyes, I'm very sorry, ki yafe min dan Allah." Bayan hannun ta tasa tana share hawayen da suka ki tsayawa, ita kanta bata san na menene ba, kawai tasan she's weak, tana jin wani irin weakness a tattare da ita, she can't take fushin sa a gareta, he's so nice to her ko yaya yayi fushi zai bata wahala sosai. Rarrashin ta ya dinga yi da kalamai masu taushi, har sai da ya tabbatar da kukan ya tsaya, sannan ya taimaka mata suka bar kasan suka koma saman gado. "Dole zanyi fushi, shi zaman aure dama zo mu zauna ne zo mu saba, I can equally make mistake, ina da kishi sosai Fatima, ba kuma wai dan naji a raina wai kin kula shi bane, son da nake miki ya saka, please ki kula sosai. " " I'm so too. " Tace bayan ta amsa masa da toh. " Baki komai ba ai, nasan wacece matata, kawai dai... " " Me?" " Ashe dai ana so na... " Duka ta kai masa ya goce " Allah da gaske, naji dadi sosai, zan biya bashin duk tears din da akayi min asarar su, amma kafin nan, zanyi tafiya, karshen week din nan. " Da sauri ta kalle shi, sai ya kama hannun ta ya fara yi mata bayani yadda zata fahimta " Kinsan yanayin aikin mu dama yadda yake, ni dinma dai kawai dai kawai dai, amma wannan karon ba zan iya kin zuwa ba, dole ne dan akwai Takawa a cikin maganar. " " Dadewa zakayi? " " Uhmm... Ban dai sani ba, amma in sha Allah ba zamu dade yadda kike tunani ba. " " Allah ya kaimu, ya bada abinda aka je nema. " " Amin ya Allah, an koma strike, akwai driver da zai dinga kaiki ya jiraki ya dawo dake, hakan nasan zai debe miki kewa, da ina tunanin ko a chanja school, amma kuma tunda har kun kai 300lv gwara ki karasa ko? ". " Eh hakan yayi. " " Yawwa my wife, yi min murmushi na gani toh." Murmushi tayi, sukayi dariya a tare suka bar komai a bayan su, suka fita domin karya kumallo. ***Zaune yake a irin kujerar nan me jujjuyawa, kansa sanye da cowboy hat, sai bakin glasses da ya rufe kusan rabin fuskar, jujjuya yake akai yana busa sigari, daga bayan sa yara ne biyu majiya karfi, kowannen su ka kalla zaka tabbatar da zai iya aikata koma wanne irin aiki ne. Knocking akayi, ya daga kansa yana duban su, kafin ya gid'a kan nasa alamar eh, wanda yake ta bangaren kofar ne yaje ya bud'e yana matsawa baya, suka shigo su biyu mace da namiji, kujerun gaban sa suka zauna, ya cigaba da busa sigarin sa ba tare da yayi musu magana ba, sai da suka dau wani yan dakiku a wajen sannan ya jefar da sigarin ya saka kafa ya murje ta. "Kun samo abinda ya kamata ku samo din?" "Za'a samo dai, komai yana tafiya according to plan, gashi zai yi tafiya." " Tafiya? " Yace yana kallon su " Eh zaiyi tafiya karshen satin nan. " " Wonderful, opportunity me kyau, lallai lokaci yayi da kowa zai samu abinda yake so. " " Menene next? " " Tafiyar sa, let me know when he's gone." " Me zakayi?" " Matsala ta ce wannan, bani da matsala da cikin gidan ku, abu biyu ne suka hada mu zuwa uku, a wannan gabar kowa has to play his on part dakansa. " "Shikenan. " Zaro wata sigarin yayi ya kunna mata wuta, suka mike suka fita, ya bi su da kallo kafin yayi murmushi. Moh zai yi tasting abinda yaji a lokacin da ya raba shi da abinda yafi so, shi abu daya ya raba shi dashi, amma shi zai raba shi da kusan abubuwa uku zuwa hudu masu matukar muhimmanci a rayuwar sa, ko zai mutu sai ya dauki fansa akansa, sai ya dandana masa bakin cikin da be taba dandana irin sa ba.   Mikewa yayi bayan ya gama zukar sigarin, ya tura kofar wani daki, ya shiga bayan ya kunne flashlight din wayar sa, saboda tsananin duhun da dakin yake dashi. A gaban mutumin da yake kwance magashiyan ya durkusa, yana tallafo kansa, sannan ya haske shi da wayar sa da ta kusan kashe masa ido "Ka kusa samu yancin ka, bayan na tabbatar da na samu duk abinda nake so a wajen shi wanda yafi ma hatta iyayen ka, kayi hakuri aiki ne ya biyo ta kanka, kai kadai ne kafi kowa kusanci dashi, dan haka dole ne kaima ya sha wahala!" "Gwara kayi ta ajiye ni a bakin dakin nan, akan kayi wani abu akan sa, wallahi wallahi kaji na rantse ma ko? Kuda idan ka bari ya taba wani abu na jikin sa, sai ya karar da duk dangin ku!" Dariya ya kece da ita mahaukaciyar dariya, ya saki kansa da ya tallafo ya bige da simintin wajen " Idan yana takama da mulki ne, ko kuma khakin da yake jikin sa, toh bari kaji, babu abinda ya isa yayi min dan nayi nisan da bazaka taba tunani ba, k'asar nan tayi lalacewar da su kansu masu tsaron lafiyar taku ba tsira sukayi a wajen mu ba, shi karamin kwaro ne." Soma takawa yayi har ya kai kofa, sannan ya juyo yace " Daga yau zuwa gobe amfanin ka zai kare, zabi na ne, na barka ka tafi, ko kuma na kare rayuwar ka gaba daya Musaddik Izzeeddin! _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/14/22, 19:05 - Buhainat: Halin Girma 35 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw *******? Da wuri Musaddik ya iso gidan, dan basu samu haduwa ba tun ranar da sukayi waya sai yau din da zai tafi, ya riga ya shirya shi kadai yake jira, yana zuwa ya dauko envelope din ya damka masa a hannun sa "Ka kula sosai dan Allah, idan har lokacin da ya kamata yayi, ban dawo ba zan fada maka sai ka damka su a hannun Aji! Dan Allah kar kayi kuskure, ka kula sosai, kai kadai na yarda dakai da wannan amanar." "In Sha Allah." Yace yana rik'e envelope din sosai.    Ciki ya koma, ya barshi a wajen ya tarar ta gama hada masa jakar sa waje daya, tana gaban jakar ta zabga tagumi har ga Allah bata son tafiyar tasa, amma kuma dole zata hakura saukin ta daya fitar da zatayi school, ga ma'aikata birjik an kara karo wasu ma, gate din ma kuma cike yake da jami'an tsaro da ba dan haka ba, ba zata iya zama a wannan tafkeken gidan ba.    Tashi tayi ganin ya shigo,ya kalle ta ya kalli jakar sai kawai ya rungume ta "Zanyi missing dinki sosai, take care of yourself for me dan Allah, idan kina bukatar wani abu, reach out to me, idan baki sameni ba, Musaddik yana nan, nayi miki saving number dinshi kema zan bashi naki." " Ai babu ma abinda zan nema, akwai komai." "In case dai." " Owk tam, nagode. " " Yawwa, muje ki rakani. " Ya rik'e hannun ta suka fito har wajen mota, ta tsaya daga gefe bayan ya shiga ya zauna, yayi mata murmushin karfafa guiwa itama ta maida masa zuciyar ta na rauni, daga mata hannu yayi har suka fice daga gidan gaba daya. ***Abinda ya faru lokacin da Bashir yazo daukar Zeenat bayan tafiyar Iman, suna barin kofar gidan yana zuwa, adaidaita sahu yazo dan ya maida machine din wa maishi, aikawa yayi a kirata, dan babu waya a hannun ta, Mama na jin sakon kiran ta zira mayafi taje wa Zeenat din tana zuwa, ta je ta same shi a tsaye yana jira ta fito suna magana da me napep din. Be yi mamakin ganin Maman ba, dan dama yasan ba za'a yi komai ta sauki ba, gaishe ta yayi taki amsawa, sai ma cewa da tayi tana bud'e hannun ta "Bani takardar yata." "Ban gane ba Mama?" "Eh ina nufin ka sauwake mata kaddareren auren ka dan ba zata koma ba ku karasa kashe ta kai da tsohuwar  matar ka." " Amma Mama Zeenat tana so na, nima Ina son ta, kiyi hakuri dai ta fito mu tafi." "Wanne so? Bayan yaudarar da kayi har kana tunanin tana son ka?" "Toh ni dai nasan auren soyayya mukayi da ita, kiyi hakuri ki bimu da addu'a kawai." "Ba zan hakurin ba, Malam takardar 'yata kawai nake so ba dogon surutu ba." "Ba zan iya sakin ta ba gaskiya, kiyi hakuri kawai." Sai ya juya ya haye napep din,da sauri ta bishi tana kiran sa, me napep yaja suka bar kofar gidan. Tana juyowa da nufin komawa gida sai ga Abba a tsaye a bayanta, ya harde hannayen sa yana kallon ta ransa a matukar bace, bacin rai da be taba yin irin sa ba tun da aka fara hayaniyar auren Zeenatun, tsoro ne ya shige ta, dan yadda taga bacin rai a fuskar sa zai iya aikata komai. "Dan Girman Allah..." Daga mata hannu yayi "Babu abinda zaki ce min, bana son naji komai! Jikin ta ne ya hau rawa, yayi ciki ta bishi tana son yi masa bayani, ba zai tsaya jin komai ba, ba kuma zai dauki maganar da sauki ba wannan karon, tayi abinda ba zai mata uzuri ba. A zafafe ya shiga falon yana k'wala kiran zeenatu, ta tashi jikin ta na rawa har tana yar da dan kwalin kanta da yake hannun ta, "Me kike yi har yanzu baki tafi ba." "Uhm.. uhm.. dama..." "Karya kike yi, munafuka!" "Minti biyar kachal na baki, ki fice ki koma gidan mijin ki, na fad'a miki!" Be jira ya sake jin ta bakin ta ba, ba kuma zai saurari magiyar da Mama take masa akan dalilin da ya saka tayi abinda tayi ba, yayi gaba kawai ya shige dakin sa ya rufo.     Kuka Zeenat ta fashe dashi, da gaske bata son komawa gidan Bashir, ya zatayi yanzu? Gashi taga wani irin fushi a fuskar Abban da bata taba gani ba,dama mama so tayi bayan ta kori Bashir din idan Abban yazo tace shi Bashir din ne yace Zeenat din ta zauna a gida zai yi tafiya ya dawo, daga nan sai suyi ta matsa mata har ya sake ta, shikenan Abban ba zai zargi komai ba, amma sai gashi komai ya lalace tun ba'a kai ko ina ba. "Kina da number Bashir ko?" Girgiza kai tayi "Dan ubanki baki haddace number sa ba? Yanzu ya kike so muyi? Dole ya dawo ya dauki ki ku tafi kafin nasan abinda zanyi akai." "Mama ni ba zan koma ba." "Aikuwa sai kin koma, baki ga fuskar babanku ba? So kike yace na tafi gida shikenan ki rasa wanda zai tsaya miki? Tashi maza ki kira bashir ga wyata kice ya dawo, idan yaso sai mu san abinda zamuyi." Kuka ta cigaba da rerawa a hankali, ta karbi wayar ta saka number tasa ta kira, tayi ta ringing amma be daga ba, ta cigaba da jera masa kira amma babu alamun zai dauka. Rasa yadda zasuyi sukayi, har goma saura gashi bata san gidan ba balle idan tafiya zatayi da kanta ta gane. Suna nan a falon ya fito, ya kalle su sannan ya fice  gaba daya. ***Bayan tafiyar sa sai taji gidan yayi mata girma da fadi, ta kwanta a saman kujerar falon tayi lamo tana jin cikin ta na juyawa sama-sama. Bacci ne ya dauke ta a wajen bata tashi farkawa ba sai da rana tayi. Sallah ta fara yi taci abinci sannan ta zauna ta dauko littafan ta na islamiya ta shiga duba su, tana muraji'ar na baya, tana so ta cigaba da karatun ta ko ita da kanta ne ta dinga karawa kanta, zatayi amfani da damar duk da sun koma boko amma ba zata kyale na islamiyya ba, akwai wasu littattafi da take son koya wanda dole sai dai ta samu manyan malamai su koya mata, amma bata san yadda zatayi ba. Tana nan zaune yayi mata text message, tayi masa reply sannan ta cigaba da abinda take har zuwa la'asar, gaba daya sai taji ta rasa ma me zatayi, sai kawai ta zagaya baya wajen ma'aikatan gidan ta same su suna hira, suka tashi da sauri suna tambayar ta abinda take so, murmushi kawai cike da mamakin yadda suke girmama ta take ta zauna a wata kujerar roba, tace zuwa tayi zaman cikin ya ishe ta, nan fa suka hau murna suka cigaba da hirar tana sauraren su, a kalla sun debe mata kewa dan bata dawo ciki ba sai bayan da aka kira sallar magriba.     Washegari ta tashi da murnar zuwa school bayan tsawon lokacin da sukayi a gida, jin ta take tamkar sabuwar shiga dan wasu abubuwan ma ta mance su, tasan da yawa duk yau zasu koma saboda dai kowa ya gaji da zaman gidan. A tsanake ta shirya tsaf, sannan tasaka madaidaicin mayafi akan doguwar rigar atamfar da ta saka brown da touches din blue, ta dauki jaka da takalmi da suka shiga sosai ta saka, tayi shigarta ta mutunci ta fito ta nufi kitchen in da ta hanyar ne ake bi zuwa bq, a kitchen ta tarar da Ummimi, tana karasa hada breakfast dinta, ta russuna har k'asa ta gaishe ta, ta amsa a sake tana dudduba aikin. "Zan je school ba jimawa zan ba, idan an gama komai sai a jera a dining, zanyi bakuwa anjima da rana." "Allah ya dawo dake lafiya gimbiya, idan kina bukatar abu ba sai kin zo ba, kira kawai zakiyi ranki ya dade." "Babu komai karki damu." "A dawo lafiya, Allah ya bada sa'a." "Amin." Tace ta juya ta fita, ta samu driver ya gyara motar, sai kawai ta fad'a baya tana tuna rayuwa yadda take a shekarun baya, shekarun da basu gaza biyu ba. Tun da suka isa makarantar duk in da suka wuce sai an kalle su, a department dinsu kuwa kamar an ga nama ko wata sabuwar halitta, dama labari ya riga ya karad'e ko ina amma dama ance gani ya kori ji, wasu takanas suke zuwa su tabbatar da gaskiyar abinda suka ji. Tayi ta zuba ido ko zata ga Zeenat amma ko me kama da ita bata gani ba, har suka gama abinda zasuyi suka koma gida.    Tun daga ranar kullum sai taje school din ta dawo, sai zaman gidan ya zama mata kad'an, duk dare kuma suke shafewa suna magana da shi a waya, ba wani sosai take jin kadai ta ba, sannan kuma duk sanda take free da rana ko ta dawo da wuri tana zama ta koya wa masu aikin karantun al'qurani da ta lura kusan rabin su basu iya ba, kawai rayuwar su sun taso ne akan hidimtawa gidan sarautar, tun iyaye da kakanni suke a haka har zuwa yanzu babu wani sauyi da ya samu rayuwar su. Hakan ba karamin dadi yake mata ba, a kalla ita ma zata samu lada me dinbin yawa.    Wasa wasa sai gashi yayi sati uku cif da tafiya, duk sanda ta tambaye shi yaushe zai dawo sai yace mata surprise zai mata kawai, haka take hakura ta kyale shi, kullum cikin shiri take dan tasan zai iya zuwa mata bakatatan, wasu magunguna da momma ta bata wanda yawancin su na fruits ne da madara su take ta faman sha, dan sosai suke mata dadi har ta kanyi mamakin kanta a lokacin da Mamman ta bata , bata wani ji dadin su kamar yanzu ba.    Wata rana a cikin ranakun da take zuwa school ta kai yamma, ta tashi duk jikin ta babu dadi, ciwo take amma bata san takamainai me yake mata ciwo ba, kamar kar taje school din amma sai ta daure dai, ta shirya ta kira Ummimi ta rakata, tunda dama sai da yace lallai ta dinga tafiya da masu rakata amma bata tafiya dasu. Tare suka tafi yau haka nan taji bata son tafiya ita kadai, suka jirata tayi lecture ta fito wajen biyar na yamma, a gajiye likis gashi ko ruwa bata saka ma cikin ta ba, kaidar tace bata cin abu a school tun da ma, sai dai idan zata dade irin haka taci ko snacks ne shima ba ko yaushe ba, dan mafiya yawancin lokuta rage kudin da Abba yake bata Mama take ta bata kadan, shiyasa ta koyi yadda zata yi karatun haka,sai kawai ya zame mata jiki ko yanzu da take da komai bata damu taci din ba    Da sauri Ummimi ta karbi Jakarta da kayan hannun ta, ta tayata bud'e mata motar ta zauna sannan ta zagaya ta shiga bangaren ta, bata lura da su biyu ne a gaba ba, har da wani sai da ya gaishe ta "Amarya barka da rana." "Barka dai, ai ban ma lura ba, ina wuni?" "Lafiya lou wallahi, dama wannan gajiya da kuka kwaso, dama munyi waya dashi ne yace na biyo ta makarantar taku sai mu wuce, zasu sauka da karfi shida da rabi, sai mu dauko shi a airport, amma fa yace kar na fad'a miki dan wai so yake yayi surprising dinki." Dariya ta saka "Lallai, ina ta tambayar sa yaushe zai dawo yaki fad'a min, so yayi kawai yanzu ma sai dai na ganshi kenan." " Ai irin wai surprise din masoya." Dariya kawai tayi, bata kawo komai a ranta ba, ganin Musaddik ne, haka kuma sai taji wani yanayi na dokin ganin mijinta, wanda yau ya cika sati uku da kwana biyar cif da tafiya. Hanyar airport din suka dauka, ta kwantar da kanta a bayan da yake saramata sosai. **A word of encouragement to All TTC mother's (Trying to conceive) do not lose hope, Allah yana tare daku, ku cigaba da addu'a, Allah ya baku 'yaya masu albarka da mu baki daya. Baa debe tsammani daga rahmar Allah. _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/17/22, 09:45 - Buhainat: Halin Girma 36 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw *******? Cikin wani yanayi taji kamar bacci yana fuzgarta, ta sake gyarawa sosai Ummimi ta matsa mata sosai ta kwanta a bayan, nan take kuwa bacci ya dauke ta. A tunanin Ummimi tsabar gajiya da wahala ce ta saka ta baccin, dan tun safe suka fito kuma tana lura bata saka komai a cikin ta ba sai ruwa, ita dai ta bata kudi taje cafeteria ta siya abinci taci, amma ita kuwa bata ci komai ba, dole ne ko ba karatu kake ba, ka jigata balle. Tausayin ta taji, musamman da ta gama fuskantar halin kirkin da, bama ita kadai ba duk ma'aikatan gidan na murna da samun ta a matsayin uwargijiyar su, babu hantara balle tsangwama, gaba dayan su son ta suke da gaske.    Tafiya suke tayi babu alamun zasu tsaya, har duhu ya fara mamaye sararin samaniya, kallon ta Ummimi tayi taga har lokacin bacci take da gaske, shiru kake ji a motar babu wanda yake magana a cikin su, a tunanin da za'a samu ko yar karamar hira ce tsakanin driver da na gaban amma babu wani wanda yayi magana a ciki, jakar dake kusa da Iman din ce ta fadi kasa, Ummimi ta sunkuya da nufin dauka, abinda ta hango a hannun shi ya saka hantar cikin ta kadawa, a firgice ta dago tana dunkule jakar a hannun ta, juyowa yayi ya dube ta, ya sake dago mata hannun nasa da kyau dan ta gani sosai, bindigar ce kuwa, tsoro ne ya kamata, "Idan kika sake kika bud'e bakin ki a wajen nan, sai na fasa kanki da alburushi." Da sauri ta rufe bakin ta da hannun ta, juyawa yayi kan driver yace " Idan ka kai karshen titin zaka gangara haggu." Da ka ya amsa, daga gani a tsoroce yake, rashin sani ya hanasu ganewa tun shigowar su motar. Kallon Iman take ganin da gaske bacci take, bacci me nauyi da ya hanata jin duk abinda ya faru, mamaki ne ya kama Ummimi, dama ta saba irin bacci haka ko kuma dai akwai matsala, da sauri ta dan taba ta, sai taga ta motsa kad'an tamma kuma bata tashi ba, ajiyar zuciya ta sauke, hawayen da take ta makale shi ya gangaro zuwa fuskarta, me yasa mutane suka lalace haka? Labarin da suke ji a gidan radio yau shine ya faru dasu? Idan har masu sarauta da masu hannu da shuni basu da tsaro toh waye kai kuwa talaka? Anya rayuwar zata tafi a haka?    Cikin tsananin fargaba take har suka karaso wani gida, karami a cikin gungurmin jeji, babu gida gaba babu baya, ba zaka taba tunanin halitta irin ta mutum zata rayu a wajen ba, tana jin yadda suka dinga shiga kan tudu da kwari alamun sam hanyar bata mota bace, ko tace mota bata taba bi ba. Murfin motar ya bud'e yana nunawa driver bindiga, suka fito a tare ya zagayo wajen sa ya rik'e kugunsa. Fito yayi da bakin sa, sai ga wasu kartin maza su biyu sun fito, tare da wata mace a bayan su, tafawa sukayi da daya daga ciki sannan yace "Kayi babban aiki, aikin da zai firgita ilahirin k'asar har ma da ketare, tana ina?" Bayan motar ya nuna masa, ya tafi zuwa wajen ya bud'e yana leka ciki "Baccin ne be sake ta ba har yanzu?" "Eh!" "Tasha ruwan kenan!" Yayi murmushi yana rufe kofar "Tasha sanda ta shigo motar." "Kayi kokari sosai... Kudos!" "Thank you sir." "This is a shame to the Nigerian Armies, The royalties, government, gaba daya ma, duk sunyi failing, ta yaya kake tunanin mutane zasu sake yarda dasu? Bayan sun damka hakkin kulawa rayuwar su garesu, sai ya zama sun k'asa tsare kan su?" Sai ya kwashe da dariya " Yaron nan a bayan mu yazo, yaron nan ta dalilin sa na rasa komai, ciki harda aikin da na kwallafa rai, saboda shine shafaffai da mai? Saboda shi din dan gata ne, shiyasa aka fifita shi akan kowannen mu, me yafi mu? Mulki?" "Oga!" " Haka ne mana!" Ya fad'a da karfi "Haka ne. Kullum cikin favoring dinsa ake, kullum cikin yabon sa ake, na kai mataki Babba amma yaron nan, ta dalilin sa komai ya baci, ya kake tunanin zan iya hakura?" "Kunsan shekarun da na dauka ina gina rayuwata har na kawo wannan lokacin?" "A ah." Suka girgiza kai dukka " Shekara goma sha daya, amma cikin sakan da be wuce goma ba, ya kwace komai, khaki na, rank dina, mutunci na a idon duniya, na muzanta, na zama abin gudu da k'yama." Duk sun yi shiru kowa na sauraren sa, shirun shima yayi dan bashi da abin fad'a kuma " Ku shigar dasu ciki, idan princess ta tashi a fad'a min." Sai ya juya ciki ransa fari tas, ya tabbatar saura kiris bomb ya tashi, bomb din da zai tarwatsa duk wani farin cikin Muhammad Ahmad Santuraki da duk wani makusancin sa, shekara biyar kenan yana bibiyar sa, ya kuma samu nasarar samun duk abinda ya samu a yanzu, wanda yake tabbatar da su kadai sun isa su tarwatsa duk wani farin cikin sa. Matsala daya da ya samu, bashi kadai ne yake son ganin bayan sa ba, nasa kawai yafi zafi ne, sai ya hada guiwa dasu, yayi amfani dasu wajen samun abinda ya samu akan sa, ya kuma tabbatar da babu wata alaka da zata sake hada su a nan gaba, ya datse duk wata hanya da zasu neme shi.    Ta jima tana bacci sosai, Ummimi dake durkushe a gabanta tana kuka sosai taga ta motsa, ta cigaba da motsawa tana yamutsa fuska kafin ta bud'e idon ta da kad'an kad'an da sukayi mata matukar nauyi, saman dakin ta fara kalla, sai kuma ta shiga jujjuya idanunta tana son gano a in da take, da sauri ta yunkura zata mike, Ummimi ta taimaka mata tana rik'e ta "Karki tashi da sauri jiri zai iya daukar ki, ina tunanin sun zuba miki magani ne.". Ta fad'a cikin muryar kuka "Ina ne nan? Me muke anan Ummi?" "Ni ma ban sani ba, wanda kukayi magana dashi, shi ya kawo mu nan, sun sato mu!" "Musaddik?" "Eh." "Innalillah wa inna ilaihi rajiun." Ta furta a hankali, kanta da yake jujjuyawa ta saka hannu ta dafe, amai ne taji yana taso mata, ta yunkura da nufin tashi amma kafin ta kai kofar har ta soma aman, wanda babu komai a cikin sa sai zallar ruwa, tun tana yi har ta koma kakari kasancewar babu abinda yake cikin ta tun safe, rik'e ta Ummimi tayi tana kuka, tana jera mata sannu, sai da taga ya lafa sannan ta taimaka mata ta maida ita gefen tabarmar da ta tashi, "Bari na samo miki ruwa, sannu." Ta tashi ta fito, su biyu ne a zaune suna karta, suna ganin ta suka tashi " Ruwa take so dan Allah. " Da Ido sukayi wa juna signal, kafin daya daga ciki ya shiga wani daki, ya dawo da ruwa ya mik'a mata, ta karba ta juya ciki, ta tarar da ita tana ta juyejuye akan tabarmar, ta rik'e cikin ta da yake murda mata kamar zata amayar da kayan cikin ta. Dagota tayi, ta bata ruwan ta kuskure bakin ta, sannan ta sha, ta koma ta kwanta tana sake rik'e cikin ta.    ***Kwanan Zeenat biy babu Bashir babu alamar sa, Abba kuma ya zuba musu Ido be sake cewa komai ba, ko Mama be sake mata maganar ba, shirun nasa yayi masifar bata tsoro, dan bata san me yake shiryawa ba, ranar suna zaune Zeenat din na cin wainar fulawa, ba wani dadin ta take ji ba amma itace kadai take mata dadin ci, sai nama da tuwo idan ta same su kamar wata tsohuwar mayya, jigum jigum suke kowa da abinda yake damun sa. Kofar falon ce ta bud'e duk suka kalli kofar a tare, Abba ne ya shigo, ya wuce dakin sa, k'asa k'asa Zeenat din tayi masa sannu da zuwa be ma ji ba, ya shige jimawa kadan ya fito, ya dubi Mama da tayi tsam tana kallon sa yace "Tunda har ban isa na saka ko na hana Zeenatu abu a gidan nan ba, kin nuna min ban isa ba tun fil'azal, na bar miki ita, idan har tana so mu shirya da ita lallai ta koma dakin ta, ke kuma, hakuri na ya gaza, kije gida kya dawo duk sanda kika shirya gyara auren yarki, idan har Zeenatu bata koma dakin mijinta ba, toh zaman mu ba zai cigaba ba. " Daga haka ya saka kai ya fice, ba don darajar yaran dake tsakanin su ba, ba kuma don darajar zaman da tayi dashi na dadi a baya ba, da zai sauwake mata ne kawai, amma hakan ba zai yiwu ba, har yanzu yana sonta yana kuma son ta gyara halayenta.    Tashin hankali ba'a saka maka rana, da girman ta da komai gotai gotai zai ce taje gida, zagaye ta dinga yi a falon kaamar tayi hauka, duk tsawon shekarun da sukayi da Ibrahim be taba nuna mata ko yatsa ba, sai gashi a yanzu da girma ya soma hawa kansu, tayi abinda gaba daya mutuncin ta ya zube a idon sa, har yana cewa zaman su ba zai yiwu ba. " Mama dan Allah kiyi hakuri, zan koma wallahi ba zanzo ku samu matsala da Abba akai na ba, zan jure koma menene dama ni na jawo ma kaina. " " Ba laifin ki bane, babu abinda zai faru , sake gwada kiran Bashir din idan be daga ba sai kawai na saka Habib ya kaiki chan gidan su, daga nan sa neme shi ai dole yazo ya dauke ki." Da sauri ta dauko wayar, ta kira amma sai taji alamar anyi blocking number, ajiyewa tayi jiki a sanyaye tana fadawa Maman, kira mata Habib tayi, tace yazo maza gida yanzu duk abinda yake yi, be dau wani lokaci ba sai gashi, ta fad'a masa abinda take so yayi,yace mata babu mota Abba ya fita, sakashi tayi yaje ya kira musu napep yazo suka tafi, suka fita ta ja ajiyar zuciya, ba zata iya jure tafiyar ko ina ba, ta riga tayi girman da zaman gidan su zai mata wahala sosai, idan kuma ta tafi bata san ta yadda zata dinga ji daga wajen Zeenat din ba. ***Yana zaune bayan sun gama wani taro da sukayi, ba zaka iya tantance yanayin da yake ciki na bakin ciki bane ko na farin ciki, kiran layin Musaddik yake amma still amsar daya ce, switch off, sunyi dashi kafin su taso zai kirashi, gashi babu wani isashen lokaci da zasu sake batawa, su biyu ne suka shigo, suka sara masa sannan suka koma gefe suka tsaya "It's time sir." Mikewa yayi be ce komai ba, ya shige cikin dakin, ya dauki jacket dinsa da dayar wayarshi, sauran kayan nasa sun riga sun fitar dasu tun dazu,gaba yayi suka bishi a baya, yana cigaba da kiran Musaddik din, ganin da gaske ba zai same shi ba, shiyasa ya sauya akalar kiran zuwa kiran ta. Jiya basuyi magana ba gaba daya, yasan tana kaiwa yamma a school haka kuma yasan ta dawo a gajiya, ko da ya kirata no answer sai kawai ya kyale ta, a zuwan suyi magana a yau kafin ya taho. Ringing wayar tayi tayi ba'a daga ba, bayan ta katse ya sake kira amma still no answer, sai ya kashe wayar tasa baki daya ya tura ta cikin aljihun wandon sa, sanda suka karaso wajen motocin da zasu dauke su, tuni duk sun shiga shi kadai ake jira, dama kuma shine Captain din tafiyar. Yana shigowa duk suka mike tsaya, irin doguwar babbar motar nan ce, sai da ya zauna sannan duk suka zauna, driver ya jasu suka bar harabar wajen.    Tun daren jiya labari ya kai fadar Maimartaba na rashin dawowar Iman din daga makaranta wanda ma'aikatan gidan ne suka kai labarin, kamar wasa da kowa ya dauka, a tunanin su ko wani wajen ta biya, amma ganin har dare ya soma yi ya saka hankali ya fara tashi, zama ma neman gagarar Fulani tayi bayan an tabbatar da bata je gidan su ba, ba kuma wani da zata je wajen sa, number driver da tata duk suna shiga amma kuma babu answer. Waya Maimartaba yayi a dare ya sanar da yan sanda abinda yake faruwa, a take ya tashi jami'an tsaron ko ta kwana, suka bazama neman, in da aka samu wayar Iman din da ta driver a cikin makarantar in da aka ajiye a waje daya cikin wata farar leda.    Tsawon daren babu wanda ya runtsa a tsakanin su, in da suka gama tabbatar da sace su akayi, kuka sosai Fulani take tana hango kalar tashin hankalin da muhammad zai shiga idan ya dawo. Zuwa safiya labari ya fara fita, bayan Maimartaba sunyi waya da gwamna, da wasu manyan jami'an tsaro, cikin kankanin lokaci labari ya baza lungu da sako na k'asar har ma da kasashen dake da makfwataka da k'asar.   Ana zargin an sace matar dan sarkin Adamawa, jikan sarkin Kano babban jami'in sojoji Captain Muhammad Ahmad Santuraki haka gidajen jaridu suka dinga wallafawa a shafukansu, nan da nan mutane suka dauka kowa na kokarin tofa albarkacin bakin sa. _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/17/22, 09:45 - Buhainat: Halin Girma 37 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw *******? Cikin matukar tashin hankali Abba ya shigo gidan, bayan abinda ya gani a shafin BBC HAUSA, ya saka shi matukat kaduwa, idan har suna nufin surukin sa kenan, toh kenan Iman aka sace? Innalillah wa inna ilaihi rajiun,tashin hankalin da ba'a saka maka rana. Sauri sauri yake yana kokarin isa bangaren Abba babba, kiran Mummy ya shigo wayar sa, "Shikenan." Ya furta "Sun samu labari kenan, ta tabbata da gaske ne." Ya sake fad'a sai kuma ya daga wayar yana kokarin daidaita tashin hankalin da yake ciki. "Hello Abban Iman, abinda nake gani a news gaskiya ne?" "Labarin da nake samu yanzu kenan, yanzu muke shirin tafiya dan samun sahihancin labarin, ki kwantar da hankalin ki, in sha Allah babu wani abu da zai faru." "Innalillah wa inna ilaihi rajiun." Ta furta tana sakin kuka "Zan tawo yanxu.." "Sai kin zo." Ya katse kiran da sauri yana shiga ciki, a tsaye ya tarar da Abban yana kaiwa da komowa, yana shiga Abba Musa da Abba Kabiru suka shigo, babu wata magana da suka tsaya yi suka fice da sauri, suka dauki hanyar gidan sarki, dan anan ne kawai zasu samu gaskiyar abinda suke so suji, da Abba Musa yace su kira Muhammad din amma kuma sai suka fasa suka ga gwara su je din kawai ba lallai shima ya iya daukar waya ba.   Haka sukayi, cikin tsananin tashin hankali suka isa gidan, bayan sun gabatar da kansu aka shigar dasu har in da maimartaba yake, babu wasu mutane sai makusantan sa, suna jimamin abinda ya same su haka bakatatan, sannan lokaci zuwa lokaci suna communicating da chan police station din, duk da babu wani labari akai, dan duk wanda yayi aikin yayi masifar kwarewa wajen gudanar da plan din nasa dan be bar duk wata hanya da za'a neme shi ba, amma duk da haka ba zasu karaya ba, zasu yi iyakar kokarin su dan ganin an samu so cikin kankanin lokaci.    Labarin da su Abba suka samu yayi masifar sake daga musu hankali dan har kwalla sai da Abba yayi ba tare da kowa ya lura, yadda ake bada labarin rashin imanin masu kidnapping din nan kawai yake tunawa, ga iman sam bata da hayaniya, zata cutu ainun a wajen su sai dai fatan Allah ya bayyana ta cikin aminci da koshin lafiya.   Suna zaune jugum kowa yana tunanin yadda Moh zai idan ya dawo, ya ci karo da wannan mugun labarin duk uban tsaron da yake ganin ya zuba a gidan sa, lallai addu'a ce kawai mafita a wannan zamanin, dan a duk in da mutum yake ba wai ya tsira daga sharrin su bane.    Haka kawai yaji kamar bashi da lafiya, duk daukin da yake na zuwa gida ya ganta bayan tsawon lokacin sai yaji kamar duk guzarin sa na barin sa. Tun a airport din yaga kamar ma'aikatan na kallon sa, kallon da ya kasa gane na menene, sai kawai ya kyale hakan a wani dalili nasu da suka sani. Daga nesa ya hango motocin sa, suna jiran isowar sa, dora jacket dinsa yayi a saman kafadar sa ya shiga takawa zuwa wajen su dan basu ganshi ba. Sai da ya kusa daf dasu sannan suka ankara, duk suka taho da sauri kowa na kokarin riga dan uwansa isa, kayan hannun sa suka karba, aka bud'e masa motar ya shiga ya zauna. "Muje mana." Yace ganin yaki tada motar "I'm sorry sir." Yace sannan ya tada motar suka bi bayan su sauran. Sake neman layin Musaddik yake a lokaci daya yana neman nata amma duk magana daya ce, switch off, kansa ne ya daure sosai ta yadda za'a ce basu da charge a wayar su kuma tun jiya, be san me yasa ba, sai kawai yaji kamar babu lafiya. "Me ya faru?" "Na'am?" "Kaji ni ai, what's going on!" "I'm very sorry sir, bamu san yadda akayi hakan ta faru ba, amma we are trying our best kuma gaba daya k'asar ma." "Ban gane ba, me kake nufi?" "Kayi hakuri sir, in sha Allah za'a gansu." " Nace maka me ya faru? Me kake nufi?" Ya fad'a a tsawace yana tasowa kamar zai dake shi "Kayi hakuri sir, ana neman Madam da driver ta da House help din, tun jiya basu daw...** " What!!!" Ya fad'a da karfi "We are very sorry sir!" " Wannan zancen banza ne, zancen wofi, menene amfanin ku? Nace menene amfanin ku?" Ya harzuko sai kawai ya taka birki suka tsaya " Ta yaya akayi tun jiya basu dawo ba, kuma babu wanda zai kirani ya fad'a min? Tun jiya fa!" " Ohhh... Innalillah wa inna ilaihi rajiun, what's going on, me yake faruwa?" A cikin tsananin tashin hankali yayi maganar, zuwa lokacin idanun sa sun yi masifar kadawa, wani abu me karfi yazo ya tsaya masa a makoshi, ya dinga jin kamar ya kamasu yayi ta bugu har sai sun fada masa yadda akayi suka yi wannan sakacin.    Basu wuce gida kai tsaye ba, station suka wuce yana ta kiraye kirayen waya cikin karfin hali, ashe tuni labarin ya kai wa shugaban su har ma da abokan tafiyar sa amma kowa yayi masa kus, ransa yayi masifar baci, ga wani irin tashin hankali da yake ciki, yana tsoron wani abu ya faru da ita, ba zai taba yafewa kansa ba, ba kuma zai yafewa duk wanda yake da hannu a wannan al'amarin ba.      Duk bayanan da ya kamata ya samu ya samu a station, abu daya ne basu da tabbaci shine in da suke, dan duk babu waya a tare dasu,sannan an cire tracker din dake hade da motar ta daina aiki tun daga cikin school din anan ne last location din motar.    Jiri ne yaji yana kokarin kayar dashi k'asa, da sauri aka bashi kujera ya zauna yana dafe kansa, wayar sa da take ta faman kara alamun kira ya zaro yana duba number din, Ammi ce tun dazu take son su yi magana be samu dama ba, yace zai kirata amma kuma yasan ta kasa hakuri ne, kowa ya shiga tashin hankali da dimuwa kasancewar kuma har an kwana amma babu wani labari.     Daga wayar yayi muryar sa a chan ciki, ya gaida Ammin ta amsa cike da tausayawa tilon dan nata, tasan yana da karfin zuciya da kokarin maida komai ba komai ba a tsawon rayuwar sa bata ga wani abu da ya gigitashi ya firgita shi ba, amma tasan dole ne wannan tashin hankalin ba zai iya rik'e shi ba, ba zai iya shanye shi ba ace matar ka na hannun bata gari, ba kuma kasan abinda zai je ya dawo ba. Lallashi da ban baki ta dinga yi masa, tana so ko yaya ne ya kwantar da hankalin sa duk da tasan ba lallai ba, yaji ta ne kawai amma bashi da sukunin nan, yana cikin wasiwasi da tunanin wanda zai aikata masa wannan danyen aikin, idan kidnapping dinta akayi saboda ransom yasan tabbas zasu neme su a tsakanin kwana uku, amma kuma idan ba dan hakan bane fa? Tsoro ne ya kara kamashi, ya mike da k'yar cikin wasiwasin abinda zai je ya dawo, baya fatan wani abu daban ya bullo wanda be taba tunani ko hasashe ba, a tunanin sa duk wani me matsala dashi ba zai wuce gidan su ba, Kamal da mahaifiyar su, wambai da sauran masu goyon bayan Kamal din, bayan su, baya tunanin akwai wani da wata matsala ta hada su da har zai iya yi masa haka.    Tunanin sa ne ya katse, yana tuna abinda yake cikin flash din nan da ya bawa Musaddik, yana bukatar sake dubawa ko zai samu wata amsa a cikin video din, amma kuma ya kalla yafi sau nawa, sai dai kamar akwai wani abu da yake missing, be san menene ba, amma kuma zai koma baya ya sake dubawa sosai. Tunanin sa ne ya tsaya akan Kamal, dalilin da ya kaishi bangaren sa har ya ajiye masa wannan macijin robar, babu wani abu da ya dauka bayan wannan ajiyar da yayi,tashi yayi da sauri "Tracker ce!" Ya furta ba tare da yasan a fili yayi maganar ba. "Me kake tunani?" Shugaban yan sandan yace shima yana tashi tsaye "Kwanakin baya an ajiye min abu me kama da micijin robar irin na wasan yara a adamawa,ina kyautata zaton tracker ce a jiki, ya akayi nayi missing step din?" "Wa kake tunani?" " Bana tunanin kowa, amma koma waye ne, yana da alaka da wannan case din." " Ina macijin robar." " Yana gida!" " Nan ko adamawa?" " Yana nan..." "Ok muna bukatar shi ko zai taimaka mana wajen binciken mu." " Shikenan." Hannu ya mik'a masa " Sai naji daga gareku." " In sha Allah zamuyi kokarin mu." " Nagode." Ya juya ya fice yana ayyana yadda zai fara bibiyar su tamkar yadda suka dade suna bibiyar sa suma. " Kamal...! I'm coming for you." A waje ya tarar dasu Abba da wasu yan tsirarin makusantan fada, sai Musaddik da yake zaune daga gefe, wani kallo Moh yayi masa suna gaisawa dasu Abba suna jajantawa juna, sai ya taso ya iso wajen su, ya tsaya daga gefe suka gama gaisawa, tafiya Moh yace su Abba suyi saboda daren da ya fara yi sosai, sallama sukayi masa akan zasu dawo gobe jikin kowa a mace suka tafi gida. " Ina ka shiga?" Ya jeho masa tambayar bayan ya raka su Abba da ido sanda suke barin station din "Ina gida, bansan me yake faruwa ba saboda an dauke min waya a masallaci bayan mun idar da sallah jiya, sai Mom ce take fad'a min wai meenal ta gani a media shine...." "Is ok." Yace yana yin gaba " Menene kake shirin yi next?" Ya bishi yana tambayar shi " Me zanyi? Bayan case din yana hannun da ya dace, sai mu zuba ido mu gani." Yayi maganar kamar be damu da abinda ya farun ba, gid'a kai Musaddik yayi ya cigaba da bin bayan sa ganin yadda yake sauri kamar zai tashi sama. Har wajen mota ya rakashi, ya tsaya daga baya maimakon ya shiga kamar yadda suka saba, alamar ya akayi Moh yayi masa ganin ya toge daga baya be shigo ba " A mota nazo, zamuyi waya Allah ya bayyana ta Allah ya rufa asiri." " Ok." Kawai yace ya zuke glass din motar sama, suka bar wajen. "His acting strange, amma tun yaushe?" Ya tambayi kansa yana mamakin yanayin Musaddik din, share zancen yayi kawai ya lumshe idon sa, kirjin sa na masa wani irin suya. A harabar masarautar suka tsaida motocin, aka bud'e masa ya fito ya nufi ginin bangaren Takawa, yanayin tafiyar sa kadai zaka kalla ka gane tsantsar damuwar da tayi masa dabaibayi, har be san kalar tunanin da ya kamata yayi ba, a wanne hali take? Me taci me suke mata? Duk shin yake masa yawo akai, a daren yau ba sai gobe ba, zai fara aikin da yake ta jinkirtawa tsawon lokaci yana jiran right time kamar yadda yasha cewa, sai dai yanzu yana ji aransa shine right time din. Tun da ya shigo Takawa yake kallon sa cike da tausayawa, akwai sauran dauriya da jarumta a tattare dashi duk kuwa da babu kaso mafi rinjaye na karsashin sa, amma karya kake daga kallon fuskar sa ka iya tantance abinda yake wakana a zuciyar sa. Hakan ya dade yana bashi nasara akan duk mutanen da basa son shi, dan be basu kofar da zasu gano lagon sa ba, kuskuren sa daya, da yake kyautata zaton shi ya basu damar cutar dashi, shine yadda ya kasa boye son da yake mata, har ya zama musu wani tsani na ganin sun kaishi k'asa. Ya jima da sanin Kilishi bata son ko ganin wulgawar shi, haka Kamal yana cikin jerin mutanen da zasu iya yin komai don ganin bayan sa, sai kuma wambai da wasu mukarrabn fadar, sai dai asalin kiyayar ba tashi bace, ta mahaifiyar shi ce da suke ganin an auro ta daga gari irin na kano, suna ganin kamar hakan zai saka kanawa su zama sune zasu mulke su. Sai dai idan ka tattara duk wadannan mutanen toh zaka samu basu da wata alaka da iman din, balle idan sun cutar da ita su amfana da wani abu, hakan ya saka kansa ya sake chunkushewa, ya rasa kalar tunanin da zai. Zubewa yayi agaban Takawar, sai a lokacin yaji kamar an zare duk wani karfin zuciyar sa, yaji bashi da sauran katabus, yaji komai masa ya saki, sai ya dinga jin sa tamkar wani karamin yaron da aka dake shi aka kuma hanashi kuka. "Karka yi kokarin shanye bacin ran da kake ciki muhammadu, ka fitar da komai zaka ji sauki." Jan jikin sa yayi zuwa gaban Takawan, ya kwantar da kansa a saman cinyar sa. Ya jima sosai a haka, kafin ya fara jin nutsuwa na saukar masa, sai a lokacin ya dago, ya zauna daidai. "Sannu, babu abinda zai faru in sha Allah, zasu dawo lafiya lou." "In Sha Allah." ***Babu wanda batan Iman be girgiza ba, hatta Mama da take ikirarin bata son ta sai da taji babu dadi, gidan ya cika duk kowa ya zo suna zaman jajantawa juna, zeenat dama ko da Habib ya kaita gidan su Bashir din achan suka same shi, yace su dawo zai zo da daddare sai su tafi, haka suka sake kwaso kafa suka dawo gashi shiru be zo ba har washegari sai kuma wannan bakin labarin. Mummy da Mamma sun zo a ranar suma, suka sauka a gidan Iman din, kana kallon su kasan suna cikin tashin hankali, kowa baya cikin nutsuwar sa musamman Abba, da mahaifiyar ta wanda suka fi kowa kusanci da ita idan ka cire mijinta. Shi ba zaka taba gane ainahin yanayin da yake ciki ba. Tunda ya shigo gidan ya shige daki ya kulle kansa, ya dauko system din sa ya jona ta, yayi playing video din nan yana son ganin wani abu. Ya dade sosai a dakin, har ma suka manta da ya shigo gidan, ba laifi gidan da mutane wanda suka zo daga chan gidan sarki, sai su Ya Maryam da yan uwa dai na kusa. Duk suna jiran tsammani. ***Sosai take galabaita saboda aman da take ta faman yi, babu wani abu da yake zama a cikin ta komai taci sai ta dawo dashi, zuwa lokacin ta gama galabaita dan ko tashi bata iyayi komai sai dai Ummimi tayi mata. Sau biyu yana fad'a musu cewa gimbiya ta bata da lafiya amma suka yi biris da ita, suka kyaleta a cikin wahalar suna sane da labarin yadda ake neman su babu dare babu rana, duk wani moves din da jami'an tsaron suke suna sane dashi. Sigari ya zuka ya fezar, sannan ya karbi sabbin layukan da ya saka aka kawo masa wajen guda hamsin, daya ya dauka, ya mik'a hannu ya dauki yar karamar waya a gefen sa ya saka, ya hau kai yayi murmushi ya shiga text message ya saka number Moh, ya rubuta _"Ba kudi muke bukata ba, rayuwar ka muke bukata a matsayin fansa ga rayuka biyu masu muhimmanci a wajen ka, matar ka da cikin da take dauke dashi." _ Yana tura wa ya balla sim din, ya kyalkyale da mahaukaciyar dariya. _" Let the game begins Captain MAS!" _ _ZAFAFA2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 8 2/19/22, 19:58 - Buhainat: Halin Girma 38 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw **** Zaune yake a office din commissioner of police lokacin da message din ya shigo wayar, karantawa yayi yana kai karshe ya mike tsaye da sauri. "Ya akayi?" CP ya tambaya shi yana kallon yana yin sa "Akwai matsala..." Sai ya mik'a masa wayar ya soma zagaye a cikin office din cikin tsananin tashin hankali, idan har akwai ciki a jikin Iman toh lallai tana cikin halin tashin hankali, yasan yadda ciki musamman a watannin farko yadda yake wahalar wa yawa yawan mata suna shan wahala kafin ciki yayi kwari wasu kamar zasu rasa ransu saboda tsabar wahala. Ya take ciki yanzu? Me take ci? "Akwai wani da kake da matsala dashi banda matsala ta cikin gida?" CP ya tambaye shi bayan ya maimaita karanta sakon fiye da sau goma, har ya gano abu daya a cikin sakon, akwai kiyayye me zafin gaske tsakanin duk wanda ya turo sakon, duk wanda yake son ranka ba karamin kiyayye yake maka.   Girgiza kai yayi ba tare da yayi magana ba, "Idan ka gamsu da maganganun da mukayi, lallai muna da bukatar Kamal a binciken mu, domin idan har ka tattara bayanan baya da na yanzu zaka gane akwai wani abu da yake a boye a bayan dukkan cases din, case din ka da Laila, evidence din da ya wanke ka, sannan matar ka, zai iya yiwuwa wani ne da yake son ta tun ba yanzu ba, ko kuma wanda yake da matsala da kai ne amma shi da kansa yake son daukar fansa shiyasa har yayi kokarin wanke ka a baya, duk wannan tunani na ne, ban ce ya zama gaskiya ba, amma ina ji a raina, cases din suna da alaka da juna." Zama ya kuma yayi a kujerar da ya tashi yana tattare bayanan dukka a kwakwalwar kansa, jiya baki daya ranar a cikin bincike yayi ta, babu mutum daya da binciken sa ya nuna masa sai Kamal. Evidence din farko shine sanda ya shiga bangaren sa, sai na biyu da suke zaune suna magana da wani mutum ya sunkuyar da kansa, wata mace a gefen sa itama babu fuskar ta, fuskar Kamal din ce kadai ta nuna wanda ya tabbata shi be sani ba, yana kyautata zaton gadar zare suka danawa Kamal din sukayi amfani da son mulkin sa suka samu abinda suke so sannan suka yi dumping din sa. "Duk abinda ya kamata ayi, ayi Sir." "Zamu fara da Kamal, ina fatan hakan ba zai zama matsala ga Maimartaba ba." "In Sha Allah." Yace yana mikewa, jiri ne ya debe shi, yayi kamar zai fadi da sauri CP ya tashi yana riko shi "Subhanallah, Capt akwai matsala ba, sai ka daure saboda tana matukar bukatar taimakon ka a wannan gabar." Gid'a masa kai yayi yana rik'e kansa da yake mugun sarawa, be runtsa ba tunda ya diro garin Kano, ba kuma yajin idan ka cire ruwa ya sakawa cikin sa wani abu, sai da ya dawo daidai sannan ya mike yayi masa sallama, ya rakashi da ido yana yaba wa kwazon sa. ***Gidan su Iman din ya wuce kai tsaye, dan sunyi waya da Abba da safe yake ce masa bashi da lafiya, kamar ma bp din sa ne yayi sama, yasan batan Iman din ne ya saka shi shiga matsalar.    A kofar gida ya tarar da Habib da saurayin nan na ranar nan, dauke kai yayi kamar be gansu ba, sai da Habib din ya taso yazo wajen sa yana kokarin kiran waya. "Sannu da zuwa." "Ah... Babban Yaya." Ya mik'a masa hannu suka gaisa, sannan yayi masa jajen abinda ya faru, suna maganar Mahfuz ya karaso wajen, ya mik'a masa hannu kansa tsaye, kamar ba zai bashi hannun ba, sai kuma ya mik'a masa a dakile suka gaisa. "Zanga Abba." "Owk Bismillah." Yayi gaba, shi kuma suka biyo bayan shi tare da Mahfuz har part din su, Abba na kwance a falo kan doguwar kujera, Mama ta shiga ciki dauko Hijab suka shigo, ya durkusa har k'asa ya gaida Abban, wanda yake kallon sa ciki da tausayawa, ya ga dauriyar sa sosai dan kana kallon sa zaka gane yadda ya tabu, ya rame sosai amma be karaya ba, be kuma zauna ba tun da ya dawo. "Akwai labari ne muhammadu?" "In sha Allah Abba, ana iyakar kokari." "Toh basu kira ba har yanzu ko?" "Basu kira ba Abba." "Shikenan Allah ya dawo mana dasu cikin koshin lafiya." "Amin Abba" "Sannu da kokari, kai ma Allah ya biyaka, Allah ya tona asirin azzalumai, tun jiya ban runtsa ba, na rasa in da zan saka raina naji dadi, shikenan mutun bashi da daraja a k'asar nan tamu? Ace satar mutum tafi satar kaza sauki? Wannan wacce irin musiba ce... Allahumma ajirni fi musibati..." "Allah ya bayyana su." " Amin ya Allah. " Suka hada baki gaba daya, shigowar Mama da Zeenat a bayan ta ne ya katse maganar da Moh yaso yayi, ya dan kalle su sai ya dauke kai ya maida wajen Abba da alamun sa ya nuna yana jin jiki. Gaisawa sukayi da Mama sama sama tayi masa jaje, sannan Zeenat da gaishe shi itama ya amsa yana mikewa. "Bari na koma Abba, duk yadda ake ciki zan kira dan Allah ka kwantar da hankalin ka." "Shikenan, Allah yasa muji alkhairi." " Sai anjima." Ya dan kalli gefen da Mama take ya fad'a sannan ya fice Habib da Mahfuz suka bi bayan sa, sun kusan kai gate din gidan Mahfuz yace " Zan iya taimakawa." Tsayawa chak Moh yayi da tafiyar da yake ya juyo. "Idan har zaka yarda zan iya taimakawa." "How? Ta yaya?" "Security ne from an intelligent agency a UK." "Sounds good." Moh yace yana dan rage hadewaar fuskar sa. Sai ya bud'e hannun sa alamun babu matsala yace "Idan har zaka iya taimakawa, shikenan sai muje ko?" "Let me freshen up, zan zo daga baya. Ina zan same ka?" " Habib ka rakoshi gida na, don't take long please." " In Sha Allah." Juyawa yayi ya fice su kuma suka koma ciki don Mahfouz ya shirya, anan suka tarar da Gaji a part din ta saka Abba a gaba tana ta rusa kuka, bata samu labarin ba sai da Moh yazo yanzu sannan tasan abinda yake faruwa, taji zancen a radio har ta tausaya amma bata kawo Iman bace ,bata ma fuskanci zancen ba kwata kwata ma gaba daya. Baki Abba yake bata akan tayi hakuri amma taki, sai kuka take ita lallai sai an kaita gidan Iman din, a dole haka Abba ya saka tabi su Habib din ko ta barshi ya ji da kansa shima kawai dauriya ce irin ta namiji.    Yana shiga gidan ya tarar da motocin masarauta, ciki ya shiga kansa tsaye, da mamaki yake kallon Fulani a zaune a falon nasu, tare da mummy da Mamma sai wasu matan, suna zaune jingum jingum cikin alhini da jimami, daga gefe hadiman Fulanin ne suma a falon, kallo daya yayi ma duk matan falon, ya karasa gaban Fulanin ya durkusa ya gaishe ta, ta amsa muryar ta na rawa alamun  bata dade da gama kuka ba, juyawa yayi ya gaida su mummy wanda sai a lokacin ya samu ganin su, ta fad'a tayi fayau amma kuma a nutse take sosai, sai yace ma Mamma ta fita fita hayyacin ta, wuce su yayi zuwa ciki, suka rakashi da kallon tausayawa.    Dafe kansa yayi bayan ya zauna a gefen gadon, komai nata yana nan a dakin hatta da handouts din da ta fito dasu ranar da zata tafin gasu nan a saman gado, be san me yasa abubuwan suka juye masa a yadda be yi zato ko tsammani ba. Wayar sa ce tayi kara, ya dauka yana kallon sunan, Bubu ne "Menene alakar Kamal da batan matar ka?" "Barka da rana Bubu..." "Barka dai, ya mukaji da alhinin? Allah ya bayyana su cikin koshin lafiya." "Amin ya Allah." "Ina jin ka, menene alakar Kamal da batan matar ka?" Saman goshin sa ya shafa kad'an, kafin yace "Bincike ne ya kawo hakan Bubu." "Shikenan, Allah ya sa muji alkhairi." "Amin ya Allah." Yace sannan sukayi sallama.    A tsammanin sa Musaddik zai neme shi da zarar gari ya waye, ya kuma rakashi duk wani waje da zai je, amma kuma ga mamakin sa sai gashi har rana ta daga babu ko waya daga gareshi, bayan yafi kowa sanin muhimmancin da Iman take dashi a wajen sa, shine mutum na farko kuma na karshe da ya yarda dashi kaf duniyar nan idan ka cire mutane hudu mafiya kusanci dashi, Ammin sa, Takawa, Aji da Bubun sa, bayan su be yarda da kowa ba sai Musaddik wanda ya yarda da tsantsar kaunar da shi ma yake masa, fiye da wadda shi yake masa, say da yawa Musaddik ya sha shiga rigima saboda shi, ya kuma sha shiga tashin hankali saboda shi, amma kuma ya kasa gane dalili daya, da zai saka Musaddik din kasa jajanta masa kamar yadda ya saba a baya, duk wani abu masa tare sukeyi.    Tashi yayi yana dan zazzagaya dakin, yana so ya dauke tunanin daga zuciyar sa,yana so yayi wa Musaddik din uzuri a karo na farko kasancewar dan Adam ajizi ne, watakila wani uzurin ne ya danne wannan din. Wayar sa ce tayi kara, ya matsa yana dubawa, sakon text message ne from an unknown number, da sauri ya dauki wayar yana dubawa. _"Ka shirya?"_ Da sauri ya maida masa reply "Waye kai, me kake so?" Sai da aka dau lokaci sannan akayi reply da wata number daban "Ashe har kana da lokacin tsayawa tambayar waye bayan rayuwar matar ka da ke cikin hatsari." "Ina zamu hadu? Ka dawo da ita nayi maka alkawarin zan kawo maka kai na da kai na." Nan ma sai da aka sake daukar lokaci kafin yayi masa reply da wata number daban kuma _"Idan na shirya zan neme ka, karka bata lokaci wajen tracking din number, ba zaka taba samu ba." _ Kiran number yayi da sauri, amma sai yaji ta a kashe, ya bi sauran layukan da sukayi magana suma duk a kashe, text message ya turawa CP na numbers din dukka.     Kira ne ya shigo wayar sa daga gate din gidan, kamar be zai daga ba sai kuma ya tuno da zuwan su Habib, dagawa yayi suka tambaye shi ko yasan su, yace a farsu su shigo brothers din Iman ne, da haka ya kashe ya sauya rigar sa zuwa mara nauyi saboda zafin da yake ji. ***Dagata Ummimi tayi ta taimaka mata bayan ta gama amai, ta gyara wajen ta dawo ta tsugunna a gabanta tana mata sannu, da kai ta amsa mata, ta rufe idon ta hawaye ya gangaro mata. Shigowa sukayi su hudu, shine a gaba suna bin bayan sa, ya zo gabanta ya durkusa ya saka hannu ya dago kanta. "Fine Lady." Ya shafi gefen fuskar ta, ta saka ragowar karfin da take dashi ta ture shi, ya tuntsure da dariya yana kallon ta "Ga Dr nan zai duba min ke, dan ina tunanin nine zan maye gurbin Capt bayan na aikashi barzahu, kina da kyau." "Dr matso, a duba min da kyau idan har ciki ne, a cire shi ko ta yaya ne, ba zan iya jure ganin sa ba, kaga auren mu ba zai dau lokaci ba idan aka cire shi." Matsawo likitan yayi, ya bud'e idon ta, sannan ya taba goshin ta, ya dauko wata roba a cikin kayan sa ya mikawa Ummimi. " Gashi fitsari zatayi." Kin karba tayi, na bayan ya daka mata tsawa, ta karba da sauri tana daga Iman din, dukkan su hawaye suke amma babu me bud'e baki yayi musu saboda tsoro. Tare sukaje tayi fitsarin suka fito ta dawo ta kawo masa, ya karba a wajen ya duba, ya kuma tabbatar da ciki ne, yan tambayoyi yayi mata akan period dinta ta amsa tana kuka. "Ciki ne oga, na sati shida." "Ya za'a yi dashi?" "Ba zai wahalar fita ba, tunda karami ne. Yanzu dai zan dawo sai nazo da maganin da zata sha." "Yayi kyau, rakashi yaro." Rik'e masa jaka wanda aka kira da yaro yayi suka fita, sannan shi ma suka fita. "Hello... Samha baby." Ya fad'a da yaji ta daga wayar "Eh tana hannu har yanzu." "Eh ya tabbatar da ciki ne, amma za'a cire shi tunda baki da bukatar shi." "A ah... Babu fa abinda zan yi wa masoyinki, kawai wata yar harkalla ce zamu karasa ta. " " Yawwa toh" tace tana jin dadi. " Sai mun sake magana ko? " " Amma ai bana samun ka kwata-kwata a waya, me yasa?" " Babu komai, idan akwai bukatar muyi magana ni zan kiraki da kai na." " Shikenan." Dariya yayi sosai bayan sun gama maganar, be san bata da tunani ba kwata-kwata sai yanzu, amfani yayi da ita ya samu abinda yake so, ba kuma zai kyale wanda ta kwallafa rai akai ba, ba zata taba samun cikar burin ta ba in dai yana numfashi. ***A waje ya tarar da su Habib din bayan ya gama parker motar, ganin tare suke da Gaji ya sakashi saurin karasawa ya taimaka mata ta fito, sannan suka gaisa ya saka aka rakata ciki su kuma yace su biyo shi garden dake baya. Kujeru ne a wajen, ya zauna sannan suka zauna suma, yana karantar yanayin Mahfuz din, sai a lokacin yayi masa kallon tsaf, ya kuma fahimci hakan yanayin sa ne, ku kuma yanayin environment din da ya taso kamar yadda Habib yayi masa bayani dazu. "Ta yaya zaka iya taimakawa?" Yace bayan ya gama nakaltar yanayin sa, gyara zama yayi sosai, yayi murmushi sannan yace zai masa yan tambayoyi,da ka ya amsa masa ya bashi go ahead. "Babu wani message ko kira da ka samu daga wajen kidnappers din?" "Akwai." "Zan iya gani?" "Why not?" Ya mik'a masa wayar, ya karba ya duba messages din dukka, ya jima yana sake dubawa kafin ya mik'a masa wayar sa "Kayi tunani sosai, wanene kake da matsala dashi, irin wadda kasan lallai da zai samu dama akan ka zai iya aikata maka komai?" "Babu shi, bansan waye ba gaskiya." " Babu ko old friend? Ko abokin aiki?" Shiru yayi cikin tunani " Think... " _" Zan dawo komai daren dadewa, sai na dauki fansa akan ka, ko da zan karar da komai da na mallaka ma duniya sai na maida rayuwar ka abun kwatance! "_ "JABIR! " Yace yana mikewa tsaye da sauri, tashi Mahfuz yayi shima yana kallon sa " Waye shi. " " Aboki na ne, abokin aiki na ne. " " Recently na samu labarin ya zama babban terrorist kuma yana da connection da manyan k'asar, bayan shi bana tunanin akwai wanda zai bukaci rayuwa ta, babu. " "Ya akayi na manta? Ya akayi? " " Kasan in da za'a same shi? " Girgiza kai yayi, " Ban sani ba. " Komawa sukayi suka zauna, Mahfuz ya ciro biro da paper ya rubuta wani abu, daidai lokacin da Moh ya daga wayar Musaddik yace ya same shi a garden, yana ajiye wayar sai gashi ya zagayo dama chan yana cikin gidan, da kallo Mahfuz ya bishi kafin ya karaso wajen yace "Waye shi?" "Best friend dina ne." "Ok." Yace a gajarce ganin ya karaso, ya mik'a musu hannu suka gaisa amma da ya bawa Mahfuz hanun sai ya rik'e hannun nasa har sai da suka kalle shi dukka, sai ya saki yana murmushi ya jingina da kujerar da yake kai, wani kallo Musaddik yayi masa ya zauna yana maida hankalin sa kan Moh. "I'm very sorry Capt..." "Babu komai, nasan wani uzuri ne dakai." Ya katse shi kafin ya karasa. "Babu wani progress ko?" Yace "Babu." "Allah ya bayyana su." "Amin." "Ya aiki?" Mahfuz ya tambayi Musaddik unexpectedly "Aiki Alhamdulillah." "Wanne aiki kake?" "Harkar kwangila, kaifa?" "Detective!" Wani kallo Musaddik yayi masa, yayi shiru,.sai kuma ya kalli Moh "Naga kamar kana da baki, dama inaso muyi maganar flash din nan ne tunda naga ka dawo." "Flash?" Mahfuz yayi karaf ya tambaya "Let's talk about that later." Moh yace sai ya mik'a wa Musaddik hannu "Suna ina?" Sosa kansa yayi "Dalilin da yasa kaga kamar ina janye kaina a case din nan kenan, wallahi bansan ya akayi ba, na rasa su gaba daya." "What!" "Kayi hakuri,ranar da aka sace wayata aka hada dasu gaba daya, bansan ya zan maka bayani ba, nasan kuma muhimmancin flash din a wajen ka, shiyasa na kasa nutsuwa." Murmushi kawai Mahfuz yayi, ya dire pen din hannun sa akan dan deborin da yake gaban sa, ya dora hannun sa akai ya jingina yana masa kallon tsaf. " Idan nace wani abu zaka yarda dani?" Girgiza masa kai Moh yayi dan maganar batan flash din ba karamin bashi mam I'llaki tayi ba. "Ina bukatar yara hudu cikin yaranka na gate." " Me zasuyi maka?" Musaddik yace ransa a bace. " Wait and see." Yayi murmushi, shi Moh ba gane kan maganar ba kwata kwata, yayi dai abinda Mahfuz yace ya kirawo su suka zo, suka tsaya daga gefe, tashi Mahfuz yayi ya zagayo ta bayan Musaddik, "Take off your mask!" "Kamar ya?" "Me kake nufi Mahfuz?" Moh da shima ya mike ya fad'a cike da mamaki " This man is deceiving you, ka kalli hannun sa, ka kalli fuskar sa, akwai banbancin skin color, he's definitely using a mask, idan har ya musa, zan tabbatar maka." "Noo...you are mistaken, wannan Musaddik ne, trusted friend dina ba zai taba deceiving dina ba,you cannot accused somebody without a proof." " Shine zan maka proving yanzu ai, wait and see, guys... Ku rik'e shi." " Dakata!" Moh yace ransa na baci, ba zai dauki wulakanta Musaddik yana kallo ba. "Waye wannan Capt, waye zai zo ya shiga tsakani na da kai?" "Calm down aboki na, misunderstanding aka samu amma zan masa magana..." Sai ya juya wajen Mahfuz din "Let's call it a day, zamuyi magana gobe, Habib ku jirani a wajen mota." "Muje Mahfuz." Wani kallo yabi Musaddik din dashi, sannan ya juya suka bar wajen da Habib. Juyawa kan Musaddik yayi da ransa yayi masifar baci, ya shiga bashi hakuri akan abinda Mahfuz din yayi, yace ya jirashi yana zuwa bari ya sallame su. Yana barin wajen ya ciro waya, ya kira shi yana matsawa chan gaba. "Akwai matsala." Yana dagawa yace "Ya fara suspecting dinka ne?" "Be fara ba, wani banzan yaro ne bansan daga ina yazo ba, yaso dole sai ya nuna masa gaskiyar mask da na saka..." "Ya yadda?" "Be yarda ba, kasan ya yarda dani sosai, so ba zai taba kawowa ba. " " You have to be very careful, shi kuma yaron zan san yadda zan yi dashi. " " Ok sir. " Ya kashe wayar yana juyowa, sukayi ido biyu da Moh da yake tsaye a bayan sa kamar mayunwacin zakin da ya shekara be ce ba. ***Assalamu alaikum sisters, masu korafi naga wasu daga cikin korafin ku, ina mai baku hakuri akan matsalolin da aka samu, dan gane da rashin posting halin girma shekaran jiya da jiya, hakan ya faru ne sakamakon ciwon hakorin da ya matsa min hade da zazzabi, wanda har ta kai ban iya samun duba sakonni ba balle har na iya zaman rubutu Duk cikin zafafa biyar babu wadda a cikin mu take jin dadi a duk sanda batayi posting ba, Allah ne shaida ana iyakar kokari wajen ganin Anyi abinda ya dace. Sai dai idan abu ya sha kan mutum a ba yadda ya iya. Allah ya huci zuciyar duk wanda ransa ya baci ta dalilin jira ko wani abu, ba da gangan bane wani lokacin kuma ajizanci ne na dan Adam. Allah ya rufa asiri ya sa mu gama lafiya 2/21/22, 08:16 - Buhainat: Halin Girma 38 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw **** Zaune yake a office din commissioner of police lokacin da message din ya shigo wayar, karantawa yayi yana kai karshe ya mike tsaye da sauri. "Ya akayi?" CP ya tambaya shi yana kallon yana yin sa "Akwai matsala..." Sai ya mik'a masa wayar ya soma zagaye a cikin office din cikin tsananin tashin hankali, idan har akwai ciki a jikin Iman toh lallai tana cikin halin tashin hankali, yasan yadda ciki musamman a watannin farko yadda yake wahalar wa yawa yawan mata suna shan wahala kafin ciki yayi kwari wasu kamar zasu rasa ransu saboda tsabar wahala. Ya take ciki yanzu? Me take ci? "Akwai wani da kake da matsala dashi banda matsala ta cikin gida?" CP ya tambaye shi bayan ya maimaita karanta sakon fiye da sau goma, har ya gano abu daya a cikin sakon, akwai kiyayye me zafin gaske tsakanin duk wanda ya turo sakon, duk wanda yake son ranka ba karamin kiyayye yake maka.   Girgiza kai yayi ba tare da yayi magana ba, "Idan ka gamsu da maganganun da mukayi, lallai muna da bukatar Kamal a binciken mu, domin idan har ka tattara bayanan baya da na yanzu zaka gane akwai wani abu da yake a boye a bayan dukkan cases din, case din ka da Laila, evidence din da ya wanke ka, sannan matar ka, zai iya yiwuwa wani ne da yake son ta tun ba yanzu ba, ko kuma wanda yake da matsala da kai ne amma shi da kansa yake son daukar fansa shiyasa har yayi kokarin wanke ka a baya, duk wannan tunani na ne, ban ce ya zama gaskiya ba, amma ina ji a raina, cases din suna da alaka da juna." Zama ya kuma yayi a kujerar da ya tashi yana tattare bayanan dukka a kwakwalwar kansa, jiya baki daya ranar a cikin bincike yayi ta, babu mutum daya da binciken sa ya nuna masa sai Kamal. Evidence din farko shine sanda ya shiga bangaren sa, sai na biyu da suke zaune suna magana da wani mutum ya sunkuyar da kansa, wata mace a gefen sa itama babu fuskar ta, fuskar Kamal din ce kadai ta nuna wanda ya tabbata shi be sani ba, yana kyautata zaton gadar zare suka danawa Kamal din sukayi amfani da son mulkin sa suka samu abinda suke so sannan suka yi dumping din sa. "Duk abinda ya kamata ayi, ayi Sir." "Zamu fara da Kamal, ina fatan hakan ba zai zama matsala ga Maimartaba ba." "In Sha Allah." Yace yana mikewa, jiri ne ya debe shi, yayi kamar zai fadi da sauri CP ya tashi yana riko shi "Subhanallah, Capt akwai matsala ba, sai ka daure saboda tana matukar bukatar taimakon ka a wannan gabar." Gid'a masa kai yayi yana rik'e kansa da yake mugun sarawa, be runtsa ba tunda ya diro garin Kano, ba kuma yajin idan ka cire ruwa ya sakawa cikin sa wani abu, sai da ya dawo daidai sannan ya mike yayi masa sallama, ya rakashi da ido yana yaba wa kwazon sa. ***Gidan su Iman din ya wuce kai tsaye, dan sunyi waya da Abba da safe yake ce masa bashi da lafiya, kamar ma bp din sa ne yayi sama, yasan batan Iman din ne ya saka shi shiga matsalar.    A kofar gida ya tarar da Habib da saurayin nan na ranar nan, dauke kai yayi kamar be gansu ba, sai da Habib din ya taso yazo wajen sa yana kokarin kiran waya. "Sannu da zuwa." "Ah... Babban Yaya." Ya mik'a masa hannu suka gaisa, sannan yayi masa jajen abinda ya faru, suna maganar Mahfuz ya karaso wajen, ya mik'a masa hannu kansa tsaye, kamar ba zai bashi hannun ba, sai kuma ya mik'a masa a dakile suka gaisa. "Zanga Abba." "Owk Bismillah." Yayi gaba, shi kuma suka biyo bayan shi tare da Mahfuz har part din su, Abba na kwance a falo kan doguwar kujera, Mama ta shiga ciki dauko Hijab suka shigo, ya durkusa har k'asa ya gaida Abban, wanda yake kallon sa ciki da tausayawa, ya ga dauriyar sa sosai dan kana kallon sa zaka gane yadda ya tabu, ya rame sosai amma be karaya ba, be kuma zauna ba tun da ya dawo. "Akwai labari ne muhammadu?" "In sha Allah Abba, ana iyakar kokari." "Toh basu kira ba har yanzu ko?" "Basu kira ba Abba." "Shikenan Allah ya dawo mana dasu cikin koshin lafiya." "Amin Abba" "Sannu da kokari, kai ma Allah ya biyaka, Allah ya tona asirin azzalumai, tun jiya ban runtsa ba, na rasa in da zan saka raina naji dadi, shikenan mutun bashi da daraja a k'asar nan tamu? Ace satar mutum tafi satar kaza sauki? Wannan wacce irin musiba ce... Allahumma ajirni fi musibati..." "Allah ya bayyana su." " Amin ya Allah. " Suka hada baki gaba daya, shigowar Mama da Zeenat a bayan ta ne ya katse maganar da Moh yaso yayi, ya dan kalle su sai ya dauke kai ya maida wajen Abba da alamun sa ya nuna yana jin jiki. Gaisawa sukayi da Mama sama sama tayi masa jaje, sannan Zeenat da gaishe shi itama ya amsa yana mikewa. "Bari na koma Abba, duk yadda ake ciki zan kira dan Allah ka kwantar da hankalin ka." "Shikenan, Allah yasa muji alkhairi." " Sai anjima." Ya dan kalli gefen da Mama take ya fad'a sannan ya fice Habib da Mahfuz suka bi bayan sa, sun kusan kai gate din gidan Mahfuz yace " Zan iya taimakawa." Tsayawa chak Moh yayi da tafiyar da yake ya juyo. "Idan har zaka yarda zan iya taimakawa." "How? Ta yaya?" "Security ne from an intelligent agency a UK." "Sounds good." Moh yace yana dan rage hadewaar fuskar sa. Sai ya bud'e hannun sa alamun babu matsala yace "Idan har zaka iya taimakawa, shikenan sai muje ko?" "Let me freshen up, zan zo daga baya. Ina zan same ka?" " Habib ka rakoshi gida na, don't take long please." " In Sha Allah." Juyawa yayi ya fice su kuma suka koma ciki don Mahfouz ya shirya, anan suka tarar da Gaji a part din ta saka Abba a gaba tana ta rusa kuka, bata samu labarin ba sai da Moh yazo yanzu sannan tasan abinda yake faruwa, taji zancen a radio har ta tausaya amma bata kawo Iman bace ,bata ma fuskanci zancen ba kwata kwata ma gaba daya. Baki Abba yake bata akan tayi hakuri amma taki, sai kuka take ita lallai sai an kaita gidan Iman din, a dole haka Abba ya saka tabi su Habib din ko ta barshi ya ji da kansa shima kawai dauriya ce irin ta namiji.    Yana shiga gidan ya tarar da motocin masarauta, ciki ya shiga kansa tsaye, da mamaki yake kallon Fulani a zaune a falon nasu, tare da mummy da Mamma sai wasu matan, suna zaune jingum jingum cikin alhini da jimami, daga gefe hadiman Fulanin ne suma a falon, kallo daya yayi ma duk matan falon, ya karasa gaban Fulanin ya durkusa ya gaishe ta, ta amsa muryar ta na rawa alamun  bata dade da gama kuka ba, juyawa yayi ya gaida su mummy wanda sai a lokacin ya samu ganin su, ta fad'a tayi fayau amma kuma a nutse take sosai, sai yace ma Mamma ta fita fita hayyacin ta, wuce su yayi zuwa ciki, suka rakashi da kallon tausayawa.    Dafe kansa yayi bayan ya zauna a gefen gadon, komai nata yana nan a dakin hatta da handouts din da ta fito dasu ranar da zata tafin gasu nan a saman gado, be san me yasa abubuwan suka juye masa a yadda be yi zato ko tsammani ba. Wayar sa ce tayi kara, ya dauka yana kallon sunan, Bubu ne "Menene alakar Kamal da batan matar ka?" "Barka da rana Bubu..." "Barka dai, ya mukaji da alhinin? Allah ya bayyana su cikin koshin lafiya." "Amin ya Allah." "Ina jin ka, menene alakar Kamal da batan matar ka?" Saman goshin sa ya shafa kad'an, kafin yace "Bincike ne ya kawo hakan Bubu." "Shikenan, Allah ya sa muji alkhairi." "Amin ya Allah." Yace sannan sukayi sallama.    A tsammanin sa Musaddik zai neme shi da zarar gari ya waye, ya kuma rakashi duk wani waje da zai je, amma kuma ga mamakin sa sai gashi har rana ta daga babu ko waya daga gareshi, bayan yafi kowa sanin muhimmancin da Iman take dashi a wajen sa, shine mutum na farko kuma na karshe da ya yarda dashi kaf duniyar nan idan ka cire mutane hudu mafiya kusanci dashi, Ammin sa, Takawa, Aji da Bubun sa, bayan su be yarda da kowa ba sai Musaddik wanda ya yarda da tsantsar kaunar da shi ma yake masa, fiye da wadda shi yake masa, say da yawa Musaddik ya sha shiga rigima saboda shi, ya kuma sha shiga tashin hankali saboda shi, amma kuma ya kasa gane dalili daya, da zai saka Musaddik din kasa jajanta masa kamar yadda ya saba a baya, duk wani abu masa tare sukeyi.    Tashi yayi yana dan zazzagaya dakin, yana so ya dauke tunanin daga zuciyar sa,yana so yayi wa Musaddik din uzuri a karo na farko kasancewar dan Adam ajizi ne, watakila wani uzurin ne ya danne wannan din. Wayar sa ce tayi kara, ya matsa yana dubawa, sakon text message ne from an unknown number, da sauri ya dauki wayar yana dubawa. _"Ka shirya?"_ Da sauri ya maida masa reply "Waye kai, me kake so?" Sai da aka dau lokaci sannan akayi reply da wata number daban "Ashe har kana da lokacin tsayawa tambayar waye bayan rayuwar matar ka da ke cikin hatsari." "Ina zamu hadu? Ka dawo da ita nayi maka alkawarin zan kawo maka kai na da kai na." Nan ma sai da aka sake daukar lokaci kafin yayi masa reply da wata number daban kuma _"Idan na shirya zan neme ka, karka bata lokaci wajen tracking din number, ba zaka taba samu ba." _ Kiran number yayi da sauri, amma sai yaji ta a kashe, ya bi sauran layukan da sukayi magana suma duk a kashe, text message ya turawa CP na numbers din dukka.     Kira ne ya shigo wayar sa daga gate din gidan, kamar be zai daga ba sai kuma ya tuno da zuwan su Habib, dagawa yayi suka tambaye shi ko yasan su, yace a farsu su shigo brothers din Iman ne, da haka ya kashe ya sauya rigar sa zuwa mara nauyi saboda zafin da yake ji. ***Dagata Ummimi tayi ta taimaka mata bayan ta gama amai, ta gyara wajen ta dawo ta tsugunna a gabanta tana mata sannu, da kai ta amsa mata, ta rufe idon ta hawaye ya gangaro mata. Shigowa sukayi su hudu, shine a gaba suna bin bayan sa, ya zo gabanta ya durkusa ya saka hannu ya dago kanta. "Fine Lady." Ya shafi gefen fuskar ta, ta saka ragowar karfin da take dashi ta ture shi, ya tuntsure da dariya yana kallon ta "Ga Dr nan zai duba min ke, dan ina tunanin nine zan maye gurbin Capt bayan na aikashi barzahu, kina da kyau." "Dr matso, a duba min da kyau idan har ciki ne, a cire shi ko ta yaya ne, ba zan iya jure ganin sa ba, kaga auren mu ba zai dau lokaci ba idan aka cire shi." Matsawo likitan yayi, ya bud'e idon ta, sannan ya taba goshin ta, ya dauko wata roba a cikin kayan sa ya mikawa Ummimi. " Gashi fitsari zatayi." Kin karba tayi, na bayan ya daka mata tsawa, ta karba da sauri tana daga Iman din, dukkan su hawaye suke amma babu me bud'e baki yayi musu saboda tsoro. Tare sukaje tayi fitsarin suka fito ta dawo ta kawo masa, ya karba a wajen ya duba, ya kuma tabbatar da ciki ne, yan tambayoyi yayi mata akan period dinta ta amsa tana kuka. "Ciki ne oga, na sati shida." "Ya za'a yi dashi?" "Ba zai wahalar fita ba, tunda karami ne. Yanzu dai zan dawo sai nazo da maganin da zata sha." "Yayi kyau, rakashi yaro." Rik'e masa jaka wanda aka kira da yaro yayi suka fita, sannan shi ma suka fita. "Hello... Samha baby." Ya fad'a da yaji ta daga wayar "Eh tana hannu har yanzu." "Eh ya tabbatar da ciki ne, amma za'a cire shi tunda baki da bukatar shi." "A ah... Babu fa abinda zan yi wa masoyinki, kawai wata yar harkalla ce zamu karasa ta. " " Yawwa toh" tace tana jin dadi. " Sai mun sake magana ko? " " Amma ai bana samun ka kwata-kwata a waya, me yasa?" " Babu komai, idan akwai bukatar muyi magana ni zan kiraki da kai na." " Shikenan." Dariya yayi sosai bayan sun gama maganar, be san bata da tunani ba kwata-kwata sai yanzu, amfani yayi da ita ya samu abinda yake so, ba kuma zai kyale wanda ta kwallafa rai akai ba, ba zata taba samun cikar burin ta ba in dai yana numfashi. ***A waje ya tarar da su Habib din bayan ya gama parker motar, ganin tare suke da Gaji ya sakashi saurin karasawa ya taimaka mata ta fito, sannan suka gaisa ya saka aka rakata ciki su kuma yace su biyo shi garden dake baya. Kujeru ne a wajen, ya zauna sannan suka zauna suma, yana karantar yanayin Mahfuz din, sai a lokacin yayi masa kallon tsaf, ya kuma fahimci hakan yanayin sa ne, ku kuma yanayin environment din da ya taso kamar yadda Habib yayi masa bayani dazu. "Ta yaya zaka iya taimakawa?" Yace bayan ya gama nakaltar yanayin sa, gyara zama yayi sosai, yayi murmushi sannan yace zai masa yan tambayoyi,da ka ya amsa masa ya bashi go ahead. "Babu wani message ko kira da ka samu daga wajen kidnappers din?" "Akwai." "Zan iya gani?" "Why not?" Ya mik'a masa wayar, ya karba ya duba messages din dukka, ya jima yana sake dubawa kafin ya mik'a masa wayar sa "Kayi tunani sosai, wanene kake da matsala dashi, irin wadda kasan lallai da zai samu dama akan ka zai iya aikata maka komai?" "Babu shi, bansan waye ba gaskiya." " Babu ko old friend? Ko abokin aiki?" Shiru yayi cikin tunani " Think... " _" Zan dawo komai daren dadewa, sai na dauki fansa akan ka, ko da zan karar da komai da na mallaka ma duniya sai na maida rayuwar ka abun kwatance! "_ "JABIR! " Yace yana mikewa tsaye da sauri, tashi Mahfuz yayi shima yana kallon sa " Waye shi. " " Aboki na ne, abokin aiki na ne. " " Recently na samu labarin ya zama babban terrorist kuma yana da connection da manyan k'asar, bayan shi bana tunanin akwai wanda zai bukaci rayuwa ta, babu. " "Ya akayi na manta? Ya akayi? " " Kasan in da za'a same shi? " Girgiza kai yayi, " Ban sani ba. " Komawa sukayi suka zauna, Mahfuz ya ciro biro da paper ya rubuta wani abu, daidai lokacin da Moh ya daga wayar Musaddik yace ya same shi a garden, yana ajiye wayar sai gashi ya zagayo dama chan yana cikin gidan, da kallo Mahfuz ya bishi kafin ya karaso wajen yace "Waye shi?" "Best friend dina ne." "Ok." Yace a gajarce ganin ya karaso, ya mik'a musu hannu suka gaisa amma da ya bawa Mahfuz hanun sai ya rik'e hannun nasa har sai da suka kalle shi dukka, sai ya saki yana murmushi ya jingina da kujerar da yake kai, wani kallo Musaddik yayi masa ya zauna yana maida hankalin sa kan Moh. "I'm very sorry Capt..." "Babu komai, nasan wani uzuri ne dakai." Ya katse shi kafin ya karasa. "Babu wani progress ko?" Yace "Babu." "Allah ya bayyana su." "Amin." "Ya aiki?" Mahfuz ya tambayi Musaddik unexpectedly "Aiki Alhamdulillah." "Wanne aiki kake?" "Harkar kwangila, kaifa?" "Detective!" Wani kallo Musaddik yayi masa, yayi shiru,.sai kuma ya kalli Moh "Naga kamar kana da baki, dama inaso muyi maganar flash din nan ne tunda naga ka dawo." "Flash?" Mahfuz yayi karaf ya tambaya "Let's talk about that later." Moh yace sai ya mik'a wa Musaddik hannu "Suna ina?" Sosa kansa yayi "Dalilin da yasa kaga kamar ina janye kaina a case din nan kenan, wallahi bansan ya akayi ba, na rasa su gaba daya." "What!" "Kayi hakuri,ranar da aka sace wayata aka hada dasu gaba daya, bansan ya zan maka bayani ba, nasan kuma muhimmancin flash din a wajen ka, shiyasa na kasa nutsuwa." Murmushi kawai Mahfuz yayi, ya dire pen din hannun sa akan dan deborin da yake gaban sa, ya dora hannun sa akai ya jingina yana masa kallon tsaf. " Idan nace wani abu zaka yarda dani?" Girgiza masa kai Moh yayi dan maganar batan flash din ba karamin bashi mam I'llaki tayi ba. "Ina bukatar yara hudu cikin yaranka na gate." " Me zasuyi maka?" Musaddik yace ransa a bace. " Wait and see." Yayi murmushi, shi Moh ba gane kan maganar ba kwata kwata, yayi dai abinda Mahfuz yace ya kirawo su suka zo, suka tsaya daga gefe, tashi Mahfuz yayi ya zagayo ta bayan Musaddik, "Take off your mask!" "Kamar ya?" "Me kake nufi Mahfuz?" Moh da shima ya mike ya fad'a cike da mamaki " This man is deceiving you, ka kalli hannun sa, ka kalli fuskar sa, akwai banbancin skin color, he's definitely using a mask, idan har ya musa, zan tabbatar maka." "Noo...you are mistaken, wannan Musaddik ne, trusted friend dina ba zai taba deceiving dina ba,you cannot accused somebody without a proof." " Shine zan maka proving yanzu ai, wait and see, guys... Ku rik'e shi." " Dakata!" Moh yace ransa na baci, ba zai dauki wulakanta Musaddik yana kallo ba. "Waye wannan Capt, waye zai zo ya shiga tsakani na da kai?" "Calm down aboki na, misunderstanding aka samu amma zan masa magana..." Sai ya juya wajen Mahfuz din "Let's call it a day, zamuyi magana gobe, Habib ku jirani a wajen mota." "Muje Mahfuz." Wani kallo yabi Musaddik din dashi, sannan ya juya suka bar wajen da Habib. Juyawa kan Musaddik yayi da ransa yayi masifar baci, ya shiga bashi hakuri akan abinda Mahfuz din yayi, yace ya jirashi yana zuwa bari ya sallame su. Yana barin wajen ya ciro waya, ya kira shi yana matsawa chan gaba. "Akwai matsala." Yana dagawa yace "Ya fara suspecting dinka ne?" "Be fara ba, wani banzan yaro ne bansan daga ina yazo ba, yaso dole sai ya nuna masa gaskiyar mask da na saka..." "Ya yadda?" "Be yarda ba, kasan ya yarda dani sosai, so ba zai taba kawowa ba. " " You have to be very careful, shi kuma yaron zan san yadda zan yi dashi. " " Ok sir. " Ya kashe wayar yana juyowa, sukayi ido biyu da Moh da yake tsaye a bayan sa kamar mayunwacin zakin da ya shekara be ce ba. ***Assalamu alaikum sisters, masu korafi naga wasu daga cikin korafin ku, ina mai baku hakuri akan matsalolin da aka samu, dan gane da rashin posting halin girma shekaran jiya da jiya, hakan ya faru ne sakamakon ciwon hakorin da ya matsa min hade da zazzabi, wanda har ta kai ban iya samun duba sakonni ba balle har na iya zaman rubutu Duk cikin zafafa biyar babu wadda a cikin mu take jin dadi a duk sanda batayi posting ba, Allah ne shaida ana iyakar kokari wajen ganin Anyi abinda ya dace. Sai dai idan abu ya sha kan mutum a ba yadda ya iya. Allah ya huci zuciyar duk wanda ransa ya baci ta dalilin jira ko wani abu, ba da gangan bane wani lokacin kuma ajizanci ne na dan Adam. Allah ya rufa asiri ya sa mu gama lafiya 2/21/22, 08:16 - Buhainat: Halin Girma 39 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw **** "Capt... Yaron nan ya bata min rai, ya za'a yi ya zarge ni haka?" Sassauta fuskar sa yayi, ya dafa shi "Karka damu yarinta ce." "Naga alama, waye shi? Aina yake?" "Bansan shi ba, abokin Habib ne I guess!" "Amma ka barshi ya zage haka, naji ma kamar hausar shi bata fita." "Eh, born and raised a UK ne, dole zaka ji banbanci, anyways ya wuce na masa fad'a kuma." "Shikenan, yanzu menene next? Da ya kamata muyi?" Daga kafada Moh yayi cikin halin ko in kula yace "Babu komai for now, muna cigaba da addu'a." "Bari na wuce, I'm sorry akan maganar missing files din nan." "Karka damu." Da kallo ya bishi har ya fice daga wajen, ya daga waya ya kira waya, sukayi magana sannan ya kashe. A kalla Mahfuz ya zama wani haske a binciken sa, kowa da yanayi da tsarin aiikin sa, ya san aikin sa sosai ya kuma masifar burgeshi, he's smart and intelligent daga ganin shi,kuma da yake akwai banbancin yadda k'asar mu take da tasu sun fi mu skills da kayan aiki.   Shugaban su ya kira, ya fad'a masa abinda ake ciki, ya kuma tabbatar masa da zasu yi duk yadda zasuyi, a yanzu za'a binciki layin mudassir din a nan za'a gane da wadanda yake waya, yana ajiye wayar ya kira Ammi sukayi magana sannan ya kira Aji da yake ta avoiding kiran sa tun ranar, yana dagawa kuwa ya haushi da fad'a akan kin daga wayar sa da yayi, hakuri ya bashi kawai sukayi magana ya kashe.   Bayan kamar awa daya aka kirashi, ya shirya a gurguje ya fita cikin tawagar yaran matasan sojoji, kowanne a cikin su a kalla zaka gane babu sauki a tattare dashi, bakin glass ne a fuskar Moh, baka ko ganin kwayar idon sa. A wani waje suka hadu, ya tarar da taron jami'an tsaro birjik kowannen su cikin shiri, babu kalar da babu na jami'an tsaro tun daga kan police, DSS, civil defense, uwa uba sojoji. Gaisuwa ya dinga amsawa daga kananan ma'aikata har ya karasa wajen manyan da suke kasan wata rumfa suna magana. Details din bayanan da aka samu ta wayar Musaddik din suke dubawa, in da ya nuna babu wata waya da yake yi illa da mutum uku, Moh din sai wata number da take kiran sa kullum a private number sai kuma Samha Bello Turaki, da Kamal Abubakar Santuraki    Kansa ne yayi masifar daurewa, menene alakar Samha a cikin case din? Karba yayi ya sake dubawa sosai ya tabbatar da abinda yake a rubuce. Yasan Laila ce take son shi ba Samha da take kawarta ba,menene akalar Samha da Iman dinsa da har za'a hada kai da ita a sace ta?be san dalili ba,  abu daya ya yarda dashi, dukkan su anyi amfani dasu ne, domin a samu galaba akan sa, su kuma idon su ya rufe, suna son ganin bayan  din suka fadawa gadar zaran JABIR! "Mun gabatar da duk binciken da zamuyi akan shi, mun kuma tabbatar da ba Musaddik bane, yayi amfani da fuska ne, sannan yayi amfani da wata na'ura da take kwafar murya, wadda take da masifar tsada Kuma alamu sun nuna ya jima tare da kai, ba zaka taba ganewa ba idan har ba sani kayi ba, Musaddik yana da kusanci da kai shiyasa har sukayi amfani dashi wajen samun kanka, da weakness dinka, sai kuma dan uwanka  Kamal da suka taimaka musu don cimma tasu bukatar da hadin guiwar Samha da bamu san wata alaka dake tsakanin ku ba." "Layin  da yake private mun saka an bud'e mana shi, kuma mun tabbatar da ana kira da layin ne daga wani bangare ma dajin falgore! " "Yana ina yanzu? " " Yana ciki, idan an gama shiryawa shine zai shige gaba, kaine team captain din da zai jagoranci tafiyar daga bangaren mu. " " Ok sir! " Yace yana sara masa, wucewa yayi zuwa in da aka ajiye fake Musaddik din, yana so ya tantance banbance banbancen dake tsakanin sa da Musaddik dinsa da ya kasa ganewa, yana durkushe a k'asa bayan dukan da ya sha, ya tabbata dai da JABIR ya tantance shi sosai kafin ya kawo shi, dan hatta tsawo da yanayin sa irin ma Musaddik din ne, fuskar sa ya dago, ya kare masa kallo zuciyar sa na tafarfasa, kamar zai daure amma sai ya k'asa, ya dunkule hannu ya naushe shi a baki, nan da nan kuwa sai jini, ya saka kafa ya hambare shi. fitowa yayi ya tsaya a filin yayi bayanin yadda zasu yi idan sun isa, duk suka amsa suka shiga motocin su a gurguje suka dauki hanyar dajin falgore.     Gudu suke kamar zasu tashi sama, haka suke a duk sanda suka fita operation amma kuma na yau yasha banban da sauran operation da suka taba zuwa, yau abun nasu ne, su aka taba kai tsaye shiyasa kowa yake ji kaamar abin ya shafe shi sosai, cikin kankanin lokaci suka isa saboda masifar gudun da suke, barbazuwa sukayi a dajin kamar yadda yake according to plan. A daidai lokacin Dr da zai kawo maganin ya iso, tana kwance kamar kullum ta gama galabaita sosai ya shigo rataye da jakar sa, tana ganin sa ta mike da sauri, bata ma san tana da ragowar karfin nan ba sai data ganshi, ya ajiye jakar ya ciro magungunan a ajiye su, sannan ya koma gefe ya tsaya yana jiran shigowar ogan, jim kadan sai gashi ya shigo, ya duba magungunan yayi masa bayanin yadda za'a sha. "Tashi!" Ya daka mata tsawa yana tamke fuska "Dan Allah kayi hakuri, dan Allah." "Wallahi sai kin sha." "Dan Allah kayi hakuri." Ummimi tace tana kuka "Shut up munafuka, idan na sake jin bakin ki sai na sheke ki har sai kin daina numfashi. " Gefe ta koma jikin ta yana ta rawa, bindiga ya ciro ya nuna Iman dashi "Karbi kisha kafin na harbe ki. " Hannu ta miko ya zuba mata, ya kafe ta da jajayen idon sa, yana nuna ta da bindigar, ta sha sannan ya juya yana murmushin mugunta ya fice likitan yabi bayan sa. Dakin da ya ajiye Musaddik da driver ya shiga, ya tarar da Musaddik din a kwance amma kuma sallah yake daga haka, kwafa yayi ya fito bayan ya rufe kofar, yazo wajen yaran nasa da suka cika harabar wajen dauke da manyan bindigu cikin shirin ko ta kwana. "Zan shiga na kwanta, ku kula sosai bana so a samu matsala." "An gama Oga."   Suka hada baki wajen fad'a, ciki ya shiga su kuma suka cigaba da tsaiwa a wajen.   Zagaye gaba daya dajin sukayi, kowa ya kama stand dinsa, Moh da sauran zaratan sojojin suka kutsa kai ciki, sai da suka dan shiga sosai sannan suka hango bukkokin dake wajen, wanda suka tabbatar da nan suke. Sake rarrabuwa sukayi waje waje, suka sake zagaye bukkukin.   Sai da suka gama shiryawa tsaf, sannan Moh ya basu signal na su yi attacking dinsu, nan fad'a musu ta sama ta ka, nan suka rikice suka shiga kokarin maida martani, sai dai yawan Jami'an tsaron ya ninninka yawan su,. Cikin baccin da ya soma dauke shi yaji alamun yamutsewar wajen, kafin ya kai ga mikewa aka bugo kofar dakin aka shigo, Moh ne a gaba yaran sa na take masa baya, dukkansu a shirye suke su bada rayuwar sa dan ceto Madam din Oga. Kasancewar be shiryawa zuwan su ba, sai ya zama kamar sun ci galaaba akansa ne, babu bindiga ba babu komai a hannun Moh, ya matse shi a jikin bango ya shiga bugun sa, bugu ba na wasa ba, sai da yayi masa laga-laga ya sake shi cikin jini ya fadi kasa, ya bi ya take kansa da kafarsa cikin tsananin bacin rai ya soma magana. "Kafin kaga karshe na, ni zan ga karshen ka da duk wanda ya goya maka baya..." " Oga an samu Madam, she's bleeding so badly." Da sauri ya juya yabi bayan dan sanda da ya shigo, ya bar yaran nasa da JABIR.   Jini ne sosai yake zuba, da sauri ya karasa gabanta, idon ta da yake kokarin rufewa da kalle shi. Rawa jikin sa yake ya tallafota jikin sa " Bude idon ki, dan Allah ki bud'e idon ke, me sukayi miki? Me sukayi miki?" Karasa rufewa idon sukayi ruf, ya dagata ya fita da ita jikin sa na rawa, idan har wani abu ya same ta, sai ya karar da dangin JABIR kaf. _ZAFAFA BIYAR 2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/24/22, 08:05 - Buhainat: Halin Girma 40 *_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_* https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share *_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb *_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_* https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS *_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_* https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw ****Wasu daga cikin sojin ne suka bi bayan sa, in da sauran jami'an tsaron suka cigaba da dudduba bukokin har suka samu nasarar ganin Musaddik da driver a wani daki, sai makamai masu yawan gaske suma daki gida, dukkan su suna bukatar taimakon gaggawa musamman Musaddik da yake cikin mawuyacin hali.    Karar harbi suka ji, daga baya wanda basu san dalilin harbin ba, a zaton su sun kama duk yaran JABIR din, da shi kansa JABIR din bayan dukan da Moh yayi masa. Zagayawa baya sukayi, suka ga mutum a kwance cikin jini, bashi da alamun yana tare da sauran yan iskan amma kuma basu san me ya kawo shi wajen ba. "Mu taimaka masa." "Waye ya harbe shi?" "Akwai sauran yan iskan a baya, let's check, ku dauke shi ku tafi dashi zamu biyo bayanki. " " Ok. " Suka ce suka taimaka masa, da k'yar yake numfashi saboda tsabar wahala, a motar da aka saka Musaddik suka saka shi, suka bi bayan motar da Moh suke ciki dan basu taimakon gaggawa. Rik'e yake da hannun ta yana kuka wiwi kukan da ya kasa dauriyar rik'e shi,  gani yake kamar motar bata sauri duk kuwa da irin gudun da suke tsulawa, idan har wani abu ya same ta, ba zai bar kowa ba wannan alkawarin sa ne.   Sanda suke karaso asibitin tuni iyayen gulma yan jarida sun iso domin samun na watsawa, kofar baya suka koma suka bi, suka shiga asibitin dan a yanayin da take ciki ba zai yarda wasu yan iska su dauke ta a hoto su yada wa duniya ba, duk ma wata gidan jarida ko talabijin da tayi gangancin haka sai ya yi shari'a dasu.    Da sauri nurses din suka karbeta, daidai lokacin da Babban likita ya karaso cikin tawagar sauran manyan likitoci mata da maza, aka shiga da ita ciki domin bata taimakon gaggawa.    Zagaye ya soma yi a wajen cikin yanayi na fitar hayyaci, wayar sa da take ta faman nemam agaji ya gaza fitowa da ita balle ya iya amsa kiran da ake ta faman doka masa da ba zai wuce daga makusantan sa ba, bashi da sukunin ciro wayar balle ma ya amsa ta, balle ya iya wata magana ba tare da yasan halin da Iman din sa take ciki ba.      Cikin kankanin lokaci asibitin ya cika da manyan mutane daga masarauta da kuma gidan gwamnati, Takawa ne ya karaso a karshe ya samu shiga wajen da Moh din yake shi kadai sai wasu sojoji daga gefe, sauran mutane suna ta dayan bangaren in da aka kai Musaddik da saurayin da aka harba wanda yake cikin yanayi mara dadi.    Yana ganin Takawa yayi saurin isa gareshi, sai kuma ya ja ya tsaya a gabansa ba, hannun sa ya kama, ya ji yadda hannun yake rawa sosai kamar wanda yake jin masifaffen sanyi. "Kayi addu'a muhammad, babu abinda zai faru kaji?" Da ka ya iya amsa masa, sai a sannan ya ga su Abba, ya matsa ya gaishe su, dukkanin su suna cikin tashin hankali, Abba kamar bashi ba saboda tashin hankali, sun riga Takawa zuwa wajen amma ba'a barsu sun shigo ba saboda tsoron da yake wajen sai da Takawa yazo sannan suka samu shigowa. Sunyi waya da Maman Iman din tun dazu ya kuma san zuwa yanzu sun karaso amma ba lallai su shigo kai tsaye ba, sai ya dubi Muhammad yace "Mahaifiyar ta suna waje, nasan ba za'a barsu su shigo ba." "Bari naje." Ya fad'a yana yin gaba, daya daga cikin sojan ya bishi suka tafi tare, daga chan baya ya hango su a tsaye suna magana da wani Soja da yaki fafur barin su, su shiga wajen, ganin Moha da kansa ya nufo wajen ya saka sojan sake kallon matan. "Alhamdulillah." Mamma tace tana share hawayen ta Bud'e musu sojan nan yayi tun ma kafin ya karaso, dan yayi masa alamar ya barsu, suka shigo suka sameshi, ya gaishe su, sannan suka tambaye shi Iman din, Alhamdulillah kawai yace suka bishi zuwa ciki duk jikin su ya kara sanyi sosai da lamarin.     Be barsu sun karasa wajen da su Takawa suke ba kasancewar duk maza ne, sai yasa aka kawo musu kujera suka zauna shi kuma ya karasa ciki.    An dauki tsawon lokaci kafin likita guda daya ta fito, har zata wuce sai ta ga Takawa, da sauri ta je ta durkusa ta gaishe shi, sannan tace suna kokarin su in sha Allah babu matsala, sannan ta je ta dauko abu ta dawo ta koma ciki.      Sun iya iyakar kokarin da zasuyi wajen ganin sun tsaida cikin amma kuma hakan be yiwu ba,saboda karfin maganin da aka bata ba zai bar cikin ba, Allah yaso babu wani illa da yayi mata bayan fitar da cikin. Wankin ciki suka hada sukayi mata sannan aka saka mata drip saboda ta rasa ruwa sosai a jikinta tsawon kwanaki tana amai sannan babu abincin da take ci. Numfashin da take fitar wa ne kadai zai baka tabbacin tana da rai bayan haka babu wani abu na jikinta da yake motsi, tayi fayau kamar ba ita ba, sai uban fari da tayi kamar babu wadataccen jini a jikinta.    Tura ta akayi zuwa dakin da aka kwantar da ita, sannan Drs din suka fito wajen da su Takawa suke, suka kwashi gaisuwa sannan sukayi bayanin yadda al'amarin ya kasancewa pills din da aka bata ne yayi karbi sosai, jiri ne ya kwashi Muhammad yayi kamar zai fadi wani bafade yayi saurin taro shi, ya rik'e shi jikin sa. Hakuri kowa na wajen ya dinga bashi, kafin a bada damar a shiga a ganta, Takawa ne ya fara shiga sannan su Abba suka shiga tare dasu Mummy, sannan suka fito aka bar Muhammad din ya shiga. Tunda ya shigo ya hangi yadda take fitar da numfashi a wahalce, jikin sa ya kara sanyi sosai, shine duk ya jawo mata wannan matsalar tana zaman zaman ta. A da ya dauka matsalar sa kawai gidansu ne, shiyasa gaba daya ya taso da tsanar mulki tun bayan da yaga abinda ya faru da Baban su Laila lokacin bashi da wani girma sosai amma hakan be bar kwakwalwar sa ba, ya taso da tsanar mulkin da ganin cewa duk wata masifa tana cikin gidan sarauta.    Sunyi aiki tare da JABIR zai iya kiransa da abokin sa mafi kusanci dashi a wanchan lokacin, bashi da hannu a matsalar da JABIR din ya samu daga sama har aka sallame shi aka kuma karawa Moh din matsayi irjn wanda ya Jabir din ne ya chanchanta, bayan nan duk wata alaka tasu ta yanke, har ya manta dashi sai lokaci zuwa lokaci yake tunashi,be taba saka wani abu a ransa game dashi ba, rayuwar sa yake kansa tsaye ba tare da sanin akwai babban makiyinsa da yake burin ganin bayan sa ba.    Maganar Takawa ce ta fado masa wadda yayi masa ita dazu kafin ya bar asibitin _"Ka sani bawa baya taba wuce ko ketare kaddarar sa, dan haka ka dauka wannan din kaddarar ka ce kayi addu'a Allah ya baka ikon cinyeta. Sanin kanka ne mutum be isa ya hana ko dakatar da kaddarar ka ba, kafi kowa sanin yaran da suke tare da kai suna tsaron ka gida da mota ba wai na matsayin da kake dashi bane a aikin ka, alfarma tace ya saka aka baka su har haka, wanda duk munyi hakan ne saboda mu baka kariya a gida da waje, sai dai yanzu na kara tabbatar wa babu dan adam din da ya isa ya tsare ka face Allah, kuma duk abinda Allah ya kaddara zai faru toh fa sai ya faru ko da a gaban idon mutum ne."_    Gaban gadon ya ja ya tsaya cikin tsananin tausayin ta, be taba kawo tunanin wani abu zai faru da su haka ba a dan kankanin lokaci nan, ya zata shikenan ta rabu da duk wata matsala tun da suka riga sukayi auren su, ashe ba haka bane. Hannun wanda babu drip a jiki ya rik'e, ya zauna a gaban gadon yana karewa fuskar ta kallo, daga gani kasan ba jin dadin baccin take ba, bacci ne me cike da wahala iri iri.     Ya jima sosai a dakin, babu motsin komai, kamar babu kowa aciki, knocking akayi, ya cire kansa da k'yar ya kalli kofar ba tare da yayi magana ba, sai da aka sake kwankwasawa sannan yace " Bismillah. " Turo kofar akayi, Zeenat da Habib ne a gaba sai Mam, sai sauran jama'ar gidan da sai yanzu suka samu damar shigowa wajen, tashi yayi daga zaunen, ya mikawa Habib hannu suka gaisa, fuskar sa ta dan daga alamun yayi kuka, ya mai jiki yayi masa sannan suka gaisa da sauran matan, suka fita tare da Habib din waje, "Ina Mahfuz?" Yayi karfin halin tambayar sa dan yayi tunanin tare zasu zo. Dan duban sa Habib din yayi kamar me tunani, sai kuma yace "Ai tare aka fito dasu daga wajen da Iman din take." Kallon rashin fahimta Moha yayi masa yace "Ban gane ba?" Kwalla ce ta zubowa Habib din yayi saurin sharewa yana daurewa yace "Dazu da safe ya fito daga gida akan zaizo ya same ka, nace zan raka shi amma ya bari anjima yace zai gane ma ai, shikenan ya tafi, bansan ya akayi ba, sai gashi shima an same shi a chan in da Iman din take." Kafin ma ya karasa tuni Moh ya firgice, yasan an ce akwai mutum uku bayan iman da Ummimi, daya an harbe shi ma aamma sam be kawo tunanin komai ba, be ma kara tunawa ba saboda damuwar da ta danne shi, yana so dai yaje ya tabbatar da Musaddik na cikin wadanda aka samo din amma sai yake ganin kamar idan ya matsa daga wajen ta komai zai iya faruwa. "Yana ina?" "Yana chan emergency unit har yanzu bamu ji komai daga garesu ba, su Abba dai suna chan?" "Innalillah wa inna ilaihi rajiun, muje." Sauri sauri ya dinga yi kamar zai tashi sama, idan wani abu ya samu yaron fa? Ya zai da ransa wai? Ba'a barin kowa ya shiga wajen nasa saboda yadda case din nasa ya zama very complicated case, bayan sun yi nasarar cire bullets din amma sam jinin ya ki tsayawa, ana kara wani, wani yana fita, su kansu abin ya basu tsoro ganin yadda yake zubar da jini, shiyasa suka hana kowa shiga, su Abba da suka dawo wajen tun da suka samu labari jikin kowa ya gama sarewa da al'amarin Mahfuz din.    Moh na isa wajen dr na fitowa daga ciki, jikin sa babu kuzari ya nufo wajen da su Abban suke, ya kalle su daya bayan daya kafin yace " Sai dai muyi hakuri... " Wani irin zubewa Moh yayi a wajen, kirjin sa na masa wani irin suya, ashe Ajali ne ya kawo shi k'asar? Ashe dama shine sanadin mutuwar sa, me yasa yayi masa wannna tsawar, me yasa ya ci masa mutunci bayan be san wani abu dangane dashi ba, "Nooo Dr... No be mutu ba, Dan Allah karka ce min ya mutu dagaske, ban kyauta masa ba, be kamata ya mutu ba, he's innocent be kamata yayi facing irin wannan mutuwar ba, me yayi? Menene nasa a ciki?" "Get hold of yourself Capt, kullu nafsin za'ikatul ma'ut, hakikaa kowacce rai sai ta dandani zafin mutuwa, shi da ya tafi be yi sauri ba, mu kuma bamuyi jinkiri ba, addu'a kawai yake bukata." Dr yace ya juya ya barsu a wajen, babu wanda ya iya motsi a wajen saboda tsabar kaduwa, yaro me zumunci me shiga rai, me son yan uwan sa, ya Yaya zataji? Labarin mutuwa irin wannan mara dadi, kullum korafin ta akan Nigeria shine rashin tsaro, ko waya sukayi ta kan ce musu Nigeria ta zama abinda ta zama, rai ba abakin komai yake ba. Kullum maganar ta kenan, tsoron ta kenan, ashe bata tsira ba, Ashe zaman ta a chan bashi ne zai sauya kaddara ba? Innalillah wa inna ilaihi rajiun kowa yake maimaitawa babu hargitsi ko hargowa, saboda dauriya irin ta maza, sai dai kana kallon su zaka san mutuwar ta dake su, musamman Habib da Moh, kafin kace kwabo labarin ya zagaye ko ina, kowa sai da ya tausaya wa Mahfuz irin kaddarar da ta fad'a masa.    Zuwan Aji da Bubu ne ya dawo da Moh cikin hayyacin sa, babu hawaye ko digo a fuskar sa amma ya daku, ya kadu da zaka iya rantsewa ya dade a kwance yana jinya me tsanani.    Baya magana bayan amsa gaisuwa sai dai kawai ya amsa maka da ka, har zuwa lokaci itama bata farka ba, yaje yaga Musaddik wanda yake da sauki sai ciwuka a jikin sa yawanci na duka ne. Sai kuma yunwa da ta ramar dashi sosai, driver da Ummimi babu abinda ya same su dama su ba sune targets din ba.    Wajen azahar ya dawo dakin da take, har lokacin bata tashi ba, mummy ce kawai a dakin tana zaune gaban gadon da Iman din take, idon ta yayi ja sosai, addu'a take tofa mata ya shigo ta tashi a kunyace tana kokarin barin dakin "Dan Allah mummy ki yi zaman ki, dama nazo na duba ko ta farka ne, zanje station din na dawo." Komawa tayi ta zauna shi kuma ya fita, ya shiga mota ya nufi station din. Direct office din CP ya wuce ya samu DSP yana press conference akan case din, kokarin fita yayi amma babu dama sun riga sun ganshi, sukayi masa cha kuwa kowa na son masa tambayoyi, be basu dama ba dan yanzu ba wannan ne a gaban sa ba, da kansa zai shirya ya basu lokaci amma ba yanxu da be ma san me yake masa dadi ba sam. Hakuri aka basu, aka kuma sallame su sannan ya samu ganin CP din sukayi magana, ya kuma shiga wajen da aka ajiye Jabir din. Yayi matukar laushi sosai saboda ba karamin duka sojajin nan sukayi masa ba, dama yasan ba zasu kyale shi ba, hakan ba dan dai basaso a samu matsala ne amma tsaf zasu iya kashe shi a wajen.     Baya jin a yanzu akwai wata halitta da ya tsana sama da Jabir din, shiyasa ya tsaya daga kofar be shiga ba, dan idan ya shiga zai iya shake shi har sai ya daina numfashi. Wani dan sanda ne a gaban sa rik'e da wani katon katako, yana masa tambayoyi, sai kuma wasu yan sandan suma daban daga gefe cikin fushi suke interrogating dinsa yana rokon suyi hakuri. Juyawa yayi ya bar wajen ya koma suka karasa magana da CP sannan ya bar station din ya dawo asinine, in da ya wuce kai tsaye wajen Musaddik, ya samu dakin da yan sanda suna daukar bayanai daga wajen sa, wucewa yayi ya koma bangaren Mahfuz da har yanzu ba'a saki gawar sa ba, sai an gama bincike tsaf sannan za'a basu suyi masa sutura. A chan ya zauna tare da su Habib dasu Abba har bayan Magriba sannan aka basu gawar tasa, suka dauke ta suka nufi gida da ita don yi masa sutura a mika shi gidan sa na gaskiya.    Zuwan su ya saka gidan rikicewa, dama kowa ya iso ana zaman jira cike da alhini, ba karamin taba kowa mutuwar tayi ba, nauyi da kunya ya Moh shiga ciki, sai yake ganin kamar shi ya jawo, da be saka shi a cikin maganar ba, da duk hakan bata faru ba, a daren aka hada shi, aka kuma rakashi gidan sa na gaskiya. Allah sarki. Mutuwa darasi ce babba, Rayuwa bata da tabbas, Allah ya bamu ikon amfani da lokacin mu kafin ya kure mana,Allah kasa mu cika da imani. Amin 😭      ***Wani irin juyawa cikin Samha yayi lokacin ta samu labarin an kama Jabir, tsoron ta daya kar sunan ta ya shigo ciki, itace ta bawa Jay din shawarar kidnapping Iman din, kuma ita kadai ce tasan plan dinsa duk da itama bata san amfani yayi da ita ba. Wayar ta ce tayi kara da take gefen ta,dan tsorata tayi, sai kuma ta kai hannu ta dauka tana kallon number, Kamal ne yake kiranta, dagawa tayi ta saka wayar a handsfree "Ashe dama abinda zaku aikata kenan ke da dan iskan chan shine kuka shigo dani ciki kuka samu duk wani bayani akan shi, daga karshe kuka watsar dani." "Ai kai ba karamin kidahumi bane, idan banda gara irin ka, waye yake da amana a wannan zamanin, kowa kansa ya sani bari kaji, dan haka karka dameni ka kyale ni naji da abinda yake damuna." "Ai wallahi kadan kika gani, asirin ki ya gama tonuwa dan na gama zayyane komai a gaban yan sanda, abubuwan da kuka sakani nayi duk na fad'a sai ki jira hukunci, wallahi ko shi MOH ya kyale ki wallahi ni ba zan kyaleli ba kinji na rantse!" Kit ta kashe wayar ta jefar da ita, "Wannan wacce irin masifa ce?" Da sauri ta ja jakarta ta fito, bata tarar da maman ta a falo ba dan haka tayi saurin ficewa ta dauki mota ta bar gidan, tana tafe tana gwada kiran Laila amma bata dagawa, ta rasa abinda yake mata dadi, sai kawai ta wuce gidan ta sameta suyi magana ko zata taimaka mata, amma tana zuwa gate sai aka hanata shiga, tayi mamaki sosai hadda fitowa tayi musu bayanin kanta, amma kemaimai suka hanata bayan sun tabbatar mata da sun gane ta, umarni ne aka basu kar su sake barin ta, ta shiga masarautar. _ZAFAFA2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/24/22, 08:08 - Buhainat: ©®*Hafsat Rano*       _Halin Girma_             *41* ***Ruwa ta fara ambata sanda ta farka, da sauri Mamma tayi wajenta itace take tsaye dama, Mummy na kan sallaya tana lazimi ta mike da sauri cikin tsananin farin ciki. "Alhamdulillah." Ta furta tana karasa kusa da Mamma da take jera mata sannu, da ido kawai take bin su tana son tuna abinda ya faru karshe. Murmushi tayi cikin dauriya tace "Mamma." "Na'am Iman, sannu kinji?." " Alhamdulillah mun auna arziki. " Ta juya tana fadawa Mummy da ta kasa boye farin cikin ta "Fatima. " "Mummy. " " Sannu kinji, akwai abinda yake Miki ciwo? " Da hannu ta nuna cikin ta, taba cikin Mummy tayi kila saboda wankin cikin da akayi mata ne, " Bari nayi musu magana tunda ta farka. " " Bari naje. " Mummy tace tana yin gaba, ta bar su da mamma tana tambayar ta. Tare suka shigo da nurses su biyu, mamma ta matsa suka duba ta, sukayi mata tambayoyi sannan suka ce a bata ruwa tasha da abinci sannan suka fita daya ta sauki file din ta daya kuma ta tafi kawo mata magunguna daga pharmacy.    Taimaka mata mamma tayi tunda an cire drip din ta kai ta toilet, ta gasa mata jikin ta, ta taimaka mata tayi wanka da brush kafin ta fito Mummy ta hada mata tea me kauri da kidney pepper soup da aka kawo daga fada.   Daure da alwala ta fito bayan ta sauya kayan jikin ta zuwa doguwar riga mara nauyi ta saka Hijab ta zauna a gadon ta biya bashin sallolin da suke kanta, sai da ta idar sannan ta dan ci abincin kad'an ta koma ta kwanta lamo tana jin jikinta babu kwari ko kad'an.    Abba ne ya shigo tare da wasu  mutane masu rawani, suka dubata sukayi mata ya jiki sannan suka tafi, Abba ya rakasu ya dawo ya zauna yana sake dubata. Tsam Mummy ta bar dakin ta koma waje ta bar Mamma a ciki suna magana da Abban, ya dan jima a ciki sai da yaga alamar ba zata dawo dakin ba bayan kuma ita ta kirashi da Iman din ta farka sai ya tashi kawai yayi sallama ya tafi akan zai dawo anjima.    A waje suka hadu da Mummy din, ya sameta har wajen da take zaunen yayi mata magana, ta amsa masa sama sama kamar tana jin haushin sa ko wani abu, be gane dalilin ta ba, ganin a waje ne ga kuma Moh da ya nufo su ya saka shi kyale ta ya tafi, suka gaisa fuskar sa fayau alamun ya samu labarin farkawar Iman din. Komawa yayi ya raka Abban har mota sannan ya dawo, ya tarar da mummy da Mamma din duk a waje, kila Mummy din ce ta sanar mata da zuwan sa shiyasa suka fito ba sai ya shiga su hau fita ba, gaishe su yayi da tambayar ya mai jiki sannan ya danyi jim a wajen sai da Mamma tace ya shiga sannan ya tashi ya nufi dakin da daukin ganin ta.    Ko sallama ya maita yayi sai da ya tura kofar ya shiga sannan ya tuna yayi sallama ta dago daga kwanciyar da tayi ta kalle shi. Da sassarfa ya karasa kuwa, ya haye saman gadon ya tattaro ta zuwa jikin sa, ya rungume ta tsam damuwar da yake ciki na raguwa. Luf tayi a jikin nasa tana jin nutsuwar da ta rasa tsawon kwanaki, bata san haka tayi kewar sa ba, sai yanzu da suke tare, kuka ta saka masa ya sake rungume ta yana jin shima kamar ya rushe da kukan. Sai da yaga kukan nata na neman zarcewa sannan ya dakatar da ita ta hanya shafa bayan ta ya shiga magana a kunnen ta "Shssh... Karki karawa kanki wani ciwon please, you are safe now. Babu wani abu da zai sake faruwa, I will protect you with my life." Shiru tayi tana jan numfashi, ya cigaba da shafa bayanta har sai da yaji tayi shiru gaba daya, sannan ya dago ta daga jikin sa yana kallon fuskar ta, murmushin ya sakar mata ta maida masa itama. " Me yake miki ciwo yanzu? " " Kai na.. " Tace a hankali " Sannu zai daina a hankali, komai zai wuce, ba zan sake tafiya ba barki ba nayi miki alkawari nan." Maida kanta tayi jikin sa ta kwantar ya gyara mata kwanciyar yadda zata ji dadi, ya saka hannu yana mata tausa a hankali.   Sun dade a haka har sai da akayi knocking a kofar, ya zameta ta kwanta sosai akan gadon ya sauka sannan yace " Bismillah a shigo." Bataliyar yan gidan su ce, tun daga kan su Ya Maryam da matan gidan hadda Dadah da wasu ma da be san su ba, a gurguje ya gaisa dasu ya bar musu dakin dan dakin ma yayi musu kad'an.    Dakin da Musaddik yake ya wuce, ya sameshi a zaune ya gama cin abinci, yayi fes dashi jikinsa kuma yayi kyau, kanin sa ne yake kula dashi suka gaisa da Moh din sannan ya basu waje dama yana so yaje ya siyo abu a shop sai yayi amfani da damar ya tafi. "Jikin ka yayi kyau sosai friend." "Wallahi Alhamdulillah, mun gode Allah, ya jikin Madam din?" "Itama Alhamdulillah wallahi, ta samu sauki." "Masha ALLAH. Allah ya kara mana lafiya baki daya. " "Amin, ka tabbata kana cikin abokai na gari, Allah ya hada mu tare a inuwar al'arshi, bansan da wanne baki zan gode maka ba, ban kuma san da wanne ido zan kalle ka na gode maka ba, ta ya akayi na kasa ganewa? Na kasa banbance ka da wani daban? How long ka zauna a wajen sa.? " " Mu daina tunawa dan Allah, tunda ya shigo hannu shikenan nasan dole zai girbi abinda ya shuka. " " Still dai inaso nasan komai... " " Ka bari mu koma gida, zan baka labarin komai, for now kayi fucusing akan case din cikin gida, yau saura kwana uku su juya komai, kana bukatar gabatar da evidence din nan." " Haka ne, kuma abinda ya faru yanzu ya saka na kara jin kowanne abu akwai good side da bad side dinsa, abinda na tsana nake ganin shine kawai matsalar ta, har naki bin umarnin Bubu akai,shi zan yi facing yanzu, zan karbi abinda ya zama mallaki na, zan farantawa mahaifi na kamar yadda ya dade yana burin ganin ranar. " " Da gaske kake? " " Da gaske nake. " " Kai masha ALLAH, Bubu zai fi kowa murna shi da Aji. Dama a komai alkhairi ake nema ba son zuciya ba,nayi murna sosai aboki na, Allah ya baka sa'a. " " Amin. " Yace yana daukar ledojin maganin sa " Kana shan magungunan nan kuwa?" " Ina sha. " " Good, da baka sha da sai na saka ka... " " Frog jump. " Ya karasa masa suka kwashe da dariya suka tafa " Wallahi ka raina ni, Capt guda, Capt Muhammad Ahmad Santuraki, babu wani respect ko? " " Ayi hakuri tsohon Capt! " Duka ya kai masa a kafadarsa, ya goce suka sake kyalkyalewa da dariya. ***Baki daya ta rasa abinda yake mata dadi, ta rasa in da zata tsoma ranta taji sanyi, cikin jikinta yayi masifar takura mata, babu abinda take so take kulafuci sai mijinta Bashir, takanas ta aika aka samo mata irin turaren da yake amfani dashi amma duk a banza, watarana sai ta shiga daki tayi kuka gashi Abba yayi shiru da maganar, ko dan abinda ya faru a kwanakin ne? Babu irin kiran da batayi wa Bashir amma sai yace mata ta kara jira zaizo,. Takanas ta samu Mama a daki da ita ma kanta ta gaji da zaman Zeenat din ta kuma damu da shirun da Abban yayi dama Bashir din. Da kallo ta bita har ta zauna a kusa da ita, tun ma kafin tayi magana ta riga tasan me ya kawo ta "Yau zan samu Abban ku da maganar, ni kaina hankali na ba akwance yake ba, kema kuma duk alamu sun nuna dakin mijinki kike so, ki tattara ki koma Allah ya baku zaman lafiya, me afkuwa ta riga ta afku shiyasa yayi biris damu shima Bashir din yasan ya gama damu, sai ki koma kawai ya zamuyi?" "Nima dama maganar da nazo muyi kenan." "Ai na sani, oh Zeenatu ana son miji. " Da sauri ta rufe idon ta, ta tashi ta bar dakin a kunyace, ita kanta bata san menene ya hau kanta ba, yadda take ji idan bata koma ba, komai zai iya furuwa da ita. Ga wani masifaffen son cikin jikin ta da take ba zata so ya taso ba tare da mahaifin sa ba, ta taba karanta wani littafi da yarinyar ciki tayi gangancin kashe aurenta ashe akwai ciki, karshe haka ta haife dan a gida kuma ta cigaba da rainon sa a cikin bakar wahala, gashi duk wanda yazo auren ta sai yace ba zai rik'e mata da ba.    Text message ta sake tura masa na ban hakuri, kamar yadda take masa kullum amma baya reply, ko ranar da yazo gaisuwa gidan taso suyi magana amma kemaimai ya ki bata dama karshe ma ya daga wayar Hajiyar sa yayi tafiyar sa ya barta a wajen. *Adamawa-Yola* Ayi maneji😢😢🙌 _ZAFAFA2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/24/22, 08:09 - Buhainat: ®*Hafsat Rano*       _Halin Girma_             *42* *** *Adamawa-Yola* Dukkan su sunyi shiru da abinda yake sak'awa a rai, idan har ta tabbata Muhammad yana da evidence akan su, toh gaba daya lissafin su ya sauya. Amma kuma akwai abin mamaki ace yasan komai tsawon wannan lokacin amma be taba fadawa kowa ba, hatta mahaifiyar sa da yafi kusanci da ita akkowaan kowa.    Sanarwar shigowar sa masarautar ya sake saka su cikin tashin hankali, rige rigen lekawa suke kowa yana so yaga da wacce yazo, ba karamin kaduwa sukayi ba ganin shi cikin shigar saurata yayi masifar kyau, ya dauki wani siririn glass fari ya dora akan fuskar sa, murmushi ne kwance a fuskar tasa yana tafiya irin ta kasaita. Fada ya wuce kansa tsaye, bayan ya tabbatar da an gama tattara duk wasu masu fad'a aji na masarautar tasu, shi kanshi Bubu a cike da Mamaki yake musamman da irin hakan bata taba faruwa, ba ruwan Muhammad din da harkar cikin gidan balle har ya nemi ganawa da manyan fadar.     yadda ya shigo fadar kai tsaye ya saka wasu da yawa daga ciki yin mutuwar zaune, sakon shi ya iso musu tun kafin ya karaso. Wajen da ya saba zama ya samu ya zauna bayan ya kwashi gaisuwa. Su hudu suka shigo a tare hadda Kamal, suka samu waje suka zauna, daga nan bubu ya soma magana cikin nutsuwa da makasudin taruwar su a wajen. "Mun taru ne domin danmu Muhammad yana da bukatar ganawa da manyan masarautar saboda muhimmiyar maganar da ta kawo shi, wadda muke kyautata zaton zata kawo cigaba a masarautar tamu baki daya." Mikewa tsaye yayi ya sake gaisuwa sannan ya soma magana idon sa fes akan wambai da jama'ar sa. "Tsawon lokaci na dauka ina bin diddigin mutuwar marigayi tsohon sarki. Duk da karancin shekarun da nake dashi a wanchan lokacin amma ban manta ba, ban manta fuskokin mutanen da sukayi sanadiyar mutuwar sa ba." Hayaniya ce ta cika fadar kowa na kokarin tofa albarkacin bakin sa cikin tsananin mamakin maganganun Mohammad din wanda shi kansa Bubun be san da wannan maganar ba. Murmushi ne a kwance a fuskar sa yana karanta tashin hankali dake kwance a fuskokin su, tuni suka fara jikewa da gumi cikin yanayi na wahalarwa " Wacce irin magana ce wannan yarima?" Gyara tsaiwar sa yayi, ya sake kafe su da ido yace "Ayi min afuwa, na dauko maganar daga sama, sai dai ba kai tsaye nazo da maganar ba sai dana tabbatar da ina da gamsashiyar shaida wanda zasu zama madafa a gareni." Babu be tanka ba, ya dai zuba masa ido yana kallon sa yadda ya dake ya sake burgeshi, ya kuma ji a ransa lallai Muhammad ya shiryawa koma menene ,yadda ya dade yana nuna halin ko in kula da harkar gidan sai ya dauka be san komai ba, ashe yana sane har yana kokarin samun hujjar da zai tsayawa wan nasa da ya tabbatar da akwai wani bayanin a cikin labarin mutuwar tasa. "Mecece hujjar taka Yarima? Ko zamu iya sanin ta?" "Kwarai." Yace yana matsawa gaban Bubu, ya fito da envelope ya ajiye a gaban sa. Wannan ita ce hujjar da na rik'e nake kuma fatan abi duddugin abinda ya faru tun daga farko sannan ayi hukunci ga duk me hannu a ciki. Wani irin zillo wambai yayi, ya kalli Kamal ya kafe shi da ido yana masa alama da ya kasa ganewa, gaba daya ma shi baya cikin nutsuwar sa sakamakon maganar mahaifin sa da Mohammad ya taso da ita haka ta sama ta ka. Matsawa jikin wambai hakimi yayi, yayi masa magana cikin rada yace "Nayi zaton mun riga mun samu shaidar da yake magana a kanta a wajen Kamal ko? Ko wata shaidar ce daban da bamu sani ba?" "Yanzu ba lokacin maganar nan bace hakimi, kasan Kamal din be san flash din menene ba ya kawo mana, muyi fatan babu wata shaidar kuma." Moh na ankare dasu, yana kuma lura da yanayin su, wato a tunanin su sun zata flash din da ya basu a matsayin Musaddik shi kadai ne shaidar sa, lallai suna wasa dashi. Budewa Bubu envelope din akayi, flash guda biyu ne a ciki sai hoto da aka dauka amma yayi dishi-dishi alamun ya kwana biyu. Kallon hoton Bubu yayi sosai amma be gane komai ba. Projector aka kawo, aka jona Moh ya harde a wajen zaman sa yana fatan duk wanda yake cikin video din ya yanke jiki ya fadi a wajen saboda tashin hankali. Jikin wambai ne ya soma kakkarwa lokacin da aka kunna video, shine yake magana da Kilishi,maganar sa radau a lokacin da yake ce mata in dai suna so su rufe sirrinsu sai dai su kawar da maimartaba, da fari batayi na'am da maganar tasa ba, amma yayi yadda zaiyi ya saka ta amince, daga nan sai hoton ya dauke sai kara shuuu da ta cika wajen, zare shi akayi aka saka dayan, wanda yafi tayar da hankalin mutane, tsohon sarki ne a kwance sanda suke kokarin kashe shi, babu irin magiyar da be musu ba, amma suka ki, suka kashe shi ta hanyar danna masa pillow har sai da ya daina numfashi gaba daya, akan dalili daya tal, dalilin ya gano zaluncin da suka dade suna masa shi da Kilishi, dalilin da su da kansu zasuyi wa fad'a bayani kafin yasa a tusa keyar su. Salati ne ya cika a fadar, Bubu ya kawar da kansa yana jin dadi da Aji baya wajen, dalilin kenan da Muhammad din ya hanashi zuwa yace ya zauna a gida, dole idan yaga tashin hankalin nan ya rikice ga yanayi na girma. Mikewa wambai yayi ya hau fad'a yana nuna Moh "Karya yake yi wallahi karya yake, wannan shiryawa akayi amma karya ne, ni zaka wulakanta ko?" Wasu fadawa ne majiya karfi suka taso, suka dankwafar dashi sannan suka ce "Karya kake yi dan talakawa, Yarima yafi karfin ka jefe shi da wannan kalmar." "Ku kyale shi." Yace kamar be damu ba, ya kalli Bubu da shima yake kallo ya yi masa murnushin kafin yace "Za'a ji sauran bayanan da dalilin su na aikata wannan mummunan aikin daga wajen su." "Me zuku ce game da wannan video da Yarima ya gabatar?" Bubu yayi maganar yana dubansu dukkasu, kamar wanda aka soma a ruwan zafi haka sukayi tsamo tsamo, babu me magana a cikin su dan basu da bakin da zasu karyata shi, hawaye sosai Kamal yake bayan ya gama amincewa dasu ashe mayaudara ne. Juyar da fuskar sa Bubu yayi, yan sandan da Moh ya kira suka shigo, suka tattara su gaba daya suka fita dasu, jikin kowa yayi masifar sanyi da abinda ya faru, sannan sun yabawa kwazon Moh, sun kuma yarda da chanchantar sa na zama shugabansu, a take wasu suka fara maganar, Bubu na jinsu ya dinga murmushi yana kallon tilon dan nasa, cikin so da kauna, a yanzu ya kara tabbatar masa da shine zabi na kwarai da zai wa al'ummar sa, ya kuma gane dalilin sa na kin amsa tayin sa tsawon lokaci, ya kuma gane dalilin sa na zuwa a sauya dukkan tsarin sarautar gidan tasu. Yana kallon yadda mutane suka dinga zuwa suna kwasar gaisuwa, fuskar sa a sake yake amsa musu, da haka ya samu ya zame ya fice daga fadar ya nufi bangaren Kilishi wanda yasan sakon sa ya riga ya iske ta, ko tana wanne hali yanzu? Zai je ya gani da idon sa kafin ya karasa wajen Ammin sa, yana son ganin Laila suyi maganar Samha bayan nan. A duk abinda ya faru abu daya ne yayi masa ciwo, shine bayyananr asalin Kamal wanda ya kasance da ne ga wambai da Kilishi, ba dan tsohon sarkin bane, dalilin da ya saka su kashe shi kenan, saboda su binne gaskiya, su binne cin amanar da sukayi masa, duk don soyayyar su da mulki. Amma dole ba yadda ya iya, dole ne gaskiya tayi halin ta, ko da be fad'a a gaban kowa ba, yasan wadanda suke da hakkin su sani zasu sani din. Da kwarin guiwar sa ya isa shashen nata, ya shiga kai tsaye ba tare da wani ta tsaida shi ba, ya kuma sameta a zaune tana ta kuka wiwi, kamar wadda aka ce wani nata ya mutu, Kamal na tsaye a kanta ransa na suya, be taba tunanin abinda suka aikata ba kenan. Wani abu ne ya daki Moha, a karo na farko yaji tausayin su dukka, yasan rudin duniya da shaidan ne ya dibi Kilishi ta aikata abinda ta aikata din, shiyasa a kullum take shakkar sa, ta kasa aikata masa komai saboda yasan wani bangare na sirrinta, a tunaniin ta maganin ta ne ya ci shi da ya nuna halin ko in kula da harkar gidan, bata san yayi hakan bane domin ya samu gamsassun hujjoji, wanda zai karya duk wani mara gaskiya da tsoron Allah, ya kuma karbi kujerar da ta jima tana dakon jiran shi. Ya kuma amsa sunan Sarki Muhammad Ahmad Santuraki! ***** Satin ta daya aka sallameta, suka tattaro suka dawo gida,kwana daya su Mamma ta kara itama ta tafi dama Mummy ta wuce tun a kwana uku da tayi a asibitin. Gidan ne duk taji yayi mata ba dadi, ta mike daga kwanciyar da tayi tunanin mutuwar Mahfuz na bijiro mata, tayi kuka sosai da ta samu labarin dalilin ta ne ya gamu da iftila'in, shiyasa aka ce ajali ko aina yake komai nisan wajen sai kaje ka tarar dashi.    Ranar da Yaya mahaifiyar sa tazo sai da kowa ya tausaya mata, dan yadda take magana kadai zaka gane yadda mutuwar ta dake ta, mutuwar danka saurayi matashi ya tasa, bata tafi ba har yanxu kuma kusan kullum sai tazo asibitin taga Iman din wadda take sake sakata jin nauyin ta har ma da shi kansa Muhammad din, kwata kwata sai ya rage zuwa asibitin dan baya son suna haduwa zuciyar sa karye wa take, daga baya ma sai ya shirya tafiya adamawa yana kuma chan har aka sallame ta be dawo ba sai waya da suke yi.   Sallama taji anayi daga falo, ta mike a hankali saboda rashin kwarin jikin da take fama dashi, ta bud'e kofar ta fito. Da dan saurin ta ta karasa ganin yan matan nan ne da suka taba zuwar mata. Su biyu ne yanzu suka gaishe ta ta amsa a sake tana zama kusa da daya da take kan three seater tace "Ashe zaku zo?" "Eh Fulani ce tace muzo mu tayaki zama kafin Ya Moha ya dawo." "Kai amma naji dadi, sannun ku da zuwa ya mutanen gidan?" "Lafiya lou, ya jikin? Allah ya kara sauki." "Amin ya Allah, Nagode." Sai suka shiga hira suna bata labarin gidan su da wasu yan uwansu da duk sai a dubiyar ta sassansu. Ummimi ce ta shigo ta gaida su ta gyara wajen dining sannan ta fita, ta dawo dauke da manyan warmers ta jera a wajen tsaf sannan ta sake fita.    Su kadai suka ci abincin dan bata da appetite har lokacin, tea kawai ta sake sha tace zata dan kwanta, ta haye sama ta barsu suna kallo da danne dannen waya.     Tayi nisa sosai a cikin baccin ta wayar ta dake jikin socket ta shiga kara, kamar ba zata tashi ba, saboda yadda baccin ya soma dadi, kiran ne ya kara shigowa bayan wanchan ya katse, ta tashi da k'yar ta dauko wayar ta daga "Hajiya kinyi bakuwa." "Wacece?" Mike mata wayar yayi "Nice Iman..." "Zeenat, sannu da zuwa bashi wayar." "Sister dina ce, ku kyale ta." Ta katse kiran ta mike gaba daya ta shiga toilet ta gyara jikinta ta sauya pad sannan ta sakko. Da fara'a take kallon Zeenat din dake zaune tana karewa falon kallo cikin yanayi me ban tausayi, bata san Iman din ta fito ba har sai da ta dan dafa ta, ta kira sunan ta "Sannu da zuwa." Tace tana murmushi "Yawwa, bacci kike kamar na tashe ki." "Wallahi kinsan har yanzu ban gama samun sauki gaba daya ba, ya gida yasu Mama?" "Lafiya lou wallahi." " Ya jikin?" " Da sauki Alhamdulillah." " Allah ya kara sauki, ya bada na aike me albarka." " Amin." "Sai kika ganni kawai." "Umm..." Tace tana mikewa tayi hanyar kitchen, taje ta fad'a musu abinda zasu kawo sannan ta dawo tace ta taso, suka shiga wani daki a k'asan, suna shiga ta cire mayafin jikin ta da dankwalin ta ajiye a gefe.    Sallama Ummimi dake dauke da tray da abinci da ruwa tayi ta ajiye ta gaishe ta sannan ta ja musu kofar. "Bismillah ga abinci." "Toh..." Ta jawo kayan ta bud'e, yawun ta ya cinke ta zauna dirshan ta shiga dibar abincin nan babu kakkautawa, Iman na kallon ta bata ce mata komai ba, sai data ci ta koshi tasha juice da ruwa sannan ta mike kafarta sanyin AC na ratsa ta sosai. "Magana ce ta kawo ni, dan Allah taimako na zakiyi Iman." "Me ya faru?" "Dan Allah yallaban zaki ma magana ya kira Bashir dan Allah ya zo ya maida ni, wallahi na gaji so nake na koma dakin mijina." "Kina nufin dama kina gida?" "Tun yaushe? Tun sunan Anty Bilki fa." "Kai wallahi ban sani ba, matsala kuka samu?" "Uhmm.." "Ina jinki." "Shi da Mama ne, bayan yazo mu tafi mama tace ba in da zani taje ta same shi a waje bansan me ta gaggayawa masa ba, shikenan ya kyale ni." "Abba kuma ya sani?" "Ya sani, har magana yayi min wallahi, amma Bashir din yaki zuwa kemaimai, har gidansu Mama tasa Ya Habib ya kaini amma sam yaki, a dah ban damu ba, amma wallahi yanzu nayi karatun ta natsu, ko dan dan tahalikin nan da yake cikina." "Kema kinyi wauta, ita rayuwar nan baki daya da kika gani kowa hakuri yake da yadda tazo masa, shi kuma arziki lokaci ne." " Haka ne, na ga aya ai, son zuciya bacin ta, daga kin gaskiya aka ce sai bata, kema sam ban kyauta miki ba abubuwan da nayi miki a baya, ko yanzu kinga sakayya, Allah ya baki miji me sonki na nuna sa'a, gashi ya hada duk wasu qualities." " Ni ban rik'e ki ba ko da din ma." " Um um Iman, ni dai kiyi hakuri dan Allah." " Na hakura toh." " Nagode Allah ya saka da alkhairi, dan Allah ki taimaka ki masa maganar nasan shi idan shi ya kirashi ba zai taba ki ba." " Bari kiga." Tace tana tashi, taje ta dauko wayar ta dawo, ta zauna sannan ta kirashi " Bari naji idan yana free sai muyi maganar kawai." "Yawwa dan Allah." "Assalamu alaikum." "Wa alaikisalam Baby, na zata bacci kike ai, shiyasa ban kiraki ba ina jira ki tashi." "Na tashi ai, ban jima ina baccin ba. " " Kar dai yaran chan ne suka hanaki baccin da shegen surutun su. " " A ah, Zeenat ce tazo. " " Zeenat? " Yace cikin son tuno sunan, " Zeenat fa. " " Oh wai matar Bashir? " " Kai ko? " " Allah na manta ta, lallai ta kyauta, duba ki tazo. " " Eh. " " Ok yayi, ya gidan ya missing dina? " " Ina nan inayi, amma kad'an. " " Kiji tsoron Allah, ni nasan kinyi missing dina kamar yadda nayi " " Umm.. haka dai kace. " " Haka ne ma, idan na dawo zan gasgata kai na ai." " Can't wait." Ta saka dariya " Toh me yake faruwa? Babu wata matsala dai ko?" " Eh toh, dama Zeenat ce tazo, shine tayi min magana akan tana so dan Allah ka kira Bashir kace yazo ya dauke ta, Ashe tun ranar da mukaje suna gida bata koma ba, shi kuma be zo ba." " Toh... Ina Zeenat din?" " Gata." " Bata wayar." " Gashi." Ta mika mata, " Ina wuni?" " Lafiya lou, ya gida?" " Lafiya lou." " Menene ya faru?" " Dama..." Ta bashi labarin da ta bawa Iman bata rage komai ba, murnushin yayi yana daga zaune, a kalla yasan zuwa yanzu ta dawo hayyacin ta, ta kuma yi nadama tun daga yadda ta kwantar da kai tana masa magana, ya kuma tabbatar da uwar ta ma tayi laushi tubus, dama abinda yake so kenan, su russuna wa Iman dinsa har su nemi alfarma a wajen ta. "Shikenan ki koma gidan zaizo anjima." "Nagode Nagode Allah ya saka da alkhairi, Allah ya kara girma..." "Amin." " Hello..." " Baby zan kiraki anjima, ki kula da kanki kinji? Bye." " Bye." Ta kashe wayar " Yace naje gida zai zo." Ta fad'a cike da murna " Masha ALLAH hakan yayi." " Bari kiga na tafi, Mama bata san nan nayo ba asibiti nace mata zani, Nagode Allah ya saka da alkhairi ya bar zumunci." " Amin." Kofa ta rakota tare da bata kaya masu yawa a cikin leda tace ta gaida gida, ta kuma sa aka fitar da ita har in da zata samu abun hawa. *Ayi min afuwa jiya nayi kuskure wajen cewa Iman tayi sallah bayan tayi bari, ban ma lura da aika-aikar da nayi ba sai daga baya, ban yi editing page din ba sam ina ta sauri na tura. Ayi hakuri kuskure ne _ZAFAFA2022🔥_* *_NANA HAFSAT(MISS XOXO_* _SO DA ZUCIYA_ *_SAFIYYA HUGUMA_* _DABI'AR ZUCIYA_ *_MAMUH GEE_* _DEEN MARSHALL_ *_HAFSAT RANO_* _HALIN GIRMA_ *_BILLYN ABDULL_* _TAKUN SAKA_ *_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇 D'aya 300 Biyu 400 Uku 500 Hudu 700 Biyar 1k *_Zaku tura kudin a_* 6019473875 *MUSAA ABDULLAHI SAFIYA* *keystone bank* *Sai shedar payment dinki a*👇👇👇 08184017082 *Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇 09134848107 2/25/22, 18:10 - Buhainat: *Hafsat Rano*       _Halin Girma_             *43* ***kiran Bashir din yayi bayan sun gama wayar, be same shi ba, kila baya kusa. Ajiye wayar yayi ya maida hankali sa wajen Aji da suke magana kafin shigowar wayar tata. "Me ma kake cewa?" "Ungo nace." Yayi masa dakuwa Dariya ya saka har da buga kafa "Dan tsohon nan akwai riciki, toh ba zan waya da matata ba, naga kaima idan yar tsohuwar chan ta kiraka cikin rawar jiki kake zuwa." "Gwara ni ai, kai daga gani mijin tace ne ai, sai uban rawar kafa sai kace kanka farau a aure." Sake fashewa yayi da dariya cikin son kular da Ajin yace " Naga alama dai kana taya yar tsohuwar chan kishi ne." " Oho dai, matanmu na dah sun fi naku na yanzu komai da komai." " Habawa, banda tawa matar dai, tawa daya tamkar da dubu ce." " Toh Baban masoyan duk duniya, kaine ma ramiyo yake ko wa?" " Romeo ake cewa, ai nama fishi." " Kaji dashi, Allah yasa dai kar ayi lusarin sarki wanda mace zata dinga jujjuya shi, ya kasa aiwatar da komai." " Ai tunda kuka dage sai kun bani mulkin nan haka zaku hakura, ana cikin zaman fada zaku ga nayi fit na fice toh Itace tayi kira." Mikewa Aji yayi cikin kuluwa yace " Ka bada maza wallahi, kaga tafiya ta ba zan iya kin wannan shirmen naka ba mara kan gado." " A gaida min tsohuwar sarauniyar taka, zan shiga anjima naci tuwon wajen yar tsohuwa." Murmushi kawai yayi, ya fice fadawan sa suka bi bayan sa, yana da kwarin sa har yanxu ba zaka taba cewa ya kai shekarun sa ba, Allah ya bashi lafiya me inganci sai dai fatan gamawa lafiya.   Yana fita Bashir ya kira, sai da ta kusan katsewa sannan ya daga yana mikewa tsaye daga kishingid'ar da yayi dan yana so yaje yaga Ammi dan da wuri sai wuce gobe, sai kuma ya gama tsaf da chan sannan zai tattaro ya dawo nan din. " Yallabai barka da warhaka, ayi min afuwa ashe ka kira." " Barka dai Bashir, eh na kira ai ban dauka ma ta shigo ba." " Wallahi network din ne, Allah ya baka yawan rai ya aiki?" " Mun gode Allah." " Masha ALLAH, Allah ya taimaka ya bada sa'a." " Amin, alfarma nake nema wajen ka." " Habawa, wane mutum, ka fadi ko menene kake so, an gama kawai." " Bashir kenan, toh Nagode. Dama so nake idan Allah ya kaimu bayan Magriba kaje ka dauki matar ka ku tafi gida, shi aure daka gani ya wuce duk in da kake tunani ko hasashe, hakuri shine ribar zaman dan haka ka ajiye duk abinda ya faru a baya, ka fuskanci rayuwar ka." "In Sha Allah an gama, dama so nake ita da mahaifiyar ta su fuskanci rayuwar yadda take." "Zuwa yanzu sun gane ai na sani, kaje ka dauki iyalin ka." "Zanje in sha Allah, nagode Allah ya kara girma." "Amin nagode." Sallama sukayi ya ajiye wayar, dama yana son yaje ya tafi da ita dan ya gane yadda ta damu ta dawo ko da text message din da take masa, shima kuma abinda yake so kenan, abu daya ya saka shi delay shine kayan dakin da ya saka akayi mata masu kyau daidai kudin sa, sai sabon gidan da Moh din ya bashi a lokacin bikin me kyau madaidaci two bedroom da falo da kitchen sai parking space, wanchan gidan da aka kaita hayar sa suka karba amma ba shine ainahn gidan da ya bashin ba.   Kayan duk sun zama ready an saka komai an kwaso kayan kitchen dinta an zuba mata gidan yayi kyau daidai gidan amarya. Shi kansa yanzu yake jin sa a angon na gaske, bayan doguwar dambarwar da suka sha da hajjajun sa karshe dai sun rabu bayan ya dawo ya tarar da ita suna aika-aikar su da kawayen ta, da yayi magana ta taso masa kamar zata dake shi, karshe ma tace ya saketa ta gaji da auren sa, ta samu wani sabon saurayin me jini a jika, da farko yayi ta mata magiya akan tayi hakuri amma fafur taki, sai kawai ya danne zuciyar sa ya saketa, aikuwa yana sakin nata yaji wani sakayau kamar an zare masa wani mugun nauyi, sai ya hau tunanin ta yadda akayi ma ya aure mace irin ta bayan ya san abinda take aikatawa, abu daya ya sani shine kwadayin abun duniya ne ya kwashe shi har ya yarda ya amince ya aureta, bayan ta jika shi da kudi masu yawan gaske. Text message Moh ya turawa Iman yace ta fadawa Zeenat ta shirya zaizo bayan sallah, aikuwa tayi mata forwarding text din tana gani kuwa ta kirata ta dinga mata godiya. Dakin Mama ta wuce ta sameta a zaune ta rafka tagumi yadda abubuwan suka sauya mata a lokaci daya shine yake bata mamaki, ba tun ranar ta gano Abba so yake ya maida auren su da Maman Iman ba, sai yau ta gasgata hakan da yace mata ya tafi Abuja. Karamin hauka tayi masa amma yayi biris yayi tafiyar sa. Ko da Zeenat ta zo mata da labarin zuwan Bashir din sai taji dadi, a kalla zata huta da maganar yan gidan da ma makwafta akan zaman Zeenat din a gidan. "Sai ki hau shiri ai, kafin yazo, kinje kin shantake a asibitin da tun dazu kika dawo ai da kin yi shirin da ya kamata." "Anya ma asibitin kawai kika je?" "Eh mama, chan naje likitan ne be zo da wuri ba." "Toh sai ki shirya." Tace mata "Toh." Daki ta koma ta dan harhada abinda zata hada, ta zauna tana lissafin awowin da suka rage, sai ga Mama ta shigo da Madara a kofi me dumi ta bata tace ta shanye, ta karba ba musu ta shanye tas ta bata kofin ta fita. Har akayi sallar magriba aka idar da wajen minti talatin be zo ba, ta gama matsuwa Mama na lura da ita, ita mamaki ma take yadda ta juye lokaci daya. Ana idar da sallar isha'i ya aiko yaro wai Zeenat tazo inji Bashir, da sauri ta mike Mama ta harare, ta koma jiki a sanyaye ta zauna "Je kace ya shigo wai." "Hankalin ki ya dawo jikinki kinji? Wannan rawar kan ta mecece? Anya ma yaron nan haka ya barki kuwa?" "Mamaaaa." "Ba wasa nake ba, ki nutsu ki dawo nutsuwar ki wannan rawar kan babu abinda zata jawo miki sai raini wajen namiji, kayi biris da harkar namiji ma amma be fasa gasa ka ba, ina ga kana rawar kafa akansa? Daga cewa gashi sai ki mike kina barin jiki ke me miji ko? Toh ki shiga taitayin ki." "Mama ai ba laifi bane, tunda shi din miji na ne." "Inyeee Zeenatu?" Ta fad'a cike da mamakin Zeenat din, sallama yayi a kofar, kafin ya shigo sanye cikin shadda sabuwa kar, sai kyalli take da kamshi, cikin ido suka kalli juna da Mama, ta kauda kanta haushin shi na tike ta, sai ta ga ma kamar da gayya yake wani irin murmushi. " Mama ana gaishe ki." Zeenat tace jin Maman bata amsa gaiswar Bashir din ba " Lafiya lou, ya gida." Harara ta watsa wa Zeenat din ta dauke kai kamar bata gani ba, sai ta tashi tsam ta tayi hanyar barin wajen tace " Ku gaida gida." " Mun gode Mama Yace yana hayewa kujerar, tashi Zeenat tayi tabi bayanta dan yi mata sallama, ya bita da kallo yana kara bararrajewa a saman kujerar. Suna shiga Mama ta turnuke ta da fad'a, ta inda take shiga ba tanan take fita ba, tayi mata tatas saboda bakin ciki, karshe tace ta bata waje. Sallama tayi mata bata amsa ba, sai ta tsaya taki tafiya tana kallon Maman " Uban me kika tsaya kina yi anan? Ko jiranki zai yi? " " Naga kina fushi ne, kiyi hakuri dan Allah ko na hakura da tafiyar kawai tunda naga kamar bakya so. " " Inji uban wa nace bana so? Yadda ma kike rawar kafar nan ko bana so zaki hakura ne? " " Eh. " Ta daga mata kai " Ke ni karki rainan hankali, wuce kibi mijinki Allah ya bada zaman lafiya. " " Amin. " Ta amsa hakan ya sake tike Maman. Ta juyar da kanta sai da Zeenat din ta fita sannan ta zauna cikin rashin sanin abinda kuma ya kamata tayi. Gashi dai a karshe abinda tayi ta yi akan Zeenat din duk ya tashi a banza, gashi ta rasa damar ta a wajen Abba wanda ba zata taba dawowa ba, karshe kuma yar ta zabi mijinta akan zaman gidan nasu. ***Da dan gudun Amaani da Amaan suka tare shi, kamar sun sanshi tun da dadewa, kamar sun saba dashi. Yana da son yara ko dan saboda be haifa da yawa bane, Amaani sak Fatiman sa sai dai ita bata da hayaniya da kwarafniya irin ta Amaani din, kamar yadda mahaifiyar su take haka take itama a nutse tun tana karama har kuma girman ta. Su suka jagorance shi zuwa ciki, ya zauna yana tuna shekarun baya da ya kasance a same wajen, a lokacin da yazo su kayi magana da Alhaji, kamar a lokacin komai yake faruwa. Turo kofar da akayi ne ya sakashi waigawa, itace dai a shekarun baya sai dai girma da ya soma kamata, duk da haka ba zaka taba bata shekarun ta ba, balle har ka kawo ta ajiye budurwa kamar Iman din, kullum cikin gyara take tsaf. Ko a baya yasan yayi missing mace kamar ta, sai dai a yanzu sam be zo da wasa ba, da gaske yake wannan karon sai dai duk abinda zai faru ya faru. Babu gudu ba ja da baya! "Sannu da zuwa." Tace tana zama a chan nesa da kujerar da yake kai. Sannan ta gaishe shi ya amsa yana satar kallon ta, shiru suka dan yi kafin ya sake bijiro mata da maganar da ta sakashi tasowa gari i gari zuwa Abujan, a tsammanin sa sai sun kai ruwa rana zata amince, amma sai ta bashi mamaki matuka, yadda kai tsaye tace Allah ya zaba musu mafi alkhairi. Da farin ciki ya baro garin na Abuja, ya dawo ya tarar da Mama bata da lafiya, ya tausaya mata tunda shi mutum ne me tausayi, har ma ya saka Habib suka kaita asibiti in da aka ce dole ta rage tunani saboda jinin ta da ya hau sosai, aka rubuto mata magunguna suka tattaro suka dawo gida. ***Bayan sun gama waya da daddare zasuyi sallama yace ta shirye shi gobe yana nan dawowa, reaction dinta kadai ya gamsar dashi yadda tayi kewar shi. Yana jin yadda take farin ciki ta cikin wayar sai dai kara irin tata ta hana ta nuna masa, a hakan ma ya gode dan yasan ya chanja ta sosai daga auren su zuwa yanzu. Sauran chanjin kuma sai a hankali zata saba da kalolin soyayyar sa masu tsayawa a zuciya. Neman baccin da take yi tayi ta rasa, ta tashi ta sauka daga gadon ta bud'e wardrobe dinta, ta hau duba kayan da take ganin ya dace ta saka, sai data dau lokaci tana zaba kafin ta tsaya akan wani hadadden lace wanda dinkin sa ya fita sosai. Murmushi tayi ta fito dashi ta ajiye a gefe ta hada da set of jewelries da zasu dace da lace din sannan ta kwanta tana lissafa kalolin girke-girken da ya kamata ta tarbi mijin nata dashi, da haka bacci ya dauke ta bayan ta gama hada komai a cikin kanta saura kawai girkawa gobe idan Allah ya kaimu. Kasancewar tana cikin zumudin dawowar sa yasa ta tashi da wurwuri, ta duba kitchen na abubuwan da zata bukata wajen girkin wanda babu ta bawa Ummimi sautu suka je da driver suka sissiyo, sannan suka shiga aikin tare da sauran ma'aikatan dake kula da kitchen din amma kuma Itace akan girkin sai dai su taimaka mata da dauko wa da mikowa. 2/26/22, 19:09 - Buhainat: *Hafsat Rano*       _Halin Girma_             *44* ***Da wurwuri yaso tahowa amma sai case din Kamal da Kilishi ya tsaida shi, sosai Kamal ya tada hankali a gidan tun bayan da ya tantance ainihin shi din waye, ya kuma gano wambai ne Mahaifin sa. Baki daya Kilishi ta nemi kwanciyar hankalin ta ta rasa, gashi har lokacin bubu be ce ga hukuncin ta ba, sannan ita kanta Laila ta birkice mata, babu Moh kamar yadda ta kwallafa rai, ga bakin cikin cin amanar da Samha tayi mata ga kuma abinda mahaifiyar ta wa mahaifin ta.    Takanas taje ta samu Bubu ta roke shi akan ya barta ta koma karatun ta dan zaman ta anan din komai zai iya faruwa,da farko be amince ba sam, yace mata be yarda ba tayi hakuri ta kawo miji aure zai mata. Sanin bata da wani tsayayye da zata nuna yau yasa ta samu Moh ta roke shi cikin kwantar da kai tace ya rokar mata Bubun ya barta. Ko da ya samu Bubun da magana shima fafur yaki, sai da yayi ta masa magiya sannan yayi masa alkwarin duk wani abu da ya faru shine zai dauki responsibility din, a haka yayi convincing Bubun ya amince yace ta koma din,amma da sharadin idan yaji wani abu mara dadi ko mara kyau toh fa shi zai kama da laifi kuma dole ya karbi aurenta.     Godiya tayi ta zuba masa kamar ta rungume shi haka take ji, har gobe tana son sa, ba kuma ztaa daina son nashi ba, zatai ta hakura for now tayi concentrating akan karatun ta, ta samo ta kammala shi kafin tasan kuma me ya kamata tayi kuma anan gaba. Akalla idan tayi nisa da gida zata manta abinda Kilishin tayi da dan lokaci ta kuma samu damar mantawa da Moh din shima na wani lokaci hankalin ta ya kwanta ta nutsu waje daya.    ***A daki ya tarar da Ammin tasa, wanka tayi ta gama shiryawa kenan zata fito ta yi breakfast ya shigo, ta bishi da kallo har ya zauna a k'asa wajen tumtum din da take hutawa idan tana dakin, ya tankwashe kafafuwan sa sannan ya gaishe ta cike da ladafi. Kusa dashi ta zo ta zauna tana amsawa, tasan sallama yazo yayi mata tun jiya dama ya sanar da ita komawar tasa yau ba kuma zai dawo ba sai ya gama da chan din, sannan yazo a shiga bikin nad'in nasa, wanda tun yanzu Bubun ya soma aikewa da goron gayyata dan taro yake shiryawa na ban mamaki.    "Tafiyar ce Babana?" "Eh wallahi, na zata ma fa baki tashi ba." "Wa? Ka manta da wuri nake tashi, kwana biyu ne da kafa ta matsa min bana samun bacci sosai da daddare sai na rama da safe." Kafar tata ya matsa mata " Har yanzu tana ciwon?" " Ta warke yanzu ai." " Allah ya kara sauki." " Amin." " Idan naje sai mun tashi dawowa gaba daya, ina fatan abun da nayi ya dace." " Kayi abinda ya dace, kuma ka farantawa mahaifi ka da zaka cika masa burin sa, Allah yayi maka albarka ya baku zuria dayyiba, inaso na goya yan jikokina a bayan nan nawa." " Dukka ma zamu baki Ammi ta, halak malak. " " Um um dai Babana, kar kayi alkawarin da ba zaka cika ba. " " Da gaske nake Ammi. " "Toh shikenan Allah ya kawo mana masu Albarka. " " Amin ya Allah. " Ya amsa yana mikewa " Ammi zan wuce, ayi mana addu'a. " " Allah ya taimaka ya bada sa'a, a gaida min da yata kafin tazo, zan kira na sake dubata idan ka sauka. " " In sha Allah Ammi ta. " Bin sa tayi da kallo har ya bace wa ganin ta, ta sauke ajiyar zuciya tana jin soyayyar tilon dan nata, tana alfahari dashi, daya ne tamkar da dubu yana mata biyayya daida gwargwado.   Be samu ganin Bubu ba, dama sun riga sunyi sallama tun jiya, dan haka kai tsaye mota ya shiga, karo na farko zaiyi tafiya cikin rakiyar tarin fadawa ba sojoji ba, wani daban yaji, gargajiya sosai da al'adah irin ta gidan sarauta. Shi kansa shigar da yayi kenan, shiga irin ta Yarima me jiran gado, a dan kwana biyun da yayi har ya saba da saka kayan , yana kuma jin dadin su dan suna sake fito da kamalar sa.    Tun daga airport ya fara cin karo da abinda ya tsana da sarauta, yadda ake kokarin kaiwa kasa wajen gaishe shi, har ga Allah baya so kuma dole zai san yadda zai ya hana irin wannan gaisuwar. Basu jima da zuwa ba jirgin su ya tashi zuwa birnin na Kano, in da ya tanadi kalolin soyayyar da zai bajewa sahibar tashi, kafin ya dawo ya karbi sha'anin mulkin da baya jin zai rage masa wani abu daga cikin irin rayuwar da ya tsara musu, sai dai yasan dole sai ya dinga raba lokacin da mutane, amma haka zai yakice ya dinga yin abinda ya dace.    ***Tun da taga komai ya gama haduwa sai abinda ba za'a rasa ba, sai ta bar musu sauran aikin su karasa ita kuma ta haye sama don yin wanka ta shirya tarban mijinta. So take ta burge shi sosai, duk da ita din ba gwanar kwalliya bace amma zata kokarta, sannan zata cire kunya ta rungume mijinta taji dumin jikin sa sosai.    Wanka tayi ta sake wanke bakin ta tas, sannan tayi amfani da mouth freshner me kamshi ta kuskure bakin sannan ta fito tayi zaman shiryawa a gaban mirror. Ta dan dau lokaci tana shiryawar duk da ba wani make up tayi ba, amma tayi kyau ainun. Kayanta da ta turara akan kabbasa ta dauko ta saka, sannan ta sake bin jikinta da turarurruka masu sanyi da dadin kamshi. Samun kanta tayi da yin murmushin yadda ta fito tayi fes, sai taga har wani fari kamar ta kara tayi fresh da ita.     Zama ta cigaba da yi a saman nata tana dakon zuwan sa. Waya ta dauko da nufin kiran Mummy sai taji karar zuge gate din gidan, ta fasa ta tashi da sauri tayi wajen window ta daga tana kallon motocin da ke shigowa suna samun matsuguni a cikin gidan. Motar da yake ciki ta zubawa ido, a hankali ya zuro kafarsa cikin takalmin sa da akayi da zallar fatar damisa, daga yanayin takalmin nasa ta gane irin shigar dake jikin sa, tun kafin ma ya gama fitowa ta gama wassafa yadda kayan suka karbe shi.    Kamar wanda aka ce ya daga kai zuwa saman, sukayi ido biyu tana leken sa, da sauri ta saki labulen sanda ya kashe mata ido daya gami da murmushin sa me tarin bayanai a cikin sa.     Gaban mirror ta koma ta sake fesa turare sannan ta shafa khumra me kamshi a tafin hannun ta, ta dauki flat shoe me kyau ta saka ta sauko k'asa. Tana saukowa yana shigowa falon. Tsayawa yayi a kofar ya toge ya bud'e mata hannayen sa, cikin sanyin ta, ta tafi zuwa gareshi, ta fad'a jikinsa ya rungume ta yana jujjuyasu a wajen, kamshin turaren ta na ratsa kofofin hancin sa. "Ya Allah, ashe haka nayi kewar ki?" "Um... Barka da zuwa yallabai." Tace tana dago kanta daga jikin sa " Barka dai gimbiyar Muhammad." " Muje ciki?" " Bismillah... Ladies first " ya matsa yana nuna mata hanya, yana so ya more kallon tafiyar ta. Bata kawo komai ba tayi gaba ya bita yana murmushi, a tsakiyar falon suka yada zango. "Wash." Yace yana taro ta jikin sa, ta zame tana masa dariya "Wanka ko lunch?" "You." Ya kashe mata ido, dariya kawai tayi, ta je ta kawo masa lemon kwakwa da tayi masa yayi sanyi sosai ta zuba masa a glass cup ta dan russuna ta mika masa, ya hada da hannun ta ya rik'e tayi yar kara "Auw, sorry baby." Ya saki hannun ta zame shi tana marairaice fuska kamar zatayi masa kuka. "Sai na rama." Ta koma ta kawo kayan abincin ta jera masa a wajen, ya mik'a mata hannu ta daga shi, ta noke tana durkusawa da nufin zuba masa, rigar ta da akayi wa dinkin V-shape daga wuyan ya kalla yana cije lips dinsa. "Bismillah." Tace tana dagowa, ga mamakin ta sai gani tayi ya zuba wa kirjin ta ido, kunya ce ta kamata ta daga da sauri, ya waske yana zamowa "Kayan nan yayi miki kyau" Kin kallon sa tayi, ya dauki spoon din ya fara cin abincin yana kunshe dariyar sa. "Ya jikin naki?" "Alhamdulillah, da sauki. Yasu su Ammi?" "Lafiya lou, suna gaida ki, tace zata kira ma ta sake duba ki kafin muje." " Ayya, na samu sauki ma ai." " Naga alama ai, har wata kiba kika kara da kyau, musamman ta nan..." Ya nuna chest dinta da idon sa, kau da kai tayi tana hararar sa " Kai ko?" " Me nayi? Daga fadar gaskia? Allah baki gani ba." " Uhummm." " Da gaske fa nake, komai masha Allah." Murmushi kawai tayi, dan ta lura jan magana yake so yayi, aikuwa ya cigaba da yi zuzutawa kyaun da tayi. Ita ma kanta tasan tayi kara wani irin kyau na ban mamaki. Sai da ya gama tas ya shanye lemon kwakwar nan sannan ya kama hannun ta suka haye saman, su Ummimi suka zo suka tattare wajen suka gyara aka saka turaren wuta. Manage muna biki ne    2/27/22, 23:33 - Buhainat: *Hafsat Rano*       _Halin Girma_             *45* ***Washegari suka tashi cikin farin ciki da annushuwa. Yana shiryawa a gaban mirror ya kalle ta ta cikin mirror din tana ajiye masa kayan da zai saka yace "Maganar school dinki, transfer zamu nema zuwa adamawa." Tsayawa tayi da abinda take ta kalle shi "Komawa zamuyi chan?" "Yes, zamu koma gida, zan ajiye aiki na, na karbi Bubu." Wani gingirim taji maganar, ta tsaya a wajen sakato tana son ta fuskanci zancen. Gabanta yazo ya tsaya yana murmushi "Kina mamaki?" "A'ah, ban gane bane I'm confused." Dariya ya saka "Don't be, ki shirya you are soon to be the wife of his royal highness!" Wani shock tayi cike da mamakin "Zaka karbi mulki?" "In sha Allah, shine burin Bubu, zan cika masa burin sa kamar yadda yake so." Da baya ta koma ta zauna a gadon kanta na mata wani iri. Matar sarki fa? Ta Yaya zata iya? Taya zata fara? Bayan bata san komai cikin sha'anin irin wannan ba, dafa ta yayi ya mik'ar da ita tsaya yana mata dariya "Look at you, bafa yaki bane, normal ne kawai." "Bansan komai ba ai, ta yaya zan fara? I'm nervous." " Karki damu kinji? Muna tare ai." " Allah ya taimaka ya bamu sa'a, Allah ya bamu ikon yin adalci da aikata daidai." " That's my queen, abinda zaki ce kenan kawai, nasan zaki iya, I trust you." " Banda fasa kai." " Da gaske nake, nasan zaki iya handling kowanne irin situation." Murmushi tayi, sai kuma wani tunani ya fado mata, " Shikenan sai ka kara aure?" Ta samu kanta da tambayar shi cikin sanyin murya " Aure kuma?" " Eh ba sarakuna basa auren mata daya ba, wasu ma har da kwarkwara suke yi." " Eh toh..." Ya mike yana saka links a jikin rigar, " Me?" " Ban dai san nawa zan ba ni ma, amma nasan zan kara uku na cike kinga hudu kenan." Gabanta ne yayi mummunar faduwa, ta dinga kokarin karanta gaskiyar sa ta hanyar kallon fuskar sa. He looks serious, sai taji wani kuka na taso mata, tayi kokarin dannewa tana kokarin barin dakin gaba daya, riko ta yayi da sauri ya dawo da ita yana dariya "Kishi?" "Zanje k'asa na dauko abu ne." Tace tana avoiding kallon fuskar sa dan ji take kamar ta fashe da kuka "I love this new side of you Baby, yayi miki kyau." Haushi ne ya sake turnuke ta, wato shi wasa ma ya mayar da abun, fusge jikinta tayi, tayi gaba da sauri ta bar masa dakin, tana fita hawayen da take da rikewa suka zubo, shikenan ace a karaamin shekarun ta zata fara zama da kishiyoyi ba ma kishiya ba, har ga Allah bata da hayaniya da fitinar da zata iya zama dasu, ga hayaniyar gidan sarauta da shegen makirci wanda take tsoro tun farkon fari da ta gano waye ta aura. Tsaye take jikin staircase bata sauka ba, ya fito ya tadda ta a wajen, sai ta waske tana kokarin sauka ya chapko ta. "Babu in da zaki sai mun karasa maganar mu." "Ni fa babu komai, abu zan dauko a k'asa." "Ba in da zaki." Ya juya da ita zuwa ciki, ya zauna ya dora ta a saman cinyarsa. "Ashe dai ana kishi na haka." "Nifa ba kishi nake ba, tambaya kawai nayi kuma ka bani ansa ai." "Bari kiji, kinga bamu ne muke da ikon tsarama kanmu rayuwa ba, idan ma ka tsara tsarin Allah daban ne. Bani da sha'awar kara aure amma bansan me gobe zata haifar ba, karki damu let's pray for the best kinji? Muhammad dinki yana sonki sosai, wannan kawai ya isheki ki mikar da kafarki kamar kin hau jirgin sama mai ya kare." Duka ta kai masa suka yi dariya a tare, a kalla dai ya fad'a mata iyakar gaskiyarsa, kuma hakan da yayi ba karamin burge ta yayi ba, taji ta kara son shi fiye da baya. Tare suka karasa shiryawa ya taimaka ya saka mata Alkyabba akan kayan ta, ya gyara mata sosai tayi kyau, ya ciro waya ya yi musu hoto me kyau, sannan suka fito, suka tarar da su Ummimi da sauran yan matan uku sun shirya tsaf suna jiran su, waje kuma fadawa ne suma a shirye an gyara motar. Hannun su sarke da juna suka sakko, duk suka zube suna kwasar gaisuwa, kafin su karasa an bud'e musu motar sai da ya bari ta fara shiga ta zauna sannan shima ya shiga. Sauran motocin su Ummimi suka shiga sai fada. Sanda suka isa Takawa be riga ya fito zaman fada ba, sai suka wuce kai tsaye wajen sa, suka sameshi a wajen karatun sa tare da Fulani,a kunyace Iman ta gaishe su amma sai taga kamar basu damu ba, sun sake sosai kamar ba sarki ba, suka dan tsokani juna da muhammad kafin su barsu ita da Fulani zuwa bangaren ta, ba chan waje suka koma ba, wani corridor suka bi har chan din, tasha kallon haduwar wajen a hanyar su ta zuwa har suka dangana da chan sashen. Har yamma likis suna gidan, bata sake ganin muhammad ba sai da yazo zasu tafi, ya shigo kamar bashi ba, hatta da takun sa sai data ga ya chanja ya zama irin na saraki masu ji da jini a jika, za'a ga hadadden young Sarki, ga kyau ga aji. Sai da ya zauna fadawan suka fita sannan ya dube ta ya kashe mata ido ba tare da Fulani ta gani ba, murmushi tayi kawai ta saukar da kanta dan Fulani ta fad'a mata yadda tsarin sarautar yake, dole tayi takatsantsan da abubuwa masu yawan gaske, ta kuma ce nan zata dinga zuwa kullum tana ganin yadda abubuwan suke kafin tafiyar su. Haka kuwa akayi, kullum sai sun fito da safe sai dare suke komawa kuma bata sake ganin shi wani lokacin ma sai dai su hadu a mota idan zasu tafi. ***Maganar Abba da Maman Iman ta Rayuwa ta cigaba da garaw