💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* *🔥The Father Of Soldiers🔥* ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ❤‍🔥💞💘? *Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad* ~💋BOSSLADY💋~ _Sabuwar Marubuciya, mai tafe da sabon salo💫_ *Abban Sojoji part 2* *EPISODE 1* Meaning Of Name *AMANI* means *wish* arabic name ne na mata🌹ina faɗin ma'anarsu ne saboda masu tambaya, sunaye ne masu kyau mutun zai iya amfani dashi in yana so wa baby girl ɗinsa😍 Ruwan sama ake yi sosai garin, yanayin yayi wani irin daɗin gaske, ga wata irin ni'imtacciyar iska wadacciyar da ta gauraye ko'ina, wurin ƙarfe 5 na marece ne amma sai kayi tunanin dare ne sosai saboda Lullumin da garin yayi, a wannan yanayin kowa na ƙumshe a bedroom ɗinsa saman gadonsa, lullu6e da bargo, baka jin hayaniyar komai ko'ina tsit a cikin gidan 😊 zaune suke acikin mota suna tattaunawa su biyu, Hafsat ce tare da wata Hamshaƙiyar mata wadda bansanta ba, jikinta na sanye da tsadadden leshi Ash colour, fara ce kana ganinta kasan taji hutu Over ya zauna mata, ita ce a mazaunin driver yayin da hafsat ɗin ke gefen ta suna tattauna wa, Hafsat ta natsu tana sauraronta " Naci sa'a da nasamu address ɗinki kuma na same ki cikin sauƙi, kuma ina fata zaki taimaka mun wurin cimma burina,' matar ta faɗi tana kallonta, Hafsat tace "ina sauraronki me kike so inyi miki ne "? Murmushi matar tasaki kafin tace "Kafin na faɗa miki abunda nakeso, pls ina so ki fara bani acct number ɗinki," Bin ta da kallo hafsat tayi cikin mamakin jin abunda matar tace, Amma batayi musu ba, ta shiga karanto mata numbar acct ɗin, ita kuma tana kwashe wa a wayarta dake hannunta, Bata jima da gama karanta mata numbar ba sai ga Alert ya shigo a wayarta ƙirrrr! Cikin sauri hafsat tasa hannu ta ɗauki ƴar purse ɗinta dake asaman Laps ɗinta ajiye, ta zugeta ta ciro wayar jiki na rawa ta duba, gabanta ne taji ya faɗi rass !! Ganin Alert na 6millions abun kamar a mafarki take ganinsa Cikin tsananin mamaki ta ɗago ta kalli matar tare da cewa "Wannan fa? Na menene? dariya matar tayi kafin tace " akwai wasu tagwayen Yara da Marshal Omar ya kawo gidan nan, Sunan su Hosana da Jahad,' Jin sunan da ta ambata yasa hafsat kallonta cikin mamaki,. Taci gaba da cewa "Ba wani aiki bane mai wahala, so nake subar gidan nan ! Suyi nesa da Marshal Omar..........' Cike da mamaki hafsat ke kallonta , babban abunda ya ɗaure mata kai shine yadda akai tasan cewa Marshal Omar ya kawo yara acikin gidan,. Daker ta iya cewa "Saboda Me za'ae hakan? "Saboda basu da amfani," matar ta bata amsa a taƙaice, Shiru hafsat tayi tana kallonta acikin zuciyarta tana Was wasi akanta, "Wacece ke? Taya akai kikasan sunan Tagwayen tare da kuma sunan Omer? "Ba buƙatar wannan, Kawai kiyi mun abunda nace in aikina yayi kyau nayi maki alƙwarin zan ninka miki abunda na baki har sau uku, Hafsat tace "To shikenan ni zan wuce ciki sai kin jini" Murmushi matar tasaki tare da cewa "sai mun sake haɗuwa," fito wa hafsat tayi daga Motar ta rufe mata sannan ta wuce cikin gidan da hanzari saboda ruwan dake sauka ajikinta, Yayin da ita kuma Matar taja motarta ta fuce daga gidan fuskarta ɗauke da murmushin nasara, tana shiga cikin babban falon ba kowa kai tsaye bedroom ɗinta ta wuce, cire kayan jikinta tayi shaf shaf ta canza izuwa riga da wando, ta ɗaure gashin kanta a baya, tana tsaye gaban Mirror tana tunanin maganar Matar nan data kawo mata ziyara sai ga Aunty Babba ta faɗo ɗakin tana faɗin "Hafsat wacece waccan matar da tazo wurinki yanzu"? Juyowa hafsat tayi tana kallonta tace "Nima bansanta ba address ɗina aka mata shine tazo da buƙatarta," "Wace irin buƙata kenan"? Aunty babba ta tambaya tana kallonta, Hafsat tace "Tayi mun magana akan cewa tana so in raba twins ɗincan da Omar ma'ana subar gidan nan gaba ɗaya, Suyi nesa dashi" tsoki aunty babba taja tare da cewa "Ita kuma wacece ita isasshiya? halan Omar take so ne shiyasa ta biyo ta wurinki?. "Bana tunanin hakan, Nafi tunanin Tasan Yaran ne shiyasa take son azubar dasu," "To ke kuma kin amince da buƙatarta kenan"? Murmushi hafsar tasaki tare da cewa "eh mommy na amince da hakan, saboda anan take ta bani miliyan shida kuma tace muddin aikinta yaci ka zata ninkamin abunda tabani ynx," tuni aunty babba ta haɗe fuska rai a6ace tace "Amma ke shashashar ina ce? Kawai daga zuwan mata sai ki amince mata da buƙatarta? matar nan fa Omar take so shiyasa takeson a salwantar mata dasu," "Koma dai menene Mommy ni bazan bari kuɗin nan su wuce ni ba, saboda ina cikin buƙatarsu, daddy baya sakarmun kuɗi yadda ya dace ke kuma tanadin ki na zuwa wurin bokane kema fa bakya bani ko sisi Burinki akan hayaam da Abrah ne," . Matsawa Aunty babba tayi kusa da ita tana cewa "Hafsat Anya kina cikin hayyacin ki kuwa? Ni kike faɗama haka"? "Na faɗi wani abune daba dai dai ba? ta tambaya tana kallon mommyn nata, Ido cikin Ido Sassauta Murya Aunty babba tayi a ƙoƙarinta nata fahimtar da hafsat tace "duk wannan tanadin da nake saboda kanmu ne fa ! Ƙaruwar mu ce, in har naci nasara akan burina Hayaam tasamu RAFAYET ita kuma Abra tasamu MARSHAL OMAR mune zamu ji daɗi, don haka am commanding u ki tattara kuɗin da tabaki ki mayar mata dasu yanzun nan !!!! ta faɗi a tsawace Dariya hafsat ta kwashe da ita hada tafa hannu bayan ta tsagaita tace "Mommy kenan !! nima fa lashe Money ce kamarki, bazan bari garabasar nan ta wuce ni ba!! Akace da arziƙi a gidan wasu ƙwara agidanku, kai agidan nakuma kwara a ɗakinku, a ɗakinku ɗin ma ya faɗo akan ka, don haka ni baxan mayar mata da kuɗinta ba!!!!!!!!! Gaba ɗaya hankalin aunty babba ya tashi don alamu sun nuna cewa Hafsat fa kamar bata cikin hayyacin ta, cikin ruɗi tace "Hafsat anya kina cikin Hayyacinki kuwa"? Shu'umin murmushi hafsat tasaki sannan tace "Kwarai kuwa! nice dae ƴarki Hafsat ɗiyar general ishaq, jika ga Abban sojoji" Jinjina kai aunty babba tayi tabbas an samu matsala, domin kuwa tasan Hafsat bazata ta6a fasa abunda tayi niya ba, Huci kawai take yi tana jinjina kanta a ƙarshe ta fuce daga ɗakin, Duk wannan suratan da Hafsat su kayi da aunty babba a kunnan Hosana wadda ke la6e a ƙopan ɗakin, jin Takon tafiyar Aunty babba yasa ta gudu izuwa cikin store ɗin da suke, "Ina kika je hosana bakya jin magana ko? salon sai sun ganki? Mun samu yau sun ƙyale mu basuyi mana komai ba, Jahad ce ke wannan maganar wadda ke atsaye tana kallon hosana, Murya na rawa hosana tace "Jahad naji abunda su Hafsat ke cewa ita da Momynta," "Me suke cewa ne"? Ta tambaya tare da matsawa kusa da Hosanar don taji dakyau, Hosana ta kora mata bayani tun daga farko har ƙarshe, Jahad ta jinjina kai tare da cewa "Ashe buri yayi kama da mutun, shiyasa ta tsane mu kenan saboda tana tunanin cewa Omar zai iya son ɗaya daga cikinmu, ran nan tace mun batason mune saboda mun shiga tsakaninta da abun harin ta, Yanzu nagane inda ta dosa, To amma wacece matar da hafsat ta haɗu da ita yau? Wadda ke son A zubar mata damu!? "Ni inaji araina jahad so suke su rabamu da ƴa'ƴa Omar kawai," hosana ce tayi maganar ido cike tab da kwalla don bata son duk wani abu yanzu dazai rabasu da Omar, "Insha Allah burinsu bazai ta6a cika ba Hosana, baza su iya raba mu ba da yaya omar ɗinmu," tayi maganar tare da janyo hosana suka rungume junan su __________________________________________ Tuni sun kammala aikin su na dinner, har sun kammala jerawa a dining Kowa ya bama cikinsa an ware, yanzu gidan ya ragu ba laifi kasancewar tun week ɗin daya wuce aka tura mutun Huɗu Aiki, Irfan jabeer, khaleed da Fawan duk basa nan, yanzu wanda suka ragu Acikin gidan Haroon, twins, junaid, Sai Marshal Omar da Sgr duk da basu cika zama cikin gidan ba suma, always working saboda suna bada gudummuwa sosai shiyasa koda yaushe suna headquater ɗinsu don ana buƙatarsu sosai game da insecurity ɗin qasar tamu, kasancewarsu kwararrune a6angaren aikin soja dama sun kasance international Armies, kowace ƙasa aduniya suna bada gudummuwarsu wurin kame tantirai sune maganin ƴan Iska, shiyasa sunansu ya shahara a faɗin duniya duk inda suka je, ansansu girmamasu ake gani kamar kamar me (Tiger da Lion) Kenan ba wasa 😇😇😇 SEHRISH Shiga bedroom ɗinta tayi Wurin isha prayer, duk ta rame kamar ba Reeshi ba, alwala ta ɗaure a toilet, ta shimfiɗa sallaya, ta gabatar da salla, bayan ta kammala ta naɗe hijab da sallayar ta tura a wardrobe ɗinta, komai nata a slow take yinshi saboda rashin kwarin jikinta da fargabar da take fama dashi na Haroon, Haye wa tayi saman gadonta tare da janyo pillow ta rungume tunani kala kala a ranta, hawaye ne suka soma gangarowa daga idonta sbd tuna yadda haroon ke ta6a jikinta, hannu tasa tana share su, daga bisa ni tayi lamo tana tunanin duniya, Tana cikin wannan halin taji an kwankwasa ƙofa, shiru tayi bata Yi magana ba cike da tsoron waye ke mata knocking, ji tayi an sake buga ƙopar muryar na rawa tace "wanene"? Muryar junaid taji yana cewa "Sehrish ni ne," Ajiyar zuciya tasaki jiki na rawa ta sauko tare da karasawa wurin kopar ta buɗe, Gabanta ne yayi mugun faɗuwa ganin haroon hankali tashe tace "Kaineeee !!!!" a tsorace tayi maganar jikinta na rawa,. Fashewe da dariya haroon yayi tare da wuce ta yashi ga ciki yana cewa "ƴar shila ni ne, ae nasan bazaki buɗe ba shiyasa nayi maki muryar junaid don na lura kuna good time dashi,' juyowa tayi tana bin shi da kallo a razane,. "Me ya kawo ka"!? "Abunda yasa ba kawo ni, Yau nazo ne ayi ta taƙare, Haƙƙina nake son ki bani," Cikin shessheƙar kuka sehrish tace "Me kake nufi wai !!! Wani haƙƙi ka ke dashi akaina? Dan Allah kabarni nayi rayuwata cikin salama !! Ka rabu dani mana !! ta6e baki haroon yayi tare da cewa "Na amince zan rabu dake, amma bisa sharaɗi ɗaya"? Ya faɗi yana kallonta fuska a ɗaure, a lokacin tadawo tsaye front of side drawer ɗinta tana facing ɗinshi, Gabanta na faɗuwa tace "Menene shi"? Cikin sanyin murya tayi maganar Haroon yace "Your Virgin!! shine abunda nake so,and if u do so i wll be out of ur life" Fashewa da kuka sehrish tayi cikin tsananin jin ƙunci da raɗaɗi aranta, tuni zufa tagama wanko mata kamar wadda aka tsamo daga cikin ruwa, tsanar haroon take ji kamar kamar me, tarasa amsar da zata bashi sai faman kerma take, A tsawace haroon yace "Ke !!! Ki amsa mun kin amince ko baki amince ba"!? A Firgice tace "Na'amince" ita kanta batasan ta bashi amsar ba saboda tsoratar da tayi da tsawarsa, Wani irin shu'umin murmushi haroon yasaki, bin shi da kallo tayi ganin yasa hannu yana zare belt ɗin wandonsa, tuni ta runtse ido ganin gashin jikin shi, bakomai ya faɗo mata arai ba fa ce Sgr shine namijin da take so tafara kasancewa dashi arayuwarta bata buƙatar wani namiji in ba shi ba, shi take so ta mallakawa komai nata muddin ta mallake sa, Jiki na rawa ta zura hannunta ta baya, taci sa'ar damƙar fititalar Kwan dake gefen gadonta, kafin haroon ya ɗago ta daddage da iya ƙarfin ta na ƙarshe ta ɗago da fitilar dake hannunta ta kwaɗa masa a tsakiyar kai !!!!! Ji kake KWASSS !!! A razane haroon ya ɗago jin saukar fitilar kafin yayi wani yunƙuri tuni Sehrish tabi ta gefensa ta watsa da gudu sai cikin toilet ta datse ƙopa sosai, ta sulale daga jikin ƙopan zuƙunne tana kuka don tasan dole haroon ya ɗauki matakin abunda tayi masa, Ba ƙaramin buguwa haroon yayi ba, don wurin harya fashe Ae kuwa rai a tsananin 6ace yace "Ke don ubanki ni kika fasa ma kai"? Sehrish dake acikin toilet murya cike da kuka tace "Ba dai ubana ba sai don Uban Mai zagi !! Fasiƙi ɗan iska insha Allah bazaka ta6a cin nasara akaina ba, sai Allah ya nuna maka iyakarka, wulaƙantacce kawai ƙazami mai warin baki," Tuni idon haroon sunyi jawur kamar garwashin wuta, ransa yayi mugun 6aci bai ta6a tunanin yarinyar zata iya mayar masa da martani ba, amma sai gashi yau ta zage shi tass, "Bazan ƙyaleki ba, sai na wulaƙanta rayuwarki ba dai kina acikin gidan nan ba kuma zaki fito ba, zamu haɗu ne wlh," Ya faɗi tare da tunkarar hanyar fita yana mayar da belt ɗin wandonsa daya fara cirewa,.(ba'aci nasara😂) Sehrish batayi shiru da bakin ta ba taci gaba da cewa " Ta Allah bata ka ba wlh !! Mugu azzalumi mummuna kawai, da wasu idanuwan ka kamar na Mujiya ni ina kokwanton Cewa anya kai Jinin Abban sojoji ne !! Sbd duk ƴa'ƴansa ba Fasiƙi irinka," Jinjina kai haroon yayi kawai yana huci, ya tura ƙopar ɗakin ya fuce, Wani sabon kukan ta sake fashewa dashi, tana faɗin "wayyo Allah na nasan haroon baxai ƙyale ni ba, nashiga uku........' Jiki na rawa ta miƙe ta nufi wurin bathroom cabinet ɗinta, akwai wasu Chemicals dake ajiye cikin toilet ɗin masu illah ga jikin mutun tamkar poison suke, ta riga ta yankewa kanta shawarar kwara ta kashe kanta ta huta da fitinar haroon, Hannunta har kerma yake yi, wata ƙaramar roba ta ɗauko mai ɗauke da chemical ɗin, buɗe murfin tayi yayin da idonta ke zubar da hayawe, bakowa ya faɗo mata arai ba face Hosana Jahad, junaid, Aunty azmee uwa uba Burin ranta, yanzu shikenan duk zata rasa su? Zata mutu tabarsu? Runtse idonta tayi aranta tana faɗin "bani da wata manufa face wannan, kuyi haƙuri ku yafe mun bazan Iya cigaba da rayuwa a wannan duniyar ba mai cike da tashin hankali, ban ta6a cutar da kowa ba, amma gashi wani nason cutar da rayuwata ....................." Cikin sauri ta shiga zazzaga hodar abakinta A dai dai lokacin Motocin Sgr da marshal Omar suka shigo cikin gidan atare jiniyarsu ta karaɗe ko'ina har cikin kunnan Sehrish Zuciyarta ce taji tayi wani irin bugu, nan take kuma zuciyarta tace "Yanzu kin amince ki mutu baki cika burinki ba!? ke fa musulma ce ! Kin kuma son hukuncin wanda ya kashe kansa da gangan!! Runtse idonta tayi hawaye na zuba, fuskar sgr kawai take tunawa da fuskar su hosana da jahad, "Ina son sake sashi a idona," ta furta da wani irin sound, nan take tayi wurgi da robar chemical ɗin dake hannunta, cikin hanzari ta shiga amayar da wanda ke bakinta agaban basin, fanfo ta kunna tashiga kuskure bakinta da hanzari ta kora aman, sannan ta wanke face ɗinta ta fito, tana tafiya zuciyarta na ƙara bata ƙwarin guiwa da cewa "Saboda wani shashasha zaki halaka kan ki, share hawayenki sehrish kina da damar rayuwa, wani banza bai isa ya tarwatsa miki burinki ba," Gyara jikinta ta shiga yi saboda tana son zuwa kai mishi dinner ɗinshi shi da Omar don ta son da yunwa suka dawo, duk da tana tsoran kada suci karo da haroon a fitarta, dama riga da wando ne ajikinta, gashin bakinta kawai ta manna, ta gyara hular kanta da mayafin da take naɗe hular dashi, bayan ta kammala ta buɗe kopan cikin fargabar ta fuce,. Ko'ina haske fauuu gidan cikin sanɗa ta wuce kitchen taji sanyi aranta ganin babu kowa, Cikin hanzari ta shirya ma Omar nasa a tray, a palor ɗinsa takai masa babu kowa aciki alamar yana cikin bedroom ɗinsa, ajiye masa kawai tayi ta fuce, izuwa kitchen ta sake shirya wani a tray sannan ta wuce upstairs part ɗin BABBAN YAYA Haryanzu jikinta kerma yake, kuma bata fasa maganar shan poison ɗin nan ba, burinta ta sanya Sgr a idonta 4 the last time before tabar duniyar, Baiwar Allah Babu kowa a palor ɗinsa tsit kake ji sai ƙamshin dake tashi, shiga ciki tayi ta ajiye masa a saman table ɗinsa, Tsayawa tayi tana faman sauke ajiyar zuciya yayin da idonta ke cike taf da hawaye, kamar daga sama taji muryarsa ta cikin bedroom ɗinsa yana faɗin "who's There"? Runtse idonta tayi saboda jin sanyayyiyar muryarsa, daker ta dai daita natsuwarta tace "Tukur ne mai aiki," Voice ɗinsa tasake ji yace "Come In! i wanna see YOU Right now," zaro ido sehrish tayi jin abunda yace wato ta shigo ciki yana som ganinta 😳😳😳😳😳 Dake ta dai dai ta natsuwarta, ta tafi izuwa cikin bedroom ɗinsa kamar yarda ya umarta ta shiga da sallama"Assalamu alaikum" "Wa'alaikum salam" ya amsa mata, tsaye yake agaban mirror jikinsa sanye da sleeping dress riga da wando Milk colour masu ɗigon² baƙi ajikinsu ba ƙaramin kyau su kayi mishi ba, turarurruka yake ta fesa ma jikinsa, Sam tagaza janye idonta akan shi daker ta iya cewa "barka da dare" ya amsa mata da "Yawwa" sannan ta ƙara da cewa "Gani" Hannu yakai ya ɗauki kalbar turaren SHUMUKH ya feshe shi sannan ya mayar ya ɗauki wani turaren na Jar yana fesawa, mutun ne mai tsananin son ƙamshi shiyasa baya gajiya da bin jikinsa da turare, Shiru sehrish tayi zuciyarta na ɗar ɗar, kusan 15 minsa sannan Boss Man ɗin yace "Ni zan zo ne"? Ya tambaya yana jiran amsa, Cikin sauri sehrish ta ƙarasa hankali atashe ta tsaya daga bayansa jikinta na rawa, Cikin natsuwa yaso ma magana" Wacece ke"? Waro ido waje sehrish tayi jin abunda yace murya na rawa tace "Ni.....mai.....aiki...ne ...." a wani irin slow sgr ya juyo kai tsaye ya tunkare ta gadan gadan, a tsorace sehrish ke ja da baya tana kallonsa tuni zufa ta gama wanko mata sharkaf a jikinta, Sam idonsa basa a kanta ƙasa suke, har sai da suka ƙurewa bangon gaba ɗaya, yarfa hannu sehrish ta shiga yi a tsananin tsorace take karanto addu'o'in da duk suka zo mata abakinta, kuma abayyane take yi saboda tsaban ruɗi tuni ƴan hanjin cikinta sun motsa, gaba ɗaya jikinta rawa yake yi kamar wadda sanyi yakama, Hannunsa yasa ya daki wall ɗin data ke manne ajikinsa ya aza hannun anan jikin bangon ya dafe sannan yace "ƙarya ke bana so arayuwata, am gonna ask u some questions idan aka min ƙarya za'a fuskanci matsala," Ya faɗi yayin da idonsa ke a lumshe tamkar a datse suke ba don komai ba sai don gudun kada mai aikin ya Sume a ƙaro na biyu saboda launin ƙwayar idonsa dake razanar da shi, . Kallon shi kawai take yi zuciyarta na bugawa da ƙarfi, daker take haɗiye yawu ga wani fitsari daya matse ta tunda taji ya ambace ta da mace tasan cewa ya gano ta kenan, "maca ce ko Namiji"? ya tambaya yana jiran amsa, Shiru tayi tana tunanin amsar da zata bashi, muddin tamasa ƙarya wannan ba ƙaramin shaqa zata sha ba, Wannan shirun da tayi masa shiya fusata shi, buɗe Blue eyes ɗinsa yayi duka akanta , ta firgita sosai amma sam ta sanƙare ta gaza motsi da alama suman tsaye tayi Hannunsa yasa ya damƙi hular kan sehrish yayi wurgi da ita tare da mayafin duka, nan take sumar kanta tasoma warwarowa tana saukowa saman kafaɗarta, kyakkyawan sumar kanta mai matuƙan kyan gaske ga laushi, mayar da hannunsa yayi saman gashin bakin da take sawa ya cire shi shima, nan take ainihin kyakkwar fuskar reesh ta bayyana a matsayim mace 😊😉 sam fa bata motsi idonta sun kakkafe sun ƙame, kamar wata saƙago haka tayi, jinjina kai sgr yayi maganar Adams ta tabbata, yayi mamakin ganin yarinya ƙarama kamar wannan da ƙarfin halin Yin shigar Maza tazo gidan sojoji aiki, ko nawa aka biyata don tayi hakan? Ya tambaya aransa, sam shi baya tunanin ta haura 12years saboda ƙarantarta dayake gani agabansa Ko shouder ɗinsa tsayin sehrish bai kai ba, daga tsaye inda yake yana kallon tsakiyar kanta saboda ba ƙaramin tsayine dashi ba, kowa yazo gabansa kallon ƙarami yake masa, Janye hannunsa yayi daga jikin wall ɗin da sehrish take sannan yayi tattaki izuwa inda fridge ɗinsa yake, buɗewa yayi ya ɗauko bottle water mai sanyi sannan ya dawo inda take tsaye, ya buɗe murfin ya yayyafa mata, a wani irin firgice sehrish ta girgiza ta dawo in sense ɗinsa, sai faman zazzare kyawawan idanunta take, bin chest ɗinsa tayi da kallo izuwa face ɗinsa cikin tsoro, hannu tasa ta shafa sumar kanta gabanta ne ya faɗi jin wayam babu yar hularta, hankali tashe ta wurga idonta inda sgr yayi watsi dasu.........nan fa tashiga faɗin "innalallahi wa'inna ilaihirraji'un dan Allah kayi haƙuri.....nashiga ukuna........' tana kuka tana magana , gaba ɗaya yayi mata rumfa tamkar Zaki haka take ganin sa agabanta 😳😳😳 Idonsa na kumshe yana sauraronta left hands ɗinsa na riƙe da bottle water ɗin, yayin da ɗayan hannun kuma ya mayar dashi jikin bangon ya dafa, sehrish kuma na agabansa suna fuskantar juna, "haɗiye wannan kukan bana so" cikin hanzari sehrish ta dakatar da kukan tashiga taitayinta, bakomai take kallo ba fa ce damtsen hannunsa, tunani kawai take yarda zai kai mata naushi tabbas tasan sai dai Uwarta ta haifi wata (Hafsat bature ana magana) 😂 Cikin natsuwa yasoma magana__________________________________ Abt payment 300 ne, still muna free pages ne wanda suka shirya 08103884440 sumin magana 👍💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* *🔥The Father Of Soldiers🔥* ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ❤‍🔥💞💘? *Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad* ~💋BOSSLADY💋~ _Sabuwar Marubuciya, mai tafe da sabon salo💫_ *Abban Sojoji part 2* *EPISODE 2* *💞LAFAZI WRITTERS ASSOCIATION*💞 Cikin natsuwa ya soma magana "tambaya biyu kawai Wacece ke? Kuma waya turo ki"? Cikin rawar murya sehrish tace "Ni ba kowa bace ba, kuma babu wanda ya turon.......'. Interrupting ɗinta yayi da cewa "ki mun magana a hankali don bana fahimta sosai," Gyara muryarta tayi sannan taci gaba da cewa "Sunana Sehrish, kuma ni babu wanda ya turo ni, banzo da nufin na cutar da kowa ba, aiki kawai nake don nasamu kuɗi........' buga wall ɗin da yayi yasata dakatawa a tsorace "Nace wa ya turo ki!!? Hankali atashe tace "Allah shine shaidata, wlh ni babu wanda ya turoni, banzo da nufin na cutar da kowa ba, ƴan uwana ne Basu lafiya an kwantar dasu asibiti ana buƙatar kuɗin aiki shine na nemi aiki gidan wata hajiya...............sehrish bata 6oye masa komai ba ta faɗa masa tass dalilin zuwanta da dalilin yin shigarta na maza batayi masa ƙarya ba ko kaɗan, ta ƙarasa masa labarin tana faman zubda hawaye tsoranta wane hukunci zaiyi mata don tasan watan Cin Ubanta ya tsaya, shiru su kayi na wani lokaci, kafin daga bisa ni Babban yayan yaja da baya ya juya bedroom ɗinsa ya shige kafin daga bisa ni, ya fito hannunsa ɗauke da wayarsa wuri yasamu ya zauna saman sofa ɗin sannan yaba sehrish damar ta matso kusa, sai da tafara tattara hularta da mayafin da yayi watsi dasu, ta ruƙesu a hannunta sannan jiki asanyaye ta matsa inda yake kamar wadda tayiwa sarki ƙarya, jikinta sai faman kerma yake, yace "su nan su? da sunan state da sunan hospital da aka kwantar dasu? and the date!? Murya na rawa tace "Hosana Sayyad, da jahad sayyad an kwantar dasu a Fmc katsina........" duka ta faɗa masa hada date ɗin da aka kwantar dasu duka don bata manta ba, danna wayar yashiga yi kafin daga bisani ya danna calling, ta soma ringing, nan take aka ɗaga wayar suka soma magana, Duk sehrish na tsaye tana kallonsa yadda yake speaking anatse, Bakowa ya kira ba face Babban Likita, dama already sai da yafara tura masa message na sunan yaran da bayanan dayake son sani sannan yakira, kuma anci sa'a On duty yake,' Tabbas yayi mamakin ganin kiran Surgeon general rafayet, kuma yayi mamakin jin sunan yaran da yakeson aduba mishi files ɗinsu, tabbas yasan yaran, waɗanda Omar ya taimaka daga wurin Police, ranshi ne ya bashi cewa may be Omar yasanar mishi game dasu ne that's why yake neman Information akansu , without wasting time Babban likita ya binciko masa files ɗinsu Hosana Da jahad na rashin lafiyarsu duka bayanan ya masa snaping dinsa ya tura masa ta whatsapp ɗinsa, bayan sun kammala phone ɗin, Sgr ya shiga whatsapp ɗinsa ya duba, sai ga Files ɗin yaran na rashin lafiyarsu raɗau da sunansu ajiki Hosana Sayyad Da Jahad Sayyad, Ajiyar zuciya yasaki yanzu ya shaida maganar Yarinyar duba time yayi dare yayi ga wani bacci daya ke ji gashi ko dinner ɗinsa bai cin ba, Ga yarinyar nan dake tsaye duk a tsorace don yana ganin yadda yatsun ƙafarta ke kerma, gyaran murya yayi sannan yace "You're not guilty of anything, the mistake you made shine shiga na maza after knowing that it is forbidden in Islam for a girl to dress like a male,' yayi maganar yana danna wayar hannunsa... Murya na rawa Sehrish tace "bazan ƙara ba........' Jinjina kansa yayi kafin yace"As from now i don't wanna see u wearing this dress again! u can go" ya bata Umarni ta tafi Wayyo Allah sam sehrish ta gaza rufe bakin ta don mamaki, kama hanyar fita tayi tana waiwayansa da kansa ya shiga saving dinner ɗinsa yana ci, Tsantsar farin ciki ne ya cika sehrish sam ta rasa inda zata tsoma ranta, ae tana fita daga part ɗinsa ta buga Wani uban tsalle na murna fuskar nan kamar wacce akayiwa Albishir da gidan Aljanna, watsa wa tayi da gudu gudu sauri sauri tana tattaka Stairs ɗin tana saukowa down a babban falon dama ba kowa nan fa tashiga rawar murna tana zagaye sofas ɗin dake a falon kamar wata yar baby, Duk wannan abun da take yi akan idon Sgr domin kuwa ya biyo bayanta ashe yana daga can Upstairs yana kallonta, don bai cika yarda da mutane ba shiyasa yayi following back ɗinta don yaga reaction ɗin da zata yi bayan da ta fita daga part ɗinsa, abunda yayi tsammani ba shi ya gani ba, zura hannayansa yayi cikin aljhun wandon baccinsa yana kallon Ikon Allah, Sam sehrish bata son babban yaya yana kallonta ba, ita kaɗai tasan farin cikin da take ciki, ta jima tana mamakin yarda Sgr ya kasance mai matuƙar sauƙin kai har haka a tunaninta zai bata horo mai tsanani daga nan akore ta kuma daga gidan, Nace "*Sehrish ba ke kaɗai ba hatta Hafsat bature da sauran makaranta labarin rayuwarki sunyi tsammanin hakan tabbas Surgeon general Rafayet ya bamu mamaki, haƙiƙa shi ɗin na daban ne*"😍 Yanzu abunda ya rage wanda take yi ma fargaba shine sauran matasan gidan shin zasu amince a ranar da ta bayyana kanta a matsayin mace !? Uwa uba Abban su,kuma tuna wannan yasa jikinta yin sanyi, dakatawa tayi daga yin wasan da takeyi na zagaye gujerun babban falon, jiki a mace ta kama hanyar bedroom ɗinta, ranta ne ya bata cewa akwai mai kallonta, Cikin sauri ta juya ta kalli upstairs a time ɗin har sgr yabar wurin ya koma part ɗinsa Ganin wayam yasa ta sauke ajiyar zuciya,ba ɗakinta ta wuce ba ɗakin aunty azmee ta wuce don sam tagaza daina murna tafison ta sanar mata abunda yafaru yau ɗin nan da zafi zafinsa, Haryanzu hannunta na ruƙe da hularta da mayafin duka ta ƙanƙame su, tsayawa tayi a ƙopar ɗakin tana bubbugawa , Azmee dake zaune saman darduma tasha hijabi ajikinta ga qur'ani agabanta hannunta kuma na riƙe da Cazbaha sai faman gyangyaɗi take yi, jin bugun ƙopa yasata cewa "Wanene" sehrish dake tsaye a bakon ƙopan tace"Nice aunty azmee" Murmushi azmee tayi tare da cewa "Ashe bakiyi bacci ba," tayi maganar tare da tashi daga dardumar ta buɗe mata ƙopa, Shiga ciki sehrish tayi tana faman zabga murmushi, a ɗan ruɗe azmee ke kallonta bayan ta rufe ƙopan tace"Yau wata rana! Sehrish kece da Murmushi haka a fuskarki? Wane albishir ne akayi maki?Cos I forgot when last naga wannan annurin a face ɗinki" cikin mamaki azmee ke wannan maganar kafin ta mayar da idonta kan Hular sehrish dake ruƙe a hannunta ta kuma cewa "Ikon Allah yau kuma hularce da mayafin duka a hannu? Dariya kawai sehrish take yi daker ta tsagaita tace "Aunty azmeee abun mamaki! Abun farin ciki !" Cike da ɗoki azmee tace "menene shi? Nan sehrish ta shiga zayyana mata abunda ya faru tsakaninta da Babban yaya daga farko zuwa ƙarshe Baki washe azmee ta ɗaga hannunta sama tana cewa "Alhamdulillah ! Alhamdulillah godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata'ala naji daɗin wannan lamarin sehrish domin kuwa Babban yaya shine nafi ji dama, gashi kuma cikin sauƙi ya amince wayyo Allah murna bansan inda zan sa kaina ba don daɗi" cike da jin daɗi azmee ke magana fuskarta a washe Sehrish tace "Amma aunty azmee su fa sauran kina ganin zasu amince in suka sani"? Ni ina tsoran ta yarda zan fara fitowa a matsayin mace cikin gidan nan," tayi maganar murya asanyaye tana kallon azmee Ƙarasawa azmee tayi ta dafa kafaɗarta sannan tace "Sehrish matsalarki tazo ƙarshe! tun da har babban yayansu ya amince ba ki da sauran damuwa, Abbansu ne kawai zamu jira muji ta bakinsa, yanzu abunda nake so dake kije kawai ki kwanta kiyi bacci zuwa gobe zamu ga yadda badaƙalar zata kaya idan matasan gidan nan suka ga tukur mai aikinsu a matsayin Mace lallai akwai tashin hankali, " azmee tayi maganar da dariya a fuskarta, sehrish kuwa dafe saitin zuciyarta tayi tana zazzare ido tace "Allah sa su amince suma," "Insha Allah" azmee tabata amasa afterwards suke yi sallama, sehrish ta koma bedroom ɗinta cike da zullumi haye wa tayi saman gadonta, ta janyo pillow ta rungume tana sakin murmushi tunawa da haɗuwarsu ta yau da babban yaya, Allah kenan a daren nan Haroon ya ƙuntata mata, har tayi addu'ar sai Allah ya nuna masa Iyakarsa akanta, to yanzu ga Iyakar tasa nan muddin sauran suka amince da ita kuwa, taci alwashin sai ta Ci mutuncin Haroon 😡👊 A fili tasoma magana " gajan haƙuri kenan Irin na ɗan adam, yanzu da na kashe kaina da shikenan nayiwa kaina, ashe Allah yana dab da kawomin sauƙi arayuwata," ta faɗi tana faman murmushi wani irin nishaɗi take ji ayau , ta kuma cewa "Anya ma zan iya bacci kuwa? gashi ina fargabar mai zai faru gobe? kwara kawai nayi Bacci na goben tayi saurin yi, AYI TA, Ta ƘARE kawai🙅, In jalasa jalasa 😂 in Zahaba Zahaba shine kawai 😅😂😹😹😹 tana gama faɗan hakan bacci yayi awon gaba da ita, kai kana ganin yadda reesh ke bacci kasan tana cikin kwanciyar hankali, murmushi Hafsat Bature tayi tana kallonta wadda ke tsaye shigowarta kenan ta window tabiyo da suffar Farar Tantabara kasancewarta Aljanar sehrish, hannu tasa tajanyo bargo ta lullu6e sehrish dashi sannan ta 6ace 6aaat..............😇 ______________________________________ Kwance suke acikin store ɗin su biyu abunsu, kamar yadda Jahad ta saba yi musu dabara, na jera masu jarkoki su koma kamar single bed sai su kwanta suna facing ɗin junansu sam bacci yagaza ɗaukarsu zullumin su mai zai biyo ba? Wata alƙibla rayuwarsu zata fuskanta yanzu? "Jahad idan Aunty hafsat ta zubar damu ina kuma zamu dosa"? Hosana ta tambaya tana kallon jahad wadda ta zuba mata ido, Cikin sanyin murya tace "Nima kaina bansani ba hosana, ina tsoran hakan," ta faɗi zuciya a karye Hosana tace "Dama Allah ya ɗauke mu yakai mu duniyar sama ko? ko duniyar taurari inda ba mutane muyi rayuwarmu mu kaɗai tare da yaya Omar tunda kowa baison mu shi kaɗae ke son mu ko? Wannan maganar ta hosana tasa jahad fashe wa da dariya daga kwancen da suke ta rinƙa 6a66aka dariya kaman kamar me, Hosana ta ɗan 6ata fuska don ita bada wasa tayi maganar ba, Daker jahad ta jinkirta da dariyar tace "Sorry hosana dole nayi dariya mana, wa kika ta6a ganin an ɗauke daga nan an kaisa sama ? Shiru tayi tana zumbura baki, jahad taci gaba da cewa "sannan kince tare da yaya Omar kaɗai zamu tafi saboda yana son mu, Shin kin manta da Sehrish ne"? Ita kuma fa? akwai wanda yayi mana wahala ne kamarta? sehrish tana son mu fiye da kowa na duniyar nan, saboda mu tashiga duk wani hali da take ciki ayanzu duk da bansan yaya rayuwarta take ba...............wani irin kuka ne yaci ƙarfin jahad har takasa ƙarasa maganar da take yi, Nan take jikin hosana yayi mugun sanyi tunawa da Sehrish ƴar uwarsu mai tsananin son su da ƙaunarsu, tuni itama idonta sun cicciko da hawaye murya na rawa tace "Ya Allah hada sehrish za'a ɗauke mu akai mu duniyar Taurari.....' dakatawa da magana tayi ganin Jahad dake kuka ta fashe da dariya, wato tayi tazarce daga kukan da take Zuwa dariya ba don komai ba sai don jin abunda Hosana ke cewa, share hawayenta tashiga yi tana faɗin "Hosana wasan ya isa haka, muyi magana ta hankali, yanzu yaya za'ayi yaya Omar yasan halin da muke ciki kafin Hafsat da Momynta su sa azubar damu yakamata muyi tunanin hakan in ba haka ba zamu shiga wani mugun hannun ne ko mu ƙare rayuwarmu adaji..............' jinkirtawa tayi da maganar tana sauraron shawara daga wurin hosana, "To ya zamuyi mu sanar mishi jahad? Bayan kullum waccen matar mai kama da samudawa mai kumatun alkubus tana tsare mu da ido duk in yazo tana hanamu kwakkwaran motsi," Shiru jahad tayi tabbas dole su nemi mafita in ba haka ba, zasu fuskanci tashin hankali Can tayi wani dogon tunani tace "Hosana mai zai hana, mu samu paper da biro sai mu rubuta mishi, in yazo sai ki lalla6a kisan yarda zakiyi ki tura masa a aljihunsa? Ko da rungumesa ne sai kiyi kamar yarda kikayi a asibitin nan kin tuna"? Murmushi hosana tasaki anzo inda keyi mata ƙaiƙayi kallon jahad tayi tace "Shawara mai kyau, amma taya zamu rubuta mishi to? Bamu da paper ba biro jahad," Shiru jahad tayi kafin tace "Akwai !!! Na tuna acikin wannan ɗakin da Momyn hafsat takaimu acikin wannan ƴar lokar naga Memo da biro," Cike da farin ciki hosana tace "dama ƙopa a buɗe take, yau ta manta bata rufe mu ba, jahad ki lalla6a ki ɗauko ki rubuta masa," Miƙewa jahad tayi tana faɗin "Zan fita dan Allah hosana karki biyo ni, nasan halin ki, in kika ja asirin mu ya tonu kashin mu ya bushe mu duka," Murmushi hosana tasaki tana cewa "sai dai in baki daɗe ba, kinsan ina jin tsoro fa nikaɗae anan," "Karki damu yanzu zan dawo," "To shikenan," hosana ta bata amsa, Ficewa Jahad tayi cikin sanɗa take tafiya babu kowa wayam sai hasken daya gauraye ko'ina, Wuce wa ɗakin tayi a hankali ta tura ƙopa tashige cikin hanzari ta nufi drawer ta zaro gidan farko ajikinta, anan taga memo ɗin da biron data gani, Fiddo su tayi jiki na rawa ta aza memon asaman drawer ɗin dayake ƙaramace, daga zukunne jahad ta soma bude papers ɗin sannan ta aza biro ta soma rubutu kamar haka _ya Omar naji ma inaso na faɗa maka halin da muke ciki, wlh bamu jin daɗin zama agidan nan, saboda basu son mu, uban aiki suke samu har bugun mu suke yi, dan Allah ya omar in kaga wannan takardar ka taimaki rayuwarmu kamar yarda kayi niya ka tafi damu inda kake rayuwa_ Kamar daga sama Jahad taji ance "Sannu da Ƙoƙari"!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!! Jin wannan maganar a bayanta yasa jahad dakatawa da rubutun da take yi, hankali a matuƙar tashe idonta sun firfirto azare, jikinta ya soma wata irin kerma, Tuni Zufa ta soma gangarowa daga fuskarta da jikinta don bala'e hatta paper ɗin da take rubutun asamanta ta jiƙe sharkaf da gumin da take fitarwa 😳😳😳 *SHIN WACECE WANNAN*‼⁉❓❓? 🔥The Father Of Soldiers🔥* ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ❤‍🔥💞💘? *Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad* ~💋BOSSLADY💋~ *Abban Sojoji part 2* *EPISODE 3-4* Sam jahad ta gaza yin kwakkwaran motsi saboda ta riga ta gane muryar wacece....... Idasa shigowa tayi da wannan takun nata, jikinta na sanye da sleeping dress red colour masu zanen flowers ajikinsu, abunka ga fara ta fito 6au acikinsu, kanta ko mayafi babu ba kowa bace wannan face AUNTY BABBA, Lokacin da ta isa inda jahad take, hannu tasa ta fisge takardar da take rubutawa, ta ɗago da ita tana karanta wa, zaro ido tayi hankali tashe tace "Keeeeee! Don ubanki ni zaki tonawa asiri!? Wato Omar kike rubutawa wasiƙa don ki faɗa mashi abunda muke yi maku ! Wlh kin shiga uku, bazan ƙyale ki ba sai kin yabawa aya zaƙinta!!!! a masifance take magana ƙarshe tayi  Wurgi da takardar ƙasa sannan azafafe da wannan hannun nata ƙirar samudawa ta damƙo mayafin dake lullu6e akan Jahad nan take ya sul6e ƙasa hakan ya bata damar damƙar gashin kanta, wani irin zafi ne ya ziyarci jahad saboda ruƙon da aunty babba tayiwa gashin kanta,     Janyo gashin tayi ta ɗago jahad dashi, jikinta sai kerma yakeyi duk ta rurruƙe hannun aunty babba dake ruƙe da gashin kanta tana faɗin "Aunty dan Allah kiyi haƙuri bazan ƙara ba....' bata ƙarasa ba aunty babba takai mata naushi a bakinta, nan take jini ya soma zuba daga bakinta le6enta suka faffashe, saboda tsananin azaba da raɗaɗi yasa jahad fashewa da wani irin matsanancin kuka na tashin hankali,    Wurgi da ita aunty babba tayi jahad ta tafi jiki a mace ta zube ƙasa, tattakawa aunty babbba tayi izuwa inda take don bata gama dukan nata ba,    Tashi zaune jahad tayi tana jan jikinta da baya da baya tana faɗin "dan Allah kiyi haƙuri bazan ƙara ba.....nasan nayi kuskure....    "Ke ƙaramar ƴar iska ce ! bakisan koni wacece ba ! Har ni zakiyi wa iya shege acikin gidana ! Ni zaki tonawa asiri Wurin Omar? idan na so yanzu saina sa wuƙa na yanka ki, shashasha... ta ƙarasa maganar tare da sake damƙo gashin jahad tashiga yi mata azaba dashi, ta ja shi da ƙarfi tamkar zata tsige shi daga kanta, tuni idon jahad yayi jawur wasu irin jijiyoyi suka firfito mata a goshin ta, don rashin imani aunty babba sai ta naɗe gashin a wuyan jahad ta shaƙeta dashi gadan gadan zata kashe ta, murya ashaƙe jahad ke fidda sounds tana faɗin "Ahh...ah..ann...bazan..ƙa..ra..ba' sam aunty babba bata da niyar ƙyale ta sai ma ƙara shaƙeta da take yi    Kamar daga sama Hosana ta faɗo ɗakin saboda tajiyo ihun jahad da farko sai tayi tsammanin kunnanta ne Suke mata gixau,amma rashin kwanciyar hankali da jin bugawar zuciya yasa hosana gaza samun natsuwa ta fito don tazo taga wani hali jahad ke ciki ta rubuta wasiƙar,   Shine ta taras da wannan tashin hankali, ihu tasaki a haukace ta watsa da gudu inda aunty babba ta shaƙe jahad ajikin wardrobe,   "Kada ki kuskura ki ƙaraso in ba haka ba zan haɗa dake kema," aunty babba ce tayi ma hosana wannan maganar batare da ta janye hannunta daga wuyan jahad ba, cikin kuka hosana ke faɗin "ki sake ta...! Ki kyale ta....kada ki kashe mun ƴar uwata.....' amma sam aunty babba taƙiya,    Ganin jahad ta soma kakarin sheƙawa barzahu yasa hosana fita hayyacin ta, aikuwa ta daddage da iya ƙarfinta na ƙarshe tasamu damtsen hannun aunty babba ta Gartsa mata lafiyayyen Cizo da hakoranta 30 cufffff    A firgice aunty babba ta saki jahad tana yarfa hannun ta sai ga jini na ɗigowa, cikin hanxari tasa ɗayan hannunta ta zame hannun rigar jikinta don taga inda hosana ta cije ta, wurin yayi jawur ga sahun haƙoran hosana nan rerass a farar fatar hannunta dama gashi dumurmur na ƴan hutu,    Cike da jin raɗaɗi tace "Innalallahi !ni kika ciza har kika fasa mun fatar jiki na !! Ya salammmm !! Kin mutu wlh !! Kin shiga uku !! tayi maganar idonta jawur saboda taji raɗaɗin cizon hosana wurin har wani Zogin azaba yake yi mata,    Ja da baya hosana tashiga yi a tsorace ganin aunty babba na tunkaro ta Kamar Damusa, gashi jahad tunda aunty babba ta sake ta, ta sulale ta sume a ƙasa balle itama ta taimaki hosana,    Hanyar fita ta nufa da gudu zata fice, cikin rashin sa'a aunty babba tasanya ƙafarta ta taɗiyo ƙafar hosana, aikuwa ba ƙaramin buguwa hosana tayi ba, gaba ɗaya ta kife ƙasan tiles ɗin ɗakin, fuskarta ta dake sa, nan take hancinta ya fashe jini ya soma kwaranyowa, haka goshinta ma ya fashe da La66anta duk sun farfashe ihun azaba kawai hosana ke saki tana faɗin "wayyo Allah na ....! Nashiga uku...na mutu na lalace !!    Aunty babba tace "baki mutu ba, don ubanki, yanzu ne zaki mutun.....tayi maganar tare da kai hannunta kan Gashin hosana wanda ya barbaje ƙasa, kwakkwarar damƙa takai masa, ta ruƙo shi dakyau ta janyo hosana dashi har sai da hosana ta miƙe tsaye tana ihu kamar ranta zai fita, daddagewa aunty babba tayi da iya ƙarfinta na ƙarshe ta buga kan Hosana jikin bangon ɗakin wayyo Allah zoka ga yarda jini ya wanke bangon, Razanan nan Ihu hosana tasaki na azaba tamkar maƙoshinta zai ballo waje nan take ta sulale ƙasa a mace....... Ihun da hosana tayi na ƙarshe wanda ya karaɗe ko'ina harya sa Hafsat dake kwance ɗakinta saman gadonta farkawa a firgice, ta diro daga saman gadonta jiki na rawa ta fito ta tunkari inda sautin ke fita cikin hanxari ta faɗo ɗakin,   gabanta ne yayi wani irin bugu ganin Momynta a tsaye tana huci kamar wata zakanya, ga kuma twins ɗin da Omar ya kawo a baje ƙasa jina jina musamman hosana an zubda jini    Hankali tashe hafsat tace "Mommy me nake gani haka !! Me kika yi masu ne !! Kashe su Ki kayi da hannun ki !!!    tsawa aunty babba ta daka mata tare da cewa "Eh kashe su nayi,akwai magana ne ! babu ruwanki dani ki koma ɗakinki zai fi miki,"   Cikin rauni hafsat tace "mommy duk rashin imani na bazan iya aikata abunda kika aikata ma yaran nan ba, ashe baki da Imani ko misƙala zarratin ! Kisan kai da hannun ki........'   Bata idasa maganar ba saboda jin saukar wani irin zazzafan mari a kuncinta, tashin hankali da ba'a sama shi rana,     Saboda zafin marin da aunty babba tayi ma hafsat yasata dafe kumatun ta ido jawur take faɗin "Mommy yau ni kika mara da hannun ki"?     "Naje na mara ! duk kece sular da kika 6atamin raina harna aikata abunda na aikata yanzu!!"     shiru hafsat tayi yayin da idonta ke fitar da wasu irin siraran hawaye masu zafin gaske,   Jikin aunty babba ne yayi mugun sanyi ganin hawayen dake fita a idon hafsat ƴarta tilo,     Cikin tashin hankali tace "ba da son raina nayi hakan ba ! Hafsat ke kika 6atamun rai da 6acin ranki na kwanta, cikin daren nan na fito saboda zuciyata batamun daɗi kawai naga yarinyar nan jahad ta nufo ɗakin nan shine na biyota in ga mai zatayi ashe wasiƙa zata rubutama Omar akan abunda muke aikata musu, da nufin inyazo su bashi.......yanzu yaya zanyi hafsat....na kashe su ba'a hayyacina ba...In Omar yazo bansan me zan faɗa masa ba......" tayi maganar tana yarfa hannunta idonta cike tab da hawaye cikin tashin hankali,    Murya na rawa hafsat tace "Mommy kin ja mana masifa da bala'e duka, ni banji xafin marin da kikayi mun ba, domin wannan kaɗanne akan Marin da zamu kar6a ni dake a wurin Yaya Omar wlh bazai ƙyale mu ba !! Yadda kika kashe su ke ma haka zaisa ayi maki hukuncin kisa babu ruwana ......    Cikin shesshekar kuka aunty babba tace "Hafsat yanzu don na kashe waɗan nan tsintattun marasa galihu nima sai Omar yasa akashe ni?    A tsiwace hafsat tace "Eh.!! dama menene alaƙarki da Shi da zai tausaya miki? Kwarama Ni zan tsira ke kuwa Yayansa kawai kike aure !! Wlh mommy kin shiga uku gaki can an garƙame ki a cell ƙarshe a yanke maki hukuncin ɗaurin rai da rai har sau biyu saboda rai biyu kika kashe.......     Hannu aunty babba ta aza akanta tana faɗin "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un nashiga Uku Ni LAILA naja ma kaina mutuwa a lokacin da ban shirya ba,       Jiki a mace aunty babba ta zuƙunna inda hosana take kwance a mace tana faɗin "kee!!!kee!!! tashi !! Maza ki tashi don ubanki ! Wlh baxa ku jamin bala'i ba, hafsat ɗauko mun robar ruwa a fridge dan Allah in yayyafa musu ko sun tashi     tayi maganar tana kallon hafsat, fuce wa hafsat tayi da sauri sai gata ta dawo hannun ta ɗauke da bottle water ta miƙa mata, kar6a Aunty babba tayi jiki na rawa ta cizge murfin tashiga yayyafa ma hosana ruwan ajikinta,    Gabansu ne ya faɗi atare ganin hosana ko motsi batayi duk sanyin da ruwan yayi hakan na nufin ta mutu kenann !!!!!!   tuni fuskar aunty babba tayi jawur kamar wadda aka nannausa saboda tashin hankali A ruɗe tace "Hafsat mun shiga uku !! Mun lalace !! Wlh ta mutu wayyo Allah na ni laila......     Hafsat dake tsaye hankali atashe itama aruɗe tace "wlh Mommy laifinki ne, kece saurin fushin tsiya ga zafin zuciya gashi nan kin kashe su, To ni wlh babu ruwana aciki, dama ban da wata alaƙa dake haihuwata kawai kikayi.......    ɗagowa aunty babba tayi ta kalle ta ido jawur cikin disashewar murya tace "Hafsat ni kike ce ma baki da wata alaƙa dani, saboda ƙaddara da tsautsayi sun rutsa dani.....'    Cikin kuka hafsat tace "Ae gaskiya na faɗa mommy ! ina bacci. na kin katse mun shi da wannan tashin hankalin, Allah mommy ba abunda zai hana Omar yasa a garkame ki a cell , har na hango ki cikin kayan gidan yari Allah bazasu yi maki kyau ba yadda kike haka ɗin nan........' tayi maganar tana nuna aunty babba dake zuƙunne agaban hosana kamar buhun masara,   "Yanzu ya zamuyi ? Hafsat kar6i robar ruwan ki yayyafa ma ɗayar muga in ita zata tashi, wataƙil ita In tafarka sai in samu sassauci awurin yanke mun hukuncin......    Cikin sauri hafsat ta kar6i robar ruwan dake hannun aunty babba ta ƙarasa inda jahad take tashiga yayyafa mata shi a fuskarta, Wani irin dogon numfashi jahad taja kafin tace "La'ila ha illallah Muhammad rasulillah....     Ganin jahad tafarka yasa aunty babba tashi tsaye ta tunkare ta tana faɗin " Alhamdulillah saura ɗayar yaya zamuyi hafsat ? Kodai kawai mu binne gawarta a cikin garden ɗin gidan nan ne?    Wani irin kallo hafsat tayi mata tare da cewa "ashe mommy hankalin ɗiyar roba ke gare ki? mu binne gawa acikin gidan nan ? Idan fatalwarta ta tashi fitowa ke zata fara ziyarta Allah,    Hannu aunty babba ta aza akai tana faɗin "Ya salam duk ni naja ma kaina"    daker jahad ta buɗe idonta wanda suka kumbura sukayi jawur, ga le6anta sunyi sutum sutum inda aunty babba takai mata naushi,    Idonta bai sauka akan kowa ba sai kan hosana dake baje ƙasa jini duk ya wanke fuskarta......   Da ƙarfi ta furta "Hosanaaaa !!!!!!!!!,' tamkar bakinta zai tsage yunƙurawa tayi ta tashi a tsananin razane ta ƙarasa inda hosana ke kwance ta zube saman guiwowinta tana faɗin "hosana ki tashi ! mai ya faru dake ne? Wa yayi maki haka !! Innalallahi'wa'inna ilaihirraji'una .....ta ƙarasa maganar tare da kifa kanta jikin hosanar tajima bata ɗago ba sai daga baya ta ɗago da kan nata tana faɗin "Dan Allah ku kaita asibiti kada ta mutu !! Kada narasa ƴar uwata,"   Kallon juna su kayi sai yanzu suka mayi tunanin zuwa asibiti don sam basuyi tunanin hakan ba,    Jiki na rawa hafsat tace "mommy ki ɗauko ta, bari naje room ɗina naɗauko mukullin mota mu tafi,"    Aunty babba tace "Toh,ki tahomun da mayafi dan Allah"   fucewa hafsat tayi tana faɗin "kiyi sauri mommy,"    Cikin hanzari aunty babba ta ƙarasa jiki na rawa, ta cuccu6i hosana ta aza aka faɗarta ta fuce da ita daga ɗakin, itama jahad ta bisu abaya     Fitowa hafsat tayi itama a lokacin har aunty babba ta buɗe back seat na motar ta kwantar da Hosana aciki itama jahad tashiga ciki sannan ta rufe,    Su kuma suka shiga front seat hafsat na a mazaunin driver ita kuma tana a gefenta,    Da gudu hafsat ta tada motar taja ta a tsiyace suka nufi hanyar fita daga gate ɗin gidan    Nan take sojojin dake gadin gidan suka tunkaro su don jin ba'asi   Aikuwa a masifance aunty babbba ta ɗaga murya tana cewa "Nice nan zan fita kar in ga wani shege ya tare mun ƙopa Wlh in bi takansa....'   Jin muryarta yasa su kayi baya baya suka bata hanya ta wuce.......... da gudu suka miƙi titi sai asibiti, kuma duk da haka sai da sojojin nan suka biyo su abaya saboda aikinsu ne basu tsaro musamman acikin daren nan, Suna isa asibitin gudu gudu sauri sauri Aunty babba ta ɗauki hosana suka shiga ciki,da hanzari reception nurses suka karbe ta aka shiga da ita ciki, anci sa'a an samu likitan dake a bakin aiki, cikin gaggawa suka shiga duba hosana,   Su kuwa su aunty babba da hafsat suna atsaye sai faman zagaye suke kowa cike da zullumin abunda zai biyo baya in yarinyar ta mutu, jahad kuwa tana abakin ɗakin da aka kwantar da hosana ta kwantar da kanta jikin door ɗin idonta na tsiyayar da hawaye masu ɗumi,😭 Gaba ɗayansu babu wanda ya samu bacci adaren nan saboda da tashin hankali,    (Na zubda hawaye saboda halin da su Hosana da jahad suke ciki Ya Allah ka kawo masu ɗauki) 😭 ______________________________________ Ana cikin kiran sallar asuba Sehrish tafarka a hargitse tana faman dafe saitin zuciyarta dake yi mata wani irin raɗaɗi, sai faman ambaton sunan Allah take yi, tabbas ranta na bata cewa wani mummunan abu ya faru dasu Jahad, cikin hanzari ta sauko daga saman gadon tana faman zagaye ɗakim kafin daga bisani ta shiga cikin toilet ta ɗauro alwala,   Fitowa tayi ta nufi wardrobe ɗinta, hijab ta ɗauko da darduma ta shimfiɗa, ta shiga jera sallah, bayan ta kammala ta zauna tare da ɗaga hannayenta sama tana addu'o'i akan su hosana da jahad da sauran al'ummar musulmai, ta jima tana addu'ar kafin ta koma saman gadon nata ta kwanta tana fuskantar sama abubuwa iri iri na zuwa mata aranta daga bisani bacci ya kwashe ta, bata sake farkawa ba sai ƙarfe 10 na safe, Firgit ta farka har time ɗin shiga kitchen ya wuce,   Zumbur ta miƙe shaf shaf ta shirya cikin shigarta ta maza da ta saba, saboda zullumi bazai barta ta fita a matsayin mace ba, a hankali ta tura ƙopa ta fuce izuwa kitchen,   Bin ta da kallo azmee tayi wadda ke gyara kitchen don harta kammala breakfast ɗin already tun ɗazu,   Da mamaki tace"Sehrish ya akai naganki kuma da shigar maza?    Shiga ciki tayi tana cewa "Aunty azmee ni tsoro nake ji Allah,"    "Wani irin tsoro kuma,ba wani tsoro abunda nake so dake bayan mun kammala jera abinci, sai ki koma ɗaki ki cire wannan gashin bakin ki sauko da gashin kanki zan kira ki, sai ki fito a matsayin mace"  Shiru tayi tana kallon yatsun hannun ta kafin tace "shikenan Allah yasa komai ya tafi adai dai, Murmushi azmee tasaki tare da jinjina kai tace"Insha Allah yanzu bari na fara jera miki warmers ɗin kina kaiwa dining,"   Ta amsa mata da "toh", tana jin ɗar axuciyarta   Cikin ƙanƙanin lokaci suka kammala jerawa, Ayaan da Jahan ne suka fara fitowa sanye cikin kakinsu gwanin kyau, Suka samu wuri suka zauna kusa da Juna, azmee ta soma saving ɗinsu, time ɗin sehrish ta shige bedroom ɗinta don ta kimtsa kamar yadda su kayi da azmee zata fito a matsayin mace, Bayansu sai kanal yusif ya fito shima sanye da Jallabiya launin ruwan toka, wuri yasamu yazauna yana gaishe da aunty azmee, da fara'a take amsa musu, cikin girmamawa su twins suka gaishe shi shima ya amsa musu daga bisa ni kowa ya mayar da hankali kan breakfast ɗinsa, Sehrish na cikin ɗaki cike da zullumin yarda za'ae ta fito a matsayin mace, tana a jikin ƙopar ɗakinta tana ruƙe da handle ɗin kopar cike da fargaba, Gyaran murya azmee tayi ta ɗan ɗaga murya tare da kwaɗawa sehrish kira da sunanta tace "Sehrish ki fito mana," Jin sunan da azmee ta ambata yasa su kallonta da mamaki, sake maimaitawa tayi "Sehrish ki fito nace," Kallon juna Ayaan da jahan su kayi sannan suka kalle ta atare suka haɗa baki wurin cewa "Wanene Sehrish kuma? Kanal yusif shima cike da mamaki yake kallon azmee jin sai faman kwala kira take yi, zuba ido su kayi don suga wanene wannan sehrish ɗin da Azmee ke faman kira, shin baƙo su kayi ne a gidan nasu ko kuwa? buɗe ƙopa sehrish tayi gabanta na faɗuwa ta tunkaro hanyar dining area ɗin, jikinta na kerma a tsorace take tafiya, gaba ɗayansu suka ɗago suna kallon ta tun kafin ta idasa bayyana a area ɗin da suke, bin ƙafafunta su kayi da kallo waɗanda ke sanye da ƴan silifas ɗinta na gado, sai faman kerma yatsun ƙafarta suke yi, Time ɗin da sehrish ta idasa fitowa a raxane jahan ya miƙe tsaye, ayaan kuwa baisan lokacin da ya saki cokalin dake hannunsa ba ya faɗa cikin plate ɗin dake agabansa, kanal yusif kuwa kallon abun yake kamar a mafarki, Bin ta suke da kallo cikin mamaki, kamar a mafarki suke kallon lamarin, ƙarasowa tayi ido a zazzare jiki na kerma, riga da wandon nan ne ajikinta , ta cire gashin bakinta, ta kuma zuba da doguwar sumar kanta har gab da waist ɗinta, ta fito asalin macen ta Tsaleliyar budurwa ƴar matashiyya, A rude jahan yace "Azmee who's she ? daga ina ta faɗo cikin gidan nan? Da iznin wa!? Ayaan kuwa cewa yayi "Ku kuke ganin mu bamu muke ganin ku ba ! Wannan Hurool ainin fa? daga aljanna ta gudo? Kanal yusif sam yagaza magana bayani kawai yake jira daga wurin azmee, ita kanta azmee ta ɗan razana da reaction ɗin da suka bayar, Sehrish kuwa a gefen azmee ta tsaya tana faman zare ido, "Azmeee Explain !!!!' jahan ya faɗi azafafe harda dakar table ɗin gabansa da tafin hannunsa, Murya na rawa azmee tace " Kuyi haƙuri dan Allah...Am wannan da kuke gani ba kowa bane face Tukur mai aikin ku, nasan zakuyi mamakin hakan...... Dakatawa tayi ganin yarda Ayaan da kanal yusif suka miƙe atare, cike da ruɗu Kanal yusif yace "What ! Wai wane tukur ɗin ake magana ! Ba dai wannan yaron mai aikin namu ba, kina nufin dama mace ce ba namiji ba ....? Ya tambaya hankali atashe , Daga sehrish har azmee sun tsorata, Hannu jahan yasa yasake bugun table ɗin abincinsu yace "Impossible bazai ta6a yiyuwa ba ! muddin kuwa hakan ta kasance dole yarinyar nan ta fuskanci hukunci mai tsanani kuma tabar gidan nan ayau ɗin nan, Fashewa da kuka sehrish tayi saboda tsorata da maganar Jahan gashi idonsa na akanta ya zare su, "Dan Allah ku kwantar da hankalin ku, laifi ne nasan ta aikata amma kuyi mata afwa, sam bata da niyar cutar da kowa.....' dakatar da ita Ayaan yayi da cewa "Ba wannan zancen ! Saboda ƙarfin hali irin na Yarinyar nan, tayo shigar maxa ta saje acikin mu tana mana aiki, babu sirrin mu da bata sani ba, babu irin firar da bama yi agabanta, har yawo muke yi da towel a ƙugunmu, muyi yawo da gajerun wanduna duk idonta na akai, kaf ta haddace ashe kallon mu kawai take yi," bil'haƙki ayaan yake kora bani, gaba ɗayansu ba komai suke ji mawa ba face yadda sehrish ta saje A cikinsu matsayin namiji na tsawon lokaci tana masu aiki, duk a tsammaninsu namiji ne ashe maca ce, tagama sanin sirrinsu saboda babu irin firar da basa yi agaban ta, sannan babu irin shigar da basa yi suna yawo duk a idonta, Hannu Jahan yasa yana ƙoƙarin zare belt ɗin wandonsa da nufin ya jibgi sehrish saboda yafi kowa fusata, gashi dama su Mace bata agabansu balle suga kyanta ko wani abu haka don su tausaya mata, A tsorace sehrish ta ƙanƙame kanta ta 6oye abayan aunty azmee tana faɗin "Nashiga uku ! Dan Allah aunty azmee ki basu haƙuri, kada su buge ni...zan tafi nabar musu gidan, ture kujerar gabansa yayi gadan gadan ya tunkari sehrish zai jibge ta, Kamar daga sama suka ji Muryar Abban su yace "Kada ka kuskura ka ta6a ta!' Atare suka ɗago suna kallonsa kowannan su na huci, Ruƙe yake da hannun junaid cikin nasa, yana sanye da jallabiya junaid kuma na sanye cikin riga fara da wando baki, ya tsorata da ganin halin da sehrish ke ciki gashi kuma yayi mamakin ganin ta ta bayyana kanta a matsayin mace, ga kuma jahan tsaye ruƙe da belt wato zai jibge ta, Idasa isowa sukayi inda suke tunkan abbansu yace wani abu Ayaan yace "Daddy dama wannan yaron tukur mai aikin gidan mu mace ne ba namiji baa !! murmushi Abbansu yasaki yana kallon su yadda duk suka zabura, Mayar da idonsa yayi kan Yarinyar dake 6oye abayan azmee yace "Ke zonan," "Sehrish ki fito Abbansu na kira," Azmee ce ke tunasar da ita, fitowa sehrish tayi jiki na kerma ta ƙarasa inda Abbansu yake tsayawa tayi at front of him murya na rawa take faɗin "dan Allah kuyi haƙuri ku yafe mun, nasan nayi laifi wlh ni banzo da niyar na cutar da kowa ba.....' tsawa Jahan ya daka mata da cewa "Rufe ma mutane baki kona zo nan na nakaɗa miki shegen duka," Abbansu yace "Ya isa haka Jahan, bana so kowa yasake magana," shiru su kayi gaba ɗayansu suna sauraron mai abban nasu zai ce, Shin ina haroon duk wannan abun dake faruwa yana a tsaye fitowarsa kenan, gaba ɗaya ransa ya gama jagulewa mamakinsa yarda akai yarinyar ta bayyana kanta A matsayin mace bayan bai idasa cimma burinsa ba, na tsoratar da ita, Amma ganin yadda su Jahan suka fusata yasa shi jin daɗi aransa burinsa karsu amince su tada 6alli sai anyi mata horo sannan a koreta shi kuma zaiyi amfani da wannan damar wurin ƙuntata mata, tsayawa yayi da murmushin mugunta a fuskarsa don yaga ya ƙarshen bada'ƙalar zata kaya, Daga shi sai gajeran wando fari ajikinsa tsaye ruƙe da ƙugu, ɗayan hannunsa na ruƙe da Brush da alama ma daga toilet ya fito, burinsa yaji mai Abban nasu zai ce, gyaran murya Abbansu yayi sannan ya soma cewa "Na riga da nasan komai game da yarinyar! Domin junaid ya jima da sanarmun komai agame da ita, duk abunda junaid ya nuna yana so aduniyar nan koma menene shi zan amince dashi, Junaid ya nuna cewar yana son Zaman yarinyar nan agidan nan, don Haka Na AMINCE masa,!" Cikin mamaki suke kallon abban nasu, Haroon kuwa tuni yayi wata irin raxana har Brush ɗin dake hannunsa ya faɗi ƙasa sbd jin abunda Abbansu yace, Murmushi kawai junaid ke saki, kallonta Abban su yayi tare da cewa "Ya Sunan Ki"? Sehrish dake tsaye agabansa idonta cike tab da kwalla duk ta tsorata murya na rawa tace "SEHRISH" Jinjina kai Abbansu yayi tare da sa hannun shi ya shafa gefen fuskar sehrish yace "Daga yau Ba sunanki Sehrish ba," cikin mamaki suke kallon Abban nasu, itama sehrish ɗin kallonsa take tana jira taji sunan daya canza mata, azmee kuwa Alhamdulillah kawai take faɗi aranta, "Kinsan menene sunan ki daga Yau"? abban nasu ya faɗi yana kallonta, Cikin sanyin murya Reesh tace "a'a". murmushi Abban nasu yayi sannan yace "daga Yau sunanki *SEHRISH SALAHUDDEEN HUSSEIN ABBAN SOJOJI*" 😇😇😇 Sakin baki su kayi suna kallon Abban nasu Duk wannan Abun dake faruwa akan idon SGR wanda ke saukowa down stairs jikinsa na sanye da t-shirt mai gajen hannu baƙa, sai dogon wando fari, sun bi shape ɗin jikinsa ya fito Handsome stylish ɗinsa, ya ɗaure sumar nan ta baya ba ƙaramin kyau yayi ba, a hankali yake tattaka steps ɗin cikin tafiyar nan tasa ta majiya ƙarfi, duk suka ɗago suna kallon shi................ __________________________________ 🔥The Father Of Soldiers🔥* ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ❤‍🔥💞💘? *Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad* ~💋BOSSLADY💋~ *💫LAFAZI WRITERS ASSOCIATION 💫* *Abban Sojoji part 2* *EPISODE 5-6* Ida sa iso wa inda suke sgr yayi idonsa yakai kan Jahan daya zare belt ruƙe a hannunsa, tunkan yayi magana jahan yayi hanxarin mayar da belt ɗinsa, mayar da idonsa yayi kan Abban nasu tare da cewa "Gm dad fatan an tashi lafiya," murmushi Abban su yasaki da cewa "Lafiya Lou son ina fata kaima haka," Sgr yace "Alhamdulillah," sannan ya samu wuri ya zauna saman ɗaya daga cikin dining chairs ɗin, kowa so ya ke yaji mai Babban yayan nasu zai ce, musamman haroon burinsa Sgr yace bai amince da zamanta ba, don yasan in dai yace hakan to Zaman sehrish ya ƙare a gidan, Ita kuwa sehrish hankalinta kwance saboda tasan yarda su kayi jiya dashi haka azmee ma, gyaran murya sgr yayi kafin yace "tsayuwar me kuke yi"? Ya tambaya yana kallon su jahan Ayaan da kanal yusif, koma wa su kayi kowa ya xauna junaid ma yasamu wuri ya zauna, sai Abban nasu dake tsaye sehrish na agabansa yaci gaba da cewa "daga yau kin zama ƙanwarsu kema ƴa' ce acikin gidan nan, duk wani abu da uba keyi ma ƴarsa nima zan miki shi, kuma duk wani abu da junaid zaiyi acikin gidan nan kema zaki iya yin shi, kuma duk wanda yayi yunƙurin 6ata miki acikinsu ki sanar mun zaki ga yarda zanyi dashi," Zuru su kayi suna sauraron Abban nasu, sehrish kuwa murmushi kawai take saki koba komai yau tasamu Uba wanda zatayi prouding dashi a faɗin duniya, ɗago idansa yayi ya kalli Babban yayan nasu, wanda azmee taci gaba da saving ɗinshi breakfst ya kira sunan shi "RAFAYET" amsa wa yayi da "Na'am Abba," batare da ya juyo ba ya kalle su, Abban yace "Ina fata kaji komai ga me da yarinyar nan ? bansan ko kana da abun cewa ba" ya tambaya yana kallonsa, kowa ya saurara don jin ta bakinsa, haroon Allah Allah yake akan Babban yaya karya amince da zamanta, Boss man ɗin sai da ya gama sipping Coffee ɗin dake hannunsa a natse sannan yace" Umarninka Shine abun bi" amsar da ya bayar kenan, wani irin farin cikine yaci ka Abban nasu saboda shi da yake tunanin zai ƙiya gashi ya amince da duk jawabinsa kai tsaye ma yace Umarninsa shine abun bi, wato duk abunda yace game da yarinyar ya amince, "Kufa kuna da Abin cewa"? Abban nasu ya tambaya yana kallom su, cikin sauri suka haɗa baki wurin cewa "Abba ae magana taƙare kawai tunda Babban yayan mu ya amince mu su wanene da baza mu amince ba"? Wannan maganar tasu tasa Azmee yin ƴar dariya ƙasa ƙasa, Jinjina kai Abban su yayi sannan yace "hakan yayi mun, sannan ko da gigin wasa ban amince wani ya cutar mun da ƴa ta ba," "An gama magana Abba" suka bashi amsa atare yace "Yawwa haka nake son ji, sannan ya mayar da idonsa kan Sehrish wadda ke faman sakin murmushi tayi zuru tana cizar akaifar hannunta da takai bakinta, ba kowa take tunani ba face Haroon yadda zata Zazzaga mashi rashin mutunci, dama taci alwashin hakan Muryar Abban su ce ta katse mata tunanin nata da cewa " daughter ki zauna kiyi breakfast tare da Abban ki da kuma ƴan uwanki," ɗan zaro ido sehrish tayi jin yace zata zauna taci abinci acikinsu cikin mamaki tace "Abba anan," tayi maganar tana nuna dining table ɗinsu, "Eh nan nake nufi" ya bata amsa sannan ya ruƙo hannunta gavan ta na faɗuwa suka samu wuri suka zauna tana gefen Junaid Abbansu kuma na gefenta sun sa ta tsakiya, Babban yayansu kuma Na a side ɗin Abban nasu, ta hannun dama yayin da suke facing Ayaan Jahaan da kanal yusif su da suke hannun haggunsu, "Azmee ke ma ki samu wuri ki zauna A cikin mu," abban su ya faɗi yana kallonta , da fara'a a fuskarta tace "ngde ssae Abba, amma ni nafison a barni a iya matsayi na, nafi jin daɗin kasancewata haka, dama damuwa ta Sehrish ce gashi kuma ta samu Ƴanci ka ƴanta ta, Allah ne kaɗai zai iya saka maka, haƙiƙa kai na musamman ne ka kasance ɗaya daga cikin mutanen da ake Alfahari dasu aduniya kuma ake alfahari da Ƴa'ƴansu kowa burinsa yayi koyi da kyawawan ɗabi'unka da halayanka Abba ba abunda zamu ce sai dai Allah yaci gaba da tsare mana kai, ya tsare zuri'arka, Ya kare ka daga sharrin mahassada da maƙiyan ka, Allah yaci gaba da ɗaukaka darajarka da ta ƴa'ƴanka a faɗin duniya, kamar yadda kake faranta ma wasu Kaima Allah ya faranta maka aranar gobe ƙiyama yasa Aljanna tazama makomarka................azmee bata tsaya ba haka taci gaba da yiwa Abbansu addu'oi' dasu kansu , gaba ɗaya sunji daɗin addu'o'inta kuma dukkansu suke amsa mata da Ameen ameen, daga bisa ni kowa ya mayar da hankalinsa ga abincin dake agabansa zanso kuka sehrish duk ta gaza samun natsuwa ba wai don bata jin daɗin kasancewarta atare dasu ba, sai don tsoran su ayaan da jahan da take yi, saboda wani irin kallo da suke mata Sam tagaza gane kallon menene wannan, dama fa su ƴa'ƴan Alexandra wuyar sha'ani ke gare su kamar uwarsu haka suke basu cika yarda da mutane ba ko kuma sake musu, junaid ne kawai mai sauƙin kai saboda kaf halayansa shigen na Abbansu ne, shin wai ina haroon ? Ae tuni ya koma cikin bedroom ɗinsa cikin tsananin ƙunci ransa yayi mugun 6aci sai faman yawo yake a ɗakinsa cike da jin baƙin ciki aransa sai faman huci yake bakowa yafi bashi haushi ba face Abbansu da Babban yayansu saboda sune suka nuna Amincewarsu da ita, a can ƙasan zuciyarshi kuma bakowa yafi ƙuntata masa ba fa ce*JUNAID* Saboda shine silar komai daya fara sanar da Abbansu akan maganar yarinyar, dama junaid ya jima yana ci masa tuwo a ƙwarya don ya lura Yaron Abbansu yafi Son shi fiye da kowa tunda har bai iya 6oye son da yake mashi agaban kowa, Kuma ya Lura cewa Babban yayansu ya mutu akansa hakan na nufin shima Yafi Son*JUNAID* bama su kaɗai ba kowa na gidan in kana so kaga fusatar shi to ka ta6a junaid nan xaka ga tashin hankali, shiru yayi a lokacin ya koma gaban mirror ɗinsa yana kallon fuskar shi ta cikin madubi, a fili yace "saboda*Junaid* Abba da Babban yaya suka mare Ni, a gaban ƙanne na, mutun Uku da suka kasance maƙiya na acikin gidan nan muddin inaso In ƙuntata musu dole saina Cutar da *JUNAID* 😳 ya faɗi tare da sakin wani irin shu'umin murmushi yace "Haroon kenan Mai Fuska biyu ! Wasu suna mun kallon shashasha ɗan giya yayin da ni kuma nake masu kallon garori wannan Alwashi ne na ɗaukarwa kaina saina Tarwatsa farin cikin gidan nan kuma ba da kowa zanyi amfani ba fa ce *JUNAID* 👌💔 "na'am " ya amsa yana Satar kallom sehrish da ta kira sunan shi ta wutsiyar idon shi, "nifa tsoro nake ji junaid nagaza cin abincin dake gaba ba," murmushi junaid yasa ki tare da cewa "CALM DOWN your mind reesh, ke fa ynx ƴar gida ce, ki saki jikinki ki ci Abincin ki a natse," murmushi tasaki yayin da ta sa hannu cikin plate ɗin dake gabanta mai ɗauke da fried chicken taci gaba da ci, ta6e baki Jahaan yayi yana kallonta aransa yace " ƴar shisshigi da kutsu bansan daga ina aka samo wannan yarinyar ba yanzu haka bata Wuce Zariyya dama gata nan kamar Zararrriya sai faman zare ido take,' ya yi maganar yana Hura hanci kamar wanda akayiwa dole yana Cusa bugger abakinsa, Ayaan kuwa cewa yake yi aransa "ƙarfin hali irin na Ifritanyar nan kalli yadda ta wani shige tsakanin Abban mu da junaid tana cin abinci ita ga isasshiya mai walkin sa, ala dole ga ƙanwar Sojoji zaki gane kurenki ! Jibi kunnuwanta don Allah kamar na Zomo falo falo sai faman ƴan ƙefce ƙefcen ido take kamar wadda aka aza A saman kujerar lantarki......,😂 Har cikim ranta sehrish duk ta tsargu da su Twins kamar tasan abunda suke cewa aransu, Azmee ce keyi mata alamar ta kwantar da hankalinta don itama ta lura da abunda su twins ke mata, wani irin Kallon hadarin Kaji 😾😼 Tuni sgr ya bar dining ɗin dama breakfast ɗinsa shaf shaf yake yinsa gyaran murya Abbansu yayi ya kalli azmee yana cewa "idan mun kammala ku shirya ke da sehrish da Junaid saboda yi wa daughter siyayyar kayan sawa da abubuwan amfani na mata, hada ma Saloon da gyaran jiki duka komai nake so ayi mata,' Atare Jahan da Ayaan suka ɗago suna kallon Abban nasu, shima kanal yusif abun ya basa mamaki, Sehrish kuwa murmushi kawai take saki haka Junaid daɗi kamar ya rufe sa, Azmeee tace "To Abba Insha Allah komai za'ayi mata," "Ke ma hada ke, azmee siyayyar duk zakuyi," cike da farin ciki azmee tace "Mun gode sosai Abba Allah yasa ka da alkairi," mayar da idonsa Abban nasu yayi kansu Ayaan da jahan da kanal yusif yace "Bafa ni zan biya kuɗin siyayyar ƙanwarta ku ba, wannan nauyin ku ne, don haka kowa ya tattaro ya bada gudummuwa, babu wasa a fuskar shi yayi maganar, shiru su kayi don baza suyi mashi musu ba, Abban nasu yaci gaba da cewa "Yusuf kai zaka biya kuɗin siyayyar kayan sawanta, Jahan kuma shi zai ɗauki nauyin kayan ado na mata da za'a siya mata, sannan Ayaan shi kuma zai ɗauki nauyin na gyaran jiki hada takalma da bags ɗin da za'a siya mata ina fata duk kunji," sam takaici ya hana twins yin magana bawai kuɗin bane damuwarsu ba sam basu da matsalar kuɗi saboda bada albashinsu suka dogara ba, Mahaifiyarsu duk ƙarshen wata tana tura masu makudan kuɗi dollars wannan ba tare da sanin Abbansu ba ko Babban yayansu ba, haushin su yarinyar da aka ƙaƙaba musu wadda basu san daga ina aka tsinto ta ba, gashi kuma har ana ɗaura musu responsibilities ɗinta, "Naji kunyi shiru"? Abbansu ya tambaya yana kallo su, Kanal yusif yace "Atm ɗin yana a cikin side drawer ɗina, junaid yaje ya ɗauko in zasu tafi,"   Jinjina kai Abbansu yayi tare da cewa "Haka nake son ji ku fa"?   har suna haɗa baki wurin cewa "akwai kuɗi cash a ɗakin mu junaid yaje ya ɗibi yarda zai ishe su,in kuma Atm suke so shima yana anan saman mirror muka barshi...." suna magana suna yatsina fuska irin an musu dolen nan, Kanal yusif yace "A'a Abba ba sai sun bada nasu ba, kawai suyi using da Atm ɗina zasu ishe su har ma su rage," acewar kanal yusif,    Abban su yace "a'a ni nafison su sauke nauyin dake akansu na ƙanwarsu yakamata tun yanzu su son yadda zasu ɗauki ɗawainiyar mace kafin Allah yasa lokacin auransu yazo," . atare suka haɗa baki wurin cewa"Aure kuma Abba,"   "Eh mana" ya amsa musu, Kallon Ayaan jahan yayi tare da cewa "tashi mu tafi lokacin aiki yayi " miƙewa Ayaan yayi yana cirar tissue yace "Abba mu mun wuce,"   Murmushi Abbansu ya saki tare da cewa "adawo lafiya, aure dae ba fashi in lokacinsa yayi mutun ko bai so saina ɗaura masa in yaso ya haɗiyi zuciya ya mutu, zan zauna in ta zuba muku ido ne,"    fashewa da dariya junaid yayi bashi kadae bama hada su azmee da sehrish, kanal yusif dae murmushi kawai yayi, Na wani lokaci kowa yabar dining ɗin cikin zumuɗi sehrish ta wuce don ta shirya zasu tafi Shopping mall ɗoki har ba'ayi, shima junaid bedroom ɗinsa ya wuce don ya kimtsa yau zasu yi fita ta musamman da sehrish don ya tsara har ice cream sai sunje sha, haka itama azmee kimtsawar take yi don su fice, Haroon sam yagaza fitowa saboda kunyar haɗuwarsa da sehrish baisan martanin da zata yi mashi ba, dama jiya ta yarda masa magana a cikin toilet ina ga yau da tasamu ƴanci Allah kaɗai yasan Zagin da zaisha, ga yunwa yana ji amma sai faman zarya yake aransa yana faɗin "Ke ma bazan ƙyale ki ba Yarinya saina ƙasƙantar dake kuma bazan fasa abunda nayi niyya ba akan Ki,*YANZU WASAN YA FARA* 🙆 Fitowa azmee tayi jikinta na sanye da doguwar riga ta atampha ta kashe ɗaurin kallabi, sai ƙamshi take cikin hanzari ta wuce kitchen saboda tunawa da Marshal Omar wanda bai fito yin breakfast ba kuma ba'a kai masa ba, shaf shaf ta shirya masa a tray ta wuce part ɗinsa ta shiga da Sallama babu kowa a falonsa hakan na nufin koma bacci bai tashi ba, ajiye masa tayi asaman ƙayataccen table ɗinsa sannan ta fuce, Tana saukowa down stairs taci karo da haroon wanda ke tafiya cikin sanɗa zai shige kitchen wai don karya ci karo da Sehrish   girgiza kai azmee tayi aranta tace "Shi ko haroon ko lafiya yake faman tafiya cikin sanɗa haka kamar mara gaskiya, Ni wlh nama manta dashi ashe yana nan,'   Gyaran murya tayi tare da cewa "barka da fitowa mlm haroon," firgit yayi tare da juyowa ya kalle ta, ajiyar zuciya yasaki ganin azmee ce "Aunty azmee barka dae fatan an tashi lafiya, shine aka manta dani ina ta fama da yunwa yanzu da ban fito ba da shikenan sai dae yunwa ta kashe ni ko? Ya tambaya hada ruƙe qugu dama ransa a 6ace yake.........   Azmee tace "Kayi haƙuri wlh ni sam na manta ban lura da baka fito ba ba,"   ta6e baki yayi tare da cewa "koda yake dama ae ni ba'a sona na lura, bama kallon mutun ake mun ba acikin gidan nan kowa ya raina ni," Murmushi azmee tasaki tana kallonsa tace "kadaina cewa haka bana jin daɗi, koda kowa zai guje ka amma kasan ina tare da kai ko? Ka ta6a ganin inda UWA ta Guji ƊANTA?" tayi maganar ne don ta kwantar masa da hankali ganin ya ɗan fusata,   Sakin fuska haroon yayi sannan yace "Shikenan nadaina aunty azmee tunda baki so, yanzu dai a haɗa mun breakfast ɗina wlh yunwa nake ji har wani jiri nake gani,    Wuce sa azmee tayi tana cewa "a ina za'a kaima abincin anan ko a ɗakin ka," cikin sauri yace "Ki haɗamun kawai natafi da abuna ɗakina naci,Zai fiye mun kwanciyar hankali na"    Kitchen ɗin tashiga ta haɗa masa a tray sannan ta miƙa masa jikinsa na rawa ya kar6a ya wuce ɗakinsa,   Gefen gadonsa ya zuna hannunsa har kerma yake yi yana cusa abincin abakinsa, kamar daga sama yaga sehrish ta bayyana agabansa jikinta sanye da Kayan Sadaukai na Yaƙi, hannunta ruƙe da Zungureriyar wuƙa kanta na ɗauke da Kambun Sarauta, hankali atashe haroon ya fesar da donuts ɗin daya cunkusa abakinsa yana kallonta cike da tashin hankali, fashewa da dariya sehrish tayi tare da cewa "Kai Haroon! Ƙaryarka taƙare ! ka jima kana ƙuntatamun gashi yanzu Allah ya ɗaukakani, babu wata sauran barazana daga gare ka ta ƙare, nazo ne don na ɗauki fansa akan ka, yanzun nan zan fille kanka da wannan wuƙar ta hannu na,   Da ƙarfi sehrish ta ɗaga wuƙar zata fille ma haroon kai, aikuwa a firgice ya miƙe tsaye yana dafe saitin zuciyarshi a tsorace Lokaci guda Sehrish ta 6ace masa 6aaat hakan na nufin ba ita bace idonsa ne ke masa gizau,amma shi tabbas ita yagani kodai yarinyar Aljana ce ? Ya tambayi kansa,.wannan ba kowa bace face Hafsat Bature Aljanar sehrish 👿 Koma wa yayi ya zauna yana ci gaba da cin breakfast ɗinsa anatse, yayin da ransa ke saƙa mashi abubuwa da dama game da mummunan ƙudirinsa __________    💪    ______________ OMAR a hankali ya soma buɗe idanunsa bakinsa na ambaton addu'ar tashi daga bacci, yayin da zuciyarsa ke cike fal da son ganin Tagwayensa, tun da asuba daya sha maganin mura bacci mai nauyi yayi awon gaba dashi sai yanzu Allah yayi mashi ikon Farkawa daga bacci, a hankali yasa hannun sa ya janye blanket ɗin daya lullu6a dashi jikinsa na sanye da Night dress riga ce dai dai guiwa mara nauyi, fararen idanuwansa yafara kaiwa ya kalli agogon dake manne jikin bango ƙarfe 12 na safe yayi mamakin yadda lokaci ke gudu har haka, ko don yayi overdose na maganin muran daya sha ne yasa shi yin dogon bacci har haka,   Cikin sauri ya yunƙura ya miƙe direct toilet ya wuce , brush yafara yi yana tsaye agaban wash basin amma idonsa Fuskar Jahad da Hosana take hasko masa ta cikin mirro ɗin gabansa, shaf shaf yayo wanka ya fito jikinsa sanye da Bathrobe(rigar wanka) fara, wadda ta tsaya masa adai-dai guiwarsa, Marshal Omar kenan Son kowa ƙin wadda tarasa 😉   kai tsaye wuce wa yayi ya ɗauki wayarsa dake a saman gadonsa, sak irin ta sgr ce, Company ɗaya ce waya ce ta musamman domin Manyan jami'an sojoji irinsu kirar Companyn Iphone Ce, hamshaƙiyar waya haɗaɗɗiyar gaske wadda kuɗinta sun haura 30millions, ba kuɗinta bane abun mamaki ba a'a amfaninta shine abun dubawa, ƴar bala'en wayace bakowa ma zai iya Controlling ɗinta ba sai mamallakinta.   dannata ya soma yi Contact ɗinsa ya shiga kai tsaye numbar aunty BABBA ya laluba, ya buga mata Calling ta shiga ringing, burinsa tayi picking yasanar da ita cewa Zai shigo kaduna don ya duba su Hosana da Jahad, almost 3 times ba'a ɗaga kiran ba, domin kuwa wayar tabar ta agida, canza ra'ayi yayi ya dannawa Wayar Hafsat kira, Suna a asibitin nan zaune saman waiting seats, bacci duk ya kwashe su daga zaune don daren jiya ba wanda ya runtsa sai da sassafe wurin ƙarfe 10 suka samu baccin wahala shima saboda likita yasanar dasu cewa Yarinyar da ranta bata mutu ba, farkawa ne kawai batayi ba doguwar suma tayi, shine suka ɗan samu natsuwa suka baje suna bacci kamar wasu shanaye ga uwar yunwa na cinsu, kiran Omar ne yashigo da ƙarfin gaske a wayr hafsat dake acikin purse ɗinta data aza saman cinyarta, a firgice suka farka su duka wuri wuri da ido, cikin hanzari hafsat ta zura hannunta cikin purse ɗinta ta duba me kira sunan MARSHAL OMAR ne ya bayyana, dafe ƙirjin tayi hankali atashe tace "MUNSHI GA UKU ! MOMMY YA OMAR NE KE KIRA"😳    Mu haɗu ranar monday Insha Allah🙏 Kar amanta da paymemt wanda suka shirya sumin magana 08103884440, 300 ne VIP kuma 700 ga wanda basa ra'ayi a grp*💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* *🔥The Father Of Soldiers🔥* ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ❤‍🔥💞💘? *Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad* ~💋BOSSLADY💋~ *Abban Sojoji part 2* *EPISODE 7-8* *AYAAN* arab name ne for boys means God's Gift (kyautar Allah) ❤️ Waro ido waje aunty babba tayi tana faɗin "Shikenan komai ya ƙare, Hafsat kada ki ɗaga kiran nan, katse shi kwai , a rude take magana, Hafsat tace "Mommy how can i reject his calls ! Idan zuwa zai fa ? ba kwara na ɗaga naji mai zai ce ba, don mu son yadda za'ae mu dakatar dashi ba.....' ta ƙare maganar tare da ɗaga kiran ta ƙara a kunnanta tana Zabga sallama, Hankali atashe aunty babba ke cewa "Kisa wayar handsfree," cikin hanzari hafsat ta mayar da kiran handsfree don aunty babba tasamu damar jin abunda Marshal Omar ɗin zai ce,   Bayan ya amsa mata sallama yace "Zan Shigo kd yau insha Allah ki sanarwa Mommynki," yana faɗin hakan ya katse kiran since bfr hafsat tace wani abu, Cikin tashin hankali Hafsat ta janye wayar daga kunnanta,a wani slow tana kallon mommynta wadda itama kallon nata take yi ido azare,   Murya tamkar zatayi kuka tace "Mommy duk ke kika ja mana wannan bala'en da muke ciki, gashi nan daga ni har ke ba wanda ya runtsa daren jiya rabon mu da abinci ma tun jiyan, yanzu kuma gashi Ya Omar zaizo, Ina fata kin tanadi bayanin da zakiyi masa game da Twins ɗinsa da kika Faffasa ma fuska, ki ka canza musu kamanni, nayi imanin kema Ya omar bazai barki ba, sai ya Canza miki kamanni, don Allah naushi ɗaya zai ma kumatun nan naki Mommy sai an neme su an rasa a fuskarki,' Tuni ido ya raina fata, aunty babba tace "hafsat ki daina mun waɗan nan suratan naki ki barni inji dakaina, yakamata musan abun yi before Omar ya diro garin nan,' Zama su kayi zugum kowa zuciyarsa na bugawa daram daram, kowa da irin idea dake zuwa masa akai,   Jahad kuwa na a ɗakin da aka kwantar da hosana dama gado biyu ne aciki, itama doctor sai da ya duba ta, baccin wahala kawai take yi saboda allurar da dr yayi mata don tasamu bacci, duk inta farka sai ta ambaci sunan Hosana saboda itace aranta, so take tama fi ƙarfin allurar da dr yayi mata, don ƙoƙori take ta tashi da ƙarfin gaske don taje ma hosana wadda ke kwance magashiyyan rai hannun Allah 😥 ______________________________________ Bayan Omar ya kammala wayar fitowa yayi daga bedroom ɗinsa ya zauna a palor saman sofa yana yin breakfast ɗinsa anatse, wayarsa ce ta shiga ringing wadda ya ajiye agefensa, kai idonsa yayi ya duba Gwaggon katsina ce ke kiransa, murmushi yasaki don kusan kullum saita kira layinsa ta tambayesa ina Ƴa'ƴan Abusufyan ɗinta ya basu su gaisa, hannu yakai ya ɗauki wayar ya kara a kunnansa yana faɗin "Gwaggona kenan fatan kin tashi lafiya," Daga can 6angaren gwaggon katsina tace "Allah sarki Omar jiya ko isasshen bacci ban samu ba saboda tunanin ƴa'ƴan abusufyan ɗina, Jiya zuciyata tayi ta bugawa inaji kamar wani abu ya same su, dan Allah Omar karka bari a cutar dasu, Sai faman zuba take masa a waya sam taƙi bari yace wani abu har sai da ta gaji ta dakata da maganar sannan Omar yace "Ki kwantar da Hankalin ki goggo na, Ƴa'ƴan abusufyan ɗinki suna nan cikin ƙoshin lafiya,"   Ajiyar zuciya tasaki kafin tace "Suna tambayata ko? Suna atare da kai Omar? Ka basu dan Allah muyi waya mana,"   omar yace "Goggo kin manta suna a kaduna,ae gidan Yaya ishaq nakai su..." Kamar tana agabansa ta zabga salati tana cewa "La'ila ha illallah Mahammadar rasulillah Omar ! dama gidan Ishaq ka kaisu? Gidan wannan matar Shuwa mai ƙirar samudawa sam matar nan bata da Imani, zuciyarta irin ta kafuran farkon ce wlh, shikenan ni Allah kaɗae yasan wane hali ƴa'ƴan abusufyan ɗina suke ciki .  ......fashe masa da kuka goggon katsina tayi, Sam omar ya gaza gane ma goggon tasu, a tunaninsa haukan nata ne ya tashi, in ba haka ba ina matar ishaq keda aibu har haka, gashi kuma ta fashe mashi da kuka, cikin rarrashi yace "Calm down your mind Goggona, ƴa'ƴan abusufyan ɗinki suna cikin ƙoshin lafiya, yau ma nake shirin zuwa in dubo su,'    Cikin shessheƙar kuka tace "To shikenan amma dan Allah Omar nidai nafison su bar gidan matar nan, adawo mun dasu nan in basu kulawa kamar yadda na kula da mahaifinsu tun yana yaro," Murmushi Omar yasaki sannan yace "Insha Allah my aunt don't worry ur self abt them, suna Lou and insha Allah in naje zan basu waya ku gaisa kiji muryarsa may be u will be calm,"   "Shikenan Omar kada ka manta sai na jika,"    Ya amsa mata da cewa "Insha Allah" daga bisa ni su kayi sallama ya ajiye wayar yaci gaba da Cin breakfast ɗinsa, Acan ciki kuwa tuni Sehrish ta shirya kayan mazan ne ajikinta tunda su ke gare ta, hijab kawai tasanya ajikinta brown colour, azmee kuwa dama atampa ce ajikinta, Mayafi kawai ta lullu6a a jikinta ba ƙaramin kyau tayi ba, suna a babban falon sai ga junaid shima ya sauko, bin shi da kallo sehrish tayi jikinsa na sanye da suits baƙaƙe kamar ma'aikacin banki, yayi kyau sosai acikinsu abun sai wanda yagani, sai faman murmushi yake saki da white teeth ɗin nan nasa kamar gonar auduga, "Gsky junaid bazan iya jerawa dakai ba, Irin wannan kyan haka," sehrish ta faɗi tana nuna shi da hannu,   Ƴar dariya junaid yasaki kafin yace "duk kyan da zanyi bazan fi ki ba, ke fa maca ce, ni kishi ma nakeyi don nasan yanzu zaki fara ɗaukar wanka da zarar munyi Siyayyar nan,"   Murmushi sehrish tasaki ita kanta har ta hango ta cikin Gown ta gayu wow, azmee ma murmushin take saki, atare suka jera suka fuce, a cikin Motar Junaid haɗaɗɗiyar gaske, Shi ke driving yayin da sehrish ke a gefensa sai faman fira suke suna zuba, azmee na a back seat tana sauraron su  wani lokacin ma tana sa musu baki suna firar atare, suna ta tiƙar dariya abinsu gwanin burgewa, har suka isa katafaren shopping mall ɗin mai matuƙar girman gaske, sehrish taga haɗuwa yau dae karo na farko data fito kuma karo na farkon data fara ziyartar wuri irin wannan, atare suka fito suka shiga wurin, Mutane gasu nan kowa ya ɗau wanka ana ta siyayya ba kowa ya tsone mata ido ba face ƴan mata da samarin dake a wurin, duk sai taji kunya ta kamata ganin yarda Matasan matan dake a wurin siyayyar suka ɗau wanka iya wanka, ita kuwa kallo ɗaya za'ae mata ansan bazata wuce ƴar aiki ba,   6oyewa ta rinƙa yi abayan junaid da Azmeee, dariya kawai junaid keyi don ya gano dalilin dayasa sehrish jin kunya tana la6ewa abayansu, Sam ruwan ido ya hana sehrish Sa hannu ta ɗauki wani abu, junaid ne kawai da azmee ke faman ɗebar mata kayayyakin sawa iri iri masu kyan gaske na mata, yawanci arab gowns ne, turkish dress, night dress, Pakistan, english wears komai jidar sa kawai suke yi, laces ne atampa ce, materials, shadda,  Everything,   Duk tana tsaye tana kallonsu kowanne ya cike shopping basket dake hannunsa, sai dai in sun matsa nan tabisu, in kuma anzo abunda zata gwada tasanya su bata taje dressing room ɗin dake a wurin ta sanya, lokacin da suka zo wurin jerin panties da bra, hannu junaid yasa ya ɗauko brazier ya ɗago da ita yana cewa "Sehrish Ga wannan gwada mu gani," Sam bata lura ba tana ta faman kalle kalle, ganin hakan yasa shi ta6o hannunta yana nuna mata bra ɗin dake hannunsa yana cewa "Ina magana," aikuwa cikin jin kunya ta zaro ido tare da sa hannu ta rufe fuska tana faɗin "junaid dan Allah kadaina menene haka agaban mutane," fashewa da dariya yayi cikin mamaki yace "menene aciki? Kunya kuma ni bansan wannan zancen ba, ni dae ki amsa kawai kije ki gwada in tayi maki, in batayi ba acanza wata shine kawai,"   Hannunta na kerma ta karba tana ɗan kallon shi, har time ɗin dariyarsa yake Don shi mamaki ta bashi wai kunya,   Shiga dressing room ɗin tayi hada datso kopa, faskekan madubi ne aciki ya cike bangon, cikin hanzari ta tu6e hijab ɗinta da rigarta, ta shiga kiciniyar zira bra ɗin daker hada su sakin nishi,   Tsayawa tayi tana kallon kanta acikin mirrow ɗin wow, ta fito ɗas abunta dama tubarkallah masha Allah full ɗinsu suke, bra ɗin ta hau raɗau launin ta maroon colour ce, abunda sehrish take ma mamaki yarda akai junaid ya nemo bra dai-dai size ɗinta,duk jerin braziers ɗin dake a wurin, Cikin hanzari ta cire ta, ta mayar da rigarta da Hijab ɗinta, sannan ta fito, karaf suka ci karo dashi abakin ƙopan ɗakin,   a ɗan razane tace"junaid yaushe kazo nan," hannu yasa ya ɗan sosa sumar kansa yana cewa "Naji kin jima ne, shine nazo in ga ko kin gaza sawa ne, sai in taimaka miki.....," ganin yarda ta waro ido waje yasa shi dakatawa, muryarta har wani shaƙewa take yi wurin cewa "Junaid kana nufi brazier ɗin zaka taimaka mun nasa !!" ta tambaya a rikice,   Kai tsaye yace "eh mana,"  Jinjina kai sehrish tayi tare da wuce shi aranta tana mamakin hali irin na junaid shidae ba ruwansa komai normal ne a wurinsa,   tsayawa ta ɗanyi da tafiya ta ɗago ta kallesa Cike da tuhuma tace "Ya akai kasan size ɗina?   Da buɗar bakinsa sai cewa yayi "Ni dana ga Zahiri," Cikin sauri yasa hannu ya rufe bakinsa saboda su6ul da bakan da yayi, kamar zatayi kuka take kallonsa tana cewa "Junaid hakan na nufin ka ta6a gani na babu kaya ko"?   Girgiza kai yayi yana faɗin "No ba haka bane reeesh, baki fahimce ni bane, Ina nufin....," sam ya gaza samun amsar da zai bata gashi ta tsare shi da ido tana jiran amsar shi,    Muryar azmee ce ta katse su da cewa "tsayuwar me kuke yi ne? Ku hanzarta mana muyi mu kammala, yaushe har muka wuce wurin Saloon ɗin,"    cikin sauri junaid yace "Hakane aunty azmee muje kawai yanzu saura me ya rage," Ya tambaya yana kallonta yayi hakan ne don ya gusarma sehrish da tuhumarsa da take yi, cikin sauri suka wuce tabi bayansu itama, A ranar yini su kayi siyayya Kamar zasu kwashe kayan Mall ɗin,komai sai da suka siyar mata shoes & bags ne  Cosmetics komai wannan ba abunda suka bari,   Daga nan suka wuce wurin haɗaɗɗen Saloon ɗin duk acikin Mall ɗin yake, a lokacin junaid ya koma cikin mota yana jiran su, Already sun kammala purchasing ɗinsu an jera Manyan akwatinan guda uku biyu sunfi girma a boot aka zuba su, Wasu kayan kuma na acikin Manyan Shopping bags an zuba su har a cikin back seat na motar, Murmushi kawai junaid ke saki ya langwa6ar da kansa jikin seat ɗin motar, babban burinsa shine yaga yarda sehrish ɗinsa zata fito amatsayin mace a fili ya furta "Can't wait to seee" tabbas yanzu ne yasan yasamu abokiyar rayuwa wadda zasu kasance atare na har iya tsawon rayuwarsu, shigowar sehrish rayuwarsa ta canza mishi wasu abubuwan da dama da yake kewarsu,daga ciki harda kewar Mommynsu da tatafi tabarsa tun yana jinjiri wannan abun ya ta6a mishi zuciya sosai raɗaɗin na'a ransa yana jin cewa duk cikinsu shike bata so, hakan yasa shima baya sonta duk in ta kira waya tana so abashi tayi magana dashi baya kar6a, har ila yau junaid bai ta6a ganin Mommynsu ba ido da ido sai dae a hoto, babu yarda batayi ba akan akawo mata shi Sydney amma abbansu yace muddin tana son ganin shi ta tako tazo da kanta in ba haka ba ita dashi har abada, saboda batayi mashi adalci ba,' wannan kenan Ya jima yana tunane tunane shi kaɗae abunsa yana ta faman sakin murmushi, adai dai time ɗin Sehrish ta fito tare da Aunty azmee, Ƙaraso wa su kayi ta bude gaban motar ta shiga aunty azmee kuma ta shige baya sannan junaid ya tayar da motar yana faɗin "Har an kammala saloon ɗin"?   ya tambaya yana ɗan kallonta tace mashi "Eh,'.   "In munje gida za'a nuna min," ya faɗi da ɗan murmushi a fuskar shi, kai tsaye yabar bakin Mall ɗin yaja Motar kai tsaye ya nufi hanyar gida dasu duk da yaso su biya wurin shan ice cream amma shi kanshi a gajiye yake yafi buƙatar gidan don ya huta, Dama jikinsa sam ba irin na ƴan wahala bane,   Motarsu na shiga babban entry ɗin gidan adai-dai time ɗin kuma Motarsu Marshal Omar ta fuce daga gidan, Tasu na shigowa tashi na Fice wa, 🙅    Bayan yayi parking ɗin motar, wani sergeant ya ƙaraso ya kwashe akwatinan da junaid ya fito a boot ɗin motarsa, , Hada jakunku nan siyayyar na cikin back seat ɗin duk ya fiddo su, yayin da sojan ke kwashe su izuwa cikin gidan, Agajiye azmee da sehrish suka shiga cikin Babban falon bakowa alamar duk sun fita, azmee ta taimaka mata suka shigar da kayan ɗakin suka jibge su da nufin in sun huta an jera su a wardrobe ɗinta,   Cike da zumuɗi sehrish ta cire hijabinta don taga gyaran gyashin da akayi mata, Gaban mirror ta tsaya tana kallon gashinta, haɗaɗɗen gyaran gashi akayi mata mai haɗe da Twist,   Sai ta rinƙa jinta tamkar Queen saboda haɗuwa, ta jima tana kallon kanta a mirror kafin ta wuce toilet don yin wanka da alwala,   Shaf shaf ta fito jikinta ɗaure da toilet, wardrobe ta wuce ta samu riga da wandonta ta zura ajikinta sannan ta ɗauki hijab da dardumar salla ta shimfiɗa, ta kabbara sallah A natse ta Gabatar da sallar, Bayan ta kammala Jiki na rawa ta cire hijab ɗinta ta ninke tare da abun sallar asaman gado ta ajiye su,    Zama tayi tana bubbude kayayyakin da aka siya mata na cikin jakun kunan, sam bakinta yaƙi rufuwa, wani haɗaɗɗen takalmi ta ɗauko high heels ta ciro shi daga kwalinsa tana gwadawa a ƙafarta ita kanta ta razana daganin yarda ƙafarta ta fito ɗass acikinsa gashi ash colour jikinsa duk kyalli yake ga wasu igiyoyi na ɗaure sa ya haɗu, Shigowa azmee tayi tana faɗin "Kai!kai! Irin wannan zallar kyau haka gaskiya naji tsoran haɗuwar da zakiyi anan," .     Dariya sehrish tayi tana cewa "dama yanzu nake so in jera kayan acikin wardrobe bansan ma ta inda zan fara ba,"   Azmee tace "kada ki damu ae shiyasa nazo saboda nata Ya ki jera su Muyi mu gama, akwai sauran aiki agabanmu ga gyaran cikin gida ga kuma aikin Kitchen,'   Miƙewa sehrish tayi ta janyo akwati nan biyu da hannunta izuwa wurin wardrobe ɗinta ta jingi ne su,itama azmee ta janyo ɗayan akwatin tana cewa "Ki barmun jeran kawai, kije ki gyara cikin gidan kafin na kammala Canza ma ɗakin nan naki kamanni," . Murmushi sehrish tasaki tare da cewa "Toh aunty azmee," Sai da tafara ɗaukar mayafinta a cikin wardrobe ɗin sannan ta fuce tana murmushi, Babban falon tafara gyarawa duk da babu wani datti a tsaftacensa yake, shaf shaf tagama, cikin hanzari ta wuce upstairs don gyara ɗakin babban yayansu, tana cikin taka steps ɗin taji motsin mutun a down, juyowa tayi don taga kowane ne, Karaf idonta suka sauka akan na HAR0ON, sam yagaza ɗauke idonsa akanta kallon kallo suka shiga yiwa juna, duk a tunaninsa sehrish zata mayar masa da martani amma abun mamaki sai yaga tasakar mashi wani irin ƙayataccen murmurshin kashe zuciya tamkar ta soke shi da kibiya a ƙahon zuciyarshi haka yaji, don har saida yasa hannu ya tarbe saitin zuciyarshi, wani irin sabon kyau yaga yarinyar tayi mishi (nace ba kabari sai ta fara ɗaukar wanka tukunna munyi wannan maganar,"   Juyawa sehrish tayi cikin hanzari ta wuce apartment ɗin SGR, tabbas taso ta mayarwa Haroon martani amma daga baya tagane cewa ba buƙatar yin hakan, yanzu fa ita tamkar Princess take ƴa ɗaya tak ga Shugaban sojoji kuma ƙanwar sojoji, dole ne taja class muƙami iya muƙami, wannan kaɗae ya isa ya kashe haroon saboda ƙululun baƙin ciki,   Zuru haroon yayi sam yagaza motsi daker ya iya ɗaga ƙafarsa ya soma tafiya jiki a mace, Har time ɗin tafin hannunsa na a dafe da saitin zuciyarshi   Bin shi da kallo junaid yayi wanda fitowar shi kenan daga sashen abbansu, Ƙarasawa yayi cikin sauri ya nufi haroon yana faɗin "Yaya Haroon lafiya meke faruwa ne, naga ka dafe zuciyarka, ince dai ba wani abu ya same ka ba,'    ɗagowa da ido haroon yayi yana kallonsa yace "Jini Junaid," Jin wannan yasa junaid tallabo shoulders ɗinsa yana faɗin "Subhanallahi jini kuma a ina yaya haroon,"    da wannan muryar tasa ta ƴan giya yace "Yanzu duk jinin dake kwaranyowa daga zuciyata ba ka gani ba? Kibiyar da aka soka mun fa? Ko shima baka gani ba"? Ya faɗi a susuce yana kallon junaid, Baki asake junaid ke kallon ikon Allah shidai baiga komai ba a ƙirjin haroon hannunsa ne kawai daya tallabe wurin, Cikin ruɗi yace"yaya haroon babu komai fa a wurin hannunka ne kawai daka sa ka dafe,   Muryar tamkar zaiyi kuka yace"Manxon Allah yayi gaskiya Junaid, shikenan bakomai jeka kawai Allah yayi maka albarka, ya kare ka daga sharrin Maƙiya,   Ya faɗi tare da janye hannun junaid daga kafaɗarsa ya wuce sa yana cigaba da sambatu    Girgiza kai junaid yayi tare da cewa "Allah ya baka lafiya yaya haroon ya yaye maka wannan shaye-shayen da kake fama dashi," Yana gama faɗan hakan ya wuce direct ɗakin sehrish don yagaza runtsawa burinsa kawai yaganta ta zura kayan mata ajikinta, yana shiga ya samu azmee tana faman jejjera mata kayan a cikin wardrobe ɗinta, ko ina da abunda aka zuba aciki, gasu nan komai ajere, gwanin kyau,   Jin sallamar junaid yasa ta juya da fara'a tana amsa mashi,   Yace "Aunty azmee ina Sehrish ne i thought zanzo na same ta anan ne,"   Azmee tace "ae tuni ta fita don gyara cikin gidan kasan munbar aiki dayawa shiyasa bamu samu hutu ba,"   ɗan zumbura baki yayi tare da cewa "Aunty azmee wane aiki kuma? Mu dawo agajiyen sai kuma ta kama wani aikin, gaskiya bai yiyuwa zanje na dakatar da ita,' ya faɗi tare da juya ya fuce Murmushi azmee tasaki aranta tana fadin "Romea kenan, Allah dae yasa sehrish tazama mallakin ka, duk da nasan abune mai wuya ayi mashi aure at his age, bansani ba shi da ita waye zai raini wani shi shagwa6a ita kuma shiririta, amma kuma raina na bani cewa akwai wanda sehrish ke so ga dukkan alamu...............    ta ƙare maganar zucin nata ayayin da ta koma gaban dressing mirror ɗin sehrish dayake wayaam babu kayan kwalliya kona shafawa illa kwalba ɗaya tak na turaren junaid da tata6a satar mashi wanda har yau bata ta6a amfani dashi ba,     Janyo trolley ɗin dake ɗauke da cosmetic tayi ta shiga jera mata su, da turarurruka da mayukan jiki masu kyau da ƙamshi da sauransu, sai gashi mirror ɗin yafito sosai na ƴar budurwa, Cikin ƙanƙani lokaci rishi ta kammala gyara masa part ɗinsa, da wata irin yunwa ta fito ga bacci tana ji tana saukowa down suka ci karo da junaid dake tunkaro stairs ɗin,   da murmushi a fuskarta tace "Junaid dama idonka biyu ae nayi tunanin kana can kana sharar bacci,' yatsina fuska yayi tare da cewa "taya zan iya bacci bayan banga gyaran gashinki ba, zuwa nayi ki nuna min in gani," ya faɗi hada ruƙe ƙugu, Dama tana kallon fuskarshi tasan rigimar ta motsa ga Idonshi sai faman lumshewa suke yi alamar bacci yake ji over,   Saukowa ta yi tana cewa "Shikenan zan nuna maka ammma kabari nafara samun natsuwa tukunna, yanzu kitchen zanje na gyara kuma yunwa ma nake ji,"     Shiru yayi baice komai Ba dayaso hannu kawai zaisa ya tu6e mayafin data yafa, abunda ya hanasa yin hakan baiso wani yagani cikin Yayyensa balle ya ƙyasa, don kishinta yake ji ayanzu kamar kamar me,   Shiga gaba sehrish tayi ta nufi hanyar kitchen, cikin hanzari yabi ta yana faɗin "Nima yunwar nake ji, zan tayaki mu gyara kitchen in mun kammala cin abincin atare,     "Shikenan bita zaizai," ta bashi amsa tana dariya, shima dariyar yayi jin sunan da tasa mashi,    "Idan baki so zan daina bin ki,' ya faɗi ayayin da suke shiga kitchen ɗin,    Sehrish tace"Nafison hakan ae, saboda kana ɗebe min kewa sosai,"   Jin hakan yasa junaid sakin murmushin murna,    Wuce wa yayi yazauna saman ɗaya daga cikin dining chairs ɗin dake kewaye da dinner table yana cewa "Ki haɗa mana corn flakes kawai mu sha, in akwai snacks ki haɗo mana dashi,   Ta amsa mashi da "Toh," A cup biyu ta haɗa musu sannan ta haɗo masu da snacks suka zauna suna sha suna fira, ? ________________AUNTY BABBA______________________ Suna cikin wannan fargabar wayar hafsat ta sake yin ringing, cikin hanzari tunkan tasa hannunta ta ɗauka aunty babba ta riga ta ɗaukar wayar asaman cinyarta, a tunaninta Omar ne amma tana dubawa taga Sunan My Dad ya bayyana, ɗagowa tayi ta kalli hafsat hankali atashe tace "Abbanki ne ke kira, Allah yasa dae ba dawowa zaiyi ba, ya salammm ni bansan meke faruwa dani yau Ba Hannu hafsat tasa ta kar6i wayar, ta amsa kiran sannan takara a kunnanta tana zabga Sallama, Janar ishaq ya amasa mata da cewa "Wa'alaikum salam my daughter, ina mommynki take ne, i ave been trying her phone number tana ringing ba'a ɗagawa why"? Ya tambaya yana jiran amsa, Murya na rawa hafsat tace "am..dama...umm...tabar wayar a ɗaki ne ina ji, saboda ta shiga kitchen,   tayi maganar tana kallon mommyn nata data ke faman dafe zuciya,tana sauraron mai zai ce saboda wayar na a handsfree,.    Genar ishaq yace "shikenan ki sanar da ita cewa cikin week ɗin nan zan dawo insha Allah,".     "Shikenan daddy Allah ya dawo daku lafiya," sukayi sallama ta ajiye wayar tana faɗin "Tabɗijan Can akwai matsala fa,"   Aunty babba kuwa miƙewa tayi tana faɗin "Nashiga uku ishaq zai dawo ga zuwan Omar yau, bansan me zan fuskanta ba a wurin kowannan su... '. Muryar hafsat ce ta katse ta da cewa "Amsar fa abayyane take mommy, ke ma kin sani Allah,saki ukun nan sun Wajaba Akan ki muddin Abba yaji abunda kika aikata, saboda wancan karan Ladi mai aikin mu da kika ma bugun mutuwa sai da ya aika ki maiduguri bayan marukan da kika sha awurinsa ina ga waɗan nan bayin Allahn da kika naƙasa har Su biyu, gasky mommy kin shiga Uku, ga kuma ƴa Omar zaizo ni addu'ata Allah yasa Abba kada ya sake ki yabarki kawai da hukuncin Omar na zuwa prison kowa ma ya huta.....   Hankali tashe aunty babba tace"Hafsat prison fa kika ce? So kike akaini can kin gaji dani kenan"? Rai a6ace hafsat tace "dole nagaji dake mommy, duk ke kika ja mana wannan masifar da muke ciki muna zaman lafiyar mu,' ta faɗi a ƙuke hada buga tsoki kamar bada uwarta take magana ba, Jinjina kai aunty babba tayi batare da tace komai ba, adai dai time ɗin dr ya fito daga ɗakin da aka kwantar dasu hosana, jiki na rawa tabishi tana faɗin "dr ya jikin nata ta farfaɗo,"?   dr yace "Alhamdulillah tafarka yanzu haka bacci take yi itama saboda allurar da nayi mata,"   ɗaga hannu tayi tana cewa "Alhamdulillah har naji ɗan sauki, amma dr babu yarda za'ae ciwon fuskarsu ya warke nan take? kumburin ya sa6e, ni dr kodai surgery za'ae musu ne acanza fuskar,' tayi maganar in serious matter tana kallon shi,    Wani irin kallo dr ɗin ke yi mata yama rasa amsar da zai bata,   wuce wa gaba yayi ya tunkari Office ɗinsa yana cewa "sam Bazaiyiyu ba gsky,ba muyin irin wannan aikin anan, kuma fuskarsu batayi komai ba da za'a canza musu Ba,da alama madam kema kina buƙatar Aduba ki,' sarai taji abunda dr ɗin yace amma bata ji zafin maganarsa ba, saboda bata cikin natsuwarta a yanzu, Yini su kayi cikin fargaba ba salla ba salati dama ba ita bace agabansu ba, an saba haɗa salloli ayisu a lokaci guda,Saboda duniya aka sa agaba Ba lahira ba, gajiya su kayi gaba ɗayansu da zaman asibitin ga uwar yunwa kamar suyi hauka, ga zullimi da fargabar zuwan Omar, ganin har Magrib tayi babu kiran Omar yasa suka fidda tsammani da zuwan shi,   Ƙarshe basu jira dr yayi discharge ɗinsu ba, aunty babba ta ɗauko hosana dake kwance saman gado agalabaice ta sa6o ta a kafaɗarta ta fito da ita, sai cikin mota ta kwantar da ita, Jahad ma tashiga motar baiwar Allah ga zazza6i tana ji, gashi dr yace suna buƙatar jini su duka biyun amma babu yarda zasu yi, rayuwarsu a tagayyare sai yarda akayi dasu,   Shiga motar hafsat tayi mazaunin driver aunty babba na gefenta suka ja motar suka bar asibitin, a time ɗin har dr ya biyo su da sauri sauri don ya dakatar dasu amma ina tuni har sun bar arean asibitin.............   A tsiyace ta shiga da motar cikin gidan tayi parking ɗinta, tana fito wa ta wuce ciki saboda jirin da take ji na yunwa, fitowa itama aunty babba tayi sam bata tsaya taɗauki hosana ba ta shige ciki itama,   Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba ganin sun tafi sunbar hosana kwance sai faman nishi take saki numfashinta na fita daker-daker,    bata son yaya zatayi ba ta ɗauke ta saboda itama babu sauran ƙarfi ajikinta, fitowa tayi daga cikin motar tana faman zubda hawaye, Iya cuta dae an cuci rayuwarsu,   Ganin yarinya tsaye abakin mota yasa wani soja ƙaraso wa yana faɗin "Lafiya dai ƴan mata meke faruwa ne,"    Cikin shessheƙar kuka jahad tace "ƴar uwata ce ciki kwance bata lafiya bansan yarda zan shiga da ita ciki ba,"    Sojan yace "Can I help"? Jahad tace masa "eh" saboda bata da wata mafita da ta wuce hakan,   Buɗe motar yayi ya zura hannunsa ya sungumo hosana dake kwance magashiyyan ya ɗaurata a kafaɗarta ya shige da ita ciki jahad ta bi bayansa,    A saman 3 seater ya kwantar da hosana, jahad tayi masa godiya sannan tasamu wuri daga ƙasa ta zuƙunna fuskarta na dai-dai saitin ta hosana, Hawayen fuskarta har ɗiɗɗiga suke yi a fuskar hosana, addu'o'i tashiga karantowa tana tofa mata,.    Duk hosana na jinta tana so ta buɗe idonta amma ta kasa saboda kumburar da su kayi, tana so ta buɗe bakinta tayi ma Jahad magana amma tagaza saboda haƙoranta kansu sun raunata sosai don ba'a rasa mai girgiɗi acikinsu, ga la66anta da sukayi suntum sam bata iya motsa su, Cikin kuka jahad tace"Hosana na sani nasan akwai abunda kike son faɗa mun amma kin kasa, kada ki damu ina jin duk wani raɗaɗi da kike ji azuciyarki, inaji inama ace zan iya ɗauke maki zafin ciwon da kike ji da tuni nayi wlh.......taƙarasa mgnr tare da kifa kanta ajikin hosanna,sun jima a haka wulaƙance babu wanda ya leƙo su, sai daga bisa ni hafsat tafito har tayi wanka da alama ta canza kayan jikinta, doguwar riga ce tasanya har ƙasa, ta ɗaure gashin kanta,   Binsu da kallo tayi gwanin ban tausayi ita kanta duk rashin imaninta yau ta tausaya ma twins ɗin,girgiza kai tayi tare da wuce wa ta nufi kitchen,   Jim kaɗan sai gata ta fito hannunta ɗauke da tray mai girma, Tea set ne ɗauke asaman shi, sai French toast ɗin da ta hado masu dashi da sauran snacks,  duk da tasan ma daker zasu iya ci    Bedroom ɗinta ta shigar masu da shi ta ajiye Tray ɗin asaman table ɗin dake a dab da gadonta, Sannan ta fito ta nufe su jin takun tafiyar hafsat yasa jahad ɗagowa daga kwancen da take tana kallonta da rinannun idanuwanta da suka jigata,       Hafsat batayi mata magana ba hannu kawai tasanya ta cicci6i hosana ta ɗaura a kafaɗarta sannan ta wuce izuwa bedroom ɗinta tana cewa jahad "Ki biyo ni,"   Cikin sauri jahad ta tashi tabi su cikin ɗakin, kwantar da hosana tayi asaman shimfiɗeɗen gadonta, sannan ta juyo ta kalli jahad tace "Ga tea nan da snacks nasan kina jin yunwa ki ɗaure ki sha,'    Girgiza kai jahad tayi tana cewa "Bazan iya cin komai ba, "Soboda me"? Hafsat ta tambaya tana kallonta,   Jahad tace "Sabodo ƴar uwata, bata ci komai ba,idan naci ita kuma fa"?    Shiru hafsat tayi jikinta yaɗanyi sanyi aranta har tana mamakin dama har yanzu akwai ƴan uwa masu ƙaunar junansu haka aduniya? Jinjina kai tayi kafin tace " kada ki damu, zan ƙara dubata yanzu insha Allah,zata ji sauƙi,"   Shiru kawai jahad tayi,amma fa ba zancen Cin abinci agare ta muddin hosana bata ji sauƙi taci ba itama, sai dae yunwa takashe ta,   "Ave a seat," hafsat ta faɗi tana nuna mata saman gadonta, Jahad tace "Ina so nayi sallah tukunna," ta6e baki hafsat tayi tana cewa "okey ga toilet nan ki shiga,"   wuce wa Jahad tayi ta shige toilet ɗin tana rufe ƙopa tafashe da kuka mai cin rai tunaninta yanzu shine yarda zasu gudu daga gidan gaba ɗaya, don yanzu ta kwammace Su ƙare rayuwarsu a titi akan su faɗa hannun wani, tunda abun nasu ba sa'a kowa baisan taimakonsu don Allah batare daya cutar dasu ba,mutun huɗu kawai tasan suna da kyakkyawan niyya akansu, tsohuwa wadda Allah yayiwa rasu sai Goggon katsina da aunty saude da Yaya Omar ɗinsu.....    hafsat na jiyo kukan jahad dake acikin toilet, jikinta duk ya ƙara mace wa, karo na farko da ta fara jin tausayin wani aduniyar nan,        gaban mirror ɗinta taje wata roba ta ɗauko ta magani na shafawa a ciwo mai kashe raɗadi,   Dawowa tayi ta zauna saman gadon ta buɗe murfin tasoma lakuto shi tana shafa ma hosana a fuskarta, cikin lokaci ƙankani wurin yayi mata wani irin sanyi tamkar an ɗebe ciwon,   "Sannu ya jikin naki," hafsat ta tambaya tana kallon hosana wadda ke ɗan buɗe ido a hankali, sam ta kasa magana,    pillow hafsat ta janyo ta sanya mata kan gadon,sannan ta taimaka wurin tada hosana zaune ta jingine ta ajikinsa,   jikinta sai faman kerma yake yi, cup hafsat ta ɗauka ta shiga haɗa mata tea,bayan ta kammala ta sheƙa mata dashi da wani kofin donya rage zafi daga bisani taimaka wurin bata abakinta, la66anta har rawa suke yi wurin buɗesu saboda wata irin mahaukaciyar yunwa da take ji, sosai tasha tea ɗin kaf tashanye har dae hafsat ta ƙara haɗa mata wani ta bata,    Jahad ba ƙaramin sanyi taji aranta ba ganin yadda hafsat ke kula da hosana tayi mamakin yarda take bata tea abakinta, tsayawa tayi tana kallon su har sai da hafsat ta juyo ta kalle ta tace "ki buɗe closet ɗina akwai hijab ki ɗauko tare da Sallaya," Bude wa jahad tayi ta ɗauko hijab tasanya sannan ta shimfiɗa carpet ɗin tashiga yin sallah Hada isha'e tayi wadda ake cikin kira,   Daker hafsat tasamu hosana taci kaɗan daga cikin snacks ɗin data kawo mata saboda ciwon da bakinta ke yi mata, tea ɗin dae ne tasha sosai,    Gyara mata kwanciya tayi, sannan ta sanya bargo ta lullu6e ta,    tashi tayi ta koma saman doguwar sofa ɗin dake facing gadonta ta haye sama ta kwanta itama,.      Bayan jahad ta kammala sallar ta ninke mata abun sallar da hijab ɗin ta mayar dasu inda ta ɗauko su,    Sannan ta koma saman gadon ta haye, ta soma haɗa tea ɗinta tasha tana ci tare da french toast ɗin da hafsat ta haɗo masu, sosai taci don bata rage komai ba duka ta lamushe, Bayan ta kammala ta shiga cikin bargon da hosana take ta kwanta itama, janyo ta tayi jikinta ta rungume ta tana kiran sunanta "hosanna ya jikin ki"? Har yanzu akwai raɗaɗi ko"?   daker tace "Eh," Jahad tace "kiyi haƙuri kinji, insha Allah bazamu ƙara shan wahala ba,inaji araina komai ya kusa zuwa ƙarshe bansani ba ko mutuwa zamuyi ba shine sauƙin mu Allah kaɗai yasani,    saurarawa tayi don jin mai hosana take cewa, saboda fuskarta na'a kwance achest ɗin jahad,sam sautin bai fita sosai    "Bana jinki hosana, kibar magana kawai kada ciwonki ya ƙara raunana,"    Shiru hosana tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, bakomai take son faɗama jahad ba face sunan YA OMAR da take kira.....................................*💋💋🔥The Father Of Soldiers🔥* ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ❤‍🔥💞💘? *Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad* ~💋BOSSLADY💋~ *EPISODE 9-10* https://youtu.be/rnmDunstSN4 Abun da ya faru MARSHAL OMAR bai samu zuwa kaduna ba sakamakon Emmergency Call din daya samu daga wurin Abbansu cewa yana bukatar shi A headquater dinsu, a lokacin Motarsu har ta fita daga garin Abuja amma suka juyo da hanzari saboda Omar baya wasa da Omarnin mahaifinsa ko musu baya iyayi mashi, duk da yadda ya matsu akan son ganin su hosana da jahad amma haka ya haƙura😔 Tun bayan da suka kammala shan corn flakes junaid ya wuce bedroom dinsa saboda dama agajiye yake, sehrish kuwa sai da ta tsaya a kitchen din har azmee tazo suka fara aiki, cikin kankanin lokaci suka kammala dinner, sannan ta wuce bedroom ɗinta ta kwanta tasha bacci har wurin magrib sannan ta tashi donyin sallah, bayan ta kammala jiki na rawa ta bude wardrobe dinta, tsayawa tayi saboda ruwan ido ta ma rasa me zata sanya acikin kayan, hannu tasanya ta janyo wata haɗaɗɗiyar Gown black colour mai kyalkyali masu daukar ido, jinjina kai tayi tare da cewa "Wannan zan sanya," tayi maganar tare da hanging dinta asaman murfin wardrobe din, shaf shaf ta tube riga da wandon dake jikinta ta tura su, cikin laundry basket dinta, sannan ta dauki rigar ta shiga kiciniyar zira ta ajikinta, bayan ta kammala ta koma gaban mirror tana kallon kanta ta cikinsa, fuskarta dauke da murmushi tana tuna yaushe rabon da taji ta acikin kayan mata, kayan ma irin wannan sabbi masu kyau, rigar tabi shape din jikinta,hannunta mai dan tsayi ne wanda ya tsaya dai-dai elbow dinta,Jujjuyawa tayi tana ƙarewa kanta kallo, kafin tasa hannu cikin jerin Perfumes dinta ta dauko kwalbar turaren TOUCH ta feffesa ma jikinta har wani lumshe ido take yi saboda yarda fragrance dinsa ke dakar hancinta, bayan ta mayar da turaren ta koma cikin wardrobe din ta ɗauko mayafi white colour tayi rolling dinsa irin lagen da larabawa suke yi masha Allah 😍 Kama hanyar fita tayi tana bude kopan azmee na sanyo kai dama dakin nata ta nufo itama, ganin yarda azmee tasaki baki yasa sehrish sa hannu ta rufe fuska don tasan kallon na menene,   "Nama rasa mai zance irin wannan kyau haka? Yarinya kamar ƴar larabawa ashe dama haka kike da Kyau ga ki dirarra,'?   Cikin jin kunya sehrish tace "Aunty azmee ko fa makeup banyi ba, i know u are just teasing me,   Azmee tace "Reesh ae ko ba kiyi kwalliya ba kyau kike, ae ni ban ma so kiyi kwalliyar yanzu, don banson ki rikita samarin gidan nan, mu rasa wa zamu ba acikin su,'   "BABBAN YAYA' ta faɗi acikin zuciyarta a fili kuma tace "Mai rabo," dariya azmee tayi tana cewa "Toh Allah yaba mai rabo sa'a time kawai zamu jira muga wanene wannan in da rai da lafiya,'   Murmushi kawai sehrish ke saki, suna cikin wannan tsayuwar motocin su suka shigo atare mai ɗauke da jiniya, azmee tace "Alhamdulillah shikenan ma, tun da kin shirya in suka shigo ki tabbatar kin kaima Babban yayansu dinner dinsa tare da Omar, yanzu ma na kammala jera na dining din basu kai ga saukowa sunci ba, dama Twins ne da suka dawo bada jimawa ba sai Junaid da HAROON, just zanji da sauran kawai,'   ta ƙare bayanin tare da kama hanyar fita daga ɗakin tana nanata mata,   Sehrish ta amsa mata da "toh insha Allah,"     cikin sauri ta koma wurin window dinta ta janye labulan ta zuge glass din tana hangensu,    kowannansu agajiye ya fito daga cikin Motar, Abbansu ne tare da marshal Omar sai SGR, Abbansu na sanye cikin kaki, haka SGR army trouser ne ajikinsa sai shirt light green mai gajeran hannu sun ɗame jikinsa, Omar kuma Shigar dazu ce ajikinsa wadda yayi shirin Zuwa Kaduna dazu, tunda Armstrong ya buɗe masa mota ya fito yake faman lumshe ido hannunsa ɗaya na acikin sumar kanshi yana yamutsa ta, kallon shi Abban su yayi tare da cewa "Ko dae saina taimaka na goyaka ne? Naga alamar baka iya tafiya," ɗago da eye balls dinsa yayi ya kalli Abban nasu sannan anatse yace "Dad kenan, ni da kai wa zai goya wani? kai ma ka sani,"    Yayi maganr tare da soma tafiya abban nasu kam dariya yayi yana cewa "Oh kana jin kanka Tamkar giwa ko? Ae ba abun mamaki bane kaga na sa6eka abayana, in banda ma yanzu daka zama jibgege haka ga tsayi nan nan nake ɗaukarka kana yaro har goya ka nake yi," duk Omar na jinsu yana murmushi kawai saboda atare suka jera suka nufi cikin gidan,   ɗan gyaran murya yayi tare da cewa "Abba yanzu ae sai dai ka goya grandchild dinka masu zuwa," Omar ya faɗi,   Abban su yace "hmmmm taya hakan zata faru bayan ƴan bukulu sun hana ruwa gudu, burina kenan kullum kamar yadda na haifa nima nawa su haifa amma abun takaici duka ya'yan nawa babu wanda ya ajiye ko budurwa bayan ni tun ina 20 years aka sanƙamamun aure muka sha soyayya gaba ɗaya,'   Omar yace "Kada ka damu Abba, Insha Allah burin ka zai cika, in har hakan zaisa ka farin ciki, kawai acigaba da yi mana addu'a,'    Jinjina kai abbansu yayi yana ɗan kallon SGR dake gefensa shiru tamkar baya jin me suke cewa,    Ruko hannunsa yayi cikin nasa sannan yace "kai fa Son, Naji baka ce komai ba ? Ko baka son farin ciki na ne?   yatsina fuska yayi tare da cewa "In dai yaron da zaka goya ne zan kawo maka shi,'   "Uwar fa"? Abban ya tambaya adai dai lokacin da suke shiga babban falon SGR yace "Babu," dariya omar kawai yake yi.abbansu kuwa baki sake yace "Shege zaka kawo min,'?   "Ko baka so ne"? Sgr ya tambaya shima da zolaya,   Abbansu yace "Ae da babu gwara ba daɗi, akawomin inaso,"    Omar yace "So funny wlh, abba son jikokin harya kai haka, to. Insha Allah ba shege acikinsu, Original zaka samu daga gurin kowan nan mun, ' cike da nishaɗi suke fira kamar bazasu iya rabu ba, wuce wa Abbansu yayi part dinsa, shima SGR tare da OMAR suka wuce Uptairs nasu parts din, 💪    Tun da Omar ya shiga bedroom dinsa ya rage kayan jikinsa toilet yashiga ya yi wanka, yafito ya zura kayan baccinsa, har cikin ransa yaso ya kira Aunty babba don abasu Hosana yaji Muryarsu amma ransa yana bashi cewa yanzu sun isa suyi bacci, wannan dalilin ya hana shi calling ɗinsu, Fitowa parlor dinsa yayi yasamu wuri saman sofa yazauna hannunsa ruƙe da wayarsa, sai lokacin yake dana sanin rashin daukar su hosana da jahad hoto ya ajiye acikin wayar shi koya samu na rage kewarsu, yana cikin wannan tunanin wayarsa ta soma ruri karatun kur'ani Ne ringin tone dinsa duba sunan daya bayyana a screen dinsa yayi nan take sunan*ABUSUFYAN*ya bayyana muraran,   Cikin hanzari ya ɗaga ya kara a kunnansa "Assalamu Alaikum Uncle Sufyan yau an tuna dani ne"?   On ther other hand ABUSUFYAN yace "Ko da yaushe cikin tunawa nake yi dakai Omar, nayi trying number dinka dazu baya shiga, kuma na jaraba ta RAFAYET tana ringing amma bai ɗaga ba,'   Omar yace " Kash ! rashin sani ɗazu ne na kashe wayar muna aiki ne shiyasa,"    Abusufyan yace "Dama inaso na maka magana ne About wannan yaran da goggon katsina ta ƙaƙabamun a matsayin ya'ya na"?   Murmushi Omar yasaki kamar yana agabansa yace "Ae ko ɗazu da safe ta kira ni awaya, kusan kullum ne sai ta mun Complain akan ƴa'ƴan abusufyan ɗinta,'    Abusufyan yace"Allah sarki, Nima tana kira na tana mun complain akan nasa ka mayar mata da ya'yana wuri ta, ynx ina yaran suke ne?  Ya tambaya yana jiran amsa Omar yace "A gidan general ishaq suke da zama, can na kaisu,"    "Ina iyayen su suke ne"? Ko yan uwan matar ishaq din ne? Ya tambaya   Omar yace "A'a Uncle yaran fa basu da kowa kamar yadda suka sanar mun, na haɗu dasu ne a asibiti cikin mawuyacin hali tagwaye ne baza su wuce 17years ba Suna buƙatar taimako,    Ajiyar zuciya abusufyan yasaki kafin yace "Meyasa ba zaka dawo dasu nan ba cikin abuja kusa da kai ba"?   "Uncle kaima ka sani, zaman su anan bazaiyi yu ba, maza ne mu duka duk ba wannan ba AMMI bazata ta6a lamuntar wani bare ya zauna acikin jinin ta ba,especially su da suka kasance basu da asali,' bayani yake masa tamkar yana agabansa   ɗan gyaran murya abusufyan yayi kafin yace "Listenin to me OMAR! kana da kyakkyawar niyya akansu, inaso ka kaddara aranka cewa waɗannan yaran jinin ka ne, kasanya wa ranka cewa Ƴa'Ƴa na ne, ya'yan ƙanin mahaifin kane *ABUSUFYAN* ina so ka basu kulawa Omar ! Dan Allah kada ka bari su wulaƙanta kayi mun wannan alƙawarin.......   Jikin Omar ne yayi mugun sanyi jin abun da Uncle Abusufyan ke faɗamasa, yanayin sautinsa da yadda yake yin kalamansa haƙiƙa ya ta6a Zuciyar Omar sosai, tunani omar yashiga yi aransa har sai da Abusufyan yace"Naji kayi shiru OMAR,"   Cikin sauri yace "Insha Allah Uncle i wll take care of them more than u think, nima inajin su araina sosai Uncle, ina ƙaunar yaran har cikin raina,   yana iya jiyo sauke ajiyar zuciyar Abusufyan alamar hankalinsa ya kwanta kuma yasamu natsuwa da bayanin Omar,   ABUSUFYAN yaci gaba da cewa "OMAR!  INA SO KA DAWO DA YARAN NAN GIDA NA DAKE ANAN SU CI GABA DA RAYUWA, KA SANYA MUSU SECURITY TARE DA MAI AIKIN DA ZATA KULA DASU, INA SO SU RAYU ACIKIN GIDA NA, KAYI MUN WANNAN ALƘAWARIN!!!"    runtse ido Omar ya ɗanyi yana jinjina kalaman Uncle din nasa daga bisa ni yace "Insha Allah Uncle zanyi komai kake so, zan dawo dasu nan acikin gidan ka kamar yarda kake so,"    Sun jima suna waya kafin daga bisa ni su kayi sallama, ya ajiye wayar yana mai tunani iri-iri aransa, yana ji aransa in ya ɗauke su hosana daga gidan aunty babba tamkar baiyi mata adalci ba don ya Lura tana son yaran kuma sun saba dasu anya kuwa zai iya cika alƙawarin Uncle Abusufyan Na dawo dasu hosana cikin Abuja da zama!!? 😟    Yana cikin wannan tunanin Sehrish ta shigo da sallama, batare da ya ɗago ya kalle ta ba ya amsa mata sallamar, sam ransa ajagule yake uncle dinsa ya ɗan ruɗa masa brain ɗinsa   Tray na a hannunta ƙarasawa tayi tare da gaishe shi "ina yini ya Omar,"  ƙiris ya rage omar ya ɗago ya kalle ta saboda Voice dinta tayi mashi kama da ta JAHAD, amma yabar Abun a matsayin muryar mai aikinsu ne ya koma masa ta Jahad Saboda kewarsu da yayi sosai Amsa mata yayi da cewa "Lafiya lou"    Ajiye masa tray din tayi mai dauke da food stuffs dinsa asaman table Din dake a front dinsa sannan ta juya takama hanyar fita tana jiyo shi yana furta "ngde,"    Sauƙin kan MARSHAL OMAR yana matuƙar burgeta, babu ruwan shi ba kamar SGR ba, yana da IZZA ta wani bangaren kamar abinci muddin takai masa sai tayi saving ɗinshi, amma Omar sam baya buƙatar wannan kawai daga an kaimasa shi yake zuba abunshi yaci,   Saukowa tayi down a lokacin har su Twins da kanal yusuf Sun hallara suna cin dinner dinsu, tayi mamakin ganin babu Abbansu da junaid may be yana a part dinsa azmee takai masu acan   Gaishe su tayi gaba ɗaya suka ɗan dago suna kallonta, Kanal yusif ya amsa mata da sakin fuska amma Ayaan da jahan kuwa sai dai suka bita da ido,😡   Har bugun zuciya take ji in ta gansu cikin hanzari ta shige kitchen ta shirya ma SGR dinner ɗinsa ta fito ɗauke da tray ahannu ta nufi hanyar upstairs dinsa,    Da sallama ta shiga palor dinsa baya aciki, ƙarasawa tayi ta ajiye masa kayan abincin saman table dinsa, sannan ta ɗan dakata ko zai fito amma shiru babu alama, . yanke shawarar zuwa bedroom dinsa tayi a bakin ƙopar shiga ta tsaya sannan tayi sallama, daga ciki taji ya amsa mata ƙasa ƙasa kafin ya bata permission ɗin shiga ciki,    A hankali ta zura ƙafa ta shiga ciki jikinta na ɗan kerma Hango shi tayi daga shi sai bathrobe ajikinsa kwance abaje saman gadonsa, alamu sun nuna cewa baiji ma da fitowa daga wanka ba, ya kwanta gajiya ce tayi masa yawa, idonsa na'a lumshe yace "Wanene ne," sehrish tace "mai aiki ce dama dinner ne na kawo maka yana a palor naga baka fito ba, Jim yaɗanyi kafin yace "Tea kawai nake buƙata,akawo mun nan,' Amsa mashi tayi da toh, sannan ta fuce ta koma palor dinsa ta ɗauko kayan tea din dake acikin tray din da ta ajiye anan sannan ta shigar masa dashi, har gab da gadonsa ta ajiye masa saman madai-dai cin table din dake a wurin ta matsa masa dashi jikin gadonsa, bin shi tayi da kallo saboda bai buɗe idonshi ba kuma baiyi yunƙurin tashi ba, yayi wani fresh dashi, Ganin alamun fa zai iya zarcewa da bacci yasa tace "Na kawo maka Tea ɗin," "I knew," ya bata amsa, jinjina kai tayi ashe yasan ta kawo ɗin, wahalar tashin ce kawai yake ji, kusan 15 mins sannan ya ƴunkura ya miƙe tare da sauko da ƙafafunsa ƙasa, rigar iya guiwar ƙafarsa ta tsaya, saukin yasa shorts daga ciki amma chest ɗin shi a buɗe yake fari kal, Zuba mishi ido tayi tana kallon ikon Allah wani irin bacci ne ke fusgar shi, ga uwar yunwa yana ji, ji take tamkar ta bashi tea ɗin abaki yasha, cikin sauri ta haɗa masa tea ɗin a cup ta ɗan tura masa agabansa tace "gashi nan,' buɗe blue eyes ɗinsa yayi a hankali sannan yakai hannu daker ya ɗauki cup ɗin yakai bakinsa yana ɗan kurba da zafinsa, ya sha ba laifi kusan sau biyu tana ƙara masa yana shanye wa, Bayan ya kammala tace "kayan dinner ɗin fa na mayar dasu"? Ta tambaya cike da jin tsoran amsar da zai bata, "In akwai fruits ki haɗo mun," ya faɗi tare da mayar da jikinsa ya kwantar akan pillow, Tattara kayan tea ɗin tayi sannan ta fuce dasu ta ajiye su a tray din dake ɗauke da warmers na abincin sannan ta ɗauke shi ta fita dashi kitchen ta shiga ta ajiye su, sannan ta ɗebo mashi fresh fruits acikin fridge, A plate ta zuba mashi su sai da tafara yayyanka mashi su sannan, tana ƙoƙarin fita suka ci karo da Haroon tsaye abakin ƙopar kamar aljani, Da ƙarfi ta furta "A'uzu billahi minashshaiɗanin rajim,' Haroon ya fashe da dariya tare da cewa "Ni ne shaiɗan ɗin, ko kin ga ƙaho akaina ne? "Eh," ta bashi amsa, Yatsina fuska yayi yana bin jikinta da kallon frm up to down kafin yace "Haɗaɗɗiyar Sura," tace "Tubarkallah masha Allah," Murmushi yaɗanyi kafin ya kuma cewa "ki dai bi ahankali naga kamar zakiyi rawar kai Kada kici ka zaƙewa mana domin kuwa har yanzu fa baki da wani matsayi acikin gidan nan, duk inda za'aje adawo bakya wuce ƴar aiki, sannan na lura kina shisshige ma wancan ifritun ko? to inaso ki sani wancan dashi da dutse duk ɗaya suke indai agame da feelings ne, mace bata gabansa koda zai kula matan ma bana tunanin irin ki, ae ma zaren ba kalar yadin bane iska ce kawai zata wahalar da mai kayan kara......... tun da yasoma magana idon sehrish suka soma ciccikowa da kwalla amma bata bari hawayen sun zuba ba, ganin zai bata mata lokaci yasa ta bi ta gefensa ta fuce da sauri, tana jiyo dariyarsa sam tarasa gane ma haroon, batasan mai ta tsone masa ba, time ɗin da tashiga bedroom ɗin SGR samun shi tayi yana ta faman sharar baccinsa alamu sun nuna cewa ma tunda tasa ƙafa ta fuce ya fara baccin, tsayawa tayi akansa tana kallonshi hannunta na riƙe da fruits ɗinsa, Yayin da idonta Suke cike da hawaye saboda kalaman haroon ita kanta tasani tabbas SGR ba tsaran yinta bane kwata-kwata bama haɗi, jinjina kanta tayi aranta tace "nasani kafi ƙarfina nesa ba kusa ba, kuma nasan cewa kafin ni akwai wanda suka ruga ni faɗawa wannan tarkon bila adadin, Amma inaji araina babu wadda zata soka dan Allah kamar yadda nake sonka, tun bansan ya kamannin fukarka suke Ba, da sunanka kawai nakamu da tsananin ƙaunarka kuma zan cigaba da addu'a akan hakan koda bazan ci nasara ba aƙarshe...Ana ahabbuk kasiran BABBAN YAYA.........❤? Wani irin juyi SGR yayi har sai da Sehrish ta ɗan tsorata gudun karya farka ya ganta, gyara kwanciyar shi yayi, yadda yake sakin numfashi anatse yana bacci ba ƙaramin tafiya yayi da ita ba, Ajiye fruits ɗin tayi saman table sannan ta matsa a hankali cike da fargaba ta janyo lallausan blanket ɗinsa jikinta na ɗan kerma ta samu ta hayo dashi jikinsa ta lullu6a masa har zuwa neck ɗinsa, Murmushi ta ɗan saki ganin ta kammala batare da ya farka ba, juyawa tayi ta tattaka izuwa inda makunnin hasken ɗakin yake ta kashe mashi shi, nan take ɗakin ya soma kyalli yana bada wani irin haske har sai da ta ɗan razana, ashe furnitures ɗin dakine masu wannan sparkling light ɗin launi daban daban suke badawa, aduk time ɗin da aka kashe hasken ɗakin Yayi dark gaba ɗaya su kuma sai su soma bada nasu hasken mai launuka, fuska ɗauke da murmushi sehrish ke kallon wannan ikon Allan Bin su take yi da kallo tun daga Bed ɗinsa da bedside table ɗinsa, drawer ɗin da ke ɗauke da mirrow jerin wurin Closet ɗinsa gaba ɗaya sun ɗau hasken nan, sai taga ya ƙara yi mata kyau sosai, Lalla6awa tayi ta koma inda yake kwance tana kallon fukarshi yadda eye lashes dinsa suka fito radau zira zira dogaye kasancewar idon na'a rufe, sun kwanta luf, Addu'ar bacci tashiga yi mashi saboda tasan cewa bai samu damar yi ba ayarda ya kwanta ɗin nan agajiye ta jima sannan ta ɗan tattofa masa ajikin bargonsa, kamar karta bar ɗakin haka take ji (Nace ba mai zai hana kawai ki kwana anan Ehen 😂) hannu tasa ta ɗauki Kayan marmarin dake acikin plate ɗin sannan ta fuce dashi bakowa a babban falon Dama tun fitowar farko da tayi duk sun kammala dinner ɗinsu sun shige cike aranta tace "Allah sarki su fawan hada rashin su yasa yanzu basu cika haɗuwa atare suna cin abinci ba ko zama a palor suna fira, ko yaushe zasu dawo? Duk da ina tsoran abunda zasu ce in suka ganni a Matsayin mace, Especially fawan nasan halinsa sosai baijin magana shine ya ta6a bani horo harna galabaita," ta ƙarasa zancen zucin nata , bedroom ɗinta ta wuce da fruits ɗin saboda dama itama bata ci komai ba, asaman gadonta ta zauna tsakiyar gadon ta lankwashe ƙafa tana shan fruits ɗin tass ta shanye su sannan ta ajiye plate ɗin asaman side drawer ɗinta, dama empty yake tunda ta rotsa ma haroon fitilar saman shi akai, bata sake ajiye komai asaman wurin ba, sauko wa tayi tashiga toilet saboda bata yi sallar isha'e ba, alwala tayi sannan ta dauko hijab ta zura bayan ta shimfiɗa carpet ta gabatar da salla, Tana gama wa ta naɗe carpet ɗin ko addu'a bata tsaya yi ba, ta tura su cikin wardrobe sannan ta haye saman gadonta taja bargo ta kwanta daker tayi addu'a kafin bacci 6arawo yayi awon gaba da ita.................(Shin ko kun lura cewa Sehrish ta manta dasu hosana da jahad bakamar da ba? hmmmmm rayuwa kenan baka ta6a sanin asalin ya mutun yake sai yasamu wurin zama koya samu abun duniya nan zaka ga zahirinsa😥) _____________________🌹🌹🌹____________________ In midnight Hosana tafarka da matsanancin Ciwo, wani sabon raɗaɗin ciwon ne ya taso mata agigice tafarka tana kuka tana zabga Uban ihu tana faɗin "Innalallahi wa'inna ilaihiraji'un , La'ila ha illallah muharammadur rasulillah Wayyo Allah na, mutuwa xanyi, gaba ɗayansu suka farka hankali atashe tun daga jahad har hafsat dake kwance saman Sofa sai da tafarka a tsorace, taruwa su kayi akanta jahad na faman yi mata addu'a tana tofa mata cikin kuka take faɗin "Hosana ki daina magana ciwon bakin ki zai ƙara raunata, dan Allah kiyi haƙuri innalallahi bansan ya zanyi ba,'tafaɗi tare da fashewa da wani sabon kukan itama, dama sai da ranta yabata cewa raɗaɗin ciwon hosana zai iya dawo wa sai gashi ya dawo, fuskar tayi suntum la66an sun kumburo hancinta ma yayi girma, idanunta ma sun kumbura duk kwantsa ko buɗe su bata iyayi saboda sun datse sosai, ita kaɗae tasan azabar da take sha ga haƙoranta suma nasu Zogin daban, ko'ina ciwo hakanne yasa ta haukace taita faman zabga salati tana kiran Sunan Allah da manzon sa 😭*💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* *🔥The Father Of Soldiers🔥* ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ❤‍🔥💞💘? *Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad* ~💋BOSSLADY💋~ *EPISODE 11-12* Ita kan ta Hafsat ba ƙaramin tashin hankali tashi ga ba ganin halin da yarinyar ta shiga, da alama ma raunukan nata sun ɗuri ruwa dole sai an fitar da ruwan Ya Salam, Yarfa hannu kawai take yi tana zabga uban kuka, hankali atashe JAHAD ta kalli hafsat tare da cewa "Aunty dan Allah ki taimaka mu mayar da ita asibiti aduba ta.....' ta ƙare maganar tana faman zubda hawaye, Ita kanta hafsat tunanin da take yi kenan can ne kawai mafi ta, ta shi tayi jiki na rawa ta ɗauko hijab ta zura sannan ta ɗauki mukullin motarta da ta bari a saman mirror, da kanta ta cuccu6i hosana daker ta ɗauko ta a kafaɗarta, ta fuce da ita cikin sauri itama jahad tabi bayanta a babban falon suka samu aunty babba saman Sofa hannunta ɗauke da plate ta dafa taliya sai faman ci take a tsiya ce saboda yunwar da ta taso ta, duk ihun da hosana take yi a kunnanta amma batayi yunƙurin tashi ba, balle taje ta dubo meke faruwa, Ganinsu afujajen yasa ta miƙewa tana cewa "Hafsat ina zuwa cikin daren nan? Ina zaki kai ta? Batare da hafsat ta kalle ta ba tace "Zan mayar da ita asibiti ne," hankali atashe aunty babba tace "Saboda me !! Acikin daren nan ! Ki barta kawai inyaso gobe dr yazo ya duba ta har gida," tsoki hafsat taja dama a ƙule take da Mommyn nata saboda duk ita taja mata halin da suke ciki,. Wuce ta tayi tana cewa "da yake ba jikin ki bane ae dole ki ce haka,' Bin su kawai aunty babba tayi da kallo har suka fuce, abayan mota hafsat ta kwantar da hosana, sannan suka shiga gaba ita da jahad, taja motar da gudu ta fuce da ita a wani privet hospital takai ta, cikin sa'a suka karbi hosana kuma nan take suka shiga bata taimakon gaggawa, Yayin da hafsat da jahad suka samu wuri suka zauna nan waje suna jira saman waiting chairs, runtse ido kawai jahad ke yi tana faman karanto addu'a, tsigar jikinta har tashi take yi saboda jin yarda ihun hosana ya cika asibitin gaba ɗaya baiwar Allah, ita kaɗai tasan azabar da take sha, Ita kanta hafsat dake gefenta jikinta duk ya gama mutuwa haƙiƙa taji tausayin Yarinyar fiye da tunanin mai tunani, Jim kaɗan suka ji tsit babu kukan hosana babu alamar shi, jin hakan yasa jahad yin zumbur ta miƙe ta tunkari ƙopan ɗakin da suka kwantar da ita, tsoranta kar ace hosana ta mutu ne shiyasa suka ji shiru, turo ƙopar Nurse tayi ta fito cikin sauri jahad ta tare ta tana cewa"dan Allah sister ya jikin nata yake? ta tambaya a ɗan ruɗe Nurse ɗin tace "Alhamdulillah, kada ki sa damuwa aranki, jikinta da sauƙi sosae anyi mata dressing na raunukan nata sannan Mun taimaka mata da pain relievers yanzu haka allurar bacci mu kayi mata, addu'a kawai zaku ci gaba da yi mata,' tana faɗin hakan ta wuce gaba, Ajiyar zuciya jahad tasaki har hankalin ta ya kwanta sosai, komawa tayi ta zauna gefen hafsat wadda ke ta faman yin gyangyaɗin bacci, Rufe idonta kawai tayi tana faman ci gaba da yiwa hosana addu'a, bata jin zata iya runtsawa a daren nan, tsawon awanni suna anan jugum time ɗin hafsat ta jima da yin nisa a baccin ta, jahad kuwa na nan ido buɗe, kamar daga sama taji hosana na kiran sunan ta ƙasa ƙasa da farko tayi tunanin gizau muryarta keyi mata amma daga baya ta tabbatar da cewa ita ɗin ce ke kiranta, Cikin hanzari ta miƙe ta shiga ɗakin samun ta tayi ta tashi zaune saman gadon, ba ƙaramin farin ciki bane ya cika jahad, ganin yadda fuskar hosana ta sa6e an matse mata ruwan anyi dressing ɗin wurin ga bandage nan a forehead ɗinta da saman hancinta, duk da fuskar ta canza sosai kamar ba ita ba, idanuwanta sun buɗe sosai tana ganin jahad takama Murmurshi 😥 Faɗawa saman gadon jahad tayi ta rungumo ta sosai ajikinta tana faɗin "Allah sarki hosana ashe kin farka ban sani ba kina ta kiran suna na, ya jikin naki? Akwai inda ke miki ciwo yanzu"? Tayi tambayar tana janye jikinta daga na hosanar, Daker ta iya cewa "Naji sauƙi sosai jahad ba inda ke mun ciwo yanzu, amma magana tana mun wahala,Kuma ina jin jikina kamar ba nawa ba" hannu jahad tasa tana shafa gefen fuskarta tace "Insha Alah zaki dawo dai-dai hosana, yanzu hankali na ya kwanta tun da naga kina murmushi nasan cewa sauƙi ya samu, yanzu ki faɗamun wanene yayi maki wannan bugun mutuwar?' turo baki hosana tayi tana cewa "Wannan mara imanin, saboda nazo na same ta, ta shaƙe maki wuya kamar zata kashe ki, na bata haƙuri ta ƙyale ki ta ƙiya shine na gartsa mata Cizo a hannun, wannan ne fa kawai yasa ta kamani ta jibga ta faffasa mun fuska..........," shessheƙar kukan da take yi ne ya hana ta cigaba da maganar Cikin sanyin Murya jahad tace "ashe duk don saboda ni ne tayi maki wannan bugun, babu komai akwai ALLAH ! , Zai bi mana haƙƙin mu duk wanda ya zalunce mu Allah zai saka mana insha Allah! Jinjina kai hosana tayi tana share hawayen ta tace "Yaya Omar bazai ƙyale su ba, duk sai sun gane kurensu..... ta faɗi wit angry face can kuma ta sake cewa "Jahad komai yasa yaya Omar har yau baizo ya duba mu ba"? Jahad tace "muyi mashi Uziri hosana, ni nasan cewa yana sane damu kuma zaizo nan very soon,' Sun jima suna yin fira atsakanin su, ita kanta jahad tasan cewa hosana juriya kawai take yi tana yin surutu, daker tasamu hosana ta koma ta kwanta, itama a gefenta ta ra6a ta kwanta, lokaci guda bacci ya kwashe su su duka, Ba ƙaramin bacci suka sha ba, don kuwa har sai da gari ya waye rana ta fito sannan jahad tafarka, hosana kuwa nata faman sharar baccin ta, ganin yadda hosana ke bacci anatse ya ƙara tabbatarwa da jahad cewa tasamu sauƙi sosai, tashi tayi ta cire hijab ɗin dake jikinta, ta shige toilet ɗin dakin Alwala tayi sannan ta fito ta ɗauki hajiabin ta zura, tana faman tunanin in da zata samu tayi sallah don babu carpet,   Fitowa tayi don ta duba hafsat samu tayi bata anan inda tabar ta jiya babu ita ba alamarta a wurin, sai taji hankalin ta ya ɗan tashi tsoranta kar ace guduwa tayi tabarsu a asibitin,   Hankali atashe ta fito harabar asibitin ga mutane nan nata wuce wa wasu na shigowa wasu na fuce wa, sai faman waige waige take yi tana neman hafsat, har wurin ajiye motoci taje taga ko zata ga motarta amma babu ita, hakan na nufin tabar asibitin kenan, da alama ma tun asubahi tabar asibitin, tuni jikin JAHAD yayi mugun sanyi,   Koma wa tayi tasamu wurin inda taga wasu mata zazzaune suna fira, tayi musu sallama suka amsa mata da fara'a    Tambayarsu tashiga yi idan suna da abun sallah su ara mata, nan wata daga cikin su ta miƙa mata sallaya ɗinsu da suka zo da ita, anan harabar jahad tayi sallah bayan ta kammala ta mayar masu da dardumar sannan ta koma ciki a kasalance, bakowa tafi ji ba face HOSANNA, yanzu in da gaske hafsat tafiya tayi tabarsu yaya zasu yi? Ina zasu dosa? bakomai ma yafi damunta ba face Hosana in tafarka ta son dole akwai yunwa atattare da ita, gashi ita ba ta da ko sisi balle ta siya musu abunda zasu samu su Ci,    Gefen hosana tasamu ta zauna wadda ke kwance tana faman sharar bacci, tagumi ta zabga tare da zuba mata Ido tana kallonta, in taƙaice muku tsawon lokaci ba hafsat ba alamarta 😧😳 Gashi in sunce zasu kai kansu gidan duka ba wanda yasan hanyar da zai bi, saboda da daddare ne kawai suka fito daga gidan baza su iya shaida kwatancen gidan ba, gashi ko Sunan unguwar basu Sani ba, ajiyar zuciya jahad tasaki aranta tana jin cewa hutu ne yazo musu, zasu ci gaba da rayuwarsu ne kawai akan titi, _____________________SEHRISH__________________ Around 8 Ta farka kai tsaye kitchen ta wuce har time ɗin rigar jiya ce ajikinta da rolling ɗinta, a kitchen ta samu Azmee harta kusan kammala breakfast din gaba ɗaya, bayan tayi sallama ta shiga suka gaisa da junan su, Daga bisa ni azmee tace "Ina fata jiya kin kai ma SGR dinner ɗinsa ko? don na shigo na taras da kayan abinci a warmers ko ta6a su ba ayi ba,'    Sehrish tace "Na babban yaya ne, Jiya bai samu yaci ba dana kai masa, Tea kawai yasha daga baya yace mun yana buƙatar fruits, shine kafin naje na kawo masa har bacci ya ɗauke sa,'   Jinjina kai azmee tayi tare da cewa "Allah sarki da alama jiya sun sha aiki ne that's why harya gaza cin abinci, Yanzu bari na shirya miki breakfast ɗinsa ki kai masa da sauri saboda nasan dole ya tashi da yunwa,'    Sehrish ta amsa mata da Toh, ta tsaya tana jiran ta shirya mata kayan breakfast ɗin nasa, Shiru tayi tana tunano maganar da HAROON ya faɗa mata jiya, akwai abunda ya tsaya mata arai take son fitar dashi "Aunty azmee dan Allah me ake nufi da ZAREN BA KALAR YADIN bane? ta tambaya tana kallom azmee dake shirya abinci cikin warmers asaman kitchen drawers din dake jere,   Ba tare da ta juyo ta kalle ta ba tace "idan aka ce Zaren ba kalar yadin bane, a tunani na ana nufin kamar abunda bai dace da wani ba, a misali kamar ace kina son wani wanda yafi ƙarfin ki nesa ba kusa ba, bari na baki wani misali ma kamar yanzu ace mace tana Son Namiji wanda ya kasance hamshaƙin mai kuɗi ne ko mai mulki ga ilmi ga kyau gashi prominent dae, ke kuma ace kin kasance ƴar talakawa ce koma kina aiki a ƙasan shi baki da duk wani abu daya mallaka da zaku zo ɗaya dashi kin ga kuwa ba sa'an yin ki bane,wannan shi ake nufi da Zaren ba kalar yadin bane......'    Jinjina kai sehrish tayi aranta tana cewa "Wato abunda haroon yake nufi kenan hmmm," Sannan a fili tace "To Aunty azmee me ake nufi da cewa ISKA NA WAHALAR DA MAI KAYAN KARA,!"?   Har sai da azmee ta ɗanyi dariya jin wannan, ɗan gyaran murya tayi kafin tace "Kamar mutun ya yi ta wahalar da kansa akan abunda bazai ta6a samu ba, yanzu in mutun ya sanya kayan kara ana iska shin kayan zasu zauna ne batare da sun tarwatse ba?   Sehrish tace "Eh hakane kuwa,"   "Yawwa ma'anar kenan, mutun yasanya wa ransa abunda bazai ta6a samu ba, kin ga zai tashan wahala ne,"   ta ƙarasa maganar tare da cewa "Zo ki ɗauki breakfast ɗin ki kai masa na kammala," ƙarasawa sehrish tayi ta ɗauki tray ɗin duk jikinta yayi sanyi ga me da abunda Azmee ta fassara mata yanzu, amma taci alwashin duk runtsi duk wuya zata jaraba Soyayyarta Agare shi ba fashi 💔     Fuce wa tayi ta miƙi hanya kamar daga sama taji muryar haroon a kunnanta yana cewa "ƴar Shila barka da safiya fatan kin kwana cikin ƙoshin lpy,    Shiru tayi bata bashi amsa ba, yana tsaye ruƙe da ƙugu daga shi sai gajeran wando ajikinsa, Ci gaba da magana yayi "Dole kisha ƙamshi baby, an fa samu Freedom dole a hura hanci, hallau dae bari na ƙara tunasar miki, shisshigi da kutsi ba zai kai ki ga cin nasara ba akan wancan Babban kayan da ki ke hari, ke bama shi ba ko junaid dana ga kina shisshige mawa wlh yafi ƙarfin ajin ki, kwara ma ni zan iya yin maneji na lalla6a ki mu rufa wa juna asiri, ke ƴar aiki ni kuma ɗan masu gida Fantsararre,,,   takaici ya hana ta cewa komai wuce wa kawai tayi upstairs,    Tun da ta nufi part ɗinsa take jin tashin ƙamshi ya gauraye ko'ina Har cikin hancin ta direct masu daɗin ƙamshi,    Bayan tayi sallama tashi ga, babu kowa a palor ɗinsa ƙarasawa tayi ta ajiye masa tray ɗin asaman table ɗinsa, tsayawa ta ɗanyi don ta jira fitowarsa,   Tana cikin tsayuwar nan wayarsa da ya bari asaman hannun Sofa ta soma ringing da ƙarfi har sai da sehrish ta ɗan yi firgit da ido, kai idonta tayi a inda wayar take hada sa hannu tana dafe kirjinta, matsawa tayi a ƙoƙarinta na ta ɗauki wayar takai masa,   Adai-dai time ɗin yafito cikin sauri Don ya ɗauki wayar saboda Kira ne mai mahimmanci agare Sa yasan dashi    Jin motsin mutun yasa sehrish ɗagowa takai ido a kansa, aikuwa a tsananin firgice ta ɗanyi wani sauti tare da yin Hanzarin juyawa cikin tsananin farga ba,    Sam baisan da mutun ba, fitowa yayi daga shi sai ɗan pant a jikinsa gaba ɗaya halittar jikinsa ta bayyana,    bin bayan ta yayi da kallo mamakin sa ganin yarda ta razana kamar taga wani dodo, wuce wa yayi yasa hannu ya ɗauki wayarsa sannan ya shige ciki yana amsa kiran a kunnansa,   Juyo wa sehrish Tayi jin alamar ya koma ciki sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, gaba ɗaya duk ta firgice ta gigice ta tsorata da yanayin da tagansa,*💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* _🔥The Father Of Soldiers🔥_ Story & Written By *BOSS BATURE* •·•·•·•·•·•·•·•·•·••?*Episode 13-14*•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•? *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(?)______________ Tsawa tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, after some minutes sai gashi ya fito jikinsa sanye da jeans da t-shirt, hannunsa ruƙe da wayarsa ya samu wuri ya zauna saman Sofa, cikin sauri sehrish ta gaishe shi "Barka da safiya, fatan ka tashi lafiya," a tunaninta bazai amsa ba amma sai ji tayi yace "Alhamdulillah Am well," murmushi ta ɗan saki, kafin ta shiga haɗa masa Tea a cup mai ɗan xafi ta tura masa agabansa, hannu yasa ya ɗauka yakai bakinsa yana kur6arsa a hankali, ci gaba da saving ɗinsa sehrish tayi, kamar daga sama taji yace "Meyasa jiya ba'a kawo min fruits dana buƙata ba"!? Murya na rawa sehrish tace "na same ka kana bacci ne lokacin dana kawo maka," ta ƙarasa maganar tana kallon fine face ɗinsa, Bayan wasu mintina ya kuma cewa "daga yanzu inaso a rinƙa kawo min Coffee or Tea wit fruits around 12 pm,"   Cikin hanzari ta amsa mashi da cewa "Insha Allah," jinjina kansa ya ɗanyi yayin da yake ci gaba da cin pancakes ɗin data haɗa masa da Zuma,    tsayawa sehrish tayi tana jiran ya kammala ta zuba mashi wani abun,   Wayarsa dake ajiye a gefensa ta soma ringing cikin sauri takai hannu zata cirar mashi tissue ya goge hannunsa adai-dai lokacin shima ya miƙa hannunsa zai cira karaf suka haɗa hannunsu cikin na juna 😌 zaro ido sehrish tayi cikin tsananin jin tsoro tana ɗan kallonsa,   Shi kuwa bin hannun Yarinyar yayi da kallo sam ba'a yi masa irin haka amma yayi mata Uziri ne saboda da alama batasan ko shi wanene ba, gata kuma ƙaramar yarinya,   "Am sorry,...' sehrish ta furta aɗan tsora ce yayin da ta janye hannunta, shi kuma ya ciri tissue ɗin a natse yace "Don't repeat that mistake again,"   Cikin sauri tace "Insha Allah," goge hannunsa yayi sannan ya ɗauki wayar ya ɗaga kiran tare da karawa a kunnansa, taso taji mai zai ce acikin wayar amma sai dai kash cikin wannan harshen taji yana magana wato Espanol da alama yafi jin yaren sosai ko kuma shi ya taso yana ji,   Zuba mashi ido tayi tana kallon shi tun daga shafaffen cikinsa har zuwa saman wide Chest ɗinsa haɗaɗɗiyar ƙira, maganar haroon ta tuna dayake cewa Zaren ba Kalar yadin bane Iska ce kawai zata wahalar da mai Kayan kara, tabbas kuwa yayi gaskiya amma in ta tuna wannan karin maganar da ake Cewa *DUK KYAN TAKALMI ƘAFA CE ZATA TAKA SHI* sai taji wata irin natsuwa tazo mata, tana tunani tana ci gaba da kallon fuskarsa yadda yake Moving pink lips ɗinsa yana magana tamkar baison yi, da kuma yarda yake faman lumshe sexy blue eyes ɗinsa ba ƙaramin Yanayi yake jefa ta ba, "Allah yasa bada budurwarsa yake waya, koda yake aunty azmee tace baya soyayya, To Allah yasa dai bada mace yake waya ba," ta faɗi acikin zuciyarta saboda ganin yarda yake ta faman lumshe idonsa kamar wanda ke waya da mace cikin shauƙi,   tana cikin yi mashi wannan kallon ƙurullan nata ya kamata, adai dai time ɗin ya ɗan ware idonsa direct suka sauka kan na sehrish dake faman Zuba masa ido tana kallonsa abunda ya tsana arayuwarsa ba, sam bata lura daya kamata ba saboda idonta na akan Sumar kansa, har sai da ya ɗanyi gyaran Murya cikin sauri ta wurga kwayar idonta kan tashi aikuwa har sai da ta ɗan Razana ganin ya aza idonsa acikin nata Unexcepted,    ƴar harara ya wurga mata sannan yace "Stop looking at me, i don't like,' ya faɗi tare da cigaba da yin wayarsa,    Sunnar da kai sehrish tayi cikin jin kunyar Kamatan da yayi tana masa kallon kurulla, amma wannan hararar daya sakar mata ba ƙaramin kashe mata zuciya yayi ba, ya jima yana wayar kafin ya kammala ya ture ta gefensa, sehrish ta cigaba da saving ɗinshi harya kammala cin breakfast ɗin nasa sannan ta tattare komai ta fuce dasu kitchen ta ajiye agefen Kitchen sink yadda in tadawo wankewa kawai zatayi, Daker ta iya fitowa daga kitchen ɗin saboda taga duk sun Hallara suna yin breakfast, tunkarar su tayi gabanta na faɗuwa saboda ganin hada HAROON zaune ga kuma Twins duk suna zazzaune, tunkan ta isa junaid na ganinta yasoma sakin murmushi kamar gonar Auduga, sallama tayi masu suka amsa sannan ta kalli Abbansu wanda keta faman sakar mata murmushi tace "Ina kwana Abba, fatan kun tashi lafiya," Abban nasu yace "Alhamdulillah My Only daughter, yanzu nake tambayar azmee take cemun kin shiga kaiwa Babban yayanku Abinci," "Eh hakane," ta bashi amsa sannan ta juya ta kalli sauran ta gaishe dasu duk suka yi tsit sai kanal Yusif daya ce "Ae nayi tunanin bazaki gaishe da yayyen naki ba, yanzun nan nayi fushi dake,"    Murmushi sehrish tasaki tana mai mamankin hali irin na kanal Yusuf sam bakamar na sauran ba,   "Samu wuri ki zauna mana," Abbansu ya umarce ta kujera taja ta zauna zuciyarta na ɗar ɗar, tana a jerin inda Abbansu yake gefensa junaid daga shi sai ita, a ɗayan side ɗinta kuwa haroon ne tabbas tasan dole ya hantare ta, ga kuma AYAAN Da JAHAN da take facing ɗinsu duk ta tsargu saboda tasan halinsu suna jere tare da kanal yusif,   azmee da kanta tayi saving ɗinta acikin plate ta buɗe saving dish ta zuba mata Chicken pper soup Sannan ta haɗa mata da Cofee acikin Cup? Sehrish ta kalli azmee tare da cewa "nagode aunty amzee" hararar ta amzee tayi alamar cewa bata son godiyar, ..a hankali take kurbar coffee ɗinta duk da kermar da hannunta ke yi, muryar haroon taji a ƙunnanta yayi ƙasa ƙasa da Voice ɗinsa don kada wani yaji yace"Su acici mala'ikun tauna, an fa samu wurin zama, to adai ci ahankali kar a shaƙe," banza tayi dashi batace komai ba, amma sam tarasa cin chicken ɗin dake agabanta shaƙe cikin plate,   Sanyayyiyar muryar junaid ce ta ratsa kunnanta da cewa "Sehrish ya akai naga yanayin ki ya canza? ko breakfast ɗinki baki fara ci ba,"    tace "bakomai junaid kawai bana jin daɗi ne, inaji kamar na tashi na tafi ɗaki kawai,"   cikin sauri junaid yace "a'a reesh pls kada kiyi haka ki daure kawai ki ci, kinji My sister," murmushi tasaki jin sunan da junaid ya kira ta dashi, ɗan ɗagowa tayi da idonta karaf suka sauka kan na Jahaan da Ayaan da suka ɗago atare, shiru tayi tana ɗan kallonsu, atare suka yatsina fuska suna yi mata wani irin kallon Tara saura kwata, ƙasa da murya Jahan yayi tare da cewa "Ayaan kalli yarda junaid ke fira da wancan yarinyar, shi junaid kowa nasa ne, baya tsoran mutane sai sunyi masa Illah," yayi maganar cikin nuna damuwa    Ayaan yace "ba kai kaɗai ba jahaan, ni ma abun na damuna wlh, shiru kawai nayi amma na lura da yadda suke shiri, bazan ƙyalesa ba dole na buga masa warning Allah,    Jahan yace "gasky kam, janyo shi yakamata muyi a ɗakin mu, muja masa kunne tunda shi shashasha ne kowacce baƙuwar fuska shige mata yake yi, sai kace ba Jinin mu ba," Ayaan yace "kwarai kuwa, ae shi junaid da kake ganinsa half cast ne, ruwan Abba ne dana Mommyn mu ya ɗauko, mu kuma ruwan mommy ne kawai ajikin mu, banda na daddy,"  Wannan maganar ta Ayaan tasa kanal yusuf fashe wa da dariya ashe duk yana jin firar tasu saboda shine kusa dasu a jere, ɗagowa su kayi suna kallonsa dukansu hada Abban nasu da junaid da sehrish da azmeee, Abban nasu yace "in ce dai ko lafiya? Kanal yusif yace "babu komai Abba, gasu nan su Ayaan da jahan ne suke fira su faɗa maka abunda suke cewa ka ji,"    tunkan Abbansu ya tambayesu suka haɗa baki wurin cewa "Babu komai Abba, firar wani film muke yi,'   girgiza kai kawai Abbansu yayi, Haroon kuwa cewa yayi "Allah yayi wa ɗan iska uwa koda ta kara ce," ya faɗi yana kallonsu salon jan faɗa kawai, Babu wanda ya tanka masa miƙewa Ayaan da jahan su kayi tare da yiwa Abban su sallama suka fuce,  💪  Fito wa marshal Omar yayi daga upstairs yana saukowa down jikinsa sanye da jallabiya ash colour sai faman ƙamshi yake yi, tunkaro su yayi Abbansu na ganinsa yafara fara'a yana cewa "Omar sai yanzu ka tashi? tun ɗazu nake ta faman waige-waige naga ta ina zaka 6ullo,    Ɗan ƙayataccen murmushi yasaki tare da cewa "Gm Abba ina fatan ka tashi cikin ƙoshin lafiya,"   "Alhamdulillah Son, Samu wuri ka zauna na baka abinci a baki," cikin zolaya yayi maganar su kuwa sauran dariya su kayi, ɗagowa OMAR yayi tare da gaishe da Azmee ta amsa mashi, sannan su kuma Su kanl yusif da junaid suka shiga gaishe shi, Haroon yace "Barka da fitowa Damusa mai maganin ƙananun ƴan iska," ɗan harararsa Omar yayi tare da cewa "Zaka fara wannan tsokanar taka ko? To ka shiga taitayin ka ko yanzun nan na saita maka waɗannan haƙoran naka, don naga ba'a jere suke ba,' shima da zolaya yayi maganar ayayin da yake zama azmee kuma ta soma zuba masa breakfast ɗinsa,    Mayar da idonsa yayi kan JUNAID dake ta faman sakar masa murmushi yace "My shagwa6a boy, irin wannan kallon haka da kake mun ko kana buƙatar wani abu ne?   Cikin jin kunya junaid yace "Babu komai ya Omar kawai inaso inta kallon ka ne, aduk lokacin danayi kewarka,"   Murmushi Omar yayi kafin yace "Ae da ka sani jiya ka shigo bedroom ɗina mun kwana tare,"   Junaid yace "ae Abba bazai bari ba, Kishi yake yi," gaba ɗayansu suka fashe da dariya jin abunda junaid yace,    Abban nasu kuwa murmushi kawai yayi tare da ɗan jinjina kai yana kallon junaid ɗin, Haroon yace "Ae na Lura da yadda Abban mu ke ji dakai, kamar kai kaɗai ya haifa bayason komai ya same ka,'    Junaid yace "Yaya haroon ka ta6a ganin inda mutun ke wasa da bugun zuciyarsa? to aeni zuciyar Abban tamu ce gaba ɗaya shiyasa Yafi sona," yayi maganar wit proud,   ta6e baki Haroon yayi yana kallonsa, MARSHAL OMAR yace "Ae bama Abban mu kaɗai ba Haroon, Junaid farin cikin kowan nan mune acikin gidan nan, bamu son wani abu ya same shi domin tamkar mu yasha fa, JUNAID BUGUN ZUCIYAR FAMILY ɗin mune gaba ɗaya,"   Kanal yusif ya ƙara da cewa"Maganarka gaskiya Ce Yaya OMAR, Ni kaina aduk lokacin dana aza idona akan na baby junaid wlh farin ciki ne ke ziyarta ta, kuma aduk lokacin da wani ya 6ata mun rai junaid ne ke lallashi na da kalaman sa masu kwantar da hankali, tabbas shi Yaro ne amma yana da baiwar iya sarrafa harshe wurin farantawa mutane," Har cikin zuciyarsa yake wannan bayanin, junaid kuwa farin ciki ya hanasa idasa shan cornflakes ɗin dake agabansa, haka zalika Abbansu murmushi ne a fuskarsa saboda bai da Burin daya wuce yaga ana yabon Jininsa, kuma ma Junaid,   Haroon kuwa tuni zuciyarsa tayi baƙiƙƙirin ji yayi bazai iya ci gaba da zama ba, don haka da hanzari ya miƙe tare da fuce wa daga babban falon gaba ɗaya, sam ba wanda ya damu dashi bare su son halin dayake ciki,   Duk fa wannan abun dake faruwa a kunnan Sehrish tana sauraron su, sam tagaza gaishe da Marshal Omar tsoran ta kada ya ƙi amincewa da ita duk da ta lura bazaiyi Tsauri ba,   Sai da tabari duk sun natsu wuri ya ɗanyi tsit sannan ta ɗanyi gyaran Murya tare da cewa "YAYA OMAR ina kwana,"     Jin Muryar mace yasa shi saurin ɗagowa yaga wacece karaf fararen idanuwansa suka sauka akan na SEHRISH, ae baisan lokacin da ya fesar da Tea ɗin daya kur6a abakinsa ba, hankali atashe yake kallonta, Ajiye cup ɗin dake hannunsa  yayi tare da miƙewa tsaye idonsa akan na sehrish wadda ta gama tsorata dashi ganin yadda ya firgita da ganinta kamar yaga wata ALJANA,  tuni jikin sehrish ya soma kerma, ita kanta azmee ta tsorata da ganin reaction ɗin Omar akan Sehrish haka zalika Abbansu kanal yusif da junaid duk mama ki ya ɗaure musu kai   Nuna ta da hannu Marshal Omar yayai tare da cewa "Keeeee !!!!!!!!!! " gaba ɗaya ya razana da ganin yarinyar, ganin haka yasa kowannan su ya tashi tsaye suna kallonsa, Abbansu yace "Omar meya faru ne? Na manta ban faɗa maka ba game da yarinyar nan ba, ƴa Ce Allah yabani daga sama.... .kallonsa Omar yayi a ruɗe kafin ya mayar da idonsa kan Sehrish wadda tuni idonta sun cuccuko da kwalla saboda tashin hankali,    da hanzari OMAR ya bar dining ɗin yayi saurin haye wa upstairs part ɗinsa, zuciyarsa a cunkushe sam yagaza gane ma Idonsa dayake yi masa Gizan Fuskar Hosana da Jahad a fuskar wannan yarinyar daya gani a yanzu,    Bedroom ɗinsa ya shiga hannu yasa ya ɗauki wayarsa daya ajiye asaman pillow, cikin hanzari ya daddana layin aunty babba ya buga mata Call, kusan 3 times yana kira bata shiga, numbar Hafsat ya kira itama tana ringing ba'a ɗagawa, Wurgi yayi da wayar saman gadonsa, tsayawa yayi yana faman sauke ajiyar zuciya, hannu yasa ya dafe kansa tamkar wanda ke fama da ciwon kai, tabbas ransa na basa cewa Ba fuskarsu hosana bace a fuskar yarinyar, ya sawa ransa cewa tsananin Son da yake yi ma yaran ce da ƙaunar da yake yi musu da kuma kewarsu da yayi ya sanya Fuskarsu keyi mashi gizau afuskar yarinyar daya gani ayanzu, tabbas Omar yayi Confusion ɗin kansa, ya rikita tunaninsa bazai ta6a yarda da abunda idonsa ke nuna masa ba akan Waccan Yarinyar................    Ajiyar zuciya yasaki aransa yana ƙara jin cewa bai kyauta musu ba da baije ya dubo su, amma ya shirya zuwa gobe domin ya duba su,   Yana gama wannan tunanin ya dawo Downstairs da sauri ya sauko a lokacin Sehrish harta gudu zuwa ɗakinta saboda ta tsorata,   Abbansu na ganinsa yace "Omar wai lafiya meya faru ne? Naga duk ka rikice lokaci ɗaya ko don saboda wannan yarinyar ne da ka gani yanzu,"   Zama Omar yayi yana cewa "No ba haka bane Abba just there's something that confused me but am ok now,"   Ajiyar zuciya Azmee tasaki jin yace babu komai, ci gaba da yin breakfast ɗinsa yayi anatse but still his brain was confused, Zuwa wani lokaci kowa ya Kammala breakfast ɗinsa sai daga bisani Sehrish ta fito suka shiga gyara gidan ita da azmee,        ______________________________________________Farkawa hosana tayi da wata irin matsananciyar yunwa don hada kukan ta dama ita bata da jumurin yunwa ko kaɗan, hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba ganin yarda hosana ke ta faman rusa kuka gashi sai faman lallashinta takeyi amma sam taƙi yin shiru sai ta runƙa cewa "baki ji yadda nake ji bane, babu komai acikina kamar zan mutu," runtse ido jahad tayi sam tarasa abunyi, yanke shawara tayi kawai tafita waje taga ko zata samo mata abinci, tun da taga akwai visitors dake zuwa wurin marasa lafiya wata'kil ko Allah ya haɗa ta dana gari su sam mata abinci taba Hosana, tashi tayi cikin sauri tana cewa "Hosana ki jira dan Allah ki daina kukan nan, yanzun nan zan dawo," shiru hosana tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, fita jahad tayi tana faman zarya a asibitin wurin nema musu abincin da zasu ci, taimako yayi ƙaranci a arayuwar nan domin kuwa duk wanda jahad ta tunkara da niyar ya taimaka musu sai suce suma bazai ishe su ba, ga abinci nan tana gani haje-haje agaban wasu sun baje suna ci amma tarasa wanda zai taimaka musu koda da rabin plate ɗaya ne,    A ƙarshe da ta gaji da yawon neman taimakon abinci sai ta samu wuri abakin wata bishiya ta zuƙunna tare da kifa kanta tana faman shesshekar kuka, babban tashin hankalinta yarda zata tunkari hosana tace mata bata samo masu komai ba, 😥 tana cikin wannan zuƙunnan Motar hafsat tashigo asibitin da gudu tayi parking ɗinta a harabar ajiye motocinsu, fito wa tayi fess da ita tayi wanka ta canza kayan jikinta yanzu tsadaddiyar atampha ce riga da skirt ajikinta sun bi shape ɗin jikinta very tight, ta ɗaure kanta da ɗan kwalin sannan ta yafa veil a shoulder ɗinta, ƙarasawa tayi ta buɗe back seat ɗin Motar hannu takai ciki ta ɗauko kwando mai ɗauke da kayan abincin da tazo masu dashi, bayan ta rufe motar ta wuce ciki sam bata lura da Jahad ba, haka itama jahad bata ɗago ba balle taganta,.    tana ƙokarin shiga cikin ɗakin da aka kwantar da hosana dr yafito suka ci karo, ganin ta yasa ya saki fara'a yana cewa" ke ce mai kula da wannan patient ɗin ko"?   Hafsat tace "Yeah its me,"   Dr yace "yawwa tun dazu take faman kukan yunwa gashi naga ba kowa tare da ita, amma tun da kin zo yakamata ki kula da ita, sannan idan ta kammala cin abincin akwai magungunanta dana ajiye wanda za'a bata,"    hafsat ta amsa mashi da cewa "Shikenan dr ngde ssae," tana faɗin hakan ta wuce ciki shi kuma ya nufi cikin asibitin,    Samun hosana tayi tayi kukan tayi mai isarta har ta gaji, tana zaune saman gadon ta kife kanta saman guiwowinta, jin muryar hafsat yasa ta ɗagowa cikin sauri,   Ae tana ganinta ɗauke da food stuffs a basket nan take jikinta ya soma rawa kaf-kaf kamar kura taga nama,    Da murmushi hafsat ta isa ta zauna gefen gadon kusa da Hosana tana cewa "Ya jikin naki"? Murya na rawa Hosana tace"da sauƙi sosai" ita burinta tafara zuba ma cikin ta abinci,   Ajiye basket ɗin hafsat tayi ƙasa, sannan tasanya hannunta ta curo flask mai ɗauke da haɗaɗɗen ruwan tea ta ajiye sa, Cup ta curo guda biyu ne a haɗe, ɗaya ta ɗauka ta bude flask ɗin ta tsiyaya mata shi sannan ta zuzzuba mata madara da bornvita aciki har sai da yayi kauri, sannan ta miƙa ma hosana, kar6a tayi takai bakinta tana sha da hanzari har wani sauti maƙoshinta keyi kwat-kwat , kusan sau 3 tana shanye wa hafsat na ƙara mata, bayan ta kammala ta ciro kula mai ɗauke da Chips haɗi na musamman, ta zuba mata a plate, miƙa mata tayi tana cewa "ki ci a hankali saboda ciwon ki," hosana ta amsa da "toh" Turawa kawai take yi abaki kamar zata haɗa da plate ɗin duka, bayan tagama dashi hafsat ta zuba mata fruits a plate ta bata, shima tashiga sha kamar kamar me,    "Ina Ƴar uwarki take ne ban ganta ba"? Hafsat ta tambaya yayin da take kallon hosana,.    Hosana tace "tun ɗazu ta fita tace na daina kukan yunwa na jira ta, har yanzu bata dawo ba,"   Murmushi hafsat tasaki tare da cewa "Nasan bai wuci taje nema muku abunda zaku ci bane, May be tayi tunanin na tafi nabarku ne,"   suna cikin magana jahad ta turo ƙopar a galabaice take tafiya saboda tsabagen yunwa, ƙafafunta har harɗewa suke yi tana tafiya kamar wadda tasha Codine,     shigowa tayi tana faɗin"hosana sai dai kiyi haƙuri wlh bansamu komai .........' ganin hafsat yasa ta dakatawa da maganar cikin mamaki take kallon su, hannu tasanya tana murza idonta don ta tabbatar wa kanta cewa ba mafarki take yi ba, sakin hannunta tayi tana ƙare masu kallo, Expecially hosana data gani sai faman cusa fruits takeyi abakinta wanda hafsat ta zuba mata, Wani irin farin ciki ne ya cika jahad har batasan lokacin da ta fashe da kuka ba Don tsabar murna,   tashi hafsat tayi ta ruƙo hannunta tana cewa "Kukan ya isa haka, tun da gani na zo ko? Halan kinyi tunanin na gudu ne nabarku shiyasa kika fita nema muku abinci"? ta tambaya tana kallon jahad dake faman shesshekar kuka tace"Nayi tunanin kin tafi kin barmu ne shiyasa na fita, ashe zaki dawo,".    ɗan murmushi hafsat tasaki tare da cewa "Am so sorry nayi laifi ban sanar muku ba, da asuba na tafi gida, nayi sallah bacci ya kwashe ni without my knowing bayan na tashi ne kuma na wuce kitchen na shirya muku breakfast dana kammala shine nayi wanka na fito,"   bayani take yi jahad na kallonta tsananin mamaki ne yakamata ganin yadda lokaci guda Hafsat ta canza musu gaba ɗaya tamkar ba ita ba, tazama wata mutuniyar kirki lokaci guda ANYA?   jan hannunta hafsat tayi ta zaunar da ita gefen hosana sannan tashiga saving ɗinta abincin tare da miƙa mata, sannan ta haɗa mata tea itama, bayan ta kammala ta samu wuri saman plastic chair ɗin dake facing gadon da suke tana kallonsu,   A hankali Jahad ke kurbar tea ɗin tana ɗan kallonta, bakomai take jin tsoro ba fa ce kada ace Hafsat tasanya musu POISON acikin abincin da takawo su,tun da dama tasan sarai neman hanyar da zasu kawar dasu suke yi, kuma wannan ce hanya mafi sauƙi, yadda hafsat ɗin ke kallonta ido cikin Ido yasa Jahad ƙara jin wani irin Tsoro aranta nan take hannunta ya shiga yin kerma kaf!kaf!kaf! 😳😳😳 Wani shu'umin Murmushi Hafsat tasa ki tana cewa "nasan mai ki ke tunani JAHAD, tabbas abunda kike tunani gaskiya ne, POISON nasanya muku a abincin saboda wannan ce hanya mafi sauƙi da zamu kawar da ku acikin arayuwarmu, kuma zaku huta da wahalar zaman duniya,"    Hankali atashe Jahad ta Zazzare ido waje jikinta na kerma tace "POISON!!!!!!!!!!!!!! "*🪩🪩🪩🪩🪩ABBAN SOJOJI🪩🪩🪩* •·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·? *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·? *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•?15-16•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•? ____________(?)____________ Story & Written by *BOSS BATURE* Firgit jahad tayi daga zurfin tunanun da ta shiga tana faman sauke ajiyar zuciya, ɗagowa ta ɗanyi ta kalli hafsat samunta tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace "Tun ɗazu na lura da kallon da kike yi mun Jahad, na menene? ɗan sunnar dakai jahad tayi tace "Babu komai kawai ina mamakin yarda kika canza mana ne ba kamar da ba, kin nuna tausayi agare mu, ba muyi tunanin haka ba, Hafsat tace "Nima kaina nayi mamakin yarda na canza wurin nuna muku tausayi, bayan ba hali na bane gaskiya, tun ina yarinya bani da tausayi ko kaɗan kuma bana son mutun mai tausayi, ban sani ba ko kunayin addu'a ne shiyasa Allah ya kawo muku sauƙi ta 6angare na.....' ta ƙare maganar tana kallonsu, Jinjina kai Jahad tayi jin abunda hafsat tace, Lallai ne Allah ne ya amshi addu'arsu ya kawo musu sauƙi ta wurin hafsat, Ajiyar zuciya Jahad tasa ki tare da juyawa ta kalli hosana wadda ke zaune wuri da ido, taci ta ƙoshi tayi hani'an, Hafsat tace "Ga maganin da dr yace abaki, tun da kin kammala cin abincin bari na baki ki sha, sannan zuwa anjima insha Allah zamu koma gida," jahad tace "Allah ya kaimu lafiya," "Ameen," ta amsa mata sannan tasanya hannu ta ɗauki ledar maganin, ta shi ga fiddo su tana duba su, kafin tasanya hannu cikin basket ɗin da tazo dashi ta ɗauko robar ruwa, ta buɗe ta bayan ta ciro maganin ta miƙa ma hosana tare da ruwan tana kar6a tana sha, haƙiƙi su Hosana da jahad ba ƙaramin kwanciyar hankali suka samu ba, saboda sun ga tausayinsu ƙarara a fuskar Hafsat kuma da alamun zasu samu sauƙi ta 6angarenta, *Shin Ya maganar matar da ta ba Hafsat miliyan shidda don ta zubar mata dasu Jahad? Kuna ganin zata fasa wannan aikin ko kuwa*? 😳 *AUNTY BABBA* 😈 Sam ta gaza samun natsuwa hankalin ta ba ƙaramin tashi yayi ba ganin yarda hafsat ta fara damuwa da twins ɗin da OMAR ya kawo, tabbas dole ta ɗauki mataki akan hakan, kuma haryanzu tana akan bakanta na sai tasa an zubar mata dasu Hosana da Jahad, *Tabbas dole na ɗauki mataki akan hakan* tayi maganar tare da dakatawa daga zirga zirgar da takeyi acikin ɗakin nata, fitowarta kenan daga wanka, ta zumbula doguwar rigar Buba ta Material, hannu takai ta ɗauki wayarta dake ajiye saman stool dake agaban mirror, cikin hanzari ta shiga contact ta dannawa wata number kira wadda tayi saving ɗinta da *BABA ALAMU* Nan da nan kiran yashiga wayar ta soma ringing zuwa wani lokaci mai numbar data kira ya amsa wayar, Cikin sauri tace "Assalamu Alaikum," daga can 6angare wata murya kakkausa ta gawurtattun ƴan iska ta amsa mata da cewa,"Hajiya Laila manyan gari, ashe kuna neman mutane? Ae nayi tunanin daga in da amfanin mutun ya ƙare a wurinki yazama shara......' dakatar dashi Aunty Babba tayi da cewa "Baba Alamu ! mu aje wannan gefe, wlh ina cikin tsananin damuwa ne, tunawa dakai yasanya na kira ka domin nasan kai kaɗai ne zaka iya yi mun wannan aikin.....' ta ɗan dakata tana jiran amsar da zai bata , Baba Alamu yace "Ae dama ke ba'ki ta6a neman mutun sai in buƙatarki ta taso, tun da ansan muna da amfani ae a rinƙa ɗan kiran mu ana bamu hasafi don tafiya tayi kyau ko?, yanzu dai faɗa mun me kike so in aiwatar kawai ! Wa kike so akashe miki har lahira? Ko wa kike so In Naƙasa Miki kasusuwansa ajefar bayan Duniya?😳 Dariya aunty babba tayi cikin jin daɗi tace "Yawwa Mutumina, dama nasan kaine kawai zaka iya share mun hawaye na, abunda ke faruwa wani ƙanin Mijina ne wlh ya tsinto wasu ƴan mata tagwaye ya kawomin a gida na, na tsani yaran nan ko ganin su bana son yi, saboda zasu tarwatsamun target ɗina abunda nakeso kawai so nake kazo ka ɗauke su Ka fitar mun dasu daga gidan nan ka kai su can bayan gari ka jefar mun dasu Can cikin ƙurmin daji wanda zasu rikice su gaza gane hanyar da zasu fita daga cikin shi,"😳 tamkar tana agabansa haka take masa bayani tana faman cizon la66a, 😠 fashe wa da dariya baba Alamu yayi daga bisani ya tsagaita yace "Ƙaramin aiki kenan, ni nama yi tunanin wani za'a kashe maki ne yanzun nan mu kai shege lahira, amma tun da wannan ne kada ki samu damuwa, yanzun dai bana nan kinsan naje lagos ƙarƙashin gada amma maƙo mai zuwa bi iznil lahi, aikin ki zai kammalu, ƴan Canji kawai zaki tanada " Aunty Babba tace "in dai wannan ne an gama, zanyi maka biya na musamman babban kaso mai tsoka, Baba Alamu yace "Shikenan sai kin jini, da zarar na dira kaduna zan zo da rugwagwar mota ta na kwashe Maki Sharar azubar abayan gari,'😂 Jinjina kai aunty babba tayi har wani sauke ajiyar zuciya take yi jin burinta zai cika na kawar da su Jahad, Sun jima suna waya da baba Alamu kafin daga bisa sukayi sallama, ta ajiye wayar saman mirror tana cewa "Yanzu abunda ya rage mun shine, na dakatar da Omar don nasan zai iya zuwa yace zai tafi dasu na lura da hakan I ave to do something ❗? .........!👷wani irin shu'umin murmushi tasa ki, saboda plan ɗin da ta tsara, ********* Sai wuraren bayan Sallar La'asar sannan dr yayi discharge ɗinsu daga asibitin kamar yadda hafsat ta buƙata don bata son zaman su a asibitin gudun kada Omar yayi musu Dirar Mikiya, duk da dr yaso ya ƙara ma hosana Jini amma ta hana hakan sai dai tayi alƙawarin cewa zata mai do ta asibitin Next time, A hankali take driving ɗinsu acikin motar, hosana na'a a back seat kwance sai faman sharar bacci take yi, yayin da jahad ke agefen hafsat dake driving, adai-dai wani Store ta tsaya da motar, sannan ta kalli jahad tace "Ki kula yanzu zan dawo," Jahad ta amsa da cewa "Toh Aunty" Shiga cikin wurin tayi bayan wasu mintuna tafito hannunta ruƙe da leda, ta buɗe motar ta shiga miƙa ma jahad ledar tayi tace "Ruƙe wannan a wurin ki," Amsa jahad tayi ta ƙanƙame ledar a hannunta, sannan hafsat taja motar suka tafi gida kai tsaye, Bayan tayi parking suka fito daga motar daker jahad tasamu hosana tafarka ta ruƙe hannunta suka nufi ciki hafsat na biye dasu, sai faman jin fargabar haɗuwa da Aunty babba suke yi, Aikuwa suna shiga suka same ta zaune a babban falon saman sofa tana faman danna wayarta, tana ganinsu ta miƙe tsaye tare da cewa "Sannun ku da dawowa, Allah sarki hosana da jahad kuyi haƙuri ban samu damar zuwa asibiti ba na dubo ku, Ya jikin naku"? ta faɗi cikin nuna tausayin su, ai ba su jahad da hosana ba hatta hafsat tayi mamakin jin abunda Momyn nata tace lokaci guda ta canza tamkar ba ita ba, tsayawa sukayi suna kallonta baki asake, Ganin hakan yasa aunty babba ƙarasawa ta ruƙo hannun kowannan su , sannan cikin sanyin murya ta wanda yayi nadama tace "Haƙiƙa nasan na cutar daku sosai, Allah ma ba zai yafe mun ba, tabbas jiki na yayi sanyi, nayi danasanin abun da na aikata muku dan Allah kuyi haƙuri ku yafe mun........' Hawaye ne suka soma saukowa daga idon aunty babba fuskarta duk a yamutse tana kallonsu, cikin mamaki hafsat tace "Shin mafarki nake ko gaske!? Mom are u serious about what are u sanying? Ko dai kin sha wani abu ne bayan na fita? kece dakan ki kike danasani hada neman gafara a wurinsa? ɗago ido aunty babba tayi tare da kallon hafsat tace "Shin ni ba mutun bace kamar kowa daba zanyi laifi na nemi gafara ba"? na zauna nayi wani tunani menene riba ta idan na cuci waɗannan bayin Allan? Allah fa dakansa ya haramta ma kansa zalunci kuma ya haramta shi atsakanin mu, kuma yace kada muyi zalunci, amma ni na kansance mai son zuciya..........' Sam ta kasa ƙarasa maganar saboda shessheƙar kukan da tafara, juyawa hafsat tayi ta kalli jahad yayin da ita kuma jahad idonta na akan Hosana wadda ke kallonta, gaba ɗayansu mamaki ne ke ɗawainiya dasu, shin taya zasu gasgata tuban da Mommyn hafsat tayi? Anya ba wata ƙullalliya bace? "Naji kunyi shiru baza ku yafe mun bane? In har baku yafe mun ba bana ji zan iya bacci adaren nan," Cikin sauri Jahad da hosana suka haɗa baki wurin cewa "Aunty mun yafe miki, Allah ya yafe mana gaba ɗaya," Murmushi Aunty babba ta saki tare da sa hannu ta haɗa su duka ta rungumesu ajikinta, tana faman ci gaba da basu haƙuri akan kuskuren da tayi masu na jibgarsu da tayi, Jikinsu duk yayi mugun sanyi, gaba ɗaya kwalwarsu ta rikice sun rasa gane dawa zasu YARDA? SHIN HAFSAT ko MOMMYNSU? Taya hakan zaiyiyu ace lokaci guda sun canza musu izuwa mutanen kirki masu tausayin su? Bayan aunty babba ta janye su daga jikinta ta mayar da idonta kan na hafsat tace "daughter daga yau inaso ki ɗauke su tamkar ƙannen ki, ni kuma insha Allah zan ɗauke su tamkar nice na haife su, zan basu duk wata kula daya dace uwa tabawa ya'yanta, " Murmushi hafsat tasaki tare da cewa "Insha Allah mommy as from now hosana da jahad sun zama ƴan gida, zasuyi rayuwar ƴanci acikin gidan nan, babu wanda zai sake cutar dasu acikin mu," Jinjina kai aunty babba tayi sannan tace "ina so daga yanzu su koma ɗakin Ladi mai aikin mu da kwana," Hafsat tace "a'a Mommy, mattress ce kawai acikin ɗakin, gaskiya ni nafison su dawo bedroom ɗina da kwana yadda zanfi basu kulawa," Aunty babba tace "hakan ma yayi, yanzu yakamata ku shiga ciki ku huta, sannan hafsat ki taimaka ma hosana tayi wanka da ruwa mai ɗumi ko taji daɗin jikinta, Hafsat tace "insha Allah mommy," sannan ta mayar da idonta kansu hosana tace "mu shiga ciki," hannun su cikin na juna suka bi bayan hafsat har izuwa cikin bedroom ɗinta, Da taimakon hafsat hosana tayi wanka ta canza kayan jikinta izuwa doguwar riga mara nauyi, bayan ta kammala hayewa kawai tayi saman gadon hafsat, tana jiran zuwan jahad wadda ta shiga toilet yin wanka itama, Ajiyar zuciya kawai hosana ke saki amma tana jin fargabar canjin da su ka gani wurin hafsat da Mommynta, sam bata amince dasu ba, kuma taci Alwashin muddin YA OMAR yazo ƙafarta ƙafarshi sai ta bishi, 😠 **********SEHRISH************** A gajiye ta shiga cikin bedroom ɗinta bayan sun kammala gyare-gyaren gidan, sai lokacin tasamu damar yin wanka tare da alwala tafito ɗaure da towel, agaban dressing mirror ta zauna saman kujera tana Shafa mai ajikinta, bayan ta kammala ta feshe jikinta da turare, sannan ta koma ta buɗe wardrobe ɗin kayanta, ta ɗauko dogon skirt brown color ta zura sannan ta sanya t-shirt fara, daga nan ta zura hijab tare da shimfiɗa carpet tayi sallah anatse, tun kafin ta kammala azmee ta turo ƙopar ɗakin ta shigo, wuri ta samu gefen gadonta ta xauna, bayan sehrish ta kammala sallar ta naɗe dardumar ta mayar da ita cikin wardrobe tare da hijabin, sannan ta juya da fara'a tana gaishe da azmee "Ina yini aunty azmee," Azmee tace "lafiya lou sehrish, zo ki zauna," Ƙarasawa tayi ta samu wuri kusa da ita ta zauna, azmeee tace "sehrish wai ina wayarki take ne? Na lura tun ranar dana baki ita, ban sake ganinta a hannunki ba, kodai baki so ne? zuru sehrish tayi don ita tuni ta manta da zancen wata waya, kuma ba kowa bane yaja mata hakan ba face haroon, shine silar damuwar da tashiga harta manta in da ta jefe wayar "Ina sauraron ki ina wayar"? Azmee ta ƙara nanata mata, cikin en ina sehrish tace "Aunty azmee tun....ranar...da...kika...ban...ita..na manta inda na ajiye...ta,' ta ƙarasa maganar tana ɗan kallonta azmee tace "Sehrish kenan kin cika shiririta yanzu wayar mai tsada ita kika 6atar? To ina so ki nemo ta yau ɗin nan duk inda take, in ma saman ceilling kika turata ki hau saman ki fiddo ta, Ki kawo min ɗaki na ina jiranki,!" tana faɗin hakan ta tashi ta fuce........ tafa hannu sehrish ta shiga yi tana tunanin ta ina zata fara neman wayar, ita kanta abuƙace take da wayar ko don ta rinƙa ɗebe kewar zama ita kaɗai aɗaki, Tashi tayi cikin ƙanƙanin lokaci ta hargitsa ɗakin wurin neman wayarta, duk ta zabure har ƙarƙashin gado ta leƙa, ta bincika cikin laundry basket ɗinta, gaba ɗaya ta zazzago kayan wankinta dake cikinsa babu komai, agajiye ta mayar da kayan, zarya tashiga yi tana tunanin ina ta wurgar da ita, ci gaba da neman wayar tayi, a ƙarshe tayi deciding zuwa ɗakin junaid ta roƙesa ya kira layin wayar ko tayi ringing, cikin hanzari ta ɗauki mayafinta dake ajiye saman bed ɗinta, ta yarfa shi a head ɗinsa, sannan ta fita cikin sauri babu kowa a babban falon direct upstairs ta wuce da ƙarfi take tattaka stairs ɗin ko kallon gabanta batayi burinta kawai ta isa bedroom ɗin junaid,. Kamar daga sama taji ta bugi wani abu da ƙarfi nan take wani irin jiri ya kwashe ta, agigice tasaki wata irin ƙara ganin yarda ta tafi gaba ɗaya zata faɗi amma ina tuni yayi mata wani irin kwakkwaran ruƙo da hannu guda ya tallabo waist ɗinta, Zazzare ido sehrish tayi cikin Jin tsananin tsoro yayin da take faman sauke ajiyar zuciya, gabanta ne ya soma faɗuwa saboda tuna hannun wa take a ruƙe, sam tagaza ɗago ido ta kalle sa, ae tun daga ƙamshin turaren nan nasa ta shaida kowane ne, ɗago da ita yayi ta tsaya da ƙafafunta sannan ya wuce abunshi, juyawa sehrish tayi cikin sauri tana kallonsa ba ƙaramin wanka ya ɗauka, har sai da ya fice daga babban falon sannan ta kawar da idonta sannan ta ƙarasa haye wa upstair ɗin, har time ɗin jikinta wata irin kerma yake yi hannunta na dafe da ƙirjinta, A hankali tayi knocing ƙopar ɗakin junaid tana buga ƙopar a slow saboda zuciyarta dake tariyo mata abunda yafaru yanzun nan, kusan 3 times tana knocking sai daga bisa tajiyo muryar junaid yace "Come in," Ashe door ɗin a buɗe take, tana zura ƙafarta ciki karaf taci ido dashi gaban mirror daga shi sai short towel a waist ɗinsa sam baisan cewa sehrish bace, ta cikin mirror ya hangota, aikuwa cikin sauri yace "dakata !! Kada ki shigo! Ja baya," dariya sehrish tayi sannan taja da baya ta tsaya jikin ƙopar tana cewa "Junaid yaushe ka fara jin kunyata har haka"? daga cikin ɗakin tajiyo muryarsa yana cewa "tun ranar dana gane cewa ke maca ce.....,' Murmushi ta saki tana faman sauke ajiyar zuciya har time ɗin temperature ɗin jikinta yayi mugun zafi ba don komai ba sai don abunda yafaru da ita yanzun nan, "Come in Sehrish," junaid ya faɗi, Shiga ciki tayi a lokacin harya zura jallabiya ash colour ajikinsa yana gyara hannun rigar, wuri tasamu agefen gadonsa ta zauna tana cewa "Junaid dama wannan wayr tawa nake nema narasa inda na jefar da ita, shine nazo ka taimaka ka kiramin layin dake cikinta, may be in tayi ringing in gano ta, Murmushi junaid yasaki kafin yace "shikenan zan kira maki ita, amma under one condition? Ya faɗi ayayin da ya tsaya agabanta ya ruƙe qugu, sehrish tace "Menene sharaɗin? Junaid yace "Tun ran nan nake ta fama dake ki nunamin gyaran gashin ki kin ƙiya, to yau indai kina So na kira layin wayarki sai kin cire mun nagani" ya faɗi yana murguɗa mata baki, Yamutsa fuska tayi tare da cewa "look junaid yanzu ba lokacin wannan bane, am not in mood Just ka kiramun wayar,' ta faɗi tana tsuke baki, Bin shi tayi da kallo ganin ya ɗan ɗaure fuskar shi alamar baiji daɗi ba, Cikin lallashi tace "junaid are u angry with me? Am sorry pls ni bazan so naga king of smile ya koma king of Angry ba,' tayi maganar da ɗan zolaya, Ɗan sakin fuskarshi yayi sannan yace "its ok, go back to ur bedroom i wanna call u righ now," Murmushi sehrish tasaki tare da cewa "yawwa mutumi na, Allah yabar mun kai," ta faɗi tare da miƙewa ta wuce bedroom ɗinta cikin sauri, Junaid kuwa acikin ransa yace "Ameen sehrish Allah yabarmun ke till the end of my life,' sannan yasa hannu ya ɗauki wayarsa dake ajiye saman mirror, contact yashi ga tare da lalubar nombar sehrish da yayi mata Saving da*FUTURE DREAM* sa'an nan ya danna mata kira, tunkan sehrish tashiga ɗakinta ta rinƙa jin ringing ɗin wayar da ƙarfin gaske, tura ƙopar ɗakin tayi ta shiga ciki tana bin inda sautin ke fitowa, ashe tana cikin bedside drawer ɗinta, duk wannan uwar wahalar da tasha, cikin hanzari ta janyo drawer chest ɗin gida na farko, sai ga wayar ajiye sabuwarta kusan 1 month kenan tana ajiye bata mutu ba, saboda ruƙon chargyn ta, ajiyar zuciya sehrish tasaki tana shasshafa screen ɗin wayar da hannunta, . .........................tuna da azmee dake jiranta yasanya ta fice da wayar cikin sauri ta isa ƙopar ɗakin azmee knocking tayi daga ciki taji azmee tace "in kin son bada wayar kika zo ba ki koma," wato har ta gane ce sehrish ce ta kwankwasa mata, Gyaran murya sehrish tayi tare da cewa "Tare da wayar nazo aunty azmee," Azmee tace "shigo ciki," Tura kopar sehrish tayi ta shiga, samun ta tayi kishingiɗe saman gadonta, ganin sehrish yasa ta tashi zaune tana cewa "yanzu naji magana," Murmushi sehrish tasaki tare da samun wuri gefen azmeen ta zauna sannan Ta miƙa mata wayar tace "Gata," Azmee ta kalli wayar tare da cewa "dama ba wani abu zanyi da ita ba, ke nake so ki runƙa amfani da ita akai-akai takasance tare dake, saboda daga yanzu duk wani mai buƙatar wani abu ke zai kira kai tsaye a waya yasanar miki," jinjina kai sehrish tayi alamar gamsuwa da bayaninta, Sannan azmee taci gaba da cewa "nikam inaso na tambaye ki, shin kin ta6a yin makaranta ne before? ɗagowa sehrish tayi ta kalle ta a wani irin yanayi kamar wani abu yaɗan sosa mata zuciya, shiru tayi na wani lokaci kafin tace "eh nayi primary bayan nan nafara secondry karatun duk ashiriri ce ƙarshe ma muna gab da zamu shiga ss3 nadaina zuwa gaba ɗaya......' ta ƙarasa maganar asanyaye Azmee tace "yanzu kina da burin ci gaba da karatun ne ko kuwa a'a? Ta tambaya tana kallonta, Sehrish tace "ina so mana sosai, ina so nayi Ilmi saboda wata rana nima nazama abun alfahari, kuma wannan burin mahaifiyarmu ne, tun lokacin da ta haife mu takance Sehrish zata zama Achitecture, Hosana kuma Doctor, Jahad kuma Nurse haƙiƙa inaso nacika mata wannan burin nata.......................' idonta ne suka cuko tab da kwalla sunnar da kanta tayi ƙasa tana kallon wayar dake hannunta, Cikin mamaki azmee ke kallonta ita kanta sehrish batasan me take cewa ba, ci gaba da magana tayi kawai tana cewa "Allah sarki a lokacin ni nafi kwarewa wurin yin zane, hosana ce mai ƙoƙari acikin mu amma yanzu bata da cikakken hankali tun lokacin da ta duro daga saman window mai tsayin gaske ..........ban......ban....... Kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da yazo mata nan take ta fashe da matsanancin kuka, Gaba ɗaya hankalin azmee ya tashi sam tarasa gane ma sambatun da sehrish ke yi, cikin ruɗu tace "sehrish wai meke faruwa ne? Su wanene waɗannan kike magana akansu ne? ƴan uwanki ne? ɗaga mata kai tayi alamar "Eh" jinjina kai azmee tayi tare da cewa "share hawayenki daina kuka ya isa haka, duk da bansan Labarin ki ba amma ina da tabbacin cewa wani mummunan abu yafaru acikinsa wanda ke yawan saki cikin damuwa, don haka zanso naji labarinki sehrish amma ba yanzu ba aduk lokacin da muka samu free time sosai zamu zauna ki bani shi tun daga farko har ƙarshensa,' "Insha allah aunty azmee na yarda dake sosai baxan 6oye maki komai ba," ta faɗi ayayin da take share hawayen ta, Bayan sun samu natsuwa su duka azmee taci gaba da cewa "Zaki fara zuwa school insha Allah....' Cikin mamaki sehrish ta ɗago ta kalle ta tare da cewa "Makaranta? Ni kuma? Aunty azmee taya za'a ɗauke ni a school bayan ko takardun kammala primary ɗin bani dasu na rasa su,' "Kada ki damu sehrish wannan ba wata damuwa bace, komai za'a iya yi maki shi insha Allah, kuɗi ne kawai ke magana, kuma ni zan tsaya maki harki samu don nasan muddin na tuntu6i koda kanal yusif ne da maganar zai iya sama maki hanya, bama shi ba junaid zai iya yi maki wannan hanyar cikin sauƙi ki fara daga ss1 daga baya kin zana Jsce in time ɗinta yayi,' Wani irin farin ciki ne ya lullu6e sehrish har tagaza rufe bakinta, aranta tana cewa nan bada jimawa ba nima zan fara zuwa makaranta kamar kowa ?Alhamdulillah 😇 Hannu azmee tasanya ta kar6i wayar hannun sehrish tana cewa "ina fata junaid ya nuna miki komai ko? "Eh harma ya tura mun wasu apps ɗin da zanyi amfani dasu," Azmee tace "okey, idan kina so kiyi amfani da data ko wurin yin browsing da sauransu just Wi-fi kawai zaki kunna, ' Jinjina kai sehrish tayi alamar gamsuwa, sun ɗan jima suna fira kafin daga bisani ta sallame ta, komawa bedroom ɗinta tayi cike da murna koba komai in tafara zuwa school zata haɗu da friends irinsu Hafsat Bature Domin ɗebe kewa 😇 Sehrish first day at school 😮 Can't wait to see 💃💃💃💃 Ga wanda ba suyi payment ba su hanzarta su biya before end of this week👍 Yanzu littafi Zai fara 🔥🔥🔥 (08103884440) LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ──────────────EPISODE 17-18 ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ💋❤? *Mallakin Hafsat Bature Moh'd* ~BossBature~ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·? bayan Jahad ta kammala wankan ta canza kaya ixuwa doguwar riga, hawa tayi itama saman gadon kusa da hosana suna daf da juna tace "hosana me kike tunani game da hafsat da mommynsu? Anya ba wani abu suka shirya mana ba? Kada fa ace so suke yi su kashe mu ko su zubar damu shiyasa suka tsara mana hakan,' tayi maganar cikin nuna damuwa a fuskarta, Hosanna tace "jahad ni nasan abunda mommynsu hafsat ta shirya mana, fuska biyu tayi mana wlh, so take ta nuna mana kulawa sosai don mu saba da ita yadda in yaya Omar yazo yace zai tafi damu muƙi binsa saboda sun nuna mana kulawa.........' dakatawa tayi da maganar jin alamun tunkarowar mutun ɗakin da suke ciki, Hafsat ce ta shigo ciki fuskarta ɗauke da murmushi tace "sannunku My sisters ya jikin naku"? Ta tambaya ayayin da take samun wuri saman room sofa ɗin tazauna, "Alhamdulillah da sauƙi" suka bata amsa atare, mayar da idonta tayi gefen kujerar da take zaune leda ce ajiye wadda taba Jahad ta ruƙe mata bayan ta fito daga store, hannu tasa ta ɗauki ledar tana cewa "Lahh Jahad wannan ae naku ne na siya maku, Chocolate ne da sweet ko bakwa so ne"? ta tambaya tana kallonsu, Suka haɗa baki wurin cewa "muna so," sannan jahad ta sauko daga saman gadon tasanya hannu biyu takar6a tana fadin "mungode Aunty hafsat," Murmushi hafsat tasaki tare da cewa "Naji daɗin sunan nan da kuka kira ni dashi, amma nafison ku kira ni da Sister Hafsat akan aunty hafsat zanfi jin daɗin hakan," Murmushi su kayi su dukan su, kafin daga bisani Jahad ta curo musu chocolate cookies ɗin data siya musu, guda biyu ta curo ta ɗauki ɗaya sannan ta miƙa ma hosana suka 6are suna sha, Har lokacin idon hafsat na akansu kallonsu takeyi gwanin burgewa, dama tun ranar farko data fara cin karo dasu sun burgeta kawai baƙin hali ne irin nata yasa bata nuna ba, Ɗagowa su kayi jin alamar shigowar mutun, AUNTY BABBA ce ta shigo fuskarta ɗauke da murmushi tana kallonsu tace "Ya jikin naku My daughters? haɗa baki su kayi wurin cewa "da Sauƙi Alhamdulillah," Jinjina kanta tayi kafin daga bisa ni ta kuma cewa "Yakamata ku fito mana kuzauna a palour ko kallo ne kuyi zai ɗebe muku kewa kuma zaku samu nishaɗi," Amsa mata sukayi da "Toh" sannan suka sauko daga saman gadon hannun jahad ruƙe da ledar choculate ɗinsu, A falon suka samu wuri saman gujera mai mazaunin mutun biyu su ka zauna tare da mayar da hankalin su Wurin kallon shirin da akeyi a tashar Bollywood, tuni kallon ya ɗauke musu hankali saboda daɗin dramar da suke yi ta india, dama kuma ga chocolate ɗinsu suna sha sai abun yaƙara nutsar dasu gaba ɗaya, AUNTY BABBA kuwa wuri tasamu ta zauna agefen gadon tana fuskantar hafsat tace "Sannu Madam," tashi hafsat tayi zaune tana cewa "Mommy dama ina son magana dake! Wannan canjin dana gani a tattare dake shin dagaske ne? Ko duk shiri ne? ta tambaya tana kallonta don jin amsar da zata bata, ɗan ƙayataccen murmushi AUNTY BABA tasaki tare da cewa "Hafsat kenan ! Ke naso ki fara faɗamun gaskiyar lamarin nan shin dagaske ne yanzu kin fara jin tausayin yaran nan? "Mommy da gaske ne, natausaya musu sosai saboda bugun rashin imanin da kika yi musu, kuma ayanzu bana son wani yaƙara ƴunƙurin cutar dasu daga ni har KE ! Ajiyar zuciya aunty babba tasaki tana mai jinjina kai tace "Shin ya maganar matar da kika amsar ma kuɗi kusan miliyan shidda? Mayar mata su zakiyi kenan.....? Hafsat tace "wannan ni tashafa mommy, zan san yarda zanyi da ita, in ma bazaiyiyu ba just zan mayar mata da kuɗinta ne," ɗan ta6e baki AUNTY BABBA tayi daga bisani tace "Shikenan Daughter but lemme remind u something, kin manta da uban bashin da Ake bin ki kenan u ave to think about it, how can u pay all ur debt? Dole ki buƙaci kuɗi ....................tana kai ƙarshen maganarta, ta tashi ta fuce tana faman sakin shu'umin murmushi aranta tana cewa "Yarinya kenan! Naki wasa ne," **********💪💪💪*************** misalin ƙarfe 5 da rabi na marece a lokacin suna dab da kammala aikace-aikacen su na girki, sai ga OMAR ya shigo cikin gidan kai tsaye kitcen ya nufa in da suke, Hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba ganin OMAR don atsorace take dashi, bai shiga kitchen ɗin ba tsayawa yayi daga waje ba tare da yace komai ba, Sehrish ce tace "Aunty Azmee ga yaya Omar nan," azmee na jin haka cikin sauri ta fito izuwa inda yake tsaye da murmushi a fuskarta tace "Omar ashe kaine ina fata lafiya dai ko," Jinjina kansa ya ɗanyi ayayin da idonsa ke kallon sehrish wadda ke acikin kitchen taƙi ɗagowa su haɗa ido dashi, har time ɗin ya gaza gasgata abunda idonsa ke nuna masa, ɗan gyaran Murya yayi tare da mayar da idonsa kan na Azmee yace "Sannuku da ƙoƙari, ina fata dai ban katse maku aikin ku ba" Azmee tace "A'a wlh Ae ma mun kammala girkin gyaran kitchen ɗin ne kawai ya rage mana yanzu," OMAR Yace "Okey, dama aiki ne nake son kuyi mun ke da waccen Yarinyar ta cikin kitchen,' Jin hakan yasa sehrish ɗan ɗagowa suka haɗa ido dashi cikin sauri ta sunnar da kai ƙasa, Azmee tace "Wane kalar aiki kenan Omar? "Zan baku makullin gidan Uncle ABUSUFYAN so nake Kuje can ku duddubamun gidan duk wani abu da ake buƙata kawai inaso ku rubuta mun shi," Murmushi azmee ta saki tare da yin ƙasa² da murya tana cewa "To fa, kodai Abusufyan ne zai dawo nigeria da zama ne? Kamar daga sama taji muryar Omar yace "Bashi bane zai dawo, wasu marayu ne nake son zubawa aciki, so inaso agyara mun gidan da duk wani abu na more rayuwa da mace zata buƙata acikin Sa, sannan bayan kun kammala wannan aikin inaso ku shirya zuwa Yi masu siyayyar kayan sawa da sauran abubuwan buƙata na mata,' Azmee tace "wannan ai aikin lada ne, insha Allah Omar zamu yi komai yadda kake so," "Hakan yayi mun, bari na ɗauko maki key ɗin gidan ku tabbatar kunje yau, zansa Junaid ya kai ku a motarsa," ya yi maganar yayin da yake wuce wa izuwa sashen Abbansu, Hannu yasa ya ciro wayarsa daga cikin aljuhun wandonsa, contact ya shiga tare da dannawa Abban nasu kira, kamar jira yake omar ya kira sa awaya sai gashi ya ɗauka, Ƙara wayar Omar yayi a kunnansa yana cewa "Abba gani nashigo bedroom ɗin naka, wurin ina key ɗin yake"? "Ka duba cikin side drawer ɗita gida na tsakiya suna anan ciki makullan na zuba su," "Ok to ngde Sosai Abbana, take care of your self for me," yana jiyo sautin muryar Abban nasu Mai haɗe da Murmushi yana cewa "Nima haka ka kulamun da kan ka," "Insha Allah," Omar ya faɗi tare da rejecting kiran, ya mayar da wayar tasa cikin aljihunsa, Kai tsaye inda Bedside drawer ɗin Abban nasu take ya ƙarasa tare da zuƙunnawa ya janyo gida na tsakiya acikinta, Sai ga makullan sun bayyana hannu yasanya ya ɗauka sannan ya fito daga ɗakin nasa, Kitchen ya nufa azmee na ganinsa ta fito, ƙarasawa yayi tare da miƙa mata key ɗin yana cewa "Ga shi nan ku tabbatar kunyi aiki mai kyau, yanzun nan zan ma junaid magana yazo yakai ku can gidan," Azmee ta amsa masa da cewa "Toh insha Allah," sannan Omar ya fuce daga main palour izuwa filin buga ball ɗinsu tunkan ya isa yake faman kwalawa junaid kira wanda ke acikin filin kwallon sai faman buga ball suke yi su uku shi da wasu daga cikin security ɗin gidan, Jin kiran Omar yasanya shi dakatawa da yin kwallon ya wurgar masu da ita sannan ya fice daga cikin ragar izuwa inda Omar yake, tsayawa yayi agabansa tare da zuƙunnawa ya dafe guiwarsa sai faman haƙi yake yi daker ya iya cewa "Yaya Omar gani," Hannu omar yasa tare da bugun bayan junaid yace "Bana hana ka buga ball dayawa har haka ba? Tun fa ɗazu dana shigo nasame ka, cikin waɗancan gardawan sai faman wahalar mun dakai suke yi," Murmushi junaid yasaki tare da ɗagowa tsaye yana cewa "Yaya Omar zandaina ne, amma yanzu tana sanya ni nishaɗi sosai," Jinjina kai Omar yayi tare da dafa kafaɗarsa yace "ko don saboda lafiyarka junaid, yakamata kadaina yawan buga kwallon ɗin nan da kuma yawan yin guje-guje,' Cikin girmamawa junaid yace "insha Allah yaya Omar zandaina," dafa kafaɗarsa omar yayi sannan yaci gaba da cewa "ka shiga ciki ka shirya zaku fita tare da Azmee da wannan Yarinyar inaso ka kaisu Gidan Uncle Abusufyan, zasu yi mun aiki ne kaima sai ka taya su," Cike da zumuɗi junaid yace "To shikenan yaya Omar, bari naje yanzun nan nashirya nakaisu," "Yawwa My boy," Omar ya faɗi tare da wuce wa gaba, Shige wa junaid yayi da gudu cikin babban falon kamar ba wanda aka gama ja ma kunne akan yin gudu ba, A lokacin azmee da sehrish sun kammala gyara kitchen ɗin, kowan nan su ya wuce ɗakinsa domin kimtsawa, Da gudu yake tattaka Matattakalar benen adai-dai lokacin SGR ya fito shima yana ƙoƙarin saukowa down, jikinsa na sanye da jallabiya fara mai gajeran hannu abun ba'a magana, tsayawa yayi yana jiran isowar junaid Domin yayi masa kyakkyawan ruƙo, sai da junaid yakai ƙarshe sannan ya lura dashi, ɗan zaro ido yayi tare da dakatawa da tafiyar gabansa na faɗuwa, sarai yasan cewa sun hana shi gudu shi kuma abun ajinin sa yake yadda kasan wanda aka sanya Ma battery haka junaid yake, Tun kafin Babban yayan nasu yace wani abu junaid yayi saurin cewa "Bazan ƙara ba wlh, na daina" ya faɗi yana ɗan raku6e fuska yana kallonsa wuri da ido, Sgr yace "Junaid na ta6a sa hannu na ajikinka, da sunan zan buge ka ga? Girgiza kai yayi tare da cewa "a'a babban yaya, baka ta6a ba kuma bana fata, ai nasan ma bazaka ta6a buguna ba," ya faɗi da murmushin nan nasa, Sgr yace "meyasa kake tunanin cewa bazan iya bugunka ba,"? ɗan cizon red lips ɗinsa tare da cewa "Because.......You love me so much......' ya ƙarasa maganar tare da wuce wa cikin sauri yana dariya, bin shi da kallo kawai Sgr yayi, tunawa yayi da wata magana da aka ta6a faɗa masa cewa *Kowa ne ɗan adam yana da lagwansa, kaima haka ga lagwagonka nan, wato ƙanin ka JUNAID, Yakamata ka kula dashi sosai, Saboda duk wanda zai kawo maka hari acikin maƙiyanka, to ina da tabbacin cewa zasu 6ullo maka ne ta wurin JUNAID, So you've to be very careful,"! Jikinsa ne ya ɗanyi Sanyi amma ta wani 6angaren yana jin cewa bazai ta6a barin hakan ta faru ba A matsayinsa na SURGEON GENERAL RAFAYET, A babban falon ya zauna saman doguwar kujera mai mazaunin mutun uku, ya kishingiɗa tare da ciro wayarsa yana daddanawa, Shigowa Omar yayi cikin babban falon ganin SGR yasa shi sakin fara'a yana cewa "Ashe kana ciki yaushe ka shigo," tashi zaune Rafayet yayi jin muryar omar, Kallonsa yayi tare da cewa "ban jima da dawowa ba, what of u ,"? ya tambaya yana kallonsa, Zama Omar yayi saman Sofa ɗin da sgr yake suna ɗan fuskantar juna yace"Nima yanzun nan nashigo, bansan kana aciki ba ae dana shigo, dama inaso nace kunyi waya da EVA? tana so tayi magana dakai sosai tayi mun magana ɗazu, its better ka kira ta if not kasan halinta ƙaramin aikinta ne kaganta a Nigeria," ɗan ta6e baki sgr yayi tare da cewa "naga missed Calls ɗinta, na manta nabi kiran nata that's why," Jinjina kai Omar yayi kafin ya kuma cewa "Har yanzu baka yanke shawara bane game da ita? Pls bro kodan saboda Uncle Donald yakamata ka sassauta mana....' Wani irin kallo Sgr yake binsa dashi kafin yace "Uncle ya riga da yasan tsarina, ko shi kansa ya tsawatar mata akaina amma taƙi ji so ni banson ya zanyi na fahimtar da ita ba," Omar yace "matsalar kenan, ni abunda yafi damuna taurin kanta, in banda ƙarfin hali irin nata taya zata ce dole sai kai zata aura? a ƙalla EVA ta baka kusan 10years aduniya, har yaushe ne zata daina wannan mafarkin? ya tambaya yana kallonsa, Sgr yace "Omar da ace zan iya canza ra'ayi na akan mace ,to ina mai tabbatar maka da cewa ita ce mace tafarko da ta cancanta ta mallake ni, saboda kusancin dake a tsakani na da ita..................." Karaf!! Maganar Sgr ta sauka a kunnan Sehrish wadda fitowarta kenan ta nufo cikin babban falon, har ta kammala shiryawa tsaf, ta zumbula jalbaba ajikinta har ƙasa maroon colour, hannunta na ruƙe da hand bag, ƙafarta kuma na sanye da flat shoes launin hijab ɗinta, fuskarta sam babu makeup ƴar hoda ce kawai ta shafa sai ta murza man baki a la66anta, amma ba ƙaramin kyau tayi ba, tsayawa tayi jiki amace tana sauraron firar tasu sam tagaza motsi, har sai da Marshal Omar ya ɗago da idonsa ya kalle ta, gabansa ne yaji yayi mugun bugu sam yagaza ganewa wannan ruɗanin dake a fuskar yarinyar nan, Sehrish bata lura da kallon da Omar keyi mata ba, juyawa Sgr yayi don yaga me Omar yake kallo ne karaf idonsa suka sauka ana sehrish wadda itama idon nata na akanshi, from up to down ya kelle ta kafin yace "Ke zonan," gabanta ne taji ya faɗi rass tayi firgit tana kallonsu, hankali atashe ta tunkare su gabanta na ɗarr!ɗaarr ta ƙarasa inda suke dab da Babban yayan nasu daya kira ta, Hannu yasa tare da ruƙo jalbabar dake ajikinta, saboda tsananin tsoro sai da sehrish ta kusa sakin fitsari tuni jikinta yasoma kerma kaf!kaf !!kaff! cikin sanyayyiyar muryar nan tasa ta natsastsu yace "Menene wannan haka ajikin ki,"? Ya tambaya in serious matter batare da ya aza idonsa akanta ba, Murya na rawa sehrish tace"hi..hij..hijabi ceeee...' "Masallaci zaki je ne"? Ya tambaya yana jiran amsa, "A'a fita zamu tare da aunty azmee," Cire hannunsa yayi tare da nuna mata hanya yace"maza ki koma, ki cire wannan abun, bana son sake ganin shi," cike da mamaki Omar ke kallon sgr har dai yagaza yin shiru yace "Rafayet nan fa ba Us bane Nigeria ce, kuma wannan shine best outfits da yace mace musulma tayi, Domin rufe surar jikinta daga jan hankalin mutane akanta saboda tsaro,' girgiza kai sgr yayi tare da cewa "ban yarda da wannan shigar ba, shin Omar taya mutun zai iya motsi acikin wannan abun"? Ya tambaya yana nuna hijabin jikin sehrish,😂 Fashewa da dariya Omar yayi kamar kamar me, ganin yarda Sgr ya haƙiƙance akan hijabin dake ajikin yarinyar, shi a ganinsa takurace kuma mutun bazai iya motsi acikinta ba, daƙer ya dakatar da dariyar tasa ya kalli sehrish tare da cewa "Ki faɗa masa yarda kike motsi acikinta may be ya fahimta," ɗan murmushi sehrish ta saki ita kanta abun ya gama ɗaure mata kai, ɗagowa da hannayenta tayi tare da cewa "Ga hannun hijabin nan, tun da na fiddo da hannun acikinsa lafiya lau nake motsi acikinta," ta ƙarasa bayanin tana kallonsa Jingina bayansa yayi ajikin sofa ɗin tare da cewa "Its Okey, u can go,' har ta juya zata tafi Omar yace "Ya Sunan ki ne? Juyo wa tayi ta kallesa da murmushi a fuskarta tace"SEHRISH" Omar yace "masha Allah suna mai daɗi, amma menene ma'anarsa? ya tambaya yana kallonta, *kyawawan halayyu na mutun," ta bashi amsa, *ina fata zaki nuna mana waɗannan kyawawan ɗabi'un acikin gidan nan, har ma ki zama alkhairi agare mu," omar ya faɗi da ɗan murmushi a fuskarsa, duk Sgr na sauraronsu duk da ya ci gaba da dannar wayarsa, Sehrish ta amsa masa da cewa "Insha Allah," sannan ta wuce Sai lokacin Sgr yace "Ashe kana surutu har haka Omar? Kallonsa Omar yayi tare da cewa"Yarinyar ce tana tattare da wani abun al'ajabi a fuskarta shiya sanya Na sake mata," "Ba kowace baƙuwar fuska yakamata ace kana sakemawa ba irin haka ba, Mata Basu da tabbas they're trouble makers," acewar Babban yaya, ƴar dariya Omar yayi batare da cewa komai ba, Sehrish kuwa kitchen ta wuce ta zubo musu coffee tare da snacks a plate Cikin tray sannan tadawo inda suke tare da ajiye masu saman Table, Omar yace "thank u miss Sehrish," Murmushi tayi masa sannan ta juya ta nufi ɗakin azmee tunkan ta ƙarasa ɗakin nata sai ga Azmee ta fito itama ta kammala shiryawa cikin atampha ja, ta aza babban mayafi milk colour launin takalminta ƙafarta, atare suka fuce suna jiran isowar junaid, Ba da jimawa ba sai ga junaid ya fito daga upstairs yana saukowa down sai faman zabga murmushi yake yi, jikinsa na sanye da haɗaɗɗiyar shadda gezner blue colour mai maiƙo sai faman ɗaukar ido yakeyi kai kace wani sabon ango ne, shaddar tasha aiki a wuyanta tsantsararre, hannunsa na ruƙe da wayarsa haɗe da key ɗin motarsa, Lokacin daya ƙarasa saukowa daga saman stairs ɗin, gaba ɗaya Marshal Omar da Sgr suka bishi da kallo, Zagayawa yayi inda babban yayan nasu yake yana isa ya manna mashi kiss agefen fuskarsa sannan yace "Zan fita, saina dawo," ko amsa bai jira ba cikin sauri ya lalla6a ya fuce yana cewa "yaya Omar kayi masa bayani, mu mun wuce ," Girgixa kai kawai SGR yayi sam ya kasa magana, wato junaid yasan cewa zai iya dakatar dashi daga fita shine yayi dabarar tserewa, Murmushi Omar yasaki tare da cewa "Junaid kenan ! komai nasa na burgewa, ya cika ƙiriniya ga shegen wayon tsiya, saboda kada ka hana shi fita shiyasa ya gudu bai jira amsarka ba," yayi maganar yana kur6ar coffee ɗin da sehrish ta kawo masu a cup, "Ina zasu je ne"? Sgr ya tambaya yana kallonsa, Omar yace "Gidan Uncle Abusufyan na aikesu, inaso zanyi amfani da gidan ne akwai wasu marayune da zan zuba acikinsa kwanan nan," Sgr yace "Omar kenan, meyasa baka sanarmun ba? ko ni ba'a buƙatar gudummuwata ne? ya faɗi yana kallonsa, Murmushi Omar yasaki dama sun saba indai irin haka ne, muddin akace aikin lada yasamu, to har rububi suke yi wurin bada taimakonsu, kowa burinsa ace da dukiyarsa za'ayi amfani wurin bada tallafi sam basa gajiya da irin wannan (Kaji masuyi don Allah) Shiyasa dukiyar tasu kullum hau hawa takeyi kamar kamar me, a ƙalla su kansu basu son adadin gidajen marayun da suka buɗe ba a kasashe daban daban kuma suke ɗaukar ɗawainiyarsu da komai, Manyan asibitoci kuwa da suka buɗe ba iyaka, wanda suma duk kyauta ne ake duba marasa lafiya acikinsu, ga makarantu na marayu da marasa hali da suke dasu ba adadi, wannan ba komai bane ba, kaɗan ne daga cikin abubuwan da suke yi na taimako, Ya Allah ka bamu arziƙi mai albarka wanda zamu amfana dashi kuma ƴan uwanmu musulmai suma su amfana dashi, ba irin arziƙin da mutun zai mallaƙe ba, ka ga ko cikin gidansa fama ake dashi basa ciyuwa balle na waje su samu😧 *****GIDAN ABUSUFYAN******* Haɗaɗɗiyar daula, Aljannar duniya tun daga kan Tanƙameman gate ɗin gidan Golden colour & brown sehrish ta saki baki tana kallo Ikon Allah, Ba don daga gidan Abban sojoji ta fito ba da sai tace wannan gidan a dubai yake, tsayar da motar junaid yayi abakin gate ɗin sannan ya fito daga cikin Motar, ya nufi jikin gate ɗin, tunkan ya isa ya danna madannin da ke ajikin key ɗin gidan a hankali gate ɗin ya soma zugewa da kansa daker daker yake tafiya saboda gidan ya jima ba'ayi amfani dashi ba tunda Abusufyan yabar Nigeria a fusace gidan yake ahaka garƙame, ganin zai 6ata musu lokaci yasa junaid sanya hannunsa yana ƙoƙarin turasa da ƙarfinsa don yayi saurin f Buɗewa, aikuwa nan take zufa tasoma wanko masa kamar wanda aka watsa ma ruwa a fuska dama jiki bana wahala ba, muryarsa kamar zaiyi kuka yace "Aunty Azmee wai bazaku fito ba mu tura, Wlh ban iyawa ni kaɗai," Jin hakan yasa su fitowa daga cikin motar suna faman tikar dariya, azmee tace"Haba junaid wannan fa ƙaramin aiki ne, sai kace ba Namiji ba haba karka ban kunya mana, Be a Man,' Kallon azmee yayi yana faman sauke haƙi yace"In dai saina tura wannan jibgegen gate ɗin zan zama namiji, to Allah abarni a jinsin mace yafi mun," Fashewa da dariya sehrish tayi har tana dafe ciki jin abunda junaid yace, harara ya watsa mata yana hura hanci, Azmee na isa jikin gate ɗin tace"Matsa ka gani junaid, ni bari in zama Namijin, ni kaɗai zan tura sa," Jin haka yasa junaid matsawa suka bata wuri don ta jaraba, gefen Sehrish ya tsaya suka zuba ido suna kallon azmee, Hannu tasanya sannan ta soma tura gate ɗin nan take ya tafi da gudun gaske ya ƙarasa zuge kansa, Zaro ido Junaid da sehrish su kayi cikin tsananin mamakin ƙarfi irin na AZMEE, A ruɗe junaid yace"Aunty azmee taya hakan ta faru? Ni nakasa turasa amma ke kina aza hannu gate ɗin ya buɗe," Murmushi azmee ta saki tare da nuna masa damtsen hannunta tace "Tsohon ƙashi kenan! ba irin naku ba na ƴan shila," Fashewa su kayi da dariya su duka kafin daga bisani suka koma cikin Motar, junaid ya shigar da ita cikin gate ɗin kai tsaye yayi parking ɗinta a harabar gidan *Shin Kuna tunanin Cewa Omar zai samu damar ɗauko su hosanna da Jahad daga gidan Aunty babba*?😟 Ku hanzarta yin payment 300 ne ga acct 3196407426 Bature Hafsat Muhammad first bank, sai aturomin shaidar biya ta numberta 08103884440, idan kuma recharge sai ayimun magana ta numberta,👍👏 [9/9, 4:03 PM] 💋BOSS LADY💋: *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* •·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·? *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ──────────────EPISODE 19-20 ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ💋❤? *Mallakin Hafsat Bature Moh'd* ~BossBature~ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·? bayan sun fito daga motar kai tsaye suka nufi hanyar da zata sadaka da babban falon gidan, Sehrish sai faman bin ko'ina take da kallo aranta tana cewa"tab ! Mace ta samu wannan amatsayin gidan aurenta, ae kawai ta bi mijinta sau da ƙafa, tabi da addu'a don ni gaskiya na mallaki wannan hamshaƙin gidan amatsayin gidana, ko ƙofar gida bana leƙawa sai in ta kama,' sai faman zancan zuci take yi har suka ƙaraso wurin wani bene mai kanannaɗa, hawa junaid yayi sannan azmee tabi shi, itama sehrish tabi bayansu, sai faman jinjina kai take yi tana cewa"lallaine Aljanna ta mai rabo ce," daker take tattaka matattakalar benen saboda gajiya don yana da ɗan tsayi, bayan sun kai ƙarshensa, wata haɗaɗɗiyar ƙopa ce wadda kai tsaye in ka bi ta zata sauke ka upstairs inda main falo ɗin gidan yake, key junaid yasanya yabude ƙopar sannan suka shiga cikinsa,wurin ya haɗu an ƙawata shi ahaka ma wai ba furnitures acikinsa, to inaga ansanya mashi kujeru da sauran abubuwan ƙayatarwa, Batare da 6ata lokaci ba, sehrish ta buɗe handbag ɗinta, memo ta ciro tare da biro, junaid da azmee suka dunga dudduba falon suna karanto mata abunda za'a buƙata acikinsa, ita kuma tana rubutawa acikin memo ɗin hannunta, bayan sun gama da falon kaf sun lissafa duk wani abu da za'a sanya mashi, Sannan acikin babban falon akwai bedrooms guda biyar ƙofofinsu na acikin falon, ciki suka shiga suna dudduba ɗakunan masu girman gaske, nan ma azmee ta faɗa ma sehrish duk abunda za'a buƙata na furnitures ta rubuta, daga nan kuma suka sauko downstairs stairs shima bene ne zai biyo dakai ƙasan, Agajiye sehrish ta kalli junaid tare da cewa "dan Allah wannan wane irin gidane haka junaid? Nafa rikice wlh, mun shigo ta Upstairs yanzu kuma ga mu a downstairs yanzu ta ina zamu bi mu fita? Ba dai sai mun koma upstairs ɗin ba don wlh ƙafafuna a sanƙare suke hawa stairs ko wahala, Junaid da fuskarsa tayi jawur ya gama cika ya 6atse saboda uwar yunwar da yake ji, ga gajiya duk ta baibaye shi, daker ya iya cewa "wannan ne damuwarki, Ni ta cikina nake yi yaushe har muka kammala muka koma gida ni daga nan ma, ba abunda zan ƙara yi Allah, ku je ku ƙarasa sauran aikin in kun kammala kuyimun magana," Wuri yasamu a sitting room ɗin dake a downstairs saman wani benci ya zauna, da alama tun lokacin da akayi ginin gidan aka barsa, don akwai tarkacen kayan aikin da aka bari acikinsa, Acikin sitting room ɗin akwai ƙofofin bedrooms guda biyu, sai kitchen mai girman gaske, sunsha aiki kaf sai da suka zagaye gidan bayan sun tabbatar sun bincika ko'ina sun dudduba abunda ya dace duka kaf sehrish ta rubuta a memo ɗinta, Ana cikin kiran Sallar magrib suka bar gidan kowa agajiye, Suna ƙarasawa gida daga babban falon kowa ya wuce ɗakinsa, shaf shaf junaid ya tu6e kayan jikinsa ya faɗa toilet donyi wanka, haka itama sehrish tana shiga ɗakin nata bayan tayi wurgi da handbag ɗinta saman gado tare da memo da biron duka, kai tsaye ta tu6e Jalbab ɗin dake ajikinta, ta cire rigar jikinta, cikin sauri ta faɗa toilet wanka tayo tare da Alwala, tana fito ta ɗaure da towel ta bude wardrobe ta ciro wata doguwar rigar mara nauyi ta zura, daker tasamu tayi sallah bayan ta kammala ta baje saman gadonta, bata ƙara sanin meke faruwa ba sam ta manta da batun jera abinci adining, gana babban yaya da zata kai mashi bacci kawai take kwasa, Azmee ce kawai tayi ƙoƙarin fitowa bayan ta canza kayan jikinta, tunda ta leƙa tasamu sehrish na jan minsharin wahala, bata tashe ta ba kitchen kawai ta wuce ta shirya masu abincin dinner ɗinsu ta dunga kaiwa a dining tana jerawa harta kammala, Daker junaid yasamu ya fito sai da yaci ka cikinshi sannan ya wuce masallaci yin sallah, Sai bayan sallar isha'i sannan sehrish tafarka tana faman zazzare ido, agogon bangon ɗakinta ta duba kusan ƙarfe goma da rabi cuf, arazane ta miƙe tana faman dafe ƙirji tuna cewa bata kaima SGR dinner ɗinsa ba, cikin sauri ta ɗauko mayafi a wardrobe tayi lagensa a kanta, sannan tafito dakin azmee tafara wuce wa don taji ko takaimasa, kwankwasawa tayi sannan ta jira ta buɗe mata, A lokacin azmee bacci takeyi jin bugun ƙofar sehrish yasanya ta, farkawa daga baccin nata, tasowa tayi ta buɗe mata ƙofa, Ganin sehrish yasa ta cewa "ashe kin tashi daga baccin? Lafiya naganki ko akwai wani abune? Sehrish tace "dama babban yaya na manta bacci yaɗauke ni ne, bankai masa ɗina ɗinsa ba, shine nazo na tambaya naji ko ankai masa," Azmee tace "Ae basu kai ga dawo cikin gidan ba Shi da Omar, pls kada ki koma bacci ko kuma ki sanya alerm na wayarki in sun dawo ki tabbatar kin kai masu abincinsu, sannan kada ki manta ki bama Omar list din da mukayi masa acikin memo dinki,' Sehrish ta amsa mata da cewa "to shikena insha Allah zan bashi, mu kwana lafiya," Tayi ma azmee sallama sannan ta fito ta wuce nata ɗakin, gefen gado tasamu ta zauna sannan ta miƙa hannu ta ɗauko handbag ɗinta, wayarta ta ciro daga ciki sannan ta shiga dannata, Tunawa tayi da maganar Azmee da tace mata in zatayi amfani da data, wi-fi kawai zata kunna, Cikin sauri tasanya yatsanta ta janyo top of the screen din wayar ta, danna wi-fi ɗin ya kunnu, tsayawa tayi tana tunanin me zata fara yi da wayar yanzu, tana cikin tunanin nan taji ƙarar shigowar motocinsu cikin gidan kusan ƙarfe 11-30 na dare, mayar da wayar tayi saman bedside drawer ɗinta ta ajiye asamanta, miƙewa tayi tana jiran su kammala shigowa sai taje ta kai masu, sai da tabari 12 tayi dai-dai a lokacin tasan sun kimtsa kowannansu na a bedroom ɗinsa, Sannan ta fito ta wuce kitchen ba ƙaramin daɗi taji ba ganin azmee ta kammala zuzzuba musu komai na dinner ɗinsu, a cikin tray guda biyu ta jera masu asaman table na kitchen ɗin, Hannu kawai tasanya ta ɗauki tray ɗaya ta wuce dashi sashen marshal Omar sallama da ƙarfi tayi saboda yaji ta da kyau, kasancewar yana acikin bedroom ɗinsa bayan tajiyo Muryarsa yana amsa mata sallamarta ta, sai ta shiga cikin falon nasa ta ajiye masa tray ɗin asaman table, sannan ta fita cikin sauri tunawa da Memo ɗin da azmee tace ta bashi, bedroom ɗinta ta shiga ta dauko memon data bari asaman gadonta, sannan ta koma part ɗin nasa a lokacin har ya fito jikinsa sanye da jallabiya ash, wuri yasamu yazauna saman sofa fuskarsa ɗauke da ɗan murmushi ganin Sehrish, Ƙarasawa tayi inda yake tare da gaishe shi "Yaya Omar barka da dare, ya gajiyar aiki," ? "Alhamdulillah miss Sehrish, ya maganar aikin dana saku? Ina fata komai ya tafi dai-dai, sannan ya gajiya nasan kun kwaso ta ko? Murmushi tasaki tare da miƙa masa memo ɗin hannunta tace"Gashi nan, mun dudduba gidan duka kuma mun rubuta duk wani abu na furnitures da za'a buƙata acikinsa," Jinjina kai Omar yayi bayan yasanya hannu ya kar6a yana duddubawa yace "Very good, naji daɗi sosai gaskiya kunyi ƙoƙari, insha Allah zuwa gobe zanyi oder na duk wannan abubuwan da kuka lissafa ana buƙata acikin gidan, zuwa dai next week zan sake tuntu6arku," Sehrish tace "toh Allah ya kaimu lafiya," Har ta juya zata tafi ya kuma cewa "kina zuwa school ne? Ko baki fara ba? Sehrish tace"a'a ban fara ba, amma aunty azmee tace zan fara cikin kwanan nan," Omar yace "Owk, inaso ne suma yaran da nakeson kawo wa cikin gidan can, su fara zuwa school amma zan jira naga wadda zaki fara zuwa, in yaso suma saina sanya su amakaranta ɗaya dake," Murmushi sehrish tasaki tare da cewa "mata ne suma? ta tambaya tana kallonsa a lokacin harya fara cin abincinsa yace "Eh ƴan mata ne, kyawawan gaske inason yaran sosai tun dana ganki sai na ga fuskarki tana koma mun irin tasu, nasan saboda son da nake masu ne da kuma kewarsu da nake yi,......' ya ƙarasa maganar asanyaye, Hakanan sehrish taji gabanta ya ɗan faɗi raaasss! amma batasan dalilin faɗuwar gaban nata ba, taso ta tambaye shi sunayen su amma tunawa da cewa ba ta kaima babban yaya abincinsa ba yasa ta saurin cewa "Allah sarki yaya Omar Allah yabaka ikon Kula dasu, yasa su zama alkhairi agare ka,' Ya amsa mata da "Amin," Sannan cikin sauri ta fuce ta koma kitchen sai da tafara haɗa masa yankakkun fruits acikin madai-daicin plate ta azashi asaman tray ɗin sannan ta fuce hannunta dauke da tray ɗin acikin babban falon suka ci karo da haroon wanda fitowarsa kenan daga part dinsu, night dress ne ajikinsa riga dai-dai guiwa, kawar da kanta tayi tare da miƙar hanya tana jiyo shi yana cewa "a rinƙa haɗawa da sallar dare ko an samu adace asamu shiga," Murmushi sehrish tasaki batare da tace komai ba bayan ta isa part ɗinsa da sallama tashiga, baya acikin falon nasa ƙarasawa tayi ta ajiye masa asaman table dinsa, sannan ta tattaka izuwa bedroom ɗinsa tsayawa tayi abakin ƙopar ɗakin nasa, sallama tayi masa amma shiru babu amsa hakan na nufin yana cikin toilet ko kuma bacci ya ɗauke sa ne, aranta tace "Allah yasa baiyi bacci ba," ɗan sa ƙafarta tayi cikin ɗakin nasa ta shiga ciki sai uban ƙamshi ke daker hancinta kamar wadda tashiga gonar turare, samun shi tayi baje a saman gadonsa daga shi sai Short ajikinsa, ji tayi gabanta ya faɗi rass saboda yadda surar shi ke ɗaukar idonta, sam tarasa me zatayi ta tashe shi don tasan dole akwai yunwa atattare dashi, kuma in ya tashi da safe yaga ba'akai masa abinci ba zai iya tuhumarta, Shawara ta rage ma mai shiga Rijiya, tana cikin wannan tsayuwar abakin ƙopan ɗaki nasa ƙafarta har ta soma rawa saboda gajiya da tsayuwa, Wani irin Juyi taga yayi daga saman gadon nasa gaba ɗaya ya tafi dukansa zai faɗo daga saman gadon, agigice sehrish ta watsa ciki da gudun gaske ta ƙarasa tare da kai hannu zata tarbesa sai gashi ya buɗe blue eyes ɗinsa kuma nan take yasanya hannusa ɗaya ya dafe ƙasan yarda bazai faɗi ba, Tsayawa tayi tana faman sauke haki tare da sauke ajiyar zuciya, matsawa yayi tare da cire hannunsa ya gyara kwanciyarsa saman bedmattress ɗin sannan ya ɗan ware idonsa akan Sehrish dake atsaye, mamaki ne ya kamasa ganin ta tsaye dab da gadonsa me hakan ke nufi badai tazo bane don ta hanasa faɗuwa ba, ƙarfin halin ta yabashi mamaki shin ko ta ina zata iya ruƙoso daga faɗuwar da ya kusan yi? tabbas da ace sehrish takai hannunta da nufin ta dakatar dashi daga faɗowa daga saman gadon,ƙarshenta ya faɗa mata ajikinta ya danneta tagaza tashi don kuwa ko kusa sehrish bata da ƙarfin da zata iya taimakonsa daga faɗuwa,' Sunnar da kai ƙasa sehrish tayi cikin jin kunya sam tarasa gane ma kanta, ita dai kawai burinta karya faɗo ƙasa yaji mummunan rauni shiyasa tayi yunƙurin tarbosa, Kasalalliyar muryarsa ce ta ratsa ta da cewa"Sannu da ƙoƙari, amma kada kiyi attempting cewa zaki ruƙoni next time, if not jikinkin ki nei zai gaya maki," Jinjina kai sehrish tayi tare da cewa"kayi hakuri bazan ƙara ba," Shiru yayi tare da mayar da idonsa ya lumshe su, yana faman sauke ajiyar zuciya, ɗagowa ta danyi tare da kallonsa tace "dama......na kawo maka dinner ɗinka ne, yana a falo na ajiye," Kusan minti 5 da yin maganarta ta sannan yace"Shigomin da fruits tare da Coffee, su kawai nake buƙata," Juyawa tayi cikin sauri ta koma cikin falon hannu tasa ta ɗauki plate ɗin dake dauke da fruits ɗin ta shigar masa dashi saman front table ɗim gadonsa ta ajiye masa, sannan ta koma ta dauko masa hadaɗɗen Coffee din dake acikin Cup ta dawo ɗakin nasa a lokacin har ya tashi zaune ya sauko da ƙafafunsa ƙasa, a gefen plate ɗin ta ajiye masa sam yagaza buɗe idanunsa da alama ba ƙaramin bacci yake ji ba, sai faman cizon pink lips ɗinsa yake yi, Ita dai burinta ya buɗe idonsa yafara shan fruits ɗin kafin ta tafi, don batason ya kwanta bai ci komai ba acikinsa 😒 Muryarsa taji yace"What are u waiting for? Ko zaki ban abaki ne? ya faɗi a time din yaɗan ware idanunsa masu ɗauke da bacci, Cikin sauri sehrish tace "a'a sai Allah yakaimu, mu kwana lafiya," ta fadi tare da juyawa cikin sauri ta fuce daga ɗakin nasa sai da tafara tsayawa ta dauki food stuffs din dake acikin tray ɗin da ta ajiye masa sannan ta fuce dasu, a kitchen tasamu wurin ta zauna saman dining table ɗin ciki, buɗe kayan abincin tayi tazauna ta shaƙe plate tana ci, bayan ta kammala ta koma bedroom ɗinta sai da tafara yin sallar isha'e sannan tayi addu'ar yin bacci taja bargo ta lullube jikinta cikin wani irin yanayi na abunda yafaru tsakanin ta da SGR, ***************AUNTY BABBA********** Da kanta ta girka masu hosana da jahad lafiyayyen abinci ta kuma jera masu shi adining, su duka suka halarta suna ci jahad na kusa da uosana polyayin da Hafsat ke kusa da mommynta dama mai 4 seats ne, Duk sun kasa sakewa suci Abincin saboda fargabar da suke ji aransu, kwarama hussana tasamu tana shan kakkauran tea ɗin data haɗa mata tare da bread wanda yaji butter ajikinsa, ɗagowa Aunty babba tayi ta kalli jahad tare da cewa "My daughter me yake faruwa ne? Naga tun ɗazu sai fama juya cokali kike yi acikin plate, yakamata ki fara cin abincin ko saiya huce"? ta tambaya cikin nuna kulawa, murya na rawa jahad tace "babu komai Aunty zanci ne yanxu," Jinjina kai aunty babba tayi tare da cewa "kwara dai kici ta da zafin ta, saboda in ta huce baza tayi maki daɗin ci ba," Jahad ta amsa da toh sannan ta soma cin taiyar pasta din dake agabanta, Mayar da idonta tayi kan na hussana tace "Yawwa my daughter, ae ke na lura bakya wasa da abinci da alama, kamar ni kike, shiyasa gani nan kamar buhun masara sai uban auki," Jin abunda tace yasamu fashe wa da dariya su duka banda hafsat dake satar kallon mommyn nata, abun ɗaure mata kai yake ganin yadda lokaci guda Mommynta ta sakewa yaran aranta tana cewa "gaskiya Mommy ba ƙaramar ƙuruwa bace wurin iya tsara tuggu, ta iya shu'umanci Allah kaɗai yasan me take shirya wa, koma dai menene nidai ina nan ina zuba ido in gani......👀 Murmushi Aunty babba tasaki tana kallonsu ganin yarda tasanya su nishaɗi aranta tace "haka nake so don kutmar ubanku a hankali zan canza muku tunani har na cimma burina," a fili kuma ta washe baki tana cewa "ku hanzarta ku kammala ci dare yayi sosai yakamata ace yanzu kun kamma yi nisa a bacci, sannan jahad kada ki manta kafin ku kwanta ki tabbatar kin ba Hussana maganinta, Jahad ta amsa mata da "toh," Bayan sun kammala yin dinner ɗin nasu suka wuce bedroom din hafsat bayan hussana tasha maganinta sannan suka kwanta, bacci mai nauyi ya ɗauke su............. Kallon Hafsat aunty babba tayi a lokacin itama idonta nakan Mommyn nata, "tun ɗazu na lura da satar kallona da kike yi shiru kawai nayi," aunty babba ta fadi tana kallonta Hafsat tace "hmmmm mommy kenan ni so nake ki faɗamun abunda kike shiryawa game da twins ɗin nan yakamata na sani," Dariya aunty babba tayi kafin tace "bai da amfani koda kin sani hafsat ! ki ma daina tambayata domin kuwa bazaki ta6ajin mutuwar sarki abakina,!" Jinjina hafsat tayi tare da miƙewa daga kan dining ɗin tace "Shikenan Mommy kwarama ki ruƙe sirrinki, yarda in asiri ya tashi tonuwa ke kaɗai zakiji jiki ban dani, ni dae nayi nan," tana faɗin hakan ta wuce cikin bedroom ɗinta, Saman Sofa ta kwanta tare da jan bargo ta lullu6e jikinta, Shu'umin murmushi Aunty babba tasaki tare da cewa "Yanzu wasan ya soma, " 😳 Nikuma nace Allah yaba mai rabo SA'A ***********AFTER 1 WEEK********* BAYAN SATI ƊAYA Acikin waɗannan kwanakin Jahad da hussana ba ƙaramin kwanciyar hankali suka samu ba, sun samu ƴanci sosai acikin gidan jikinsu yayi kyau ba laifi sun ɗan murmure, gashi hafsat bata gajiya da ɗawainiya dasu har fita takeyi dasu yawan shaƙatawa, su fita shan ice cream ko kuma ziyarta gidan friends ɗinta, Aunty babba dae ta zuba ma sarautar Allah Ido burinta kawai Baba alamu ya diro Garin kaduna kafin Zuwan Omar, don tuni Baba Alamu yasanar da ita cewa suna kan hanya yau Litinin zasu sauka kaduna, 😳 A 6angaren Sehrish kuwa tana cikin farin ciki matuƙa saboda makaranta da zata fara zuwa, an riga da an kammala yi mata komai hatta Uniform ɗinta an kawo mata su kusan kala 3, ga sandals ɗinta masu kyan gaske, ga jibgegiyar school bag ɗinta da aka siya mata tare da textbooks na amfani da sauransu, abunda ya rage mata yanzu shine fara zuwa makarantar acikin satin nan, 😇 Tuni Marshal Omar yayi oder na haɗaɗdun furnitures made in dubai, kamfanin da yayi siyayyar kayan su da kansu, suka tsara mashi gidan wa'iyazubilla wurin kyau ba'a magana, komai sabo fal acikin gidan, kayan kitchen ne kayan ɗaki kayan falo komai fa wannan an zuba acikinsa ba abunda ya bari, bari in taƙaice muku zance hatta wannan kayan store na abinci yasa an jibge masu shi, duka freezer ɗin dake acikin gidan yasa an cike masu shi da Kayan marmari dana sha, komai fa Omar ya tanadar musu na jin daɗin Rayuwa, dama abunda ya hana shi zuwa kaduna kenan saboda yafi son saiya fara gyara masu gidan ya sanya musu komai na more rayuwa acikinsa sannan ya je yaɗauko su, kuɗi sosai Omar yaba Sehrish da azmee don suje yi musu siyayya, koda suka tambaye shi size dinsu na kayan da zasu siya masu gudun kar ayi kuskure, sai yace musu komi zasu siya irin na Sehrish saboda yana da tabbacin cewa tsayinsu da komai na jikinsu bazai wuce na SEHRISH ɗin ba, da sukayi masu siyayyar kaya masu yawan gaske kamar irin na sehrish amma nasu yafi yawa saboda su biyu ne, ƙarshe sai dai motar kamfanin da su kayi siyayar ta kawo musu kayan har gidan Abusufyan saboda motar junaid bazata iya kwashe su duka ba, saboda shine ke ɗawainiya dasu duk in da zasu fita, finally dae komai ya kammalu,👍 Ga masu karantawa a facebook indai kuna son Cigaba da kawo muku littafin Abban sojoji to ku hanzarta yin payment recharge card zaku tura ta wannan numbar 08103884440, 200 ne saura 3 pages free ya qare, Ga masu acct gashi nan 3196407426 first bank, Bature hafsat Muhammad, wanda sukayi payment ina sane dasu kuma kuɗinsu bazai tafi abanza ba🙌 [9/12, 8:44 AM] 💋BOSS LADY💋: *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* •·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·? *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ──────────────EPISODE 21-22 ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ💋❤? ~Story & Written~ *BossBature* •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·? Ringing ɗin da wayarta ke faman yi ne ya tashe ta daga guntun baccin daya ɗauke ta, farkawa tayi tana faman yin Hamma, hannu ta miƙa tare da ɗaukar wayarta dake ajiye saman side drawer, duba screen ɗin wayar tayi don taga wanene ke kiranta, lokaci guda gabanta ya faɗi rass ba arziƙi ta miƙe zaune saman gadon tana duban sunan mai kiram nata, sam tagaza sa hannu ta ɗaga kiran saboda tasan mai zai biyo baya,   Kusan sau uku kiran nashigowa cikin wayar ta ta, amma taƙi ɗagawa daga bisa ni mai kiran nata yadaina kira,   Can sai ga ƙarar shigowar Message cikin sauri tasa hannu ta buɗe sakon ta soma karantawa kamar haka _Babu buƙatar yin Sallama! Malama hafsat kin ban mamaki,Na kwashi uban kuɗi nabaki donki gudanar mun da aiki na, amma sai gashi Labari ya risƙeni cewa Anganki kina yawo dasu agari,Don haka ina so ki mayar mun da kuɗina yau ɗin nan in ba haka ba kotu ce zata raba ni dake_!!!!!!!!    Wata Irin nannauyar Ajiyar zuciya Hafsat tasaki afili take furta "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un, ni sam na manta da maganar wannan matar ashe tana sane da kuɗinta, gashi har na fasa su, yanzu dole ne na biya ta kuɗinta ko na samu salama, tabbas zata iya ja mun bala'e Ya zanyi ni! Gashi Yau Daddy zai dawo in yaji wannan abun tabbas Nashiga Ukuna!   Yunƙurawa tayi cikin sauri daga saman gadon jikinta na sanye da dogon wando baƙi sai ƴar Riga fara mai dogon hannu ajikin rigar an rubuta *I Love Paris*    Hannu tasa ta ɗauki ribbom ɗinta da ke ajiye saman mirror, ta ɗaure sumar kanta dashi sannan ta fito cikin hanzari, a babban falon tasamu Jahad da hussana zaune saman 3 seater suna kallo a plasman dake facing ɗinsu, jin alamar tafiyar hafsat yasa su ɗagowa tare da haɗa baki wurin cewa "Barka da fitowa Aunty hafsat," daker ta iya yi masu murmushin yaƙe tace "Yawwa My Twins," sannan cikin sauri ta wuce upstairs direct izuwa bedroom ɗin aunty babba, tun kafin ta shiga ɗakin nata take faman kwala mata kira Mommy!mommy!!Mom!!" Aunty babba da fitowarta kenan daga bathroom waist dinta daure da farin towel tana faman tsane gashin kanta da karamin towel tace"daughter lafiya kike mun irin wannan kiran na tashin hankali !!!," Shiga ciki hafsat tayi tana cewa "Mommy akwai matsala wlh! Dakatawa da tsane gashin kanta tayi sannan ta juyo ta kalli hafsat tare da cewa "Matsala kuma ta me kenan"?Cikin tashin hankali hafsat tace "Mommy wannan matar data ban kuɗi don na zubar mata dasu hussana da jahad, wlh itace ta kira ni yanzu, ban ɗaga kiran ba shine ta turo mun saƙon cewa na biya ta kuɗinta ko kuma ta haɗa ni da hukuma!!Ta ƙarasa maganar tana jira taji mai Aunty babba zata ce, abun mamaki sai taga ta fashe da dariya mai sautin gaske....... Cikin ruɗu hafsat tace "Mommy na faɗa maki tashin hankalin da nake ciki maimakon ki tayani jimami amma sai naga kina dariya saboda me!? tsagaitawa da dariyar Aunty babba tayi sannan tace"Hafsat kenan to ni menene ruwa na aciki? Ki mayar mata da kuɗinta mana shine kwanciyar hankalin ki," Muryarta tamkar xatayi kuka tace "Amma mommy sarai kinsan cewa nariga da na ta6a kuɗin nan kusan dubu ɗari takwas nayi amfani dasu aciki, Bani da kuma hanyar da zan biya su shiyasa nazo wurin ki saboda nasan akwai kuɗinsu Jahad wanda yaya Omar ya bayar ayi masu hidima, Inaso ki bani su don na biyata kuɗinta," Turusss ! aunty babba tayi kafin tayi Uwar shewa tace "Ahayyeeeee ! Anzo wurin dana fi so !! tabbas don kuɗi akwaisu kuwa suna kwance cikin bank account ɗina suna bacci, Ko sisi wlh baxan baki ba !! Har ni zaki watsa ma ƙasa a ido saboda waɗancan tsintattun yaran da ke da kan ki kika ce zasu iya zama nakiyar da zata tarwatsa mun plan ɗina, amma sai gashi akan idona kike nuna masu soyayya don ki 6atamun rai Ko?, don haka kije kiji da matsalar ki ! Ni babu ruwana acikin lamarin ki!!! Ido cike taf da kwalla hafsat ke kallonta cikin tsananin 6acin rai da ƙuna har ta nufi hanyar fita daga ɗakin ta tsaya tare da juyowa ta kalle ta tace "Mommy naji duk abunda kika ce ! Nayi mamakin yarda kike tada jijiyoyin wuya akan kuɗin da bada gumin ki kika same su ba! Kuɗin nan Mallakin Su hussana ne! saboda su Omar yabada ayi masu hidima, ke kuma kika kwamashe su Saboda son zuciyarki, don haka muddin kika ce zaki hanani kuɗin nan, zan kira yaya Omar ne na tona maki asiri game da duk irin cin Zalin da kika yima Twins ɗinsa.............' dakatawa tayi da maganar tana faman haƙi, Aunty babba kuwa wani irin shu'umin murmushi tasaki kafin tace "and then So What Hafsat! Go ahead ki faɗa masa wlh ko ajiki na! Ni nasan yarda zan fidda kaina wlh, kece a ruwa bani ba, Ni dan Allah fuce mun daga ɗaki............ tayi maganar tare da nuna ma hafsat hanya alamar ta fuce mata daga ɗakinta, murmushin takaici kawai hafsat tasaki kafin tasa kai ta fuce daga ɗakin, cikin tsananin jin 6acin rai Fuuuuu ta wuce izuwa downstairs ta wuce bedroom ɗinta, wuri ta samu gefen gadonta ta zauna cikin tashin hankali tana cikin wannan tunanin message ya sake shigowa cikin wayarta data bari saman gadon,Hannu tasa ta ɗauki wayar tare da buɗe saƙon ta karanta kamar haka "ina tsammanin jin alert ɗin kuɗina, a yau ɗin nan in ba haka ba, nasamu labarin cewa yau general ishaq zai dawo wato Abbanki, kai tsaye zanzo har gidan ku, adai-adai lokacin dana tabbatar cewa ya iso gari zan shigo na tada maki 6alli" Shiru hafsat tayi gabanta na wani irin faɗuwa tuni idonta sun canza launi, bata da wata mafita daya wuce ta koma ma mommyn nata, ta lalla6a ta tasamu tabata kuɗin ta mayar ma jarababbiyar matar nan, ko sun rabu lafiya, Zumbur ta miƙe tashi ga yin sintiri acikin ɗakin nata cikin tsananin damuwa, Sallamar Jahad ce ta katse mata dogon tunanin da ta shiga, "Jahad har kun gama kallon"? ta tambaya yayin da take ƙaƙaro murmushi a fuskarta, Jahad tace "A'a aunty an fara kiran sallar la'asar ne shine nashigo nayi sallah," Hafsat tace"Allah sarki, na lura bakya wasa da sallah Jahad, da zarar lokacinta yayi komai kike saina ga kin dakatar dashi don yin ibadah,"Murmushi jahad tasaki tare da shige wa ciki tana cewa "aunty babu abunda yakai sallah muhimmanci acikin dukkan aiyuka, babu wani jin daɗi na duniya da zai sanya na manta da yin ibadata abisa lokacinta..........' Wayar Hafsat da tayi ringing ya hana jahad ƙarasa jawabin nata, cikin sauri hafsat taƙarasa ta ɗauki wayar tare da dubawa, ganin numbar matarnan ce tsanya ta, yin wurgi da wayar, hankali tashe ta fuce daga ɗakin......... Shiru jahad tayi cikin mamamki ganin yarda hafsat tayi wurgi da wayarta ga fuskarta da alamun damuwa hakan na nufin wani abu na damunta, "Ya Allah ka yaye ma aunty hafsat damuwar dake damunta, ka kawo mata mafita Alfarmar Annabi Muhammad (S.A.W)," ta faɗi acikin ranta sannan tashige cikin toilet donyin alwala,kai tsaye Hafsat ta koma ɗakin Aunty babba, lokacin da ta shiga har ta kammala shirya kanta cikin atampha Embellished mai tsadar gaske da kyau, tana zaune saman stool agaban mirror tana shafa jan baki abakin ta, Hafsat ta shigo, wuri tasamu gefen gadonta tazauna tana kallonta,Juyowa Aunty babba tayi ta kallota tare da sakin Murmushi tace "My daughter, Look at my face how do i look? Kinsan yau Abban ki zai dawo, Shiyasa na taƙarƙare ina masa kwalliya, yau inajin kaina tamkar sabuwar amarya," Fuska a ɗaure hafsat tace"Kinyi kyau,"Aunty babba tace "Ae ko baki faɗa ba, nasan cewa ni kyakkyawa ce, tun da gashi nan ke ma albarkacin kyau na kin samu har kinyi ɗan haske da dogon hanci ga gashi har kina taƙama," Hafsat tace "hmmm mommy kenan, amma dai kinsan cewa Hanci na ba irin naki bane ko? kuma da kike maganar kyau kar ki manta Abbana fa kyakkyawa ne hausa fulani," Tsoki aunty babba tasa ki tana cewa "Menene wani hausa fulani, Jinin Larabawa ake magana, kowa yasan mu da kyau babu jinsin da suka kai mu kyau aduniya kaf," ɗan guntun murmushi hafsat tasaki kafin tace"Ae shi kyau mommy ba'a fuska yake ba, ko a Surar jiki, a zuciya yake!! Duk kyan mutun muddin zuciyarsa baƙa ce, to ya tashi abanza mummuna ne shi,'Jin abunda hafsat tace ne yasa ta ajiye jan bakin dake hannunta tace "Tashi ki fuce mun daga ɗakina ! Bansan ma uban me yakawo ki ba," Shiru hafsat tayi batare da ta motsa daga inda take ba, illa kawai ta zuba mata ido,"baxaki fuce mun daga ɗaki na ba"? ta faɗi fuska aɗaure, Sassauta murya hafsat tayi tare da cewa "Kiyi haƙuri mommy in na 6ata maki rai, zuciyata ce bata mun daɗi........' Aunty babba ta katse ta da cewa "don zuciyarki bata maki daɗi shine kika zo na wanke maki ita? Ko me? girgiza kai hafsat tayi tare da cewa "kusan hakane mommy, ni yanzu zuwa nayi ki taimaka mun na mayar ma matar nan kuɗinta, ta addabe ni da kira, narasa ya zanyi," Murmushi aunty babba tasaki tare da juyowa sosai tana fuskantar hafsat tace,"Na Amince zan baki kuɗin ki mayar mata, amma bisa wasu sharuɗɗa! In kin bi muzauna lafiya daga ni har ke!? jinjina kai hafsat tayi tace "ina sauraronki, wasu sharuɗɗa ne? aunty babba tace "Inaso ki amince da maganar Fitar da yaran nan daga cikin rayuwarmu !!!!!! ɗagowa hafsat tayi aɗan razane tana kallonta..............Murmushi Aunty babba ta saki kafin taci gaba da cewa "Abun da nake son ki fahimta hafsat, ko da mun bar Omar ya ɗauki yaran nan ya tafi dasu can gidansu, wlh baza su ta6a samun kwanciyar hankali ba, domin kuwa Ke kinsan wacece Ammi ta tsani mutumin da bai da asali ya ra6i jinin ta, koda Omar yakai su can wlh ba zasu tsira ba!domin kuwa Ammi na zuwa zatasa a Kore su daga gidan! don haka yakamata kiyi tunani akan hakan kwarama cikin ruwan sanyi mu rabu dasu Lafiya, Shiru Hafsat ta ɗanyi na wani lokaci kafin tace,"Yanzu mommy Idan na Amince, su kuma yaran Yaya rayuwarsu zata kasance?ina za akaisu? Ina tsoran Rayuwarsu ta salwanta ! Aunty babba tace "Hafsat don me zaki damu akan haka? ni in dai kin Amince zan sa akai yaran gidan marayu acan zasu samu kulawa, kuma dama can yafi dacewa dasu, in yaso sai mu runƙa zuwa muna kai musu Ziyara tare da tallafi koya kika ce? shiru hafsat tayi na wani lokacin sannan tace"Shikenan Mommy na yarda da hakan, Amma yaya Omar fa? In yazo yaya zamu ce mashi in ya tambayi twins ɗinsa? ɗan murmushi aunty babba ta saki ba ƙaramin daɗi taji ba jin yarda hafsat ta amince yanzu komai zai fi zuwa mata da sauƙi, taci gaba da cewa "Hafsat duk yarda zamuyi kada mu bari Abban ki yasan da yaran nan har izuwa gobe, Akwai wanda nayi ma magana zai zo gobe insha Allah, Shi zai kai su gidan marayun, Sannan maganar Omar tunda har yakai yanzu bai zo ba, inajin cewa tabbas akwai abunda ya tsaida shi wannan ba matsala bace kibar mun komai a hannuna ni nasan yarda zance mashi ya yarda.................. Jinjina kai hafsat tayi jikinta a matuƙar mace saboda sabon da tayi da Su hussana da jahad sam batason rabuwa dasu amma kuma babu yarda zatayi this is the Only solution !!! Ajiyar zuciya ta saki tare da kallon Mommyn nata tace "Shikenan Mommy, ni zan wuce ɗaki sai naji ki ............ Muryarta na rawa take magana cikin sauri ta ƴunƙura tare da miƙewa ta nufi hanyar fita ɗakin tana jin Muryar Aunty babba tana cewa "Yanzu zan tura maki da kuɗin ki mayar mata abunta, kar taja mana bala'e Hafsat bata ce komai ba saboda yanayin da ta shiga, cikin sauri ta fuce kai tsaye ta shiga bedroom ɗinta, Lokacin da ta shiga ta samu su hussana da jahad zaune saman darduma suna karatun Al'qur'ani da kansu, sai taji zuciyarta ta ƙara karaya, cikin sauri ta faɗa toilet tare da rufo ƙopa tana faman shessheƙar kukan rabuwa dasu......................................... __________________SEHRISH__________ Sam bakin ta yaƙi rufuwa don Murya, tun ɗazu ta shimafiɗa uniform ɗinta saman gadonta tare da sandal ɗinta da kuma school bag ɗin duka, ta tasa su gaba sai kallonsu take yi,bakomai take tunani ba face yarda zata fara shiga school gobe Talata, irin wankan da zata ɗauka,tana daga zuƙunne saman gadon nata sae faman sakin murmushi takeyi, hannu tasa tare da shafa uniform ɗin data jera tana cewa "daga gani zasuyi mun kyau,oh ni reeshi yanzu zanyi new friends a makaranta, da na banza da na kirki, Allah dae ya haɗa ni dana gari, ba wanda zasu canza min tunani na ba, ina ƴar talaka dani," ta faɗi da ƴar dariya, Turo ƙopar Azmee tayi tare da shigowa tana cewa "Da alama yau sehrish kin manta da shiga kitchen ko? kin barni da aiki narasa dalilin dayasa kika zubama kayan makarantar nan naki ido,sai kace ba mallakin ki ba"?    tayi maganar yayin da take ƙarasawa ciki, ɗagowa sehrish tayi ta kalle ta fuskarta washe tace "Am sorry aunty azmee, Yanzun nan nake shirin fitowa wlh, na kammala salla ne shine nake ɗan ƙara binsu da kallo,    girgiza kai Azmee ta ɗan yi kafin tace "maza ki tattara kayan nan, ki mayar dasu cikin wardrobe, Kizo maza mu kama aiki,'    Sehrish ta amsa mata da Toh sannan ta miƙe cikin sauri ta sauko daga saman gadon, Tattara kayan Uniform ɗin tayi takai su cikin wardrobe, bayan ta kammala ta ɗauki mayafinta saman gadonta, tayarfa shi akanta dama riga da skirt ne ajikinta,    Cikin sauri tabi bayan Azmee suka fuce izuwa kitchen,   Cikin hanzari suka soma shirye shiryen fara girkin dare, suna cikin aiki Azmee nagaban gas tana tafasa nama, yayin da sehrish ke ta faman fere kayan lambu asaman Chopping board,    Faɗowa junaid yayi cikin kitchen ɗin jikinsa na sanye da Kayan ball yellow sai faman zufa yake yi da alama shigowarsa kenan daga wurin ball, sam yagaza rufe bakinsa sai faman murmushi yake yi,   "Wlh harka ban tsoro junaid, yarda ka faɗo suddenly,jibi jikin ka sai faman zufa kake yi," Sehrish ta faɗi tana nuna sa da wuƙar dake hannunta,   Juyowa azmee tayi tana kallonsa batare da tace komai ba,   "Zuwa nayi in tunasar maki cewa, gobe ni zan kai ki school da mota ta," ya faɗi yana faman sauke ajiyar zuciya,. Sai lokacin azmee tace "Salon wahalar da kai junaid, ka bari tahau school Bus mana,ƙwara tasa ba da bin motar makaranta tun yanzu, amma in kace zaka runƙa kai ta ɗawainiyar zatayi yawa, kuma kasan sarai Babban yayan ku baya so kana fita ko?.ta faɗi tana kallonsa,.   turo baki junaid yayi tare da ɗan buga ƙafarsa yace "Nidai Aunty azmee zan kaita, just for tomorrow cos this is the first time da zata fara zuwa school ɗin yakamata tasan wasu abubuwan inaso zan nuna mata ne, tun da ni nasan school ɗin sosai...."   gaba ɗaya kallon shi suke yi yarda yake magana cikin shagwa6a, yana faman bubbuga ƙafa Dariya azmee tayi don ta Lura rigimarsa ce ta tashi, dama aduk lokacin daya buga ball sosai yagaji alokacin rigimarsa tafi tashi,   Sehrish tace "Shikenan junaid gobe kai zaka kaini school, amma yanzu kana buƙatar yin wanka ka ɗan huta,,"    ɗan murmushi yayi jin abunda tace "Amma ina jin yunwa fa sosai," ya faɗi yana kallonta   "Shikenan kada kadamu yanzun nan zan kawo maka abinci,"   "Yawwa My lovely sis," ya faɗi tare da kama hanya ya wuce upstairs room ɗinsa,    A tray ta shirya masa coffee tare da snacks, sannan ta fito ta wuce upstair domin takai masa, tana hawa saman stairs ɗin sai ga SGR shi da Marshal Omar suna nufo stair ɗin, ganin su zo dab da benen yasa ta saukowa gaba ɗaya don tabasu wuri su wuce, dukansu suna sanye da jean da t-shirt, sai faman sauri suke alamar akwai wani Uzuri dake gare su, suna ƙarasowa inda take tsaye tayi saurin cewa "ina yinin ku," Omar ne kawai yasamu damar Amsa mata, amma shi SGR sam ko kallo ma hasalima baisan da mutun a wurin ba, gabanta ne ya faɗi don alamu sun nuna cewa ba ƙaramin abubane ganin yanayin fuskar kowannansu Especially Omar da ta sani, Kullum cikin sakar mata fuska yake duk in suka haɗu amma yau dakyar ya amsa mata gaisuwarta,   Bin su tayi da kallo, yayin da suka wuce kai tsaye hanyar fita falon suka nufa, har sun kusa fita Omar ya juyo ya kalle ta, bakomai yasa Shi juyowa ba fa ce tuna Hussana da jahad yau tsawon wata kenan baije ya dubo su, saboda busy ɗin daya shiga, yana da burin zuwa ɗaukosu amma aiyuka sun hana shi, Ajiyar zuciya yasaki tare da mayar da kansa suka sa kai suka fuce,    sam sehrish tagaza yin motsi da ƙafafunta, hakanan ta dunga jin gabanta na faɗuwa, bata kai ga hawa benen ba, taji dirar motoci cikin gidan nan take ta sake jin faɗuwar gaba, cikin sauri ta haye upstairs ɗin da hanzari ta shiga bedroom ɗin junaid a lokacin yana cikin toilet yana wanka, ajiye masa tray ɗin tayi saman table, sannan tafito da sauri-sauri ta fito daga babban falon ta tsaya abakin ƙofar shigarsa, .    Kamar dai ranar da SGR da Omar suka zo Nigeria tare da uban security guards na sojoji haka yau ma, tsoro ne yakama sehrish gudun kar ace US zasu  koma,     Tana ganin lokacin da suka shiga cikin motocinsu kuma nan take motocin ajere suka nufi dogon titin da zai fidda ka daga cikin gidan,    Komawa ciki tayi da gudun gaske ta faɗa kitchen tana faman kwalama aunty azmee kira, a ɗan razane azmee ta juyo ta kalle ta tare da cewa "Sehrish lafiya kuwa kike ta faman kwalamun kira haka!?   Cikin tsananin tashin hankali tace "Aunty azmee meke faruwa ne? Yanzun nan naga Babban yaya tare da Yaya Omar, sun fito fuskokinsu ba annuri kuma ga tarin motoci can sun fita dasu,"    tsayawa azmee taɗan yi jimmmmmmm tana ɗan tunani kafin tace "Tabbas ina hasashen cewa Us zasu tafi Saboda ɗazu da safe naji ƙishin-ƙishin ɗin cewa Momynsu matar Uncle ɗinsu donald tana fama da blood cancer, To ina da tabbacin cewa kodae ta rasu ne...........'    Zaro ido sehrish tayi cikin tsananin tashin hankali take furta "Innalallahi wa'inna ilairaji'un Allah yasa bata mutu ba, Yanzu shikenan in suka koma ko yaushe zasu dawo.....'    Murmushi Azmee tayi kafin tace "naga kin tayar da hankalin ki, nasan saboda Tafiyarsu Rafayet ne bawai don jin mutuwar ba,     Hannu sehrish tasa tare da rufe fuska saboda hawaye da taji sun tafo mata,    bin ta da kallo kawai azmee tayi cike da mamakin ganin  tana shessheƙar kuka,    Matsawa tayi kusa da ita tare da dafa ta tace"Sehrish !! Wannan kukan na menene? Ba dai don tafiyarsu bane?    shiru kawai tayi batare da tace komai ba, ita kaɗai tasan me take ji aranta, gaba ɗaya fuskarta ta damuje da hawaye,     Jinjina kai azmee tayi tare da cewa "Ki koma ɗaki ki kwanta kawai,"   Cikin kuka sehrish tace "a'a aunty azmee zanyi aikin,"    Azmee tace "a'a banaso ki tafi kawai zan ƙarasa abuna,"    Juyawa sehrish tayi tare da fuce wa daga kitchen ɗin ta koma bedroom ɗinta, saman gado tafaɗa tare da cigaba da kukan, To fa sehrish komai yasata yin kuka? Allah wa'alamu,   Azmee kuwa ta jima tana mamakin dalilin kukan Sehrish tarasa gane mata, aranta tana cewa "Badai saboda tafiyar SGR take kuka ba? Don ta lura da yadda sehrish ke matuƙar ƙaunarsa, sam bata iya fira batare da ta, Amabaci sunan shi ba ita dae kawai tafison jin Ana maganarsa,nan zakaga sakewarta,    "Lallai ne akwai Babbar Matsala, muddin abunda nake zargi ya tabbata,ya zama dole in ja ma Sehrish burki, don gujema kamuwa da CIWON ZUCIYA,"!! Azmee ta faɗi acikin ranta,   _______________________ Sehrish kuwa Tuni wani Irin zazza6i taji ya rufe ta lokaci guda, jikinta har kerma yake yi wurin janyo bargonta dake asaman gadonta ta lullu6e jikinta dashi, tana faman fidda numfashi mai zafin gaske, sam tarasa ina zata tsoma ranta ita kaɗai tasan irin raɗaɗin da take ji acikin zuciyarta Har wuraren Sallar Magrib sehrish bata motsa ba, tana nan yarda take ƙudundune cikin barko,tamkar mai bacci alhalin nan Idonta biyu jikinta ne kawai da bayayi mata daɗi, Acan ciki kuwa fitowa junaid yayi bayan yasha baccin sa, ya sauya kayan jikinsa izuwa riga da wando, lokacin daya sakko down yayi mamakin ganin Azmee ita kaɗai tana faman jera masu dinner a dining, ƙarasawa yayi cikin sauri yana cewa"Aunty Azmee ina sehrish ɗin ne? Ita bazata fito ta tayaki ba? Azmee ta ɗan ɗago ta kallesa tare da cewa "Junaid ni kaina bansan meke damun Sehrish ba, Lafiya lou fa muke aiki da Ita, amma tunda tazo ta tambaye ni game da babban yayanku da Omar da taga sun fito fuskarsu cikin wani irin yanayi, kuma taga Sun fita tare da motoci dayawa, shine nake ce mata may be Us zasu je, tunda ɗazu da safe naji ƙishin ƙishin ɗin cewa Matar Uncle ɗinku donald tana fama da blood cancer may be ta rasu ne.....shine fa kawai sehrish takama kuka har nace mata ta koma ɗakinta kawai ni zanyi aikin," ta ƙarasa maganar cikin damuwa, Junaid kuwa shiru yayi hankalinsa ya rabu gida biyu, sam ya rasa gane inda maganar Azmee ta dosa, cikin mamaki yace "Us kuma? Taya babban yayan mu zaibar ƙasar nan batare da sani na ba? Anya kuwa aunty Azmee am just doubting about it bana tunani Us zasu je, kuma Matar uncle donald bana tunanin ta rasu gaskiya, tunda da naji ko a wurin Abban mu ne, Ni dai Allah yasa ba wani abu bane ya faru mummuna," ya faɗi cikin tashin hankali kafin ya wuce yana cewa "Bari naje wurin Sehrish ɗin naji meke damunta," Azmee tace "to shikenan," A hankali ya tura ƙopar ɗakin yashiga da sallama, tsayawa yayi yana kallonta yarda take ƙudundune cikin bargo, A hankali ya kira sunanta "Sehrish..........' shiru bata amsa masa ba, ƙarasawa yayi izuwa gab da gadon nata yaɗan zauna gefe tare da sa hannu ya yaye mata bargon dake jikinta, dogon numfashi taja tare da cewa "Junaid ka mayar mun da bargona, Sanyi nake ji," Junaid yace "Reesh wai meke damunki ne? Aunty azmee ta faɗamun cewa kinbar kitchen kina faman kuka? Cikin kuka tace "Junaid wai dagaske ne cewa Babban yaya da Yaya Omar us zasu koma yau? Sakin baki junaid yayi yana kallonta cikin tsananin mamaki amma bai kawo ma ransa komai ba sai cewa yayi "Sehrish dama akan wannan kika shiga damuwa? to ki kwantar da hankalin ki, Yaya Omar da yaya Rafayet bana tunanin sun bar ƙasar nan ne, Aunty azmee ce kawai tace maki hakan a hasashen ta, just calm down ur mind My lovely sis... . ...........jin abunda junaid yace yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da miƙewa zaune daga saman gadon tana cewa "ngde da jin hakan junaid, naji ma anata kiran sallar magrib bari naje nayi alwala," junaid yace "to shikenan nima bari naje nayi salla,pls reesh karki ƙara sa damuwa irin haka, kuma in kin kammala sallar, ki fito muyi dinner atare," Murmushi ta sakar masa tare da cewa "Ok my lovely bro, da zarar nayi sallah zan fito nima," lumshe ido junaid yayi tare da buɗe su akanta fuskar nan ɗauke da Murmushi, sai da yaga sehrish tashiga toilet sannan yafuce hankalinsa a kwance..........................? remain 2 pages free su ƙare, wanda baiyi payment ba ya hanxarta Yi, Abban Sojoji 300 ne, discount da nayi na Abbban sojoji fans group ne kawai 200, Vip kuma 700, bank details ɗin da za'a tura,3196407426 First bank, Bature Hafsat Muhammd Evidence of payment 08103884440 [9/13, 11:08 AM] 💋BOSS LADY💋: *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* •·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·? *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ──────────────EPISODE 23-24 ﻗﺼ? ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴ? ﺳﺤﺮﻳ? ﻭﺍﻟﺠﺮﺍ? ﺍﻟﻌﺎ? ﺭﺍﻓﻴﺖ💋❤? *Mallakin Hafsat Bature Moh'd* ~BossBature~ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·? Fitowa tayi tana faman yarfar da ruwan alwalar dake hannunta,hijab da sallaya ta ɗauka a wardrobe, ta shimfiɗasu tare da kabbara sallah,bayan ta kammala tabar darduman anan saboda in an kira isha'e, hijab ɗin ta cire tare da ajiye shi saman gadon sai ta ɗauki Mayafinta, ta yafa shi akanta, Fitowa tayi kai tsaye ta wuce dining, a lokacin junaid ma yana a wurin tare da Haroon sai kanal Yusif duk suna zaune, yayin da Azmee ke faman ɗawainiyar Zuba masu abinci,    Ƙarasawa tayi tare da cewa "Sannu da aiki Aunty Azmee," Juyowa azmee tayi tare da kallonta tace"Yawwa mutuniyar sarkin kuka, Lamarinki naban mamaki kamar me iska,"    Sunnar da kai Sehrish tayi tana ɗan Murmushi kafin daga bisani ta gaishe da Kanal yusif da fara'arsa yace "Our Princess,duk yau ban saki a idona ba, Yakamata ace kina sakewa da ƴan uwanki sosai,"    Murmushi kawai Sehrish tayi tare da zama kusa da junaid suna facing ɗin kanal yusif da haroon ta hannun dama,    Zuba mata abinci azmee ta soma yi a plate, junaid dake a gefenta yace"Da ace baki fito ba ko, da bazanci komai ba Allah,"    Kafin sehrish tace wani abu haroon yayi saurin cewa "Saboda ciki ɗaya kuka fito ko? murmushi junaid yayi tare da cewa "Yaya Haroon yadda na ɗauƙi Sehrish ta wuce haka a wurina," ta6e baki Haroon yayi yana kallonta, Harara Sehrish taɗan wurga masa tare da murguɗa masa baki, jinjina kansa yayi tare da cewa "An fa samu freedom of sitting the same table da Ƴa'ƴan masu gida dole ayi iya shege,    Jin wannan maganar ta Haroon ta sanya junaid ɗaure fuska lokaci guda yace "Yaya haroon me kake nufi da hakan?    Haroon yace "Abunda ranka yabaka"   Dakatawa kanal yusif yayi daga cin abincin da yakeyi ya ɗan bubbuga plate ɗin dake gabansa da cokalin hannunsa ya bada sauti sannan ya aza idonsa akan na Haroon, Ganin irin kallon da kanal yusif ya jefa masa ne yasa shi, yin tsit ya shiga taitayinsa,    Mayar da idonsa yayi kan Sehrish yace"Sister Yaushe ne zaki fara zuwa school ɗin? yayi hakan ne donya mantar da ita maganar haroon, ganin yarda tayi sanyi lokaci guda,   daƙyar ta ƙaƙaro murmushi tare da cewa "Gobe ne insha Allah,"   Kanal yusif yace "Masha Allah,A matsayina na yayan ki, akwai wani jan hankali da nakeso nayi maki, kin ga gobe zaki fara zuwa, kuma zaki fara haɗuwa da sababbin ƙawaye iri-iri,akwai good friends waɗanda zasu dunga ƙarfafa maki guiwa akan karatu ta hanyar baki shawarwari masu kyau,bayan su kuma akwai bad friends gur6atattu waɗanda majority ɗinsu ba karatu ya kaisu ba,Asarar kuɗin iyayensu kawai suke yi, basa karatu ƴan abi yarima asha kiɗane,babban ma tashin hankalin yanzu majority na irin waɗannan ƙawayen ƴan Lesbian ne,fitsararru marasa kunya waɗanda suka gagari iyayensu da malamansu, burinsu kawai su 6ata tarbiyyar wasu, bana so ki kasance ɗaya daga cikin irin waɗannan ko kusa, dayawa wasu suna kuskuren yin abota da irin waɗannan bad friends ɗin, sai suce ae basu suke aikatawa ba,sun manta cewa zama da maɗaukin kanwa shi ke kawo farin kai,to koda gigin wasa bana so ko fira ta haɗaki da irin waɗan gur6atattun balle harku ƙulla Abota, Ina gargaɗin ki akan hakan ! And i want u to know that Ke yanzu kina ɗaya daga cikin Mutuncin gidan nan!! Kuma kinsan yarda sunan family ɗinmu ya karaɗe ko'ina, ba inda ba'asan Jinin SALAHUDDEEN HUSSEIN ba, don haka yazama dole ki kiyaye mutuncin family ɗinmu da kuma ƙimarsa, ina fata kina fahimtar abunda nake cewa"? Ya tambaya yana kallon sehrish wadda ta natsu tana sauraronsa cikin sauri tace "Ina fahimtar duk wani abu da kace yaya yusif, kuma insha Allah zan kiyaye faruwar hakan,kuma naji daɗi sosai harma baxan iya misaltawa ba,saboda na samu ɗan uwa nagari wanda yake mun nasiha akan na tsira da mutunci,babu wanda ya tunasar dani akan hakan sai kai, kuma insha Allah bazan ta6a baku kunya ba, zan kasance ɗaya daga cikin abun Alfaharin gidan nan,"   taƙarasa maganar yayin da idonta suka ciko da kwalla, gaba ɗaya Azmee da Junaid sun kasa kunne suna sauraron maganar tasu, dukansu babu wanda baiji daɗin maganar Kanal yusif ba, Illa mutun ɗaya Wato Haroon wanda ke ta faman tur6une fuska yana faman hura hanci aransa yana cewa "Insha Allah ni kuma bazan taba barin ki ki xama abun alfaharin gidan nan ba, balle har ki samu matsayi acikinsa, saina san yarda zanyi in tarwatsa komai har inyi sanadiyar korarki acikin gidan nan," ya faɗi yana kallon sehrish rai a6ace yana faman tura dambun nama abakinsa har yana shaƙewa,    Kanal yusif kuwa murmushi ya saki sannan yaci gaba da cewa "Allah ya yarda Sehrish,Nima inason ki zama Abun alfaharin mu gaba ɗaya," ya ƙarasa maganar tare da sanya hannu ya ɗauki glass cup dake ɗauke da Lemu mai sanyi yakai bakinsa yana kur6a,   ƙasa-ƙasa da murya junaid yayi tare da cewa "sehrish nima fa naso nayi maki nasiha akan zuwanki makaranta, amma kash sai gashi Yaya yousouf ya riga ni, amma duk da haka ban makara ba, don Allah sehrish karki canzamun koda kin fara zuwa school don nasan zaki ƙara wayewa sosai..........'   Murmushi sehrish ta saki jin abunda junaid yace, kafin tace "Insha Allah junaid hakan baxata ta6a faruwa ba,mu aminnan juna ne zamu kasance atare ako wane hali na rayuwa, kaine abokin shawara na,"   ajiyar zuciya junaid ya saki aransa yana ƙara samun kwanciyar hankali jin bayanan da sehrish tayi masa,   wayar haroon ce dake acikin aljihunsa ta soma ringing taken waƙar nan da ake cewa "ɗan duniya hayaƙin taba," jin ringing ɗin wayar yasa kanal yusif girgiza kai tare da cewa "Allah ya shirya ka,"   Haroon yace "Ameen don son Annabi," sannan yayi saurin tashi daga dining ɗin yakama hanyar fita daga falon yana zaro wayar daga aljihun wandonsa, ɗaga kiran yayi tare da karawa a kunnansa yana cewa "Shegen bisa ashe har ka isa hotel ɗin, ae ko gani nan zuwa Yanzun nan Allah yasa ka taho mana da harkar nan..........' ya yi maganar da dariya a fuskarsa kafin yasa kai ya fuce,   Bayan sun kammala dinner ɗin junaid suka wuce masallaci tare da kanal yousouf jin ana kiran isha'e,.    Itama Sehrish bayan ta kammala dinner ɗin tare da azmee suka kwashe kayan da sukayi amfani dasu izuwa kitchen, Sehrish ce ta wawwanke su tare da jerasu a ma'ajiyarsu,   Bayan ta fito suka ci karo da azmee tace " Inaso naje na kwanta,pls kada ki bari bacci ya kwashe ki, idan Twins sun dawo ki tabbatar kin kai masu dinner ɗinsu, Shima Abbansu pls ki kaimasa nasan ƙila sai wurin 12 zasu shigo,.    Sehrish tace "To aunty azmee insha Allah baxanyi bacci ba, zan kai masu in sun dawo,"    daga nan azmee ta wuce ɗakinta, itama sehrish bedroom ɗinta tashiga, sai da tafara shiga toilet ta kuskure bakinta, dama da alwalarta,    Fitowa tayi ta ɗauki hijab ɗinta da ta ajiye saman gadonta, ta kabbara sallah _________________________________________________ Tuni General ishaq ya iso gidan ya cika tab da mutane tare da jami'an sojoji da suka rakosa, su Aunty babba sai faman rawar kai akeyi miji ya iso gari, a lokacin hafsat har ta shirya kanta itama tsaf ta kimtsa cikin haɗaɗɗen cord lace Ash colour mai adon duwatsu,rigar mai dogon hannu sai skirt ba ƙaramin kyau kayan su kayi mata ba, gashi dama takware wurin iya kashe kallabi, tare da Mommyn nata da wasu daga cikin abokanan aunty babba da suka zo dana hafsat suke taimakawa wurin tarbar baƙi da abunsha dana ci,    "Jahad ya Omar shiru kodai ya manta damu ne"? Hussana ta faɗi fuska tamkar zatayi kuka tana kallon jahad suna zaune dab da juna daga gefen gadon hafsat,    "Hussana bana tunanin hakan, Ya Omar yana son mu sosai ni ina da tabbacin yana sane damu,kuma zaizo ne insha Allah," acewar jahad Hussana tace "Ni inajin tsoron a rabamu da ya Omar, wlh banso banso....'   Kamar daga sama suka ji Muryar Aunty babba tace "Saboda ƙanin ubanki ne ko? ta faɗi ayayin da take shigowa, arazane suka miƙe tsaye su duka suna kallonta, su biyu suka shigo cikin ɗakin ita da wata hajiya, amma ita ta tsaya daga baya    Kusa dasu taje sannan tasoma magana "Ko da gigin wasa bana so wata daga cikin ta leƙo da kanta daga cikin ɗakin nan ! Saboda Mijina ya dawo kuma banaso ya gan ku, ina fata kun gane?   Cikin sauri suka haɗa baki wurin cewa "Insha Allah aunty bazamu fito ba,"    ta6e baki tayi sannan ta juya bayanta ta kalli matar da suka shigo tare tace "Hajjaju gafa yaran nan da nake faɗa baki, Omar yakawo min cikin gidana,"    ƙarasa shigo wa ciki matar tayi jikinta na sanye da shadda gezna green colour tasha uban aiki a wuyan rigar, tayi ɗaurin ɗan kwalin ture kaga tsiya sannan ta yarfa gyalenta a kafaɗarta,    Alokacin da matar ta ƙaraso Jahad taganta nan take gabanta yayi wani irin bugu zaro ido tayi tana kallonta saboda son tuna inda tasan fuskarta,   Hajjaju kuwa tana ganin su hussana da jahad farat ɗaya ta gane su, a ɗan razane ta dafe ƙirji tare da cewa "Kaiii !!!" taja maganar da ƙarfin tana kallonsu cikin mamaki da al'ajabin wannan Ikon Allahn,   tuni aunty babba tagama ruɗewa ganin yadda hajjaju ta razana da ganinsu, da kuma yarda jahad ta firgita itama wannan alama ce dake nuni da sun san juna kenan ko yaya,   Cike da mamaki Aunty babba tace "Wai meke faruwa ne hajiya rabi? kinsan su ne?   Cikin sauri hajjaju tace "A'a bansan su ba, Kamar dae nata6a ganin mai kama dasu ne,"    tayi maganar tare da ruƙe hannun Aunty babba taja ta, suka fuce daga ɗakin,    Kallon jahad hussana tayi tare da cewa "Jahad wacece wannan matar? Naga kin razana da ganinta,"    "Nima so nake na tuna inda nasanta," Jahad ta faɗi tana faman cizon akaifar hannunta da takai abakinta,   Hajjaju kuwa da taja Aunty babba suka fuce can suka nufa wurin kitchen suka tsaya, ga mutane sai faman shige da fuce suke,.   "Dan Allah ki faɗamun gaskiya hajjaju raina na bani cewa kinsan yaran can ko? Aunty babba ta tambaya tana kallonta cike da son jin ƙarin bayani daga wurinta,   Jinjina kai Hajjaju tayi tare da cewa "Yau naga ikon Allah, Lallai ne duk zakaran da Allah ya nufa da cara,to fa sai yayi ta, haƙiƙa nayi matuƙar mamakin yarda akai har Allah ya haɗa Omar da waɗannan yaran , kai kaga wani ikon Allah nan ! mai matuƙar ban mamaki da Al'ajabi?   Hajjaju tayi maganar cikin nuna mamakinta, Aunty babba kuwa cewa take yi "Hajjaju kin barni acikin duhu, wlh har kinsa hantar cikina ta kaɗa dan Allah kisanar dani me kika sani agame dasu?   dariya hajjaJu tayi tare da tafa hannayenta tace "Ana bura'uba a lagos! yo ke laila da kike cewa zaki sa a zubar maki da waɗannan yaran don ki nisanta su da Omar, idan Kin toshe wannan hanyar to ita waccen ɗayar hanyar da ta ruga isa inda bakya so ya zakiyi da ita?    gaba ɗaya fa Aunty babba ta gama rikicewa da bayanin hajjaju, cikin tashin hankali tace "wai me kike nufi ne hajjau, kiyimun bayani mana yadda zan fahimta !!!    ta faɗi tare da ɗan jan guntun tsoki, Murmushi hajjaju tasaki sannan tace "Ni baza kiji mutuwar sarki abakina ba!kawai abunda nakeso ki sani shine babu wanda ya isa ya hana ruwa gudu sai Allah! Bakin alƙalami dai ya ruga daya bushe, Amma fa waɗannan yaran da kike gani wlh ikon Allah ne su, tunda har Allah ya haɗasu da Omar aikuwa magana ta ƙare, Yakamata kisan abunyi,'   Hajjaju tayi maganar tare da wuce wa ciki tabar Aunty babba tsaye abakin kitchen baki asake, lokaci guda taji ta ƙara tsanarsu hussana da jahad tabbas suna tattare da wani abu yaran, duk da bata fahimci inda maganar hajjaju ta dosa ba,   ranta ya gama 6aci tsoki ta buga tare da cewa "ta tsaya tayimun bayani amma ta tsaya yimun wasu sambatun banza dana wofi,ni duk tasa hankalina ya ƙara tashi, kuma wlh goben nan zansa a Kwashe mun su aje can azubar dasu tsakar daji, sai dae abunda bangane ba acikin maganar hajjaju wacece ɗayar hanyar da take nufi wadda ta isa inda banaso!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!? ta tambayi kanta sai dae kash babu amsa hakanan ta koma ciki tana faman sambatu aranta,     Zumbur !! Jahad tayi tare da kallon husana tace "Wlh nasanta!! Nagane ta !! Itace matar da ta taimaka mana a asibiti har ta biya kuɗin gadon Ki husana, wlh itace matar da tasama ma SEHRISH aiki, hakan na nufin ta son inda sehrish take.....!!   Cikin tsananin farin ciki jahad tayi maganar, hussana ma aɗan raxane tace "dagaske jahad itace tasama ma sehrish aiki? Ke nan itace kawai zata iya faɗa mana inda ƴar uwarmu take kenan,.     jahad tace "eh itace, nagane ta yanzu ya za'ayi muyi magana da ita, gashi aunty ta hanamu fita, amma ni dae inason magana da ita kodan saboda ta faɗa mana inda sehrish take,' jahad tayi maganar fuskarta tamkar zatayi kuka,    Cikin sanyin murya hussana tace "Jahad kada ma musa rai don nasan bazata faɗa mana ba, ita fa ƙawar Aunty ce, kuma kinsan muguwace idan halinsu ɗaya fa? Bazata ta6a faɗa mana ba, Ni tsorona ma kada ta faɗa ma wannan muguwar auntyn inda sehrish take, suna iya zuwa su cutar da ita, Allah yasa sehrish tana lafiya banaso wani abu yasame ta.........'" tayi maganar cikin shessheƙar kuka,    "Da gaskiyar hosana,Nima ina tunanin hakan Allah yasa karta faɗama auntyncan inda ƴar uwarmu take, amma dai ni inason naga matar na roƙeta akan ta faɗa mana inda sehrish take,yakamata musan inda take, wane hali take ciki, gashi yanzu sai mutuwa akeyi Ya Allah kasa sehrish tana araye har mu haɗu," tayi maganar idonta cike tab da hawaye,   daga bisani ta kalli hosana tace "ki zauna hosana kada ki fito bari ni naje nayi magana da matar na roƙe ta, ta faɗamun inda rishi take,"   Hosana tace "toh," sannan tasamu wuri ta zauna gefen gadon tana faman sauke ajiyar zuciya,   Cikin sanɗa jahad ta futo daga kopar ɗakin ta tsaya tana ɗan leƙa kanta, mutane tagani gasu nan sai faman zarya sukeyi acikin babban falon,    A hankali ta miƙi hanya ta soma tafiya tana faman waige-waigen neman hajjaju, ta ɗanyi nisa a tafiyar ta ta, tajiyo magana daga bayanta ana cewa "Nasan cewa ni kike nema ko"? Cikin sauri jahad ta juyo bayanta, hajjaju ce tsaye tana kallonta fuska ɗauke da murmushi, Ajiyar zuciya jahad ta saki sannan itama ta mayar mata martanin murmushin tare da gaishe ta, hajjaju ta amsa mata da cewa "Nayi mamakin ganin ku, anan gidan ko ba'a faɗamun ba nasan cewa kunsha wahalar rayuwa don nasan Laila sarai muguwace bata da Imani,kuma tana sanar dani game daku a waya sai dai bansan cewa ku bane," Jinjina kai Jahad tayi tare da cewa "Munsha Wahala sosai tamkar ba zamu rayuwa ba,dan Allah ki faɗa mana ina Sehrish take? Munyi kewarta sosai, rabon mu da ita, tun da ta tafi aikin nan da kika sama mata,bayan wasu kwanaki hosana ta 6atar mana da wayar da muke amfani da ita wurin kiranta, shikenan rabuwarmu da ita......' jahad ta ƙarasa maganar idonta cike tab da kwalla,    ɗan shuru hajjaju tayi tana kallonta gwanin ban tausayi kafin tace "Kiyi haƙuri, amma bazan iya shaida a ina sehrish take ba nikaina,saboda nasaba hulɗa da yara ina sama musu aiki, bazan iya tuna a wane gari nakai sehrish ba, bazan iya tunawa ba......'   Jin hakan yasa Jahad fashe wa da kuka mai cin rai, matsawa hajjaju ta ƙara yi gab da jahad tasanya hannunta tare da dafa kafaɗunta tace"kiyi haƙuri Jahad, ina mai matuƙar jin takaicin gaza taimaka maku akan halin da kuke ciki, haƙika kun ga rayuwa, amma ni abunda nakeson sani taya akai kuka haɗu da Omar? bayan naji labarin rasuwar tsohuwa ya gigita ni matuƙa, sannan naji labarin cewa ana zargin cewa kune kuka bata poison amma bansan ya ƙarshen labarin yake ba,'.    Cikin shessheƙar kuka jahad tace "bayan tsohuwa ta rasu, mutane suka ce mune muka kashe ta alhalin mu bamu da masaniya akan mutuwarta, shine aka kaimu police station, munsha Wahala sosai saboda bamu da sheda, ana shirye shiryen za'a miƙa case ɗinmu kotu, hussana tayi rashin lafiya shine dalilin dayasa ƴan sanda suka tafi da ita asibiti tare dani, Acan ne Allah ya haɗamu da yaya Omar shine ya kwace mu daga hannun police ɗin kuma ya kashe case ɗin gaba ɗaya......' ta ƙarasa maganar tana faman sauke ajiyar zuciya,   Murmushi hajjaju tasa ki tare da cewa "Allah sarki Omar mutumin kirki ne sosai, yana da tausayi inama ace tunfarko ba nan ya kawo ku ba, wlh da kun more rayuwarku,amma sai dai kash yayi kuskuren jefa rayuwarku cikin haɗari batare da sanin shi ba, Amma insha Allah Laila bazata ta6a cin nasara akanku ba,'   Jinjina kai kawai Jahad ke yi, bayan sun ɗanyi shiru hajjaju tace "Muje ɗakin da kuke,ina son ganin ƴar uwarki danaji kin kirata da hussana, bazan manta ba itace a lokacin kwance saman medical bed ansa mata oxygen tana shaƙar numfashi cikin mawuyacin hali, Amma yanzu naganta taji sauƙi sosai jiki yayi kyau,' hajjaju ta faɗi da ɗan murmushi a fuskarta yayin da suke nufar ɗakin hafsat atare,    Suna shiga suka samu hussana atsaye sai faman zirga-zirga take yi burinta kawai jahad tadawo kusa da ita,    Tsayawa tayi ganin sun shigo tare da matar, Murmushi hajjaju ta sakar ma hussana tare da ƙarasawa inda take ta rungumo ajikinta, tana ɗan bubbuga bayanta tace "nasan ke baki sanni ba,sabosa lokacin kina kwance rai hannun Allah, amma ni nasan ki saboda naganki a lokacin, naji daɗi sosai dana ganki cikin ƙoshin lafiya,    Hajjaju ta ƙarasa maganar tare da janye hussana daga jikinta, ita dai hosana kallonta kawai take yi don batasan ta ba, mayar da idonta tayi kan jahad tace "ta faɗa maki inda sehrish take?   Jahad tace "a'a hosana, tace itama ta manta inda takaita aiki saboda ta saba kai yara aiki bazata iya tuna inda takai su ba,"    Jin haka yasa Hosana fashewa da kuka tana cewa "..yanzu shikenan bazamu ƙara ganin sehrish ba....   Hajjaju tace "Ki daina kuka hosana,wayace maki bazaku sake ganin sehrish ba? Ki daina wannan tunanin Insha Allah zaku haɗu da ƴar uwarku, abunda nakeso daku kawai ku cigaba da addu'a insha Allah zaku dace,"   Jahad tace "kullum muna cikin yin addu'a,Kuma zamu cigaba da yi har illa masha Allah"     Murmushi hajjaju ta kuma yi sannan tace "Ni zan wuce,Ku kula da kan ku,Allah ya Albarkanci rayuwarku, yaci gaba da tsare ku aduk inda zaku kasance arayuwar nan,"   Suka amsa mata da "Amin," sannan tasa kai ta fuce tana mai jin rashin daɗin gaza taimaka masu da tayi na ƙin faɗa masu inda ƴar uwarsu take, bayan ta son inda take,   Komawa sukayi atare suka zauna jikinsu amace, Shin mai zai biyo baya?😥 Bayan wasu lokutta, duka baƙin da suka zo suka tafi gidan yayi tsit ba hayani, suna cikin wannan zaman na jimamin Ga samu ga rashi, na hajjaju da suka haɗu da ita yau, sun son itace kaɗai zata faɗa masu inda Sehrish take gashi itama tace bata sani ba, hakan ba ƙaramin kashe musu zuciya yayi ba, daker suka samu bacci ya ɗauke su, _______________________ Fitowa daga wanka general ishaq yayi jikinsa sanye da gajeran wando, Closet ɗinsa ya nufa tare da sa hannu ya buɗe ya ɗauko jallabiya ya zumbula ajikin shi, Sarai yasan cewa tana ɗakin Amma sai yayi tamkar bai ganta ba, sai da ya kammala kimtsa kansa sannan yace "Ya Rashin Ji"? Ya tambaya yana kallon kansa acikin Mirror, mamaki ne ya kama aunty babba jin abunda yace, tana zaune daga gefen gadonsa tace "Nifa ce ba hafsat ba," ta faɗi tana kallonsa Ishaq yace"Nasani ae, dake nake magana, duk rashin jin hafsat ae bata kai ki ba, kefa tamkar 6eran gida kike wurin 6arna da rashin ji," ɗaure fuska tayi jin abunda yace rai a6ace tace "Alamu sun nuna cewa ba kayi kewata ba ko? shiyasa kake gayamin magana, ko da yake dama kai ae ba ka iya soyayya ba, Iya ruƙe bindiga kaɗae ka sani," ......juyowa Ishaq yayi yaɗan kalle ta tare da ta6e bakinsa yace "ban iya soyayya ba, amma gashi nan har kin haifi hafsat dani ko? Naga wannan ma ae wani sashe ne na soyayya," ya ƙarasa maganar tare da wuto wa ya haye saman gadonsa ya kwanta yana cewa "Idan kin tashi fita daga ɗakin kada ki manta, ki kashe mun hasken inaso nayi bacci," a ƙule aunty babba ke kallon shi, can kuma ta miƙe fuuuuu ta nufi hanyar fita har takai bakin ƙopar ɗakin ta kuma tsaya tare da juyowa tana kallonsa, abun mamaki sai ta same shi yana ta faman tiƙar dariya, Bakomai yasa ta tsayawa ba face tsananin son kasancewa dashi da take yi, dakatawa da dariyar yayi sannan yace "nifa ba korarki nayi ba, zaki iya dawowa kiyi zaman ki," murguɗa masa baki tayi aranta tace "shashasha dama nasani ae dole ka buƙace ni," shi kuma aransa yace "Mayya, Jibi yarda take ta hau hawa kamar buhun harawa, duk an cinye mun abincin gidana," 😂 Kamar taji mi yace ta ɗan kallesa tare da jinjina kanta tace "bari na kawo maka Tea," "Ok i wll be waiting for u," ya faɗi yana faman yin dariya ƙasa-ƙasa, general ishaq kenan tamkar Abbansu haka yake indai wurin iya zolaya ne, ****************************** A 6angaren sehrish kuwa, sam taƙi bari bacci ya ɗauke ta sai faman gyangyaɗi take yi tana zaune asaman kujerar dake gaban mirror burinta kawai su twins su dawo ko tasamu ta kai masu abincinsu, sune kawai suka rage mata takai mawa, domin kuwa ta jima da kaima Abbansu nashi tunda ya dawo, Basu tashi dawo wa cikin gidan ba sai wuraren ƙarfe Sha biyu da rabi suka shigo suka shigo cikin falon kai tsaye ɗakinsu suka wuce, shaf shaf suka shiga rage kayan jikinsu, sai da ya rage daga su sai shorts ajikinsu, sannan suka shige toilet donyin wanka, sun jima aciki kafin daga bisa ni suka fito kowannansu ɗaure da towel a waist ɗinsa, closet ɗinsu suka buɗe jerin kayansu ne ajere komai iri ɗaya, kamar yadda suke tagwaye haka komai nasu yake iri ɗaya, kimtsawa su kayi cikin sleeping dress riga da wando milk colour, faɗawa su kayi saman gadon Su tare da rungume junansu suka ci gaba da abunda suka saba, kamar injina haka suke sam basa gajiya,abun ya zamar masu jangwangwam, Kwankwasa ƙopar bedroom ɗinsu akayi, kusan sau uku basu ji ba, sai ana huɗun Jahan yace "Wai Uban wanene yake buga ma mutane ƙopa? Atunaninsa Sehrish ce tazo kawo masu dinner ɗinsu, Amma sai yaji akasin hakan Muryar haroon yaji yace "Ubanka ne shege, zoka buɗe mun ƙopa in shigo," Uban tsoki Jahan yasaki tare da ƙara ƙanƙame Ayaan ajikinsa yana cewa "wlh bazan buɗe masa ƙopar ba, bansan uban me yakawo shi bedroom ɗinmu ba," Ayaan yace "Amma sweet heart baka tunanin wani abu mai mahimmanci ya kawo shi"? ya faɗi yana faman lumshe idonsa akan Jahan, guntun tsoki jahan yaja tare da cewa "Wlh bazan buɗe masa ba, yazo yayi disturbing ɗinmu ne kawai," duk abunda suke cewa a kunnan haroon dake tsaye abakin ƙopar ɗakin nasu, Jinjina kansa yayi yace "Yara kenan dani kuke magana," hannunsa ya tura cikin aljihunsa tare da zaro wayarsa yaci gaba da daddanata na wani lokaci, daga bisani ya mayar da wayar cikin aljihunsa sannan ya ɗaga murya tare da cewa "tunda bazaku buɗe mun ƙopar ba, ku duba wayoyin ku acikin whatsapp ɗinku na turo maku wani saƙo mai mahimmanci," Jin hakan yasa su dakatawa gaba ɗayansu cikin sauri jahan ya zura hannunsa asaman side drawer ya ɗauko wayarsa da hanzari ya miƙe zaune, whatsapp ɗinsa yashiga mamaki ne yakamasa ganin Numbar da yayi saving da yaya Haroon ya turo masa Video, cikin sauri yashiga chat ɗin tare da danna video ɗin ya buɗe...........lokaci guda jahan yayi wata irin Zabura sai gashi tsaye saman gadon hannunsa na kerma gaba ɗayama jikinsa, nan take kuma wata irin Zufa ta shiga wanko masa duk da sanyin A.c in dake ɗakin, Zazzaro idonsa yayi hankali a matuƙar tashe yace "AYAAN MUN SHIGA UKU!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!! jin hakan yasa Ayaan tasowa shima ya miƙe tsaye yana cewa "jahan menene ya faru na ga duk ka razana," Miƙa masa wayar yayi batare da yace komai ba, amsa Ayaan yayi yana duba video ɗin, porn video ɗinsu ne shida Jahad, gasunan kwance saman gado a ɗakin hotel ɗin da suka kama, tsantsar mamaki ne a fuskar Ayaaan a ruɗe yace"Jahan taya yaya haroon ya samu wannan video ɗin? "Nima shine abunda ban sani ba," Jahan ya faɗi cikin tashin hankali, Muryar haroon ce ta dakatar dasu da cewa "Oya, azo abuɗe mun ƙopar," A hanzare suka diro daga saman gadon tare da nufar ƙopar suka buɗe masa, shigowa yayi yana faman sakin shu'umin murmushi yace"Ƴan duniya, fararen Balbelu tun yaushe kuka fara wannan harkar bansani, ahhh gaskiya wannan anyi mun nisa har suna haɗa baki wurin cewa "yaya Haroon ba yin kan mu bane, dan Allah ka rufa mana asiri," atsiyace yabi su da wani irin kallo kafin yace "taya kuke tunanin zan iya rufa muku asiri hakanan siddin ragadan ku ci banza!!? nifa dama nasani duk kaf zuri'armu babu fasiƙai irin ƴa'ƴan mommynku, masu jaza mana bala'e acikin zuri'armu,' yayi maganar fuska aɗaure yana kallonsu Jin wannan magana ta haroon ya sanya su jin wani irin ɗaci aransu, Ci gaba da magana haroon yayi "kai nifa tunda Mommynku ta nuna ta tsane ni bataso na, Nima naji cewa bana ƙaunarku! bama wannan ba adalilin ku yasa abba yadaina so na kwata-kwata nazama abun ƙyara acikin gidan nan, don hak wannan babbar dama ce agare ni, Idan har na ɗaura wannan videon a Social media, Abban mu ya gani to tabbas nan take zuciyarsa zata buga ya mutu! idan kuma babban yayan ku ya gani hohohoho ku kunsan mai zai faru, Idan Ammi tagani shikenan zata rabaku da mahaifinku ne na har Abada dama ba sonku take ba, tabbas wannan babbar dama ce agare ni !!! Ya faɗi da dariya a fuskarshi tuni Ayaan da Jahan sun zube agabansa saman guiwowinsu idonsu cike tab da hawaye, tabbas sunyi mamakin Kalaman haroon yadda ya nuna irin tsanar da yayi masu tamkar ba jininsu ba, cikin tsananin ƙunci suke cewa "Yaya Haroon pls ka rufa mana asiri dan Allah, kada kace za kayi amfani da wannan damar wurin tarwatsa farin cikin gidan nan, kaifa ɗan uwan mu na jinin mu dan Allah yaya haroon ka dubi girman Allah kada kayi mana haka," Fashewa da dariya haroon yayi yana binsu da wani irin kallo na ƙasƙanci yace "Au haba? Ashe nifa jinin ku ne? Amma taya akai bamu kama? Ikon Allah sai yau kukasan da hakan? kaiiiii ! Ni saima yanzu na lura wai yau ƴa'ƴan Alexandra ne durkushe saman guiwowinsu agabana suna neman afwa hada matsar kwalla kodai mafarki nake yi ne? Yayi maganar tare da sa hannunsa yana murza idanunsa wai donya tabbatar ba mafarki yake yi ba, shiru su kayi gaba ɗaya jikinsu ya mutu sai uwar zufa dake wanko masu, ga jikinsu dake ta faman kerma yayin da idanunsu suka ciko tab da kwalla, gwanin ban tausayi Murya na Rawa Ayaan yace "Ka faɗi komai kake so za muyi maka donka rufa mana asiri," Haroon yace"yanzu naji magana, Anzo dai-dai wurin dana fi so," ya faɗi tare da ƙara gyara tsayuwarsa yace "Abu biyu nake buƙata muddin kukayi mun hakan to shikenan zamu raba jaha daku,". Cikin sauri suka amsa masa da cewa "muna sauraronka," wani irin bazawarin murmushi ya saki kafin yace "Nima fa kwararrene a irin wannan harkar taku! gashi kuma dama na jima ina sha'awarku musamman junaid, Kai yaron akwai sirrin kyau atattare dashi kuma daga gani zaiyi ni'ima sosai........' a firgice jahan ya daka masa tsawa tare da cewa "Ya isa haka!! Komai za kayi ka tsaya a iya kan mu kawai, amma koda gigin wasa kada ka ƙara kiran Sunan junaid da waɗannan munanan kalaman naka! saboda ba zaka ta6a samun abunda kake so agame dashi...........' cikin sauri Ayaan ya rufe ma jahan baki muryarsa cikin kuka yace "Jahan dan Allah kayi shiru, kada ka ƙara ja mana wani bala'en, ka bari muji da wanda muke ciki," shiru jahan yayi yana faman sakin Huci ji yake tamkar ya tashi ya shaƙe wuyan Haroon, Hannu haroon yasa abaki irin mamakin nan yace "Wow wai meyasa kowa yake ma junaid irin wannan zazzafar soyayyar har haka? Gaskiya anyi mun nisa kaina na cikin duhu, farin jinin junaid yayi yawa ina kishi da hakan," ya faɗi yana dafe saitin zuciyarshi . Ayaan yace "Ba son junaid muke ba, Ƙaunarsa muke yi saboda shi ɗin jinin mu ne," ta6e baki haroon yayi tare da ɗan jinjina kai yace "hmmmm ni wannan ba damuwata bace ba, abu biyu nake buƙata daga gare ku, inaso ku gamsar dani acikin daren nan, saboda inji irin naku salon, Sannan abu na biyu kuɗi nake so kimanin naira miliyan 50, in kun mun hakan zaku zauna lafiya, Wani irin kallo suke bin shi dashi, Jahan yace "50m fa kace? Ina zamu same su? ka ruga da kasan iya salary ɗin mu, kuma ba tarawa muke yi ba, kashewa muke yi," haroon yace "Wannan ba damuwa ta bace, in kun so there's many way da zaku samu waɗannan kuɗin ! Yayan ku fa billionare ne! Mahaifiyarku ma billionaire ce, yadda take son ku ɗin nan, da zarar kun mata waya kunce kuna son Ƴan silalla zata turo maku," Murya a sanyaye Ayaan yace "mun ji zamu samu kuɗin mu baka amma dan Allah kada kace zaka aikata wannan abun damu, wlh bazamu iya ba, iya mu biyu ne kawai ba kowa muke bi ba, ka faɗi mashi jahan kada ya cutar da rayuwarmu bazamu iya jurewa ba........................" bugun ƙopar da akayi ne ya hana Ayaan ƙarasa maganarsa, Cikin sauri Haroon yayi tsalle yashige bayan labule ya 6oye, tashi su kayi atare suna faman sa hannu suna goge hawayen dake fuskarsu, sannan jahan yayi ƙoƙarin cewa "Wanene? Sehrish dake tsaye ruƙe da tray a hannunta tace "Ni ce sehrish," Ayaan yace "Shigo ciki," Tura ƙopar tayi da tray ɗin hannunta mai ɗauke da food wermers tare da kayan tea ta shiga ciki, tsayawa tayi tana kallonsu cikin mamaki ganin yadda fuskokinsu sukayi Jawur, idanunsu sun Canza launi alamar sunsha kuka, Muryarta na rawa tace "Dama.............' bata ƙarasa ba Jahan ya katse ta da cewa "Ki barshi kawai, bazamu iya cin komai ba, ki koma da kayan," Shiru tayi aranta tana mai mamakin jin yadda Jahan ke mata magana cikin sanyin Murya, shi da kullum atsiwace yake mata magana, Jinjina kai tayi tare da yin juyi zata futa karaf idonta suka sauka kan ƙafafun haroon dake 6oye bayan labule, tana ganinsu tagane cewa ƙafafunsa ne kamar na shebur haka suke, tsananin tsoro da mamaki ne suka kamata daker ta iya fuce wa daga ɗakin, Kai har ta futa tana waiwayen ɗakin nasu, cikin mamaki take cewa "Meke faruwa ne? Naga fuskar Ayaan da jahan jawur alaman sunsha kuka, kuma menene yakai ƙafafun haroon ɗakin, hakan na nufin shine 6oye bayan labule? ko uban me yakaisa ɗakin hada su 6oyewa abayan labule, gaskiya akwai wani mummunan abu dake faruwa, Nashiga ukuna Allah yasa dae Haroon kada ya cutar dasu don nasan halinsa ba ƙaramin shaiɗani bane...........' ta ƙarasa zancan Zucin nata ayayin da take saukowa down daga saman stairs ɗin, Kitchen ta shiga ta ajiye tray ɗin, sannan ta wuce bedroom ɗinta cike da zullumin abunda tagani, A daren ranar haroon sai da ya tabbatar ya wulaƙantar da rayuwar Ayaan da jahan domin kuwa har sai da Ayaan Ya sume sannan ya ƙyalesu ya fuce yana ƙara jaddada masu maganar kuɗinsa, bayan ya fita jahan ya fashe da wani irin matsanancin kuka na tashin hankali yana jijjiga jikin Ayaan dake sume aƙasa 😭 [9/15, 9:20 AM] 💋BOSS LADY💋: *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* ~🔥The father Of Soldiers🔥~ *Episode 25-26* *Story & Written by*💫 *Hafsat Bature Moh'd* *BOSS LADY* cikin sauri Jahan ya miƙe fitowa daga ɗakin yayi ya sauko down kai tsaye freezer ɗin dake a babban falon nasu ya tunkara, buɗewa yayi tare da zura hannu ya ɗauki robar ruwa mai sanyi, sannan ya juya ya koma ɗakin nasu, bayan ya buɗe robar ruwan ya ɗebo ya yayyafa masa a fuskarsa, wata irin doguwar ajiyar zuciya Ayaan ya saki tare da buɗe idonsa da sukayi jawur dasu yana kallon jahan dake zuƙunne agabansa, ganin Ayaan ya farka yasa jahan faman sauke ajiyar zuciya, yayin da hawaye ke sintiri a fuskarsa yana kallon ɗan uwan nasa, Buɗe baki Ayaan yayi zaiyi magana, nan take wani irin yunƙurin amai yazo masa, a hanzarce ya zabura ya miƙe duk jikinsa ba ƙwari da gudun gaske ya faɗa toilet agaban basin ya tsaya yana faman kwarara aman, biyo sa jahan yayi cikin toilet ɗin tsayawa yayi kusa dashi ya sanya hannunsa yana ɗan bubbuga bayan Ayaan cikin muryar kuka yake cewa "Ayaan kayi haƙuri ina mai takaicin wannan ranar, naji natsani kaina Ayaan saboda nagaza ceton ka a hannun wancan fasiƙin, tabbas Haroon bai da Imani ko misƙala Zarratin kashe mu kawai yake son yi, ni ina kokwantan cewa Anya haroon JININ MU NE !!!!!!!!!! dakyar Ayaan yasamu ya dakata da Aman hannunsa yasanya yana tarbo ruwan dake kwararowa daga jikin fanfon yana kuskure bakinsa, bayan ya kammala ya kashe Tap ɗin, Sannan ya ɗago da shanyayyun idanuwansa ya kalli jahan yace "Haroon bai da Imani, Ƙazamin banza mugu macuci kuma Azzalumi wlh Allah bazai ta6a ƙyalesa ba sai ya bi mana haƙƙin mu, Jahan ni sam bana jin kunyar videon tsiraicin mu ya fita, babban abunda nake jimawa shine Mutuncin mahaifin mu da kuma na Babban yayanmu, jahan dole mu nemi mafita akan wannan Baƙin Shaiɗanin...........' ya ƙarasa maganar yana faman sakin Numfashi mai zafi, don tuni zazza6i yakama jikinsa, Jahan yace "yanzu dare yayi Ayaan,Gobe sai musan Abunyi amma gaskiya bazan ƙara bari haroon ya ƙara kusantar ɗaya daga cikin mu ba, ko nawa yakeso muyi ƙoƙari mu biyasa shine kawai !!! Sun jima suna jimamin abunda yafaru dasu kafin daga bisani suka sake sabon wanka don tsarkake jikinsu, bayan sun fito suka zura jallabiya ajikinsu, sai da Jahan ya canza musu bedsheet sannan suka kwanta, sun juma idonsu a buɗe kafin daga bisani bacci ya ɗauke su 😥 (Arayuwa kowa da irin tashi jarabtar, babu wanda Allah baya jarabta, kuma bawai don baya son mu bane a'a face don ya jaraba imanin mu) **************Morning*********************** tun da sassafe sehrish ta farka daga baccin da ta koma na asuba, fuskar nan awashe yau zata fara shiga school, jiki na rawa ta faɗa toilet shaf-shaf tayi wanka ta fito jikinta ɗaure da farin towel, Uniform ɗinta ta curo daga cikin wardrobe duka ukun, ta jera su saman gadonta tana tunanin wanne zata sanya, duk kala ɗaya ne amma na farkon riga ce da mini skirt ɗan dai-dai guiwa shafa su tayi tare da girgiza kai tace "Ba wannan zansa, basu son cewa ni musulma bace, taya zansa wannan gajeran skirt ɗin cinyoyi awaje kamar ƴar christiana," tayi maganar tana yatsina fuska, buɗe na biyun tayi riga ce tare da skirt pencil ba ƙaramin ɗame jikin mutun zaiyi ba, "Kamar dae wadda zata club," ta faɗi tana ƴar dariya, na ƙarshen ta buɗe riga ce tare da dogon wando, duka uniform ɗin suna da Top wadda ake sanyawa daga sama bayan an zura rigar sai kuma guntun hijab wanda daƙyar ya dire kafaɗa, "Kwarama wannan zasu fi dacewa dani," ta faɗi tare da hanzarin komawa gaban mirror sai da ta kammala shafe jikinta da body oil tabi ta feshe shi da turare ko'ina yakama ƙamshi sannan ta koma gaban gadon tana zura uniform ɗinta, lokacin da ta kammala zura kayan duka ta kalli kanta a mirror sai da taji gabanta ya faɗi saboda yadda kayan suka hau jikinta su kayi mata wani irin kyau, Rigar white colour ce wandon kuma Maroon colour launi ɗaya da Top ɗinta, jujjuyawa tayi agaban mirror ɗin sannan ta sakarwa kanta murmushi, sai da tagama shiriritar sannan ta ɗauko takalmanta, tsayawa tayi tana ƙoƙarin zura safa a ƙafarta, ta aza ƙafar asaman kujerar gaban mirror tana gyaggyara safar, Azmee ta shigo ɗakin da sallama tana yin arba da sehrish ta soma washe baki tana cewa La!la! Irin wannan kyan haka, Masha Allah gaskiya uniform ɗin nan ba ƙaramin kyau su kayi maki ba Sehrish sai kace donke akayi su," Murmushi kawai Sehrish ke saki tana ɗan kallonta a lokacin ta kammala sa safar da takalmin a ƙafar daman ta, saura ta hagun zata sanya mawa, "aunty azmee ina kwana fatan kun tashi lafiya," ta faɗi tana aza ɗayar ƙafar saman kujerar , Azmee tace "Lafiya lou Alhamdulillah, naga sai faman shiri kike yi, maganar breakfast ba? "Aunty azmee lokaci zai ƙure ne, idan nadawo zanci," ta faɗi tana zura safa a ƙafar hagunta, Azmee tace "Kin ta6a ganin inda akaje ɗaukar karatu da yunwa? gaskiya bazaiyiyu ba, akwai sauran miyar jiya na ɗumamata saina haɗa maki da dankalin dana soya kici, bari na kawo maki" ta fadi tare da juyawa ta fuce cikin sauri bayan wasu mintina sai gata ta dawo hannunta ɗauke da plate, soyayyan dankalin ne aciki tare da jar miya, ajiye mata tayi asaman side drawer ɗinta, sannan ta koma ta ɗauko mata kayan tea don ta haɗa tasha, "Nagade sosai Aunty azmee da kulawarki," sehrish ta faɗi a lokacin ta baro gaban mirror ɗin, wuri ta samu gefen gadon ta zauna tana cin breakfast ɗinta, yayin da azmee ta fuce tana cewa "ki hanzarta ki shirya kafin Junaid ya fito," ta amsa mata da "Toh," A can ciki kuwa tuni junaid ya farka saboda ya tashi da wuri ya sanya alerm a wayarsa, shaf shaf yayi wanka ya fito ya kimtsa cikin pakistani riga da wando farare amma anyi masu ado da stone launi daban daban ajikinsu, ba ƙaramin kyau yayi ba, bin jikinsa yayi ya feshe shi da Spice bomb, sannan ya gyara sumar kanshi, gaban mirror ya tsaya yana kallon kansa yace "Nima kaina nasan cewa Ni kyakkyawa ne, Son kowa ƙin wadda ta rasa, Allah kaɗai yasan ƴan matan da suke crushing akaina," ya faɗi yana tsumbula yatsansa na tsakiya a dimple ɗin fuskarsa daya Lotsa, daga bisani ya ɗauki key ɗin motar shi tare da wayarsa ya fito daga ɗakin, cikin hanzari ya sauko down babu kowa saboda duk basu tashi daga bacci ba, wuri ya samu asaman Royal sofa ɗin dake a falon mai mazaunin mutun 3 ya zauna yana jiran fitowar sehrish, wayarsa ya shiga daddanawa, message ya tura mata cikin wayarta, na cewa yana jiranta ta fito, a lokacin ta kammala kur6ar tea ɗin data haɗa, message ɗin junaid ya shigo mata karantawa tayi "Am waiting for u reesh,' murmushi ta saki cikin sauri ta miƙe tare da ɗaukar guntun hijabin ta zura ajikinta, sannan ta ɗauki School bag ɗinta ta ɗan sagala hannun jakar a kafaɗarta, sai da ta ɗauki wayarta sannan ta fito daga ɗakin, kai tsaye ta nufi falon tunkan ta ƙarasa junaid ke kallonta baki asake, Ganin hakan yasa ta sakin dariya, ƙarasa wa tayi wurinsa tare da tsaya agabansa ta ruƙe waist ɗinta tace "Nayi kyau,"? Cikin mamaki yace "Reesh irin wannan kyau haka? Anya karfa malaman makarantar su rikice? innalallahi," ya faɗi tare da aza hannunsa akansa, ɗan bubbuga ƙafarta tayi tare da cewa "ka tashi mu tafi junaid har 8:30 fa tayi," Mamaki tayi ganin yarda yake kallonta hannunsa yakai tare da cafko wutsiyar gashinta da ta sauko har tsakiyar bayanta yace "Sehrish jibi fa? Babu wani dogon hijabin ne sai wannan? Taya zaki bar gashin nan haka bainan nasi? Kowa ya kalla? Sai lokacin ma ta ankara sam ta manta bata sanya ribom ba ta ɗaure gashin, dafe kanta tayi tare da cewa "kash ! Wlh mantawa nayi ban ɗaure gashin ba, kuma fa in na sanya ribbom gyaran gashin da akayimun zai 6ace," tashi junaid yayi tare da ruƙo hannunta yace "Mu shiga cikin ɗakin na ɗaure maki shi, nasan yarda zanyi batare dana 6ata maki gyaran gashin ba," bin shi tayi suka wuce ɗakin nata, duk wannan abun dake faruwa akan Idon haroon sam basu ankara dashi ba, tun fitowar sehrish yake tsaye ruƙe da qugu daga shi sai gajeran wando fuskar nan a murtuke kamar ta shanu, jinjina kansa yayi tare da cewa "Wato ni waccen ƴar shilan zata raina ma wayau, in na ta6a jikinta taita ƙyamata amma gashi junaid har wani ruƙe hannunta yake yi, hada su shiga ɗaki ko uban mi zasu yi aciki,"? Ya tambayi kansa can kuma ya saki wani irin shu'umin murmushi yace "Wannan babbar dama ce agare ni ! Zanyi amfani da ita wurin gur6ata sunanta acikin gidan nan, Zan ƙala mata sharrin cewa ta koyama junaid lalata, kuma na kama su hannu dumu-dumu, " fashe wa yayi da wannan mahaukaciyar dariyar tasa kafin ya juya ya nufi hanyar komawa dakinsa yana cewa "Yarinya kin gama yawo acikin gidan nan, sai kin gane baki da wayau !," yana tafiya yana sambatu har ya shiga ɗakinsa, Junaid kuwa bayan sun shiga ɗakin sehrish ta cire hijabin nata agaban mirror suka tsaya, ribbom ɗinta dake ajiye saman mirror ta ɗauko tare da miƙa masa, hannu yasa ya kar6a sannan yashiga kiciniyar tattara gashin kanta donya ɗaure mata, Murmushi ta dunga saki saboda jinsa yadda junaid ke faman nishi aranta tace"junaid ba ƙaramin rago bane, yanzu gashin kan nawa ma yagaza ɗaure wa, shi dai sai kace ba namiji ba, sam babu wannan karsashin na maza atattare dashi...... Muryarshi ce ta katse ta da cewa "Gulma ta kike ko"? Cikin sauri tace "a'a ni na isa," Murmushi kawai yayi, daƙyar yasa mu ya tattara sumar kan sehrish ya ruba ta biyu ya haɗa ya ɗaure," sannan ta mayar da hijabin nata, "Gaskiya junaid ka iya dabara, gashi nan yanzu babu gashin bai leƙo ba," ruƙo hannunta yayi tare da cewa "Mu tafi ko," cikin sauri ta bishi suka fito da hanzari suka fuce, Buɗe mata motar yayi ta shige sannan shima ya zagaya yashiga ciki, yana a driver seat ita kuma tana a gefensa, tayar da motar yayi sannan suka fuce daga gidan, A natse yake yin driving ɗin sehrish na satar kallon shi tace acikin ranta "koya akai ya iya driving yanzu yadda yake shagwa6a66an nan karfa wata rana ya tunkari babban mota damu kwatsam ta rotse damu duk mu mutu.....' "Matsalar ɗan nigeria kenan, duk wani bala'e shike fara kira ma kansa, yanzu ko menene na wannan tunanin"? Cikin mamaki tace "Acikin Zuciya fa nayi maganar" ta faɗi tana kallonsa Junaid yace "Eh nasani, ae muddin zaki yi gulmata acikin zuciyarki to fa saina ji don haka ki kiyaye," ya faɗi yayin da yake shan kwana dasu, Shiru tayi tun daga lokacin bata sake maganarsa ba acikin zuciyarta amma fa tayi mamaki don ita tasan cewa acikin zuciyarta tayi maganar amma gashi yaji," Tunkan su ƙarasa sehrish ke hangen katafariyar makarantar motoci sai shiga suke yi ciki suna sauke ɗalibai, tsayawa zayyana kyawun makarantar 6ata baki ne, gashi bani da isasshen lokacin yin wannan bayanin 😆 A parking space dinsu junaid ya sauke sehrish tare da cewa mun iso, atare suka fito gaban sehrish ne ya faɗi ganin tsala-tsalan ƴan mata young ladies irinta sun ɗau wanka, ƴa'ƴan masu kuɗi wayayyun gaske tun daga shigarsu zai tabbatar maka da cewa An sangarta su da yawa, saboda majority ɗin matan Mini skirt ne ajikinsa sai santala santalan cinyoyi awaye, kuma mafi yawancinsu babu hijab ajikinsu gyaran gashi ne kawai iri-iri, wasu kuma skirt ɗin nan ne ajikinsu waton pencil yabi shafe ɗin jikinsu, iya guiwar ƙafarsu ya tsaya, waro ido waje sehrish tayi tana cewa "kai!kai!!kai!!! Junaid mu koma gida, gaskiya bazan iya zama a school ɗin nan ba, wannan sunfi ƙarfi na Allah," Fashewa da dariya junaid yayi ganin yarda sehrish duk ta dabarbar ce, hannunta na kerma ta ruƙo rigarsa tana 6oyewa abayansa tana faman yi masa sambatun su koma gida, abu kamar wasa har hankalin wasu students ɗin suka dawo kansu ganin yadda Yarinyar ta ƙanƙame jikin dan uwan nata hada su hawaye a fuskarta, Shima kansa junaid sehrish ta rikita shi hankali atashe yake cewa "dan Allah sehrish ki daina, karki bani kunya mana kalli yarda hankalinsu yafara dawowa kan mu innalallahi, yanzu da ace school bus ce ta kawo ki bansan ya zaki ƙare ba," "Junaid nidai mu tafi gida, Allah bazan zauna anan ba" ta faɗi tana shesshekar kuka 😆 dariya kamar zata kashe junaid ba shi kaɗae ba hada wasu daga cikin ɗaliban dake a wajen, Wasu gungun ƴan mata ne suka ƙaraso kusa dasu, ɗaya daga cikinsu tana cewa " Wow friends kalli wani handsome guy nan ya burgeni sosai," Jin hakan yasa sehrish dakatawa da kukan tana ɗan kallonsu kai kana ganinsu kaga jarababbu, Murmushi ta gefenta ta saki tare da cewa "Kamar nasan shi a tiktok fa, zanso ko na tuna sunan shi daga gani cele ne shi sosai," Sai faman surutu suke yi suna yaba kyan junaid, "Kai nifa bazan iya jure ba, sai nayi ma shi magana," ɗaya daga cikinsu ta faɗi atare suka iso dab da su junaid da sehrish, su uku ne matan junaid yace "Sannun ku fa," suka amsa mashi da "Yawwa," sannan ɗaya daga cikinsu tace "Kamar na sanka,"ta faɗi cikin rangwaɗa Junaid yace " Sunanki Parveena," zaro ido su kayi jin yadda junaid ya faɗi sunan ɗaya daga cikinsu kai tsaye, Nuna ɗayar yayi ta tsakiyarsu yace "ke kuma Sunanki Amrish ta ƙarshen kuma sunanki Naja'at," ya faɗi da murmushi a fuskarshi, su kuwa sai faman yarfa hannu suke yi suna kallon shi cikin mamaki jin yadda ya zayyana sunayen su gaba ɗaya, Cikin mamaki wadda ya kira da Amrish tace "Dan Allah ya akai kasan sunayen mu"? Ta tambaya cike da zumuɗin son jin amsa, Duk wannan abun dake faruwa akan kunnan sehrish wadda ke ruƙe da rigar junaid taɗan la6e abayansa, Junaid yaci gaba da cewa "Ban son ku ba nima kawai abunda nasa ni ke Amrish kece kullum kike isarmu da surutu a group, ke kuma parveena baki da aikin yi sai turo hotunan Chacolate iri-iri, Sannan ke kuma Naja'at kinfi kowa iya turo hoton abinci duk in zaki ci sai kin turo mana hotansa," Gaba ɗayansu suka saka ihu da sowa har suna haɗa baki wurin cewa "Wai dama kaine ! junaid romeo ko? Murmushi junaid ya saki tare da cewa "Ni ne, bamu ta6a haduwa ba amma muna yin chat sosai ta whatsapp a group, na ruƙe fuskar kowannan ku da sunayen ku,". Ba ƙaramin farin ciki su kayi ba, Amrish ta nuna sehrish tare da cewa "wannan fa? sister ɗinka ce"? Junaid yace "Eh, younger sis ɗina ce, new comer ce yau tafara zuwa," Parveena tace "No wonder, that's why naga tana hiding kanta abayanka, amma kamar batason mutane ko? Naga ko son kallon mu bata yi," Junaid yace "No just kin gane shagwa6a6iya ce, Last born ɗin mu ce bata saba shiga cikin mutane ba kullum tana a gida, so aduk lokacin da aka fito da ita cikin mutane tana ɗan razana," tunda ya soma jawabi sehrish ke kallon shi baki asake, jin irin ƙaryar daya zuƙa mata nafarko yace ƙanwarsa ce ita, kuma ya laƙwafa mata sharrin cewa tana shagwa6a bayan shine shagwa6a66e, jinjina kanta kawai takeyi, Amrish tace "Ayyah na tausaya mata but she's so cute kuma ta fito daga babban gida yakama ace tana shiga mutane," ta6e baki sehrish tayi tana ɗan kallonsu, 6an6aro hannunta junaid yayi daga jikin rigar shi, sannan ya miƙa ma Amrish yace "Gata nan dan Allah amana na baki ita, ki tafi da ita ba ta son komai ba da yake ita ɗin rainon kakarmu ce, sai ahankali," 😆 Murmushi Amrish ta saki tare da kar6ar hannun Sehrish tace"aikuwa na gode sosai da wannan kyautar, kuma zan ruƙe amana," Cikin raha sukayi sallama da Junaid yayin da suka shiga ciki da Sehrish duk ta zama tamkar mutun-mutumi , suna tafiya tana waiwayon junaid shima kansa sam yagaza tafiya kallonta kawai yake yi, sai yaji duk kewarta ta kama shi daker ya ɗaga mata hannu tare da yi mata bye-bye,' Sannan ya buɗe motarsa ya shige, yayi mata key sannan yaja ta da gudu yabar makarantar, sai da yayi nisa da driving ɗin sannan yayi parking ɗin motar agefen titi yana shesshekar kuka yana cewa "ko na minti ɗaya bana son rabuwa dake sehrish kewarki nake yi," yayi maganar tare da curo handkerchief ɗinsa daga front pocker ɗin rigarsa yana faman share hawayensa, ya jima acikin motar duk kasala ta dabaibaye shi daker ya iya tayar da motar yaci gaba da driving ya miƙi hanyar komawa gida 😥 Parveena da Naja'at Class ɗinsu suka wuce, Amrish ce tayi ɗawainiya da Sehrish ta raka ta har Admin ɗinsu wurin principal ɗin makarantar, maca ce hamshakiyar gaske tun da taji sunan sehrish tagane cewa daga Family ɗin Salahuddeen Hussein take, hakan yasa ta sake mata sosai har tana jan ta da fira, daga bisa ni taba ma Sehrish Sunan Class ɗin da zata zauna, Science department ne kuma an ci sa'a Class ɗinsu ɗaya da Amrish SS1 science C, Madaddalar ƴan iska ba 😂 (Nima Science C nayi a school ɗinmu wlh basa jin magana, dama anyi ittiƙafi babu wanda yakai ƴan C rashin jin magana) Hannunta na ruƙe dana Sehrish suka tunkari benen da zai sadaka da Upstairs ɗin makarantar, anan Classes ɗin suke akwai kuma na down, sehrish dae sai bin ko'ina take da kallo makarantar ta haɗu kamar ba wurin ɗaukar karatu ba saboda tsaruwarta ga wuraren shaqatawa, shiga Class ɗin sukayi mutun goma ne a cikinsa a ƙa'ida kowane class mutun 12 ne kacal acikinsa maza 6 mata 6, idan aka haɗa da Sehrish da Amrish 12 kenan student ɗin cikin sa, gaba ɗaya Ido yadawo kan Sehrish kowa da irin kallon da yake yi mata, Mazan class din kuwa tuni sun soma sakin baki suna cewa "Wow so beautiful, so hot, She looks so sexy," Gabanta ne ya faɗi kowa da irin abunda yake cewa, Matan kuwa wani irin kallo suke binta dashi irin kallon hadarin kajin nan,' ƙara ƙanƙame school bag ɗinta tayi daga tsayen da take, Amrish ce ta soma magana" Hello Class we ave a new comer today, She's from awesome family, i hope zaku bata hankalin ku domin tayi mana Introducing kanta," ta ƙarasa maganar tare da kallon Sehrish tace "Pls introduce ur self," ɗan gyaran murya Sehrish tayi sannan ta soma cewa "am....Sehrish Salahuddeen Hussein by name, 17years old.... Alhamdulillah I love the Way i am," Wannan bayanin na sehrish yasa su gaba ɗayansu Clapping hands ɗinsu suna tafa mata, musamman ƙarshen maganarta ta ƙayatar dasu, Sun mata kyakkyawar tarba duk da akwai waɗanda tunda ta shigo ma basu ɗago da kansu ba daga saman desk sun kife shi kamar masu bacci, Kowane seat mutun ɗaya ne, Amrish ta sama ma Sehrish gurbi a Middle Roll na Class ɗin 0a Second seat Amrish kuma na'a First seat, sai da tafara neman alfarma wurin asalin mai seat ɗin na sehrish akan tabar mata, kuma cikin sa'a ta amince shine har tasamu gurbi abayanta, komai yazo mata cikin sauƙi kuma ba ƙaramin daɗi taji ba na haɗuwarta da AMRISH 💃 ******************AUNTY BABBA*********************** tun da sassafe suna kwance wayarta ta soma ringing a firgice ta farka jikinta na sanye da kayan bacci brown colour, leƙa fuskar Ishaq tayi taga koya buɗe ido samun shi tayi sai faman Sharar baccin sa yake, don haka a hankali ta lalla6a ta sauko daga saman gadon cikin sanɗa, Bayan ta sauko ta ɗauki wayarta data ajiye saman side drawer ɗin shi, sannan ta lalla6a ta shige cikin toilet ta duba mai kiran nata mutumin da tayi tsammani shi ta gani wato*BABA ALAMU* murmushi ta saki cikin sauri ta ɗaga kiran ta kara a kunnanta tun kafin tayi magana baba alamu yace "Na faso gari fa, tun jiya da daddare inata kiran layin ki baya shiga," Aunty babba tace "wlh bansan ka kira ba, dayake nabar wayar acikin ɗakina sai da asuba na ɗauko ta, tun jiya nima nake jiran kiran naka mutumina," Dariya baba Alamu yayi sannan yace "Ae ke baki sani ba, jiya muna dira gari na kwaso rugwagwar motata na shigo unguwarku don in sanar maki kawai sai naga waɗannan Masu fuskar shanayen tsaitsaye ruƙe da bindiga ae ba arziƙi naja motata na koma," Fashewa da dariya aunty babba tayi tace"Ae mijina ne yadawo jiya shiyasa kaga sojoji nan," Baba Alamu yace "Oh to ashe angon ne yadawo, yanzu dae ya za'ayi wurin fitar da yaran kinsan fa wlh shegen tsoran Soja nake, don kwanaki sun ta6a tarar mu a hanya suka sanya mu tsallen kwaɗi a tsakiyar titi da rana tsaka," Aunty babba tace "Ae basu da Imani, musamman in suka ji su acikin kakin nan sai su dunga ɗaukar kansu tamkar wasu dodonni, yanzu abunda za'ayi kana ina ne? Baba alamu yace "yanzu haka na fito da mota ta ina kan hanyar zuwa unguwarku amma fa bazan shigo ciki ba sai dai ki san yarda zakiyi a fito da yaran, Aunty babba tace "Shikenan ka jira ni, zaka ga kirana yanzun nan bada jimawa ba,". bayan ta kammala maganar ta kashe wayar sannan ta fito daga cikin toilet ɗin cikin sanɗa ta lalla6a ta fuce daga ɗakin, Kai tsaye ta nufi ɗakin hafsat ta shiga, tsayawa tayi tana kallonsu hussana da jahad dake ta faman sharar bacci baje saman gadon hafsat, yayin da ita kuma hafsat ɗin ke kwance saman doguwar kujerar ɗakin tana bacci, da alama dukansu daga tashin asuba suka koma bacci, jinjina kanta tayi sannan ta ƙarasa dab da hafsat ta ɗansa hannu ta bubbuga ƙafarta, a dan firgice hafsat tafarka tana cewa "wanene," Murya ƙasa ƙasa aunty babba tace "ke ki taso inason magana dake," Bin ta da kallo hafsat tayi tana yamutsa fuska Alamar bacci bai ishe ta ba, daker tasa hannunta ta janye bargon data lullu6e rabin jikinta da tashi sannan ta miƙe tsaye tabi bayan aunty babba, suka fito daga ƙopar ɗakin suna fuskarta junansu hafsat tace "Meya faru mommy naga kin tashe ni ina tsaka da bacci na? Aunty babba tace "Mutumin fa wanda zai kai su hussana da jahad gidan marayu ya ƙaraso....," jin hakan yasa hafsat canza fuska tuni tace "Mommy yanzu dole sai kin raba ni da yaran nan? Wai me suka tsare maki ne? Dan Allah mommy kibarsu suyi rayuwarsu cikin salama, sun sha wahala fa baki tausayin su? tsoki Aunty babba ta buga tuni ta tamke fuska tace "Tausayin Uban me? menene alaƙata dasu? ke bana son zancen banza mun riga da mun gama magana dake don haka ! Ke nake so ki fidda yaran nan daga cikin gidan nan!! In yaso zan baki numbarsa in kin fitar dasu acikin motarki sai ki kira shi ki bashi su ya tafi dasu can Orphanage home ɗin," Murya asanyaye hafsat tace"shikenan mommy amma ina so ki sani haƙƙinsu ba zai ta6a barin mu ba! Sai Allah ya saka musu duk wani cin zalinsu da mu kayi,!!!!!!!!!!!!!!!! tana faɗin hakan ta juya tare da shigewa cikin ɗakin, wani irin matashin murmushi aunty babba tasa ki tare da cewa "Komai zaki ce ki ce, nidae in dae burina zai cika ba abunda bazan iya aikatawa ba ehen," acan ciki kuwa bayan hafsat ta shiga wuri tasamu gefen gadon ta zauna maimakon ta tashe su sai kawai tafashe da kuka mai cin rai Sautin kukanta ne ya farkar da jahad a firgice ta tashi zaune hankali atashe take cewa "Subhanallahi Aunty hafsat meya faru naga kina kuka? Meya same ki? jahad ta tambaya fuskarta cike da nuna alamun damuwa, Ci gaba da kukan hafsat tayi sam ta gaza cewa komai jikinta har wani jijjiga yake yi, jahad ta kuma cewa "dan Allah sister hafsat ki daina kuka, ban ta6a tunanin zanga wannan ranar ba, idan wani abu ke damunki, zan taya ki addu'a Allah ya yaye maki jin wannan maganar ta jahad yasa hafsat ƙara sautin kukan nata, ɗagowa tayi ta kalli jahad idanunta jawur suna fitar da zafafan hawaye tace"Jahad ba saboda kaina nake wannan kukan ba, face saboda ku ! Ina tausayinku, Nasaba daku zan iya cewa akanku nafara jin tausayin wani ɗan adam aduniyar nan !! tun da jahad taji hakan gabanta ya faɗi Rasssss !! Duk da hafsat bata fito fili ta faɗa mata kai tsaye abunda yasa ta kuka ba, miƙewa hafsat tayi tana faman sharar hawaye tace "Ki tashi hussana ku shirya inaso zan fita daku," Jiki a mace jahad tace "Toh," cikin sauri hafsat ta fuce daga ɗakin, Jahad kuwa jikinta har kerma yakeyi saboda tsoran inda hafsat zata kaisu, daker tasamu hussana ta farka daga bacci sannan ta sanar da ita cewa ta tashi su shirya Sister hafsat zata fita dasu, Batare da sunyi wanka ba, tsaka tsami kawai su kayi acikin toilet sannan suka fito suka shirya, jahad ta zumbula doguwar riga Orange colour ta yafa mayafi launin fari akanta, ita kuma Hussana riga ce Square neck green colour, sai Skirt Ethnic maxi ta sanya ajikinta yana da dan faɗi ya bude da ƴar bazarsa, ba ƙaramin kyau su kayi mata ba, Mayafi tasamu launin skirt ɗin black colour mai ɗigon fari² ajikinsa, tayi rolling ɗinsa tamkar yadda Jahad tayi, Kallon hussana kawai jahad keyi kallon tausayi don ita ranta yana bata cewa lokacin barinsu gidan ne yayi, yanzu kuma zasu fuskanci wata ƙaddarar !!! lokacin da suka fito daga ɗakin hannunsu ruƙe dana juna, Aunty babba na'a falon sai faman zagaye zagaye take yi, tana ganinsu ta nufo su cikin sauri gudun kada ishaq ya farka daga bacci ya fito yagansu, Tana ƙaraso wa inda suke tace "Ku biyo ni," sannan ta juya ta miƙi hanyar fita daga falon, bin bayanta su jahad su kayi gabansu na faɗuwa, suna fitowa daga falon a harabar gidan tuni hafsat ta fito da motarta, buɗe musu motar aunty babba tayi tana cewa "Maza ku shiga ciki, ku jira hafsat yanzu zata zo, Allah ya kiyaye hanya," ta faɗi tana faman tiƙar dariya sannan ta rufe musu motar, Kusan minti goma sha biyar suna zaune jigum cikin motar gaba ɗayansu babu mai magana duk jikinsu yayi mugun sanyi ganin yarda Aunty babba ke faman yi musu dariya, tun daga haka suka gane cewa ba lafiya," 😳😳😳 _wannan na jiya ne da banyi ba, da Anjima zan saki next page insha Allah kuma shine, Ga masu son cigaba da karanta Littafin Abban Sojoji su tuntu6e ni ta wannan numbar (08103884440) [9/16, 2:19 PM] 💋BOSS LADY💋: 💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋 The father Of Soldiers Story & Written by_*Boss Bature* page 27 Fitowa hafsat tayi hannunta janye da trolley ba komai bane aciki ba fa ce kayansu jahad, ɗayan hannun nata kuma na ruƙe da basket na breakfast dinsu data haɗo masu, 😥😥😥 Tana isowa ta buɗe boot ɗin motar ta saka trolley ɗin sannan ta rufe, duk aunty babba na tsaye ruƙe da qugu tana sakin murmushi, Bude back seat ɗin hafsat tayi inda su jahad ke zaune ta miƙa musu basket ɗin, hannu na kerma jahad ta kar6a, Sannan ta rufe musu murfin motar, har tasa hannu zata buɗe gaban motar ta shiga ta juyo ta kalli aunty babba idonta jawur tace "Baki bani numbar mutumin ba, wanda kika ce zai kaisu Orphanage home ɗin," cikin sauri aunty babba ta ɗago wayarta dake hannunta, tashiga contact numbar baba alamu ta lalubo, sannan ta shiga karanto ma hafsat ita kuma tana rubutawa a wayarta, bayan ta kammala sa numbar tashige cikin motar kafin ta rufo ƙopar ta aza idonta akan aunty babba tace "Ina fata kin ji daɗi mommy, yau hussana da jahad zasu bar miki gidanki, sai ki zuba ruwa a ƙasa kisha don murna," tana faɗin hakan ta datse motar tare dayi mata key, ta juya sitiyarin motar tayi baya² da ita sannan ta karya kwana ta juyar da ita direct ta nufi gate ɗin gidan ta fuce da motar aguje, Lumshe ido Aunty babba tayi afili tace "Alhamdulillah na kawar da wannan matsalar, yanzu abunda ya rage mun shine zuwa wurin boka domin gudanar da target ɗina na gaba," tana faɗin hakan ta nufi cikin gidan fuskarta washe yau ta rabu da alaƙaƙai, sai da ta ɗan yi nisa da motar ta fito bakin titi sannan ta dakatar da driving ɗin, wayarta ta ɗauko dake ajiye agefe, Lambar baba alamu ta danna ma kira, bayan ya ɗaga ta sanar dashi kwatancen inda motarta take, bayan ta katse kiran ta ambaci sunan Jahad da Hussana, atare suka amsa mata da "Na'am," juyo taɗanyi ta kallesu da idanunta waɗanda suka canza launi, cikin sanyin Murya tace"kun san inda za'a kai ku"? Har suna haɗa baki wurin cewa "A'a," Shiru taɗanyi kafin taci gaba da cewa "Gidan marayu !!!!!!!' Zaro ido su kayi gaba ɗayansu hankali atashe suna kallonta, hussana da tagaza jurewa tuni ta soma kuka tana cewa "Yaya Omar fa? dan Allah kar akaimu can ku bari yaya Omar yazo ya ɗauke mu mana, ni bana son mu rabu dashi," Murmushin takaici jahad ta saki tare da cewa "Aunty hafsat ba wai gidan marayun ke bama so ba, kawai ni so nake naji da sanin yaya Omar za'a kaimu can"? girgixa kai hafsat tayi tare da cewa "Jahad bada sanin shi ba, kuma nima ba da son raina ba na amince da hakan, amma ina so ku sani can shine zaifi muku zama cikin salama, saboda shi kan shi ya Omar ya manta daku tun da gashi ko kira a waya yadaina yi, babu tabbacin cewa ma yana ƙasar tunda dama banan yake zaune ba, don haka ku Cire tsammani da shi, kawai ku rungumi ƙaddara, kuyi haƙuri³," har kusan sau uku tana maimaita masu kalmar suyi haƙuri,. Hussana dae bata dakata da kukan da takeyi ba sai ma sautin da ta ƙara, jahad ta jinjina kai idonta acikin na hafsat tace "Shikenan Aunty hafsat, kada ki sa damuwa aranki, mu kan mu bamu ta6a tunanin zamu kawo wannan lokacin araye ba, amma gashi mun kawo da ran mu da lafiyar mu, wannan alama ce dake nuni da cewa Allah yana sane damu !!! Kuma shine zai kare mu aduk inda muka kasance a faɗin duniyar nan! mun gode sosai da kulawar da kika nuna mana," daga haka jahad tayi shiru idonta na zubar da hawaye hussana kawai take kallo wadda ke ta faman shessheƙar kuka, Jikin hafsat ya gama yin sanyi sam tagaza yin kwakkwaran motsi, suna cikin wannan Yanayin Motar baba Alamu ta ƙaraso dab da tasu, wata tsohuwar jeep ce ta ragwaggwa6e ta fita hayyacinta, kai wannan motar ko kyauta aka bani ita wlh na kwammace in ƙaraci yawona da ƙafafuwana saboda muninta, gaba ɗaya fa glass ɗin motar ya faffashe kana hangen cikin motar, babban abunda zai ɗaure maka kai shine yadda yakeyi wurin tayar da motar domin kuwa babu wurin zura mukulli atada mota, sai dae wasu wayoyi gasunan birjik su yake haɗawa sannan ya tashi motar, hankaɗa murfin motar yayi sannan ya fito, wani irin Matsolan mutun ne ramamme sai uban ƙasusuwa gashi baƙi wulik kana ganinsa kaga cikakken ɗan duniya, fuskarsa yana da wasu irin tsaguna waɗanda zasu tabbatar maka da cewa Magobiri ne, yadda kasan kwarya haka tsagunan fuskarsa suke, yana da kwalakwalan idanuwa kuma jawur dasu, ga wani irin fankacecan hanci harya so yafi ƙarfin fuskarshi, haƙoran bakinsa kuwa sunyi jawur dasu saboda Cin goro, a shekaru zai iya zarce shekara hamsin, jikinsa na sanye da wani tsohon yadi wanda yausha rabon da yaji dutsen guga tun 1960 😔 fitowa hafsat tayi ita kanta da ta ga mutumin sai da gabanta ya faɗi saboda muninsa, shi kuwa washe baki ya shiga yi yana cewa "Yarinya ta girma ! komai yaji dai² nasan baki sanni ba, amma ita jatumarki kullum tana bani labarinki," ɗaure fuska hafsat tayi zuciyarta har wani tashi take yi, hannunta na kerma ta buɗe masu hussana motar, fito wa Su kayi atare da jahad duk jikinsu ya gama mutuwa, musamman da su kayi arba da baba alamu, sai duk suka firgita jiki na kerma Hussana ta ƙanƙame jahad saboda tsoro, Buɗe boot ɗin motar hafsat tayi tare da curo masu trolley ɗin kayansu ta miƙa ma jahad ta kar6a, sannan ta ɗauko masu food basket ɗinsu da suka manta, ta miƙa ma hussana daker ta kar6a, Cikin kuka Hussana ke cewa "Aunty hafsat dan Allah kada ki tafi kibarmu a hannun wannan mutumin !!" rigima sosai hussana ta sanya, hafsat kuwa tsananin tausayinsu duk ya kamata, purse ɗinta ta ɗauko cikin motar, sannan ta ƙirgo kuɗi kusan dubu 30 ta miƙa ma Jahad tace "Ki ruƙe wannan a wurinki nasan za suyi maki amfani, ni zan wuce," Bin ta da kallo kawai jahad ke yi idonta na zubar da hawaye duk yadda hussana ke faman rusa kuka tana rurruƙe mayafin jikin hafsat amma hakan bai hanata tafiya ba, cikin sauri ta shige motarta, taja ta da gudun gaske tabar wurin, Mayar da idonsu su kayi kan Baba alamu wanda ke ta faman bin jikinsu da kallo yana sakin wani irin shu'umin murmushi, hannu yasa ya buɗe masu motar yace "Maza ku shiga ciki," Amsar trolley ɗin yayi ya bude boot ɗin motar ya wurgar dashi ciki sannan ya datse shi, shiga ciki su kayi gabansu na faɗuwa zuciyarsu nayin wani irin bugu mai sauti, dawowa yayi ya shige gidan gaba sannan ya jona wayoyin nan take motar tayi wata irin ƙara ƙirrrrrrrr bakin hayaƙi ya soma fita ta baya, sannan yaja motar da gudun gaske ya miƙi hanya dasu, ****************** tun jahad tana ganin gine-gine da gifcin mutane har ta soma ganin dajijjika, hakan yasa hankalin jahad ya tashi ganin ya fidda su cikin gari bayan cewa Hafsat tayi zai kai su gidan marayu, zazzare ido jahad ta soma yi gabanta na wani irin bugu, juyawa tayi don taga wane hali hussana ke ciki, abun mamaki saita samu hussana sai bacci take shara hannunta ƙanƙame da kwandon abincin su, Kai tsaye baba alamu ya kutsa dasu cikin dajin mai uban bishiyoyi da ciyayi ba gifcin mutun acikinsa sai dabbobi dake shawagi, Murya na rawa jahad tace "Bawan Allah ina zaka kaimu ne !? Ba gidan marayu akace zaka kaimu ba,"? Ta tambaya idonta cike taf da hawaye cikin tsananin tsoro, fashewa da dariya baba alamu yayi sannan yace "A sanin ku ba, amma ni ba gidan marayu nayi da ita hajiyar zan kaiku ba, ce mun tayi in zubar mata daku acikin daji," Cikin kuka jahad tace "Dan Allah kada ka cutar damu , ka sauke mu kawai anan," Baba alamu yace "Yarinya kenan ki daina wannan tunanin, ae tunda idanuwa na suka yi arba da surar jikinku na kwaɗaitu da son kasancewa tare daku, don haka zan kai ku gidan gonata dake acikin dajin nan don na runƙa rage zafi daku," ya ƙarasa maganar da wata irin shaƙiyar dariya, Jahad kuwa neman hanyar fita take yi daga cikin motar amma ta gaza buɗe murfin motar saboda ya datse shi sosai, duk wannan tashin hankalin da ake ciki hussana bata sani ba, saboda baccin da takeyi, jahad bata haƙura da ƴunƙurin buɗe motar ba sai da ta sanya iya ƙarfinta na ƙarshe ta tunkuɗe murfin motar ya buɗe aikuwa nan take baba alamu ya girgiza motar da mugunta, hakan yasa jahad ta faɗo ƙasa timmmmm ! ta gangara Ta bugi wani dutsi nan take goshinta ya fashe, Shi kuma yaja motar da gudu ya tafi da hussana acikinta, hankali a matuƙar tashe jahad ta ɗago daga jikin dutsen jini na zuba a goshinta, miƙewa tayi da gudun gaske tabi motar tana kuka tana ambaton sunan HUSSANA, muryarta har wani shaƙewa take yi saboda yadda take kwala mata kira ga uban gudun da takeyi don ta taddo motar, amma ina tuni yayi mata nisa ga tafin ƙafarta da ƙayoyi suka sossoke ta duk ƙafar ta fashe, jini nata faman gangarowa a ƙarshe data gaji da bin motar jiri na kwasarta nan take ta yanke jiki ta faɗi sumammiya acikin korayen ciyayin dake a wurin, 😭 Kiran ƙarshe da jahad ta kwalama hussana kafin ta sume har cikin zuciyarta taji shi tuni ta soma ƙoƙarin buɗe idanunta wanda ke cike da bacci, a lokacin har baba alamu yashiga da ita gidan gonarsa ƙopar katako ce ke gare sa tamkar ɗan gate, bayan ya shigar da motar ya fito ya rufe ƙopar gidan gonar da kwaɗon dake ajiki, Sannan ya koma tare da buɗe murfin motar inda hussana ke zaune tana faman lullumshe ido alamar bacci bai isheta, so take ta buɗe Idonta taga ina jahad take amma sam bacci ya hana Ta, hannu baba alamu ya zura tare da ɗauko hussana ya sa6ata a ƙafaɗarsa ya miki hanyar wata ƙopa inda ya dosa ya buɗe ta ya shige da ita ciki sannan ya sauke ta ƙasa har tana yin tangyaɗi zata faɗi, sai da baba alamu ya datse ƙopar ɗakin gam yadda bamai shigowa sannan ya juyo yana kallon hussana tare da washe waɗannan haƙoran nasa marasa saiti, A lokacin Hosana ta dawo cikin hayyacinta baccin yabar jikinta, bin wurin tayi da kallo ɗakine mai faɗin gaske babu komai aciki sai jarkokin ruwa da bulo bulo, da wani ajiyayen genarator tsoho, sai sauran tarkace, wurga idonta tayi akan baba alamu dake tsaye agabanta yana washe mata baki, nan take ta buga uban tsalle taja da baya tana faɗin "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un nashiga uku, Ina jahad take! Wayyo Allah na Me zaka yi mun meyasa ka kawo ni nan ! tayi maganar tana ja dabaya a tsorace Baba alamu ya kashe mata ido ɗaya tare da cewa "daɗi zan baki, kiyi shiru da bakin ki kada wani yaji mu, indai kina son ganin ƴar uwarki to ki bani haɗin kai muyi mu gama cikin salama,' Yayi maganar tare da kai hannu zai shafa fuskarta a firgice taja baya tana girgiza masa kai atsorace take cewa "Dan Allah kada ka cutar dani, ka ƙyale ni bani da lafiya, idan ka ta6ani mutuwa zanyi," ta faɗi tana faman zazzare ido, ga wata irin zufa dake wanko mata dakyar take haɗiyar numfashi, "Ba zaki mutu ba, bada zafi zan miki ba kaɗan kaɗan, in dai baki bani haɗin kai ba zan ƙwata ta ƙarfi kuma naƙi nuna miki inda ƴar uwarki take," Cikin kuka hussana tace "a'a nidai kada ka cutar dani bana so, kadaina matsowa kusa dani, wlh Allah bazai barka ba kuma yaya Omar ma bazai ƙyale ka ba sai ya kashe ka," fashewa da dariya Baba alamu yayi tare da gwalo ido yana mata gwalo yace "Wanene wani Omar kuma? babu kowa anan daga ni sai ke ! Kuma yanzun nan zan kawar da sha'awata tare dake," yayi maganar tare da yin kwakkwaran taku ya fusgo mayafin jikin husana nan take ya zame ƙasa, watsa wa tayi da gudu ciki tana kuka cikin rashin sa'a tayi tuntu6e da bulo ƙafarta ta harɗe ta kife ƙasa gaba ɗaya......................... dariyar mugunta baba alamu ya saki ganin abun yazo mashi cikin sauƙi, nan take ya shiga kwance zariyar wandonsa, daker hussana take jan numfashi saboda buguwar da tayi wani irin ciwon kai yafar mata lokaci guda, jin motsinsa dab da ƙafafunta yasa ta dumbuzar ƙasa a hannunta, ta daddage ta tashi zaune tare da watsa mashi ita a fuska, nan take yashiga yin tsalle yana faɗin "kai ! Kai!! Kai !! Don ubanki ni kika watsa ma ƙasa a ido! aiko bazan ƙyale ki ba, saina wulaƙanta rayuwarki, Jin hakan yasa hussana zabura tare da miƙewa tsaye zata gudu batayi wani aune ba taji yaja rigar jikinta nan take ta soma yage wa, juyowa tayi tare dasa hakoranta ta gartsa mashi Cizo, azaba da raɗaɗi suka sa shi sakin ihu, kuma hakan ya ƙara fusata shi, a fusace yabi ta tare da damƙo gashin kanta ya janyo shi da ƙarfi ta dinga sakin ihu tana kuka tana kiran Sunan Jahad, Matse ta yayi ajikinsa tare da sa hannun shi biyu ya ƙarasa yage rigar jikin hussana gaba ɗaya, hankali a matuƙar tashe husana ta watsa mashi miyau afuskarsa biji-bijin daya daya fara gani ne yasa shi ɗan dakatawa, hannunta ta sanya tare da ingije shi da ƙarfin gaske gaba ɗaya baba alamu yayi taga² zai faɗi ƙasa, Cikin sauri hussana ta tattare rigarta ta kare kirjinta da ita, hanyar fita daga ɗakin ta nufa da gudun gaske tana kuka burinta kawai ta isa kopar ta buɗe ta fuce tana cikin gudun nan baba alamu ya taso a matuƙar zuciye ya nufe ta da sauri yakai hannunsa tare da jan rigarta data rufe jikinta da ita, gaba ɗaya ya 6an6are rigar daga jikinta ya cire ta gaba ɗaya ya ruƙe a hannunsa, Wani irin kuka hussana ta saki mai matuƙar cin rai ganin yarda ya cire mata rigarta, gashi ko brazier bata sanya ba, ƙirjinta gaba ɗaya sun fito, hannunta ta sanya ta tarbesu tana kuka kuma hakan baisa ta daina tunkarar ƙopar ba, Bin ta baba alamu yayi da gudun gaske saboda ya ruƙo ta jikinsa don ya idasa nufinsa, Sai dae ina kafin yayi wani kwakkwan yunƙuri tuni anyi ma ƙopar ɗakin wani irin kwakkwaran Naushi nan take katakon jikinta ya farfashe gaba ɗaya ta buɗe, A tsorace baba alamu ya dakata yana faman zazzare ido don son ganin wanene wannan ya faɗo masa cikin gidan gonarsa !!!!!!!!!!!! Ita kanta hussana ta firgita tsayawa tayi jikinta na wani irin kerma ga zazza6i daya lullu6e ta, har lokacin hannunta na tarbe da ƙirjinta, Duro ƙafarsa yayi cikin ɗakin tamkar damusa wani irin kakkarfa ne mai ban tsoro, jikinsa na sanye da Jacket baƙa daga ciki kuma farar t*shirt ce wadda ta bayyana ƙirar ƙarfinsa, Sai dogon wando baƙi, bai bamu damar muga fuskarsa ba domin kuwa tana sanye cikin face mask baƙi, idonsa kuma na sanye da baƙin glass, gaban hussana ba ƙaramin faɗuwa yayi ba duk ta gama tsorata, baba alamu kuwa murya na rawa yashiga cewa "kai...Wai Wanene kai ! daga ina kake? Mai ya kawoka gidan gonata ! ya tambaya yana tada jijiyoyin wuya, Har lokacin bai da alamar yin magana, a hankali ya sanya hannunsa tare da ruƙo jaket ɗin dake ajikinsa ya cire ta gaba ɗaya yayi wurgi da ita, sannan ya mayar da hannun nasa ya tu6e t-shirt ɗin dake ajikinsa ya rage babu riga ajikinsa, Hankalin baba alamu ba ƙaramin tashi yayi ba ganin irin damtsen hannunsa a murmuɗe ga ƙirjinsa dake motsi abun gwanin ban tsoro, tuni zuciyar hussana tayi wani irin bugu nan take ta tafi zata sulale ƙasa, da Hanzari ya tarbota jikinsa gaba ɗaya tafaɗa a faffaɗan ƙirjinsa, hakan ya bashi damar zura mata t-shirt ɗinsa ajikinta donya rufe mata jikinta, bayan ya kammala sanya mata rigar, ya buɗe bakinsa ta cikin face mask ɗin yayi fito mai sautin gaske har saida baba alamu ya firgita yana faman kwalala ido, Da gudun gaske wani Saurayi ya shigo ya tunkare sa, batare da yace komi ba ya miƙe masa Hussana, cikin sauri yasa hannu ya ɗauketa tare da azata a kafaɗarsa ya fuce da ita, sai lokacin Yasa hannu ya cire glass ɗin fuskarsa tare da yin wurgi dashi, Azazafe ya sanya kyawawan idanuwansa waɗanda suka Canza Launi izuwa ja saboda tsananin 6acin rai, gadan gadan ya tunkari Baba alamu wanda ke shirin guduwa, hannunsa yakai tare da damƙar wuyan rigarsa ya ɗaga shi sama, ya dawo dashi ƙasa ya buga kansa jikin bulo nan take haƙora biyu daga bakin sa suka fito Jaga-jaga da Jini, saboda tsananin azaba da raɗaɗi ya sanya Baba alamun sakin futsari a wando yana cewa "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un na bani na 6atare na lalace nashiga uku, Dan Allah ka ƙyale ni wlh nabi Allah nabi manzonsa .,........... tsawa mutumin ya daka masa tare da cewa "Kasan da Allah kake ƙoƙarin aikata ma ƙaramar yarinya faɗe tsofe tsofe dakai!! mutun mara imani da tausayi irinka wanda baisan darajar ƴa' mace ba Sam bai cancanta daya cigaba da rayuwa ba,' ɗagowa baba alamu yayi yana ja da baya da baya idonsa jawur, jini na kwaranyowa daga bakinsa yana cewa "Dan Allah kada ka kashe ni ! Kabarni a haka naji jiki sosai, ina da ƴa'ƴa da mata in ka kashe ni zasu shiga wani hali.....' bai bari ya ƙarasa maganar ba, yakai masa wata irin mahangul6a da hanunsa nan take yasake fasa ihu, "Karka kuskura ka sake buɗe wannan ƙazamin bakin naka da sunan zakayi mun bayani ! Bani da lokacin sauraron jawabin Ka, har kana da bakin da zakace mun kana da ƴa'ƴa da mata, don ubanka su yaran daka ɗauko donka lalata ma rayuwa daga sama suka faɗo? Ko su basu da dangi ne da zasuyi kuka in sun rasa su? Idan ka lalata masu rayuwa kana da tabbacin zasu ƙara numfashi ne ko baza suyi ba ? Ka yi tunanin hakan? ! idan wani ya lalata rayuwar ƴarka yaya zaka ji? Ka ƙiyasta yaya raɗaɗin yake azuciya............yana faɗin hakan yasa hannu ya rarumesa tare da wujijjiga shi ya sake buga kanshi ajikin bulo ɗin nan take kansa ya fashe jini ya soma kwaranya, ko shurawa baiyi ba nan take ya mutu a mace............ (Yanzu ina amfanin irin wannan rayuwar? Ka mutu kana aikata irin wannan mummunan zunubin batare da ka shiryu ba? Shin mai zaka ce ma Ubangiji? mutum baison lokacin mutuwarsa ba, shiyasa ake so koda yaushe mutun ya kansance cikin shiri kuma ya kasance yana aikata abun kirkiri, sam baba alamu baisan cewa yau wa'adinsa zai cika ba, Ga yarda ƙarshem shi takasance Ya Allah kasa muyi kyakkyawan ƙarshe, kuma ka kare mu daga aikata aikin dana sani 🙏😥 duk da ya mutu amma hakan bai masa ba saboda raɗaɗin da yake ji azuciyarsa, hannu yasa ya rarumi ƙaton dutsin dake ajiye a ƙasan wurin zai rotsa masa kai, cikin sauri matashin nan daya fita da husana ya faɗo ɗakin ya tunkaresa tare da hanzarin ruƙo hannunsa yana cewa "Yalla6ai kabarshi haka mana, ya riga daya mutu," fisge hannunsa yayi yayin da idonsa ke cike tab da hawaye da wani irin huci yake cewa "Kabarni kawai na tarwatsa kansa ko zuciyata ta samu salama, kasan yarda nake ji acikin zuciyata kuwa, tamkar ana rura garwashin wuta acikinta saboda tsantsar baƙin cikin da nake ji, WANNAN MUTUMIN YA SHIGA HURUMINA !!!!!!!!!!!!!!!!!!!! ⁉❗‼❗❓❓❓❓❓❓ *SHIN WANENE WANNAN MUTUMIN DAYA FARMAKI BABA ALAMU ACIKIN GIDAN GONARSA AYAYIN DA YAKE ƘOƘARIN KETA HADDIN HUSANA*❓⁉ *WANENE SHI*❓❓ _*amsar tana a wurin hafsat Bature muhammad Boss Lady domin son sanin wanene wannan sai ku antaya kuɗinku naira 300 kacal Vip kuma 700 a wannan acct number ɗin 3196407426 first bank Bature hafsat Muhammad ku tura shaidar biya ta wannan layin da kuma masu tura recharge card 08103884440 kada ku bari abaku labari , masu karantawa ta facebook masu ƙaramar waya Recharge card zaku tura koda digits ɗinsa ne 200 only in kun daure kun biya da dama zaku cigaba da samun posting insha Allah Ku fara biya da hanzari daga yau zuwa monday, har yanzu dae nice dae Hafsat Baturen da kuka sani mai sauƙin kai, ban canza ba, kaɗanne kawai zasu fahimce ni👍👏* Alhamdulillah finally na kammala *💋💋okay MAJOR ya sake ruƙo hannunsa tare da cewa"Sorry Sir! Nasan Abun da ciwo, Amma mu gode ma Allah da muka ƙaraso akan Lokaci batare daya kai ga Cutar da ita ba" huci kawai yake yi yana kallonsa da idanuwansa waɗanda suka canza Launi bakomai yake tunawa ba fa ce yarda Baba alamu ya yayyaga ma Husana rigar jikinta, in ya tuna wannan abun zuciyarsa Tafarfasa take yi saboda 6acin rai, muryar major ce ta katse shi da cewa" Allah ya huci zuciyarka yakamata mu hanzarta barin gidan gonar nan domin muyi gaggawar kai su asibiti, Jin hakan yasa shi yin saurin zura hannu tare da curo wayarsa daga aljihun wandonsa, nan take ya shiga camera tare da saita gawar baba Alamu ya ɗauke ta hoto da kyau, bayan ya ammala ya mayar da wayar cikin aljihun sannan ya kalli Major yace "Duba min aljihun wandonsa kona rigarsa kaga ko za'a samu waya," Cikin hanzari Major ya zura hannunsa cikin aljihun baba alamu daker ya lalubo wata ƙaramar waya nokia, taji duniya don bala'e batteryn wayar saida aka sanya robali sannan aka ɗaure shi baya cikon da akayi masa,duk ta rakwakkwa6e wayar, "Sir ga wayar," ya faɗi tare da miƙa masa, bai kar6a ba bin wayr yayi da kallo kafin yace "Major cewa nayi ka ɗauko mun wayarsa ba wannan abun ba," ya faɗi yana nuna wayar hannun major ɗin Ƙiris ya rage major ya fashe da dariya saboda ya lura cewa Boss Man ɗin nasa baya cikin hankalinsa, "Sir wannan itace wayar, ka duba da kyau ta tsufa ne sosae shiya sanya ka ganta hakan," Ajiyar zuciya ya saki tare da cewa "Keep it in ur place, zan neme ta," yana faɗin hakan yakama hanyar fita daga ɗakin, Muryar Major ce ta dakatar dashi da cewa "yalla6ai rigar fa? zan iya ɗauko maka ita," ya tambaya yana jiran amsa , Bai amsa mashi ba ya fuce kawai cikin sauri major ya ɗauko Jacket ɗinsa da yayi wurgi da ita sannan ya fito daga ɗakin ruƙe da ita a hannunsa a lokacin har yakai wurin motarsu da suka zo da ita, kai kana ganin yarda sukayi parking ɗinta kasancewa a tsiyace suka shigo da ita, domin kuwa har katakon ƙopar gidan gonar duk sun tarwatsa shi, Cikin sauri Major ya rufa masa rigar abayansa shi kuma ya ƙara gyarata ajikinsa sannan ya zuge zeep ɗinta, buɗe motar yayi sannan ya shige back seat ɗin shikuma major ya shige driver seat sannan ya tayar da motar yayi baya² da ita kafin ya karya kwana ya fito daga gidan gonar da gudun gaske yake driving ɗinsu, Sam ya gaza ɗauke idonsa akan hosana dake langwa6e asume kusa dashi, duk gashin kanta ya gama tarwatsewa dama a hargitse yake sai kuma aka ƙara hargitsar dashi, duk ya rufe mata fuskarta, lumshe idonsa kawai yayi har lokacin yana mamakin yarda akai wannan Lamarin ya afku amma yana da tabbacin cewa major yana da masaniya akan hakan," adai dai hanyar da baba alamu yayi wurgi da jahad Major yayi parking ɗin motar, cikin sauri ya buɗe motar ya fito gabansa ne kawai ke faɗuwa tsoranshi kar ace ta mutu, wani saurayi ne zuƙunne a inda jahad take yashe, da alama ba ƙaramin taimako yayi mata ba, domin kuwa ya ciccire mata ƙayoyin da suka soki ƙafarta sannan kuma yayi amfani da Mayafinta wurin kekketa shi izuwa kashi uku, ya ɗaure mata goshinta sannan kuma ya naɗe mata ƙafafunta dake zubar da jini, Fitowa major yayi shima yana kallonsa, "Major karfa ace yarinyar nan ta mutu," ya faɗi a tsananin tsorace "Sir she's still alive, suma ce kawai," ya bashi amsa, saurayin yace"yalla6ai tana buƙatar taimakon gaggawa saboda jinin dake bleeding a goshinta da kuma tafin ƙafarta," Cikin tsananin tashin hankali ya ƙarasa tare dasa dukkan hannayensa ya tallabo JAHAD ya ɗaukota da sauri Major ya buɗe masa motar ya shigar da ita a kusa da Hossana ya zunar da ita a sume, sannan shima yashiga motar, zuge glass ɗin yayi tare da kallon saurayin yace"Ka shiga mu tafi tare," saurayin yace"yalla6ai machine ɗina fa"? tunkan ya bashi amsa major yayi saurin cewa"daraban kayima arziƙi ƙulli ana maganar arziƙi wake ta wani machine"? Jin haka yasa saurayin tasowa sai da ya bari major yashiga, sannan shima ya shiga kusa dashi ya zauna, rufe motar su kayi sannan da gudu suka bar dajin suka miƙi santalelen titin da zai sadasu da inda suka dosa Kallonsu kawai yake yi ransa na ƙara ƙuna ganin irin jigatar da yaran su kayi yaran daya kai Amana, sam kwalwarsa ta rikice yarasa gane ma wannan lamarin ba komai yake son ji ba face yarda akai har tsohon can ya ɗauko yaran izuwa cikin gidan gonarsa don ya lalata rayuwarsu! taya akai ya fito dasu daga gidan general Ishaq? taya akai Aunty laila tayi gangancin da har wani zaizo ya ɗauki twins ɗinsa? da sa hannun wa akayi wannan ƙulla-ƙullar, tabbas kowaye bazai ƙyale shi ba, muddin ya gano gaskiyar lamarin!!, ya ƙarasa zancen zucin nasa adai² lokacin da suka ƙetaro Abuja, kai tsaye suka wuce dasu izuwa katafaren asibitin SGR, ***************SEHRISH*************** Sam bata gane mai ake koyarwa acikin class ɗin saboda wata irin yunwa dake jibgarta ga wani irin bacci da take ji, sai faman hamma take yi tana lumshe ido, Wuraren ƙarfe tara da rabi, time ɗin break yayi gaba ɗaya ƴan class ɗin sai fita suke yi don suje cin abinci, Sehrish na kwance saman desk ɗin gabanta sai faman sharar bacci takeyi, juyowa Amrish tayi daga seat ɗinta tana kallonta, murmushi ta saki tare da sa hannunta taɗan bubbigi bayan sehrish tace "Get up baby ! time ɗin break yayi, yakamata mu fita," daker sehrish ta buɗe ido tare da ɗago kanta daga saman desk ɗin tana kallonta biji², miƙewa Amrish tayi ta fito daga seat ɗinta, sannan ta ruƙo hannun sehrish tana cewa"Get up mana Let's go,ko bakya jin yunwa ne"? ta tambaya tana kallonta, miƙewa sehrish tayi tare da biyota suka fito daga Class ɗin gabanta nata faɗuwa tsoranta kar ace siyen abincin zasuyi don ko sisi bata fito dasu ba, babu wanda ya bata kuɗi, saukowa sukayi daga saman benen duk inda suka bi sai an samu wanda zai yi ma Amrish magana, kuma yawanci akan Sehrish suke tambayarta ko ƴar uwarta ce, sai dae kawai tace musu eh, saboda tasan son jin gulma ne kawai, Hanya suka miƙa bada jimawa ba suka ƙaraso Lunch room ɗin makarantar wurin cin abincinsu, lokacin da suka shiga wurin mamaki ya kama sehrish ganin ɗalibai aciki kowa zazzaune saman dining tables masu mazaunin mutun 4, kowa wanne gabansa cike shaƙe da abinci sai ci suke yi, Ruƙo hannunta Amrish tayi adai² wani tebur da bakowa tace ma sehrish tazauna sai faman zare ido take yi gabanta na faɗuwa tsoranta kar ace tabada kuɗin abinci, "Me kike so na amso mana muci"? Amrish ta tambaya tana kallonta daga tsaye, zuru sehrish tayi tana tunanin yarda za tace ma Amrish bata da ko sisi,' "Kin yi shiru baki ce komai ba"? Amrish ta tambaya a ƙagare, murya na rawa Sehrish tace "Ni bana jin yunwa, a ƙoshe nake," Cikin mamaki amrish tace "but alamu fa sun nuna cewa kamar kina jin yunwa? Yakamata ko Coffee ne kisha taya zaki zauna da yunwa acikin ki"? sehrish tace"kada ki damu bana jin yunwa ne kawai," jinjina kai amrish tayi tare da cewa "its ok bazan takura maki ba, tunda kince bakya jin yunwa, ni bari naje na amso abunda zanci," tana faɗin hakan ta wuce wurin masu zuba masu abincin, ɗagowa sehrish tayi tana kallon students ɗin dake zazzaune suna faman cin abinci hankalinsu akwance, haɗiyar miyau tashiga yi ganin yarda suke Cusa pancakes da zuma abakinsu, sunnar da kai tayi gaba ɗaya tarasa yaya zatayi ga yunwa tana ji amma tana tsoran taci musu abinci ba kuɗin biya, tana cikin wannan tunanin sai ga Amrish tadawo hannunta ɗauke da plate guda biyu da murmushi afuskarta, ta ajiye su saman table ɗin sannan ta juya ta koma domin amso masu abunsha, Zuru sehrish tayi tana kallon plate ɗin mai ɗauke da banƙararriyar kaza ta gasu sosai hada ƙaramar knife wadda mutun zai yanka yaci, ɗayan plate ɗin kuma Snacks ne acikinsa shaƙe, runtse ido tayi tana ji tamkar takai ma plate ɗin hari, sai faman cixon la66a takeyi, dawowa Amrish tayi hannunta ruƙe da Laca sera mai sanyin gaske roba biyu, wuri tasamu tana fuskantar sehrish tazauna tana cewa "Wai haryanzu kina akan bakan ki na ba zaki ci komai ba"? tun yanzu zamu fara haka dake? ɗan murmushin yaƙe Sehrish ta saki tare da cewa "ba haka bane just bana jin yunwa ne shiyasa," ta faɗi tamkar zatayi kuka, Ido ya gani rai naso, Murmushi kawai Amrish tayi kafin tasa hannu ta ɗauki ƙaramar wuƙar dake ajiye saman kazar tashiga yankar naman tana ci, Ƙiris ya rage sehrish tasaki miyau saboda tsabagen kwaɗaituwa da tayi cikin sauri ta gyara natsuwarta gudun kar tayi abun kunya agaban sabuwar ƙawarta, Muryar amrish ce ta katse ta da cewa "Ko lemun ba zaki sha ba"? Cikin sauri tace"eh a ƙoshe nake," giɗa kai tayi sannan taci gaba da cin abunta, suna cikin zaman nan sai gasu Naja'at da parveena sun shigo, kai tsaye wurinsu suka nufa suka samu wuri suka zazzauna, Naja'at tace "Wlh da wata irin yunwa na fito Class ɗin can, sam bana gane ma karatun, dama can nifa ba gane math nake ba,' tayi maganar tare da sa hannu ta ɗauki robar lacasera tare da buɗeta ta kwafa abakinta tana kwankwaɗa, hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba ganin tashanye mata lacasera ɗin da Amrish ta kawo masu, Ana cikin haka parveena ta tsoma hannu suka cigaba da cin roasted chicken ɗin da Amrish ta kawo masu, kafin kace mai tuni sun kwamushe komai, duk tana zaune tana faman haɗiyar yawu, sai da suka kammala sannan ma suka lura da ita, parveena tace "Au! Wai dama Yarinyar nan tana a wurin nan? Yo aini yunwa tasa nagaza gane ku nawa ne zaune a table ɗin muka tarar," ta faɗi da mamaki Naja'at ma tace"ko ni ban lura da ita ba, sai da kikayi magana Allah, sannu ko? Meyasa ke bakici komai ba ne," Tamke fuska sehrish tayi rai a6ace tace "bana jin yunwa," jinjina kai su kayi atare naja'at tace "halan kinyi breakfast dayawa ne a gida"? A ƙule sehrish tace "Bansani ba," acikin zuciyarta tayi maganar a fili kuma tace "eh," daganan suka ci gaba da firar su har Parveena ta ƙaro masu abincin duk tana zaune suka zauna suka lamushe suka bar rishi da tanɗar baki, da lokacin komawa Class yayi kowa ya wuce Ajinsu naja'at da parveena class ɗinsu ɗaya don haka suka wuce atare, ita kuma tabi Amrish izuwa nasu Class ɗin, Sehrish ba ƙaramin jiki taji ba, saboda azabar yunwa har wani jiri take gani, dishi² ta runƙa gani a idonta sam batasan me aka koya masu bama, Lokacin da suka taso daga school tunani ta soma yi wa zai zo ya ɗauke ta, ga school bus tashigo cikin makarantar amma tsoranta kar ace kuɗi za'a biya,tsayawa tayi hannunta ruƙe da school bag ɗinta sai faman lullumshe ido take yi, suna cikin tsayuwar nan sai ga drivern Amrish ya iso, sallama tayi ma sehrish sannan ta shige cikin motar suka tafi, Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba, ganin sai zuwa ake ana kwashe sudents ɗin ita gatanan tsaye zugudum babu alamar wani zaizo ya ɗauke ta, tana cikin wannan tunanin motar JUNAID tashigo cikin makarantar adai² inda take tsaye yayi parking ɗin motar tare da zuge glass ɗin motar yace "madam muje ko," ajiyar zuciya ta saki ba ƙaramin daɗin zuwan shi taji ba, buɗe motar tayi tashiga sannan yaja motar suka fita daga makarantar, Miƙar hanya yayi dasu yana cikin driving ɗin yaji sehrish ta faɗo masa a kafaɗarsa ta langwa6e, saboda shock ɗin daya ji har saida yaɗan ci burki a tsakiyar titin, aza idonsa yayi akanta, wani irin wahalallan bacci ne ya ɗauke ta batare da saninta ba, shine ta faɗo masa a shoulder ɗinsa, gaza janye idonsa yayi akanta yadda take ta faman sharar baccin ta ba ƙaramin kyau tayi masa ba, ya jima yana kallon kyakkwawar fuskarsa, sam.ya manta cewa a tsakiyar titi suke, sai go slow suke haɗawa batare da saninsa ba, har sai da wani babban mutun yayi masa magana ta waje, sannan ya tashi motar yaci gaba driving ɗinsa cikin kasala, har suka ƙaraso gidan adai² parking space ɗinsu ya ajiye motar, sannan yajuya ya kalli sehrish tare dasa hannunsa ya shafa gefen fuskarta tare da ambaton sunanta"Sehrish mun iso gida fa, wake up pls ," ya furta yana kallon yadda take motsi da idonta alamun zata tashi, daker ta iya buɗe idonta tana kallon shi sunyi jawur dasu ga bacci ga yunwa, junaid yace "reesh kamar baki lafiya fa? Look at ur eyes fa sun janza kala, A kasalance tace "yunwa nake ji sosai banci komai ba tunda naje school, ga wani wahalallan bacci da nake ji," ta ƙarasa maganar tana faman yin hamma, har time ɗin suna acikin motar, Tun da tasoma magana junaid ya saki baki yana kallonta har sai da takai ƙarshen maganarta sannan yace "Kina nufin wai baki ci komai ba a school to saboda me? Ya tambaya yana kallonta Yamutsa fuska tayi tare da cewa "junaid ban fa da ko sisi balle na sayi abinci, shiya sanya," Wani irin kallo junaid ke bin ta dashi kallon na tausaya maki, ga takaicin daya hanasa yin magana,jin yayi shiru yasa ta cewa "ka tashi mu shiga ciki, kuma naga kana kallonta," A ƙule yace "Haushi kika ban ne,shiyasa nagaza magana, reesh waya ce maki sai kin biya kuɗi zaki ci abinci? An fa riga anbiya kuɗin komai na school ɗinki, tun daga school fees har kuɗin abincin ki dana school bus da zaki dunga hawa har na tsawon 3 months fa," Jin haka yasa sehrish zaro ido waje baki asake tana mamakin ashe itace shashashar batasani ba ta hana kan ta cin haƙƙinta, ashe an biya kuɗin komai ita kanta takaicin ne yasa ta yin kasaƙai, Fitowa sukayi daga motar atare suka shige cikin gidan a babban falon suka rabu ta wuce bedroom ɗinta shi kuma ya wuce upstairs ɗakinsa, babu kowa acikin gidan abunda ya ɗaure mata kai, tana shiga ciki tayi wurgi da school bag ɗin sannan tashiga tu6e uniform ɗin suma duk nan tayi watsi dasu saman gadonta, bayan ta kammala ya rage daga ita sai half vest da gajeran wando, toilet tashige shaf shaf tayi wanka tare da ɗauro alwala tafito, cikin hanzari ta buɗe wardrobe ɗinta ta zumbula doguwar riga, sannan ta zura hijabi tare da shimfiɗa darduma ta kabbara sallar, tana kammala sallar ko addu'a bata tsaya yi ba, ta haye saman gadonta ta baje tashiga sharar bacci maganar yunwa kuma wata'kil saita tashi sannan tashiga neman abinci, Turo ƙopar Azmee tayi ta sameta tana ta jan minshari bin ko'ina tayi da kallo ganin yarda tayi wurgi da school bag ɗinta ga uniform ɗinta data watsar saman gadon, murmushi kawai tayi tare da girgiza kai tace "ƴan makaranta kenan, tun yau anfara wurgi da shool bag ga uniform a watse saman gadon maimakon ta ninke su," ta faɗi da murmushi a fuskarta sannan taja mata ƙopar ta fuce, ta jima tana bacci sai wuraren sallar la'asar sannan tafarka da wata irin matsiyaciyar yunwa ba arziƙi ta fito ta wuce kitchen, har time ɗin babu kowa, roƙon da take yi Allah yasa babban yaya ba us suka koma ba, Acikin tray ta haɗa abincinta sannan ta zauna a kitchen ɗin tana ci tana tunanin duniya,' **********Twins*************** Duk yinin ranar ba inda suka je saboda tashin hankali sam sun rasa inda zasu tsoma ransu, tun da sanyin safiya bayan sun dawo daga sallar asuba, haroon ya faɗo masu ɗaki domin ya ƙara jaddada masu akan buƙatun daya nema a wurinsa, Jahan ya tsawatar masa akan cewa ko nawa yake so zasu bashi amma kada ya sake yayi kuskuren cewa zai ƙara kusantar ɗaya daga cikinsu, da jin wannan maganar sai haroon yace ya amince amma bisa sharaɗin cewa zasu ƙara mashi miliyan 80 in har suna son ya daina bibiyarsu Kuma cikin sati guda kacal ya basu in ba haka ba zai tona masu asiri 😥😳 tun safe basu ci komai ba, ko fitowa ba suyi ba daga bedroom ɗinsh, kuma babu wanda ya lura da hakan illa junaid da yayi ta tambayarsu har ɗakinsu sai da yazo yayi ta faman knocking yana kiran sunan su, suna jin shi tamkar zasu yi kuka amma basu amsa mashi ba,ƙarshe yayi tunanin cewa basa nan yayi tafiyarsa, Ayaaan ya sha kuka aduk lokacin daya tuna abunda ya faru dasu daren jiya sai yayi yunƙurin amai, yanzu haka ma yana zaune gefen gadon idonsa jawur ya ɗago ya kalli jahan dake ta faman safa da marwa acikin ɗakin yace "Dan Allah jahan mu hanzarta mu sama mashi kuɗin daya buƙata, if not wlh so yake ya kashe mana rayuwa," ya faɗi yana faman matse hancinsa da yayi jawur saboda matsar daya sha da hannunsa, Jahan ya dubesa cikin damuwa tare da cewa "Ayaan bansan ya zanyi ba ! Wa zan fara tunkara game da kuɗin nan? duk wanda zamu tambaya acikin brothers ɗin mu ko Abban mu dole sai sunji me zamuyi dasu kafin su bamu, daga baya ma zasu tambaye mu ina abunda muka siya dasu, don haka Mommy ce kawai nake tunanin zata iya bamu kuɗin amma matsalar shine tana fushi da mu saboda bama kiranta a waya muna gaishe ta," Jahan ya ƙarasa maganar tare da samun wuri ya zauna kusa da Ayaan ɗin, "Jahan mom ita kaɗai ce solution, mu jaraba kiranta kawai mu sanar mata mu ji mai zata ce," "Video call zamu kira ta, may be tafi tausaya mana in taga yanayin mu" Acewar jahan, yayi maganar tare da miƙewa ya ɗauko laptop ɗinsu dake ajiye saman drawer ɗinsu, komawa yayi ya zauna dab da Ayaan sannan ya zaro wayarshi tare da buɗe laptop ɗin, duk ayaan na zaune zugudun yana jiransa ya kira, zama su kayi suka ƙurama screen na laptop ɗin ido suna jiran mommyn nasu ta ɗaga kiran cikin sa'a ta ɗaga masu kiran, har haɗa baki suke yi wurin cewa "Mommy," tana zaune cikin haɗaɗɗen garden saman gujera hannunta ɗauke da cup na coffee da alama sha takeyi, ta jima tana kallonsu sai daga bisani tace "sai yau kuka ga damar kira na"? "Sorry mom ba haka bane.....," suka faɗi atare, girgiza kai alexandra tayi tare da cewa "to menene? halan wani abu ku ke buƙata shiyasa kuka kira ni"? Shiru su kayi suna kallonta ba bakin magana, tsoki taja tare da cewa "if u can't talk to me, i will reject the call right now"! Cikin sauri jahan yace "pls mommy don't reject the call, zamu yi magana, pls Ayaan kayi mata bayani" ya faɗi yana kallon Ayaan shima murya tamkar zaiyi kuka yace "Jahan i don't know what to say, kai kayi mata bayani pls," mamaki ne ya kama Alexandra ganin yadda suke ta jayayya akan wanda zaiyi mata bayanin dangane da kiran da sukayi mata, tsawa ta daka masu tare da cewa "bana son shiriri James! kuyi mun bayanin kiran da kuka yi mun within 5 mins if not zan kashe kiran " Natsuwa su kayi gaba ɗayan su sannan jahan ya soma cewa "Mom dama.....um......kuɗine...muke....so...awurin ki, ki bamu," tana jin haka ta fashe da dariya hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba jin yarda mommyn nasu ke 6a66aka dariya, Ayaan yace "mom why are u laughing pls, don Allah ki tausaya mana mommy muna cikin wani hali ni da Jahan....' dakatawa tayi sannan ta soma magana anatse "Har nawa ne kuɗin"? Jahan yace "80million," ɗan zaro ido tayi tare da cewa "har 80m? what are going to do with it? Ayaan yace "mom dan Allah kada ki tambaye mu me zamuyi dasu, saboda ba zamu iya yi maki ƙarya ba, kawai ki taimaka ki ba mu," Murmushi ta ɗan saki tana kallonsu na wani lokacin kafin tace "Ni a wuri na miliyan tamanin tamkar naira tamanin take, naji zan taimaka na baku amma bi sa sharaɗi ɗaya"! Har sun fara sakin fara'a amma jin maganarta ta ƙarshe yasa su dakatawa da murna, Jiki asanyaye Jahan yace "what mom"? alexandra tace "Inaso ku sa ROMEO ya kira ni a waya, sannan ya kira ni da sunan mommynsa Kuma ya bani haƙura na bijire mun da yake yi, kiran yakasance video call ne, in har ku ka sa romeo ya amince ya kira ni awaya,i promise to give each one of u 50 50millions,' tayi maganar tare da jaddada musu, Zaro ido suka yi gaba ɗayansu ga samu ga rashi, domin kuwa sunsan cewa Junaid bazai ta6a kiran mahaifiyarsu ba harya bata haƙuri kuma ya kirata da sunan mommynsu tabɗijancan, gaba ɗaya sun tafi zurfin tunani suka ji tace "i will be waiting to hear from u guys," tana faɗin hakan ta kashe video call ɗin, Hannu ayaan yasa ya rufe laptop din sannan ya kalli jahan wanda shima kallonsa yake yi yace "Yanzu ya zamuyi jahan? ga samu ga rashi ! duk da nasan junaid yana son mu sosai kuma yana yi mana biyayya zai iya yi mana komai amma banda wannan ALFARMAR, zugudum su kayi cikin tsananin tashin hankali da kuma tunanin yarda zasu tunkari junaid da maganar! 😥 ***********JAHAD***********"** a hankali ta soma buɗe idanunta biji² ta dunga gani a idonta, daker take motsa su zata buɗe su, sai faman ambaton sunan Allah take yi a hankali, lokacin da taƙarasa buɗe idanun nata mamaki ne ya kamata ganin ta kwance a wani ɗaki, komai na cikinsa fari ƙal a tsaftace, ga mutanen dake tsaye akanta farare fat hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, gaba ɗaya ranta ya bata cewa mutuwa tayi ne, saboda yanayin wurin da ta gani fari ga mutanen dake tsaye akanta farare, hawaye ne suka soma zubo mata a idanunta cikin kuka take cewa "Ya Allah kasa ba mutu nayi ba,nabar hussana aduniya wurin wancan fasiƙin mutumin, nashiga uku wa zai taimake ta acan, meyasa mutuwa bata ɗauke mu, mu biyu ba atare? Sai ta ɗauke ni nikaɗae tabar hussana a waccen duniyar mai cike da ruɗani," gaba ɗaya jahad ta fashe musu da kuka, Hankalin nurse ɗin dake tsaye da likitan ba ƙaramin tashi yayi ba, cikin sauri su kayi kanta, ko da jahad tagansu sai ta ƙara sautin kukan tana cewa "innalallahi wa'inna ilaihirraji'un,! dan Allah su wanene ku farare haka, ina hussana take, zama nurse ɗin tayi daga gefenta sannan tace "Sannu da jiki ƴar uwata, ni ce nurse ɗin dake kula da ku, sunana Camila ke fa"? Jin tayi mata magana raɗau da hausa yasa jahad dawowa cikin hayyacinta sosai tana kallonta da mamaki, kana kallonta ka ga english woman, Cos majority na ma'aikatan asibin sgr daga u.s suke, wasu daga india, wasu kuma ƴan nan nigeria, akwai kwararrun likitoci da nurses acikin asibitin, ƴunƙurawa jahad tayi zata tashi cikin sauri Camila tasa hannu tare da mayar da jahad kwance tace "Ana miki ƙarin jini ne, ko baki lura ba ne"? ta faɗi tana kallonta da murmushi a fuskarta, ɗan juyawa jahad tayi ta kalli ledar ƙarin jinin da akeyi mata, sassauta muryarta tayi sannan tace "sister dan Allah ina ne nan? Kuma waya kawo ni nan? Murmushi Camila tayi sannan tace "nan asibiti ne, sannan yayanki ne ya kawo ki domin mu baki kyakkyawar kulawa!" Cikin mamaki jahad tace "Yayana kuma? ae ni bani da kowa aduniyar nan ƴar uwata ce kawai hussana nasani, dan Allah tana ina"? tayi maganar tana jiran amsa, duk tattaunawar da suke yi dr Emran na tsaye yana jin su , kafin Camila ta buɗe baki tace wani abu sai ga MARSHAL OMAR ya shigo ɗakin shida Major, gaisawa su kayi da dr emran, sannan ya matsa wurin da jahad ke kwance, tsayawa yayi yana kallonta fuskarshi asake saboda ganin yarda ta wartsake alamar tasamu kyakkwar kulawa awurin Nurse ɗin, Sam jahad bata lura da marshal omar ba dake atsaye har sai da ya ambaci sunanta "JAHAD," A razane ta wurga kwayar idonta akan shi, ganin Ya Omar ɗinsu yasa ta zabura zata tashi zaune da sauri Camila ta mayar da ita, duk tabi ta zazzare idonta tana nuna shi da hannu tana ambaton sunan shi cikin tsananin mamaki, tashi Camila tayi taba Omar wuri donya zauna kusa da jahad saboda ta lura yarinyar nason magana dashi, Zama Omar yayi saman chair ɗin dake facing medical bed ɗin da jahad ke kwance asama sannan yace "Ya jikin naki"? tana jin haka ta fashe da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita, hannunta tasa ta ruƙe hannunsa tana cewa "Ya Omar ina ka shiga tsawan kwanaki kabar mu, bakasan halin da muke ciki ba..........' tana magana muryarta na shasshaƙewa saboda kukan da take, sam Omar ya gaza cewa komai tuni idonsa sun cicciko da kwalla, Jahad taci gaba da cewa "Ya Omar har yanzu nagaza yarda cewa kaine! dan Allah kayi mun magana taya akai haka tafaru ya omar, kuma ina hossana take? mutumin nan ya gudu da ita ya omar..........." kasa ƙarasa maganar tayi saboda hannunsa daya sanya ya rufe mata bakinta........................................Bin idanunta yayi da kallo itama tana kallon nashi hawaye ne cike taf da idonta, bai janye hannunsa daga bakinta ba har sai da ya tabbatar cewa ta samu natsuwa sannan ya zame hannunsa yace "Jahad duk wani abu dake faruwa ni bansani ba,bani da masaniya akai,jiya ne aka turomin saƙo da privet number bansan ko wanene be,let me show the message, Hannu yasa ya curo wayarsa daga trouser pocket ɗinsa kunna wayar yayi sannan ya shiga wurin messages ya buɗe saƙon ya nuna ma jahad don ta gani, Zuba ma screen ɗin wayar tayi da ido tana karantawa kamar haka _"Omar ka yi ganganci daka bar rayuwar yaran nan a hannun Laila, ina baka shawarar ka hanzarta zuwa ka ɗauko su, saboda naji cewa gobe goben nan za'a fitar dasu daga gidan_" Janye wayar yayi sannan yace"lokacin da message ɗin ya shigo mun bana cikin natsuwa ta, saboda mun shiga tashin hankali,ƙanne na da aka tura aiki miyagu suka farmake su, mun samu nasarar ceto rayuwarsu kuma mun kama wasu daga cikin waɗanda suka farmake sun, yanzu haka da nake maki magana ɗaya daga cikinsu yana kwance a A&E ward, baisan inda kansa yake ba,saboda sai da suka banka mashi kayan miyagun ƙwayoyi sannan suka azabtar dashi, ba don Allah yasa an samu wani daga cikinsu ba yayi mana waya da shikenan ba'asan mai zai biyo baya ba, Shiru Omar ya ɗanyi na wani lokaci kafin yaci gaba da cewa "tun shekaran jiya da muka fita daga gida muna can wurin cetonsu,a asibitin nan aka kwantar da waɗanda suka raunata sosai daga cikinsu,gaba ɗayan mu babu wanda ya samu runtsawa adaren jiya saboda tashin hankalin kada mu rasa su,kuma a daren jiyan ne acikin asibitin nan saƙon ya shigo mun,duk nabi na rikice saboda narasa yarda zanyi, Major shine babban na hannun dama na, shi na kira na nuna mashi saƙon da aka turomin game daku, koda ya gani sai cewa yayi dama ya jima yana son ce mun wani abu, amma ba zai iya sanar dani ba saboda bayason shiga tsakanina da matar yayana, sai abun ya ɗaure mun kai jin abunda yace,a lokacin ban matsa masa ba akan son sanin wani abu ne yake son sanar dani ba,a time ɗin duk da halin da nake ciki burina kawai inzo in ganku, Major shine yace nabar masa komai a hannunsa kar na damu, sai a washe gari major ya sanar dani cewa mu shirya mu tafi, sannan kuma yaban wata number yace mu bi diddiginta, atare dashi muka fito mu biyu kawai muka miƙi hanya, da wayata nayi amfani wurin bindiddigin numbar daya bani har muka ƙaraso titin da dajin nan yake,mu ka shiga cikinsa kai tsaye, muna cikin tafiya naji an kwala mun kira ta waje "yalla6ai," cikin sauri na zuge glass ɗin motar don naga wanene, shine naga wani saurayi zuƙunne a ƙasa, ga ki kuma kwance a sume duk jini a goshin ki, hankali atashe na zabura zan fito daga cikin motar, kawai sai saurayin nan yace "yalla6ai ya gudu da ɗayar acikin motarsa, gashi can ya miƙi hanyar da tayi dama don Allah ku ceto rayuwarta, " jin haka yasa gaba ɗaya na rikice, cikin sauri major yaja motar mu da gudun gaske muka bi motar wannan tsohon mutumin da gudun gaske har cikin gidan gonarsa, ina shiga najiyo kukan hossana hankalina ba ƙaramin tashi yayi ba, tuni na makance na afka ma ƙopar ɗakin gidan gonar na tarwatsa ta, ina shiga naga hossana a lokacin har yayi nasarar yage mata rigarta ya ruƙe ta a hannunsa, raina yayi mugun 6aci abunda ya hanani yin motsi a lokacin saboda bansan wane irin hukunci zan yanke masa ba,yanzu haka da nake baki labarin nan babu wannan tsohon a duniyar nan saboda na kashe shi,kuma na ɗauko hoton gawarsa don na nuna ma hossana," Wani irin murmushi jahad ta saki har ta gaza rufe bakinta don murna,shima Omar ɗin murmushi yakeyi yana kallonta, Nasan dayawa za suyi mamakin yarda akai hakan ta kasance,abun da ya faru shine cikin sojojin dake gadin gidan general ishaq akwai wani matashi Abokin major ne, a lokacin da suka kawo su hussana da jahad gidan Omar ya shiga tare da su ciki , A nan major suka haɗe da wannan saurayin abokinsa ne tun suna yara ,sunan Shi Osman bayan sun gaisa Osman ke cewa "Abokina waɗancan yaran fa? dana ga ka shiga ciki dasu ƴa'yan wanene? ko dai ogan naku ne yayi aure matar ta haihuwa, Dariya Major yayi tare da cewa "Wai dama Osman har yanzu kana nan da shegen sa idon nan naka? Haba no wonder shiyasa Allah yabarka a matsayin mai gadi, in banda abun ka ina ogan mu yakai shekarun da zai iya ajiye ƴa'ƴa kamar waɗancan? shima fa ba wani babba bane duka shekarunsa bazasu wuce 28 years, matsayi ne kawai Allah ya bashi," jin haka yasa osman ɗan zaro ido tare da cewa "ka ce ashe shima ɗan shila ne, amma dan Allah tun yaushe nake ta fama dakai ka taimaka ka sama mun aiki a ƙarƙashinsa amma ka ƙiya, kafi son kaita ganina a matsayin mai gadin gidan genar, kalli fa yarda na rame nayi baƙi, kai kuwa har wani tumbi kafara ajiyewa saboda jin daɗin rayuwa, wlh abota bata ce haka ba," ya faɗi yana tsuke fuska, dafa kafaɗarsa Major yayi tare da cewa "Ina sane da wannan Osman, kuma insha Allah zanyi ƙoƙari na sama maka gurbi a kusa dashi, mutumin kirki ne sosai yana da sauƙin kai kuma ina jin daɗin aikin dashi,yana kyautatamun domin kuwa kafin ƙarshen wata yayi ina samun ninkin ba ninkin abunda nake samu a albashina wurinsa," jinjina kai Osaman yayi zugudun yayi masa fuskar tausayi kafin yace "Kaji daɗi mutumina,ni dai zan jira naji daga wurinka don Allah karka manta kasa ma mun kusanci dashi, nima na dangwali arxiki," Major yace"baka da damuwa, yanzu ma haka ga wani aiki ka samu, waɗancan yaran da kake gani ogan mu yana sonsu sosai, bashi da alaƙar komai dasu hasalima a asibiti ya taimake su,ya kawo su nan ne domin su zauna tare da matar yayansa ishaq, to ni hakan bai kwanta mun araina ba, shi ne nakeso ka sanya mun ido akansu! ka zama tamkar ɗan leƙen asiri duk da nasan hakan ya sa6ama dokar aikin ku amma inaso kayimun wannan Osman,ka lura da duk wani motsinsu acikin gidan nan, so nake kayi aiki tamkar jami'in sirri! dalilin dayasa nayi hakan saboda bana son duk wani abu da zai cutar dasu don na lura da yadda ogan mu ke tsananin ƙaunar yaran,ni kuma bana son duk wani abu da zai 6ata masa rai, ta6a yaran nan tamkar ta6a masa zuciya ne," ya ƙarasa maganar yana kallon osaman da yayi kasaƙai, daga bisani yace "Na amince zanyi hakan, amma wlh ka sani duk ranar da asirina ya tonu, sunanka na ciki ! don ba zan shiga haɗari ni kaɗai ba," dariya major yayi sannan yace"Ai ni babu wanda ya isa ya ta6ani muddin ina tare da Marshal, don haka kaima ka kwantar da hankalinka, ba abunda zai same ka face alkhairi,tunda ka amince zaka yi ɗin, inaso duk wani hali da suke ciki ka tabbatar da ka kira wayata ka sanar mun," Osman ya amsa masa da "toh," daga nan su kayi sallama, a lokacin marshal Omar ya fito daga cikin gidan jikinsa asanyaye suka shiga cikin mota su ka tafi, tun daga wannan lokacin Osman ya zaman ɗan leƙen asiri duk wani hali da su hossana ke ciki yana sane dashi kaf, kuma duk rana yana kiran major ya sanar dashi halin da suke ciki, Major bai ta6a sanar da marshal Omar ba, saboda gudun karya shiga tsakanin shi da matar yayansa ishaq,kullum yana sanar da osman cewa yaci gaba da sa musu ido, Idan har masu karatu zasu iya tunawa akwai lokacin da Aunty babba tayima su hussana da jahad bugun mutuwar nan, har suka kaisu asibiti bayan sun dawo suka shige cikin gida ita da hafsat suka bar jahad tsaye gaban motar tana kuka saboda hossana na'a cikin motar kwance rai hannun Allah gashi bata iya ɗaukarta bare tashiga da ita cikin gidan, a lokacin idan zaku tuna akwai wani soja daya zo yana tambayarta meke faruwane, take ce masa ƴar uwartace acikin motar kwance bata lafiya kuma bazata iya ɗaukarta ba, sai sojan yace maza "Can i help," take ce masa eh, yasa hannu ya ɗauki hossana ya shigar mata da ita ciki, ya kwantar da ita saman doguwar kujera, yayin da jahad tabisu, to wannan sojan ba kowa bane face Osman abokin major ɗan leƙen asirinsa, ko lokacin da zai fita daga falon bayan ya kwantar da hossana sai da ya ɗan tsaya daga bakin ƙopar ya juyo yana kallon jahad dake zukunne saman guiwarta agaban hossana tana yi mata addu'a tana kuka, jinjina kansa yayi tare da fuce wa bayan yafita, ya ɗauko wayarsa tare da buga ma major kira, bayan ya ɗaga kiran yake sanar dashi abunda ke faruwa, nace wa shifa yana zargin cewa Matar ishaq tayima yaran mugun bugu har ma ɗaya daga cikinsu ta jigita sosai tamkar ba zata rayuwa,don haka ya hanzarta sanar da ogansu Omar yazo ya kwashi yaran tunkan ta kashe su, har lokacin major bai sanar da Omar ba game da wannan ma, saboda yana tunanin koya faɗi masa daker ya yarda kuma yasan makircin mata, abun zai iya dawowa kansa, tun fa lokacin da su jahad da hossana ke wanki abayan gidan ita da jahad, Osman yake ganinsu sai yazo ya gifta ta wurinsu tamkar yana yin waya alhalin su yake kallo, har video yake yi masu yana turawa major donya gani," Major ya tsorata da ganin irin uƙubar da yaran suke sha, Bayan wannan lokacin kuma sai salon ya canza, duk osman na zuba ido yana kallon ikon Allah yarda hafsat ke nuna ma yaran soyayya, aduk lokacin da hafsat ta fita dasu cikin motarta, sai osman ya bisu da machine ɗinsa dom yaga ina zata dasu, dashi suke yin yawo abayansu batare da sun sani ba, duk inda zasu osman na biye dasu a sirrince, daya kira Major ya sanar dashi abunda ke faru na cewa yaran fa yanzu suna samun kulawa sosai a wurin mutanen gidan, sai major yace mashi "Wannan salon da suka canza,alama ce dake nuni da cewa sun kusa salwantar da yaran,ina da tabbacin cewa so suke su zubar dasu kaci gaba dasa musu ido,daga yanzu banaso ko bacci ka dunga yi osman, saboda wannan lokacin ne mafi haɗari, aduk lokacin da maƙiyin ka ya canza maka salo na soyayya to kaji tsoransa halakar dakai zaiyi," Tun daga lokacin da Major ya sanar dashi haka, bawan Allah osman bai ƙara yin bacci ba, koda bashi ke akan duty ba, yana nan yana lura da shige da ficen da hafsat keyi dasu hossana, A ranar da baba alamu zai tafi dasu hossana, akan idon osman Aunty babba ta fito tare dasu jahad da hossana,ta buɗe masu motar hafsat suka shiga, duk yana kallonsu, daga bisani kuma sai yaga hafsat tafito hannunta ɗauke da trolley hakan na nufin wani ne zaiyi balaguro, bayan hafsat ta shiga cikin motar taja motar tafito dasu daga cikin gidan, cikin sauri osman ya hau mashine ɗinsa da yake ajiyesa acikin gidan yabi bayansu a hankali yake tuƙa mashin ɗin don kar su ganshi, da hafsat ta tsayar da motar abakin titi tana jiran ƙarasowar baba alamu, sai osman ya dakata da tukin mashin ɗinsa, cikin sauri ya sauka tare da samun wuri ya cire rigar jikinsa ta kakin sojoji ya 6oyeta a ƙarƙashin wani benci dake agaban wani shago dake rufe, sannan ya tu6e wandon jikinsa ma, ya ajiyesa a ƙarkashin bencin bakomai yasa shi yin hakan ba face don karsu ganshi da kakin sojoji yana binsu, Asirin shi zaiyi saurin tonuwa ne, Sai daya rage daga shi sai farar shirt da gajeran wando ajikinsa a lokacin motar baba alamu taƙaraso,cikin sauri Osman ya zuƙunna agaban mashin ɗin tamkar ya samu matsala yana gyaransa, alhalin nan duk salon dabaru ne na jami'ae, yana gyaran mashin ɗin yana satar kallonsu, akan idonshi hafsat ta buɗe ma jahad da hossana mota suka fito sannan ta ɗauko masu trolley ɗinsu da food basket ɗinsu ta basu,bayan hafsat ta tafi, baba alamu ya amshi akwatin Su hossana da jahad ya wurga cikin boot ɗin motarsa, daga nan jahad da hossana suka shiga cikin motar, shima ya shiga tare da tashin motar suka tafi, cikin sauri Osman ya haye mashin ɗinsa tare da tashinsa yabi bayan motar baba alamu da gudun gaske amma bai bari ya ƙurewa motarsa ba kasancewar Motar baba alamu glass ɗin jikinta duk ya fashe, muddin osaman ya ƙurewa motar tofa zasu iya hango shi, hakan yasa ya basu tazara sosai, yana cikin tuƙin mashin ɗin ya ɗan jinkirta tare da zura hannu cikin aljihun wandonsa ya zaro wayarsa tare da bugama major kira, bayan ya ɗaga yake sanar dashi duk abunda ke faruwa, Hankali tashe major yace "Osman kada ka bari ya kubce maka, kaci gaba da bin motarsa, sannan kabar wayarka a kunne zamu biyo diddigin layinka, mu zo inda kuke," bayan osman ya amsa masa, ya mayar da wayar, sannan ya ƙara ma mashin ɗinsa gudu, a lokacin da motar baba alamu tashiga dajin da gudun gaske, jahad na ƙoƙarin fitowa tana ihu bayan ta samu ta harba murfin motar ya buɗe, sai baba alamu ya girgiza motar da mugunta, ta faɗo ƙasa timmmm goshinta ya bugu, ta taso da gudu tana bin motar tana kiran sunan hossana daga bisani ta yanke jiki ta faɗi, adai-dai lokacin shi kuma osman ya ƙaraso ba komai yasa shi yin jinkiri ba fa ce wayar da yayi da major shiyasa bai ƙaraso akan lokaci ba har baba alamu ya kubce mashi, ganin jahad da yayi yashe a ƙasa ta sume ga jini, ba ƙaramin razana yayi ba, cikin hanzari yayi wurgi da mashin ɗinsa ya nufe ta hankali atashe, ya zuƙunna gabanta yana faɗin "ke!ke!! tashi ki tashi dan Allah, kada ki mutu," Adai-dai lokacin kuma motarsu Marshal Omar ta faso cikin dajin ta hanyar tracking layin osman da sukayi yasa har suka ci nasarar cimma inda yake, Osman na ganin motarsu Marshal yasan cewa sune aciki, a lokacin omar ya zuge glass ɗin motar a tsorace ganin jahad kwance duk jini a goshinta, harya harzuƙa zai fito daga cikin motar, cikin sauri Osman yace "yalla6ai ya gudu da ɗayar, gashi can ya miƙi hanyar dama da ita, don Allah ku ceci rayuwarta," jin haka yasa Omar fasa fitowa daga cikin motar, cikin sauri major yaja motar da gudun gaske suka bi motar baba alamu a lokacin ya ɗanyi masu nisa, hayaƙin da bayan motar baba alamu ke fitarwa shine yasa suka gane hanyar da yabi, suna isa basu tsaya buɗe kopar katakon gidan gonar ba, kai tsaye major yabi ta ƙopar atsiyace ya tarwatsa katakon gidan gonar suka shige, Tamkar zaki haka omar ya fito daga cikin motar ya afkawa ɗakin da baba alamu ya shige da hossana, *Wannan shine abunda ya faru taƙaice kenan* "Ya omar ina hossana take ita'? Omar yace"hossana tana cikin ƙoshin lafiya, itama ƙarin jini akeyi mata, yanzu haka bacci take sha tana a kusa da ɗakin nan," ajiyar zuciya jahad ta saki kafin ta kuma cewa "ya omar kullum hossana saita ambaci sunanka, komai akayi sai tace "ya Omar fa," ita bata son rabuwa da yaya omar ɗinta," Murmushi Omar ya saki jin abunda jahad tace, "Amma ya Omar ba zaka ƙara rabuwa damu ba ko? dan Allah kada ka haɗamu da kowa kabarmu kawai a wurin ka, kai kaɗai ke son mu," tayi maganar idonta akansa tana jiran amsar shi, Omar yace "ko wancan time ɗin bada son raina nabar ku ba, jahad you're always in my mind ina jin ku araina,amma yanzu komai ya wuce just forget about the past, ku ƙaddara cewa wani abu bai ta6a faruwa da rayuwarku ba na ƙunci, saboda yaya omar ɗinku ya shirya maku kyakkyawar rayuwa ta jin daɗi da walwala, masarauta ce wadda ku kaɗai zaku mulketa sai yadda kuka ga dama zakuyi acikinta, hatta yaya omar ɗinku zai zama tamkar bawa agare ku," dariya kawai jahad ke faman tiƙa saboda murnar jin abunda omar ke cewa, hatta dr Emran da Camila dake tsaye murmushi kawai suke saki, shima major dake tsaye daga ƙopar ɗakin murmushi ne a fuskarsa, ƙarasa shigowa ciki yayi yana cewa "Sir idan ba damuwa inaso a bani muƙami acikin masarautar nan, zanso na zama sojan dake kula da princesss ɗin dake acikinta, bama ni kaɗai ba ga abokina osman nan shima yana roƙon gimbiya jahad da ta bashi damar zama ɗaya daga cikin masu kula dasu," Abun sai ya zama tamkar shirin wasan kwaikwayo gaba ɗayansu dariya ce a fuskarsu, hakan ba ƙaramin farantawa omar rai yayi ba ganin yadda jahad ke faman tiƙar dariya, sai yaji sanyi aransa sam ya gaza janye idonsa akanta, Muryar Camila (kameela) ce ta katse su da cewa "Yalla6ai nima idan ba damuwa ina neman alfarmar zama ɗaya daga cikin masu yi ma gimbiya jahad hidima, ko da a matsayin jakadiya ne mafi kusanci dasu," Fashewa da dariya jahad ta ƙara yi daga kwancen da take har omar na cewa "Bi a sannu my baby, kada ki shaƙe," gaba ɗayansu sun natsu sai raha akeyi, suka ji Muryar hosana kamar daga sama tace"YA OMAR," Atare suka juya suna kallonta, tsaye take a bakin ƙopar ɗakin daker take buɗe idanunta tana kallonsu, hannu tasa ta murza idonta sannan ta ƙara buɗe su da kyau donta tabbatar da abunda idonta ke gane mata, tabbas kuwa shine wato yaya Omar ɗinta, tsananin farin ciki ne yasa hossana ƙarasa shigewa ciki da gudun gaske tana isa inda Omar yake ta zube saman guiwowinta tare da kifa kanta asaman laps ɗinsa tana kuka, Shiru su kayi gaba ɗayansu na wani lokaci suna sauraren kukan da hossana ke yi, gaba ɗaya jikin omar ya gama mutuwa saboda yasan yarda yarinyar ke tsananin ƙaunarsa dole tayi kewarsa, hannu omar yasa tare da shafa gashin kan hossana cikin muryar lallashi yace "Am so sorry hossana,nasan nayi laifi ban ma san da wane baki zan iya baki haƙuri ba," Maimakon ta ɗago sai ta daddage ta gartsa mashi ciwo a laps ɗinsa, runtse ido omar yayi saboda yaji zafin cizon, babu wanda ya lura da abunda ke faruwa sai jahad, tun da taga omar ya runtse ido tasan cewa Hossana Cizon shi tayi, tayi mashi hakan ne don yasan irin raɗaɗin da suka ji acikin zuciyoyinsu na ƙin zuwan da yayi ya tafi dasu, buɗe idonsa yayi a hankali yana sauke ajiyar zuciya ya kalle ta, a lokacin itama ta ɗago tana faman huci ta ɗaure masa fuska tare da haɗe masa girar ƙasa da sama tana kallon shi, Cikin sanyin murya ya sake maimaita "Am sorry again," ya furta tare da kai hannunsa a fuskarta yana share mata hawayenta dake kwaranyowa daga idonta, Cikin kuka tace "Ya omar yanzu ka kyauta abunda kayi mana? ka tafi kabarmu cikin tashin hankali ko waiwayon mu, ba kayi ba yanzu da mun mutu shikenan bazan sake ganin Ka ba sai dai a lahira ko? ƴar dariya omar yayi tare da cewa "Amma ae yanzun baku mutu ba ko? Kuna raye kuma ga yaya Omar ɗinku atare daku, mai yayi saura yanzu"? ya tambaya yana kallonta Hossana tace "sai ka kaimu gidan ku inda kake rayuwa, don wlh duk inda zaka je, ƙafarka ƙafarmu, mu da kai mutu ka raba takalmin kaza," ta ƙare maganar tana zumbura baki, Gaba ɗayansu na cikin ɗakin dariya kawai suke yi, Kallon dr emran omar yayi kafin yace "yanzu mai ya rage dr?yaushe kake tunanin za'a sallame su, in yaso sai acigaba da basu kulawa acan gida? dr emran yace "zuwa night, ae jikinsu yayi ƙarfi yanzu saboda ƙarin jinin da akayi masu, idan ma ba damuwa Camila zata iya cigaba da kula da lafiyarsu, in har kana buƙatar hakan, tunda dama naji tace tana son zama hadimar princess ɗin naka," Murmushi suka saki gaba ɗayansu banda hossana don batasan zancen ba, tuni ta mayar da kanta akan laps dinsa tana faman sauke ajiyar zuciya, dukkan tsanani yana tare da sauƙi, mahaƙurci kuma mawadaci ne wata rana, babu wani yanayi na rayuwa da yake kasance wa na dundundun, Innallaha ma'assabirin tabbas wannan haka yake, iya haƙuri dae su hossana sunyi kuma sun jurema duk wata jarabawa da suka fuskanta na ƙuncin rayuwa, basu fasa yin addu'a ba suna kai kukan su ga Allah ba kuma basu fidda rai da cewa Allah zai kawo masu ɗauki ba, idan muka sa haƙuri kowa zai cimma nasara, gashi yanzu zamu iya cewa Masha Allah 😍👑 **************Twins ******************* daker suka samu suka yi wanka suka canza kaya izuwa jeans da t-shirt suka fito wuraren ƙarfe 5 na yamma, tafiya suke yi gabansu na faduwa tsoransu kar suci karo da haroon don yanzu ya zamar masu tamkar dodo, suna cikin tafiya sai ga Junaid ya fito daga upstairs yana ganinsu ya ɗan zaro ido cike da murna yace "Yaya Jahan ina kuka shiga inata neman ku, naga da safe ko breakfast ba kuyi ba, duk na shiga damuwa," ya yi maganar tare da ƙarasa saukowa down ɗin yayi ya tunkaresu, suna tsaye baki asake suna kallon shi saboda neman shi suke yi ruwa a jallo, yana ƙarasawa yabi su ɗaya bayan ɗaya yayi hugging ɗinsu tare da manna musu kiss a gefen fuskarsu, irin gaisuwar da suka saba, Ganin sun zuba mashi ido batare da sunyi mashi magana ba yasa shi bubbuga ƙafarsa tare da cewa "Dan Allah wai menene haka duk kun Canzamin, ko magana ma ba zaku iya yi mun ba why pls? ya faɗi tamkar zaiyi kuka, gyaran murya jahan yayi tare da cewa "no ba haka bane junaid, ba mu jin daɗi ne, ni da Ayaan shiyasa ka ganmu a haka, yanzu haka ma kai muka fito nema akwai maganar da muke son yi dakai, amma ba'a nan ba, acikin ɗakin ka," junaid yace "magana kuma dani? Allah yasa ba laifi nayi ba" Murmushi Ayaan ya saki tare da cewa "ba laifi kayi mana ba junaid taimako ne ma zakayi mana," ruƙe ƙugunsa yayi sannan yace "Naji toh, amma kafin nan sai naga kun ci abinci tukunna, saboda baku ci komai ba tun safe ina sane da hakan, bayan na hana ku zama da yunwa," Yadda yayi maganar tamkar wani yayansu, alhalin sun girme shi, Murmushi suka saki atare sannan jahan a ruƙo hannunsa tare da cewa "Zamu ci abincin ne,amma kafin nan, mu shiga daga ciki muyi magana, tasa ƙeyarshi su kayi har cikin ɗakinsu, suka tsaya daga tsaye suna fuskantar shi, gaba ɗaya sun rasa ta inda zasu soma neman alfarmar nan a wurin junaid, Ganin sun tsayar dashi sun zuba mashi ido yasa shi hasala tare da cewa "Yaya Jahan nifa bansan menene ma'anar zuba mun idon nan da kuka yi kuna kallona ba," ya faɗi yana hura hanci, Ayaan ne ya soma magana "am...junaid ka gane, dama wata alfarma ce muke nema awurin ka, "Am listening to u," junaid ya faɗi yana kallonsu Jahan ya daura da cewa "junaid sabo da mu zakayi wannan abun, so muke ka kira Mommy a waya video call ka bata haƙuri sanna ka ambaci sunanta ka kirata da Mommy, dan Allah junaid.........' tunkan jahan ya ƙarasa maganar tasa junaid yabi ta gefensu zai fuce daga ɗakin yana cewa "da nasan wannan alfarmar zaku nema awurina, wlh da ban 6ata lokacina wurin sauraronta ba, Cikin sauri suka ruƙo rigar jikinsa har suna haɗa baki wurin cewa "Janaid dan Allah ka taimaka ma rayuwarmu, kai kaɗai ne a yanzu zaka iya fitar damu daga halin da muke ciki pls junaid do this favour for us" a fusace junaid ya fusge rigar shi daga hannunsu yace "Wlh bazanyi ba, ni bazan ta6a kiran wannan matar da sunan mommyna ba, saboda bata sona ta tsane ni, Yana faɗin hakan ya kama hanyar fita, Ayaan yayi sauri sake cafko rigarsa, aikuwa a fusace junaid ya sanya hannunsa tare da buge na Ayaan, rai a6ace jahan ya janyo shi tare da kwashe shi da mari, zaro ido junaid yayi yana kallonsu yayin da ya sanya hannunsa ya dafe kuncinsa saboda zafin marin da jahan yayi masa, tunda yake arayuwarsa zai iya cewa ba'a ta6a bugunsa ba, ko da wasa wani bai ta6a yin gigin ta6a fatar jikin junaid ba da sunan bugun, amma sai gashi yau an samu wasu daga cikin yayyansa da yake matuƙar ƙauna yasa hannu ya mare sa, tuni idonsa sun ciko da kwalla red lips ɗinsa har rawa suke yi wurin cewa "Yaya jahan ! Yau kai da kanka, kasa hannu ka mare ni? Saboda na bijire ma buƙatarku? akan abunda yake haƙkina nifa aka cuta, abun har yanzu yana yi mun ciwo azuciyata bana faɗi ne kawai..............' kuka ne yaci ƙarfinsa har ya gaza ƙarasa maganar tasa yaci gaba da sharar kwalla, tuni jikinsu yayi mugun sanyi musamman jahan daya mare sa, baisan lokacin da shima ya fashe da matsanancin kuka ba, hakan yasa junaid dakatawa da kukansa ganin yarda Yayansa jahan ke kuka agabansa tamkar ƙaramin yaro, nan take hankalinsa ya tashi cikin sauri yasanya hannayensa a fuskar jahan yana share masa hawayensa yana cewa "dan Allah yaya jahan ka daina kuka, bana son ganin hawayen nan naka, in dai ni ne na sanya ka, yin kuka wlh zan baka hakuri ka yafe mun bazan ƙara, Cikin shessheƙar kuka jahan yace "junaid naji na tsani kaina fiye da tunaninka, wai yau ni ne na kasance mutun na farko daya fara ta6a lafiyar jikin ka, da wannan mummunan hannun nawa, ina danasanin wannan ranar kuma bazan ta6a yafe ma kaina ba..........' gaba ɗaya tausayin jahan ya gama kama junaid cikin sauri ya janyo shi ajikinsa tare da rungume shi sosai yana ɗan bubbuga bayansa, cikin muryar rarrashi yake cewa "Ba laifinka bane yaya jahan, Laifina ne nayi rashin kunya, na buge hannun ayaan duk da raina ne a6ace bansan nayi hakan ba, amma ku yafe mun abisa kuskuren da nayi maku bazan ƙara ba,' gaba ɗayansu sun shiga cikin wani kalar yanayi, Ayaan kam tuni jikinsa ya gama mutuwa saboda tausayin junaid da kuma kansu daya kama shi, Bayan sun tsagaita jahan ya janye jikinsa daga na junaid sannan yace "Junaid dan Allah kayi mana wannan alfarmar na roƙe ka kai kaɗae ne zaka iya fidda mu cikin halin da muke ciki, kuma nason kana tsananin son mu ba zaka so wani abu ya cutar damu ba,' ya ƙarasar maganar yana kallonsa da idanunsa da suka gama runewa, Jiki a mace Jahan ya kalli Ayaan cikin tsananin damuwa, ganin junaid yayi shiru baice komai ba yasa su yin saurin zubewa agabansa saman guiwowinsu suna roƙonsa, Cikin tsananin tashin hankali shima junaid ɗin ya zube saman guiwowinsa agabansu tare da fashewa da wani sabon kukan yana cewa "meyasa zakuyi mun haka?yaya Ayaan da ya jahan saboda me zaku duƙamin nifa ƙaninku ne, ku kuma yayyena ne dan Allah kudaina mun hakan banaso! banaso!!bana so!!" ya ƙarasa maganar tare da cewa "naji na amince zan kirata, Amma ba yanzu ba," ajiyar zuciya suka sauke gaba ɗayansu nan take suka ji wani irin sanyin ya ratsa zuciyoyinsu, Ayaan yace "yaushe zaka kirata"? Junaid yace "an jima kaɗan," ya faɗi a shagwa6e Murmushi suka saki gaba ɗayansu har haɗa hannu suke yi wurin goge masa hawayansa da suka wanke masa fuska, har lokacin suna a zuƙunne su duka ukun suna fuskantar juna, Jahan yace "Am Sorry junaid, ka yafe mun marin da nayi maka, nayi dana sani sosai," ya faɗi cikin sanyin murya, Junaid yace "gsky bazan yafe ba yaya Jahan har sai kunci abinci sannan nagani da idona tukunnan, Ayaan yace "shikenan junaid komai kake so zamu yi," Murmushi ya saki sannan ya ruƙo hannayen su suka miƙe tsaye atare, bayan sunyi wiping tears ɗinsu, Sannan suka fito daga ɗakin nasu, Ajere suka jera suna tafiya sun sanya shi tsakiyarsu a lokacin Sehrish da azmee suna a cikin kitchen suna aikace-aikacen girkin dinner ɗin gidan, Sai da junaid ya tabbatar Ayaan da jahan sun zauna saman dining chairs ɗin sannan yace "ku jira ni, yanzun nan zan kawo maku abinci ku ci," ya faɗi da murmushi a fuskarsa sannan ya wuce kitchen ɗin, har lokacin jahan dana sani yake yi akan marin da yayiwa junaid,ya gaza yarda cewa shi da kansa ya ɗaga tafin hannunsa ya zabga ma romeo ɗinsu mari, yana ganin abun tamkar a mafarki,😥Kitchen ya wuce yana ganin sehrish ya soma sakin murmushi, sallama yayi masu sannan ya shiga, amsa mashi su kayi gaba ɗayansu, sannan ya matsa wurin sehrish dake agaban chopping board tana yayyanka kayan lambu,   "Reesh idan akwai abun da kuka kammala inaso ki shiryamun a tray zan kai ma yaya Ayaan da Yaya jahan ne, yunwa suke ji ssae," ya faɗi yana yamutsa fuska tamkar shike jin yunwar, zuba mashi ido sehrish tayi tare da cewa "junaid ! meya faru dakaine? waya mare ka har haka"?    Cikin sauri junaid yasa tafin hannunsa ya rufe gefen fuskarsa yane cewa"ki daina ɗaga murya sehrish kada wani yaji, banaso wani yaji kiyi shiru kawai da bakin ki,"  Jikinta ne yayi wani irin sanyi aranta tana mamakin yarda akai har wani ya aza tafin hannunsa a fuskar junaid ga sahun yatsu nan sun bayyana raɗau a fatar fuskarsa yayi jawur wurin, Jinjina kanta kawai tayi tare da cewa "Shikenan bari na shirya maka abincin ka kai masu," ta faɗi tana kallonsa cikin jin tausayinsa, Ajiyar wuƙar hannunta tayi sannan ta wuce ciki donta haɗa masa, hannu yasa ya ɗauki knife ɗin da ta ajiye yaci gaba da yanka mata lettus ɗin data bari,  Azmee ce ta taya ta zuba masu acikin warmers duk tana jin magananun da suka yi ita da junaid, aranta tana mamakin marin da taji sehrish ta ambata anyiwa junaid, har satar kallonsa tayi taga yarda fuskarsa tayi jawur gefen da aka maresa ga alama nan tabbas in wani yaji acikin gidan sai an tada husuma,    Ruƙo tray ɗin tayi a hannunta zata wuce takai masu cikin sauri junaid ya ajiye wuƙar ya tare ta da cewa "kawo na kai masu,"miƙa mashi tayi yasa hannu ya kar6a yana kallon fuskarta da murmushi yace "thank u," itama murmushin ta sakar mashi duk tashiga damuwa akan yanayin fuskarshi,  Yana karba ya fuce yakai masu, yadda yabarsu haka ya same su, sunyi zugudun suna kallon junansu, Jahan na ganinsa ya saki fara'a tare da cewa "Yawwa heart beat mun gode sosai da irin kulawar daka ba mu, duk ka damu akan mu," murmushi junaid ya saki a lokacin ya ajiye masu tray ɗin kayan abincin asaman table ɗin,    Jikin Ayaan har kerma ya keyi wurin ɗaukar jug ya zuba lemu mai sanyi acikin cup yana kwankwaɗa, abun ya ɗaure ma junaid kai ashe dai da gaske yunwar suke ji,    Shima jahan jiki na rawa ya shiga zubama kansa abincin, cikin sauri junaid ya wuce wurin freezer ɗinsu ya buɗe tare da ɗuko masu cool drinks ya kawo masu agabansu,   Hannu jahan yasa ya ɗauki bottle water yana kwankwaɗa har yana kusa shaƙewa, agalabaice ya ajiye robar ruwan sannan ya kalli Junaid dake tsaye akansu yace "Allah yayi maka albarka junaid, kaje ka ci gaba da wasan ka,"    Juya junaid yayi ya koma kitchen wurinsu sehrish, tana ganinsa tace "Za'a a ƙara masu abincin ne"? Girgiza kai junaid yayi tare da cewa "zuwa nayi na taya ku aikin, bana jin daɗin zama ni kaɗai ne,"  Azmee tace"so kake kaja mana ko? taya za'a ganka acikin kitchen kana tayamu aiki, kaima kasan ba zaiyiyu ba,"   turo bakinsa yayi tare da cewa "Aunty azmee nifa ba wani abu zanyi mai yawa ba, kawai zan taya sehrish yanka kayan lambun ne,"    "Ban amince ba junaid, wai ni yau ba ka zuwa wurin buga ball ɗinka ne? ina laptop ɗinka ne? kaje ka kunna kallo kayi mana ko ka buga game,"    Ruƙe qugu yayi tare da cewa "Aunty azmee korata kawai kike son yi ne, to Allah ba inda zani ƙafata ƙafar sehrish, tazo mu tafi tare," ya faɗi da shagwa6a   Dariya su kayi gaba ɗayansu, sai lokacin sehrish tace "junaid ɗina shigo ciki ka samu wuri ka zauna, zan haɗa maka Cornflakes, kana sha kana kallon yarda muke girki,"    Murmushi ya saki sannan ya shige ciki tare da samun wuri saman dinning chairs na kitchen din ya zauna yana jiranta,   Jinjina kai azmee tayi tare da cewa "Shaƙuwarku fa da junaid ƙara gaba take yi, don na lura kema bakyaso yayi nisa dake,"   Sehrish tace "Aunty azmee yana ɗebe mun kewa sosai, ina jin shi tamkar ƙanina ne shiya sanya.... .  ' Muryar junaid ce ta katse ta da cewa "Wanene ƙanin naki"?   Cikin sauri sehrish tace "bafa maganarka muke yi ba" tayi maganar yayin da tasa hannu a cup board ta zaro kofin tare da wuce wa wurin dispenser saboda ta ɗebi ruwan zafin da zata haɗa masa dashi, "Koma meye dae zanji ne," ya faɗi yana ɗan hararar ta daga inda yake, Bayan ta haɗa masa takai masa nan ya zauna yana sha suna fira tare dashi, ________________________________ After magrib prayer motocinsu suka dunga shigowa cikin gidan da gudun gaske atare suka yi parking ɗinsu, Abbansu ne tare da SGR suka fito, motar dake bayansu kuma Su irfan ne tare da jabeer da khaleed, kana ganin su kasan sunji jiki, amma su da sauƙi babu alamar rauni ajikinsu sun dai jigata ne,   buɗe motar dake bayan tasu suka yi wadda fawan ne kwance acikinta, gaba ɗaya jikinsa sahun bulali ne ta ko'ina, saboda hasken fatarshi duk zanen bugun da miyagun su kayi mashi ya fito raɗau jawur wani wurin ma harya fashe, amma da yake ya samu emmergency treatment duk ansanya mashi magani awurin, babu riga ajikinsa gajeran wando ne kawai guntu suka barshi dashi, asaman ƙirjinsa hada ɗinki akayi masa, ba ƙaramin jiki ya ji ba yaji gata sosai, Amstrong ne babban na hannun daman SGR ya fiddo shi tare da Irfan suka tallabo shi sannan suka wuce dashi cikin gidan, har lokacin bai dawo cikin hayyacinsa ba saboda hodar da suka shaƙa mashi,    Suma sauran mutanen da suka halarta domin yi masu jaje duk suka harhaɗu nan suna tayi ma Abbansu Allah kyauta, daga bisani suka haɗu gaba ɗayansu izuwa cikin gidan,    Tun da Sehrish taji dirar motaci tarasa samun kwanciyar hankali burinta taga su wanene suka zo, a lokacin sun kammala aikace-aikacensu na kitchen fitowarta kenan daga wanka, ta buɗe closet dinta ta zura doguwar riga sannan ta matsa jikin window tana leƙensu bata samu damar ganinsu da kyau ba saboda mutanen dake zagaye ta ko'ina, Jiki asanyayae ta rufe window in gabanta na faduwa tsoranta kar ace wani ne ya rasu, hannu ta aza akanta tana ambaton "innalallahi wa'inna ilaihirraji'un ya Allah kasa ba wani bane ya mutu,"  Cikin sauri ta bar wurin tare da  buɗe kopar ɗakin nata ta fito waje a lokacin itama Azmee tafito daga ɗakinta a ruɗe jikinta na sanye da zumbuleliyar hijabi alamar salla ta kammala yi, ko addu'a bata tsaya yi ba ta fito saboda jin jiniyar shigowar motocinsu,    tsayawa su kayi gaba ɗayansu suna son ganin abunda ke faruwa, gaba daya sun rikice ganin yarda Amstrong da irfan suka shigo da Fawan duk ciwuka ajikinsa saman 3 seater suka zaunar dashi saboda masu zuwa dubiya, Fitowa Ayaan da jahan sukayi daga ɗakinsu suma jin hayaniyar dake cikin gidan ganin fawan a wannan yanayin yasa su ƙarasawa da gudun gaske suka zube saman guiwowinsu agaban shi cikin tsananin tashin hankali suke cewa "fawan meya faru dakai haka? Waye yayi maka haka? Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un,   Daker fawan ke iya kallonsu duk da baya iya tantance su wanene agabansa amma yaji muryarsu, juyawa su kayi suna kallon Irfam da jabeer don son jin ƙarin bayani,    Jabeer yace "Fawan bazai iya yi maku magana ba a halin yanzu baima san ko ku su wanene ba, addu'a kawai zakuyi masa,' jin haka yasa hawaye soma zuba daga idanunsu,   Shigowar da mutane suka soma yi ne yasa su samun wuri ƙasa suka zauna kowa ya zabga tagumi, kana kallon fuskar Abbansu kasan cewa acike take da tashin hankali saboda arayuwarsa ya tsani abunda zai ta6a masa jininsa,  Ganin SGR ya shigo yasa sehrish jin faɗuwar gaba, gaba ɗaya babu annuri a fuskarshi, white shirt ɗin dake ajikinsa duk shedar jini ne daya fallatsar masa hada hannunsa, ba jinin kowa bane face jinin waɗanda suka farmaki su fawan, mugun bugu sukayi masu na fitar shari'a gaba ɗayansu suna a headquater dinsu an killace su can domin horar dasu da kuma yin bincike akansu, Tuni jikin sehrish ya soma yin kerma saboda tashin hankalin da tagani ajikin SGR tunaninta ya gama bata cewa ko harbinsa akayine da bindiga shiyasa taga jini, hannu tasa ta rufe fuskarta tana kuka da gudun gaske ta juya ta koma ɗakinta saman gadonta ta faɗa tana cigaba da kukan,"   Abun ya ɗaure ma azmee kai ganin yarda sehrish ta gudu tana kuka kuma tasan ba don komai bane fa ce sai don ganin jini a jikin rigar sgr da hannunsa,    Ganin manyan mutane sun fara cika babban falon yasa azmee komawa cikin ɗakinta jiki asanyaye, zama tayi tana jiran mutane su ragu sai taje ta dubo shi,    Hannu Abbansu yasa ya ruƙo na Ayaan yace "taso ina son magana dakai,"  Tasowa ayaan yayi daga zaunen da suke yabi abbansu suka ɗanyi nisa da mutane sannan ya kallesa yace "Ina junaid yake"?   Ayaan yace "ina ji yana a ɗakinsa bana tunanin ya fita, Amma abba tayaya hakan tafaru da Fawan? Suwaye suka yi mashi haka? ya fadi idonsa cike tab da hawaye,   Dafa kafaɗarsa abbansu yayi shima fuskarshi tamkar zaiyi kuka yace "Ayaan bamu son ko su wanene ba, Babban yayan ku da Omar sune suka je wurin da suka farmake su, kuma sun samu nasarar kashe wasu daga cikinsu, yanzu haka akwai mutun 3 daga cikin miyagun suna a headquater ɗin mu,"    "Abba don Allah karku kyalesu akashe su kawai," ayaan ya faɗi cikin jin ɗaci aransa   "Ba zamu ƙyalesu ba ayaan, mutanene masu haɗarin gaske, babban tashin hankalin ɗaya daga cikinsu da muka aza shi saman kujerar lantarki muka bashi horo ya bamu wasu bayanai nacewa macace take basu Umarni duk wani kashe-kashen da suke yi a ƙasar nan,"!     waro ido Ayaan yayi cikin tsananin mamakin abunda Abban nasu ya faɗa masa, aruɗe yace "What! Mace kuma Abba? mace wannan dana sani?   "Of course Ayaan, ba kai kaɗae ba kowa daga cikin mu yayi mamakin jin hakan, yadda akasan mata da rauni amma har acikinsu asamu wata mai ƙarfin halin haɗa tawagar ƴan ta'adda masu farmakar mutane suna kakkashe su, Amma koma wacece insha Allah zamu ganota bi'iznillah zata ɗanɗani kuɗarta!"    Jinjina kai Ayaan yayi yana cewa "Insha Allah Abba, Allah ya tonu asirinsu aduk inda suke, abun yayi yawa wlh rashin imanin nan har ina? mutun baya tuna cewa shima wata rana zai mutu yabar duniyar ne?shin menene ribarka idan ka kashe wani bayan kai baka isa ka hana kanka mutuwa ba?    Kafin Abbansu yace wani abu muryar kanal yusif ta katse su da cewa "Abba ka matso kusa mutane suna son magana dakai,"   Amsa mashi yayi da "toh gani nan zuwa" sannan ya kalli ayaan yace "Abun dayasa na tambaye ke game da junaid kasan halin shi, muddin ya fito yaga halin da fawan ke ciki tofa zai iya sume wa ko ya zauce, dan Allah kusan yarda za'ae ku hana shi fitowa daga ɗakinsa indae yana ciki,"     Ayaan yace "Shikenan abba bari naje na duba shi," cikin sauri ayaan ya wuce upstairs ɗakin junaid, a hankali ya tura ƙopar ɗakin cikin sanɗa ya shiga, abun mamaki samun shi yayi saman gadon shi zaune ya toshe kunnan shi da headphone yana kallo acikin laptop ɗinsa baya jin duk wata hayaniya da akeyi acikin gidan,     Murmushi Ayaan ya saki sannan ya ƙara ja mashi ƙopar ɗakinsa dakyau ya rufe masa ita, sannan ya juya ya sauko down wurin su, Har wurin dare mutane suna ta zarya agidan sai wuraren ƙarfe 9:30 sannan suka fara raguwa, tuni Sgr ya wuce part ɗinsa saboda ya gyara jikinsa ga matuƙar gajiyar da yayi idonsa ma kansu daƙer yake buɗesu ga yunwa ga bacci, har lokacin zuciyar shi tafarfasa takeyi duk in ya tuna irin artabun da su kayi tare da miyagun nan, duk da sunci nasara akansu sosai, bakomai bane ya tsaya masa aran shi ba face wannan maganar nace wa macace take ɗaukar nauyin tawagar miyagun dake kashe-kashen, yaci alwashin cewa sai ya gano ko wacece ita,  yanayin salon nata ya nuna cewa hada ɗaukar fansa take yi,' 😳😳😳 A asibiti marshal omar ya barsu hussana a hannun Camila kafin zuwa da safe zaisa a sallame su, shi da major suka wuce izuwa gida saboda kiran wayarsa da ake ta faman yi ga kuma tsananin damuwar daya shiga game da halin dasu Fawan ke ciki, daker sehrish tasamu ta fito sam tagaza samun natsuwa ta ko ina, ta damu da yanayin da taga Sgr da kuma halin da fawan ke ciki, a ƙopar ɗakin azmee ta tsaya sannan ta kwankwasa tare da jiran ta buɗe mata,    tana tsaye azmee ta bude ƙopan tana kallonta tace "kin gama kukan?  Shiru kawai tayi tana wasa da yatsun hannunta,  "hmmmm me kike yi ma kuka ne ɗazu"? Cikin sanyin murya tace"babu komai Aunty azmee kawai nadamu ne da halin dana ga fawan,'   Jinjina kai azmee tayi tare da cewa "gsky yaji jiki sosai, nima na tausaya masa bawan Allah, Yakamata muje mu duba shi, dama na jira ne mutane su ɗan rage sosai," Sehrish tace "ae nagama babu kowa a falon bansan inda suka kai shi ba," "Sun kwantar dashi ne, a ɗakin da suke kwantar da mara lafiya, bari nazo mu tafi tare, inyaso in mun dawo sai mu jera masu dinner ɗin duk da nasan abune mai wuya ma a samu wanda zai iya cin abincin, don duk suna cikin damuwa," tana fadin haka tashige cikin ɗakin bada jimawa ba ta fito sanye da mayafi, sannan suka jera da sehrish izuwa ɗakin dake anan downstairs, A buɗe suka same shi don haka su kayi sallama, muryar kanal yusif ce ta amsa masu tare da cewa "ku shigo ciki mana,"     shiga ciki sukayi sehrish har tsoran kallon jikin fawan takeyi, wanda ke kwance saman gadon idonshi arufe alamar ya samu bacci, Ayaan da jahad ne zaune daga gefen gadon sai kanal yusif dake atsaye, Azmee tace "Yusif ashe haka abu ya faru? Mu ba mu sani ba"!  Kanal yusif yace "Wlh kuwa aunty azmee abun babu daɗin ji, ƴan ta'adda ne su kayi masu kwanton 6auna, amma anci nasarar Cafke wasu daga cikinsu,"   Cikin nuna jimami aunty Azmee tace "Allah ya kiyaye gaba, ya tonu asirin waɗannan mutanen, wlh duk jikina ya mutu dana ga fawan acikin wannan halin bawan Allah, Allah dae ya tashi kafaɗunsa,"   Suka amsa mata da ameen, sai lokacin sehrish tace "Yaya yusif ya mai jiki"?   Yace "Alhamdulillah da sauƙi sosai harma ya samu bacci,"    Tace "Allah ya bashi lafiya,"   "Ameen ," suka amsa mata  Kanal yusif yace "Aunty azmee ku matso kusa dashi kuyi mashi addu'a yana buƙatarta sosai," matsawa su kayi atare kusa da fawan suna yi masa addu'a tare da tattofa masa, daga bisani su kayi masu sallama suka fito waje   Kitchen suka wuce atare don sun shirya abincin dining azmee tace "bari na haɗa maki, ki kaima babban yayansu nasan zai buƙaci wani abun,"    "Toh," ta amsa mata, suna cikin kitchen ɗin haroon ya shigo cikin babban falon daga waje ya shigo ciki hango sehrish da yayi yasa shi wuce wa cikin kitchen ɗin, kamar yarda ya saba fado masu batare da sallama ba haka ya shiga,    ɗagowa su ka yi suna kallon shi hankalin shi kwance tamkar baisan meke faruwa ba, azmee tace "haroon me kake buƙata ne"?    tsoki ya ɗan ja tare da cewa "tun yaushe nake ta faman zarya ina jiran a jera mana abincin dare amma shiru babu, so ake akashe ni da yunwa ne"? yayi maganar fuska aɗaure yana kallon sehrish wadda tuni ta kawar da kanta,   Azmee tace "kayi haƙuri haroon, saboda halin da su fawan ke ciki ne ga kuma mutane shiyasa ba mu samu damar fitowa ba mun jera,"   Uban tsoki ya kuma bugawa wanda har sai da suka ɗan razana suka kallesa yace "And then so what? Mutuwa fawan ɗin yayi ne da zaku fake da cewa halin da yake ciki ya hana ku jerawa mutane abincinsu"? Ya tambaya a ƙule  Mamakine ya kamasu jin abunda yace yadda ya nuna ko ajikinsa halin da fawan ke ciki,     nuna sehrish yayi da hannu tare da cewa "Ke! ki kawo mun abinci na yanzun nan a bedroom ɗina ina jiran ki,   Cikin sauri sehrish tace "Ni babban yaya zan kai mawa yanzu, sai dai ko in aunty azmee ta jera a dining ka zauna ka ci,'    Zaro ido haroon yayi afusa ce yace "Ke! Ni kike fadama cewa wani wai babban yaya zaki kaima abinci"? Ke ga futsararra ko"? ya tambaya yana faman huci    da ido azmee tayi ma sehrish alamar tayi shiru da bakinta, tsit tayi bata kuma cewa komai ba,   cike da bada umarni yace "Ina jiran ki ki kawo mun idan kuma ba haka ba zaki ga mai zai biyo baya," yana faɗin hakan ya fuce daga kitchen ɗin,   Murya tamkar zatayi kuka tace "Aunty azmee nifa bazan kai masa ba Allah,"   Azmee tace "sehrish ki daure ki kai masa, nikaina na tsorata da yarda yake mana magana, ina tunanin kamar yayi shaye-shaye ne baya cikin hayyacinsa,"    "Aunty azmee nifa bazan kai masa ba,kema da kan ki kince baya cikin hayyacinsa yanzu in naje zai iya kai mun bugu,"    ganin ta dage akan cewa ba zata je ba yasa Azmee cewa "to shikenan bari ni nakai masa, ke kuma ki kaima Sgr nasa," ajiyar zuciya sehrish ta saki tare da cewa "to," bayan sehrish ta kammala shirya masa a tray ta wuce upstairs part ɗinsa, sallama tayi ba'a amsa ba don haka tashiga daga ciki, babu kowa acikin falon alamar yana a cikin bedroom ɗinsa,    takawa tayi izuwa ƙopar bedroom ɗin nasa tayi masa sallama kusan sau uku sannan ya amsa mata da cewa"Come in,"   Shiga ciki tayi zuciyarta na dar-dar lokacin da ta aza idonta akanshi yana zaune gaban dressing mirror saman chair din dake gaban madubin, ya sanya tafin hannayensa ya tallabo gefe da gefen fuskarsa ya zabga tagumi agaban mirror, sam babu riga ajikin shi daga shi sai short green colour, da alama ma daga wanka ya fito yagaza yin komai shine ya zabga tagumin, Sumar kanshi duk ta barbazo ta rufe masa gefen face dinsa, da wasu siraran gashi da suka sauko ta saman fuskarsa idonshi na arufe saboda gajiyar da ta lullu6e ga66ansa da kuma baccin da yake ji ga kuma yunwa duk shi kaɗai tsayawa sehrish tayi jiki asanyaye tana kallon shi tsananin tausayin shi ne yakamata ganin yarda ya zabga tagumi da hannayensa biyu, alamar baya jin daɗi   Ta jima tana kallon shi kafin ta ɗanyi gyaran murya tace "dama abinci ne na kawo maka, bansan ko kana buƙata ba," ta fadi adan tsorace gudun kar tayi kuskure a maganarta,    daker ya buɗe bakinsa tare da cewa"keep it on the table, then i wanna see u," gabanta ne ya faɗi rass ! jin abunda yace na yana son ganinta ƙarasawa tayi ta ajiye masa dinner din saman table ɗinsa, sannan ta matsa kusa dashi ta tsaya sannan tace "gani,"   Hannu yasa ya ɗauko wata ƙaramar kwalba ta magani daya ajiye a saman mirror din sannan ya miƙa mata tare da cewa "rub it on my back," ya fadi tare da kifa kansa saman gaban mirror ɗin yadda zata samu damar murza masa maganin, tama rasa ta ina zata fara shafa masa shi, gaba daya duk tabi ta rikice wai yau itace sgr da kansa ya bata magani don ta shafa masa abayansa, jikinta har kerma yakeyi tsoranta kar ta fasa masa fatar bayansa saboda hasken fatar fes tamkar in kasa yatsa jini zai fito,   Matsawa ta ƙara yi dab dashi sosai sannan ta buɗe mufin kwalbar, tasa yatsa ta lakuto maganin tare da ɗan russinawa ta lakuta masa shi abayan, sannan tasanya hannunta a hankali tana shasshafa masa shi, tun da Allah ya halicce ta bata ta6a jin skin mai tsananin laushi da daɗin tabawa ba irin fatar bayan sgr,  Shi kuwa ajiyar zuciya kawai yake saukewa saboda relief daya fara samu sosai na ciwon da ga6o6insa suke masa, tun sehrish nayi masa da hannu ɗaya har takai ga ajiye kwalbar maganin ta sanya duka hands ɗinta a faffaɗan bayansa tana yi masa massage, a tunaninsa in ta kammala zata cire hannunta ne, amma sai yaga ta zarce gaba ɗaya babu alamar zata daina shafa masa gashi kuma yaji ko'ina na bayansa yaji maganin sosai, shiru kawai yayi bai ce komai ba, almost one hour kenan sehrish na shafa masa magani har sai da ya ɗan ɗago da kansa daga kwancen da yake tare da cewa "Har yanzu maganin bai shafu bane"? Cikin sauri ta janye hannunta tare da ɗagowa tana kallonsa suka haɗa ido ta cikin mirror,   gabanta ne taji ya ƙara faɗuwa rass ganin yarda kwayar idonsa ke shining sai taga tamkar tana canza launi ne daga blue zuwa green,.     sunnar da kanta tayi ƙasa tana faman haɗe yatsun hannunta dake dankare da maganin data shafa mashi, lumshe idonsa yayi tare da sake buɗe su yace "kin haɗo mun da coffee ne? ya tambaya a kasalance hakan ba ƙaramin kashe ma sehrish jiki yayi ba, tuni ta nemi natsuwarta tarasa sai ta kama en ena tana faman wurwurga ido  "Its ok, idan babu akawo mun shi," ya faɗi tare da mayar da idonshi ya lumshe su, Juyawa sehrish tayi cikin sauri ta fuce izuwa kitchen donta haɗo masa, a lokacin har azmee ta kammala shirya masu abincin dinner ɗin a dining amma babu kowa asaman shi alamar basu kaiga fitowa ba,  tayi mamakin hakan duk da tasan cewa duk suna cikin damuwa ne,bata ji daɗin hakan ba, tasa ba ganin mutanen gidan cikin raha suna nishaɗi suna cin abinci yau kuma wayaam babu kowa, Yau da gobe kenan,    tana acikin kitchen ɗin bayan ta kammala haɗa masa coffee din ta ruƙo cup ɗin a hannunta, sai ga haroon ya faɗo mata kamar daga sama cikin sauri taja da baya hankalinta atashe, daga shi sai vest da singlet, shu'umin murmushi ya saki yana kallonta yace "ke shine nasa ki kaimun abinci kika ƙi ko? Ke ga isassa mai walkin sa harni ɗan masu gida zan saki aiki, ki bijire mun," ya faɗi yana kallonta   Murya na rawa sehrish tace "kayi hakuri dama na fara kaima babban yaya ne, kafin na kawo maka nakan......'  Bata ƙarasa ba ya katse ta da cewa "Sorry for your self sehrish! wlh kin shiga uku ! kin jefa kanki cikin masifa, daga rana irin ta yau inaso kullum ki kasance cikin yin sallar dare kina rokan Allah akan ya kare ki daga Sharrina," zaro ido tayi tana kallonsa jin abunda yace cikin tsananin tashin hankali tace "saboda me zaka ce haka"? laifin me nayi maka, dan Allah kabarni inyi rayuwata cikin salama,"   Fashewa da dariya yayi kafin ya tsagaita da cewa "kinsan wani abu?kina da kyau sosai musamman idan kika tsorata idanunki ba ƙaramin fizgata sukeyi ba, idan kika amince a shirye nake dana aure ki, kuma zan shiryu nadaina duk wani abu da nake yi, amma idan kika bijire mun I pity u wlh," cikin sanyin murya yake yi mata magana,.   Tamkar zatayi kuka tace"Dan Allah na roƙe ka kayi hakuri nidai ka fita daga cikin rayuwata, kabarni dan Allah kaje can ka samu mace irinka ka aura, amma ni ina da wanda nake so," tayi maganar tare da bi ta gefensa gabanta na faduwa ta wuce cikin sauri,   murmushi kawai haroon yayi tare da jinjina kansa aransa yace "nasan ba kowa take hari ba face wancan mai zubin ifritan, ni kuma ba zan ta6a bari hakan ta faru ba, target ɗina na farko da zanyi zan fara 6ata sunanki ne a wurinsa," yana fadin hakan ya saki shu'umin murmushi tare da wuce wa room ɗinsa   Maganganun da haroon ya faɗa mata sun tsaya mata arai, tunaninta ya rayuwarta zata kasance nan gaba acikin gidan batasan me haroon zai yi mata ba, tana tunanin tana tattaka stairs ɗin jiki amace, adai² lokacin Marshal ya shigo gidan cikin sauri saboda yarda yake agajiye shima, har sai da ta juyo daga saman stairs din ta ɗan kalle sa, ta other side ɗin yabi ya wuce part ɗinsa da hanzari sam bai lura a ita ba,    bakomai bane ya faɗo mata arai face yaran da taji yace zasu zauna gidan Uncle Abusufyan ɗinsu, ko ya ɗauko su? ta tambayi kanta  cikin sauri ta wuce part ɗinsa bedroom ɗinsa ta shiga da sallama ya iznin shiga, a lokacin harya dawo gefen bed ɗinsa ya zauna yana cin abincinsa, yau ba sai ya jira anyi saving ɗinsa,   ƙarasawa tayi kusa dashi sannan ta samu wuri agefen plate ɗin abincinsa ta ajiye masa cup ɗin,"  A hankali ya furta "thanks,' a tunaninsa zata tafi amma sai yaga tayi masa tsaye akansa, sam bata son ta tafi tabarshi saboda a ganinta in ta tafi bazai ƙarasa cin abincin bacci zai iya ɗakarsa, Hannu yasa ya ɗauki cup of coffee ɗin data kawo masa sosae yasha, bayan ya kammala ya ajiye shi, sannan ya gyara kwanciyarshi ya kwanta luf abunsa, ya janyo blanket ɗinsa ya rufe har zuwa chest ɗinsa nan take bacci ya ɗauke sa,  bata bar bedroom ɗin nasa ba sai da ta tabbatar tayi masa addu'a tukunna tasa hannu ta kwashe kayan abincin acikin tray ta fuce dasu a hannunta,    Kitchen ta koma da hanzari ta haɗa ma Marshal Omar nasa shima acikin tray sannan ta wuce masa dashi part ɗinsa, tana shiga a lokacin ya fito sanye da jallabiya fara wuri ya samu asaman 3 seater ya zauna hannunsa ruƙe da wayarsa ganin sehrish yasa shi sakar mata murmushi tare da cewa "kamar kinsan a yunwace nake abunda nake jira kenan,"   Murmushi ta saki tare da ƙarawa ta ajiye masa tray ɗin asaman table ɗin dake a gabansa sannan tace "Ya mai jiki ya omar, naji abunda ya faru Allah ya kiyaye gaba, ya tonu asirin su,"   "Ameen Ameen," ya amsa mata, hannu tasa ta buɗe warmer tare da ɗaukar plate da saving spoon zata zuba masa abinci taji yace "baki tambaye ni twins ɗina ba"? Murmushi ta ɗanyi tare da ɗagowa ta kalle shi tace "dama ƴan biyu ne"? Yace "eh kamannin su ɗaya sak, ke ma haka fuskarki irin tasu ce sak komai da komai,"    gabanta ne taji ya faɗi jin abunda omar yace dakatawa tayi da zuba mashi abincin tana son tunano wani abu arayuwarta amma sam takasa tunawa, tabbas tana jin cewa akwai wani abu da ta manta arayuwarta mai matuƙar muhimmanci agare ta, a duk lokacin da tayi ƙoƙarin tunawa sai taji zuciyarta tayi mata wani irin nauyi sosai, "Wata rana zan kawosu ku ga juna, saboda inaso ki ga abun al'ajabin da nake son nuna maki," Cikin sauri tace "Shikenan ya Omar Allah ya kaimu lokacin nima zanso nagansu," ta jima suna dan fira dashi kafin daga bisani ta bar part ɗin nasa ta koma ɗakinta,   Bayan Omar ya kammala cin dinner ɗinsa fitowa yayi tare da wuce wa ɗakin da suka kwantar da fawan   Yanayin daya samu Twis zaune zun zuba mashi ido ga kanal yusif shima zugudum duk cikin jimami, gyaran murya yayi duk suka ɗan ɗago kana yace "ku tashi ku je ku kwanta, tun da ya samu bacci"    Amsa mashi su kayi da "toh" sannan suka miƙe tare da fuce wa daga ɗakin shima yusif yayi yabi bayansu, zama Omar yayi daga gefen fawan dake ta faman sharar bacci, addu'o'i ya shiga karantowa yana tatto fa masa, ya jima yana yi masa addu'a sannan ya tashi yabar ɗakin tare da tufe masa ƙopa, **************** Wuraren ƙarfe sha biyu ya fito cikin sanɗa hannunsa ɗauke da pillow yana duddubawa yaga in ba kowa duk sunyi bacci lokacin murmushi ya saki tare da cewa "sheggu saboda wancan ɗan shilan shine duk suka susuce har suka gaza cin abinci, bari na ƙarasa shi lahira sai in ga ya zasu yi, zasu bi shi ne  Yana faɗin hakan ya wuce ɗakin da suka kwantar da fawan cikin sanɗa ya tura ƙopar tare da sa ƙafa yashiga cikin, bin shi yayi da kallo jinjina kansa yayi sannan ya lalla6a ya haye saman gadon tare da ɗaga pillow ɗin ya taushe ma fawan hancinsa dashi , nan take fawan yafarka tare da zazzare idanunshi yana mutsu-mutsu sam bashi da sauran ƙarfi ajikinsa da zai iya kwatar kansa........... ... ... sai faman kiciniya fawan yake yi saboda ya kwaci kansa daga hannun haroon wanda ya taushe masa fuska da pillow da mugunta ma yake kara danna masa shi, tun fawan yana wutsil wutsil da ƙafafunsa numfashinsa na kokarin daukewa gaba daya har jikinsa ya fara saki, suna cikin wannan halin aka kwankwaso kopar da karfin gaske,a wani irin tsorace haroon yayi wurgi da filon dake hannun shi, yayi wuff tamkar giftawar walkiya ya afka bayan labule ya boye yana faman zazzare idanun shi kamar na mujiya tsoran shi kar ace wani ne ya taso cikin daren nan, Hannu yasa a hankali yaɗan buɗe labulen don yaga kowanene, gabansa ne yayi bugun bugu ganin Abbansu ya shigo ciki jikinsa sanye da jallabiya fara, cikin sauri haroon ya mayar da labulen ya rufe ruff tuni zufa ta soma tsattsafo masa a jikinsa tamkar wanda aka tsamo daga kogin maliya, ?    ganin yarda fawan ya tashi zaune saman gadon yana faman hargowa yana fadin "zasu kashe ni ! bansan me nayi masu ba! Sun biyo ni don su kashe ni, ku ce musu su daina azabtar dani !!!! Gaba ɗaya ya zauce sai zuba sambatu yake yi yana zazzare ido,    A hanzarce Abban nasu ya ƙarasa tare da haye wa saman gadon dab dashi yana cewa"fawan sannu ya jikin? ka dawo cikin hayyacin ka ko? ka kwantar da hankalin ka, kana a gida yanzu babu wanda zai iya cutar da kai,'.  ?    girgiza kai fawan yashiga yi yana sake maimaita cewa "Har yanzu suna nan, bibiyata suke yi so suke su kashe ni, ni bansan me nayi masu ba," yana magana daker daker yake sakin numfashi, hancinsa har ya fara bleeding kaɗan jinin ke ɗigowa,    tallabo fuskarsa Abban nasu yayi tare da ɗago da ita don ya kalle shi sosai yace "fawan Ni ne fa,Abban ku ina tare dakai, babu wani anan da zai cutar da kai,"   A hankali fawan ke kallon Abban nasu yayin da idon shi ke rurrufe wa yace "Abba ruwa zan sha," ya faɗi agalabaice, ?    Cikin sauri Abban nasu ya matsa tare da kai hannun shi saman bedside drawer ganin dakwai bottle water mai sanyi ajiye asama, ɗauko wa yayi tare da buɗe murfin ya kwafa masa abaki yana sha, jikin shi har wani kerma yake yi tamkar zai kwace roban ruwan daga hannun Abban nasu daya kwafa mashi, ganin yarda yake shan ruwan throat ɗinsa har wani sauti yake fitarwa kwattt!kwattt!! Saboda yarda yake kurbarsa a zafafe, ba ƙaramin tausayi yaba Abban nasu ba, tamkar ya zubar mashi da kwalla haka yake ji, daurewa kawai yake yi   Sai da ya shanye kusan rabin ruwan sannan ya janye mouth ɗinsa alamar ya ƙoshi, sannan Abban nasu ya rufe robar ruwan ya mayar da ita saman side drawer din ya ajiyeta,   Sannan ya mayar da idon shi kan fawan dake ta faman sauke ajiyar zuciya yana fidda sound na radaɗin ciwo abakinsa,   Haroon daka la6e acikin labule yace "shegen yaji dannar manya,an gaya ma jin ƙamshin mutuwa wasa ne,dole ka nemi ruwa yaro, ba don jatuminka ya faɗo cikin ɗakin nan ba, da yau saina aika ka barzahu wurinsu munkar, gskiya Abba ya kawo mun cikasss amma ba komai mu haɗe gaba,' ya faɗi yana cizon la66ansa,   Haroon kenan duk da yana cikin tashin hankali amma hakan bai hana shi sambatun nan nashi ba, mutuwa ce kawai zata iya zuge zeep ɗin bakinsa,  muryar shi na rawa yace "Abba ashe zan ƙara rayuwa? abba nasha wahala sosai tamkar bazan rayu ba,ashe da rabon na sake ganinku a idona"? Ya faɗi yayin da idonshi ke zubar da kwalla,    shima Abban nasu jiki asanyaye yace"Fawan nasani wlh,nashiga damuwa sosai game da halin da kake ciki har nagaza runtsawa saboda son nazo naga wani hali kake ciki,kayi haƙuri fawan iya cuta dae sun cuce ka sosai sun raunata dukkan ga66an jikinka, amma nayi maka alƙawarin cewa ɗaya daga cikinsu bazai sha ba, wlh muddin ina da raina da kuma lafiyata saina ƙuntata duk wani jin daɗinsu na duniyar nan,"   Lumshe ido fawan yayi tare da kwantar da kanshi a kafaɗar Abban nasu yana sauke ajiyar zuciya sannan yace "Abban sunce fansa suke ɗauka akan family ɗin mu,wannan harin da suka kai mana, ba don kowa su kayi shi ba face saboda mu kawai,"  Jin wannan maganar ta fawan tasa zuciyar Abban nasu yin wani irin bugu duk da yasan maganar revenge ɗin amma baisan cewa akan ƴa'ƴansa bane abun zai afka,   "Insha Allah, Allah bazai ta6a Basu nasara ba fawan,zamu tashi tsaye wurin ganin mun kawar da koma su wanene su,Kuma zamu dage da addu'a akan Allah ya tonu asirinsu ya Kuma Kare Mana zuri'ar mu da dukkan al'umar musulmi,"   "Ameen Abbana," ya amsa mashi daker,   Haroon dake a la6e bayan curtains duk yana sauraronsu gaba daya ya ƙagu abban nasu ya fuce daga dakin shima ko ya samu ya gudu,tuni kafafunsa suka soma daskare wa suna mashi raɗaɗi saboda tsayuwar da yayi, ga wani irin fitsari daya matse shi, sai uwar zufa ke wanko masa daga fuskarshi, runtse idanun shi yayi yana cewa "wayyyo Allah na, ko yaushe wannan tsohon zai ware nima in samu in gudu,lallaima mutumin nan wato saboda wannan ɗan shilan shine harya gaza yin bacci, ya wani kwaso kafafunshi yazo don ya gan shi,ina sane da komai wato ya daura son duniya ya aza masu,duk ranar dana hallaka ɗaya daga cikinsu zanga in haukacewa zaiyi ko kuma zaiyi suicide ne,'    Ya faɗi yana cizon lips dinsa yana wani irin huci, bude idonshi yayi tare da sa hannu ya sake bude labulen a hankali ya leƙa su, har time din abban nasu na zaune dirshan saman bedmattress din, fawan kuma ya kwantar da kanshi a kafaɗar shi,da alama ma bacci yayi awon gaba dashi gaba ɗaya ya lafe masa kwance luffff abunsa,    Tuni ran haroon ya ƙara 6aci saboda takaici da baƙin cikin dayake ji aduk lokacin daya ga Abbansu na nuna ma ƴa'ƴan alexandra soyayya,zuciyar shi tafarfasa take yi saboda jin haushi, mayar da idon shi yayi kan pillow dinshi da yayi wurgi dashi kasa, nan gabansa ya faɗi tsoranshi kada abban nasu yaga fillon don za'a iya samun matsala,   Bari dae in taƙaice maku zance,Abban su bai bar ɗakin ba anan bacci ya ɗaukesu su duka biyun azaune fawan kwance a shoulder ɗinshi,   Kamar yarda suka kwana a zaune suna bacci haka Sir Commender Haroon ya kwana a tsaye ba bacci duk yarda yayi motsi zai fito sai Abban nasu ya buɗe ido, hakan ne ya hana shi fitowa daga bayan labule,    ya kuke tunanin wanda  ya kwana atsaye idonshi buɗe fuskarshi zata kasance, koda yake fa soja ne 😂    (Wata dae tace commendern ƴan Iska dae, Bana sojoji ba)😹😹😹 ****************************Morning tun da sassafe sehrish tafarka daga guntun baccin daya ɗauketa bayan Sallar asuba anan saman sallayar ta kwashe da bacci, duk jikinta amace tafarka sai faman hamma takeyi saboda yunwar da take ji, gashi yesterday night bata samu enough sleep ba saboda tayi nafilfilin dare,    tunawa da school yasa ta yin hanzarin tashi tashiga toilet shaf shaf tayi wankan ta, fitowa tayi jikinta ɗaure da towel fari, a bakin ƙopar toilet ɗin ta tsaya tana kallon uniform ɗinta da sukayi uban squeezing tun jiya da tadawo school ta cicciresu ta jefar saman gadonta bata ninke su ba kuma anan tabarsu,girgiza kai tayi sannan ta ƙarasa agaban mirrow ta tsaya tana shafa body oil ɗinta,bayan ta kammala ta feshe jikinta da turare sannan ta koma ta buɗe wardrobe ɗinta, hannu tasa ta ɗauko ɗayan uniform ɗinta mai pencil skirt ɗin nan sannan ta dawo ta ajiyesu gefen gadon tashiga zura su ajikinta, tana cikin sa kayan maganar haroon ta faɗo mata aranta nace wa ta fara sallar dare domin neman tsari daga sharrin shi, tabbas maganarsa ta girgiza ta saboda tun daga lokacin da ta dawo daki at midnight tafarka tayi nafilfili saboda neman tsari daga sharrin shaiɗanin mutun irin haroon, ta jima tana jin cewa wasu abubuwa zasu faru tabbas acikin gidan!!!!! duba da irin mafarkin da tayi a baccinta na jiya, kuma taci Alwashin cewa ashirye take data fuskanci duk wani abu da zai taso ta ɗaura ɗamarar yin yaƙi da duk wani da zaizo don tarwatsa rayuwarta ko kuma family ɗin SALAHUDDEEN HUSSEIN, Hakan na nufin SEHRISH ta shirya zama AYYANA wato mai bama family ɗinsu kariyyya daga miyagu irinsu Haroon da kuma ire-irensa masu irin wannan mummunan kuɗirin,nace ba Allah ya ba mai rabo sa'a,     Tana cikin wannan tunanin azmee ta kwankwaso ƙopar ɗakin tana cewa "Allah sa dai kin tashi," Murmushi sehrish tayi a lokacin ta kammala sanya uniform ɗin, ba ƙaramin kyau sukayi mata ba tafito ɗass especially skirt ɗin da ya bi shape ɗin jikinta sosai,    ƙarasawa tayi ta buɗe mata ƙopar ɗakin tana cewa "ae tun ɗazu na tashi nama kammala shirya wa,"   Bin ta da kallo azmee tayi tana jinjina kai kafin tace "To fa yau wankan skirt aka ɗauka? masha Allah kinyi kyau ƙanwata, ya maganar breakfast fa? ta tambaya tana kallon ta,   Sehrish dake ta faman murmushi tace "aunty azmee yau a school zanci abinci na gaskiya,amma zansha koda tea ne,"   Azmee tace "okey, shikenan bari na kawo maki tea ɗin,' gefen gado ta Zauna tana jiran dawowarta, A 6angaren haroon kuwa bashi ya samu damar barin ɗakin da fawan ya ke ba har sai wuraren sallar asuba bayan abbansu ya kwantar da fawan dake ta faman sharar bacci a kafaɗarsa, sannan ya samu yabar ɗakin don zuwa yin sallah, sir commender haroon na ganin haka ya lalalla6a ya fito ya sungumi pillow ɗinsa daya shigo dashi, sai da ya jinkirta abakin ƙopar ɗakin ya tabbatar da cewa sun harhaɗu sun tafi gabatar da sallar asuba sannan ya koma ɗakin shi, agalabaice ya hankaɗa kopar bedroom ɗin nasa yayi wurgi da filon hannun shi,sannan ya afka toilet don tuni mararsa ta ɗaure saboda fitsarin dayayi ta ruƙo har na tsawon awannni, fitowa yayi daga toilet ɗin har wani biji biji yake gani saboda yarda idanun shi suka galabaita sun kumbura sunyi jawur saboda rashin baccin da baiyi ba, saman gadon shi ya afka batare da tunanin yin sallar asuba ba, sai ma addu'a daya shiga yi yana cewa "ya Allah ka yafe mun,zan ɗan rama baccin da banyi ba da safe in na tashi zanyi sallar anjima,'yana faɗin hakan ya shiga sharar baccin shi, Babu wanda ya tayar da junaid daga bacci saboda basu son kwata-kwata yaga fawan ko kafin su tafi yin sallar asuba sai da Abbansu ya buɗe door ɗin ɗakinsa ya same shi baje magashiyyan yana sharar bacci rungume da pillow, murmushi kawai yayi tare da rufa masa door ɗin suka wuce mosque, turo ƙopar azmee ta ƙara yi hannunta ɗauke da tea set ta miƙa ma sehrish cikin sauri sehrish tasa hannu ta kar6a tana cewa "Nagode aunty azmee," Azmee tace "ki hanzarta fa kada kiyi late dayawa,"   "Toh," ta amsa mata sannan ta shiga shan tea ɗin, . har azmee zata fita sehrish tayi saurin cewa "Aunty azmee dama inaso nakaiwa babban yaya nashi kafin natafi school,"    tsayawa azmee tayi hannunta ruƙe da door handle ta juyo ta kalle ta tana ɗan murmushi tace "i knew, raina sai da ya bani cewa sai kinyi magana akan RAFAYET, ,ɗan sunnar dakai sehrish tayi tana kallon tea ɗin dake hanunta yana faman tiririn zafi    "Ni nake maki magana ba tea ɗin dake hannunki ba, naga kin zuba mashi ido,' guntun murmushi sehrish ta saki kafin ta ɗago tana kallonta daƙer ta iya cewa "aunty azmee baya jin daɗi jiyan nan that's why nake so nakai masa breakfast ɗinsa,nasan zai buƙace shi,"   Sakin baki azmee tayi irin mamakin nan tace "to ko dai kece ALEXANDRA ban sani ba,'   shiru sehrish tayi tana sakin murmushi saboda tagane cewa wannan sunan mommynshi ne,shiyasa azmee ta kirata da sunanta,    fuce wa azmee tayi tana cewa "shikenan kiyi sauri kizo ki kai masa breakfast ɗin," tana jin haka tayi saurin ajiye tea ɗin hannunta asaman bedside drawer inda kayan tea ɗin suke,    hijab ɗinta ta ɗauko ta zura ajikinta yar dai² shoulders ɗonta, sannan ta wuce kitchen ɗin tayi mamakin ganin yarda azmee tayi uban aiki duk ita kaɗai, da alama ma tun bayan sallar asuba bata koma bacci ba,saboda tasan cewa dole manyan baƙi su hallara saboda zuwa duba fawan, ..shirya ma sehrish tayi breakfast ɗin SGR acikin ƙayataccen tray sannan ta miƙa mata, ruƙo wa tayi a hannunta sannan ta miƙi hanyar zuwa part dinsa, tana cikin tafiya taji anyi gyaran murya juyowa tayi da sauri don taga wanene junaid ne tsaye jikinsa sanye da shirt pulover tare jeans, ......har ya kammala shiryawar shi cike da ɗaukin kaita makaranta ya fito, sai faman zabga murmushi yake yi sam baida wata damuwa, ɗan dawowa baya tayi dai² saitinsa sannan tace "junaid ! Ya akai naga kana ta faman zabga murmushi, kai bakasan meke faruwa ba acikin gidan nan"? tayi maganar tana kallon shi, ..cikin mamaki junaid yace "kamarya kenan? meya faru ne ni bansan komai ba,"   Jinjina kai sehrish tayi tare da cewa"jiya wani abu ya faru mai matuƙar raxanar wa, zan faɗi maka amma bari nadawo," ta faɗi tare da saurin haye wa upstairs tana murmushi, taso ta faɗama junaid abunda ya faru amma azmee dake tsaye daga kitchen tayi mata alamar karta kuskura ta faɗa masa, shine dalilin dayasa tace mashi ya bari tadawo, . tuni jikinsa yayi sanyi a ƙagare yake daya ji mai reesh zata sanar dashi,   Kitchen ya wuce wurin azmee da sallama ya shiga sannan ya gaishe ta yana cewa "Aunty azmee a shirya mun breakfast a yunwace nake, gashi inaso nayi sauri nakai sehrish school,   Sakin baki azmee tayi tana kallon shi kanta ya gama ɗaure game da lamarinsu su duka biyun, ita tagaza samun natsuwa saboda son takaima babban yaya breakfast ɗinshi, shi kuma junaid damuwarsa yakaita school,kowa da wanda ya damu dashi kenan,   Zama yayi saman dining chairs yana jiran azmee dake shirya mashi bf ɗinsa ta kawo mashi yaci, Acan ciki kuwa bayan sehrish ta isa part ɗinsa da sallama ta shiga baya cikin falonsa don haka ta wuce bedroom ɗinsa tsayawa tayi daga bakin door ɗin sannan tayi masa sallama, da wannan sexy voice ɗin nashi ya amsa mata, tare da bata permission din shiga daga ciki, .a hankali tasa ƙafarta ta shiga ciki tsayawa tayi zuciyarta na faman bugawa ba ƙaramin kyau yayi mata ba, ya juya bayansa yana tsaye a agaban mirrow jikinsa na sanye da bathrobe white colour wadda ta tsaya mashi dai² guiwarsa,a buɗe rigar take bai ɗaure igiyarta ba, amma akwai shorts ajikinsa,sumar kan nan tashi ta zubo mashi tayi irin Curly ɗin nan dark brown very smooth ta rufar masa abayansa, da alama bai jima da fitowa daga wanka ba, ...gaba ɗaya jikin sehrish ya gama mutuwa murus cos aduk time ɗin da tayi arba da wannan kyakkyawar surar jikin tashi rasa hankalinta take yi gaba ɗaya duk ta bi ta susuce,tana hangen shi ta cikin mirror saboda madubin yana facing dinta,   tabbas yaji alamar shigowar mutun tun da harya bada iznin shigowa daga ciki amma har yanzu baiji an motsa ba, a hankali ya ɗago da blue eyes ɗinsa ta cikin mirror ɗin karaf suka sauka akan na rishi dake tsaye jikinta na rawa ɗan zaro idanun nata tayi tana kallon nashi dake kallon cikin nata ta cikin mirror, hankali atashe cikin tsananin tsoro tayi saurin sunnar da nata ƙasa gabanta na faɗuwa,   gyaran murya ya ɗanyi kafin yace"a ajiye mun shi a palor, sannan agyara mun bedroom dina,' amsa mashi tayi da "toh" sannan ta juya ta fuce tana faman sauke ajiyar zuciya, a saman table ta ajiye masa sannan ta ɗan tsaya tana jiran ya kammala kimtsawa,after some minutes ya fito jikin shi sanye da tunic shirt milk colour tare da trouser, sai ƙamshi yake fitarwa, shiga cikin falon yayi ya samu wuri ya zauna saman royal sofa ɗin sannan ya shiga yin breakfast ɗinsa anatse, Wuce wa sehrish tayi cikin bedroom ɗinsa ta shiga gyara masa shi komai agyare yake,bedsheet ɗinne kawai da yayi squeezing ya tattare inda ya kwanta, cire shi tayi sannan ta musanya masa wani sabo mai kyan gaske ta shimfiɗa masa, bayan ta kammala gyara ko'ina cikin sauri tafito saboda tunawa da school karta yi late, a lokacin da ta fito samun shi tayi yana yin waya da alama kan fawan suke magana da mutumin daya kira shi awaya,        Kama hanyar fita tayi har takai baƙin ƙopa ta ɗan juyo tana kallon shi gudun kar ace yana buƙatar wani abu gashi zata tafi batare daya bata izni ba, ganin alamar mutun ta wutsiyar idonshi yasa shi ɗan juyawa karaf suka haɗa ido da sehrish dake tsaye tana kallon shi cikin sauri tace "Can i go"? tayi maganar aɗan tsorace,   Lumshe idonshi yayi tare da ɗan jinjina kai alamar eh,   Murmushi sehrish ta saki sannan ta fuce cikin sauri aranta tana cewa "Sannu bata hana zuwa,"😇   Saukowa down tayi cikin sauri adai dai lokacin ta ji saukar motoci cikin gidan alamar sunyi baƙi, kitchen ta wuce anan tasamu junaid zaune saman dinner table harya kammala cin breakfast ɗin shi, yana ganinta yace "dama yanzu nake shirin biyo ki, bansan meya tsayar dake ba gashi har time ya ƙure ma,da ace ana bugu a school ɗin wlh da kinsha bulala yau," dariya sehrish tayi jin abunda yace   "Bari na ɗauko school bag dita," ta faɗi tare da juyawa cikin sauri ta koma bedroom ɗinta,   Sallama junaid yayi wa aunty azmee sannan yabaro kitchen din, jin sallamar Cg Abbas yasa shi ɗagowa cikin tsananin farin ciki yace "Yaya Abbas kaine tare da Aunty Amani !!!"  murmushi suka saki gaba ɗayansu da yake tare suka zo shi da AMANI yana sanye cikin shigar shadda maroon color ita kuma tana sanye da Arab gown white colour mai kwalliya ajikinta na duwatsu tayi rolling veil a kanta, ba ƙaramin kyau tayi ba,   sam junaid ya gaza rufe bakinsa don murna, buɗe mashi hannu abbas yayi cikin sauri junaid ya ƙarasa tare da faɗawa ya rungume shi sosai ajikinsa yana cewa "i really missed u our last born, duk da ina fushi dakai saboda baka son zuwa kawo min ziyara,' yayi maganar a lokacin da ya raba jikin shi dana junaid,   ɗan turo mouth dinsa yayi cikin shagawa6a yace "Yaya Abbas saboda me zaka ce kana fushi dani dan Allah, bakasan yarda na damu dakai ba koda yaushe inason zuwa amma shaiɗan ya hanani zuwa,' dariya sukayi gaba ɗayansu jin abunda junaid yace,   ɗan gyaran murya amani tayi masa tare da cewa"Junaid ni baka ganni bane"?   matsawa yayi tare da kai hannu zai rungumeta ajikin shi, ae kuwa a razane Abbas ya finciko rigarshi tare da janyo shi baya baya yana cewa "Sannu mati na mata,!matar tawa zaka rungume agabana? salon mu koma gida ta juya mun baya ko?"   Fashewa da dariya Amani tayi shima junaid ɗin dariyar yake yi cikin jin kunya ya sunnar dakai, shi aganin shi ba wani abu bane don ya rungume matar yayan shi, duk cikin waye wa ne,   Abbas ya kuma cewa "Oh ni junaid? Yanzu fa in na ƙyale ka sai ka rungume ta ko"?    ɗaga mashi kai yayi alamar Eh, hannu abbas yasa tare da ɗan jan kunnan shi har yayi ƴar ƙara yana faɗin "wayyo yaya Abbas karka cire mun kunne na in rasa na jin magana,"    "Hanzarta ka cire masa kunnan, hukuma ce zata raba ni dakai," acewar Abbansu wanda bai jima da fitowa ba ganin su yasa shi tunkaro su,    Murmushi suka saki gaba ɗayansu, adai dai lokacin Sehrish tafito daga ɗakinta, harta sanya Sandals ɗinta taruƙo school bag ɗinta, ƙarasawa tayi inda suke,   tunkan taƙaraso Amani ke kallonta cikin jin bugun zuciya, shi kanshi Abbas kallon matashiyar yarinyar yake yi cike da mamakin ina aka samu yarinya mace acikin gidan, Ganin duk hankalinsu yadawo kanta yasa jikinta ya soma yin kerma, dakatawa tayi da tafiya sannan cikin en ina tace "umm....ina kwananan ku,"   atare abbas da abbansu suka amsa mata banda Amani dake tsaye ƙiƙam tana kallonta cikin tashin hankali, ita kanta sehrish atsorace take da kallon da Amani ke yi mata,    "Zonan My daughter nayi missing ɗin ganinki, gashi bakya zuwa kina gaishe da Abbanki ko"? Yayi maganar yana kallonta,   Ƙarasawa sehrish tayi gab da Abban nasu ta tsaya tana faman ƙaƙume hannun jakarta da ta sargafo a kafaɗarta, Hannu yasa tare da shafa gefen fuskarta yace"yaushe kika fara zuwa school ne ba'a sanar mun ba"? ....daker sehrish ta iya cewa "jiya ne nafara zuwa," Jinjina kansa yayi tare da cewa "okey,ki maida hankali sosai akaratun ki kinji ko? Banda biye ma ƙawaye    "Insha Allah Abba," ta amsa mashi, Baki asake Abbas yace "yakamata a wayar mun dakaina mana, ina aka samu yarinya kyakkyawa kodai daga cikin danginmu ne na damaturu ko zariyya"?   Ya tambaya aɗan ruɗe yana kallon Abban nasu, tunkafin Abban nasu yace wani abu junaid yayi saurin cewa "ƙanwata ce yaya Abbas, sunanta Sehrish kuma abbane yayi mun ƙanwa da ita, itama ƴar Abban mu ce, ba'a jima da haihuwarta ba, nasan zakayi mamakin yarda tayi saurin girma har haka, ka tambayi Abba zaiyi maka bayanin komai,'    yana faɗin haka yaja hannun sehrish suka bi ta gefensu suka fuce,   Dariya kawai Abbansu ke saki hada shi Abbas ɗin,   "Ji wata shiririta irinta junaid,hakanan kawai ya zabga mun ƙarya, ina na ajiye matar bare harna haifi ƴa kamar wannan,'  Ya fadi tare da yi masu alamar su shiga daga ciki, bin shi su kayi tare da samun wurin saman royal sofa mai mazaunin mutun uku suka zauna, Amani na kusa da Abbas yayin da Abban ke fuskantar su yace "sannun ku da zuwa,nayi mamakin ganinku da wuri haka," Abbas yace "tun jiya muka so muzo,amma dare yayi sosai lokacin, wlh sam nagaza samun natsuwa ne game da halin da naga fawan a asibiti, shine nace mata tashirya muzo har gida mu duba shi,"    yayi maganar fuskarshi dauke da damuwa, Amani ma tace "Abba ya mai jiki? sai jiya da daddare yake faɗamun abunda ya faru dasu fawan hankali na ya tashi sosai, tun jiya nima naso ko wayane nakira na tambayi jikin shi amma duk layin dana kira ba'a ɗagawa," Abba yace "ae ba zaki same su ba, saboda duk muna cikin damuwa ne,bakowa ma yasan inda ya jefa wayarshi ba,abun ne ya tayar mana da hankali sosai, Cikin sanyin murya tace "Allah sarki Allah ya bashi lafiya,ya tashi kafaɗun shi, su kuma waɗanda sukayi mashi wannan aika aikan Allah ya toni asirin su,"   "Ameen Ameen," suka amsa mata  Daga bisani Abbas yace "bari mu shiga ciki mu dubo shi,"   Miƙewa su kayi hada Abban yayi masu jagowa izuwa ɗakin da aka kwantar da fawan,   Da sallama suka shiga ciki, har lokacin fawan na kwance sai faman sharar bacci yake yi, Abbas yace "masha Allah jikin nasa yafara sauƙi, tun da harya samu bacci,"   "Ae tunjiya dana shigo ɗakin na same shi yana ta faman fisge-fisge yana cewa sun biyo shi zasu kashe shi,saina zauna wurin shi anan zaune muka kwana ni dashi da asuba ne nabar ɗakin," Abban nasu ne yayi maganar ayayin da yake samun wuri gefen gadon tare da zama yana kallon fawan ɗin dake kwance magashiyyan yana kwasar bacci,   matsawa Abbas yayi shima tare da samun wurin kusa da Abban nasu ya zauna sannan yakai hannun shi ya dafa forehead din fawan yana cewa "Baƙaramin jiki yaji ba gaskiya,sun azabtar dashi sosai bawan Allah, amma asannu zai warware insha Allah,   Kafin Abban nasu ya kuma cewa wani abu wayar Amani dake acikin handbag ɗinta tashiga yin ringing da ƙarfin gaske,   Kallonta Abbas yayi tare da cewa "ki fita waje ki amsa wayar," cikin sauri ta amsa mashi da toh sannan ta fuce,  dama so take ta fita daga ɗakin saboda gulmar data ciyota kunsan mu mata abun ajinin mu yake,da zarar abun gulma ya samu nan take zaka ga jikin mutun har rawa yake yi don ya faɗama ɗan uwansa, (Amma fa ni bana gulma) 😒 Cikin sauri Amani ta sauko down stairs jikinta har rawa yake yi ganin Azmee na jera masu breakfast a dining table, yasa cikin sauri ta wuce wurinta    Azmee naganin ta ta soma sakin fara'a tana cewa "aaa yau kune agidan namu? saukar yaushe," Batare da Amani ta amsa mata ba tace "Yawwa Aunty azmee dama akwai abunda nakeso na tambaye ki,"!   Cikin mamaki azmee tace "meke nan"?   "Ga me da Yarinyar dana gani acikin gidan nan, wata ƴar matashiyya shin ita ɗin jinin su Abba ce?   murmushi azmee ta saki aranta tace "Gulma ajali, in ba'ayi ba a mutu," a fili kuma tace "abokiyar aikina ce a aka kawo don ta runƙa tayani aiki,"   yamutsa fuska amani tayi kan ta yagama ɗaurewa ta kuma cewa "ƴar aiki fa kika ce? But i was confused ya akai naganta cikin uniform kuma har junaid na kiranta da ƙanwarshi? Kuma naji Abba ma ya kirata da My daughter,duk kuma a matsayin mai aikin?   dariya azmee tayi ganin yarda amani ta ɗaga hankalinta akan sehrish   "tabbas mai aiki ce itama, amma abba ya mayar da ita tamkar ɗiyarsa,bata da banbanci da sauran ƴa'ƴanshi a yanzu, saboda yana son Yarinyar sosai,"   Jin haka yasa Amani ɗan zaro ido waje bata ƙara cewa komai ba saboda wayarta da ta ƙara yin ringing, cikin sauri ta zura hannu tare da buɗe handbag din ta zaro wayarta, tare da duba screen din wayar don taga mai kiranta, sunan Aunty laila ne ya bayyana asama, kallon Azmee tayi tare da cewa "ina zuwa," tayi maganar tare da kama hanya ta danyi nesa da azmee sannan ta ɗaga kiran tare da kara wayar a kunnanta tana cewa "barka da safiyya Auntyna fatan kin tashi lafiya," Murmushi Aunty babba tasa ki daga can 6angaren tace "Lapiya lou Alhmdllh my sister, nazo maki da labari mai daɗi ina fata kina da kunnan saurara,"   Amani tace "nima ae ina tafe da labari zazzafan gaske, amma bansan wa zai fara bada labarin shi ba acikin mu,"    Saurarawa tayi tana jiyo dariyar aunty babba ta cikin wayar sai da ta tsagaita da dariyar sannan tace "ina tunanin labarina yafi naki daɗi kuma zaifi ƙayatarwa, bari dae ni nafara baki,"   murmushi Amani tayi tamkar tana agabanta tace ina sauraronki auntyna,   gyaran murya Aunty babba tayi sannan tace "ina yaran nan da nake baki labari Omar ya kawo mun gidana?   Amani tace "eh nagane su," Aunty babba taci gaba da cewa "ae tuni nasa an kwashe su, an jefar mun dasu bayan gari,yanzu haka hankalina kwance na rabu da alaƙaƙai, yanzu banda wata sauran damuwa saura target ɗina nagaba nake jira...." tunkan taƙarasa maganar Amani ta kwashe da wata irin mahaukaciyar dariya, Jin dariyar da amani keyi ne yasa aunty babba dakatawa da maganarta tana sauraronta ta cikin wayar, ganin cewa amani bata da alamar jinkirtawa da yin dariyar da takeyi ne yasata cewa "ke bana son iya shege, na ji kina mun dariya kodai daɗin labarina ne yasa ki jin daɗi har haka," ta tambaya tana jiran jin mai amani zata ce,   daƙyar Amani ta tsagaita da yin dariyar sannan tace "Aunty laila an fa yanka ta tashi,labari da ɗumi ɗuminsa idan ma kina atsaye to wlh ki zauna don kar in sanar dake ki yanke jiki ki faɗi,"   Jin maganar Amani yasa hankalin aunty babba ɗugunzuma,murya na rawa tace "ba atsaye nake ba,ina zaune saman 2 seater ne ina shan tea,dan Allah ki sanar mun wane irin labari ne wannan,"    wani irin shu'umin murmushi amani tayi kafin ta soma cewa"Yanzun nan muka zo gidansu Abbas saboda mu duba jikin fawan da miyagu suka kai masu hari, ina fata kinsan wannan labarin"? Ta tambaya tamkar tana agabanta, Aunty babba tace "eh nasani,ae muna nan muma zamu zo tare da ishaq don mu duba jikin shi,"   Jinjina kai Amani tayi sannan taci gaba da cewa "Shin ko kinsan cewa akwai wata matashiyyar yarinya kyakkyawar gaske da muka tarar acikin gidan !!!'   darammm !!!gaban aunty babba ya faɗi rasss a firgice ta saki cup ɗin dake hannunta ya tarwatse ƙasa, zumbur ta miƙe tsaye tana cewa "kamarya Amani ! Bangane abunda kike cewa ba anya ba kunne na bane suka jiyo mun hakan"?   dariya amani tayi kafin tace "ba kunnanki bane Aunty laila,zahiran ne wannan nake faɗa maki, wlh da ido na naga yarinyar,kyakkyawar gaske har na tambayi azmee nake cewa wacece ita yarinyar kodai cikin danginsu Abba take, sai azmee ke sanar dani cewa house maid ce itama amma Abba ya mayar da ita tamkar ƴarsa, har fa school sun sanya yarinyar babban abunda zai tayar maki da hankali sai kin ga yarda Abba ke kiranta da ɗiyarshi, yarinyar ba ƙaramin wuri ta samu ba....... Fuska a damuje aunty babba tace "nifa hanyanzu ban fahimta ba, shin yarinyar ƙarama ce sosai ko babba"?   Amani tace "ina fa, wlh balagagga ce nace maki fa matashiyar budurwa kyakkyawar gaske mai cikar sura,ni kaina dana kalle ta sai da gabana ya faɗi to ina ga matasan gidan da suka kasance maza ne dukansu,   Jin wannan maganar yasa aunty babba dake atsaye tana zarya a falon nata, aza hannunta na dama akanta, ɗayan kuma na ruƙe da wayar tashiga cewa "Ae shikenan wlh an yanka ta tashi, ni ina nan sake da baki ina murnar rabuwa da waɗancan tagwayen da Omar ya kawo min ashe abanza ga wata can ta riga ƙetare iyakar da bana so aje,amma an gama dani wlh ya akai har takai wannan lokacin gidan baki sanar dani ba,"? ta tambaya a kiɗime,   Amani tace "nafa ce maki ni kaina bansan da zamanta ba, yau ɗin nan muka ganta kwatsam tafito ɗas da ita cikin school uniform wlh abun ba'a magana yarinya haɗaɗɗiyar gaske,tasamu wuri fa sosai agidan, kuma yarda naga Abbansu na kiran sunanta da daughter dinshi kinga kuwa hakan na nufin nan gaba ma da sunan Surikata zai kirata,"    ƙasa ƙasa amani ke sakin dariya tana sauraron aunty babba dake faman Zabga salati, dama dagangan take tunzurata don ta rikitar da ita,  "Nashiga ukuna,wannan masifar har ina matashiyar budurwa kuma agidan surikina, wlh hakan bazai ta6ayiyu ba, wlh saina son yarda zanyi na rabata da gidan, badai zamu zo da ishaq ba hmmmm zanganta ne !! zanga KOWACECE ITA 😳😳😳   Sun jima suna waya da aunty laila kafin daga bisa ni sukayi sallama da juna amani ta koma daga ciki, ranta fess don tasan yau ko bacci aunty babba bazata iya yi ba har sai taganta a Abuja, gata ga yarinyar data bata labarinta, Fitowa hafsat tayi daga bedroom ɗinta jikinta sanye da sleeping dress ganin mommyn nata tsaye tana ta faman zarya a falon tana zazzaga bala'e ita kaɗai kamar zararriya, hakan yasa hafsat ƙarasawa kusa da ita tana cewa "wai mommy lafiya kuwa kike ta faman tada jijiyoyin wuya duk akan wanene? Uban tsoki Aunty babba ta saki sannan tace "wani mummunan labari amani ta sanar dani yanzun nan, wlh nagaza samun natsuwa, so nake kawai naganni a abuja wlh,"   Wuri hafsat ta samu tare da zama saman 2 seater sannan tace "mommy wannan wane irin labari ne haka daya tayar maki da hankali haryasa kika fasa cup ɗin da kike shan tea dashi," tayi maganar ayayin da take kallon kofin da aunty babba ta saki ƙasa ya fashe,   juyo tayi ta kalle ta rai a6ace tace "ba dole hankali na ya tashi ba, ina murnar rabuwa dasu hossana da jahad sai gashi yanzu Amani ta kirani awaya tana sanar dani cewa sunje gidan su Abba, sun tarar da wata matashiyar budurwa wai mai aikice fa, amma abba ya mayar da ita tamkar ɗiyar cikinsa," tayi maganar tana huci,   Shiru hafsat ta ɗanyi na wani lokaci kafin daga bisa ni ta saki ƙayataccen murmushi tace "Mommy kenan, dama kina tunanin haƙƙinsu hossana da jahad zai barki ne? to inaso ki sani haƙƙinsu ne yafara bibiyarki, kuma ba zaki ta6a cin nasara ba akan wannan yarinyar da aka baki labarinta yanzu, saboda mommy sam baki kyauta ma rayuwar yaran nan ba, basu miki laifin komai ba kinsa an kwashe su,ki kayi mun ƙaryar cewa gidan marayu za'a kaisu ashe zubar dasu kikasa ayi,yanzu wayasan wani hali suke ciki.........' hawaye ne suka soma zarya a fuskarta saboda raɗaɗin da take ji aduk lokacin da ta tuna dasu hossana da jahad,tun jiya da aunty babba ta sanar da ita cewa ba gidan marayu tasa akaisu ba, zubar dasu tasa ayi bata ƙara samun kwanciyar hankali ba, abun namata ciwo azuciyarta . kallonta kawai aunty babba keyi ganin yarda take zubar da tears ɗinta akan tsintattun yaran da bata haɗa alaƙar komai dasu ba,   tsoki ta sake ja tare da cewa "kin dai ji haushin rayuwarki wlh, saboda waɗancan marasa galihun kike ta faman sharara kuka,har kina ikirarin haƙƙinsu ne ke bi na,to ki zuba ido ki gani saina sa anyi waje da waccen yarinyar da amani taban labarinta,"    afusace hafsat ta miƙe tana kallonta tace "mommy! Ina miki fatan nasara," tana fadin hakan ta juya tare da komawa bedroom ɗinta,   Jinjina kai aunty babba ta shiga yi tana faman sakin huci kamar zakayan, afili tace "Tabbas dole nasan kowacece wannan yarinyar dake ƙoƙarin tarwatsa mun plan ɗina, yakamata nasan abunyi dole na kira HAYAAM awaya in sanar da ita cewa ta tattaro kayanta itama ta koma gidan da zama, tunda har ƴar aiki ta samu irin wannan gatancin ina ga ita da take ƙanwata !!!!!!🤭   Sai faman balbali bala'e take yi ita kaɗae tana ci gaba da zarya a falon, ******************************* tun bayan da junaid ya sauke sehrish a school su kayi sallama ta shige ciki shi kuma yakama hanyar komawa gida yana driving yana tunanin fuskar rishi ɗinsa tsantsar sonta ne ke sanya shi jin wata irin kasala a jikinsa, lokacin da ya ƙaraso gida sai da gabanshi ya faɗi rass ganin dandazon motoci suna ta shiga gidan nasu,manya manyan mutane ne aminnan abbansu suke ta zuwa dubiyar fawan, wasu daga cikinsu manyan shuwagabannin sojoji ne da kuma mr president da kanshi ya tako yazo don duba jikin ɗan aminin nasa atare dashi hada mataimakinsa da kuma babban ɗansa Captain Shattima wanda ya kasance aboki ne ga Marshal Omar da SGR tun a U.s don acan shima yayi karatunsa na Airforce, halayyarsa da ɗabi'unsa sak irin nasu ne shiyasa tafiyar tasu tazo ɗaya, ƙwararre ne a6angaren aikin shi, sannan kuma shima mace sam bata gaban shi,tamkar dae su ɗin dae,   Gida fa ya ɗinke ɗuff da mutane tamkar rasuwa akayi, ta ko'ina jinsin bil'adama ne ke ta shigowa,   Hankalin junaid ba ƙaramin tashi yayi ba tunkan yayi parking ɗin motarsa yake ta faman sharar hawaye tsoran shi kar ace wani abune ya faru dasu fawan saboda yasan sune basa a gida anturasu aiki,a hankali ya tsayar da motar sannan ya buɗe murfin motar ya fito yana kallon mutanen dake shigowa, ...jingina bayansa yayi ajikin motar tashi sannan ya zura hannun shi cikin trouser pocket ɗinsa, wayar shi ya zaro tare da shiga contact ɗin wayarsa, lambar abbansu ya gano sannan ya buga masa waya,   ta jima tana ringing kusan sau uku kafin Abban nasu ya ɗaga kiran,   Kara wayar yayi a kunnansa tare da fashe mashi da kuka,   Shiru Abbansu yayi yana sauraran kukan da junaid ke yi masa acikin wayar,   Cikin shesshekar kuka yace "Abba......wanene ya mutu, naga dandazon mutane acikin gidan...'daker ya iya yin maganar zuciyar shi na faman bugawa,    "Kana ina ne"? abban nasu ya tambaya .."gani awaje abba, nakasa shigowa,ina jikin motata yanzu haka ban jima da shigowa gidan ba, saboda nakai sehrish school ne,"   Ajiyar zuciya abbansu ya saki kafin yace "sauraran ni kaji da kyau, babu wanda ya mutu, nasan halinka ne shiyasa tun jiya ban sanar maka ba, amma yanzu zan faɗa maka, but promise me first cewa zaka daina kuka,"    Ajiyar zuciya junaid ya shiga saukewa yana cewa "Okey, abba nadaina tell me pls,"    gyaran murya abban nasu yayi tamkar yana agaban shi sannan yace "abunda ya faru shine, su irfan da aka tura aiki,miyagu suka farmake su amma alhmdllh duk suna cikin ƙoshin lafiya, fawan ne kawai suka samu nasarar cutar dashi harya zauce ssae tun shekaran jiya suna asibiti ana duba su sai jiya ne muka dawo gida tare da su............'   tunkan abban nasu ya ƙarasa maganar tashi tuni Junaid ya saki wayar dake hannun shi sakamakon faduwar da yayi nan take ya sume...................dama abunda abbansu ke gudu kenan  hankali atashe yake cewa "junaid!junaid !!! Kana jina kuwa !! Meya faru ne,   yarda yake fidda sautin maganar yasa kowa dake a falon kallon shi, dama duk suna a falon sun hallara saboda sun fiddo da fawan yana kwance asaman 3 seater yana amsa ya jikin da mutane keyi masa, gaba ɗaya hankalin kowa ya tashi,suka shiga tambayar shi meke faruwa ne, zumbur ya miƙe yana cewa "wlh junaid ne daga faɗi mashi halin da fawan ke ciki shikenan ya yanke jiki ya fadi ina tunanin ya suma ne awaje,' "Subhanallahi," mutanen wurin suka haɗa baki wurin cewa haka, fawan dake kwance kuwa tuni ya shiga kiran sunan junaid yana fadin "Abba akawo mun junaid inason ganin shi," ya faɗi akasalance,tun jiya dama yake so yasa shi a idonshi amma bai samu dama ba,   atare abbansu da cg abbas suka fito domin ɗauko shi, tun kan su isa sai gashi ɗaya daga cikin soldiers din dake cikin gidan ya ɗauko shi sa6e a kafadarshi, cikin sauri Abbas ya kar6e shi tare da yima sojan godaiya, sannan su ka koma ciki dashi, ********************SGR hospital tun safe su hossana da jahad suke ta faman jiran yaya Omar ɗinsu saboda yazo ya ɗauke su amma shiru babu alamarshi, suna kwance a gado ɗaya saboda since yesterday night hossana ta maƙale ma jahad aɗaki ɗaya suka kwana tana agefenta,hankalinsu kwance saboda kyakkyawar kulawar da suka samu a wurin nurse Camila,tun da sukayi breakfast wanda anan asibitin suke rabawa marasa lafiya abinci kyauta kuma lafiyayyen gaske,sunci sunyi hani'an suna jiran omar yazo, duk in Camila tashigo duba su sai sun tambayeta yaya Omar dinsu yazo? Sai tace musu a'a su ƙara jira kaɗan tun suna tambayarta har suka gaji suka daina, Around 12 na rana, Motar Omar ta shigo cikin asibitin, bai samu damar zuwa ba saboda busy ɗin daya shiga hakanne yasa shi aiko major domin ya ɗauko su kamar yarda yayi musu alƙawarin cewa da safe zai sa asallame su, dalilin dayasa ya turo masu da major kenan amaimakon shi,   Bayan major yayi parking ɗin motar sannan ya fito ya shiga ciki, kai tsaye ɗakin dasu su hossana ke ciki ya nufa,   suna ganin shi suka fara murna don sunsan cewa yana tare da Ya omar,      "Ya jikin naku"? Cikin sauri suka amsa mashi da cewa "Alhmdllh jiki da sauƙi," Yace "masha Allah,kun ganni ni kaɗai ko? Hossana tace "eh, ina ya omar din, shi bai zo ba tun ɗazu muke jiran shi,"   Murmushi major yayi kafin yace "kuyi mashi Uziri yana busy sosai, amma ya aiko ne nazo don na duba ku,sannan nasa a sallame ku mu tafi gida,"   ba ƙaramin daɗi suka ji ba, don aƙagare suke da su ga inda zasu zauna wurin da zasu fara sabuwar rayuwa,   "bari naje naga dr, yanzu nan zan dawo," yayi maganar tare da fuce wa daga ɗakin,   Cike da murna hossana tace "Shikenan mun rabu da wahala, yanzu zamu fara kyakkyawar rayuwa, saboda nasan yaya omar har makaranta zai samu,har na hango ni yarda zan koma nan da 1 month,"  Kallonta jahad tayi da yake sun tashi daga zaune tace "jibgegiya zaki koma kamar buhun fulawa,nikaina naƙosa naga yarda rayuwarmu zata canza,abu biyu nake tunawa da suke sani kwanciyar hankali na farko shine bani da wata sauran damuwa dama hossana ke nafi ji, damuwata aduk lokacin da muka shiga hadari kece ina tsoran kar na rasaki,abu na biyu kuma shine ƴar Uwarmu SEHRISH,duk da bansan a ina take ba amma inaji araina cewa TANA TARE DAMU, INA NUFIN TANA A KUSA DAMU SABODA INAJI A ZUCIYATA!! With confidence tayi maganar in serious matter,   jinjina kai hossana tayi kafin tace "Jahad nima inaji araina cewa REESHI TANA A KUSA DAMU,komai ma zaizo mana cikin sauƙi yanzu tunda zamu samu kwanciyar hankalin nemanta,ga kuma YA OMAR,NASAN DAGA MUN FAƊA MASA CEWA ƳAR UWARMU TA 6ATA MUNA NEMANTA KUMA KAMANNIN MU ƊAYA SAK MU TRIPLET NE,SAI MU FAƊA MASHI SUNANTA NASAN ZAI TAIMAKA MANA WURIN GANO TA.................✍️💋 Shin mai zai faru idan Aunty babba tayi arba da fuskar Sehrish😳 yaya zata kasance tsakanin Haroon da twins? Baku tunanin cewa dole ALEXANDRA tazo nigeria domin duba jikin fawan😲? haka zalika AMMI ma muna hasashen zuwanta domin ganin fawan😲, ga kuma goggon katsina karfa ace itama zata zo domin ganin fawan shin ya zatayi a lokacin da tayi arba da fuskar sehrish wadda takasance kamanninta ɗaya da ƴa'ƴan abusufyan ɗinta?🤣, to kodai shima abusufyan dake zaune ƙasar turkey zaizo nigeria ne?😯, ni duk bama wannan ba🤨 abunda yafi damuna shine HAYAAM ƙanwar aunty babba wadda ke shirin dawowa gidan da zama 🥱 in har dagaske ne kenan sehrish itace a tsaka mai wuya tabɗijan can, ga haroon ga aunty babba ga wata wai hayaam🥴 wayyo har kaina yafara ciwo don tunanin yadda zatakasance, yakamata naje na kwanta fa, amma kafin nan akwai hasashe ɗaya daya rage mun shin ya zata kasance idan Hossana da jahad suka sanar da Omar game da ƴar uwarsu wadda takasance ita ɗin ƴar ukunsu ce kuma sunanta SEHRISH 🥺🥺🥺     💋Boss Bature💋_ dawowa major yayi shida dr Emran,a cikin ɗakin da aka kwantar dasu hossana,fuskar major ɗauke da murmushi yace. "An yi discharge ɗinku,kwanan asibiti ya ƙare yanzu zamu wace gida,"    Murmushi suka saki gaba ɗayansu,jiki na rawa hossana ta sauko daga saman gadon,itama jahad lalla6awa tayi a hankali ta sauko saboda ƙafarta,   Kallonsu dr emran yayi tare da cewa"zamu yi missing ɗinku sosai gsky,amma tun da a wurin omar ku ke, zamu dinga zuwa muna ganinku,"    Murmushi suka saki gaba ɗayansu,gaisawa major ya ƙara yi da dr emran sannan yayi mashi sallama, ?   shiga gaba yayi su hossana suka bi bayanshi, daker jahad ke taka ƙafarta da taimakon hossana take tafiya saboda ta dafa kafaɗarta gudun karta fama ciwon ƙafarta,     A haka har suka ƙaraso harabar asibitin wurin ajiye motocinsu, hannu major yasa tare da buɗe masu ƙopar back seat don su shiga su zauna,har jahad tasa kai zata shigo suka jiyo muryar nurse camila tana cewa "wait !! Wait !!,   Dakatawa su kayi gaba dayansu suna kallonta dama kuma sun so su tambaye ta,ɗan zaman da su kayi da ita ba ƙaramin shiga ransu tayi ba, ƙarasowa tayi kusa dasu tana faman sauke ajiyar zuciya hannunta na ruƙe da jakar kaya, daga bisani ta ɗago fuskar nan ɗauke da murmushi tace"ba sallama twins?yanzu da banzo ba shikenan zaku tafi ko? Ku barni da kewarku,   murmushi sukayi gaba ɗayansu jahad tace "a'a bamu ganki bane shiyasa,"    kallon major tayi tare da cewa "tare dani zaku tafi, saboda already mun yi magana da marshal omar, ya dauke ni amatsayin wadda zata cigaba da kula da lafiyarsu,inaso naga gidan saboda in na tashi zuwa,   wani irin farin ciki ne ya rufe su hossana da jahad saboda sun lura da irin mutuncin dake gare ta, ba ƙaramin kula zasu samu a wurinta ba,   Murmushi major yayi tare da cewa "naji daɗin jin hakan sosai,saboda na lura da yadda kikeson yaran ina fata zaki kasance tare dasu,kuma zaki riƙe su amana,".     Jinjina kai Camila tayi tare da cewa "NA RIƘE AMANA,"   daganan suka shiga cikin motar jahad da hossana suna a back seat,major na a mazaunin driver yayin da Camila ke Zaune a other seat ɗin,"     a hankali yake driving dinsu harya fuce daga asibitin,ya miƙi shantalelen titi dasu, ajiyar zuciya kawai suke sauke wa ga wani farin ciki daya baibayesu, ba don komai ba sai don sanin cewa Ƙarshen wahalarsu yazo, yanzu lokacine da zasu huta ma rayuwarsu,suyi rayuwa ta ƴanci kamar kowane ɗan adam, batare da an ƙuntata masu ba ko an cutar 😇   Lokacin da suka ƙaraso gidan Uncle Abusufyan nan fa hossana ta zaro ido tare da buɗe baki alamar mamaki yarda kasan ƴar babyn roba haka ta koma sam bakinta yaƙi rufuwa don murna, ita kanta jahad bakinta a buɗe don murna fararen hakoran nan nata kamar gonar auduga, adai dai bakin gate ɗin major ya tsayar da motar sannan ya danna horn da ƙarfin gaske,   sai gashi an buɗe masu gate ɗin ta ciki, ba kowa bane face abokin Major ɗan leƙen asirin shi, acikin gidan ya kwana saboda omar ya dauke shi aiki, bayan alherin da yayi masa na kyautar mota sabuwa mai kyau da tsadar gaske, ga kuma uban salary daya yanka masa,😇    A hankali major ya shigar da motar cikin gate ɗin ɗan dagatawa yayi da driving ya zuge glass ɗin motar ya kalli osman yace "Shege mutumina, ka ga yarda ka canza jiya izuwa yau har wani haske ka fara? Cike da zolaya yayi maganar,   Dariya Osman yayi tare da cewa "ba dole kaga canji ba,an gaya ma yin karin kumallo da farfesun kaza wasa ne? mutun ya kwana a ac,sannan yayi wanka acikin kwami haba ae dole ma ne in canza,"    gaba ɗaya suka fashe da dariya jin abunda yace,    Major yace "nifa wasa nake maka malam, taya zaka canza kawai daga jiya zuwa yau don ka kwana a ac, kayi breakfast da farfesun kaza? Nace sannu ko uban son banza ae sai nan da irin one month haka,nan zamu ga canji,   Murmushi osman yayi tare da cewa " ka shiga ciki ka sauke su,in ka dawo zamuyi magana dakai, akwai labari mai daɗi," ?    Major yace "okey bari nazo," yayi maganar tare da sauke glass din motar ya wuce dasu ciki, adai adai stairs ɗin da zai sadaka da main palour ɗin gidan ya sauke su,    Buɗe motar Camila tayi ta fito, sannan suma su jahad suka fito daga ciki suna ƙarewa katafaren gidan kallo ya haɗu iya haɗuwa abun ba'a magana, Omar yasa an canza mashi komai nashi an ƙara ƙawata gidan sosai,    gaba dayansu sun ƙame suna kallon haɗuwar gidan, ganin basu da niyyar shiga daga ciki yasa major cewa "let's go in pls,"    Cikin rashin sani jahad ta take ƙafarta ba don komai ba sai don hankalinta daya tafi wurin ƙarewa gidan kallo,ƙara tasaki tana yarfa hannu tana faɗin "wash Allah na," jin haka yasa camila tayi saurin dawowa ta inda suke, ta taimaka mata wurin yin tafiya don su shiga ciki, Major ne yayi masu jagora su kuma suna abayan shi, har suka shiga cikin haɗaɗɗen jigunannan falon,nan fa suka baza ido suna kallon haduwarshi, wasu irin matsiyatan royal sofa set ne acikin sa masu numfashi ɗunɗuma ɗunɗuma a jere launin su brown colour,ga wasu set na Cushions Jere asamansu difference colour,duk gasu nan ba ƙaramin ƙawata kujerun su kayi ba, daga tsakiya wani ƙayataccen table ne legs dinshi brown ne, while daga saman glass ne, an ajiye flower asaman shi, ga fruits basket mai dauke da kayan mar mari, ba komai yafi tafiya da hankalin hossana ba face tanƙameman kwan filitar dake bama ɗakin haske tamkar zai faɗo ma mutun akai haka yake, sai kuma tv stand din dakin faskekiyar plasma ma ce mai dauke da speakers na jin sauti, ga wani telephone table dage a gefe, bari dae in taƙaice maku zance komai wannan da kuka sani a palour an zuba masu shi,    Sai faman yarfa hannu hossana take yi, yarinya fa takusa zauce wa ganin irin gidan da yaya Omar dinsu ya gwangwaje su dashi, wani abun ma sai mun shiga bedroom,    Jahad kuwa murmushi kawai take saki tana bin ko'ina da kallo,ita kanta Camila gidan ba ƙaramin burgeta yayi ba komai tsaf a natse ba tarkacen hauka,    Can dae hossana tace "Allah yasa ba mafarki nake yi ba,dan Allah koma mafarki nake yi jahad kada ku tashe ni," ta fadi tana faman hadiyar yawu, Dariya su kayi gaba ɗayansu, Major yace "wannan zahiran ne ba mafarki ba ne, kaɗan daga cikin irin son da ya'ya omar dinku yake yi maku kenan,zai iya yin komai akanku more than u think, ni dae fatana agare ku shine ku kasance masu yi mashi biyayya, ku bishi sau da ƙafa kada kuyi amfani da son da yake yi maku wurin karya mashi zuciya,ko ku ce zaku canza halayyarku saboda wata dama da kuka samu, yanzu lokaci ne da zaku more rayuwarku bayan duk wahalar da kuka sha,"    Sosai major yashiga yi masu nasiha, duk sun kasa kunne suna sauraronshi,sannan kuma suna amsa mashi da insha Allah,   Bayan ya kammala daga ƙarshe yace "ku samu wuri ku zauna mana,nasan kuna jin yunwa yanzu zan sa ayi maku oder na abincin da zaku ci, sannan ga bedroom nan zaku iya shiga ciki ku huta,"   A natse suka ƙarasa tare da samun wuri suka zauna fuskar nan fa awashe,   Mayar da idonshi yayi kan Camila yace "zamu tafi tare ne? Na sauke ki a asibitin ko kuwa,"   cikin sauri tace "no i will stay here wit them,cos i ave done my work bani da sauran duty till tomorrow,"   Murmushi kawai major yayi sannan yace "okey," sannan yasa kai ya fuce, A jiyar zuciya ta sauke tare da samun wuri itama ta zauna, bayan ta ajiye jakan kayan data zo da ita,   kallon juna suka shiga yi suna murmushi,yanayin iskar falon badae daɗi ba yadda sanyin ac ke ratsa sassan jikin mutun,    Ganin sun zauna shiru yasa Camila cewa "ba ku buƙatar shiga daga ciki ne? ta tambaya tana kallonsu   Jahad ce tafara cewa "inason nayi wanka, hossana ma tace "nima,"    tashi camila tayi tare da cewa "mu shiga daga cikin ɗakin to, nima inason nayi wankan," tayi maganar tare da ɗaukar jakar kayanta,   gaba tayi suka bi bayanta ɗaya daga cikin bedrooms ɗin suka tunkara, ƙoparsa a rufe take amma bada key aka datse ta ba, hannu tasa ta tura nan take ƙopar ta buɗe, shiga ciki su kayi atare, haɗaɗden bedroom mai ɗauke da tafkeken gado fankacece, yaji lumbutsetsiyar katifa lallausar gaske ga wasu matassan kai masu laushi asama an jera su, irin gadon da kana hawa saman shi ko bakayi niyyar yin bacci ba nan take zai ɗauke ke saboda daɗinsa 🥱 an gyare komai an shimfiɗe shi da bedsheet,side by side na gadon akwai side drawers, masu ɗauke da lamps,  daga can ɗayan bangaren ɗakin kuwa wurin Closet dinsu ne, ga wani haɗaɗɗen Dressing mirror an cika masu front dinshi da kayan make up da tsadaddun mayuka na jiki, komai an sanya masu, jerin wurin takalmansu,hand bags da sauran abubuwa da dama ba abun da omar yabari komai ansa masu,    jahad ce tafara shiga toilet ɗin don a ƙagare take da tayi wanka,lokacin da ta shiga cikin toilet nan fa taga zallar haɗuwa ta jima tana bin ko'ina da kallo kafin daga bisa ni tayi wankar daker tare da yin alwala saboda in an kira sallah tayi, fitowa tayi a hankali waist dinta daure da towel mai ɗan tsayi wanda ta samu acikin toilet ɗin, hannunta na ruƙe da doguwar rigarta da ta cire, samun su tayi zazzaune daga gefen gadon suna fira da hossana da Camila,   Ganin ta fito yasa camila tashi ta shiga toilet ɗin, a cikin laundry basket ta turo rigar, sannan ta ɗan juya ta kalli hossana dake ta faman lumshe ido alamar bacci tace "karfa kiyi bacci don na son halinki, ki bari kiyi wanka ke ma,"    Murmushi tayi kafin tace"ae bazan iya bacci ba jahad, saboda gani nake kamar in na kwanta zan farka na ganni a gidan wannan matar da ta azabtar damu,nakasa yarda cewa wai mune acikin wannan katafaren gidan nan mu kaɗai abun mu,gsky yaya omar ba ƙaramin ƙaunarmu yake yi ba,"     Jahad tace"nikaina ina mamakin hakan hossana,ashe akwai wata rana da zato mana irin wannan,mun samu yaya mai son mu tamkar ƙannensa duk don saboda mu ya Omar yabar komai nasa don ya ceci rayuwarmu,har yanzu ina mamamkin hakan hossana, yaya omar ya sanar dani cewa ɗan uwanshi yana kwance rai hannun Allah babu tabbacin cewa zai rayu,amma a hakan ya tsallake shi yazo wurin mu wannan wane irin mutun ne?samun mai iri Kyakkyawar zuciyarshi zaiyi wuya a faɗin duniya (shiyasa Hafsat bature take kamu) 🙄    ta yi maganar ne a lokacin datakai wurin closet tana neman ta inda zata buɗe shi,tana aza hannunta a jikin closet din nan take doors din dake jiki suka zuge da kansu, har sai da jahad ta ɗan tsorata tayi baya,tasowa hossana tayi itama tana kallon wurin kayan nasu, yadda suke tagwaye haka omar yasa aka jera masu komai kala biyu, jerin wurin pyjamas ɗinsu daban, jerin wurin dogayen riguna daban,jerin wurin jeans da t shirt daban, ga jerin under wears shima daban, komai nasawa ajiki an zuba masu shi,har sun wuce iyaka,   "jahad har naji inason nayi wanka wlh,saboda in canza kayan jikina," acewar hossana dake ta faman yarfa hannu tana kallon kayan,   Hannu jahad tasa tare da curo wasu pakistan masu kyan gaske,tana shafa jikinsu tunkan tasa har ta gano kyan da zasu mata,       a gefen gado ta ajiye su, sannan ta koma gaban mirror tana shafe jikinta da ɗaya daga cikin mayukan da tagani ajare, bayan ta kammala ta kuma feshe jikinta da turare mai ƙamshin gaske,    Sannan ta dawo ta tsaya a gefen gadon tana zura kayan ajikinta, duk hossana na can tsaye wurin closet ɗin tana ƴan ta6e ta6e,ji take tamkar tabi kowannansu ta gwada ajikinta,    Bayan jahad ta gama kimtsawa cikin pakistan din komawa tayi gaban mirror tana kallon jikinta,riga ce mai dogon hannu har guiwar ƙafarta sai wandon burgujeje irin nasu,ta yafa mayafin asaman kafaɗarta, sumar kanta kuma ta zubo a bayanta, murmushi kawai takeyi tana kallon kanta a cikin mirrow,   Muryar hossana ce ta katse ta da cewa"kinyi kyau sosai jahad saina ga kin koma mun tamkar ketrina kef,"      Jahad tace"sannu shugaban makaryata ni bada ketrina nake kama ba sai dae helen,oumma tace kamannin mu sak irin nata,' tayi maganar tana gyara gefen gashinta da hannunta,   Hossana tace"wacece helen kuma"?   "Ƴar film ce mana ta ƙasar ethiopia," Jahad ta bata amsa atakaice, kafin hossana ta ƙara cewa wani abu, sai ga Camila tafi to daga toilet din daga ita sai ɗan pant da bra, cikin sauri suka sanya tafukan hannayensu tare da rufe fuskokinsu cikin jin kunya,   tsayawa tayi tana kallonsu cikin mamaki take cewa"why are u hidding ur face pls? Can i know   Jahad tace"mun ji kunya ne,"    Murmushi camilla tayi tare da girgiza kai tace"kuna da kunya sosai,in dae haka ne kam ba zaku iya rayuwa a ƙasar mu ba,"     "Wata ƙasa ce"? Hossana ta tambaya,   Camila tace "Mexico," Jinjina kai tayi tare da cewa"ni ko sunan ƙasar ma ban ta6a ji ba gsky...."jahad ce ta katse ta da cewa "hossana zoki wuce kije kiyi wankan kema,"  Amsa mata tayi da toh sannan ta wuce cikin toilet ɗin,   Ita kuma jahad ta kama hanyar fita daga ɗakin har lokacin fuskarta na rufe da tafin hannayenta, abun sai ya ba camilla dariya sosai,   Sai da ta fita daga bedroom ɗin sannan ta soma sauke ajiyar zuciya, shiga cikin falon tayi, tana ƙare masa kallo, zagaye shi ta shiga yi tana tatta6a dogayen curtains ɗin dake kewaye dashi,    Sallamar Osman ce ta dakatar da ita, cikin sauri ta amsa mashi da wa'alaikum salam,sai da ya fara tambayar iznin shiga daga ciki, ta amsa mashi sannan yasa kai cikin falon,    Hannun shi na ruƙe da manya ledoji na abincin da yayi masu oder a restaurant,yarda yaga jahad ta kimtsa tamkar ba ita bace ya gani  acikin daji ba sume cikin ciyayi,ba don akwai dressing na ciwo a forhead dinta ba, da bazai iya shaida taba,  .murmushi kawai yayi tare da miƙa mata ledojin hannun shi, cikin sauri tasa hannu ta kar6a tana yi masa godiya,   Har ya juya zai fita sai kuma ya juyo ya kalle ta yace"pls game da abunda ya faru da ku a gidan yayan Omar,wurin matar yayan shi kada ku sanar dashi komai don nasan zai tambaye ku ne,   Murmushi jahad tayi tace"insha Allah ba zamu sanar mashi ba,"    "Yawwa" ya faɗi tare da juyawa yasa kai ya fuce,    Ajiyar zuciya ta sauke tare da ajiye ledojin a saman table,tana jiran su kammala kimtsa wa su fito suci atare,    Goya hannayenta tayi a ƙirjinta tana faman sakin murmushi,bakowa ne ke faɗo mata aranta ba face yaya Omar dinsu,ta ƙosa ta sashi a idonta saboda tayi mashi godiya sosai,kuma tayi missing din wannan kyakkyawar fuskar tashi,    tana cikin wannan tsayuwar sai ga Camila ta fito fes abunta har ta canza kayan jikinta,v neck shirt ce ajikinta fara sai wando jeans, ta ɗaure sumar kanta da ribbom,fuskarta asake ta ƙaraso tare da samun wuri saman 3 seater ta zauna tana kallon jahad tace"kina so ciwon naki ya dawo sabo mu koma asibiti gobe ko?   Girgiza kai jahad tayi tare da cewa"a'a bansan na take ta bane,ciwon bai mun zafi yanzu ina ji kamar naji sauƙi ma,"     Tace "duk da haka yakama ki kula just in case,"    Amsa mata tayi da toh sannan tace "ga abinci nan,an aiko mana shi," ta fadi tare da ƙarasawa wurin table ɗin ta matsar mata dashi kusa da kujerar da take zaune,    Sannan itama ta samu wuri ta zauna a kusa da ita,hannu camila tasa ta buɗe ledar ta farkon,kayan ciye ciye ne gasu nan chips, bugger, shawarma da sauran wasu tarkacen, ɗayar ledar kuma da ta bude masu fried meat ne (tsiren nama) mai yawan gaske yaji kayan haɗi sai ƙamshi yake yi,   Dole ne su buƙaci plate don haka jahad ta tashi tare da cewa "bari na ɗauko mana plate," camila tace "plate yayi kaɗan tray zaki samo mana,"  Amsa mata tayi sannan ta tunkari doors din dake a cikin falon tana neman kitchen babu alamar kitchen na a wurin,   "Ki duba down stairs baza arasa acan ba," acewar camila,   Cikin sauri jahad ta hau benen da zai sauke ta a dowm stairs tana sauka cikin sittingroom din ta hango kitchen ɗin, tasha mamakin ganin yarda aka ƙawata ɗakin,    Cikin hanzari ta wuce kitchen ɗin an tsara shi sosai,ƙarasawa tayi jikin kitchen shelves anan ta samu trays a jere ta ɗauki ɗaya,komai na cikinsa sabone wasu acikin kwalinsu wasu kuma a buɗe suke, tare da cokali ta haɗo masu da knife saboda taga tsiren naman basu zuge shi ba acikin tsinken shi yake,zasu buƙaci su yayyanka shi in zasu ci,   Fitowa tayi daga kitchen ɗin sannan ta koma upstairs ɗin, tunkan ta ƙarasawa ta samu hossana zaune agefen camila hannunta ɗauke da tsiren naman nan ta tura abaki sai ci take kamar kura,hankalinta kwance, bakomai bane ya burge jahad ba face ganin yarda hossana tayi wani irin kyau cikin gajeran skirt mini tare da riga ƴar t shirt tabi shape din jikinta, hada ƴar hoda ta shafa ma fuskarta da jan baki,    Ganin jahad ta soma washe mata baki, girgiza kai jahad tayi tare da cewa "dama nasan dole kiyi ƙara'e hossana irin wannan ɗaukar wanka haka,"    "Kaɗan kika fara gani ma,aunty camila ma tace in ta samu hutun aiki zata kaimu saloon a gyara mana gashi tare da ƙunshi ma duka za'a yi mana,"    murmushi jahad tayi a lokacin taƙarasa wurin table ɗin, aza tray ɗin tayi asaman shi sannan ta samu wuri ta zauna itama suka saka Camilla a tsakiyarsu,    ita ta baje masu tsiren acikin tray ɗin ta jera masu shi,sannan ta zuba masu chips ɗin daga gefe,    Nan fa suka gyara zama duka ukun suka tasar ma kayan lashe lashen, ba baka sai kunne, ba kaji komai sai sautin taunar shi da suke abakinsu, **********************SEHRISH tun da english teacher ɗinsu ta fita daga class ɗin, sehrish ta kifa kanta asaman desk din gabanta tana ta sharar bacci, har amrish ta gane mata daga jiya izuwa yau sam bata gajiya da yin bacci,alamu ma sun nuna cewa bata fahimtar komai kanta dashi da kwankwon ashana duk ɗaya suke,tashi amrish tayi tare da fitowa daga seat ɗinta ta ɗan sa hannunta tare da bubbuga bayan sehrish tace"ki tashi mu tafi time ɗin break yayi," kusan sau uku tana tashinta daƙer ta buɗe idonta da suka canza launi saboda bacci, miƙa tayi tare da yin hamma alamar yunwa take ji ga baccin ma bai isheta ba, fitowa tayi daga seat ɗin nata tana cewa"ashe har lokacin break yayi " Amrish tace"taya za'ae ki sani, bayan baccinki kawai kike tasha, anya kuwa ma kina yin bacci a gida ne? Ta tambaya tana kallonta a yayin da suke fita daga class ɗin,   "Ina yin bacci mana sosai,"_ "To meyasa kike yin bacci a class?ko karatu ma bakya saurara salon azo yin test ko exam kiyi ta baza idanu kina kallon question paper kina cizon biro ko? Ta fadi fuskarta ɗauke da dariya, itama sehrish din dariya tayi tana cewa "insha Allah hakan ma bazata faru ba,kafin lokacin zanyi karatu sosai,"   Suna tafiya suna fira har suka isa Lunch room ɗin nasu atare suka shiga ciki, students duk sun hallara suna ta having lunch dinsu,   ruƙo hannun sehrish tayi tare da kaita gaban table ɗin da zasu zauna,sai da rishi ta zauna saman table chairs din sannan amrish ta wuce ciki don ta amso masu abunda zasu ci,   Ajiyar zuciya sehrish ta saki tana kallon students din dake zaune a wurin suna cin abincinsu suna shan fira abunsu,zahiri su take kallo amma abaɗi ba komai take tunawa ba face fuskar SGR ɗinta,murmushi ta saki aranta tana cewa "koyana ina yanzu?me yake yi?ko yaci abincinsa?Allah yasa dae baibar cikin shi da yunwa ba, babu mai bata amsar tambayarta, cigaba da cewa tayi"bani da wani burin daya wuce naganshi cikin nishaɗi batare da wata damuwa ba,amma narasa dalilin dayasa kullum fuskarshi aɗaure baison yin fara'a,inaso na kawo sauyi a cikin zuciyar shi ya Allah ka bani wannan damar da zan zama ɗaya daga cikin farin cikin ran shi,"     Gaba ɗaya tayi nisa acikin tunaninta, batasan meke wakana ba kwatsam taji hannun mutun a ƙirjinta an shafa mata, a wani irin firgice ta buɗe idanunta gabanta na faɗuwa,    Bin su da kallo tayi atsananin tsorace, kai kana ganinsu kasan tantiran ƴan iska ne,su biyu ne mata jikinsu na sanye da uniform riga da wannan mini skirt ɗin,kai kace ba musulmai ba saboda ko head babu akansu, iya gashi ne kawai suka ɗaure abayansu shima ɗin na ƙari ne, ga uban bleaching sun sha abun dae kawai ba'a magana,.   Kallon juna su kayi suna dariya kafin ɗayar tace "wow gaskiya an mana nisa, Sofia tun yaushe aka kawo wannan zazzafar a school ɗinmu batare da sanin mu ba"? ta tambaya tana faman sakin murmushi gefen fuska, tuni jikin sehrish yayi mugun sanyi bakomai ta tuna ba face nasihar da kanal yusuf yayi mata kafin tafara zuwa school,   wadda ta kira da sofia tace"ni kaina bansani ba, amma yanzu tunda Allah ya haɗamu da ita, zatayi mana bayani ne, ta faɗi tana kallon sehrish tare da kashe mata ido ɗaya tace"ƴan mata,naga kin ɗaure fuska may be don na shafa chest ɗinki ne batare da izninki ba,ae mun afwa irin salon tamu gaisuwar kenan,ya sunanki ne"?    ƙara tamke fuska sehrish tayi jikinta na rawa Allah Allah take yi Amrish tadawo don tasan ita zata iya dasu,    ɗan ta6e baki zeenat tayi tare da cewa"Can't u talk to us? May be don baki son ko mu su wanene ba a school ɗin nan ba,zamu yi maki uziri ne," ta faɗi tana yarfa hannunta, yatsun nan zira zira tayi fixing nails dogaye a hannunta,    shiru sehrish tayi burinta amrish ta ƙaraso in ba haka ba tashi zatayi tabar musu table din gaba ɗaya ta koma Class, duk da yunwar da take ji acikinta,   Suna cikin zaman ne sai ga Amrish ta ƙaraso fuskar nan ɗauke da murmushi ta ruƙo tray a hannunta mai ɗauke da plate biyu na abincinsu tare da coke,   Sehrish na ganinta ta shiga sauke ajiyar zuciya,amma abunda ya daure mata kai time ɗin da amrish ta ƙaraso kai tsaye bayan ta ajiye masu tray ɗin asaman table din, sai ta miƙa ma Zeenat hannu suka gaisa tare da cewa"Am really glad to see u guys, nayi missing ɗinki sosai my zeenat," murmushi zeenat tayi tare da cewa"nayi missing ɗinki nima,bcox of u na matsa wa mommy sai mun dawo nigeria sbd a ƙagare nake da na haɗu dake ko fa isasshen bacci bana samu saboda rashinki,"     bin su da kallo kawai sehrish takeyi baki asake, yarda suke magana tamkar irin mace da namijin nan,   Muryar sofia ce ta katse su da cewa "oh ni ba'a ma ta tawa ko Amrish? Zeenat kaɗai kika gani shikenan bari na tafi," ta faɗi tana ƙoƙarin tashi cikin sauri Amrish tayi holding hands dinta tana cewa"am sorry kada ki tashi pls, in naga zeenat ina mantawa da komai ne,"   ɗaure fuska sofia tayi tace"i can't stay here,cos am getting jealous bazan iya jure yarda kike son Zeenat ba,   Dariya zeenat tayi tana cewa"in dai akan Soyayyata da amrish ne ke 6ata maki rai sai dae ki mutu,"     ta faɗi tana mayar da idonta akan sehrish da tayi zugudun tana kallon ikon Allah,   wuri Amrish tasamu ta zauna, kusa da sehrish suna facing ɗin su Sofia da zeenat,   ɗan kallonta amrish tayi tare da cewa"am sorry my friend nabarki da yunwa ko"? ta faɗi tana kallon Sehrish wadda jikinta ya gama mutuwa,   "A'a" ta bata amsa a takaice, Mayar da idonta tayi kansu zeenat tace"bansan zaku zo ba ae dana haɗo mana abincin tare,amma bari na tashi yanzu naje na ƙaro mana yadda zai ishe mu,"    cikin sauri zeenat tace"no ba sai kinje ba its ok ba mu jin yunwa a ƙoshe muke,"     murmushi amrish ta saki tare da kallon sehrish tace"bismillah mufara ci time ɗin komawa class ya kusa,"     Gaba daya hannunta kerma yakeyi a haka ta ɗauki spoon ɗin zata fara cin fried rice din da takawo masu shaqe da plate,tana ɗebowa shinkafar na zube wa saboda rashin natsuwar da take ciki ba don komai ba sai don zeenat data tsare ta da waɗannan manyan idanun nata zubin na karuwai a tsaitsaye suke ga eye lashes da tayi fixing sinsu kamar ɗiyar roba,   Ganin yarda hannun sehrish ke kerma ta kasa kai koda one spoon ne yasa Amrish ɗagowa ta kalli zeenat wadda ta zuba mata ido ko kyafta su bata yi,   ɗan gyaran murya Amrish tayi tare da cewa"Zeeta pls kidaina kallonta hakan na hana ta samun natsuwa,class mate ɗina ce jiya tafara zuwa school bata saba da kowa ba,"   ƙayataccen murmushi zeenat ta saki tare da cewa"its okey,ashe new comer ce, tayi mun kyau ne shiyasa nagaza janye idona akanta,ina fata kin sanar da ita komai game da zama cikin team ɗin mu?   Cikin sauri amrish tace"a'a pls mubar maganar nan,ita ba'a team ɗinmu take ba kawai class muka haɗa da ita,"    zeenat tace"that's impossible amrish tun da har kina yawo da ita a school dole ta zama ɗaya daga cikin mu,not only that yarinyar ta burgeni sosai........'kasa ƙarasa maganar tayi saboda ƙarar cokalin amrish data bugi gefen plate dinta dashi tace"Zeeenat! Nace kidaina wannan maganar agabanta bana so," rai a6ace tayi maganar sannan ta mayar da idonta kan sehrish tace"pls ki ci abincin ki,"   gyaɗa kai sehrish tayi tare da mayar da hankalinta akan abincin dake gabanta,ci take amma batasan inda abincin ke zuwa ba,saboda tsoro da ruɗin da ta shiga,   yunƙurawa su kayi su biyun atare suka miƙe, cikin sanyin murya amrish tace"Am sorry zeenat i don't mean to hurts u,just bana son muna wannan maganar agabanta ne,saboda batasan komai ba ko mutane batason shiga cikinsu," hankali atashe take maganar tana kallon su,   atare suka yatsina fuska sannan zeenat tace,kinsan bana fushi dake amrish shiyasa kike mun duk abunda kika ga dama,amma ina so ki sani 6ata mun rai tamkar 6atawa mommynki raine, kuma kinsan mai zo biyu baya ya zama dole kibi umarnin duk abunda nace, don haka wannan yarinyar dole tashiga team ɗin mu !!!   tana gama faɗin hakan taja hannun sofiya suka fuce daga lunch room din   ita dae sehrish zuru tayi tana kallon ikon Allah bayan sun fuce ta mayar da idonta kan amrish wadda jikinta yayi mugun sanyi tuni kuma idonta sun cicciko da kwalla, amma bata bari sun zubo mata ba, sai ma kallon sehrish da tayi tare da ƙaƙaro murmushi tace"ki ci gaba da cin abincin ki mana,naga kin tsaya,"   jiki asanyaye sehrish ta mayar da hankalinta kan abincin tana ci amma zuciyarta ajagule saboda halin da taga Amrish ta shiga akan waɗannan ƴan matan da suka zo,ko su wanene oho, Ta tambayi kanta, ***************************Twins Fitowarsu kenan daga wanka atare kamar yarda suka saba kwatsam sai ga haroon ya turo ƙopar ɗakin nasu fuskarshi ɗauke da wannan shu'umin murmushin nashi, tsayawa yayi yana binsu da wani irin kallo jikinshi na sanye da Crazy jeans tare da wata figaggar riga daya sanya, ya tada kwalar rigar tsaye,sam haroon baya kama da musulmai ko a fuska, balle ma daya kasance yana sanya chain a wuyan shi da kuma earrings irin yarda jigunannun ƴan iska ke sakawa,   Kallon juna su kayi atare kafin suka mayar da idanunsu akanshi,tuni ran Jahan ya 6aci ganin yarda yake bin jikinsu da kallo kamar wani tsohon maye, dama daga su sai short towels ajikinsu, farar surar ne mai jan hankali ta bayyana muraran,   ɗaure fuska jahan yayi tare da cewa "me ya kawo ka ɗakin mu? me kuma kake buƙata,indai kuɗi ne suna nan zamu baka,"    ta6e baki haroon yayi tare da yatsina fuska yace "yakamata kasan yarda zakayi magana dani with respect,ko don darajar wannan videon dake ajiye acikin wayata,'    tsuke fuska su kayi atare zuciyarsu na tafarfasa tamkar su rufe shi da bugu haka suke ji,    Cigaba da magana yayi "zuwa nayi don na ƙara tunasar daku, don na lura kamar kun manta da maganar dukiyata dake a wurinku, saboda waccan farin balbelen ɗan uwan naku da bai lfy na lura duk kun wani tashi hankali akanshi,'   Buga tsoki ayaan yayi yace "kada ka sake kiran shi da sunan balbela kadaina haɗa sunayen mu dana dabbobi domin kuwa mu bamuyin munayen ɗabi'un da za a haɗa sunan mu dana dabba, domin kuwa dabba yasan inda yake"    waro ido waje haroon yayi jin abunda ayaan yace a tsananin mamaki yace "Ayaan ni kake kira da sunan dabba"?! Ya tambaya a dan fusace   Cikin sauri jahan yace"kayi shiru ayaan kada kaja mana wani bala'en don na lura bai da Imani ko misƙala zarratin, tunda har bai damu da halin da ɗan uwansa ke ciki ba, burinsa kawai ya ƙuntata ma rayuwarmu," yayi maganar yana jefar haroon din da mugun kallo,   fashewa da dariya haroon yayi hada dafe cikinsa kafin yace "Waye kuma ɗan uwana? ae ni bana ɗaukarku jini na,ko ajinsi ku farare ne ni kuma baƙar fata ne, in fact ni bani da wata alaƙa daku, Uba fa kowa muka haɗa uwa kuma kowa da tashi, bayan shi kuma sai me?   shiru su kayi suna sauraron shi gaba ɗaya tsanarshi ƙara ninkuwa take yi acikin zuciyarsu,     juyawa yayi tare da cewa "Zan wuce ni ku huta lpy ƴan samari," yana faɗin hakan ya fuce yana sakin dariya kamar zautacce,   Mayar da ido ayaan yayi kan jahan yace "bro i ave an advise abt that bastard, why not mu kashe shi kawai kowa ya huta, cos i don't think ko mun bashi kuɗin zai goge videon,"    aɗan razane jahan ya kalle shi yace "ashe baka da hankali ayaan, kisa fa kace? Mu zamu kashe shi? In muka jefa kanmu cikin matsala fa? ya fadi yana kallon sa,    Ayaan yace "ba wata matsala jahan, just lettus kill him kowa ya huta !!!!!!!!!    "Mu bashi time in har muka bashi kuɗin bai goge videon ba, sai mu kashe shi kawai,don da abunda zai ta6a mutuncin family dinmu gwara abunda zai tada masu hankali na ɗan wani lokaci ya wuce" Acewar jahan,    Gaba daya sun amince da shawarar kashe haroon 😳 Duk mutanen da suka zo duba fawan duk sun ragu, har sun mai dashi daki sun kwantar dashi tun ɗazu,   Junaid kuwa lokacin da Abban su yashigo dashi ɗakin shi ya wuce dashi tare da kwantar dashi ya farfaɗo daga suman da yayi amma ya dasa da bacci,    Yanzu wanda suka rage a cikin gidan daga su matasan gidan sai abokin su sgr Shattima sun hallara a garden din gidan suna tattaunawa tare da marshal Omar dashi babban yayan,    Cg Abbas ya jima da tafiya amma yabar Amani a gidan saboda yace zai dawo da daddare ya ɗauke ta, duk ita ta taya azmee rarraba ma masu zuwa dubiya lemun a cups har suka lafa,    shigowa ɗakin Abbansu yayi yana kallon junaid dake baje asaman bed dinsa yana ta sharar bacci, ƙarasawa yayi wurin shi tare da zama daga gefen gadon nashi, sannan yaɗan sa hannun shi tare da bubbuga ƙafar junaid kamar mai jira aikuwa a firgice ya tashi zaune yana faman zazzare kyawawan idanun shi da suka canza launi saboda bacci, yana jin muryar abbansu ya kira sunan shi nan take ya fashe da wani sabon kukan yana cewa "Abba yaya fawan ! Yana ina ! meya faru dashi.....'  Murmushi abbansu yayi yana kallon shi yarda yake kuka yana magana red lips din nan nashi na shagwa6a66u sun tatta6e,    Cikin natsuwa abban nasu ya soma cewa "Calm down ur mind junaid,ɗan uwanka yana cikin ƙoshin lpy yanzu haka yana can medical room dinmu mun kwantar dashi, shima sai kiran sunanka yake yi yana cewa Abba ina junaid akawo mun shi in ganshi, inaso in ganshi,"    jin wannan maganar ta abban nasu yasa junaid dakatawa da yin kukan nashi ya zuro da ƙafarsa zai sauko daga saman gadon, abbansu ya ruko hannun shi tare da cewa "pls junaid kada kaje mashi kana wannan kukan saika tayar mashi da hankali yaga kamar mutuwa zaiyi,   Cikin sauri junaid yasanya tafin hannayenshi tare da share hawayen dake zubo masa sannan abban nasu ya saki hannun shi, jikin shi har rawa yake yi wurin saukowa daga gadon, bin shi da kallo abban yayi har cikin ranshi yana mamakin yarda junaid ke tsananin son ƴan uwanshi don ji yake yi da wani abu ya same su kwara shi ya same shi koda mutuwa ce,akwai wani lokaci da abbansu bazai ta6a mantawa ba in ya tuna abunda ya faru har dariya yake yi wani sa'in kuma yaji saukar hawaye, wannan ba kowane lokaci bane face lokacin da junaid yana da kananun shekaru, idan suka je masallaci tare dashi suke zuwa saiya bari an kammala salla an natsu liman na kora addu'a, sai shi kuma ya ɗaga hannayen shi sama ya ɗaga murya yana cewa "Ya Allah ya Allah kasa na riga Abbana mutuwa da ƴan uwana,ya Allah kafara ɗaukar raina kafin nasu," a lokacin kowa mamaki ya kama shi jin abunda ƙaramin yaron kecewa, har wasu ke tambayarshi dalilin dayasa yake son ya riga abban nasu mutuwa da yan uwan shi sai cewa yayi "Saboda idan na riga su mutuwa bazan ga tasu mutuwar ba in tazo,zuciyata zata samu salama akan na rasa su da raina," gaba daya mutanen dake a masallacin abun ya basu mamaki sosai, kuma ka'ida ne duk in suka je masallaci tare dashi dole liman ya jira shi ya kammala addu'o'in shi mutane na amsa mashi da ameen, kafin shi liman yayi tashi addu'ar saboda rigimarshi,   Murmushi abbansu ya saki lokacin daya kammala tunanin nashi aranshi yace "Allah yabar mana kai junaid,ni kuma banaso naga mutuwarka nafiso nariga kowannan ku mutuwa don bazan juri ganin gawar ɗaya daga cikinku ba a kan idona," jikin shi a kasalance yake wannan zancen zucin,   Wayarsa ce ta soma ringing daga cikin aljihun rigarsa ta yadi, cikin sauri ya zura hannu ya ɗauko ta tare da duba sunan mai kiran nasa sunan AMMI ne ya bayyana akan screen din wayar hakan na nufin mahaifiyarshi ce Ammi ke kiransa    Nan da nan ya shiga natsuwarshi tare da ɗaga kiran ya kara a kunnan shi ya zabga sallama,    daga can bangaren Ammi ta amsa mashi sallamar sannan tace"yaro na ya kake ya kuma jikokin nawa? Naji abunda ya faru da fawan shiyasa ma na kira don na tambayi ya jikin nashi,    Tamkar yana agabanta cikin biyayya ya soma magana "lpy lou ammi suna cikin ƙoshin lpy,amma ba zaki zo gida ki duba jikin nashi ba?   "Hmmmm ni me zanzo inyi agidanka? Ae yafi ƙarfi na, daga nan ma zan iya yi masa ya jiki ba sai na kwaso jiki nazo ba balle inga abun tashin hankali abun kunya,'    nan da nan fuskar Abban nasu ta canza jin abunda tace,    "Ammi dan Allah kidaina faɗin hakan bana jin daɗi saboda me zaki ce gidana yafi ƙarfinki bayan nikaina a ƙarƙashin ikonki nake ke fa kika haife ni, kuma wane irin abun tashin hankali da abun kunya kike magana akai"? yayi maganar fuskarshi a yamutse,   tsoki taja tamkar zata fasa screen din wayar sannan tace "babu wani iko da nake dashi akanka hussein! Tunda har ban isa nasaka abuba kayi, wato son ƴa'ƴa ya rufe maka ido ko? ka daina ganin kowa da gashi? ba yarda banyi dakai ba akan ka tattara ƴa'ƴan nan duka ka haɗasu ka aurar kaƙi jin maganata, ka tara ƙattan maza,garada acikin gida sai sinturi suke yi acikin gidan ka,kaine jagoransu kai Gwauro su kuma tazurai gasu nan jibga jigba dasu kaƙi aurar dasu, daga anyi magana sai kace baka son ka takura masu ko kace ba su isa suyi aure ba don ka rainawa mutane hankali, dukansu kaf babu wanda in aka aura masa mace bazai iya yi mata ciki ba hatta wancan shagwa6a66en daka sangarta.......'   runtse ido abbansu yayi tare da saurin cewa "Ammi dan Allah kidaina fadin hakan, aure fa lokaci ne kuma in yayi duk zan aurar dasu ne.....'    wani tsokin ta sake buga mashi kafin ta kuma cewa "haka kullum kake faɗamin, narasa meyasa ƴa'ƴana duk basu jin maganata,daga kai har azeeman da wancan fitsararren da yayi hijra yabar ƙasar batare da sani na ba, ban ta6a tunain hussein zaka yi mun haka ba saboda duk kafi yi mun biyayya acikinsu amma yanxunn. .....' kukan da ta fashe dashi ne ya yasa ta kasa ƙarasa maganar nan take hankalin abbansu ya tashi, muryarsa har rawa take yi wurin cewa"Ammi dan Allah kidainamun kuka, ke fa mahaifiyata ce saboda me zakiyi mun kuka, hakan zai iya jefa rayuwata cikin matsala,dan Allah kidaina na roƙe ki mommyna indai akan wannan maganar ne yasa kike mun kuka wlh ashirye nake da nayi maki biyayya koba da son ransu ba, zan aurar dasu ne kawai saboda farin cikin ki !!!!!   jin abunda yace ne yasa ta sassauta kukan nata tace "yaushe kenan zaka aiwatar da hakan? kasan natsufa sosai kada na mutu ba'ayi auran nan ba, dan Allah hussein ka tattarasu duka ka aurar a lokaci ɗaya in har kayi mun hakan zan shaida cewa kai hussein ɗinane dana haifa,'    Ajiyar zuciya abban nasu ya sauke yana kara gyara wayar a kunnan shi yace "Insha Allah ammi nan bada jimawa ba,amma ki ban time saboda yanzu muna cikin fargaba game da waɗanda suka kaima su fawan hari,kin san sunce fansa suke ɗauka,kuma babban tashin hankalin ma maca ce AVENGER ɗin,'   shiru ammi ta ɗanyi kafin tace "Shikenan hussein,nima na shiga damuwa dana ji hakan,dama nasan dole hakan ya faru saboda mahaifinku kafin yabar duniya ya tara maƙiya sosai kasancewarshi kwararren jami'en Soja sun halaka dubban masu tada ƙayar baya a ƙasar nan, shiyasa nake tunanin ko daga 6angarensa ne maƙiyan suke son ɗaukar fansa,duk da nasan cewa wannan mai shuɗin idon baya rasa maƙiya don mutun ne mai haɗarin gaske shima baya gajiya da kame ƴa'ƴan mutane yana kaisu lahira, kaga kuwa dole su ɗauki fansa suma,yakamata kasanya tsaro sosai agidanka, kuma akwai shawarwarin da nakeso na baka,"    Abba yace "Ammi dan Allah kixo gida mana,ina ga zaifi in kika zo sai mu zauna mu tattauna akan matsalar tunda wannan abun ya shafi zuri'armu, kuma nama fi jin cewa akaina abin zai ƙare tunda ni ne na tara ƴa'ƴa,"     Ammi tace "shikenan zan fidda lokaci nazo insha Allah, amma inaso ka sani in zanzo saina tattara ƴan matan family ɗinmu gaba ɗaya na kwaso su don suzo ayiwa ƴa'ƴanka baiko dasu,"    dariya kawai abba yayi yana sauraronta sun jima suna fira kafin daga bisani su kayi Sallama 😊   ya ajiye wayar gefen shi yana ɗan murmushi,    A can kuwa junaid na isa ɗakin da fawan yake kwance yana bacci, cike da tausayi yake kallon shi yadda yake jan numfashi da ƙarfi da ƙarfi,   ƙarasawa yayi tare da hayewa saman gadon yayi zaman cin tuwo tare da zabga uban tagumi yana kallon shi hawaye na zuba a fuskarshi,    Jin shessheƙar kukan junaid a kunnan shi yasa shi farkawa daga baccin da yake yi, ya buɗe idon shi a hankali yana kallon shi, yarda ya tallabe fuskarshi hannu bibbiyu ya tasa shi gaba yana sharar kwalla,a hankali fawan ya furta "junaid "   Kallon shi kawai junaid yake yana cigaba da matsar kwallo,hankalinsa ba ƙaramin tashi yayi ba ganin yarda jikin fawan yayi ruɗu ruɗu da bulali wurin yayi jawur ya faffashe duk da anyi masa dressing na wurin an shafa masa magunguna,ga kuma ɗinkin da akayi masa a chest ɗinshi,   dakyar ya daddage ya tashi daga zaune yana fuskantar junaid ɗin daya tasa shi gaba,     "Junaid," fawan ya sake ambaton sunan shi a karo na biyu ganin yarda ya zabga tagumi yana kallon shi hawaye na zubowa gefe da gefen fuskarshi, zama su kayi suna fuskantar juna, kallon shi kawai junaid keyi batare da yace uffan ba,   daƙyar fawan ya ƙaƙaro murmushi yana kallon shi, hannun shi yakai tare da shafa gefen fuskar junaid yace "bari nabaka wani labari ƙanina,"  junaid ya zuba mashi ido yana sauraron shi,   fawan yace "lokacin da waɗannan miyagun suka ɗauke ni ko, suka shiga dani wani ƙogon dutse mai rikitarwa, suka ban za6i biyu, su kashe ni ko su azabtar dani wanne nakeso, kasan me nace masu? ya fadi yana kallon shi, girgiza kai junaid yayi alamar a'a,   Fawan yaci gaba da cewa "a lokacin kai kawai ka faɗo mun araina, aranar da zamu tafi kai ta zabga kuka kana cewa babu inda zamuje ƙafarka ƙafarmu dakyar abba ya shawo kanka, ka tuna abunda ka faɗamun lokacin?   shiru junaid yayi yana tuna lokacin daya cakumi rigar fawan yana ce "ya fawan kayimun alƙawarin cewa zaka dawo araye inaso na sake ganin ka,' a lokacin fawan yace mashi "junaid ae tafiya ba mutuwa bace, insha Allah zan dawo araye in Allah ya yarda," murmushi junaid yayi tuna wannan   shima fawan murmushin yayi sannan yaci gaba da cewa "saina ce masu ni bana tsoran mutuwa, ban isa na hana kaina mutuwa ba in lokacina yayi, kamar yarda kuma baku isa ku hana kan ku mutuwa ba idan tazo maku, sai ɗaya daga cikin su yace mun "Ka za6i ka mutu kenan? mu kashe ka kawai? Saina girgiza kai nace "a'a ku azabtar dani kuyi mun duk irin hukuncin da zakuyi mun amma kubar ni da raina saboda akwai ƙaramin ƙanina da nayi ma alƙawarin cewa zandawo da raina, inaso na cika mashi wannan alƙawarin nasa na gani na araye, bana so na karya mashi zuciya nafiso ko mutuwarce ma to na mutu agabanshi yadai ganni da raina...............' dakatawa fawan yayi da maganar saboda hawayen da suka zuzzubo mashi, junaid kuwa tuni ya fashe da wani irin matsanancin kuka mai cin rai,  haɗe kansu su kayi wuri ɗaya suna faman shessheƙar kuka atare,   dakyar fawan yaci gaba da cewa "Shine suka bankamun kayan maye sannan suka ɗaure ni tamkar dabba, su ka dunga zuba mun bulali da kaca a jikina har saida suka ga jini na zuzzuba ajikina amma hakan bai ishe su ba, ba don su babban yayan mu sun zo ba to da tabbas kashe ni sukayi niyyar yi a lokacin, Amma alhamdlh naji daɗi sosai da Allah yacika mun burina na ganin na rayu don na cika maka alƙawarinka...... .. murmushi junaid ya saki tuni ya ji sanyi ya ratsa mashi zuciyarsa,   janye kansa yayi daga na fawan sannan yace "kana jin yunwa in kawo maka abinci"?    girgiza kai fawan yayi tare da cewa "junaid a ƙoshe nake,ɗazu azmee ta haɗamun kakkauran tea tare da fruits na sha,naji daɗin su sosai,"    "Bari nabarka ka huta sosai, na katse maka baccinka, amma ka sani zan dawo don atare zamu kwana," yayi maganar yana ƙara jaddada masa ayayin da yake sauka daga saman gadon,   Murmushi kawai fawan ke bin shi dashi harya fice daga ɗakin,komawa yayi a hankali ya kwantar da bayansa saman filonsa tare da lumshe idon shi,    Cikin sauri junaid ya fito tare da tunkarar hanyar fita saboda tunawa da sehrish wadda ke a school, lokacin tashin su yayi gashi time na salla na kokarin wuce shi, yana dab da fita daga ƙopar Amani ta kwada masa kira, dakatawa yayi tare da juyawa yana kallon ta da murmushi a fuskarsa, cikin sauri ta ƙaraso gab dashi tana cewa "ina zaka je ne? Junaid yace "inaso zance masallaci ne nayi sallah, daganan zan wuce na dauko sehrish daga school,"    ɗan jinjina kai tayi kafin tace "wannan yarinyar da muka gani ɗazu itace sehrish"? Ta tambaya tana kallon shi duk da tasan akanta yake magana   "Yeah itace," ya bata amsa atakaice tare da fucewa yana cewa "Sauri nake aunty amani time ɗin sallah zai wuce ni,"     Juyawa amani tayi tana jinjina kai, a ƙagare take da junaid ya dauko yarinyar daga school saboda tana son ta sake ganinta har ma ta yi magana da ita,  *wannan kenan*😍👍 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 ? ? ? *Boss Bature* Who's the AVENGER❗‼️⁉️ ************************** Har suka koma Class jikin sehrish a sanyaye ita kuma amrish fuskarta ta nuna alamun damuwa sosai game da abun da zeenat tace mata, gaba ɗayansu dae babu daɗi har suka taso daga school ɗin,tsayawa su kayi daga wajen school din sai ga drivern Amrish ya ƙaraso, juyawa tayi ta kalli sehrish tace"Ni zan wuce,sai mun haɗu gobe in Allah yakaimu,"   Jinjina kai sehrish tayi tare da cewa"Allah yakaimu lpy,"   "Ameen" ta amsa mata sannan ta wuce cikin motar,   ta jima a tsaye tana jiran ƙarasowar motar junaid dalilin dayasa bata hau bus ba kenan saboda tasan dole yazo ɗaukarta,masu motoci saiyi mata tayi suke don tazo su rage mata hanya amma taƙi yarda tahau motar kowa saboda tasan cewa ba kowa bane zai ɗauke ta don Allah ba, tana cikin wannan tsayuwar ta hango motar junaid ya shawo kwana,murmushi ta soma saki tamkar tayi tsalle don murna tunkan ya ƙaraso ta tunkari motar da sauri,   yana tsayar da motar ta sanya hannu ta buɗe motar sannan tashiga ciki tare da rufe motar,   juyawa tayi ta kalle shi tare da cewa "ka manta dani ko"? Ina ta faman jiranka,"    ɗan murmushi yayi yace "am sorry ba da son raina ba reesh, kina araina ynx ma daga mosque na wuto nan,' ya ƙarasa maganar yana kallonta, bin fuskarshi tayi da kallo alamun damuwa ta gani sosai atattare dashi,tuni itama taji zuciyarta babu daɗi, cikin sanyin murya tace "junaid kayi kuka yau ko? kuma kana cikin damuwa"?    jinjina mata kai yayi alamar eh,   ɗan 6ata fuska tayi tare da cewa "dan Allah junaid kadaina sa damuwa aranka wlh bana so, natsani naga mutun mai cike da farin ciki irinka a Yanayi na damuwa,'    A kasalance yace "don't worry ur self,zan daina ne reesh da zarar nasamu abunda nakeso, ki sani acikin addu'arki da kuma sauran ƴan uwana,'   "Insha Allah junaid bana mantawa da kowannan ku acikin addu'a ta," ta fadi tana jaddada masa maganarta,    "Yanzu kayi mun dariya in gani magana kona samu kwanciyar hankali,"   tunkan takarasa maganarta, ya wage bakinsa yana dariya,bin fararen haƙoransa tayi da kallo a jere tsaf suke tamkar mai tallar maclean saboda kyal ɗinsu, ga 2 dimples dinsa da suka lotsa sosai,   Yatsanta takai acikin dimple ɗinsa ta zura shi saboda burgetan da yayi, sun jima suna shiririta acikin motar kafin ya tayar da motar suka miƙi hanya, cike da nishaɗi suke sauraron waƙar da junaid ya kunna masu ta lilin baba,natsuwa yayi a hankali yake driving yana sauraron muryar rishi dinsa dake bin waƙar   "Kaine zuciya take ta yabo🎶kaine nawa in da rai da rabo, amanar zuciya ka damkeee, da kaine zanyi Wuff, zanyi wuff zanyi wuff🎶🎶   Fashewa da dariya junaid yayi saboda daɗin waƙar da yaji, sai yaji tamkar dashi take, musamman da tadinga nuna shi da hannu tana cewa(dakaine zanyi wuff)    Tana kai baitin ƙarshe shima ya ɗauka,    "Ke ce zuciya take ta yabo kece tawa inda rai da rabo,amanar zuciya ki damkeee, da kece zanyi wuffff !🎶    Zuba mashi ido sehrish tayi tana kallon shi, yana driving yana raira wakar kuma yana ɗan waiwayon ta,   gaba ɗaya sun shagala basuyi aune ba, suka ji wata mota a bayanzu ta bugi motarsu da karfin gaske,ƙarar da sehrish ta saki ne yasa junaid sakin sitiyarin motar gaba ɗaya, aikuwa nan take motar ta karkace ta nufi wata tamkekiyar bishiya da gudun gaske,   Waro ido sehrish tayi tare da cewa "Junaiiiid !! Innalallahi wa'inna ilaigirraji'un,   Ƙanƙame shi tayi ajikinta saboda gaba ɗaya yagama rikice wa, gaba ɗaya sun ƙanƙame juna, maimakon Sehrish ta taimaka mashi ya rike sitiyarin motar yayi control dinta, Amma saita janyoshi jikinta ta kankame suka bar motar Tana control din kanta,    Cikin ikon Allah motar ta kashe kanta adai dai bakin bishiyar ƙiris ya rage su gabje ta da ba ƙaramin buguwa zasu yi ba,    Ajiyar zuciya suka shiga sauke wa tare da dagowa atare suna kallon bishiyar, Allah ya takaita wahala da motar ta kashe,    Sai faman zazzare Ido suke Yi su duka biyun, sun ji kamshin mutuwa, juyawa Sehrish yayi tare dasa hannu ta zuge glass din motar Don taga wanene ya bugi motarsu,   wata bakar motace Mai black tunted kirar range Rover, Kamar jiranta suke ta leƙo,suma na cikin motar suka zuge nasu glass din motar,   Gabanta ne yayi mugun bugawa daraaam !! Ganin mutanen dake cikin motar, giggan Yan iska ba Imani a fuskarsu bakeke ne wulik, kana ganinsu kasancewa turo su akayi, da gangan suka bugi motar Junaid din,"   duk Tasha jinin jikinta, ɗaya daga cikinsu ne ya ɗago mata hannu tare da cewa"hi We're sorry guys mun bugi motarku batare da mun sani ba,kuyi mana afwa,amma yakamata kija masa kunne ya dinga kulawa wurin yin driving yana yin tukin ganganci, hakan zai iya halakar daku wata rana,"   Suna faɗin hakan suka ja motar tasu da gudun gaske suka bar wurin,   Ajiyar zuciya ta sauke tare da juyawa ta kalli junaid wanda yayi wuri wuri da ido, duk a tsorace yake da abunda ya faru dasu,    Murya asanyaye tace "junaid kayi sauri mubar wurin nan,"   daker ya iya tashin motar sannan yaja ta da baya baya suka baro jikin bishiyar, ya hau kan titi dasu sannan ya miƙi hanyar gidan,.     gaba ɗaya sehrish jikinta ya gama yin sanyi saboda ta hasko wani abu game da bugun motar junaid da sukayi,maganar da sukayi mata tamkar gargaɗi ne sukayi mata akan wani abu da zai faru dasu,tabbas tashiga ruɗani,   A hankai suka shiga babban entry din gidan, yayi parking motar sannan suka fito atare kowa na faman sauke ajiyar zuciya,atare suka jera suka nufi cikin gidan   ɗan kallon sehrish yayi ganin tamkar ranta ya 6aci don haka yace "am sorry rishi laifina ne,nayi ganganci dana kunna mana waka acikin mota har muka shagala sosai,"   fuskarta a yamutse tace "its not ur fault junaid, ba ka yi tuƙin ganganci ba,da gangan suka bugi motar mu,karka sama kanka damuwa ni bana ganin laifinka, Allah zai saka mana ma,"   tuni yaji sanyi ya ratsa ransa, bayan sun shiga babban falon ta wuce bedroom ɗinta, shima kuma ya wuce nasa ɗakin,    Shaf shaf ta tu6e uniform ɗinta,  asaman gadon tabarsu tare da school bag din duka, toilet ta fada tayi wanka tare da dauro alwala, tana fito wa ta bude wardrobe dinta tare da ciro wata gown mara nauyi ta zura, sannan ta shimfiɗa carpet ta zura hijab tare da kabbara sallah, anatse tayi sallarta, bayan ta kammala bata ko nemi abinci ba saboda taci tayi hani'an a school, gado kawai ta haye tare da baje wa tana bacci,   Shima junaid daya wuce nashi dakin nashi ya faɗa toilet ya yi wanka tare da canza kayan jikin shi izuwa riga da wando,    Yana kokarin fitowa daga ɗakin sai ga su twins sun faɗo ciki atare sun ɗau wankan jeans da t shirt,   Yana ganin su ya saki fara'a tunkan su fara magana yace "maganar kiran mommy ce ko"?   dariya su kayi atare, ayaan yace "ashe dae ka gane,Allah yasa bamu takura maka ba,"   girgiza kansa yayi tare da cewa"a'a yanzun nan zan kirata insha Allah,"   Jahan yace "yawwa masoyi junaid mai son farin cikin ƴan uwan shi,pls idan ka kirataa wayar,kayi mata biyayya kaji? kada kace zaka ƙi mata magana, ita mahaifiyarmu ce,idan bata son ɗaya daga cikin mu ae bazama ta ɗauki cikinmu ba balle har ta ruƙe sa na tsawon wata rana, kuma tayi naƙudar haihuwarsa,nasan kai mai ilmi ne junaid kasan hukuncin wanda ya sa6a ma iyayensa dan Allah ka manta da komai," yarda jahan ke yi masa nasiha cikin daɗin rai yasa shi jin sanyi aransa harma yaji cewa ya ƙosa ya kirata a wayar,    "Shikenan ya jahan da ya ayaan,zan kirata yanzun nan amma ba a gabanku zanyi wayar ba,idan nagama dae zan sanar daku duk yarda mukayi da ita,"   Cike da farin ciki suka ce "yawwa ɗan ƙanin mu, yanzun nan kuwa zamu fita daga ɗakin,sai mun ji ka," suna fadin hakan suka juya tare da fucewa daga ɗakin hada rufo masa ƙopar da kyau,   ɗan murmushi junaid yayi sannan ya koma gefen gadonsa ya zauna tare da kai hannu ya ɗauki wayarsa dake asaman side drawer,    Zuba ma screen ɗin ido yayi yana tunanin ta yarda zai fara kiran mommyn tasu, for the first time zaiji muryarta,a lokacin baya kusan kullum saita kirashi awaya bai ɗauka don ko saving na numbarta baiyi ba,saboda haushin ta da yake ji,    A hankali yashiga danna wayar, kai tsaye cikin messages yashiga saboda akwai last messages da ta tura mashi, buɗe sakon yayi ya ƙara karanta shi "Thanks 4 ignoring me, i won't call u again bye,"    tanan ya ɗauki number tare da danna mata kira, ta shiga ringing,   Almost 3 times tana ringing ba'a ɗauka ba,ana huɗunne yana ƙara kira tayi picking,shiru yayi baice komai ba,har sai da tashiga tambayar wanene jin anyi mata shiru, yanayin muryarta akasalance saboda bacci,     Cikin harshen spanish take tambayar wai wanene,   Sai a lokacin junaid ya ambaci sunan "Mommy," shiru tayi tana nazari don ta gano muryar wacece wannan acikin ƴa'ƴanta,bakowa bane ya faɗo mata aranta ba face Romeo ɗinta duk da basa waya amma abbansu na turo mata voice ɗinshi da yake mata recording aduk lokacin da suke fira dashi ko kuma lokacin da yake tsaka da shagwa6a,   tuna wannan yasa Alexandra cewa "Romeo ɗina ne"? Ta tambaye shi donta tabbar cewa shiɗinne da take hasashe,    Ashagwa6e yace "junaid ɗin abbana ne," Jin hakan yasa alexandra tashi daga kwancen da take asaman shimfiɗeɗen gadonta, cikin sauri takai hannu ta kunna bedside lamp, bedroom ɗin nata ya ɗanyi haske tamkar zata iya gashinin zahiran agabanta, cikin tsananin farin ciki tace "allah yasa ba mafarki nake ba,romeo da kan shi yau ya kira ni a waya, harya kirani da sunan mommyn shi, cikin tsantsar farin ciki take maganar, Duk junaid na sauraronta sai da takai aya sannan yace. "Mom ki ƙaddara cewa mafarkine, saboda bashi da banbanci da mafarkin cos i called u by force ba don son raina ba, ya faɗi with angry face tamkar yana agabanta,   murmushin takaici tayi kafin tace"na sani dama saka akai ka kira ni,koma manene laifina ne nasan fushi kake yi dani,baka sona romeo ni kuma nadamu dakai sosai.....' ta faɗi cikin muryar kuka,   "Mom ba ki sona,da ace kina sona da baki tafi kinbarni ba a lokacin da bansan komai ba soyayyarki kawai nake buƙata da kulawarki, amma duk wannan bai dame ki ba,kin tafi kinbar ɗan jinjiri ya yi rai ko kar yayi duk bai dame ki ba,kashe ni kika so kiyi............' Fashe mata da kuka yayi mai cin rai, nan da nan hankalinta ya tashi duk yadda taso ta lallashe shi ya daina kukan amma yaƙiya,janye wayar tayi daga kunnanta tare da zuba ma screen ɗin wayar ido tana sauraron kukan shi, har cikin ranta ba ƙaramin ɗaci ta ji ba, tama rasa ta yarda zata fahimtar dashi, Sai da junaid yayi mai isar shi sannan ya tsagaita yana faman sauke ajiyar zuciya,    Jin haka yasa tace "pls can i turn it to video call,cos i wanna see u face to face," Rai a6ace junaid yace "ban amince ba mommy,if u really want to see my face then come to nigeria,"   Murmushi taɗanyi sannan ta kuma cewa "ka yafe mun junaid ɗin abbansa,ba don bana sonka ba na tafi nabarka, nafi kowa sonka junaid saboda ni na haifeka,duk da nasan cewa a wurinka bancancanta na amsa sunan mahaifiya ba, amma inaso kaa sani nikaina ba'a son raina nabar ƴa'ƴana ba, bakowa bane ya son da wannan ba saboda ba kowane zai yarda dani ba, amma an takuramun an ƙuntatamun ko bacci bana iyayi a ƙarshe ma naji ƙasar gaba ɗaya tafita raina na dinga jin tamkar ƙona fatar jikina akeyi wannan shine dalilin dayasa nabar ƙasar, kai kuma abunda yasa ban tafi dakai ba shine, soyayyar da mahaifinka ke yi maka,idan na tafi dakai ya zai ji a zuciyar shi? shi kan shi bai fahimci hakan ba kowa tunaninsa na tafi don son raina ne amma ba haka bane junaid, akwai wani 6oyayyen lamari dake faruwa acikin gidan nan,nayi ƙoƙarin na fahimtar da abbanku saboda ni ina da masaniya akan wani abu, amma abbanku sai ya nuna mun cewa kawai don na tsani baƙar fata ne yasa nake zargin wasu,bayan ba haka bane ni duk wanda na tsana hakanan batare da wani dalili ba to yana da wata muguwar manufa ne... '   Shiru junaid yayi yana sauraronta, bai cika ɗaukar komai serious ba arayuwarshi amma maganar mommynsa taɗan ta6a shi kaɗan, bazai ce ƙarya take masa ba saboda shi kanshi ya jima yana tunanin dalilin dayasa mom ɗinsa tabarshi, saboda shi ya kasance yaron da kowa ke so mai farin jinin gaske, taya za'ace uwar da ta tsugunna ta haife shi, itace zata ƙisa ta guje shi just without any reason !? Idan ka samu kaɗan ka gode ma Allah gobe saiya baka mai yawa😁 Cikon page din ɗazu dama 3 page nace zan haɗe maku, sa'an nan ku gyara zama 😱😨 Ina guga ina editing gashi nan har na ƙona mata hijabi ynx jira nake tadawo inga mai zatayi mun😇🤣       Hafsat Bature           (Boss Lady) _💋Boss Bature💋_ Murmushi taɗanyi sannan ta kuma cewa "ka yafe mun junaid ɗin abbansa,ba don bana sonka ba na tafi nabarka, nafi kowa sonka junaid saboda ni na haifeka,duk da nasan cewa a wurinka bancancanta na amsa sunan mahaifiya ba, amma inaso kaa sani nikaina ba'a son raina nabar ƴa'ƴana ba, bakowa bane ya son da wannan ba saboda ba kowane zai yarda dani ba, amma an takuramun an ƙuntatamun ko bacci bana iyayi a ƙarshe ma naji ƙasar gaba ɗaya tafita raina na dinga jin tamkar ƙona fatar jikina akeyi wannan shine dalilin dayasa nabar ƙasar, kai kuma abunda yasa ban tafi dakai ba shine, soyayyar da mahaifinka ke yi maka,idan na tafi dakai ya zai ji a zuciyar shi? shi kan shi bai fahimci hakan ba kowa tunaninsa na tafi don son raina ne amma ba haka bane junaid, akwai wani 6oyayyen lamari dake faruwa acikin gidan nan,nayi ƙoƙarin na fahimtar da abbanku saboda ni ina da masaniya akan wani abu, amma abbanku sai ya nuna mun cewa kawai don na tsani baƙar fata ne yasa nake zargin wasu,bayan ba haka bane ni duk wanda na tsana hakanan batare da wani dalili ba to yana da wata muguwar manufa ne... '   Shiru junaid yayi yana sauraronta, bai cika ɗaukar komai serious ba arayuwarshi amma maganar mommynsa taɗan ta6a shi kaɗan, bazai ce ƙarya take masa ba saboda shi kanshi ya jima yana tunanin dalilin dayasa mom ɗinsa tabarshi, saboda shi ya kasance yaron da kowa ke so mai farin jinin gaske, taya za'ace uwar da ta tsugunna ta haife shi, itace zata ƙisa ta guje shi just without any reason !? ?   gaba ɗaya ya tafi duniyar tunanin ya amince da zancen mahaifiyar shi ko kuwa, shessheƙar kukanta daya ji ne yasa shi dawowa cikin hayyacinsa cikin sauri yace "its okey mom,ni banason nayi sanadin da zan zubar da hawayen wani,bare ke da kike mahaifiyata ma,"    Ajiyar zuciya alexandra tashiga saukewa jin kalamansa masu daɗin gaske, muryarshi ce tasake katse ta da cewa "pls wipe ur tears mom,"    Murmushi ta saki tamkar tana agabansa,hannu ɗaya tasa tana share hawayenta kamar yarda ya umarta tayi, ? . bayan ta gogesu tace "baka son ganin hawaye ne? amma meyasa baka amsa kirana duk in na kira wayarka, ko na kira wani nace ya baka muyi waya,a duk lokacin da hakan ta faru ina zubar da hawaye na sosai,   Murya asanyaye take magana, har cikin zuciyarshi yake jin maganar mommyn nashi,   "Mommy inaso zan aje waya,i wll call u next time, Cikin sauri tace "ka haramta mun ganin fuskarka ko? Shikenan my romeo,ka faɗi kome kake so zan maka shi"   "Komai nace kiyi zaki yi ne"? Ya tambaya yana jiran amsa   "zan yi maka shi koma menene,"   murmushi junaid yayi sannan yace"yaya ayaan da jahan suna son wani abu wurin ki, kiyi masu shi, sannan ki dawo gida ki bani kulawar da baki bani ba tun ina yaro,"    Murmushi tayi sannan tace"shi kaɗai kake so"?  Yace "eh,"     Jinjina kai tayi tare da cewa"duk abunda kace zanyi saboda in tabbatar maka da cewa ina tsananin ƙaunarka my romeo,sannan koda daga bayane kaga wani abu kana so ka sanar mun, zanyi maka koma menene shi indae acikin duniyar Nan yake, sun jima suna yin wayar daga bisani su kayi sallama, bayan ya ajiye wayar ya dinga jin wani irin sanyi na ratsa zuciyarshi ga wani irin kwanciyar hankali da yazo mashi yasan cewa duk saboda wayar da yayi da mom in shi ne yasamu wannan natsuwar, Sai wuraren ƙarfe 4'dai dai sehrish ta farka tana faman yin hamma, ba ƙaramin daɗin baccin taji ba,saukowa tayi daga saman gadon nata ta wuce toilet jim kaɗan tafito da alwalarta, hijab ta dauko ta zura a jikinta sannan ta kabbara sallah, tun tana cikin yin sallar taji ana knocing ƙopar ɗakin nata, don haka tana kammala shafa addu'a ta miƙe a hanzarce ta buɗe ƙopar,gabanta ne taji ya faɗi rass ganin matar nan ta ɗazu,murya na rawa tace "ina yini," murmushi Amani tayi tare da cewa "lpy ya kike,"? "Ina lpy," ta bata amsa ataƙaice, dan ta6e baki amani tayi kafin tace"naso ɗazu dana ganki da safe muyi magana amma naga kina cikin sauri ne zaki school," ta fadi a wayance   Sehrish tace"eh hakane," duk tarasa natsuwarta, tsoranta me take son ce mata, ?   Amani taci gaba da cewa"Tun yaushe kika fara aiki a gidan nan ne"? Saboda ni ban ta6a ganinki ba gsky,"   Sehrish tace"banjima da farawa ba,"   "Amma nayi mamamkin yarda shaƙuwa ta shiga tsakanin ki da mutanen gidan har abbansu ya mayar dake ɗiyarshi,kuma naga kina da kusanci ssae da junaid har yana ruƙe maki hannunki kamar wata ƙanwarsa, bayan matsayinki bai wuce na ƴar aiki ba," ɗagowa sehrish tayi a ɗan rikice tana kallonta jin abunda tace,    Murmushi amani ta kuma saki kafin tasanya hannu ta dafa kafaɗar sehrish tace"idan ba damuwa inaso in baki wata shawara wadda zata amfane ki, domin na lura kinason jefe kanki cikin hatsari, karfa ki ruɗa kan ki,".   Jinjina kai sehrish tayi tare da cewa"ina sauraronki," amani taci gaba da cewa"ki nisanta kanki daga kowa na cikin gidan nan,ka da ki bari wani ya so ki acikin matasan gidan nan,kuma kada ki kuskura ki bari zuciyarki ta faɗa tarkon son wani,idan da hali ma ki tsaya a iya matsayinki na ƴar aiki,zaki fi samun kwanciyar hankali,"   Tun da tasoma magana sehrish ke bin ta da kallo fuskarta ta nuna alamun rikicewa don sam batasan inda zancen matar ya dosa ba,   "Kada kice na cika ki da surutu,its just an advise in kinyi amfani da ita ke zata amfana,but if u don't hmmmmm u can even lost ur life........'  Wani irin bugu zuciyar sehrish taji saboda abunda amani tace, na cewa zata iya rasa rayuwarta, tuni jikinta ya shiga yin kerma alamomin tsoro sun bayyana a fuskarta, hankali atashe take cewa"meyasa kika ce haka?saboda me zan rasa rayuwa ta?don kawai naso wani ko wani ya so ni acikin gidan nan"? Ta tambaya tana kallon Amanin,    Kafin Amani tace wani abu, muryar Azmee ta katse mata hanzarinta da cewa"tsayuwar me kuke yi ne, ke da nace ki kira mun ita don tazo mu haɗu mu fara girkin da wuri"? Ta tambaya tana kallon Amani, . cikin sauri Amani ta dan basar tare da sakin fara'a a fuskarta tace"dama muna ɗan tattaunawa ne,kinsan bata sanni ba nima kuma haka, so ina gabatar mata dakaina ne don musan juna,"   Zuba mata ido sehrish tayi kawai baki asake tana kallonta,   Azmee tace"Hakan na da kyau, sehrish wannan matar yayanku ce Abbas sunanta AMANI,ina fata zaki saki jiki sosai da ita domin kuwa tana da mutunci sosai,   daƙer sehrish ta ƙaƙalo murmushi tace"Insha Allah aunty azmee,"    tayi maganar tana kallon Amanin ita ma kallonta takeyi har lokacin, Azmee ta lura da kallon kallon da suke yi don haka tace"Amani mu wuce kitchen,ke ma sehrish ki ajiye hijabin jikinki ki zo mufara aiki,"    Juya ciki sehrish tayi su kuma suka wuce kitchen ɗin, kanta ya gama ɗaurewa da maganganun da Amani ta gaya mata,amma duk da hakan ba tajin zuciyarta zata karaya saboda wasu ƴan kalamanta,hannu tasa tare da tu6e hijabin ta ajiye ta nan saman gadon, sannan ta ɗauko ɗan mayafinta cikin wardrobe tayi rolling ɗinsa,   A dai dai lokacin da ta fito daga ɗakin ta tunkari hanyar kitchen ɗin sai ga haroon ya fito daga part ɗinsu,sai da taji gabanta ya faɗi don ita yanzu kallon shaiɗan take yi mashi saboda ƙahone kawai babu akanshi,    Ƙarasowa yayi inda take suna facing ɗin juna yace"mutuniyar ba hello ba hi,laifin me nayi maki ne"? Yayi maganar yana ɗaga mata gira tare da kashe mata ido,   Tsuke fuska tayi tare da bi zata wuce cikin sauri yasha gabanta tare da ware hannayensa yace"daga kin ƙara motsowa zan rungume.........' kasa ƙarasa maganar yayi gabansa na faduwa ba don komai ba sai don ido biyun da su kayi da SGR wanda ke shigowa cikin babban falon su biyu ne tare da shattima suka shigo,banda omar wanda tun a masallaci suka rabu,   Cikin sauri haroon ya canza kalamansa da cewa"kin gane dole kisa tsoran Allah acikin zuciyarki idan kinason rayuwarki tayi kyau,amma in kika ce zaki biye ma ƙawayen banza zasu kaiki ne su baro ki," ya dage sai zuba yake yi mata,juyawa tayi don taga wanene ya shigo saboda ganin yarda haroon yabi ya susuce ya sauya magana,    hada ido su kayi da shi adai dai lokacin yana ƙoƙarin kawar da nashi idon daga na haroon,har cikin zuciyarta taji wani irin sanyi aranta dama da kewarshi tadawo gidan,ganin shattima na kallonta yasa tayi saurin cewa"ina yinin ku"? "Lafiyalou Alhmdllh ƴan mata," ya amsa mata fuskarshi asake,sannan suka wuce upstairs part dinshi,sam takasa janye idonta daga kallon Bayan sgr da takeyi ko kyaftawa ba tayi har suka 6ace ma ganinta,hakan ba ƙaramin fusata haroon yayi ba rai a6ace tace"Ke!!kina a gabana kuma kike kallon wani"?    ƴar dariya sehrish tayi kafin tace"Namiji nake kallo," tana faɗin hakan tabi ta gefenshi ta wuce izuwa kitchen,baki asake haroon ya tsaya yana huci jin abunda tace,aransa yace"lallai ma ƴar shilan can harni zata ce ma Namiji take kallo,hakan na nufin ni kallon ɗan daudu takeyi mun,zan yi maganinta ne! Watan fara shan uƙubarki yayi acikin gidan nan !!zan 6ata maki suna a wurin shi dama kowa na gidan nan"!!! Yana gama faɗin hakan ya gyaɗa kanshi yana sakin shu'umin murmushi ya fuce daga falon. Shiga kitchen din tayi ta same su har sun fara aikin girkin,sallama tayi masu suka ɗago suna kallonta atare, azmee tace"sannu da zuwa za'a fara aikin ne,"   Ɗaga kai tayi tare da cewa"eh amma inaso nafara kaima su babban yaya abunsha naga sun shigo tare da wani ynx," zuru amani tayi tana kallon ikon Allah,   Azmee tace"toh bari na haɗa maki tare da snacks ki kai masu,"    ɗan murmushi sehrish ta saki tana jiranta duk in ta ɗago sai sun haɗa ido da Amani,sai tayi saurin kawar da idonta,   Bayan azmee ta kammala haɗa mata two cups na coffee a saman tray tare da plate mai ɗauke da snacks ta miƙa mata,kar6a sehrish tayi ta rike da kyau a hannunta sannan ta juya ta fuce daga kitchen ɗin tana faman sauke ajiyar zuciya,     Wuce wa tayi upstairs tayi a bakin falon ta tsaya tare da yin sallama,muryar wannan abokin nan nasa taji ya amsa mata da cewa"wa'alaikum salam," sai da ta dai dai ta natsuwarta sannan tashiga ciki gaban ta na faɗuwa kamar kullum,    Shattima ne kawai ta samu zaune saman 3 seater yana danna wayarshi,  Ƙarasawa tayi tare da ajiye tray din saman table din gabansa,maimakon ta tafi saita tsaya tana faman wasa da yatsun hannunta burinta kawai taga sanyin idaniyarta tasan cewa zai fito shiyasa ta tsaya,   Hannu shattima yasa ya ɗauki cup of coffee din yakai bakinsa yana kurba da alama ba ƙaramin daɗi yayi masa ba,sam takasa tafiya saboda bata ga sgr ba,ganin tayi masa tsaye yasa shi jinkirtawa da shan coffee ɗin da yake yi yace"Ya sunanki ne"? firgit ta ɗanyi tare da kallon shi tace"Sehrish," jinjina kan shi yayi kafin ya ƙara cewa wani abu sai ga Sgr ya fito sanye da short ajikinshi tare da singlet,nan da nan sehrish ta shiga natsuwarta, wuri ya samu ya zaune gefen shattima, cikin sauri ta ɗauki cup ta miƙa masa hannu yasa tare da kar6a yana dan sipping dinshi a hankali,   Mayar da idon shi yayi kan sgr yace"wannan fa ban ta6a ganinta ba is she ur sister? Ya tambaya yana kallon shi,   "U can ask her," ya faɗi batare da ya dago ya kalle shi ba, murmushi shattima yayi tare da mayar da idon shi kan sehrish yace"kina da connection dasu ne,ko yar wurin Aunt dinsu ce ko uncle dinsu"?   ɗaga mashi kai tayi alamar"eh" sunnar da kai tayi cikin jin kunyar ƙaryar da tayi,   Shattima ya kuma cewa"amma Abba yayi maki miji kuwa"? ɗagowa tayi tare da dan zare ido saboda jin abun yace mata,mamakin ta yadda yake ta tambayarta bayan sam ko a fuska baiyi kama da mai son surutu ba shima,    girgixa kai ta kuma yi tare da cewa"a'a bai mun ba"  "Because of what?ko babu wanda kike so acikin matasan gidan nan"? maimakon ta bashi amsa sai ta ɗan saci kallon Sgr dake kur6ar coffee din hannun shi,   Wani irin murmushi shattima ya saki saboda yaga inda sehrish take kallo, acikinsa ransa yace"hmmmm dama nasani,"   A fili kuma yace"yana da kyau ko'? A firgice sehrish ta mayar da idonta kan shattima tace"Wa"? da ido yayi mata nuni da Sgr, sunnar da kai tayi tana murmushi tace"eh,"    "Shi bai yarda da mace ba,yace mata matsala ne arayuwar namiji,but i want to ask u something a misali mace ta samu righteous husband kamar wannan lu'u lu'un,wanda ya haɗa komai ga kyau ga ilmi ga dukiya, kina tunanin akwai macen da zata yi gangancin Mallakarsa har ta zama matsala arayuwarshi balle ta 6ata mashi rai"?    jikin sehrish tuni ya soma kerma saboda tsoran dogon sharhin da abokin sgr ɗin ke yi mata,babban tashin hankalin ma gashi a kusa duk da yayi tamkar baya jinsu,ammma ae kunnan shi a buɗe suke ba'a toshe ba dole ne yaji abunda suke cewa,muryarta na rawa ta buɗe baki zatayi magana kenan kwatsam taji wannan sanyayyiyar muryar tashi tace"ba kowace mace bace zata so ni dan Allah in fact duk macen da zata soni sai don waɗannan abubuwan daka lissafa," yayi mgnar again batare da ya kalle su ba, sai ma hannun shi daya zura cikin short pocket dinsa ya ciro wayarsa dake ringing tare da yin picking ya kara a kunnan shi yana magana cikin harshen turanci,   gaba ɗaya jikin sehrish yayi mugun sanyi kalamansa akwai ƙamshin gsky acikinsu,yanzu ta ƙara gane dalilin dayasa mace sam bata agabanshi,saboda yasan cewa duk wadda zata so shi,ba zata so shi dan Allah ba face sai don wani abu daya mallaka,kamar wannan kyakkyawar surar tashi mai matuƙar jan hankali,da dukiyarsa kuma,  ga kuma ilmi duka dai😇 Amma har ga Allah ita ba don dukkan waɗannan abubuwan ba take son shi ba,ataƙaice ma tunkan taga fuskarshi tunkan tasan koshi wanene ta afka ma tarkon son shi ta hanyar sunan shi kawai da taji suna faɗi BABBAN YAYA,   gaba ɗaya ta tafi zurfin tunani muryar shattima ta dawo da ita daga dogon tunanin nata da cewa"dagaske ne abunda ya faɗa"? ya tambaye ta yana jiran amsa,ba komai yasa shattima sakin jiki da sehrish ba face tun da yaga yarinyar da suka shigo ta gaishe shi da ya kalle ta ba fuskar kowa ya gani ba a fuskarta ba face fuskar SGR bi ma'ana sun dace sosai,saboda tunda yake arayuwarshi bai ta6a ganin yarinyar da ta dace da Sgr ba face wannan yar matashiyar duk da ya lura cewa kamar tayi masa ƙanƙanta,yarinya ce ssae amma kuma tana da duk wani abu da namiji zai buƙata ajikin ƴa mace,🥱   A hankali sehrish ta buɗe bakinta tare da cewa"hakane gskya ya faɗi....." daƙer takai ƙarasa maganarta, cikin sauri tace"kuna buƙatar wani abu"? shiru shattima ya ɗanyi saboda ya lura da chanjin da yarinyar tayi,kuma yasan saboda kalaman sgr ne,may be tana son shi ne da alama, ya faɗi aranshi a fili kuma yace"just its okey zaki iya tafiya,mun gode da wannan,"    Murmushi ta ɗanyi sannan ta juya da sauri saboda kukan daya ciyo ta har takai bakin ƙopa ta ɗan juyo tana kallon shi, anatse yake yin wayarshi ya jingina bayansa ajikin kujerar,sa kai tayi ta fuce wuri tasamu anan upstairs ɗin ta zuƙunna ta cigaba da shan kukanta jikinta har rawa yake yi,tuni eyes dinta sun canza launi, fuskarta ta tur6une saboda kuka sai faman murzar hancinta takeyi kamar zata 6alle shi,sam ta manta da aikin dake gare su a kitchen su azmee nacan da amani sun taƙarƙare suna ta aikace aikace ba sehrish, gashi Amani sai faman tambayar azmee take yi na cewa har yanzu yarinyar bata dawo ba daga kai ma Sgr coffee,ko mai ta tsaya yi? Ita dae azmee bata ce komai ba, da tacika ta da tambayar ne tace"may be shi ya tsare ta,kinsan ita ke kula da apartment dinsa, Jin hakan ba ƙaramin tayarwa Amani hankali yayi ba,daure wa kawai take yi tana aikin,    Hawansa kenan upstairs ɗin ya miƙi hanya yana cikin tafiya yaji shessheƙar kukan ƴar mace,mamaki ne ya kama abbansu ganin yarinyar zukunne ta takure kanta sai faman matse hanci take yi tana kuka,tuni hankalinshi ya tashi ƙarasawa yayi inda sehrish take zukunne,a firgice ta miƙe tsaye lokacin da tayi arba da Abban nasu sam bata lura dashi ba sai da taji takon takalminsa na tunkarota,    lokaci guda ta rikice duk ta susuce tsoranta mai zata sanar mashi in ya tambayeta dalilin yin kukan nata,   Ko da ya isa dab da ita sai ya tsaya yana ɗan nazarin fuskarta,tsananin tausayin yarinyar ne ya kama shi,dama ita mace abun tausayi ce musamman in ta kasance ba'a gaban iyayenta ba,babu kowa nata a kusa da ita da zai lallashe ta ya kuma janyo ta jikin shi don jin damuwarta,ya mayar da ita yar shi amma kuma bai da isasshen lokacin jin abunda takeso ko me ke damunta,    Sunnar da kai sehrish tayi ƙasa murya na rawa tace"ina yini abba,"   bai amsa mata gaisuwarta ba sai cewa yayi"meya faru ne naga kina kuka? cikin en ina tace"babu komai," hannun shi yakai gefen fuskarta yace"ko da zaki yi ma kowa ƙarya,kada kice zaki yi ma abbanki,ga hawaye nan nagani suna zuba a idonki,kawai dai bakya son faɗamun ne," shiru tayi bata ce komai ba tana faman wasa da yatsun hannunta,   Murmushi yayi ganin tana ɗan satar kallon shi kamar wata mara gaskiya,   Cikin zolaya yace"faɗa mun gaskiya kodai aure kikeso ne?kin rasa wa zaki faɗamawa shine kika la6e anan kina kuka ko"? ɗagowa sehrish tayi taɗan zare ido can kuma ta fashe da dariya gaba ɗaya, shima dariyar yayi dama yayi hakan ne don yasata farin ciki yasan mata daga anyi masu maganar aure sai jin kunya da dariya,   ganin haka yasa shi ƙara cewa"hmmmmm dama nasani,mu aje wannan maganar a gefe nasan cewa akwai wanda kike so acikin ƴa'ƴana don na iya haihuwa gasu nan tubarkalla masha Allah ƴan mata sai rububi sukeyi hada masu kirana awaya duk safiyar Allah suna gaishe ni wai nan suna yi ma kansu ko ƴa'ƴansu kamun ƙafa,ni kuma har yanzu basu kwanta mun araina ba,Amma ke ɗin nan ko ta dabance in har kinaso in baki ɗaya daga cikinsu dole kema ki fara kamun ƙafa daga yanxu,"  Magana yake a natse sehrish kuwa ta kasa kunne tana sauraron shi,mamaki ya gama kamata yarda Abban nasu sukutun da guda yake fira da ita lallai ba ƙaramin wayayyen mutun bane,   bayan yakai ƙarshen maganar tashi tace"amma Abba,ni bansan yarda ake yin kamun ƙafar ba," ta faɗi cikin jin kunya,   dariya yayi tabi shi da kallo sai taga ya koma mata junaid saboda tsananin kamanceceniyar dake a tsakaninsu don dai shi fuskarshi akwai manyantaka, Bayan ya tsagaita da dariyar yace"kina nufin baki san yarda ake kamun ƙafa ba in mutun nasan abu,to ki tambayi AZMEE ta faɗa maki zata koya maki,   Jinjina kai tayi tare da cewa"insha Allah zan tambayeta,"   Murmushi yayi kafin yace"daga ynx zan fara zuba ido in ga yadda zaki fara kamun ƙafar naki,idan kinyi abu mai kyau sai na duba na gani wanne ya dace acikinsu na baki,idan marks ɗinki yakai matakin A1 to zan aura maki ɗaya daga cikin manyan ne, idan kuma Credit kika samu zan haɗaki da ɗaya daga cikin youngers ɗinsu,amma fa ki sani idan marks ɗinki yazo da matsayin(f)to zan aura maki Haroon ne........... " dariyar da sehrish ta fashe da ita ne ya hana shi ƙarasa maganar, zuba mata ido yayi yana kallonta sai ya dinga ganin kamanceceniyar fuskarsu da ta yarinyar sam yarasa gane dawa take masa kama nan da nan kan shi ya ɗaure yashiga mamakin kamannin daya gani kodae idonshi ne ke nuna mashi hakan tabbas fuskarta tayi tamkar photocopy ɗin fuskar ƙanwarsa AZEEMA,   daker sehrish ta tsagaita da dariyar tace"Abba zan tafi kitchen nabarsu suna aiki,"    Murmushi yayi tare da cewa"hakan nada kyau,kwara tun ynx ki koyi girkin shima yana daya daga cikin jarabawar da zan maki don bazan aura ma ƴa'ƴana macen da bata iya girki ba,then idan nasamu free time zan wa junaid magana ya kira mun ke don mu ƙara tattaunawa,"   Amsa mashi tayi fuskarta cike da annashuwa tabi ta gefenshi tana faman sakin murmushi ba don komai ba sai don maganar Abban nasu dayace idan marking ta F9 ne zai aura mata haroon hakan na nufin shi kanshi yasan cewa haroon cikon bencin gidan ne 🤣😂😅   Har juyawa abban nasu yayi yana kallonta a lokacin tayi nisa wurin sauka daga stairs ɗin,ajiyar zuciya ya saki saboda ganin farin ciki a fuskar yarinyar, dama yayi hakan ne don ya mantar da ita damuwar da ta shiga har ta la6e tana kuka,kama hanya yayi ya wuce,dama bedroom ɗin junaid ya nufa, *************************** Tun ɗazu da suka kammala lunch ɗinsu after Azhar hossana da Camila suka koma bedroom din saman katafaren gadon suka baje suna bacci abun ba'a magana,ita kuwa jahad sam tagaza yin bacci tun  da tayi sallar la'asar tafito daga ɗakin ta tsaya a falon tana zagaye, bakomai take burin gani ba face Ya Omar dinsu ko zafin ciwon ƙafarta yanzu tadaina ji,har wurin ƙarfe biyar da wani abu tana wannan safa da marwar in betwn seater's ɗin dake a palourn,tana cikin wannan zagayen MARSHAL OMAR ya shigo falon da sallamar shi, sam bata ji shi ba saboda ta juya masa baya tamiƙi hanya tana tafiya,   Murmushi ya saki ya tsaya yana tunanin wacece acikinsu jahad ko hossana,koma dae wacece ba ƙaramin kyau tayi masa ba acikin kayan,yaji daɗin hakan saboda dama burinshi ya gansu cikin jin daɗi da walwala,ganin bata da alamar juyowa yasa shi yin gyaran murya da ɗan ƙarfi, cikin sauri jahad ta juyo tana faman zare ido don batayi tsammanin ganin mutun ba,nan da nan wani irin farin ciki ya mamaye fuskarta da karfi ta furta"Ya Omar," lumshe idonshi yayi tare da buɗe su yana murmushi,   Watsa wa tayi da gudu tamkar zata rungume shi,sai da taje dab dashi sannan taci burki tana dariya,yana ganin hakan ya gane cewa Jahad ce,don da ace hossana ce sai tayi hugging dinshi,   "Fatan na same ku lafiya"? Ya furta yana kallonta,fuskarta awashe tace"Alhmdllh ya omar,dama tun ɗazu nake jiran zuwan ka, ashe zaka zo da har na fidda rai,    Omar yace"naso nazo ɗazu to bansamu hali ba,shiyasa na aiko maku da major don ya ɗauko ku,ina fata gidan yayi maku?   "ya omar ni nama rasa da wasu kalmomi zanyi amfani dasu wurin yi maka godiya Allah.........."tuni idanunta sun cicciko da kwalla sun soma gangarowa daga cikin idanunta,   Cikin sauri yace"Why jahad?me yasa zakiyi mun kuka bayan kinsan bana son ganin hawayen ku,sannan bana son godiya kada na sake ji,duk wani abu da nayi maku nayi shi ne don Allah,kuma haƙƙin ku ne dake akaina har yanzu ma ni ji nake kamar akwai sauran abubuwan da banyi maku ba, ..kallon shi kawai take yi yana bayani har yanzu tana mamakin kyakkyawar zuciya irinta Marshal omar, Cikin shessheƙar kuka tace"ya omar kai wane irin mutun ne?narasa dame zan fasalta ka,kyawawan ɗabi'unka da halayenka da kyakkyawar zuciya irin taka bana tunanin a doran duniyar nan za'a samu mai irinsu,koda za'a samu sai anci baƙar wahala kuma cikin kashi 100 bai wuci asamu kashi biyu ba,kai na musamman Ne ya omar,ina taya iyayenka farin ciki sosai da samun ɗa kamarka,saboda kai abun alfahari ne........ni bansan da me zamu saka maka ba ya omar,ka bamu kyakkyawar rayuwa ka cire mu daga ƙangin rayuwar da muke ci,a lokacin da muke tunanin cewa kowa ya tsanemu bai son mu mutuwa ma kawai muke jira,sai gashi Allah ya haɗamu dakai,tun a lokacin nasan cewa kai kyauta ne daga Allah...........   tun da jahad ta soma kora jawabi ya goya hanneyen shi a faffaɗan kirjinshi ya natsuwa yana sauraronta fuskarshi ɗauke da murmushi,saboda kalamanta ba ƙaramin shigarshi su kayi ba yadda take magana a natse ga wata irin murya dake gareta mai sanyin gaske irin muryar da duk 6acin ran da kake ciki in. Ka ji ta sai ka manta dashi,ae jahad akwai natsuwa ga tawakkali nima na shaida hakan 😘 "Ya omar ka faɗamun dame zamu saka maka?nasan ma babu Ba mu da abunda zamu iya saka maka aduniyar nan face addu'a itace kawai ke gare mu,i will keep pryaing 4 u ya omar hada family ɗinka duka zan saku a addu'ata till the end of my life bazan manta ba aduk lokacin da nayi sallah ko nayi karatun alkur'ani har night prayers ma zan dinga tashi inayi just because u ya omar and ur family,   ta ƙarasa maganar tana faman sauke ajiyar zuciya har lokacin hawayen fuskarta basu tsaya da kwarara ba,   Hannu omar yasa tare da zaro handkerchief ɗinsa dake front pocket dinsa dake a t shirt din jikinshi,   Da hannun shi yasa yana wiping tears dinta a hankali,runtse idonta tayi tana jin wani irin yanayi mara misaltuwa a tattare da ita,   Muryarshi ce ta tsinkaye ta da cewa"jahad ngde ssae kalamanki kawai da kikayi mun a yanzu ma sun wadatar dani,sannan idan kuna so ku saka mun abunda nakeso shine koda nan gaba kada ku juyamun baya bana son ku canzamin inaso ku tsaya a yarda nasan ku,ina tsananin ƙaunarku sosai bana son abunda zai raba ni daku,inason zumunci ya ɗaure a tsakanina daku daganan har can...... katse shi tayi da cewa"har ina kenan ya omar,"   Cikin zolaya yace"gidan Aljanna mana," dariya tayi sosai kafin ta tsagaita da dariyar tace"insha Allah ya omar ba zamu ta6a baka kunya ba,zamu kasance kamar yarda kakeso,"   Jinjina kansa yayi sannan yace"where's my hossana banganta ba,ko tana ciki ne? Ya yi nuni da hannun shi,   Jahad tace"hossana suna ciki tare da wannan nurse camila din sai sharar bacci suke yi tun ɗazu,"   Murmushi yayi tare da cewa"naso na ganta,"   Cikin sauri tace"ya omar ka shigo daga ciki mana ka zauna na kira maka ita don itama hossana a ƙagare take data ganka,"   Omar yace"sauri nake na koma gida yanxu,ki gaishe mun da ita dae,ko kuma zan kira wayane ae akwai telephone sai mu gaisa," jinjina kai tayi tare da cewa"shikenan zan sanar mata,amma nasan zatayi kuka in taji cewa kazo kuma ka tafi bata ganka ba,    juyawa yayi yana faman sakin murmushi har ya kusa fita daga falon tace "ya omar," juyowa ya kuma yi yana kallonta,    "Tun jiya inata so in kazo inyi maka ya mai jiki,abun yana araina ɗan uwanka daka sanar mun cewa bai lpy,"    Omar yace"oh fawan da sauƙi jikin shi sosai,kada ki damu zan bashi waya inyaji sauki ssae sai kiyi mashi ya jiki,"   Jinjina kanta tayi alamar toh daga nan sukayi sallama ya fuce daga falon,   Ajiyar zuciya ta saki tare da wuce wa ciki fuskarta asake 😇 ****AUNTY BABBA****** 💋Boss Bature💋_ ********AUNTY BABBA************ Zaune take agaban dressing mirror ranta a matuƙar 6ace fuskar nan tayi jawur saboda kukan da taci,ta zabga uban tagumi zuciyarta sai faman tafarfasa take yi,bakomai bane ya haddasa mata wannan 6acin ran ba face General ishaq daya hanata zuwa abuja,duk yarda ta kwallafa rai akan zuwa abujan ya hanata,sai da ya bari tasha wankanta ta kimtsa cikin leshi ta yafa mayafi ta ruƙo jakarta, tana fitowa ta same shi zaune a falo jikin shi sanye da gajeran wando baki,wani irin kallo yabi ta dashi tare da cewa"Ina zuwa," washe masa baki tayi tare da cewa"Abuja mana,kai fa kace zamuje duba jikin fawan," kai tsaye yace"ae nafasa wannan,ni kaɗai zanje inyaso ko a waya ne kun kira Abba kuyi masu Allah kyauta," Tur6une fuska tayi tare da cewa"dan Allah idan wasa kake mun ka daina," ?   Shima ya tamke fuskarshi yace"ba wasa nake ba,ni kaɗai zanje inyaso saina wakilce ku,"   Hankali tashe tace"Haba Abban hafsat sai da na kammala shirina, tafiya kawai ta rage zaka ce wai an fasa gaskiya ni sai naje," ta faɗi tare da ruƙe qugunta tamkar zata buge shi,   Miƙewa ishaq yayi fuskarshi ba wasa yace"to ki sani muddin kikasa ƙafarki kika bar gidan nan without my permission hmmmmmm ke kinsan mai zai biyo baya,    Yana faɗin hakan ya fuce ma daga falon yabarta,   da gudu ta koma bedroom ɗinta a ƙasa ma tayi wurgi da handbag ɗinta saman gado ta faɗa tadinga shan kukan baƙin ciki har bacci ya kwashe ta, Ta jima tana baccin kafin ta tashi cike da kunci ta koma gaban mirror ta zabga tagumi rai a6ace, Download>>> Dangin Rabi Complete Document Ta jima tana tunanin meyasa general ishaq ya hanata zuwa gidansu don ta duba jikin fawan,abun ya ɗaure mata kai saboda shi da kansa yace zasu je dubiya atare amma ya canza ra'ayinsa yanzu,    tsoki ta buga tare da kai hannu ta ɗauki wayarta dake agaban mirror ɗin,contact ɗinta ta shiga ta lalubo numbar wayar HAYAAM ta danna mata kira,ringing ta shiga yi kusan sau uku ba'a ɗaga ba, tana a cikin toilet kiran ya shigo a lokacin wayar na hannun wani matashin saurayi dake zaune saman wani haɗaɗɗen gado, daga shi sai shorts ajikin shi ya baje abun shi, ganin sunan Aunty Layla ya bayyana akan screen ɗin wayar yasa shi ɗaga murya tare da cewa"babe!babe!ur phone is ringing,   Daga cikin toilet ɗin tace"wanene ke kirana?in dae mommy ce ko Abi ka kashe wayar gaba ɗaya bana son takura,   "No basu bane,wannan auntyn naki ne Layla," Jin sunan Aunty laila yasa ta yin wuff ta fito daga cikin toilet ɗin, doguwa ce sosai fara sol babu ko tabo ajikinta kai kana ganin fatar nan zakasan cewa ba ƙaramin kuɗi take kashe mata ba saboda yarda take ɗaukar ido, ta ko'ina Allah ya bata ga dogon wuya, Bin ta da kallo saurayin yayi sam yagaza janye idonshi akanta sai kace batare suke rayuwa acikin gidan ba, Towel ne kawai ta ɗauro ajikinta cikin hanzari ta miƙa hannunta tare da kar6ar wayar tana cewa"nashiga ukuna Aunty laila kuma a awaya?yanzu zata rufe ni da faɗan ba gyara ba dalili mtswwwwww ?   Ta ƙarasa maganar tare da ɗaga kiran ta kara a kunnanta tana faman zazzare manyan idanunta, A ƙule aunty babba tace"ina kika je ne inata faman kira ba'a ɗagawa? Cikin en ina tace"Nashiga toilet ne yanzu na fito na sami wayar tana ringing asaman gado, aunty babba tace"hmmmm kina a gida ko kina awaurin yawon gantalin naki? Cikin sauri tace"am....ina a gida......" bata bari ta ƙarasa ba a tsawace tace"Karki kuskura kiyimun karya Hayaam ina sane da duk wani yawon gantali da kikeyi ana sanar mun da komai,saboda tsabagen iya shege da fitsara idonki ya buɗe wuyanki ya isa yanka hada tattara kaya da komawa gidan saurayi da zama koba haka akai ba? Ta tambaya azafafe tamkar tana a gabanta,tuni ran Hayaam ya 6aci juyawa ta ɗanyi ta kalli Sofwan dake kallonta bai sauraron me suke cewa amma ya lura da yanayin fuskarta daya canza saboda hayaam bata iya 6oye 6acin ranta duk mun ƙanƙantarsa,   sassauta muryarta tayi tare da cewa"Aunty layla mgnr da kika faɗa gaskiya ne,i can't hide it 4 u ni bazan iya rayuwa a cikin gidan nan ba saboda baida marar raba da kwango a wurina,fentin gidan duk ya ƙoƙe kamar munfi kowa talauci a layinmu,bama wannan ba ɗakinmu bai da banbanci da kwankon ashana katifa ce kawai duk ta gwaigwaye sai akwatin kayan mu, ko na fidda kuɗi na siyi furnitures mommy bata barin komai sai dae kawai nadawo na taras ta siyar da komai ta hanani jin daɗin rayuwa kuma kinsan ni macace mai son rayuwar hutu rayuwar ƴanci wannan shine dalilin dayasa nabar masu gidan don wlh ko abincin da suke ci ynx 6ata mun ciki yake yi saboda wannan yarinyar ƙanwar Amani ita suke ba girkin gidan,yarinyar da bata wuci 14years duk wani aiki na gidan ita take yin shi har yanzu mommy bata haƙura ba akan ɗaukar fansar abunda mommynsu tayi mata" yadda take magana kaɗai ya isa ya tabbatar maka da cewa ba ƙaramar ƴar duniya bace magana take tana faman wurga ido tana kora jawabi  Jinjina kai aunty babba tayi tare da cewa"ae ni tayimun dai dai,wato wayewa tasa kin manta da irin azabtarwar da matar nan tayi mana shine har kike ganin laifin mommynmu,kwara su kashe yarinyar ma kowa ya huta ae ni nafison su wulaƙantata," ta fadi tana faman huci kamar tana agabanta, Download>>> Yaro Ne Complete Document Ganin wayar tasu ba mai ƙarewa bace yasa Sofwan tasowa daga saman bed dinsa ya sauko, takawa yayi izuwa bayan Hayaam dake atsaye ya rumgumota tare da zagayo da hannayen shi ta waist ɗinta sannan ya kwantar da kanshi daga gefen wuyanta yana cewa"babe yaushe wayar zata ƙare?nifa a ƙagare nake, ƙasa ƙasa da murya tayi tare da cewa"pls karkaja min bala'e,"  ? Muryar aunty babba ce taci gaba cewa"Yanzu abunda nakeso dake kibar komai da kike yi ki tafi abuja gidan surukaina acan nakeso ki cigaba da zama,   Ƙiris ya rage hayaam ta saki wayar dake a hannunta saboda jin sa6on da auntyn nata ke faɗi, cikin ruɗu tace"haba dae Auntyna amma dae wasa kike yi ko?if not ni mai zai kaini gidan in-lows din mu da zama abun ma babu daɗin ji........, Tsawa aunty babba ta daka mata tare da cewa"ke dalla yi mun shiru!duk ƙoƙarin da nakeyi akanki bakya gani!kina nan sake da baki ga wata can a gidan matsayin yar aiki Abbansu ya mayar da ita ɗiyarshi sun gatanta yarinyar har makaranta take zuwa,idan har kikayi gangancin rasa wannan damar ta komawa gidan da zama ina mai tabbatar maki da cewa Kin rasa cikar burinki na har abada," shiru hayaaam ta ɗanyi gabanta na faɗuwa saboda ba abunda ta tsana fiye da ace zata Rasa SURGEON GENERAL RAFAYET saboda mutuwar son da take yi mashi ta kwallafa rai akanshi a lokacin baya tasa naci sosai akan shi sa'adda suke zuwa gidan sosai,amma tun da ta lura cewa kafin ya ma ɗaga idonshi ya kalli mace aiki ne don sai da ta share 2 weeks a gidan sau ɗaya suka ta6a hada ido shima ɗin by mistake ne ya ɗago a lokacin,abun ya tsaya mata arai, yadda take da kyawun surar nan babu namijin da zaiganta ya kawar da ido batare da ya neme ta ba sai akan SGR,tun a lokacin ta soma fidda rai akan shi amma yanzu aunty laila ta soma dawo da ita kan network, lumshe idonta tayi tana tuna kyakkyawar fuskarshi har lokacin sofwan na manne da jikinta ya lafe mata kamar wani maye,   ƙara kara wayar tayi akan kunnanta tace"Aunty laila komai zan iya yi akan na mallake shi,saboda shine namijin daya haɗa komai da nake kwaɗayi nake tsananin so a jikin ɗa namiji,amma abunda bansani ba aunty layla shin kina ganin zasu kar6e ni in naje gidan a matsayina na ƙanwar matar yayansu? Wani irin shu'umin murmushi Aunty babba ta saki wato anzo dai dai wurin da tafi so, miƙewa tayi daga zaunen da take agaban mirror tashiga zagaye bedroom ɗin nata tana cewa"Hayaaam baki da Matsala indae a gidan nan ne! Kinsan yarda Abbansu ke da son ƴa'ƴa hannu biyu zai kar6eki abu daya kawai nasani shine dole sai da iznin Abi sannan zai kar6eki don haka kibarmun wannan a hannuna ni zanyi magana da mommynmu tunda ita ke juya shi da zarar tayi mashi magana zai amince!abunda kawai nakeso dake hayaam shine kiyi gaggawar komawa gidan da zama acikin watan nan!Ke bama sai kin je da komai ba tsurarki zaki tafi batare da trolly na kayanki ba,saboda inaso ki fara fakewa da cewa kinje duba Fawan ne da bashi da lafiya daga nan kawai saikiyi zaman ki dirshan babu mai tanka maki saboda duk matasan gidan miskilai ne babu ruwansu,da ace dae yana da ƴa'ƴa mata shine za'a samu matsala kinsan mu mata da bakin ciki da hassada muke....'   Murmushi kawai hayaam ke saki tana faman lumshe ido tare da cizon pink lips dinta saboda shock ɗin da takeji na sofwan dake bin jikinta da hannun shi yana shafa ko'ina,Auntyna indae ni ce just karki samu damuwa,ki ƙaddara cewa gani can ma acikin gidan ina watayawa ta,ita kuma wannan yarinyar da kika sanar mun cewa tana zaune a gidan tuni zansa su yi mata checking out badai ni bace ba hmmmmmm,   Dariya aunty babba ta saki tare da cewa"har naji sanyi araina,burina na dab da cika," Download>>> Yar Harka Complete Document   Sun jima suna wayar kafin daga bisani suka yi sallama da junansu,    Buge hannun sofwan tayi tare da cewa"duk kabi ka takuramin wai kai wani irin jarababben mutun ne mai nacin tsiya haba mtwww,"taja dogon tsoki   Baki asake yabi ta da kallo tare da cewa"ni kike ma tsoki wai?wato wannan haɗamammar auntyn taki takira duk ta tunzuraki akan abunda bazai ta6a faruwa ba,duk naji mai kuka tattauna da ita,   ya fadi yana faman sakin hucin 6acin rai,murmushi hayaam ta saki tare da cewa"Sofwan zamana dakai ya ƙare!!!!!!! ?   Zaro ido waje yayi yana kallonta hankali atashe yace"saboda me hayaam?kada kiyimun haka don Allah!amma dae nasan wasa kike mun ko?   ƴar dariya tayi kafin tace"na ta6a maka wasa irin wannan?zanje na nemi namijin duniya ne!cikakken namiji jarumin gaske wanda ya kasance burin kowace ƴa mace ne shi bazanyi gangancin rasa cikar burina ba sofwan....... Bata ƙarasa ba ya dauke ta da mari ji kake faaaauuuu!    Rai a 6ace yace"Wlh baki isa ba hayaam ki katse mun jin daɗina ba!!saboda ke dakikiya ce sam bakisan meke maki ciwo ba wannan wani irin abun kunyane zaki kwasa kawai ki koma gidan surukanku da zama?Anya kuwa yayarki ba mahaukaciya bace.....    bata bari ya ƙarasa maganar tashi ba ta zame hannunta data dafe kuncinta dashi ta daddage ta zabga mashi zafafan maruka har guda uku sannan tace"karka kuskura ka ƙara kiran auntyna da sunan mahaukaciya!!maganar tafiya kuma ba fashi sofwan inka ga ban tafi ba to wlh numfashi na ne ya tsaya don ko ba ƙafa saina je,😳   Tuni sofwan ya rikice ganin yarda hayaam ta zabga masa mari batare da jin komai ba,duk irin yarda yake tarairayarta don karya rasa ta amma lokacin guda auntynta ta canza mata tunaninta,   Kallonta ya shiga yi yana girgiza mata kai yayin da idonshi suka cicciko da kwalla muryarshi a kasalance yace"Hayaam kada kiyimun haka dan Allah!saboda ke na wulaƙanta iyayena na baro komai nawa don muyi irin rayuwar da kikeso,wannan gidan fa duk don saboda ke na gina shi hayaam,ki duba gidan da iyaye na suke ciki duk ya rakwakkwa6e amma saboda ke na gidan wannan katafaren gidan ko don saboda wannan pls hayamm kada kibarni komai kikeso zanyi maki shi," yayi maganar tare da zubewa saman guiwowin shi a gabanta yana faman sharara hawaye,amma maimakon yaga alamun tausayi a idonta saima ta fashe mashi da dariya tashiga tafa hannaye tana cewa"sofwan kaifa dakanka kace ka wulaƙanta iyayenka saboda Ni?shin ni wacece a wurinka?mutumin da bai daraja iyayensa ba musamman uwarsa data tsugunna ta haifeshi taci baƙar wahala kanshi!ga kuma mahaifinsa daya fitar da gumi wurin nema masa kyakkyawar rayuwa duk bai duba wannan ba,burinka kawai ka farantama wasu can waɗanda basu son ciwonka ba,waɗanda ko yau ka faɗi ka mutu wlh shewa zasu yi suce Allah raka taki gona,shine har kake mun kwatance da ka wulaƙanta iyayenka don saboda wata banza can Ni?hanyar Aljanna nake sanya ka kota wuta?ko zan taimake ka ne ranar lahira?sofwan haƙƙin iyayenka ma kawai ya isa ya tarwatsa dukkan wani farin ciki na rayuwarka!!idan ma naci gaba da ra6arka nima zan shiga matsala ne don haka kawai muyi break up kawai kowa yayi rayuwarshi,"   ta ƙarasa maganar tare da ruƙe waist dinta tana kallon shi a tsiyace,   Miƙewa yayi daga kneel down din da yayi ya kalleta da fuskar tausayi yace"kada kiyi mun haka hayaam indae alaƙata da iyayena ne zan gyara komai...'   girgiza mashi kai tayi tare da cewa"na yaushe sofwan?hmmm ba don Allah zama kayi masu ba sai don saboda ni abanza kam,shiyasa koda yaushe soyayyar SGR take ƙara ninkuwa araina duk da irin tarin dukiyar dake gare shi hakan baisa ya canza ma iyayenshi ba ko wani nashi,zokaga Namijin gaske mai tsananin biyayya ga iyayensa wanda yasan darajarsu yake binsu sau da ƙafa kaifa? Har yau mahaifinka bai daina siyar da kifi a gefen titi ba, ga Mahaifiyarka cen kullum safiyar Allah sai tafito da murhu kopar gida tana suyar ƙosar da kunu,taya ma zan cigaba da kasancewa dakai!!? Kana da arziƙin da zaka iya ciyar da karuwai ka gina ma iyayensu gida ka kuma gina masu su kansu Amma iyayenka fa!!!?   shiru Sofwan yayi yana kallonta idanun shi sunyi jawur dasu ga wani ƙululun baƙin ciki daya tsaya masa a maƙoshinsa,   Wuce wa hayaaam tayi wurin wardrobe dinshi saboda anan kayanta suke nasawa, hannu tasa ta buɗe wurin kayanta tana raira waƙar nan ta namej dayake cewa"ko babu mota ba abun hawa wlh saina jee,"    A wani irin fusace Sofwan ya cafki hannunta data ruko bra dinta dashi,dakatawa tayi da yin waƙarta ta tace"Malam sakarmin hannu na,"   Yana wani irin huci yace"Hayaam baki isa kibar gidan nan ba, batare da kin mayar mun da duk wani abu dana kashe maki ba!!wlh bazaki ci bulus ba,duk kin taƙaitani duk ƙarshen wata saina kawo maki kayan abinci kwalin indomie kwalin taliya da sauran kayan abinci, sannan duk ƙarshen sati muna zuwan shopping mall dake nayi maki siyayya kuma mu fita restaurant cin abinci,ga kuma kuɗin mayukan da nake siya maki su kansu kudinsu yakai na dubu dari biyar,in kin ga kin bar gidan nan to ki tabbata kin haɗa mun kuɗaɗe na kin mayar mun dasu," ya ƙarasa maganar yana jifanta da wani irin kallo,   ta6e baki tayi tare da cewa"Naji duk zan biyaka ni kuma da me zaka biyani jikina da kayi amfani dashi?donni ma bazaka Ci bulus ba tunda ba uwar mutun ta haife ni ba,ka biyani budurcina nima saina biyaka kudinka"A shagale take maganar tana faman sakin murmushi,   Shiru sofwan yayi yana faman mazurai aransa yana tunanin taya zai biyata virgin dinga da take magana akai?   tsoki taja tare da buge hannunshi tabar shi tsaye a wurin ta koma daga gefe tana zura brazier dinta,   Muryarshi ce ta kuma katse ta da cewa"naji wannan tabbas bazan iya biyanki budurcinki ba,amma inaso ki sani bazan bari ki ɗauki ɗaya daga cikin abunda nasiya maki ba da kudina,daga ciki kuma hada kayan sawa don dama a tsiyace kikazo gidan nan, Download>>> Babban Yaya Complete Document   harara ta wurga mashi tare da cewa"Matsalarka ce wannan!ae ni abun kunya gaba na bashi ba baya ba,in ka hanani sa sutura sai in tafi a zir abuna," ganin tana shirin ɗaura mashi hawan jini yasa shi buga jikin wardrobe din da hannunshi yana kallonta idonshi jawur rai a tsananin 6ace ya fuce yabar mata ɗakin gaba daya, Murmushi tasaki tana cizon la66anta aranta tace"ƙaramin ɗan duniya har ni zakayi wa barazana," ******************* Tsare ta da ido hafsat tayi wadda shigowarta kenan  bedroom din ta, Ta jima a la6e tana sauraron firar da mommyn nata keyi da Hayaam a waya, sai da tabari ta kammala sannan tashiga daga cikin ɗakin tana kallonta, tunkan tace wani abu aunty babba tayi saurin cewa"to ƴarsa ido uban me yakawo ki dakina? murmushin takaici hafsat tayi kafin tace"narasa meke damunki mommy!gaba daya naji wayar da kikayi da aunty hayaam,saboda me zaki ce ta tattara kaya ta koma gidansu Abbana da zama?wannan wane irin abun kunya ne ace ƙanwar matar yayansu tana rayuwa acikin gidansu? menene alaƙarta dasu?gsky wannan tsarin sam baiyi ba mommy yakama ki dakatar da hayaam daga zuwan gidansu........' tunkan taƙarasa aunty babba ta kwatsa mata tsawa tare da cewa"munafuka!!ashe la6e kikeyi mun ni narasa gane meke damunki hafsat!!tunda waɗancan yaran da omar yakawo mun suka zo gaba ɗaya duk sun canzamin ke, yanzu bakya goyon bayana......' Tana magana tana yin nuni da hannunta dake ruke da wayarta, ta6e baki hafsat tayi tare da cewa"Mommy kenan,mgnr da kika faɗa gaskiya ce,Jahad da hossana ba ƙaramin sauyani su kayi ba saboda akansu na fara tausayin wani dan adam a duniya,sun goga mun kyawawan ɗabi'unsu da halayansu waɗanda ke baki ta6a gwadamun ba,haƙiƙa nayi rashinsu sosai kuma ina fata Allah ya ƙara hadani dasu wata rana.....' murya asanyaye tayi maganar,   Sakin baki Aunty babba tayi tana kallonta kamar me son gano wani abu can dae tace"Hafsat kodae kece kika sa Abbanki ya hanani zuwa abuja ganin jikin fawan?ina zargin hakan!! kaitsaye tace"Nice mommy!ni nasame shi na roƙe shi akan cewa kada yabari ki tafi ke kaɗai sai tare dani saboda bana jin daɗi yanzu bazan iya zuwa ba,"   a fusace tace"Meyasa"! Murmushi hafsat tayi tare da cewa"Saboda ba don Allah zakije ba!bakuma don kije duba jikin fawan ba face donki je ganin yarinyar da Aunty Amani ta sanar dake, ni kuma gsky bana son ma ki ganta balle har kiyi yunƙurin cutar da ita, don kuwa bazan sake bari ki cutar da wani ba saboda wani buri can da kike dashi wanda bazai ta6a cika ba.......' Da gudu hafsat ta fuce daga dakin ganin yarda Aunty babba ta zabura zata cafkota takai mata bugu,'   bedroom ɗinta ta koma tana faman tiƙar dariya hadasu dafe ciki, Ita kuwa aunty babba tuni idonta sunyi jawur saboda 6acin rai,tama rasa me zatayi ta huce,ashe hafsat ce ta hana ishaq barinta taje abuja yau lallaikam zata ci ubanta ne dani take magana, Ta fadi tana faman huci, *********AFTER 2WEEKS************ *Bayan Sati uku* Tuni jikin fawan ya ɗan murmure yaji sauƙi sosai har yana iya miƙewa ya taka yaje inda yake so hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba,a 6angaren su twins kuwa murna har ba'a magana saboda alert ɗin kuɗin da mommynsu ta turo ta wayar jahan a cikin dollar acct dinsa, a tsakar dare alert din yashigo a lokacin suna maƙale da juna kamar yadda aka saba,gaba ɗayansu suka buga shewa cikin jin daɗi ba don komai ba sai don zasu rabu da matsin Haroon su huta,a daren ranar har nafilar dare sukayi atare suka roƙi Allah akan ya yaye masu masifar dake damunsu, sun sha kuka kamar kamar me,sannan kuma sun shirya zuwa bank domin su kar6o masa kuɗinshi miliyan tamanin su damƙa mashi,😣 dama sai zarya yake yi masu kullum safiyar Allah yana musu barazana,ba don sun nuna mashi kuɗin ba dake cikin acct dinsu ba ya gani awayarsu, da bazai ƙyalesu ba, DOWNLOAD: "HARIJI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT" A 6angaren Hossana da Jahad kuwa hmmmmm just speechless,wata irin rayuwar hutu da jin daɗi suke gudanarwa acikin hamshaqin gidansu,babu ruwansu da kowa su biyu abunsu sai Camillah dake yawan zuwa dubasu wani lokacin takan tsaya ta kwana ma acikin gidan,ba ƙaramin gyarasu tayi ba,domin kuwa sun canza fiye da tunanin mai tunani,fatarsu kanta abun kallo ce, ga wasu irin surorin kyau da suka bayyana ajikinsu,sun koma rainon Madara rainon bonvita 😂 Ƴancin da su hossana suka samu ko mutanen nigeria a 1960 basu samu makamancin shi ba,hossana fa har wasu kumatun jin daɗi tafara ajiyewa🤣 dama bata wasa da abinci gashi Omar ya cika masu store da kayan abinci kala kala, ga freezer dinsu dake shaƙe da kayan sha,kullum in jahad tayi mata maganar tadinga ci ahankali sai tace"ina ruwanki!In suka ƙare yaya Omar zai siya mana wasu," 🥱 Marshal omar bai barsu hakanan ba, sai da ya ƙara masu security guards har mutun huɗu, Osman kuma shine a matsayin drivern da zai dunga kaisu School da wuraren shaƙatawa,tuni ya cike masu form na school koda akazo wurin sanya sunan uba ya tambayesu sunan mahaifinsu sai cewa suka yi "kasa mana sunanka kawai ya omar,mu bamu da uba," wani irin kallo yayi masu tare da cewa"ban shirya haramta ma kaina ɗaya daga cikin ku ba,don haka zan sanya maku sunan Uncle ɗina ne a matsayin Mahaifinku amma banawa ba,' Sam basu gane mai ya omar ɗinsu ke nufi ba da cewa bai shirya haramta ma kanshi ɗaya daga cikinsu ba,sun dai bar abun ne kawai azuciyarsu,   Alhamdulillah Omar ya kammala cike masu form da sunan Uncle dinshi,JAHAD ABUSUFYAN da kuma HOSSANA ABUSUFYAN,ba ƙaramin daɗi suka ji ba saboda jin ya saka masu sunan mutumin nan da goggon katsina ta ƙaƙaba masu amatsayin Ubansu, sunan makarantar da suka fara zuwa D.A International acadermy wato makarantar da Sehrish ke zuwa🤔 _💋Boss Bature💋_ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 11:30 na dare Fitowarta kenan daga toilet jikinta ɗaure da towel,ba ƙaramin canzawa tayi ba gaba daya ta sauya saboda hutun da take samu ga kuma kwanciyar hankali,tun daga kan natural skin colour dinta zaka gane hakan,yanzu bata wasa da tsaftace jikinta kullum cikin ƙamshi take,   Ƙarasawa tayi gaban mirror tana cigaba da tsane jikinta da towel ɗin hannunta,bayan ta kammala tayi hanging dinsa daga gefen mirror din,sannan ta kai hannunta jikin drawer chest na mirror,janyowa tayi tare da zura hannunta ta ɗauko hand dryer,jona ta tayi ajikin socket nan take ta soma buso da iska, cikin sauri ta kanga ta saitin kanta taci gaba da busar da gashinta,cikin nishaɗi take yi saboda ta mayar da abun tamkar na wasan yara, natsuwa tayi tana tunano abunda suka tattauna da Azmee acikin kitchen bayan ta sanar da ita maganar da sukayi da abbansu nacewa tafara kamun ƙafa tun daga yanzu,   dariya sosai azmee tayi tare da cewa"Abba da zolaya wato in marks dinki yazo da F shine zai aura maki haroon gsky kwara ki dage,"   Murmushi sehrish tayi tare da cewa"Amma aunty azmee ya akeyin kamun ƙafa inaso na iya"?    ɗan gyaran murya azmee tayi kafin tace"Kyautatawa mana,kinsan ita zuciya nason mai kyautata mata,kamar abbansu atlease yakamata ace duk safiyar Allah kina zuwa har bedroom ɗinshi kina miƙa gaisuwa hakan zai ƙara maki daraja a idanunshi kuma zai tabbatar da cewa kina da tarbiyyya sosai,sannan 6angaren girki yakamata ace ma yanzu kinfi ni iya girki,tuntuni dama inaso nayi maki magana akan koyon girki,saboda maza nason macen da ta iya girki,kin ga mazan gidan nan basa wasa da abinci akwai son cin mai daɗi,shiyasa nake da kusanci dasu sosai saboda yarda nake masu girki,don haka kema daga yanzu ki fara trying bafa dole sai irin nawa ba a'a salo na daban yakamata ki koya,bari na baki satar amsa kamar abincin gargajiya haka namu na hausawa saboda a gidan nan sunfi sabawa da abincin turawa,yakamata ki fara jaraba yi masu shi,ki koyi sarrafa abinci kala kala hada abunsha da kuma irin kayan makwalashe haka da sauransu,sannan 6angaren tsafta domin kuwa itace gaba da komai,idan ma kina da tsafta to ki ƙara akan wadda kike da ita,saboda mazan gidan nan basa son ƙazanta ko miskala zarratin,tun daga kan tsaftar jiki yakamata ki fara kulawa,wurin yin shaving na armpit dana under,da kuma kula da teeth dinki wurin yin brush akai akai banda barin datti ajiki,da kuma kula da gashin kanki wurin gyare shi,hatta nails ɗinki ki runƙa kula wurin yankesu banda tara akaifa,ina fada maki wannan ne domin amfanin kanki,don ita mace da tsafta akasanta da son ado,inaso kema ki kasance haka.........   Sosai azmee ta koyar da ita abubuwa da dama na rayuwa waɗanda zasu amfane ta,kuma tun daga lokacin duk in suka shiga kitchen suna aiki tana ƙara ilmantar da ita,hakan yasa sehrish ta soma canzawa sosai, yanzu kullum cikin gyara kanta takeyi,sannan bata wasa wurin koyon girki dalilin hakan yasa tashiga whatsapp grp na koyon girki,kullum tana cikin ɗaukar videos ɗin girki tana kallo donta koya,a hankali a hankali yanzu harta fara jin zata iya jaraba yi masu abinci acikin gidan 😇 murmushi ta saki bayan ta kammala tunanin a fili tace"bansan da wasu kalmomi zan iya godema aunty azmeena ba,saboda tagama yi min komai a rayuwa ina jinta tamkar mahaifiyata ne,Ya Allah ka barni da aunty azmee na,"?    jin alamar shigowar motocinsu yasa ta yin saurin cire hand dryer ɗin daga socket ta mayar da ita inda ta ɗaukota, sannan ta taka izuwa wurin wardrobe ta buɗe tana neman kayan da zata sanya,wurin jerin kayan baccinta ta duba,wasu riga da wando ta dauko ƴan qasar indonesia masu matuƙar kyan gaske ga laushi jikinsu,launinsu maroon colour ne masu ɗigon baƙi baƙi ajikinsu, cikin sauri ta zurasu ajikinta sannan ta ɗauki mayafi tayi rolling dinsa akanta, sai da ta tabbatar da cewa sun shigo ciki kusan 15 mins ta ƙara sannan ta buɗe ƙopa tare da fitowa daga ɗakin nata,ƙafarta na sanye da flat shoes,miƙo hanya tayi tana tafiya a hankali ta biyo ta main palour din babu kowa har sun wuce ciki,kitchen ta wuce don ta haɗa mashi tea tare da kayan marmarin dayake buƙata kamar kullum, Tare da Marshal Omar suka bar gidan,amma SGR ne kawai ya dawo saboda Omar ya wuce wurin su Hossana,tun akan hanya suka rabu dashi, a galabaice ya shiga part dinsa saboda rashin jin daɗin jikinshi dayake yi,tun safe bai da lafiya amma saboda juriya irin tashi da ƙarfin hali ba wanda ya lura da hakan,wani irin sever headache tare da zazza6i mai zafine ya rufe shi, Jikin shi na sanye da Army trouser tare da shirt light green colour,kai tsaye yana shiga bedroom dinsa ya faɗa saman bed dinsa batare da ya rage kayan jikinshi ba,saboda rashin ƙarfin jikin shi da yake ji,abun yazo mashi wani iri saboda kafin yayi ciwo da wuya mutun ne mai cikakkiyar lafiya,sam bai sanarwa kowa ba saboda baya son tayar masu da hankali kuma baison aga raunin shi, Sehrish Fitowa tayi daga kitchen ɗin hannunta ruƙe da tray mai ɗauke da ƙayataccen plate na fruits sai cup mai ɗauke da Hot tea sai faman tiririn Zafi yake yi,a natse take tafiya kai tsaye ta nufi stairs ɗin tana cikin tafiya kamar daga sama taji muryar haroon yana cewa"Wurin Namiji za'a ne"? A wani irin firgice ta juya tana neman ta inda zata ganshi,   Yana zaune saman 3 seater shi kaɗai abunshi jikin shi na sanye da night dress riga dai dai guiwa,ya aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya yana faman sakar mata murmushi,     Ba ƙaramin tsoro ya bata ba saboda bata tsammace shi a wannan lokacin ba,cikin sauri ta wuce upstairs gabanta na faɗuwa aranta tana cewa"Anya haroon Ba Aljani bane?in ba haka ba yaushe har ya shigo babban falon nan amma banga gifcin shi ba," tana tafiya tana sambatu aranta har ta ƙarasa part dinsa, sai da ta tsaya tare da dai daita natsuwarta sannan tashiga ciki, wayaam babu kowa a falon hakan na nufin yana a cikin bedroom dinsa, Takawa tayi a hankali har zuwa ƙopar bedroom din nashi sannan tayi sallama,kusan sau uku ba'a amsa mata ba sai a na huɗun ne taji muryarshi ƙasa ƙasa ya amsa mata "come in,"   a hankali tasa ƙafarta tashiga ciki,lokacin da ta ɗago da idanunta nan take taji faɗuwar gaba rasss!yanayin da taganshi yayi uban goho saman gadon yana fitar da numfashi daƙer daƙer ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,tuni jikinta yayi mugun sanyi,ƙarasawa tayi ciki tare da ajiye mashi tray din saman table tace"Sannu da dawowa ga tea nan na kawo maka,ko akwai wani abu da kake buƙata"? shiru bai bata amsa ba sai numfashi kawai da yake fitarwa mai hucin zafi,bin shi tayi da kallo sumar kanshi ta rufe dukkan fuskarshi side by side,tana so ta tambaye shi ko lpy amma tana jin tsoro,   Kusan 15 mins tana a tsaye bai ce komai ba ƙoƙari yake ya tashi amma sam jikinshi ya hana shi,sai da yayi dagaske sannan ya samu ya miƙe tare da matsowa ya sauko da legs dinsa ƙasa idanunshi a rufe rufff,fuskarshi ba ƙaramin canzawa tayi ba,jikin shi sai kerma yake yi tamkar wanda yashiga snow hatta pink lips dinsa sun gaza tsayuwa,tsananin tausayin shi ne ya kama sehrish saboda ta tabbatar da cewa bai da ƙoshin lpy sbd alamomin da tagani atattare dashi,tuni taji hawaye na ƙoƙarin zubowa daga idonta,   muryarshi ce ta tsinkayeta da cewa"ki duba a cikin side drawer ɗina thete's a jotter wit pen pls bring it 4 me," cikin sauri sehrish ta matsa tare da kai hannu jikin side drawer ɗin,ta janyo gida na farko ajikinta, anan ta samu Jotter ɗin tare da biro,ɗaukowa tayi tare da miƙa mashi,   daƙer ya cire hannunshi ya kar6a har lokacin eyes ɗinshi na'a rufe,aza jotter ɗin yayi daga gefen table ɗin gabanshi,buɗe papers din ciki yayi kafin ya aza biro din ya soma rubutu bayan ya kammala yayi tearing wurin da yayi rubutun ya ɗauko takardar ya miƙa ma Sehrish,cikin sauri tasa hannu ta kar6a tare da aza idonta kan rubutun wani irin handwritting gare shi domin koda ta kalla ko *A* bata iya ganewa ajiki ba hakan yasa ta kalle shi tare da cewa"Bangane menene ka rubuta ba,"ta faɗi a ɗan tsorace "Go nd bring it 4 me," shine kawai abunda ya iya furta mata, Cikin sauri sehrish ta kama hanyar fita daga bedroom ɗin nashi tana waiwayonshi,   Saukowa down stairs tayi tana faman cizon yatsa saboda tarasa gane menene ya rubuta mata,tamkar zatayi kuka,tana cikin wannan halin muryar haroon ta katse ta da cewa"Can I help u"? ɗagowa tayi aɗan razane tana kallon shi,fuskarnan tashi nadauke da murmushi yasa hannu ya kar6i takardar yana duba rubutun jiki,daga bisa ni yace"Ki jira ni anan yanzu zan dawo," yana fadin hakan yajuya da sauri ya shige part ɗinsu na nan downstairs, ajiyar zuciya ta saki aranta tana Allah Allah saboda tsoron kada haroon ya tafka mata kuskure don tasan halin shi,bai da tabbas gajiya da tsayuwa tayi,don haka ta samu wuri saman last step na benen ta zauna tana jiran dawowarshi,. Ba da jimawa ba sai gashi ya fito daga part din nasu, sai faman sauri yake yi irin da himmar nan hannun shi na ruƙe da syringe da kwalbar injection,tunkan ya ƙaraso sehrish ta miƙe tare da sa hannu ta kar6a tana yi mashi godiya,,   da buɗar bakinsa sai cewa yayi"Ba sai kin gode mun ba,Aikin lada ne fa nidae burina ki kai mashi allurar ya hanzarta yi yanzu,in ma godiyar ce gobe da safe kinzo ki same ni kiyi mun ita," yana magana yana sakin wannan shu'umin murmushin nasa, jiki asanyaye tasa hannu ta kar6a tana kallon fuskarshi shima kuma ita yake kallo da wannan murmushin nashi, cikin sauri ta juya tare da hayewa upstairs cikin sauri take tattaka matattakalar benen har ta wuce part dinsa Ruƙe qugu haroon yayi tare da sakin wani irin bazawarin murmushi yace"Lokacin Bacci yayi bari naje na kwanta gobe da safe akwai labari zazzafa,ƴar shila zata zo miƙo mun godiya da kanta," ya fadi tare da sakin dariya ya wuce sashen shi   Lokacin da sehrish ta koma ɗakin nashi yarda tabarshi haka ta same shi zaune idonshi a rufe, cikin sauri ta ƙarasa tare da miƙa mashi allurar da sirinjin tace"Ga allurar," hannu Sgr yasa ya kar6a daƙer ya iya buɗe idonshi sam baya iya gane wace kalar allura ce yarinyar ta kawo mashi saboda idanunshi biji biji suke gani hakan bai bashi damar karanta abunda aka rubuta ajikin ƙaramar kwalbar allurar ba,    fasa bakin kwalbar yayi tare da curo sirinjin ya fiddo da kan allurar ya tsoma acikin kwalbar ya zuƙo ruwan allurar iya yadda yasan ya dace yayiwa kanshi, .Tuni jikin sehrish ya soma rawa saboda tsoron allura gareta,cikin sauri ta kama hanyar fita daga dakin saboda ta bashi damar yin allurar,   Muryarshi ce ta tsinkayeta da cewa"kada ki tafi," ya furta yana faman sakin huci daga bakin shi da hancinsa, A bakin ƙopar ta tsaya idonta a rufe jikinta na kerma,muryarshi ta kuma ji yace"ki zo," cikin sauri ta koma ajiyar zuciya tasaki ganin harya kammala yin allurar, miƙa mata kwalbar allurar yayi tare da syringe din duka yace"kisa a dustbin," amsa mashi tayi tare da kar6a ta wuce wurin bedroom dustbin dinshi ta saka tarkacen allurar, sannan ta dawo ta tsaya tana jiran jin ko zai buƙaci wani abu tunda ya nuna baison ta tafi,   Lokacin da allurar ta gama gauraye ko'ina na jikinshi da wani irin ƙarfi ya ware idanunshi azare,har sai da sehrish taɗan ja da baya saboda firgitar da tayi,bin yatsun hannunshi tayi da kallo ganin yarda yake wawwaresu suna miƙewa tsaye,tamkar dae yadda mutun ke komawa Zombie acikin film,gabanta ne yashiga faɗuwa saboda tsoran da taji murya na rawa tace"Zan iya tafiya"?   ɗagowa yayi da wannan sexy blue eyes din nashi da launinsu ya ƙara Cizawa gwanin ban tsoro kai kana ganinsu kasancewa akwai matsala,ido cikin ido yake kallonta batare da ya kawar da idonshi ba hakan yasa zuciyarta ƙara karaya ga wani irin fargaba daya zo mata,ganin irin kallon da yake yi mata ne yasa nan take tadinga jin bugun zuciya,ja da baya ta soma yi jikinta na kerma har lokacin bai janye idonshi daga kanta ba bin ta kawai yayi da kallo,sai da taga taɗanyi mashi nisa sannan ta nufi hanyar fita daga bedroom din nashi da saurin gaske sai dai ina, kafin ta Ankara tuni SGR yayi wani irin kwakkwaran motsi tare da miƙewa tamkar wani Zaki ya bi bayanta azafafe yakai ma Waist ɗinta wani irin ruƙo ya ɗaga ta sama gaba ɗaya ta saki wata irin razananniyar ƙara mai rikitarwa bata gama rufe bakinta ba yayi wani irin wurgi da ita kai tsaye ta faɗa tsakiyar gadon shi yaraaaff tuni mayafin da tayi rolling dashi ya jima da barin jikinta !!!! Ba ƙaramin buguwa sehrish tayi ba daƙer ta iya tayar da kanta daga jikin bedmattress ɗin ta ɗago hankali a matuƙar tashe take kallon shi ganin yasanya hannayenshi tare da ruƙo shirt ɗin dake ajikinshi ya cire ta gaba ɗaya tare da yin wurgi da ita ƙasa,    gabanta ne yasake yin wani irin mugun bugu tuni hawaye sun soma wanke mata fuskarta cikin tsananin tashin hankali take girgiza mashi kai tana cewa"innalalahi wa'inna ilaihirraji'un nashiga uku !!!!"    Sam babu alamar sassauci a tattare dashi kai kana ganin yanayin action dinsa zakasan cewa ba a hayacinshi yake ba, Hatta ƙarfin jikinshi bana shi bane a matsayin shi na wanda bai da Cikakiyar lafiya, Ganin ya zame belt ɗin wandon jikinshi gaba daya yayi throwing dinsa, tare da sa hannu yana ƙoƙarin zame wandon dake jikinshi, hakan ya ƙara tsoratar da sehrish yunƙuri tayi da ƙarfi zata diro daga saman gadon ta gudu,aikuwa batayi wani aune ba taji saukarshi saman gadon gaba ɗaya ya afka mata tare da yi mata Rumfa da faffaɗan ƙirjinshi tsulundum taji ta ajikinshi,🙆🏽‍♀   nan fa ido ya raina fata,dukkan ilahirin jikinta rawa yake yi gaba ɗaya tagama rikicewa muryarta har wani shaƙewa take yi wurin cewa"Dan Allah kayi haƙuri kabarni na tafi,ni nasan cewa ba halinka ba....ba yin kanka bane.......' kasa ƙarasa maganar tayi saboda idonshi dake kallon cikin kwayar idon nata,SGR fa a halin yanzu zamu iya cewa baya ji baya gani,    Wani irin huci yake yi yana groaning just like a hungry lion,runtse idonta tayi saboda bazata juri kallon cikin nashi ba yayin da idonta ke cigaba da zubar da hawaye...........🙆🏻‍♀️🙆🏻‍♂️? Zuwa ga masu share na littafina lokacin da mutun zai sayi littafin nan ba muyi yarjejeniya nacewa zai turama wasu ba, amma sai gashi grp ba iyaka ana tura littafin koma waye yaje don kanshi kuma yasani akwai haƙƙina akanshi👍ya Allah kashiga tsakanina da koma waye, ************* It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku😍u  💋Boss Bature💋 runtse idonta tayi saboda bazata juri kallon cikin nashi ba yayin da idonta ke cigaba da zubar da hawaye........... Jin shiru yasata ta sake buɗe idanunta don taga me ya dakatar dashi har lokacin blue eyes ɗinshi na akan fuskarta tamkar mai nazarin wani abu,Allah sarki duk da bai a hayyacinsa yana ƙoƙarin ya dakatar da kanshi yayi control na kansa,Amma ina allurar ƙara zaburar dashi takeyi,sai faman ciccije pinkish lips dinsa yake yi,gaba ɗaya sumar kanshi ta lullu6e fuskarsu su duka biyun,    wata irin Zufa tagani tana tsattasofa mashi daga fuskarshi hakan ba ƙaramin razanar da ita tayi ba,ɗigowa sweat din tadinga yi daga fuskarshi tana sauka a fuskar Sehrish,    tuni ta soma haɗiyar yawu ganin yaƙi moving daga rufe ta da yayi hakan yasa,ta tattara dukkan ƙarfinta gaba ɗaya don ta ingije shi kota samu yayi gefe ɗaya ita kuma ta gudu,amma abun mamaki koda tasa hannunta tayi attempting ingije shi,ko motsi wannan baiyi ba saboda wani irin ƙarfine yazo mashi bana wasa ba, ..zaro ido tayi tana kallonshi hankali atashe,abun mamaki for the first time saita samu fuskarshi ɗauke da wani irin ƙayataccen murmushi naban mamaki lokaci guda yagama kashe mata jiki gaba ɗaya taji wata irin kasala ta rufar mata,    kwakkwarar damka yakaima wuyan rigar jikinta ya yage ta biyu nan take big boobs dinta suka bayyana gashi bata saka brazier ba,kokawa suka shiga yi dashi domin kuwa ta damƙe rigarta da yake ƙoƙarin yin wurgi da ita,sai faman ƙoƙarin rufe ƙirjinta take yi da ita,a ƙarshe daya fi ƙarfinta sai ta fashe mashi da wani irin matsanancin kuka da ƙarfin gaske take cewa"...Ya Allah ka kawo min ɗauki......Ya Allah ka dawo dashi cikin hayyacinshi ni nasan cewa ba yin kan shi bane.....   tuni ya afka ma ƙirjinta ya tasar masu, hannu takai tana ƙoƙarin janyo bedside lamp ɗinshi amma koda ta ruƙo fitilar ji tayi bazata iya cutar da shi ba kokaɗan saboda tsananin son da take yi mashi,tana jin duk wani motsin shi ajikinta,    Har bakinta takai a damtsen hannunshi don ta gartsa mashi cizo amma ina koda ta aza teeth ɗinta a fatar jikinshi sai dae kawai tafashe da kuka saboda bazata iya ba😢    Suna cikin wannan yanayin Marshal Omar ya faɗo cikin falonsa dawowarshi kenan daga wurinsu hossana bakomai ne ya kawo shi ba face message ɗin da sgr ya turo mashi a wayarshi nacewa bashi da lafiya,bai sanar mashi ba a lokacin da suke atare sai da suka rabu yana acikin mota ya rubuta mashi message ɗin, ganin saƙon da yayi ne yasa shi yin hanzarin dawowa gidan don ya duba shi,    Yana shigowa falon yaji sautin kukan Sehrish acikin ɗakinsa ga wani irin gurnani da sgr keyi na irin kura taga naman nan, hankalin shi a matuƙar tashe ya afka bedroom ɗin nashi,ba ƙaramin razana Omar yayi ba ganin yarda Sgr ya rufar ma Yarinyar gaba ɗaya ya danneta a lokacin harya zame dogon wandon jikinshi,shorts ne kawai ya rage mashi shima ƙoƙarin zame shi yake yi daga jikin shi,    A tsawa ce Omar ya kwaɗa mashi kira da ƙarfin gaske ya furta "RAFAYET!!!!!!!!!!!!!!!!! Tamkar maƙoshin shi zai 6allo waje haka ya ambaci sunan har kunnan sehrish, amma shikuwa gogan sam ba alamar yaji balle ya ɗago,    Ganin hakan yasa Omar yin hanzarin ƙarasawa tare da kai hannunshi a matuƙar zafafe ya damƙi sumar kanshi da karfin gaske ya janyo shi yayi wurgi dashi gefe guda saman gadon,   Cikin sauri sehrish ta rufe ƙirjinta da rigar ta wadda sgr ya yage mata ita,tashi tayi zaune tana ta faman sessheƙar kuka ga jikinta dake ta faman kerma,    tamkar zaki haka Sgr ya kuma ɗagowa daga wurgin da Omar yayi dashi gaba ɗaya ya makance,wani irin ihu sehrish tasaki ganin yasake nufota yana wani irin gurnani,   Cikin hanzari Marshal Omar ya damƙo damtsen gannunshi yana cewa"Wai meyake damunka ne!!!me kake ƙoƙarin yi ne!!!    Juyowa sgr yayi yana wani irin huci ya kalleshi tamkar baisan omar ba haka ya zabura ya miƙe tsaye tare da dirowa daga saman gadon ya daddage ya dunkule hannunshi yakai mashi kwakkwaran naushi a saman ƙirjin shi,ba ƙaramin zafi Omar yaji ba,rai a6ace shima ya cakume shi tare da kai mashi naushi,nan fa suka kaca me gaba ɗayansu tamkar ƴan wrestling haka suka shiga bugun junansu,   ganin haka yasa sehrish saukowa daga saman gadon dama ta samu ta zura rigar ajikinta duk da ta yayyage daga gabanta sai dae ta sanya hannu ta ruƙo rigar ta tattare wurin daya yagen,cikin sauri ta kama hanyar fuce wa daga ɗakin,aikuwa karaf akan idon Sgr a wani irin zafafe yayi wurgi da Marshal Omar gefe guda, da gudun gaske yabi sehrish tare da cafkota jikinshi nan take ta sake fashewa da wani irin matsanancin kuka,     Da hanzarin gaske Omar ya yunƙura ya taso yabi bayanshi tare da rurruƙe hannunshi tabaya da ƙarfin gaske,sai da yayi da gaske sannan yayi wurgi da sgr gefe guda, hakan yaba sehrish damar watsawa a guje tabar ɗakin,   Kafin Sgr ya yunƙura ya taso tuni Omar ya janyo ƙopar ɗakin ya datse ta, ya rage daga shi sai shi acikin ɗakin suna kallon kallon,    Omar bai ta6a tsorata da sgr ba sai ranar ganin yadda yake zazzare mashi ido tamkar baisan shi ba, gaba ɗaya kanshi ya gama ɗaurewa saboda yasan cewa ba Halin shi bane,shi da sam mace bata agaban shi ko kallo wannan amma kuma ace yau shi da kanshi yake ƙoƙarin yiwa Mace fyaɗe,bayan shike hukunta masu aikatawa da hannunshi,lallaikam akwai matsala,    ganin yadda yake ta faman huci yana cizon la66a yana kallonshi yasa shi saurin dakatar dashi da hannu yana cewa"Look rafayet!!! Ni nasan ba yin kanka bane,nasan ɗan uwana bazai ta6a aikata hakan ba,dan Allah ka amsa mun don na tabbatar da cewa ba yin kanka bane.......'kafin Omar yakai ƙarshen maganar tashi tuni sgr ya kai mashi kwakkwaran ruƙo duk irin nauyin marshal Omar sai da sgr ya ɗaga shi ya ɗaɗɗagoshi tare da yin wurgi dashi,aikuwa ba ƙaramin buguwa Omar yayi don gaba ɗaya yatafi ya zube gaban drawer dinsa nan take forehead dinsa ya bugu ajikinta har wurin yaɗan fashe kaɗan dafe goshin sa yayi tare da ɗagowa da idonshi ya kalli sgr cikin sanyin murya yace"Ni fa ne Omar ɗinka yau da kanka kake buguna?so kake ka kashe ni,    tamkar tunzura shi yayi maganar da yayi aikuwa gadan gadan ya tunkare shi da wannan tafiyar ta basawa,   "In fa na biye mashi wlh naƙasa ni zaiyi da alama," ya fadi acikin ranshi, cikin sauri Omar ya tashi tare da yin hanzarin afkawa cikin toilet ɗinsa ya rufe ƙopar,yayi hakan ne saboda tsoran karsu raunata junansu don inya bugeshi ba ƙyaleshi zaiyi ba ƙarfine zai haɗu da ƙarfi daganan kuma abunda zai biyo baya su dukansu bazasu ji daɗin shi ba,   Tamkar zai 6a66ake ƙopar toilet din haka yadinga bugun ƙopan saboda Omar ya buɗe mashi yashiga,su cigaba da gashi don ba ƙaramin fusata shi yayi ba so yake ya karairaya ƙasusuwan jikinshi,    "Wlh ka yi mai isarka,bazan buɗe ƙoparba," yana magana dariya tana cin shi saboda lamarin ya gama ɗaure mashi kai,    tuni jiri ya soma ɗibar sgr ja da baya baya yadinga yi yana ambaton sunan Allah nan take ya yanke jiki ya faɗa saman gadonshi abaje ya sume,   jin shiru tsit yasa Omar sanya hannu tare da buɗe ƙopar toilet ɗin yaɗan leƙo,ganin shi kwance saman gadon ya sume ba ƙaramin sanyi yaji ba aranshi,   fitowa yayi daga cikin toilet ɗin yana faman sauke ajiyar zuciya,ƙarasawa yayi inda sgr ɗin yake,hannayen shi yasanya tare da tattaro dogayen ƙafafuwanshi ya azasu saman gadon gaba ɗaya, sannan ya gyara mashi kwanciyarshi tare da janyo blanket dinsa ya lullu6e mashi jikinshi,     Addu'o'i ya tattofa mashi sannan ya kama hanyar fuce wa daga ɗakin harya kai baƙin ƙopa karaf idonshi ya sauka kan Syringe din allurar da sehrish ta zuba acikin dustbin,cikin sauri yakai hannunshi cikin dustbin ɗin tare da ɗauko kwalbar allurar yana karanta rubutun dake ajikinta,nan da nan hankalin shi yayi wani irin mugun tashi tuni kanshi ya gama ɗaurewa tunaninsa taya akai SGR yayi ma kanshi wannan allurar!!!!?    "I can't believe it!!!" ya furta yana sake jujjuya kwalbar dake hannunshi,    Tare da ita ya fito daga ɗakin yaso yaje wurin Yarinyar saboda ya rarrashe ta ya fahimtar da ita amma dare yayi sosai baisan awane hali take ciki ba yanzu,wuce wa bedroom ɗinshi kawai yayi tare da kwalbar ruƙe a hannunshi saboda yin Investigation akanta,dole ya binciki yarda akai akasamu allurar acikin gidan saboda dama sun jima suna neman haramtaccen companyn miyagun kwayoyin dake sarrafa allurorin a 6oye masu cire imanin mutun lokaci guda, 😳😳😳   *** A 6angaren sehrish kuwa abun gwanin ban tausayi haka ta faɗa ɗakinta tana faman shan kuka,gefen gadonta tazauna domin ƙarashe kukan nata,ta jima batare da yin motsi ba,hannunta na ruƙe da rigarta sai ƙara matse wurin take yi tana kuka,duk wurin da sgr ya damƙa ajikinta ba ƙaramin raɗaɗi yake yi mata ba saboda baiyi mata ruƙon wasa ba,idanunta sun kumbura sosai saboda kukan da tasha.......'   Bakomai tafi ji ba face yarda taga Omar na bugunshi,tsoranta karya lahanta shi akan abunda take da tabbacin cewa ba yin kanshi bane,😢 Daƙer ta iya miƙewa ta wuce toilet saboda ta tsarkake jikinta,rufe ƙopar toilet ɗin tayi kusan 15 mins sai gata ta fito ɗaure da towel tana faman sauke ajiyar zuciya,har cikin ranta ba ƙaramin sanyi taji ba da Marshal Omar yazo don da baizo ba adai dai wannan lokkacin da SGR ya jima da yin raping dinta,kuma babu tabbacin cewa zata rayu saboda ba ɗigon Imani atattare dashi lokacin,      Wardrobe ɗinta ta buɗe tare da curo wata rigar baccin ta zura ajikinta, sannan ta koma tare da hayewa saman gadon,janyo bargonta tayi tare da lullu6e jikinta dashi, rufe idanunta tayi nan take brain ɗinta,ta tariyo mata fuskar sgr lokacin da yake kallon cikin idanunta sweat dinshi na zuba a fuskarta nan take wata irin kasala ta rufe mata jikinta,sam bacci yaƙi ɗaukarta saboda daga tazo runtse idonta sai taji kamar SGR zai faɗo mata cikin ɗakin,firgita ta dinga yi duk tabi ta tsoratar da kanta duk da ta rufe ɗakin ammma ji take kamar zai biyota ne,saboda yarda taga ya buge omar ya afko mata ɗazun,tana cikin wannan halin wayarta ta buga uban ringing aikuwa a gigice ta wuntsila ta faɗo ƙasa daga saman gadon tana ƙoƙarin shigewa ƙarƙashin gadon,yadda kasan wadda sanyi ya kama,haƙoranta sai kerma sukeyi kaf!kaf!!kaf, yatsun hannunta kuwa kamar waɗanda aka sanyawa battery sai rawa sukeyi ba ƙaƙƙautawa,ta jima a haka tana faman zazzare ido, sai daga bisani ta gane cewa wayarta ce ke ringing,lalla6awa tayi tataso tana tafiya cikin sanɗa har ta ƙarasa wurin side drawer ɗinta buɗewa tayi tare da ɗaukar wayarta ta dake ringing,tamkar wayar zata sul6e daga hannunta saboda kermar da fingers din nata keyi,Sunan AMRISH ne ya bayyana akan screen din wayar,lokaci ta duba kusan ƙarfe ɗaya da rabi na dare,katsewa kiran yayi saiga message ya shigo nata,cikin sauri ta buɗe tare da karantawa kamar haka   _Hi reesh,nayi missing ɗinki sosai shiyasa na kira don na tsoratar dake saboda nasan cewa zaki firgita in kirana yashigo a wannan lokacin,May be ma kina nan kina Jan minshari ne_    Murmushi sehrish tayi sosai bayan tagama karanta,reply ta mayar mata da cewa"i missed u too my lovely friend,kinci nasara akaina saboda kin tsoratar dani sosai,gobe ba school amma zamuyi video call ne,"    Bayan ta kammala tura mata saƙon ta mayar da wayar asaman drawer din ta ajiye,safa da marwa tashiga yi acikin bedroom dinta tana tunanin taya akai Sgr yyi attempt na raping ɗinta!!!? tsayawa tayi cak lokacin da zuciyarta ta ambaci sunan HAROON,gabanta ne taji ya faɗi bakomai ta tuna ba face maganar daya yi mata nacewa"Basai kin gode mun ba Aikin ladane,nidai burina ki kaima shi ya hanzarta yi gobe da safe kinzo kiyi mun godiyar,    Dafe ƙirjinta tayi cikin tsananin tashin hankali, hannu ta aza akai muryarta na rawa tace"innalallahi wa'inna ilahirraji'un nashiga ukuna!!haroon yaja mun bala'e...tabbas shine silar komai !! Shiya bani allurar dana kaima babban yaya, wayyo Allah na...yanzu dole su tuhume ni akanta!!Haroon ya gama dani.............   A daren ranar sehrish bata runtsa ba yarda taga rana haka taga dare,tasha kuka kamar kamar me ƙarshe ma tashiga toilet tayo alwala tafito ta shimfida carpet tashiga jera salloli har sai da ƙafafunta suka soma raɗaɗi sannan ta dakata tare da ɗaga hannayenta sama tana roƙon Allah ya tsareta daga sharrin Haroon,sai wuraren asuba bayan tayi salla sannan bacci yayi awon gaba da ita a saman sallayar,💔         Morning ❤❤? Wuraren ƙarfe takwas azmee tashiga bugun ƙopar bedroom dinta,har cikin tsakiyar kanta tadinga jin bugun,a gigice tafarka tare da miƙewa ta nufi kopar ta buɗe tana tambayar wanene,   Bin ta da kallo azmee tayi ganin yarda fuskarta ta kumbura suntum ga idanunta ma sun ƙankance saboda rashin isasshen bacci,hankali atashe tace"Lafiyarki kuwa sehrish?Anya ma kinyi bacci jiya? Fuskarki kamar ta wanda yasha kuka?     Maimakon ta bata amsa sai ta fashe da wani kukan saboda tunawa da halin da take ciki,ganin hakan yasa azmee shiga cikin ɗakin tare da rufo masu ƙofa,.     ruƙo hijabin sehrish tayi taja ta suka zauna daga gefen gadonta sannan ta kalle ta anatse tace"faɗamun meya faru ƙanwata?meyasa ki shiga cikin damuwa....."    cikin shessheƙar kuka sehrish ta Zayyana mata dukkan abunda ya faru adaren jiya ta ƙare da cewa"a....Aunty azmee wlh ba laifina bane Haroon ne ya bani allurar, banyi tunanin zai cutar dashi bane,yanzu ni bansan ya zanyi ba! Idan babban yaya ya tuna abunda ya faru jiya dole ya tuhume ni akan ni na kawo mashi allurar.........'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya zo mata,   Shiru azmee tayi kamar mai nazarin wani abun kafin daga bisani tasanya hannunta a kafaɗar sehrish din tace"Just Calm down ur mind!ki share hawayenki,ynx yakamata muyi tunanin samun solution before ya tuna din, amma nayi mamakin a ina haroon ya samu allurar daya baki ashe dama kuna ƴar tsama dashi baki ta6a sanar mun ba!?   cikin shessheƙar kuka sehrish tace"bansan me nayi mashi ba aunty azmee haroon ya tsaneni nima bana son ganinshi saboda ya jima yana ƙuntatamun bana son na tayar maki da hankaline shiyasa ban ta6a sanar dake ba......'    Jinjina kai azmee tayi kafin tace"Kinyi kuskure sehrish!!baki ɗaukeni kamar yarda na ɗauke ki ba,rashin gayan mun da kikeyi shine zai jefa ki cikin matsala....'rai aɗan 6ace azmee keyi mata magana,   "Aunty azmee kiyi hakuri nasan nayi kuskuren rashin sanar dake yanzu nagane hakan,"     ajiyar zuciya azmee ta saki kafin tace"shikenan ya wuce,naji daɗi sosai da yakasance Omar ne ya ƙwaceki a wannan lokacin da bansan mai zai biyo baya ba,ynz babban matsalar dole ne suyi zargin wani abu akanki,koda Omar ya tambayeki wanene ya baki allurar ki sanar mashi kawai that's the only solution!!!    girgiza kai sehrish tayi tare da cewa"a'a aunty azmee bazan iya cewa haroon ne ya bani allurar ba,saboda bakowa ne zai yarda dani ba,kuma zai iya ƙullamun sharri ne,ina tsoran hakan,"    gyaɗa kai azmee tayi tare da cewa"hakane kuma kin faɗi gsky,abun zai iya juyewa ya dawo kanki,amma naso ki sanar dasu cewa shi ya baki allurar saboda ki samu ki tsira,amma bakomai nasan cewa Omar zai fahimce ki in kikayi mashi bayani,babban tashin hankalin shine idan shi Sgr din ya tuna abunda yafaru gsky akwai matsala!!!!    Sun jima suna tattaunawa kan yarda zasu shawo kan matsalar kafin daga bisani Azmee tace"ki kwanta ki huta don nasan jiya bakiyi bacci ba,ni bari na wuce kitchen,"   Amsa mata tayi da toh,sannan ta cire hijab ɗin jikinta ta kwanta saman lallusan katifan gadon,lamo tayi a hankali brain din tadinga tariyo mata abunda ya faru adaren jiya,musamman yarda yayi mata rumfa da wide chest dinshi yana faman gurnanin nan yana kallon cikin idonta,wani irin yanayi mara misaltuwa, ba ƙaramin shock taji ba alokacin duk da tana cikin tashin hankali hakan bai hanata jin emotion dinshi ba,    Hannu tasa tare da janyo fillow ta rungume shi sosai ajikinta saboda yanayin daya zo mata tuni taji wata irin kewarshi ta lullu6eta kamar maijin zazza6i,runtse idonta tayi nan take wannan ƙayataccen murmushin daya sakar mata jiya yadawo mata a idonta,cikin sauri ta buɗe su tana faman sauke ajiyar zuciya,ban ta6a ganin kyakkyawan murmushi ba sai adaren jiya Ya Allah ka mallaka mun shi ❤💋?   Ta furta fuskarta dauke da murmushi daga bisani wani baccin ya kuma yin awon gaba da ita, ****** fitowa Omar yayi daga bedroom dinshi jikin shi na sanye da jallabiya maroon colour,jiya da tunanin abunda ya faru tsakanin SGR da yarinyar nan ya kwana,burin shi kawai yaje yaga ya rabin ranshi ya kwana, shiga part dinsa yayi tare da wuce wa bedroom dinshi, abun mamaki samun shi yayi tsaye agaban mirror jikinshi na sanye da bathrobe ya ɗaure suman kanshi ta baya,da alama fitowarshi kenan daga bathroom,   shiga ciki omar yayi tare da yi mashi gyaran murya,juyawo sgr yayi ya kalle shi tare da 6ata fuska yace"Am angry wit u omar,bana son ganinka cos i even texted u about my sick amma shine ko kazo ka ganni ko? Ya fadi tare da tsuke mashi fuska,   Tsayawa Omar yayi yana kallon shi kamar mai nazarin wani abu,yayi wani fresh dashi sam babu alamun damuwa attare dashi,    Cikin mamaki yace"Oh kana nufin ka manta abunda ya faru jiya"?   "Meya faru"!? Ya tambayana yana kallonshi aɗan ruɗe,    matsawa kusa dashi Omar yayi tare da aza hannnayenshi akan shoulders ɗin Sgr yace"Wai dagaske kamanta komai?duk abunda ya faru jiya"?   girgiza mashi kai yayi tare da cewa"Omar ni fa i don't know what are u talking abt explain to me pls,   fashewa da dariya Omar yayi daker ya tsagaita yace"pls ka tuna mana ko kaɗanne,   Shiru sgr yayi yana bin shi da kallon bana son raini, can dae yace"Jiya ni bansan ina kaina yake ba,i Can't remember,    jinjina kai Omar yayi har lokacin fuskarshi ƙumshe da dariya yace"kaine kayiwa kanka allura jiya?   ɗan yatsina fuska yayi kafin yace"yeah its me meya faru ne?   girgiza kai omar yayi tare da cewa"babu komai kawai inaso inji kaine ka ɗauko allurar?kuma kasan wace allurace kayi ma kanka"?   ɗan shiru Sgr yayi yana kallon fuskar Omar na wani lokacin a ƙoƙarinshi na ya tuna meya faru,ajiyar zuciya yasaki tare da cewa"Bani bane,wannan yarinyar ne, itace ta ɗaukomin,"    ruƙo hannunshi Omar yayi yaja shi suka zauna daga gefen gadonshi sannan yace"da ka tashi yau da safe kana nufin kwata kwata baka ga wata alama ba ajikin ka ba"?    ɗaure mashi fuska yayi yace"Omar banason wannan tmbyar nifa ban gane me kake nufi ba,"    Hannu omar yasa yana shafa ƙirjinshi yace"kwantar da hankalin ka mana,just tell me da wani yanayi ka tashi yau ajikin ka,    Shiru sgr yaɗanyi na wani lokacin kafin yace"bro i can't explain it,yanayi mara misaltuwa jiya na kwanta da ciwo, but dana tashi naji ni'ima atattare dani ga wani ƙarfi da nake Ji not only that omar When I went to the toilet, I saw something that really confused me because I had never seen it before..................🙊 Weekend mu haɗu on monday insha Allah, don't forget to follow me on tiktok boss_bature❤️ 💋Boss Bature💋 Follow this link to join my tiktok acct 👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 "What's it"? Omar ya tambaya yana kallon shi, ganin yarda Omar ke kumshe dariya yasa shi fasa yin maganar ya ɗan ɗaure face ɗinshi yace"omar banason wasa fa pls tell me the truth, Did something happen last night? Naga bed sheet dina duk yayi wani squeezing kamar anyi dambe asaman shi,     dariya sosai Omar yayi kafin yace"no ba wani abu just forget about it, na same ka ne kawai a wani yayi na ciwo so na ɗan taimaka maka ne har nasamu bacci ya ɗauke ka," ta6e baki sgr yayi yana kallon shi don bai yarda da abunda ya faɗa mashi ba, hakanan omar bazai tasa shi gaba yana mashi dariya ba just without any reason,     miƙewa Omar yayi tare da kallon shi yace"bari na sauka down ko kana buƙatar wani abu ne nasa akawo maka"?   juyawa sgr yayi ya kalli tray din da ke ajiye saman table ɗinshi yace"wannan yarinyar tazo ta tattara wannan kayan,ga bedroom dina ma inaso a gyaramun,"    "Okey zan faɗa mata, ka huta my man,"    Juyawa omar yayi zai fuce har yakai bakin door din ya waiwayo  don ya kalli sgr karaf suka haɗa ido, cikin mamaki yace"Omar nifa wani kallo naga kana min irin kallon jarababben namijin nan......' ya faɗi yana tsuke mashi fuska,   Fucewa omar yayi yana ƴar dariya, yamutsa fuska sgr yayi tare da cewa"Omar nason haukata ni, bansan wannan dariyar nashi me yake nufi ba," yayi maganar tare da kwantar da bayanshi saman lallausar mattress ɗin, kwakkwaran juyi yayi asaman gadon, kai tsaye idonshi ya sauka akan siraran gashin dake zube saman bedsheet dinsa, cikin sauri ya ɗago da kanshi tare da zuba ma gashin ido, mamaki ne ya kamashi taya akai gashin kanshi ya zuba don kuwa yana da tabbacin cewa sumar kanshi bata kakka6a saboda gyaran da take sha, hannun shi yakai a hankali tare da ɗauko siraran gashin guda uku ya zuba masu ido yana kallonsu, dogon gashi ne mai tsayin gaske, sak irin launin sumar kanshi wato dark brown colour, natsuwa yayi yana nazarin gashin, kafin yasanya hannunshi tare da ɗaukar siraran gashin a hannunshi,yunƙuwa yayi tare da miƙewa daga saman gadon, ya nufi gaban dressing mirror dinshi, zama yayi asaman front chair din madubin, sannan ya ajiye siraran gashin asaman shi, hannu yasa tare da tsinko gashin kanshi siriri guda ɗaya, sannan ya ajiye shi a gefen waɗancan sauran guda ukun, within 5 mins ya gane difference ɗin dake tsakanin su,tabbas wannan ba hairs ɗinshi bane to na wanene, asaman bedsheet ɗinshi kuma?  hannu yasa ya ɗauki siraran gashinan guda uku, sannan ya tashi tsaye ya nufi bedside drawer ɗinshi, buɗewa yayi tare da buɗe jotter ɗinshi dake ajiye acikinta, a shafi na farko ya saka siraran gashin sannan ya rufe jotter ɗin, tare da mayar da drwer chest din ya rufe, wuce wa yayi wurin closet ɗinshi domin shirya kanshi, ***********💋  bayan fitar marshal omar daga part din  Sgr kaitsaye down stairs ya wuce wurin dining area dinsu ya nufa ganin aunty azmee nata faman jera masu breakfast dinsu, tunkan ya ƙaraso ta soma sakar mashi murmushi tana cewa"Omar barka da fitowa fatan ka tashi lafiya,"?     fuskarshi asake yace"lafiya lou Alhmdllh,"    shiru ya ɗanyi kafin yace"am ina wannan yarinyar take ne sehrish"? Har sai da gaban azmee ya fadi rass jin abunda yace,dama tasan saiya tambayeta akan maganar nan,    murya na rawa tace"bata jin daɗi ne tana a bedroom ɗinta,ni nace mata ta kwanta ta huta shiyasa bata fitowa. Ba.......'   "Ta sanar dake game da abunda ya faru jiya"? Ya katse ta da tambaya,    "Eh ta sanar dani komai," ta fadi adabarbace,    Omar yace"okey ina son magana da ita, ki ce tazo tasame ni a part ɗina ina jiranta,"   Cikin sauri ta amsa mashi da toh, sannan ta bar jera abincin da take yi ta wuce ɗakin sehrish,    A hankali ta tura ƙofar tashiga da sallama, kwance ta same ta sai faman sharar bacci take yi, har lokacin jikinta bai daina yin kerma ba,    matsawa tayi dab da ita tare da sanya hannu ta ɗan bubbugi kafadarta "Sehrish !!sehrish!!   Har cikin dodon kunnanta taji kiran a firgice tafarka tare da miƙewa tsaye tana cewa"La'ila ha'ilallah.........' rufe mata baki azmee tayi tare da cewa"ki natsu ni ce" a hankali tashiga sauke ajiyar zuciya tana kallon azmeen da idanunta da suka canza launi saboda bacci,  Janye hannu azmee tayi daga bakinta sannan tace"Omar ne ke son magana dake yace ki same shi a part ɗinshi yanzu,"    zare ido sehrish tayi murya na rawa tace"Aunty azmee ni kuma.....na shiga uku....me zai tambaye ni......'. Katse ta azmee tayi tare da cewa"kada ki damu nasan game da allurar nan ne zai tambaye ki, kawai ki fada mashi gaskiya a wuce wurin,"     fuskarta tamkar za tayi kuka tace"Aunty azmee ina tsoro fa kada naja ma kaina,"    girgiza kai azmee tayi tare da cewa"ba wani tsoro omar zai fahimce ki, kina 6ata lokaci fa ki tashi ki tafi,  Tana kai ƙarshen maganar ta juya ta fuce daga ɗakin, jiki asanyaye sehrish ta sauko daga saman gadon, hannu tasa ta ɗauki hijab ɗinta wadda ta ajiye asaman gadon milk colour ta zura ajikinta,   Buɗe ƙopar ɗakin tayi ta fito tare da miƙar hanya ta wuce part dinsa, tsayawa tayi daga ƙopar shiga tana ƙoƙarin dai daita natsuwarta,sallama tayi mashi amma shiru ba'a amsa ba, ƙafa tasa tashiga daga ciki,babu kowa a falonsa komai anatse yake sai ƙamshi dake tashi,    Shiga ciki tayi tare da samun wuri ta tsaya a kusa da royal sofa din dake a kewaye, gabanta sai faɗuwa yake yi kamar mara gaskiya,     "Ya Allah ka bani ikon amsa tambayar da zaiyi mun,bana son nashiga matsala da kowa acikin gidan nan, nasan zasu iya zargina wayyo Allah na," ta furta tana faman yarfa hannunta, cike take da zullumin me zai biyo baya,   tana cikin wannan tsayuwar wayar shi ta shiga ringing a firgice taɗan ja da baya saboda bata tsammaci jin sautin wani abu ba, bin wayar tayi da kallo tana ajiye asaman 3 seater din don anan yabarta,     katsewa kiran yayi sai ga wani ya kuma shigowa, matsawa tayi a hankali saitin kujerar tana kallon wayar, ranta ne yabata ta ɗaga kiran taji wanene wata'kil kiran gaggawa ne,    Tamkar ana tunzurata haka taji, hannu takai tare da ɗaukar wayar tayi picking call din tare da karawa a kunannta, tun kafin tayi sallama taji ance"Ya Omar shi ne jiya kace in ka koma zaka kira ni awaya amma naji shiru ko? Muryar hossana ce ke magana,   Shiru sehrish tayi tana sauraron maganarta,.    Acan kuwa jin tsit Omar ɗin yayi mata shiru yasa ta cewa"kana ji na kayi mun shiru ko, Allah idan bakayi magana ba yau ko breakfast bazanyi ba....' ashagwa6e tayi maganar,    murmushi sehrish tayi jin yarda yarinyar ke magana, sai a lokacin tace"bashi bane, baya kusa ne,"  ?   Jin muryar mace yasa hankali hossana tashi ruƙe qugu tayi dama tana atsaye jikinta nasanye da kayan bacci riga da wando red colour, ta ƙara kara telephone din a kunnanta, tace   "ƙanwarshi ko budurwarshi ko matarshi wacece ke aciki ? ta tambaya a ƙule,     "Matar shi ce," sehrish ta faɗi cike da zolaya, aikuwa nan take hankalin hossana ya tashi, muryarta tamkar zatayi kuka tashiga kwalama jahad kira tana cewa"Jahad!!Jahad!! ashe dama ya omar yana da aure shine bai fadamana ba,     Yadda hossana ke kwala mata kira yasa ta fitowa daga kitchen cikin sauri ta nufe ta tana cewa"Hossana lafiya meya faru ne kike kwalamun kira? Ke da waye a waya? Ta tambaya a yayin da take ƙarasawa wurinta,   duk sehrish ta kasa kunne tana jinsu,  Cikin shessheƙar kuka hossana tace"Ashe dama ya omar na da aure bai fadamun ba,"    Cike da mamaki jahad tace"kai haba wai dagaske?    "Eh mana gatanan muna magana awaya," ta faɗi rai a6ace tana miƙa ma jahad telephone ɗin,,   Hannu jahad tasanya ta kar6i wayar sannan anatse tace"Assalamu Alaikum," fuska dauke da murmushi sehrish tace"Wa'alaikum salam,"   Jahad tace"ina kwana aunty,"    "Lafiya lou," sehrish ta amsa,  Jahad ta kuma cewa"dagaske ne kece matar yaya Omar"? ta tambaya tamkar tana a gabanta, Sehrish tace "eh nice,"   jinjina kai jahad tayi tare da ɗan ta6e baki tace"Amma bai ta6a sanar mana ba, dan Allah sabon aure ne ko tsoho "   Ƙiriss ya rage sehrish ta fashe da dariya daƙyar ta basar da ita tare da cewa"tsoho ne, mun jima atare ynx haka ma ina ɗauke da juna biyu ina fata zaku zo suna in na haihuwa,"    Jiki asanyaye jahad tace"insha Allah idan ya barmu zamu zo, amma aunty baki faɗa mana sunanki ba"?    Ƙara kashe murya sehrish tayi tare da cewa"sunana Zainab amma mijina yana kira na da Hayaty," KARANTA ZAFAFA 2022 ✓Gurbin Ido... Na Huguma (Zafafa2022) ✓Inaya By Mamuhgee (Zafafa2022) ✓Sanadin Labarina By Hafsat Rano (Zafafa2022) ✓Babu So... By Billyn Abdul (Zafafa2022) ✓Farhatal Qalb By Mss Xoxo (Zafafa 2022)   Jinjina kai jahad tayi tare da kallon hossana wadda ke tsaye cikin ƙunar rai,   Sun jima suna waya da sehrish kafin suyi sallama, mayar da wayar sehrish tayi ta ajiye saman seater ɗin, sannan ta koma tana faman tiƙar dariya,    ɗagowa jahad tayi ta kalli hossana gaba ɗayansu jikin su yayi mugun sanyi, duk basu ji daɗin cewa ya omar yana da mata ba, sam hossana ta gaza jurewa komawa tayi saman 2 seater ta faɗa tare da kifa kanta tana kuka, jahad kuwa kitchen ta wuce saboda tabaro dankalin da take soya masu, ita kanta jurewa kawai take yi amma ba ƙaramin ɗaci taji ba na jin cewa ya Omar dinsu yana da aure, tsayawa tayi agaban fan din dake asaman gass sam ta kasa juya dankalin saboda tashin hankali, cikin sanyin murya tace"koma wacece matar shi ina tayata murna sosai, domin kuwa tayi dacen miji nagari........' kwalla ce ta zubo daga idonta ɗas ta zuba ƙasa, 😖 ?    Shigowa omar yayi cikin falon nashi, sehrish na ganin shi nan da nan ta shiga natsuwarta,    "Ina kwana ya omar"?   kallonta yayi tare da sakar mata murmushi yace"lfy lou Alhmdllh, ki zauna mana," ya faɗi tare da samun wuri ya zauna asaman 3 seater,  wuri tasamu itama ta zauna suna fuskantar juna,    sunnar dakai tayi ƙasa tana jiran jin mai zai ce mata,   Cikin natsuwa ya soma magana "Am really  sorry abt wht happend last night, banji daɗin abunda sgr yayi maki ba, nasan abun zai tsaya maki aranki,amma inaso ki sani ba yin kanshi bane! wannan allurar ce da kika kai mashi ya sanar dani cewa ke kika kai mashi ita...........' hankali tashe sehrish take kallon shi a tunaninta sgr ya tuna abunda ya faru ne,    Cigaba da magana omar yayi anatse yace"Calm down ur mind, sgr ba zai iya tuna abunda ya faru ba a yanzu amma fa dole ya tuna wata rana abun zai dawo mashi ne akan shi, so nake ki fadamun a ina kika samu allurar da kika kai mashi ? Da sanin ki kika kai mashi ita? Ya tambaya yana kallon fuskarta cike da tuhuma ,   Lokaci guda duk ta dabarbarce ta rasa natsuwarta,      " Tell me the truth who brought it to u? don nasan ba ke kika dauko ta ba, in fact bamu da irinta acikin gidan nan...'    shiru tayi tana kallon shi zuciyarta na raya mata ta fada mashi gaskiya kawai,     murya na rawa tace"Ya omar ni ba da sani na ba Allah, babban yaya yayi mun rubutu a paper ya bani, ko a lokacin sai da nace mashi ni bansan meya rubuta ajiki ba, amma yace mun naje na ɗauko mashi kawai saboda baya cikin hayyacin shi ne, lokacin dana fito da takardar a hannuna  ina zullumin meya rubuta ajiki shine kawai sai ga h.....h.....' wani irin ruƙo taji anyima maƙoshinta tamkar wani abu ya tokare wurin,nan take taji numfashinta na shirin ɗaukewa gaba ɗaya, kakari tashiga yi tana ƙoƙarin furta sunan haroon amma sound ɗin ya ƙi fidduwa daga bakinta, abun mamaki abun al'ajabi,    Ganin yarda zufa ke tsattsafo mata gefe da gefen fuskarta gashi sai faman numfarfashi take yi sama sama,   Hakan ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba cikin sauri yace"Ke lafiya meke faruwa ne? Ko baki da lafiya ne?    cikin kuka tace"maƙoshina ne ke mun ciwo, nagaza furta sunan wanda yaban allurar raɗaɗi nake ji a wurin,     tashi marshal omar yayi tare da ƙarasawa wurin frigde din dake a falon shi, buɗe wa yayi tare da ɗauko bottle water mai sanyi, sannan ya dawo ya zauna dab da sehrish ya buɗe murfin robar ya miƙa mata, cikin sauri ta kar6a tana sha sai da tashanye kusan rabi sannan ta janye tana faman sauke ajiyar zuciya,   Hannu omar yasaka tare da kar6a robar daga hannunta yasanya murfin ya rufe sannan ya ajiye robar ruwan a ƙasa, mayar da idonshi yayi akan sehrish sannan cikin natsuwa yace"pls taimako nake so kiyi mana,bansan wacece ke ba amma har a raina naji, na yarda dake dan Allah karki sa na fara zarginki, ki fadamun gaskiya wanene ya baki allurar da kika kai mashi? allura ce mai haɗarin gaske a lokacin da Allah baisa na faɗo na ceceki a hannun shi ba tabbas ba zaki rayu ba....    Hankali atashe sehrish ta ɗago idanunta tana kallon shi, nan da nan taji wasu hawayen sun sake wanko mata fuskarta cikin shessheƙar kuka tace"ya omar wlh ni bansan komai akai ba bazan iya cutar dashi ba kuma nima bazan so na cutar da kaina ba..........'    jinjina kanshi yayi tare da cewa"to ki fadamun wanene ya baki allurar"?    buɗe baki tayi zata furta haroon nan take ta sake ji an damƙi maƙoshinta saboda zafin da taji kawai saita fashe mashi da kuka saboda ta rasa yarda zata yi ta sanar mashi........'    Zuba mata ido yayi yana kallonta tana ta faman shan kuka, tuni yaji tsananin tausayinta ya kamashi,musamman daya dinga ganin fuskarta kamar su jahad ne ke kuka,     Cikin sauri ya dakatar da ita da cewa"its okey, kiyi hakuri banyi hakan dan na 6ata maki rai ba, inaso kawai na gano wanda ya baki allurar ne don inyi investigation akan shi, amma tunda bakison faɗi, zaki iya tafiya,     tsagaitawa tayi da kukan tana kallon shi cikin sanyin murya tace"dan Allah  kada ka zargeni wlh bazan iya cutar da wani acikin gidan nan ba, saboda na ɗauke ku tamkar ƴan uwana na jini na.......'      murmushi Omar ya ɗanyi kafin yace"don't worry ur self nima kamar yarda kika ɗauke mu haka muka ɗauke ki, ki kwantar da hankalin ki komai ya wuce insha Allah,amma aduk lokacin da kika tuna sunan wanda ya baki ita, ki hanzarta sanar mun pls......'    "Insha Allah zanyi hakan," tashi tayi tare da yi mashi sallama ta nufi hanyar fita daga falo dinsa, a hankali take tafiya hannunta dafe da saitin zuciyarta, muryar shi ce, ta sake katse ta da cewa"yana buƙatar a gyara mashi bedroom ɗinsa yakamata ki je, a firgice ta juyo tana kallon shi, ganin yarda ta razana ne yasa shi cewa"ki kwantar da hankalin ki, kada abunda ya faru jiya yasa ki dinga jin tsoranshi, nasan ko wanene ɗan uwana, am really proud of him, ki saki jikin ki in ba haka ba zai gane cewa wani abu ya faru adaren jiya,    jinjina mashi kai tayi tare da cewa"toh zanyi yarda kace," tana fadin hakan tasa kai ta fuce,    Murmushi Omar yayi saboda tunawa da babban aikin da sgr yaso yayi jiya, tabbas da yarinyar ta rasa ranta don ayadda yake jin wannan ƙarfin ba ƙaramin illatata zaiyi ba,    "godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata'ala da yabani ikon zuwa adai dai wannan lokacin har na ceci rayuwarta, na kuma taimaki ɗan uwana daga aikata wannan aika aikan," ya furta yana faman sauke ajiyar zuciya, *************💋 Gaba ɗaya sun hallara a saman dining chairs suna yin breakfast dinsu, Abban su tare da junaid, sai Ayaan da jahan ga kuma su irfan khaleed da jabeer da kuma Fawan, har yanzu bai fara sanya riga a jikinshi ba sai dae gajeran wando kawai yake zurawa yayi ta yawon shi,   "Aunty azmee ina reesh take ne, banganta ba"? Junaid ya tambaya yana kallon azmee dake tsaye tana saving dinsu,     Abbansu ma yace"tun ɗazu nake so in tambaye ta nima, yau banga daughter ɗita ba ina tashiga ne?   Murmushi azmee tayi tare da cewa"tashiga sashen Omar ne,"    cike da mamaki jabeer yace"wacece kuma sehrish? ko dai wannan yarinyar dana gani tana yawo acikin gidan nan? Ya tambaya yana kallonsu,   irfan yace"nima ina taso na tambaya wlh, naga kyakkyawar yarinya tana ta yawo acikin gidan nan gwanin burgewa,"   da buɗar bakin fawan sai cewa yayi "Oh wai dama mutun ce? Ae ni nayi tunanin ko idona ne ke ganemun ita shiyasa ban ta6a tambaya ba," dariya suka fashe da ita gaba ɗayansu banda shi fawan din da yayi mgnr, saboda shi bada wasa yayi maganarshi ba, duk a tunanin shi ko ya samu ta6uwa ne shiyasa yake ganinta,       "Sunanta Sherish tare da azmee suke aiki, amma na mayar da ita ƙanwarku ina fata zaku ji daɗin hakan, tunda dama baku da ƙanwa mace," acewar abbansu,    kallon juna su kayi atare kafin fawan ya kuma cewa"ni duk ba wannan ba, wai ina tukur mai aikin mu ne? Nayi kewar shi sosai tunda muka dawo banga gifcin shi ba acikin gidan nan,"? ya tambaya yana kallon junaid dasu twins,   murmushi suka shiga saki gaba ɗayansu batare da sunce komai ba,     Khaleed yace"wannan sullu6iyon mai aikin namu, dama nasan bazai kai labari ba halan an kore shi daga aikine"?    Junaid ne yace"kai yaya fawan yanzu kuna nufin baku gane wanene tukur ba? Wannan yarinyar fa itace fa tayi shigar maza tana mana aiki........'    Saboda tsabar ruɗu har suna haɗa baki wurin cewa"Are u serious!? ɗaga kai yayi tare da jaddada masu maganar shi yace"of course ku tambayi abba kuji,"     Kallon abban nasu sukayi suna jiran jin bayani murmushi yayi tare da cewa"itace mai aikin da kuka bari a matsayin namiji,"     cikin mamaki suke kallon shi sam sun gaza cewa komai saboda abun yafi ƙarfinsu wai tukur mai aikinsu ne ya koma mace ? dama maca ce tayi shigar namiji kenan? Murmushi fawan yayi aranshi yace "lallaikam nama har gida," kamar abbansu yaji mai yace sai ɗagowa yayi ya kalli fuskokinsu yace"ko da gigin wasa bana son wani ya ta6a mun ɗiyata,ko kallon banza wannan ban amince wani yayi mata ba,"     har suna haɗa baki wurin cewa"Insha Allah hakan ma bazata faru ba, ae ƙanwarmu ce," dariya junaid yayi ƙasa ƙasa saboda yasan halinsu sarai musamman fawan,  Sehrish~   Koda ta fito daga part ɗin omar, wuri ta samu anan upstairs ɗin ta zuƙunnna tana shan kuka ba don komai ba sai don baƙin cikin kasa furta sunan haroon da tayi, taso ta sanar ma Omar kodan ta fita zargi amma hakan yaci turo saboda maƙoshinta da taji an shaƙe mata shi, babban abunda take fargaba shine kada su fara zarginta akan abunda ba laifinta bane, yanzu kuma duk ranar da sgr ya tuna da wannan abun daya faru a tsakaninsu dole ya tuhume ta, batasan wane irin kallo zaiyi mata ba,😖   "Ashe so yayi ya kashe ni !" ta furta cikin sanyin murya, "ni bansan me nayi mashi ba, ya Allah ka kare ni daga sharrin shi, ya Allah kada ka bashi nasara akaina,"    tana cikin wannan tunanin sam bata ji takon tafiyarshi ba, fitowarshi kenan daga part dinsa ya kimtsa cikin suits farare ba ƙaramin kyau suka yi mashi ba,    tsayawa yayi yana kallon ikon Allah yarinyar da yake ta faman jira ta gyara mashi bedroom dinshi itace zuƙunne tana shessheƙar kuka, cike da mamaki ya ƙarasa har inda sehrish take sam bata zaci ganin shi ba, sai dae taga ƙafafunshi masu sanye da haɗaɗɗun takalma, gabanta ne taji yayi wani irin bugu duk da bata san wanene ba amma tana da tabbacin cewa shi neeee saboda ƙamshin turaren nan nashi,    ƙara ƙanƙame jikinta tayi tana faman zazzare ido a tsorace, muryarshi ce ta ratsa kunnanta da cewa"ke tashi tsaye,"    cikin sauri sehrish ta miƙe tsaye jikinta na kerma kamar wadda taga wani horror sam taƙi yarda ta kalli fuskarshi saboda ta tsorata dashi,      shiru ya ɗanyi baice komai ba tamkar mai nazarin wani abu, hannunta yabi da kallo sai faman kerma yatsun hannun suke yi,    "Are u okey"? ya tambayeta,cikin sauri tace"eh"     "Okey agyaramin bedroom ɗina," yana faɗin hakan ya kama hanya  ya wuce,   Sam takasa janye idanunta daga kallon bayanshi  har sai da ya 6ace ma ganinta, sannan ta wuce part din nashi, lokacin data shiga bedroom dinshi ba komai ta tuna ba face abunda ya faru atsakaninsu daren jiya, bin shimfiɗeɗen gadon shi tayi da kallo har yanzu zanin gadon a cukuikuye yake, saboda damben da suka sha jiya, hannu takai tare da yaye bedsheets ɗin nashi ta rungumo shi a kirjinta tana shinshina ƙamshin turarensa, ita kaɗae tasan irin yanayin da tashiga a wannan lokacin duk da firgicin da take ci amma hakan bai hanata jin wannan yanayin ba.............💋😉 *💋Boss💖Bature?*✍️ A galabaice take hura wutar murhun wani irin uban hayaƙi yake fitowa baƙiƙƙirin duk ya cika kitchen din, idanunta sunyi jawur kamar na mai shan taba, matashiyar yarinyace da bazata wuce shekara goma sha huɗu ba aduniya, a wani matsakaicin gida na masu rufin asiri, jikinta na sanye da koɗaɗɗen zani na atampha tayi ɗaurin gaba dashi, duk ya yayyage jikinshi yayi baƙiƙƙirin saboda dauɗa, gaba ɗaya ita kanta yarinyar abun ban tausayi ce, ta bushe ta rame ta ƙanjame yadda kasan skelaton haka take, saboda kasusuwan wuyanta da suka firfito mata waje kamar zasu fito daga fatar jikinta saboda tsabar rama, saboda koɗewar da fatar jikinta tayi baza ma a iya tantace launin fatarta ba, fara ce ko baƙa 😢 sai faman goho take yi agaban murfin tana hura wutar da bakinta amma wutar taƙi kama wa, zuƙunnawa tayi gaban murhun ta zabga uban tagumi hawaye na faman kwararowa daga idanunta, cikin murya kuka ta soma cewa"Ya Allah ka kawomin karshen wahalar da nake sha acikin gidan nan........'     Muryar mammynsu ce ta katse ta da cewa"AMAL!! wai uban wa kike so yayi wankin nan ne? zaki fito kiyi shi ko saina maki dukan tsiya ne? Hankali atashe tace"mammy iccen girkin ne ɗanye baya ci, tun ɗazu nake faman wahalar hura shi amma yaƙi ruruwa,"    Uban tsoki matar ta buga tare da cewa"wannan ba damuwa ta bace ba, ki tabbatar da kin hura wutar ta kama,sannan ki fito ki wanke mana kayan mu, bayan kin gama kuma ki share gidan,"     cikin ƙunar rai ta amsa mata da "toh," Sannan taci gaba da hura wutar don ta kama,     cigaba da magana matar tayi tana cewa"Yayarki nacen gidan huta, ta manta dake gaki nan a wulaƙance kin zama tamkar baiwa a wurin mu, da ace tana sonki ae bazata barki a hannun mu ba,"    Shiru Amal tayi hawaye na zuba daga idonta, har yau tagaza yarda cewa yayarta zata iya yi mata hakan, saboda me zata tafi tabarta hannun waɗannan mugayen? Ta tambayi kanta,    muryar mammyn tasu ce ta sake katse ta da cewa"hmmm dama tsiyar talaka kenan anyi mata hanyar arziƙi amma ta manta da mutane, baƙin halinku iri ɗaya dana uwarku, ae duk laifin laila ne ko uban waya faɗa mata ana yiwa ƴa'ƴan kishiya abun arziƙi," tana zaune saman gujera ƴar tsugunno sai faman sambatu takeyi kamar zautacciya, wata tsamurarriyar mata ce fara siririya ta fara tsufa don gashin kanta harya fara hurhura, jikinta na sanye da atampa riga da zane, ta tsoge ɗaurin ɗankwalin nan ture kaga tsire, hannunta na ruƙe da aswaki sae faman kwalkwalar haƙoranta takeyi wadanda sukayi jawur saboda tsabar cin goro, kai kana ganin ta zaka shaida cewa ba ƙaramar jarababbiya bace, irin tsaffin nan da basa gajiya da mita,    daƙer Amal tasamu wutar ta huru, sannan ta fito agalabaice, kai tsaye ta wuce inda uban kayan wankin suke dila guda,gaba ɗaya kayan sawarsu ne su duka dana uwar dana su abra da hayam, ga zannuwan gado da barguna duk sun tara mata su don ta wanke, abun babu imani acikin shi, babu irin wahalar rayuwar da yarinyar bata shaba,uƙuba iri iri suke yi mata, ko bacci bata samu, in ma tayi baccin da duka suke tashinta, ko kuma taji saukar ruwa bokiti guda ajikinta, fatar jikinta duk cizon sauro ne gashinan ruɗu ruɗu, saboda awaje take kwana, su kuma su shige ɗaki sai ita kaɗai ga tsora da Allah yayi mata, kullum cikin zullumin mai zai faru da ita take yi, duk yarda taso su haɗu da yayarta abun yaci tura, a halin da ake ciki ita kanta Amani batasan cewa yarinyar na raye ba, tun wani zuwa da tayi suka sanar da ita cewa yarinyar ta 6ace an neme ta an rasa, hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, a lokacin tasha kuka sosai wurin neman yarinyar amma babu ita babu alamarta, tun tana sanyawa a nemo mata ita har tagaji ta daina saboda kullum babu labarin anga yarinyar shiyasa ta fidda rai da ita, ashe lokacin 6oye yarinyar sukayi a gidan makwabtansu acikin wani ɗaki aka rufe ta kamar akuya, duk in amani zataso maiduguri sai su kaita can gidan ajiya har tazo ta tafi bazata sani ba, hakan yasa basu ta6a haɗuwa da ita ba tun auranta da Abbas na wata takwas a lokacin abun ya faru, taso ta ɗauki yarinyar ta zauna a wurinta amma saboda baƙin hali irin nasu sun hanata ganin ƴar uwarta....😭     "Maza ki hanzarta ki wanke mana kayan," muryar mammynce ta katse ta,     Hannu tasa ta ɗauki bokitin dake ajiye awurin kayan, sannan ta wuce izuwa inda fanfonsu yake,ruwa ta tarbo acikin shi sannn ta ɗauke shi tadawo ta ajiye, ledar klin ta dauka tare da fasawa ta zazzaga aciki sannan tashiga tsoma kayan aciki tana wankewa idonta na zubar da kwalla,      suna cikin wannan zaman suka ji ƙarar dirar mota a ƙofar gidan, washe baki mammy tashiga yi tana cewa"ƴar albarka ta iso, nasan tadawo mana da abun arziƙi, ni dae naji daɗi ƴa'ƴana badae farin jini ba........' bata ƙarasa maganar ba Hayaam tashigo cikin gidan  ba ƙaramin wanka ta ɗauka ba, jikinta na sanye da swiss lace ash colour, doguwar riga akayi mata dashi, ta matse ta tsam tamkar in tayi motsi rigar zata yage saboda yarda tayi tighting ɗinta, ta  kashe ɗaurin kallabi nan, mayafin kuma ta aza shi a kafaɗa,    fuskarta ɗauke da murmushi ta ƙarasa wurin mammyn tasu, tashi tayi ta rungumeta tana cewa"ƴar albarka sai yau zan saki a idona"?   Murmushi hayamm tasaki tare da cewa"Ammi yau ɗin ma sa'a kika ci, ki gode ma Allah da kika ganni yau, domin kuwa gobe zan wuce abuja nazo ne nayi maki bankwana saboda zan koma can da zama ina fata Aunty laila ta sanar dake game da komawa ta can? Ta tambaya tana kallonta,    gaba ɗaya Amal ta kasa kunne tana sauraronsu,    Washe baki tayi tare da cewa"ta sanar dani mana, ae ba ƙaramin daɗi naji ba kwara ki tattara ki tafican kema ki shafo mana arziƙi,"     Fari da ido hayaam tayi tare da cewa"baki da damuwa in dae nice mommy, arziƙi mun gama yin shi, muddin burina ya cika tuni zan canza maku tamfatsetsen gida na kece raini, na siya maku manyan motoci na alfarma sannan na biya maki aikin hajji, mommy kuɗi fa har sai kin gaji dasu wlh," ta faɗi tana faman sakin murmushi,    Cike da farin ciki mammy tace"Allah?   "wlh kuwa mommy," hayamm ta bata amsa,     ganin amal na kallonsu yasa mammyn kwatsa mata tsawa tace"zaki mayar da hankalin ki kan kayan da kike wankewa ko saina zo nan na karya maki wuya, magulmaciyar banza ƴar sa ido," jiki na rawa amal ta mayar da hankalinta kan kayan da take wanke wa,      ruƙo hannun hayamm mammyn tayi sannan tajata suka shige cikin ɗakinsu, don kar taji me zasu ce,     a hankali take wanke kayan  tunani iri iri na zuwa mata aranta, tana yawan jin suna ambaton abuja abuja, kodai can aunty amani take zaune ne? Ta tambayi kanta, jinjina kai tayi tare da cewa"ina da tabbacin cewa auntyna tana zaune acan itama, dole na nemi mafita bazan zauna su kashe ni ba, zan gudu ne batare da saninsu ba," ta fadi tare da tsame rigar da ta sanya acikin ruwan wankin..........'😳   **************** A 6angaren su hossana kuwa saboda damuwar da suka shiga na jin cewa ya Omar ɗinsu na da aure gaba ɗayansu ba wanda yayi breakfast saboda damuwa, su kansu sun rasa gane dalilin dayasa suke jin kishin matar shi data kirasu a waya,  abincin da jahad ta shirya masu har yayi sanyi saboda tun safe yake ajiye saman dining table babu wanda ya ta6a shi, gashi har ƙarfe ɗaya yanzu yayi na rana,      A tare suke kabbara sallah bayan sun kammala suka zauna suna addu'o'i, shiru jahad tayi tana sauraron addu'ar hossana da take yi,    "Ya Allah kasa mafarki ne ba gaske ba na cewa ya Omar yana da mata, in ma dagaske ne ya Allah kasa ya sake ta su rabu, zuciya ta tafarfasa takeyi mun bazan iya jurewa ba........'     katse ta Jahad tayi da cewa"hossana kina a hayyacinki kuwa? ya sake ta fa kika ce? Idan yana son matar shi fa?    harara hossana ta jefa mata tare da cewa"waya faɗa maki yana sonta? Auren dole ne akayi masu, da ace yana sonta ae da bai 6oye mana cewa yana da mata ba har da ciki...'        Itama jahad ɗin harar ta mayar mata tare da cewa"baki da hankali wlh,dagaske ɗin ke zararriya ce, yaya omar yana son matarshi, ke bakiji muryarta ba yarda take magana daga gani tana cikin kwanciyar hankali, kuma tana samun soyayyar mijinta tunda gashi har tana da ciki zata haifa mashi baby..........' jahad bata ƙarasa maganar ba, hossana takai ma wuyan hijabinta cakuma tana cewa"Ni ce zararriya? ɗaga kai jahad tayi alamar e,     Bugu hossana tashiga kai mata, ganin bazata iya jurewa ba yasa suka kacame da faɗa, abu kamar wasa sai da dukkansu suka sha kuka, dama ransu a6ace yake, duk don saboda matar Omar,    (Sehrish tayi tsiya) tsaf ta kammala gyara mashi bedroom dinshi da toilet dinshi da falonsa duka ko'ina a kimtse tabar mashi shi, fitowa tayi ta sauko down stairs a lokacin duk sun kammala yin breakfast ɗin nasu babu kowa a falon, kai tsaye ta wuce bedroom ɗin Haroon gabanta na faduwa rass rass, ƙopar a rufe take don haka saita sanya hannu tare da yin knocking ɗinta, daga cikin ɗakin tajiyo muryarshi yana cewa"Wanene"?    "Ni ce," ta bashi amsa cike da ƙarfin guiwa,    buɗe mata ƙopar yayi fuskar nan ɗauke da murmushi, jikinshi na sanye da singlet fara tare da shorts baƙi,    "shigo daga ciki mana," ya faɗi yana nuna mata hanya, kallon shi kawai takeyi , sa kai tayi ta shiga ciki  daga tsaye ta tsaya tana kallon shi, rufe ƙopar yayi sannan ya juyo ya kalle ta yace "wlh har naji sanyi araina dana ganki cikin ƙoshin lafiya,ae nayi tunanin  e warhaka kina asibitin kwance magashiyyan rai hannun Allah.....' bai ƙarasa maganar tashi ba tace"me nayi maka? Meyasa kake son kashe ni? saboda me ka bani wannan allurar?     tafi yayi da hannunshi yana dariya, wuce ta yayi tare da samun wuri daga gefen gadonshi ya zauna yana facing ɗinta yace"Ko da ace zan iya kashe kowa a duniyar nan, ni bazan iya kashe abunda raina ke so ba!!! nasan cewa ba zaki mutu ba, akwai wanda zaizo ya taimake ki shiyasa nayi hakan ! kinfiye taurin kai shiyasa na gwada maki kaɗan daga cikin shaiɗancina, kin manta maganar da kika faɗa mun nacewa NAMIJI kike kallo? Shiyasa na haɗaki da namijin...........' ƙarasa maganar yayi yana faman tiƙar dariya, sakin baki sehrish tayi tana kallon shi. Da ƙyar ya tsagaita da maganar tashi yana kashe mata ido yace"Yarinya taji maza,baki ban labari ba ya kuka ƙare jiya?     shiru tayi tana kallon shi kawai saboda abun yafi ƙarfinta haroon ba ƙaramin shaiɗani bane,      ta6e bakin shi yayi yana kallonta sannan yaci gaba da cewa"wannan allurar da na baki, miyagu irina suke amfani da ita, aduk lokacin da mutun yayiwa kanshi allurar nan, imanin shi gaba ɗaya take cire wa, zai iya yi ma mata sama da goma sha biyar raping a lokaci guda batare da ya gaji ba tamkar engine zai dinga aiki, sannan koda ace mahaifiyarshi ce akusa dashi itama hakan ce zata faru da ita ba zai iya tantance fari ba balle baƙi, saboda gaba ɗaya take tayarwa mutun da wata irin jarababbiyar shawa'a da kuma ƙarfi na ban mamaki, kuma muddin a lokacin bai samu ya kawar da sha'awarnan  ba, to fa zuciyarshi zata iya bugawa nan take,.......'    tunda ya soma bayani sehrish ke kallon shi cikin tsananin tashin hankali har sai da yakai ƙarshe sannan cikin sanyin murya tace"me yasa ka fita daban acikinsu ne? Saboda me kake son cutar da shi ne? idan ni nayi maka laifi saboda me laifin zai shafe shi?       shu'umin murmushi haroon ya saki  kafin yace"tun ina yaro nake da son yin mugunta, ni ko dariya ban cika yi ba sai in anyi abun mugunta sannan take zuwa mun, burina kawai naga kowa cikin masifa da tashin hankali,natsani inga ana ta rayuwar farin ciki mai ɗaurewa, wannan ne dalilin dayasa nakeson in kawo canji acikin gidan nan,". Hankali kwance haroon ke kora mata bayani batare da nuna alamun wasa ba,     tuni taji idonta sun ciko da kwalla cike da takaici tace "tausayinka nake ji ! kana bani tausayi saboda kai abun tausayi ne, ban ta6a tunanin cewa a jinin abba za'a samu mai irin waɗannan mugayen ɗabi'un da halayen irin naka ba, saboda me yasa kai ba zaka yi koyi da sauran ba? ka zama mutumin kirki tamkar sauran"?     tasowa haroon yayi daga zaunen da yake ya ƙarasa dab da inda take  a wannan karan fuskarshi babu wasa acikinta yace"kina so in shiryu ne? In zama mutumin kirki?    ɗaga mashi kai tayi alamar eh,   Murmushi haroon yayi kafin yace"kece mutun ta biyu, da kikayi mun fatan shiriya arayuwata, sai dae kash hakan bazai ta6a yiyuwa ba sehrish ni ba cikakken mutun bane kamar yarda kike tunanin....................' a wani irin firgice sehrish ta ɗago tana kallon cikin idanunshi fuskarta cike da tsoro tace"kana nufin kai ba mutun bane"?     dariya ya ɗanyi kafin yace"kona faɗa maki ba zaki yarda ba, amma bari na sanar dake wani abu da baki sani ba, ni da kaina na turo marshal Omar ɗakin sgr domin ya taimake ki ! kuma ni ne nan na hana ki furta sunana agaban Omar, na shaƙe maki maƙoshinki na hana sautin fita daga bakin ki, shin bakiyi mamakin taya akai duk nasan da wannan ba !!!!!!!!!!!    Zazzare ido sehrish tayi gabanta na faɗuwa, tuni zufa ta soma tsattsafo mata, ja da baya da baya tadinga yi tana kallon shi.....   dariya sosai haroon yayi kafin yace"Shiyasa nace ki nemi tsari daga sharrina wlh ni shaiɗanin aljani ne ba mutun ba..........'   tunkan ya ƙarasa maganar tashi  Da gudun gaske sehrish ta  juya tare da buɗe ƙopar ɗakin nashi ta fuce ji kake garam !!!! Ƙopar ta datse,    Fashewa da dariya haroon yayi hada dafe cikin shi, daga bisani kuma ya ɗan tsagaita da dariya tare da cewa "Yarinyar tana da kyau, shiyasa na tsoratar da ita saboda inga kyawawan idanuwan nan nata masu kashe mun zuciya," ya furta tare da kai hannun shi saitin zuciyarshi yana faman sakin murmushi...............😳 tashin hankali anya kuwa haroon 👹😈      Ko kallon gabanta ba tayi saboda gudun da take yi gaba ɗaya ta gama firgita da haroon, bata yi wani aune ba ta faɗama junaid wanda ya nufo part din nasu, aikuwa gaba ɗaya suka faɗa ƙasa a manne da juna, atare zuciyoyinsu ke bugawa, musamman sehrish yana jin yarda zuciyarta ke faman bugawa da ƙarfi da ƙarfi, sun jima a haka kusan 8 mins sannan junaid ya ambaci sunanta "Sehrish,"     lamo tayi a jikinshi tana faman sauke ajiyar zuciya sai da ta samu natsuwa sosai sannan ta ɗago daga jikinshi,tayi gefe guda zaune dirshan tana kallon shi, tasowa yayi daga kwancen da yake yana faman sakar mata murmushi, tun safe yakeson ganin ta amma basu haɗu ba sai yanzu, shima zama yayi suna fuskantar juna da ita, wankan jeans da t shirt red colour ne ajikinshi, sai faman ƙamshi yake yi,       "Me ya faru ne naga kina ta tiƙar gudu kodai motsa jiki kike yi ne? ae muna da wurin gym acikin gidan nan,'    Ya faɗi yana kallonta, tayi mashi zuru da ido,    Ganin bata da niyar yin magana yasa shi cewa "Labari mai daɗi "! cike da zumuɗi tace "dagaske ? Wani irin labari ne wannan,  "Mafarki nayi jiya,"  "Me ya faru acikin mafarkin"? ta tambaye shi cike da son ji,     gyara murya yayi tare da cewa" mafarki nayi da wani narkeken zaki acikin wani ƙurmin daji ya biyo ki da gudun gaske, kamar zaki tashi sama haka kika dinga gudu kina ihu, kinsan waye ya cece ki a wannan lokacin"? Ya jefa mata tambaya, hankali tashe tace "A'a," ƴar hararar ta yayi tare da cewa"Ni ne nan, nazo da suffar jemage na ɗauke ki da fika fiki na mukayi sama can cikin gajimare...........' ganin yarda sehrish ta fashe da dariya yasa shi dakatawa da labarin yana kallonta, nuna shi tayi ta yatsa tana cewa"junaid kaji tsoran Allah, jemage fa kace? taya jemage zai iya ɗaukar mutun ? sannu malam fesal ka feso mun ƙarya,   gaba ɗaya suka sanya dariya, ba ƙaramin nishaɗi junaid ya sanyata ba duk da fargabar da take ciki, sun jima a zaune ƙasa suna fira, kafin daga bisa ni suka tashi, shi ya wuce mosque ita kuma  ta wuce bedroom ɗinta saboda tayi sallar itama,``The father Of Soldiers```   Story &  Written         By        Hafsat Bature ********** zaune take agaban mirror ta kammala shiryawa cikin doguwar rigar material blue colour mai kyan gaske, rigar tabi shape ɗin jikinta daga can ƙasa yayi ƴar baza tamkar mermaid haka shape ɗin ya bada,hoda ta ɗauka tana shafa ma fuskarta, bayan tagama ta ɗauki jan baki red colour ta murza, ba ƙaramin kyau tayi ba, set na brushes ɗinta ta ɗauko ta gyara eye brows ɗinta,bayan ta kammala gyara gashin giran, ta ɗauki ribbom ɗinta data ajiye saman mirror ɗin, tattara sumar kanta tayi tana kiciniyar ɗaure gashin amma sam tagaza saboda yawan da yayi,ita kanta tayi mamamkin yarda gashinta yake toho,ba ƙaramin tsayi yayi ba ga yawan gaske dami guda dashi,bakomai ya jawo hakan ba face mayukan da take amfani dasu na gyaran gashi sun amshi kanta sosai,    Sakin gashin tayi ya tarwatse a bayanta,saboda gajiyar da tayi da ruƙon shi,hannu takai cikin jerin perfumes dinta ta dauki kwalbar turaren flower bomb wanda junaid ya ɗaukar mata a lokacin da suka je siyayya saboda shima yana da irin shi, shiyasa ya haɗa mata dashi don suyi anko, feshe jikinta tayi da turaren ko'ina ya ji, nan take daddaɗan ƙamshinsa ya gaure ko'ina na ɗakin gaba ɗaya,mayar da kawalbar turaren tayi bayan ta kammala fesa wa, sannan ta zuba ma madubin ido tana kallon fuskarta,fuskar sgr ta dinga gani acikin mirror ɗin,nan take ta tuna lokacin da ta watsa a guje zata bar ɗakin ya biyota da gudun gaske tare da ruƙota a jikinshi,tafin hannunta tasa tare da rufe fuskarta tana faman sakin murmushi,sake tunawa tayi da lokacin da ya yage rigar jikinta kai tsaye ya afka mata,nan take taji wani irin sanyi da kasala sun rufar mata,gaba ɗaya fa sehrish ta shiga yanayi cike da shauƙi take tariyo duk wani abu da ya faru da ita a daren jiyan ta shagala sosai, taji knocking daga waje, muryarta cike da kasala tace"Wanene"?  .muryar Azmee tajiyo tana cewa"Auntynki ce," jin hakan yasa sehrish tashi tare da ƙarasawa ta buɗe mata ƙopar,tana a tsaye jikinta sanye da jallabiya ta mata maroon colour, ta yafa mayafi akanta ba ƙaramin kyau tayi ba,   sakin baki tayi tana kallon Sehrish kafin tace"Masha Allah, irin wannan kyau haka? sai kace sabuwar amarya,kinyi kyau sosai,"murmushi kawai sehrish ke saki,    matsa mata hanya tayi tare da cewa"Aunty azmee ki shigo daga ciki mana,"    "A'a basai nashigo ba, dama nazo naji ya kuka ƙare da Omar?ina fata kin sanar dashi gaskiya?     shiru sehrish tayi tana tunanin amsar da zata bata,ranta ne ya bata cewa kawai ta amsa mata da eh,saboda tana da tabbacin cewa muddin ta faɗa mata cewa takasa furta sunan haroon agaban Omar to tabbas azmeen zata iya cewa zata sanar dashi ita da kanta,idan kuma hakan ya faru to tabbas itama azmeen zata fuskanci irin abunda sehrish ta fuskanta wurin Furta sunan Haroon,kuma bazata so hakan ya faru ba don ba ƙaramin raɗaɗi taji ba,.    Sam ta tafi duniyar tunani taji muryar azmee ta katsa ta da cewa"Lafiya kuwa naji kinyi shiru baki ban amsa ba"?.     cikin sauri sehrish tace"aunty azmee na sanar dashi gaskiya kuma yace zaiyi bincike akan haroon ɗin,"    "Kin tabbata"? ɗaga kai sehrish tari alamar eh,   Jinjina kai azmee tayi tare da cewa"kayan sunyi maki kyau sosai Allah," murmushi sehrish tayi tana sunnar dakai,    Azmee ta kuma cewa"Munyi magana da junaid akan kayan nan naki da aka kai ɗinki,yace mun tailor din ya kammala ɗinki shi zaije ya amso maki kayan," cike da farin ciki sehrish tace"ngde sosoe aunty azmee na,"  ?   Murmushi azmee tayi tare da kai hannu taja kumatunta tace"bani zaki godemawa ba, ko kin manta waɗanda suka bada kuɗi akayi maki siyayyar ne"?    girgiza kai sehrish tayi tare da cewa"a'a ban manta ba,amma ina jin kunyar zuwa inyi masu godiya,"    "Gaskiya yakamata kije kam,zasu ji daɗi sosai su son cewa kinji daɗin abunda sukayi maki,ki same su kiyi masu godiya,"    "Insha Allah zanje," ta amsa mata, sakin kumatun nata tayi sannan ta juya zata futa, har ta ruƙe ƙopar zata buɗe ta jinkirta kamar mai tunanin wani abu, sake juyowa tayi tare da kallon Sehrish dake a tsaye tace"wai nikam akwai abunda nake taso in tambayeki tuntuni sai in ta mantawa,"    cike da kulawa sehrish take kallonta don jin me zata ce,   Cigaba da cewa tayi "a kwanakin baya kinyimun magana akan cewa kinason zuwa garinku domin ki duba ƴan uwanki da basa lafiya ko"? ta tambaya tana kallonta,    A ruɗe sehrish tace"ƴan uwana kuma aunty azmee? Su wa kenan ? ni ba muyi wannan maganar ba kodai kin manta ne"?    hararar wasa azmee tayi mata tare da cewa"banason wasa fa, kinsan me nake magana akai mana, nan kwanaki kikazomin kina kuka kina cewa in taimaka maki kije kiga ƴan uwanki shine kuma yanzu zaki ce mun har kin manta?    Hankali tashe sehrish tace"aunty azmee ni bani da wasu ƴan uwa, bani da kowa wlh, bansan akan me kike magana ba,"     mamaki ne ya kama azmee ganin yarda sehrish ta haƙiƙance akan cewa bata da wasu ƴan uwa kuma fuskarta babu alamun zolaya,bayan ita da kanta ta sanar da ita game dasu,    ɗaure mata fuska tayi tare da cewa"banason rainin hankali sehrish!kina nufin dama baki da wasu ƴan uwa!ƙarya ce kawai kika shirga mun?tun farkon zuwanki gidan nan aiki, kika sanar dani cewa ƴan uwanki ne basu da lafiya shiyasa kikazo neman kuɗin da za'ayi masu aiki, har na ranta maki kuɗi dubu ɗari tara domin ayi masu aiki a amatsayin kuɗin aikin ki na shekara ɗaya da rabi, shima wannan duk plan ne kika tsara mun !!!!?  Rai a6ace azmee ke magana hakan ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba, tuni idonta suka soma zubar da hawaye saboda tagaza gane kan me azmeen ke magana akai,.  ?    "Aunty azmee wlh ni duk bansan anyi wannan ba! Bamu ta6a magana dake akan cewa ina da wasu ƴan uwa ba,kuma ni ban amshi wasu kuɗi ba saboda ayi ma wasu aiki ba.....'    tunkan ta ƙarasa maganar azmee ta kwatsa mata tsawa tare da cewa"Ya isa haka Sehrish!!ashe dama ke maƙaryaciya ce!! kin cuce ni kinyi mun karyar cewa kina da ƴan uwa,ashe duk tsara ni kikayi saboda ki samu kuɗi,danasan haka kike da tunfarko ban yarda dake ba, wlh sehrish kinban mamaki kuma na gama yarda dake.......' tana kai ƙarshen maganarta, a fusace ta juya zata bar ɗakin cikin sauri sehrish ta ruƙo jallabiyar jikinta,muryarta na rawa cikin kuka tashiga cewa"wlh aunty azmee bansan komai game da abunda kike faɗa ba,na rantse maki da Allah wlh bani da wasu ƴan uwa aduniyar......' Karanta>>> Taswirar Ƙaddara Complete Novel Document   girgiza kai azmee tashi ga yi tana cewa"wlh kin ban mamaki sehrish,bansan haka kike ba ae da tun farko ban bari kin fara aiki agidan nan ba!!kin cuce ni kin rushe duk wata yarda da nayi maki,sai faman rantse rantse kikeyi mun ko tsoran Allah bakiji," rai a6ace azmee tayi maganar tare da fusge rigarta daga riƙon da sehrish tayi mata, cikin sauri tasa kai ta fuce daga ɗakin,   A wani irin yanayi sehrish ta zube saman guiwowinta tana faman sharara kuka,mutun ɗaya da ta yarda da ita aduniyar nan ayau ta juya mata baya akan abunda batasan dashi ba,har ga Allah ita gaskiyarta take faɗi amma azmee taƙi fahimtarta,tuni zazza6i ya fara hawa jikinta,sam tagaza tashi daga kneel down din da tayi 😭 Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! ?      Tun da azmee ta fuce daga ɗakin sehrish, kai tsaye ta wuce nata bedroom ɗin, shiga ciki tayi tana faman safa da marwa,ranta ba ƙaramin sosuwa yayi ba,gaba ɗaya taji sehrish tafara fitar mata arai,saboda ƙaryar da ta shirga mata,cikin ƙunar rai take cewa"kin cuce ni sehrish,banta6a tunanin zakiyi mun haka ba,natsani makaryaci arayuwata, me yasa tunfarko bata fito fili ta faɗamun cewa kuɗi takeso ba,don me za tayi mun ƙarya?    tuni idon azmee sun cicciko da kwalla saboda ƙululun baƙin cikin daya tsaya mata arai,daƙyar ta iya samun wuri ta zauna daga gefen gadonta tana cigaba da tunani acikin ranta,   "ɗan adam kenan!yanzu duk yardkyautatama yarinyar can sai da ta butulce mun,saboda farin cikinta nakeyin wasu abubuwan don na faranta mata,amma hakan bai hana tayi mun ƙarya ba!!idan har dagaske ne sehrish ba ta da wasu ƴan uwa ƙarya  ne tayimun,TO WAYE TASA NA TURA MA KUƊIN!!!!!!? miƙewa azmee tayi lokaci guda gabanta yashiga faɗuwa tuni taji zufa tasoma tsattsafo mata,hankali tashe tace"nashiga uku!! tabbas na tafka kuskuren yarda da yarinyar can!! meyasa tunfarko najata ajikina?kada fa ace da wata manufa tazo cikin gidan nan!!!   abubuwa iri iri suka dinga zuwa mata acikin ranta game da SEHRISH,😥 Lamarin dae ba daɗin ji 💋BOSS BATURE💋 A 6angaren su hossana kuwa tun bayan da suka yi faɗan nan atsakaninsu,su kayi fushi da junansu,saman gado hossana ta haye tana baccin wahala bayan ta gama shan kukan nata,Jahad kuwa bayan sun gama faɗan toilet tashiga tayi wankanta,bayan ta fito ta shirya cikin riga fara off shoulder tare da dogon wando baƙi,ba ƙaramin kyau tayi ba,musamman gyaran gashin kanta wanda akayi masu a wurin saloon ya ƙara ƙawata ta sosai,   komawa tayi ta zauna daga gefen gadon kusa da hossana, bin ta da kallo tayi sai faman sharar bacci takeyi tana jan minshari,haryanzu kayan baccin nan ne ajikinta tun na daren jiya, ?    Hannu tasa tare da bubbuga bayanta a hankali tana cewa"hossana ki tashi!ko baki jin yunwa ne?     tsoki taja tare da juya mata ƙeya don karta takura mata, sake bugun bayanta jahad tayi tace"wai ba zaki tashi bane!?     buge hannunta hossana tayi tare da cewa"ki rabu dani, babu ruwanki dani,idan banyi wankan ba jikinki ne ko nawa?ko kin ta6a ganin zararre mara hankali yayi wanka ne? ni mahaukaciya ce kibarni inyi rayuwata.......'cikin kuka hossana ta ƙarasa maganar,da alama abun ya ta6a mata zuciya dama ta tsani akirata da zararriya,   Cike da lallashi jahad tace"am really sorry hossana nasan ban kyauta ba,raina ne ya 6aci shiyasa har na gaya maki hakan,bazan ƙara ba insha Allah,"     tayi maganar tare da ruko hannun hossana donta tashi,fisge hannunta tayi daga cikin nata tace"pls jahad leave me alone,zuciyata ba ta mun daɗi,yaya Omar kawai nake jira yazo,"    Murmushi jahad tayi tare da janyo gashin kan hossana tana wasa dashi a hannunta tace"faɗa mun gsky hossana kodae son yaya omar kike ne"?     juyowa hossana tayi tare da kallonta fuskarnan ɗauke da murmushi tace"eh ina son yaya omar sosai ke fa"?     jiki asanyaye jahad tace"Wani kalar so kike nufi? Na soyayya da aure? ta tambaya tana kallonta,   hossana tace"shi nake nufi,jahad inason ya omar sosai,"   shiru jahad tayi gabanta na faɗuwa tuni yanayin fuskarta ya canza izuwa matsananciyar damuwa,ganin hakan yasa hossana tashi zaune tana kallonta tace"jahad naga kamar fuskarki ta canza meya faru ne"?    cikin sauri ta basar tare da ƙaƙaro murmushi tace"bakomai hossana,ni zan wuce kitchen na shirya mana lunch," tana faɗin hakan ta miƙe da hanzari tabar bedroom ɗin nasu,saukowa daga saman gadon hossana tayi tare da wuce wa cikin toilet don tayi bath,    sam jahad tagaza jurewa tana fitowa daga bedroom ɗin ta wuce cikin falon tare da samun wuri saman 3 seater ta zauna jiki amace,   "dagaske ne hossana ya Omar take so?amma hossana ba ta da cikakken hankali bana tunanin tasan menene *SO* ya Allah kasa hakane saboda bazan iya jurewa ba......' ta furta tare da kai hannunta saman goshinta,bakomai bane ya faɗo mata aranta ba face farkon haɗuwarsu dashi a asibiti,lokacin ba ƙaramin tafiya yayi da zuciyarta ba saboda yarda yake acting dinsa,kyawawan ɗabi'unsa da halayansa sune suka sa jahad faɗawa tarkon shi, ita kanta bata tashi tabbatar da hakan ba sai ranar daya sanya handkerchief dinsa yana goge mata hawayenta..........."    tayi nisa cikin tunanin nata  muryar hossana ta katse ta da cewa"jahad nayi tunanin zanzo na sameki a kitchen ne ashe kina nan zaune," firgit jahad tayi tana kallonta sai da ta dai²ta natsuwarta sannan tace"har kinyi wankan kenan," ta faɗi tana kallon hossana dake nufota jikinta na sanye da gown black colour, ta saki curly hairs ɗinta ya barbazo mata abayanta,     Amsa mata tayi da cewa"Eh baki ga har na canza kaya ba," ta faɗi tare da jujjuya mata donta gani,   Murmushi jahad tayi tare da cewa"kinyi kyau sosai," ta ƙarasa maganar tare da miƙewa tsaye tace"kizo muje kitchen ɗin atare saiki tayani aiki, muyi sauri mu kammala,"   Amsa mata tayi da toh, sannan suka wuce atare kitchen ɗin atare,   *************** Zaune yake acikin motarsu Ƙirar mercedes S450,ash colour,jikin shi na sanye da kakin sojoji,sai faman duba wrist watch ɗin dake hannun shi yake lokaci zuwa lokaci,gajiyar da yayi da jira ne yasa shi ɗauko wayarshi daga cikin trouser pocket dinsa ya buga ma Jahan kira nan take kiran ya shiga bada jimawa ba Ya ɗaga kiran, tsoki ayaan yaja tare da cewa"Wai kuɗin sunƙi fidduwa ne? Nifa nagaji da jira wlh," fuskarshi a yamutse yayi maganar,.     on the other hand jahan yace"Am sorry yanzu haka ma na fitowa daga bankin gani nan zuwa," ?    katse kiran ayaan yayi tare da mayar da wayar inda ya ɗaukota ya ajiye,   Cikin ƴan mintuna saiga Jahan ya fito daga cikin bankin hannunshi ruƙe da jaka,   Yana ƙarasawa gaban motar ya buɗe back seat dinta tare da yin wurgi da jakar ciki, sannan ya rufe ya kuma buɗe front seat ɗin ya shiga ya zauna a gefen Ayaan dake zaune a driver seat,   "Yau dae zamu jefar da kwallon mangwaro mu huta da kuda," acewar Jahan,murmushi ayaan ya saki yana kallon shi yace"baka ji daɗin da nakeji ba wlh,saboda a ƙagare nake da mu bashi kuɗin nan mu huta da shegen nacin nan nashi,ya takurama rayuwarmu gaba ɗaya,Haroon bai da imani jahan," fuskarshi a yamutse yayi maganar.  Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! ?         "har yau in na tuna abunda yayi mana zuciyata tafarfasa takeyi mun saboda 6acin rai,haroon ya wulaƙanta arayuwarmu,Allah bazai ta6a barin shi ba, Insha Allah ƙarshen shi bazaiyi kyau ba," acewar jahan    Jinjina kai Ayaan yayi kafin yace"amma Jahan kana tunanin in muka bashi kuɗin nan zai goge video ɗin duka?am just doubting about it,don na lura ba ƙaramin shaiɗani bane,    jahan yace "ae ba zamu bashi kuɗin ba har sai mun tabbatar daya goge videon agabanmu mun gani,"     "Duk da haka nidae ina fargaba wlh," cike da damuwa ayaaan yayi maganar,   Sun jima suna magana kafin daga bisani Ayaan ya tashi motar suka miƙi hanyar gida,babu wanda ke ma wani magana acikin motar saboda duk sun tafi duniyar tunani, gaba ɗaya zulluminsu akan haroon,   Koda suka ƙarasa cikin gidan basu shiga da kuɗin ba,acikin motar suka barsu cikin jakar saboda tsaro, sun ajiyeta ne da nufin in dare yayi suzo su ɗauketa su kai mashi,    Bayan sun fito daga motar kaitsaye suka shiga cikin gidan tare da wucewa bedroom ɗinsu don rage gajiyar da suka kwaso, Sehrish Tasha kuka kamar kamar me,har sai da zazza6i da ciwon kai mai tsanani suka rufar mata sannan ta lalla6a ta haye saman gadonta ta kwanta,ta jima tana roƙon Allah akan yasa mafarki ne ba gaske ba,abunda ya faru tsakaninta da Aunty azmeenta,gaba ɗaya jikinta baya mata daɗi saboda dama can akwai fargar haroon dake damunta ga kuma wani ciwon kan ya taso mata na Azmee,duk ita kaɗae😢   ta jima tana juyi asaman gadon amma bacci yaƙi ɗaukarta sai ma ciwon nata dake ƙara gaba,fuskarta harta fara kumbura saboda kukan da tasha,dakyar ta lalla6a ta tashi jikinta na kerma ta wuce toilet jin an fara kiran sallar la'asar,bayan wasu ƴan mintina tafito daga ciki tana faman ƙanƙame jikinta saboda sanyin daya rufar mata gashi ta ta6a ruwa,    wurin wardrobe ɗinta ta wuce tare da buɗeta, ta zura hannu ta ɗauki hijab ɗinta ta zurata ajikinta sannan ta ɗauko carpet ta shimfiɗa,sam babu natsuwa ajikinta haka ta kabbara sallar tana karanta fatiha hawaye na wanko mata a fuskarta a haka ta kammala sallar tare da zama saman dardumar ta ɗaga hannayenta sama cikin shessheƙar kuka tashiga cewa"Ya Allah kasa aunty azmee tadawo cikin hayyacinta ta gane cewa ni ba ƙarya nake mata ba,bansan ya zanyi ba in ta juyamin baya,Ya Allah ka yayemun damuwar da nake ciki,ka kawomin sauƙi acikin rayuwata.........' sosai sehrish tashiga jera addu'o'i tana roƙon Allah akan abubuwan dake damunta, Karanta>>> Kishi Da Aljan Complete Novel Document    ta jima zaune saman dardumar tana tunanin maganganun aunty azmee,har lokacin tana kokwantan cewa anya Aunty azmee tana a cikin hayyacinta kuwa,    Har kusan ƙarfe biyar sehrish bata motsa ba tana zaune zugudun,sai da biyar da rabi ta buga,sannan ta tashi jiki a mace ta cire hijabin tare da naɗe carpet ɗin duka ta haɗa ta jefa asaman gadonta,cikin toilet tashiga ta wanko fuskarta sannan ta fito ta ɗauki mayafi acikin wardrobe ɗinta ta yafa shi asaman kanta, sannan ta buɗe ƙopar ɗakin ta fito,    Kitchen ta wuce saboda sanin cewa suna da aikin dinner,lokacin da ta ƙarasa kitchen ɗin tuni Azmee har tayi nisa a aikin nata,shiga ciki sehrish tayi tare da tsayawa tana kallon azmee dake tsaye agaban kitchen sink tana wanke naman da ta ɗebo acikin roba, Gabanta na faɗuwa tace"Sannu da aiki aunty azmee," tamkar bata ji taba haka ta shareta, kusan sau uku sehrish na maimaita maganar amma taƙi amsawa,    Jiki asanyaye sehrish ta ƙarasa gaban chopping board ganin ta jera vegetables ɗin da zata yayyanka,  hannu takai zata ɗauki wuƙa,muryar azmee ce ta katse ta da cewa"kada ki ta6amun komai! Zanyi aikina ni kaɗai kamar yadda nasaba yi lokacin da baki nan,don haka ki fuce kibarmun kitchen ɗin....' fuska aɗaure tayi maganar batare da ta juyo ta kalli. sehrish ba, .  cikin tashin hankali sehrish tace"meyasa kika ce haka aunty azmee?tare muka saba yin aiki amma yau ke da kanki kike korata!?     rai a6ace azmee ta ɗago tare da nuna mata hanyar fita tace"dan Allah sehrish ki fuce kiban wuri!aikine nace bana so ni zanyi kayana,bana buƙatar taimakon ki,     ganin yarda azmee ke kwatsa mata tsawa yasata fashe wa da matsanancin kuka tana cewa"aunty azmee dan Allah kada kiyimun haka, nasaba dake na ɗauke ki tamkar mahaifiyata,wlh bazan iya yi maki ƙarya ba,ni bansan akan me kike magana ba,dan Allah kada kiyi fushi dani akan abunda banda masaniya akanshi,"!   tunda tasoma magana azmee ta zuba mata ido tana kallon ikon Allah,tamarasa me zatayi ma Sehrish ta huce,ƙiri ƙiri tana neman raina mata wayau,    "Sehrish in har kinason na kuma yarda dake to ki faɗamun gaskiya waye  kika bani acct number dinsa na tura kuɗin dana baki naira dubu ɗari tara da kikayi mun ƙaryar cewa ƴan uwankine basa lafiya!!?    Jinkirtawa sehrish tayi daga kukan da takeyi tana tunanin wai ma ina takai kuɗin?bama wannan ba yaushe ta amshi kuɗin?     "Ina sauraronki"! Muryar azmee ce ta katse ta daga tunanin da ta tafi,     girgiza kai tashiga yi tana cewa"aunty azmee kiyi haƙuri amma ni bansan me kike magana akai ba,"    tabbas in taci gaba da sauraron Sehrish ranta zai cigaba da 6aci ne don haka tace"ki wuce kiban wuri banasan sake jin wata magana daga bakin ki," jiki asanyaye sehrish ta juya tare da barin kitchen ɗin,    a hankali take tafiya jikinta ba kwari,   "Sehrish"! Muryar junaid ce ta katse ta,a hankali ta ɗago ta kalli gefen hagunta ta inda yake tunkarota,shigowar shi kenann cikin babban falon,    tunkan ya ƙarasa ya lura da yanyinta,tsayawa yayi kusa da ita yana kallon fuskarta da tayi suntum saboda kukan data sha,    Cikin sanyin murya yace"reeeesh! Meya faru ne kike kuka?    ganin cewa bata da wanda zata faɗawa mawa face junaid tunda shine abokin shawararta, don haka ta sanar dashi dukkan abunda ya faru da ita, tsakaninta da aunty azmee    Cike da mamaki junaid ke kallonta tamkar mai nazarin wani abu can dae yace"sehrish saboda me za kiyima aunty azmee ƙarya?meyasa zaki ce mata baki da wasu ƴan uwa?     gaba ɗaya sehrish tagama ruɗewa cikin tashin hankali tace"junaid wlh bani da ƴan uwa,ni bani da kowa ba ƙarya nayi mata ba,'    harara yaɗan watsa mata kafin yace"idan har dagaske baki da ƴan uwa,to su wanene kike kira a wayata? Lokacin da kike ɗaukar mun phone ɗina batare da sani na ba?kin manta last time har na nuna maki message ɗin da ƴar uwarki ta turo a wayata?sannan har kika roƙeni akan na kaiki ki gansu? A lokacin nace maki ki bari sai babban yayanmu sun koma Us ni da kaina zan kaiki ki gansu ko shi ma duk kin manta? Ya ƙarasa maganar cike da tuhuma,    wani irin jiri sehrish tadinga gani a indonta,a hankali tashiga furta "innalallahi wa'inna ilaihirraji'un!!!" ganin tana ƙoƙarin zubewa yasa shi yin saurin ruƙo shoulders ɗinta yana cewa"ko baki da lafiya ne"? Ya tambaya yana kallon eyes ɗinta dake a rufe, .....daƙyar ta iya furta cewa"junaid inaso nashiga bedroom ɗina,inaso na kwanta,"    gaba ɗaya sehrish tayi confusing ɗinshi lamarin ya ɗaure mashi kai,ruƙo hannunta yayi ya taimaka mata suka nufi bedroom ɗinta,buɗe mata yayi tashiga ciki, sai da yaga ta kwanta saman gadon sannan ya rufo mata ɗakin,   Cikin sauri ya wuce kitchen wurin Azmee,da sallama yashiga kitchen ɗin a lokacin tana tsaye agaban gass tana motsa farfesun data ɗaura,jin muryarshi yasa ta juyo wa fuskarta babu fara saboda ruɗin da sehrish ta jefa ta aciki, Amsa mashi sallamar tayi sannan tace"junaid kana buƙatar wani abune"?     girgiza kai yayi alamar a'a Sannan yace"dama kan maganar sehrish ne,ta faɗamun duk abunda ya faru,bansan meke damunta ba,ni kaina tayi confusing ɗina,"     "Junaid sehrish tayimun ƙarya,ban ta6a tunanin haka daga wurinta ba,meyasa za tayimun ƙaryar cewa tana da ƴan uwa,bayan ba haka bane saboda kawai ta cimma wani buri nata shine ta shiryamun plan,"!  Karanta>>> Shakuwa Ce Complete Novel Document    "Aunty azmee bana tunanin sehrish tana cikin hayyacinta ne!saboda nima nasan da maganar ƴan uwan nata,da wayata takeyin amfani wurin kiransu tun a lokacin baya,akwai ma last message da sister ɗinta ta turo mata a wayana,nacewa suna buƙatar taimakonta har a lokacin naso na tura masu kuɗi amma lokaci guda wayarsu tadaina shiga kwata kwata,sehrish da kanta ta nemi na kaita garinsu tagansu,nace mata Sai babban yayanmu ya koma Us sannan zan kaita amma yanzu kuma ace ta manta komai? Yyi tmbyar yana kallon azmee itama kallon nashi takeyi,   Cikin mamaki tace"junaid naji kace tana amfani da wayarka wurin kiransu,kuma har message sun tura maka dan Allah idan wayar na'a kusa inason gani,'    cikin sauri junaid ya zura hannu acikin aljihun wandon jeans ɗinshi ya curo wayar,dannata yashiga yi can cikin messages ɗin shi yashiga sai ga saƙon da Jahad ta tura mata,   Ƙarasawa yayi dab da azmee ya miƙa matar wayar yana cewa"kin ganshi nan,"   Hannu tasa ta kar6i wayar tashi ta zuba ma screen ɗin wayar ido tana karanta saƙon, Jinjina kai azmee tayi tare da cewa"Tabbas ƴan uwanta ne,idan bazan mantaba ta ta6a ambaton sunan JAHAD da HOSSANA amatsayin ƴan uwanta na jini,amma meyasa sehrish take ƙoƙarin mantawa dasu?ko don saboda tana cikin wannan daular ne......'   Junaid ne yayi hanzarin katse ta da cewa"i don't think so!rishi bazata ta6a mantawa da ƴan uwanta ba saboda abun duniya,na yarda da sehrish sosai kuma nayi imanin cewa rishi bazata ta6a yi maki ƙaryaba!tabbas akwai wani abu dake faruwa ne!!amma rishi bata cikin hayyacinta!!, .. azmee ta gamsu da bayanin shi amma har lokacin tana mamakin yarda akai hakan ta faru,    jinjina kai kawai tayi tace"yanzu ya zamuyi da ita junaid?inaso ni nasan awane hali ƴan uwan nata suke ciki ne,saboda inaso na haɗata dasu tun a lokacin naci burin hakan,nayi alƙawarin zan haɗata da ƴan uwanta,saboda yarda naga tana shiga damuwa akansu,    "Aunty azmee,yanzu babu halin yin wannan,in ma muka ce zamu cigaba dayi mata magana akansu to fa za'a samu matsala saboda zata iya samun ta6in hankali,amma in muka bi komai a hankali insha Allah dakanta zata dawo cikin hayyacinta wata rana,addu'armu kawai take buƙata,    Ajiyar zuciya azmee tayi maganganun junaid sun sa ta fara saukowa daga fushin da tayi da ita,    amsar wayarshi yayi daga hannunta sannan ya kuma cewa"pls aunty azmee karki ce zaki juya mata,ko kice zaki canza mata hakan zai iya haifar mata da damuwa,saboda ta saba dake sosai ta ɗauke ki tamkar mahaifiyarta,"   murmushi azmee tayi tare da cewa"shikenan junaid romeo insha Allah hakan ma bazata ta6a faruwa ba,kana da hankali sosai junaid shiyasa kake shiga ran mutane,ni nagaza fahimtar rishi,amma kai gashinan ka fahimce ta,"    murmushi shima yayi tare dasa kai ya fuce daga kitchen ɗin, ************* Agalabaice Amal ta kammala wanke uban kayan da suka tula mata,kaf sai da ta wankesu,ba ita ta kammala wankin ba sai wuraren la'asar,da zazza6i taƙarasa shi,gaba ɗaya ga66an jikinta ciwo suke yi mata,    ɗakinsu tashiga ganin babu kowa aciki saboda duk suna can ɗakin mamynsu hayaam da abra wadda bata jima da dawowa ba,tana jiyosu acikin ɗakin suna ta faman ciye ciyen kayan daɗin da abra tadawo masu dashi,babu wanda ya tuna da ita duk wannan uban aikin da tayi masu,shiga ciki tayi jikinta na kerma ta faɗa saman lumbutsetsiyar katifarsu,bargo taja ta lullu6e jikinta dashi,dakyar take numfashi,da wani irin hucin masassara numfashin ke fita,rayuwarta gwanin ban tausayi tun safe ko wanka batayi ba,saboda babu lokacin yin wanka,koda tayi niyyar yin wankan,sun riga da sun hanata amfani da sosonsu ko sabulun wankansu,wani lokacin in jikinta ya soma yi mata tsami,ruwa kawai take ɗiba tashiga ta watsa,daga bayane tayi dabarar yankar buhu tayi amfani dashi amatsayin soso, ba sabulu haka take gurje jikinta dashi,😭   Cike take da tsoran karsu shigo su same ta acikin ɗakinsu,saboda sun hana ta shiga ko'ina na gidan in ba kitchen ba,shima ɗin in zatayi masu girki ne, tana acikin wannan yanayin tajiyo murya abra tana cewa"ke!uban mi ya kawo ki cikin ɗakin mu?ba mamynmu ta hanaki shigar mana ɗaki ba!! A fadace tayi maganar,tana a tsaye bakin ƙopar ɗakin,yarda kasan photocopy ɗin aunty babba haka kamanninta suke,   Shiru Amal tayi batace komai ba zuciyarta ce kawai ke ta faman bugawa,   Rai a6ace abra tace"ko ki tashi kona zonan inyi wurgi dake ƙazama kawai,"    har lokacin Amal tagaza motsawa saboda nauyin da jikinta yayi mata,jinjina kai abra tayi tare da shiga ciki azafafe don tayi wurgi da ita,har takai hannu zata fisgi bargon da ta lullu6e dashi,jin muryar hayaam yasa ta dakata daga ƙoƙarin cire mata bargon da take yi,   Shigowa cikin ɗakin tayi tare da cewa"meya haɗaki da ita ne,naji kina ta faɗa,"?    turo baki abra tayi tare da nuna Amal ɗin da hannu tana cewa"baki ga yarda ta haye mana katifarmu ba da wannan baƙin jikin nata duk dauda,"    Sai lokacin Amal tasamu damar buɗe bakinta daƙyar murya na rawa tace"dan Allah kuyi haƙuri bani da lafiya,banjin daɗin jikina,"😭? dakatar da abra hayaam tayi tare da cewa"ki rabu da ita,wahalar tayi yawa just for to day ta huta,tunda bata da lafiya," sam ba haka taso ba,bata ji daɗi da Hayaam ta hanata hukunta amal ba,a fusace ta fuce daga ɗakin tana huci Shiga ciki hayaam tayi tare da samun wuri daga gefen katifar ta zauna,jin muryar Amal tana sambatu  na raɗaɗin ciwo yasa ta kasa kunne tana sauraronta, ?    "Ina jin cewa bazan rayu ba,dan Allah ku kaini wurin auntyna,inaso naganta kafin na bar duniya,"    dariya Hayaam tayi tare da cewa"aikuwa dae ba zaki ta6a ganinta ba adae nan duniyar, ae kin ɗaura aure da wahala tunda kika bari aka haifoki acikin gidan nan," tayi maganar tana ƙarashe dariyarta,   Amal kuwa fashewa tayi da kuka mai cin rai,    tsawa hayaam ta daka mata tare da cewa"yi mun shiru, kuka baya maganin komai sai ma ya ƙara jaza maki wani ciwon," shiru Amal tayi tana shassheƙar kuka ƙasa ƙasa Shigowa abra ta sake yi hannun ta ɗauke da wayar amani iphone 13 sai faman ruri take yi,miƙa mata wayar tayi tare da cewa"Sofwan ne ke kiranki,"  "ɗan wahala," ta fadi tare da kai hannu ta amshi wayar,juyawa abra tayi ta kalli Amal dake ƙumshe cikin bargo,guntun tsoki taja tare da cewa"salon ki sakarwa mutane miyan bacci asaman katifarsu,sai kin shanye shi don ubanki," ta ƙarasa maganar tare da kama hanya ta fuce daga ɗakin, Kara wayar tayi a kunnanta bayan tayi picking call ɗin,magana suka shiga yi dashi akan tafiyarta,duk wulaƙancin da tayi mashi hakan baisa ya rabu da ita ba, sai ma kiranta da yayi akan cewa gobe yanaso su tafi tare yakaita abujan, Sun jima suna waya kafin daga bisa ni su kayi sallama, tana ƙoƙarin ajiye wayar wani kiran ya sake shigowa,tsoki ta ɗanja tare da cewa"wani jarababben ne kuma yake kira na"!?    Duba screen ɗin wayar tayi Sunan AMANI ne ya bayyana,ɗan juyawa tayi ta saci kallon Amal dake ƙumshe cikin bargo alamu sun nuna cewa bacci yayi awon gaba da ita,hakan ne yasa ta ɗaga kiran tare da karawa a kunnanta tare da yin sallama,   On the other hand amani tace"wa'alaikum salam,hayam y kk ya gida yasu mammy"?    yatsina fuska tayi tare da cewa"duk suna lafiya,"    Amani tace"labarine ya same ni daga wurin aunty laila nacewa zaki koma gidansu Abbas da zama,sam abun bai dace ba wannan abun kunyar har ina?menene alaƙarmu dasu da har zaki koma gidan surukan mu da zama?amatsayin ƙanwar matar yayansu!  Jin wannan maganar ta Amani yasa ran hayaam 6aci,miƙewa tayi daga zaunen da take saboda tsiwa tamkar zata fasa screen ɗin wayar haka tashiga cewa"Ki tsaya iya matsayinki AMANI!!babu ruwanki dani, iya sa idone kawai naki  kada kice zakiyi mun shisshigi acikin lamarina! Ni ba kamar Aunty laila bace data saba jan ki ajiki har tayi maki sanadin auren Abbas,kina magana ne da HAYAAM!!!yakama ki iya bakin ki!!!! ?   jin yarda hayaam ke zazzaga mata rashin mutunci yasa tayi rejecting kiran,   tsoki hayaam ta saki tare da cewa"matsoraciyar banza!!ae banso kika kashe kiran ba,so nayi na sauke maki kwandon rashin mutunci shashasha kawai," rai a6ace ta ƙarasa yin maganar tare da yin wurgi da wayar saman katifar,kama hanyar fita ɗakin tayi domin taje ta sanarwa mamaynsu yarda su kayi da Amanin,  fitarta ke da wuya, Amal ta buɗe idanunta  waɗanda suka kumbura jawur saboda raɗaɗin ciwo, ta samu bacci amma tsiwar hayaam ce tafarkar da ita, gaba ɗaya duk wayar da su kayi da amani tana ji a kunnanta,saboda taji lokacin da hayaam ta ambaci sunan Amani, Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! ?    A hankali ta sanya hannunta tare da yaye bargon,a galabaice ta ɗan tashi zaune, hannu takai tare da ɗaukar wayar hayaam wadda tayi wurgi da ita asaman katifar kuma cikin sa'a wayar bata kai ga shiga security ba,    jiki na kerma ta shiga wurin kiran,sai ga sunan amani ya bayyana a list ɗin farko da tayi waya dasu,cikin sauri Amal ta buɗo numbarta, zuba ma numbar ido tayi tana tunanin yarda zata ɗauki numbar,babu wurin da zatayi copying dinta,tuni hawaye sun soma zarya a fuskanta, wannan shi ake ce ma ga ƙoshi ga kwannan yunwa,   runtse idonta tayi tare da buɗe su  akan screen ɗin wayar,nan take taji cewa zata iya haddace numbar akanta,muddin taci gaba da bitarta akanta, a hankali take ƙarewa numbers ɗin kallo tana naɗarsu akanta,motsin mutun taji alamar an tunkaro ɗakin cikin sauri  Amal ta fita daga wurin numbar amanin ta danna power ɗin wayar tayi duhu sannan ta ajiyeta,da hanzari tashige cikin bargon ta lullu6e dukkan jikinta, Hayaam ce tashigo  kai tsaye ta ƙarasa inda wayar take tasanya hannu ta ɗauka tare da fucewa daga ɗakin,   ajiyar zuciya Amal tashiga saukewa,har lokacin tana cigaba da bitar numbar amani akanta, ******************* Bacci sosai sehrish tasha, har wuraren ƙarfe biyar da wani abu babu alamun zata farka kamar matatta, kusan sau huɗu azmee na leƙowa don taga kota farka saboda ta lallashe ta akan abunda ya faru amma duk in tashigo sai ta same ta tana ta faman shan bacci,  Ƙarar jiniyar motocinsu ce tasa sehrish farkawa a gigice, fuskar nan tayi jaga-jaga da ita saboda kukan da tasha,ko da ta farka zuciyarta nata faman bugawa, a kasalance ta tashi zaune saman gadon tana faman sauke ajiyar zuciya, idonta takai kan agogon bangon dake manne, hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba ganin cewa har lokacin sallar magrib yayi, gashi ba tayi la'asar ba, cikin sauri ta sauko daga saman gadon ta wuce cikin toilet donta ɗaura alwala, ? Yau da wuri suka dawo, Abbansu tare da marshal Omar da kuma Sgr sai kanal Yousouf, a nan main palour ɗin suka rarrabu, Abbansu tare da kanal yousouf suka wuce bedroom ɗinsu dake a nan down stairs, Omar da Rafayet atare suka haye upstairs,  Tuni azmee ta kammala jera masu dinner ɗinsu a dining, duk anan suka hallara suka ci abincin, banda sgr da bai fito ba, bayan sun kammala ita tashiga kwashe warmers din da sauran tarkacen da sukayi amfani dashi tana kaiwa kitchen, ganin tana ta faman ɗawainiya ita kaɗae ba sehrish yasa junaid kama mata kayan suna kaiwa kitchen atare ba ƙaramin daɗin hakan taji ba,barin shi tayi a cikin  kitchen ɗin ita kuma ta wuce don ta gyara masu  dining area ɗin, kafin ta dawo har junaid ya kammala yin wanke wanken kayan da sukayi amfani dashi, tare da gyara kitchen ɗin tsaf tamkar ba'ayi amfani dashi ba,    tsayawa tayi tana kallon shi yana ƙoƙarin haɗama sehrish cornflakes acikin  kofi,   Juyowa yayi ya kalle ta tare da cewa"aunty azmee irin wannan kallo haka"?  Murmushi tayi tare da cewa"junaid kai na musamman ne,kana bani mamaki yanzu kai da kanka kayi wanke wanken nan?kuma ka gyara kitchen ɗin nan?  Murmushi yayi tare da cewa "menene aciki aunty azmee?nifa ba aikin da bazan iya yi ba,kuma aiyukan mata suna burge ni sosai, naji ma ina shawa'ar inga ina wanke wanke girki da shara,"    dariya sosai azmee tayi tana girgiza kai tace"gsky baka da dama junaid, koda yake abune mai kyau ka koya,yana da amfani hakan saboda wata rana zaka taimaki matarka ne da wasu aiyukan cikin gidan,Ko ba haka ba?" ta tambaya tana kallon shi,.     ɗaga mata kai yayi alamar eh, sannan yace"aunty azmee ki tayani da addu'a Allah ya cikamin burina,inaso nayi aure very soon insha Allah end of this year.....' kasa ƙarasa maganar yayi ganin yarda Azmee ta saki baki galala tana kallon shi,   fashewa da dariya yayi a lokacin har ya kammala haɗa ma sehrish cornflakes ɗin,    "Joking aside pls faɗamun gaskiya amma dae wasa kake mun ko"?    girgiza mata kai yayi alamar a'a sannan yace"just keep praying for me, insha Allah soon i wll get marriage," yana faɗin hakan ya kama hanyar fucewa daga kitchen ɗin hannun  shi ɗauke da Cup sai faman tiriri yake, Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! ?   shiru azmee tayi tana kallon bayanshi har ya 6ace mata, lamarin ya ɗaure mata kai tabbas tasan halin junaid tunda harya iya furta mata aure yakeso to kuwa fa auren zaiyi dagaske, kuma duk abunda ya nuna yanaso sai abbansu ya mara mashi baya,  "Ashe zamu sha biki," ta faɗi da dariya a fuskarta,     Knocking kopar ɗakin sehrish ya shiga yi, a lokacin har wani baccin ya soma ƙoƙarin ɗaukarta asaman sallayar,tana jin bugun ƙopar a firgice ta tashi tana faɗin "Waye"!    daga waje junaid yace"Mijinki ne insha Allah," ita kanta batasan lokacin da tasaki murmushi ba, ?   "Ka shigo ciki," ta bashi amsa, tura kopar yayi tare da sa kai yashiga ciki yana faman zabga mata murmushin nan nashi, wuri yasamu kusa da ita anan ƙasa ya lankwashe ƙafarsa ya zauna tare da miƙa mata cup ɗin yace"nasan zaki buƙaci wannan,haɗine na musamman daga mijinki insha Allah,"  fashewa da dariya tayi tana kallon shi, kafin ta zuro hannayenta daga cikin hijabin jikinta ta kar6a, jikinta har rawa yake yi wurin ɗaukar spoon ɗin dake aciki tashiga ɗebowa tana kaiwa bakinta, ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,   Tun tana sha da cokali har ta tsame cokalin daga cikin kofin ta miƙa mashi tare da cewa"ruƙe mun," hannu yasa ya kar6a, kafa cup ɗin tayi abakinta tashiga kwankwaɗarshi harta shanye duka,  tausayi ta bashi saboda ya lura ba ƙaramar yunwa take ji ba, cikin sanyin murya yace"nasan kina jin yunwa sosai,bari naje na kawo maki dinner ɗinki," yayi maganar tare da yunkurawa zai miƙe cikin sauri tace"a'a nagode da wannan ma,ba yunwa bace damuwata ba, abunda ke damu na shine Har yanzu aunty azmee fushi take dani"? fuskarta ɗauke da damuwa tayi maganar,    "Kada kisa damuwa aranki, nayi ma aunty azmee magana kuma ta fahimce ki,tun ɗazu ma take ta son tayi magana dake,"    Cike da farin ciki tace"dagaske Aunty azmee bata fushi dani kuma nema na take"?    jinjina mata kai yayi alamar eh, cikin sauri ta miƙe tana naɗe dardumar don taje ta ganta,     ɗaukar cup din da ta ajiye yayi sannan yayi mata sallama ya fuce daga ɗakin,     cire hajib ɗin tayi, sannan ta ɗauko mayafi mai girma ta rufe jikinta dashi, buɗe ƙopan tayi sannan ta fito tare da wuce wa ɗakin azmeen, kwankwasa mata ƙopa tayi, a lokacin azmee bata jima da kammala salla ba,    tasowa tayi tare da sanya hannu ta buɗe mata ƙopan, jikinta na sanye da dogon hijabi hannunta na ruƙe da cazbaha,    Zuba ma sehrish ido tayi tana kallonta, cikin en ina tace"Aunty azmee dama junaid ne yace kina son gani na," ta ƙarasa maganar tana sunnar dakai cike da fargabar amsar da Azmeen zata bata,   murmushi azmee tayi tare da cewa"hakane tun ɗazun nake ta son in yi maki magana amma duk in nazo saina same ki kina bacci," jinjina kai sehrish tayi sannan tace"nasan na 6ata maki rai aunty azmee, ki yafe mun,"    hannu azmee tasa tare da shafa gefen fuskarta tace"just forget about the past komai ya wuce ki manta kawai, yanzu ma nake shirin zuwa in shirya maki abinci don nasan kina jin yunwa sosai,   Murmushi sehrish tayi ba ƙaramin kwanciyar hankali tasamu ba,       Sannan tace"bari na barki  ki huta nasan kinyi aiki sosai kin gaji,banji daɗi ba ɗazun da kika hanani tayaki aiki," cikin sanyin murya ta ƙarasa maganar,    Azmee tace"ki manta da wannan, yanzu kije ki haɗa abincin ki ci," amsa mata tayi da toh,sannan ta juya zata fita, Muryar azmee ce ta sake katse ta da cewa"Au na manta ban sanar dake ba, babban yayan ku fa ya dawo, yau da wuri suka shigo, shi kaɗae ne ma ya rage bai ci abincin shi ba, ki fara kai mashi pls,"   Amsa mata tayi da toh sannan tasa kai ta fuce daga ɗakin nata,   *SGR* gaba ɗaya hankalin shi na akan Laptop dinsa da yake dannawa, yana a hakimce saman royal sofa mai mazaunin mutun biyu, jikin shi na sanye da kimono robe ta cotton,green colour jikinta akwai zane zane masu kyan gaske, rigar bata rufe faffaɗan ƙijinshi ba,hakan ba ƙaramin kyau ya ƙara mashi ba,ya ɗaure igiyar rigar adai dae saitin shafafen cikin sa, a natse yake danna laptop din da zira ziran yatsun hannun shi, ƙamshi ta ko'ina    da sallama sehrish  ta shiga falon nashi, batare da ya ɗago ba ya amsa mata sallamar, ?     Shiga ciki tayi hannunta na ɗauke da ƙaramin tray mai ɗauke da fruits tare da coffee,    koda ta ƙarasa dab dashi murya na rawa tace"sannu  da aiki,fatan kana lafiya,"   "Alhmdllh," ya amsa mata har time ɗin bai ɗago ba, ajiye mashi tray ɗin tayi daga gefen laptop ɗinsa, sannan tace"kana buƙatar wani abu"? hannu yasa ya ɗauki cup of coffee ɗin yakai bakinsa ya ɗan kur6a, janye shi yayi daga bakin shi sannan anatse yace"na manta phone ɗina asaman pillow a ɗaukomin ita," juyawa sehrish tayi da sauri zata kama hanyar zuwa bedroom ɗin nashi kamar daga sama taji gaba ɗaya mayafin jikinta ya sulale ƙasa daga jikinta, cikin sauri ta juya tare da kai hannu zata ɗauki mayafin daya faɗi ƙasa, ganin ƙafar sgr tayi asaman mayafin ya take shi da farar ƙafarshi, kasa ɗaukar mayafin tayi saboda fargabar da tashi ga, ranta ne ya bata cewa ba dagangan yayi hakan ba, da alama baisan ya take mata mayafin ba,   A ɗan tsorace tace"mayafi na" batare da ya ɗago ya kalle ta ba yace "ina Sane," jiki asanyaye ta juya tare da nufar ɗakin nashi, tsoranta kar ace alluran nan ta jiya bata sake shi ba,    faɗawa cikin ɗakin nashi tayi tare da nufar saman pillow ɗinsa wayar na ajiye asama,hannu takai zata ɗauki wayar kwatsam taji motsin mutun abayanta hakan ya sanyata juyowa a firgice gaba ɗaya sumar kanta ta watso harta gaban fuskarta, tsananin tsoro ne yakamata ganin mutumin da tabaro yana shan coffee tsaye agabanta, a wani irin yanayi yake bin jikinta da kallo tundaga kan ƙafarta har izuwa saman ƙirjinta, ganin haka yasa sehrish ta soma ja da baya a tsananin tsorace saboda tunawa da abunda ya faru jiya atsakaninsu hakan na nufin cewa Allurar bata sake shi bane, har yanzu akwai saura ajikin shi,  Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! ?    tuni zufa tasoma tsatstsafo mata a fuskarta, takawa sgr yayi yana matsawa kusa da ita, ja da bayan da zata ƙara yi ke da wuya , gaba ɗaya ta faɗa asaman gadon shi, bin ta saman gadon yayi gadan gadan ya tunkareta, hakan yasa ta fashe da matsanancin kuka atsorace ta dinga girgiza mashi kai tana cewa"wlh bani bace na ɗauko allurar ba ! Bani ita akayi....ba zan iya cutar dakai ba.......!!" sai faman sambatu takeyi ita kanta batasan me take cewa ba saboda ya ƙureta sosai ta runtse idanunta zuciyarta nata faman harbawa, sam batasan cewa sgr yana cikin hayyacin shi ba,da gangan yayi mata haka saboda akwai abunda yakeson ganowa game da daren jiya da kuma abubuwan da ya gani na canji a bedroom ɗinshi da kuma body ɗinshi, yasan cewa itace last person daya kasance tare da ita,       jin shiru baice komai ba yasa ta ɗan buɗe idonta, ba komai yake kallo ba face doguwar sumar kanta, sai yanzu ya gane inda ya samu siraran gashi guda uku masu tsayi, hakan na nufin gashin kan Yarinyar ne ya tsinta asaman gadon shi ɗazu da safe, acikin sambatun da tayi mashi ta ambaci cewa ba ita bace ta ɗauko allurar ba, ba ta ita akayi, nan ma ya gane cewa kwa6a tayi mashi jiya har ya ɗirka ma kanshi allura, that's why omar ya tambaye shi akan cewa shi ya dauko allurar, natsuwa yayi a hankali yana ƙare ma fuskar sehrish kallo, ita kuwa sai faman haɗiyar yawu take yi saboda tsoro ga zufa dake gangarowa ta cikin gashin kanta kamar mara gaskiya, duk da sanyin A.c dake gudana aciki,    rufe idanuwanta tayi tana faman karanta addu'oi' acikin bakinta,    for the first time daya ƙarewa wata ƴa mace kallo irin wannan aduniyar nan, yana kallon kyakkyawar fuskarta ne aƙoƙarin shi na ya tuna abunda ya faru jiya,amma yarda take motsi da siraran la66anta tana karanta addu'oi'n neman tsari hakan ba ƙaramin burge shi yayi ba, sai ya samu kan shi da shagala wurin kallon bakinta, tunanowa yayi da ranar daya turketa amatsayin mace yarda ta tsorata har ta sume mashi, shi kuma rayuwarshi mace mai shegen tsoro ba ƙaramin burgeshi takeyi ba,ba don komai ba sai don ya ruƙa tsorata ta don ya samu nishaɗi,     ɗan gyara muryarshi yayi tare da cewa"jiya kin ban allura nayi ma kaina har nayi ƙoƙarin yin raping ɗinki, ko ba haka akayi ba? ya tambaya fuskarshi a ɗaure,.     hankali tashe sehrish ta shiga furta"innalallahi wa'inna ilaihirraji'un. Nashiga uku, kasan Allah ni bani bace na ɗauko allurar ba  bansan komai akai ba,.     shiru sgr yayi yana kallonta har lokacin taƙi buɗe idanunta, abunda bata sani ba shi guessing yayi bai tuna komai ba, amma yayi mata rijiya ta faɗa,    cigaba da magana yayi anatse"then tell me who brought it to u"?     shiru tayi lamo saboda tasan ba zata iya furta sunan haroon ba, ganin taƙi magana yasa shi daka mata tsawa tare da cewa"ba magana nake maki ba!!," wannan tsawar da yayi mata ne yasa ta sume mashi, dama sai da ranshi ya bashi,   Saukowa daga saman gadon yayi tare da fucewa izuwa palour dinshi, kai tsaye ya wuce wurin fridge ɗinsa tare da buɗewa ya ɗauko bottle water mai sanyi, sannan ya koma cikin bedroom ɗin nashi,zama yayi daga gefen gadon tare da sanya hannu ya buɗe roban rubar saida ya fara sha sannan ya ɗebo a hannun shi ya yayyafa mata a fuskarta, a gigice ta ware idanunta kai tsaye suka shiga cikin nashi a lokacin ya mayar da  bottle din abakin shi yana ƙara shan ruwan, tamkar a mafarki take ganin abun har lokacin jikinta bai daina kerma ba, cire roban ruwan yayi daga bakin shi sannan ya mayar da murfin ya rufeta tare da ajiyewa saman side drawer ɗinshi,     sannan yayi mata nuni da hanyar fita yace"zaki iya tafiya," cikin sauri ta sauko daga saman gadon nashi, hanyar fita ta nufa da sauri da sauri, jinkirtawa tayi tare da ɗan juyawa don ta saci kallon shi, samun shi tayi a kashingiɗe saman gadon ya aza head dinsa asaman pillow, eyes dinshi a lumshe tamkat zasu rufe amma hasken kwayar idonshi blue ya ɗan fito alamar bai runtse idanun duka ba,    Muryarshi ce ta ratsa kunnanta da cewa"akwai wani abu ne"? Cikin sauri ta girgiza kai alamar a'a sannan ta fuce daga ɗakin, sai da tafara ɗaukar mayafinta dake zube a ƙasa, ta yafa shi akanta sannan ta fuce daga part ɗin nashi, tafiya take anatse fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi tayi mamakin yarda akai Sgr bai tuhumeta ba,bayan ya tuna duk abunda ya faru atsakaninsu jiya, tayi tunanin zata sha mari ne a wurin shi amma sai gashi abun yazo mata da sauƙi, har yau tana mamakin sauƙin kai irin nashi da ba kowa zai fahimta ba, amma tabbas bai da girman kai ko kaɗan, jan ajine kawai dake gare shi ko jinin sarauta bazai nuna mashi wannan ba, Domin kuwa shi kanshi Sarki ne mai cike da ƙarfin iko👑   a hankali take taka steps ɗin down stairs zata sauko, jin alamar shigowar mutun cikin babban falon yasa ta tsagaitawa da tafiyar tana kallon shi, jahan ne ya shigo cikin falon hannun shi ruƙe da jakar kuɗin da zasu ba haroon, ganin yarda yake tafiya cikin sanɗa yasa ta gane cewa bai son wani ya ganshi cikin sauri ta ja da baya tare da samun wuri ta la6e,    sai faman ƴan waige waige yake yi yaga ko akwai mutun amma wayaam ba kowa hakan yasa cikin sauri ya wuce bedroom ɗinsu, ajiyar zuciya sehrish ta sauke tare da lalla6awa ta fito kai tsaye ta nufi kitchen tana zullumin ko menene Jahan ya ɗauko acikin jakar hannunshi, da alama dae wani mugun abunne tunda har yake sanɗa don kar aganshi, ta faɗi acikin ranta a lokacin da take ƙarasawa cikin kitchen ɗin don ta zuba ma kanta abincin da zata ci,    turo ƙopar yayi a hankali yashiga daga cikin ɗakin nasu, jin alamar shigowar mutun yasa ayaan dakatawa daga zirga zirgan da yake yi acikin ɗakin,   Cikin sauri ya nufe shi yana cewa"Jahan ka tabbata babu wanda ya ganka"? Amsa mashi yayi da cewa"eh babu da alama duk sunyi bacci, kazo yanzu mu hanzarta mu kai mashi kuɗin,"    Atare suka fito daga bedroom ɗin nasu,  duka suna sanye cikin jallabiya, ɗakin haroon suka nufa, koda suka ƙaraso ƙopar ɗakin a rufe take, kwankwasawa Jahan yashiga yi a hankali,   "Su waye ne"? Ya tambaya daga ciki, Har suna haɗa baki wurin cewa "twins ne ",    kwance yake daga saman gadonshi,daga shi sai shorts ajikinshi ba riga, tasowa yayi tare da nufar kofan yasa hannu ya buɗe masu tare da cewa"ku shigo daga ciki," kallon juna su kayi kafin daga bisani suka shiga daga ciki,   tunda haroon yayi arba da jakar kuɗin dake hannun jahan yashiga sakin murmushin nan na shu'umanci yana cewa"ince dae kuɗina ne acikin jakar nan ko"? yayi maganar tare da miƙa hannu zai kar6i jakar,janye ta jahan yayi tare da cewa"ka fara goge  video ɗin tukunna mu damƙa maka su,"    ta6e baki yayi yana kallon su,kafin ya juya ya nufi saman gadonshi inda wayar shi ke ajiye ya ɗaukota, yatsan shi yasa ta buɗe sannan ya shiga wurin videos ɗinshi ya lalubo nasu daya ɗauka sannan ya miƙa masu tare da cewa"Gashi nan ku goge da kan ku,ina ga hakan zai fi ko"?  Kallon juna suka sake yi duk jikinsu yayi sanyin, tsoransu karya cuce su,ayaan ne ya kar6i wayar tashi yayi deleting ɗinsa gaba ɗaya, sannan ya kalli haroon ɗin dake ta faman sakin murmushi yace"ka  tabbata babu wani videon namu dake gare ka bayan wannan!?   ɗaga mashi gira yayi alamar eh, jahan yace'laptop ɗinka fa babu wani aciki"? nan ma ya sake cewa"babu wannan ne kawai gare ni,"    ajiyar zuciya suka saki gaba ɗayansu,  Miƙa mashi wayar Ayaan yayi, sannan jahan ya damƙa mashi jakar kuɗin, kar6a yayi yana cewa"kun tabbatar  cewa miliyan 80 ɗinne"?   ayaan yace"ka ƙirga su mana sai kaga in sun cika,"  Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! ? Zuƙunnawa haroon yayi tare da zuge zeep ɗin jakar, sai ga bandir bandir ɗin ƴan dubu dubu, dami dami shaƙe acikinta, hannu yasa tare da curo bandir guɗa ɗaya yakai a saitin hancin shi yana shinshinasu yace"Anya wannan ba kuɗin ganye bane?harara suka watsa mashi jahan yace"a'a na bishiya ne," dariya haroon yayi yana faman shaƙa kuɗin a hancin shi,   gaba ɗaya ransu ya gama 6aci burinsu ya ƙirga kuɗin yaga in sun cika, amma ya tsaya yi masu shegantaka,    tass ya fiddo da kuɗin ya ƙirga su, duk dami ɗaya na dubu ɗari ne, a haka yayi counting ɗinsu 80 millions ne bayan ya kammala ƙirgasu, ya shiga cusa su acikin jakar kaf ya kwashe su, sai da ya zuge zeep ɗin sannan ya ɗago ya kalle s u cike da shaƙiyanci yace"Au na manta ban baku la'ada ba,"    atare suka haɗa baki wurin cewa"mun fi ƙarfinsu,kai ke buƙatarsu kai daga ganin mu kasancewa ba matsiyata bane,"    "Wow," ya furta yana tafa hannunshi "abu yayi kyau ƴa'ƴan billionaire,karfa kuce zaku gayamin magana!ku fuce mun daga ɗaki cikin salama,"    Jahan yace"ba sai ka kore mu ba, mukan mu aƙagare muke da mu fita mubar maka wannan ƙazamin ɗakin naka wanda ko numfashi mutun daƙyar yake iya fitarwa!!kuma inaso ka sani Haroon baka ci bulus ba, zamu rama duk wani wulaƙancin da kayi mana!!   yana kai ƙarshen maganar tashi ya ruƙe hannun ayaan suka juya zasu fita daga ɗakin karaf idonsu ya sauka akan mutumin dake shigowa cikin ɗakin, A wani irin firgice suka ja da baya gaba ɗayansu, shi kanshi Haroon ya sha jinin jikin shi saboda basu son da mutun ba, gaba ɗaya duk abunda suka tattauna acikin kunnanshi kaf ya gama naɗar komai,    hankali tashe suke kallon shi,kamar yarda shima hankali atashe yake kallon su  Follow my tiktok acct 👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 Atare suka sauke ajiyar zuciya lokacin da suka shaida cewa junaid ne,sai faman murza idanunshi yake yi da hannunshi,da alama magagin bacci ne ya shigo dashi,hakan ya basu tabbacin ba lallai in ya fahimci komae ba,     cikin sauri Jahan yace"junaid tun yaushe kake anan?me kake yi har yanzu baka yi bacci ba"?    Cikin shagwa6a yace"nima bansan ya akai na shigo ba,dan Allah kutaimaka mun ku kaini ɗakin abbanmu in kwanta,wurin shi nake son zuwa,"  Shu'umin Murmushi haroon yasaki yana kallon shi,   ganin yarda yake binshi da kallo yasa su twins saurin ruƙe hannun junaid suka fuce dashi daga ɗakin,     "Ayaan kaje kawai ka kwanta,ni bari nakai shi ɗakin Abban namu," Amsa mashi yayi da toh,sannan ya wuce bedroom ɗinsu,   Shi kuma jahan zuƙunnawa yayi tare da ce mashi"ka hau na goya ka karka faɗi,"    daddagewa junaid yayi ya haye bayanshi tare da ƙanƙame shi,sannan jahan ya miƙe ɗauke dashi abayansa ya wuce bedroom ɗin Abban nasu,    A hankali ya tura ƙopar bedroom ɗin Abban nasu,yana kwance sai faman sharar bacci yake yi asaman royal bed ɗinshi,shiga da junaid ciki yayi a hankali ya sauke junaid saman gadon daga gefen abban nasu,      gyara kwanciya junaid yayi tare da rungumo Abban nasu da hannunshi sannan yace ma Jahan"thank u,"   murmushi jahan yayi ba ƙaramin burge shi yayi ba,sam junaid bashi da wata damuwa,sai yaji dama shine ke irin rayuwar shi,    "Sleep well," ya furta tare da juyawa ya fuce daga bedroom ɗin yana sauke ajiyar zuciya,ɗakinsu ya koma lokacin daya shiga a kwance ya samu Ayaan har bacci yayi awon gaba da shi,shima wucewa yayi tare da haurawa saman gadon ya kwanta daga gefenshi, Yaushe rabon da suyi bacci irin na daren nan harsun manta,saboda fargabar haroon kullum da damuwarshi suke kwana,yau dae sun huta ma rayuwarsu tunda sun sallame shi, A 6angaren haroon kuwa tun bayan da suka fita ranshi ya raya mashi cewa tabbas akwai alamar tambaya game da zuwan junaid bedroom ɗinshi,saboda tun da yake junaid bai ta6a faɗowa ɗakinshi ba irin haka,duk irin magagin baccin da junaid yake yi bai ta6a zuwa ɗakin shi ba,amma sai yau kwatsam zai faɗo mashi ɗakin shi adai² lokacin da suke tattaunawa dasu twins kuma? Anya ba turo shi akayi ba?    zama yayi daga gefen gadon nashi yana tunani,dakyar ya iya tashi yakai hannu ya kinkimi jibgegiyar jakar kuɗin,wuri yayi mata acan cikin ɗakin nashi ya 6oyeta,    Sannan ya koma tare da hayewa saman gadonshi ya kwanta,      ********************* Washe gari  A hankali ya buɗe idanunshi da su kayi mashi nauyi saboda bacci,hannu yasa tare da yaye blanket ɗin daya lullu6a dashi,miƙa hannu yayi tare da ɗaukar wayarshi dake ajiye saman bedside drawer dinshi,missed calls ya gani nasu hossana da jahad,tashi yayi daga zaune yana kallon screen ɗin wayar tashi,jiya yaso yaje ya duba su amma bai samu time ba,    danna musu kira yayi tuni tashi ga ringing,   A lokacin Jahad ce acikin falon zaune saman 2 seater tana ta jiran kiranshi,hossana kuwa tana can tana sharar bacci,     har ta fidda ran cewa zai kirasu saiga kiran nashi ya shigo,cikin sauri ta miƙe ta nufi telephone ɗin tasa hannu ta dauka tare da karata a kunnanta,    Cikin sanyin murya tace"Assalamu Alaikum ya Omar an tashi lafiya,"   murmushi yasaki tamkar yana agabanta yace"lafiya lou Alhmdlh,nayi laifi ko?jiya banzo na duba ku ba,ayi mun afwa ina busy sosai,amma kuna araina,"    "Babu komai ya Omar,dama mun damune akan rashin zuwan naka,kuma mun kira wayarka jiya da safe,baka a kusa sai dai matarka Aunty zainab ta ɗaga kiran,"     "What!matata kuma? Wacece kuma aunty zainab?pls explain to me ni bangane me kike cewa ba,"    murmushi jahad tayi tare da cewa"Ya omar meyasa ba ka sanar damu cewa kana da aure ba?baka so mu sani ne?   Sam Omar baisan inda zanjen nata ya dosa ba,    "Jahad nifa bansan me kike cewa ba! Wacece kuma matata?   kafin jahad tace wani abu,sai ga hossana ta fito da saurin gaske jikinta sanye da kayan bacci,tana ƙarasowa tasa hannu ta kar6i telephone ɗin tare da karata a kunnanta cikin shagwa6a tace"eh mana ya omar ashe kana da aure,jiya da safe mun kira wayarka,mace ta ɗaga kiran tace mana kai mijinta ne kuma baka a kusa,sannan kuma tace mana tana ɗauke da juna biyu,kuma sunanta zainab amma kana kiranta da Hayaty,"    tunkan ta ƙarasa maganar Omar yashiga 6a66aka dariya,natsuwa su kayi gaba dayansu suna sauraron sautin dariyarshi,   "Ya omar kayi shiru baka ce komai ba," muryar hossana ce ta katse mashi dariyar tashi,daƙyar ya tsagaita tare da cewa"Am sorry na fahimci abunda kuke cewa,bazan iya yi maku bayani anan ba,insha Allah bayan na kammala breakfast dina zan shigo sai muyi magana ta fahimta ko?    Atare suka haɗa baki wurin cewa"Eh muna jiran zuwanka,sannan in ka tashi zuwa kazo mana tare da Hayati ɗinka muganta,"    murmushi kawai yayi tare da rejecting call ɗin,sai lokacin ya duba kiran nasu da sukayi mashi jiya acikin wayarshi,cike da mamaki yaga kiran da sukayi mashi jiyan da safen kuma already an ɗaga kiran,natsuwa yayi yana tunanin wanene ya daga mashi kira harya tsara wannan ƙaryar,tabbas junaid zai iya yi mashi wannan aikin,.     Miƙewa yayi tare da saukowa daga saman gadon nashi,ya wuce cikin toilet dinshi,within 15 mins ya fito ya wuce wurin closet ɗinshi,tsaf ya kammala shiryawa cikin shadda purple colour ba ƙaramin kyau tayi mashi ba yabi jikinshi duka ya feshe shi da turare,   Bayan ya ɗauki wayar shi ya fito tare da wuce wa part ɗin Rafayet,da sallama ya shiga ciki,baya acikin falon shi don haka ya wuce cikin bedroom ɗin shi,   Yayi mamakin ganin shi a kwance saman shimfiɗeɗen gadonshi,jikin shi na'a sanye da bathrobe da alama bai jima da fitowa daga wanka ba,    Shiga ciki omar yayi tare da samun wuri daga gefen gadon ya zauna sannan ya ambaci sunan shi a hankali"Rafayet wai haryanzu bacci kake yi?    Yamutsa fuska yayi alamar idonshi biyu sannan yace"Omar,yau lalaci nake ji ajikina,duba fa ka gani tun ɗazu nayi wanka amma nagaza tashi in shirya kaina,"    sakin baki Omar yayi yana kallon shi tare da jinjina kai yace"nasan meye matsalarka,wato har yanzu abun nan bai bar jikinka ba ko? Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! ?    "Mekenan"? Sgr ya tambaya yana kallon shi daga kwancen da yake,    Murmushi Omar yasaki batare da yace komai ba,    Miƙewa Sgr yayi tare da tashi daga zaune suna fuskantar juna shi da Omar yace"Na fa tuna duk abunda ya faru jiya a tsakanina da yarinyar nan,"!   "dagaske"? Omar ya faɗi da ɗan mamaki a fuskarshi,   "yeah,amma bakomai na tuna ba,so nake ka faɗamun gaskiyar abunda ya faru,time ɗin da ka tarar damu asaman gadon nan,shin na cire shorts ɗin jikina ko ban cire ba"?    tunkan ya ƙarasa maganar omar ya soma sakin dariya,   Ɗaure fuska sgr yayi tare da cewa"pls Omar banason wasa,just tell me the truth,cos banaso yarinya ta raina ni,"     tsagaitawa omar yayi sannan ya zayyana mashi dukkan abunda ya faru tsakanin shi da Sehrish,    hannu sgr yasa tare da dafe forehead ɗinshi yace"OMG!Omar ashe kaine ka katse mun jin daɗina a wannan lokacin!meyasa baka bari na ƙarasa aikina ba"? ya ƙarasa maganar yana jifar shi da harara,    dariya omar ya kuma yi kafin yace"nifa taimakonka nayi,kisan kai fa zakayi,"    tsuke fuska yayi tare da cewa"babu wani nan,ni narasa meyasa kake mun haka,"   Yayi maganar tare da kai hannu ya dauki pillow ya wurga mashi shi a fuskarshi,tarbe pillow ɗin Omar yayi a hannunshi tare da cewa"Am sorry bro,bansan abun yayi hurting ɗinka ba,amma ae ko yanzu bata 6aci ba,kasan inason farin cikin ka,bari natashi naje na kira maka yarinyar sai ka ƙarasa aikin naka,"   Yana kai ƙarshen maganar tashi ya mike tare da nufar  hanyar fita daga bedroom ɗin  yana  karashe dariyar shi,yana jiyo muryar sgr cike da zolaya yana cewa"Am waiting," Kai tsaye bayan Omar ya fito daga sashen sgr down stairs ya sauko tare da fuce wa daga main palour din,ko breakfast din bai tsaya yayi ba ya wuce wurinsu hossana, Wuraren ƙarfe tara kiran Amrish ya tashe ta daga dogon baccin daya ɗauke ta tun bayan sallar asuba,dakyar ta iya buɗe idanunta da sukayi nauyi saboda bacci,hannu takai tare da daukar wayar dake ajiye asaman side drawer ɗinta,picking call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta a kasalance tace"Assalamu alaikum Amrish irin wannan kira haka tunda sanyin safiya"?    daga can 6angaren Amrish tace"Sleeping sickness wai kina nufin har zuwa yanzu baki tashi daga bacci ba?duba time ki gani kusan 9 fa yanzu,"   Jin haka yasa sehrish sa hannu tare da janye blanket ɗin jikinta ta tashi daga zaune tana kallon clock, ɗan xaro ido tayi tare da cewa"subhanallahi wai har 9 tayi?meyasa aunty azmee bata tashe ni ba,ya ilahi,"    dariya amrish tayi tare da cewa"kin cika bacci reeshi yakama kije kiga psychiatric doctor ya duba brain ɗinki,"    ɗaure fuska sehrish tayi kamar tana agabanta tace"oh ashe dama kallon da kike mun kenan ko?      muryarta cike da dariya tace"no ba haka bane inason lafiyarki ne shiyasa na baki shawarar kije aduba ki,"    "Okey thanks for ur advise amma fa ni ba inda zanje,da raina da lafiyata bazan kwasa na tafi asibiti ba,salon su ja man bala'e,"  ƙarasa maganar tayi tare da cewa"pls inason zan shiga kitchen yanzu,i wll call u later bye,"     sallama su kayi da amrish sannan ta mayar da wayar saman side drawer ta ajiyeta, saukowa tayi daga saman gadon cikin sauri ta wuce cikin toilet, brush tayi tare da wanko fuskarta sannan ta fito ta wuce wurin wardrobe ɗinta,buɗewa tayi tare da ɗauko mayafi ta daure shi akanta kamar ɗan kwali, Lokacin da fito har azmee ta kammala jera masu breakfast ɗin asaman dining,junaid ta samu tare da fawan zaune suna yin breakfast dinsu,kamar waɗanda yunwa ta koro sai faman turawa suke yi abakinsu suna ci,    dagowa junaid yayi tare da kallonta nan take ya sakar mata murmushi tare da kiran sunanta"sehrish,"    Juyowa fawan yayi tare da kallonta yace"ke zo nan,"    nan da nan taji gabanta ya faɗi dama basu ta6a magana dashi ba,   jiki asanyaye ta ƙarasa inda suke dai dai kusa dashi sannan ta tsaya tana faman ƴan kame kame,    cikin sanyin murya yace"jira kike na fara gaishe ki ne"?   cikin sauri sehrish tace"ina kwana,ka tashi lafiya,"   fashewa da dariya junaid yayi yana kallonsu,harara fawan ya watsa mashi tare da mayar da idonshi kan sehrish yace"lafiya lou,haka yadace daga yanxu basai nace ki gaishe ni ba,daga zarar kin ganni kiyi hanzarin gaidani amatsayina na yayanki,"   Murmushi sehrish tayi tare da amsa mashi da"toh,"     junaid yace"bismillah ki zauna muyi breakfast atare mana," girgiza kai tayi tare da cewa"a'a inaso zan shiga kitchen ne wurin aunty azmee,"   Amsa mata yayi da"okey,"   Sannan cikin sauri ta juya tare da nufar kitchen din,    time din da taƙarasa kitchen ɗin azmee ta kammala gyare kitchen din tsaf, dakyar ta iya cewa"ina kwana aunty azmee,"    sai lokacin ta lura da ita,murmushi tasakar mata tare da cewa"lafiya lou babyn junaid,sai yanzu kika tashi daga baccin naki?dazu nashiga ɗakin naki na sameki kina bacci,    ciki sehrish ta shiga tana cewa"Aunty azmee ae da kinsani kin tashe ni,nikaina banasan yawan baccin nan da nake yawan yi,"   Azmee tace"ai baida amfani atlease yakamata ace duk in kika kammala sallar asuba ki daure kina karanta al'qur'ani, sannan ki dinga yawaita yin azhkar,insha Allah duk wani abu dake damunki Allah zai yaye maki shi,"   "Insha Allah zan yawaita yinsu kamar yarda kikace,yanzu inaso in kaima babban yaya breakfast ɗinshi,bansani ba ko kin kai mashi,    Azmee tace"a'a ban kai mashi ba,bari na haɗa maki sai ki kai mashi,"    Tsayawa sehrish tayi tana jiranta,   Bayan azmee ta kammala shirya mata breakfast din nashi acikin tray ta miƙa mata,hannu biyu tasa ta kar6a tare da kama hanya ta fuce daga kitchen ɗin,   Da sallama abakinta tashiga part din nashi,     har time din bai fito ba,yana acikin bedroom ɗinshi,ƙarasawa ciki tayi tare da ajiye mashi tray din asaman table,sannan ta wuce izuwa bedroom ɗinshi daga bakin kopar ta tsaya tare da maimaita sallamar,    daga cikin bedroom ɗin tajiyo muryarshi yana cewa"wanene nan"   tuni tasha jinin jikinta,musamman data tuna abunda ya faru jiya ba ƙaramin tsoro ya bata ba,    murya na rawa tace"Ni ce,breakfast nakawo maka,"    "Okey,come in," a hankali tasa ƙafa tare da shiga ciki zuciyarta nata faman ɗar ɗar,   tsayawa tayi daga bakin ƙopan tana kallon shi,har lokacin yana kishingiɗe kamar yarda Omar ya barshi,    ganin ta tsaya abakin ƙopar yasa shi cewa"lafiya?    cikin sauri tace"bakomai," "Okey shigo ciki,ki fara gyara min toilet ɗina,"    ƙarasawa ciki tayi a hankali take tafiya tana satar kallon shi,eyes ɗinshi na'a rufe tamkar mai jin bacci,duk wani motsinta acikin kunnanshi yake jinshi,tura ƙopar toilet ɗin tayi tare da shigewa ciki,    Sai bayan da ta shiga ciki sannan ya buɗe idanun shi tare da bin ƙopar toilet ɗin da kallo,tunawa da abunda ya faru jiya tsakaninsu yayi,mayar da idonshi yayi tare da lumshe su,    ba da jimawa ba sehrish tafito daga cikin toilet tare da cewa"na kammala gyarawa,saura bedroom din,"    buɗe idanunshi yayi ba tare da ya kalleta ba yace "okey,ki duba cikin closet ɗina,ki ciro mun kayan da zan sanya,"   Cike da mamaki ido waje sehrish tace"dani kake"?    "Ni da waye" ya tambaya a ataƙaice,d'an murmushi tayi tare da wuce wa can ciki wurin wardrobe ɗinshi,mai girma da faɗin gaske gaba ɗaya glass ne ta gabanta,daga waje kana iya hango kayan sawarshi dake aciki gasunan abun kamar a company jeri jeri komai a tsare,tana ɗauke da sliding doors ajikinta,   Hannu sehrish takai ajikin wardrobe ɗin nan take ƙopar ta zuge da kanta,abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,ruwan ido ta tsaya yi tama rasa wanne zata ɗauko mashi,saboda kowanne acikin kayan sawar nashi kyau suke yi mata,wata ƙopar ta zuge anan taga jerin kayan hausawa ta jima tana mamakin ashe yana dasu amma bai ta6a sanyawa ba,hannu tasa tare da ɗauko mashi haɗaɗɗiyar shadda gezna sky blue mai ɗaukar ido,    ruƙowa tayi a hannunta tare da dawowa wurin gadon Shi a lokacin harya gaji da jiranta ya sauko da ƙafafunshi ƙasa yana ƙoƙarin tashi,jin takon tafiyarta yasa shi ɗagowa yana kallon kayan data ruƙo a hannunta,   tsayawa tayi dab dashi sannan ta miƙa mashi,     ƙin kar6a yayi saima nuna mata hanya da yayi tare da cewa"basu nakeso ba,ki canza mun wasu bana sa kalar wannan,"       Jiki asanyaye sehrish ta koma ta maida shaddar sannan ta ɗauko mashi jeans da t shirt baƙa,       Komawa tayi tare da miƙa mashi,hannu yasa ya kar6a tare da furta"thanks" a gefen shi ya ajiye kayan sannan ya miƙe tare da kai hannu ya zame bathrobe ɗin jikin shi,cikin sauri sehrish tayi hanzarin barin bedroom ɗin takoma daga waje tana faman sauke ajiyar zuciya,ƙiris ya rage sgr ya saki murmushi don ba ƙaramin dariya ta bashi ba,ita duk atunaninta babu shorts ajikinshi shiyasa tayi saurin guduwa daga ɗakin nashi,   Tsaf ya kammala zura kayan ajikinshi bayan ya gama ya koma gaban dressing mirror ɗinshi tare da kai hannu ya ɗauki kwalbar turarennan nashi shumukh yabi ko'ina na jikinshi ya feshe shi da shi,sannan ya koma wurin shoe rack ɗin shi tare da zaro takalma ya zura a ƙafarshi,    tana atsaye tana jiran fitowarshi muryarshi ta ratsa kunnanta da cewa"ki shiga ciki ki gyara mun,"   Sannan ya wuce ta izuwa cikin falon nashi,    Shiga ciki sehrish tayi anatse ta soma gyara mashi bedroom ɗin nashi,     ************** A hankali motarsu tashiga cikin gidan abusufyan major ne ke driving ɗinshi yayin da yake zaune a back seat na motar,   Bayan yayi parking ɗin motar omar ya fito tare da wuce wa ciki,   Koda yashiga cikin falon samun su yayi azune saman 3seater sun haɗa kai sun kurawa plasma tv ɗin dake manne abango suna kallon tashar bollywood,    ba ƙaramin burgeshi su kayi ba,gyara muryar yayi tare da yi masu sallama,atare suka dago tare da kallon shi,hossana na ganin shi ta miƙe da gudun gaske ta tunkare shi,dakatar da ita yashiga yi da hannun shi amma ina sai da ta faɗa mashi,sosai ta rumgume shi tare da kwantar da kanta a saman wide chest ɗinshi,lokaci guda yaji wani irin yanayi atattare dashi,   Jahad kuwa a fusace tace"hossana menene haka wai?ba zaki bari ya ƙaraso ciki ba?    tamkar bata jita ba,haka ta ƙara ƙanƙame shi tana cewa"ya Omar nayi missing ɗinka sosai,jiya ko isasshen bacci bansamu ba saboda ban saka a idona ba,   hannu omar yasa tare da janyeta daga jikinshi suna kallon juna ido cikin ido yace"Am sorry pls,amma yanzu ae gashi nan nazo ko?   daga mashi kai tayi alamar eh,sannan tasanya hannunta cikin nashi suka ƙarasa ciki atare suka zauna kusa da Jahad saman 3 seater ɗin da take,   Cikin sanyin murya tace"sannu da zuwa ya omar,yasu abba da sauran mutanen gidan,   Fuskarshi dauke da murmushi yace"yawwa jahad,duk suna lafiya,ina fata kuma nasame ku cikin ƙoshin lafiya,"    Amsa mashi tayi da eh,sannan tace"namanta ban tambayeka ba,yasu Aunty zainab,"?    kafin yace wani abu hossana tace"ya Omar wai dagaske kana da aure"?a shagawa6e tayi maganar tamkar zatayi kuka,    cikin natsuwa ya soma kora masu jawabi"Ni banta6a aure ba,saurayi ne ni,ko budurwa ban ta6a ajiyewa ba,"   Jahad tace"amma ya Omar wacece ta ɗaga kiran wayarka da mukayi a lokacin?     shiru ya danyi kafin yace"ina tunanin younger brother ɗina ne Junaid,ya cika zolaya sosai," Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! ?   maimaita sunan Jahad tayi "JUNAID!ya omar ƙaninka ne shima?   kallonta yayi tare da cewa"eh ƙanina ne,yana da kyau sosai ga kyan hali sannan ya iya kyakkyawan murmushi kuma shagwa6a66e,"   Murmushi su kayi jin yadda Omar ke zayyana musu ƙanin nashi da alama dae ba ƙaramin sonshi yake ba,    "Ya omar ka nuna mana hotonshi mu gani mana," acewar hossana,   Batare da 6ata lokaci ba Omar ya zura hannu a ajihun wandonshi ya ciro wayarshi tare da shiga gallery ɗinshi,hoton junaid ya buɗo tare da miƙa ma Hossana,hannu tasa ta kar6a tana kallon hoton cike da mamaki tace"wow! yaya Omar wai dagaske ƙaninka ne?wlh yana da kyau sosai dan Allah ka kaimu gidanku wata rana mu ganshi,"   Jin yarda hossana keta santin hoton junaid yasa Jahad sa hannu tare da kar6ar wayar,   Lokaci guda taji gabanta yayi wani irin bugu,tunda ta aza idonta akan kyakkyawar fuskar junaid bata ƙara cewa uffan ba,sam tagaza janye idanunta akan fuskarshi,bakomai take furtawa acikin zuciyarta ba face"Tabarakallahu Ahsanul khaliqin,"    Muryar omar ce ta katse ta da cewa"jahad naji kinyi shiru"?   jiki asanyaye ta ɗago tare da kallon shi tace"ya omar pls zan iya tafiya da wayarka cikin ɗakinmu?yanzu zan dawo,"   murmushi ya saki tare da cewa"ba damuwa zaki iya zuwa,"   cikin sauri ta miƙe tare da nufar bedroom ɗin nasu ta shige ciki,      "Ya omar bari nakawo maka breakfast nasan baka ci komai ba," hossana ce tayi maganar yayin da take miƙewa daga saman kujerar,"  Ruƙo hannunta yayi tare da cewa"dawo ki zauna,idan kika tafi wa zai tayani fira,"    ƙayataccen murmushi tasaki tare da komawa ta zauna daga gefenshi sannan tace"Ya Omar yaushe zakayi aure ne?   "Ranar dana samu maisona," ya bata amsa yayin da idonshi ke akan agogon hannunshi,   cikin shagwa6a tace"ya omar ni nasan cewa kana da ƴan mata dayawa da suke sonka,kawai dae kaine baka shirya yin auren ba,"   "haryanzu bansamu kalar wadda nakeso ba hossana,"  ɗan turo baki tayi tare da cewa"ka faɗamun kalar matar da kakeso ka aura,zan tayaka da addu'a insha Allah,"   murmushi ya ɗanyi tare da kwantar da bayanshi ajikin sofa ɗin yadda zai samu damar kallonta sosai sannan yace"Inason mace natsastsiya kamila,miskila mai ilmin addini dana zamani,mai ladabi da biyayya,idan Allah ya bani mace mai irin wannan suffar tuni zanyi wuff da ita,"    tunkan ya ƙarasa maganar hossana ta ɗaure mashi fuska,sunnar dakai ƙasa tayi tamkar zata zubar da hawaye,   "Meya faru ne"? Ya tambaya yana kallon ta,   Cikin shessheƙar kuka tace"ya omar ba dole sai mace nutsastsiya ba,ko miskila,in dai tana sonka tsakani Allah kawai ka aureta,"    kawar da fuskarshi gefe guda yayi yana murmushi,   Sanya hannunta tayi acikin nashi tare da kwantar da kanta asaman kafaɗarshi, ...sun jima a haka batare da wani yace ƙala ba,kusan 30 mins sai ga jahad tafito hannunta ɗauke da wayarshi,tsayawa tayi tana kallonsu shi ya lumshe ido,hossana kuma har ta fara bacci,   murmushi ta saki tare da samun wuri ta zauna daga gefen shi sannan ta ambaci sunan shi "ya Omar,"   Buɗe donshi yayi a hankali yana kallonta,miƙa mashi wayar tayi tare da cewa"thanks,"hannu yasa ya kar6i Wayar sannan ya mayar da idonshi tare da rufe su,.     Ajiyar zuciya tasaki tare da miƙewa ta koma cikin bedroom ɗinsu,saman gadonsu ta haye a inda ta ajiye drawing book ɗinta,ashe lokacin da ta kar6i wayar omar ta shigo dashi bedroom ɗin nasu,zama tayi tare da ɗauko kayan zanen ta acikin school bag ɗinta,a natse ta zauna tare da zana fuskar,ba ƙaramin kyau zanen yayi ba,fuskar ta fito raɗau dauke da wannan murmushin nashi,zuba ma zanen ido tayi tana kallon shi,lokaci guda taji tana son taganshi face to face~~~~    ************************ Yau tunda ta farka da kewarsu jahad ta tashi saboda mafarkinsu da tayi,fitowa tayi daga cikin bedroom ɗinta jikinta na sanye da riga bubu ta material,   tsayawa tayi daga tsaye tana sauraron wayar da Aunty babba keyi,da alama da hayaam suke magana saboda taji ta ambaci sunanta sai faman 6a66aka dariya take yi,    "wlh ba kiji irin farin cikin da nake ji ba,yau burina zai cika na ganin kin koma gidan da zama,hayaam bana so ki raga ma yarinyar nan!so nake acikin one week ki ƙuntata ma rayuwarta har taji ta tsani zama acikin gidan,maƙirci kawai zaki cigaba da haɗa mata ae nasan kin ƙware a wannan 6angaren shiyasa nake yin ki,"    girgiza kai hafsat tayi tare da ƙarasawa ciki ta samu wuri saman 2 seater ta zauna tana sauraronta,sun jima suna wayar kafin daga bisa ni su kayi sallamar,mayar da wayar tayi tare da ajiyewa agefenta,sannan ta ɗago tare da kallon hafsat tace"gulmawuya halan kin fito don kiji abunda muke tattaunawa ne?   Murmushi hafsat tayi tace"mommy kenan ashe haryanzu kina akan bakanki na ganin cewa hayaam ta koma gidansu Abbana da zama hmmmm whatever ni wannan ba damuwa ta bane,kawai akwai shawarar da nakeso na baki in ba damuwa,"   zuba mata ido aunty babba tayi tana sauraronta,.    Ci gaba da magana hafsat tayi"Mommy aunty hayam zata koma gidan da zama wannan ba laifi bane Amma zai iya zama abun kunya,amma maganar a ƙuntata ma rayuwar yarinyar dake acikin gidan sam wannan bai taso ba,in ba haka ba wlh zaku yi danasanin yin hakan,"   wata uwar harara aunty babba ta watsa mata kafin tace"ke tashi ki ban wuri!tun kafin ranki ya 6aci,"   Maƙe kafaɗa hafsat tayi tare da cewa"mommy dama ita gaskiya ɗaci gare ta,kullum ina faɗa maki kiji tsoran Allah,ki daina biye ma ruɗin duniya.....'   Katse ta aunty babba tayi tare da cewa"karfa kice zakiyi mun nasiha,ko iyayen da suka tsugunna suka haife ni ban ta6a sauraran nasiharsu ba balle ke ƴar cikina dana haifa,   tana kai ƙarshen maganarta,takai hannu tare da ɗaukar wayarta sannan ta miƙe tare da wuce wa ciki,   "Mommy ae da alama basu  yi maki nasihar ma,don da ace suna yi maki da duk ba haka ba,nibansan ma ya akai abba ya auroki ba anya ba rufa ido kukayi mashi ba,"    "Hafsat! Me kike cewa"? A ɗan firgice hafsat ta juya tana kallonta duk a tunaninta ta jima da barin falon ashe bata ƙarasa fita ba,   Cikin sauri tace "haka nace ni dae na gode ma Allah daya bani uwa tagari kamar ki,"    ba don ta yarda da maganarta ba ta juya tare da wuce wa upstairs,   Ajiyar zuciya hafsat ta saki tana faman tiƙar dariya, ? ? _💋Boss Bature💋_ Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 Lokaci guda Amal ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya,ashe magen hayam ce ta faɗo ɗakin,sai faman kuka takeyi miyauu miyauu,da alama yunwa take ji ne,Batare da 6ata lokaci ba Amal ta zuƙunna ta shiga tattara kuɗin da sauri da sauri jikinta na kerma,don a matuƙar firgice take saboda magen nan data tsorata ta,   Miƙewa tayi hannunta ɗauke da kuɗin cikin sauri ta fice daga ɗakin,komawa tayi cikin ɗakinsu hayamm,jiki na rawa ta buɗe wardrobe ɗin kayansu,doguwar riga ta ɗauko ta Abra tare da mayafinta, A hanzarce ta shiga zura rigar ajikinta,ba ƙaramin yawa rigar tayi mata ba har ƙasa take ja,ga wuyar rigar da yayi mata yawa,yafa mayafin tayi,   Sannan cikin sauri ta fito daga cikin ɗakin,a nan waje ƙopar ɗakin ta ɗauki slippers tare da zura wa aƙafarta,    Jiki na kerma AMAL ta kama hanyar fucewa daga cikin gidan,sai da takai baƙin ƙopar fita sannan ta ɗan tsaya tare da juyawa tana kallon cikin gidan yayin da hawaye ke shararowa daga idonunta,bazata ta6a mantawa da irin uƙubar da tasha acikin gidan ba, ta dan jima a haka,daga bisani tasa kai cikin sauri tabar gidan,    Kamar walk'iya haka Amal tabar santar gidan gaba ɗaya,duk da bata jin kwarin jikinta,haka ta jure ta kama hanyar sauri sauri gudu gudu,ita kanta batasan ina zata dosa ba,amma tana da tabbacin cewa tasha zata nema domin ta hau motar zuwa Abuja, ...(Finally Amal taci nasarar barin gidan,saura fatan sauka lafiya) ***************** Sosai jahan ke ta faman sakin dariya cike da nishaɗi,bakomai yasa shi dariya ba face Ayaan dake zayyana mashi irin halin daya shiga na barazanar da haroon ke masu,hankalin su kwance basu da wani sauran damuwa,suna a kwance cikin hotel room ɗinsu,basu jima da fitowa daga wanka ba,kowannansu na sanye da white shorts ajikinshi,suna rungume da juna cikin lallausan bargo,   "Wlh jahan naji jiki sosai,wai ashe haka abun yake?sai gani a sume,gaskiya haroon ba ƙaramin shaiɗani bane,nasha Wahala a ranar nan,"      "dama kai rago ne Ayaaan,nafi ka juriya shiyasa abun yazo maka ahaka,ranar naji kishi da baƙin ciki sosai,har yanxu in na tuna abun ba ƙaramin ƙuna zuciyata ke yi mun ba,"acewar jahan,    "Pls ni banaso muna tuna abunda ya wuce,hakan zai iya sanya mana damuwa acikin zuciyoyin mu,mubar maganar kawai,"   Jahan yace"shikenan mu bar maganar amma inaso na tambayeka pls,yanzu kwatsam a lokacin nan da ace bamu ba haroon kuɗin nan ba,ya saki videon mu a social media har Abba da babban yayanmu suka gani,me kake tunanin zai biyo baya,"   Da wasa jahan yayi maganar amma har sai da zuciyar Ayaan ta ɗan buga,    "Abunda zai faru shine,zuciyar Abban mu zata buga anan take ya yanke jiki ya faɗi,babban yayan mu kuma zai yi mana bugun mutuwa,abunda ba'a fata kenan,"Ayaan ya ƙarasa maganar yana dariya,     Shima jahan dariyar yayi yana cigaba da sauraron shi kafin daga bisani suka ɗaura daga inda suka tsaya,"    **************Sehrish Tun bayan da tadawo cikin bedroom ɗinta,wanka tayi tare da ɗauro alwala,bayan ta kammala sallar,ta koma wurin wardrobe ɗinta,ta ciro kayan da zata sanya,dogon wando ne na roba,Army trouser tun lokacin da suka je siyayya,ta ɗauke shi saboda ba ƙaramin burgeta kayan sojoji suke yi ba,tare da farar shirt off shoulder ta zura ajikinta,ba ƙaramin kyau tayi ba,komawa tayi gaban dressing mirror ta ɗauki turarenta tabi ko'ina na jikinta ta feshe shi,wuri ta samu saman chair ɗin da ke a front ɗin madubin,ribbom ɗinta ta ɗauko tare da zura shi a hannunta,yau taci alwashin saita ɗaure gashin kanta, da iya ƙarfinta na ƙarshe ta tattare gashin ta haɗo shi wuri guda,tare da zura ribbom ɗin ta ɗaure shi sosai,ya sauko a gadon bayanta,    Murmushi ta saki tana kallon kanta acikin mirror ɗin kafin daga bisani ta miƙe tare da wuce wa gaban gadonta,within 15 mins ta kammala gyara bedroom ɗinta,komawa tayi tare da hayewa saman gadon,takai hannu ta ɗauko wayarta dake ajiye saman side drawer,    Wi-fi ta kunna nan take messages ɗin whatsapp dinta suka soma shigowa acikin wayarta,shiga whatsapp grp tayi na school ɗinsu,new student ne ke ta introducing ɗin kansu tare da pics ɗinsu,tunani ta soma yi bata da hoto ko ɗaya,gashi tana buƙatar pictures saboda ita ma tayi nata introduction din,    tana cikin wannan tunanin kiran junaid ya shigo wayarta,cikin sauri tayi picking tare da karawa a kunnanta,   Tun kafin tayi sallama yace"yunwa nake ji,"yana faɗin hakan ya katse kira,murmushi Sehrish tayi tare da cewa"shagwa6a66e kawai"   Ajiye wayar tayi saman pillow sannan ta miƙe tare da saukowa daga saman gadon,sam ta manta bata yafa mayafi ba,saboda saurin da take yi nata kai mashi tadawo don tayi pictures din,takalmi kawai ta zura a ƙafarta,sannan ta buɗe ƙopar ta fita,   A natse take tafiya hanyar kitchen ta nufa,wayam babu kowa a main palour ɗin da alama duk suna cikin bedroom ɗinsu wasu kuma sun fita,    Batare da 6ata lokaci ba ta haɗo mashi cornflakes tare da snacks acikin tray,kai tsaye ta wuce upstairs bedroom ɗinshi,   Tsayawa tayi tare da yin knocking ƙopar bedroom ɗin nashi,   daga ciki tajiyo muryarshi yana cewa"a buɗe take fa,just come in,"   a hankali ta tura door din tare da shiga cikin ɗakin nashi,   yana tsaye agaban mirror waist ɗinshi na ɗaure da farin towel da alama fitowarshi kenan daga wanka,    ƙarasawa ciki tayi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman table din dake kusa da gadon shi,    Juyowa junaid yayi daga gaban mirror ɗin da yake,zuba mata ido yayi yana kallon bayanta,wandon jikinta ba ƙaramin fidda mata shape ɗin jikinta yayi ba,   takawa yayi a hankali ta bayanta ya tsaya sannan yakai hannunshi tare da ruƙo lallausan sumar kanta,a firgice Sehrish ta juya tana kallon shi,sakar mata wannan kyakkyawan murmushin nashi yayi,   A hankali ta ambaci sunan shi"junaid"!   bai amsa mata kiran sunan shi da tayi ba,sai cewa yayi"reesh ina mayafin ki yake ne"?    Sai lokacin ta tuna cewa bata yafa komai ba ajikinta ta fito,    "Mantawa nayi ban sanya ba,"ta bashi amsa tana kallon fuskarshi,   "Kinyi kyau sosai,but pls kada ki ƙara fitowa haka batare da mayafinki atare da ke ba,"ya ƙarasa maganar cikin sanyin murya,   Har lokacin bai saki wutsiyar gashinta ba daga hannun shi,sai faman murza gashin yake acikin hannun shi,   Sakin gashin yayi tare da zagayawa da hannun shi ta bayanta,ya zame ribbom ɗin dake akanta,nan take sumar kan ta tarwatse abayanta,duk tana tsaye tana kallon shi batare da ta hana shi ba,    tura hannunshi yayi acikin lallausan gashin kan nata,wasa ya shiga yi mata dashi,ganin abun nashi ba mai ƙarewa bane yasa tace"junaid wai menene haka?kamar wata ƴar baby ka kama mun sumar kai sai murzawa kake yi,"    Murmushi yayi tare da cewa"kwarkwata nake son cire maki,don nasan baza a rasa su acikin kan nan naki ba,abunda baki sani ba su suke saki yawan mantuwa,"   Buge hannun shi tayi tana dariya tace"wlh ka 6aci da ƙarya junaid,bansan waya koya maka ƙarya ba,"   tayi maganar tare da wuce wa tana nufar hanyar fita daga ɗakin,cikin sauri yakai hannu tare da ruƙo nata acikin nashi yace"pls kada ki tafi,ki tsaya na kammala lunch ɗin mana,inyaso sai mu fita atare,     Batare da musu ba tace"bazan tafi ba amma zan fita daga waje,idan ka kammala sanya kayan saina shigo,"     ƙarasa maganar tayi tare da fucewa ta tsaya daga waje tana jiran shi, Shaf shaf ya kammala shirya wa cikin jeans da t shirt,sannan ya samu wuri daga gefen gadon ya zauna tare da kwala mata kira,    dawowa ciki tayi tare da takawa zuwa gefenshi ta zauna,    "Sehrish inason magana dake," Yanayin yarda junaid yayi mata maganar da wata irin kasalalliyar murya yasa ta jin faɗuwar gaba batare da sanin dalilin hakan ba,      Cikin sauri ta juyar da fuskarta tana kallon cikin idanunshi tace"menene junaid"   ƙara matsawa yayi kusa da ita,fuskarsu ta kasance a kusa data juna,numfashinsu har harhaɗewa yake dana juna don ƙiris ya rage tsinin hancin shi ya ta6a nata,hakan ba ƙaramin tsorata sehrish yayi ba,tun da take arayuwarta bata ta6a ganin fuskar junaid da irin wannan yanayin ba batare da Murmushi ba,sam babu murmushin nan a fuskarshi,   Cikin en ina sehrish tace"..junaid wai menene haka?me yake faruwa ne"?   Lumshe kyawawan idanuwanshi yayi tare da sake buɗesu a hankali ya furta"I LOVE U REESH,I wanna be with u,for the rest of my life," in serious matter junaid yayi maganar,amma sai Sehrish ta fashe.da dariya kamar kamar me,    Mamakine ya kamashi ganin tana yi mashi dariya,   Miƙewa tayi daga saman gadon nashi tana ci gaba da yin dariyar,dakyar ta tsagaita tare da kallon shi tace"gaskiya junaid ka iya wasan kwaikwayo,wlh ni har gabana ya faɗi duk atunanina wani abun kirki ne ashe zolayar taka ce ta motsa,"   Hankali atashe junaid ya miƙe tsaye yana kallonta yace"reesh nifa ba wasa nake maki ba,inason bayyana maki irin tsananin son da nake maki ne,"    Muryarta ƙumshe da dariya tace"wlh junaid da ace kai actor ne acikin film ba ƙaramin ƙayatarwa zaka yi ba,saboda ka iya tsara wasan kwaikwayo,"    Tana kai ƙarshen maganarta,ta kama hanya da sauri ta fuce daga cikin ɗakin nashi tana ƙarashe dariyarta,   Jiki a mace junaid ya koma tare da zaunawa saman gadon,    jinjina kai yayi tare da cewa"tashin hankali!ashe irin kallon da sehrish keyi mun kenan!yanzu taya za'ae na bayyana mata irin yarda nake ji a game da ita?   Ya jima yana wannan tunnanin aranshi kafin daga bisani ya mayar da idanunshi akan cornflakes ɗin da ta haɗo mashi,.    A sanyaye yakai hannu tare da ɗaukar spoon ɗin dake acikin cup din,ya fara ɗebowa yana kaiwa bakin shi, adai dai lokacin da Sehrish ke gabda shiga Corridorn da ɗakinta yake Sgr ya fito waya kare a kunnan shi,da alama waya yake yi,karaf idonshi ya sauka akan bayanta wanda lallausar gashin kanta ke baje har wurin ƙugunta,don bata maida ribbom din da junaid ya cire mata ba dama dakyar ta ɗaure shi ɗaxu,ƙarasa fitowa yayi slowly ya dafa handrail da hannunsa guda har lokacin yana amsa wayan da yake yi, yayin da blue eyes dinsa ke bin bayanta da kallo, ba komae ne ya ja hankalin shi ba face Army trouser din dake jikinta don ba ƙaramin kyau yayi mata ba dama kuma favorite color dinsa ne...... _💋Boss Bature💋_ Wuraren biyu na rana hossana tafarka daga dogon baccin daya ɗauketa,miƙewa tayi daga kwancen da take asaman sofa,sai faman hamma takeyi tana murza idanunta, a hankali ta ware idanunta tana neman Omar da bacci yayi awon gaba dasu,wayam tagani babu shi alamar ya tafi bataso hakan ba, dakyar ta iya tashi daga saman sofa din,tana tafiya a hankali saboda jirin da take ji,ga wata irin Yunwa dake cin ta, Bedroom ɗinsu ta shiga,a nan ta samu jahad zaune saman darduma ta jima da kammala sallar Azhar,amma bata bar saman sallayar ba,tana zaune zugum tana tunanin duniya, Jin alamar tafiyar mutum yasa ta juyowa tana kallon hossana dake tunkarato, Ƙarasawa tayi wurin jahad tare da zuƙunnawa kusa da ita tace"jahad ashe ya omar ya tafi bai tashe ni ba,ko sallama ba muyi ba,"murya a kasalance ta ƙarasa maganar, murmushi jahad tayi tana kallon fuskarta tace"kada ki damu,in dae ya Omar ne zaki iya ganin shi da anjima ko da daddare ma," Ta ƙarasa maganar tare da cewa"ko kina jin yunwa ne?naga kina ta hamma" "E inaji sosai,'ta bata amsa, Jahad tace"Okey,yanzu nake shirin tashi na shiga kitchen in girka mana abunda zamu ci,amma kafin nan ki fara ɗaukar fresh milk a fridge sai ki haɗa da wani abu kisha,sannan in kin kammala kiyi sallah,gashi har time ma ya wuce,' amsa mata tayi da toh,sannan ta miƙe tare da fucewa daga bedroom ɗin, Murmushi jahad tayi tare da cewa"nan ba da jimawa ba zamu sha bikin Amarya hossana tare da bride ɗinta ya Omar," Yunƙurawa tayi tare da miƙewa daga saman sallayar, hannu takai zata cire hijabin jikinta, nan take ta tunano da maganar da mahaifiyarsu ta ta6a yi masu a lokacin da suke tare da ita, "Burin da nake dashi kafin nabar duniya Allah ya nuna mun ranar Aurenku,kamar yarda na haife ku arana ɗaya haka nakeso na aurar daku ku duka ukun arana ɗaya kuma a lokaci ɗaya,zan cigaba da yi maku addu'a Allah ya baku mazaje nagari," Cikin sauri jahad ta ƙarasa cire hijabin tare da ajiyeta nan saman gadonsu,sannan cikin sauri ta fito cikin falon anan tasamu hossana zaune saman 3 seater hannunta ɗauke da sinkin bread tare da fresh milk sai cusawa abaki takeyi tana haɗawa da madarar, jin alamar tafiyar mutum yasa ta ɗagowa tana kallon jahad dake tunkarota, Ganin yanayinta yasa hossana cewa"jahad meya faru naga kamar kina cikin damuwa"? jiki asanyaye jahad tace"hossana mun manta ba muyi ma Ya Omar maganar SEHRISH ba!banji daɗi da muka manta da batun nemanta ba,baiwar Allah bamusan wani hali take ciki ba," cike da damuwa Jahad ta ƙarasa maganar tare da samun wuri saman hannun kujera ta zauna, Nan take yanayin hossana ya canza,lokaci guda taji komai ya fita ranta, ba don komai ba sai don tunawa da Sehrish, murya na rawa ta soma cewa"inason ganin sehrish sosai jahad, zan sanarwa ya Omar ya nemo mana ita,bazan ƙara mantawa ba insha Allah," "Nima bazan manta ba, da zarar yazo zamu sanar dashi,". a cewar jahad, Daga haka ta miƙe tare da wucewa kitchen, ********************** Wuraren ƙarfe biyar na yamma,motar sofwan ta shigo layin gidan,tun a bakin Gate security guards suka tsayar da motar tasu,kamar wasu zakuna haka sojojin suka tunkari motar shi,hankali tashe ya juya tare da kallon hayaam dake manne ajikinshi tana bacci ta aza kanta asaman kafaɗarshi,jikinta na sanye da dogon hijabi har ƙasa ta sanya niƙab a fuskarta,kamar wata Malamar Addini,   da ƙarfi ya ambaci sunanta"Hayaam!!Hayaam!!"har cikin kanta ta dinga jin kiran nashi,daƙyar ta iya buɗe baki tare da cewa"wai menene"?    "Mun ƙaraso gidan fa,dan Allah ki tashi kiyi ma waɗannan dakarun bayani,nifa a tsorace nake dasu,".    guntun tsoki taja ta janye jikinta daga nashi,sannan tace"haba sofwan bafa yau ka fara zuwa gidan nan ba,menene abun tsoro aciki,sai kace ba namiji ba,"    wani irin kallo yayi mata tare da cewa"ba yau na fara zuwa gidan ba,amma ae ko lokacin da na ta6a zuwa ɗaukarki a iya bakin babban gate ɗin nan nake tsaya......' Bai ƙarasa maganar ba,saboda bugun glass ɗin motar daya ji anyi daga waje,muryar wani basamudan soja ce ta karaɗe kunnansu da cewa"Oya wind down ur glass,"   A hanzarce Sofwan ya sauke glass ɗin motar,yana ta faman mazurai kamar wani mara gaskiya,    tambayarsu yashiga yi"Su wanene ku!kuma wurin wa kuka zo,?    Murya na rawa sofwan yashiga nuna hayaam yana cewa"am..yalla6ai..itace zatayi jawabi,bani ba,"    girgiza kai hayaam tayi tare da kai hannu ta ɗauko purse ɗinta dake ajiye saman laps ɗinta,cikin sauri ta ciro wayarta tare da ruƙe ta a hannunta,nan fa tashiga tunanin wa zata kira acikinsu don yayi masu magana subarsu su shiga,   "Madam ke muke jira,bama son 6ata lokaci and remove dat thing u covered ur face with" muryar sojan ce ta sake katse ta,yana nuna nikab din da yatsansa.   Tuni taji zufa ta soma karto mata a fuskarta da sauri tasa hannu ta cire nikab din,contact ɗinta tashiga tare da dialing numbar Kanal Yousof,cikin rashin sa'a wayar tashiga ringing amma ba'a ɗaga ba almost 3 times,cikin sauri ta kuma lalubo numbar Junaid,har ta gama ringing junaid bai ɗaga kiran ba,da alama shima baya kusa da wayar tashi,   Hankalin Hayaam ba ƙaramin tashi yayi ba,dama su biyu kawai take da numbarsu a wayarta gashi duk sunƙi ɗaga kiran,     ganin zata 6ata masu lokaci yasa sojoji bashi umarnin yaja motar shi yabar wurin,      Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshinta,ba ƙaramin 6acin rai tashiga ba,amma babu yarda zatayi dolenta su koma,   Sofwan na ƙoƙarin tashin motar su bar wurin,sai ga motar Sgr ta kunno kai daga cikin babban gate ɗin gidan, Zuba ma motar ido sukayi gaba ɗayansu musamman hayaam da take jin cewa sauƙi yazo mata,don tasan kowanene zai bada Umarnin abarsu su shiga ciki ne, "Sir I think something is wrong here," Amstrong ne yayi mashi magana, Don haka sgr ya bashi command ɗin ya tsayar da motar tasu don jin meke wakana, A daidai saitin motarsu Hayaam Amstrong ya dakatar da tasu motar,sannan a hankali a wani irin slow glass ɗin motar suka soma saukewa atare, Waro ido waje hayaam tayi nan take zuciyarta tayi wani irin bugun bazata,ba don komai ba sai don ganin mutumin da tajima bata sashi a idonta ba,wato abun harinta, A hakimce yake zaune a back seat ɗin motar,ba ƙaramin kyau yayi ba yayi wani fresh dashi,musamman wankan daya ɗauka,Red shirt ce ajikinshi,tare da black trouser, launin rigar ya ƙara fito da wannan hasken fatar nashi sosai fari sol kamar ka ta6a jini ya zuba,sumar kan nan kuwa tana ɗaure abayanshi,yayin da idanunshi ke lumshe tamkar mai jin bacci, Cikin sauri sojan ya ƙarasa inda yake tare da buga ƙafa ya sara mashi sannan yace"Sir,wasu baƙin fuska ne ke son shiga cikin gidan,kuma basu da shaidar da zamu iya barinsu su shiga cikin gidan,shiyasa muka dakatar dasu, kusan 5 mins bai buɗe bakin shi ba,babu alamar cewa zaiyi magana ma,kowa yayi tsit yana jiran jin ta bakin shi,kai har sai da sojan ya fidda rai da zaiyi magana sannan Calmly yace"What about asking their details? Sojan yace"ban tambaye su wannan ba,amma bari naje na tambaye su," juyawa yayi tare da ɗan matsawa kusa da motar Sofwan yace"yana buƙatar bayani a wurinku,ku gabatar da kanku don yasan su wanene ku," jin shiru hayaam bata ce komai ba yasa sofwan juyawa zaiyi mata magana,sakin baki yayi yana kallon ikon Allah,gaba ɗaya hankalinta ya tafi kan Sgr,ba ƙaramin tafiya da imaninta yayi ba, Nan take yaji wani irin kishi ya rufe shi,acikin ranshi yace"haba no wonder,sai yanzu na gane dalilin dayasa hayaam ta haukace mun akan wannan Namijin,mutum kullum ƙara kyau yake yi,kamar shi yayi kanshi don kyau,muddin irin wannan na yawo agari tofa bazamu ta6a yin kasuwa ba," "Don't waste our time"! muryar sojan ce ta katse mashi tunanin nashi, Cikin sauri yace"Hayaam!magana fa ake maki,kiyi masu bayanin alaƙarki da mutanen gidan," Ajiyar zuciya hayaam tasaki,sannan anatse ta soma magana"ka sanar dashi cewa ƙanwar matar yayansu ce hayaam," Juyawa sojan yayi tare da komawa wurin motarsu Sgr yace"yalla6ai tace ita ƙanwar matar yayanku ce kuma sunanta Hayaam," a hankali sgr ya ɗan buɗe idanun shi, Hakan yasa Hayaam dake hangen shi ta soma washe baki,ba don komai ba sai don ita atunainta sgr ya gane jawabin da Sojan yayi mashi, Cike da ƙasaita yace"sam wannan bayanin bai kwantamin araina ba!infact,I don't know any person wit dat name hayaam or what...,ban ta6a jin sunan ba,Sergeant!!a sallamesu su koma,nd add more security!!" Yana ƙarasa maganar tashi,glass ɗin motar ya ɗaga sama sannan a hankali Amstrong ya tashi motar,anatse yake driving ɗinshi har suka bar wurin gaba ɗaya, dariya ce ƙumshe abakin sofwan amma ya gaza fitar da ita saboda tsoran 6acin ran hayaam,sam yaƙi yarda su haɗa ido da ita,saboda tsoran karta huce akanshi, Kamar ta aza hannu akai ta fasa ihu haka taji,zuciyarta har wani boiling take tana burning saboda tsantsar 6acin rai da baƙin ciki,ashe duk haukan nata ma abanxa ne Sgr baisanta ba,baisan wacece ita ba duk zuwan da takeyi gidan a lokacin baya, daƙyar sofwan ya daure ya cije tare da ce mata"mu juya ko"? A tsiwace tace"bansani ba!!mtswww" ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki, Can kuma tace"babu inda zanje wlh,kota tsiya kota arziƙi wlh saina shiga cikin gidan koda kuwa zamu kwana anan ne,don bazanyi tafiyar banza ba," Cikin sanyin murya sofwan yace"Hayam ki bi komai a hankali!su fa waɗannan mutanen da kika gani ba kamar sofwan ɗin da kika raina bane,muddin kikace zakiyi masu rashin kunya wlh dukan tsiya zaki sha,kakkarya ƙasusuwan jikinki zasu yi,kuma kada kiyi tunanin cewa zakiyi masu kwarkwasa ko kija hankalinsu da kyanki,don wlh babu ruwansu da mace,su ba mayin mata bane irina,so u ave to be very careful," ya ƙarasa maganar fuskarshi ɗauke da dariya,don yau ba ƙaramin nishaɗi yasamu a wurin Sgr ba,ba ƙaramin burge shi yayi ba yanayin acting ɗinsa babu wasa aciki,Namijin ne dae na gaske, Tsuke fuska hayaam tayi,harara ta watsa mashi tare da jan dogon tsoki batare da tace komai ba, tunani tashiga yi akan yadda za'ae su shiga cikin gidan,nan take zuciyarta ta bata shawarar ta kira Aunty babba ta sanar mata,tana ƙoƙarin kiran nata sai ga Motar Haroon ta shararo da gudun gaske cikin layin, tunkan ya ƙaraso wurinsu ya rage gudun motar tashi,sai da yazo dai dai bakin gate ɗin gidan sannan yayi parking ɗin motar tare da sauke glass ɗinta,da alama yasha ya bugu har takai mashi karo,saboda yarda idanunshi ke ta faman rurrufewa sunyi luhu luhu dasu, dakyar ya iya tsayar da idanunshi akan Motar sofwan,nan take suka hango mashi kyakkyawar fuskar hayaam,ɗaga murya yayi tare da kwala ma sojojin kira,cikin sauri suka tunkari motar tashi tare da sara mashi, Yatsina fuska yayi ya kallesu a wulaƙance yace"Meke faruwa anan ne?su wanene acikin motar can"? ɗaya daga cikinsu ne yace "Yalla6ai,ba mu san ko su wanene ba,mun hana su shiga ciki ne saboda basu da shaidar da zamu iya barinsu shiga cikin......' Tunkan ya ƙarasa maganar haroon ya katse shi da cewa"Saboda gidan na ubanku ne!wai ma uban wanene ya kafa wannan dokar ta hana mutane shiga cikin gidan nan ne!"?ni banga amfanin takurawa mutane ba,idan tsaro ne ba Allah ke tsarewa ba mtswwww, Shiru sojojin sukayi suna sauraron faɗan nashi kamar ubansu,hayaam kuwa tunda taji yana zazzaga masifa yasata ɗagowa tana kallonsu,ganin yarda yake banbamin bala'e akan an hanasu shiga yasa ta soma sakin murmushin jin daɗi, Sofwan kuwa jinjina kai yayi tare da cewa"ikon Allah,kowanene wancan jarababben da yake ta faman tada jijiyoyin wuya,da alama ba ƙaramin hatsabibi bane,' Cikin lallashi sojojin suka haɗa baki wurin cewa"Sorry sir!Allah ya huci zuciyarka!" Hura hanci haroon ya shiga yi kafin daga bisani yace"Ban amince abarsu su shiga da motar da suka zo da ita ba!shi namijin yaja motar ya koma gidan ubansa,ita kuma budurwar kuce mata tashigo daga cikin motata na sauke ta cikin gidan,idan har bata amince ba to su tattara su koma inda suka fito,". "An gama yalla6ai,"atare suka amsa mashi,sannan suka juya tare da tunkarar motar sofwan,tun kafin su ƙaraso hayaam ta buɗe motar jiki na rawa ta fito saboda taji duk bayaninshi acikin kunnanta, Hankali tashe sofwan yace"Hayaam ni kuma awani matsayi kika ajiye ni ne"? Batare da ta waigo ta kalleshi ba tace"Zan kiraka a waya,in nasamu lokaci,ta bude back door ta dau jakanta" Jiki asanyaye Sofwan yaja motar,yayin da zuciyarshi ke cike da 6acin ran abunda tayi mashi,yasha wahalar kawota,amma ko godiya babu balle yayi tunanin sake samun wani abu awurinta,tuni yaji hawaye sun cika mashi idanunshi,tabbas hayam ta cuce shi sosai ba ƙaramar wahala yasha akanta ba,duk don ya mallake ta amma gashi nan ya tashi a tutar babu!dashi da Zero basu da bambanci ƙwara ma zero yana da amfani wurin yin lissafi, Shu'umin murmushi haroon ya saki lokacin da hayaam ta ƙaraso jikin motar tashi,hannu tasa tare da buɗe gaban motar tashiga ta zauna tare da rufe motar,sannan ta mayar da idonta akan haroon daya zuba mata ido ko kyaftawa baiyi, ita kanta saida tasha jinin jikinta da ganin irin zubin shi,cikin sanyin murya tace"Sannu ko," ɗan ta6e la66ansa yayi tare da cewa"Yawwa,amma naga baƙuwar fuska ina buƙatar ƙarin haske," Cike da kwarkwasa tace"Sunana Hayaaam,ni ƙanwar Aunty laila ce da kuma Aunty Amani," murmushin gefen fuska haroon yasaki kafin yace"Wow,no wonder that's why naga kamanceceniyar ki da Aunty laila,ashe ke ƙanwarsu ce,amma fa am really sorry game da abunda ya faru,securities ɗin gidan nan basu son ciwon kansu ba,in ba haka ba taya zasu ga mace kamila irinki sanye cikin dogon hijab kuma su hanaki shiga? Sunnar dakai Hayaam tayi tana faman sakin shu'umin murmushi,aranta tace"dalilin dayasa na sanya dogon hijabi kenan saboda nasan cewa kowa zaiyi tunanin ni mutuniyar kirki ce,hmmmmm basu san cewa da fuska biyu nazo masu ba," (Rashin sani yafi dare duhu!hayaam batasan da wa take magana ba," "Kada na cika ki da surutu,bari nashiga dake cikin gidan," Ya faɗi tare da jan motar da gudun gaske ya shige cikin babban gate din gidan (Finally hayaam ta samu nasarar shiga cikin gidan)  *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. Abban sojoji part 2 ? Bayan Haroon yayi parking ɗin motar,hayaam tayi mashi godiya tare da ɗaukar bag ɗinta,ta fito daga cikin motar sannan ta nufi cikin gidan,   Shu'umin murmushin nan nashi ya saki yabi ta da kallo tare da cewa"Nifa bana abu don Allah,kowani tsautsayin ne da ƙaddara suka kawo ta cikin gidan nan!Allah yasa ta kwanan mana biyu...." ya jinjina kai tare da cewa "tsuntsu daga sama gasasshee!"ya ƙarashe maganar tashi tare da zura hannun shi cikin aljihun jeans ɗin dake a jikinshi,wayar shi ya ciro tare da duba screen ɗin, missed calls aka mashi da wata hidden number,     shiru yayi yana tunanin taya zai bi kiran saboda kira ne mai mahimmanci a wurin shi gashi dole sai in shi mai 6oyayyiyar numbar ne ya kira ka,   Yana cikin wannan tunanin sai ga kiran ya sake shigowa,cikin sauri yayi picking call ɗin tare da kara wayar a kunnan yana jiran jin me za'a sanar dashi   Wata irin muryace ta irin hamshaqan matan nan waɗanda suka ji duniya ta soma magana"Haroon!kana shirin jamin bala'e ko?meyasa ka fiye shiririta ne?ko kamanta plan ɗin mu ne"?    nan take haroon yashiga en ina murya na rawa yace"ban manta ba,inaso nabi komai a hankali......'bata bari ya ƙarasa maganar ba ta kwatsa mashi tsawa"Ya isa Haka! kasani wlh akanka bazan bari nayi gangancin rasa damar da nake da ita ba!haroon zaka iya rasa ranka muddin kace zaka kawomin wasa acikin lamarina!kai kasan wacece NI!bani da imani,"   Wata irin zufa ce ta soma gangaro mashi daga cikin sumar kanshi,lokaci guda duk yabi ya rikice yashiga zazzare idanu,    sautin dariyarta ce ta karaɗe kunnan shi,tsagaitawa tayi da yin dariyar sannan ta sassauto da muryarta wurin cewa"Am sorry fa,na tsorata ka ko? Nannauyar ajiyar zuciya haroon ya saki tare da cewa"Yanzu me kike so ayi ne,just command me zanyi maki koma menene,"!    "So nake ka kashe JUNAID!saboda shikaɗai ne hanyar da zanbi wurin ƙuntata masu,banaso junaid ya rayu,muddin yana araye toh farin cikin gidan zai cigaba da wanzuwa ne,ni kuma abunda bana so kenan!,"      girgiza kai haroon yashiga yi tare da cewa"Kiyi haƙuri wannan ne karo na farko da kika ban umarni na musa maki tunda na fara maki aiki!junaid is innocent  I can't kill him,zan iya kawar maki da duk wanda kikeso acikin gidan nan,Amma banda junaid!banda Abbana,Rafayet kuma yafi ƙarfina banda wata hanyar da zan iya cutar dashi,sai ma in jefa kaina cikin matsala!"    fashewa da dariya tayi tamkar zata fasa screen ɗin wayar,bayan ta tsagaita da yin dariyar taci gaba da magana"kasan koni wacece,kasan kuma abunda zan iya!idan har bazaka iya kawar mun dasu ba,to ni zan iya kawar dasu ta cikin ruwan sanyi,Haroon u must do what i command you!if not i wll expose ur secrets,kai kasan me zai biyo baya,ko ka kashe junaid ko kuma ni in kashe maka rayuwa gaba ɗaya...!!!!    Waro ido waje Haroon yayi yana sauraronta,   Cigaba da magana tayi"Maganar videon su Twins daka ɗauka,nasan ka goge na wurinka,amma akwai wani a hannuna,zanyi amfani dashi wurin tarwatsa zuciyar mahaifin nan nasu,da kuma masoyina Rafayet!inason ganin tashin hankalin shi sosai...."   A tsorace haroon yace"Kada ki kuskura ki saki bidiyon nan!in ba haka ba asirina zai tonu ne!kuma kina sane da cewa,muddin asirina ya tonu to ke ma kin gama yawo!!atare zamu fuskanci sakamakon mu,zasu kamo ki ne aduk inda kika 6uya!!"     ya ƙarasa maganar yana faman sakin huci yayin da idanun shi sukayi jawur saboda tsananin 6acin rai,    fashewa ta kuma yi da wata irin mahaukaciyar dariya kafin ta tsagaita da yin dariyar tace"Haroon!Iska bata ruƙuwa!domin ni tamkar iskar nake,kada kamanta ina amfani da baƙaƙen aljanu wurin gudanar da aiki na,kuma zanyi amfani dasu ne wurin ganin na tarwatsa dukkan zuri'ar Salahuddeen Hussein!wannan alwashi ne na ɗauka,rai uku masu mahimmanci suka kashe mun,ni kuma rayuka zan ɗauka!don bana yafiya arayuwata!"   Shiru yayi bai ce komai ba kusan minti biyar, sam baison wani abu ya samu abbanshi shi kaɗae yafi ji sannan yace"Maganar yaran nan fa?su kuma ya zakiyi dasu?    "Inaso saina fara sanya soyayyarsu acikin zukatan ƴan uwansu sosai,saboda inaso inyi amfani da wannan damar ne wurin ƙuntatawa dukkan wani jin daɗi na zuri'arsu,kamar yarda suka ƙuntata ma tawa zuri'ar,"     Jinjina kai haroon yayi kafin ya kuma cewa"Yanzu menene plan ɗinki"?    Wannan karan anatse ta soma magana"plan ɗina shine kawar da junaid,dalilin dayasa nakeson kawar da junaid shine!sihirina bazai ta6a tasiri akan Rafayet ba har sai an samu lagwanshi,kuma ba kowa bane lagwanshi ba fa ce Junaid,da zarar ya rasa junaid zaiyi sakaci da ibadarshi hakan zai bani damar yin aiki akanshi,kuma shi ya kasance Bugun zuciyar family ɗinsu inaso na ɗanɗana masu raɗaɗin rasa mutumin daka kwallafa rai akansa!sannan maganar bidiyon nan zan sake shi a social media kowa ya gani,daga zarar hakan ta faru nasan cewa Martabar family ɗinsu da kuma ƙimar da suke dashi a duniya gaba ɗaya zasu zube,kowa zai tsani zuriyarsu duk wata daraja da suke dashi a idon duniya zata tashi abanza ne!ni kuma hakan nakeso,kafin na saki bidiyon inaso kayi amfani da kuɗin da suka baka wurin barin ƙasar,ka koma malaysia da zama,na shirya maka komai najin daɗin rayuwa acan,giya da mata har saika gaji dasu,"    shu'umin murmushin nan nashi ya saki aranshi yana ayyana irin rayuwar da zaiyi acan cikin daular da aka shirya mashi,nan take yaji cewa zai iya aikata komai takeso,   Sam yama manta da waya yake yi saboda tsabar farincikin da ya ziyarce shi,mayar da bayanshi yayi a jikin seat na motar yana cigaba da sakin murmushi,    "Kana jina kuwa,"muryarta ce ta ratsa kunnan shi,hakan yasa ya dawo daga dogon tunanin daya tafi,    Sai da ya samu natsuwa sannan yace"Naji duk abunda kika ce,hakan yayi mun sosai,musamman da kika ambaci giya da mata,sai naji wani nishaɗi araina dama irin rayuwar da nakeson yi kenan,amma akwai wata shawara da nakeson baki,in ba damuwa,"   Tace"ina sauraronka haroon," "Ga me da bidiyon tsaraicinsu twins,kada ki sake shi a social media pls,sun riga sun biyani kuɗi kamar yarda na buƙata,shiyasa nakeso ayi masu sassauci,mutun biyu kawai nakeson suga bidiyon nan Abban su da kuma wannan ifiritun sarkin jin kan nan,sannan maganar kashe junaid nasan ban isa na hanaki aikata abunda kika yi niyya ba,amma abunda nakeso ki bar komai a hannuna,ni ko ke babu wanda zai kawar dashi!kiyi amfani da sihirin ki kawai ta cikin ruwan sanyi yarda babu wanda zai zarge ni!!"      Dariya sosai tayi da alama shawarar Haroon tayi mata,    Sannan tace"daga yau komai zai fara"!!! murmushi haroon ya saki tare da cewa"Allah yaba mai rabo sa'a"   daga haka su kayi sallama ya kashe kiran,kasa fitowa daga cikin motar yayi ba don komai ba sai don kasalar da yaji ta baibaye shi,fuskar junaid kawai yake gani acikin idanun shi,😢    ****************** Lokacin da Hayaam ta shiga cikin gidan da sallama abakinta tashiga main palour ɗin,tsayawa tayi da tafiya ganin babu kowa acikin babban falon,takun tafiyar da taji ne yasa ta juyawa ta gefen hagunta tana kallon mai tafiyar,bakowa bace face Sehrish sai faman sauri take yi don ta shiga kitchen,har yanzu shigar ɗazu ce a jikinta,amma ta yafa mayafi ajikinta tayi rolling ɗinshi,    ta wutsiyar idonta ta hangi mutum hakan yasa ta dakata da yin tafiyar ta ɗan juya don taga wanene,karaf idonta suka haɗu akan na Hayaam,cike da mamaki take kallonta,batasan ko wacece ita ba,amma ganin hasken fatarta yasa tayi tunanin ko ƴar uwarsu Junaid ce,    tunkararta sehrish tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta ƙarasa inda hayaam take,tunkan sehrish ta ƙaraso zuciyar Hayaam ta shiga bugu,don ta gane cewa itace Ƴar aikin da Aunty laila take bata labarin cewa tana rayuwa acikin gidan,yarinyar da Abbansu ya mayar da ita ɗiyar shi,    fuska ɗauke da murmushi sehrish tace"Sannu da zuwa,"    hayaam tace"yawwa,ina mutanen gidan nan?naji shiru ko ba kowa ne"?   sehrish tace"duk sun fita,amma junaid da Fawan suna acikin bedroom ɗinsu,sai Aunty azmee tana acan cikin kitchen,    Jinjina kai Hayaam tayi har ta buɗe baki zata kuma cewa wani abu,sai ga Azmee ta fito daga cikin kitchen ɗin,ganin Hayaam yasa ta soma Sakin fara'a kamar gonar auduga,cikin sauri ta tunkaro wurinsu tana cewa"Wata sabon gani!Anya ba idona ne ke nuna min badaidai ba?   dariya hayaam tayi tare da wuce sehrish ta tunkari wurin Azmeen suka rungume juna,   ɗago da ita azmee tayi daga jikinta tana cewa"Oh ni Hayaam!ashe dama zan sake ganinki a duniyar nan?gaskiya kun yada zumunci!ina ji tun bikin Amani yaushe rabon ki da gidan nan!    Sai faman washe baki Hayaam takeyi ba don komai ba sai don sanin cewa Azmee zata kar6eta hannu bibbiyu kuma zata goya mata bayan zama acikin gidan,      "Kai Aunty azmee,nafa zo bayan bikin Amani kin dai manta ne,gaskiya nayi missing ɗinku sosai,shiyasa ma nace dole nazo naganku,"   Magana takeyi amma hankalinta na akan Sehrish,dake tsaye tana sauraronsu,    Azmee tace"mu ma munyi kewarki sosai,amma dai bada wuri zaki koma ba ko?don bazan bari ki tafi batare da kin zauna mana ba,".     Anzo wajen da tafiso nan fa tashiga washe baki tana cewa"ae Aunty azmee har sai kun gaji dani,in dae ba ku kuka kore ni ba,amma ni ina nan ba inda zanje,"   murmushi Azmee tayi tare da cewa"Ae bama wanda zai kore ki hayaam,".   taƙarasa maganar tare da mayar da idonta kan sehrish tace"wannan Hayam kenan!ƙanwar matar yayansu ishaq,da kuma Amani wadda tazo ran nan harna gabatar maki da ita"?   wani irin bugu taji zuciyarta tayi mata ba don komai ba,sai don tuna kalaman Amani da tayi in har wannan takasance ƙanwarta ce,lallaikam akwai matsala,   da ƙyar sehrish ta ƙaƙalo murmushin yaƙe sannan tace"Allah sarki,ashe kanwarsu ce,naga suna yanayi da Aunty amanin,"    ta6e baki hayaam tayi jin abunda sehrish tace,    ruƙo hannunta Azmee tayi tare da cewa"Kada na cika ki da surutu,mu shiga ciki ki huta don nasan ba ƙaramar gajiya kika kwaso ba,"   atare suka wuce ciki da Azmeee,zuru sehrish tayi ita dai tun da tayi arba da Hayaam taji sam bata kwanta mata arai ba,kama hanyar shiga kitchen ɗin tayi tana cikin tafiya taji muryar junaid ya ambaci sunanta,    dakatawa tayi da tafiyar sannan ta ɗan juya tana kallon shi,fuskar nan tashi a yamutse alamar daga bacci ya tashi,sai faman sakar mata wannan kyakkyawan murmushin nashi yake,    acikin ranta tace"Shagwa6a66e halan yunwa yake ji ne,"    ƙarasa saukowa yayi daga saman stairs ɗin kai tsaye wurinta ya nufa,      Lokacin da ya ƙaraso inda take tsaye muryar shi cike da kasala yace"Reesh har yanzu Abbanmu bai dawo ba"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh,tamkar zaiyi kuka yace"dama nasani,tunda wannan abokin nashi yazo mai farin gemu,nasan cewa ba zai barshi ya shigo ciki ba,yana can yaja shi sun tafi yawo gidan abokanansu,"   maganar shi ba ƙaramin dariya taba Sehrish ba,    "Amma dae baka da mutunci junaid,abokin abban naku ne kake ce ma mai farin gemu"?    turo baki yayi cike da shagwa6a yace"eh mana,farin gemu gare shi,ae ba ƙarya nayi ba, Ya ƙarasa maganar da cewa"nidai yanzu ki taimakamin bana jin daɗin bakina farfesu nakeson sha,"    bin lips dinshi tayi da kallo yarda yake magana ashagwa6e,sunyi dark red dasu kamar wanda yashafa jan baki,       Tunanowa tayi da maganar shi ta ɗazu da ya furta mata kalmar so,acikin ranta tace"yanzu ace dagaske junaid sona yake yi,tabbas zan iya haƙura da wanda nakeso don na aure shi,saboda ba ƙaramin tausayi yake bani ba,komai nashi kuma yana burgeni,sai dai bansan ya rayuwar auren mu zata kasance ba,yarda yake shagwa6a66en nan ba ƙaramar wahalar shi mace zata ci ba,wannan rainon shi ma zanyi kenan?kullum sai ya tashi tsakar dare da kukan rigima,don haka sai in tanadi feeder da zan rinƙa haɗa mashi madara yana sha.......' Kasa ƙarasa zancen zucin nata tayi saboda dariyar data zo mata,tafin hannunta tasa tare da rufe bakinta,ta ƙumshe dariyar don karta fito da ita,junaid ya gani ranshi ba ƙaramin 6aci zaiyi ba,   Harara ya watsa mata tare da cewa"meyasa kike kallona ne?kuma kinsa hannu kin rufe mouth ɗinki da alama baki da gaskiya sehrish,"    kafin tace wani abu,sai ga haroon ya faɗo cikin main palour ɗin,jin takon tafiyar shine,yasa gaba daya suka juya suna kallon shi,adaidai lokacin shima ya ɗago da idanunshi kai tsaye suka sauka akansu, Nan take sehrish taji gabanta ya faɗi rass,saboda ta tsani ganin shi acikin idanunta,   da alama wurinsu yake tunkarowa,murmushi junaid ya shiga sakar mashi yana cewa"Ya haroon sannu da dawowa,"     "Yawwa baby junaid,me kuke yi anan ne"? .   yayi maganar yayin da yake ƙarasawa wurinsu,    sunnar dakai sehrish tayi batare da ta ɗago sun haɗa ido dashi ba,   Junaid yace"muna magana ne da sehrish,"   ɗan ta6e bakin shi yayi kafin yace"okey,ka wuce ciki inason magana da ita,"    batare da musu ba junaid ya wuce cikin palourn tare da samun wuri saman 3 seater ya zauna,     ja da baya sehrish tayi aɗan tsorace tana jiran jin mai zai ce,    "Kinyi kyau sosai,shigar jikin ki tayi mun,"ya fadi yana faman bin wandon jikinta da kallo,    Shiru tayi mashi batace komai ba,jira kawai take yayi ƙoƙarin ƙure mata ta watsa a guje,    "dama nasan ba zaki ce komai ba,hakan yayi mun sosai,bakomai ne yasa nace inason magana dake ba face don in baki wata shawara mai kyau,sai dai bansan ko zaki ɗauka ba   Sai lokacin ta ɗago da idanunta tare da kallon shi tace"wata irin shawara kenan?kada kayi tunanin cewa zan ɗauki shawarar ka,saboda kai ba abun yarda bane!nagama yarda da duk wani abu da zai fito daga wurinka,burinka kawai ka cutar dani!"    hannunshi ya zura acikin aljihun shi tare da ƙara matsawa dab da ita yace"shawarar ba akanki bane!akan junaid ce!    daram!!taji gabanta ya faɗi a ɗan rikice take kallon shi,    "Nasan tunda na ambaci sunan junaid,yanzu zaki so ki saurari me zance,don na lura ba ƙaramin jinshi kike yi ba,"   Murya na rawa sehrish tace"me...me..kake son cewa ne agame da junaid?me junaid yayi ne?     Maimakon ya bata amsar tambayarta sai cewa yayi"ran nan nayi maki ƙarya na cewa ni shaiɗanin aljani ne,wannan maganar ba gaskiya bace,abunda ya faru shine akan idona Omar yashigo cikin falon nan kai tsaye naga ya wuce upstairs sai raina ya bani cewa dole zai ji sautin kukan ki,kasancewar part ɗinshi dana sgr basu da tazara sosai a tsakaninsu,maganar cewa ni na shaƙe maki maƙoshinki alokacin da kika zo ambaton sunana agaban Marshal Omar shima duk ƙaryace,bani nayi maki hakan ba,kawai nayi guessing ne kuma da alama na canka dai dai,nasan kin tsorata alokacin kuma kinyi tunanin cewa ni ba Mutum bane,don haka inaso kisa aranki cewa Ni haroon cikakken mutum ne kamar kowa,"yana ƙarasa maganar tashi yasa ƙafa zai wuce part ɗinsu, ..cikin sauri sehrish tace"ka manta baka ban shawarar da kace zaka bani ba,"    dakatawa yayi da tafiyar batare da ya juyo ba yace"ku dage da addu'a," yana fadin hakan yasa kai ya wuce ciki,    Tsayawa tayi cike da zullumin maganar haroon nacewa su dage da addu'a,tana cikin wannan yanayin muryar Azmee ta katse ta da cewa"Sehrish!tsayuwar me kikeyi anan ne?nayi tunanin zan zo na same ki a cikin kitchen,'   cikin sauri sehrish ta nufe ta,tana cewa"yanzu nake ƙoƙarin shiga kitchen ɗin,wani abune ya ɗauke mun hankalina,"    Atare suka shiga kitchen ɗin,batare da 6ata lokaci ba suka soma aikace aikacen girke girken nasu kamar yarda suka saba,       Tun bayan da azmee takai hayaam ɗaya daga cikin bedroom ɗin da suka saba ajiye baƙi insun zo,zame hijab ɗin jikinta tayi,wata ƴar short gown ce ajikinta daidai guiwarta,kai tsaye toilet ta faɗa,bayan wasu ƴan mintina sai gata ta fito waist ɗinta ɗaure da towel,sai lokacin ta tuna cewa ashe tabar trolley ɗin kayanta acikin boot ɗin motar Sofwan,yanzu dole ta neme shi ko don ya kawo mata abunta,    ƙarasawa tayi tare da hayewa saman gadon ta zauna,sannan takai hannu tare da ɗauko purse ɗinta da ta ajiye asaman gadon tun shigowarta tare da Hand bag ɗinta,     wayarta ta ciro anan taga missed calls na Aunty babba har kusan uku,   Murmushi ta saki tare da bin kiran nata,wayar na fara ringing Aunty babba ta ɗaga,.    kara wayar a kunnanta tayi tare da cewa"Auntyna takaina!yanzun nan naga missed calls ɗinki,banji ma da fitowa daga toilet ba,   on the other hand aunty babba tace"kin isa gidan ne!"?   Hayaam tace"eh,yanzu hakama gani asaman gadona inaso nayi bacci don na rage gajiyar dake ajikina,amma fa aunty nasha wahala kafin nasamu shiga cikin gidan nan!"    Aunty babba tace"wahala?kamarya kenan?     Nan hayaam ta kwashe duk abunda ya faru a wurin shigowarsu cikin gidan ta sanar mata,    uban tsoki aunty babba ta saki tare da cewa"Ke kika ban haushe wlh!taya zaki tsaya yi masu kwatance cewa ke ƙanwa tace?to menene alaƙar dake tsakani na dasu ne da har zasu shaidaki!tun a lokacin yakamata ki kirani awaya sai inyi ma wani magana daga cikin gidan akan yayi masu magana su barki ki shiga,amma don kince hayaam ƙanwar matar yayansu,to koni nan da kike gani Sgr baisan sunana ba,bare har yasan naki sunan hayaam,wannan mutumin ma bana tunanin yasan kamannin fuska ta nikaina,"    yatsina fuska hayaam tayi tare da cewa"aunty inaso in kwanta bacci nake ji," .  Aunty babba tace"to shikenan!kardae ki manta da abunda yakai ki cikin gidan,so nake kafin sati mai zuwa naji ana zancen bikinki da Sgr,kafin shekara mai zuwa kuma inji kukan jariri,"   Fashewa da dariya hayaam tayi jin abunda Aunty babba ke cewa,    Sun jima suna waya kafin daga bisani sukayi sallama,wurgi da wayar tayi gefe guda sannan ta kwanta asaman lallausan bedmattress ɗin,nan take bacci yayi awon gaba da ita, ********************** Abun da ya faru bayan barin Amal gidan,wuraren bayan sallar la'asar mammy da Abra suka shigo cikin gidan,jikinta na sanye da hijabi abra kuwa atampa ce ajikinta ta aza mayafin asaman kafaɗarta,sai faman fira suke yi atsakaninsu,    "Mammy yanzu me zakiyi da kuɗin nan da sofwan ya baki?naga kamar suna da yawa,dama akwai ankon bikin wata ƙawata da nakeson yi,kinga sai ki aramun dubu takwas aciki inyi amfani dasu," .   tsuke fuska mammyn tayi tare da cewa"matsalarki kenan!daga kinga wani ya bani kuɗi sai ki bijiro da maganar anko,tun wuri ma ki fidda rai don ko sisi bazan baki acikinsu ba,malam zan kaima cikon kuɗin shi sannan sauran ni zanyi amfani dasu,ko ɗan farfesu naman nan an samu ayi,dama na kwana biyu ban sha ba,   ta ƙarasa maganar a lokacin da suka ƙarasa tsakiyar filin gidan,.    Rai a6ace abra tace"mammy kalli kiga fa har yanzu yarinyar nan bata fito daga ɗakin ba,ko ubanwa takeso ya ɗaura mana girki?gidan ma ko share shi ba tayi ba!    cike da masifa mammy ta shiga kwaɗa mata kira"Amal!!Amall!!don ubanki kina ina ne?bazaki fito kiyi mana aikin cikin gida ba!   Jin shiru bata amsa masu ba,yasa mammy ce ma Abra"maza kije ki tashe ta,ta fito tayi mana aiki,ko tasha na jaki,"   Kama hanyar ɗakin nasu abra tayi har ta kusa shiga ɗakin,ta tuna wata mugunta,cikin sauri ta juya tare da nufar fanfon cikin gidan,ƙaramin bokiti ta ɗauka na plastic ta ciko shi da ruwa sannan ta wuce dashi ɗakin a hannunta,    Murmushi mammy tasaki tare da cewa"haka nakeso,ƴa'ƴana su dinga koyi dani,"ta faɗi hakan tare da sa ƙafa ta wuce cikin ɗakinta,    ae tana shiga cikin ɗakin ta aza idonta akan gadonta inda tabar kuɗin da sofwan ya bata nan taga wayaam babu komai a wurin,hannu tasa tare da murza idanunta don ta tabbatar da abunda idanunta ke nuna mata,again ta kuma ganin wayaam babu komai asaman gadon,   Cike da mamaki tace"wai ba nan na jiye kuɗin da sofwan ya bani ba?kodai na jefa su wani wuri ne bansani ba!   ta faɗi hakan tare da sanya hannu ta zame zanin gadon tana kakka6e shi wai koda zata ga kuɗin a ƙasan shi,nan ma babu,   Cikin sauri ta zuƙunna tare da zoƙa kanta tana leƙen ƙasan gadon koda sun faɗo sun shige ƙarƙashin gadon,nan ma wayaam babu su,    Hankali atashe ta miƙe tana tafa hannu ranta ajagule tace"To wai kodai kuɗin nan ƙafafu ke gare su ne?in ba haka ba taya akai suka bar saman gadon nan!nifa nan na ajiyesu ban canza masu wuri ba,"   Lokaci guda tabi ta rikice ta rasa natsuwarta,saboda mace ce mai shegen son kuɗin tsiya,har faɗi take da naira biyar ɗinta ta faɗi kwara haƙorinta guda ya cire,    Acan kuwa bayan Abra tashiga cikin ɗakin da Amal take,sam bata lura babu mutun asaman katifar ba,saboda yarda shape din bargon ya bada kamar akwai mutun acikin shi,   Ciza le6anta tayi tare da cewa"ƴar jakar uba,yau zaki gane kuranki,wato banza tasamu tun jiya kike ja mana na rago asaman katifarmu duk kin 6ata mana katifarmu da yawun bacci,yanzu zanyi maganinki,ƙazama kawai   ta ƙarasa maganar tare da ɗaga bokitin ta kwarara ruwan asaman bargon tana faman 6a66aka dariyar mugunta,abun mamaki shiru babu alamar Amal zata saki ihun jin saukar ruwa ajikinta,.    Hakan yasa dariyar abra ta soma komawa ciki,ganin yarda bargon ya lafe ajikin katifar,yasa ta gane cewa babu mutum asaman katifar,   Hankali atashe ta saki bokitin ƙasa tana faman kwala ma Amal kira, Shiru bata amsa ba,cikin sauri ta fito tana nemanta a tsakar gidan,babu inda bata duba ba daga kitchen har cikin toilet ɗinsu duk bata nan,   da gudun gaske ta koma ɗakin mamynsu a firgice mammyn ta ɗago tana kallonta ganin yarda ta faɗo mata yasa tace"Abra lafiya meke faruwa ne"!    Muryarta har wani shakewa takeyi wurin fadin"Mammy!babu Amal acikin gidan nan!Amal ta gudu!dama saida raina ya bani cewa zata iya guduwa,'    jin hakan yasa mammy cewa"hakan na nufin itace ta kwashe kuɗin da Sofwan ya bani?    "Mammy dagaske baki ga kuɗin ba!aiko indae hakane toh Amal itace ta kwashe kuɗin,innalallahi bansan ya akai wannan daƙiƙiyar yarinyar har tayi tunanin guduwa ba,ina mata kallon shashasha....'     Katse ta mammy tayi da cewa"amma shegiyar yarinyar nan ta gama dani wlh!naci buri akan kuɗin nan,maimakon ta gudu tabarmin kuɗin shine ta haɗa dasu ta gudu,insha Allah a wulaƙance rayuwarta zata ƙare,Allah ma yasa kidnappers su ɗauketa su kwace kuɗin,sannan su lalata rayuwarta....."    "Subhanallahi!!me nake ji haka!"   Muryar Abbansu Abra ce ta karaɗe kunnansu,shigowarshi kenan cikin gidan ya same su suna ta tsinar Amal,    wani koɗaɗɗen mutum ne,tamkar baya a cikin hayyacinshi haka zubin shi yake,tsohon yadi ne ajikinshi duk yayi uban squeezing,kamar kanshi farau talauci,    ƙarasawa bakin kofar dakin yayi yana tambayar lafiya menene ya faru,     Tsawa mammy ta daka mashi tamkar ba mijinta ba haka tashiga ɗura mashi zagi    "Munafukin banza,munafukin wofi kazo kaji abunda muke tattaunawa ne!Anya bakaine kayi ma Amal hanyar guduwa daga cikin gidan nan ba!wlh ban yarda dakai ba!ka faɗamin gaskiya taya akai Amal tabar cikin gidan nan!?don nasan hakanan banza Amal baza tayi tunanin barin gidan nan ba!dole da taimakon wani,    Tuni yasha jinin jikinshi,saboda mugun tsoranta yake ji,gaba daya ta gama asirce shi,shiyasa baida ikon yin komai sai da Umarnin ta,    tsawa ta daka mashi tare da cewa"ba zaka faɗamun gaskiya ba!taya akai amal tabar gidan nan!    Zuru yayi da ido sai faman kyafta ido yakeyi yana mazurai kamar mara gaskiya,    tsoki abra taja tare da cewa"mammy dama kin daina wahalar da kanki,Abba bai ma da cikakken hankalin da zai iya taimakon Amal wurin barin gidan nan!6ata mana lokaci kawai zaiyi,ni ina ganin ki fito kawai muje mu nemo ta acikin gari,    harara Mammy ta watsa mashi tare da fitowa daga ɗakin ita da Abra suka kama hanyar fita daga gidan,   Bayan sun fuce daga cikin gidan,matsawa abi yayi tare da kai hannu ya ɗauki kujera ƴar tsugunno ya zauna asamanta,    Muryar Amal ya tuna acikin kunnan shi,ashe sun haɗu da ita akan hanya sai faman sauri take yi tamkar zata tashi sama,kamar daga sama taji an ruƙo mata rigar jikinta a firgice ta juya tana kallon shi,ganin Abbansu ne yasa ta fashe da kuka don tasan cewa zai iya mayar da ita gida,cikin shessheƙar kuka tace"Abie nasan inda Aunty amani take,bazan cigaba da zama acikin gidan nan ba,kana gani zasu kashe ni,amma ba ka iya tsawatar masu akan su daina cutar dani,dan Allah Abie kabarni in tafi,kada ka sanar ma mammy cewa ka ganni akan hanya,ka nuna cewa bakasan komai ba,"   tsananin tausayinta ne ya kama shi,nan take yaji cewa zai iya taimakonta gudun karta faɗa hannun mutanen banza,tun da ƙaramar yarinyace mai ƙananun shekaru tsaf za'a iya yi mata wayau,    "Kiyi haƙuri Amal akan dukkan abunda ke faruwa,nima bada son raina bane,bani da yarda zanyi ne gaba daya mammy ta addabi rayuwata,ta hanani dukkan wani farin ciki na rayuwata,tun bayan da Allah yayi ma mahaifiyarku rasuwa ban ƙarasamun kwanciyar hankali ba,komai na duniyar nan ya fita raina Amal,mammy ta jima tana cutar da rayuwata da kuma rayuwarki,yanzu ina da kwarin guiwar iya taimaka maki!dama abunda yasa tuntuni banyi hakan ba saboda bani da ikon yin magana dake acikin gidan,inaji ina gani an rabani da ƴata kuma ana cutar da ita akan idona,babu komai akwai ranar sakayya,"   Yana kai karshen maganar tashi ya ruƙo hannun Amal tare da janta suka tafi,da kanshi yakaita tasha sannan ya damƙa ma drivern amanarta,kasancewar drivern ɗaya daga cikin abokanshi ne ana mutunci sosai,agaban motar drivern yayi mata wuri ta zauna kusa dashi,   Sai lokacin drivern yake tambayarshi inda zasu sauke ta a abujan,shi kanshi abie baisan inda amani ke zaune ba acan,    Cikin sauri Amal tace"ina da numbar wayar Aunty amanin,idan mun isa sai ya kira mun ita awaya,nasan zata zo,"    Murmushi abie yasaki yana tsaye daga waje yashiga tofa mata addu'o'i tare da yi masu fatan sauka lafiya,    tuni Amal taji hawaye sun wanke mata fuskarta,ji take kamar ta fito daga cikin motar tabi mahaifinta,haƙiƙa ta tausaya mashi sosai,haka ta dinga jin raɗaɗi azuciyarta har motar tasu ta kusa barin tashar,ya jiyo muryar Amal tana kwala mashi kira,   "Abie!!Abie!!" da saurin gaske ya ƙarasa inda motar take,kowa na cikin motar tsayawa yayi yana sauraron muryar yarinyar,    murmushi ta sakar mashi,tare da zura hannu cikin aljihun rigar Abra dake ajikinta,zaro kuɗin nan tayi kusan dubu arba'en,sannan ta zura hannunta ta saman glass ɗin murfin motar ta miƙa mashi su,    ganin ya tsaya yana kallon kuɗin yasa tayi saurin cewa"Abie dan Allah kada ka tambaye ni ina nasamu kuɗin,in dai ka yarda dani to ka kar6a kawai nasan kana buƙatarsu,"     Murmushi yayi tare da sanya hannu ya kar6i kuɗin,sannan a hankali glass ɗin ya soma dagawa sama,    Tana jiyo muryarshi yana cewa"ki kula mun da kanki,sannan in Allah ya haɗaki da ƴar uwarki Amani,ki gaishe mun da ita,kice Abbanta yana gaishe da ita sosai,     har motar tabar tashar Amal bata daina leƙenshi ba ta glass ɗin motar,haka zalika shima yana atsaye yana kallon motar tasu,har sai da ta 6ace ma ganin shi,sannan ya haƙura ya juya tare da kama hanya ya soma tafiya yayin da idanunshi ke akan hannunshi yana kallon kuɗin da Amal ta bashi,   Ba ƙaramin daɗin kuɗin nan ya ji ba,yaushe rabon daya ruƙe naira dubu tashi ta kanshi harya manta,ba damar ya samu kuɗi yashiga gidan shi,da zarar mammy ta gani zata amshe kuɗin,ko sisi bata son taga ya ruƙe a hannun shi,tafi son taganshi a matsiyacin shi yana yawo,wannan ba damuwarta bace,    Sanin cewa zata iya ganin kuɗin a hannunshi ta kwace mashi su hakan yasa baiyi gangancin zuwa gidan dasu ba,kai tsaye ya wuce wurin wani abokin shi mai siyar da nama abakin hanya,wuri yasamu ya zauna bayan sun gaisa ya bashi ajiyar kuɗin duka,sannan yace ya zuba mashi naman na dubu uku yaci,bai bar wurin ba sai da yaci ya ƙoshi sannan sukayi sallama da mai naman ya wuce gaba,    Murmushi abie ya saki bayan ya kammala tunanin nashi yace"Allah sarki Amal!kin taimaki mahaifinki,ba don ta bani kuɗin nan ba,da yau haka zan kwana da yunwa,"      Mammy da abrah tamkar zasu yi hauka wurin neman Amal,gida gida haka suka dinga bi suna nemanta,saƙo da lungu ba inda basu duba ba,har bayan sallar magrib suna waje wurin nemanta,a ƙarshe dasuka gaji agalabaice suka koma gidan suna faman haki kamar waɗanda suka sha gudu,tun acikin zauren gidan mammy ta yanke jiki ta faɗi a sume,saboda tsabar baƙin cikin Amal data gudar mata da kuɗinta, . hankali atashe abra tashiga zabga ihu tana kuka tana ambaton sunan mammy,   Da alama dae mammy sai anyi jinya, **************************** Around 11pm, fitowa tayi daga cikin toilet jikinta na sanye da sleeping dress riga da wando,white colour,da alama tayi shirin kwanciya,tun acikin toilet take jin wayarta na ringing,hakan ne ma yasa tayi hanzarin fitowa,ƙarasawa tayi cikin sauri tare da kai hannu ta ɗauki wayar dake ajiye asaman mirror,duba sunan mai kiran tayi,ganin baƙuwar number yasa taƙi ɗaga kiran,sai tayi rejecting ɗin kiran,kafin ta ajiye wayar sai ga wani kiran ya ƙara shigowa na baƙuwar numbar, Cike da mamaki tace"Wai wanene ke kirana a irin wannan lokacin,kuma da bakuwar number,salon ajamun bala'e,bari dae in ɗaga inji,picking call ɗin tayi tare da karawa a kunnanta,muryar namiji ce taji ya zabga mata sallama,aikuwa cikin sauri ta katse kiran tana faman dafe saitin zuciyarta,ta tsorata da jin muryar me kiran nata,koma wanene ba ƙaramin mutum bane,   tsayawa tayi tana tunanin wa tasani da wannan muryar,bata ta6a jin mai irinta ba,    tana cikin wannan yanayin sai ga message ya shigo cikin wayarta,cikin sauri takai hannu tare da janyo saƙon daya shigo daga saman screen din wayar tashiga karantawa kamar haka    _baiwar Allah,ina ta kiran wayarki kin ƙi ɗagawa,dama ƙanwarki Amal ce ta ban numbarki don na kira na sanar dake cewa kizo ki ɗauke ta,ni ne drivern daya kawota abuja,idan ba damuwa ki kira kuyi magana da ita,don kiji muryarta_   Wani irin bugu zuciyarta tayi,cikin tsananin mamaki tashiga maimaita sunan Amal,muryarta na kerma tashiga cewa'Amal!wata Amal yake nufi!ko dai Amal ƙanwata!!!    Cikin sauri ta danna ma numbar kira,yatsun hannunta har kerma sukeyi don aƙagare take da taji bayanin mutumin daya turo mata saƙon........... Pls read this👇👇👇 *Assalamu Alaikum,barkanmu da juma'a fatan kowa na lpy,yauwa inaso indan yi wani karin haskene,aduk lokacin da bansamu yin update ba har ranar ta wuce ina kokarin ganin nayi long page don yayi covering da wanda bansamu yi ba,nasan wasu sun fahimci hakan,yayin da wasu kuma basu fahimci hakan ba sai suyi ta maganar page kaza yakamata inyi tunda banyi na rana kaza ba,duk page da nake saki yafi ƙarfin page guda a ƙa'idar page,ina haɗe 2 pages ne sometimes ma yana haura 2 pages, Shiyasa in na sanya short page wasu ke complain saboda sun saba ganin long page,sannan ban kin yin typing sai don uzurin da ba yadda zanyi,da fatan zaku fahimce ni,sannan akwai masu maganata abayan idona nacewa wai ina jan littafi? Allah sarki rashin sani yafi dare duhu,bani da wani burin daya wuce inga na kammala littafin nan ayanzu saboda abubuwa da sukayi mun yawa,bani ke jan littafin nan ba!bada son raina ba kuma hakana ke faruwa ba!yanayi ne dake nake ciki,yakamata mutane su dinga yi mun uziri bai kamata arinƙa yi mun irin waɗannan maganganun ba,duk wanda kuma yake yi Alhakina na akanshi, wai wasu ma har cewa suke yi don naga littafinna yasamu kar6uwa mutane naso. shiyasa nake jan labarin,wlh dana ji wannan maganar kamar na fasa ihu don takaici, hmmmm babu komai akwai Allah,to my real fans nagode kwarae da hadin kai da kaunar littafi na da kuke,godiya mara adadi kuci gaba da yi mun uziru kuma acigaba da yi mun addu'a,shine kawai insha Allah komai mai wuce wane,Littafin nan inaji araina cewa kammaluwarsu tazo zanyi ƙoƙarin tabbatar da hakan!insha Allah*? *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. 🤍❤? Kiran na shiga drivern ya ɗaga,cikin sauri ta kara wayar a kunnanta tare da yi mashi sallama tace"kayi haƙuri bawan Allah,ban fahimci zancen ka bane,dan Allah ka ƙara yi mun bayani yarda zan gane,"    drivern yace"ƙanwarki ce Amal na kawota Abuja,yanzu haka ita kaɗai ta rage acikin tashar nan,kiyi hanzari kizo ki ɗauke ta saboda dare yana yi kuma ni yanzu nakeson na juya,"   Cikin sauri tace"ka turomin da address ɗin wurin gani nan zuwa,"      Amsa mata yayi da toh,sannan ya kashe kiran,ba da jimawa ba sai ga message ya shigo wayarta na address ɗin inda suke,   Da sauri Amani ta ƙarasa wurin wardrobe ɗinta tare da buɗewa ta ɗauko mayafi tayi rolling ɗinshi akanta,sannan ta dawo ta dauki purse ɗinta dake ajiye asaman bedside drawer ɗinta,         gaba ɗaya duk tabi ta dabarbarce ko escort bata nema ba, da kanta ta shige motarta,ta fisgeta da gudun gaske ta fice daga cikin gidan,driving take tana ta faman sambatu"Ya Allah ka tabbatar mun da abunda nake tunani,Allah yasa Amal ce ƙanwata,Ya Allah kasa itace,wayyo Allah da naji daɗi,       ji take kamar motar bata sauri,tamkar tayi fiffike ta tashi sama don ta ƙarasa da wuri, tun bayan da Drivern ya turama Amani adireshin wurin inda suke shiru bata ƙaraso ba,gashi dare sai ƙarayi yake,kuma babu wani passenger daya rage acikin station ɗin sai ita kaɗai kwallin kwal,sai kuma wasu daga cikin mazauna station ɗin,tana zaune acikin motar baiwar Allah ba ƙaramin galabaita tayi ba,ga gajiyar tafiya ga kuma ciwo da take fama dashi,don har yanzu zazza6in nan bai bar jikinta ba,ganin cewa zasu 6ata mashi lokaci gashi yana da wani uzuri mai mahimmancin da yake so yaje yayi,hakan yasa yace ma Amal ta fito daga cikin motar,daƙyar ta iya miƙewa tare da saukowa daga cikin motar ta fito waje tare da tsayawa tana jiran jin me zaice, Ruƙo hannunta direban yayi sannan yajata izuwa wurin wani benci yace ta zauna anan ta jira ƴar uwarta tazo,kada taje ko'ina,shi zai wuce don yana da uzuri,   Hankalin Amal ba ƙaramin tashi yayi ba ganin direban zai tafi yabarta acikin station ɗin gashi babu wata ƴa mace aciki sai ita kaɗae,   Shi kanshi baiso hakan ba,saboda amanace aka bashi,amma ba yarda zaiyi,ya zamar mashi dole ya juya ya koma da motar,    tana ji tana gani direban nan ya shige motarshi tare da janta yabar cikin tashar da ita,   Lokaci guda wani irin sanyi ya lullu6eta,nan da nan jikinta ya shiga rawar ɗari,hatta haƙoranta sai faman kakarwa suke yi suna fidda sauti kaf kaf suna game wa da juna,ƙanƙame jikinta tayi tana ta faman ambaton sunan Allah abakinta,   Tana cikin wannan yanayin tajiyo takun tafiyar mutane daga gefen hagunta,cikin sauri ta juya don taga su wanene,gabanta ne yayi wani irin faɗuwa ganin wasu giggan tantirai su uku suna tunkaro wurin da take,sai faman nunata sukeyi da hannu da alama ma abuge suke,sun sha takai masu karo suna tafiya suna tangal tangal kamar zasu faɗi,    ganin hakan yasa Amal ta miƙe cikin sauri ta soma tafiya tana waiwayonsu,muryar wani daga cikinsu ne tajiyo yana cewa"kai karfa ta kufce mana,naga kamar tana so ta tsere mana," haba ina ae Amal na jin wannan maganar ta manta da yanayin da take ciki,takai hannu tare da tattare rigar jikinta ta watsa aguje kamar zata tashi sama,suma ganin ta fara gudu yasa suka bi ta aguje don su taddota,    Gaba ɗaya duk tabi ta rikice tana gudu tana waiwayonsu hakan yasa ta hau saman titi batare da saninta ba,kafin tayi wani aune tuni wata mota tayi awon gaba da ita,wata irin razananniyar ƙara Amal ta saki yayin da ta baje asaman titin idonta na kallan sama,jini na zuba ta saman goshinta da kuma hancinta,da la66anta duka sun raunata,    Waro ido waje tantiran nan sukayi ganin abunda ya faru,aikuwa a gaggauce suka zura da gudu don kar ace sune suka kashe ta,     Hankali tashe suka tsayar da motar,sannan atare suka fito daga cikinta da hanzari suka tunkari wurin da yarinyar take kwance,gaba ɗayansu suna sanye da kakin sojoji ajikinsu,     Zuƙunnawa daya daga cikinsu yayi yana kallon fuskar yarinyar dake ta faman faɗin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,"    "bata mutu ba,har yanzu tana numfashi amma tana bleeding ya kamata muyi saurin kaita asibiti,"    Na zuƙunnan ne yayi magana,sannan batare da 6ata lokaci ba,yasa hannunshi tare da sungumarta asaman kafaɗarshi cikin sauri suka wuce da ita cikin motarsu,a back seat ɗin motar ya zaunar da ita,sannan shima ya shiga daga gefenta ya zauna tare da ruƙota jikinshi,   Shi kuma ɗayan ya shiga gaban motar tare da yi mata key,yaja ta aguje suka juya domin zuwa kai yarinyar asibiti,    Adai dai lokacin da Motar tasu take ƙoƙarin shiga shantalelen titin dake a left hand dinsu,Motar Amani ta kunno kai ta titin dake a right-hand ɗinsu, a wani slow Amani ta zuge glass ɗin motarta tana bin tasu motar da kallo saboda kukan mutum da tajiyo acikin motar ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba,aranta tana cewa"Allah yasa dae ba wani mummunan abunne ke faruwa acikin motarcan ba,"   Tana ƙarasa maganar taja motarta da gudun gaske ta ƙarasa cikin tashar motocin,wuri ta samu tare da yin parking ɗin motar,cikin sauri ta fito tana faman gyara mayafin dake ajikinta,hannu tasa tare da ciro wayarta dake acikin purse ɗinta,sannan ta dannawa direban kira,cikin rashin sa'a aka sanar da ita cewa numbar da take kira a kashe take,    hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,   A ruɗe ta soma cewa"kodai ƙarya mutumin nan yayi mani ne?amma meyasa zai kirani a waya ya sanar dani cewa ƙanwata Amal ya kawo Abuja,kuma sannan yanzu na kira wayar shi a switch off,Ya ilahi amma dae bai kyautamun ba wlh,"    tana cikin wannan zancen zucin sai ga waɗannan tantiran guda uku da suka biyo Amal,ganin su yasa Amani tayi tunanin ko ta tambayesu may be a dace,   da hanzari ta tunkare su tare da yi masu sallama,    a firgice ɗaya daga cikinsu ya shiga cewa"wlh ba mu muka kashe ta ba,kawai mun ganta ne acikin tashar nan zaune ita kaɗae,shine muka biyota don mu tambayeta ina iyayenta suke ne...."tun kafin yakai ƙarshen maganar tashi wani daga cikinsu ya buge mashi baki tare da cewa"Ƙarya Haramun!Aunty bari na faɗi maki gaskiyar lamari,mu ɗinnan da kika ganmu 6arayi ne masu yankar aljihu,mun biyota ne domin mu kwamushe ƴan kuɗaɗen dake hannunta tana ganin mu sai ta watsa aguje,tana ta faman gudu kamar zata tashi sama kawai sai ga wata mota tayi Wuff ta ɗauke ta sama........'   gaba daya basu acikin hayyacinsu da alama giyar ce takai masu karo,sai faman kora mata bayanin abunda bata tambayesu ba suke,   Murya na rawa Amani tace"dan...Allahh ban gane akan me kuke magana ba?wacece kuma kuka bi aguje har mota ta buge ta?wace yarinya ce,!kuyi mun bayani,ni ina neman ƙanwata ne Amal,ɗazu wani driver ya kirani a waya ya sanar dani cewa ya kawota inzo in ɗauke ta kuma shine ma yaban addreshin wurin nan,"   Har haɗa baki suke yi wurin cewa"ae itace yarinyar da muke yi maki magana akai Aunty,ae yanzu haka ma yarinyar tana acikin motar waɗanda suka banketa,yanzun nan suka bar wurin nan da ita,   Tun kafin ya ƙarasa maganar Amani ta juya da saurin gaske ta nufi motarta saboda tunawa da tayi da Motar da tagani ta gifta ɗazu da kukan yarinya acikinta,   buɗe motar tayi tare da shigewa ciki taja ta da gudun gaske,tana jiyo muryar waɗannan matasan suna cewa"Aunty Allah tsare hanya,"        *************************** SEHRISH Sam ta hana idanunta bacci saboda jiran dawowar babban yaya,yau harya haura lokacin daya saba dawowa hakan ba ƙaramar damuwa ya jefata ba,harta sauya kayan jikinta izuwa na bacci riga da wando masu laushin gaske orange colour,tun wuraren ƙarfe sha biyu daidai takai mashi fruit a ɗakinshi,Coffee ne kawai bata kai mashi ba saboda tasan cewa bazai shaba idan ya salafce,don ta lura cewa yafi buƙatar shi da zafi zafinshi,don wani sa'en har yana tururi yake shan shi,    sai faman safa da marwa takeyi acikin ɗakin har sai da ƙafafunta suka soma yi mata raɗaɗi sannan ta koma tare da samun wuri gefen gadonta ta zauna,lokaci guda kuma ta soma sakin hammar bacci,duk yarda sehrish taso ta hana kanta bacci amma abun yaci tura,sai gata kwance abaje tana ta faman sharar bacci asaman gadonta,   da yake ta sama ranta abun sai gashi ta farka wuraren ƙarfe daya na dare,daƙyar ta iya mikewa tsaye tana kallon clock ganin ɗaya ta buga yasa taji gabanta ya faɗi rasss,tsoranta kar ace ya dawo tana cikin sharar baccin nan,   Cikin sauri ta taka izuwa wurin window ɗinta,hannu tasa tare da janye curtains din sannan ta zuge glass ɗin tana hangen wajen harabar ajiye motocinsu,anan ta hangi motarshi ajiye alamar ya dawo kenan,     dafe saitin zuciyarta tayi gabanta na faduwa a fili tace"Nashiga uku ashe ya dawo,yanzu ya zanyi kenan nasan ranshi zai iya 6aci akan ban kai mashi coffee ɗin ba,"   cike da takaici taja guntun tsoki tare da cewa"duk wannan baccin ne daya ɗauke ni,da hakan bata faru ba,yanzu ya zanyi kenan gashi dare ma yayi sosai,in naƙi kai mashi matsala, in nakai mashi ma hakan zai iya jamin wani abun kuma,"   taƙarasa maganar tare da yanke shawarar takai mashi kawai,hannu takai tare da daukar mayafinta,ta rufe kanta dashi,sannan ta zura silifa aƙafarta,a hankali ta buɗe ƙopar ɗakin kamar mara gaskiya haka ta dinga tafiya har ta isa kitchen,shiga ciki tayi tare da wuce wa kai tsaye wurin cupboard,hannu tasa tare da curo cup ɗin data ware mashi nashan coffee ɗinshi,batare da 6ata lokaci ba ta zuba mashi coffee ɗin da zafin shi aciki cup,asaman plate ta aza mashi kofin sannan ta nufi hanyar fita,tana ƙoƙarin fita daga cikin kitchen ɗin sai ga Hayaam ta faɗo ciki,ba ƙaramin tsorata Sehrish tayi ba don har saida takusa zubar da coffeen dake hannunta,ido azare take kallonta don bata tsammaci mutum ba adai dai irin wannan lokacin,   tun da tazo gidan take ƙumshe aɗakinta tana baccin lalaci,koda ta farka bata fito waje ba,sai yanzu Allah yayi ta samu ta fito,short gown ɗin nan ce ta ɗazu ajikinta,kan nan nata ko arziƙin dankwali babu balle mayafi,sai dai gashin kanta data ɗaure abayanta,    Murya a sanyaye sehrish tace"Sannu da fitowa,ya gajiyar tafiya,"   Ƙayataccen murmushi hayaam ta saki tare da cewa"yawwa ƴan mata,gajiya tabi jiki yanzu ina jina normal,"   Ta ƙarasa maganar tare da kallon cup din dake ruke a hannun sehrish tace"Wannan fa?ke zaki sha ne"?   girgiza kai sehrish tayi tace"a'a banawa bane,babban yaya zan kaimawa ne,"   yamutsa fuska amani tayi tare da cewa"Oh ashe ya dawo cikin gidan kenan,"   Sehrish tace"eh,ya dawo," "ra'ayin kanki ne kai mashi coffeen ko kuma shi ya buƙata ne"?ta kuma jifarta da tambaya,     "Ai shi ba'a yi masa katsalandan,shi yace na rinƙa kai mashi a kullum wuraren ƙarfe sha biyu idan sun dawo daga aiki," ta bata amsa tare da kama hanya zata wuce,   Cikin sauri hayaam ta sake shan gabanta tare da cewa"gaskiya bai kamata ace ƙaramar yarinya kamarki tana kai mashi abunsha adai dai irin wannan lokacin ba,sam wannan tsarin baiyi ba,yakamata ace yanzu kina kwance kina bacci ko don saboda zuwa school yana da kyau ki rinƙa yin bacci da wuri," ..murmushin yaƙe sehrish tayi sannan tace"nagode da shawararki,amma wannan aikina ne kula dashi,kuma nasaba da yin hakan"    ganin hayaam zata 6ata mata lokaci yasa tayi saurin wuce wa batare da ta saurari sauran abunda zata ce mata ba,   jinjina kai hayaam tayi tare da cewa"yarinya dani kike magana,wato har wani faɗamun take itace mai kula dashi,shisshigi kawai da kutsi," ta faɗi hakan tare da jan dogon tsoki ta wuce bedroom ɗinta,    lokacin data ƙarasa part ɗinshi baya acikin falon hakan yasa kai tsaye ta wuce bedroom ɗinshi,sallama tayi mashi amma shiru ba'a amsa mata ba,almost 4 times tana zabga mashi sallama amma tsit babu alamar za'a amsa mata,   saurarawa tayi don taji ko zata ji motsin shi aciki,nan ma shiru ranta ne ya bata cewa kawai tashiga cikin bedroom ɗin nashi,    ƙafa tasa tare da shigewa ciki,nan take ƙamshin turaren nan nashi ya daki hancinta har saida ta ɗan ja da baya saboda yarda ƙamshin ya shigeta kai tsaye,sauke ajiyar zuciya tayi tare da ware idanunta tana bin bedroom ɗin nashi da kallo,wayamm tagani babu shi acikin ɗakin,tsayawa tayi tana tunanin ko'ina ya shiga ne,kodai bai dawo bane?amma kuma ae ga motarsu can awaje alamar sun dawo,har ta yanke shawarar barin ɗakin,zata juya kenan eyes ɗinta suka sauka akan fruits ɗin da takai mashi,wanda ta ajiye mashi asaman table din dake kusa da gadonshi,a rufe takai mashi kayan marmarin amma sai taga an cire plate din data rufe su dashi,alamar ya fara shan fruits ɗin kuma ya dakata,ranta ne ya bata cewa may be yana acikin toilet ne,    murmushi ta ɗanyi sannan ta ƙarasa wurin table ɗin tare da ajiye mashi cup of coffee din  agefen kayan marmarin,   tsayawa tayi tana tunanin ko dae ta tsaya ya fito daga cikin toilet ɗin wata'ƙil zai buƙaci wani abun bayan wannan,wata zuciyar kuma ta bata shawarar cewa ta tafi kawai tabar dakin saboda dare yayi sosai,    tana cikin wannan tunanin,sgr ya fito daga cikin toilet,waist ɗinshi na ɗaure da short towel wanda bai kai guiwar ƙafafunshi ba da alama wanka yayi aciki, sam bai lura da mutum a cikin bedroom ɗin nashi ba,gadan gadan ya tunkari wurin dressing mirror ɗinshi,cikin rashin sani tafin ƙafarshi ya hau saman 6awon ayabar daya ci ɗazu,ya maƙale masa a jikin shirt ɗinsa saida zai shiga wanka ne ya lura dashi yasa hannu ya ka6e shi ya faɗi anan ƙasa,aikuwa nan take wani irin mugun sul6i ya kwashe shi bazato ba tsammani gaba ɗaya ya tafi a burkice zai faɗi,a firgice sehrish ta juya tare da yin ƙoƙarin taimaka mashi cikin sauri ta ruƙo shi nan take ƙarfin shi ya rinjayi nata gaba daya suka faɗa saman shimfiɗeɗen gadonshi a manne da juna,tashin hankali da ba'a sama shi date,   wata irin nauyayyiyar azuciyar zuciya Sgr yashiga saukewa,tabbas ya ɗan firgita saboda bai tsammaci hakan ba,bai ta6a yin irin wannan gangancin ba,hada ƙarin sam ya manta da 6awon ayabar a wurin bai jefa shi dustbin ba,da ace sehrish bata ruƙo shi ba awannan lokacin da ba ƙaramin buguwa zaiyi ba yanda yake dogon nan,    atare zuciyoyinsu suka shiga bugawa da ƙarfi da ƙarfi,gaba ɗaya sehrish ta gama tsorata abun tamkar a amafarki take ganin shi,ta gaza yarda cewa itace tare da Surgeon general Rafayet kwance asaman gado ɗaya kuma amanne da juna,    gaba ɗaya jikinshi ya rufe nata hatta face ɗinta tana a saitin wide chest ɗinshi,tana jin yarda yake ta faman sauke ajiyar zuciya,da kuma yarda heart ɗinshi ke beating very fast,    tsit kake ji daga ita harshi an rasa mai wani kwakkwaran motsi,danshin ruwan dake ajikinshi ba ƙaramin sanyaya mata jikinta yayi ba,daƙyar take iya breathing saboda hancinta daya manne da fatar ƙirjinsa,haka la66anta ma suna manne da fatarshi,   Boss man ɗin fa ya gaza ɗago da jikinshi daga nata,ba don komai ba sai don yarda abun yazo mashi unexpected,ba ƙaramin jinjinawa lamarin yayi ba shi kanshi,    Jin yarda yarinyar keta kokawa wurin fitar da numfashinta,yasa ya daure tare da yunkurawa zai tashi daga jikinta,baiyi wani aune ba towel din dake ɗaure a qugunshi ya shiga warwarewa gaba daya dama daurin ya saki,   Shi kanshi baisan lokacin daya mayar da jikinshi asaman nata ba ya kwantar da kanshi a saman left shoulder dinta,bakomai ne yasa yayi hakan ba face gudun kar towel din jikinshi ya saki agabanta,don muddin hakan ta faru tofa wannan karon ba sume mashi zatayi ba,zuciyarta ce zata buga tabar duniyar saboda tsabar firgici don ya lura yarinyar ba ƙaramar matsoraciya ba ce,     wani irin yanayi mara misaltuwa taji atattare da ita,jikinta yayi wani irin sanyi sanyi kasala kasala haka,sam bata jin nauyin jikinshi akan nata sai ma yanayin da hakan ya jefa ta,     idanunta na'a rufe sam tagaza buɗesu ba don komai ba sai don tsoran abunda zai biyo baya,a matuƙar tsorace take hakan yasa ko kwakkwaran motsi tagaza yi,lumshe idanunshi yayi yayin da hancinshi ke gogar fatar wuyanta,fragrance ɗin turarenta ne yake kaimashi ziyara acikin hancinshi,ƙamshin ba ƙaramin daɗi yayi mashi ba,har lokacin tana jin yarda numfashinshi ke fita afatar jikinta,   almost 15mins suna cikin wannan yanayin,tajiyo hannunshi a hankali ya zura shi adai dai saitin waist ɗinshi don ya gyara ɗaurin towel dinshi,wannan moving ɗin da ya runka yi da hannunshi awurin yana gogar jikinta ba ƙaramin kashe mata jiki yayi ba,amace ta mace gaba ɗaya tashiga wani irin yanayi na daban....,    sai da ya samu ya ɗaure towel ɗin sannan a ƙaro na biyu ya ɗago da kanshi don ya raba jikinshi daga nata,nan take sehrish ta saki wata irin razananniyar ƙara gaba ɗaya ta gigita shi,ashe raɗaɗin Earring ɗinta ne daya sargafo gashin kanshi ya harɗe acikin ɗan kunnan,wannan ɗagawar da zaiyi ajikinta shine sumar kanshi taja ɗan kunnan nata da ƙarfi wannan ne dalilin dayasa ta fasa ƙara,cikin sauri Sgr ya mayar da kanshi tare da kwantar dashi agafen fuskarta,fashewa da kuka sehrish tayi sosai saboda ba ƙaramin zafi taji ba,don wurin harya fara fidda ɗigon jini,a hankali ya buɗe blue eyes ɗinshi tare da bin kunnan nata da kallo yarda sumar kan nashi ta harɗe acikin earring ɗin shine yafi komai bashi mamaki,tunani ya soma yi taya za'ai ya cire gashin nashi acikin ɗan kunnan nata?dole akwai buƙatar yabi a hankali wurin zagayo da hannun na dama don ya cire shi,    A hankali ya ɗago da fuskarshi daga gefen fuskarta,ya kasance cewa suna facing ɗin juna sosai,hatta numfashinsu yana haɗewa dana juna,wannan shessheƙar kukan da takeyi ne yaja hankalinshi wurin kallon fuskarta,la66anta har kerma sukeyi yayin da idanunta ke arufe,   Muryar shi ce ta katseta da cewa"I don't wanna hear that sound again,"   Cikin sauri sehrish ta tsagaita dayin kukan gaba daya,ta koma tana faman sauke ajiyar zuciya,   buɗe idanunta tashiga yi waɗanda ke cike tab da ruwan hawaye,tun kafin ta ƙarasa ware idanun nata take hangen hasken blue ɗin kwayar idanun shi,a hankali ta ƙarasa buɗe idanun sosai akan kyakkyawar fuskarshi dake fuskantar tata,duk da irin bugun zuciyar da take ji amma hakan baisa ta mayar da idanunta ba ta rufe su,    A natse ta soma bin pink lips ɗinshi da kallo shape ɗinsu ba ƙaramin kyau ne dasu ba,tausasan gaske,mayar da eyes ɗinta tayi akan dogon hancin shi da tsinin ke dab da nata hancin,ta jima tana kallon hancin nashi daga bisani kuma a hankali ta aza idanunta acikin nashi nan take taji wani irin bugun zuciya,     sai faman lumshe idanunshi yake yana kuma opening ɗinsu saboda baccin da yake ji,dama agajiye ya dawo cikin gidan,a hankali yake ɗan waresu akan idanunta,anatse yake bin long eyes lashes din idonta da kallo,har yanzu akwai sauran tears dake dripping a cikin idonta,sun jiƙa eyes lashes ɗin nata sharkaf,    Eyes balls ɗinta yabi da kallo a lokacin itama nata na'a kan kwayar idon tashi tana ƙarewa launin idon nashi kallo,kasa janye idanunshi yayi acikin nata,kamar yarda itama tagaza janye nata acikin nashi duk da tsoran kwayar idon nashi da take ji,    Suna cikin wannan yanayin a hankali ya zagayo da right hand ɗinshi ta saman kanta,ya ƙaraso dashi wurin ɗan kunnan nata sannan ya haɗa da hannun shi na hagu ya shiga ƙoƙarin cire gashin nashi daga jikin earring ɗin nata,         runste ido sehrish tayi saboda zafin da take ɗan ji a wurin,ganin hakan yasa ya haɗe fuskokinsu awuri guda,jin yarda lips ɗinsa suka manne da nata tamkar zaiyi kissing ɗinta hakan ba ƙaramin rikitar da ita yayi ba,    duk yarda yaso ya cire gashin daga jikin ɗan kunnan abun ya gagara ganin hakan zai 6ata mashi lokaci yasa yayi deciding tsinka gashin kan nashi daya sargaho earring ɗinta,    Cikin sa'a ya katse gashin nashi yabar mata sauran siraran da suka ruƙo dan kunnan nata,    Sai da ya raba ɗan kunnan sannan yaji wata irin kasala ta baibaye shi,lokaci guda ya rasa karfin janye jikinshi daga nata,ya dai samu ya ɗan janye face ɗin shi daga nata,sai kan head ɗinshi ya koma asaman boobs ɗinta,lamo yayi yana jin wani irin yanayin da bai ta6a ji ba arayuwarshi har wani bacci sosai ya dinga fisgarshi,sehrish kuwa tuni bacci yayi awon gaba da ita don bazata iya jurewa wannan yanayin ba,hannunta na asaman waist ɗinshi ta ƙankame shi sosai ajikinta,hada ƙarin hakan ya ƙara kashe mashi nashi jikin,   Mamakine ya kama hayaam ganin cewa har yanzu Yarinyar bata fito daga part ɗin sgr ba,ashe tun bayan da sukayi magana da sehrish ta koma bedroom ɗinta sam tagaza samun natsuwa shine ta dinga leƙowa don taga ko yarinyar ta fito daga part ɗin nashi,amma shiru babu alamar cewa ma zata fito,hakan ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,nan tashiga zargi kala kala acikin zuciyarta tana cewa"ko uban mi ya tsayar da ita ɗakin shi a irin wannan lokacin,ni dama banyarda da yarinyar can ba,daga ganinta irin sumu-sumu kasau ɗinnan ne,wlh saina yi maganinta bazan bari taci gaba da shiga sashen shi ba,     tun tana sa ran fitowar sehrish harta haƙura ta koma bedroom ɗin data sauka,shiga ciki tayi tana ta faman sambatu kamar wata zararra duk akan sehrish ne take wannan 6acin ran,      ****************** *Junaid Romeo* Bacci yake yi amma gaba ɗaya jikin shi kerma yake yi sosai da sosai,sai faman mutsu mutsu yake yi da alama baijin daɗin jikin shi,wata irin Zufa ce take tsattsafowa daga jikin shi saƙo da lungu na jikinshi gaba ɗaya ya kasance ajiƙe yake sharkaf,a wani irin firgice Junaid ya farka arazane yana faman zazzare manyan idanunshi da suke cike tab da kwalla,   Yana ƙoƙarin kai hannu ya tashi Abbansu dake kwance a gefen shi,sai ga wani baƙin hayaƙi ya fito daga Cikin mirror ɗin ɗaƙin mai yawan gaske baƙi wulik,bin hayaƙin junaid yayi da idonshi yana kallon shi a matuƙar tsorace,tattarewa hayaƙin yayi wuri guda kai tsaye ya nufi wurin shi,gaba ɗaya ya tunkare shi,ganin hakan yasa junaid faɗawa jikin abban nasu tare da ƙanƙame shi gaba ɗaya duk yabi ya firgice,kafin Abban nasu ya farka tuni wannan baƙin hayaƙin ya mamaye jikin junaid ta ƙofar hancin shi yabi ya dinga kurɗaɗawa cikin jikinshi,fashewa da matsanancin kuka junaid yayi yana ambaton sunan abban nasu,"Abba ka tashi dan Allah,abba pls ka tashi,bansan meke shirin faruwa dani ba,Abba ka tashi kaga halin da baby junaid ɗinka yake ciki",   duk wannan koke koken da junaid keyi abun mamaki ko motsi Abban nasu baiyi ba,sosai junaid ya dinga jijjiga jikinshi yana ambaton sunan shi amma shuru bai farka ba,babu alamar cewa zai farkama,    Allah sarki,sun sangartar da junaid sosai wanda hakan yasa bai iya ambaton wata addu'a acikin bakin shi ba,sai ihu da yake yi yana koke koke,ko addu'ar bacci wannan junaid bai ta6a yi ma kanshi ba,saboda ya saba kullum in Abbansu na nan shike yi masu addu'ar su kwanta atare,in kuwa abbansu bai nan anyhow yake baccin shi batare da tunanin yin addu'a ba,tsantsar son da suke yi mashi ne yasa basu son ya wahala ko kaɗan,junaid bai ta6a zuwa islamiyya ba don koyon wani abu na addini,amma Abbansu da kuma ƴan uwanshi suna zaunar dashi su koyar dashi wasu abubuwan sosai,a kwanakin baya har malami abbansu ya samo wanda zai dinga koya mashi karatu,tun rana ta farko da malamin yazo zai koya mashi karatu basu ƙara ganinshi ba,6at aka neme shi aka rasa,kusan sau huɗu hakan na faru duk in Abbansu ya samo malamin da zai koyar dashi addini daga yazo sau ɗaya sai a neme shi arasa,hakan yasa daga baya ya haƙura da neman malaman da zasu koyar dashi,musamman da yaga ƴan uwanshi na koyar dashi acikin gidan sai hankalinshi ya kwanta da hakan,abun da baisani ba kosu da suke koya mashi agabansu yake nuna ya fahimta kuma ya gane karatun amma da zarar yabar wurin karatun tofa komai ya zube acikin kanshi,yadawo zero 0    Wani irin sanyine ya gauraye ko'ina na sassan jikinshi,lamo yayi abayan abban nasu yana faman sauke ajiyar zuciya,a wannan yanayin kuma bacci yayi awon gaba dashi,🥺    Meke shirin faruwa ne!? A hankali ta soma buɗe idanunta dake ɗauke da bacci biji biji ta soma gani kafin daga bisani suka washe ta dinga ganin komai normal,jin babu nauyin mutum akanta yasa ta gane cewa sgr ya bar jikinta,cikin sauri ta miƙe zaune tare da kai idanunta inda yake kwance yana bacci,zuba mashi ido tayi tana kallon shi,yanayin yarda yake baccin zai tabbatar maka da cewa yana cikin kwanciyar hankali da natsuwa,    A hankali takai hannu tare da jan blanket ɗinshi ta rufe mashi jikin shi har wurin wuyan shi sannan ta saki bargon,    tamkar karta tafi tabarshi haka ta dinga ji,hannu takai tare da ruƙo sumar kanshi mai laushin gaske,ta tattare mashi ita tare da yin gefe guda da Ita,hakan ne ya bata damar kallon kyakkyawar fuskarshi sosai,   Cikin sanyin murya tace"inason farin ciki ya cigaba da wanzuwa a wannan kyakkyawar fuskar taka,kuma insha Allah zan tabbatar da hakan,zan cigaba da addu'a akan Allah ya mallakamin kai amatsayin abokin rayuwata,duk da nasan cewa zaiyi wuya hakan tafaru saboda kafi ƙarfina sosai nesa ba kusa ba"    Jiki asanyaye taƙarasa maganar yayin da ta juya tare da saukowa daga saman gadon nashi,sai da tafara kashe mashi hasken ɗakin sannan ta fuce daga part ɗin nashi,   A 6angaren Amani kuwa tunda tabi bayan motarsu da gudun gaske,bata ci nasarar taddo tasu motar ba saboda suma gudun sukeyi tuni sun 6ace ma ganinta,jiki asanyaye tayi parking ɗin motarta agafen titi,tamkar zata fashe da kuka haka ta dinga ji,hannu takai tare da ɗaukar wayarta dake ajiye asaman laps dinta,missed calls ta gani na Abbas har kusan shida,duk bata ji ringing ɗin da wayar keyi ba,saboda bata cikin natsuwarta hankali atashe tace"nashiga uku!Ashe abbas ya kira ni bansani ba,yanzu mai zan faɗa mashi,gashi ban hadu da wadda akace Amal ce..."    fuskarta a yamutse tayi maganar,yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin dialing ɗin numbarshi tabi kiran da yayi mata,tana fara ringing ya ɗaga kiran,cikin sauri takara wayar a kunnanta,saurarawa tayi tana jiran jin me zaice,    "Ki dawo gida inason ganinki," Yana faɗin hakan yayi rejecting ɗin kiran nata,   Nan fa ido ya raina fata,a kasalance ta tashi motar tare da karya kwana ta miƙi hanyar komawa gida, ************************* Sosai Amal ke kuka tana ambaton sunan Allah abakinta duk tabi ta zauce,   Rai a6ace JAHAN yace"yarinyar nan tayi mun shiru!nagaji da jin tsiwarta,duk tabi tayi confusing ɗina,Ayaan kodai ka toshe mata baki ko kuma in dakatar da driving ɗin nan don ni bazan juri tsiwarta ba,"    cikin sanyin murya Ayaan yace"pls take it easy Jahan,yarinyar nan fa ba ƙaramin jiki take ji ba,ita kanta bazata iya control ɗin kanta ba saboda raɗaɗin ciwon da take ji,"   Uban tsoki jahan yaja yana faman hura hanci,adai dai lokacin suka ƙaraso da Amal katafaren asibitin sgr,shiga da motar ciki yayi tare da samun wuri yayi parking ɗinta,fitowa Ayaan yayi kafaɗar shi ɗauke da Amal kai tsaye ya wuce da ita cikin asibitin,   Jahan kuwa zaman shi yayi acikin motar yana jiran ƙarasowar ayaan ɗin,don yace bazai shiga cikin asibitin ba,ya miƙata kawai ya fito su juya,    Ayaan na shiga ciki da sauri reception nurses suka kar6e ta,tare da wuce wa da ita medical room don a kwantar da ita,    tsayawa yayi yana faman zarya a wurin,kiran jahan ne ya shigo wayarshi cikin sauri ya ɗaga kiran tare da karata a kunnan shi,    tunkafin yayi magana jahan yace "what are u waiting for Ayaan!tun da ka miƙa ta awurinsu ka fito kawai mu juya gida,"    amsa mashi yayi da okey,sannan ya kashe kiran,   harya juya zai fita daga corridor ɗin,yajiyo muryar wata nurse tana dakatar dashi,tsayawa yayi tare da juyawa yana kallonta,ƙarasowa tayi da sauri cikin harshen turanci ta soma yi mashi magana"sir yarinyar taƙi bari mu dubata,da alama tana da damuwa sosai,akwai wani suna da take ta ambato abakinta,in badamuwa muna so ka shigo daga ciki kayi mata magana,may be ta samu natsuwa,"    batare da musu ba,Ayaan yabi bayanta har cikin ɗakin da suka kwantar da Amal,sai faman kuka takeyi tana kiran Sunan Aunty amani,tana cewa dan Allah su kira mata ƴar uwarta karta mutu bata sata a idonta ba,    ganin shi yasa sauran nurses ɗin dake aciki suka ja da baya tare da bashi wuri don ya wuce,   Ƙarasawa ayaan yayi tare da samun wuri daga gefen gadon da take kwance,yama rasa ta yarda zai shawo kan yarinyar don tayi nisa bata jin kira sai faman sharara kuka takeyi ta cika ko'ina da kukan nata,    tsawa ya daka mata,aikuwa a firgice ta mayar da idanunta akanshi yayin da jikinta yashiga yin kerma saboda tsoran da taji,   Yarda ya zare mata idanunshi ba ƙaramin tsoro taji ba musamman launin kwayar idonshi da takasance ash colour,   Lokaci guda tayi tsit tana faman zazzare idanu,   dama yayi mata hakan ne don tayi shiru,sassauto da murya yayi tare da cewa"faɗamun menene damuwar?bakyaso ne ayi treating wounds ɗin dake ajikin ki?ko so kike ki mutu ne?   Cikin shesshekar kuka tace"banso na mutu,inason ganin Auntyna ne,dan Allah ku kira mun ita tazo naganta kafin na mutu,inason ganinta,"    tsananin tausayinta ne ya kama shi,bin idanunta yayi da kallo ganin yarda hawaye ke kwaranyo daga cikinsu,yarinyar dae ba ƙaramin jiki taji ba da alama,    ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa"yanzu baki da lafiya,ki bari su duba jikinki,in yaso zuwa gobe ni dakaina zan kira maki auntynki a waya,kin amince da hakan"?    amsa mashi tayi da eh,sannan ya miƙe tare da yi masu sallama,ya fuce daga asibitin,    shaf shaf suka bar Asibitin da motarsu, Koda Amani ta koma gida,abbas baiyi mata faɗan komai ba,ko tambayarta inda taje baiyi ba,hakan ba ƙaramin daɗin yayi mata ba,dama fargabarta kenan karya tuhumeta akan ina taje acikin daren nan, *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. _💋Boss Bature💋_ قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Amalil Islam Kwance take saman gadon asibitin hankalinta kwance sai faman sharar bacci take,tasamu kulawa sosai wurin nurses ɗin nan gaba daya duk wani rauni da taji anyi mata dressing ɗin wurin,a daren jiyan nan har ƙarin ruwa su kayi mata fiye da leda ɗaya don taji jiki,da safe kuwa kyakkyawan breakfast tasamu na kyauta da suke rabawa asibitin,sai da taci tayi hani'an sannan tafara wannan baccin,har farkawa tayi tana neman waɗanda suka kawota asibitin don su kira mata Auntynta kamar yarda ɗaya daga cikinsu yayi mata alƙawarin cewa zai kira mata ita, nurse ɗin dake kula da itace ta sanar da ita cewa basu zo ba,sam hankalinta bai tashi ba,don ita ji take koda basu zo ba,ba inda zataje ita fa tayi gida acikin asibitin don ba ƙaramin daɗinshi take ji ba, Wuraren ƙarfe 12,Motarsu Jahan ta shigo cikin katafaren asibitin,a hankali sukayi mata gurbi a parking space ɗinsu,ɗagowa jahan yayi tare da kallon ayaan dake a gefenshi yace"zan jiraka anan and don't keep me waiting"    Wurga mashi kallo Ayaan yayi tare da cewa"bro kai fa baka da imani na lura,jiya kaine kayi causing accident ɗin nan,yarinyar ta raunata amma ko zuwa ciki ka leƙata bakayi ba,atlease ya kamata kaje ka dubata yau,"    ɗaure fuska Jahan yayi yace"bani ne Sila ba!yarinyarce ta fado mana agaban moto dinmu all of a sudden,har nagaza cin burki,so am not guilty,'    Cikin lallashi ayaan yace"pls mu shiga atare mana,"yarda yayi maganar da ƴar shagwa6a afuskarshi yasa Jahan cewa"taci albarkacin wannan shagwa6ar da kayimun da ba don haka ba,ba inda zanje,"    Murmushi Ayaan yayi tare dasa hannu ya buɗe motar ya fito waje,shima Jahan ya fito daga cikin motar,atare suka jera tare da nufar interior din asibitin,    Ayaan ne ya fara shiga room ɗin da aka kwantar da Amal sannan jahan yabi bayansa suka shiga ciki atare,   Lokacin da jahan ya aza idonshi akan Amal dake baje saman gadon tana sharar bacci,a wani irin firgice yaja da baya yana faman zare ido,   Kallonshi ayaan yayi tare da cewa"meya faru ne bro?naga kamar ka tsorata da wani abu,   Nuna amal yayi da yatsan shi tare da cewa"Ayaan dama wannan halittar muka kwaso acikin motar mu jiya?shiyasa akace rashin sani yafi dare duhu Ya ilahi da nasan hakane da ban sha wahalar ɗaukota ba Allah,dole ayi mana wankin mota yau,"    baki asake ayaan ke kallonshi,duk wani wulakanci da anzo kan Jahan to an ƙare,don shi kankat ne dama yana ɗaya daga cikin waɗanda suka ɗauko ɗabi'un mahaifiyarsu da halayyarta kaf bai bar komai ba,"    girgiza kai kawai Ayaan yayi tare da wucewa wurin gadon da Amal take,wuri yasamu asaman chair ɗin dake fuskantar gadon nata ya zauna yana kallonta gwanin ban tausayi,   Jahan kuwa koda ya matso wurin bed din nata,goya hannun shi yayi asaman ƙirjin shi yana binta da kallo a ƙyamace yace"Anya Ayaan yarinyar nan ma tana numfashi kuwa?karfa mu ƙarasa gawar da ba tamu ba"   Murmushi kawai Ayaan yayi tare da kai hannu ya dan bubbugi pillown da Amal ta kwantar da kanta sama,   Firgigit ta ware idanunta tana faman binsu da kallo ganin mutum biyu iri ɗaya,hannu tasa tare da ɗan murza idanunta tana ƙare masu kallo, lokaci guda ta gane cewa identical twins ne,    "Barka da safiya,ya jikin naki,"?ayaan ne ke tambayarta fuskarshi asake,hakan ne yasa ta gane cewa shine na jiyan nan da yayi mata alƙawarin kiran Auntynta,   Ƙoƙarin tashi Amal tashiga yi,cikin sauri Ayaan ya taimaka mata ta zauna tare da dan tada bayanta a jikin pillown,    Cikin sanyin murya tace"Alhmdllh,naji sauƙi sosai,"    "Kinyi breakfast"? Ya kuma tambayarta,ɗaga mashi kai tayi alamar eh,   Lumshe idonshi yayi tare da cewa"Masha Allah,so now tell me, how can i help u? Zuba mashi ido tayi tana kallonshi,hakan ya tabbatar mashi da cewa bata gane me yake nufi ba,don haka yace"ina nufin taya zan iya taimaka maki ne?wurin haɗuwa da Auntyn naki"?   Cikin sauri tace"ina da numbarta akaina," Amsa mata yayi da okey,sannan ya zura hannunshi acikin trouser pocket dinshi ya ciro wayarshi,karanto mashi numbar Amal tashiga yi shi kuma yana dialling numbers ɗin acikin wayarshi,bayan ya kammala rubuta numbar ya buga call ɗin nan take Sunan Matar yaya ya bayyana akan wayarshi,tsananin mamaki ne ya kama shi aranshi yace wannan ae numbar Amani ne matar Yaya Abbas,kanshi ya gama ɗaurewa a lamarin,har kiran ya katse amani bata ɗaga ba,almost 6 times yana kiran numbarta amma ba'a daga ba,hakan yasa ya ɗan dakata tare da kallon Amal yace"idan ba damuwa inason jin yaya kuke da Auntyn nan taki da kika ban numbarta....'tunkan ayaan ya ƙarasa maganar jahan ya buga tsoki tare da cewa"Ayaan am tired ka tashi kawai mu tafi,bansan menene amfanin tambayarta ba,    mayar da idonshi yayi akan na Jahan yace"pls ka bani time,zan faɗa ma dalilin dayasa nake tambayarta,"   tsuke fuska jahan yayi yana faman hura hanci,    "Ina sauraronki," muryar ayaan ce ta katse mata tunanin data tafi,   Murya asanyaye tace"ƴar uwatace ita,na jima ina nemanta bamu ta6a haɗuwa da ita ba,ita ma kuma nema na takeyi,tunda tayi aure na rabu da ita,shine yanzu nasamu sunan garin da take nazo,amma bansan a ina zan sameta ba,abu ɗaya kawai nake dashi numbar wayarta,drivern daya kawoni ya kirata a waya ya sanar da ita cewa tazo ta ɗauke ni,batazo ba shine wasu mutane suka biyoni acikin tashar,wannan ne dalilin dayasa nayi gudu harna faɗa saman titi Motarku ta buge ni.........'    jinjina kai Ayaan yayi tare da cewa"Yanzu idan na kaiki gidan Auntynki,Ni kuma wani tukuici zaki bani,"    cike da mamaki tace"kasan inda take ne"?   Lumshe idonshi yayi tare da cewa"a'a bansan inda take ba,amma inaso zan kaiki wani wuri in ba damuwa,bari nasa doctor ya sallame ki,sai mu tafi atare,Zaki bini?    shiru ta danyi tana tunanin karfa tayi gangancin binsu wani abu ya faru da ita,tunda ita dae batasan ko su wanene ba,amma ta wani 6angaren taji cewar zata iya binsu saboda ta yarda dashi sosai,ba don komai ba sai don yarda yake yi mata magana cikin lallami,"    amsa mashi tayi da eh,miƙewa ayaan yayi daga saman chair din,ruƙo hannun jahan yayi tare da janshi gefe guda yace"ko kasan cewa numbar da yarinyar can ta bani na kira mata auntynta,ta matar Ya Abbas ce Amani!"   Fuska ɗauke da mamaki Jahan yace"Really?kenan ƙanwarta ce ita,amma indai hakane ya akai ita yarinyar ta kasance haka?   Ayaan yace"abunda nake tunani kenan nima,"    jahan yace"Ba shakka,dama na jima ina tunanin taya akai Ya ishaq da Ya Abbas suka auri waɗannan matayan nasu,Nidae raina ya jima yana bani cewa matsiyatan talakawa ne,saboda koda mu kaje ɗaurin aure fa a maid,bakaga tsohonsu ba wani zararre dashi,yadin jikinshi duk ya koɗe,zariyar wandonshi fa har ƙasa take ja,abun kunya...'   Rufe mashi baki Ayaan yayi cikin sauri saboda yarda yake magana yana ɗaga Voice ɗinshi,yarinyar zata iya ji,    "Pls jahan its okey,mubar wannan zancen nidae yanzu so nake mu ɗauki yarinyar mukaita gidan Auntyn nata...'tunkan Ayaan ya ƙarasa maganar Jahan yace"Wai a motar wa kake nufin za'a kaita?ae wlh waccan sauran ramin bazata ƙara zauna mana a motar mu ba,sai dai ka tsaida taxi ta kai ku atare,ni kaga tafiyata"yana kai ƙarshen maganar tashi ya juya tare da fucewa daga cikin room ɗin,    girgiza kai kawai Ayaan yayi tare da cewa"sai yanzu nasan da wa nake tare,Jahan sam baka da mutunci,haihuwarmu kawai akai atare amma zuciyoyinmu ba iri ɗaya bane,ni ta 6angaren Abba nake kai kuma ta 6angaren Mommynmu kake da kuma Ammi dama sune masu zafi,' Batare da 6ata lokaci ba,Ayaan yasa aka sallami Amal ba don komai ba sai don yayi suprising ɗinta,kamar yarda jahan yace sai dai su hau taxi hakan ce tafaru,a bakin Hospital ya tsayar masu da taxi suka shiga ciki atare, **********************Reeshi Zaune suke acikin class sun natsu suna sauraron karatun da akeyi masu,malaminsu ne mai koyar dasu islamic studies,tun da ya fara karatun ya lura da yarinyar dake kwance tana yi mashi bacci acikin class,shiru kawai yayi baice komai ba,sai da ya kammala karatun sannan yace"wacece waccan yarinyar dake yi mun bacci acikin class"?ya tambaya yana nuna sehrish da maker ɗin hannunshi,   kamar jira ƴan class ɗin sukeyi ya tambayesu nan fa kowa yashiga bada bayani,    "Uncle ae wannan yarinyar da kake gani sleeping sickness gare ta,ba'a ta6a yin darasi ba idonta biyu,kullum cikin bacci take kamar mai tsohon ciki," fashewa da dariya ƴan class din sukayi,   Wani kuma yace"sir,da zarar tearcher ya shigo cikin class shikenan zaka ga ta fara hamma,daga nan sai bacci,"    Bayan ya gama sauraron bayanansu,ya taka ya ƙarasa inda seat din sehrish yake,hannu yasa tare da ɗan bugun desk din,a firgice sehrish tafarka tare da ɗago da kanta daga saman desk ɗin tana kallonshi,    jallabiya ce ajikinshi fara,ya tara dogon gemu,kana ganinshi zaka san cewa ba ƙaramin malamin addini bane,fuskarshi na manne da farin glass yayin da kanshi ke anaɗe da rawani,     hankali tashe sehrish ke kallonshi tayi wuƙi wuƙi da ido saboda tsoran karya hukunta ta akan baccin da take yi mashi a class,    Cikin harshen larabci yace mata ta miƙe tsaye,jiki na rawa sehrish ta miƙe tana faman zazzare ido,    "Kalli cikin idona,"ya bata umarni,sunnar dakai sehrish tayi tana faman jin wani irin bugun zuciya,maimaita mata ya sake yi da cewa"bakiji me nace ba!ki kalli cikin idona!"    ƙin ɗagowa tayi da idonta ta kalleshi,kuma nan take jikinta ya shiga yin kerma,   Ƴan class ɗin duk sun zuba ido suna kallonsu,musamman amrish da tashiga damuwa ganin kamar malamin nason takurawa ƙawarta,   Cikin sauri tace"pls uncle ayi mata afwa,bazata ƙara ba,'   Batare da ya kalleta ba yace"Amrish ba laifi tayi mun ba,in fact nikeson taimakonta,shin wannan yarinyar ƴar wani gida ce"?ya tambaya yana jiran amsarsu,har lokacin sehrish na tsaye kanta na kallon kasa a matuƙar tsorace take,    amsa mashi su kayi da cewa"bamu san a wani gida take ba,lokacin da aka kawota class ɗinnan tayi introducing ɗin kanta amman bata faɗa mana family status ɗinta ba,,'   Amrish tace"nima bansan taƙamaimai daga inda take ba,amma akwai wani elder bro dinta dana sani sunan Shi Junaid romeo,muna shiri sosai dashi,'   mayar da idonshi yayi kan fuskar sehrish yace"Ke!a wani gida kike?su wanene iyayenki?   murya na rawa tace"Ni....ni..daga family din SALAHUDDEEN HUSSEIN nake Abban sojoji....'tunkan ta ƙarasa maganar malamin ya waro ido waje yana kallonta,bama shi ba hatta sauran student ɗin cike da mamaki suke kallonta,sun jinjinawa gidan da tafito bakomai yafi ɗaure masu kai ba face yarda ta kasance ba ruwanta da kowa haka,bayan duniya tasan da zamansu,   "Kina nufin ke ƙanwar Surgeon genaral rafayet ce!da marshal Omar!"? Amsa mashi tayi da cewa"eh,"kuma har lokacin bata ɗago da ido ta kalleshi ba,   Jinjina kanshi yayi yana tuna wani abu daya ta6a faruwa dashi wanda ke da alaƙa da gidan,"     gajiya da tsayuwa sehrish tayi nan take idonta suka soma shararo da kwalla,don bata da juriyar wahala irin hakan,tun lokacin data fara rayuwar hutu da jin daɗi,    "Insha Allah bazan fasa ba,kamar yarda nayi kyakkyawar niyyar taimakawa tun a lokacin baya,don haka zan taimaka maki tunda Allah ya haɗani dake," malamin ne yayi wannan maganar,sannan ya mayar da idonshi kan amrish dake zaune a seat ɗinta tana kallonsu yace"Amrish idan na kammala yi maku karatu ki same ni a office ɗina zan baki ruwan addu'a kiba wannan yarinyar tayi amfani dashi," Amsa mashi tayi da toh sir,sannan yaja da baya tare da juyawa ya koma wurin board,    Jiki asanyaye sehrish ta koma tare da zaunawa tana faman sauke ajiyar zuciya,aranta tana mamakin ruwan addu'ar mi zai bama amrish ta bata,gaskiya ni bazanyi amfani dashi ba,lafiya ta lou,koya ban zubarwa zanyi.......'   Sai faman sambatu takeyi ƙasa ƙasa sam takasa samun natsuwa har sai da Malamin yabar Class ɗin,tashi amrish tayi tare da binshi don ta amso mata ruwan addu'ar dayace zai bata. bayan mai taxi ɗin ya sauke su,hannunshi ruke dana Amal suka shiga cikin gidan,gaba ɗaya duk tabi ta susuce tana kallon katafaren gidan duk a tunaninta kodai gidansu ne ya kawo ta? Lokacin da suka shiga katafaren palourn babu kowa acikin shi,tsayawa yayi tare da ita atsaye yana jiran ganin ko wani zai fito,ita kuwa Amal wuyanta kamar zai tsinke saboda kalle kalle muryar Ayaan ce ta katse ta da cewa"har yanzu ciwon na maki zafi?girgiza kai tayi tare da cewa"a'a babu zafi ina lafiya,"   "Okey,ki ɗan ƙara jira nasan matar gidan zata fito ne,bari na sake kiran layinta,"   Hannu yasa tare da ciro wayarsa yana ƙoƙarin danna ma Amani kira,kunnan shi suka jiyo mashi takun takalmanta kwas kwas,ɗagowa su kayi gaba ɗaya suna kallonta,hannunta na ɗauke da tray da alama kayan breakfast ɗinsu da suka ci na safen nan ta fito dashi daga bedroom ɗinta dake a upstairs,jallabiya ce fara ajikinta ta yafa mayafin akanta,   A hankali take saukowa down stairs sam bata lura da mutane ba,ƙura ido Amal tayi tana kallonta sam takasa gane wacece,juyawa ta danyi tare da kallon Ayaan tana neman ƙarin bayani,a lokacin shima idonshi na akanta yace"baki gane ta ba ko"?   ɗaga mashi kai tayi alamar eh,murmushi yayi tare da cewa"Bari ta matso kusa,"   Gyaran murya Ayaan yayi wanda hakan yasa Amani tayi firgit tana kallonsu,murmushi ta saki ganin Ayaan cikin sauri taƙarasa saukowa daga saman stairs ɗin ta tunkaresu,zuba mata ido Amal tayi tana kallonta tabbas taso ta shaidata amma abunda yayi confusing ɗinta shine,taya zata kasance wadda take tunani tunda saurayin ya kawota gidan tafi tunanin ko Auntynshi ce,   Tunkan Amani ta ƙarasa inda suke,hankalinta yakai ga Amal binta da kallo ta dinga yi cike da mamakin ina Ayaan ya samo wannan yarinyar haka,duk taji jiki kodai ya fara taimakon marayu ne,   tsayawa tayi kusa dasu idonta na akan Amal ita ma kallonta takeyi,ji tayi gabanta na faɗuwa rasss rassss,cikin sauri ta mayar da idonta akan Ayaan murya na rawa tace"who...who is she pls?    Murmushi ayaan yayi yace"i don't even know,ni dai ta bani numbar auntynta ne tace na kira mata ita,shine dana sa numbar Auntyn nata sai sunanki ya bayyana akai,that's why nayi deciding kawota wurinki,maybe adace.........'tunkan ya ƙarasa maganar a firgice Amani ta saki tray ɗin hannunta ya tarwatse ƙasa,zube wa tayi saman guiwowinta kusa da Amal ɗin ta ruƙo hannunta tana cewa"Amal kece dagaske nake gani,ko idona ne Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,"!!!   Tuni hawaye sun cicciko acikin idonta,   Itama Amal ɗin tuni ta fara shararo hawaye saboda ta ganeta yanzu musamman data ambaci sunanta,   Cikin shessheƙar kuka tace"Ni...Ni ce aunty Amani,ashe dama zan sake ganinki arayuwata.........'kukane yaci ƙarfinta hakan ne yasa takasa ƙarasa maganar,atare suka fashe da kuka suna yi kamar kamar me,    Muryar Ayaan ce ta katse su da cewa"pls Aunty amani,ki lallasheta akwai wounds ajikinta idan tana kuka hakan zai ƙara mata raɗaɗin ciwon,"dakyar Amani ta tsagaita da kukan nata kallon fuskarta har izuwa jikinta,tayi matuƙar tsorata da ganin yarda yarinyar ta tsotse ta rame ta ƙanjame kamar kwarangwal,ƙashin wuyanta kamar zai ballo waje,komai na yarinyar da zai nuna cewa ita macece babu shi,sai dai ta hanyar shigarta ta mata da kuma muryarta,    Janyota tayi ajikinta tare da rungumeta sosai tana ci gaba da ambaton sunanta"Amal amal ɗita ce ta koma haka?meya faru dake Amal ya akai kika 6ata,ki ka tafi kika barni inata nemanki Amal,"   Ganin halin da suka shiga yasa Ayaan yanke shawarar tafiya yabarsu,juyawa yayi kawai tare da kama hanya ya fuce daga falon dama jahan sai doko mashi calling yake,   Anan ƙasa Amani da Amal suka zauna atare suna fuskantar juna,   "Amal kina jin yunwa"? Jin wannan tambayar yasa hawaye suka ƙara cika mata ido,yaushe rabon da wani ya tambayeta tana jin yunwa harta manta Allah sarki ɗan uwa mai ɗaɗi,musamman in ya kasance shaƙiƙin kane kuma kuna son junanku,    Murya asanyaye tace"bana jin yunwa naci abinci a asibiti,"    Jinjina kai Amani tayi tare da cewa"inason jin Ya akai kika 6ata Amal kika barni?mammy ta sanar dani cewa bakyajin magana wai kina zuwa yawo sun hanaki kin ƙiya shine kika 6ace aka neme ki aka rasa....'    Girgiza kai tashiga yi yayin da hawaye ke cigaba da sharara a idonta tace"Aunty amani wannan duk ƙaryace suke yi maki!nagode ma Allah da ya haɗani dake,a yau inaso zan sanar dake komai game da irin cin zalin dasu Mammy sukayimun na raba ni dake,    Hankali tashe Amani ke kallonta murya na kerma tace"faɗamun meya faru dake!wani irin cin zalin su kayi maki,"   Batare da 6ata lokaci ba,Amal ta zayyana mata duk irin ƙarairayin da sukeyi mata akan cewa ta 6ace,da kuma irin wahalar da takesha a hannunsu da kuma kaita da sukeyi gidan makwabtansu ana kulleta,babu abunda Amal ta 6oye mata kaf takwashe ta sanar da ita,   A kiɗime Amani ta miƙe tsaye cikin tsananin 6acin rai,jikinta har kerma yake yi,wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga shararowa a idonta,    Sai faman cizon yatsa take yi tana danasani,kai aƙarshe data rasa abunyi sai ta sake fashewa da wani matsanancin kukan tana girgiza kai tana cewa"Wlh bazan ta6a raga masu ba!mugaye azzalumai kawai,banta6a ganin mutane masu zuciyar kafirai ba irin tasu,Sun cutar dake Amal kuma sun cutar dani sun yaudareni sunyi mun ƙarya suna samun kuɗi awurina na cewa za'a ba malamai suyi addu'ar neman sa'a akanki ashe duk ƙarya ne!!!!basu tsaya a iya kanmu ba sun cutar da mahaifiyarmu har saida tabar duniya ga mahaifinmu da suke ta gana ma azaba,nayi tunanin soyyaya suke nuna min ta ƴan uwantaka shiyasa na saki jiki dasu har nake ƙoƙarin taimaka musu wurin cimma wannan mummunan ƙudirin nasu,ashe cutata suke suna can suna gana ma ƙanwata azaba,na cuci kaina!tun yanzu Allah ya fara nunamin irin kuskuren da nake ƙoƙarin yi na taimakama waɗancan bijimayen.......'tsagaitawa tayi da maganar tana faman shessheƙar kuka,daga bisani ta ɗaura da cewa"wlh saina tarwatsa duk wani plan ɗinsu uban kowa ya rasa don bazan kyalesu ba,muddin ina numfashi hayaam ko abra ɗaya daga cikinsu bazai ta6a auran jinin salahuddeen hussein ba!!!!, abun ba ƙaramin ƙona ma Amani rai yayi ba,ta fusata ainin zuciyarta har wani tafarfasa take yi saboda 6acin rai, Hannu tasa tare da matse kwallarta sannan ta juya tare da takawa takai hannu ta ruƙo hannun Amal ta miƙar da ita tsaye,sannan ta wuce da ita cikin bedroom ɗinta gado ta nuna mata tare da cewa"Amal ki kwanta ki huta kin raunata sosai,amma karki samu damuwa tunda Allah ya haɗaki dani ƙarshen wahalar ki tazo insha Allah,zakiyi rayuwa tare da Auntynki zan baki kyakkyawar kulawa,kuma zan kira doctor domin ya ƙara dubamin lafiyarki da kyau har kiji sauƙi, Ba ƙaramin daɗi Amal taji ba farin ciki har bakinta ya gaza rufuwa,sai da amani ta tabbatar cewa Amal ta kwanta sosae saman gadon sannan ta zauna daga gefen gadon tana kallonta har bacci yayi awon gaba da ita,amani bata bar wurin ba,kallonta take hawaye na zuba a idonta haƙiƙa su Mammy da Aunty babba ba ƙaramin cutarta su kayi ba, Jinjina kai tayi tare da cewa"rama cuta ga macuci ibada ne,Aunty laila kin shiga uku dani,zanbi duk hanyar da zanbi don ganin na tarwatsa plan ɗinki,dama ke jani talau ce sai yarda akai dake sannan kike bi,zanyi amfani da wannan damar wurin lalata shirinki" Haka Amani ta dinga tufka da warwara a ƙarshe ta shirya nata plan ɗin. **************** Hayaam na zaune saman gadonta hannunta ruƙe da wayarta tana jiran shigowar kiran Sofwan,harta fidda rai da zai kawo mata trolley ɗin sai ga message ɗinshi ya shigo wayarta,cikin sauri ta buɗe tana karantawa, _hi beb ya kike ya kwanan gidan surukai ina fata kina lfy,nafa zo gidan ki turo wani ya amsar maki trolley ɗin kayan,don bazasu bar ni nashigo ba_ Jin hakan yasa tayi saurin saukowa daga saman gadon tare da ɗaukar dogon hijabinta dake ajiye saman gadon,zurawa tayi ajikinta sannan tafito daga cikin bedroom ɗin,kama hanya tayi ta fito main palour ɗin tana wurga ido don tasamu wanda zai kar6ar mata kayanta,tana cikin wannan tunanin sai ga Fawan ya fito daga part ɗinsu, kwala mashi kira tayi cike da kisisina tace"Fawan"! ɗagowa yayi yana kallonta da wannan kallon nashi na rainin wayau, cikin sauri hayaam ta nufe shi sai da tazo kusa dashi sannan tace"dan Allah taimako nakeso kayimun,wani brother ɗina ne ya kawo mun trolley ɗin kayana,an hanashi shigowa ciki shine nace ko zaka taimaka ka amso mun," Yatsina fuska fawan yayi tare da cewa"Am sorry ni bazan iya wannan wahalar ba,zan dai kira ɗaya daga cikin security guards ɗin na basu umarnin su barshi ya shigo abokina ne inyaso sai kije ki kar6o kayanki," washe baki hayaam tashiga yi tana cewa"thank u so much fawan,kana da mutunci sosai naji daɗin taimakonnan da kayimun,' ɗan ta6e baki fawan yayi tare da kai hannu ya ciro wayarshi a aljihun rigarshi,call ya buga tare da kara wayar a kunnanshi,ɗaga kiran akayi sannan ya sanar dasu cewa subarshi ya shigo abokinshi ne,amsa mashi sukayi sannan ya kashe kiran, batare da ya kalleta ba yace"kije ki amso kayanki," da hanzari Hayaam ta juya tare da kama hanyar fucewa daga falon sai faman sauri take yi kamar zata tashi sama, Ruƙe ƙugu fawan yayi tare da cewa"Ikon Allah,nifa bangane ma Yarinyar can ba,Naji tana cewa zata amshi trolley ɗin kayanta me hakan ke nufi"?ya jefa ma kanshi tambaya,cizon la66ansa yayi tare da cewa"zaki gane kuranki ne,"yana faɗin hakan ya kama gabansa *💋Boss Bature💋* Wuraren ƙarfe 1:30 junaid ya ɗauko sehrish daga school,tun acikin mota ya lura da yanayinta duk a yamutse babu natsuwa a tattare da ita,har tambayarta yayi ko bata jin daɗine,sai ta sanar dashi cewa bacci ne kawai take ji,jin haka yasa ya ƙara gudun motar har suka ƙaraso cikin gidan, Fitowa tayi daga cikin motar tare da komawa ta buɗe back seat ɗin ta curo school bag ɗinta sannan ta wuce cikin gidan da sauri, Abun ya ɗaure ma junaid kai,ganin ta tafi batare da ta jirashi ba kamar yarda suka saba shiga cikin gidan hannunsu ruƙe dana juna, hannu yakai tare da buɗe motar ya fito bayan ya rufeta,ya kama hanyar shiga interior ɗin gidan,koda ya shiga main palour ɗin kai tsaye ya wuce upstairs bedroom ɗinshi don shima a gajiye yake, wani irin zazza6ine ya rufar mata,dama tun lokacin da suka haɗa ido da wannan malamin taji gaba ɗaya yanayinta ya sauya,tana shiga bedroom ɗinta tayi wurgi da school bag ɗin ƙasa,sannan ta faɗa saman gadonta tare da kwantawa tana faman juyi asaman shi, A wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita, Turo ƙopar bedroom ɗin nata junaid yayi anan ya same ta tana ta faman sharar bacci ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa zai fuce daga ɗakin karaf idonshi suka sauka akan Bottle water ɗin da malamin nan yaba Amrish takai mata,ashe lokacin da ta shigo ɗakin tayi wurgi da jakar nan take robar ruwan ta gangaro daga cikin jakar,saboda ta manta bata rufe zeep ɗin wurin data sanyata ba, Murmushi junaid yayi yace"Oh ni reeshi kamar wata ƙaramar yarinya,wai yawo da robar ruwa acikin school bag hmmm,"yayi maganar tare da ƙarasawa yakai hannu ya sungumi robar ruwan, Jin salaf babu sanyi ajikin robar ruwan yasa shi cewa"bari naje na sanya mata shi a fridge,zai fi daɗin sha," Yana ƙarasa maganar ya juya tare da fucewa daga ɗakin nata,kai tsaye ya wuce wurin fridge ɗinsu,hannu yakai tare da buɗewa ya sanya robar ruwan aciki,sannan ya mayar ya rufe ya kama hanya yabar wurin, After some minutes sai ga su twins sun faɗo cikin main palour ɗin dawowarsu kenan daga masallaci,raba hanya su kayi Jahan ya wuce bedroom ɗinsu,shi kuma Ayaan ya wuce wurin fridge saboda wani irin ƙishin ruwa da ta zo mashi,hannu yasa tare da buɗe fridge ɗin,ya ɗauko bottle water ɗin da Junaid ya ajiye, Buɗe murfin yayi tare da kafawa abakinshi ya shiga ɗaɗɗakar ruwan,sai da yayi rabin robar ruwan sannan ya mayar da ita cikin fridge ɗin ya ajiye, Shafa ƙirjinshi yayi tare da cewa"Alhamdulillalh yanzu naji wani sanyi ya ratsa maƙoshi na," Yana faɗin hakan ya nufi bedroom ɗinsu,lokacin daya shiga samun Jahan yayi kwance yana jiranshi ya ƙaraso, ɗaga kafar da zaiyi kenan yaji gaba ɗaya jikinshi ya shiga jijjiga ta ko'ina,ganin hakan yasa jahan tashi daga zaune yana cewa"lafiya Ayaan meke faruwa ne!! A wani irin galabaice Ayaan ya zube saman guiwowinshi yana ambaton sunan Allah abakinshi,kafin Jahan yayi wani yunƙurin durowa daga saman gadon tuni ayaan ya yanke jiki ya faɗi kasa abaje idonshi na kallon ceilling yayin da launin idanunshi suka 6ace 6aat sai farar kwayar idon, "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un," jahan ne ya ambaci hakan a lokacin da ya ƙarasa durowa daga saman gadon ya ƙaraso a hanzarce inda Ayaan yake, ya zube saman guiwowinsa agabanshi,hankali atashe yake ambaton sunan shi "Ayyaaan!!!Ayaan dan Allah ka tashi!meke faruwa dakai ne rabin raina!!.,....' ganin bai da wata mafita yasa ya miƙe da gudun gaske ya fuce daga ɗakin nasu don yaje ya sanar ma wani, Fitar Jahan ke da wuya,wani siririn hayaƙi baƙi wulik ya dinga fitowa daga ƙofofin hancinshi da kuma bakin shi,da yawan gaske hayaƙin ke kurɗaɗowa ya mamaye ko ina,kafin wani lokaci ya disashe tare da 6ace wa 😳😳😳 *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.     _💋Boss Bature💋_ قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Am really sorry 4 the late post👌 Wata irin zufa ce ta soma tsastsafo mashi a jikinshi kamar wanda aka tsamo daga cikin ruwa,lokaci guda yashiga Sakin atishawa yafi talatin a jere suke fitowa daga bakinshi,daga bisani kuma a hankali launin kwayar idonshi ya bayyana,komai nashi ya dawo yarda yake,ganin shi kwance a ƙasa yasa shi yin hanzarin miƙewa tsaye yana tunanin wai menene yakai shi ƙasa kwance?me ya faru dashi ne?hannu yasa yana shafo zufar dake a gefen fuskarshi har lokacin bata daina zuba ba,hakan yasa ya nufi toilet tare da shigewa ciki don yayi wanka, Bai jima da shiga ba sai ga Jahan ya faɗo ɗakin yana atare da kanal yousouf,tsayawa su kayi abakin ƙopar ɗakin,Jahan na mamakin Ina ayyan daya bari cikin wani hali yashe a ƙasa Kallon shi kanal yousouf yayi tare da cewa"Kace mun Ayaan ya faɗi ƙasa jikinshi na kerma,gashi kuma ni banga Ayaan ba,"   Fuskarshi aruɗe yace"Ya yousouf nikaina abun ya ɗaure mun kai,nan fa nabarshi kwance cikin wani yanayi yanzu kuma babu shi a wurin," jin hakan yasa hankalinsu tashi su duka biyun,   tsayawa su kayi kowa da abunda ranshi ke bashi,suna cikin tsayuwar nan sai ga Ayaan ya buɗe ƙopar toilet tare da fitowa jikinshi ɗaure da towel,ga danshin ruwan dake ajikinshi alamar wanka yayi,abun ba ƙaramin ɗaurewa jahan kai yayi ba hatta kanal yousof ɗin,shi kuwa hankalinshi kwance har zai gifta ya hangesu tsaye ta wutsiyar idonshi,hakan yasa ya ɗan ja da baya tare da juyawo yana kallon su,cike da mamaki yace"Ya yousouf!Jahan!meya faru naganku a tsaitsaye kunyi curko curko?ko lafiya,"?    ajiyar zuciya jahan ya sauke tare da tunkarar shi kai tsaye ya rungumo shi ajikinshi yana ɗan bubbuga bayanshi yace"babu komai ayaan,nashiga damuwa ne ɗazu dana ga ka yanke jiki ka faɗi nayi tunanin kowani mummunan abune zai faru dakai that's why nayi deciding kiran ya yousouf don yazo ya duba min kai," ya ƙarasa maganar tare da raba jikinshi daga na Ayaan,    "Nifa lafiyata lou,babu abunda ya faru dani,kawai jiri ne ya ɗan ɗebe ni but now Alhamdulillah har wani ƙarfi nake ji ajiki na,ko in gwada maka ka gani," yarda yayi maganar tare da ɗaga masu damtsen hannunshi ba ƙaramin dariya ya basu ba,girgiza kai kawai kanal yousouf yayi tare da juyawa ya fuce daga ɗakin,    wucewa Ayaan yayi ya nufi mirror,cikin sauri Jahan ya bishi tare da hugging ɗinshi ta baya ya kwantar da kanshi a saman kafaɗar Ayaan,    Shiru Ayaan yayi yana tunanin mai jahan ke ƙoƙarin yi mashi ne,menene dalilin rungumar da yayi mashi ne hada wani kwantar da kanshi a saman shoulder ɗinshi,bai ƙarasa zancen zucin nashi ba,yaji hannun Jahan agabanshi yana ƙoƙarin zame towel ɗin jikinshi,aikuwa a wani irin firgice ya ka6e mashi hannunshi tare da yin wurgi dashi gefe guda,sannan ya juyo fuskarshi a ɗaure yace"Jahan bana son iskanci!menene haka?bakasan me ka kama mun bane?so kake ka ciremun towel ɗin jikina ne!"   Murmushi Jahan ya saki tare da cewa"Ayaan banason irin wannan wasan pls,ka riga da kasan abinda nake buƙata a wurinka,"    Fuska ayamutse Ayaan ke kallonshi,ganin hakan yasa jahan tunanin cewa kodai bai jin daɗine duba da abunda ya faru dashi ɗazu,bai ƙara yi mashi magana akan abun ba saboda yasan cewa jarabar tashi zata motsa ne kuma zaizo ya sameshi ne,komawa yayi saman gadon tare da kishingiɗawa yana kallon Ayaan daga kwancen da yake, Ganin yarda jahan ke zuba mashi ido ko kawar dakai baiyi,hakan yasa shi tsuke fuska tare da barin gaban mirrorn ya shige can cikin ɗakin don ya sanya sutura,sa6anin da basa jin kunyar wannan bawani abu bane awurinsu in ɗaya ya tu6e kaya agaban ɗayansu. ❤🤍? Around 3:30,sehrish ta farka tana faman murza idanu,ba ƙaramin bacci tasha ba,sai hamma take saboda wata irin yunwa dake cinta,dama ko a school bata wani ci abun kirki ba,hannu tasa tare da yakice hijabin dake jikinta tayi wurgi da ita gefe guda,sannan ta zuro ƙafafunta tare da saukowa daga saman gadon,tsayawa tayi tana kallon school bag ɗinta da tayi wurgi da ita ƙasa bakomai ya faɗo mata a rai ba face Ruwan addu'ar da Malamin nan mai farin glass ya bata,ƙarasawa tayi tare da zuƙunnawa ta janyo bag ɗin,tana dudduba cikinta sam babu roban ruwan aciki,abun ya ɗaure mata kai,hannu tasa tare da zazzage kayan cikin jakar duka amman babu robar ruwan,   Tunanowa tayi da abunda Amrish ta faɗa mata"Ga ruwan addu'ar da malaman yace na baki,kuma yace indai bakiyi amfani dashi ba,ƙusumbi zai fito maki abayanki,"waro ido waje sehrish tayi tuna wannan maganar ta amrish nan take yatsun hannunta suka shiga kerma hatta la66anta,gaba ɗaya duk tabi ta rikice ba don komai ba sai don tsoran ƙusumbin da akace zai fito mata,mugun tsoran ƙumbin take yi saboda taji ana cewa aljanune ke ajiya a cikin ƙusumbin,ƙyamar abun take ji,    Hawaye ne suka soma wanke mata fuskarta murya na rawa tashiga furta"innalillahi wa'inna ilaihir rajiun, nashiga ukuna!wayyo Allah na,yanzu ya zanyi?nan fa na ajiye robar ruwan nan amma yanzu na duba babu ita.....yanzu shikenan ƙusumbi zai fito min ya suffata zata koma tare da ƙoƙo abayana............'fashewa tayi da matsanancin kuka,anan wurin ta tsugunna tana matse kwalla duk tabi ta rikita kanta,sai da tayi mai isarta sannan ta miƙe tana faman shasshekar kuka takai hannu tare da tattara books ɗinta tana mayar dasu cikin school bag din,bayan ta kammala ta ɗauke jakar taje ta ajiyeta,    Rage kayan jikinta tayi,ya rage daga ita sai white short da half vest,sannan ta shige cikin toilet cike da kasala,   Ta jima acikin toilet din kafin ta fito jikinta ɗaure da towel,har lokacin idanunta na cike tab da hawaye,zulluminta ƙusumbin da akace zai fito mata,saboda tasan in hakan ta faru hatta Junaid sai ya guje ta,shi da yafi kusa da ita,da wannan yanayin ta kammala shirya kanta cikin wando palazzo maroon colour tare da halter shirt black colour,just imagine it ba ƙaramin kyau rigar tayi mata ba,ta ɗame jikinta sam rigar bata da hannu amma ta rufe ƙirjinta har neck ɗinta ta zagaye shi,komawa tayi gaban mirror tana feshe jikinta da turaren nan nata mai ƙamshin gaske,kafin daga bisani ta ɗauko ribbom launin wandonta maroon colour,tattare gashin tashiga yi zata ɗaure shi amma ina duk yadda taso ta haɗe shi wuri guda ta ɗaure abun yaci tura,har wani huci takeyi saboda 6acin ran yaƙi ɗauruwa,tana cikin dambe da gashin,taji ana kwankwasa mata ƙopa,dakatawa tayi da ɗaure gashin tace"Wanene,"   "Auntynki ce,"muryar azmee ce ta bata amsa daga waje,    ƙarasowa Sehrish tayi tare dasa hannu ta buɗe mata kopan,sanye take cikin hijabi hannunta ruƙe da cazbaha fuskar nan ɗauke da murmushi tace"irin wannan kyau haka? . sunnar dakai sehrish tayi tare da cewa"Ina yini aunty azmee,"   "Lafiyalou,tun ɗazu naso nazo na dubaki amma bansamu hali ba,ya school ɗin"?   "Alhamdulillah Aunty azmee," "ina fata kina lafiya,naga kamar akwai damuwa a fuskarki"?   girgiza kai sehrish tayi tace"a'a lafiyata lou,dana dawo ne bana ɗan jin daɗin jikina shine na kwanta nayi bacci sosai banjima da tashi ba,shiyasa fuskata take a haka,"   Jinjina kai azmee tayi tare da cewa"okey,nagane ina fata kinyi sallah,   "A'a yanzu nake shirin yi," Azmee tace"okey ya kamata ki hanzarta yi time har zai wuce,"   Ta ƙarasa maganar tare da juya zata fita,tsayawa ta ɗanyi tare da jiyowa tana cewa"Oh namanta ban faɗa maki ba,ɗazu da safe da kika tafi school,hayaam ce taje kaima Sgr breakfast ɗinshi,'   Jikin sehrish ne yayi sanyi tunkan ta ƙarasa jin abunda takeson faɗa mata tasoma jin jealous a zuciyarta,   "Yanzu kenan itace zata cigaba da kula da part ɗinshi tana kai mashi abinci"?yarda sehrish tayi maganar taba azmee dariya,saboda a wani irin yanayi na tashin hankali tayi tambayar,    "Kin tari numfashi na baki bari na ƙarasa maganar ba ai,Hayaam takai mashi abinci amma baici ba yace ta mayar dashi saboda shi ba'a sharing a aikinsa,yafison mutum ɗaya daya fara yi mashi aiki yaci gaba da yi batare da an canza mashi wani ba,ko kuma mutum biyu na mashi aiki at thesame time bayaso,"    Wani irin ƙayataccen murmushi sehrish ta saki,farin ciki kamar anyi mata albishir da gidan Aljanna,tama rasa bakin magana sai faman zabga murmushi take,    Azmee taci gaba da cewa"yanzu haka tun safe ba'a gyara mashi bedroom ɗinshi ba,na dai kai mashi breakfast ɗinsa,amma ban gyara ba saboda ba aikina bane,aikinki ne don haka da zarar kin kammala salla ki hanzarta zuwa ki gyara mashi part ɗinshi before ya dawo,"    Dakyar Sehrish ta iya amsa mata da toh,kamar jira take azmee tabar ɗakin tana fita tashiga daka uban tsalle tana rawa don murna,    Sam ta manta da maganar roban ruwanta da take nema,    Sai da tayi salla sannan ta koma gaban dressing mirror ta shafa jan baki launin wandonta maroon colour ba ƙaramin kyau yayi mata ba,bayan ta gama ta kara feshe jikinta da turare sannan ta koma wurin wardrobe ɗinta tare da ɗauko mayafinta,ta yafa shi ajikinta,ta ɗauko takalmi baƙi ta zura a ƙafarta Open toe mai ɗan tsini,sai gashi ta fito ɗass da ita,    hannu tasa tare da buɗe door din ɗakin ta fito tare da kama hanyar fita daga corridor din,   Adaidai lokacin Hayamm ta fito daga masaukinta,itama ta ɗauki wankan lace mai ɗan karan kyau,riga da skirt ash colour,kayan sun matseta sosai,daga saman rigar kamar boobs ɗinta zasu fito waje gaba ɗaga,skirt ɗin kuwa wata tsaga gare shi tun daga guiwar ƙafarta tafara har wurin ƙafarta kana hangen fatar ƙafafunta,high heels ne a ƙafarta tana tafiya sautin na fita kwas kwas,ta cuge ɗaurin ɗan kwali abunta yarda kasan wadda zata gasar miss world    jin takun tafiya yasa sehrish jiyuwa bayanta,har sai da gabanta ya faɗi da tayi arba da hayaam saboda wankan data ɗauka tayi uban makeup kamar wata aljana,bakin nan yasha jan janbaki ta wani cuno shi irin na masifaffu, Tuni sehrish tasha jinin jikinta ganin irin wankan da Hayaam ta ɗauka,ba ƙaramin kyau tayi ba kuma zata ja hankali sosai, kawar da kai sehrish tayi tare da juyawa zata tafi,muryar hayaam ce ta katse ta dacewa"Wait inason magana dake ƴan mata," tsayawa sehrish tayi tana jiran jin me zata ce mata, Koda Hayaam ta ƙaraso,bin sehrish tayi da wani irin matsiyacin kallo tun daga ƙasa har sama sannan tace"nasan gabanki ya faɗi kuma kin tsorata da ganin irin kyau da kuma kyawun sura da Allah yayi mun," ɗaure fuska sehrish tayi batace komai, Hayamm taci gaba da cewa"so nake ki fahimci cewa ni ba sa'ar yinki bace!bansan wani irin shisshigi kike ma Sg rafayet ba da har kika samu matsayi a wurinshi,inaso na gargaɗeki ne, kuma naja kunnanki akan ki fita daga sabgarshi saboda yafi ƙarfinki nesa ba kusa ba,don na lura abunda kike hari kenan,in ma banda haɗama irin taki ina zaki kai mutum kamarsa?dan Allah jibarki fa ƴar ƙarama dake amma sai kankanbar tsiya,wai ma menene connection ɗinki da mutanen gidan nan ne? tayi tambayar tana kallon sehrish yayin da fuskarta ke ɗauke da shu'umin murmushin nan nata, jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba don tuni idanunta sun cicciko da kwalla,daƙyar ta iya shanyesu sannan ta dake tare da cewa"Bansan meyasa kike gayamun waɗannan maganganun ba,da alama dae baƙin cikin ɗazu ne da sgr ya ƙumsa maki shine kikeson ki huce akaina,sannan kuma yaushe nace maki inason shi ne da har kike cewa yafi ƙarfi na?bama wannan ba,Naji kina magana akan cewa menene alaƙata da mutanen gidan to bari na baki amsa," matsawa sehrish tayi dab da Hayaam sannan tace"Ni yar aikinsu ce,biya na suke ina masu aiki kuma suna jin dadin aikina shiyasa nasamu kar6uwa a wurinsu,kuma ina alfahari da hakan,wannan shine alaƙata dasu,ke kuma fa?ƙanwar matar yayansu ce fa?ina alaƙa take anan? Lokacin da sehrish takai ƙarshen maganarta,waro ido waje Hayaam tayi tana kallonta,bata ta6a tunanin cewa yarinyar zata iya mayar mata da martani ba ashe itama ba kanwar lasa bace,ranta ba ƙaramin 6aci yayi ba,tuni idonta sun canza launi saboda fusatar da tayi, Sehrish kuwa murmushi ta saki tare da juyawa ta kama hanyar tabar wurin, Wani irin tafarfasa zuciyarta keyi mata,tama rasa mai zatayi ma sehrish ta huce don tsabar takaicin maganar da ta yada mata, "Da ace ban mayar mata da martani ba,dani zan kwana da baƙin ciki," sehrish ce tayi maganar a lokacin da take ƙarasa shiga part ɗin sgr, Sai faman murmushi take saki abunta,wucewa tayi cikin bedroom ɗinshi,wannan daddaɗan ƙamshin turaren nasa ne yayi mata maraba da zuwa,duk da baya cikin ɗakin amma ƙamshinsa ya gauraye ko'ina, Lumshe idonta tayi tare da buɗesu a hankali suka sauka akan shimfiɗeɗen gadonshi,tunawa tayi da abunda ya faru jiya atsakaninsu nan take taji wani irin yanayi atattare da ita,nan take tashiga tariyo dukkan abunda ya faru jiya a tsakaninsu,musamman lokacin daya kwantar da kanshi asaman chest ɗinta sai taji shi tamkar babynta,hmmmmmm shiga ciki sehrish tayi batare da 6ata lokaci ba,tashiga gyara mashi bedroom ɗin nashi,tamkar sabo haka ta Canza mashi kamanni,bayan ta kammala da bedroom ɗin,ta cire mayafinta tare da ajiye shi daga gefen gadon sannan ta koma cikin toilet ɗinsa don ta gyara mashi, Bata jima da shiga ciki ba,sgr ya dawo cikin gidan,har yanzu wankan ɗazu ne ajikinshi,na warp shirt da black trouser,da alama a ɗan gajiye yake,kai tsaye ya nufi upstairs part ɗinshi,hankalin Hayaam ba ƙaramin tashi yayi ba lokacin data ga gifcinshi yana ƙarasa hawa upstairs ɗin,taso ta tarbe shi tayi mashi sannu da zuwa kota samu yasan ya idonshi acikin nata,amma bata samu damar yin hakan ba,saboda fargabarshi da take ji, A wani irin gajiye ya shiga bedroom ɗinshi yana faman lumshe blue eyes dinshi saboda baccin da yake ji,yana ƙarasawa ciki yasanya hannayenshi tare da ɗebe rigar jikin shi gaba ɗaya,ya azata asaman laundry basket dinshi,zame belt ɗin wandonshi yayi sannan ya zame shi daga jikinshi ya ajiye shi asaman rigar,ya rage daga shi sai shorts ajikinshi, Komawa yayi tare da hayewa saman royal bed dinshi ya kwanta don ya ɗan runtsa,sosai ya miƙe saman gadon yana faman sauke ajiyar zuciya har bacci yayi awon gaba dashi,almost 6 mins sai ga sehrish ta fito daga cikin toilet ɗinshi,tunkarar gadon tayi saboda ta ɗauki mayafinta sai da ta kusa dab da gadon sannan idonta suka hango mata Boss Man ɗin nata kwance yana bacci,wani irin bugu taji zuciyarta tayi mata har sai da taɗan ja da baya tana kallonshi,hannu tasa tare da ɗan murza idanunta donta tabbatarwa idonta abunda take gani wai ko gizau ne,amma zahiran taƙara shaida cewa sgr ne da kanshi ya dawo, Hankali kwance yake baccin shi,ya zagayo da left hand dinshi ta saman sumar kanshi,yayin da hannun damanshi ke asaman shafaffen cikinshi, Ji tayi bazata juri kallon surar jikinshi ahaka ba saboda gudun jefa kanta cikin matsala,don ba ƙaramin fisgarta yake yi ba,kamar irin magnet din nan, Har ta kama hanyar fita daga bedroom din nashi cikin sauri taji jelar gashinta na gogar hannunta,tsayawa tayi Cak tunawa da Mayafinta data ajiye asaman gadon nashi kafin tashiga gyara mashi toilet ɗinshi,a hanzarce ta juya tana kallon inda ta ajiye mayafin,waro ido waje tayi cike da fargaba ganin yarda sgr ya mamaye mayafin nata gaba ɗaya,ya kwanta asaman shi,tabɗijan can Tunani tashiga yi kodai ta tafi tabar mashi mayafin tunda ba iya ɗaga shi zatayi ba,wata zuciyar kuma tace,idan ya farka ya samu mayafin naki asaman gadonshi bakya tunanin cewa zai iya zargin wani abu akanki?dole ya tuhume ki akan miya kawo mayafinki saman shimfiɗarshi,haka in kika fita ba mayafin wani ya ganki kin fito daga part dinshi haka fa,kiyi tunani sehrish barin mayafin risky ne,haka zalika daukarshi ma zai iya zama risky, Runtse idanunta tayi tamkar ta fasa ihu saboda tsabar takaici,taji haushin cire mayafinta da tayi tun farko da bata jefa kanta cikin matsala ba, Nan fa tashiga tunanin yarda za'ae ta dauke mayafinta batare da Sgr ya farka daga baccin shi ba, cikin sanɗa sehrish ta soma tafiya a hankali tana tunkararshi a tsorace batare da sautin takon tafiyarta na fita ba, Sai da tazo dai dai kusa dashi sannan tashiga cizon yatsa tana tunanin wai ma taya zata janyo mayafin daga jikinshi,Sehrish da kasada, Hannu tasa tare da ɗan kamo mayafin daya leƙo daga bayanshi tana janshi a hankali don ya sulalo daga bayanshi,amma ko motsi wannan baiyi ba don ba ƙaramar danna sgr yayi mashi ba,gaba ɗaya nauyin jikinshi na akan mayafin taya zata iya janye shi!? tun tana jan mayafin a hankali yana turjewa har takai ga hasala tashiga janshi da ɗan ƙarfi har sai da sehrish tashiga fitar da wani irin gumi a fuskarta,sakin mayafin tayi tana faman huci,duk da haka bata daddaraba,sai tasa hannu tare da dafa mattress ɗin ta haye saman gadon kaɗan daga gefenshi,hannu takai zata ruƙo mayafin karaf idonta suka sauka akan farar fatar ƙirjinshi,mayar da idonta tayi akan damtsen hannunshi,haryanzu akwai sauran zanen nan nashi na tattoo bai ƙarasa gogewa ba gaba ɗaya,tun farkon zuwanshi 9ja tare da zanen ajikinshi ya dawo kamar tambari ne na mukaminshi ba ƙaramin kyau yayi mashi ba, Gaba daya sehrish ta shagala da kallon surar jikinshi,kafin tayi wani aune,Sgr yayi wani irin kwakkwaran juyi zai gyara kwanciyarshi,aikuwa gaba ɗaya ya haɗa da sehrish yayi juyin tare da sanya hannunshi yayi hugging ɗinta tighly a faffaɗan kirjinshi,duk a tunaninshi pillow ne ya rungumo hakanne yasa ya matseta sosai a ƙirjinshi kamar yarda ya saba rungume pillow in zaiyi bacci wani sa'in,tashin hankali da ba'a sama shi date, Tabɗijancan,ƙiris ya rage sehrish ta saki fitsari saboda tsabar tsoran da taji,hankalinta yayi matuƙar tashi,saboda tasan mai zai biyo ba in sgr ya farka yaganta manne ajikinshi,yasan na jiya taimakon shi tayi gudun karya faɗi,na yau kuma mai zai kira shi!?meya kawota saman gadonshi da har ta faɗa jikinshi!? yarda ya matseta a ƙirjinshi ko kwakkwaran motsi sehrish ba ta iya yi,ba ƙaramin ruƙo yayi mata ba,tunkan ya farka taga irin hukuncin da zai yi mata harta fara zubar da hawaye,kai tsaye kuma hawayen suke shafar fatar jikinshi, sai faman shessheƙar kuka takeyi ƙasa ƙasa yayin da la66anta ke gogar fatar breast dinshi,gaba ɗaya Wannan jan bakin data shafa ya koma a fatarshi,sosai zanen lips ɗin sehrish ya fito raɗau tare da kalar jan bakinta maroon colour,duk bata lura da hakan ba,saboda la66an nata amanne suke a wurin, Tana cikin wannan yanayin tajiyo takun tafiyar mutum a falonsa alamar ana tunkaro bedroom ɗinshi,hakan ba ƙaramin firgita sehrish yayi ba,nan take tashiga haɗiyar yawu a tsananin tsorace, Muryar Abbansu tajiyo yana cewa"Wai har yanzu rafayet bai dawo bane?inaso naji ko sunyi waya da Mommynshi ne game da zuwanta Nigeria,' "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,"sehrish ce ta ambaci hakan acikin zuciyarta,"Shikenan na mutu wayyo Allah na,ya Allah ka kawomun ɗauki,daga wannan sai wannan......'bata ƙarasa zancen zucin nata ba tajiyo muryar Marshal Omar yana bashi amsa da cewa"Abba ashe muna da manyan baƙi cikin watan nan,don munyi waya da goggon katsina ma ta sanar dani cewa mu shirya ma zuwanta don in ta tashi zuwan bazata zata yi kuma ba zata tafi ba har sai taga An shafa fatihar kowannan mu.....' ya ƙarasa maganar da dariya a fuskarshi, Suna tafiya suna nufar bedroom ɗin sgr yayin da suke fira a tsakaninsu, Abban nasu yace"Albishirinka," Cike da zumuɗi Omar yace"Goro," "Fari ko ja"? Abban nasu ya tambaya fuskarshi ɗauke da murmushi, Omar yace"Fari," ƙayataccen murmushi Abban nasu ya saki kafin yace"Uncle ɗinku Abusufyan shima yana nan tafe insha Allah,sannan Auntynku azeema tana nan tafe,uwa uba kuma Ammynku itama tana nan tafe,don haka ku shirya don ta sanar dani cewa muddin tazo sai an ɗaura auran kowannanku,da alama zata zo tayi yaƙi da tazuranci ne acikin gidan nan.....'ƙarasa maganar yayi muryarshi ɗauke da dariya,shima Omar dariyar yayi yana girgiza kai yace"Abba Allah yaso ni,ina da wadda nakeso,don haka ni bani da matsalar komai wlh,Alhamdulillah Allah ya kawota Lafiya musha biki,' Cike da mamaki Abban nasu yace"wai dagaske Omar kana da wadda kakeso?hakan na nufin kayi budurwa baka sanar dani ba"? ɗaga kai Omar yayi alamar eh,wani irin farin cikine ya cika abban nasu har ya gaza magana sai faman sakin murmushi yake yi yana cewa"Ikon Allah," A ƙopar shiga bedroom ɗin sgr suka tsaya suna cigaba da tattaunawa cike da nishaɗi atsakaninsu, Saboda tsabar tashin hankali har wani zazza6i ya lullu6e sehrish tuni temperature ɗin jikinta yayi wani irin zafi,zuciyarta har wani bugu takeyi daram!daram!!fargabarta karsu shigo su same su a wannan yanayin ita da sgr, Hayaniyar da suke yi ce,ta fara disturbing ɗin baccin nashi,hakan yasa ya fara motsi alamar zai farka,waro ido waje sehrish tayi cike da fargaba jin alamar zai farka, Hannunshi ya janye daga ruƙon da yayi ma sehrish,hakan ne ya bata damar kufcewa daga jikinshi,kamar walƙiya haka ta mirgina tare da faɗawa ƙasan gadon,sam bata ji zafin buguwar da tayi ba,tana faɗowar nan ta yunkura tare da miƙewa tayi wuff ta faɗa bayan labulan ɗakin shi, Shigarta ke da wuya,Abba da marshal suka shigo cikin ɗakin nashi atare bakunansu ɗauke da sallama, A hankali sgr ya soma buɗe idanunshi dake cike da bacci ga wata irin kasala data mamaye shi don baccin bai ishe saba,daƙyar ya iya sa hannunshi tare da dafa mattress ɗin ya tashi daga zaune tare da jingina back ɗinsa asaman pillow yana kallon Abban nasu tare da Omar sai faman lumshe ido yake yi, Zama Abban yayi daga gefen gadon nashi yana kallon fuskar kyakkywan yaron nashi yace"Rafayet bacci kuma a irin wannan lokacin?ko baka ga time bane? Sai lokacin sgr yakai idonshi akan diamond clock ɗin dake manne a bangon ɗakinshi ƙarfe 6:30 na yamma, lumshe idonshi yayi kafin ya waresu akan Abban nasu yace"Abba bansan time ɗin da baccin ya ɗauke ni ba" jinjina kai abban nasu yayi kafin yayi yunƙurin cewa wani abu karaf idonshi suka sauka akan jan bakin sehrish dake zane asaman breast ɗinshi, waro ido waje abban nasu yayi tare da cewa"Kai me nake gani haka kodai idona ne"?yarda yayi maganar a ruɗe yasa marshal Omar ɗan matsowa daga tsayen da yake ya russina yana ƙare ma Ƙirjinshi kallo,cike da mamaki Omar yace"ba shakka Abba,ba idonka bane wannan alamar sumbata ce,ga zanen la66an mace nan raɗau asaman fatar kirjinshi, Gaba daya sun gama confusing ɗin Sgr,sam bai gane inda zancen nasu ya dosa ba," Hankali atashe Abbansu yace"Rafayet tell me the truth!wa kayi feeding haka har ta goga maka jan baki asaman breast dinka!!!" Saboda tsabar kiɗima tuni jikin sehrish ya soma tsastsafo da wata irin zufa,duk da sanyin ac dake gauraye da ko'ina, Ganin yarda sgr ya dabarbarce kamar bai gane kan me suke magana ba,hakan yasa omar ƙarasawa gaban dressing mirror ɗinshi,yasa hannu tare da ɗauko ƙaramin madubin dake ajiye asaman shi, Ƙarasowa yayi wurinshi tare da saita mashi madubin yarda zai gani da kyau, Ware manyan idanunshi yayi yana kallon zanen la66an dake asaman chest ɗinshi cike da tsananin mamakin a ina ya same shi....... *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.*💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Ansamu long page🥱 ________________________Zuba mashi ido su kayi suna jiran amsa,Omar yace"pls ka faɗa mana gaskiya kawai,wacece wani abu ya shiga tsakaninka da ita har akasha wannan Love haka?kaga dai daga ni sai Abba babu wanda zaiji abun da ya faru,"wani irin kallo sgr ya wurga yana mashi ƴar harara yace"Omar bana so, ka fara ko"?   Murmushi Abban nasu yayi kafin yace"abunda Omar ya faɗa gaskiya ne,Son bai kamata ka 6oye mana komai ba tunda Allah dai yasa yau asirikinka ya tonu munga komai,ashe kana kula mata har romance kake dasu asaman gado ko?faɗamun ƴarwa ka kwamushe acikin ɗakinka har akai abun arziƙin nan bansani ba,"cike da zolaya Abban nasu ke magana,   ɗaure fuska Sgr yayi tare da haɗe girarsa wuri guda ya tsuke small lips ɗinshi yana kallonsu,yarda suka tasa shi gaba suna tuhumarshi kamar wani ƙaramin yaro ba ƙaramin hasala shi yayi ba,gashi sam ya rasa amsar da zai basu tunda bai isa ya ƙaryata abunda suka gani ba asaman ƙirjinshi,don shi kanshi a ruɗe yake da lamarin abun ya ɗaure mashi kai,taya aka samu jan bakin mace raɗau haka asaman ƙirjinshi!?bai gama zancen zucin nashi ba muryar Omar ta katse mashi tunani,   "Abba zargi fa ya tabbata,kalli ka gani,"Omar ne yayi maganar yayin da yake ruƙo mayafin sehrish dake a ƙasan laps ɗin Sgr ya danne shi,    dafe kirji abban nasu yayi cike da razana yace"ƙalu innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Rafayet!wannan fa?ya akai yazo wurinka"?ya tambaya hankali tashe yana kallonshi, Runtse ido sehrish tayi daga 6oyen da take bayan labulen ɗakin,hada ƴan matan hawayenta saboda tsoran hukuncin da zata kar6a,   Cikin sauri sgr ya aza eyes ɗinshi akan mayafin da Omar ya ruƙo a hannunshi just speechless,amace bakin shi ya mutu yama rasa bakin magana abun ya zarce tunaninshi,   Omar ne yace"Abba tunda kaga yayi tsit ya gaza magana,to ya aikata ɗinne kasan mara gaskiya,ni fatan da nakeyi ma Allah yasa iya mayafi ya cire mata bai........'kasa ƙarasa maganar yayi saboda saukar pillow daya ji a saman fuskarshi,hannu yakai zai ƙara rarumar wani pillow abban nasu ya dakatar dashi da cewa"Wannan fa alamar rashin gaskiya ce,tun ɗazu kaƙi buɗe baki ka ce uffan,sai faman ƴan kame kame kakeyi mana,kaji tsoran Allah ka faɗa mana gaskiya,Rafayet yin hakan kuskure ne bai kamata don kana ra'ayin mace ka runƙa kawota har bedroom ɗinka ba asaman gadonka don ka rage zafi da ita ba,in kaga yarinya kanaso Ni zakayi ma magana sai aje masallaci ashafa fatiha kaga shikenan sai a kawo maka ita ɗakinka babu mai jin kanku,taka ce halak malak.....'   Zare blue eyes ɗinshi yayi yana kallon Abban nashi,rai a6ace ya ciji la66ansa tare da ɗago pillown hannunshi ya ɗaga sama zai jefa ma Abban nasu a saman fuskarshi,sai kuma ya saki filon a saman katifar,    Ganin ya dakata yasa Abban nasu cewa"ae fa kai yanzu komai ma zaka iya,saurayin da zai iya kawo mace ɗakinshi har saman gadonshi acikin gidan ubansa meke bazai iya ba Omar? Ya ƙarasa maganar yana kallon Omar dake ƙumshe da dariya yace"of course Abba,ina goyon bayan maganar ka,yanzu sai dai mu bishi da addu'a don na lura yarinyar ba ƙaramin zautar dashi tayi ba tunda gashi har ya gaza buɗe bakinshi yayi mana magana,rashin gaskiya dai baiyi ba,"   gaba ɗaya sun gama hasala Sgr,yama rasa amsar da zai basu su dukansu,a ƙarshe ma daya rasa abunyi kawai sai ya fashe da dariya unexpected,tsananin mamaki ne ya kamasu ganin Sgr yana 6a66aka dariya yau shi da kanshi,yaushe rabon da suga sgr yayi dariya irin haka,white teeth ɗinsa sun fito rairasss,da wuya kaga yana dariya sai dai wannan murmushin nashi na gefen fuska shima kuma in kaga yayi wannan murmushin tofa zai bada horo ne,don ya iya murmushin mugunta,    Hannu sehrish tasa a hankali ta ɗan yaye labulen tana leƙensu,ba ƙaramin bugun zuciya taji ba,kasa janye idonta tayi daga kallon kyakkyawar fuskar sgr da yake ta faman dariya kamar zautacce,gaba ɗaya dimples ɗin fuskarshi sun lotsa sosai abun ba'a magana sai wanda ya gani,suman tsaye sehrish tayi amace ta mace wurin kallon fuskarshi,aranta tana maimaita kalmar nan"tabarakallahu ahsanun khaliqin,"    Har wani duƙar da kanshi yake yi ƙasa yana dariyar hakan yasa sumar kanshi ta ɗan yarfo ta gaban fuskarshi,   Atare Omar da Abbansu suka haɗa baki wurin cewa"ikon Allah,abun mamaki abun al'ajabi,"    Tsagaitawa yayi da dariyar lokaci guda ya ɗaure fuskarshi tamkar dariya bata ta6a wanzuwa a fuskarshi ba,takaici ne dama ya ishe shi shiyasa ya fashe da dariyar,   Cikin sanyin murya yace"joking aside pls,abba nikaina bansan ya akai nasamu zanen lips ɗin nan asaman chest ɗina ba,sannan bansan ya akai mayafin nan yazo bedroom ɗina ba,na rasa ta yarda zansa kuyi understanding ɗina,gaba ɗaya kunyi confusing ɗina,kun tsareni da tambaya kamar wasu lauyoyi,that's why nayi shiru bance komai ba,"ya ƙarasa maganar a kasalance,    Murmushi Abban su ya saki yana kallon face ɗinshi,bakomai ya faɗo mashi araiba face Mommynsu,komai na fuskarshi irin na mahaifiyarshi ne,yafi kama da ita amma akwai wasu abubuwan daya ɗauko na Abbansu,    "Zan shiga toilet,"ya faɗi tare da saukowa daga saman gadon ya kama hanyar shiga toilet ɗin,    Bin bayanshi su kayi da kallo har ya shige cikin toilet ɗin, Sannan Suka janye idanunsu,cikin sauri Omar ya samu wuri tare da zaunawa yana fuskantar abbansu ya ruƙo hannunshi tare da cewa"Abba,dan Allah ka aurar damu tare, nida Rafayet,kayi mun wannan alfarmar"   Murmushi Abbansu ya ɗanyi kafin yace"Omar bangane me kake nufi ba,har yanzu ɗan uwanka bai janye ra'ayin shi akan mace ba,ni kuma banson na takura mashi,duk da banda burin daya wuce wannan nima,inaso naga auran kowanne daga cikinku,musamman auran shi saboda ina tunanin cewa in soyayya ta shiga zuciyarshi zai rage wannan zafin kan nashi,zai sassauto ya zama tamkar kowa,idan har rafayet baiyi aure ba ya tsaya akan bakanshi,tabbas za'ayi asarar namiji har namiji Omar,bansan ya zanyi dashi ba,"yanayin da abban nasu yayi maganar zai tabbatar maka da cewa abun ba ƙaramin ciwo yake masa ba,   "Abba kadaina cewa bakasan yarda zaka yi dashi ba,shifa ɗanka ne halak malak Allah ya mallaka maka,kuma kana da iko Akanshi,idan yau kaso Abba gaba ɗayanmu zaka iya yi mana aure batare da son ranmu ba ko batare da saninmu ba kuma dole muyi maka biyayya,"    zuba mashi ido Abban yayi yana sauraran bayanin shi, Ƙasa ƙasa da murya Omar yayi gudun kada Sgr yafito daga cikin toilet ɗin yaji abunda suke tattaunawa,   Yasa shi yin hakan sannan yaci gaba da cewa"Abba,namiji irin rafayet,aure akeyi masu batare da saninsu ba,sai dai kawai suji an ɗaura auran...  "   Katse shi abban nasu yayi da cewa"baka tunanin cewa zai iya sakin matar anan take,kasan shifa ba'ayi mashi dole,"?     Murmushi Omar yayi tare da cewa"Abba ka fahimta mana,kaifa kake iko dashi,ka sama mashi mace ta gari wadda kasan cewa bazaiyi dana sanin zama da ita ba,ko kuma ni kaban za6i zan sama mashi macen data dace da rayuwarshi,ka aura mashi ita batare da sanin shi ba,sai bayan an ɗaura auran ka ware rana ɗaya ka sanar dashi cewa Umarnine ka bashi amatsayinka na mahaifinshi,in ya kuskure kuma yasan sauran,"   dariya sosai Abbansu yayi yana sauraron omar dakyar ya tsagaita da dariyar yace"Omar ka iya zolaya Allah kamar mahaifiyarku,yanzu rafayet kakeso nayima auren dole?so kake ya tashi bomb acikin gidan nan"?   "Abba baka fahimce ni ba,tunda muka taso tare da ɗan uwana,komai namu iri ɗaya muke yinshi tamkar twins haka muke,duk abunda nayi rafayet sai yayi shi,haka shima duk abunda yayi nima saina yi shi,yanzu abba aure ne zai banbanta ni da ɗan uwana"?   In serious matter Omar ke magana,wannan yasa Abban nasu ya gane cewa ba zolaya bace yake mashi,har cikin ranshi yake maganar kuma ba ƙaramin jin abun yake ba acikin zuciyarshi,bai gama zancen zucin nashi ba omar yaci gaba da cewa"Abba tuntuni ban ta6a sanar dakai ba,amma yau zan sanar dakai komai,najima inason na cika maka burinka na ganin cewa munyi aure, ba don komai ba sai don saboda farin cikinka,bakomai ne yasa nayi jinkirin yin aure ba face Rafayet!inason aure bawai banaso ba,rafayet shine dalilin dayasa naƙi yin aure,saboda ina ganin cewa kamar banyi mashi adalci ba,inna riga shi yin aure,saboda mun saba komai atare duk wani cigaban da zamu samu atare muke samun shi abba,taya zanso na samu wannan babban cigaban batare da ɗan uwana ba"? Ya ƙarasa maganar muryarshi asanyaye yana kallon Abban nasu, Gaba ɗaya Omar ya gama kashe ma Abban nasu jiki,ba ƙaramin tausaya mashi yayi ba,lalle ba ƙaramar shaƙuwa bace a tsakanin shi da ɗan uwanshi ba,tun da har zai iya hana kanshi wani jin daɗi na rayuwarshi saboda ganin cewa tamkar baiyi mashi adalci bane,    "Abba,na jima ina jiran ganin cewa ɗan uwana ya fara soyayya koya fara maganar aure,amma har yanzu ba wani sauyi abun ba ƙaramin ta6amin zuciyata yake ba,bana faɗi ne kawai saboda nasan faɗin bashi da amfani zan 6ata bakina ne kawae,sau da yawa ina janshi da fira akan mace don na bugi cikinshi naji koya fara ra'ayin yin aure amma kullum babu wani cigaba game da haka,Abba rafayet shine yasa Omar ɗinka ƙin yin soyayya tun da jimawa kuma shine ya hana nayi aure,wanda bani da burin daya wuce wannan arayuwata....,.......'   Kasa ƙarasa maganar yayi saboda siririn hawayen daya zubo mashi a idonshi na hannun dama,   Cikin sauri abban nasu ya sanya hannunshi tare da yin saurin goge masu shi yace"Omar ban ta6a tunanin haka ba,meyasa tuntuni baka sanar dani wannan maganar ba?meyasa nagaza fahimtarku amatsayina na mahaifinku?ashe shaƙuwar dake tsakaninku har takai haka?nagode ma Allah sosai da kuka kasance masu son junanku,ina matuƙar alfahari daku ƴa'ƴana," magana yakeyi yayin da idanunshi suke cike tab da kwalla,   Sehrish kuwa dake la6e bayan labule sai faman shessheƙar kuka takeyi ta rufe bakinta da tafukan dukkan hannuwanta,tsananin tausayinsu ne ya kamata,tunda take a rayuwarta bata ta6a ganin ƴan uwa masu matuƙar ƙaunar junansu ba irin ahalin salahuddeen hussein,akwai soyayya da shaƙuwa tsakaninsu,zumuncin dake tsakaninsu mai ƙarfi ne sosai,da ace kowane ahali zasu kasance haka da ba ƙaramin cigaba za'asamu ba,amma yanzu zamanin da muke ciki,babu wannan soyayyar atsakanin shaƙiƙai ma,sai kaga na waje ma wani can yafika kusanci da ɗan uwanka shaƙiƙinka,idan kuwa akazo kan shiga matsala ko damuwa tofa zaka ga mutum indai bashi ta shafa ba,babu ruwanshi da damuwa akan halin da ɗan uwanshi yake ciki,sai ma ya kasance ɗan uwanka yana cikin ƙunci da matsanancin damuwa,amma kai kuma hankalinka kwance sai ma ajika kana ta faman tiƙar dariya,mai makon arunƙa jajantawa juna,shiyasa dayawa zaka ga na waje ma wani yafika kusanci dashi saboda yafi damuwa da ɗan uwan naka,wanda dayawa hakan ke jefa rayuwar ɗan uwan cikin hatsari,ba'a janshi ajiki cikin gida tun daga iyayen har ƴan uwan,bakamar salahuddeen hussein ba, ya ɗauki ƴa'ƴanshi tamkar abokanan shi,ƙaramin ɗanshi ma tamkar amininshi ya mayar dashi,kuma hakan yasa basa jin shakkar sanar da mahaifinsu abu in ya same su,ko neman shawara awurinshi,wanda a yanzu zaka ga cewa wani a gidansu tsoro ma yake ji ya sanar cewa wani na cutar dashi awaje,saboda wasu iyaye basa tsayawa su fahimci ƴa'ƴansu daga sun ji abu sai afara hantarar mutum in ƙarami ne kaga an haɗa mashi da bugu ma,babu wannan shaƙuwar ta iyaye,da ƴan uwantaka da har mutum zai iya faɗin damuwarshi acikin gidansu,sai dae ya nemi abokinshi ya sanar dashi halin da yake ciki instead of wani nashi nakusa dashi,daga nan kuma awajen in Allah yasa abokin ba nagari bane shine zaka ga anzo ana danasani, don mafi akasarin mutane na fadawa mugun hali ne ta sanadiyyar abokai,ku yi koyi da wannan ahalin wurin nuna ma junanku soyayya,ku zama naku ku kaɗai babu mai jin kanku👌👍 Sehrish bata bar bedroom ɗin sgr ba,har sai da aka kira sallar magrib suka fita tare da abbansu domin zuwa yin sallar magrib sannan ta samu cikin sauri ta ɗage curtains ɗin,da hanzarin gaske ta sungumi mayafinta sannan da sauri hadda gudu ta haɗa wurin barin part ɗinsa, Saukowa downstairs tayi a lokacin duk sun tafi salla masallaci,kai tsaye kitchen ta nufa tunkan ta ƙarasa ta hangi Azmee da hayaam suna ta haramar kammala dinner ɗin ranar,duk sai taji babu daɗi taso ace tare da ita suka fara,jiki asanyaye ta shiga kitchen ɗin da sallama a bakinta, Juyowa sukayi suna kallonta atare,da alama ma sun kammala aikin nasu,Azmee ce ke haɗawa Hayaam warmers acikin tray tana kaiwa dining, "Kin kammala gyara mashi part ɗin nasa ne?azmee ce ta jefa mata tambaya, "Eh,nagama," "Ya akai kika daɗe acan ne"? Sunnar da kai tayi tana wasa da yatsun hannunta saboda ta rasa amsar da zata bata, Hayaam kuwa sai faman wurga mata harara take yi kamar kwayar idonta zata faɗo ƙasa, Murmushi azmee tayi tare da cewa"ki wuce kije kiyi sallah,kada ki samu damuwa,nasan cewa wani abunne ya tsayar dake," Ajiyar zuciya sehrish ta sauke kafin ta juya tasa kai tabar cikin kitchen ɗin,bedroom ɗinta ta nufa domin tayi sallah, A 6angaren su hossana kuwa,tun bayan da suka dawo daga school suke ta faman saran zuwan Omar amma baizo ba,burin jahad ta sanar dashi cewa taga ƙaninshi a school ɗinsu,gaba ɗaya yinin ranar sunyi shi ne cike da kewar Ya omar ɗinsu musamman hossana ko lunch bata ci ba tunda suka dawo gashi ko'a school ma bataci komai ba,saboda tayi alƙawarin cewa tare da ya omar zasu ci abinci zai bata abaki,hakan yasa taƙi cin komai,duk yarda jahad taso ta fahimtar da hossana akan ta zauna taci abinci sam taƙi,har dai tagaji ta ƙyaleta, sai faman zagaye takeyi acikin bedroom ɗinsu,fuskar nan ɗauke da murmushi ae tunda tayi arba da Romeo sam tagaza samun natsuwa wani irin tsantsar son shi da ƙaunarshi takeji kamar kamar me,fiye da yarda take jin ya omar ma lokacin da taso shi,saboda shi son da tayi mashi hada ƙarin don ta kyautata mashi ne akan irin ɗawainiyar da yake yi dasu,shi kuma kalar son da take yi ma junaid kallo ɗaya tayi ma kyakkyawar fuskarshi tabi ta rikice,kuma tunda Omar ya furta cewa ƙaninshi ne nan take taji ya kwanta mata aranta,sai dai abunda jahad bata sani ba shine,junaid ba babba bane kamar yarda take tunani, **********haroon Gaba ɗaya ya rikita ɗakin nashi wurin neman kuɗin da su Twins suka bashi,sam hankalin shi ya gaza kwanciya yama rasa inda zaisa kanshi,wata irin zufa ce ke gangaro mashi a fuskarshi saboda tsabar 6acin rai,yafi ƙarfin awa 2 yana neman jakar kuɗin amma babu ita ƙasa ko sama,an ɗauke ta daga ɗakinshi babu ita babu alamarta,yayi ma bedroom ɗin nashi kaca kaca wurin binciken inda jakar kuɗin take,kamar zaiyi hauka saboda yarda ya zauce,sun rigada sun gama tsara plan ɗinsu, shirin tafiya kawai ya rage mashi daga zuwa ya ɗauki jakar kuɗin an ɗauketa daga ɗakinshi,gashi ya rasa wanda ya shigo har cikin bedroom ɗinshi ya ɗaukar mashi ita,komawa yayi gefen gadonshi ya zauna yana faman huci kamar wani zaki,tunani ya shiga yi wanene zai iya shigowa ɗakinshi ya ɗaukar mashi jakar kuɗin shi?kodai su twins ne suka yi mashi wayau,don sunsan cewa ya goge videon shine suka ɗauke jakar kuɗin,tabbas kuwa sune saboda su kaɗai ne suka san da kuɗin acikin bedroom ɗinshi, Jinjina kanshi yayi yana huci yace"yara kenan harni zakuyiwa wayau,ƙananun ƴan iska kawai masu kwana da wando,saboda sun mayar dani shashasha shine suka zagayo ta bayan idona suka ɗauki jakar kuɗin,wlh sai kunyi danasani saina illata rayuwarku gaba ɗaya muddin baku maido mun da kuɗina ba,"ya faɗi a lokacin da ya miƙe tsaye zumbur yana faman naushin tafin hannunshi na dama da hannunshi na hagu,tashin hankali da ba'a sama shi date, **********************Amani Zaune take saman 3 seater,yayin da Amal ke zaune kusa da ita,ta fito fess abunta tayi wanka ta bata kaya ta canza duk da rigar tayi mata yawa saboda kayanta ne taba ma amal ɗin ta sanya kafin zuwa gobe zata je da ita shopping mall ta zabi abunda take so,ta kuma yi mata siyayyar kayan sawa da sauran abubuwa na rayuwa wanda zata buƙata, Hannunta na ruƙe da wayarta,shiga contact ɗinta tayi tare da nemo numbar Aunty babba ta buga mata call,nan take wayar tashiga ringing, Hafsat na faman zarya acikin parlourn nasu taji shigowar kira a wayar mommynta dake ajiye saman hannun kujera,cikin sauri takai hannu tare da ɗaukar wayar,ganin sunan Amani ya bayyana ne yasa ta juya tare da tunkarar kitchen ɗin,tunkan taƙarasa aunty babba tafito daga kitchen din jin ringing ɗin wayarta,miƙa mata wayarta tayi tare da cewa"Amani ce ke kira," Yatsina fuska tayi tare dasa hannu ta kar6i wayar bayan tayi picking ta kara wayar a kunnanta tana cewa"Sai yau kika tuna dani"?_ on the other hand Amani tace"Am really sorry auntyna takaina,kullum kina araina,kawai abubuwane sunyi mun yawa," tsoki aunty babba taja tare da cewa"Abubuwa su kayi maki yawa,ciki gare ki ko goyo"?_ Amani tace"ko ɗaya daga cikinsu babu,pls mubar zancen ae nabaki haƙuri,yanzu akwai maganar da nakeso nayi maki pls," Aunty babba tace"kunne ke ji," "dama maganar Amal ne!wai har yanzu ba labarinta?ba'asan inda take ba?nagaza samun kwanciyar hankaline saboda mafarkin da nayi jiya agame da ita," Shu'umin murmushi Aunty babba tasaki tare da cewa"Yawwa dama inaso nayi maki magana game da Zancen neman Amal,munyi waya da mammy ta sanar dani cewa an samu wasu malaman da zasuyi mata sauka,manyan malamai ne na addini kuma da zarar sunyi saukar nan ake cin sa'a buƙata ta biya," Ƙiriss ya rage Amani ta saki dariya,don tsabar takaici da ban haushi,aranta tace wai sai yaushe matar nan,zata daina ƙarya ne? Juyawa tayi ta ɗan kalli Amal dake zaune hankalinta kwance idonta na kallon plasma tv ɗin dake facing dinsu,tana kallon tashar mbc 3, gyara murya Amani tayi tare da cewa"Masha Allah,gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba auntyna takaina,ashe ansamu wasu malaman ae ni indai akan Amal ne ko nawa ne zan iya badawa,ko bani dasu zan nemo ne,'_ Jin haka yasa aunty babba,janye wayar daga kunnanta tana faman 6a66aka dariyar mugunta,duk hafsat na tsaye tana kallonta baki asake saboda tasan da zancen neman Amal ɗin,kuma a gabanta Jiya abra ta kira mommyn nata tana sanar da ita cewa Amal ta gudu,sarai tasan cewa yarinyar ta gudu shine kuma takeson ƙara cutar da Amani saboda tsabar son abun duniya? "Yanzu nawa zan tura kenan"?acewar Amani, Aunty babba tace"ba wasu kuɗine masu yawa ba,dubu ɗari takwas ne,ae ni nayi mamakin ma yarda suka faɗi kuɗin da sauƙi har haka," murmushin takaici amani ta saki kafin tace"okey,zanyi maki magana indae na samu kuɗin,yanzu dae mu koma zancen Hayaam,shin har yanzu tana maid ne ko tazo Abujan nan"? "Tun jiya fa ta ƙaraso,yanzu ae ta jima da zama ƴar gida,"ta ƙarasa maganar tana washe baki,anzo inda tafi auki, ɗan ta6e baki amani tayi tace"Okey yayi kyau,yanzu komai zai fara tafiya dai dai,akwai wani albishir da zanyi maki," Natsuwa Aunty babba tayi tare da cewa"ina sauraronki ƙanwata,faɗamun albishir ɗin," Shu'umin murmushi Amani tasaki tare da miƙewa daga saman sofa ɗin tabar Amal zaune tana kallo,takawa tayi nesa da falon,sannan tace"Nasan inna faɗa maki albishirin nan ko bacci ba zaki iya yi ba saboda tsabar farin ciki," A ƙagare Aunty babba tace"dan Allah shaƙamun mana kanwata wane irin albishir ne wannan, Murmushi Amani ta kuma yi sannan tace"nasamo ma Hayaam maganin mallaka a wurin wani hamshaƙin boka,aikin shi tamkar yankan wuƙa yake,saboda Ni shaidace akan idona aka ta6a amfani da maganin kuma yaci," Cike da farin ciki Aunty babba tace"Wai dagaske"? dariya amani tayi tare da cewa"dagaske mana!,wata neigbour ɗinace keson ƙanwarta ta auri ƙanin mijinta,sun rasa yarda zasu jawo hankalinshi acikin gidannan saboda mutunne mai matuƙar ji dakai,kamar dai sgr,ina baki labari kwatsam sai ga wata ƙawarmu ta bamu labari akan wani shu'umin boka,agabana aka shirya zuwa wurin bokan suka amso maganin,a yanzu dai labarin da nake baki,yarinyar na nan ta aure shi hada ciki ma sai faman shan soyayya suke abun gwanin burgewa,"_ Saboda tsabar Murna Aunty babba ta gaza rufe bakinta dakyar ta iya cewa"Yanzu ya za'ae kenan asama ma Hayaam maganin?nawa zamu nema"? "Ko sisi basai kin bada ba Auntyna,fisabilillah na amso ma hayaam maganin da kuɗina ai nima kanwata ce ko,nidae burina shine inga ta auri sgr Abra kuma ta auri marshal Omar," washe baki Aunty babba tashiga yi tana cewa"Allah sarki Amani,ashe haka kika damu da ƙannen namu?gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba,yanzu kenan Hayaam zatazo ta kar6i maganin gidanki kenan"? Amani tace"eh,in ma batasamu zuwa ba ni zanje nakai mata shi,babu damuwa,"_ Sun jima suna waya kafin daga bisani firar tasu ta ƙare anan, Tuntsirewa da dariya Aunty babba tayi tana tafa hannu tashiga cewa"ban ta6a ganin ƴar wahala ba irin Amani,duk irin abunda nakeyi mata amma ita burinta ta taimakamun wurin ganin na cimma burina,gaskiya na tausaya mata,abun tausayi, girgiza kai kawai hafsat tayi tare da wucewa ciki tabar mommyn nata tana ta faman sambatu, A can 6angaren kuwa fashewa da dariya Amani tayi tare da cewa"Aunty laila kenan!ke atunaninki kinyi mun wayau bakisan cewa Amanin da kika sani ada ba ita bace ayanzu ba,ashirye nake dana kwance dukkan wasu notikan kanki,zan mayar dake kamar wata zararra,ita kuma hayaam zanyi amfani da wannan damar wurin ganin na canza mata halittar jikinta,kamar yarda kuka canzawa Amal kamanni ta tsotse ta rame ta ƙanjame haka itama nakeson ta koma,dama ance ramuwar gayya tafi ta gayyar zafi,that's my plan! Tana faɗin hakan ta juya tare da komawa wurin Amal ta zauna,kallonta Amal tayi tare da cewa"Aunty amani,dan Allah kiyi haƙuri da abunda zan faɗa maki,bansan ko zai 6ata maki rai ba,nasan cewa su mammy sun cutar damu sosai,amma kada kice zaki ɗauki fansa,mubarsu da Allah kawai shi zai saka mana,sannan in zamu iya mu taimaki mahaifinmu don yana cikin mawuyacin hali" Shuru kawai amani tayi batace mata komai ba,amma fa har yanzu tana akan bakanta,maganar mahaifinsu kuwa tasan matukar mammy na numfashi bazata barshi ya sarara ba,don ba karamar shedaniyar mata bace,ita kanta yanzu tana shakkun in don Allah aka hadata da Abbas. _💋Boss Bature💋_ ______________________tunda yadawo daga masallaci yake jin jikinshi wani irin yanayi mara daɗi,bedroom dinshi ya shiga tare da nufan saman gadonshi ya haye yana faman sauke ajiyar zuciya,pillow ya jawo tare da aza kanshi a saman shi yana faman lumshe ido,yana cikin wannan yanayin yaji fitar wani abu daga hancinshi mai ruwa ruwa,cikin sauri junaid ya tashi daga zaune yana kallon pillown nashi,zuba ido yayi yana kallon jinin daya ɗigo daga hancinsa,abun yayi matuƙar ɗaure mashi kai,kafin yayi wani yunƙuri sai ga wani ɗigon jinin ya sake fitowa daga ƙopan hancinshi,abu kamar wasa jinin ya dinga ɗiɗɗigowa saman bedsheet ɗinshi,   Hankali tashe junaid ya sauko daga saman gadon da saurin gaske ya faɗa cikin toilet ɗinsa,kai tsaye ya nufi wash basin,dafa shi yayi yana kallon fuskarshi acikin mirror ɗin,hancin shi yabi da kallo ganin yarda hancinshi ke cigaba da bleeding,sam bai damu ba saboda yasan cewa yana yawan yin nose bleeding,don haka tunaninshi ha6o ne kawai,   Hannu yakai tare da kunna tap ɗin,ruwa ya soma shararowa da gudun gaske,tarba hannunshi yayi tare da ɗebo ruwan ya watsa a fuskarshi yana wanke blood ɗin,murzar wurin ya shiga yi don jinin ya tsaya amma yaƙi daina zuba,ya kusan 15mins a haka sannan jinin ya dakata da ɗigowa,ajiyar zuciya ya saki tare da kai hannu ya kashe tap din,   Sannan ya fito daga cikin toilet ɗin,yana ƙoƙarin ɗaga ƙafarshi ya nufi gadonshi,wani irin jiri ya kwashe shi,hannu ya aza asaman kanshi tare da ambaton sunan Allah,yayin da idanunshi ke ganin mashi biji biji,   Yana cikin wannan yanayin Sehrish ta faɗo cikin ɗakin ambaton sunanshi ta shiga yi "junaid, junaid.....,"   ganin shi atsaye abakin ƙopar toilet ya sata tsayawa tana kallonshi tare da cewa"baby junaid meya faru ne naganka haka?baka jin daɗine,"    Jin muryarta yadinga yi acikin kanshi tamkar ana buga ganga,hakan yasa ya yanke jiki zai faɗi gadan gadan,   A wani irin slow sehrish ta ƙarasa wurin da sauri ta ruƙo shi suka faɗi ƙasa atare,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba jin yarda yake kokowar fitar da numfashinsa,hankali a matuƙar tashe take faɗin"Innalillahi_!junaid!meke faruwa dakaine!me yake damunka ne?ka faɗamun dan Allah,    Ko iya ɗaga la66ansa ba yayi bare ya iya furta mata wata kalma,hannunshi dake kerma yasa tare da ƙara ƙanƙameta sosai ya kwantar da kanshi asaman ƙirjinta yana cigaba da ƙoƙarin fitar da numfashinsa,hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,tuni ta soma fitar da ƴan matan hawaye,yanke shawarar zuwa ta sanar ma wani tayi don a hanzarta zuwa aga halin da yake ciki,ƙoƙarin janye jikinta tayi daga nashi,tamkar zata rabashi da ranshi haka yaji,ƙanƙameta ya kuma yi sosai da sosai sai lokacin ya iya furta"rishi kada ki tafi ki barni a yanayin da nake ji zan iya mutuwa," Cikin shessheƙar kuka take cewa"junaid ka bari inje in sanar dasu,idan wani abu ya same ka fa"?    "A'a nidai kada ki tafi kibarni,"ya ambaci hakan da wata irin kasalalliyar murya,tsananin tausayinshi ne ya kamata,mayar da hannunta tayi abayanshi tare da ƙara rungumo shi ajikinta tana tofa masa addu'a,lamo yayi ajikinta yana faman sauke ajiyar zuciya,lokaci guda kuma numfashin ya daidaita kamar yarda yake ada,komai nashi yadawo normal,wani irin sanyine ya ratsa zuciyarshi,idonshi na arufe yake shaƙar ƙamshin turaren rishi ɗinsa,gaba ɗaya ya shiga yanayin da bai ta6a shigar irinsa ba, Muryarta ce ta katse shi da cewa"junaid kana lafiya kuwa?naji ka tsit"?    shiru yayi mata,saboda bayason tasan cewa ya dawo cikin hayyacinsa,baison ta raba jikinta da nashi,ɗumin jikinta ba ƙaramin daɗi yayi mashi ba,yaushe rabon da yaji ɗumin mace haka akusa dashi tun yana da kananun shekaru,tunda mommynshi tabarshi,Aunty azmee ta ɗaura da shayar dashi,shima ɗin da zarar ta kammala bashi nono ƴan uwanshi ke ɗauke shi daga wurinta,don basu son rabuwa dashi kona minti ɗaya,ya saba da jikin abban shi,dana ƴan uwanshi yayi missing wannan feeling ɗin,    Jin yarda junaid ya lafe mata ajikinta kamar jinjiri,yasa tayi tunanin cewa kodai ya cika ne,cikin sauri takai hannu tare da ɗago da kanshi tana kallon fuskarshi,waro ido waje tayi ganin yarda yake ta faman sakin murmushin nan nashi,ranta ne ya bata cewa Dama duk plan ne ya tsara mata don ya tsoratar da ita,ɗaure fuska tayi tare da cewa"janaid wannan duk shirinka ne ko? don ka tsoratar dani," Buɗe idanunshi yayi a hankali yana kallon fuskarta data zuba mashi ido,tana mashi kallon Tuhuma,   Murmushi ya kuma saki tare da cewa"dan Allah rishi ki mayar dani a jikinki na kwanta,ba kiji wani irin daɗi dana ji ba,daɗi kamar nayi bacci,"ya ƙarasa maganar yana lumshe mata ido,tsuke fuska sehrish tayi tare da cewa"amma ka rainamin wayau junaid!wai meyasa ka fiye shiririta ne,kalli fa, ka gani hada hawaye na soma zubarma saboda halin da na sameka aciki,ashe duk plan ne ko"?    girgiza mata kai yayi tare da cewa"ba haka bane reesh,kona faɗa maki gaskiya ba zaki yarda ba,"   A hankali ta kwantar mashi da kanshi ƙasa,sannan ta matsa tare da saita fuskarta akan tashi tana kallon shi,shima binta yayi da kallo yarda ta duƙo da fuskarta asaman tashi sumar kanta kuma tayi masu rumfa,tunda ta faɗo bedroom ɗin nashi tashigo da gudu don ta tarbe shi mayafinta ya sulale ƙasa daga jikinta,    "Junaid waye uncle Abusufyan?naji abbanku na cewa zaizo nigeria,kodai shima ɗin yayanku ne"?   girgiza mata kai yayi alamar a'a yace"uncle ɗinmu ne,ƙanin mahaifinmu dake zaune a ƙasar turkey"    jinjina kanta ta ɗanyi kafin ta kuma cewa"bayan shi kuma naji Abbanku yana cewa,Mommynku zata zo itama,tare da wata goggonku ta katsina da kuma Ammi da Aunty azeema,duk zasu zo,"    Sai da ya bari takai ƙarshen maganarta sannan ya ɗan harareta tare da cewa"Ashe dama jin gulma ne ya kawoki ɗakin"?    Murmushi tayi tace"no ba haka bane junaid,inason nasansu ne saboda na koyi zama da kowannansu,bana so na samu matsala da kowa acikin family ɗinku,"    "Zan faɗa maki halin kowannansu amma bisa sharaɗi ɗaya'?ya jefa mata tambaya,   Tace"ina sauraronka wane sharaɗine wannan"?_   murmushi ya saki tare da kai hannunshi ya nuna mata red lips ɗinsa yace"kiss on lips,if u agree then saina faɗa maki,"    hannu tasa tare da ɗan buge bakinshi tace"pls junaid banason wasa fa,in zaka faɗamun ka faɗamun kawai,in ba haka ba zan tashi inyi tafiyata,"   tayi maganar tare da yunƙurawa zata miƙe cikin sauri ya ruƙo hannunta tare da cewa"rishi mommyn mu bata da sauƙi,nima haka naji ana faɗa,amma in har zaki iya zama da babban yayanmu to wannan bazai maki wuya ba,bambancin ita mace ce kinsan ku mata da tsiwa kuke,   Dariya tayi tana sauraronshi "Uncle ɗinmu kuma Abusufyan,wayayyen mutun ne,idan yazo zakiji daɗin zama dashi,bafa wani babba bane autansu daddynmu ne,yana da sauƙin kai sosai amma idan mutun bai kwanta mashi araiba hmmmmm bazasu ta6a jituwa ba,Aunty azeema kuma kamar abbanmu take wurin faran faran da mutane ga son ƴa'ƴa,zakisha mamaki idan tazo ta ganki sosai zata jaki ajikinta,goggon katsina kuwa......"bai ƙarasa ba ya kama dariya,   Murmushi ta saki tare da cewa"me tayi ita?ko batasan mutane"?    Girgiza kai yayi tare da cewa"a'a tanason mutane sosai,matsalarta ɗaya tana da mental illness.......'   Tunda junaid ya ambaci mental illness taji gabanta ya ɗan faɗi kaɗan kamar maison tuna wani abu acikin brain ɗinta,   "tana da ban dariya sosai,tana fa iya ganinki tace ke ɗiyar wani ce acikin family ɗinmu kuma dole ki yarda da hakan in ba haka ba ta sanya rigima hada kuka ma,'   Sai faman zuba junaid yake yi yana korama sehrish jawabi,ita kuwa tuni tayi nisa cikin tunaninta,kalmar da ya faɗi na cutar ta6in hankali ta tsaya imata arai,so take ta tuna waye ta ta6a sani da irin wannan lallurar amma sam tagaza tuna hakan,   Ganin ta tafi duniyar tunani yasa junaid kai hannu ya janyo sumar kanta yana cewa"wai menene haka reeeshi,kin barni ina ta zuba kamar rediyon da bata da saiti,"   Firgita ta ɗanyi tare da kallon shi har lokacin yana daga kwance tace"junaid thanks for the information,zan koma bedroom ɗina naji ana kiran sallar isha,kaima ka tashi kaje kayi sallar,'    Ba musu ya amsa mata da cewa"bari nayi alwala sai mu fita atare,"   Amsa mashi tayi da toh sannan ta miƙe tare da juyawa ta ɗauko mayafinta daya faɗi kasa ta rufe kanta dashi,toilet junaid ya shiga shaf shaf yayi alwala,bayan ya fito atare da ita suka saukko downstairs,    Anan ya haɗu dasu Irfan zasu masallacin suma yabi bayansu suka tafi,    Komawa bedroom ɗinta tayi kai tsaye ta fada toilet ta ɗauro alwala,bayan ta fito ta ƙarasa wurin wardrobe dinta tare da ɗaukar hijabinta da sallaya ta shimfiɗa tare da kabbara salla,anatse ta kammala sallar,fitowa tayi daga dakin nata sannan ta wuce kitchen don ta shirya ma kanta abincin da zata ci saboda yunwar data taso mata, _💋Boss Bature💋_ A hankali Motarsu tashiga babban gate din gidan Abusufyan,major ne ke driving dinshi yayin da Omar ke hakimce a seat ɗin baya,sai faman zullumin haɗuwarshi da hossana yake saboda yasan cewa ba ƙaramin fushi take dashi ba,saboda ƙin zuwan da yayi, Parking ɗin motar major yayi sannan ya fito tare da buɗe mashi motar,a hankali Omar yasa ƙafa tare da fitowa daga ciki,sannan cikin sauri batare da 6ata lokaci ba ya wuce cikin gidan, Tunkan yasa ƙafarshi cikin parlourn nasu yajiyo shessheƙar kukan hossana,tsayawa ya ɗanyi yana sauraron abunda suke cewa,    "Hossana wai ba zaki daina kukannan ba?salon ki 6ata kwalliyarki ko"?   "Jahad ba zaki gane bane,bakisan yarda nake ji bane,saboda ya omar nayi kwalliyar nan,amma ta tashi a banza,yau ma bazaizo wurin mu ba...'cikin shessheƙar kuka ta ƙarasa maganar, ƙayataccen murmushi Omar ya saki a fuskarshi,kafin yasa kai tare da shiga cikin palourn,samunsu yayi zaune asaman 3 seater,hossana ta kwantar da kanta asaman hannun sofa ɗin,yayin da jahad ke gefenta tana rarrashinta,gaba daya duk sunyi wanka sun canza kayan jikinsu,riga da skirt ne ajikin jahad,hossana kuma gown ce mai kyan gaske,    jin alamar motsin mutum yasa jahad ɗagowa tana kallon shi,cike da mamaki ta buɗe baki zatayi mashi magana,da hanzarin gaske ya dakatar da ita ta hanyar yi mata nuni da hannunshi alamar ta tashi ta tafi,murmushi jahad tayi tare da miƙewa cikin sanɗa tabar saman sofa ɗin ta koma saman 1 seater ta zauna tana kallon dramar da ya Omar ɗinsu zai shirya,cikin sanɗa ya lalla6a tare da komawa wurin da jahad ta tashi ya zauna,sannan yakai hannunshi tare da ɗan janyo wutsiyar gashinta, A fusace tace"dan Allah jahad ki rabu dani inji da abunda ke damuna,ki tashi kiban wuri," Murmushi Omar yayi tare da cewa"zan tafi amma ki fara faɗamun meyasa kika damu da yaya Omar ɗinki har haka"? Sam hossana bata gane voice ɗinshi ba saboda ranta a6ace yake, "Saboda inason shi sosai,jahad nasan ni kawai nake haukana,yana can wurin hayatyn shi,suna shan soyayya.....' Katse ta Omar yayi da cewa"kina kishi ne"? A faɗace tace"saboda me bazanyi kishi ba,nima ae zuciyata ce a ƙirjina ba dutse ba," Wannan maganar ta hossana ba ƙaramin dariya taba marshal Omar ba,hatta jahad sai da ta murmusa daga inda take, Kwantar da kanshi ya ɗanyi abayanta yana cewa"am really sorry babyn Omar,nayi missing ɗinki sosai,nasan nayi laifi ayimun afwa bazan ƙara ba..."jin muryar Omar raɗau a kunnanta yasa tayi hanzarin ɗagowa tana kallonshi da idanunta da suka cicciko da kwalla, Waro ido Omar yayi yana kallonta ba ƙaramin tsorata yayi ba da ganin makeup ɗin da ke a fuskarta,ta dambara Uwar foundation kamar wata aljana,Jan bakin da ta shafa ya 6ata fuskarta har wurin cheeks ɗinta saboda uban kukan da tasha,ga maskara ta zazzago mata a ƙasan idonta, Hankali tashe Omar yace"subhanallahi,kuke ganinmu bamu muke ganinku ba,Babyn Omar wannan kwalliyar fa?dama itace kwalliyar da ake cewa anyimun don inzo in gani,"cike da zolaya yayi maganar,amma tamkar ya tunzura hossana nan take ta 6are baki itare da fashewa da wani sabon kukan, Dariya jahad ta dinga tiƙa kamar kamar me har tagaza dakatar da kanta, Yama rasa ta inda zai fara shawo kanta don ya lallashe ta,hakan ya ƙara hasalata,kamar wata ƙaramar yarinya,ba ƙaramin tausayi ta bashi ba yasan duk don saboda rashin zuwan shi ne,hannu yasa tare da janyota jikinshi yayi hugging ɗinta sosai yana ɗan bubbuga bayanta,lokaci guda ta nemi kukan da takeyi ta rasa,sai gata tana faman sauke ajiyar zuciya, a hankali ya furta"am really sorry hossana,bazan ƙara 6ata maki rai ba,kullum zan dinga zuwa idan ma bansamu halin zuwa ba zan kira ku awaya mu gaisa," Ya ƙarasa maganar tare da cewa"kin yafe mun"? ƙasa ƙasa tace"na yafe maka,amma karka ƙara," murmushi yayi tare da ɗagota daga jikinshi yana kallon fuskarta,sai faman cin magani takeyi tana haɗe mashi fuska, "Kin ci abinci kuwa"? "A'a banci ba," "Why"? Ya tambaya yana kallon bakinta da take ta faman turowa irin na shagwa6a66u, "Kai nake jira kazo ka bani abaki," "Really"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh, Juyawa ya ɗanyi tare da kallon jahad dake zaune tana kallonsu gwanin burgewa yace"dagaske hossana bata ci komai ba"?_ Amsa mashi tayi da eh,jinjina kai yayi sannan yace"ki kawo mata dinner ɗinta anan,sai na tabbatar da taci ta ƙoshi sannan zan tafi," Murmushi jahad tayi tare da miƙewa ta wuce downstairs don pta shiryo masu dinner din," _💋Boss Bature💋_ Yau da wuri suka dawo cikin gidan wuraren karfe goma dai dai,wani irin tsoro da fargaba sehrish taji,musamman da azmee ta sanar da ita cewa ga dinner ɗin sgr can taje takai mashi,bakomai ya faɗo mata arai ba face abunda ya faru ɗazu tasan cewa dole ya tuhumeta saboda ita kaɗai ce macen da take shiga part ɗinsa,sai faman zarya takeyi acikin bedroom ɗinta,tana tunanin yarda zata tunkare shi ayau ɗinnan, Hayaaam Tafiya takeyi cikin sanɗa tana waige waigen ko akwai wani a main palour din cikin sa'a taga babu kowa,murmushin mugunta ta saki tare da nufar kitchen din,tana shiga tayi arba da tray na abincin da Azmee ta shirya ma Sgr,asaman dogon table na kitchen ɗin ta ajiye mata,jinjina kai hayaam tayi tare da cewa"hmmmmm yarinya kenan yau zaki fara sanin koni wacece wurin iya makirci," Tana faɗin hakan ta shiga ciki kai tsaye ta tsaya wurin tray din,hannu tasa tare da buɗe warmer ɗin dake ɗauke da chicken ppr soup,sai faman ƙamshi yake yi,murmushi hayaam tasaki tare da kai hannu cikin sumar kanta,ta cinko gashin kanta sannan ta jefa acikin chicken ɗin hadasa hannu ta motsashi aciki,sannan ta rufe murfin,duk hakan bai mata ba sai da tabi komai na abincin ta sanya gashi aciki,sannan cikin sanɗa tabar kitchen ɗin,tana faman sakin dariya don tasan cewa da zarar sgr yaga gashin nan yarda yake da tsaftar nan ba ƙaramin ƙyamatar yarinyar zaiyi ba,kuma tasan dole ya koreta daga yi mashi aiki,bama wannan ba dole ya hukuntata, tashin hankali da ba'a sama shi date, 💋💋💋 Fitowa sehrish tayi bayan ta gama zullumin nata,kitchen ɗin ta nufa batare da 6ata lokaci ba ta ɗauko tray ɗin a hannunta tare da wuce wa upstairs,hakanan tadinga jin gabanta na faɗuwa kamar wani mummunan abu zai faru da ita,tsayawa tayi abakin ƙopar shiga falon nashi,sai da ta dai²ta natsuwarta sannan ta zabga sallama,tana jiran jin amsawar shi, Jin shiru yasa ta ƙara maimaita sallamar,har kusan sau uku ana huɗun ne tajiyo muryarshi yace"Come in," Ae tunda taji Voice ɗinsa jikinta ya shiga yin kerma,addu'o'in neman tsari tashiga karantowa abakinta,ta jima atsaye tana faman zullumin abun da zaibiyo baya kafin daga bisani ta daure tare da shiga cikin falon nashi,ƙamshin turaren nan nasa ne ya wanko mata hancinta har saida ta lumshe idanunta,tunkan taƙarasa ta hango shi kwance ya miƙe kafafunshi asaman 3 seater,jikinshi na sanye da pyjamas yellow,ba ƙaramin kyau su kayi mashi ba,kunnanshi na kare da wayarshi alamar waya yake yi,    Gabanta na faɗuwa haka ta nufe shi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman table dinsa,saboda tsabar rashin gaskiya,tana ajiye tray ɗin ta juya cikin sauri zata bar parlourn nashi,kamar daga sama taji anyi ma mayafinta kwakkwaran ruƙo ta baya,nan take mayafin ya sulale daga jikinta,zazzare ido waje sehrish tayi jikinta na kerma,nan take tashiga haɗiyar yawu,tsayawa tayi tana jiran maizo biya baya,    Jin alamun motsin shi abayanta ya tabbatar mata da cewa shine yaja mayafinta daga jikinta,tsayawa tayi tana ambaton sunan Allah abakinta,ganin kusan minti biyar bata ji ya ƙara motsawa ba yasa tayi hanzarin juyawa a wani irin firgice sam bata tsammaci yana tsaye abayanta ba sai dai kawai taji ta kai mashi karo,ja da baya ta ɗanyi tana faman zare ido,tunkan ya tambayeta ta shiga cewa"dan Allah kayi haƙuri,nasan na 6ata maka rai,wlh nima bada son raina hakan ya faru ba,nashiga na gyara maka bedroom ɗinka ne,bayan na kammala shine na ɗan cire mayafina na ajiye asaman gadonka don naji daɗin yin aikin,ashe kafin na fito daga cikin toilet ɗin ka dawo,shine na same ka akwance kana bacci saman mayafina,saboda ina tsoran ka farka ka ganshi yasa nayi ƙoƙarin janshi daga jikinka,shine...cikin bacci batare da saninka ba ka...........'kasa ƙarasa maganar tayi saboda jin yatsun hannunshi da tayi asaman lips ɗinta,alamar tayi mashi shiru,sannan ya hankali ya ɗan ware eyes ɗin nashi akan fuskarta............ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. 💋BOSS BATURE💋 Follow this link to join my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Father of soldiers (takun ƙarshe) A tsananin tsorace take kallon fuskarshi ganin ya ware idanunshi yana kallon fuskarta,a hankali ya zame finger ɗinshi daga saman tausasan la66anta dake ta faman kerma,sai faman haɗiyar yawu take yi tsoranta wane hukunci zaiyi mata,sau biyu yana ƙoƙarin buɗe mouth ɗinsa zaiyi magana amma ya kasa,saboda ya rasa me zaiyi ma yarinyar,tun da yake wata ƴa mace bata ta6a ƙetare iyakar da yarinyar ta ƙetare ba,a matsayinta na wadda ba muharramarsa ba kuma ƴar aikin gidansu,ƙara matsawa yayi kusa da ita,cikin sauri sehrish ta ƙara ja da baya,tana faman girgiza mashi kai Alamar yayi haƙuri karya hukunta ta,tuni ta soma fitar da ƴan matan hawaye a idonta,ba komai take kallo ba face damtsen hannunshi da kuma wannan faffaɗan ƙirjin nashi,uwa uba yarda ya tsaya agabanta tamkar wani zaki, Hannunshi yakai tare da ruƙe waist ɗinshi yana kallon yatsun hannunta dake ta faman kerma,  A natse ya soma magana"I will punish you for the mistake you made in my bedroom on my bed,so that you know under whom you are working,cos u crossed your boundary," Gabanta ne taji yayi wani irin bugu jin abunda sgr yace,hankali tashe take kallonshi,muryarta har kerma take wurin cewa"bazan ƙara ba,"    girgiza kanshi yayi alamar bai amince ba sannan yace"You are going to start frog jumping around the chairs without stopping, if you do that I will let you go, but if you dare stop,I will punish you badly," yana ƙarasa maganar tashi ya juya tare da komawa saman sofa ɗin yana kallonta yace"Am watching u,"yayi maganar tare da nuna mata blue eyes ɗinshi da 2 fingers ɗinshi,alamar idonshi na akanta,     Tamkar ta fashe da kuka haka taji,ga matuƙar tsoranshi da take ji,ga punishment ɗin daya bata na tsallan kwaɗi abunda ta tsana arayuwarta saboda tasan wahalarshi,ba abune mai sauƙi ba bazata ta6a mantawa da lokacin da fawan ya sanyata frog jump ba har jini ya 6alle mata,saboda tsabar wuyar da tasha har suma tayi lokacin,    gyaran muryar da Sgr yayi mata ne yasa tayi saurin zuƙunnawa tare da kama kunnanta da hannayenta sannan a hankali ta soma yin tsallen kwaɗin,in da Allah yasota ma Wando ne ajikinta ba skirt ba da abun yafi muni,da sauri take yin tsallen har ta zagaya ta bayan sofas ɗin ta kuma dawowa ta gabansu duk yana kallonta,tun Sehrish tana yin tsallen kwaɗin cikin daɗin rai har ƙafafunta suka soma rurruƙewa,wani irin zogi suka shiga yi mata,nan take hawaye suka fara shararowa daga idanunta har da majina duka ta haɗa,   Yana jin shessheƙar kukanta amma ko ajikin shi,a ƙarshe ma sai ya ɗauki lemu mai sanyi ya tsiyaya acikin cup ya shiga kur6arshi a bakinsa yana sha,tun yana shan lemun daga zaune har ya ɗan kishingiɗa kafaɗarshi saman sofa hand ɗin,    A wani irin galabaice sehrish ke ɗaga kafafunta tana yin tsallen kwaɗin,a ƙalla ta zagaye kujerun kusan sau takwas amma sgr baice ta dakata ba,tun tana sa ran zai tsayar da ita harta fidda rai,saboda tsabar tsoro da firgicin da take ciki yasa ta gaza gane cewa sgr fa bacci ya kwashe shi asaman sofa ɗin,duk in ta zagayo ta wurinshi sai taga kamar idonshi biyu,batasan cewa tuni bacci yayi awon gaba dashi ba,har ya ajiye cup ɗin dayake shan lemun dashi, Wani irin matsanancin ciwon kaine ya far mata,ga raɗaɗin da kafafunta keyi mata,lokacin da ta ƙara zagayo wa ta wurin shi,cikin shessheƙar kuka tace"...Am really sorry babban yaya,i ave realized my mistake,bazan ƙara ba nayi maka alƙwarin hakan," tabbas yajiyo muryarta acikin ears ɗinshi amma sam bazai iya buɗe idanunshi ba,saboda nauyin baccin da yayi,   Ganin bai tanka mata ba,yasa sehrish cigaba da yin tsallen kwaɗayin da takeyi dakyar dakyar,tana cikin wannan yanayin wani irin stomach pain ya taso mata haikam,nan take ta yanke jiki ta faɗi saboda galabaitar da tayi,taji jiki sosai, Sai faman zagaye hayam takeyi a tsakanin upstairs da kuma down,ba don komai ba sai don taga a wani yanayi Sehrish zata fito daga sashen sgr,har wani murmushin mugunta take saki don tasan cewa muddin Sgr yaga siraran gashi a cikin abincinsa dole ya kikkifa Mata mari,sannan ya kore ta daga yi mashi aiki,daganan  ita kuma zata samu shiga a wurin shi,gajiya ta fara yi da zagayen ganin cewa har ƙarfe sha biyu na dare tayi Sehrish bata fito daga part ɗinshi ba,hakan ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,baƙin ciki kamar ya kashe ta,tsayawa tayi ruƙe da qugu tana cewa"Ko uban me yarinyar can takeyi a part ɗinsa har wannan lokacin bata fito ba!wlh na tsani yarinyar can,ko son ganinta bana yi,shisshiginta yayi yawa nasan yanzu haka tana can ta liƙe mashi tana kalle mun surar jikin mijina,Allah bazan ƙyaleta ba sai nayi maganinta mtssw,!"ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki sannan ta kama hanyar komawa bedroom ɗinta tana faman sambatu kamar wata zautacciya ," _💋Boss Bature💋_ Kwance yake asaman gadon Abbansu hannunshi rungume da pillow,yayin da idanunshi ke arufe tamkar mai bacci, Yana jin lokacin da abbansu ya fito daga cikin toilet jikin shi sanye da Jallabiya,ƙarasowa yayi wurin gadon tare da samun wuri daga ɗan gefe ya zauna,sannan ya ɗan juya tare da kallon fuskar junaid da yayi likimo kamar mai bacci,hannu yasa tare da shafa sumar kanshi yace"sarkin rigima yayi bacci,"ya faɗi da murmushi a fuskarshi,janye hannunshi yayi daga saman sumar kan junaid,sannan ya miƙa hannu tare da ɗaukar wayarshi dake ajiye a saman bedside drawer,contact ɗinshi ya shiga ya lalubo numbar mommynsu junaid ya danna mata kira,nan take kiran ya shiga,cikin sa'a ta ɗaga kiran nashi,murmushi yayi tare da kara wayar a kunnanshi yace"Noorul ƙalbina"   On the other hand alexandra tace"yau kuma soyayyarce ta motsa?ni zaka yaudara da kalamanka saboda kaji cewa zanzo nigeria ko?to ae ba saboda kai zanzo ba,zanzo ne don naga Yarona kuma da zarar nazo zan ɗauke abuna na dawo Australlia dashi,don bazan barshi a hannunku ba don ban yarda da irin rainon da kake mashi ba,"    girgiza kai abbansu yayi tare da cewa"Yaushe zaki canza ne?ke ko tausayina bakya ji ne?baki damu da halin da nake ciki ba,na rashinki a kusa dani,ina fa sonki har yanzu kuma ban rabu dake ba,kece kika rabu dani kika kama hanya kika bar ƙasar nan batare da sani na ba,yanzu kinyi mun adalci"? Cikin sanyin murya ya ƙarasa maganar yana sauraron Amsarta Junaid daya kasa kunne yana sauraransu sai faman murmushi yake yi idonshi a rufe,    Shiru Alexandra tayi yayin da idanunta ke kallon sararin samaniya ta cikin windown katafaren bedroom ɗinta,kunnanta na kare da wayarta tana sauraron shi,muryarshi ta kuma ji yana cewa"kinyi shiru baki ce komai ba"?   Ajiyar zuciya ta sauke tare da ɗan jinjina kai tace"me kake so yanzu"?     Runtse ido abbansu yayi saboda ya rasa yarda zai fahimtar da ita,wata irin bauɗaɗɗiyar mace ce,ko don tayi aikin soja ne yasa ta kasance haka,saboda a tsaye take ba irin raunin zuciyar nan na mata,    "Hossein in baka da abun cewa,Ni zan aje waya ne,"   Muryarta ce ta kuma katse shi,a lokacin ranshi ya gama 6aci a faɗace yace"Fatima na gaji da irin wulaƙancin da kikeyi mun,nayi danasanin haɗuwata dake tun farko,kuma nayi danasanin haɗa zuri'a dake,saboda kin cutar da rayuwata,sam baki respecting ɗina a matsayina na mijinki,kuma uban ya'yanki,idan kinsan zaki tafi kibarni meyasa tunfarko kika sanyamun soyayyarki acikin zuciyata?    Muryarshi araunace yayi maganar yanayin sautin kamar zai fashe mata da kuka,    Jin tayi shiru bata ce mashi uffan ba yasa shi cewa"banaso ki dawo ƙasar nan!ki cigaba da zama acan,saboda zuwan naki baida amfani awurina,kuma babu ruwanki da ƴa'ƴana  dama can baki damu dasu ba,tun da har zaki iya tafiya kibarsu,batare da tunanin yaya rayuwarsu zata kasance ba"!   Jin wannan maganar ta Abban nasu yasa hawaye suka soma gangarowa a idanun junaid,sam baiji daɗin yarda mommynsu ke 6ata ma Abbanshi rai ba,    Bai jira Alexandra ta bashi amsa ba ya katse kiran nata tare da yin wurgi da wayar gefe guda,jiki amace ya kifa kanshi asaman gadon,idanunshi sunyi jawur sun cicciko da kwalla,    a hankali hawayen suka soma gangarowa,kamar daga sama yaji tafin hannu a fuskarshi,cikin sauri yakai idonshi akan junaid dake share mashi hawayen fuskarshi,   Cikin shessheƙar kuka yace"Abba don Allah kadaina zubar da hawayenka akan mommynmu,ba dole sai da ita zaka samu farin ciki ba Abba,Ni na isheka duk wani farin cikin duniyar nan,Abba ka ta6a faɗamun cewa ko kallona kayi kanajin sanyi aranka,why zaka Sanya ma kanka damuwa akan mommynmu?ka rabu da ita kawai Abba,akwai mata da yawa agari waɗanda suka fi ta hankali.........'    Murmushi Abban nasu yayi jin abunda junaid yace,    Miƙewa yayi daga zaune suna fuskantar juna yace"junaid bazaka gane ba!mommynku ba kamar sauran mata take ba,idon har tana raye ni bazan iya kula wata ƴa' mace ba,"    ɗaure fuska junaid yayi tare da zum6ura baki yace"Saboda me Abba?me tafi sauran matan?duk yarda take 6ata maka rai?     "Junaid she's special saboda ta bani babbar kyautar da har yau in na kalleta nake jin farin ciki araina,"    Cike da mamaki junaid yace"Wata irin babbar kyautace wannan? Ya tambaya yana kallon Abban nasu,    Murmushi Abbanshi yayi tare da nuna shi da yatsanshi yace"Am talking about u junaid!Matar da ta haifamun lu'u lu'u kamarka taya zan iya rabuwa da ita junaid?ta bani farin cikin da har na bar duniyar nan bazan ta6a samun makamancinshi ba,kyakkyawan yaron da kowa ke alfahari dashi,kowa yake so kuma yake ƙauna,Junaid bani da burin da ya wuce in farka in ganka akusa dani da ranka da lafiyarka...........'   Tsagaitawa yayi da maganar yana kallon junaid da bakinsa yaƙi rufuwa saboda tsabar farin ciki kamar ya zuba ruwa ƙasa yasha,sai faman washe baki yake yi,kamar wanda akayima albishir da gidan Aljanna,ya ma rasa mai zaiyi don tsabar farin ciki,a ƙarshe ya faɗa jikin Abban nasu tare da rungumeshi ya ƙankame shi sosai ajikinshi yana faman dariya,     Zagayo da hannunshi yayi yana ɗan bubbuga Bayan junaid yaci gaba da cewa"I love u so much my baby boy,Allah ya nuna mun ranar auranka kafin nabar duniya,koda ace shine abu na ƙarshe da zan gani kafin na koma ga mahalicci na,Ina rokon Allah ya nuna min wannan ranar,da shagwa6a66an yarona zaiyi aure,zanso naga yaron da matarka zata haifa mana,wanda zamu dinga kira da Babyn baby,"   Fashewa sukayi da dariya, suka dinga yi atare,har lokacin basu raba jikinsu ba,    Ƙarar shigowar message a wayar Abban nasu ce,yasa junaid janye jikinshi daga na abban nasu sannan ya rarrafa tare da kai hannu ya ɗauko mashi wayar,ya miƙa mashi,   Kar6a Abba yayi tare da duba message ɗin da aka turo mashi yana karantawa kamar haka    "Forgive  me my love.......nasan na 6ata maka rai sosae,kayi haƙuri ka yafe mun kuma inaso kasan cewa nima ina sonka sosai har yanzu ba abunda ya sauya na sonka acikin zuciyata,zan dawo nigeria ne saboda na gyara alaƙata da uban ƴa'ƴana,da kuma ƴa'ƴan nawa,ka shirya tarbar amaryarka Alexandra...........'   gaba ɗaya ya rikice saboda tsabar farin cikin saƙon da ya shigo mashi,saboda ruɗu har hannu yasa yana goge idanunshi wai ko badaidai ya karanta bane,saboda tunda yake arayuwarshi alexandra bata ta6a bashi hakuri ba,bai ta6ajin kalmar sorry daga bakinta ba,koda ace tayi mashi laifi sai dai shiya bata haƙuri ya rarrashe ta amma badai ita ba ae tafi ƙarfin wannan,amma yau ita da kanta take bashi hakuri!?_   Ganin yarda Abban nasu ke ta sakin murmushi yasa junaid cewa"Abba menene naga kamar farin ciki a fuskarka,"   Miƙa mashi wayar abban nasu yayi dama tsakaninsu babu 6oye 6oye,   "Junaid dubamin ka gani,kodai idona ne ke nunamin ba daidai ba,wai mommynku ce ke ban haƙuri da kanta,"   hannu junaid yasa ya kar6i wayar daga hannun Abban nasu ya shiga karanta saƙon,nan take yaji wani irin sanyi aranshi,    "Junaid baka ji farin cikin dana ji ba wlh,naji daɗin saƙon nan na mommynku,da ace bataban haƙuri ba da bansan a wani yanayi zan kwana ba yau,"   Murmushi junaid yayi bayan ya kammala karanta saƙon cike da zolaya yace"Su Abba an kusa angwancewa,amarya mommyn junaid zata dawo,amma dai Abba idan tadawo nigeria ba zaka kore ni daga kwana bedroom ɗinka ba ko?    Wani irin kallo abban nasu ya jefa mashi tare da cewa"Ae aranar da tadawo,zaka tattara yanaka yanaka kabarmin ɗakina,dama nagaji da kwana tare da ƙato a ɗakina.....'kasa ƙarasa maganar yayi saboda dariyar daya kwashe da ita,junaid kuwa tsuke fuska yayi yace"Allah Abba ba inda zanje ko mommy ta dawo,sai dai mu rinka kwana tare daku,ku sanyani a tsakiyarku muyi bacci atare," ashagwa6e ya ƙarasa maganar tashi,    harara abba ya watsa mashi tare da cewa"Allah ya kiyaye mu kwana tare da kai,"    Da buɗar bakin junaid sai cewa yayi"Abba kaima ya haramta a musulunce ka kwana tare da mommynmu......'tunkan ya ƙarasa maganar tashi,Abban nasu ya wawuro pillow tare da buga mashi asaman kanshi yana cewa"gidan ubanwa ka ta6a jin haka junaid?waya koya maka wannan kalamin ƙabihin?    dariya junaid ya shiga yi yana tarbe pillown da yake bugun shi dashi,gaba daya suka shiga yin wasan bugu da pillow shi da abban nasu,yarda kasan wasu ƙananun yara,sun jima suna shiririta kafin daga bisani bacci ya kwashe su gaba ɗayansu kowa hannun shi ruke da pillow, _💋Boss Bature💋_ Tun bayan da Jahad ta haɗo mashi abincin a tray,ta kawo mashi anan ƙasa ya sauko tare da hossana suka zauna,da kanshi ya dinga ɗebo abincin yana bata abaki tana ci,sai da ya tabbatar da taci ta ƙoshi sannan ya ƙyaleta,ya jima a wurinsu suna fira atare gwanin ban sha'awa kafin daga bisani wurin sallar isha'e yayi masu sallama da nufin zaije yayi sallah ya dawo kafin ya wuce gida, Lokacin da Omar ya dawo,bai same su a palourn ba babu kowa aciki,hakan ya tabbatar mashi da cewa sunyi bacci don yadan jima daya fita masallacin,tsayawa yayi yana tunanin ya tafi ko ya tsaya,harya juya yaji cewa bazai iya tafiya batare daya ƙara sanya Hossana a idanunshi ba,    juyawa yayi tare da nufar bedroom ɗinsu,a hankali ya tura door ɗin ɗakin,sannan yasa kai ya shiga da sallama abakin shi,    Sunyi nisa acikin baccinsu,hankalinsu kwance sai faman sharara bacci suke yi,kowaccen su na sanye cikin kayan baccinsu,jahad riga da wando farare,hossana kuma ƴar riga ce dai dai guiwa pink colour,sharara rigar take,saboda daɗin bacci ta hankaɗe rigar tayi sama hakan ya bayyana santala santalan cinyoyinta da suka ji hutu,dama bata iya kwanciyar bacci ba,    tsayawa Omar yayi yana kallonsu ta hanyar hasken Bedside lamps ɗin da suka kunna,sun haskaka wurin gadon nasu,yarda suke bacci cikin kwanciyar hankali ba ƙaramin kyau su kayi mashi ba,har ya yanke shawarar ya juya yabar bedroom din idonshi suka sauka akan laps ɗin hossana dake dan  kerma alamar sanyi ya kama kafafunta,kafin su kwanta sai da Jahad ta lullu6esu,cikin bacci hossana tayi wurgi da bargon gaba ɗaya,ya yi gefe guda can ƙasan ƙafafunsu,    ƙarasawa ciki omar yayi da nufin ya rufe su da bargon,amma tunda ya isa wurin gadon,ya gaza janye idanunshi daga kallon surar jikin hossana,abun da bai ta6a yi ba,tamkar ana ingiza shi zuwa gare ta haka ya dinga ji,nan take yaji wata irin ƙishirwar sha'awarta ta kama shi lokaci guda,gaba daya ya makance akanta har baisan lokacin da ya faɗa jikinta ba gaba ɗaya,ya shiga ƙoƙarin biyan buƙatarshi,tuni ya zame hannun rigar jikinta,ya sulale ta izuwa kasa har wurin stomach ɗinta,ba ƙaramin rikicewa yayi da gani booobs ɗinta ba,a cike fam suke tuni suka tsone mashi ido,gaba daya omar ya farmasu kyakkyawar damƙa yayi masu ya shiga murzasu a hannunshi,jikin shi har kerma yake yi,laushin su ba ƙaramin gigita shi su kayi ba hakan yasa yakai bakinsa gaba ɗaya,    A wani irin firgice hossana ta farka saboda raɗaɗin da taji kan nipples ɗinta,jin mutum asaman jikinta yasa ta fasa wata irin razananniyar ƙara mai sautin gaske tana faɗin"Jahad!!jahad!!nashiga uku!Abba zai cutar dani!dan Allah kadaina !ka bari!kada ka kashe ni mutuwa zanyi!dan Allah kabari Abba banso!!!!!gaba daya Omar baya a hayyacinsa ƙoƙarin zame belt ɗin wandonshi yake yi don ya cimma inda yake son zuwa,     Wannan ihun da hossana keyi ne ya farkar da jahad,a wani irin gigice ta yunƙura tare da miƙewa zaune tana kallon wannan tashin hankalin,kamar a mafarki haka take kallon Lamarin,saboda tsabar ruɗu bata gane fuskar waye ba,da hanzarin gaske ta dunƙule hannayenta tare da daddagewa ta ɗuma mashi dundu abayanshi,amma ko gizau Omar baiyi ba sai faman cigaba da abunda yake ƙoƙarin yi yake,    Fasa ihu jahad tayi tana faɗin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"gaba daya ta rasa ta yarda zata iya ceton Hossana,ƙoƙarin ruƙo shi ta shiga yi,aikuwa gaba ɗaya Omar yayi wurgi da ita,gaba ɗaya jahad ta gangara ta faɗa ƙasan gadon,kanta ba ƙaramin buguwa yayi ba,kafin jahad ta yunkura ta taso daga faɗawar nan da tayi,hossana ta daddage ta gartsa mashi cizo asaman damtse hannunshi,kusan sau uku tana cizon shi amma ko gezau baiyi ba,gashi harta fasa mashi fatar jikinshi,shaidar jinin harya fara fitowa ajikin farar shirt ɗin dake ajikinshi,   Ganin yana ƙoƙarin zame pant ɗin jikinta daya rage mata,yasa Hossana fashewa da wani irin sabon kuka tana cewa"Jahad kizo ki taimakeni!zai kashe ni!Abba zai cutar da rayuwata!Ya Omar bazai barka ba sai ya kashe ka........"idanunta na arufe take ambaton hakan yayin da hawaye ke 6ulbulowa daga cikinsu kamar an kunna fanfo,    Lokaci guda tunaninshi yadawo cikin hayyacinshi ta dalilin sunan shi da hossana ta ambata,zaro ido Omar yayi hankalinshi a matukar tashe yake kallon hossana daya raba ta da kayan jikinta,innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,A uzubillahi minasshaiɗanin rajim!!!shine abunda ya shiga ambata abakinshi,gaba ɗaya yabi ya gigice kanshi yashiga sara mashi da wani irin matsanancin ciwon kai,kunyar duniya tabi ta baibaiye shi,a hanzarce ya miƙe da saurin gaske ya fuce yabar bedroom ɗin,cikin sa'a batare da Hossana ta buɗe idanunta ba,kuma batare da jahad taganshi ba,dukansu babu wanda ya shaida shi,ƙaramin kuskure kan iya jefa mutum faɗawa tarkon shaiɗan,omar yayi danasanin dawowarshi cikin gidan,yayi danasanin shiga bedroom ɗinsu,in banda tsautsai da ƙaddara bai ta6a gigin shiga ɗakinsu ba sai yau,      Fucewarshi ke da wuya,jahad ta ɗago da kanta daga buguwar da tayi a ƙasa wurin harya ɗan fashe kaɗan,da saurin gaske ta haye saman gadon tana faman shessheƙar kuka,tsayawa tayi tana faman wurga ido cike da mamaki ganin babu mutumin nan dake ƙoƙarin keta haddin hossana,abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,6aat babu shi babu alamar shi,   Cikin sauri ta ƙarasa wurin hossana dake a kwance babu kaya ajikinta,da alama suma tayi saboda tsabar firgicin data shiga,     Hannu jahad takai tare da janyo bargo ta lullu6e mata jikinta,sannan ta rungumota ajikinta tana faman ambaton sunanta"Hossana!!hossana!!!"ganin ko motsi taƙiyi yasa hankalin jahad tashi,jijjigata tashiga yi tana cewa"Hossana ki farka dan Allah!!ki tashi!Allah yasa bai kaiga cutar dake ba!nashiga ukuna ni yau!meyasa haka ke faruwa dake ne?burin kowa yaga ya lalata maki rayuwarki hossana!meyasa bazasu barki kiji da abunda ke damunki ba!meyasa bai tunkare ni ba sai ke........'kasa karasa maganar tayi saboda kukan daya ciyota,mai raɗaɗin gaske,gaba daya ta fashe da matsanancin kuka tana cewa"Ya Allah kasa mafarki nake ba gaske ba!!Allah karka nunamin wannan ranar da zan rasa ƴar uwata!!hossana dan Allah ki tashi kada ki mutu kibarni.......'   Ganin ko motsi hossana taƙiyi yasa jahad sakinta tare da yin saurin saukowa daga saman gadon,da gudun gaske ta fito cikin falon tare da nufar telephone don ta kira Ya omar ɗinsu ta sanar dashi abunda ke faruwa cewa wani ya shigo musu cikin gidansu,    Hannunta har kerma suke yi wurin daukar telephone ɗin tare da danna numbers ɗinsa ta buga mashi kira,Allah Allah take akan ya ɗaga kiran ta sanar mashi saboda tsoran Kada mutumin ya ƙara dawowa,ga kuma hossana dake kwance araye ko amace,    Lokacin da kiran Jahad ya shigo wayar Marshall Omar,yana acikin motar shi bawan Allah,duk yabi ya takure yaji ya tsani rayuwarshi gaba ɗaya,kamar ya binne kanshi haka yake ji,wasu irin zafafan hawaye ne ke gangarowa daga idanunshi sai faman cizon la66anshi yake yi,idanunshi sunyi jawur,    Jikin Major ba ƙaramin sanyi yayi ba,saboda ya gane halin da Ogan nashi yake ciki,ga wayarsa sai faman ringing takeyi amma yaƙi ɗaukota bare yayi picking call ɗin,   A hankali major yayi parking ɗin motar tasu agefen titi ba don komai ba sai don baijin zai iya cigaba da driving yayin da oganshi ke cikin wani yanayi,    Ganin ya tsayar da Motar yasa Omar cewa"major meyasa ka tsayar da motar"?    Cikin sanyin murya major yace"ka gafarce yalla6ai,bazan iya driving ɗin bane,saboda gaba daya jikina amace yake,guiwowina sun sage tamkar anzare lakar jikina haka nake ji,bansan me ya faru dakaiba amma ina da tabbacin cewa wani abu mara daɗi ne yasaka shiga wannan halin da kake ciki,"    Muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"Major yau nayi abun kunya,naji kunya sosai kamar na binne kaine,ashe dama shaiɗan baida tabbas"?yayi tambayar yayin da zuciyarshi ke cigaba dayi mashi ƙuna,   Cigaba da magana yayi"major yau ni da kaina nayi attempting rape,kuma ba kowa nayi yunkurin aikata ma hakan ba face hossana.....' *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI.  MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.      *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Abban sojoji paid book ne,ga duk mai buƙatar karanta cigaban shi yayi mun magana kai tsaye ta number ta 08103884440 Whatsapp only banda phone calls, 300 ne only 🤝 Cigaba da magana yayi"major yau ni da kaina nayi attempting rape,kuma ba kowa nayi yunkurin aikata ma hakan ba face hossana.....'    Jin abunda omar yace yasa major cikin tashin hankali yace"Subhanallahi!!yalla6ai garin yaya hakan ya faru!nidai nasan cewa bayin kanka bane,na yarda dakai sosai,Ni shaidane akanka yalla6ai,kai da kanka kake hukunta masu aikatawa,kana ɗaya daga cikin mutanan dake daraja ƴa mace,ba zaka ta6a yin hakan abisa son ranka ba,"    "Major naji haushi sosai,zuciyata batamun daɗi,duk nabi na tsani kaina,nayi abun kunyar da bazan ta6a mantawa ba,indama na godema Allah yaran basu shaidani ba,da idanunsu da ace sun gane ni ne da nasan cewa duk wani girma na da suke gani zai zube ne,kuma zasu fara tunanin cewa ba don Allah na taimaki rayuwarsu ba...."    tsananin tausayinshi ne ya kama major,da yana da halin da zai cire damuwar dake acikin zuciyar ogan nashi da tuni yayi exchanging heart ɗinsu,ba don komai ba sai don ya tsani yaga marshal acikin wani hali na ƙunci,    daƙyar major ya kwantar mashi da hankalinshi ta hanyar yi mashi tausasan kalamai masu daɗin gaske har sai daya ga ya shiga natsuwarshi sosai sannan ya tashi motar suka nufi gida,    kuka sosai jahad keyi ganin tana ta jaraba kiran layin Omar amma ba'a ɗagawa,a ƙarshe ma da ta ƙara kira sai ta samu wayar a switch off,jiki asanyaye ta mayar da telephone din ta ajiye asaman table ɗin,    dafe kanta tayi saboda wani irin raɗaɗi da taji yana yi mata,gaza tsayawa tayi da ƙafafunta nan take ta yanke jiki ta faɗi ƙasa asume, Tashin hankalin da ba'a samashi date!a can 6angaren sehrish ta sume,anan 6angaren kuma hossana da jahad sun sume,ko mai zai biyo baya? Wuraren ƙarfe 1:30 na dare,Ayaan na kwance cikin kayan baccinsa,yaji hannun mutun acikin wandonshi,a firgice ya farka tare da ware idanunshi akan wanda ke lalubar jikin nashi,ganin jahan asaman jikinshi yasa yayi hanzarin yin wurgi dashi gefe guda ya tashi zaune rai a6ace yace"Jahan!banason wannan wasan!karka kuskura ka ƙara ta6a jikina in ba......'bai ƙarasa maganar ba saboda haɗe bakinsu da jahan yayi wuri guda yashiga ƙoƙarin zura harshen shi acikin bakinsa,    Hankali tashe Ayaan ya rurruƙe shi yana kiciniyar kwace kanshi daga hannun jahan amma abun yaci tura,kamar wani zombie haka ya koma mashi, Muryarshi har shaƙewa takeyi wurin cewa"Ja...ja..jahan!ka rabu dani!wai meyake damunka ne!baka da hankaline kasan me kake ƙoƙarin yi mun ne,yayi maganar tare da janye jahan daga jikinshi yana kallon shi,    Wata irin zuface ke gangarowa daga cikin sumar kanshi saboda tsabar jarabar da yake ji,   A kasalance yace"ayaan kadaina mun wasan nan,kasan fa abunda nake buƙata awurinka,ka bani haɗin kai kamar yarda muka saba,baka ji yadda nake ji ba ajikina....'Ya ƙarasa maganar yana faman lumshe idanunshi,   Ayaan kuwa kallonshi yake yi gwanin ban tsoro,lokaci guda kuma ya tuna komai yace"Jahan kayi haƙuri bazan iya ba,na ƙyamaci abun acikin zuciyata,ya fita raina gaba ɗaya,bazan iya cigaba da aikata wannan mummunan zunubin ba,bayan Allah ya yaye mun,idan harna biye maka muka aikata hakan,hukunci zai hau kaina,Allah bazai......'kafin Ayaan ya ƙarasa maganar tuni Jahan yayi kukan kura ya afka mashi,don bazai juri sauraron kalamanshi ba,saboda a ƙagare yake daya kawar da muguwar sha'awar data taso mashi mai tare da wani irin raɗaɗi,   Dambe suka shiga yi atsakaninsu,jahan na ƙoƙarin zame ma Ayaan kayan jikinshi,yayin da Ayaan ke ƙoƙarin kufcewa daga hannunshi ya gudu,wani irin ƙarfi jahan ke ji gaba daya ya zauce ya fara fita hayyacinshi burinshi ya biya mashi buƙatarshi,kafin wani lokaci jahan ya yayyaga ma Ayaan rigar jikinshi,yayi mata kaca kaca,ruƙo wandon jikinshi yayi tare da janshi ya zame gaba ɗaya,ya rage daga shi sai short ajinshi,a lokacin ya tattara dukkan wani ƙarfin shi yayi wurgi da jahan gefe guda saman gadon,sannan da gudun gaske ayaan ya sauko daga saman gadon ya faɗa cikin toilet ɗinsu tare da rufe ƙopar,yana faman sauke ajiyar zuciya,a bakin kopar ya tsaya tare da kasa kunne yana sauraran gurnanin da Jahan keyi,   tsigar jikinshi ce ta soma tashi tsaitsaiye,nan take idanunshi sukayi wani irin ja tamkar garwashin wuta,saukar bulali ya dinga ji ta ko'ina abayanshi nan take yabi ya gigice ya dinga sakin ihu yana kuka mai cin ran,   Runtse ido Ayaan yayi wani irin tausayin shi ne ya kama shi,saboda yasan irin halin da suke shiga aduk lokacin da basu kusanci junansu ba,tabbas Jahan bazai rayu ba muddin bai bashi haɗin kai ba,fashewa da kuka Ayaan yayi tare da sulalewa ya zukunna abakin ƙopar toilet ɗin yana faman shassheƙar kuka,   Yana jiyo yarda jahan ke ta faman ihu yana kuka,akan kunnanshi yaji sautin faɗowar jahan daga saman gadon,ta hanyar sautin da yaji timmmmmm!   rarrafowa jahan yayi daƙyar yake jan jikinshi har ya isa bakin ƙopar toilet din,muryarshi na kerma yace"Ayaan yau kai da kanka kake guduna!bayan kasan irin halin da muke shiga aduk lokacin da bamu aikata hakan atsakanin junan mu ba!so kake na mutu ko"? daƙyar sautin maganarshi ke fita,maƙoshin shi tuni ya jima da bushewa ƙamas,numfashinshi daƙyar yake fita, Cikin muryar kuka Ayaan yace "am really sorry jahan,ina mai matukar takaicin gaza taimakonka a wannan lokacin,zanyi kuka sosai in na rasa ka jahan,bani da tamkarka aduniyar nan,ina tsananin kaunarka sosai ɗan uwana,kayi haƙuri ka yafe mun........"kasa ƙarasar maganar yayi saboda kukan daya ciyoshi,    tamkar zaiyi hauka haka ya dinga ji,gaba daya rayuwarshi tashiga cikin ƙunci,idonshi ya makance,makoshin shi ya bushe,ya rasa duk wani kuzarin jikinshi,lokaci guda ya zama zautacce yabi ya burkice sai faman magiya yake yi ma Ayaan ya taimaka ma rayuwarshi amma ina Ayaan sam yaƙi buɗewa bama alamar zai buɗe, Wani irin sauti Jahan ya shiga fitarwa tamkar ranshi ne ke fita,hakan ba ƙaramin gigita Ayaan yayi ba,muryar jahan yaji ƙasa ƙasa yana cewa"Ayaan maƙoshina ya bushe!mutuwa zanyi ka taimakamin da ruwa insha,"agalabaice yake maganar,   Da hanzarin gaske Ayaan ya buɗe ƙopar ɗakin,anan yayi arba da Jahan baje ƙasa rai hannun Allah jikinshi sai karkarwa yake,wasu irin sahun bulali ne a jikinshi ta ko'ina ga shaidarsu nan asaman farar fatar jikinshi,dama babu kaya ajikinshi iya gajeran wando ne ya bari,    ɗaga ƙafa ayaan yayi zaije ya ɗauko mashi ruwan,kamar daga sama yaji jahan ya ruƙo kafarshi da ƙarfin gaske nan take ya kife ƙasa timmmm,jan jiki Jahan yayi tare da hayewa saman jikin Ayaan ya ƙankame shi ruƙo bana wasa ba,sannan ya shiga biyan buƙatar shi,wa'iyazubillah!wannan wata irin masifa ce!   Gaba ɗaya jahan ya gama kashe mashi jikinshi,ko hannunshi bai iya ɗagawa,babban abunda yake tsoro kada wani ya faɗo ya same su acikin wannan yanayin da suke,    kiciniyar kwace kanshi ya shiga yi da iya ƙarfinshi na karshe amma hakan ya gagara,a ƙarshe daya rasa yadda zaiyi saiya daddage ya garza ma jahan cizo asaman ƙirjinshi,ko gizau baiyi ba,    wani irin juyi Ayaan yayi anan ya samu nasarar hankaɗe jahan yayi gefe guda ƙasa,shi kuma ya tashi cikin sauri yana gyara short ɗin jikinshi,       Har yasa ƙafa zai bar ɗakin,yaji gabanshi yayi wani irin mugun bugu,cikin sauri ya juya tare da kallon jahan da idanunshi ke kallon sama,kwata kwata baya motsi komai nashi ya tsaya cak da yin aiki,waro ido waje yayi da hanzarin gaske ya koma wurinshi tare da zubewa saman guiwar ƙafafunshi yana ambaton sunanshi hankali a matukar tashe!   "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Jahan!jahan!don Allah kayi magana!ɗan uwana kada ka mutu ka barni!bana fata ace ni nayi silar barinka duniya!na cuce ka jahan nagaza cetonka!ka yafe mun ba laifina bane!"    Kuka sosai Ayaan keyi yana jijjiga jikin Jahan,bai da wata mafita a halin yanzu,ji yake tamkar ya watsa aguje yaje ya sanar ma su Abbansu halin da ake ciki,amma fargabar kada ace jahan ba mutuwa yayi ba,in har hakan ta faru to tabbas zai iya farkawa agabansu ya cakume shi ya shiga ƙoƙarin biyan bukatar shi agabansu,tunda baya acikin hayyacinshi,    Yasha kuka sosai kamar kamar me,a ƙarshe ya yanke shawarar zuwa ya ɗauko ruwa don ya yayyafa mashi ajikinshi ya ga ko zai farka,   A hanzarce ya miƙe tare da kama hanya ya fuce daga cikin bedroom din,   Sauri yake yi tamkar zai tashi sama aranshi sai addu'a yake yi Allah yasa jahan ba mutuwa yayi ba, Fitar shi ke da wuya daga cikin bedroom din nasu,Haroon ya faɗo cikin ɗakin afusace don yayi masu magana akan Money bag ɗinsa da yake zargin su suka ɗauke shi,koda yayi arba da jahan kwance aƙasa baya motsi,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,ta6e baki yayi tare da shigewa ciki,ya zukunna adaidai inda jahan ɗin yake kwance,yakai hannu tare da shafa ƙirjinshi,da yake shu'umine,nan take ya gane awane hali jahan yake,    sunnar da kanshi yayi tare da haɗe bakinshi wuri ɗaya dana jahan,zura tongue ɗinshi yayi acikin bakin jahan,aikuwa awani irin yanayi Jahan yayi motsi alamar yaji abunda yakeso,batare da 6ata lokaci ba Haroon ya shiga biya mashi buƙatar shi,      Ayaan na ƙarasawa wurin fridge ɗin yasa hannu tare da buɗewa cikin sauri,hannu yakai cikin jerin bottles water ɗin dake a jere cikin frigde ɗin,har zai ɗauki robar ruwan swan idon shi ya sauka akan Robar ruwan addu'ar nan da junaid ya ajiye ta sehrish,bakomai ne yaja hankalin shi akan robar ba,face rubutun Larabcin dake rubuce ajikinta,tunda akeyi masu order na abunsha,ba'a ta6a kawo masu kalar robar ruwan nan ba,mai rubutun labarabci ajikinta,zubama robar ido yayi yana kallonta nan take abunda ya faru ɗazu ya faɗo mashi aranshi,wasiwasi Ayaan yashiga yi acikin ranshi yana cewa"wannan roban ruwan kamar itace na ɗauka ɗazu nasha!kuma tunda nasha ta komai nawa ya canza,tabbas ina tunanin cewa tana tattare da wani abu ajikinta,amma kuma waye ya ajiyeta indai haka ne?don ina da tabbacin cewa ba'a kawo mana kalar wannan bottle water ɗin acikin gidan mu!bari na jaraba kaima Jahan ya sha,tanan zan gane abunda ke tattare da robar ruwan nan!"   Yana ƙarasa zancen zucin nashi batare da 6ata lokaci ba,ya sungumi robar ruwan a hannunshi,bayan ya rufe frigde ɗin,da saurin gaske ya wuce part ɗinsu,   Yana gab da shiga bedroom ɗin nasu,ya dinga jin wani irin gurnani mara daɗin ji,a wani irin tsorace ya afka cikin ɗakin,waro idonshi waje yayi saboda tsabar 6acin rai baisan sa'adda yayi wurgi da Robar ruwan dake a hannunshi ba,nan take ta faɗi ƙasa tana gangarawa murfinta ya cire,ruwan cikinta ya kwarare ƙasa gaba ɗaya,    A fusace ya ƙarasa tare da damƙar rigar haroon da iya ƙarfin shi na ƙarshe yayi wurgi dashi gefe guda,ɗagowa haroon yayi yana kallon Ayaan da idanunshi waɗanda suka canza launi izuwa jawur dasu,sai faman lashe bakinshi yake kamar wani tsohon maye,    Rai a6ace ayaan yace"wai kai wani irin daƙiƙin mutum ne dabba!kuma jahili wanda baisan ciwon kanshi ba!mugu azzalumi kawai,banta6a ganin fasiƙin mutum irinka ba!wanda baya tsoran Allah!"ran Ayaan ba ƙaramin 6aci yayi ba,yana magana hawaye na gangarowa daga idanunshi masu zafin gaske,    Duk a tunaninshi haroon zai ji haushin kalamanshi,amma abun mamaki fuskarshi ɗauke da wannan shu'umin murmushin nashi yace"Kwantar da hankalin ka mana!nifa ceton rai nike,duk irin son da kake ma Jahan ka gaza taimakon shi,kana ji kana gani zai mutu,ni kuma bazan so haka ba saboda inason ɗan uwana,shiyasa nayi hakan don na cetoshi daka halaka......'   Tunkan ya ƙarasa maganar Ayaan ya daka mashi tsawa tare da cewa"Karka kuskura ka ƙara ambaton sunan jahan a matsayin ɗan uwanka!kai ba jinin mu bane,mutun mai halin dabbobi irinka bazai ta6a zama jinin mu ba,yanzu bana doubting akan haka,Haruna kai ba ɗan uwanmu bane!ka wulaƙanta rayuwarmu,Allah ba zai ta6a barin ka ba,ƙarshen ka bazai yi kyau ba haroon!tun wuri ina baka shawarar ka tattara kayanka kabar gidan nan tun kafin lokaci ya ƙure maka!!!!"    fashewa da dariya haroon yayi,a yayin da yake miƙewa tsaye daga zaunen da yake a ƙasa,takawa yayi izuwa wurin da Ayaan yake sannan yace"naji duk bayananka akaina,kuma naji shawarar da ka bani,inaso ka sani cewa ko kaɗan banji tsoro akan kalaman da kayimun ba,ka ajiye wannan zamuyi magana akanshi,abun da ya kawoni ɗakinku shine Jakar kuɗin Da kuka kaimun ban ganta ba,an ɗauke ta daga ɗakina,kuma ba kowa nake zargi ba face ku,saboda ku kaɗae kukasan da zancen kuɗin,bayan ku babu wani da yasan da maganar!!ina jakar kuɗina take!!"     takaici ne yasa Ayaan kasa yin magana tabbas da ace yana da halin kawar da haroon da tuni yakai shi inda ya dace,    Cike da takaici Ayaan yace"maganar ɗauke jakar kuɗinka sam bata shafe mu ba,don haka tun wuri ka nemi wanda ya ɗauke maka kuɗinka!idan ma kanaso kayi amfani da wannan damar ne don kayi mana wayau ka ƙara samun wasu kuɗin awurinmu to inaso ka sani cewa ko sisi bazasu ƙara fitowa a wurin mu ba!bazamu baka ba!kaje kayi duk abunda kaga dama,'   Wani irin huci haroon ya runƙa fitarwa yana kallonshi yace"Kadaina yi mun magana A gadarance!taƙamarka kun goge videon dake a wurina to inaso ka sani cewa akwai wani videon a wurina!ni ba shashasha bane kamar yarda kukayi tunani!dama sai da raina ya bani cewa akwai wata ƙullalliyar da kuka shiryamun,don haka muddin baku dawomun da jakar kuɗina ba saina fallasa ku Uban kowa yaga abunda kuke aikata........'bai ƙarasa maganar ba saboda Ayaan daya kwashe da wata irin mahaukaciyar dariya,nan take kan haroon ya ɗaure yashiga mamakin dalilin dariyar ta Ayaan,   Sosai Ayaan yake 6a66aka dariya kamar kamar me,hada dafe cikinshi,tashin hankalin da ba'a sama shi date,kwatsam yake zuwa,   duk wannan surutan da suke yi Jahan yana kwance a ƙasa sai faman juyi yakeyi saboda raɗaɗin da cikinshi ke yi mashi,sam baya acikin hayyacinshi,saboda he isn't satisfied,    "Me kake yi ma dariya"?haroon ya jefa mashi tambaya,   tsagaitawa da yin dariyar yayi yana Girgiza kai yace"Haroon ka gama yawo!wlh ka mutu!kai baka da tunani ne,bazan baka satar amsa ba,amma kaje kayi tunanin waye ya ɗauki jakar kuɗin nan!taya akai wani yasan da zancen jakar kuɗin nan har ya bi ɗakinka ya ɗauke ta!junaid kaɗae ne ya shigo cikin bedroom ɗinka a lokacin da muke tattaunawa,kuma kasan cewa junaid baya acikin sense dinshi ya shigo,koda ace yana cikin hayyacinshi bazai iya ɗaukar maka jakar kuɗin nan ba!to waye ya ɗauki jakar kuɗin?mu dai bamu bane!"?   shiru haroon yayi yana kallonshi gaba ɗaya ayaan ya burkita mashi tunaninshi,hakanan ya dinga jin gabanshi na faɗuwa,bai ƙara tanka ma Ayaan ba,cikin sauri ya kama hanya tare da fucewa daga ɗakin, Ajiyar zuciya Ayaan ya sauke,jin hannun mutum a ƙafarshi yasa yayi hanzarin kai idanunshi ƙasa yana kallon Jahan dake ta faman fitar da numfashi sama sama,hankali tashe ya shiga neman robar ruwan daya shigo da ita acikin ɗakin,can ya hangota ta gangara wurin shoe rack ɗinsu,murfinta ya cire ga ruwan ciki ya malale ƙasa,dafe kansa yayi da hannunshi na hagu cike da takaicin ruwan daya zube,    ƙokari jahan yake yayi mashi magana akan ya kira mashi Abbanshi karya mutu baisa shi a idanunshi ba,amma kwata kwata sounds ɗin bai fitowa abakinshi,ko idonshi bai iya budewa bare ya iya yin magana,gaba ɗaya Ayaan ya rasa yarda zaiyi,kanshi ya gama kwancewa,kamar yayi hauka haka yake ji,yana cikin wannan yanayin dubara tazo mashi,juyawa ya kuma yi yana kallon roban ruwan,Ruwan ya malale gaba ɗaya kasa ya tattaru a wuri guda,    Da saurin gaske ya ƙarasa wurin robar ruwan,tare da zubewa saman guiwowinshi,hannu yakai tare da ɗago da robar ruwan ya zaunar da ita ta tsaya tsaye,sannan cikin sauri ya sanya tafukan hannayenshi tare da kwalfo ruwan acikinsu,ya dinga zubasu acikin robar,yana ɗebowa wani na zubewa ahaka ya samu ya ɗan tara kaɗan wanda bai wuce ayi mashi kur6a uku ba ya ƙare,    ɗaukar robar ruwan yayi da sauri ya koma wurin jahan tare da zuƙunnawa agabansa,sannan yasa hannunshi na dama asaman lips ɗin jahan yana ƙoƙarin buɗe bakinshi,ya rufe bakin gam,hakan yasa Ayaan ya gaza samun damar buɗe mouth din nasa,   tsoranshi kar ace jahan ya mutu,saboda yayi delaying wurin kawo mashi taimakon gaggawa,   "Jahan pls,ka buɗe nasamo maka ruwan ka sha!banaso na rasaka ɗan uwana,"muryar shi tamkar zaiyi kuka haka ya dinga rokon shi akan ya buɗe bakin nashi ya sanya mashi ruwan,amma ko motsi wannan baiyi ba,   hannunshi har kerma yakeyi wurin ɗaga robar ruwan ya kaita saitin idanunshi yana duba rubutun dake ajikinta,larabci ne kuma shi baijin harshen larabci,balle ya gane me aka rubuta ajikinta,   Ganin zai rasa ɗan uwansa yasa ya ajiye robar ruwan ƙasa,sannan ya daddage da iya ƙarfinshi na ƙarshe ya sanya dukkan hannayenshi biyu ya shiga ƙoƙarin buɗe bakin Jahan,cikin sa'a bakin ya ɗan saki,da sauri Ayaan ya ɗauko robar ruwan tare da kafata a bakin Jahan nan take ruwan ya dinga shiga acikin bakinshi daƙyar daƙyar,wani na shiga wani na fita,ahaka yasamu ya bashi,bayan ya kammala yayi wurgi da robar ruwan gefe guda,sannan ya zauna tare da zabga tagumi yana jiran ganin sakamakon da zai biyo baya,hawaye sai shararo mashi suke a idanunshi,aranshi yana cewa"idan na rasa jahan bansan ya zanyi da rayuwata ba,nima zan bishi ne kawai,"    Yayi maganar tare da runtse idanunshi yana matse hawayen dake fita daga eyes ɗinshi,   Kafin Ayaan ya ankare,wannan baƙin hayakin ya soma kurɗaɗowa ta cikin ƙofofin hancin jahan,yarda kasan an koro shi daga cikinsa,haka ya dinga fitowa kafin kiftawar ido,hayaƙin yayi disappearing gaba ɗaya,tamkar bai ta6a existing ba,     Fitarsa ke da wuya,zufa ta soma tsastsafowa a jikin jahan,kamar an watsa mashi ruwa ajikinshi,haka zufar tashiga feso mashi,a hankali bakinsa ya buɗe ya shiga ambaton"La'ila ha'illallah!    A wani irin firgice Ayaan ya ware idanunshi sai lokacin ya kalli jahan dake kwance zufa ta gama wanke mashi jikinshi,wani irin farin ciki ne ya cika Ayaan la66ansa har rawa suke yi wurin ambaton sunan shi"ja..jahan"   Amsa mashi yayi da"Na'am," "Alhamdulillah!Alhamdulillah!Allah na gode maka!" Ayaan ne ke faɗin hakan yayin da yakai hannunshi yana tatta6a fuskar jahan dake ƙoƙarin buɗe idanunshi,     Tunani yazo ma Ayaan aranshi yace tabbas Ruwan cikin robar can ba normal ruwa bane da suka saba sha,akwai wani abu atattare dashi,tun da gashi Yaba jahan yasha kuma ya tashi da irin yanayin daya tashi dashi ɗazu da rana daya sha ruwan,ya tashi yana zufa kuma shima Jahan gashi zufar ce ke fita,hakan na nufin cewa shima Jahan ya warke kenan,   Ƙarasa tunanin nashi yayi tare da kai goshinsa ƙasa yayi sujjada yana ma Allah godiya,🥰    Bayan Jahan ya gama farfaɗowa,Ayaan ya taimaka mashi wurin kaishi toilet yayi wanka,nan take yaji wata irin natsuwa ajikin shi,basu 6ata lokaci ba wurin hayewa saman gadonsu,tare da lullu6ewa da bargo saboda baccin da kowannansu ke ji,yau gaba dayansu sunyi bacci cike da kwanciyar hankali,kuma Ayaan Yaci alwashin sai yayi investigation akan wannan robar ruwan da suka sha, (Banji daɗi da ruwan addu'ar nan ya zube ba,wlh nima ina buƙatar shi don nasha) Yanayi mara daɗi,a daren ranar Omar ya kwana yana kukan zuciya saboda abunda yayi ƙoƙarin aikata ma Hosana, ya kwana da tunanin wane hali suke aciki?sunyi bacci kuwa?baida amsar tambayoyin shi dole sai inya gansu,gashi baya jin zai iya takawa yaje dubasu saboda fargabar karsu gane cewa shine yayi masu wannan abun kunyar,matsananciyar damuwar daya sa ma ranshi ne da tunane-tunane ya haifar mashi da wani irin severe headache na 6arin kai,yaji jiki adaren nan har magani yasha amma bai sauka ba,a haka ya kwana yana juyi asaman gadonsa,   Adaren ranar nan dai abubuwa dayawa sun faru masu daɗi da marasa daɗin ji,dama haka rayuwa take ba kullum ake jin daɗin ta ba,idan yau anyi farin ciki,gobe zai iya kasancewa baƙin cikine,idan yau anyi dariya gobe zai iya kasancewa kuka ne,haka rayuwar ke tafiya babu wani yanayi da yake kasancewa permanently,Allah yasa mu dace,yasa mu fi ƙarfin zuciyoyinmu,kuma ya kare mu daga aikata aikin danasani,wasu sun ɗauki rayuwar duniya wani abu,da har suka ɗauke ta da zafi suna aikata abunda suka ga dama,sun manta da cewa acikin seconds za'a iya zare ransu su bar duniyar gaba ɗaya suje su fuskanci abunda suka shuka,duka nawa ne jin daɗin duniyar?basa tuna donme aka halicce su,ta wace ƙopa suka faɗo duniyar nan,taya zasu koma ga mahaliccinsu?daga kai fa sai likkafaninka za'a binne ka cikin ƙabarinka,sai kuma halinka daka je dashi,na gari ne kona banza,😢Allah yasa mu cika da kyau da imani🙏 Wuraren sallar Asuba Sgr ya farka daga dogon baccin daya ɗauke shi,a hankali ya buɗe eyes ɗinshi,yayin da bakinsa ke ambaton addu'ar tashi daga bacci,a kasalance ya miƙe daga kwancen da yake saman doguwar kujerar,mamaki ne ya kama shi ganinshi kwance a palour ɗinsa yana bacci instead of saman gadon shi,ya jima yana mamakin yarda bacci yayi awon gaba da shi adaren jiyan nan,sauko da ƙafafunsa yayi ƙasa,idanunshi suka sauka akan tray ɗin da sehrish ta kawo mashi na dinner ɗinsa da baici ba jiya,tsayawa yayi yana ƙoƙarin tuna abunda ya faru adaren jiya,yunƙurawa yayi tare da tashi tsaye daga saman sofa din ya soma takawa walking slowly,jin sul6in wani abu a ƙasan tafin kafarshi yasa shi yin saurin kai idonshi wurin yana kallo,mamaki ne ya kama shi ganin Mayafin yarinyar nan yashe a kasa,yasan cewa shiya cire mata mayafin amma abunda ya ɗaure mashi kai zaman me gyalenta keyi acikin part ɗinsa?    russunawa yayi tare da kai hannunshi ya ruƙo gyalen tare da ɗagowa dashi yana kallon shi,sai lokacin ya tuna abunda ya faru jiya tsakanin shi da ita,na commanding ɗinta da yayi akan tayi tsallen kwaɗi,to ina yarinyar take,tambayar daya jefa ma kanshi kenan,    Cikin sauri ya zagayo ta bayan sofas ɗin tunkan ya ƙarasa ya hangi yarinyar kwance magashiyyan a sume bata motsi,tasha wahala sosai sam baiyi tunanin cewa zata cigaba da yin frog jump ɗin ba,yasan ba komai ne yaja hakan ba face tsananin tsoronshi da take ji,shiyasa bata yi tunanin ta tafi ba,tunda taga bacci yayi awon gaba da shi,      A hankali ya ƙarasa takawa inda take sannan yaɗan zuƙunna agabanta yana kallon sumar kanta data rufe mata fuskarta,hannu yasa tare da ruƙo gashin kan nata,ya janye mata shi daga saman fuskarta ixuwa gefe guda,    Zuba ma kyakkyawar fuskarta ido yayi yana kallon yarda tayi jaga jaga da hawaye duk ta yamutse saboda kukan da tasha,idonta sun kumbura,haka la66anta ma sunyi suntum dasu,tsananin tausayinta ne ya kama shi,baiji daɗin baccin daya ɗauke shi ba,da baibari tasha wahalar nan ba,ba da nufin ya cutar da ita yayi hakan ba,kawai yaso ya ɗan hukuntata ne donta kiyaye shi sosai,     miƙewa yayi tare da nufar wurin fridge ɗinshi,ya buɗe ya ɗaukko bottle water daga ciki mai sanyi,sannan ya dawo inda sehrish take ya cire murfin tare da ɗebo ruwan a hannunshi ya yayyafa mata shi a fuskarta,ruwan na sauka asaman fuskarta,taja dogon numfashi tare da sauke nannauyar ajiyar zuciya,a hankali tashiga mutsu mutsu zata buɗe idanunta,    "Get up" yace,jin muryarshi yasa sehrish ware idanunta akan sgr dake zuƙunne agabanta,jikinta har kerma yake yi wurin yunƙurawa tare da tashi daga kwancen da take ta zauna,tun kafin taji me zaice ta shiga bashi haƙuri tana cewa"dan Allah ka yafe mun babban yaya,bazan ƙara maimaita kuskuran da nayi....,.'    Kasa ƙarasa maganar tayi,a firgice ta shiga girgiza mashi kai ganin yadda ya ɗago da hannunshi,duk a tunaninta marinta zaiyi amma sai taga akasin hakan,a hankali ya aza tafin hannunshi a saman lallausar fatar gefen fuskarta,ɗan zaro ido sehrish tayi tana kallon fuskarshi,yayin da shi kuma yake kallon brownish lips ɗinta dake ta faman kerma,    Almost 5 mins sannan yace"Tashi ki tafi,"ya ambaci hakan tare da zame hannunshi daga gefen fuskarta sannan ya miƙe tsaye hannunshi ruƙe da bottle water ɗin yana maida murfin robar,daddagewa sehrish tayi tare da yunƙurawa daƙyar ta miƙe,aikuwa nan take ƙafafunta suka bada wani irin sauti ƙasss!,a gigice ta saki wata irin razananniyar ƙara nan take ƙafafun suka gaza ɗaukarta,gaba ɗaya ta tafi zata kife ƙasa,sai dai ina kafin takaiga ƙasan tuni hannun sgr ya damƙi qugunta kwakkwaran ruƙo yayi mata da hannu ɗaya,gabanta ne taji yayi wani irin bugu daga bisani kuma ta shiga sauke ajiyar zuciya ba ƙaramin tsorata tayi ba,har lokacin hawaye ne ke zubowa daga cikin idanunta,janyota Sgr yayi ta faɗo saman jikin shi gaba ɗaya,sannan ya ɗan russinar da kanshi tare da ɗago da ita,ya sanyata a saman kafaɗarshi,yadda kasan ya ɗauki wannan ɗiyar robar ƴar tsana,haka ya sa6i sehrish asaman shoulder ɗinshi,tafiya ya soma yi ɗauke da ita,ya ƙarasa wurin fridge ɗinshi tare da ajiye roban ruwan dake hannunshi,sannan ya juyo tare da kama hanya ya fito daga part dinshi kai tsaye ya nufi downstairs,ajiyar zuciya sehrish ke ta faman saukewa tayi lamo abunta,yadda take jin daɗin kafaɗar tashi tamkar ta hau Jirgin sama,    A natse yake taka matattakalar benen ɗauke da ita har ya ƙarasa saukowa da ita cikin Main palour ɗin nasu,bin ko'ina yayi da kallo babu kowa da alama basu kammala shirin zuwa yin sallar asubahin ba,duk da dama lokaci bai ƙarasa yi ba,a lokacin ake ta haramar fara kiran sallan, Tunani ya shiga yi a ina zai sauke yarinyar,don shi bai ta6a sanin ma a ina yarinyar take rayuwa acikin gidan ba,har wani lumshe ido sehrish take yi saboda yanayin da ta shiga wata irin kasala ga baccin da take ji,ta gaza yarda cewa sgr ne da kanshi ya sa6ota asaman kafaɗarshi,jin abun take kamar a mafarki,duk da halin da take ciki amma har addu'a take yi cikin ranta Allah yasa dagaske ne ba mafarki bane,    Yana cikin wannan tsayuwar ɗauke da sehrish a kafaɗarshi,kwatsam Abbansu ya fito daga bedroom ɗinshi ya tunkaro main palour din,sai faman sauri yake yi don yaje ya tashi sauran su tashi su kimtsa lokacin sallah yayi,tunɗazu yake trying numbers ɗinsu don ya tashe su amma mutum ɗaya ne kawai yayi picking call ɗin,wato kanal yousouf,amma sauran babu wanda ya ɗaga alamar basu tashi daga bacci ba,    Da wa Allah ya haɗa shi?ae yana fadowa babban falon karaf idanunshi suka sauka akan Sgr dake ɗauke da Sehrish a kafaɗarshi,har sai da gabanshi ya faɗi,cikin sauri Abba ya ɗan ja da baya saboda kar Sg rafayet ya ganshi,har wani murza idonshi yake yi da hannayenshi don ya ƙara tabbatarwa da kanshi abunda yake gani,wai ko idanunshi ne ke nuna mashi ba dai-dai ba,lamarin ya ɗaure mashi kai,tsananin mamaki ne matuƙa ya kama shi,har ƙara leƙawa yake yi don ya tabbatar ma kanshi wanene acikin matasan nashi ya ɗauko mace a kafaɗarshi,    Hasken fatar sgr,da kuma wannan doguwar ƙirar tashi ne suka tona mashi asiri,uwa uba doguwar sumar kanshi,   Doubting ya shiga yi yana cewa"Anya kuwa shine?kodai idona ne ke nuna min ba dai dai ba,kodai tsufa ne yazo mun gadan gadan harya sa nake ganin hakan!kai wannan fa Rafayet ne ba wani ba,yarinyar daya ɗauko a kafaɗarshi kuma wannan yarinyar ce sehrish!ita kaɗae ce ƴar matashiya acikin gidan!idan har zargina ya tabbata toh me ya haɗa shi da yarinyar ne harya ɗaukko ta saman kafaɗarshi?Hakan na nufin a bedroom ɗinshi ta kwana"? Ya jefa ma kanshi tambaya,gaba ɗaya ya kuma ruɗewa,   Can dai yace"Ina yi mashi kyakkyawan zato,amma tabbas akwai alamar tambaya anan!"   Shiru ya ɗanyi yana ƙara leƙensu,abunne ya daure mashi kai sosai tunda yake bai ta6a ganin sgr da mace haka ba,aranshi ya shiga cewa kodai Ya fara kula mata ne?wata'ƙil akwai wata alaƙa atsakanin shi da yarinyar,'   Jinjina kanshi yayi tare da cewa"Biri yayi kama da mutum tabbas!sai yanzu na gane inda ya samu jan baki asaman ƙirjinshi,Oh ni hussein ina nan sake da baki ana mun aika aika acikin gidana!nagode ma Allah daya nunamin wannan abu akan idona,nasan me zanyi!"   Yana fadin hakan ya juya tare da komawa part ɗin nasu,don ya tashi sauran dama Upstairs ya nufa don ya tashi Omar,abunda yasa ya koma saboda baison sgr ya ganshi ya gane cewa ya ganshi ɗauke da Yarinyar a kafaɗarshi,    Jin takun tafiya yasa Sgr juyawa don yaga wanene,Azmee ce ta fito tana ta faman ƴan waige-waige,bakomai ne ya fito da ita ba face neman Sehrish, taje bedroom ɗinta donta tashe ta daga bacci taga babu kowa,hakan yasata fitowa don ta nemeta acikin gidan,    "Ke,zonan,"a ɗan firgice Azmee ta kallo inda yake,dama tunda taji an ambaci hakan tasan cewa Sgr ne,saboda shi kaɗai ke mata wannan kiran kai tsaye kamar wata ƙaramar yarinya,ko sunanta bai iya faɗi sai dae ke,don shi a yadda ya ɗauka duk wata mace ƙarama take awurinshi,   Fargaba ta shiga yi,ganin Sehrish kwance a kafaɗarshi,zullumi ta shiga yi acikin ranta,tsoranta kar ace wani abu ta aikata masa,    ƙarasawa tayi kusa dashi murya na rawa tace"Gani yalla6ai," Ko uffan baice mata ba,a hankali ya saukko da sehrish daga saman kafaɗarshi ya tsayar da ita akan ƙafafunta dake ta faman kerma,cikin sauri Azmee ta ruƙo hannunta,hankali tashe take kallonta ganin yadda ko'ina na jikinta ke kerma,cike take da son jin me ya faru da ita,Me ya haɗata da sgr da har ya ɗaukkota haka asaman kafaɗarshi,    Juyawa sgr yayi cikin sauri ya haye saman stairs da sauri da sauri yake taka steps ɗin sai da yakai step na ƙarshe sannan ya ɗan tsaya kamar mai nazarin wani abu, A lokacin azmee ta ruƙo sehrish tana taimaka mata wurin yin tafiya,a hankali a hankali suka nufi part dinsu,gaba ɗaya sehrish taji wani irin yanayi a tattare da ita,sam bataso sgr ya sauketa daga saman kafadarshi ba,don ba ƙaramin relief ta samu ba,ita kaɗae tasan yarda take ji aduk lokacin da takasance tare dashi,   Runtse idonta tayi yayin da hawaye ke cigaba da zubowa sun jiƙa mata fuskarta sharkaf,suna cikin tafiyar nan,ranta ya bata cewa ta ɗan jiyo ta kalle shi,taga yana nan ko ya tafi,   A hankali ta ɗan juyo da fuskarta, ta kalli upstairs din,adaidai lokacin shi ma Ya juyo da fuskarshi a wani slow,kai tsaye idanunshi suka sauka acikin nata dake kallon shi,gaza janye idanunshi yayi daga kallon hawayen dake shararowa a fuskarta,wani irin tausayinta ne yaji ya kama shi,saboda yasan cewa shine silar zuban hawayen nata,kamar yarda yake kallonta,itama haka take kallonshi duk da sunyi nisa da juna,a hankali ya lumshe idanunshi tare da ɗauke kanshi daga kallonta ya ƙarasa hawa upstairs ɗin da sauri ya wuce bedroom ɗin shi,    Sai bayan da ya 6ace ma ganinta sannan itama ta juyar da kanta tare da mayar da hankali wurin yin tafiyar,har cikin bedroom azmee takaita,ta taimaka mata wurin hayewa saman gadon,ta kwanta yayin da idonta ke kallon ceiling ba komai take tunawa ba,face yarda Sgr ya tarbo waist ɗinta a lokacin da tazo faɗuwa,da kuma lokacin da ya ɗaurota asaman kafaɗarshi,da kuma kallon nan daya juyo yana yi mata kafin ya tafi,   Zama azmee tayi daga gefen gadon tana kallonta tace"Me ya faru dake ne sehrish?meya haɗaki da sgr dana ga ya ɗaukko ki asaman kafadarshi"?    bata 6oye mata komai ba ta sanar da ita duk abunda ya faru a tsakaninta da sgr,   Jinjina kai Azmee tayi tare da cewa"u ave to be very careful rishi,tun farko saida na gargaɗeki akan shi,amma baki ji ba ko?    Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Aunty azmee ina kiyayewa,wannan ma matsala aka samu har na manta da gyalena asaman gadonshi,banyi tsammanin zai dawo ba a wannan lokacin......'   Shiru Azmee ta ɗanyi kafin tace"Shikenan amma duk da haka ki ƙara kiyayewa nan gaba,karki ƙara yin  gangancin maimaita kuskuren da kikayi yau,"    Sehrish tace"Insha Allah bazan ƙara ba,"    "Allah yasa,ni zan wuce,ki daure ki tashi kije kiyi sallah," Amsa mata tayi da"toh," sannan azmee ta miƙe tare da fucewa daga bedroom ɗin nata,ajiyar zuciya sehrish ta sauke,tunda ta kwanta ko kwakkwaran motsi wannan bata iya yi ba,jikinta duk yayi mata tsami,ta so ta tashi ta ɗan gasa jikin da ruwan zafi amma sam tagaza motsi,kamar an aza mata Bulo asaman jikinta haka ta dinga ji,yayi mata wani irin nauyi,a wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita.    _💋Boss Bature💋_ A washe gari Around 7:00am A firgice Jahad ta farka daga dogon suman da tayi,sakamakon jin saukar ruwan sanyi da tayi asaman fuskarta,a gigice ta tashi zaune,lokaci guda ta fara ambaton sunan Hosana!hosana!   "Jahad ki buɗe idonki Ni ce fa" Jin muryar mutum a kusa da ita yasa ta ware idanunta tana kallonta,bakowa bace face Nurse Camilla,zuwanta kenan ta shigo cikin falon taci karo da Jahad a sume ƙasa,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,da sauri ta ɗauko ruwa mai sanyi ta yayyafa mata,   A hankali jahad ke kallonta da idanunta waɗanda suka rune saboda kukan da tasha,   Sanye take cikin jeans da t- shirt tare ta ɗaure sumar kanta da ribbom,      a ɗan ruɗe tace"Jahad me ya faru ne?na shigo na same ki a sume menene ya faru dake ne"?   Cikin shessheƙar kuka tace"Hossana tana cikin ɗaki,bansan tana a raye ba ko ta mutu,jiya da daddare wani ya faɗo mana a cikin bedroom ɗin mu har yayi ƙoƙarin yin raping ɗinta........'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya kufce mata,hankali a matuƙar tashe camilla ta miƙe tare da nufar hanyar zuwa ɗakin nasu,   Miƙewa jahad tayi tabi bayanta cikin sauri,zuciyarta nata faman bugawa saboda fargabar a wane hali hossana ke ciki, karfa ace wannan mutumin ya ƙara dawowa don ya cutar da ita,   Yadda jahad ta bar hosana haka suka sameta,naɗe cikin bargon a sume bata motsi,    Hawa saman gadon camila tayi ta ƙarasa kusa da Hosana tare da kai hannu ta shafa wuyanta,kallon jahad tayi dake atsaye cike da fargaba tace"dauko mun ruwan da na bari a falo," amsa mata tayi da toh sannan ta fuce daga cikin bedroom ɗin,within minutes sai ga Jahad ta dawo hannunta ɗauke da bottle water ta miƙa ma Camilla,hannu tasa ta kar6a sannan ta buɗe murfin ta debo ruwan tare da watsa ma hossana a fuskarta,nan take hossana tafarka daga suman da tayi,a wani irin razane ta zabura zata yaye bargon jikinta tana cewa"karka ta6ani Abba banso banso!ka ƙyale ni in tafi,inba haka ba Ya omar zai kashe ka...."  Cikin sauri Jahad ta haura saman gadon tare da rurruƙeta tana gyara mata bargon jikinta gudun kar tsiraicinta ya fito,ganin tana ta faman fisge fisge tana hargowa yasa Camilla tayi mata magana cikin sanyin murya tace   "Hosana!ki kwantar da hankalin ki,babu kowa anan da zai cutar dake,Ni ce Sister Camilla tare da ƴar uwarki jahad a kusa dake,dan Allah ki shiga natsuwarki,"cikin rarrashi takeyi mata magana, Jahad tace"Hossana gani a kusa dake ki buɗe ido ki kalle ni,"   Jin muryar jahad yasa hossana ta buɗe idanunta tana kallonsu ɗaya bayan ɗaya,fuskar nan tayi sumtun saboda kukan da tasha,idanunta duk sun ƙankance,     "kiyi haƙuri hossana,koma waye Allah bazai barshi ba,nayi ƙoƙarin na kwace ki daga hannunshi amma Allah bai nufa ba,inda na gode ma Allah da bai ƙarasa nufinshi akanki ba,nayi ƙoƙarin na kira ƴa Omar,amma layinshi yaƙi shiga,amma zuwa anjima zan ƙara jaraba kiran shi,nasan zai ɗaga,"   Cikin shessheƙar kuka tace"Jahad ki kira mun shi,a kiramun ya Omar yazo,inason naganshi,shi nakeson gani,"    Jiki a sanyaye Jahad tace "Kada ki damu zan kira maki shi,insha Allah,"  gaba ɗaya lamarin ya girgiza Camilla,ta jima tana hasashen waye yayi ƙoƙarin cutar da yaran acikin gidan!duk irin tsaron dake gareshi,ba ita ba hatta jahad tashiga zargin waye yayi masu wannan zuwan da daddare don ya cutar da hossana,sun jima suna wannan tunanin, a ƙarshe dai bakowa suka fi zargi ba face ɗaya daga cikin security guards ɗin gidan,   Bayan sun gama jimamin nasu,Camilla ta tashi tare da fucewa daga bedroom din ta nufi kitchen don ta shirya masu breakfast,   yayin da ita kuma Jahad,ta taimaka ma hossana bayan ta sanya rigarta sannan ta kaita toilet ta taimaka mata wurin yin wanka da ruwa mai ɗumi yarda jikinta zai ɗan warware,sai da su kayi alwala sannan suka fito daga cikin toilet ɗin, doguwar riga ta ɗaukko mata acikin wardrobe ta bata ta sanya sannan suka zura hijabansu atare,jahad ta shimfiɗa masu darduma suka hau sama tare da daidaita natsuwarsu suka kabbara sallah,har lokacin jikin hosana sai faman kerma yake yi,a tsananin tsorace take da abunda ya faru da ita adaren jiyan nan,bayan sun kammala sallar jahad tace mata taje ta kwanta tayi bacci,ita zata wuce kitchen wurin Camila,ta taimaka mata suyi aikin breakfast ɗin atare,   Bayan jahad ta fuce daga bedroom ɗin,hossana ta miƙe daga saman dardumar jikinta nata faman kerma ga rawar ɗari da take yi,saboda sanyin da take ji,lalla6awa tayi tare da hayewa saman gadon,takai hannu tare da janyo bargon ta ɗan kakka6e shi zata rufe Jikinta dashi,kwatsam taji sautin faɗuwar wani abu ƙasa,cikin sauri ta leƙa ƙasan gadon tana kallon abun nan daya fado daga saman gadon, Diamond ring ne ɗan ziriri dashi sai faman ƙyalli yake,gabanta taji ya faɗi rass!ganin zoben da tayi ya faɗo ƙasa,yunkurawa tayi tare da tashi daga zaune sannan takai hannu ƙasan gadon tare da ɗaukko zoban,ɗago shi tayi a daidai saitin idanunta tana ƙare mashi kallo, Zaro ido tayi hankalinta a matuƙar tashe ta furta"Ya Omar!!!!!!!!!" 😳 *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.    *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Abban sojoji paid book ne,ga duk mai buƙatar karanta cigaban shi yayi mun magana kai tsaye ta number ta 08103884440 Whatsapp only banda phone calls, 300 ne only 🤝 Zuba ma zoben ido tayi tana kallonshi hankalinta a matuƙar tashe,gabanta na faduwa,a hankali take jujjuya shi a hannunta,lokaci guda hawaye suka fara gangarowa daga idanunta cikin shessheƙar kuka take cewa"I can't believe it! Ya omar ɗina ne yayi ƙoƙarin raping dina? Shine yaso rabani da mutuncina?why ya Omar why!?innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Allah kasa mafarki nake ba gaske ba.......'kukan da yaci ƙarfinta ne yasa ta gaza ƙarasa maganar,nan fa tashiga shararar kwalla,abun ba ƙaramin ciwo yayi mata ba,bata ta6a tunanin haka daga wurin shi ba,wannan zoben nashi ne,shi ya tabbatar mata da cewa Ya omar ɗinsu ne yayi yunƙurin yi mata wannan aika-aikan,amma meyasa!? tsagaitawa tayi da kukan tashiga girgiza kanta tana cewa"A'a ya Omar ɗina bazai ta6a yi mun haka ba,na yarda dashi sosai,nasan cewa bada son ranshi yayi mun hakan ba,Ya Omar bazai ta6a cutar da hosanar shi ba,ina yi mashi kyakkyawan zato kuma bazan ta6a tona mashi asiri ba,bazan bari kowa yaga zoben shi ba ko jahad bazan nuna mawa ba,saboda nasan ba dole ta fahimce shi ba,kamar yarda ni na fahimce shi,"ƙarasa maganar tayi tare da ƙankame zoben asaman ƙirjinta ta ɗan runtse idanunta hawayen naci gaba da sauka asaman fuskarta, Dama ance so hana ganin laifi,hosana ta makance akan son ya Omar ɗinta,kuma ta yarda dashi 100%, tana cikin wannan yanayin taji motsin mutum cikin sauri takai hannu tare da janyo bargo ta ƙudundune acikin shi,6oye zoben tayi acikin aljihun rigar jikinta,sannan ta sanya tafin hannayenta tana goge hawayen fuskarta, Jahad ce ta shigo hannunta ɗauke da kakkauran tea mai zafi sai faman tiriri yake yi,ƙarasawa tayi tare da samun wuri daga gefen gadon kusa da hosana ta zauna, a hankali tace"ƴar uwata rabin raina ga tea na kawo maki, ki tashi kisha shi da zafi zafinshi karya huce nasan zaki ji dadin shi,'cikin lallami take yi mata magana saboda tasan a halin da take na fargaba tana buƙatar kalamai masu daɗi da zasu sanyata farin ciki, lamo hosana tayi batare da ta motsa ba abunda yasa tayi hakan saboda tanason ta daidaita natsuwarta don kar jahad ta gano wani abu, jin shiru yasa jahad,kai hannunta na dama ta ɗan bubbugi kafaɗarta tace"tashi mana hosana ko kinyi bacci ne"?ta tambaya tana kallonta naɗe cikin bargo, Har jahad ta yunƙura zata tashi,hosana ta soma motsi alamar zata farka,komawa jahad tayi ta zauna tana jiranta ta tashin,a hankali ta yaye bargon tare da tashi daga zaune tana mutsistsika idanunta alamar yanzu ta tashi daga guntun baccin daya ɗauke ta,wartsakewa tayi ta buɗe ido tana kallon Jahad, Murmushi jahad ta sakar mata tare da cewa"babyn Omar ya jikin naki?nasan har yanxu kina fargaba akan abunda ya faru dake jiya,dan Allah hosana kada kisa damuwa kinji?insha Allah koma wanene asirinshi zai tonu,zamu faɗama ya Omar zai gano koma wane tsinan.........'a firgice Hosana ta toshe ma Jahad baki da tafin hannunta tana cewa"Jahad dan Allah kidaina maganar nan,kina tunamun abunda ya faru jiya,ni banason ma ana maganar nan,gabana faɗuwa yake yi,'ta ƙarasa maganar a sanyaye tare da zame hannunta daga bakin jahad, Ajiyar zuciya jahad ta sauke tare da cewa"Shikenan mubar maganar,yanzu dae ga tea ɗin kisha,kuma sister camilla tace na tambayeki in akwai abunda kike buƙata a girka maki kici," Hannu hosana tasa ta kar6i cup ɗin da jahad ta miƙo mata sannan tace"Bana buƙatar cin komai yanzu,ni dai akira mun ya Omar yazo inason ganin shi,' Murmushi jahad tayi tare da cewa"kada ki damu babyn Omar,nasan zaizo ne ina ta trying numbarshi amma taƙi shiga still switch off,amma nasan zuwa anjima zai kunna wayar ne," Jin haka yasa jikin hosana yin sanyi,don tasan dalilin dayasa Omar ya kashe wayarshi,bata ji daɗi ba saboda tasan zai sanya damuwa sosai aranshi,tausayinshi ne taji ya kama ta,babban abunda take fargaba shine kada ya hana kanshi zuwa wurinsu, tashi jahad tayi tare da fuce wa daga bedroom din ta koma kitchen,yayin da ya rage hosana ce kaɗai saman gadon tana kur6ar tea ɗin a hankali,duk jikinta yayi sanyi, After some days Abu kamar wasa yau almost 1 week kenan ba Omar ba alamar shi,hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,kwana huɗu ba Omar ko layin shi suka kira kullum a switch off suke samun shi,hakan ba ƙaramin tayar masu da hankali yayi ba,sun shiga damuwa sosai na rashin zuwan shi,musamman Hosana duk tabi ta takure kanta,ko abincin kirki bata iya ci,ko isasshen bacci bata samu,kullum cikin kuka take na rashin ganin ya Omar ɗinta,duk bayan ƴan mintina sai taje ta ɗauki telephone ta danna mashi kira,da zarar taji wayar akashe sai ta fashe da kuka,daƙyar jahad ke samu ta lallashe ta,akwai lokacin da jahad ta farka tsakar dare ta samu Hosana saman darduma tana yin sallar dare abunda bata ta6a ganin hosana tayi ba,kuma duk don saboda ya Omar ta tashi yin sallar daren,tana roƙon Allah yasa Ya omar yazo karya rabu dasu,batasan yaya rayuwa zata kasance mata ba,batare da ya Omar ɗinta ba,tana yin addu'ar tana matse kwalla,a wannan lokacin ba ƙaramin tausayi taba Jahad ba, A washe garin ranar jahad ta yanke shawarar zuwa tasamu Osman ta sanar dashi game da halin da suke ciki na damuwa da rashin ganin ya Omar ɗinsu,ko da Jahad taje ta samu Osman ta faɗa mashi,yayi mata alkwarin cewa zai bincika masu shi, Bayan tafiyar jahad,Osman ya nemi major a waya ya sanar mashi abunda ke faruwa,na halin da yaran suke ciki akan rashin ganin Marshal da basuyi ba na tsawon kwanaki ,jiki a sanyaye Major yace mashi yaci gaba da kwantar masu da hankali,insha Allah zaizo ne abubuwane sukayi mashi yawa. Hankalin Omar ba ƙaramin tashi yayi ba,lokacin da major ya sanar dashi halin da su jahad da hosana suke ciki,tsananin tausayinsu ne ya kamashi,musamman hosana da aka sanar dashi cewa ko isasshen bacci bata samu saboda damuwa akan shi,tamkar ya zubar masu da hawaye haka yaji,duk yarda yaso ya daure ya hana kanshi fargabar tunkararsu amma ya gaza yin hakan,ya nisanta kanshi dasu ne, saboda gudun karya ƙara jefa kanshi cikin matsala,shi kanshi daurewa kawai yake yi amma ba ƙaramin cutuwa yake yi ba,yana tsananin son ganinsu yanaso yaga wane hali suke ciki, amma ba yarda ya iya. A 6angaren Sehrish kuwa ba ƙaramin jiki taji ba,a washe garin ranar da Sgr ya sanyata tsallen kwaɗi,ko school bata je ba,saboda jinyar jikinta da ta tsaya yi,ƙafafunta sunyi suntum,tun da ta lafe saman gadon ko motsi bata son yi,ba ƙaramin jiki taji ba sai da azmee ta taimaka wurin gasa mata ƙafafun da ruwan zafi,tayi mata tausa sannan taji sauƙin jikinta sosai har ta samu ta warware taci gaba da ƙiriniyarta kamar yarda ta saba. Hayamm taji haushi sosai kamar ta binne kanta saboda tsabar baƙin ciki,tun washe garin ranar da azmee taje gyara part din Sgr,ta fito hannunta ɗauke da tray ɗin kayan abincin da baici ba,jiki na rawa hayaam ta ƙarasa tare da kar6ar tray ɗin tace tabar mata kayan takai kitchen, tana shiga kitchen dasu ta shiga buɗe kayan don taga idan sgr yaci abincin,sai dae abun takaici bai ta6a komai na abincin ba,yarda sehrish takai mashi shi haka aka dawo dasu bai ta6a komai ba,lemu kawai yasha,kuma ta manta bata zuba gashin acikin abun shan nashi ba,taji takaicin hakan kamar ta aza hannu abisa kanta tayi ihu saboda haushi,amma taci alwashin cewa saita shirya mata wani tuggun tunda ta tsallake wannan. A 6angaren su Twins kuwa sai dae muce Alhamdulillah,Yara sun zama mazajan gaske,rayuwarsu ta gyaru sosai,yanzu basa wasa wurin yin ibadarsu suna neman tsarin ubangiji,don wani lokacin atare suke tashi suyi ƙiyamun laili da sauran nafilfili,sannan basa komawa bacci bayan sallar asuba,zama suke yi suyi ta karatun alkur'ani mai girma har gari ya waye, Allah sarki rayuwa kenan ayayin da matsalar su jahan ta ƙare, shi kuma junaid wani mummunan al'amari ya soma faruwa dashi batare da sanin kowa ba,shi kaɗae yasan halin da yake ciki,kuma yaƙi sanar ma kowa saboda baison ya tashi hankalin Abbanshi da kuma na ƴan uwanshi,baka ta6a gane halin da yake ciki saboda babu abunda ya canza na daga ƙiriniyarshi, da kuma wannan kyakkyawan murmushin nashi,abun yana damunshi sosai, wannan ɗigon jinin dake fitowa ta ƙopar hancinshi, kullum ne saiya tashi tsakar dare batare da sanin Abbansu ba, ya shiga cikin toilet yana wanke hancinshi, abun sai ƙara gaba yake yi, ga yanayin da yake tsintar kanshi aciki,yanayi mara daɗi wata irin kasala da kuma yawan faɗuwar gaba,da kuma razanar da yake yawan yi,ko kiran sunan shi kayi da karfi sai ya firgita,ba kowa ya lura da hakan ba,tabbas rayuwar Junaid tana cikin hatsari sosai,a cikin jikinshi ciwon ke cin shi batare da sanin kowa ba, hmmmmmmm. A 6angaren Commandern ƴan iska kuwa wato haroon komai ya gama hargitse masa,kamar wani zautacce haka ya koma wurin neman jakar kuɗin shi,sam ya rasa samun kwanciyar hankali gaba daya plan ɗin da ya shirya na barin nigeria yana shirin rugujewa saboda rashin kuɗin nan,a ƙarshe ya yanke shawarar turo ɗayan videon nan nasu jahan don ya sake yi masu barazana dashi,su ƙara mashi wasu kuɗin da zai samu yabar ƙasar tunkan asirinshi ya tonu, Wannan kenan👌 Gaba daya an canzama gidan kamanni sai faman gyare-gyare akeyi mashi ta ko'ina,kwararrun ma'aikata aka ɗauko wurin tsara decoration ɗin da za'ayi ma gidan, yarda kasan za'ayi wani shagalin biki haka suka ƙawata gidan,duk wannan shirye shiryen da suke yi na tarbar manyan baƙinsu ne da zasu zo acikin kwanakin nan,a yau dae mutum biyu ne zasu fara zuwa,daga ciki akwai uncle Abusufyan da zaizo daga ƙasar turkey,sai kuma hajiya azeema da zata zo daga lagos, gaba ɗaya tunanin matasan gidan Abbansu yasa aƙawata gidanne kawai saboda zuwan su Ammin sa ne,abunda basu sani ba shi da wata manufa yasa a gyara gidan, Tofah, Wuraren ƙarfe 7:00am dai dai sehrish ta kammala shirinta na zuwa school,tana tsaye agaban mirror sai faman feshe jikinta takeyi da turare,bayan ta kammala ta koma wurin gadonta tare da kai hannu ta ɗauki hijab ɗinta data ajiye anan saman gadon ta zura ajikinta, bata ɗauki school bag ɗinta ba saboda tana so tafara zuwa kitchen wurin su Aunty azmee ta kar6a ma babban yaya breakfast ɗinshi takai mashi, fitowa tayi daga cikin bedroom ɗin tana tafiya tana ƴan kalle kalle kamar zatayi tuntu6e,decoration ɗin da akayima gidan ba ƙaramin kyau yayi mata ba,don ba ƙaramin ɗaukar ido yake yi ba, Ƙarasawa kitchen ɗin tayi tare da tsayawa daga bakin kopar tayi masu sallama,Azmee ce kaɗae acikin kitchen ɗin,jin muryar sehrish yasa ta juyowa fuskarta ɗauke da murmushi tace"Ƴan makaranta har an kammala kimtsawa ne? murmushi sehrish tayi tare da cewa"ina kwana Aunty azmee,ya aiki"? Azmee tace"Alhamdulillah,shigo daga ciki mana in haɗa maki breakfast ɗinki ki ci kafin ki tafi,' "A'a Aunty azmee bana jin yunwa,idan naje school zanci acan,' har ta ɗanyi shuru, cike da son jin gulma ta kuma cewa"Aunty azmee wai wanene zaizo zo yau"? Murmushi azmee tayi tare da cewa"Masu kama dake ne zasu zo yau,' "Masu kama dani kuma Aunty azmee"?ta tambaya fuskarta ɗauke da mamaki, azmee tace"kwarai kuwa kuna kama da azeema kanwar Abbansu junaid dake lagos,amman kinfi kama sosai da Uncle ɗinsu, Abusufyan dake zaune a ƙasar turkey shima zaizo yau,' wani irin farin cikine taji ya lullu6eta,saboda ɗokin ganin wannan uncle ɗin nasu da take yawan jin suna ambatar sunanshi,a ƙagare take da ta sanya shi acikin idonta, "Aunty azmee dagaske muna kama dashi?ko wasa kike yi mun"? Azmee tace"dagaske nake mana,ban ta6a faɗa maki ba,amma maganar gaskiya kamanninki dashi har sun 6aci,kullum na kalli fuskarki sai ya faɗo mun araina,saboda komai na fuskarki irin nashi ne,tun daga kan idanuwanki,hancinki,da kuma bakinki duk irin nashi ne,ke hatta launin fatarki chocolate colour irin nashi ne,da ace Abusufyan ya ta6a yin aure,zan iya rantsewa cewa ke ƴarsa ce' tunda azmee ta soma magana sehrish ta saki baki tana sauraronta, "abun ya jima yana ɗaure mun kai,shiru kawai nayi,amma kamanceceniyarki da wasu daga cikin matasan gidan nan har taso tayi yawa," Cika da mamaki Sehrish tace"Aunty azmee wai dagaske"? murmushi azmee tayi kafin taci gaba da cewa"na ta6a yi maki wasa ne irin haka"? Girgiza kai sehrish tayi alamar a'a, Cigaba da magana azmee tayi"kina yanayi da Abbansu junaid sosai kuma kina kama da Auntynsu Azeema,hatta junaid akwai kamanceceniya atsakaninku abunda yasa baza a gane ba saboda hasken fatarshi,amma kina kama da shi,bayan shi kuma sai Marshal Omar,shima akwai kamanninshi atattare dake,da kuma kanal yousouf,na jima da lura da hakan," tunda sehrish taji wannan jawabin na azmee take ta faman sakin murmushi,daɗi kamar ya kashe ta saboda ance tana kama da uncle Abusufyan ɗinsu, "Aunty azmee naƙosa na ganshi,Allah yasa kafin nadawo daga school ya ƙaraso,da kaina zanje inyi mashi sannu da zuwa sannan in kai mashi abun sha," Dariya azmee tayi tana cewa"Allah yasa toh,amma kin manta baki ce insha Allah ba," cikin sauri sehrish tace"Insha Allah Aunty azmee," Suna cikin firar nan tasu,sai ga junaid ya faɗo cikin kitchen ɗin ko sallama babu a firgice suka ɗago suna kallonshi, daga shi sai gajeran wando fari ajikinshi,sai faman washe baki yake yi,kamar wanda akayima albishir da gidan Aljanna, "Junaid anya lafiyarka kuwa?kaine yau kake yawo da short ajikin ka?ko ka manta akwai sehrish dani acikin gidan"? Acewar Azmee, Murmushi ya saki tare da nuna sehrish da hannunshi yace"Wurinta nazo,inason magana dake reesh,in ba damuwa ki biyo ni muje bedroom ɗina,' Kallon azmee tayi don taji me zata ce, "kije mana,amma kada ki jima," Amsa mata tayi da toh sannan tabi bayan junaid suka fuce atare izuwa bedroom ɗinshi dake a upstairs, atare suka shiga cikin ɗakin nashi,har wurin gadonshi yakaita sannan ya tsaya tare da nuna mata shaddojin daya jera asaman gadon nashi yace"Pls reeshi ki za6amun ɗaya mai kyau,inaso yau nayi shigar mutunci don na burge uncle Abusufyan yasan cewa na girma yanzu,'ashagwa6e junaid ya ƙarasa maganar, Sehrish kuwa zuba ma tsadaddun shaddojin ido tayi tana kallonsu,kala biyar ne sun sha uban aiki ajikinsu,hannu tasa tana ɗaɗɗaga kayan tace"junaid ae ni nama rasa wadda zan za6a maka acikinsu,saboda kowacce kasa acikinsu kyau zatayi maka,bakasan cewa kaine keyi ma kayan kyau ba"? Tayi maganar tare da ɗan juyawa tana kallon junaid dake tsaye yana ta faman sakin murmushin jin daɗin yarda sehrish ke hura mashi kai, ta jima tana ruwan ido kafin ta cankar mashi wata haɗaɗɗiyar shadda gezner Ash colour sai faman salƙi take yi, mika mashi tayi tare da cewa"Wannan tayimun sosai kuma ina da tabbacin cewa in har ka sanyata ajikinka,sai uncle abusufyan ya razana da ganin irin kyan da zakai,' Kar6ar shaddar yayi daga hannunta yace"thank u so much reesh,amma fa ba yanzu zan sanyata ba,sai zuwa anjima in zanzo ɗaukarki daga school zaki ga kalar wankan da zan ɗauka," murmushi tayi tare da kama hanyar fita daga cikin bedroom ɗin nashi tana cewa"Allah ya kaimu lafiya,yanzu dae zan jiraka,in ka kammala shirin ka fito mu tafi kar nayi late,' Amsa mata yayi da toh,bayan ta fita ya tattara shaddojin duka ya mayar acikin wardrobe ɗinshi, ya zaro wasu jeans da t-shirt ya shiga zura su ajikinshi _💋Boss Bature💋_ Lokacin da sehrish ta koma kitchen ɗin bata samu Azmee ba,sae dae Hayaam ta samu acikin kitchen ɗin,tana atsaye ta ruƙe qugunta kamar mai jiran wani abu, Ganin sehrish yasata cewa"Sannu ko" firgit Sehrish tayi tare da kai idonta inda hayaam ta ke atsaye tana sakin wannan shu'umin murmushin nata, "Yawwa"ta amsa mata atakaice tare da wucewa wurin trayn da azmee ta ajiye mata saman table wanda ta shirya ma sgr breakfast ɗin shi aciki,hannu biyu tasa ta ɗauki tray ɗin sannan ta kama hanya tare da fucewa daga kitchen din,hakanan ta dinga jin kamar bata yarda da hayaam ba,anya ba wani abu takeyi acikin kitchen ɗin ba?in ba haka ba meyasa ta tsaya atsaye ruƙe da qugu,kamar mai jiran wani abu, haka tayi ta wasiwasi acikin zuciyarta har ta ƙarasa part ɗin sgr, Sallama ta fara yi mashi,jin shiru ba'a amsa mata ba,yasa tayi tunanin ko yana acikin bedroom ɗinshi ne, A hankali tasanya kafarta tare da shigewa cikin palourn komai agyare tsaf ta same shi,asaman table ta aza mashi tray din sannan ta tsaya tana jiran fitowarshi ko zai bukaci wani abu, tana cikin tsayuwar nan tajiyo muryarshi daga cikin bedroom ɗinshi yana tambayar wanene anan!" Cikin sauri tace"Ni ce,dama breakfast ne na kawo maka," kusan minti biyar da yin maganarta sannan taji yace"A shigo min da coffee shi kawai nake buƙata," murmushi ta ɗanyi tare da mika hannu ta ɗauki cup of coffee ɗin dake acikin kayan breakfast ɗin nashi,ta nufi bedroom ɗin hannunta ɗauke da cup ɗin, sai da ta tsaya abakin ƙopar shiga Sgr ya bata izini sannan tasa kai tashiga,wani irin daddaɗan kamshin turarensa ne ya bugi hancinta,nan take taji wani irin yanayi atattare da ita, lumshe donta tayi tare da buɗesu a hankali ta kallo inda sgr yake, a hakimce ya ɗan kishingiɗa daga gefen katafaren gadon nashi, Gaza janye idanunta tayi daga kallon kyakkyawar surar jikinshi,wankan daya ɗauka ba ƙaramin fisgarta yayi ba,white trouser ne na suits amma bai sanya coat ɗin sama ba,iya vest ɗin ciki ya bari tabi shape ɗin jikinshi,daga ƙasan vest ɗin ta ɗan tattare hakan ya bayyana farar fatar shafaffen cikinshi, ya harɗe kafafunshi wuri guda yayin da idanunshi ke a lumshe, tafiya take tana tunkarar inda yake idonta akanshi har ta ƙarasa tare da ajiye mashi cup ɗin asaman bedside table ɗinshi tace"Gm sir,ga coffee nan na kawo maka,ko akwai wani abu da kake buƙata"? Bai amsa mata ba,a hankali ya dan buɗe idanunshi sannan ya yunƙara tare da miƙewa daga zaune ya sauko da ƙafafunshi ƙasa, Zaki iya tafiya,ya ambaci hakan ayayin da yakai hannu tare da ɗaukar kofin coffeen yakai bakinshi yana kur6ar shi anatse, Juyawa sehrish tayi ta kama hanyar fita daga bedroom ɗin a hankali,ji take kamar karta tafi ta barshi,don bata gaji da kallon kyakkyawar fuskarshi ba, Yana cikin shan coffeen nan wani abu ya sarƙe mashi adaidai saitin throat ɗinshi,a hanzarce ya ajiye cup ɗin tare da zura fingers ɗinshi guda biyu cikin bakin cikin sa'a ya ruƙo siririn abun, Lokacin daya fiddo da abun daga bakin nashi yayi arba da dogon gashi,ware idanunshi yayi, hankali a matukar tashe yana kallon gashin yace"in my coffee...! Jin wannan maganar tashi yasa sehrish saurin juyawa don taga menene,a lokacin har tasa ƙafa zata fita daga ɗakin, Gabanta ne taji yayi wani irin mugun buga ganin siririn gashin da Sgr ya ruƙo a hannunshi, Yunkurin amai yashiga yi,nan take ya miƙe da saurin gaske ya faɗa toilet,kai tsaye ya ƙarasa gaban basin yana kwarara aman,tamkar ƴan hanjin cikinshi zasu fito,kasancewar shi mutum mai tsaftar gaske ga ƙyanƙyami ya tsani ƙazanta a rayuwarshi duk mun ƙankanta,ranshi ba ƙaramin 6aci yayi ba,gashi a abun shansa kuma har ya shiga bakinsa!!,a wannan lokacin komai zai iya aikatawa he can't even control him self, cos he has a very bad temper,kuma ta motsa. Tap ya kunna,ruwa yashiga zubowa yana kora vomitting ɗin da yayi,sannan ya tarba tafin hannayenshi biyu tare da ɗebo ruwan ya watsa su a fuskarshi yana faman sakin huci, Sehrish dake atsaye abakin kopan bedroom ɗin nashi,jikinta sai faman kerma yake yi,gaba daya tabi ta rikice kan ta ya gama ɗaurewa,taya akai aka samu gashi acikin abun shan Sgr?ita dae tasan cewa ba gashin kanta bane,saboda ta sanya hijab ajikinta,hasalima ba ita bace ta shirya mashi kayan breakfast ɗin nashi ba,tunkan taga hukuncin da zaiyi mata har tafara matsar kwalla,don tasan bazai ƙyale ta ba,dole ya hukunta ta, A fusace ya fito daga cikin toilet ɗin,sai faman huci yake yi,ɗagowa yayi da idanunshi yana kallon inda sehrish take atsaye jikinta sai kerma ya keyi,tunda taga zufa na gangarowa a gefen fuskarshi, ta ƙara tsorata sosai, tamkar wani zaki haka ya tunkaro ta,a tsananin tsorace sehrish ta shiga ja da baya tana girgiza kai cikin shessheƙar kuka take cewa"wlh bani da masaniya akan gashin nan,banawa bane bansan ya akai ya shiga cikin abun shanka ba,' wata irin tsawa da Sgr ya daka mata nan take sehrish ta firgita agigice take zazzare ido tana kallon fuskarshi, biting lips ɗinshi ya shiga yi,yama rasa wane irin punishment zaiyi mata, Nuna ta da dogon yatsan sa yayi tare da cewa"as from today!bana son na ƙara ganinki a part ɗina!' Cikin shessheƙar kuka sehrish tace"Am really sorry babban yaya........ba laifi na bane bada sani na gashin ya faɗa aciki ba..........'tun kafin ta ƙarasa maganar ya ɗaga hannunshi da nufin ya sharara mata mari,runtse ido sehrish tayi tana jiran jin saukar marin nashi a kuncinta, ji yayi bazai iya ba saboda tunda yake arayuwarshi bai ta6a gigin ta6a jikin wata ƴa mace ba da sunan bugu,tun suna yara Abbansu ya hane su da yin wannan,kullum yana tunasar dasu akan su dinga daraja ƴa mace, Dunkule hannunshi yayi tare da yarfar dashi gefe guda,sannan yace"Get out from my bedroom!since before I show u my true colour!, ya ƙarasa maganar tare da juyawa yabarta tsaye anan tana faman shessheƙar kuka, Ji tayi bazata iya jure hukuncin da Sgr yayi mata ba, na hanata aiki a ƙarkashin shi ba, gaba ɗaya jikinta ya gama yin sanyi, a wani irin yanayi ta zube asaman guiwowinta,cikin sanyin murya,muryarta na rawa tace"nasan na 6ata maka rai sosai,na cancanci kowane irin hukunci daga gare ka,amma ina neman alfarma a wurin ka........'dakatawa tayi da maganar tana kallon bayan shi daya juya mata, ganin ya tsaya da yin tafiyar yasa ta gane cewa ita yake sauraro, anatse taci gaba da magana"ka yanke mun kowane irin hukuncin daya dace da laifin dana aikata,amma kada ka hanani yin aiki a ƙarkashinka,wannan horon yayi mun tsauri sosai,bazan iya jurewa ba,tun da nake maka aiki banta6a yin irin wannan gangancin ba,ina kiyaye wa sosai wurin ganin na tsaftace duk wani abu da zan kawo maka kaci ko ka sha,ba zanso wani abu da zai cutar dakai ba,wannan ma bansan ya akai hakan ta faru ba,don Allah kayi haƙuri ka yafe mun............'ƙarasa maganar tayi cikin shashsheka yayin da hawaye ke cigaba da zuba a idanunta, shiru Sgr ya ɗanyi na wani lokaci batare da ya motsa ba,hakan yasa ta fidda rai da cewar zai yafe mata, Hannu tasa tana sharar hawayenta tana kallon bayanshi,cigaba da tafiya sgr yayi kai tsaye ya tunkari wurin dressing mirror ɗinshi,hannu yasa tare da janyo drawer chest din dake ajikinshi,sabon scissors ya ɗauko cikin ledarshi, ya fiddo dashi yana kallonshi, lokacin daya juyo hannunshi ɗauke da almakashin nan,hankali atashe sehrish ta zaro ido tare da miƙewa tsaye daga kneel down ɗin da tayi tana ja da baya tana girgiza mashi kai,alamar karyayi mata haka, Gadan gadan Sgr ya tunkare ta,hannunshi ɗauke da almakashin nan sai faman salƙi yake yi,hannu sehrish ta aza asaman kanta tana cewa"Nashiga uku!innalillahi wa'inna ilaihirraji'un..........dan Allah kada ka datse mun gashin kaina ......'tana magana tana ja da baya yayin da shi kuma yake tunkararta,abu kamar wasa haka suka shiga zagaye ɗakin yana binta tana ja da baya,a ƙarshe daya fusata a zafafe ya damƙo hijabin dake jikinta tare da tun6uke ta daga jikinta yayi wurgi da ita gefe guda,yarda ya fusge hijabin daga jikinta gaba ɗaya ta tafi zata faɗi kasa,yakai hannu tare da janyo ta ta faɗo saman wide chest ɗinshi,kuka take kamar ranta zai fita saboda ba ƙaramin so takeyi ma gashin kan nan nata ba,ta kwallafa rai akanshi shiyasa kullum take ƙokari wurin gyara shi,har tasamu tatara shi da yawa bayan yanke shin da akai da zata fara aiki gidan,gashi yau akan kuskuren da ba ita ta aikata ba,za'ayi mata aski tana ji tana gani ba yarda zata yi, tunda sehrish ta faɗa jikinshi gaba ɗaya ya rasa duk wani kuzari na jikinshi,ƙamshin turaren jikinta ba ƙaramin kashe mashi jiki yayi ba,abunda bai ta6a yi ba arayuwarshi,a hankali yakai hannunshi tare da Cire ribbom ɗin da ta ɗaure gashin kanta dashi,ya warwaro shi duka tare da yin wurgi dashi gefe guda ya fadi kasa saman hijab ɗinta, Nan take lallausar suman kan nata mai laushin gaske ya tarwatse abayanta yayi mata tamkar hijabi, Ai ina baku labari tunda boss man ɗin nan ya zura hannunshi acikin sumar kanta nan fa yashiga murza gashin acikin hannunshi,laushin gashin kan nata ne yake fisgarshi har yayi hakan batare da saninshi ba, A hankali ya russinar da kanshi tare da kai tsinin hancinshi saman sumar kanta yana shaƙar daddaɗan kamshin dake fitowa daga cikin sumar kan nata,wani irin bugu zuciyarshi tashiga yi da sauri sauri take harbawa, ƙankame shi sosai sehrish tayi ta hanyar zagayo da hannayenta abayan waist ɗinshi ta ruƙo shi sosai kamar wani zai kwace mata shi,ba ƙaramin yanayi ta jefa Sgr ba ta kara sanya mashi kasala ajikinshi,kamar yarda itama ta shiga yanayin,tunda ta lafe mashi ajikinshi tayi lamo,wata irin natsuwa ta ji da bata ta6a ji ba atattare da ita,shessheƙar kukan nan da takeyi gaba daya ta neme ta ta rasa,tsit tayi tana sauraron heart beat ɗinshi, Suna cikin wannan yanayin na shauƙi sai ga Abbansu ya faɗo cikin part ɗin nasa yana neman shi,ganin baya acikin falon yasa ya wuce izuwa bedroom ɗin shi,tunkan ya ƙarasa ya hange su manne da juna kamar tip da tyre, adaidai ƙopar shiga bedroom din nashi,abban nasu ya tsaya cike da mamaki yana kallon wannan abun al'ajabin,ko motsi basa yi,bakomai yafi ɗaure mashi kai ba,face yarda sgr yake cakuɗa sumar kan yarinyar acikin hannunshi sai faman murzar gashin kan nata yake,ga kuma hancinshi daya cusa asaman kan nata yana shaƙar kamshin da sumar kan nata ke badawa mai daɗin gaske, Ita kuma ta ƙankame mashi qugunshi da hannunta,ta kwantar da kanta asaman chest ɗinshi, baki asake Abbansu ke kallon wannan tashin hankali,jinjina kai ya shiga yi cikin ranshi yana cewa"Oh ni hussein!tun yaushe wannan al'amarin ya soma faruwa acikin gidan nan batare da sani na ba!Hmmmm yanzu haka zare mata ido yakeyi yana tsoratar da ita don ya samu abunda yake so,nasan maganinka Rafayet,"ya faɗi hakan tare da kama hanya yabar part ɗin nashi fuskarshi ɗauke da murmushi,don shi wannan abun farin ciki ne awurinshi,ji yake kamar ya zuba ruwa ƙasa yasha don tsabar farin cikin ganin rafayet tare da mace,baida burin daya wuce wannan arayuwarshi,shi dae yaga Sgr yafara kula mace da sunan soyayya,yau dae gashi Allah ya nuna mashi, Janye hancinshi yayi daga cikin sumar kan nata,sannan ya tattaro gashin nata tare da sanya almakashin ya datse mata shi,sosai ya yanke gashin,yabar mata guntu wanda ko kafaɗarta bai sauko ba,' hankali a matuƙar tashe sehrish ta raba jikinta da nashi, da sauri takai idonta akan hannunshi dake ruƙe da dogon gashin daya yanke mata,kamar a mafarki take kallon gashin nata daya yanke mata, A hanzarce takai hannu tare da shafo kan nata don taji sauran daya rage mata, Fashewa tayi da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita,dakyar takai hannu tare da ɗaukar hijab ɗinta, sannan ta juya tare da watsawa aguje tana kuka ta fuce daga cikin ɗakin nashi, ajiyar zuciya ya sauke tare da takawa izuwa gaban dressing mirror ɗin nashi ya mayar da scissors ɗin aciki tare da gashin kan sehrish daya datse,duka ya tura shi aciki ya ajiye,sannan ya maida drawer chest ɗin ya rufe, Komawa yayi tare da haye wa saman gadonshi ya kwanta,yanayin da bai ta6a ji ba atattare dashi ba yake ji,tsananin tausayinta ne ya kama shi,har ya dinga jin tamkar baiyi mata adalci ba daya datse mata gashin kanta,ya lura ba ƙaramin so takeyi ma gashin kan nata ba,lumshe idanunshi yayi a hankali yana tariyo abunda ya faru tsakaninta dashi,especially lokacin da ta watsa da gudu tana kuka,duk baiji daɗi ba saboda shi baiyi mata hakan da nufin ya 6ata mata rai ba.          *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Saboda masu complain, nacewa nace zan tura da safe ban turo ba,Allah ne bai nufa zan tura da safen ba, Ga half page nan,later zan tura sauran komawa cikin bedroom ɗinta tayi tana ta faman sharar hawaye ranta na kuna,wuri ta samu ta zauna daga gefen gadonta tana ƙarashe kukan nata,babban takaicinta guntun gashin da Sgr ya bar mata da kyar in zaiyi parking da ribbom,koma yayin ba lalle ribbom din ya tsaya ba,ta jima tana azaune tana matsar kwallar bakin ciki,kafin daga bisani ta miƙe tare da nufar wurin dressing mirror ta tsaya tana kallon kanta acikin madubin,cikin shessheƙar kuka tace"Meyasa bai aske gashin duka ba yabarmun kwalkwali?me zanyi da guntun gashin nan daya barmun?ban son gashin!na tsani ganin shi,'ita kaɗae take ta faman sambatu rai atsananin 6ace, Kwankwasa ƙopar ɗakin nata akai,a tsiwace tace"Wanene"!   Muryar junaid taji daga waje yana cewa"It's me junaid,tun ɗazu fa nake jiranki,ki fito mu tafi na sauke ki,'a ƙagare yake maganar don ya gaji da jiranta, Ita gaba ɗaya ma ta manta da batun zuwa makarantar,sai da junaid ya tunasar da ita,     hannu tasa tana share hawayenta tace"junaid ka jira ni,acikin mota yanzun nan zan fito,"   Amsa mata yayi da"Okey," sannan ya juya tare da barin kopar dakin nata, Sai da tafara shiga toilet ta wanko fuskarta sannan ta fito tare da ɗaukar hijab ɗinta dake ajiye gefen gadon ta zura ajikinta Cikin sauri ta fito ɗauke da school bag ɗinta,ta fice waje wurin harabar ajiye motocinsu,hannu tasa tare da buɗe motar junaid ta shiga daga ciki ta zauna,   ɗan kallon fuskarta yayi tare da cewa"Reesh,na jima ina jiranki,bansan me ya tsayar dake ba,gashi ma har kinyi late,ina fata dae lafiya?" daƙyar ta ƙaƙaro murmushi tare da cewa"lafiya lou ba wani abu,mu tafi kawai ina ƙara makara,"    ajiyar zuciya ya sauke tare da jan motar suka bar gidan. Ita kuwa Hayaam dama tunda taga Sehrish ta nufi part din sgr da coffeen ta sulale ta shige dakinta don kar a gano abunda ta aikata. *HOSSANA* Zaune take saman gadonsu ta takure kanta sai faman shessheƙar kuka takeyi,ta sanya uniform ajikinta amma taƙi tashi ta zura hijabin,ta hana kanta duk wani jin daɗi, Fitowa jahad tayi daga cikin toilet tana kallonta gwanin ban tausayi tace"Hossana,dan Allah kidaina wannan kukan,duk kinbi kin takure kanki,ni nasan cewa ƴa omar ba hakanan ya daina zuwa wurin mu. Ba,Abubuwane suka yi mashi yawa shi ya sanya bai samu halin zuwa ba,' muryarta na rawa tace"jahad ba zaki gane bane,bazan ta6a samun kwanciyar hankali ba in har bansa ya omar a idona ba,Allah in har baizo ba yau,zanci shinkafar 6era ne na mutu kowa ya rasa,'   dariya jahad ta fashe da ita,hakan yasa hosana ɗaure fuskarta tana jifarta da harara tace"jahad dariya kike mun ko?   tsagaitawa tayi da dariyar tana girgiza kai tace"hosana dole nayi dariya,shinkafar 6era fa kika ce?   ɗaure fuska tayi tana murguɗa mata baki,   Murmushi kawai jahad tayi tare da komawa wurin closet ɗinsu,ta buɗe tare da ciro uniform ɗinta ta shiga zura su ajikinta,shaf shaf ta kammala shiryawa,ta ɗauko school bag ɗinta,sannan ta dawo wurin hosana tace"tashi mu tafi kada mu makara,"   Girgiza kai hosana tayi tace"Jahad ku tafi kawai,ni zan zauna a gida,saboda ko naje ba gane karatun zanyi ba,'   Zuƙunnawa jahad tayi agabanta tace"pls hosana ki daina sa damuwa aranki kinji?ni da kaina yau zan nemo maki ya Omar,'   jin abunda jahad tace yasa hosana sakin murmushi tace"dagaske Jahad"?   ɗaga mata kai tayi alamar eh tace"nayi maki alkwarin,duk inda yake indae yana acikin garin nan saina nemo maki shi,"   Wani irin farin ciki ne ya lullu6e hosana,jiki na rawa ta tashi ta ɗauko hijabinta bayan ta zura safarta da takalmanta suka fuce atare,    A waje suka samu motar osman na jiransu,bayan sun shiga ya tashi motar ya fuce dasu daga cikin gidan,hosana sai murna take jahad tace zata nemo mata Omar,batasan cewa ita da wasa ta faɗa mata ba don ta sanyata farin ciki ne kawai, Wuraren ƙarfe 12 na rana,jirginsu hajiya azeema yayi landing daga lagos,kanal yousouf ne tare da su irfan suka je tarbosu,a lokacin hayaam suna a kitchen tare da azmee suna shirya lunch ɗin gidan da kuma na tarbar baki,daga kasa ƙafarka acikin main palour ɗin zaka ji daddaɗan ƙamshin abincin da suke girkawa ya gauraye ko'ina, Cike da son jin gulma hayaam tace"Aunty azmee,wai Uncle ɗin nan nasu da zaizo daga ƙasar turkey,yana da aure ne"?   Azmee tace"a'a bai ta6a aure ba,ina tunanin ma ko budurwa bai ta6a ajiyewa ba,"   jinjina kai hayaam tayi tare da cewa"tabɗijancen amma da alama zaiyi ji da kai,"   murmushi azmee tayi tare da cewa"yarda kike tunani ba haka yake ba,Abusufyan wayayyan mutun ne,ta wani 6angaren ma bai ɗan jin magana amma dai nasan yanzu ya kimtsu tunda girma ya kama shi,amma lokacin baya da yake zuwa mana nan, yarda kikasan junaid haka ɗabi'unshi suke,da yake shi rainon goggonsu ne,'    murmushi hayaam tayi tana ɗan ta6e baki tace"Amma aunty azmee,ita wannan yarinyar sehrish,yakamata ace aikinta ya qare acikin gidan nan,tunda gani nazo kuma zan jima anan ne,ni a ganina bai kamata tana yawo acikin gidan nan ba,ita kaɗae ƴar matashiyya da ita,ya kamata ace tana gaban iyayenta yanzu,'ta ƙarasa maganar tana faman yatsina fuska,ta zuba ma azmee ido tana jiran jin me zatace, shiru azmee tayi saboda bata da amsar da zata bata, Cigaba da magana hayaam tayi"Yarinyar ta cika rawar kai sosai,yakamata ta tsaya a iya matsayinta na ƴar aiki mana,ni ina ganin akwai abunda take hari acikin gidan nan shiyasa ta liƙe har ta samu matsayi a wurin babban yaya," "Hayaam muyi sauri mu kammala aikin girkin nan,lokaci yana ƙure mana,"da gangan azmee tace mata haka,don ta dakatar da ita daga yi mata zancen Sehrish,don ita ta tsani gulma arayuwarta,   ta6e baki hayaam tayi,aranta kuma taji haushin yarda azmee ta katse mata hanzarinta batare da ta ƙarasa maganarta ba,daga bisani kuma ta saki shu'umin murmushin nan nata,tana tunanin ko ya Sehrish ta ƙare da sgr,don tasan cewa dole yaga gashin nan kuma zai hukuntata akan hakan,taso taje tayi masu la6e amma tsoro ya hanata gudun kar wani ya kamata asoma zarginta, Ƙasa ƙasa tayi da murya tare da cewa"Koda ace bai hukunta ta ba,nasan cewa zai fara tsanarta ne,kuma zai gane cewa ƙazama ce ita,zanci gaba da shirya mata makirci har nasamu na maye gurbinta a wurin sg......'bata ƙarasa maganar ba,saboda jin shigowar Hajiya Azeema tare dasu kanal yousouf da sauran da suka je ɗaukota,zuba ido hayaam tayi tana kallonta,ganin irin ruwan wankan gwala gwalan data ɗauka,   jikinta na sanye da material launin sararin samaniya,mai tsadar gaske sai faman ƙyalli yake yi,rigar takai mata har wurin guiwarta,sai zane data ɗaura,ta yafa gyale asaman kafaɗarta,yayin da ta kashe ɗaurin ɗan kwalin nan ture kaga tsiya,amma ita nata sunan shi ture kaga arziƙi,don akwai abun arziƙi,gaba daya earrings dinta da awarwaron hannunta da kuma sarƙar wuyanta duk gold ne,ta wanku iya wankuwa,Hajiya azeema kenan ɗaya daga cikin biloniyas din family nasu,idan aka cire shugaba kuma jagora wato Surgeon General Rafayet, Sai faman sakin murmushi take yi,tsantsar farin cikine ya lullu6eta yau gata agidan ɗan uwanta hussein,anjima ba'a haɗu ba,harkar kasuwanci ta 6oye ta,saboda bata cika zama a nigeria ba,kunsan business woman bata nan bata can kullum cikin hawa jirgi take wurin zuwa harkar kasuwancinta,   Atare suka ƙarasa cikin main palour ɗin,Kanal yousouf na ruƙe da Trolley ɗin da tazo dashi,    Anatse take bin ko'ina na gidan da kallo komai ya canza mata,ba kowa take muradin gani ba,face Junaid don har mafarkin shi tayi,shiyasa ta ƙagara tazo don tagan shi,juyawa tayi tare da kallon irfan tace"wai ina yaya hussein ne?naga kamar ba kowa gidan ko"?   "Abban mu ya ɗan fita garden tare da babban yayan mu da kuma ya Omar,amma ina da tabbacin cewa nan bada jimawa ba zasu shigo ciki,"ya ƙarasa maganar tare da nuna mata wuri yace"Aunty ki zauna mana,bari nayi ma Aunty azmee magana ta haɗa maki farfesun nan nata,nasan baki manta ɗanɗanon shi ba,"   dariya tayi tare da dan bugun kafadarshi tace"wato kallon acici kakeyi mun ko?daga zuwana ko hutawa banyi ba zan fara neman farfesu,kamar wata mayya,ni duk bama wannan ba,nifa hankalina bazai kwanta ba in har bansa junaid acikin idona ba,'    Kanal yousouf yace"Aunty gaskiya nafara kishi da junaid,haba kowa junaid junaid,ko hutawa ba kiyi ba amma kin fara ambaton sunanshi kamar shi kaɗae ne ɗa acikin gidan nan,"cikin zolaya yayi maganar tashi, Kafin Azeema ta kuma cewa wani abu,sai ga azmee ta fito daga cikin kitchen fuskar nan ɗauke da murmushi tana cewa"wata sabon gani, hajiya azeema,Sai yau zamu sake sanyaki acikin idanunmu"?tayi maganar a yayin da take ƙarasawa wurinta suka rungume juna,dama suna ɗasawa da ita,mutuniyarta ce kodan saboda iya girkin azmee yasa take shiri da ita sosai,don ita bata wasa da abinci,akwai son cin mai daɗi,kullum tazo Abuja wurinsu burinta tasha farfesun azmee,   Raba jikinsu sukayi dana juna,Azmee taci gaba da cewa"Hajiya azeema kece kika koma haka? Dariya azeema tayi tace"kinji ki da wata magana,kamarya na koma?nasan halinki fa azmee yanzu kince na ƙara ƙiba,'   Azmee tace"kin tsargu kenan,tunda gashi nan kin rigani faɗin abunda zance,'   Ta ƙarasa maganar tare da ruƙo hannunta tace"nasan kin kwaso gajiya sosai,shiyasa na gyara maki shinfiɗa inda zakije ki yada gajiyar da kika kwaso,sannan akwai special suya da kuma wannan farfesun da kika fiso na shirya maki shi,da zarar kin kammala hutawa zan shiryo maki shi,kici ki ƙoshi,nasan mutuniyar tawa bata wasa da cikinta,akwai bama ciki haƙƙinsa,"     Sai faman murmushi hajiya azeema ke saki,da alama taji daɗin karramawar da azmee tayi mata sosai,atare suka wuce ciki izuwa bedroom din da zata sauka,dama already azmee ta gyara mata ɗakin sai ƙamshi yake,    bayan sun shiga bedroom din,Sai da suka ƙara gaisawa sosai,kafin daga bisani Azmee tabar cikin ɗakin ta koma kitchen,    Ajiyar zuciya hajiya azeema ta sauke tare da cire mayafin cikinta ta ajiye shi saman gadon,sannan ta wuce cikin toilet,   Bayan shigarta kanal yousouf ya shigo cikin bedroom din hannunshi ruƙe da trolley dinta,jingine mata shi yayi ajikin wardrobe,sannan ya juya ya fuce,    fitowa azeema tayi daga cikin toilet din har lokacin fuskarta ɗauke da murmushi a fili tace"oh ni,koya junaid ya koma yanzu?nasan cewa ya ƙara girma sosai,gaskiya nayi missing shagwa6ar shi,nasan cewa da zarar yaji cewa na ƙaraso,zaizo ya ishe da rigima yana cewa Ina tsarabar shi,'ta ƙarasa maganar tare da hayewa saman gadon ta ɗan kishingiɗa donta runtsa, Bata jima da kwanciya ba,Abbansu ya shigo cikin gidan tare da sgr da marshal atare suka ɗunguma zuwa masaukin nata,a hankali abba ya tura ƙopar ɗakin suka shiga da sallama,   Jin muryar ɗan uwanta,yasa ta yunkura tare da miƙewa daga zaune tana kallonsu fuskarta ɗauke da murmushi,    Ƙarasawa ciki su kayi,sgr da omar suka samu wuri saman doguwar sofa din dake dakin suka zauna suna fuskantarta,yayin da Abbansu kuma ya samu wuri gefen gadon kusa da ita ya zauna fuskar nan awashe sai faman farin ciki yake yi na ganin ƴar uwarsa daya jima basu haɗu ba,    gaisawa suka shiga yi da junansu,don ba ƙaramin kewar juna sukayi ba,   Abba yace"ina fata dae da shirin zama kika zo mana,dan wannan karan bazan bari ki koma ba,nagaji da kewarku da nake ta faman yi,'    "Yaya hussein,nasan ban kyauta ba,na rashin zuwana wurinku,abubuwane sunyi mun yawa shiyasanya na jima banzo ba,amma Insha Allah wannan karan har sai kun gaji dani,zan zauna ne har sai an ɗaura auren junaid,'   Fashewa sukayi da dariya gaba dayansu,banda Sgr wanda tun shigowarsu,ya jingina bayanshi ajikin sofa din tare da lumshe idanunshi,sarai azeema ta lura dashi dama sai da ranta ya bata cewar bazai tanka mata ba,    Omar yace"ae ni fushi nake da Auntyn tawa,haba aunty azeema yau kusan wata nawa kenan?yaushe rabon da mu sanyaki a idanunmu,baku son zuwa ganin ƴa'ƴanku,kuma babu damar mutum yace zaizo ganinku saboda kullum baku a ƙasar,'ya ƙarasa maganar tare da ɗaure fuskarshi,    dariya azeema tayi tana cewa"kwantar da hankalinka mutumina,ae wannan zuwan daka ga nayi,bazan koma ba har sai naga an shafa fatihar auranku,kai da wannan namijin zakin,'   tayi maganar cikin zolaya tana kallon Rafayet,aikuwa ya ƙara ɗaure fuskarshi alamar baiso,   Murmushi Abbansu yayi tare da cewa"kada ki samu damuwa,ae kuna anan ma zamusha biki,Abusufyan kawai nake jira ya ƙaraso,don nafison ya shaida wannan ɗaurin auren,ayi komai tare dashi don shine waliyyi"   Jin wannan maganar ta Abban nasu yasa shi buɗe idanunshi tare da miƙewa daga saman sofa ɗin ya nufi hanyar fita,duk suka zuba mashi ido, Sai da yakai bakin kopar fita sannan ya ɗan juyo tare da kallon inda Hajiya azeema take zaune yace"Allah ya huta gajiya,"yana faɗin hakan yasa kai ya fuce daga ɗakin,   Girgiza kai Abbansu yayi tare da cewa"Rafayet sai addu'a abun nashi ƙara gaba yake yi,"murmushi kawai azeema tayi aranta tace"Jinin Alexandra kenan,in har rafayet baiyi mun haka ba,bazan tabbatar da cewa nononta ya sha ba, Ganin rafayet ya fice yasa Omar miƙewa tare da yi masu sallama ya fuce yabarsu donsu samu damar tatttaunawa atsakaninsu yasan sunyi kewar juna sosai, Bayan fitar Omar,azeema ta kalli abban nasu tare da cewa"Yaya hossein,ya maganar zuwan Abusufyan din?dagaske ne yau ɗin shima zaizo?kasan fa ya jima yana samana ran cewa zaizo sai kuma yaƙi zuwa daga baya,abun na damuna sosai,"fuskarta ɗauke da damuwa tayi maganar,   "ya tabbatar mun da zuwan nashi,kuma ina da tabbacin cewa wannan karan dagaske yake mana ba wasa ba,inaso yazo saboda akwai abubuwa da dama da nake son muyi magana akai,na damu dashi sosai,na damu da halin da yake ciki," Jinjina kai tayi tace"amma abba,akwai wata alfarma da nake nema awurinka,"    "Wace alfarma kenan"?acewar abban nasu,   Cigaba da magana tayi"idan Abusufyan yazo nigeria wannan karon banso ku bari ya koma turkey,dan Allah ka ruƙe shi anan,ya zauna akusa dakai,banason yanayin nesa dakai,har yanzu akwai sauran yarinta atattare dashi,shi ne ƙarami acikinmu akwai buƙatar mu janyo shi ajikinmu,don muji menene ke damunshi,meyasa baya son zama ƙasar nan,ni nasan akwai dalilin da yasa abusufyan yake gudun zama anan,tabbas akwai damuwa atattare dashi,"    Abba yace"dama ni bazan barshi ya koma can ba,bazan ƙara yin gangancin barinshi yayi nesa dani ba,koda can daya bar ƙasar batare da sanin mu ya tafi ba,narasa gane mashi ni kaina,ba yarda banyi dashi ba akan yadawo nan gida amma yaƙi saurare na,wannan karan dae mun ci sa'a ya amince zaizo,kuma insha Allah idan yazo bazan barshi ya koma ba,zan ruƙe shi awurina,'   Ajiyar zuciya azeema ta sauke,hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,dama ita burinta Abusufyan yadawo kusa da Yayansu hossein su zauna atare da ƴa'ƴanshi,tafi son taga sun haɗa kansu wuri ɗaya,ita kanta ba da son ranta take zaune a lagos ba,sabo ne kawai sai kuma harkokin kasuwancinta da suka fi yawa acan,    Sun jima suna fira tsakaninta da ɗan uwanta,kafin daga bisani yayi mata sallama tare da fucewa daga ɗakin,komawa azeema tayi tare da kwantawa saman gadon,nan take bacci yayi awon gaba da ita, A 6angaren sehrish kuwa tunda taje school,fuskarta babu annuri ko kaɗan duk tabi ta takure kanta asaman seat ɗinta,ko magana batasan yi,juyowa Amrish tayi ta kalli fuskarta tare da cewa"wai meyake damunki ne Sehrish?duk kin bi kin canza,ki faɗamun mana in akwai damuwa,may be ina da shawarar da zan iya baki,"    shiru tayi na wani lokaci kafin tace"Zan faɗa maki,but pls kada ki sanarwa kowa,"   "Insha allah,i will keep ur secret bazan bari kowa yaji ba,"amrish tayi maganar tare da mayar da hankalinta kan sehrish,    matsowa sehrish tayi kusa da amrish tayi ƙasa ƙasa da muryarta sannan tace"Amrish,babban yayanmu ne ya datse mun gashin kaina,dana kwallafa rai akanshi,na jima ina gyara gashin kaina,sai da yayi tsayi sosai yayi kyau,shi kuma ya datse mun shi da almakashi,baki ga wanda yabar mun ba,ɗan guntu ko parking ma bayayi,in nasa ribbom ma zamewa yakeyi,baya ruƙe gashin,'    Hankali tashe Amrish tace"Are u serious!shi da kanshi yayan naku ya yanke maki gashi?baisan cewa gashi tsada yake yi ba,?amma garin yaya hakan ya faru?ta tambaya tana jiran amsarta,   shiru ta ɗanyi kafin tace"ni kaina bansani ba Amrish,da safe ne naje kai mashi coffee,yana cikin sha wani abu ya sarƙe mashi a throat ɗinshi,ashe gashi ne ya faɗa ciki,kuma ni banawa bane,nayi ƙoƙarin nayi mashi bayani akan hakan,amma bai saurareni ba,kawai yasa almakashi ya datse mun gashin,'ƙarasa maganar tayi muryarta tamkar zata fashe da kuka,   hannu amrish tasa tare da dafe goshinta tace"Ya salam,amma banji daɗi ba wlh,ni babban abunda nafi takaici shine,wazai aure ki a haka da guntun gashi,kinsan fa mazan yanzu sunfi son mace mai dogon gashi,"cike da zolaya amrish tayi maganar tana ƙumshe dariya abakinta,   Harara sehrish ta watsa mata tare da cewa"Oh abun ya zama na zolaya ko?ina faɗa maki damuwata maimakon ki tayani jimami shine kike mun dariya,'    "No,ba haka bane sehrish,nadamu nima sosai,rai na ya 6aci amma kada ki sa damuwa aranki,zan iya taimaka maki da hular gashi in kinaso,'    Cike da farin ciki sehrish tace"dagaske kike ko wasa"?   Amrish tace"am serious,ina dasu ajiye a gida zan ɗauko maki ɗaya daga cikinsu,amma bisa sharaɗin zaki kawo mun gashin kanki da babban yayanku ya yanke maki,inaso zanyi amfani dashi wurin haɗa wata hular gashin,ba ƙaramin kuɗi zamu samu ba,'    murmushi Sehrish ta saki tare da cewa"shikenan insha Allah,zan kawo maki gashin gobe in zanzo school,'    "Allah ya kaimu lafiya,"Amrish ta amsa mata,ci gaba da fira su kayi atsakaninsu har sae da malamarsu ta shigo sannan suka dakata da yin surutun nasu, _💋Boss Bature💋_ Ana gab da za'a tashe su daga school,ciwon ciki yazo mata mai tsananin gaske,gaza jurewa tayi hakan yasa ta miƙe tare da zuwa wurin Aunty ɗinsu ta nemi izinin fita a wurinta,bayan ta amince mata ta fito daga class ɗinsu,sai faman sauri takeyi,hannunta ɗauke da school bag dinta,wani corridor ta nufa inda toilets din makarantar suke a jere,ɗaya daga cikin toilet din ta buɗe tare da shigewa ciki ta rufo shi,juyawa tayi tana kallon cikin toilet din komai na cikinshi fari ƙyal atsaftace,hannu tasa tare da zuge zip ɗin jakarta,ta ciro pad din da tazo da ita guda ɗaya,dama tun last week take jin alamun zuwan al'darta amma baizo ba,sai dae stomach pain da take ta fama dashi,wannan dalilin ne yasa take yawo da pad a jakarta just in case,    ajikin towel hanger,ta rataya jakarta,sannan ta zame dogon wandon jikinta,pant ɗin ta curo tana dubawa taga ko ya fara zuba,babu ajikin pant ɗin,amma da taje wurin yin tsarki bayan tayi fitsari sai ga ɗigon jinin ya fito,cikin sauri ta sanya pad din ajikin pant dinta,sannan ta sanyashi ajikinta,ta ɗauko dogon wandon ta mayar ajikinta,sai da ta zura shi ajikinta,ta ɗauko jakarta tana ƙoƙarin fita daga cikin toilet din kenan,cikinta ya murɗa mata,wani irin raɗaɗi mara daɗin ji,nan take ta zukunna ƙasa hannunta dafe da cikinta,zufa ce ta shiga gangaro mata agefen fuskarta,daƙyar take fitar da numfashi,lokaci guda gaba daya ta galabaita ta fita hayyacinta,anan ta faɗi kwance saman tiles tana juyi ita kadae acikin toilet ɗin,babu wanda yasan abunda ke wakana. *Junaid* *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 *Na sadaukar da wannan zazzafan page din,ga dukkan masoyan littafin Abban sojoji,especially members na paid grp dina,Abban sojoji paid grp,Father of soldiers,Abban sojoji Vip grp,da kuma Junaid romeo Much luv Allah yabar zumunci anatare insha Allah (08103884440)*😍😘 *Bazan manta daku ba,waɗanda suka ƙarfafamun guiwa wurin rubuta littafin nan,har yau ina alfahari daku, Fadeela lamiɗo da kuma sadeeq abubakar CEO na Lafazi writer association,da kuma auntyna takaina,bazan fadi sunanta ba,sai na nemi ixninta saboda tsaro🤣😂😅 Da kuma sauran members dinda akayi fadi tashi dasu,suma duk zan fadi sunayensu nan gaba* *Abban sojoji paid book ne,duk maison siye zaiyi mun magana kai tsaye ta layina,but pls banda kiran waya,only message ta whatsapp,bana shariya muddin mutun ya turamun saƙo zan duba ne,indae ina free,in mutun yayi payment zan tura mashi duka na baya da aka wuce shi har inda muke so* ❤🤍❤ *Junaid* Tun bayan daya kai Sehrish school ya biya gidansu wani abokinshi,wanda tun suna secondry school suke tare,acan ya yini har bacci yayi awon gaba dashi asaman gadon mamarsu abokin nasu,saboda tsabar gatanci bama gadon abokin nashi ba,a ɗakin mamarsu yayi baccin,daga shiga su gaisa da ita,ya samu ta shiga cikin toilet,shi ne ya ɗan kishingida saman gadon ya shiga sharar bacci,wuraren ƙarfe daya ya farka ganin lokacin tashin su sehrish daga school ya kusa yi,nan yayi sallama da mutanen gidan,jiki na rawa ya shiga motarshi tare da barin gidan,   da gudu ya fisgi motar saboda ya ƙarasa gida da wuri,ba don komai ba sai don alkawarin da yayi ma sehrish na cewa in zaizo ɗaukarta daga school zai nuna mata wankan da zai ɗauka na shaddar shi,    yana ƙarasowa cikin gidan bayan yayi parking din motarshi,ya wuce cikin main palour ɗin,a lokacin duk sun fita yin sallar azhar da ake cikin kira,bedroom dinshi ya shige tare da rage kayan da ke jikinshi ya faɗa cikin toilet,shaf shaf yayi wanka cikin minti goma sha biyar,ya fito daga cikin toilet din,jikinshi sanye da bathrobe,     Gaban dressing mirror dinshi ya zauna,yadda kasan mace haka ya zauna yana gyara jikinshi,sai da yabi ko'ina na jikinshi ya shafe da mai,sannan ya shiga gyara sumar kanshi,bayan ya kammala ya miƙe tare da komawa wurin wardrobe,ya buɗe tare da ɗauko shaddar,a natse ya shiga zura kayan ajikinshi bayan yasa vest da short farare kal,rigar takai masa har guiwarshi,sai wandon,lokacin daya kammala sanya shaddar ajikinshi dawowa yayi tare da tsayawa gaban madubi yana kallon fuskarshi ta ciki ya Allah!shi kanshi sai da ya tsorata da irin kyan da yayi,kamar shiya zana kanshi don kyau,shaddar ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,sae faman salƙi take ajikinshi kamar wani sabon ango,kyakkyawan murmushin nan nashi ya saki tare da cewa"junaid kenan yakamata ka zama namiji mana,ka cire duk wata fargaba yau ka tunkari sehrish gaba da gaba ka bayyana mata irin son da kake mata batare da jin shakkar komai ba,'    shiru ya danyi aranshi yana cewa"gaskiya ina jin fargaba fa,anya reesh zata amince da son da nake mata?in tace bata sona fa?tabbas zan iya rasa raina,amma zan jure yau dae na fahimtar da ita tsananin son da nike mata,'   Ƙarasa maganar yayi tare da ɗauko hula mahadin kayan wadda take tsadaddar gaske sai daukan ido take itama ash colour ya aza saman kanshi,hmmmm abun ba'a magana madarar kyau ba kaman da sumar kanshi ta dan fito daga baya.   Zura takalmanshi yayi masu kyau da tsadar gaske suma mahadin kayan,sannan ya koma gaban dressing mirror ɗin ya ɗauko turarenshi ya shiga feshe jikin shi dashi ko'ina saƙo da lungu,nan take ƙamshin ya gauraye ko'ina na ɗakin,   Key ɗin motar shi ya dauko sannan cikin sauri ya fito daga ɗakin nashi ya sauko downstairs,babu kowa a falon duk sun tafi salla, A hankali yake driving din motarshi fuskar nan dauke da annuri,sae da yafara tsayawa masallaci yayi sallah,sannan ya miƙi hanyar makarantarsu sehrish,shiga ciki yayi tare da yin parking ɗin motar sannan ya fito ya tsaya tare da jingina bayanshi a jikin motar,zuba ido yayi yana jiran fitowar sehrish amma babu ita babu alamarta,ga students sai fitowa sukeyi,wasu na hawa bus wasu kuma ana zuwa ɗaukarsu,    Gajiya ya fara yi da tsayuwar, "Wai ina reesh ta shige ne,ta barni tsaye ina ta faman jiranta,'rai aɗan 6ace yayi maganar,    Juyawa yayi tare da kifa kanshi ajikin motar ya ɗan lumshe idanunshi,    adai dai lokacin Jahad ta fito hannunta ruƙe da school bag ɗinta,tana neman hossana duk atunaninta zata same tane a wurin da suke jiran osman yazo ɗaukarsu amma babu ita,da alama ma Osman ɗin bai ƙaraso ba,   guntun tsoki taja tare da juyawa zata koma ciki,karaf idonta suka sauka akan Junaid,cike da mamaki take kallonshi,tana ɗan leƙen fuskarshi daga inda take, Bakomai ne ya faɗo mata aranta ba,face alƙawarin da tayi ma hosana nacewa zata nemo mata ya Omar,aranta tace"ya Omar yace ƙaninshi ne wannan,kodae naje na tambaye shi ina ya Omar yake,may be ya taimakamun wurin haɗa ni dashi,   ƙarasawa wurin motar junaid tayi ta ɗan tsaya daga bayanshi,tare da yi mashi gyaran murya don ya juyo,    jin shiru bai juyo ba yasa tayi mashi sallama"Assalamu Alaikum,"   Nan ma bai juyo ba,hannu tasa ta ɗan ta6a bayanshi a hankali,aikuwa a firgice ya juyo,ita kanta jahad sae da ta ɗan tsorata taja da baya ganin yarda ya juyo kamar ya tsorata,     Murmushi ta sakar mashi tare da cewa"am sorry,naga kamar ka razana,tun ɗazu nayi maka sallama baka ji ba,'    harara junaid ya watsa mata,har sae da tasha jinin jikinta,rai a6ace yace"yanzu abunda kikayi mun kin kyauta!kinsan tun yaushe nike atsaye nan ina jiranki!"    Gaba ɗaya jahad ta gama ruɗewa jin abunda Junaid ke cewa, Cikin sauri tace"dama...am..inaso ne na tambayeka game da yayan.......'   Kafin ta ƙarasa maganar tuni junaid ya gama hasala,ruƙo hannunta yayi tare da buɗe motar,yace mata wuce ki shiga,    Murya na rawa jahad tace"bangane me kake nufi ba?   A tsiwace yace"Ni ki wuce mu tafi,'   duk yarda jahad taso ta fahimtar da junaid cewar ba ita bace wadda yake nema ba,amma yaƙi fahimta,shi duk atunanin shi sehrish ce,   Tursasa mata yayi har sae da tashiga cikin motar,sannan ya shiga yaja motar da gudu ya fisgeta suka fuce daga cikin makarantar, A natse yake driving lokacin daya hau saman shantalelen titin,zuba mashi ido jahad tayi tana kallonshi,ta wutsiyar idonshi yake kallonta,ganin yarda ta zuba mashi ido yasa shi ɗan juyowa tare da sakar mata wannan kyakkyawan murmushin nashi,   mamaki ne ya kama jahad,gaba ɗaya abun ya gama ɗaure mata kai,aranta tace kodae yana da ta6in hankali ne?in ba haka ba, nida bamu ta6a haɗuwa dashi ba amma kuma ya nuna ya sanni har ya tursasa mun na shiga motar shi,yanzu ni bansan ya zanyi na fahimtar dashi ba,kada hosana ta fito tayi ta nemana acikin school,    "Reesh banji kin yabi wankan nawa ba?ko banyi kyau bane,"yayi maganar a yayin da yake kokarin parking ɗin motar a gefen titi,sannan ya juyo yana kallonta,   zuru jahad tayi tana kallonshi,hakan ba ƙaramin 6ata mashi rae yai ba,cikin shagwa6a yace"Wai menene haka reesh,duk kin bi kin wani sauya mun,saboda ke fa na ɗau wankan nan don nazo na nuna maki,amma kin zuba min ido kina kallona kamar yau kika fara gani na,'   A tsorace take da shi,don tagama yarda cewa yana da ta6in hankali,cikin en ina tace"amm...ni fa...ba..' kasa ƙarasa maganar tayi gabanta na faɗuwa,ganin yarda junaid ya matso dab da ita,ya ƙureta gaba ɗaya ƙamshin turaren shi ya gama kashe mata jikinta,   murmushi ya ɗan sakar mata tare da cewa"kallon ya isa haka reesh,let's talk about serious issue,akwai abunda na jima inason sanar dake,amma inajin fargabar amsar da zan samu a wurinki,'ya ƙarasa maganar yana kallon cikin kwayar idanun jahad amatsayin sehrish,    a hankali jahad ke bin kyakkyawar fuskarshi da kallo,tun daga kan eye brows ɗinshi,dogon hancinshi da kuma red lips ɗinshi,komai nashi mai kyau ne kuma mai jan hankali,    Anatse yaci gaba da magana,"reesh,nasan cewa baki ɗauke ni cikakken namiji ba kamar saura,saboda na cika wasa da shiririta da kuma shagwa6a,kuma bani da aikin yi sae zama acikin gida kamar mace, nasan ba kowace mace bace zata so ta aure ni a haka" ya ɗan dakata da maganar yana kallonta,wannan karon babu alamar wasa a fuskarshi,   natsuwa jahad tayi tana sauraran shi,    Hannayenshi yakai tare da ruƙo nata cikin nashi,nan take jahad taji gabanta ya faɗi,   ɗagowa yayi awani irin yanayi yaci gaba da magana"duk wannan abun da nake reesh zan daina in baki so,idan har kika amince mu kayi aure,xan zama kamar yarda kikeso,nidae burina ki amsa mun cewa kina sona,kuma zaki aure ni,ni ban ta6a son wata ƴa mace ba in bake ba,na shaƙu dake sosai kuma ina da tabbacin cewa in mukayi aure zaki bani kyakkyawar kulawa,pls reesh tell me will u marry me"?    Tamkar zai yi kuka haka yayi mganar yana jiran amsarta,   Shiru jahad ta ɗanyi tana yanke shawara da zuciyarta,tunda dae bai da cikakken hankali bari na jaraba biye mashi kona samu mu rabu lafiya Ƙarasa zancen zucin nata tayi tare da mayar da idanunta akan nashi tace"bana tunanin cewa akwai macen da zata samu namiji kamarka ta nuna bataso,kai na daban ne,kana da komai da mace zata buƙata a wurin namiji,kayi mun sosai kuma ka kwantamun araina,tayin soyayyar da kayimun na kar6a hannu bibbiyu,kuma na amince zan aure ka.....'    Tsantsar mamaki ne ya kama junaid bai ta6a tunanin cewa rishi zata amince da soyayyarshi ba,cikin sauƙi haka batare da ta wahalar dashi ba,ajiyar zuciya ya shiga saukewa wani irin farin cikine ya lullu6e shi,mara misaltuwa a hankali ya shiga furta"Alhamdulillalh Allah nagode maka daka nuna min wannan ranar,dama sae da raina ya bani cewa reeshi ɗina bazata gujeni ba...."   Fuskar jahad ɗauke da murmushi take kallonshi har lokacin hannunshi na ruƙe da nata,    farin cikin da tagani a fuskarshi yasa taji aranta dama dagaske ita yake so,da ta bashi kyakkyawar kulawa,amma da alama akwai wadda yake so,tunda taji ya ambaci sunan reesh wannan ne yasa jikinta yin sanyi, "Allah yasa ba mafarki nake ba,in ma mafarki nake kada ki tashe ni,'yayi maganar yana dariya tare da zame hannun shi daga nata,ya tallabo fuskarta da tafin hannayenshi,yana ƙare mata kallo,hakanan ya dinga jin kamar ta canza mashi,ƙura mata ido yayi kamar mai son gano wani abu,   "Reesh kin canzamin sosae,sai nike ganin kamar bake ba,'    Shiru jahad tayi tana cigaba da kallonshi,sakin fuskarta yayi tare da zura hannunshi cikin hijab ɗin jikinta,ae kuwa a firgice jahad ta ƙanƙame jikinta dake ta faman kerma cike da tsoran abunda zaiyi mata,    Cikin lallausar suman kanta yakai hannunshi yana shafa gashin kanta yace"meyasa baki ɗaure gashin kanki ba?bai takura maki ahaka?    atsorace jahad tace"ni na cire shi,yana acikin school bag ɗina,"    Zame hannunshi yayi daga cikin hijab ɗin nata,   "Zan ɗaure maki shi,ki ɗauko ribbom ɗin naki,"   Kamar karta ɗauko mashi amma tunawa da cewar yana da ta6in hankali in ranshi ya 6aci zai iya kai mata bugu,hakan yasa ta janyo school bag ɗin tare da zuge zip ɗin,ta curo mashi ribbom din ta miƙa mashi sannan ta mayar da jakar abayanta,   kar6a yayi tare da zura shi a cikin hannunshi,sannan ya ƙara matsawa kusa da ita sosai,cire hijabin jikinta yayi sannan ya janyota asaman chest ɗinshi,gaba ɗaya jahad ta gama rikicewa,ba ƙaramin yanayi junaid ya jefa ta ba,   lamo tayi ajikinshi tana shaƙar daddaɗan ƙamshin turarenshi,   Xuba ma yalwataccen gashin nata ido yayi yana kallonshi,kafin daga bisa ni ya sanya hannunshi tare da tattaro shi wuri guda,ya ɗaure mata shi da ribbom ɗin,    muryarshi taji acikin kunnanta yana cewa"Reesh,ya akai naga launin gashin kanki ya canza?ba brown colour bane?yanzu kuma naga ya koma dark black,?kodai idona ne ke nuna min ba daedae ba'?shiru jahad tayi batace mashi komai ba,saboda bata da amsar da zata iya bashi,   jin tayi shiru yasa ya ƙyale maganar,hannu yasa tare da rabata da jikinshi,bin ta da kallo yayi ganin yarda take ta faman lumshe ido kamar mai jin bacci,   Cikin sanyin murya yace"Reesh,kina jin feelings ɗin da nake ji agame dake"?   buɗe ido jahad tayi sosai tana kallonshi da wata irin kasalalliyar murya tace"eh,'    jinjina kanshi yayi tare da cewa"nasani,dama nasan kema zakiji abunda nake ji,pls reesh just for today kawai,kiyimun kiss koda a gefen fuskata ne,inaso naji ya ake ji,'   Shiru jahad tayi tana tunanin ya zatayi da wannan ɗan tahalikin,gashi duk yabi ya kashe mata jikinta,ita tausayi ma yake bata saboda ta6in hankalin da yake fama dashi,tausayin shi ne taji ya kamata,mutun har mutun amma bai da cikakken hankali tunda inda yana da hankali ai ba yarda za'ai ya kasa gane ba itace wadda yake nufi ba,tunawa tayi da hosana dake fama da irin lalurarshi,amma nashi haukan yafi na hosana,don bata ta6a ganin wanda bata sani ba,ta liƙe mashi da sunan tasan shi,     bata ƙarasa zancen zucin nata ba,muryar shi ta kuma katseta da cewa"pls reesh,just for today,"    ajiyar zuciya jahad ta saki tare da kai bakinta zata manna mashi kiss acikin dimple ɗinshi,batayi wani aune ba taji bakinta acikin nashi tsulundum,sakamakon wata mota da ta bugi bayan motar shi,wannan girgizar da motar tashi tayi ne yasa bakinta komawa cikin nashi,gaba ɗaya junaid yabi ya rikice ya zauce ya haukace mata,sosai ya ƙankame ta ajikinshi,yana kissing ɗin bakinta ta hanyar zura tongue dinshi acikin bakin,ita kanta jahad a lokacin ta gaza control ɗin kanta,biye mashi tayi, Sosai junaid ya shiga romancing ɗinta kamar zai zauce,duk yarda jahad taso ta kwace kanta a hannunshi amma yaƙi barinta,sai da yayi mai isarshi sannan ya zame jikinshi daga nata,cikin sauri jahad ta kifa kanta asaman laps dinta,tana faman sauke ajiyar zuciya,sam tagaza yarda cewa itace da kanta ta ba wani namiji damar kissing lips ɗinta abunda bata 6ata yi ba,to dama dae duk inda mace da namiji suka ke6e irin haka na ukkun su shaidan ne,Allah ya kyauta.     jikinshi ne yayi sanyi,shi kanshi baisan cewa abun zai kaisu ga haka ba,daƙyar ya iya tashin motar da wata irin kasala ajikinshi yake driving din,ya hau saman titi sosae tare da wucewa dasu gida,    _💋Boss Bature💋_ tashin hankali!Lokacin da Hosana ta fito a nan ta samu osman yana jiransu tsaye a bakin motarshi,    ƙarasawa tayi wurinshi tana cewa"ya Osman Ina jahad ɗin?ina ta nemanta banganta ba,nayi tunanin ta rigani fitowa ne,"    "Wai kina nufin jahad bata acikin school ɗin naku"?ya tambaya hankali a tashe yana kallonta,. daga mashi kai tayi alamar eh tace"babu kowa acikin makarantar ya Osman,na duba ko'ina ban ganta ba,"   Gabansa ne ya faɗi rass,saboda kullum jahad ita ke riga hosana fitowa,yau kuma hosana ta rigata fitowa,tabbas akwai matsala,   cikin sauri yace"shiga ki zauna bari nashiga cikin classes din na duba ko zan same ta acan,Allah dae yasa ba wani mummunan abune ya faru da ita ba,'   Ya ƙarasa maganar tare da yin saurin shigewa cikin makarantar,buɗe motar hosana tayi tare da shigewa ciki ta zauna tana jiranshi,   lokacin da Osman ya shiga cikin classes din yana neman jahad,duk ajin daya duba babu kowa wayam duk sun tafi gida,ko'ina ya dinga bi na makarantar saƙo da lungu yana dubawa amma babu jahad babu alamarta,tun yana sa ran ganinta har ya fidda rae,yafi ƙarfin awa ɗaya da rabi acikin makarantar yana neman jahad amma bai ganta ba,   Cikin sauri ya fito jiki na rawa ya koma cikin motar,ya zauna a mazaunin driver,   Ganin ya dawo shi kadae yasa hosana cewa"Ya osman ina jahad din?baka ganta ba"?    "Na duba ko'ina banganta ba,bansan ina jahad taje ba,bari na fara kaiki gida nasan kin gaji sosai,"    jan motar yayi tare da fucewa daga cikin gate ɗin makarantar,duk yabi ya ruɗe saboda fargabar kada ace wani abune ya faru da jahad,yana jiyo hosana tana shessheƙar kuka tana cewa"Nashiga uku,Allah yasa jahad bata 6ace ba,bansan ya zanyi ba in na rasata ba,kamar yarda na rasa sehrish,"     "Kada ki damu jahad tana cikin ƙoshin lafiya,zan nemo maki ita,in ma ban sameta ba,zan kira major na sanar dashi halin da ake ciki,nasan zaiyi ma marshal Magana,"ya ƙarasa maganar a lokacin da yake shiga kwanar gidan Abusufyan, Yana shiga ciki ya sauke hosana,sannan ya fisgi motar da gudun gaske ya fuce daga gidan, Abunda ya faru bayan fitar motar osman daga cikin school din,Sai ga sehrish hannunta ɗauke da school bag ɗinta,daƙyar take iya tafiya saboda ciwon da tasha,ta jima acikin toilet din tana juyi kafin Allah ya kawo mata sauƙi harta samu ta fito, ganin babu kowa acikin makarantar yasa taji gabanta ya fadi,nan tashiga fargabar Allah yasa junaid bai tafi ba,tasan dole ya gaji da jiranta, Lokacin da taƙarasa wurin gate din taga babu kowa sai security guard din dake tsaron makarantar,tamkar ta aza hannu akai ta fashe da ihu haka taji, Ganin yarinya tsaye cikin damuwa yasa mai gadin ya ƙaraso wurinta yana tambayar ko lafiya, muryarta tamkar za tayi kuka tace"Mai ɗaukata nake nema,kuma naga babu kowa acikin makarantar,bansan ya zanyi ba," mai gadin yace"meyasa baki fito kin tsaya anan waje ba?me kikeyi acikin makarantar ne"? cikin shessheƙar kuka tace"bani da lafiya ne,bacci ne ya ɗauke ni kuma babu wanda ya tashe ni,shiyasa bansamu na fito ba akan lokaci," "Kuma baki da waya a hannunki"?acewar mai gadin, ɗaga mashi kai tayi alamar eh, "Ko numbar wani baki ruƙe a cikin kanki ba," "Bani da numbar kowa,ban ruke akaina ba," Cike da takaici mai gadin yace"kaji matsalar,ni yanzu bansan ya zanyi dake ba,amma me zai hana ki ɗan fita daga wajen gate ɗin,wata'ƙil shi drivern naki ya dawo daukarki,nasan ma zai dawo ne,da zarar sunji shiru baki ƙarasa ba", Amsa mashi tayi da toh,sannan ta fice daga cikin makarantar ta tsaya a bakin gate din,tana ta ƴan waige waige ko zata hango motar junaid, _💋Boss bature💋_ A hankali motar junaid ta ƙetare babban gate din gidan nasu,a lokacin jahad ta ɗago da kanta,ta cikin glass ɗin take hangen katafaren gidan,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,yau gata acikin gidansu ya Omar dinsu,koba komai zata hadu dashi harma ta sanar dashi halin da suke ciki na rashin ganin shi,addu'a tashiga yi acikin ranta Allah yasa Ya Omar na nan, tsayar da motar junaid yayi tare da buɗewa ya fito sannan ya zagaya ya buɗe ma Jahad motar,cikin sanyin murya yace"Reesh,am really sorry game da abunda ya faru a tsakanin mu,na fita hayyacina ne shiyasa,kinsan cewa ba halina bane.....kuma bazan ƙara ba insha Allah, Murmushi jahad ta sakar mashi ayayin da take fitowa daga cikin motar tace"just forget about it,komai ya wuce,na yarda dakai sosai nasan cewa bada son ranka hakan ta faru ba, ba ƙaramin daɗi junaid yaji ba,ya jima yana mamakin nasarar daya samu akan reeshi ɗinsa,farin ciki kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha, Bayan ya rufe motar ya ruƙo hannunta suka shige cikin gidan atare,a ruɗe jahad ke kallon katafaren gidan,jinjina kai kawai takeyi acikin ranta tana cewa"wai dama a wannan daular ya Omar ke rayuwa!gidan yayi mun kyau ya haɗu sosai,Allah yasa yana ciki,inaso na cika ma hosana alƙawarinta na ganin na haɗata da ya Omar dinta, Babu kowa acikin main palour ɗin,sakin hannunta junaid yayi tare da cewa"bari na shiga ciki na huta,da anjima zan shigo muyi magana," amsa mashi tayi da toh,cikin sauri junaid ya wuce bedroom din Abbansu, tashin hankali,jahad fa batasan ina zata dosa ba,gata dae acikin gidansu Omar,batasan a ina zata ganshi ba, Tsayawa tayi ƙiƙam batare da ta motsa ba, Gyaran muryar da taji ne yasa ta yin saurin juyawa don taga wanene, Azmee ce ta fito sai faman sakar mata murmushi takeyi,jikinta sanye da jallabiya,ta ɗaure kanta da mayafi,ta fito fess abunta, Gaban jahad ne ya shiga faduwa aranta tashiga tunanin cewa kodae wannan ce mahaifiyarsu?Amma meyasa naga tana sakar mun murmushi kamar tasanni itama...? Bata ƙarasa zancen zucin nata ba,azmee ta ƙaraso tare da janyota jikinta ta rungumeta tana cewa"Sannu da dawowa kyakkyawata,ya school din? Tayi maganar tare da raba jikinta daga na Jahad, Zuru jahad tayi duk tabi ta dabarbarce ta rasa ganema wannan abun al'ajabin,tamkar a mafarki haka take ganin wannan ikon Allah, "Rishi lafiya naga kina bina da kallo?kodae bakya jin daɗi ne?nayi magana baki amsa mun ba" Cikin en ina jahad tace"am...um...lafiya lou,makaranta Alhamdulillah,' Azmee tace"ko ke fa,shigo daga ciki na hada maki lunch ki ci,ko kya dawo daedae don na lura yau ba ƙaramar yunwa kika kwaso ba," Tayi maganar tare da ruƙo hannun jahad taja ta suka nufi dakin sehrish,da kanta ta buɗe mata kopa tare da shigar da ita ciki tace"ki zauna ki huta,yanzu zan haɗo maki lunch,"tana faɗin hakan ta rufe mata dakin, Abun ya gama ɗaure mata kai,juyawa tayi tana ƙarema bedroom ɗin kallo ba ƙaramin kyau yayi mata ba,daga bisani kuma ta shiga damuwa akan wane hali hosana ke ciki,tasan cewa zasu nemeta sosai,kuma in basu ganta ba hankalinsu bazai ta6a kwanciya ba, komawa tayi daga gefen gadon sehrish ta ɗan zauna,ya zama dole in koma gida,kada hosana tayi ta kukan rashina akusa da ita,bansani ba ko zan samu ya omar acikin gidan nan ba,ni ba komai yafi ɗauremun kai ba face yarda suke nuna kamar sun sanni,bayan bamu ta6a haduwa da kowannansu ba,to kodae dukkansu suna da mental illness ne?ta jefa ma kanta tambaya, Turo kopar azmee tayi tare da shigowa hannunta ɗauke da tray wanda ta shirya mata lunch,ƙarasawa tayi tare da ajiye mata tray din asaman bedside drawer dinta tace"Wannan farfesun da kike gani,hajiya azeema na shirya mashi,ƙanwar abbanku da nake gaya maki,tana nan ta iso,nasan bakisanta ba,amma kin ta6a ganinta lokacin da Sgr da Omar suka dawo daga U.S kin tuna"? Fuskarta ɗauke da murmushi takeyi mata maganar, Jin ta ambaci sunan Omar yasa jahad cewa"Ya Omar na nan"? Azmee tace"eh,yana acikin part dinshi,amma meyasa kika tambaye shi?maimakon ki tambayeni mutumin ki Sgr"? "Babu komai,kawai inason ganin shi ne,"ta bata amsa, Azmee tace"ki bari idan kin kammala shan farfesun sae kije ki same shi adakin shi,' gyaɗa kai jahad tayi tare da cewa toh,nagode sosai,bari na fara sha, Juyawa azmee tayi tare dayi mata sallama ta fuce daga dakin,a ranta tana tunanin ko wani abu ke damun rishin ne taga duk tayi sukuku. Zama jahad tayi tare da dauko plate ɗin dake ɗauke da farfesun,sae uban ƙamshi ke tashi,duk da tana cikin tashin hankali hakan bai hanata shan farfesun nan ba,sae da taci ta ƙoshi, sannan ta miƙe tare da shiga toilet ta wanko hannayenta, Bayan ta fito komawa tayi saman gadon ta zauna cike da zullumin mai zai biyo baya, _💋Boss Bature💋_ Marshal Omar na kwance saman gadonshi yayin da idanunshi suke kallon saman ceiling bakomai yake tunani ba face hosanar shi,kowane hali take ciki yanzu?taci abinci kuwa?tambayoyi iri iri ya shiga yi ma kanshi, yana cikin wannan tunanin wayarshi dake ajiye gefenshi ta shiga yin ringing,miƙa hannu yayi tare da daukar wayar,duba mai kiran nashi yayi ganin sunan Major ya bayyana akan screen din wayar yasa shi saurin ɗaga wayar tare da karata akan kunnanshi, Ko sallama major baiyi mashi ba saboda tsabar tashin hankalin da yake ci, "Yalla6ai yarinyar nan fa ta 6ace,an neme ta an rasa ko'ina na makarantarsu,ɗazu osman ya kira ni awaya yake sanar dani cewa yaje ɗaukarsu a school,hosana kaɗae ya gani banda jahad,mun duba ko'ina babu ita," Waro ido waje Omar yayi ba arziƙi ya sauko daga saman gadon yana cewa"Major!ban fahimci me kakeson sanar dani ba!kayi mun da yaren da zangane," Major yace"yalla6ai,jahad ce ta 6ace a school,' Rai a6ace Omar yace"Garin yaya hakan ta faru!taya akai Osman yayi gangancin da har ya bari jahad ta 6ace bai ganta ba!'duk inda take ku nemo mun ita in ba haka ba,ran kowa zai 6ace don bazan lamunta ba," Yana ƙarasa maganar ya kashe kiran,gaba daya ya rasa inda zaisa kanshi yaji daɗi,hankalin shi ba ƙaramin tashi yayi ba,tsoronshi kar ace jahad ta gudu ne don taje nemanshi saboda halin da hosana ke ciki, Zagaye ya shiga yi acikin ɗakin nashi,zuciyarshi nata tafarfasa saboda tsabar 6acin ran da yake ciki,abubuwa sunyi mashi yawa,yana cikin damuwa sosai,ga kuma wata damuwar da major ya ƙara mashi,na 6atan jahad, ɗago da wayar ya sake yi a hannunshi ya shiga dialing wasu numbers, sannan ya dannama numbar kira,nan take kiran Ya shiga aka ɗaga wayar, tun kafin yayi magana wata murya kakkaura ta karaɗe kunnanshi da cewa"We are waiting for ur command sir," Cikin harshen turanci omar ya shiga basu bayani akan 6atan jahad, Ya ƙarasa maganar tare da cewa yanzun nan zan tura maku da hoton ta,banason ta ƙara 1 hour awaje,duk inda take ku nemota,adawo mun da ita gida," "Okey sir,'suka amsa mashi,sannan yayi rejecting kiran nasu, sai bayan daya kashe wayar sannan ya tuna cewa baida hotonsu,amma yasan baza arasa ba wurin osman, Batare da 6ata lokaci ba,ya kira osman awaya,bugu ɗaya osman ya ɗaga kiran cike da fargabar abunda omar zai sanar mashi, "Osman!" Murya na rawa osman yace"Na'am yalla6ai," "Inaso ka turomin hoton jahad yanzu in kana dashi awayarka,inma babu ka ɗauko mun hoton fuskar hosana,ina jiranka yanzu karka 6ata mun lokaci,' yana kai ƙarshen maganar tashi ya katse kiran,cigaba da zagaye ɗakin yayi yana jiran osman, within 15mins,sai ga kiran osman ya shigo, ɗaga kiran yayi tare da karawa a kunnanshi, On the other hand Osman yace"yalla6ai na turo da hoton,ta cikin Whatsapp dinka," "Okey," ya amsa tare da katse kiran,yatsun hannunshi har kerma sukeyi wurin duba whatsapp dinshi,anan yaga hoton da Osman ya turo mashi,zuba ma hoton ido yayi yana kallonshi,nan take yaji kewarta ta kama shi sosai,hoton hosana ne Osman ya ɗauko mashi,da alama sabon hotone yayi mata da wayarshi,ko uniform dinta bata cire ba,fuskarta da alamun hawaye saboda kukan da tasha na 6atan Jahad, Lumshe idonshi yayi tare da buɗesu akan hoton yana ƙare mashi kallo,a hankali ya furta"I love u so much hosana,nayi missing ɗinki sosai,kamar nayi hauka,nashiga damuwa sosai akan rashin sanyaki a idona,bazan iya jurewa ba hosana,kina buƙata ta a kusa dake,zanzo don na lallashe ki nasan zaki shiga damuwa sosai akan rashina da kuma rashin jahad akusa dake, Tura masu hoton yayi sannan ya kira major awaya ya sanar dashi cewa ya jira shi a waje,gashi nan fitowa, Yana kammala yin wayar cikin sauri ya fito daga part ɗinshi,ya sauko downstairs,da sauri da sauri yake nufar hanyar fita daga main palour din, yana ɗaga ƙafarshi zai fita yaji an ambaci sunan shi"Ya Omar," gabansa ne yaji yayi wani irin bugu,aranshi yace"wannan ae muryar Jahad ce, da saurin gaske ya juya tare da kai idanunshi wurin da jahad take tsaye sanye cikin uniform tana kallonshi,fitowarta kenan daga bedroom din sehrish,cikin sanɗa take tafiya zata gudu daga gidan,kwatsam ta hango shi sai faman sauri yake yi zae bar gidan, Kanshi ya gama ɗaurewa binta yayi da kallo gaba ɗaya ya rikice aranshi ya shiga tunanin cewa anya ba kunnan shi bane suka jiyo mashi muryar jahad!wannan ae yarinyar gidansu ce sehrish,muryarta ce tayi mashi gizo yaji kamar ta jahad, Murmushi ya saki tare da nufarta yana cewa"Sister har kin dawo daga school ɗin?ya karatun naku,ina fata kina mayar da hankali ko? Kamar zatayi kuka tace"Ya Omar,Jahad fa ce! Nice jahad,ya Omar meyasa ka tafi kabarmu,"! Zaro ido waje Omar yayi cike da mamaki yake kallonta, muryar shi na rawa yace"Jahad!dagaske kece kodae kunnena ne ke jiyemun ba dae dae ba"? fashewa tayi da kuka tare da ƙarasawa wurinshi ta kwantar da kanta asaman ƙirjinshi tana cewa"Ya omar dama kana nan,da ranka da lafiyarka amma kadaina zuwa wurinmu?meyasa ya Omar?bakasan halin da muka shiga ba ni da hosana,na rashin ganin ka,' tashin hankalin da ba'a sama shi date, ruko hannunta Omar yayi tare da janta suka shiga cikin wani corridor inda ba kowa,sannan ya kalle ta cike da mamaki yace"Jahad!nagaza yarda cewa kece!taya akai kikasan gidan mu har kika zo? cikin shessheƙar kuka tace"bani na kawo kaina ba,kawo ni akayi,wannan ƙanin naka junaid,wanda ka ta6a nuna mana hotonshi nida hosana a gida,shi ya ɗaukko ni daga school ya kawo ni gidan nan,bansan meyasa ya ɗauko ni ba,ya nuna kamar yasanni bayan bamu ta6a haduwa dashi ba.....' Tun kan ta ƙarasa maganar Omar yace"subhanallahi!an samu matsala,junaid yayi kuskuren ɗauko ki jahad,Yarinyar gidan nan yaje daukowa a school,da yake kuna kama da ita sosai,komai na fuskarku iri ɗaya sak,shiyasa ya ɗaukko ki amaimakonta,' mamaki ne ya kama jahad jin abunda Omar yace,sae lokacin ta tuna da sunan da Junaid ya dinga kiranta wato Reesh,taya akai suke kama da yarinyar gidansu har kanin nashi ya gaza banbantasu!" ta jefa ma kanta tambayar da bata da amsarta, "Jahad,muje na sauke ki gida,in yaso sai mu ƙarasa tattaunawa acan," Ya ƙarasa maganar tare da fitowa ruke da hannunta suka fice daga cikin babban falon,anan waje ya samu Major tsaye jingine da mota yana jiranshi, Koda ya ganshi ruƙe da hannun jahad mamaki ne ya kamashi,dama shi bai ta6a ganin Sehrish ba,tunda ba shiga ciki yake yi ba,basu ta6a arba da ita ba, Fuskarshi dauke da murmushi yace"Sir!anganta kenan"? Omar yace"eh,ba rabon musha wahala,wai junaid ne ya ɗaukota daga school shi duk atunanin shi wannan yarinyarce ta cikin gidan nan,da yake kamanninsu iri daya sak,' major yace"ikon Allah,amma ni ban ta6a ganin yarinyar ba,' ya ƙarasa maganar a yayin da yake buɗe masu mota suka shige ciki,sannan ya tashi motar yabar gidan ɗauke dasu, _💋Boss Bature💋_ A 6angaren sehrish kuwa,tana cikin tsayuwar nan agefen titi tana jiran zuwan junaid,sai ga motocin waɗannan fusatattun sojojin da Omar ya turo don su nemo mashi jahad,ae koda sukayi arba da sehrish,suka duba hoton da Marshal Ya tura masu suka ga iri ɗaya fuskar,sae ransu ya basu cewa itace yarinyar da Omar yace su nemo mashi, Da sauri suka tsayar da motocin nasu tare da diddirowa daga saman motocin tamkar wasu zakuna haka suka tunkari sehrish, Kamar ance ta juya,idanunta sukayi arba da waɗannan sojojin dake tunkararta hannunsu ruke da bindigu,bakomai ne ya fado mata a ranta ba face Ƴan boko haram da ƴan bindiga daɗin dake ta sace mutane agari, ja da baya tashiga yi gabanta na faduwa maimakon suyi mata magana cikin daɗin rae sai suka daka mata tsawa tare da cewa"ke zonan"! Aikuwa a firgice sehrish ta watsa da gudun gaske ta saki jakar makarantarta ƙasa,bin ta sukayi da gudun gaske,tana gudu suna bin ta tamkar zata tashi sama, yarda kasan wadda taci ƙafar kare haka ta dinga gudu,ita kanta batasan inda ta dosa ba,gudu kawai takeyi, adaidai nan su Omar suka ƙaraso gidan uncle Abusufyan,Wayarshi ta shiga ruri,cikin sauri ya fiddota daga cikin aljihun wandonshi,yayi picking call ɗin tare da kara wayar a kunnanshi yayi sallama, Muryar ɗaya daga cikin sojojin ce yaji yana cewa"Sir,munga yarinyar da ake nema,amma taƙi bari mu kama ta,' Hankali tashe Omar yace"Kada ku bari ta kufce maku,kuyi ƙoƙari ku kamota,kuyi mata magana cikin sanyin murya,saboda yarinyar tana da tsoro sosai,kun firgitata ne shiyasa ta gudu, "Okey sir,ya amsa mashi tare da katse kiran, "Yalla6ai meya faru ne"! Cike da takaici Omar yace"Major,an samu matsala!sojojin dana tura don su nemo mun jahad,sunyi arba da yarinyar gidan mu,dama na faɗa maka cewa kamanninsu sak iri ɗaya,ɗazu nace ma Osman Ya ɗauko mun hoton fuskar hosana,saboda in tura masu suyi amfani dashi wurin nemo min jahad,to da wannan hoton su kayi amfani wurin nemanta shine Allah ya haɗasu da ita yarinyar da junaid yayi musanya da jahad,' Tunda yasoma magana jahad ke kallonshi cike da mamakin wannan wani irin kamanni ne,dayasa har ba'a gane banbancinsu!? Major yace"Amma nayi mamaki yalla6ai!wannan wata irin kamanceceniya ce atsakaninsu da har ba'a iya bambanta tsakaninsu"! Omar yace"nikaina major abun ya jima yana ɗaure mun kai wlh,da farko nayi tunanin cewa saboda ƙaunar da nakeyi ma su hosana ne yasa nake ganin fuskarsu akan fuskar yarinyar,amma yau da junaid ya dauko jahad a matsayin ita yarinyar,sai na tabbatar da cewar ba gizau bane,tabbas kamanninsu ne ɗaya! Major yace"abun mamaki abun al'ajabi!yalla6ai kada kace na cika ka da surutu,dan Allah yaya kuke da ita yarinyar?ko ƴar wurin uncle ɗinku ce,' ya ƙarasa maganar adaedae lokacin da yayi parking ɗin motar a cikin gidan Abusufyan, murmushi Omar yayi tare da cewa"ƴar aikin gidanmu ce,sunanta Sehrish! Yarinyar tana da kirki sosai shiyasa Abbanmu ya mayar da ita tamkar ɗiyarshi,yanzu amatsayin kanwarmu take............' Waro ido waje Jahad tayi cike da tsananin mamaki ta furta"SEHRISH!!!!!!!!!!!!!!!!" juyawa Omar yayi yana kallonta jin yarda ta ambaci sunan kamar tasanta,shima major juyowa ya danyi daga zaunen da yake a front seat din suna kallonta, "Jahad kin santa ne!"? Muryarta na kerma tace"Ya...Omar...Bansan ko ita bace ba,amma akwai ƴar uwarmu da muka jima muna nemanta,kamanninmu sak iri ɗaya,Mu ƴan ukune dani da hosana da kuma ita,Sunanta Sehrish atare aka haife mu,ciki ɗaya muka fito tare da ita,arana ɗaya kuma a lokaci ɗaya.......' Kallon juna Omar da major sukayi cike da mamaki suke sauraronta,sae da takai ƙarshen maganarta,sannan Omar yace"Dama ke da Hosana ba twins bane!!!"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh,tace"WE'RE TRIPLET". Wannan shirin da kuke karantawa ba ammasco bane suka ɗauki nauyin kawo maki shi ba,Boss bature ce da kanta,ta shirya kuma ta gabatar,😂 Idan har kinji daɗin wannan update ɗin,kiyi following din acct dina a tiktok😍😂ga link can na bada daga sama *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.   *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Abban sojoji paid book ne,ga duk maison karanta cigabanshi zai biya 300 ne za'a tura mashi nabaya har inda muka tsaya,ga mai buƙata direct zaiyi mun magana ta whatsapp ɗina 08103884440, pls banda phone calls,Mijina ya hana ana kira na awaya🤭🤫 ❤🤍❤ Gaba ɗaya farin ciki ya lullu6e Marshal Omar da kuma major,tunda su kaji bayanin Jahad suka tabbatar da cewar ba shakka Itace ƴar uwartasu da take magana akai, "Jahad,wannan maganar ba anan ya kamata muyi ta ba,mu shiga daga ciki" buɗe motar Omar yayi tun kafin major ya buɗe mashi,fitowa jahad tayi itama,sannan shima major ya fito,duka dae a tare suka ɗunguma izuwa cikin gidan,har lokacin jikin jahad rawa yake yi,saboda tsabar doki da kuma zumuɗin ganin cewa Sehrish ce yarinyar da Omar ke magana akai, Lokacin da suka shiga cikin palour ɗin atare,hosana na a kwance saman 3 seater,tasha kuka harta gaji shine ta ɗan kishingiɗa nan,bacci ya kwashe ta, ko uniform din bata cire ba,bin ta da kallo Omar yayi bakomai ya faɗo mashi a rai ba,face abunda yayi ƙoƙarin aikata mata,tausayinta ne ya kama shi sosae,tsayawa yayi atsaye ya zuba mata ido ko kyaftawa baiyi, "Ya Omar,ka zauna mana,"muryar jahad ce ta katse mashi kallon da yake ma hosana,   Wuri ya samu saman 2 seater ya zauna,jahad kuma ta zauna asaman 1 seater,mayar da idonshi yayi kan major ganin ya tsaya daga tsaye yace"bismilllah mana,ave seat," ya nuna mashi gefen shi,murmushi major yayi tare da ƙarasawa ya zauna daga gefen Marshal,   "Jahad,inaso kiyimun bayani sosai yarda zan fahimta game da ƴar uwarku,taya akai kuka rabu da ita har tsawon wannan lokacin'? Omar ne ya jefa mata tambayar,gaba ɗaya suka zuba mata ido suna sauraron jin abunda Jahad zata ce,    "Ya omar ba da son ran mu muka rabu da ita ba,ƙaddara ce ta rabamu da ita,amma muna son junan mu sosai.....'dakatawa tayi da maganar yayin da idanunta suka cicciko da kwalla,   Anatse taci gaba da magana"ƴar uwarmu tana son mu sosai,tasha wahala akanmu,a lokacin baya Dani da hosana an ta6a kwantar damu asibiti,za'ayi ma hossana aiki,ana neman kuɗi kusan dubu ɗari tara da za'ayi mata aikin,bamu da ko sisi,bamu da mai taimakon mu sae Allah,mu kaɗae muke rayuwarmu tare da wata tsohuwa wadda take ruƙon mu a wurinta,wannan dalilin ne yasa sehrish ta nemi aikatau,don ta biya kuɗin aikin hosana da kuma na maganin da za'a siyamun,babu yarda muka iya alokacin wannan kaɗae ce mafita,muna ji muna gani ƴar uwarmu ta tafi neman kuɗi saboda ta nema mana lafiyarmu,ya Omar Sehrish tayi duk wata gwagwarmaya akanmu,damu da ita duk kanmu ɗaya,amma ita tamkar uwa take a wurinmu,tamkar yaya take a wurinmu,bamu da tamkarta aduniyar nan,rishi har ranta zata iya sadaukarwa saboda mu,nayi kukan rashinta sosai,nayi baƙin cikin yin nesa da ita........tun muna yara muke tsananin son junan mu,rayuwarmu a wulaƙance mukayi ta sakamakon mugun uba da muke dashi wanda bai ta6a nuna mana soyayya ba........'fashewa tayi da matsanancin kuka,   Gaba daya jahad ta gama kashe masu jikinsu yayi sanyi,   dakyar ta tsagaita da yin kukan taci gaba da magana"bayan sehrish ta tafi aiki,cikin sa'a ta samu kuɗin aikin hosana ta biya,lokacin da aka sallame mu daga asibiti,muka koma gidan tsohuwar da take kula damu,anan muke rayuwarmu,kullum muna kiranta awaya mu gaisa da ita,ita ma kuma tana kiran mu awaya taji ya lafiyar mu take,akwai wani lokaci da maganin hosana ya ƙare,ciwonta ya soma dawowa ta dinga hauka tana ƴan buge buge,hankali na ya tashi,gashi bamu da kuɗin da za'a siya mata wasu magungunan,shine na yanke shawarar sanar ma rishi halin da ake ciki,don ta taimaka mana dana magani,na tura mata saƙo ta waya,sai gashi ta turo mun da amsar cewa mu tura mata da acct number,cike da zumuɗi na zura hijabi na shiga gidan makwabtanmu wurin ɗiyar matar,don ta rubutamin acct number ɗinta tun da mu bamu da ita,ashe lokacin da na fita daga gidan,hosana tafarka daga bacci tana son shiga toilet,shine ta ɗauki wayar dana bari saman jakar kayanmu ta shiga toilet da ita,kafin nadawo cikin gidan hosana ta jefar da wayar cikin masan,wannan shine silar da muka rasa sehrish gaba ɗaya,saboda ba mu da wata hanyar da zamu iya magana da ita,sae ta wannan wayar.......'ƙarasa maganar tayi tana faman share kwallar da ke kwaranyowa daga idanunta,   sunnar dakai omar ya ɗanyi,yayin da yake jin zuciyarshi wani kala ba daɗi,haka shima major duk tausayin yaran ya kamashi,musamman ƴar uwarnan tasu sehrish,yarinyar tayi bajinta sosai,   ɗagowa omar yayi tare da kallonta yace"Jahad,inaso ki faɗamu taya akai kuka shiga hannun ƴan sanda?wane laifi kuka aikata ne"?   Cikin shessheƙar kuka tace"bamu aikata laifin komai ba ya Omar,sharri ne akayi mana,abunda ya faru bayan hosana ta jefar da wayar acikin rami,sae ga tsohuwar nan da take rainon mu ta shigo cikin gidan,anan ta same mu ni da hosana muna faɗa akan wayar da ta jefar mana,sai take tambayar meya faru ne muke faɗa,shine na sanar da ita abunda ya faru,hankalinta ya tashi sosai akan wayarta da mukayi mata asararta,rai a6ace ta shige cikin ɗaki ta rufe ƙopa,duk bamuji daɗi ba lokacin saboda bata ta6a nuna mana 6acin ranta ba irin na ranar,atsaye muka kwana muna bata haƙuri akan ta buɗe mana ƙopa mu shiga ciki,saboda a gidan ɗaki biyu ne,amma ɗaya ya rushe saboda ruwan saman da aka ta6ayi mana mai ƙarfi,ya Omar aranar waje muka kwana har ciwon hosana ya tashi,kafin washe gari kuma taji sauƙi,koda muka farka munyi tsammanin zata buɗe mana ƙopar amma abun mamaki sae muka ga ƙopar adatse,tun muna sa ran zata buɗe mana kopar har muka fidda rae,a ƙarshe agidan makwabtan mu muka shiga yin sallar asuba,anan ma muka ci abinci,da mamansu yarinyar ta tambayemu meya faru,muka sanar da ita duk abunda ya faru,shine yarinyar gidan ta rakomu har gidan mu,muka haɗu tare da ita muna babbuga ƙopar,a ƙarshe hosana ce tayi ƙoƙarin 6alle ƙopar......anan muka samu gawarta,ashe tun daren jiyan ta mutu.......mutane kuma suka daura mana laifin kisan nata,saboda sun gano cewa guba aka bata taci,wannan ne dalilin da yasa ƴan sanda suka kaimu police station,bayan an gama tattara hujjojin da za'a miƙa mu kotu dasu,sae kuma ciwon hosana ya tashi acikin cell,wannan ne farkon fitarmu daga cikin cell aka kai hosana asibiti,Ya omar kaji yarda akai muka kasance a hannun ƴan sanda..... "Ƙarasa maganar tayi yayin da hawaye ke ta faman sintiri a fuskarta,   "Ina mahaifiyarku take ne"?omar ne ya kuma tambayarta,   Jahad tace"bamu san inda take ba,bani da tabbacin cewa tana a raye kota mutu,abu ɗaya nasani koma a wane hali take yanzu indae tana araye to bata acikin hankalinta,"   Jinjina kai Omar yayi kafin yace"Insha Allah zan bincika komai a sannu zan gano duk wanda yayi sanadiyar shigarku cikin wannan halin,bazan ƙyaleshi ba,koda uban da ya haifeku ne,zan yanke mashi hukunci daidai da zunubin da ya aikata,'    major yace"wannan gaskiya ne,yalla6ai Allah ya taimaka kuma yayi jagora,nidae yanzu babban burina shine ƴan ukun nan,su kasance a ƙarƙashin kulawar family ɗinku,"   Omar yace"abun ya ɗaure mun kai major,kaji wani iko na Allah nan,gaba ɗaya yaran su ukun suna a ƙarƙashin kulawar family dinmu,duka Allah ya haɗasu awurinmu batare da saninsu ba,kuma batare da sanin mu ba,ita ɗayar ƙaddarar aiki ce ta kawota gidan mu,yayin da su kuma su hosana da jahad,ƙaddarar zaman asibiti ce ta haɗani dasu a lokacin da hosana ke hauka hannunta ruƙe da bindiga,Major abun akwai wata sarƙaƙiya acikinshi,tabbas akwai abunda Allah yake nufi da waɗannan yaran!akwai wani abu da Allah ke son bayyana mana shiyasa ya haɗasu duka awurin mu!"   Zuba mashi ido jahad tayi tana kallonshi ita kanta abun ya ɗaure mata kai,   Shi kanshi major ya shiga kokonton cewa Anya yaran basu da alaƙa dasu Marshal Omar?juyawa yayi ya dan kalli fuskar marshal sannan ya mayar da idonshi akan hosana,sae lokacin ya dinga ganin wata irin kamanceceniya atsakaninsu sosae,tabbas akwai wata alaƙa ta jini a tsakaninsu,shiru kawai yayi baice komai ba,   Kowa ya tafi duniyar tunani hafsat bature ma,ta ɗan ajiye typing tana tunanin wannan abun daya ɗaure mata kai tamau...,   "Ya Omar,"gaba dayansu sukayi firgit suna kallon Hosana dake kwance tafarka tana faman mutsistsike idanunta,jin muryar Omar yasa ta ambaci sunan shi,   Murmushi ya dan saki tare da ambaton sunanta "Hosana",   miƙewa tayi zaune tana ƙare masu kallo gaba ɗayansu,tashi Omar yayi ya koma gefenta ya zauna yana kallonta,    lokacin da ta tabbatar cewa shine saita fashe mashi da kuka tana cewa"Ya omar fushi nake dakai,meyasa ka tafi kabarmu kadaina zuwa wurin mu?laifin me mukayi maka da har kayi mana wannan horon"? Lallashinta ya shiga yi yana cewa"Am really sorry hosana..pls stop crying and wipe ur tears,komai ya wuce yanzu muna tattaunawa ne game da ƴar uwarku Sehrish...... '   Tunda ya ambaci sunan sehrish hosana tayi tsit ta nemi kukan da takeyi ta rasa la66anta har rawa sukeyi wurin cewa"Anganta ne ya omar?"   Murmushi Omar ya saki tare da cewa"An ganta hosana!ƴar uwarku da ku ka jima kuna nema,ashe itace yarinyar dake yi mana aiki agidan......"bai ƙarasa maganar ba hosana ta fashe da kukan murna tana cewa"Ya omar tana ina?ina rishi ɗinmu take?inaso naganta!tana ina,wayyo Allah na....'   Yarfa hannunta tashiga yi saboda tsabar farin ciki bakinta yaƙi rufuwa hawaye na zuba fuskar kuma ɗauke da dariyar farin ciki,   Itama jahad farin cikin ne tsantsa afuskarta yau takasance babbar rana agaresu rana mafi girma arayuwarsu ranar da Allah yasa suka gano inda ƴar uwarsu sehrish take,dole suyi farin ciki,bama su kaɗai ba,hatta masu karanta labarin rayuwarsu da kuma marubuciyar data zauna ta tsara labarin ita da kanta tana taya su farinciki,Ya Allah ka ƙara danƙon ƙauna atsakaninmu da ƴan uwanmu masu son mu,Allah ka bamu ikon faranta ma juna da kuma taimakon junanmu,a gudu tare kuma atsira tare? Omar ya jima a wurinsu hosana kamar karya tafi ya barsu haka yaji,abunda yasa bai tafi dasu yau ba saboda Yarinyar gidan tasu da ba'a gani ba,yafi son sai sun ɗauko yarinyar sannan ya kaisu gidan nasu don suga ƴar uwarsu ido da ido,zai so yaga wannan farin cikin a fuskokinsu, Bayan tafiyar su Marshal Omar,jahad da hosana duk sun bi sun ruɗe saboda tsabar murna ko abincin rana basu ci ba,sai faman sintiri sukeyi acikin babban falon nasu,aƙagare suke dasu ga sehrish,zuciyarsu sae faman azalzalarsu take akan son ganinta kamar suyi hauka. 💋BOSS BATURE💋 Ga wani tashin hankalin kuma,duk yadda sojojin nan suka so su kama sehrish abun yaci tura domin kuwa sehrish ta kubce masu,babu irin neman da basuyi mata ba,amma babu ita 6at ta 6ace kamar al'jana,abu kamar wasa har bayan sallar La'asar basu ganta ba, Niko sehrish ina kika shiga ne!kai jama'a daga antaro nan sae kuma nan ya ruguje, tunda Abbansu ya sanar mashi game da zuwan Aunty azeema,jiki na rawa junaid ya fito daga dakin Abbansu da gudun gaske ya nufi ɗakin da aka saukar da ita,faɗawa cikin ɗakin yayi ko sallama babu saboda tsabar ɗoki,a lokacin tana daga zaune saman gadonta tana daddana wayarta,sam bata lura dashi ba,bata ji shigowarshi ba,sae dae kwatsam taji faɗowarshi jikinta,gaba ɗaya ya ƙanƙameta sosai,yana yi mata kukan shagwa6a wai yayi missing ɗinta sosai, Dariya sosai hajiya Azeema tashiga yi tana cewa"Oh ni junaid,tun ɗazu nake ta tambayar ina babynmu yake ina babyn mu yake,duk na ƙosa naganka naso ace ina shigowa cikin gidan nan kaine mutun na farko da zaka fara tarbata da wannan sumbatar taka,"   ta ƙarasa maganar tare da ɗago shi daga jikinta tana bin shi da kallo tace"Masha Allah,junaid kaine ka koma haka?ka ƙara girma sosai kyakkyawan yarona,nayi missing ɗinka sosai,"   murmushi junaid ya sakar mata tare da cewa"mommy azeema ina tsarabata?me kika kawo mun"?   Dariya tayi tana girgiza kai tace"Tsarabarka na nan junaid,wannan karan nazo maka da abun ban mamaki,inaso inga farin cikin da zakayi idan nabaka tsarabar nan,"   cike da zumudi junaid yace"tana ina,"   Harara ta ɗan watsa mashi tare da cewa"Shine damuwarka?ka manta baka bani kiss dina ba,"   matsawa junaid yayi tare da kai bakinshi gefen fuskarta ya manna mata kiss sannan ya ɗago yana kallonta yace"yanzu sai aban tsarabata ko"?   Dariya tayi tace"ɗaukomin trolley ɗin kayana,"tayi maganar tana yi mashi nuni da trolleyn da Kanal yousouf ya jingine mata ajikin wardrobe,   jiki na rawa junaid ya saukko daga saman gadon ya taka izuwa wurin wardrobe din ya ruƙo trolleyn tare da janyoshi har wurin gadon ya miƙa mata shi,sannan ya zauna daga gefe ya zuba ido yana jiran ganin tsabar da tayi mashi,    hannu tasa ta buɗe trolley din ta curo wani ɗan kit ƙarami sai faman ƙyalƙyali yake yi yadda kasan da gold akayi jikinshi,tunkan ta buɗe shi junaid ke ta faman haɗiye yawu yarda kasan yaga abunci,     Murmushi ta danyi tare da kallon fuskarshi tace"close ur eyes,"   Rufe ido junaid yayi kamar yarda ta umarta,    Murmushi ta kuma yi tare da buɗe akwatin tace"Now Open ur eyes,"    A hankali junaid ya buɗe idanunshi kai tsaye suka sauka akan danƙareran Zoben diamond ɗin da ta siya mashi tare da agogonshi,sae faman ƙyalli suke suna ɗaukar ido,diamond bana wasa ba,wanda aƙalla price ɗinsu yayi miliyan ɗari uku,   Waro ido waje junaid yayi yana bin su da kallo saboda tsabar farin ciki ya gaza rufe bakinshi,hannunshi na kerma ya kar6i akwatin yana ƙare masu kallo, Cikin tsantsar farin ciki yace"aun...aunty..wannan duk nawa ne"?    dariya Azeema tayi ganin yarda yabi ya rikice ta wani 6angaren kuma ba ƙaramin daɗi taji ba,saboda bata da wani burin daya wuce taga ta faranta mashi,tana son ganin farin cikin junaid sosai,yaron tun yana ƙarami take tsananin son shi,   "Junaid duk naka ne wannan,Na musamman ne nasa akayi maka shi,duk duniya babu mai irin shi sae kai kaɗae,ni da kaine na bada sample ɗin yadda za'a haɗa maka shi,ka duba a jikin zoben ka gani,Harafin J ne ajiki wato farin sunanka," Wani irin farin ciki ne,ya cika junaid,a ƙarshe daya rasa abun cewa kawai sae ya fashe mata da kuka Yana cewa"mommy azeema,narasa da wasu kalmomi zan iya gode maki,babu su abakina,kin sanyani farin ciki sosai da wannan kyautar da kika bani.    Hannu tasa tare da shafo gefen fuskarshi izuwa cikin sumar kanshi tace"kasan dae babu godiya atsakaninmu ko?nayi maka wannan ne saboda inga farin cikin ka,kuma Alhamdulillah nagani kuma naji daɗi sosai,abu ɗaya zakayi mun yanzu shine ka share hawayenka,bana son ganinsu suna zuba,"   Cikin sauri junaid ya sanya hannunshi tare da goge hawayenshi duka,sannan ya mayar da hankali yana kallonta,   Cigaba da magana tayi a natse"junaid kana addu'a kuwa"?   gabanshi ne yaji yayi wani irin bugu jin tambayar da Aunty azeema tayi mashi,baisan dalilin dayasa tayi mashi wannan tambayar ba,   A ɗan ruɗe yace"Mommy meyasa kikayi mun wannan tambayar"?   shiru ta ɗanyi kamar mai nazarin wani abu kafin taci gaba da cewa"junaid bibiyar rayuwarka akeyi!" Hankali atashe junaid yace"Ni kuma mommy azeema,to meyasa ake bibiyar rayuwata?su wanene ke bibiyar rayuwata,me nayi masu?kuma me suke so atare dani?"gaba ɗaya ya gama ruɗewa, "Just calm down ur mind,ba wani abu bane na tashin hankali ba,banaso ka sanya damuwa a ranka junaid,amma ya zama dole na sanar dakai,akwai wata baiwa da Allah yayi mun,duk in nayi mafarki yana xama gaskiya,bawan da yasan da hakan sai ni,abubuwa da yawa kafin su faru acikin gidan nan,ni nake fara ganinsu acikin mafarki na,Allah yana nuna mun...'ajiyar zuciya ta dan sauke tana kallon junaid daya kasa kunne yana sauraronta,    kafin taci gaba da cewa"Nayi mafarki akan ka junaid,mafarkin ya tsoratar dani sosai,wannan dalilin ne ma yasa na nace akan saina zo,ba don komai ba sai don na ganka naga wani hali kake ciki......'    gaba daya hankalin junaid yayi mugun tashi muryar shi na rawa Yace"Mommy azeema,dan Allah ki fahimtar dani wani kalar mafarkine wannan?wani mummunan abune zai faru dani ne?mutuwa zanyi ko?dama najima ina ji araina cewa bazanyi tsawancin kwana ba.........'bata bari ya ƙarasa maganar ba,tasa tafin hannunta ta rufe mashi bakinshi,tsit junaid yayi jikinshi na rawa,zuciyarshi naci gaba da bugawa da ƙarfi da ƙarfi,   Cikin sanyin murya tace"Junaid,babu wanda ya isa yayi maka abunda Allah baiyi maka ba!tabbas rayuwarka na cikin hatsari sosai saboda duk wani dake son ganin bayan zuri'armu ta wurinka zai biyo junaid,dole sae da kaine za'a iya cutar damu junaid saboda kaine lagwon kowannanmu,kaine farin cikin mu gaba ɗaya.....' ƙarasa maganar tayi tare da zame hannunta daga bakinshi,    Jikin junaid yayi mugun sanyi,bakomai ya faɗo mashi aranshi ba face wannan ɗigon jinin dake ɗigowa daga hancinshi,da kuma daren ranar nan daya farka tsakar dare yaga wani baƙin hayaki ya fito daga cikin madubin ɗakin Abbansu,ya tunkaroshi ya shiga ta ƙopar hancinshi,a lokacin bayan ya farka washe gari,duk tunaninshi mafarki ne yayi ba gaske ba,amma yanzu da Aunty azeema tayi mashi wannan maganar sae wani tunanin ya faɗo mashi aranshi,tun daga daren ranar da hayaƙin nan ya shiga ta ƙopar hancinshi,a washe garin ranar jinin nan ya soma ɗiɗdigowa daga hancinshi,tabbas akwai wani 6oyayyen abu dake shirin faruwa dashi,   Tuna wannan abun yasa junaid ɗagowa idanunshi awaje yana kallon mommy azeema yace"Nashiga uku!mommy ina cikin tashin hankali!mutuwa zanyi bazan rayu ba...kashe ni zasu yi....bazasu bar ni da raina ba ..zasu rabani da Abbana'    Ganin yarda junaid yabi ya gigice yasa ta ruƙo hannunshi sosai tace"Ka natsu junaid!ba kayi imani da Allah bane?   Cikin shessheƙar kuka yace"nayi Imani da Allah mommy azeema,amma ni bana so na mutu yanzu,inaso na rayu ko don nacika ma abbana burinshi da kuma burin da nake dashi...  '   Katse shi tayi da cewa"tunda kayi imani da Allah,to inaso kasa aranka cewa babu wani mahaluƙi daya isa ya cutar dakai a faɗin duniyar nan face da izinin sa,sannan inaso ka dage da addu'a na sanka junaid baka ba addu'a mahimmanci sosai,kuma ita addu'a da kake gani takobin mumini ce,ka tashi tsaye ka dage da addu'a ka yaƙi duk wani wanda ke son ganin bayanka,kayi mun alƙawarin hakan,nima kuma zan tayaka da addu'ar,sannan zanyi ma abbanku magana akan ya dinga tashin ka tsakar dare kunayin sallah atare koda ace shi bai tashi ba,in har ka farka to ka shiga toilet ka dauro alwala kayi sallarka,sannan kuma zan sanar ma sauran ƴan uwanka duk zanyi masu magana akan su tayaka da addu'a Allah ya tsare mana babynmu,'   Wani irin sanyi yaji ya ratsa zuciyarshi,kalaman Aunty azeema ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya su kayi ba,ya samu ƙwarin guiwa sosai awurinta,har ya daina jin damuwa a ranshi,   "Kana da budurwa"?cike da zolaya tayi mashi maganar,don ta kawar da damuwar dake aranshi,   Sunnar da kai junaid yayi tare da cewa"am...um....eh..'   Dariya Aunty azeema tayi tana cewa"wai kunya ta kake ji ne?dalla faɗamun ni inji,"   Hannu yasa yana ɗan sosa ƙeyarshi yace"mommy azeema,akwai wadda nakeso sosai,kuma itama tana sona sosai,acikin gidan nan take,tare da Aunty azmee suke aiki,yau ta sanyani farin ciki sosai mommy,ta kar6i soyayyata,aure kawai ya rage yanzu inyi ma Abbanmu magana.....'kasa ƙarasa maganar yayi ganin yarda Azeema ta saki baki galala tana kallonshi,    Cike da jin kunya junaid ya kifa kanshi asaman laps dinta yana faman tiƙar dariya,   Suna cikin wannan rahar,wayar Hajiya azeema ta shiga ruri,tsagaitawa tayi daga yin dariyar da take,sannan takai hannu tare da ɗaukar wayar dake ajiye gefenta,ta duba mai kiran nata,a fili tace"Abbanku ne ke kirana,bari na ɗaga naji me zaice mun,"ta ƙarasa maganar tare da kara wayar a kunnanta,   Lamo junaid yayi kwance saman laps ɗinta,ba komai yake tunawa ba face soyayyar da suka sha tare da rishi ɗinsa acikin mota,soyayyarta ƙara ninkuwa takeyi acikin zuciyarshi,musamman da ta kar6i soyayyarshi hannu bibbiyu kuma ta amince zata aure shi,yanzu bai da sauran damuwa,dama itace damuwarshi kullum fargabarshi taya zai tunkareta da zancen soyayyar,zata amince ko bazata amince ba!?   Yana cikin wannan zancen zucin nashi yaji muryar azeema tana cewa"Alhamdullillah!Alhamdulillah mun gode ma Allah daya sauke su lafiya,ba don na tara gajiya ba,da ba abunda zai hana nima na biku Airport din mu tarboshi ..'    cike da farin ciki junaid ya ɗago yana cewa"Mommy,Uncle ɗinmu ne ya ƙaraso nigeria"?    Fuskarta dauke da murmushi tace"Eh,yanzu Abba ke sanar dani cewa sun shirya zasu tafi airport ɗauko shi,jirgin nasu bai kaiga ƙarasowa ba,amma kafin su isa airport din zai ƙaraso da yardar Allah,   Cikin sauri junaid ya sauko daga saman gadon jikinshi na rawa yace"Mommy azeema,ki ajiye mun gift ɗina a wurinki,zanzo na kar6a anjima,inaso zanje airport ɗin nima tare dasu Abbanah,'ko amsarta bai saurara ba,ya fuce da sauri da sauri, Murmushi Azeema tayi yayin da take bin bayanshi da kallo har ya fuce, Goggon katsina Da gudun gaske ta fito daga cikin ɗakinta,hannunta ruƙe da wayarta saboda tsabar farin cikin jin zuwan Abusufyan ɗinta da abbansu junaid ya sanar mata, Adai dai lokacin Saude da dr haris suna manne da juna saman 3 seater a falo suna shan soyayya,yana ƙoƙarin manna mata kiss asaman wuyanta,kwatsam sai ga goggon katsina ta faɗo cikin falon tana murna ganinsu yasa ta aza hannu akai tana cewa"La'haula masalli ila!acikin gidan nan ake wannan baɗalar? A firgice suka ɗago suna kallonta hankali tashe,kamar yarda itama take kallonsu hankalinta atashe,    sunnar dakai ƙasa sukayi suna ƴan kame kame,    Jinjina kai tayi tare da cewa"munafukan Allah,yau asirinku ya tonu,dama abunda kuke aikatawa kenan duk in nashige cikin ɗaki ko?cike da tuhuma tayi masu maganar,.     buɗe baki saude tayi da niyar tayi magana,goggo tayi mata dakuwa da hannunta tace"Ungo nan,ja'ira dama kar nake kallonki,munafuka ashe shiyasa kullum nace zan maidaki rugarku sae kiyi mun narai narai da ido kamar na mujiya kina cewa bakison ki koma kiwon shanu,ashe kina nan kin kama wani shanun kina ta tatsa,ina nan sake da baki,Allah kaɗae yasan me kuke aikatawa,ni ban yarda daku bama Allah,ka fadamun gaskiya Harisu iya shinshine-shinshinen kuka tsaya ko kun zarce nan? Tayi maganar tana wurga mashi harara,duk kunya ta gama rufe shi,   Cike da jin kunya suka sunnar dakai ƙasa atare suna sauraronta,sae da takai aya sannan Dr haris yace"Mommyna ni fa ba abunda ya shiga tsakanina da ita,wannan ma da Allah yasa kika gani sharrin shaiɗan ne, ba yin kanmu ba......'bai ƙarasa maganarba,goggo ta tsige kallabin dake kanta,ta wurga mashi shi kafin ya ƙarasa saman fuskarshi,cikin sauri saude ta tarbe kallabin goggon a hannunta,   Baki asake goggo tace"Saude! don tsabar iya rashin kunya da tsageranci akan idona kike kare mashi don na jefe shi da kallabina?wato ya saba baki kina sha shiyasa kika raina ni ko"?    Waro ido waje Saude tayi tana kallonta hankali atashe tace"nashiga uku goggo,me kike nufi daya saba bani ina sha"?   Harara goggon katsina ta watsa mata tana murguɗa mata baki tace"nima bansani ba,nasan dae kina bashi kuma shima yana baki,Allah ya shiryeku in masu shiryuwa ne,sae yanzu nagane kuskuren danayi na barin ki acikin gidan nan,batare da an shafa fatihar Auranku ba,gashi yanzu kuna ƙokarin haifo min ɗan gaba da fatiha.....'fashewa tayi da kuka,cikin shesshekar kuka taci gaba da cewa"Allah sai kin bar gidan nan saude...bazan cigaba da zama dake ba,kina lalatamin yarona,kafin zuwanki gidan nan harisu ko kalmar kiss baisani ba,amma sae gashi yau na same shi yana ƙoƙarin manna maki kiss kamar wani maye,yabi ya kanenayeki don tsabar jaraba irinta ƴaran zamani,acikin gidajen iyayensu ma bazasu iya kame mutuncinsu ba,ni bandamu ba duk abunda zakuyi kuyi,amma ba agaban idona ba.....'   Atare Dr da saude suka kalli juna cike da mamakin jin abunda goggo tace,wato komai zasuyi suyi amma ba'a gaban idonta ba,tashin sense,    Miƙewa haris yayi tare da takawa inda take ya ruƙo hannunta,cikin lallashi yace"Goggo pls komai ya wuce,kuskure ne mun riga da munyi,kuma bazamu ƙara ba,kiyi haƙuri kinji mommyna"    fisge hannunta tayi daga cikin nashi tace"kada ma Allah yasa ku daina,ni wannan ba damuwata bace,yanzu ni bani da sauran damuwa zan tattara nabar maku gidan,idan kunga dama kuyi aure,in baku ga dama ba ku cigaba da abunda kuka saba,Allah dae na kallon mutun,'   Tayi maganar tana wurga ma saude harara,haushinta takeji kamar ta rufeta da duka,    "Mommyna,ina zakije ne?naji kina cewa zaki bar mana gidan"?cike da damuwa yayi maganar   Murguɗa mashi baki tayi tare da cewa"gidan Abba mana,zanje inga Abusufyan ɗina ne,yanzun nan zan shirya in tafi,'    "Mommyna pls ki bari sae gobe zan kaiki da kaina har can ki ganshi,amma yanzu marece yayi fa,naji kamar ana kiran sallar magriba ma,dare zai yi mana a hanya,'cikin lallami yake yi mata magana,don yasan halinta bamai iya mata,   Turo bakinta tayi tana gunguni kamar wata ƙaramar yarinya tace"Allah bamai hanani zuwa,sai naje naga Abusufyan dina tare da ƴa'ƴanshi,'   ɗaure fuska babban likita yayi tare da cewa"Muddin kikasa ƙafa kika bar gidan nan,akwai karnukan layi na nan suna ran gadi acikin anguwar nan,da zarar sunyi arba dake hmmmmmm Allah kaɗae yasan mai zai biyo baya,    tunda taji ya ambaci sunan karnuka,nan take jikinta ya shiga kerma,saboda mugun tsoransu take ji,bata ƙara tanka masu ba,jiki na rawa ta wuce bedroom ɗinta,   Ajiyar zuciya Dr haris ya sauke tare da juyawa ya kalli saude dake ta faman sakin murmushi yace"wlh naji kunya sosai,mommyna bata da saiti,komai yazo bakinta faɗinshi takeyi,yadda kasan rakwa6a66iyar motar da burki ya kwace mata,'.    Fashewa da dariya sukayi,daga bisani Saude ta tsagaita da yin dariyar tace"babyna,addu'a yakamata muyi mata akan Allah ya bata lafiya,idan tadawo dai dai mu kanmu zamuji daɗi sosai,saboda goggo tana da kirki sosae,'   Murmushi Dr haris ya kuma yi tare da cewa"insha Allah zamu cigaba dayi mata addu'a Akan Allah ya bata lafiya,'   _💋Boss Bature💋_    Wuraren ƙarfe 6:30 jirginsu Abusufyan yayi landing a Nnamdi Azikiwe International Airport Abuja, gaba ɗaya su Abba sun gama hallara a airport ɗin suna jiran saukowarsu daga cikin jirgin,kowannansu a ƙagare yake daya ga fuskar Abusufyan da suka jima basu sanyashi a idanunsu ba,nikaina wlh amatse nake dana ga wannan Abusufyan ɗin da kowa yake ta ɗokin ganinshi, Gaskiya namatsu,namatsu namtsu, inga wannan ɗan tahalikin, daga cikin waɗanda suka hallara domin tarbar shi akwai Abbansu tare da junaid,kanal yousouf da kuma Irfan,jabeer,khaleed da kuma fawan,bayansu kuma akwai Twins suma duk suna zazzaune asaman waiting seats na airport din suna jiran ƙarasowarshi,suna zaune suka ji ana annoucement din ƙarasowar jirgin daya zo daga ƙasar turkey, Tsantsar farin cikine ya bayyana a fuskokinsu,duk suka zuba ido suna jiran 6ullowarshi, Passengers ne suke ta fitowa daga cikin jirgin kowannansu fuskarshi asake,sae bullowa sukeyi ta ko'ina, Sannu a hankali ya aza kafarshi asaman matattakalar benen,masha Allah sae dae muce tabarakallahu ahsanul khaliqin,   giant ne yana da tsayi da kuma cikakkiyar sura mai jan hankali,ta ko'ina Allah ya hore mashi,a launin fata kuwa chocolate colour ne,kala mai tsada,fatar nan tashi taji hutu ko a ido ka kalleta sae kasan cewa ba ƙaramin hutu taji ba,jikinshi na sanye da Suit maroon colour launin glass ɗin dake manne a fuskarshi,wani irin daddaɗan kamshi ne ke fesowa daga jikinshi,hannunshi na sanye da tsadaddan agogo na diamond,   A hankali ya ɗaga hannunshi tare da kai shi saman fuskarshi ya zame glass ɗin da ke manne a fuskar,lumshe idanunshi yayi tare da waresu a hankali yana kallon mutanen dake shawagi a wurin,   Yayi kewar ƙasar shi sosai,shekara kusan goma sha wani abu,bai taka ƙasar ba,sai yau Allah ya dawo dashi, "Ƙaddara ta sake dawo dani wannan ƙasar" ya furta hakan yayin da yake ƙara ruƙe trolley ɗin hannunshi,jan shi ya shiga yi yayin da yake ci gaba da saukowa daga saman matattakalar jirgin,   Dirar shi ke da wuya,yaji an ambaci sunan shi da wani irin sauti yaji ance"Uncle Abusufyan! "firgit yayi tare da kai idanunshi wurin da yaji an ambaci sunan,   Waro ido yayi waje fuskar nan dauke da farin ciki ya ambaci sunan Junaid,   Da gudun gaske junaid ya ƙarasa tare da faɗawa saman faffaɗan ƙirjinshi,ya kankame shi sosai kamar zai shige jikinshi,   sosai Abusufyan ke sakin dariyar farin ciki yana ƙara bubbuga bayan junaid da hannunshi yana cewa"WOW MASHA ALLAH MY BABY BOY KAINE KA KOMA HAKA,GASKIYA NAYI MISSING ƊINKA SOSAI JUNAID,AM REALLY GLAD TO SEE U ........' ya ƙarasa maganar tare dasa hannunshi ya ɗago junaid daga saman kirjinshi yana kallon fuskarshi,yayi mamakin girman yaron lokacin da daya tafi yana ɗan ƙaraminsa ya barshi, ganin hawaye na sauka asaman fuskar junaid yasa shi cewa"meya faru junaid?kai da zan ga kana farin ciki sae kuma naga hawaye a idanun ka why?   Cike da shagwa6a junaid yace"uncle bakaine ka tafi kabarmu ba,shekara da shekaru ka manta damu,ba ka damu da kazo ka ganmu ba,"    ƙayataccen murmushi Abusufyan ya saki tare da cewa"Am really sorry my boy,nasan ni mai laifine ayimun afuwa pls,shiyasa nadawo nigeria don in goge laifina....'   Yana cikin maganar tashi sai ga su Abba sun ƙaraso wurinsu tare dasu kanal yousouf,   Gaba daya suka ƙarasa one by one suna rungume shi ajikinsu cike da nuna farin cikin ganinshi, Sae da ya kammala rungumarsu,sannan ya ɗago yana kallon ɗan uwan nashi daya tsaya gefe guda,yana kallon shi fuskarshi aɗaure alamar fushi yake dashi, Tunkarar shi yayi zai rungume shi,cikin sauri Abba ya dakatar dashi ta hanyar ɗaga mashi hannu yace"karka kuskura ka ƙaraso nan,bana son ganinka,ni banma san ya akai nazo airport ɗin nan ba," Hannu uncle abusufyan yasa tare da kama kunnan shi yana cewa"Am sorry my bro,ayi mun aikin gafara nasan nayi laifi,amma zan gyara kuskure na,yanzu dae ka barni in rungumeka kona ji sanyi araina,' Buɗe mashi hannu Abba yayi alamar ya taho,faɗawa jikin shi abusufyan yayi sosai suka rungume junansu,tuni hawaye suka cicciko a idanuwan kowannansu muryar abbansu junaid tamkar zaiyi kuka yace"Hakanan ka tafi ka barni batare da sani na ba,me yasa kayi mun haka abusufyan?duk irin son da nake maka,ka tafi ka barni da raɗaɗin rashin ka acikin zuciyata,abun ba ƙaramin ciwo yake yi mun ba," ya ƙarasa maganar a lokacin da yake ƙoƙarin raba jikinshi daga na Abusufyan, Jikin shi yayi mashi sanyi,duk sai yaji ba daɗi,kuma bai kyauta masu ba, daƙyar yace"Ka yafe mun ɗan uwana,na cutar dakaina,na raba kaina da ƴan uwana,bawai don bana son kasancewa atare da ku ba......' Kasa ƙarasa maganar yayi saboda wani abu daya tuna a rayuwarshi daya ta6a faruwa dashi..., Jinjina kai kawai Abbansu junaid yayi tare da ruƙo hannunshi yace"Komai ya wuce,tunda kadawo nigeria,kuma inaso ka sani bazan ƙara bari kabar ƙasar nan ba,komai kakeso ka faɗamun zanyi maka shi,in ma akwai wani abu dake damunka duk ka sanar mu,zanyi ƙoƙari wurin ganin na share maka hawayenka,dama ni sae da raina ya bani cewa bada son ranka kabar ƙasar nan ba,akwai wani abu dake faruwa wanda kaƙi sanarma kowa.....' "Abba,uncle fa ya gaji sosai,ya kamata muyi hanzarin wucewa gida tare dashi,idan ya kwanta ya huta sae mu ƙara gaggaisawa dashi," Kanal yousouf ne ya katse mashi hanzarinshi, murmushi abba yayi tare da janyo hannun abusufyan suka kama hanyar fitowa daga airport din,gaba dayansu suka ɗunguma izuwa wurin da suka ajiye motocinsu,murmushi kawai Abusufyan keta saki yana kallon ƴan uwan nashi kamar ya haɗiyesu haka yake ji,saboda tsabar son da yake yi masu. Finally Uncle Abusufyan ya ƙaraso nigeria,saura mommynsu junaid da kuma Ammi,su muke jira, Koda suka ƙaraso cikin gidan,anan main palour din suka zazzauna ana ƙara gaisawa da juna,a ƙarshe abba ya ruƙo hannun ɗan uwan nashi yakai shi izuwa cikin bedroom ɗin da aka tanadar mashi,katafaren ɗakinsa da zai zauna aciki,sae da abba ya tabbatar da cewa Abusufyan ya shige cikin ɗakin sannan yaja mashi ƙopar ya rufe, Gaskiya zanso kuga irin farin cikin da ahalin nan suke yi na zuwan Uncle dinsu Abusufyan, Wuraren ƙarfe 11 na dare lokacin komai ya lafa,junaid ya nufi bedroom ɗin sehrish yana nemanta ganin bata fito ba,lokacin daya je,ɗakin nata ya shiga wayam yaga babu kowa,jiki na rawa ya wuce ɗakin azmee yana tambayarta ina reesh take,azmee tace"tun ɗazu dana kai mata lunch ban ƙara sanyata a cikin idanuwana ba,"fitowa junaid yayi daga ɗakin azmee hankalinshi a matuƙar tashe,saƙo da lungu na gidan ya dinga bi yana dubawa bai ganta ba,lokacin daya tabbatar da cewa sehrish bata acikin gidan,jiki na rawa ya wuce ɗakin Abbansu anan ya same shi zaune shi da Uncle abusufyan suna ƙara tattaunawa a tsakaninsu, Ganin yarda junaid ya faɗo masu ba sallama yasa suka shiga tambayarshi ko lafiya,hankali tashe yace"Abba,sehrish nake nema,na duba ko'ina acikin gidan nan bata nan,' cike da mamaki abusufyan ya maimaita sunan Sehrish abakinshi, Abba kuma yace"tun yaushe tabar gidan?baka je ɗaukota daga school bane"? "Abba naje,dakaina na ɗaukota kuma na kawota acikin gidan nan,amma yanzu na duba ko'ina babu ita," Jin wannan maganar ta abba yasa shi miƙewa daga zaunen da yake gefen gadon ya nufi junaid yana cewa"muje wajen," Juyawa junaid yayi suka fuce atare,yayin da suka bar Abusufyan azaune cikin ɗakin, Hankalin kowa fa ya tashi,abun sai ya baka mamaki,ashe ba ƙaramin so sukeyi ma yarinyar ba,duk wanda akace mashi Sehrish ta 6ace ba'a ganta ba,sae kaga ya fito daga bedroom dinshi yadawo falo cike da damuwa,gaba daya sae da kowannansu ya hallara banda Sgr,saboda tun ɗazu yabar cikin gidan, Hankalin Marshal omar ba ƙaramin tashi yayi ba,jin ana neman Sehrish,sam ya manta da bata a cikin gidan,tunda junaid yayi musanyarta da jahad,ya tura sojojin nan don su nemo mashi jahad,su kayi arba da yarinyar saboda kamanceceniyar dake atsakaninsu yasa sukayi tsammanin Jahad ce,yayin da suka bi ta da nufin su kamata ita kuma ta watsa aguje,tabar masu school bag ɗinta a ƙasa,babu irin neman da basuyi mata ba,amma babu ita ba alamarta 6at ta 6ace masu.........Shin Ina sehrish ta shiga ina!? "Abba wai meke faruwa ne naga kunyi curko-curko anan,kamar kuna cikin damuwa,"hajiya azeema ce ke tambayarshi a lokacin da take ƙarasowa inda suke tsaitsaye,duk sun hallara gaba dayansu kowa yana cike da zullumin abunda zai biyo baya game da yarinyar da ta 6ata, "Yarinyar dake taya azmee aikice ta 6ace,an nemeta an rasa babu ita acikin gidan nan,"ya bata amsa fuskarshi cike da damuwa, Fawan yace"Abba ita yarinyar bata da waya ne"? junaid ne ya bashi amsa da cewa"akwai waya a hannunta,amma na kira layinta a kashe,tun ɗazu nake trying still switch off, Hajiya azeema tace"gaskiya akwai matsala,yakamata ayi hanzarin binciko inda yarinyar take," Gaba daya duk sun shiga damuwa,musamman junaid hada ƴan hawayenshi, Gyaran murya Marshal Omar yayi suka mayar da hankalinsu akanshi,sannan yace"kada ku damu,insha Allah za'a ganota,na zuba sojoji acikin garin nan suna nan suna bibiyarta,kuma insha Allah zasu gano mana ita," Abba yace"naji daɗi sosai Omar,Allah yasa su gano mana ita,hankalina bazai ta6a kwanciya ba in har yarinyar nan bata dawo cikin gidan nan ba,' Ya ƙarasa maganar tare da kallon su fawan yace"kuje ku kwanta,insha Allah za'a gano ta," Har suna haɗa baki wurin cewa"Abba,ba zamu iya runtsawa ba,in har ba'a ganta ba,zamu zauna anan ne mu jira har Allah yasa ta bayyana,' Abun ba ƙaramin mamaki ya ba Abbansu ba bai ta6a tunanin cewa sun damu da yarinyar ba,sae yau,abunda ke faruwa ita mace ce,kuma matashiya dole kowa yayi zullumin ina ta shiga,waya dauketa,sace ta akayi ko kuma cutar da ita akayi,? *Sehrish* *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.     *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari, "Aunty azmee wai meke faruwa ne naga kowa ya hallara a falo fuskokinsu kuma da alamun damuwa atattare dasu,wani abu ya faru ne"?Hayamm ce tayi mata wannan tambayar,fitowarta kenan daga bedroom dinta,da alama tafara bacci,sae faman hamma takeyi, Azmee dake tsaye daga wurin corridor ɗin shiga bedrooms ɗinsu,ta juya tare da kallonta tace"Ba dole ki ganmu a haka ba?Sehrish ce ta 6ata an nemeta an rasa,shiyasa kika ga kowa hankalinshi atashe,   cike da mamaki hayaam tace"Wai don sehrish ta 6ata shine kowa ya tashi hankalinshi haka?suka hana idanunsu bacci saboda wannan yarinyar?sae kace dae wata ƙanwarsu ko ɗiyar Uncle ɗinsu?menene alaƙarsu da ita da har zasu sanya damuwa aransu don ta 6ace!ƴar aiki fa ce ba wata tsiya ba,"    "Hayaam!Anya kina cikin hayyacin ki kuwa?mutun fa akace maki ya 6ace ba dabba ba!don me ba zasu tashi hankalinsu ba?don tana ƴar aiki?kamar kece fa ace kin 6ata acikin gidan nan!kina nufin kada kowa ya damu kenan tunda ke ma baki da irin alaƙar da kika ce dasu kamar dae ita din yarinyar!in fact sun ma fi sabawa da ita yarinyar,saboda hidimar da takeyi masu kullum tana cikin yi masu ɗawainiya acikin gidan nan,ta wuce ƴar aiki a wurinsu,tamkar ƴar uwarsu ta Jini suka ɗauke ta......'   Tunda Azmee ta soma magana,Hayaam take kallonta Rai a matuƙar 6ace jin maganganun da take gaya mata,bata ta6a tunanin cewa azmee zata iya furta mata su ba,a tunaninta matsayinta yaci ace tayi respecting ɗinta amatsayin wadda yayyanta ke auran wasu daga cikin matasan gidan,   "Aunty azmee yanzu saboda waccen ƙasƙantacciyar yarinyar kike gayamun magana!kin manta matsayina acikin gidan nan ne!ya kamata ki iya bakinki,ina girmamaki ne kawai saboda girma da darajar da kike dasu awurina,"   Ƙarasa maganar tayi tana faman huci,saboda an 6ata mata rae,nace sannu ƴar masu gida,   girgiza kai kawai Azmee tayi,dama tasan halin hayaam ciki da bai,bata da kunya futsararriya ce ta gidan gaba,tuna wannan yasa ta fasa mayar mata da martanin maganganunta,   murmushi kawai tayi kafin tace"Hayaam ni ban faɗa maki hakan don na 6ata maki rai ba,kawai banji daɗin maganganun da kika faɗi bane agame da rishi,koba komai ita mutunce mai daraja,kuma yarinya ce dole mushiga damuwar rashin.....'.   Bata bari azmee takai ƙarshen maganarta ba,ta buga uban tsoki tare da cewa"Ni bangan abunda damuwa ba anan,Ita tasan inda takai kanta,wama ya sani ko tana ɗakin hotel Kwance tare da kwartonta,ku kuna nan kun tashi hankalinku a banza"   Waro ido waje Azmee tayi jin abunda hayaam tace,   Shu'umin murmushin nan nata ta saki tare da juyawa ta nufi hanyar bedroom dinta,tabar azmee atsaye baki a sake tana bin ta da kallo,   Lokacin da hayaam ta shige cikin ɗakinta,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta ba don komai ba,sae don jin 6atar sehrish,addu'arta Allah yasa karsu ganta, A fili ta dinga cewa"Allah yasa mota ta take kanta ta mutu kowa ya huta,dama natsani ganin yarinyar nan acikin gidan nan,"ta ƙarasa maganar tare da faɗawa saman gadonta hankalinta kwance, Azmee kuwa lamarin ya fi ƙarfinta,ta jijjiga sosai da jin kalaman hayaam akan sehrish,tabbas ba ƙaramin tsanarta tayi ba,wannan ma in ta samu dama da alama zata iya halakar da ita gaba ɗaya,' *Boss Bature* Abun da ya faru lokacin da Sojojin nan suka bi sehrish a guje suna ƙoƙarin kamata ta kubce masu,ta hanyar faɗawa wata corner,kafin da gudun gaske sojojin suka bi ta cikin kwana din don su kamota sae dae kash,lokacin da suka ƙarasa cikin lungun tuni sehrish ta jima barin shi,da sauri suka bi lungun har ƙarshen shi,anan suka tarar da dogon titi,ko'ina sun duba babu ita,hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,basu ga ta zama ba haka suka karaɗe ko'ina na garin wurin neman Yarinyar, Yayin da suke ta yawan neman sehrish,ashe tana ƙarƙashin teburin mai siyar da kayan marmari a bakin hanya,lokacin da ta faɗo lungun ta futo aguje tarasa inda zata sanya kanta,kwatsam ta hango teburin nan na mai kayan marmari,babu wanda ya lura da ita lokacin da ta saɗaɗa cikin sanɗa,ta shige ƙarƙashin teburin jikinta nata faman kerma,gaba ɗaya duk tabi ta rikice ta ruɗe,ta razana kuma ta firgita sosai,sanadin wannan uban gudun da tayi ne,ya ƙara mata raɗaɗin ciwon cikinta ya dawo sabo,a can ƙasan mararta ta dinga jin wani irin zogin ciwo mara daɗin ji,kuka sosai takeyi ƙasa ƙasa duk tabi ta takure kanta a ƙarkashin teburin,ta ƙankame jikinta saboda wani irin Sanyi dake shigarta,ba ƙaramin kamu sanyin yayi mata ba,ko'ina na jikinta sae faman kakkarwa yakeyi,hatta teeth ɗinta gamewa sukeyi da juna,Sehrish taji jiki sosai fiye da tunaninku,baiwar Allah tama rasa inda zata tsoma ranta taji daɗi,don ta jigata sosae ga uwar yunwar dake cin ta don ma ciwo da fargaba sun hana ta fahimci tana jin yunwar,gaba daya ta fita hayyacinta,wuraren ƙarfe sha ɗaya lokacin kowa ya watse babu mutane a wurin mai kayan marmarin,A hankali ta fito daga ƙarkashin Teburin tare da miƙar hanya tana tafiya tana tangaɗi akan hanya kamar wadda tasha Giya,da ƙyar take takawarma don jan kafa kawae take,a lokacin ita kanta batasan inda ta dosa ba,saboda ta fita hayyacinta, Tana cikin wannan tafiyar agefen titi,wata mota baƙa ƙirar Rav 4,tayi parking adai dai inda sehrish take,wasu matasa ne kusan su Huɗu jigunannun ƴan iska,Zubin ibliss ne suka fito daga cikin motar,dukansu suna sanye cikin Riga da wando crazy jeans,Kallo guda zakayi masu kasan cewa ba Allah aransu,fitsararru ne na ƙarshe,wani ɗan iskan gyaran gashi ne akansu,na tantirae wanda suka haura matakin deegre a6angaren Tashanci,    Jin motsin mutane yasa Sehrish yin firgit agigice ta juya tana kallonsu hankali a matuƙar tashe,kafin tayi wani yunƙuri tuni suka ɗauketa tare da toshe mata baki da tafin hannu suka turata acikin motarsu,back seat suka wurgata ciki,sannan suka shige ciki,tare da jan motar da gudun gaske suka fisgi Motar,    kokowa sehrish ta shiga yi tana ihu tana hargowa tana ambaton innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!ku rabu dani!ku ƙyale ni!ku barni na tafi gida,nashiga uku,Wayyo Allahna,   daya daga cikinsu ne ya sanya hannunshi tare da toshe mata baki ya daka mata tsawa yace"Ke!yi mana shiru anan,kin cika mu da hayaniya,its better ki rufa mana baki,don babu mai taimakonki anan,"    Ba ƙaramin tsorata tayi ba,kankame jikinta tayi tana cigaba da ambaton sunan Allah acikin bakinta,    Da gudun gaske suka shigar da motar cikin wani ƙayataccen garden tare da yin parking dinta,   Buɗe motar sukayi gaba dayansu suka fito,na ƙarshen ne ya fito hannunshi ɗauke da sehrish yayi wurgi da ita,gaba daya ta gangara goshinta ya bugu jikin wata bishiya,dafe wurin tayi tana faman shesshekar kuka,ba ƙaramin buguwa tayi ba,dakyar tasamu ta ɗago daga kwancen da take aƙasa,    buɗe idanunta tayi waɗanda suka kumbura suka ƙankance saboda kukan da tasha,a firgice taja da baya ta ƙure ma bishiyar dake bayanta tana kallonsu,idanunta azazzare hankalinta yayi mugun tashi,   Su duka huɗun suna tsaye agabanta,kowannansu na kwance belt din wandonshi,girgiza masu kai tashiga yi tana cewa"dan Allah kuyi hakuri.. ..kada ku cutar dani....kada ku rabani da mutunci na....ku ƙyale ni na tafi gida ..bani da lafiya..."   Abun nasu babu imani kwata kwata,duk wannan magiyar da sehrish keyi masu hakan baisa sunji tausayinta ba,   A wulakance daya daga cikinsu yakai hannunshi tare da Fisge hijabin dake jikinta yayi wurgi dashi gefe guda ya faɗi ƙasa,   Cikin sauri sehrish ta ƙankame rigar jikinta,saboda ta matse ta kirjinta ya fito sosai,    gaba daya sun kwaɗaitu da ita,musamman da sukayi arba da kyakkyawar surar jikinta,mai matuƙar jan hankali,    tamkar zata shige ma bishiyar haka ta manne tana kara matse kanta ajikinta,hawaye sae faman sintiri sukeyi a fuskarta,cikin shessheƙar kuka tace"dan Allah ku ƙyale ni na tafi gida!bansanku ba bansan su wanene ku ba,bansan me yasa kuka ɗaukoni ba......'ƙasa karasa maganar tayi saboda jin daya daga cikinsu ya cafko gaban rigarta,da ƙarfi yajata nan take ta tashiga yagewa Allah yaso akwai farar half vest da tasanya daga ciki,daddagewa tayi ta gartsa mashi cizo asaman hannushi,a gigice ya saki rigarta,tattare wurin tayi da hannunta,jiki na rawa ta yunƙura zata tashi ta gudu,    Wani daga cikinsu yasanya kafarshi tare da taɗiyo kafarta,nan take sehrish ta kife ƙasa,ta bugu sosai saukin ma ciyayi ne awurin ba duwatsu ba,.    fashewa sukayi da dariyar sheƙiyanci suna kallonta,kafin daga bisani ɗaya daga cikinsu,ya afka mata yana ƙoƙarin keta mata haddinta,   fashewa da kuka sehrish tayi mai sautin gaske saboda tarasa yarda zatayi ta kwaci kanta ahannunshi,    Damƙa yakai ma wandon jikinta yana ƙokarin zame shi kenan, dai dai lokacin wata danƙareriyar mota jeep ta kunno kai cikin garden ɗin atsiyace mai motar ke driving ɗinta, motar na tsayawa yasa hannu tare da buɗewa ya fito daga cikinta,gaba ɗaya matasan nan guda ukun dake awurin zuba mashi ido sukayi atare suna tunanin wanene wannan ya faɗo masu acikin garden ɗin lokacin da suke tsaka da jin dadinsu,ya rufe fuskarshi da face mask,sannan ya manna baƙin glass a fuskarshi,wannan yasa ba zasu iya tantance ko wanene shi ba   Jin sautin kukan yarinyar a cikin kunnanshi yasa shi juyawa cikin sauri yakai idanunshi akan wanda ke ƙoƙarin rabata da kayan jikinta,a wani irin zafafe ya tunkare shi,kwakkwaran damƙa yakai ma wuyar rigar shi da hannu ɗaya,ya ɗago shi tare da yin wurgi dashi gefe guda,   Kallon juna sauran suka shiga yi,hankalinsu tashe ganin yarda ya ruƙo shi da hannu guda,duk girmanshi yayi wurgi dashi, Kafin yayi wani yunkurin tashi daga wurgin da yayi dashi,ya dunƙule hannunshi tare da kai mashi naushi agefen fuskarshi,Nan take haƙora guda biyu suka 6allo tare da fadowa daga cikin bakinshi ɗauke da jini,   Koda sauran matasan nan guda uku suka ga wannan tashin hankali,maimakon suyi ta kansu,rabon wahala sae suka tunkareshi suna naɗe hannun riga alamar zasu yi mashi rubdugu,    Kamar jira yake su ƙaraso wurinshi,dukkansu ya haɗa yayi masu shegen duka,gaba ɗayansu babu wanda bai raunata shi ba,sae faman juyi sukeyi a ƙasa suna fadin Wash!Ash!    Juyawa yayi tare da kallon Yarinyar dake kwance ƙasa sai faman burgima takeyi tana fadin kada ku rabani da mutuncina,ku ƙyale ni na tafi gida,banaso!banaso ku daina ta6amun jikina,gaba daya sehrish bata a cikin hayyacinta juyi kawai takeyi tana sambatu,   juyawa yayi batare da yaje wurinta ba,dama taimako ne ya kawo su cikin garden din,Hanya ce ta biyo dasu ta saman titin shine suka ji sautin kukan mace acikin baƙar motar dake a gabansu wannan ne dalilin dayasa suka biyo bayan motar har suka gano inda suka shiga,cikin sa'a kuma suka tarar da abunda suke zargi,   Karasawa yayi wurin motar tasu tare da buɗewa ya shiga ciki ya zauna yana faman sauke ajiyar zuciya,    "Sir,yarinyar fa"? Drivern dake driving ɗinshi ne yayi maganar,     Muryarshi a kasalance yace"Armstrong,muje gida kawai,am very tired,so i need some rest,'    Armstrong yace"Sir,ya kamata ka ƙarasa aikin ladar da ka fara a taimaki yarinyar asan daga ina take"   "Banyi niyya ba!,why ta fito wannan lokacin almost midnight,zata tashi ta koma inda ta fito ne"ya bashi amsa,   Sam baiji daɗi ba,bai so Sgr yaƙi amincewa dasu taimaki yarinyar ba,yana ji yana gani zasu bar yarinyar kwance acikin garden ɗin cikin wani hali na neman agaji,ba yarda zaiyi,   Tashin Motar armstrong yayi tare da janta baya baya sannan ya karya kwana suka fuce daga cikin garden din,    Lumshe idanunshi yayi yana faman sauke ajiyar zuciya wani irin bacci ne ke fisgarshi,kwanakin nan yana stressing kanshi sosae,matsaloli sunyi yawa a kasar daga wnn sai wnn,abunda ma yafi bashi haushi yadda aka bar yarinya mace kamar wannan ta fito a irin wnn lokacin.   Yana cikin wannan yanayin,ringing din wayarshi ya karaɗe kunnansu,cikin sauri yakai hannu cikin aljihun wandon jikinshi ya curo wayar tare da duba sunan mai kiran nashi,My Own Father,sunan da ya bayyana akan screen din wayar tashi kenan,    ganin Abbansu ne yasa shi yin saurin picking call ɗin tare da kara wayar a kunnanshi yana sauraronshi,   On the other hand abban nasu yace"Rafayet!kana ina ne"?   Sgr yace"Abba yanzu muna kan hanyar dawowa gida ne,akwai wani abu ne"?ya tambaya yana jiran amsar da zai bashi,   Cikin tashin hankali Abban nasu yace"Rafayet!yarinyar nan fa,ta 6ace an nemeta ko'ina acikin garin nan ba'a ganta ba"    "Abba,I don't understand what u'r talking about,wace yarinya ce ta 6ace"?   Kora mashi bayani abban nasu ya shiga yi game da 6atan sehrish,"    Cikin sauri Sgr yayi rejecting kiran abban nasu tare da dakatar da Armstrong daga yin driving din da yake yi yace mashi"mu koma garden din nan,kayi sauri," "okey sir,"ya amsa mashi tare da karya kwana ya miki hanyar da zata maida su can wurin da suka baro,   Tunda Abbansu ya sanar dashi 6atan sehrish,yake ji aranshi cewa kamar itace yarinyar da waɗannan matasan suka kai cikin garden din nan suna ƙoƙarin lalata mata rayuwarta,tabbas yana ji aranshi cewa itace yarinyar,duk da bai kalli fuskarta ba,amma yana ji aranshi cewa itace, Bayan sun shigar da motar cikin garden ɗin,da sauri sgr ya fito daga cikin motar tare da nufar inda Sehrish take kwance bata iya ko motsi,sai numfashi da take fitarwa sama sama,Kuma har lokacin matasan nan guda huɗu da yayi masu bugun mutuwa suna nan baje ba wanda ya iya tashi,   Ƙarasawa sgr yayi tare da zuƙunnawa wurin da sehrish take kwance,ya sanya hannunshi tare da juyo da fuskarta da kyau yana kallonta,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,taya akai yarinyar takai wannan lokacin awaje bata koma gida ba?da alama daga school take tunda ga uniform nan ajikinta,runtse idanunshi yayi tare da cizon la66ansa, buɗe idanun yayi gwanin ban tsoro sun canza launi saboda tsananin 6acin rae,aranshi yace wai dama ita ce!?   Wurga idanunshi yayi yana kallon matasan nan dake baje ƙasa suna ta faman juyi,yunkurawa yayi a zafafe ya nufesu,naɗe hannun jacket din jikinshi yayi,One bye one ya bisu sae da ya canza masu kamanni yarda ko uwar da ta haifesu in ta gansu bazata ganesu ba,sae da ya tabbatar cewar bazasu ƙara amfanuwa ba,sannan ya haƙura ya ƙyalesu,    dawowa yayi wurinta ya sake zukunnawa tare da sanya hannayeshi biyu,ya ɗaukota tamkar yar baby ya nufi motar da ita,   Tun kan ya ƙaraso Armstrong ya buɗe masu mota,shiga ciki sgr yayi tare da ita,sannan armstrong ya koma ciki yaja motar suka bar cikin garden din,    asaman kafadarshi sehrish ta kwantar da kanta,tare da ƙankameshi sosai jikinta nata faman kerma,yayin da idanunta ke a rufe la66anta nata faman kerma,   gyaran murya ya ɗanyi tare da ce ma armstrong ya kashe na'urar A.C,'   "Okey sir,"ya amsa mashi,batare da 6ata lokaci ba,ya kashe sanyin ac na motar gaba ɗaya,ya kunna masu warmer,na'urar dake dumama yanayi tamkar room heater,nan take cikin motar yayi ɗumi mai daɗin gaske,   A hankali jikinta ya rage kermar da yake yi,zuba ma fuskarta ido yayi yana kallon yadda la66anta keta faman kakarwa,har lokacin bata daina wannan sambatun da takeyi ba,kawar da idanunshi yayi daga kan fuskarta ya mayar dasu saman wuyanta,kafin yayi ƙasa da idanun nashi izuwa saman ƙirjinta,cikin sauri ya kawar da idanunshi gefe guda,saboda wani irin bugu da zuciyarshi tayi,    Janyeta yayi daga jikinshi ya jinginata ajikin seat na motar,sannan ya sanya hannunshi tare da cire jacket ɗin jikinshi,janyo sehrish yayi ya zura mata rigar sanyin tashi ajikinta,bayan ya kammala sanya mata rigar,ya janyo ta ajikinshi sosai ya ruƙota,saboda kermar da jikinta keyi,a firgice take har lokacin,ƙara ƙanƙame shi tayi sosai tana mutsistsike rigar jikinshi da hannunta,bai yi wani aune ba yaji hannunta asaman mararshi,ba ƙaramin gigita yayi ba,wani irin shock yaji ajikinshi,lokaci guda ta jefa shi cikin yanayi,sam ya gaza janye hannunta daga wurin,duk wannan abun da sehrish takeyi mashi bada saninta ba,saboda bata acikin hayyacinta,batasan wanene shi ba,raɗaɗin ciwo ne kawai ke fisgarta,    Kafin Sgr yayi yunkurin zame hannunta daga saman mararshi tuni ta zarce da hannunta inda ba'ason zuwa,a gigice ya damƙo hannunta cikin nashi yana faman jan numfashi,runtse idanunshi yayi yana cizon pink lips ɗinsa,ware idanun nashi yayi a hankali sun canza launi izuwa dan ja,    ƙasa ƙasa yaji muryarta tana cigaba da cewa"kada ku cutar dani dan Allah,ku barni na tafi, karku raba ni da mutunci na.....'   lumshe idanunshi yayi a yayin da yake cigaba da kallon kyakkyawar fuskarta,jacket ɗin da ya sanya mata ba ƙaramin kyau tayi mata ba,duk da tayi mata yawa sosai,    yarda take motsi da tausasan la66anta tana sambatu ba ƙaramin burgeshi tayi ba,gaba ɗaya ya tsinci kanshi da bin su da kallo ko ƙyaftawa baiyi,   Murmushi kawai armstrong ke saki yana driving ɗinsu anatse,ta cikin mirrow yake satar kallon Sgr daya kura ma sehrish ido yana kallonta ko ƙyaftawa baiyi, Kasancewar akwai hasken fitilun motar daya haskaka ko'ina na cikinta, wannan ne ya bashi damar ganinsu sosai,sun burgeshi sosai,bai ta6a ganin Sgr nama wata ƴa mace irin  kallon daya kamashi yanayi ma ƴar tahalikar ba,tabbas kowacece wannan ba ƙaramar mai sa'a bace,ya fadi hakan acikin ranshi,   ƙoƙarin kwantar da kanshi yayi agefen wuyanta,gyaran muryar da yaji ne yasa shi ɗagowa,kumshe dariya armstrong yayi,bakomai yasa shi yi mashi gyaran murya ba fa ce don ya tunasar dashi cewa bafa su kaɗae ne acikin motar ba,yana a kusa kar Ogan nashi ya sa6a number a gabanshi,   Harara sgr ya wurga mashi tare da miƙa hannunshi ajikin motar,ya danna wani wuri,nan take Labule ya sauko daga sama,ya raba tsakaninsu da armstrong ya kasance bai iya hangensu,balle ya san meke wakana,   Dariya sosai armstrong ya shiga yi,abun ba ƙaramin ƙayatar dashi yayi ba,bai so sgr ya sanya labule atsakaninsu ba,yaso yabarshi yaci gaba da kallonsu don ba ƙaramin kyau sukayi mashi ba,   a hankali motar ta ƙetare babban gate din gidan nasu,bayan sun ƙarasa ciki wuring parking space,tsayar da Motar armstrong yayi sannan ya fito cikin sauri ya zagaya tare da buɗe mashi mota,   A lokacin Hayaam na a tsaye gaban window tana leƙen motar tasu,dama tun ɗazu ta tsaya ajikin windown tana jiran dawowarshi,don takai mashi abinci tunda sehrish ta 6ace,tasan cewa yanzu dole ya haƙura ita taci gaba da kai mashi,cike da zumuɗin ganinshi,hayaam ke washe baki tana leƙo motar tasu,fitowar shi kawai take jira daga cikin motar,ta baza idanuwanta kamar na mazuru tana jiran ganin shi,ganin ya zuro kafarshi daga cikin motar yasa Hayaam lumshe ido tana sakin murmushin nan nata,   Lokacin da ya ƙarasa fitowa daga cikin motar,hannu shi ya sanya tare da ɗauko sehrish gaba daya ya azata asaman kafadarshi,   Nan take murnar hayaam ta koma ciki,hankalinta a matukar tashe take kallonsu,har hannu take sanyawa tana murza idanunta wai ko idonta ne ke nuna mata ba dae dae ba,lokacin da ta tabbatar da abunda idanunta ke nuna mata,na ganin Sgr ɗauke da Sehrish a kafaɗarshi,nan take ta fashe da matsanancin kuka tana bubbuga ƙafa,bakin ciki kamar ya kasheta,wani rin ƙululun baƙin ciki ne taji ya tokare mata a maƙoshinta,kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu haka ta dinga ji,   cikin shessheƙar kuka take cewa"Wlh na tsani yarinyar nan!bansan ganinta!ƙoƙari take ta rabani da abunda nake hari!ni bansan ma ya akai ya ganta ba,harya ɗaukota acikin motarshi!Allah bazan barta ba saina illata ta,tunda har ta sanya na zubar da hawayena akanta!saina ga bayanta kafin ita taga bayan nawa"!   Haka hayaam taci gaba da sambatu tana zagaye dakin nata kamar wata zararriya,   Atare suka sauke ajiyar zuciya lokacin da Sgr ya shigo cikin main palour din,kafadarshi ɗauke da sehrish,gaba dayansu sunyi mamakin ganinshi tare da ita,yarda akai har ya hadu da yarinyar,   fuskar Abbansu dauke da farin ciki ya shiga furta"Alhamdulillah!Alhamdulillah Allah mungode maka,ba rabon asha wahala!"   Wani irin farin ciki ne ya lullu6e junaid ganin sehrish dinshi,duk da ya ɗan tsorata da ganin yarda sgr ya daukota kamar bata numfashi,suma sauran duk sunyi tsaitsaye suna jiran jin bayani daga wurinshi, Ƙarasawa ciki yayi tare da kwantar da ita saman 3 seater,   Muryar Abbansu yaji a bayanshi yana cewa"Meya same ta ne?a ina kuka ganta"?   Bai bashi amsa ba sae da ya fara juyawa ya kalli su fawan dake atsaye suna kallonsu yace"Tsayuwar me kuke anan,ba kuje kun kwanta ba,"? "Sun shiga damuwa ne na rashin ganinta da akayi,shiyasa suka gaza runtsawa suma,"abban nasu ne ya bashi amsa,   "Kowa yaje ya kwanta,"cike da bada umarni yayi maganar,nan da nan kowa ya kama hanyar zuwa bedroom ɗinshi ba tare da sunji wani bayani ba,   Mutum uku ne suka rage atsaye suna sauraron jin bayani daga wurinshi,Abbansu da kuma marshal omar sae kanal yousouf,    Matsawa omar yayi kusa da sgr dake atsaye ya dafa kafadarshi tare da cewa"Bro,a ina kuka same ta ne? da kyar Sgr ya iya buɗe bakinshi ya kwashe dukkan abunda ya faru ya sanar masu,   ba ƙaramin tausayinta suka ji ba,jikinsu duk yayi sanyi sosai,bayan komai ya daidaita,Sgr ya wuce part dinshi a gajiye, Azmee ce tayi ƙoƙarin ɗaukar sehrish ta wuce da ita cikin bedroom ɗinta,asaman gado ta kwantar da ita,tare da jan bargo ta lullu6e mata jikinta,ta jima azaune cikin ɗakin nata tana kallonta a ranta tana tunanin ya akai ta fita daga gidan,a lokacin ta samu bacci,sae da dare ya raba sannan azmee ta koma ɗakinta, Koda sgr ya shiga bedroom din shi,gaba daya kasala ta gama mamaye mashi ko'ina na jikinshi,hakanan ya dinga jin kamar yaje ya ganota,wane hali take ciki,ta samu bacci kuwa,tunani ya soma yi anya ba dalilin datse mata gashin da yayi bane yasa tayi yunƙurin guduwa daga wurinsu ba?saboda ya lura ba ƙaramin so take ma gashin kannan nata ba, Ya ƙarasa zancen zucin nashi a yayin da yake ƙarasa cire kayan jikinshi,zame belt ɗin wandonshi yayi ya tube shi daga jikin trouser ɗinshi,abunda sehrish tayi mashi ɗazun ne ya faɗo mashi a ranshi,lokacin da takai hannunta asaman mararshi,tuna wannan yasa shi jin wani yanayi mara misaltuwa atattare dashi,ya rasa me yasa yarinyar take ƙoƙarin canza mashi alƙiblarshi,da alama in baiyi dagaske ba zata ci nasara akan shi ne, Sai da ya kammala cire kayan jikinshi ya rage daga shi sae white short ajikinshi,sannan ya wuce cikin toilet don yin wanka, Bayan ya kammala wankan ya fito jikinshi sanye da bathrobe fara,wata irin kasala ta mamayeshi,har ya gaza shirya kanshi acikin sleeping dress dinshi,a ƙarshe ya lalla6a tare da hayewa saman gadon shi,hannu ya miƙa tare da janyo pillow ya rungumo shi asaman faffaɗan kirjinshi,a hankali ya rufe idanunshi da niyyar yin bacci nan take brain dinshi,ta shiga tariyo mashi abunda ya faru tsakanin shi da sehrish,ranar da ya taka 6awon ayaba,ta tarboshi suka faɗa saman gadon shi atare,' Mamaki ne ya kama sgr,ya shiga tambayar kanshi Why yake tunaninta?me yasa yake tuna abubuwan da suka faru atsakaninshi da yarinyar?me yasa take ta faɗo mashi aranshi? juyi yayi asaman katafaren gadon nashi ya canza position din kwanciyar tashi,ya jima a wannan yanayin kafin ya samu bacci yayi awon gaba dashi, A tsakar dare junaid ya farka daga bacci,dama tun kafin ya kwanta baccin yake ta addu'ar Allah yasa ya farka tsakar dare yayi sallah,sae gashi kuma cikin sa'a ya farka,dama sama rai ne abun,saukowa yayi daga saman gadon ya wuce cikin toilet,jim kaɗan ya fito daga cikin toilet din,ruwan alwala na ɗiɗɗigowa daga fuskarshi,darduma ya dauko tare da shimfiɗata,ya kabbara salla tare da wannan kyakkyawanr niyyar tashi,anatse ya shiga jera sallolin batare da gajiyawa ba,tun yanayi cikin daɗin rae,har ƙafafunshi suka soma rurruƙewa sannan ya sallame sallar tare da lankwashe kafafunshi asaman sallar ya ɗaga hannayenshi yana addu'o'i yayin da hawaye ke 6ul6ulowa daga cikin idanunshi,gwanin ban tausayi, Bayan ya kammala addu'o'in nashi ya tattara dardumar ya ninketa,bayan ya ajiyeta,yana ƙokarin komawa saman gadon ya kwanta,wani abu ya faɗo daga cikin hancinshi,cikin sauri junaid yakai idanunshi a kasan inda abun ya fadi, Dunƙulen jini ya gani,nan take hankalinshi yayi mugun tashi,jikin shi ya shiga kerma,gaba ɗaya yabi ya rikice ya razana sosai,ganin yarda dunkulen jinin ke faɗowa daga hancinshi,da gudun gaske ya faɗa cikin toilet,agaban basin ya tsaya tare da dukar da kanshi,dunkulen jinin ya cigaba da fadowa,tashin hankalin da ba'a sama shi date,haƙika junaid yana cikin mawuyacin hali,gashi yaƙi sanarma kowa bare atari abun da wuri,kuma da alama koma meye ya gama yi mashi Illah, Daƙyar ya samu dunkulen jinin ya daina 6ul6ulowa daga hancinshi,ya wanke fuskarshi tare da kora jinin da ruwa ya wuce,. Sannan ya fito daga cikin toilet din hannunshi ruƙe da tissue din daya yago,zukunnawa yayi tare da kwashe dunkulen jinin daya fara fitowa daga hancinsa ya faɗi kasan tiles din dakin,acikin tissue din ya dauke shi sannan ya jefa acikin room dustbin dinsu, jikin shi yayi mugun sanyin da bai ta6a yi mashi ba,Wanda hakan ya ƙara tabbatar mashi da cewa da wuya ya rayu,in ba wani ikon na ubangiji ba, jiki asanyaye ya taka izuwa wurin bedside drawer,ya ɗauki wayarshi dake ajiye anan sama,lalubo numbar mommynsu yayi tare da danna mata kira, Ringing ta shiga yi,kusan sau uku ba'a ɗaga ba,ana hudunne ta ɗaga kiran tare da cewa"Hello,babyn Abbanshi,yau kaine da kanka ka kirani awaya?ae nayi tunanin ka manta dani" maimakon yayi mata magana,sae ji tayi ya fashe mata da kuka, A gigice Alexandra ta shiga ambaton sunan shi tana cewa"Ju..ju..junaid..meya faru ne!me yasa kake kuka?waya ta6a min kaine!? Cikin shessheƙar kuka ya soma magana"Mommy ba zaki zo ba ko"! Yanayin yarda taji muryarshi yasa jikinta yin sanyi, Cigaba da magana yayi"dama nasani baki sona mommy,da ace kina sona ba zaki kai wannan lokacin baki zo kin duba halin da nake ciki ba,Mommy so kike sae ranar dana mutu sannan zaki zo ki ga gawata!" gabanta ne taji yayi wani irin bugu,maganar shi ba ƙaramin kashe mata jiki yayi ba,muryarta na rawa tace"pls Romeo na,kadaina wannan maganar banason ji,dan Allah kadaina......'yana jin shessheƙar kukan mommyn nasu, cikin sanyin murya yace"Shikenan zan daina mommy,amma inaso na sanyaki acikin idanuna,inaso na ganki a matsayin mahaifiyata,don Allah kizo mommy kafin na mutu ....idan baki zo ba bazan yafe maki ba.....' Wannan maganar ta junaid ba ƙaramin firgita momyntasu yayi ba, Hankali tashe ta shiga cewa"its okey,zanzo zanzo kayi shiru kaji zanzo insha Allah,' "When"?yayi maganar ayayin da yake share hawayen fuskarshi da hannunshi guda,yayin da dayan ke maƙale da wayarshi, "Ko da yaushe kakeso junaid zanzo," Jinjina kanshi yayi tare da cewa"gobe mommy,idan ya wuce gobe ba zaki ganni ba," cikin sauri tace"zanzo kaji My baby boy,ina sonka sosai," Lumshe idanunshi yayi har cikin ranshi yaji wani irin sanyi ya ratsa shi,yanzu baida wani burin daya wuce ya sanya mahaifiyar shi acikin idanunshi,bai ta6a ganinta ba ido da ido,tsoranshi karya mutu bai sanyata acikin idanunshi ba, "Naji kayi shiru baka ce komai ba" Muryarshi a kasalance yace"Bacci nake ji mommy zanje na kwanta,dare yayi sosai,yanzu ma farkawa nayi daga bacci,shine na kiraki a waya," murmushi tayi tamkar tana a gabanshi tace"kafin ka aje wayar zan tambayeka wani abu," Junaid yace"ina sauraronki mommy," Cigaba da magana tayi "ranar daka fara gani na,ido cikin ido faɗamun wane kalar farin ciki za kayi,kuma wata irin tarba zakayi mun," Sae lokacin junaid ya ɗanyi murmushi tare da cewa"Bazan iya bayyana farin cikin da zanyi ba,a wannan lokacin,abu daya kawai nasan zanyi shine zan rungumeki sosai na kankameki na kwantar da kaina asaman ƙirjinki sannan na kira ki da sunan Mommyna," dariya sosai Alexandra tayi ba ƙaramin daɗin maganar shi taji ba, tsagaitawa tayi da yin dariyar da takeyi sannan tace"Ni kuma kasan me zanyi a wannan lokacin"?. "A'a sai kin faɗamun,"ashagwa6e yayi maganar, Alexandara tace"ni kuma a wannan lokacin da zan fara sanyaka acikin idanuna a matsayin yaron dana bari tun yana ɗan jinjirinsa na tafi nabarshi ban ƙarasa shayar dashi ba,zanji kunyar ka sosai junaid kuma zan zubar da hawayena a wannan lokacin,sannan in janyo ka ajikina nayi hugging naka very tight,zan shafa sumar kanka da hannuna.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda wani sabon kukan da taji yazo mata, cikin shassheƙar kukan taci gaba da cewa"Junaid ka yafe mun,na cutar dakai sosai,ban kyauta maka ba,nayi maka alƙawarin cewa muddin nazo nigeria zanyi maka duk wani abu da banyi maka ba,a lokacin da kake yaro,shayar dakai ne kawai bazan yi ba,shima ɗin don saboda ka wuce matakin da zan shayar dakaine,amma har goya ka sai nayi,komai zan maka junaid,koda yaushe zan kasance tare dakai,zan baka farin cikin da ban baka ba a lokacin da kake yaro... ' natsuwa junaid yayi yana sauraron kalaman mommyntasu,hankalinshi ba ƙaramin kwanciya yayi ba,ta faranta mashi rae sosai a daren ranar,sun jima suna waya,kafin daga bisani sukayi sallama ya ajiye wayar saman drawer din,sannan ya koma saman gadon ya kwanta,tare da aza kanshi asaman bayan Abban nasu dake ta sharar bacci, Allah sarki junaid,bazan ta6a mantawa da wannan lokacin ba arayuwata,na zubar da hawaye na sosae akan rashin shi da nayi............" A 6angaren su hosana kuwa,saboda sun kwallafa rai akan ganin sehrish daren ranar ko bacci ba suyi ba,a zaune suka kwana,su biyu tsakiyar gadon sun manne da Juna, "Jahad me kike tunani"?hosana ce ta tambayata tana kallon fuskarta ganin tana ta faman sakin murmushi, Jahad tace"Ina tunanin ko ya Sehrish ta koma yanzu?ta ƙara haske ne?ko ta ƙara kiba?Ya zata ji idan ta ganmu.!      *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari, "Nima jahad,inaso naga ya rishi ɗinmu ta koma,a qagare nake da naje naganta,Allah yasa gobe ya Omar yazo ya ɗauke mu da wuri  ya kaimu gidansu,"cike da farin ciki tayi maganar, "Da zarar mun ga rishi shikenan bamu da sauran damuwa,abu ɗaya ya rage mana shi ne ganin Mahaifiyarmu, Inason sake ganinta bansan a wane hali take ciki ba,"jiki asanyaye Jahad ta ƙarasa maganar,   haka suka zauna tsawon daren nan suna jiran safiya tayi. Wuraren sallar asuba,gaba daya matasan gidan suka hallara domin zuwa gabatar da sallah,daga ciki hada Uncle ɗinsu Abusufyan,a jere suka jera tare dashi,yadda kasan tsaran su Sgr haka ya koma acikin su, A 6angaren sehrish kuwa,raɗaɗin ciwon nan ne ya kuma tashinta daga dogon baccin daya ɗauke ta,wata irin zufa ce ta shiga gangaro mata a gefen fuskarta,jikinta na ta faman kerma,daƙyar ta iya yunƙurawa ta miƙe daga zaune tana faman ƙanƙame jikinta tana dan bin dakin da kallo,sam bata lura da jacket ɗin da Rafayet ya zura mata ba, Jin alamun ana kwankwasa ƙopar dakin yasa ta yin saurin cewa"wanene," Muryar azmee taji daga waje tana cewa"Ni ce sehrish," Bayan ta bata amsa ta turo ƙopar ta shigo,saboda a buɗe tabar mata ita daren jiya,   "Kin tashi kenan,"ta ambaci hakan yayin da take ƙarasawa daga gefen gadon nata ta zauna tana kallon fuskarta,    Muryarta na kerma tace"Aunty azmee bana jin daɗi,tun jiya nake fama da ciwon ciki sosai,bansan me yasa junaid baizo ya ɗaukeni daga school ba,ina fata dai lafiyarshi qalou ko"?tayi tambayar fuskarta ɗauke da damuwa,   Cike da mamaki Azmee tace"kamarya junaid baije ya ɗauke ki daga school ba!?nifa da kaina na ruƙe hannunki lokacin da kika dawo daga school na kawoki har cikin bedroom ɗinki sannan na shirya maki lunch ɗinki,"   Tunda azmee tasoma kora mata jawabin nan,gaba daya duk tabi ta rikice saboda bata gane inda ta dosa ba,   "Aunty azmee wlh bani bace,nifa bani da lafiya,ina can kwance cikin toilet ɗin makarantar mu,bana acikin hayyacina,har aka tashi daga skul bansani ba,sae bayan da kowa ya watse sannan naji sauƙin cikin nawa,shine har na samu na fito,lokacin da nazo bakin gate ɗin babu kowa acikin makarantar,mai gadi ne ma yace na koma daga waje na jira mai zuwa ɗaukar tawa..............'gaba ɗaya sehrish ta kwashe duk abunda ya faru ta sanar ma Azmee har zuwa inda taji an ɗauketa an turata cikin mota,tun daga nan ne bata ƙara sanin meya faru ba, Hankalin Azmee fa ya tashi,abun ya ɗaure mata kai,musamman da taga Uniform ajikin sehrish wannan ya ƙara tabbatar mata da cewa daga school ɗin take,tunani ta shiga yi,shin wacece kuma Yarinyar da junaid ya ɗauko daga makaranta a maimakon ita sehrish din!kodae Aljana ce ya ɗauko!tabbas zai iya yiyuwa aljannar ce in ba haka ba,kamanninsu yayi yawa komai na fuskarsu iri ɗaya,   jin sehrish na sakin nishi yasa azmee dawowa daga duniyar tunanin data tafi,cikin sauri ta ruƙo hannunta tare da cewa"Tashi mu shiga toilet na taimaka maki kiyi wanka da ruwan zafi,kafin mu fito nasan cewa sun dawo daga masallacin,zanyi ma wani daga cikinsu magana yayi ma babban yayansu magana akan ya baki maganin da zaki sha ki samu sauki,   a hankali tasamu ta sauko daga saman gadon tabi azmee suka shige cikin toilet din,daga baya azmee ta fito ta barta acikin toilet din tana ƙarasa wankan,    Zagaye ɗakin nata Azmee ta shiga yi,yayin da take cigaba da tunanin Wacece wannan yarinyar da tazo gidan ɗazu mai irin fuskar sehrish komai da komai,tabbas mutunce ba aljana ba,abun yayi confusing dinta,    amma me yasa ta tambayeni ya Omar na nan amaimakon Sgr!    Azmee ce ta jefa ma kanta wannan tambayar,lokaci guda ta tuna da twins ɗin da Omar yace zai kawo gidan Abusufyan ɗinsu,tabbas ba shakka yarinyar tasan Marshal Omar shiyasa har ta tambayeta shi,   cike da mamaki azmee ta ɗan tsaya daga zagayen da take yi na wani lokaci ta ɗanyi shiru tana nazarin wani abu kafin daga bisani tace"in har dagaske ne abunda nake hasashe,wannan yaran da Omar yake Ruƙo a wurinshi,ƴan uwan sehrish ne!dama ta ta6a sanar dani cewa su ƴan ukune,kuma kamanninsu ɗaya sak!ina tunanin cewa Yaran suma a makarantarsu sehrish suke,wannan dalilin ne yasa junaid yayi kuskuren ɗauko yarinyar amaimakon sehrish !" Bata da tabbacin abunda take hasashe ko gaskiya ne,amma ranta na bata cewa tabbas haka ne!    fitowar sehrish daga cikin toilet,yasa azmee juyawa tana kallonta,daƙyar take iya ɗaga kafarta,jikinta na sanye da inners farare,half vest da kuma white short wanda bai kai guiwarta ba,   Ganin yadda take tafiya tana dafe saitin mararta yasa azmee,ƙarasawa wurinta da sauri ta janyo ta ajikinta,ta taimaka mata harta haye saman gadon,abu kamar wasa sehrish ta soma yarfa hannu tana ambaton sunan Allah abakinta,daga bisani kuma tashiga bubbuga ƙafafunta asaman gadon tana matse cikin nata,   Cikin fita hayyaci take cewa"Aunty zan mutu!cikina zafi yake mun,kamar ana ƙona ƴan hanjin cikina,ko'ina raɗaɗi yakeyi mun,"   Jin wannan maganar ta sehrish ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba, juyawa tayi da sauri ta fuce daga cikin ɗakin,kai tsaye ta nufi main palour din tana jiran ƙarasowar su,saboda taji dirar motocinsu alamar sun shigo cikin gidan,     Marshal Omar ne tare da Sgr suka fara shigowa cikin babban falon,yayin da Uncle abusufyan ke abayansu shi da Abbansu sae Junaid dake ruƙe da hannun Uncle din nasu acikin nashi,   ganin azmee atsaye cikin damuwa yasa Omar cewa"meya faru ne naganki atsaye nan? tsayawa da tafiyar suka yi gaba daya suna jiran jin amsarta,    hankali amatuƙar tashe azmee tace"Sehrish ce bata jin daɗi sosai,tana acan ɗaki na barota tana ta kuka tana cewa zata mutu..dan Allah a taimaka mata,"     Omar yace"subhanallahi!meya ke damunta ne?   "Ciwon ciki ne,"ta bashi amsa,matsowa Abbansu yayi kusa dasu Omar yace"Tasha magani ne"?   "Bata sha komai ba,"azmee ta amsa mashi,   Mayar da idanunshi yayi kan Sgr dake tsaye ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi,    Yace"Ko zaka iya taimakawa ka duba mana ita ne?in yaso ko allura ce sae ayi mata,zata fi samun relief ɗin ciwon nata,"   sakin hannayenshi yayi daga saman chest dinshi,sannan ya kalli azmee tare da cewa"muje ɗakin nata,"   murmushi Abbansu ya ɗan saki ba ƙaramin daɗi yaji ba,daya amince zai duba ta,shi fa yanzu abbansu kallon mata da miji yake yi masu,tun ranar daya fara kamasu manne da juna,tun daga ranar ya daina yi masu kallon wai saurayi da budurwa,fatihar ce kawai ba'a kaiga shafawa ba,   "Yaya hussein wai wacece bata da lafiya ne"?Abusufyan ne yayi mashi tambayar a lokacin da suke wucewa daga cikin,   Fuskar abba ɗauke da murmushi yace"Yarinyar dake taya azmee aiki ce,itace ɗazu junaid yake magana akan ba'a ganta ba,hankalinmu duk ya tashi da 6atanta,cikin ikon Allah sae gata an samu rafayet ya dawo da ita cikin gidan nan," Abusufyan yace"Allah ya bata lafiya," Abba ya amsa mashi da ameen,   Daganan suka raba hanya dashi,kowa ya wuce bedroom ɗinshi, Acan kuwa,bayan Azmee tayi ma sgr jagora har izuwa ɗakin sehrish,ita tafara shiga sannan ya bi bayanta har izuwa wurin gadonta,karo na farko kenan da Sgr yafara shiga ɗakin Sehrish,lokacin ne yama san inda dakin yake,tsayawa yayi daga tsaye yana kallonta,sae faman juyi takeyi atsakiyar gadon gaba ɗaya tagama fita hayyacinta saboda raɗaɗin ciwon cikinta,   Hannu azmee tasa tare da janyo bargo ta lullu6e mata jikinta,ganin yarda surar jikinta ta fito sosai,    "Wane kalar ciwon ciki ne takeyi"?yayi maganar ba tare daya kalli azmee ba,yana da tabbacin cewa menstruation ne,amma yafiso yaji daga bakinta,   "Na al'ada ne,"azmee ta bashi amsa,   "Okey,"ya ambaci hakan tare da juyawa ya fuce daga ɗakin,   Komawa azmee tayi tare da zama daga gefen sehrish tana kallonta gwanin ban tausayi,Ba ƙaramar wahala tasha ba,ta jigata sosai,ta wani 6angaren kuma taji daɗi da Sgr ne zai dubata,don tasan cewa zata samu kyakkyawar kulawa awurinshi,zaiyi mata abunda ya dace ne,"   15mins da fitar shi,sae gashi ya dawo cikin ɗakin hannunshi ɗauke da Allura har ya ɗura ruwan allurar acikin sirinjin,    Ganin shi yasa azmee mikewa daga zaunen da take gefen gadon ta bashi wuri don ya samu damar yi mata allurar,   Zama yayi daga gefen gadon tare da ruƙo hannun sehrish da ta fito dashi daga cikin bargon da azmee ta rufa mata ajikinta sae faman hargowa take tana ambaton cikinta,    Yana ƙokarin tsira mata allurar,ta ware idanunta sosai kai tsaye suka sauka akan Syringe ɗin dake hannunshi,duk da bata acikin hayyacinta amma ta gane cewa Allura ce fa za'ayi mata,   a firgice sehrish ta fusge hannunta tare da yin wurgi da bargon da azmee ta yafa mata,gefe guda ta jefar dashi,matse kanta tayi ajikin headboard na gadon tana faman shesshekar kuka tana cewa"banaso!dan Allah ku kyaleni kada kuyi mun allura,"gaba daya duk tabi ta firgice dama ta tsani allura arayuwarta mugun tsoranta take ji,     sanin cewa Sgr yana da bad temper bazai iya jure koke-koken da sehrish keyi mashi ba,muddin taƙi tsayawa zai iya kwashe ta da mari,don ta dawo dai dai,   Cikin sauri azmee tace"Zan iya ruƙe maka ita?   "E" ya bata amsa ataƙaice, Wucewa saman gadon azmee tayi tare da rurruke sehrish,aikuwa a gigice sehrish ta shiga kokawar kwace kwanta hada gartsa mata cizo a hannunta,     Cire hannunta tayi daga ruƙon da tayi ma sehrish,saboda taji zafin cizon da tayi mata,   Ganin haka yasa sgr bata Umarnin ta fita daga ɗakin,    Saukowa azmee tayi daga saman gadon,tare da kama hanya ta fuce daga cikin dakin,   A waje ta samu junaid atsaye sae faman zagaye yake yi a wurin ɗakunan nasu,bawan Allah duk ya rasa natsuwarshi tunda yaji cewar Sehrish bata da lafiya,   "Junaid," jin an ambaci sunanshi yasa shi yin firgit ya juya yana kallon azmee dake tsaye a kopar dakin,   Ƙarasawa yayi wurinta fuskarshi ɗauke da damuwa yace"Aunty azmee wai meya faru da sehrish ne?ina taje ne?duk nabi na ruɗe wlh,bansan ta yadda akai ta sanya ƙafa tabar gidan nan ba,nifa dakaina na ɗaukota daga school na kawota gida,"   ruƙo hannunshi azmee tayi taja shi daga dan gefe suna fuskantar juna tace"Junaid ka kwantar da hankalinka,ba abunda ya faru da sehrish,stomach pain ne kawai kuma insha Allah zata ji sauƙi ne,sannan maganar fitar sehrish daga cikin gidan nan,kada kayi confusing kanka,ka manta da wannan kawai,komai ya wuce,"   ajiyar zuciya ya shiga saukewa,har cikin ranshi yaji daɗin bayanin da azmee tayi mashi,   "Yanzu kaje ka kwanta mana,zuwa da safe in yaso sae kazo ka dubata ko"?   cike da shagwa6a yace"Aunty azmee kona koma ɗaki bazan iya bacci ba,in har ban sanyata acikin idanuna ba,'   Murmushi azmee tayi tace"ummm romeo kenan shugaban ƴan soyayya,dama tunda na ganka nan tsaye nasan cewa abunne ya motsa,"   Sunnar da kai ƙasa junaid yayi yana faman sakin murmushi,     A nan suka tsaya suna cigaba da yin fira atsakaninsu,janye mashi hankali azmee ta dinga yi saboda ta lura da yadda yake firgita duk in yaji sautin kukan sehrish,daƙyar tasamu junaid ya wuce bedroom dinshi itama ta wuce nata ɗakin,   suna barin wurin hayaam ta fito daga ɗakinta,cikin sanɗa take tafiya harta ƙaraso wurin kopar ɗakin sehrish,anan ta tsaya tare da jingina kanta ajikin ƙopar ta kasa kunnanta tana sauraran kukan da sehrish keyi,duk atunaninta ita kaɗaice acikin ɗakin take kuka,hakan yasa taji daɗi acikin ranta har tana cewa"Shegiyar Allah yasa ta mutu kowa ya huta,wlh bazan shiga in taimaketa ba,koda ciwon zai kashe ta, acan cikin ɗakin kuwa duk yadda sgr yaso sehrish ta tsaya yayi mata allurar abun ya faskara,taƙi bashi haɗin kai,sae faman yawo take mashi da hankali,wannan ne yasa shi fusata har ya daka mata tsawa,wannan tsawar da sgr ya daka ma sehrish yasa ta dawo cikin hayyacinta sosai,waro ido waje tayi hankalinta a matuƙar tashe take kallon sgr,abun kamar a mafarki take kallonshi,wai dama shine!taya akai ya shigo ɗakinta? a tsananin tsorace take binshi da kallo,jallabiya ce fara ajikinshi mai gajeran hannu,hakan ya bayyana damtsen hannun nan nashi,    zazzare ido tashiga yi tana kallon kyakkyawar fuskarshi,   Matsawa sgr yayi kusa da ita,suna facing din juna face to face,a hankali yake bin fuskarta da kallo yayin da itama take ƙare ma tashi kallo,har lokacin kokwanto takeyi anya shine da kanshi ya shigo ɗakinta,Sgr sukutum da guda yau a bedroom ɗinta zaune gefen gadonta,a kusa da ita?   Hmmmmm ina labarin Hayaam dake la6e ajikin ƙopar ɗakin tana sauraron kukan Sehrish,ae tun lokacin da taji muryar sgr ya daka ma sehrish tsawa,jinjina kai ta shiga yi tana faman sakin huci kamar wata zakanya saboda tsabar 6acin rai da takaici,acikin ranta tashiga cewa"lallaima yarinyar nan,wato harta samu matsayin da sgr zai dinga takawa da ƙafafunshi yana shiga ɗakinta,'   ɗagowa tayi tare da aza hannunta asaman kanta tana cewa"nashiga uku ni yau hayaam bansan ya zanyi da yarinyar can ba,tana shigar min gonata!tabbas dole nayi wani abu akanta,bazan ƙyaleta ba tayi nasara akaina ba,   Tana cikin wannan zancen zucin nata ta jiyo muryar sgr yana magana daga cikin ɗakin,cikin sauri ta kasa kunne tana sauraron me yake ce ma sehrish ɗin,    "Bana son wannan koke koken da kikeyi mun,kamar zan rabaki da ranki ne,"!.    tsit Sehrish tayi tana sauraranshi,yayin da take bin pink lips ɗinshi da kallo,   Cigaba da magana yayi anatse yace"idan kika natsu,ba da zafi zan maki ba,a hankali zanyi maki,batare da kowa ya ji mu ba,"    tashin hankali tunda hayaam taji wannan zancen da Sgr yakeyi ma sehrish nan take taji gabanta ya faɗi rass,zullumi ta shiga yi gabanta na faduwa,duk atunaninta wani mummunan abunne sgr da sehrish ke aikatawa,gaba daya ta rasa natsuwarta,kamar ta fada cikin ɗakin  taga me suke aikatawa haka take ji aranta,zuciyarta sae faman azalzalarta takeyi tana tunzurata akan ta shiga taga me sukeyi,   Yanayin yarda sgr keyi mata magana cikin sanyin murya,yasa taji wani irin yanayi atare da ita,da kanta ta miƙa mashi hannunta don yayi mata allurar,   Hannunshi yasa tare da ruƙo wrist din hannunta,sannu a hankali ya zura allurar a cikin jijiyar hannun nata,lokacin da tsinin allurar ya ratsa cikin jijiyar,a ɗan razane sehrish ta saki ƴar ƙara tare da runtse idanunta tana faman cizon la66anta,   a hankali sgr ya ɗago da blue eyes ɗinshi yana kallon fuskar sehrish,zuba mata ido yayi yana kallon eye lashes ɗin idanunta masu tsayin gaske,kafin ya mayar da idanun nashi akan la66anta dake ta faman kerma,tana ɗan cizon gefensu da Teeth ɗinta,   gaba daya ya gaza control ɗin kanshi,har ya gaza janye idanunshi daga kallon la66anta da yake yi,ba ƙaramin yanayi ta jefa shi ba,cos she looks so sexy a wannan lokacin komai tayi bashi sha'awa yake yi,   siraran hawaye ne suka shiga gangarowa daga cikin idanunta,batare da saninshi ba yakai hannu zai share mata hawayen,buɗe idanuwan da tayi ne yasa shi dakatawa tare da janye hannunshi, ya kawar da kanshi gefe guda a lokacin ya kammala yi mata allurar,    tayi danasanin buɗe idanuwanta da tayi,taso ace ya sanya hannayen shi ya share mata hawayen,ko ba komai zata ajiye wannan ranar a matsayin ɗaya daga cikin ranakun da suka kafa tarihi a rayuwarta,    Ganin ya miƙe tsaye tare da kama hanyar fita daga cikin bedroom ɗin nata yasa tayi saurin cewa"ngd da taimakon da kayi mun,"   Batare da ya juyo ya kalleta ba yace"get well soon" Yana ƙarasa maganar tashi yasa hannu ya ruƙe handle ɗin ƙopar zai buɗe door ɗin ɗakin,jin motsin shi yasa jiki na rawa hayaam ta watsa da gudu izuwa cikin bedroom ɗinta, Upstairs ya nufa ya wuce part ɗinshi a wani irin yanayi ya faɗa saman katafaren gadonshi,yayin da idanunshi ke kallon saman ceiling ɗin ɗakin nashi,    Wani abu ne ya faɗo mashi aranshi,lokacin suna da shekaru goma sha wani abu a duniya,a katafaren gidansu dake a los angeles California,su shida suke rayuwa acikin gidan bayan masu aikin dake kula dasu,Uncle donald tare da matar shi wadda suke kira da Mommy,sae Ƴa'ƴansu mata guda biyu Eva da jessy,Sae shi tare da Omar,wata irin rayuwar farin ciki sukeyi acikin gidan,saboda tarairayar da suke samu a wurin matar uncle ɗinsu kamar ita ta haifesu,Allah ya jarabceta da son su,ko ƴa'ƴan data haifa batayi masu irin son da takeyi ma Sgr da Omar,A wannan lokacin Uncle Abusufyan ya ta6a yi masu zuwan bazata,sunyi murna kamar kamar me,suka manne mashi suna tambayarshi ina tsarabar da yazo masu da ita,   Hannu yasa tare da ciro wasu hotuna biyu daga cikin aljihunshi,ya aza hotunan asaman table ɗin gabanshi,ya kifa hotunan yarda bazasu iya tantance hotunan menene ba,    yana daga zaune saman 3 seater,su kuma suna atsaye ruƙe da qugu suna jiran ganin wannan tsarabar da yazo masu da ita,maimakon suga chocolate suga iyayen shan zaƙi sae suka ga Hotuna guda biyu,nan take suka ɗaure fuskokinsu,atare suka haɗa baki wurin tambayar shi menene wannan yake 6oye masu acikin hotunan   Abusufyan yace"so nake kowanne daga cikinku ya za6i ɗaya daga cikin hotunan,kuma duk abunda mutun ya za6a dole ya rungume shi hannu bibbiyu,kun amince da hakan"?   "Yeah,"suka amsa mashi,, "Waye zai fara canka acikin ku"? Shiru rafayet yayi tare da maƙe kafaɗarshi alamar bazai fara ɗauka ba,Kallon Omar Abusufyan yayi yana jiran jin shi mai zaice ko zai fara ɗauka ne,   da yake shi mai sauƙin kaine,baiyi gardama ba,ya sanya hannu tare da ɗaukar ɗaya daga cikin hotunan,juyo da hoton yayi ta gaba yana kallon shi,   Kyakkyawar yarinyace,ƴar ƙarama bazata wuce 5 years ba,tana tsaye akayi mata hoton,'   Murmushi Omar ya shiga saki yana kallon hoton,   "Saura kai Mr arrogant,pick d other one,"yayi maganar cike da zolaya yana kallon Sgr,   tsuke baki yayi tare da miƙa hannunshi ya ɗauki ɗayan hoton daya rage asaman table ɗin,ɗago dashi yayi tare da juyo da gaban hoton yana kallonshi, Koda yayi arba da hoton yarinyar daya dauka nan take ya ɗaure fuskarshi ya haɗe girar idanunshi alamar ranshi ya 6aci,     Muryarshi tamkar zaiyi kuka yace uncle I don't like her, she's ugly, she doesn't have even shoes on her feet,ko gashin kanta ma bata iya gyarawa,ƙazama ce"   Fashewa da dariya Omar yayi hada dafe cikin shi,hakan ya ƙara fusata sgr,   Abusufyan kuwa,ruƙo hannunshi yayi cikin sanyin murya yace"Look rafayet,itama ba laifinta bane kuma bada son ranta ta kasance haka ba,kai kana da gata ne shiyasa kake ganin cewa ita da son ranta ta kasance hakan,Bata da wanda zai gyara mata gashin kan nata ne,babu wanda zai janyota ajikinshi yayi mata wanka ne,kuma kaga ƙarama ce bata da hankalin da zata iya gyara jikinta da kanta,dole sai an nuna mata ga yadda zatayi sannan tayi.....'   Shiru Sgr yayi yana faman hura hanci shi an haɗa shi da mahaukaciya,ɗago da hoton yayi yana ƙare mashi kallo kafin ya kuma kallon uncle ɗin nasu yace"Ita bata da Mommy ne?ina daddyn ta yake ne?ko basu raye ne"?ya jera mashi tambayoyin yana jiran amsar su,   Abusufyan yace"bata dasu, marainiya ce,amma yanzu ta samu,in har ka amince zaka aureta,kaga shi kenan zaka ruƙe ta amana,kuma zaka dinga gyara mata gashin kanta,kana sanya mata takalma,har ma wanka sai kayi mata....'tun kafin abusufyan ya ƙarasa maganar Sgr ya bubbuga ƙafafunshi rae a6ace yake cewa"Uncle I can't marry her,but since I hv a lot of money i will give her to buy whatever she wants" Murmushi Abusufyan yayi yana kallon shi,wato shi bazai aureta ba,amman tunda yana da kudi da yawa zai bata kuɗi ta sayi duk wani abu da take so,yaji daɗin jin maganarshi,koba komai yaron yana da tausayi ta wani 6angaren,dama ya jarabasu ne don yaga reaction ɗin kowannansu,kuma ya samu abunda yake so, Har kawo yanzu,wannan hoton da uncle abusufyan ya basu,yana nan a wurinsu kowannansu ya adana hoton kamar yarda uncle ɗin nasu ya roƙesu akan su ajiye hotunan a wurinsu,karsu yadda su,' "Har yau uncle abusufyan,bai faɗamun wace yarinya ce ajikin photon nan ba,inason nasan kowacece ita,saboda in taimaketa,kamar yarda nayi niyyar taimakonta," Sgr ya fadi hakan. Lumshe idanunshi yayi tare da gyara kwanciyarshi,nan take bacci ya ɗauke shi, *su wanene acikin hotunan da Uncle abusufyan ya basu*!        _Ayi mun uziri,in bansamu damar yin posting gobe ba,abubuwa sunyi mun yawa sosai,bansan ya zanyi ba,amma koda ace banyi a gobe ba zan yi ƙoƙarin biyan bashin wanda banyi ba,tunda ina ƙoƙarin ganin na Kammala littafinn ne insha Allah Zan yi kokarin sanya maku long pages,sannan kuma Labarinsu sehrish da nake tacewa za'ayi za'ayi lokacin shi yazo dama akwai abunda nake jira ne_ *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack A*💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖 *Ga duk mai buƙatar littafin abban sojoji,from book one zuwa book two har inda muka tsaya,300 ne idan yayi payment za'a tura mashi duka sannan za'a sanyashi a grp da zai cigaba da samun cigaban shi akai akai,ga mai buƙata yayi mun magana kai tsaye ta whatsapp ɗina 08103884440 pls banda phone call,ban san meyasa wasu suke kirana a waya ba,Only message nace,kuma insha Allah mutun yayi mun magana bazan share shi ba,zan bashi amsa ne akan lokaci indae ba busy nake ba,sannan masu cewa suna som Book 3,pls su daina abun yana 6ata mun raina,cos ni ban rubuta book 3 ba,wasu can sarakan iyayi ƴan shisshigi suka haɗamun document ɗinshi,to abunda nake so na sanar daku,Abban sojoji dae Iya book two zai ƙare insha Allah,babu wani book 3,🤗* *Kada ku manta muna acikin takon ƙarshe ne🔥🔥🔥* _Father Of soldiers❤story and written by Hafsat Bature Mohamed Boss Lady_ ❤🤍❤ Gagarumar Walima Abba ya shirya masu awashe garin ranar,na murnar dawowar Abusufyan Nigeria,tun da wuri aka soma shirye shiryen gudanar da ita,basu yi inviting ɗin kowa ba,anan cikin gidan kawai za'ayi ta,yasu yasu batare da wani bare ya shigo ba,don nasan halin sumayyer yanzu ta kwaso ƙafa tace zata, Gaba ɗaya ko'ina na gidan ya karaɗe da ƙamshin dadɗaɗan girkin dasu azmee ke yi acikin kitchen ita da Hayaam,tun da sanyin safiya suka fara aikin girke girken,tun bayan da  Abbansu junaid ya sanar da ita game da walimar,suka soma gunadar da aikin batare da 6ata lokaci ba, Matasan gidan kuwa wankan shadda zasu ɗauka gaba ɗayansu,kamar yarda Abbansu ya basu Umarnin su sanya shadda ajikinsu in kuma ba shadda ba kowane kalar kaya zasu iya sanyawa ajikinsu indai namu ne na hausawa,duk sun amince da hakan, "Azmee wai ita yarinyar can bazata fito ta tayamu aiki bane?tun safe muke ta faman aikace aikace ko leƙowa batayi ba,"Hayaam ce tayi maganar yayin da take ta faman kwa6a fulawa acikin roba,duk ta haɗa gumi a fuskarta,' Azmee tace"kema ae ban matsa maki ba,naga kamar kina son aikin ne shiyasa ma nayi maki magana,amma idan kin gaji ko yanzu ma zaki iya tafiya," Rae a6ace tace"yanzu me ya kawo wannan maganar Aunty azmee?nifa ina magana ne akan waccen yarinyar sehrish ya kamata ta fito ayi aikin da ita,na lura kamar bakiso inayi maki magana akanta,kin gatanta yarinyar sosai,shiyasa bata da aikin yi sai dae ta zauna tayi ta sharar bacci kamar matacciya,bata tsinana uban komai acikin gidan nan hakanan take sunan yar aiki...." juyowa azmee tayi daga tsayen da take agaban gas cooker,ta kalli hayaam dake ta faman hura hanci ga uban gumi ta haɗa,   "Hayaam!sehrish ba tada lafiya,shiyasa ban tashe ta daga bacci ba,tun jiya da daddare take fama da raɗaɗin ciwon ciki daƙyar ma aka samu tayi bacci,wannan dalilin ne yasa banyi yunƙurin tashinta daga baccin ba,"    ta6e baki hayaam tayi tare da cigaba da aikin da takeyi cikin ranta tana fadin"ta dai gama iskancinta tayi bacci, Marshal Omar Tun yana cikin toilet wayar shi ke ta faman ringing,cikin sauri ya fito daga cikin toilet ɗin,jikinshi ɗaure da towel,ƙarasawa yayi inda ya ajiye wayar asaman pillow,ya miƙa hannunshi ya ɗauki wayar yana duba mai kiran nashi,murmushi yayi aranshi yace"Allah yasa jiya sun samu bacci,don na lura da yadda suke ta faman ɗokin son ganin ƴar uwar nan tasu,nima kaina a ƙagare nake dana haɗasu wuri guda,don su cigaba da rayuwa atare,   Picking call ɗin yayi ya kara wayar a kunnanshi,   Tun kafin yayi sallama muryar hosana ta katse mashi hanzarinshi da cewa"Ya omar!yaushe zaka zo ne!kai muke ta jira,jiya fa ko bacci ba muyi ba,   Tana kai ƙarshen maganarta Jahad ta kar6e da cewa"ya Omar dan Allah ka tausaya mana,wlh ko breakfast ba muyi ba,kuma muna jin yunwa amma mun fi so muci abinci atare da ƴar uwarmu," Jin wannan maganar ta Jahad,yasa jikin shi yin sanyi,da alama ba ƙaramin so suke yi ma junansu ba,   "Ya omar kayi shiru,"muryar hosana ce tayi maganar a ƙagare,   cikin natsuwa ya soma magana"kuyi haƙuri kunji,insha Allah yau zaku ga ƴar uwarku,bazan samu zuwa ba,amma zan turo major ya ɗauko ku,abunda nake so daku yanzu,ku ci abinci ku ƙoshi,sannan kuyi wanka ku shirya ku sanya kaya masu kyau,a kowane lokaci zaku iya ganinshi yazo,"   Yana jiyo muryoyinsu ta cikin wayar suna ta faman fadin Wayyo daɗi yau zasu ga rishi ɗinsu,'   Sallama yayi masu bayan ya ajiye wayar,ya juya tare da wuce wa wurin closet ɗinshi,tsaf ya shiga shirya kanshi acikin rantsattsiyar shaddar shi. SEHRISH, Kwankwasa ƙopar ɗakin da akayi mata ne da ƙarfi,yasa ta tashi a firgice tana faman zazzare ido,ƙankame bargon jikinta tayi tana ƙara lullu6e jikinta dashi,fuskarta duk a yamutse saboda kukan da tasha jiya,amma yanzu Alhamdulillah tun da tafarka babu wannan ciwon cikin atare da ita,tamkar bata ta6a yin ciwo ba haka ta farka,taji sauƙi sosai,    "Reesh,baby junaid ne fa,in shigo daga ciki"? Muryar junaid ce taji yana magana daga waje,   akasalance tace"eh,ka shigo," . tura ƙopar yayi tare da sanya kafa ya shigo cikin ɗakin hannunshi ɗauke da cup sae tiriri ke fitowa daga ciki,bakomai bane aciki face Corn flakes daya haɗo mata,yaji Uwar madara acikinshi,    Sae faman murmushi yake sakar mata,wuri ya samu daga gefen gadonta ya zauna,sannan yace"reesh ya jikin naki?jiya ko bacci banyi ba saboda damuwa da halin da kike ciki,'   "da sauƙi junaid,yanzu bana jin ciwo atare dani,na wartsake sosai,amma ina fata kaima kana cikin ƙoshin lafiya ko?naga fuskarka kamar ta canza kamanni,kayi haske sosai kuma fuskar ta ɗan sauya haka,Lips ɗinka sun ɗan kumbura kaɗan kalarsu ta ƙara cizawa sosai'tayi maganar yayin da take ƙare ma fuskar tashi kallo kamar wata malamar duba   Junaid yace"farin cikin da kika bani jiya shine ya canza mun kamannin fuskata,ko kin manta abunda mu kayi jiya acikin Mota tare da ke?fuskarshi ɗauke da murmushi yayi maganar,   Cike da mamaki sehrish tace"wane abu kenan?yaushe muka haɗu acikin mota?bayan bakazo ka ɗauke ni daga school ba,ni da ka manta dani junaid,nasha wahala jiya sosai,kamar bazan rayuwa ba,na neme ka na rasa.......'muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,   "Sehrish!me kike nufi da banzo na ɗauke ki ba?ko raɗaɗin ciwo yasa kin manta da abunda ya faru jiya atsakaninmu"?   girgiza kai tayi alamar a'a tace"Nifa bakazo ka ɗauke ni ba,jiya da aka tashi daga school ciwon ciki ya kamani,shine na shiga toilet anan na yanke jiki na faɗi saboda azabar ciwon da nasha,gaba daya nafita hayyaci na.......'gaba ɗaya sehrish ta bashi labarin abunda ya faru da ita tun daga A har zuwa Z,abu ɗaya ne bata sanar dashi ba,shine zuwan waɗan nan matasan guda huɗu da suka ɗauketa a mota, Tun da ta soma kora mashi bayani,hankalinshi yayi mugun tashi,jikin shi har kerma yakeyi wurin cewa"reesh dagaske ne duk abunda kika faɗamun"!.   ɗaga mashi kai tayi alamar eh,sannan tace"ka faɗamun me ya hana ka zuwa ka ɗauke ni junaid?nayi tunanin zaka dawo ka ɗauke ni,in kaji shiru ban dawo gida ba,amma bakazo ba,'   Gaba daya ta gama rikitar dashi duk yabi ya ruɗe,muryarshi har rawa takeyi wurin cewa"wlh nazo jiya school ɗinku,kuma naɗauke ki dakaina acikin motata.......'gaba daya junaid ya kwashe duk abunda ya faru tsakanin shi da jahad ya sanar ma Sehrish,   Zuba mashi ido tayi tana kallonshi ita kanta hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba da jin labarin da junaid ya bata,   "Junaid!ban karyata ka ba!amma anya ba gamo kayi ba?zai iya yiyuwa fa aljana ce in ba haka ba,taya za'a ce tana kama dani komai da komai har ka gaza gane cewa ni ce ko bani bace,"?a ruɗe tayi maganar tana kallon junaid, Junaid sarkin tsoro tuni idanunshi sun cicciko da kwalla tsoranshi kar ace lokacin mutuwar tashi ne yayi shiyasa ya fara ƴan gane gane,zai iya yiyuwa ma mutuwarce tafara kawo mashi ziyara kafin tayi wuff dashi,   tuna wannan yasa shi fashe mata da kuka yana cewa"innalillahi wa'inna ilaihir raji'un shikenan lokacina yayi sehrish,dama nasan daƙyar zan wuce yau araye,....'   Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin yarda junaid ya fashe mata da kuka,da alama ya tsorata sosai'   "Junaid ya isa haka,ka daina kuka kaji,insha Allah ba yanzu zaka mutu ba,har sai mun yi aure mun haifi ƴa'ƴa,in ma zamu mutu atare mutuwar zatazo ta ɗauke mu,'   Jin wannan zancen na sehrish yasa shi yin tsit yana faman sauke ajiyar zuciya,ga dariya na cinta amma tana tsoran karya kuma fashe mata da wani kukan,aranta tace"Tabɗijancan su junaid ansha soyayya da al'jana,da sauƙi ma tunda iya kiss suka tsaya," Miƙa mata cup ɗin hannunshi yayi tare da cewa"gashi kisha,corn flakes ne ni na haɗa maki da kai na,"wani irin tausayinshi ne taji ya kamata,musamman yarda ya nuna damuwarshi akanta,har ya haɗo mata cornflakes dakanshi don tasha,'   zuba mashi ido tayi tana kallonshi,fuskarshi duk a yamutse babu alamun natsuwa atattare dashi,duk ya firgice da jin cewa ba ita bace ya ɗauko a school ba,kuma hankalinshi bazai ta6a kwanciya ba har sae ya tabbatar da cewa ba aljanu bane suka fara kawo mashi ziyara,   Cikin sanyin murya tace"Junaid,dan Allah ka share hawayenka kaji?ko ka manta da alƙawarin da ka ta6a yi mun na cewa ba zaka ƙara yin kuka ba"?   Muryarshi akasalance yace"nadaina,kiyi haƙuri bazan ƙara ba," yayi maganar yayin da yake miƙe mata cup din,   "Ba zaka ban abaki nasha ba"? ɗagowa yayi yana kallonta jin abunda tace,tayi mashi hakan ne don ta kawar da damuwar dake a fuskarshi, Matsawa yayi kusa da ita sosai,sannan ya zura hannunshi tare da dauko cokalin ciki,ya ɗebo cornflakes ɗin ya miƙa mata abakinta,   Buɗe bakinta tayi ya zuba mata aciki,a hankali take murzar shi abakinta tana haɗiyar shi,yayi mata daɗi sosai saboda madarar daya zuba aciki, Haka yaci gaba da bata abakinta tana sha,tun fuskarshi na aɗaure harya fara sakin wannan murmushin nashi,ganin ya washe daga damuwar da yake ciki yasa sehrish cewa"junaid,Wai jiya Uncle ɗin nan naku ya ƙaraso ne"?   "Eh,yanzu haka yana acikin gidan nan ma,ya kamata kije ki gaishe su,hada aunty azeema kanwar Abbanmu itama tazo jiya,"   wani irin farin ciki ne ya lullu6eta cike da zumuɗi tace"inaso naje na gaishe shi,amma ina jin fargabar zuwa wurin shi,"   Junaid yace"meyasa toh?na gaya maki cewa basu da matsala,uncle dinmu mutun ne mai sauƙin kai fiye da tunaninki,haka Aunty azeemarmu ma tana da mutunci sosai,baki ga gift ɗin da takawo mun ba,zan nuna maki anjima,zaki sha mamaki,"   murmushi sehrish tayi a lokacin harya kammala bata corn flakes ɗin, "Bari nashiga toilet nayi wanka,idan na kammala shiryawa sai mu tafi tare da kai ka rakani wurinshi in gaishe dashi,' Amsa mata yayi da toh,sannan ya miƙe tare da ɗaukar cup ɗin daya ajiye asaman side drawer dinta,ya fuce dashi, Ajiyar zuciya ta sauke,bayan fitar shi ta sauko daga saman gadon tare da nufar dressing mirrow dinta ta tsaya tana kallon kanta ta cikin madubin,hannu tasa ta shafo sumar kanta da sgr ya datse mata shi,nan take ta tuna da abunda ya faru jiya lokacin daya shigo yi mata allura,wannan kallon da yayi mata ya tsaya mata aranta,da kuma kalaman da ya furta mata cikin sanyin murya,tabbas tana ji aranta cewa sgr ya fara jin abunda take ji agame dashi,duk da tasan cewa zaiyi wuya ya gane cewa akwai soyayya atattare dashi,kuma zaiyi wuya ya iya furta mata ita, ta cikin mirror ta hango jacket din da sgr ya sanya mata,tana ajiye saman gadon,juyawa tayi cikin sauri tare da kai hannu ta ɗauko rigar sanyin tana kallonta,   tunani tashiga yi rigar wanene wannan?taya akai tazo bedroom ɗinta kuma asaman gadon nata!?   ƙamshin Turaren jikin jacket dinne ya bata amsar tambayar da take nema, Matse rigar tayi a hancinta,anan ta dinga jin ƙamshin turaren Sgr sosai ajikin rigar wannan ya tabbatar mata da cewa tashi ce,a hankali tashiga tunanin ta yadda akai jacket dinshi tazo bedroom ɗinta,kodai jiya ne daya zo yi mata allura.....  ' kwankwasa kopar da akayi ne ya dawo da ita daga zurfin tunanin da tashiga,   "Wanene"?ta tambaya tana kallon kopar, Turo kopar azmee tayi tare da shigowa ciki tana cewa"ni ce sehrish,ya jikin naki fatan kin tashi lafiya,tun ɗazu nake ta zarya wurin leƙowa ɗakinki inga ko kin farka daga baccin,amma duk in nazo sai in same ki,kina ta sharar bacci,'   murmushi sehrish tayi tana kallonta tace"ina kwana Aunty azmee?fatan kun tashi lafiya,ya aiki"? "Alhamdulillah sehrish,jiya mun shiga damuwar rashinki,kuma sai gashi Allah yasa an gano ki,da ba'a ganki ba,da bansan inda zan sanya raina ba,"ta ƙarasa maganar yayin da take ƙarasa shigowa daga ciki,ta tsaya a kusa da sehrish suna fuskantar juna,   "Aunty azmee wai meya faru dani jiya?ya akai nadawo cikin gidan nan?waye ya ɗauko ni?kuma naga wannan jacket din asaman gadona,kamar ta babban yaya ce," Azmee tace"ae jiya,shi da kanshi ya dawo dake acikin gidan nan,gaba ɗayanmu munyi mamakin ganinshi ɗauke da ke a kafaɗarshi,duk da banji da kyau ba,amma naji yana ba Abbansu labarin cewa acan suka same ki cikin wani garden wasu matasa suna ƙoƙarin lalata maki rayuwarki ..........'tunkan azmee ta ƙarasa maganar sehrish ta tunano da abunda ya faru jiya,sai lokacin komai ya dawo cikin kanta,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta jin cewa Sgr ne da kanshi ya taimaki rayuwarta a hannun waɗannan miyagun da suka kai mata hari,kuma taji daɗin bugun da yayi masu,don akan idanunta ya naushi ɗaya daga cikinsu,har haƙoran shi guda biyu suka 6allo daga bakinshi,tun daga sannan ne bata ƙara sanin meya faru ba,amma tabbas taji lokacin daya ɗauke ta a hannunshi ya sanyata acikin motarshi,kuma tana da tabbacin cewa shine ya sanya mata rigar sanyinshi,kilan saboda yaga jikinta na kermar sanyi,   Cike da farin ciki tace"Aunty azmee lokacin da babban yaya ya shigo dani cikin gidan nan akwai wannan rigar ajiki ne ko"?   ɗaga mata kai tayi alamar eh, Washe baki ta shiga yi kamar wadda akayi ma albishir da gidan al'janna,   Murmushi azmee tayi ganin yarda sehrish ke ta faman murnar jin cewa sgr ne ya taimake ta,   hannu tasa tare da dafa shoulders dinta tace"Ki shirya yau akwai walima acikin gidan nan,zuwa anjima wuraren ƙarfe huɗu za'a soma gudanar da ita,inaso kiyi kwalliya sosai yau,yanzun nan zan sanya junaid ya kar6o maki kayanki,wlh mantawa nakeyi,'   "Aunty azmee baki ga abunda babban yaya yayi mun ba?taya zan iya yin gayu da wannan guntun gashi dake akaina"tayi maganar tana damƙo wutsiyar gashin kan nata,   Sae lokacin azmee ta lura da kan nata,hankali atashe tace"garin yaya hakan ya faru?waye ya yanke maki gashi har haka"?   "Babban yaya mana,saboda laifin da bani na aikata ba,ya sanya almakashi ya datse mun gashin kaina,banji daɗi ba,saboda nasha wahala wurin tara shi da yawa yanzu bansan ya za'ae nadawo dashi ba,"cike da damuwa tayi maganar,abun har yanzu yana yi mata ciwo, "Wani laifi kenan kika aikata"? Sehrish tace"a cikin coffee ɗin da nakai mashi jiya da safe,yana cikin sha,gashi ya sarke mashi a makoshi,ran shi ya 6aci sosai har ya yanke mun gashin kaina,wlh aunty azmee ba gashin kaina bane,ni banta6a yin kuskuren barin kaina abuɗe ba,lokacin da nake acikin kitchen,"   shiru Azmee tayi na dan wani lokaci kafin tace"bakomai kawai,kiyi haƙuri nasan kowanene ya aikata hakan,amma banaso ki sanya damuwa aranki,"   "Shikenan,yanzu bari naje nayi wankan,"ta ambaci hakan tare da ajiye jacket ɗin asaman gadon,   "Kinason ƙunshi ne?idan kina ra'ayi zan zana maki da kaina na iya sosai,"   "Inaso sosai Aunty azmee,yaushe rabon dana ga lalle a hannu na har na manta wlh," Azmee tace"yanzu kije kiyi wankan,kafin dai zuwa ƙarfe huɗun zamu kammala komai,'   ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta fuce daga cikin ɗakin,   Wuce wa cikin toilet sehrish tayi domin yin wanka 💋Boss Bature💋 Zaune suke acikin mota su biyu,Ayaan ne ke driving ɗinsu yayin da jahan ke zaune gefen shi sae faman buga tsoki yake yi yana cewa"Ayaan wai ina zaka kaimu ne!ni fa gida nace maka mu koma,banaso afara shagalin walimar nan,bana a kusa,'   Murmushi ayaan yayi tare da cewa"kai dai kawai ka zuba ido ka gani,wani abun mamaki ne nakeso na gwada maka,nasan cewa zai girgiza ka sosai,'ya ƙarasa maganar yayin da yake shigar da motar tasu gate din gidan Yayansu Abbas, Jahan yace"wai dama nan zaka kawo mu?muyi me kenan?Anya kuwa ayaan kasha maganinka na safe kuwa?   dariya Ayaan yayi tare da cewa"a'a ban kaiga sha ba,amma yanzun idan nakai ka cikin gidan nan,na nuna maka abunda nakeso ka gani,bayan mun fito zaka faɗamun ni dakai waye mai buƙatar shan magani acikin mu,"cike da zolaya Ayaan yayi maganar, shiru jahan yayi bai ƙara cewa komai ba ya zuba ma sarautar Allah ido,   Bayan Ayaan yayi parking ɗin motar,ya fito tare da zagayawa ya buɗe ma jahan motar tare da nuna mashi hanya da hannunshi yace"mun ƙaraso yalla6ai," harara jahan ya watsa mashi tare da zura ƙafafunshi ya fito daga cikin motar,yana faman ɗaure fuska ya wuce gaba ayaan yabi bayanshi suka shiga cikin gidan,   Da sallama abakunansu suka shiga cikin babban falon gidan,a lokacin Amani na a cikin kitchen tana aikin breakfast,jin sallamarsu twins yasa ta fitowa da sauri don taga su wanene,   Ba ƙaramin mamaki tayi ba,ganin ayaan da jahan atsaye ruƙe da hannun juna, Ƙarasawa wurinsu tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Sannunku da zuwa,ashe kune sam banyi tsammanin ganinku ba,"   Kawar da kai gefe jahan yayi batare da yace komai ba,.   Ayaan yace"yawwa Aunty amani,kun tashi lafiya,fatan mun same ku lafiya?   Ta amsa mashi da cewa"Lafiya lou Alhamdulillah,nayi farin cikin ganinku,ku ƙaraso daga ciki mana," Jahan yace"sauri muke zamu wuce,Ayaan ka shiga daga ciki ku gaisa ni zan jiraka a mota,'yayi maganar tare da juyawa zai fuce,   Cikin sauri Ayaan ya ruƙo hannunshi tare da cewa"haba jahan wai menene haka?just 15 mins zamuyi fa kafin mu wuce gida,'   ɗaure fuska jahan yayi alamar an takura mashi,   Amani kuwa murmushi kawai tayi,tana mamakin yarda suka kasance twins komai nasu iri daya,amma hali ba iri ɗaya ba,Ayaan ta 6angaren Abbansu yake,shi kuma jahan sak mommynsu ce,   daƙyar Ayaan ya samu jahan ya bisu suka shiga cikin falon,atare suka zauna saman 3 seater,ita kuma ta zauna saman 2 seater tana fuskantar su,yarda jahan ke ta faman yatsina fuska,ba karamin dariya yaso ya bata ba,ji yake kamar ya ɗosana ass ɗinshi asaman ƙayoyi haka yake ji, Ayaan ne ya soma magana"Aunty amani kinji mu shiru ko?ba mu sake zuwa mun duba jikin Amal ba,ban ji daɗi ba wlh abubuwa ne sunyi mana yawa,amma tana aran mu,shiyasa ma muka yanke shawarar zuwa yau mu duba ta,' taji daɗin kalaman ayaan sosai,fuskarta ɗauke da murmushi tace"Amal taji sauƙi sosai,kullum sai ta tambayeni ina twins ɗin nan suke,musamman kai Ayaan tafi tambayarka saboda kaine ka kawota wurina,yanzu bari naje na kawo maku abun ta6awa,kafin na kira maku Amal ɗin ku gaisa," Ta ƙarasa maganar tare da mikewa ta wuce cikin kitchen, Tana barin wurin jahan ya buga tsoki tare da cewa"Wlh ayaan ka bani haushi!ka zauna ka gama tsara mata ƙaryar cewa mun zo duba jikin wannan ƙarmasasshiyar yarinyar ne,yarinyar da nama manta da zancen ta ni,mtswwww,'ya kawar da kanshi gefe yana hura hanci, Ayaan yace"Am sorry bro,nasan ban kyauta ba,amma kayi hakuri kasan banason 6acin ranka,ni aganina bamu kyauta ba,tun ranar da nakawo yarinyar nan,ba mu ƙara zuwa mun dubata ba,kuma abunda ya dace ace munyi ne," ta6e baki jahan yayi tare da kallonshi yace"sannu ko?sarkin tausayi," Jin takun tafiyar Amani ne yasa su kayi shiru,ƙarasowa ciki tayi hannunta ɗauke da tray,cups ne guda biyu,sae lemu masu sanyi acikin roba tare da plate na snacks,asaman table ta ajiye masu sannan ta juya tana cewa"bari na kira Amal din ku gaisa," ɗaukar lemun ayaaan yayi tare da buɗe shi ya tsiyaya masu acikin cup,ya dauki ɗaya ya miƙa ma Jahan,ya kar6a sannan shi kuma ya ɗauki ɗayan,yana sha, Saukowa amani tayi daga upstairs,ta dawo wurinsu ta zauna saman sofa din tana cewa"gata nan zuwa," Ayaan yace"Allah ya kawota lafiya," Gaba daya sun mayar da hankalinsu wurin shan Lemun dake hannunsu,su ka jiyo takon takalminta,kwas kwas, Ayaan ne ya fara ɗago da ido yana hangen yarinyar dake saukowa daga saman benen,juyawa yayi ya kalli amani tare da yin ƙasa da murya yace"ita ce ko"? .murmushi amani tayi tare da daga mashi kai alamar eh, Satar kallon jahan yayi wanda hankalinshi ba a kansu yake ba, A hankali Amal ta ƙarasa saukowa daga saman benen ta nufo inda suke,lokacin da ta ƙaraso wurinsu fuskarta ɗauke da murmushi tace"sannunku da zuwa," Kai tsaye muryarta ta daki dodon kunan Jahan,daɗin muryarta ne yasa Jahan juyowa cikin sauri don yaga wacece,ai yanayin arba da wannan kyakkyawar fuskar ta Amal nan take ya saki Cup ɗin dake hannunshi ƙasa,ya tarwatse lemun ciki ya zube, A gigice ya miƙe tsaye yana kallonta yayin da zuciyarshi ke bugawa da ƙarfi da karfi,yarda kasan hurool aini awurin kyau haka yarinyar ta koma mashi, fara ce tass,har ma tafi Amanin haske,fatar jikinta har wani ƙyalli takeyi saboda gyaran da tasha,tabarakallah masha Allah ta ko'ina amal ta haɗa,ga manyan idanun nan nata dara dara dasu,ga dogon hancin nan nata kamar zaiyi sujjada,la66anta kuwa sunyi red colour sosai tamkar ta shafa janbaki,idan tayi murmushi kamar gonar auduga saboda hasken haƙoranta,lallai ba ƙaramin gyara Amani tayi ma ƙanwarta ba,ta canza mata kamanni sosai,ta fito a balarabiyarta,sleeping dress ne ajikinta pink colour riga da wando,ta yafa gyale fari asaman kanta, dare ɗaya Allah kanyi bature,acewar ayaan, Ina labarin Jahan daya miƙe tsaye ya zuba mata ido yana kallonta ko ƙyaftawa baiyi,abun tamkar a mafarki yake kallonshi,gaba daya ya gama ruɗewa,muryarshi na rawa yace"ke!kece!'cike da mamaki yayi maganar, Amal kuwa aɗan tsorace taja baya,tana faman zazzare mashi kyawawan idanunta,ganin yarda ya harzuƙo kamar zai rufe ta da bugu, murmushi kawai Amani ke saki ita da ayaan suna kallonshi,dama wannan duk shirin Ayaan ne, "Aunty amani!surgery akayi mata ne?if not taya akai tayi transforming haka"? A ruɗe jahan ke tambayarta, miƙewa tsaye amani tayi tare da takawa zuwa inda suke ta ruƙo hannun Amal tana cewa"ikon Allah ne jahan,babu wani surgery da akayi mata,gyarane kawai tasha,dama can Amal kyakkyawa ce,wannan asalin kamannin fuskarta ne ya dawo,' Jiki asanyaye Jahan ya koma tare da zaunawa saman sofa din,har lokacin bai janye idanunshi daga kallon fuskar Amal da yake yi ba,kamar ya haɗiyeta haka yake ji,ya jima yana mamakin wannan ikon Allahn, Miƙewa Ayaan yayi tare da cewa"mu zamu wuce gida,ana can anata shirye-shiryen haɗa walimar murnar dawowar uncle abusufyan,ina fata zaki zo mana tare da Amal,'yayi maganar yana kallon Amani, Tace"mai zai hana,ae muna nan zuwa anjima insha Allah,tare da mu za'a buɗe taron walimar," "Allah ya kawo ku lafiya,'yayi maganar tare da mayar da idanunshi kan JAHAN daya ƙurawa Amal ido kamar mazuru yace"bro,tashi mu tafi mana,kada time ya ƙure mana," jiki amace jahan ya miƙe tare da ruƙo hannun ayaan cikin nashi,su kayi mata sallama tare da kama hanyar fita daga falon, Suna tafiya Jahan na waiwayon Amal kamar zaiyi tuntu6e,hakan ba ƙaramin dariya yaba shi ba,saida suka fito daga cikin falon,bayan sun shiga cikin motarsu,Ayaan ya ɗan kallo shi cikin zolaya yace"Jahan ya kaga ƙarmasasshiyar ne?ko nace kingin rami ko?ya ma kace mun ran nan a asibiti daka ganta"? A tsiwace jahan yace"bansani ba!dallah ni ka tashi motar mu tafi gida," dariya sosae Ayaan yayi yayin da yake tashin motar,ya ja ta suka bar gidan,yana driving yana kumshe dariya abakinshi,jin yarda Jahan ke ta faman buga tsoki,duk yabi ya susuce tunda yayi arba da Amal acikin idanunshi,ya nemi natsuwarshi ya rasa,a haka har suka ƙaraso cikin gidan, wuraren ƙarfe sha biyu,sgr ya fito daga cikin toilet jikinshi sanye da bathrobe,yayin da hannunshi ke ruƙe da guntun towel wanda yake goge Sumar kanshi dashi,agaban dressing mirror ya tsaya yana ƙarasa goge sumar kan nashi,koda ya ɗago da idanunshi da niyyar ya kalli fuskarshi acikin madubin,sae ya dinga ganin fuskar sehrish acikin mirror ɗin amaimakon tashi,lokaci guda ya shiga tariyo duk abunda ya faru jiya atsakaninsu,tun daga lokacin daya je taimakonta,har izuwa lokacin da yaje yi mata allura,tana faman cizon la66anta,hakanan yaji yana marmarin son ganinta acikin idanunshi,tambayoyi ya shiga yi aranshi yana cewa meyasa batazo ta kawo min breakfast ba?ko har yanzu jikin nata ne? Jin takun tafiyar mutun abayanshi yasa shi kai idanunshi wurin ta cikin madubin ya hange ta tsaye duk a tunaninsa yarinyar ce tazo,koda yayi arba da fuskar hayaam sai ya kawar da fuskarshi cike da mamakin wacece wannan?meya kawota bedroom ɗinshi, ƙarasawa ciki hayaam tayi tana tafiya cike da kwarkwasa,wankan atampa ta ɗauka ajikinta,riga da skirt ne,kayan sun matse ta sosai,sun bayyana surar jikinta soaai,musamman saman rigarta boobs ɗinta sun fito waje kamar zasu ciro daga cikin rigar,akwai mayafi a jikinta lokacin da ta fito daga bedroom ɗinta,tana ƙarasowa ɗakin nashi ta cire mayafin tare da ruƙe shi a hannunta don taja hankalin shi,cike da ƙwarin guiwa tazo ɗakin nashi,saboda kwallin data shafa ma idanunta,wanda bokansu ya bata don tayi amfani dashi,ya tabbatar masu da cewa muddin sgr ya sanya idanunshi acikin nata,shikenan sun gama dashi,zai haukace akanta,ya rasa natsuwarshi, Tsayawa tayi daga bayanshi,tare da kashe murya tace"ya kake ranka shi daɗe,ka tashi lafiya," Shiru Sgr yayi bai amsa mata ba,gaba daya lamarin ya gama ɗaure mashi kai,ƙarfin halinta ya bashi mamaki, daƙyar ya iya buɗe baki yace"Ke!wacece ke!what are u doing in my room?yayi maganar batare daya sanya idanunshi acikin nata ba zagayowa hayaam tayi ta gabanshi tamkar zata manna ƙirjinta asaman nasa, Cike da rangwaɗa tace"Zuwa nayi don na gyara maka bedroom ɗinka,tunda ita yarinyar dake kula da part ɗin naka,bata jin ɗaɗi bazata iya yin aikin ba,idan ba damuwa inaso ka bani damar na ci gaba da kula dakai kanka,ina mai tabbatar maka da cewar zaka ji daɗin kasancewa tare dani,saboda ni ina da komai da komai,ba gyara ɗaki kaɗai ba,hatta ɗebe maka kewa zan dinga yi,nasan dole ka buƙaci mace akusa dakae especially da daddare haka. Tashin hankalin da ba'a sa mashi date,yau hayaam tazo yi ma Sgr kwartanci acikin ɗakinshi,ita ga kwararriyar ƴar bariki,tana magana tana ƙara kusanta jikinta da nashi, Just speechless gaba daya ta gama rufe mashi bakinsa,ya rasa abun cewa,shiru kawai yayi yana jira yaga me take ƙokarin yi mashi,daga nan zai san wane irin hukunci ya dace da ita,don ya lura cewa giya tasha,tana bukatar adawo da ita cikin hayyacinta,kuma har lokacin bai kalli cikin idanunta ba,   Wannan shurun da yayi ne yasa hayaam ta fara tunanin cewa kodae ya amince mata ne?shu'umin murmushin nan nata ta shiga saki tana bin surar jikinshi da kallo sae faman haɗiyar yawu takeyi kamar zata lashe shi,aranta tana cewa"dama nasani,muddin yayi arba da sura ta,dole ya kwaɗaitu,yanzun nan zan canza mashi alƙibla,zanja hankalin shi sosai,har nasamu abunda nakeso,   Kafin Sgr yayi wani yunƙuri gaba daya hayaam ta afka mashi tai hugging nashi sosae,tashin hankali saboda tsabar mamakin daya shiga ne yasa bai janyeta Ba,kanshi ya gama ɗaure wa,domin kuwa tunda ya ke arayuwarshi wata ƴa' mace bata ta6a kuskuren ta6a wani sashe na jikinshi ba koda gigin wasa,sae wannan mai rabon shan dukan, ita kuwa hayaam jin bai yi yunkurin yi mata wani abu ba yasa ta fara kokarin tura hannunta cikin Bathrobe din dake a jikinshi don tasan takan yadda zata ida kashe mashi jikinshi,aikuwa a zafafe ya finciko ta,ya ware faffaɗan tafin hannunshi da ƙarfin gaske ya kifa mata mari zazzafan gaske gami da hankadata ta daki dressing mirrorn,agigice hayamm ta fasa wata irin razananniyar ƙara,wani irin jiri ne ya ɗebe ta,nan take ta yanke jiki ta faɗi ƙasa tana birgima,taji ƙamshin mutuwa wlh,ihu ta shiga saki tana fadin Wayyo Allanta,   Adai dai lokacin Sehrish ta shigo part dinshi hannunta ɗauke da tray,na breakfast dinshi data kawo mashi,ganin bashi a parlourn yasa ta nufi bedroom din bakinta dauke da sallama, tana sanya ƙafarta acikin bedroom ɗin,ta jiyo sautin wannan ƙarar da hayaam ta saki,a firgice ta saki tray ɗin hannunta ya faɗi ƙasa kayan abincin suka tarwatse ƙasa,hankali a matuƙar tashe take kallonsu,sautin faɗuwar tray ɗin hannunta ne yasa sgr juyowa karaf idanunshi suka shiga cikin na sehrish,zuba mashi ido tayi tana kallonshi yayin da shima yake kallonta sae faman huci yake yi yarda kasan mayunwacin zaki,da ace sehrish bata faɗo ɗakin nan ba,da ba ƙaramin illata Hayaam zaiyi ba,so yayi ya nakasata,yarda bazata ƙara yin gigin takowa tazo bedroom ɗinshi balle har tayi yunƙuri ta6a wani sashe na jikinshi ba,   atsorace sehrish ta mayar da idanunta kan Hayaam dake a baje ƙasa,magashiyyan sae faman Birgima takeyi har lokacin bata dawo cikin hayyacinta ba,wato taji tafin hannun maza,dama zafin hannu gare shi,shiyasa bai cika son yakai bugu ba,saboda za'a iya samun matsala,da mari kaɗae zai iya sumar da mutun, A zafafe Sgr ya juya ya tunkari hayaam dake baje kasa,da alama yau fa hayaam sai dai buzun ta,ganin hakan yasa hayaam da kyar ta rinka jan jiki tana ja baya gami da yi masa magiyar yayi hkr kar ya kasheta hannunta guda dafe da kuncin,gaba daya sautin jin kunanta ya ɗauke ɗuff ta 6arin da daya mare ta,cikin husky voice yace"who the hell are u? da sauri cikin shesshekar kuka la66anta na kerma tace"ni...ni..ƙanwarku ce....au ƙanwar matar yayyen kuce ishaq da abbas" tsayawa Sgr yayi lokaci guda ya gane itace yarinyar da tazo rannan har aka faɗa masa"to waye ya shigo da ita gidan? Ya jefa ma kansa tambaya, Ganin abunda ke faruwa yasa Sehrish ja da baya zata watsa aguje saboda tsoran kar itama laifin da hayaam ta aikata ya shafe ta,   da wata irin murya taji yace"ke!zonan,"   Jiki na rawa sehrish ta shigo cikin ɗakin nashi,sae faman kerma take yi kamar yace zai buge ta,   ƙarasawa kusa dashi tayi tana faman zazzare idanu hankali atashe take kallonshi,tana jiran jin me zaice mata,   daidaita natsuwarshi yayi tare da sassauto da muryarshi calmly yace"ya jikin naki!'?   Tsananin mamaki ne ya kama sehrish,jin abunda yace mata,kuma da irin muryar da yayi mata maganar,hakan yasa taji hankalinta ya kwanta,   muryarta na rawa tace"naji sauƙi sosai,yanzu bana jin ciwo atare dani," Jinjina kanshi yayi kafin ya kuma cewa"Okey,Allah ya ƙara lfy,' "Ameen,"ta amsa mashi, shiru suka ɗanyi na wani lokaci,kafin ya mayar da idonshi kan hayaam dake ta faman yi mashi tsuwa acikin dakinshi duk ta cika masu kunnuwansu,   A fusace yace"get out from my bedroom!'   Jiki na rawa hayaam ta miƙe da gudu zata fuce a tsawace sgr ya tsaidata ta hanyar cewa" hey! juyowa tayi har lokacin hannunta na akan kumatunta ya cigaba da cewa "make sure u pack all ur shit and leave this house! A kausashe yayi maganar, idasa fucewa daga cikin ɗakin tayi tana cigaba da shar6ar kukan nata, Lumshe idanunshi yayi tare da buɗesu akan fuskar sehrish da tai tsuru² jin ance hayaam ta tattara kayanta ta bar gidan, yace"yanzu ya za'ae da breakfast ɗina da kika zubar mun a ƙasa?   cikin sauri tace"bari naje na haɗo maka wani" juyawa tayi da niyyar ta tafi,kwatsam taji ya ruƙo hannunta acikin nashi,a ɗan tsorace ta juyo tana kallonshi,gabanta ne taji yana faɗuwa ganin yarda Sgr yake kallonta,nan fa ta shiga taitayinta,   "Meyasa jiya,baki dawo gida ba?ko saboda na datse maki gashin kanki ne"?    Girgiza kai sehrish tashiga yi tana cewa"a'a ba haka bane,bani da lafiya ne,bacci ya ɗauke ni a school bansamu wanda ya tashe ni ba lokacin da aka tashi har junaid yazo dauka na bai ganni ba,shiyasa bansamu nadawo gida ba,'   Kallon bakinta dake bayanin kawae yake har ta gama,a hankali ya furta Okey,sannan ya saki hannunta daga ruƙon da yayi mashi,   juyawa tayi da sauri ta ƙarasa bakin kopar dakin nashi,zukunnawa tayi ta kwashe kayan abincin data zubar mashi aƙasa,duka ta tattara su acikin tray din,sannan ta fuce daga ɗakin nashi, Gaba daya ta rasa natsuwarta,wani irin yanayi ta dinga ji atare da ita,kallon nan da yake yi mata ba ƙaramin kashe mata jiki yakeyi ba,kamar wadda aka cire ma lakar jikinta haka ta dinga jin kasala, A kitchen ta samu azmee tana wanke kayan abincin da sukayi amfani dashi na breakfast,   Ganin ta ɗauke da tray a hannunta yasa azmee cewa"Har ya kammala yin breakfast ɗinne"?   girgiza kai tayi alamar a'a tace"matsala aka samu,ni ce na 6arar da kayan abincin,shine yace na sake kawo mashi wani,'   Azmee tace"wasa wasa sehrish kema kin iya shiririta wlh,kina sake da baki har kika zubar mashi da kayan abincin ko?   "Ae bada sanina,hakan ya faru ba,"ta yi maganar yayin da take ƙarasawa cikin kitchen ɗin,   "Shikenan bari na sake haɗa maki wani breakfast din ki kai mashi,Amma kada ki jima a part din nashi fa,da zarar na kammala gyara kitchen din,zanyi maki ƙunshin,ko baki so ne'?   "Inaso mana,"tayi maganar fuskarta ɗauke da murmushi,   Batare da 6ata lokaci ba,Azmee ta kammala shirya mata wani kayan abincin acikin tray,ta bata takai mashi,sae da ta ja mata kunne akan karta kuskura ta ƙara zubarwa,'   fitowa daga cikin kitchen din sehrish tayi,fuskar nan ɗauke da annuri,wani irin daɗi takeji aranta,kamar anyi mata albishir da gidan aljana,   A hankali take taka stairs din,yayin da Zuciyarta ke tariyo mata abunda ya faru aɗakin sgr,batasan meya faru tsakaninshi da hayaam ba,da har ya kwashe ta da mari,amma koma meye dae tana da tabbacin cewa wani abu tayi mashi ba dae dae ba,   Ta6e baki tayi tana cewa"to ni ina ruwana?meye damuwata da ita?koma meye ita taja ma kanta,nasan cewa babban yaya bazai ta6a ɗaga hannu ya mari mace ba hakanan batare da wani dalilin ba,na yarda dashi sosai,kuma baiyi mun kama da irin mazan dake dukan mace ba,Yau dae hayaam take kowa ma,tasha mari wlh ko a ha6ar zani na,ba ƙaramin daɗi naji ba wlh,babban yaya ya burgeni sosai daya kwashe ta da mari,gobe ma in halinta ne ta ƙara yi mun shisshigi a aikina,angaya mata cewa sauƙi ne kula da babban yaya?nikaina kullum cikin fargabar kada nayi mashi kuskure nake,shiyasa nake lalla6ashi kamar kwai acikin cokali,Allah sarki yau hajia hayaam taji tafin hannun babban yaya koya raɗaɗin yake?tabb dole ma akwae mugun radadi tunda ta kasa cire hannu daga kan kuncinta, gwara ni Almakashi yasa ya datse mun gashin kaina,nan da wani lokaci gashin zai fito,ita kuwa marinta fa yayi? nasan har abada bazata manta da wannan ranar ba, ashema hakanan take ma mutane kankanba ko sanin wacece ita bai yi ba" Dariya sosai sehrish takeyi kamar wata zautacciya,sae faman sambatu takeyi,da alama taji daɗin Marin da Sgr yayi ma Hayaam,abun ko ajikinta,   Lokacin da ta shiga part ɗin Sgr,a kishingiɗe ta same shi saman doguwar kujera,ya miƙe kafafunshi,bai kaiga shiryawa ba,Vest ce kawai ajikinshi sae shorts farare,   Karasawa ciki tayi tare da ajiye mashi tray din asaman table,sannan tace"ga wani breakfast ɗin na kawo maka,"   sauko da ƙafafunshi yayi ƙasa ya miƙe daga zaune,ya jingina bayanshi a jikin sofan yana jira tayi serving ɗinshi,   Sehrish ta jima awurin sgr tana mashi ɗawainiya har sai da ya kammala yin break fast din nashi,sannan ta koma ta gyara bedroom ɗinshi,bayan ta gama ta dawo ta gyara falon sannan ta ɗauko kayan abincin da yayi amfani dasu,ta wuce dasu kitchen,sae da ta wanke komai ta mayar dashi a ma'ajiyar shi,sannan ta wuce ɗakin azmee don suyi maganar zanen lallen da zatayi mata, Wuraren ƙarfe biyu na rana,Junaid ya kar6o mata kayanta,akwati guda ne na atampha da lace,da kuma shadda,hada materials,duk an ɗinka mata su, acikin bedroom ɗinta ya ajiye mata akwatin kayan, sae da suka kammala sallar azhar,tukunna suka zauna zaman yin ƙunshi,anan corridor din ɗakunan nasu azmee tayi masu shimfiɗa suka zauna sama,tunda suka fara ƙunshin junaid keta zarya awurin sae faman santin kunshin sehrish yake yi,tun kafin a wanke mata ƙunshin ma,cikin nishaɗi suke yin firar su,tana yi mata ƙunshin suna fira tare da junaid,don ya kasa ya tsare sae anyi tare dashi, A6angaren Hayaam kuwa tunda ta faɗa cikin bedroom ɗinta saman gado,take ta faman shessheƙar kuka,fuskarta tayi jawur saboda kukan da tasha,gefen fuskarta dauke da sahun yatsun sgr ruɗu ruɗu sun fito wurin ya kumbura sosai gashi kunnanta daya dumm take jin shi,tunda take arayuwarta wani ɗa namiji bai ta6a gigin ta6a lafiyar jikinta ba,sae akan Sgr ta fara shan mari,ta jima tana mamakin yarda ya ɗaga hannu ya kwasa mata mari,duk irin yarda ta ɗau wanka,ta bayyana surar jikinta don taja hankalinshi amma hakan baiyi tasiri akanshi ba,kwallin data shafa kuma ya tashi abanza saboda bai kalli cikin idonta ba bare asirin ya kamashi,   ɗagowa tayi daƙyar take iya buɗe idanunta,wayarta ta ɗauko dake ajiye saman side drawer na gadonta,layin Aunty babba ta kira,wayar ta shiga ringing, Cikin sa'a ta ɗaga kiran,Aunty babba nayin sallama,hayaam ta 6are baki ta fashe da wani sabon kukan,   Tunda Aunty laila taji kukan hayaam hankalinta yayi mugun tashi,daga zaune take saman kujera amma tana jin kukan hayaam ta miƙe tsaye tana tambayar lafiya!   Cikin shessheƙar kuka hayaam tace"Aunty lailai,yau Sgr ya gama dani,ya wulakantani kuma ya tozarta ni,yayi mun abunda wani ɗa namiji bai ta6a yi mun ba!'   Hankali tashe Aunty babba tace"Me yayi maki ne!kiyi mun bayani yarda zangane,kuma kidaina wannan kukan da kikeyi,"   dakatawa da yin kukan hayaam tayi sannan taci gaba da magana tana cewa"Mari na fa yayi,banyi mashi komai ba ya ɗaga hannu ya kwasa mun mari agaban waccen ƙaskantacciyar yarinyar ya mare ni....'   Tunkan ta ƙarasa maganar Aunty babba tace"Ƙarya kike hayaam!Sgr bazai ta6a marinki ba batare da kinyi mashi laifi ba!dole akwai dalilin dabyasa ya mare ki,don nasan halinki baki da hankali,kuma baki da kamun kai,halan ƙoƙarin kai mashi hari kikayi saboda gajen hkr!!"   Cikin en ena hayaam tace"nifa banyi mashi komai ba,kawai da safe ne nashiga ɗakin shi lokacin ya fito daga wanka,nayi ƙoƙarin jan hankalinshi ne da surar jikina,amma ko kallo ban ishe shi ba,shine nayi hugging nasa nayi ƙoƙarin ta6a short ɗin jikinshi don in tayar mashi da sha'awar shi,amma shine kawai ya kwashe ni da wani mahaukacin mari.....'   dafe kai Aunty babba tayi tana cewa"ka ji tsiyar!wlh kin ban kunya hayaam!bansan ke wata irin mace bace!sam baki da kamun kai,idan jarabarki ta motsa, me yasa bazaki iya control din kanki bane agabanshi!wannan mutumin fa da kaina nayi maki alƙwarin cewa mijinki ne shi,idan kikayi haƙuri nan da ɗan wani lokaci zaki mallake shi duka,sae kiyi yarda kika ga dama dashi,amma tun yanzu saboda gajan haƙuri irin naki kin gaza jurewa,kina ƙokarin lalata mun shiri na!bazaki ta6a burge Sgr ba,saboda shi irin mazan nan ne da basa ra'ayin mace mara kamun kai ballagaza,wadda bata iya 6oye zalamarta akansu......' Ɗaure fuska hayaam tayi jin yarda Aunty babba ke ta zaginta a fakaice, Rai a6ace tace"Aunty laila nifa ban kiraki don kici mun mutunci ba,sae faman gaya mun magana kikeyi ta inda kike shiga bata nan kike fita ba,ni da na kawo maki kukana maimakon ki share mun hawaye na,Amma shine kike ta zazzaga mun masifa!wannan abun fa ba laifina bane,ko kece kika ganshi a yanayin dana same shi dole ki kai mashi attack balle ni da nake budurwa........'   Waro ido waje Aunty babba tayi rae a6ace tace"Hayaam don ubanki ni kike gayama wannan maganar!ashe ke daƙiƙiyace baki da hankali!an gaya maki ko wace mace irin ki ce mara aji da zata dinga kai kanta wurin namiji har tana ƙokarin ta6a jikinshi!ni tunda nake arayuwata ban ta6a kusantar mijin da banawa ba,duk irin mugun halin da nake dashi kuwa,a iya miji na natsaya ban zarce nan ba!amma ke fa?kullum kina yawon biɗiɗi wurin raba jikinki ga kowane ƙazamin namiji yayi amfani dake,don ki samu kuɗi,ki faɗamun wace riba kika ta6a samu a yawon barikancin naki!acikin mazan da kikayi mu'amala dasu akwai shegen daya ta6a cewa zai aure ki ne!!saboda baki da wani amfani awurinsu,tamkar totuwar masara kike da zarar sun cinye masarar jikinshi ya gama amfani sae su jefar dashi ƙasa,ni kuwa kinga ina da daraja tunda ina da aure kuma a ƙarkashin kulawar mijina nake,shiyake amfani dani kuma shi yake bani kuɗin da zanyi abunda nake so,riba biyu ga kuma lada ina samu......'   Wani irin huci hayaam ta shiga fitarwa saboda tsabar 6acin ran kalaman da Aunty babba ta gaggaya mata, Muryarta har shaƙewa takeyi wurin cewa"Aunty Laila!!ni kike faɗama waɗannan munanan kalaman!yau da kanki kike yi mun gori?Ya salam!wlh bazan ƙyale ki ba,kamar yarda kikayi mun gorin aure,nima zan raba auran ki Da Ishaq,ki dawo bazawara," fashewa da dariya Aunty babba tayi tana girgiza kai kafin tace"ni zan aje waya,kada ki manta kisha maganinki na rana,don da alama kin manta jawabin da likitan mahaukatan nan yayi maki,akan kula da shan magungunan ki akai akai,"ta ƙarasa maganar tare da kashe wayar,   Wani irin ihu hayaam ta zabga tare da aza hannunta saman kanta,tana fadin innalillahi wa'inna ilaihirraji'un...." Zafi biyu,gana marin da Sgr yayi mata ga kuma na zafafan kalaman da Aunty babba ta gaggaya mata,zuciyarta tamkar ana rura mata garwashin wuta haka ta dinga ji,wani irin zazza6i ne ya lullu6eta,nan ta baje saman gadon tana ta faman birgima a ranta tana cin alwashin ba zata bar gidan ba har sai taga bayan Sehrish don ita taja mata duk wadannan abubuwan da suka faru da ita.          warah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari*, Wuraren ƙarfe 4:30 gaba ɗaya matasan gidan sun hallara a baban falon gidan wanda yasha decorations abun ba'a magana,yayi kyau over tamkar wani babban hall na taro,an ƙawata shi sosai hada wasu kujerun aka ƙaro,an tsara komai na wurin anyi table arrangements,kowane table yana zagaye da Kujeru guda uku uku wadanda ke dauke da seat cover haka ma tables din,a jere Ayaan da Jahan irfan da khaleed da kuma jabeer da fawan,suka shigo main palour ɗin kowannansu ya ɗau wankan tsadaddiyar shadda ajikinshi,bayansu sae kanal yousouf shima ya fito cikin nashi wankan,ba ƙaramin ƙyau sukayi ba,sai hotuna suke ɗauka da wayoyinsu,kafin camera man ɗinsu wato junaid ya kammala shirin nashi ya fito ya ɗauke su hotuna,dama shine maiyi masu hoto duk in suka shirya walima irin haka,acikin gida, Lokacin da Abbansu ya fito jikinshi sanye da shadda fara taji aiki ajikinta,koda sukayi arba dashi da sauri suka ƙaraso wurinshi suna yaba wankan daya ɗauka,   "Abba harka fi mu yin kyau wlh,gaskiya bamu yarda ba Abba,'   Dariya sosai Abban nasu yayi yana kallonsu one by one,wani irin farin cikine ya lullu6e shi ganin ƴa'ƴan nashi gaba ɗayansu agabanshi,duk da ba wasu acikinsu,amma yasan duk zasu hallara ne suna ciki suna shiryawa,   "Abba,bari mu fara ɗaukar hoton tare dakai kafin Baby junaid ya ƙaraso,"   fawan ne yayi maganar yana kanga wayarshi saitin fuskar Abban nasu, dakatar dasu Abba yayi yana tambayar ina Abusufyan yake ne?bai fito bane? Kanal yousouf yace"naje bedroom ɗinshi lokacin yana acikin toilet ɗinshi,amma ina da tabbacin zuwa yanzu ya kammala wankan ƙila ma harya shirya shima,"   Jinjina kai abban nasu yayi tare da cewa"Gaskiya sae dae kuyi haƙuri to,babu wanda zanyi hoto dashi har sae naga ɗan uwana akusa dani,dashi nake son na fara ɗaukar hoton nan,don haka ku jirani yanzun nan zamu fito tare,"   Bashi wuri sukayi ya wuce ɗakin Abusufyan,tura ƙopar yayi yasa kai ya shiga ciki,a lokacin Abusufyan yana tsaye gaban dressing mirror yana maƙala links ɗin hannun rigar shaddar daya sanya,madarar kyau,gezner ce ajikinshi green colour,sae faman salƙi takeyi,yayi kyau Over,ta cikin madubi ya hangi shigowar yayan nashi,   Ƙayataccen Murmushi ya saki tare da cewa"Yaya hossein,yanzu nake shirin fitowa nima,wlh bacci ne ya ɗan dauke ni bayan mun dawo daga sallar la'asar,shiyasa na makara ban kimtsa da wuri ba,"   Ƙarasawa ciki Abba yayi yana cewa"tun ɗazu nake ta baza idanu inga 6ullowarka,amma bangani ba,shine nace bari ni nazo da kaina na janyoka mu fita tare,don na sanar dasu cewar babu wanda zan ɗauki hoto dashi har sai naga ɗan uwana mun fara yi dashi ,'   juyowa Abusufyan yayi a lokacin ya kammala sanya links ɗin ya kalli abba yace"yaya hossein bansan da wasu kalmomi zan iya bayyana maka irin farin cikin da nake ciki ba,wlh sai yanzu nake danasanin yin nesa da ƴan uwana,domin kuwa babu abunda yafi kasancewa tare da ahali daɗi aduniyar nan,' Abba yace"ae bazan ƙara yin gangancin barinka kabar ƙasar nan ba,wancen lokacin ma satar hanya kayi ka gudu batare da saninmu ba,amma wannan karon zan sanya tsaro sosai akanka,ko nan da bakin gate zaka je sai da izinina,zan sanya security guards ɗin da zasu dinga bibiyarka a 6oye," Dariya sosai Abusufyan yayi kafin ya tsagaita da yin dariyar yace"Ya hossein nima bazan ƙara maimaita kuskuren da nayi ba,na tafiya nabarku,nasan ban kyauta ba,wlh naji ba daɗi sosai lokacin da junaid ya ƙankame ni yana murnar zuwana hada hawayenshi,sae naji wani iri araina,na tafi na barshi yana ƙarami bai mallaki hankalinshi ba,amma yanzu dana dawo na same shi ya girma sosai,a waya ne kawai nake jin muryarshi,iya wannan shaƙuwar da mukayi ta waya itace tasa ya ruƙe ni sosai aranshi,insha Allah bazan ƙara tafiya nabarku ba,nayi alkawarin hakan," Ba ƙaramin farin ciki Abba yayi ba,da jin kalaman ɗan uwan nashi,ruƙo hannunshi yayi acikin nashi tare da janyo shi suka fito daga cikin bedroom din, Kamar jira suke Abban nasu ya fito tare da uncle Abusufyan da sauri suka nufesu fuskar kowannansu ɗauke da farin ciki mara misaltuwa,nan fa suka shiga ɗaukar hotuna, 💋Boss Bature💋 Tabarakallahu ahsanul khaliqin!Azmee ce ta ambaci hakan yayin da take kallon sehrish dake tsaye,sanye cikin tsadadden cord lace red colour yasha adon duwatsu ajikinshi,riga ce har guiwa sae zani,azmee da kanta ta ɗaura mata ɗankwalin golden colour tamkar gwargwaro haka ta ɗaure mata shi a kanta,fuskar nan tasha make-up ɗan light ba over ba,ta gyara jagirar idanunta duk da ta ƙara zana ta da eye pencil brown colour,ta ko'ina kwalliyar ta fiddo mata da zunzurutun kyawun fuskarta,hancin nan yayi tsayi,ga bakin nan nata yasha jan janbaki,yadda kasan wadda zata gasar sarauniyar duniya haka ta fito ɗass da ita,wasu matsiyatan takalma ƴan ubansu azmee ta ɗauko mata daga cikin shoe rack dinta,ankle strap masu tsinin gaske golden colour ne suma,launin head dinta,wayyo Allah bournvitar kyau just imagine it, Wuyanta na sanye da ziririyar sarka golden colour,haka earrings dinta,da kuma rings ɗin da ta zura a hannunta duk launi ɗaya ne, Kai jama'a!,ga zanen fulawar da azmee tayi mata a hannunta na jan lalle,yayi mata kyau sosai hannun nata kamar a lashe don kyau, "Juya a hankali ki kalli madubi,"Azmee ce tayi mata maganar tana faman sakar mata murmushi, Ajiyar zuciya sehrish ta sauke tare da juyawa awani slow ta kalli kanta acikin mirror ɗin, Gabanta ne taji yayi wani irin bugu lokaci guda,zuba ma kanta ido tayi tana kokwonton Anya itace kuwa!? Yarfa hannu tashiga yi aruɗe take cewa"Aunty azmee wai dagaske ni ce!dama haka nake da kyau kamar macen aljanna! Am just speechless oh my God!! 🤣😂 Maganar sehrish ba ƙaramin dariya taba Aunty azmee ba,kama hanyar fita tayi daga cikin ɗakin tana cewa"Bari naje na fara jera abincin a falo,pls kada ki fito yanzu sai nan da 15 mins nake son ki fito saboda inason inga reaction ɗin matansan gidan idan sukayi arba dake,"tana kai ƙarshen maganar ta fuce, Ƙayataccen murmushi sehrish ta sakar ma kanta tana kallon kyakkyawar fuskarta acikin madubin,lokaci guda Sgr ya faɗo mata acikin ranta,lumshe idanunta tayi tare da buɗesu a hankali tana ƙara bin jikinta da kallo, Sae ta dinga jin kanta tamkar amarya a wannan lokacin,amaryar kuma ta Sgr, "Ya Allah ka nuna min wannan ranar da nake ta mafarkin zuwanta,ranar da zan kasance mallakinshi,shi ma kuma ya kasance mallakina,a wannan ranar nayi ma kaina alkawarin cewa ko bacci ba zanyi ba,zan kwana ina sallar dare,ina miƙa godiya ta ga Allah daya cikamin burina,a washe garin ranar kuma zan tashi da azumi,' ta ƙarasa zancen zucin nata tare da samun wuri saman kujerar gaban madubin ta zauna, Gaba daya duk sun zazzauna saman kujerun yayin da table din ke shaqe da kayan ciye ciye iri²,Abusufyan tare da Abban nasu sae junaid suna a zaune wuri daya,Ayaan da jahan da kuma fawan suna zaune suma a wuri daya suna cin abincinsu,Irfan da jabeer sae khaleed suma suna zaune a table daya, Kanal yousouf ne ya buɗe masu taron da addu'o'i,kafin su fara kulu washarabu hani'an,sunyi haje haje da naman kaji,farfesu iri iri da sauran kayan maƙwalashe, ,kowa ya mayar da hankalinshi akan abincin dake gabanshi,   "Wai ni ina Rafayet da Omar ne?naga kowa amma bandasu,"Abusufyan ne yayi ma Abba maganar a yayin da yake ɗaukar cup na lemu,yakai bakinshi yana kur6a,   "Ina tunanin suna ciki suna shiryawa,kasan su fa manya ne nasu wankan ba irin namu bane,nasan shiyasa suka jima aciki basu fito ba,"a cewar abbansu, "Naga alama,amma ni ko ina so na tambayeka yaya,wai har yanzu Sgr da Omar basu fara soyayya bane "?yayi tambayar yana kallonshi,   Murmushi Abba ya ɗanyi kafin yace"Omar dae ya sanar dani cewa akwai yarinyar da yake so,kuma ashirye yake daya aureta,amma shi rafayet har yanzu fa babu wani sauyi yana nan yadda kasan shi,amma kwanan nan na fuskanci kamar akwai wani abu atsakaninshi da yarinyar gidan nan,wadda na faɗa maka cewa tana taya Azmee aiki,kamar akwai soyayya atsakaninsu,duk da dae bani da tabbacin hakan,"   tunda suka soma magana junaid baisan me suke tattaunawa ba,saboda hankalinshi na can wurin tunanin abu biyu,rishi ɗinsa da kuma zuwan mommynsu a takure yake,gaba ɗaya ya gaza samun natsuwa saboda ya kwallafa rae akan zuwan nata, Abusufyan yace"yanzu me ka yanke shawara agame dasu ne?zaka tunkari Sgr da maganar yarinyar ne ko kuwa"? "A'a,bana tunanin cewa zai amince cewa yana sonta harma ya yarda ayi auren kasan halin shi,yanzu dai akwai wani shiri da nakeyi dama zuwanka kawai nake jira,nan da sati mai zuwa zan sanar dakai insha Allah," Murmushi Abusufyan yayi tare da cewa"Allah ya kaimu lafiya," Abba ya amsa mashi da Ameeen, Juyawa abbansu yayi tare da kallon junaid ya ambaci sunanshi,   Firgit junaid yayi tare da aza idanunshi kan abban nasu yace"Abbana," ..murmushi sukayi gaba ɗayansu,Uncle abusufyan yace"junaid kodae ka fara soyayya ne?tun ɗazu muke magana amma hankalinka na'a wani wuri,"   Murmushi ya ɗanyi tare da sunnar da kanshi ƙasa yana kallon plate dake ajiye gabanshi shaƙe da Chips,tun da Azmee ta zuba mashi bai ko ta6a shi ba,   "Junaid naji kayi shiru kodae dagaske ne abunda Uncle ɗinku yace ka fara soyayya"?Abbansu ne yayi maganar cike da zolaya yana kallonshi,   Duk kunya tabi ta kama junaid,ba wai abban nasu yake ji ma kunya ba,uncle ɗinsu yake ji ma kunya,don ta Abbansu har zancen aure suna yi dashi in wasan nasu ya motsa,   yana ƙoƙarin buɗe baki yayi magana,wayar shi ta shiga ringing,jikinshi na rawa ya zura hannunshi a aljihu ya curo wayar yana duba sunan mai kiran nashi,private number ya gani wato anyi hidden ɗin numbar,kallon abbansu yayi tare da cewa"Abba zan amsa waya," amsa amshi yayi da cewa"okey,amma kada ka jima,muna jiranka,don bamu gama hotunan ba,"   Murmushi ya saki tare da miƙewa yabar wurin,sae da yayi nesa dasu sannan ya ɗaga kiran tare da kara wayar a kunnanshi yana jiran jin wanene ke kiran nashi,   Wata sanyayyar murya yaji ta karaɗe kunnan shi da cewa"babyn abbanshi kana ina ne"?   Tunani ya shiga yi kodae mommynshi ce don haka yace"ina a gida ne,"   Matar tace"Idan ba damuwa kazo Airport kadauke ni,na ƙaraso Nigeria amma banaso kowa yasan da maganar,kai kadae kawai nakeso kazo ɗaukana,Kada ka bari kowa ya biyo ka"   da ƙarfi junaid ya ambaci sunan mommy fuskar nan tashi cike da farin ciki yace"mommy am coming right away"   Matar tace"okey,idan ka fito daga cikin gidan ka sanar mun,"   Cike da zumuɗi ya amsa mata da toh,sannan jiki na rawa ya katse kiran tare da zura wayar a aljihun shi,   Gaba ɗaya ya gaza rufe bakinshi saboda tsabar farin ciki,juyawa yayi yana kallon ƴan uwanshi dake zazzaune kowannansu fuskarshi ɗauke da farin ciki,aranshi yace"kodai na sanar masu cewa mommy ta ƙaraso?kuma dae tace kar na faɗama kowa,gaskiya bazan faɗa masu ba,zan basu mamaki ne nasan in suka ga mommy zasu yi murna sosai,amma kuma inason na sanya rishi a idanuna kafin nabar gidan nan,bari nayi sauri naje naga wankanta na yau,   Yayi maganar tare da nufar corridorn ɗakinsu sehrish da sauri da sauri ya ƙarasa kopar bedroom ɗin nata,   A lokacin tana acikin bedroom din nata sae faman zagaye takeyi,tarasa ya zatayi ta fita,kunya take ji su ganta da kwalliyar jikinta, Jin kwankwasa ƙopar ɗakin nata yasa ta cewa"wanene," daga waje junaid ya amsa mata da cewa"Mijinki ne insha Allah,"   Murmushi ta saki tare da cewa"ka samu iznin shigowa ciki,daga matarka insha Allah,"   tura ƙopar yayi tare da sanya ƙafa ya shiga cikin ɗakin,koda yayi arba da sehrish nan take yaji gabanshi ya faɗi,kokwonto ya shiga yi yana tambayar kanshi Anya wannan sehrish ce kuwa?   matsawa kusa dashi tayi tace"meya faru junaid naga ka toge anan?   "Reesh,kinyi kyau Over,"cikin sanyin murya yayi maganar,don ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,   Ƙayataccen murmushi ta sakar mashi tare da cewa"saboda kai nayi wannan kwalliyar,launin lips dinka red colour ne,shiyasa nima na sanya jan lace don inyi anko da kai,to ya kaga wankan"? tayi maganar tare da jujjuya mashi bayanta don ya kalla da kyau,aikuwa ba ƙaramin ruɗashi tayi ba,gaba daya yabi ya susuce, Kamar yakai mata runguma haka yaje ji,amma ba halin yin hakan jikin shi sae faman kerma ya keyi, juyawa tayi tare da nufar bedside drawer dinta,ta ɗauko wayarta tare da dawowa saitinshi ta ɗaga wayar tare da cewa"ka shirya in ɗauka?'tayi maganar tana jiran jin amsarshi, Jin hannunshi ta gefen waist dinta yasa ta ɗan razana kaɗan,sosai ya ruƙo qugunta tare da kwantar da kanshi saman kafaɗarta yace"ki ɗauka," Zuba mashi ido tayi ta cikin camera ɗin tana kallon fuskarshi,hakanan ta dinga jin zuciyarta nayi mata wani irin bugu,muryarta akasalance tace"junaid ka buɗe idanunka,taya zan ɗauka dakai ido a rufe"? Murmushi yayi tare da buɗe idanunshi yana cewa"Reesh,ƙamshin turaran nan naki,kashe mun jiki na yake yi,ba kiji yarda nake ji ba,don Allah reesh,kada ki guje ni kinji"? Martanin murmushin ta mayar mashi sannan tace"junaid banda hankaline da zan guje ka?angaya maka kai irin mazan da ake gudu ne?kai fa na musamman ne junaid,tun farkon ranar dana fara zuwa aiki gidan nan,dakai nafara cin karo,a lokacin da nayi arba da wannan kyakkyawar fuskar taka mai ɗauke da wannan tsadadden murmushin,lokaci guda na rasa samun natsuwa,kasan Allah junaid da ace siyar da wannan murmushin naka kakeyi da ba ƙaramin ciniki zakayi ba Allah," Fashewa da dariya junaid yayi saboda jin kalaman sehrish akanshi,ba ƙaramin hura mashi kai tayi ba,kuma ta samar da farin ciki acikin zuciyarshi, ɗaukar hoton sehrish ta shiga yi,style iri iri suka shiga yi ita da junaid,hada wanda ya manna mata kiss a gefen fuskarta,da kuma wanda ta lotsa yatsanta acikin dimple dinshi,hotunan sunyi kyau sosai, Sae da suka kammala hoton sannan ta lura da zoben diamond ɗin dake hannunshi,sae faman ƙyalli yake yi, Waro ido waje tayi alamar mamaki tace"wow junaid wannan fa,waya siya maka shi!" "Mommy azeema ce ta bani shi,dama ɗazu na sanar dake cewa zan nuna maki gift din da takawo mun,to itace wannan,' Ya ƙarasa maganar yana nuna mata zoben da Wrist watch din, "Junaid sunyi kyau wlh,musamman daya kasance kaine ka sanyasu," "Thank u reesh,sunyi mun kyau amman idan ke kika sanyasu sae sun fi yi maki kyau,bari na ciro maki su ki sanya,nafison su kasance a hannunki," cikin sauri tace mashi"no junaid that's impossible,Auntynku azeema ce ta baka shi,muddin ta neme shi a hannunka bata ganshi ba zata nemi jin ba'asin inda ka kai su,kuma ma in banda abun ka junaid wannan ae irin naku ne!kamar diamond ne fa,nida ko zoben azurfa ban ta6a sanyawa a hannu ba,balle diamond! Kafin ya buɗe baki ya bata amsa wayarshi ta shiga ruri,nan take ya tuna da abunda mommynshi ta sanar mashi na cewa ta ƙaraso nigeria tana a Airport yaje ya ɗaukota, Jiki na rawa yayi ma sehrish sallama tare da fucewa daga cikin bedroom ɗin, Junaid bai sanar ma kowa ba,ya shige motarshi tare da janta yabar gidan gaba ɗaya,ya miƙi hanyar zuwa airport din cike da zumuɗin son ganin Mommyn tashi. 💋Boss Bature💋 A hankali sehrish ta sanya kafarta tare da fitowa daga cikin bedroom ɗin nata,a natse take tafiya yayin da takalman kafarta ke bada sauti kwas,kwas duk in ta takasu ƙasa,cike da fargaba ta tunkari babban falon gidan, Jin takun takalmanta ne yasa matasan dake zaune acikin falon dawo da hankalinsu akanta,koda su kayi arba da sehrish,lokaci guda sukayi tsit yarda kasan mutuwa ta gifta,babu mai magana acikinsu ba don komai ba,sae don kallon da suka bita dashi, Abbansu ne yayi ƙoƙarin cewa"Masha Allah my daughter,irin wannan kyau haka kamar sarauniyar kyawun duniya"?yayi maganar fuskarshi ɗauke da murmushi, Ita ma murmushin ta shiga sakar mashi tare da ƙarasawa wurin table dinsu don ta gaishe dashi,a lokacin Abusufyan yabar wurin saboda kiran wayar da akayi mashi,yaje ya amsa kiran ne, "Ina yini Abba," Lafiya lou daughter,tun ɗazu nake jiran fitowarki amma ban ganki ba,har azmee na tambaya ta sanar dani cewa kina nan zuwa, Ya ƙarasa maganar tare da cewa"kinyi kyau sosai,da ace ƴa'ƴana zasu bari dana yi ta biyu dake......'yayi maganar cike da zolaya yana satar kallonsu fawan da suka ƙure ta da ido suna kallonta,koda suka ji abunda Abban nasu yace nan take suka ɗaure mashi fuska alamar basu son zancen,hakan ba ƙaramin dariya ya bashi ba, Sehrish kuwa sunnar dakai ƙasa tayi tana wasa da yatsun hannunta cike da jin kunyar Abban nasu, "Have a seat my daughter,"yayi maganar tare da nuna mata empty chair din da junaid ya bari, Janyo kujerar tayi ta zauna har lokacin ta gaza sakin jikinta, Muryar fawan ta jiyo yana cewa"Sister idan an kammala,zamu yi pic atare," Jahan yace"tunda tayi kwalliya ae dole ka nemi yin hoto da ita,mayen mata kawai,waccen dae tafi ƙarfinka Allah,ko kallonta ka cika yi sai Abban mu ya tuhume ka,don na lura da yadda yake ji da ita kamar mommynmu ce ta haife ta," . Dariya su kayi gaba dayansu, Fawan yace"wai ni ina wannan tsinken sigarin take? Atare suka haɗa baki wurin cewa"wa kenan"? Irfan dake zaune a next table ɗin da ke akusa da nasu yace"yana magana ne akan wannan ƴar moli-molin da ke yawo acikin gidan nan," Kamar zautattu haka suka fashe da dariya,har sae da Abbansu ya tambayesu ko lafiya,suka ce mashi babu komai,nishadi kawai sukeyi, adaidai wannan lokacin Abusufyan ya dawo wurin da suke,da alama ya kammala wayar da yake yi,wuri ya samu ya zauna yana fuskantar sehrish,daga ita har shi ba wanda ya lura da wani, Gyaran muryar da Abba yayi mashi ne yasa shi ɗagowa yana kallonshi yace"meya faru ne yaya"? Da ido yayi mashi nuni da sehrish yace"baka ganta bane," A hankali Abusufyan ya mayar da idanunshi kan sehrish dake zaune tana faman wasa da yatsun hannunta,gabansa ne yayi wani irin mugun bugu ji kake daram!!!a gigice ya miƙe tsaye hankali tashe yake kallonta, Miƙewa Abba yayi yana kallonshi ganin yarda ya tsorata da ganin yarinyar, Sehrish kuwa tuni ta firgita da ganin yarda Abusufyan ya razana da ganinta,hankali atashe itama ta miƙe tsaye tana kallonshi ido cikin ido, Gaba daya fa kowa na falon ya miƙe yana kallon ikon Allah,duk atunaninsu uncle din nasu ya kamu ne shiyasa ya firgita da ganinta, jikinshi har kerma yakeyi wurin nunata da hannunshi,ƙoƙari yake yi ya ambaci sunanta amma sam ya kasa faɗin sunan,saboda ya kakare mashi,wata irin zufa ce ta shiga gangarowa daga gafen fuskarshi,wannan abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yayi ba, Adai dai wannan lokacin Sgr da Marshal Omar suke saukowa down stairs atare,Omar ne agaba jikinshi sanye da shadda maroon colour,yayin da Sgr ke sanye cikin riga da wando na lallausan voile baƙi,wa'iya zubillah wato tsayawa bayyana irin yarda yadin yayi mashi kyau ma 6ata baki ne,don zan iya karashe littafin nan gaba ɗayanshi wurin kwatanta haɗuwar da sgr yayi acikin boyel ɗin wanda akai ma dinkin Senator style,irin style din da rigar bata karasa kaiwa gwiwa ba yayin da wuyan ke a matse sannan hannun rigan ya dan wuce gwiwar hannunshi kadan,yayin da takalman kafarshi da agogon hannunshi duk launi ɗaya ne da boyel ɗin jikinshi,bai sanya hula ba akanshi,sai dae ya ɗaure sumar kan tashi,a tsakiyar kanshi,hakan ba ƙaramin kyau ya ƙara mashi ba,wani irin daddaɗan kamshi ne ke fitowa daga saƙo da lungu na jikin kowannan su,fuskar nan tashi kamar ya aza mata makeup saboda tsabar kyan da tayi,yadin ba ƙaramin fito da hasken fatar shi yayi ba,yayi fari sol dashi,kamar asace don kyau,yarda kasan diamond haka ya koma,tauraro mafi haske acikin taurari. cike da wannan tafiyar tasu ta majiya karfi suka ƙarasa saukowa daga saman benen, Adai dai lokacin wayar Omar ta shiga ruri,hannu ya zura tare da curota daga cikin aljihun wandon shaddarshi,ganin sunan major ya bayyana akan screen din wayar yasa shi picking call ɗin ya kara wayar a kunnan shi tare da cewa"kun ƙaraso ciki ne? On the other hand major yace"Eh,yalla6ai yanzu haka mun ƙetaro babban gate din gidan tare dasu,yayi maganar yana kallon su hosana dake zaune a back seat ta cikin mirror din gaban motar,fuskokinsu dauke da farin ciki yau zasu ga Sehrish ɗinsu, Omar yace"Okey,ka shigo dasu kawai,"yana fadin hakan ya katse kiran sannan ya bi bayan Sgr suka ƙarasa cikin main palour din. *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari*, "Meya faru Abba"? Marshal Omar ne yayi mashi tambayar yayin da yake kallonshi kafin ya mayar da idanunshi kan Abusufyan dake tsaye duk a rikice,tsayawa Sgr yayi tare da goya hannayenshi asaman wide chest ɗinshi,tunda ya ƙaraso wurin idonshi na akan Sehrish da abusufyan dake atsaye cikin wani yanayi ita Sehrish a tsorace shi kuma Uncle abusufyan duk a firgice, Fuskar Abbansu aruɗe yace"nikaina bansan meke faruwa ba,uncle ɗinku ne tun da yayi arba da yarinyar nan duk yabi ya rikice,ya rasa natsuwarshi,"ya ƙarasa maganar yana yi mashi nuni da Sehrish, Matsawa Omar yayi tare da dafa kafaɗar Abusufyan yace"Uncle meya faru ne?ko kasanta ne"?    Shiru Uncle sufyan yayi batare da yace komai ba amma duk yanayin shi ya canza sosai,idanunshi har lokacin suna akan Sehrish kamar yarda itama take kallonshi,   Suna cikin wannan yanayin kowa ya miƙe tsaye,   Major yayi sallama,Omar ya bashi iznin shigowa daga ciki,   6oyewa jahad da hosana su kayi a bayan major saboda fargabar haɗuwa da dangin ya Omar ɗinsu, ..murmushi Marshal ya saki yana hangen ƙafafuwansu, Zuba ido kowa yayi yana jira yaga su wanene waɗannan dake ta 6oyewa,kowa ya mayar da hankalinshi akan Major dake tunkaro su, Koda major ya ƙaraso wurinsu,sae yace"Jahad hosana ku fito ga ƴar uwarku nan,"   Jin haka yasa su yin hanzarin fitowa daga bayanshi,   Tashin hankalin da ba'a sama shi date,   Waro ido waje su fawan su kayi suna kallonsu,tun daga Ayaan jahan,irfan khaleed da jabeer da kuma kanal yousouf kowannansu ya gama kiɗima da wannan abun al'ajabin,kowa ya gaza buɗe baki yayi magana,kallonsu kawai sukeyi,idan suka kalli Jahad da hosana sae su mayar da idanunsu kan Sehrish,   Tsayawa sukayi daga bayan sehrish,basu da tabbacin cewa itace amma ransu na basu hakan,   Atare suka haɗa baki wurin ambaton Sunanta,   "SEHRISH" Gabanta ne taji ya faɗi rassss,a firgice ta juya bayanta don taga su wanene suka ambaci sunanta,zuba masu ido sehrish tayi tana kallonsu,lokacin da ta juyo suka tabbatar da cewar itace rishi ɗinsu,wani irin farin ciki ne ya cika su,jiki na rawa suka tunkareta zasu rungumeta,abun mamaki sae suka ga tana ja da baya baya fuskarta da alamun tsoro tace"su wanene ku!ni bansan ku ba,dan Allah kada ku matso kusa dani,"   gabansu ne suka ji ya faɗi rass,nan take kuma idanuwansu suka cika tab da kwalla,   Muryar jahad na rawa tace"sehrish,ashe zamu sake sanyaki acikin idanuwanmu?mun rasa ki a lokacin da muke tsananin buƙatarki,ba mu ta6a tunanin cewa zamu ƙara haɗuwa dake ba,sae gashi Allah ya ƙara haɗamu.., "Sehrish.......'hosana ce ta ambaci sunanta,   Zuba ido kowa yayi yana kallon Wannan ikon Allah,   Girgiza kai sehrish ta shiga yi jikinta na rawa tace"Ni...ban..sanku ba..dan Allah ku daina kiran sunana,banason ji,"   Fashewa da kuka sukayi su biyun jin abunda tace masu,   "Omar kun barmu acikin duhu,!dan Allah ku sanar damu ina aka samu waɗannan twins ɗin!"Abbansu ne yayi maganar yana kallon Marshal, Abusufyan kuwa tunda yayi arba da Jahad da hosana ga kuma sehrish,batare da sanin kowa ba,yabar wurin izuwa bedroom ɗin da ya sauka,wani irin matsanancin ciwon kaine ya taso mashi,ga wani zazza6i daya lullu6e shi lokaci guda ya rasa in da zai tsoma ranshi,abun ya gama gigita shi, Gyaran Murya Omar yayi kafin ya soma magana anatse yace"Abba waɗannan twins ɗin da kake gani,sune yaran da nake baka labari,mun haɗu dasu a asibiti cikin mawuyacin hali,na taimakesu a wannan lokacin har na kawosu gidan Uncle abusufyan don su cigaba da rayuwa acikinshi,tun da nake dasu ba mu ta6a tattaunawa agame da danginsu ba,saboda tun lokacin da na fara haduwa da su sun sanar dani su basu da kowa,bayan nakawo su gidan uncle abusufyan aranar dana fara ganin Yarinyar nan sehrish,abun ya ɗaure mun kai ganin kamanninsu iri ɗaya sak da yaran da nake ruƙo a wurina,nasha tambayar sehrish ko tana da ƴan uwa don in bugi cikinta inji ko tana da alaƙa da yaran dake wurina,amma sae tace mun ita bata da kowa,daga baya na dinga tunanin cewa kodai son da nake ma Jahad da hosana ne yasa nake ganin fuskarsu akan ta yarinyar,amma abun da ya faru jiya ne ya tabbatar mun da cewa Bani kaɗae ke ganin kamanninsu ba,junaid yaje ɗaukar sehrish lokacin da aka tashe su daga school,cikin rashin sani ya ɗauko Jahad!amaimakonta ya kawota cikin gidan nan....! Tunda Omar ya soma magana kowannansu ya kasa kunne yana sauraronshi,fuskokinsu da alamun mamaki sosai,   "Jahad hosana da kuma sehrish,uwarsu ɗaya ubansu ɗaya,su ƴan Uku ne!na jima ina mamakin Yarda Allah ya haɗasu dukkansu a ƙarƙashin kulawar family dinmu,ni na haɗu dasu hosana a wani hali na rayuwa na taimakesu na kawosu gidan Uncle abusufyan,yayin da Sehrish aiki ne ya kawota cikin gidan nan.....'   Yana kai ƙarshen maganar Abbansu yace"Amma Omar abun ya ɗaure mun kai wlh!taya akai duk hakan ya faru?   matsawa Omar yayi wurin da su hosana suke tsaye suna faman sharar kwalla saboda ganin yarda sehrish ɗinsu ta nuna batasan su ba,duk murnar da suke tayi ta koma ciki,   Ruƙo hannun Jahad yayi cikin sanyin murya yace"Jahad,ki faɗa masu yarda akai kuka rabu da ƴar uwarku,har tsawon wannan lokacin baku atare,"   Daƙyar jahad ta Iya bayyana masu dukkan abunda ya faru,tun kafin zuwan sehrish aiki,har abunda yayi silar rabuwarsu da ita,da kuma wahalar da suka sha kafin Allah ya haɗasu da Marshal Omar,   Wani irin tausayinsu ne ya kama matasan gidan,jikin kowa yayi mugun sanyi,hatta Sgr dake tsaye yana kallonsu ba ƙaramin tausayi suka bashi ba,yaran sun sha wahala sosai,   "Amma Omar meyasa tun farko baka faɗamun komai agame dasu ba?ae da tuni mun haɗasu da ƴar uwarsu wuri guda sunyi rayuwarsu,"acewar Abbansu muryarshi tamkar zaiyi kuka yayi maganar,dama shi akwai tausayi Omar yace"Abba,nima naso nayi hakan,kayi haƙuri da rashin sanar maka da banyi ba,amma yanzu gasu nan na kawo maku su,kuma ina fata zaku kar6esu hannu bibbiyu kamar yarda kuka kar6i ƴar uwarsu sehrish,!!!   Hankali tashe sehrish tace"Ni ba ƴan uwana bane ya Omar,wlh bansansu ba,bansan su wanene su ba,dan Allah kada ku haɗa ni dasu,bansan ganinsu,bazan iya rayuwa wuri ɗaya tare da su ba,' Wannan kalaman na sehrish yasa kowannansu kallonta cike da mamaki,ƙiri ƙiri ga abu ya fito zahiri amma ta nuna cewa ba ƴan uwanta bane!bayan sunji cewa saboda su ne tazo aiki agidan don ta samu kudi,"   "Rishi mune ba ƴan uwanki ba!sehrish yau da kanki kike faɗin hakan!dan Allah kidaina cewa haka,wlh zuciyata zata iya bugawa na mutu....'jahad ce tayi maganar yayin da idanunta ke fitar da wasu zafafan hawaye masu ɗumin gaske, ..hosana tace"sehrish kin manta ni nima?kin manta hosanarki da kika bari kwance gadon asibiti bata acikin hayyacinta"?muryarta asanyaye tayi maganar,   gaba ɗaya sun rikita sehrish,ko son kallonsu bata yi,in su kayi magana ƙara mata ciwon kai sukeyi,kamar yarda suke kuka haka itama ta fashe da kuka tana rantsuwar cewar batasan su ba, tashin hankali! Sai lokacin kanal yousouf yace"Ina azmee take ne?fawan kaje ka kira mana ita,ina da tabbacin cewa tasan wani abu game da yarinyar nan,tunda tafi kusanci da ita,zai iya yiyuwa akwai wani abu da ta ta6a sanar mata,'   Fawan ya amsa mashi da toh,sannan cikin sauri ya wuce sashen su azmee don ya kira ta,   Ganin yadda su Hosana da jahad ke ta kuka yasa Abbansu junaid cewa"Ku zo nan,"   Hannunsu cikin na juna suka ƙarasa wurinshi,   bin fuskokinsu yayi da kallo na wani lokaci,kafin ya sanya tafin hannayenshi yana goge ma hosana hawayenta,cikin lallashi yace"kudaina kuka ya isa haka,kada ku sa damuwa aranku,yanzu lokacin farin ciki ne,tunda ƴar uwarku tana atare daku yanzu kuma insha Allah,babu wanda zai ƙara rabaku da ita,"   Cikin shessheƙar kuka jahad tace"Amma ta nuna batasan mu ba ai,"   Abba yace"kada ku damu da wannan,wasa take yi maku,zuwa anjima zata dawo dai dai ne,' "Rishi ba wasa take mana ba,"acewar hosana,bayin Allah gaba ɗaya duk zazza6i ya lullu6esu,   Tunda fawan ya sami azmee aɗakinta,ya sanar da ita game da bayyanar ƴan uwan sehrish,farin ciki ya cikata ta shiga faɗin"Alhamdullillah,Alhamdulillah" Jiki na rawa ta biyo bayan fawan suka nufo falon,   Tunkan su ƙarasa ciki take hangensu Jahad da hosana dake tsaye agaban Abbansu junaid,abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,yanzu ta ƙara tabbatar da cewar Dagaske ne!sehrish tana da ƴan uwa,kuma su ƴan ukune,hakan na nufin cewa Sehrish ba ƙarya tayi mata ba,   Tana ƙarasowa sehrish ta nufeta tare da faɗawa jikinta ta rungumeta tana kuka tana cewa"Aunty azmee ni bansan su wanene waɗannan ba masu kama dani,sunce wae sun san ni,bayan ba haka bane,ni bani da wasu ƴan uwa,'bubbuga bayanta azmee ta shiga yi tana lallashinta,   "Azmee muna sauraronki,ko akwai wani abu da kika sani game da ƴan ukun nan!kunfi kusanci da Sehrish nasan cewa dole akwai wani abu da ta ta6a sanar maki agame da rayuwarta,"   Marshal Omar ne yayi maganar, Azmee tace"Sehrish bata ta6a sanar dani wani abu game da rayuwarsu ba,amma ina da masaniya akan Ƴan uwannan nata........'gaba ɗaya azmee ta sanar dasu,yarda sukayi da sehrish tun farkon zuwanta,da kuɗin da ta nema awurinta na biyan kuɗin aikin hosana,duka kaf ta kwashe ta sanar dasu,   "A lokacin ni da kaina,na kar6i acct numbar likitan da yake kula da ƙanwar tasu,na tura mashi kuɗi dubu ɗari tara na aikin yarinyar,acikin kuɗaɗen dana jima ina tarasu na albashina da kuma wanda kuke bani don inyi hidimar kaina....'   Tunkan ta ƙarasa maganar Sgr ya dakatar da ita da hannunshi,   Sai lokacin ya samu damar buɗe bakinshi yace"Meyasa baki sanar da waninmu game da waɗannan yaran ba!bayan ta sanar dake halin da ƴan uwanta suke ciki?sannan waya baki iznin bata kuɗi har 90k batare da sanin kowa ba?kuma kika hana ta zuwa ganin ƴan uwanta saboda kunyi yarjejeniyar zatayi aiki acikin gidan nan harna tsawon shekara ɗaya da rabi,Why AZMEE!?   Hankalin azmee ba ƙaramin tashi yayi ba jin tuhumar da sgr yake yi mata, "Ba laifina bane Rafayet!duk wani abu daya faru nayi ne saboda sehrish!bakomai ne yajawo hakan ba face tsoron kar asirinta ya tonu ku gane cewa ita mace ce ba namiji ba,Abban ku ya nemi mai aiki namiji,amma sai ga sehrish tazo aiki amatsayin namiji,dagani harku babu wanda yasan cewa ita mace ce ba Namiji ba,Ni ce na fara gane cewa ita mace ce,akwai wata rana da naje kiranta don muyi aiki,anan na same ta akwance babu gashin bakin nan da take sanyawa ga kuma dogon gashi akanta hakan ya tabbatar mun da cewa ita mace ce ba namiji ba,koda na sanar mata cewa nagane ita mace ce,a lokacin ta dinga roƙona akan na rufa mata asiri batason kowa ya sani,saboda sanin halin matasan gidan nan da nayi na rashin son ganin mace acikinsu,kuma ga laifin ƙaryar da tayi na zuwa a matsayin namiji,wannan ne dalilin dayasa na rufa mata asiri ban sanar ma kowa ba,daga baya kuma bayan kowa ya gane cewa ita mace ce,naso nayi mata maganar ƴan uwanta amma sehrish sai ta nuna mun cewa ita bata da wasu ƴan uwa aduniyar nan ita kaɗaice........'tun daga farko har ƙarshe azmee ta sanar dasu dukkan wani abu daya faru tsakaninta da sehrish akan maganar ƴan uwanta,da kuma abunda junaid ya sanar da ita na wayarshi da sehrish take ɗauka a 6oye tana kiran ƴan uwanta,komai ta sanar dasu,   Gaba daya sun gamsu da bayananta,duk da basu ji daɗin halin da ƴaran suka kasance aciki ba,sun so ace tuntuni sunsan da zancen,da tuni sun jima da kasancewa a wurinsu,   Jin takun tafiya yasa suka ɗan juya don ganin wanene,Hajiya azeema ce ta fito daga masaukin da ta sauka,ta ca6a ado,wurinsu ta nufo tana tambayar lafiya? mai ya faru ta gansu atsaitsaye cirko-cirko?   Koda ta ƙaraso cikin babban falon karaf idanunta suka sauka akan Jahad hosana da kuma sehrish dake manne da azmee taƙi sakinta,saboda halin da take ciki,   Cike da mamaki tace"Ya hossein!su wanene waɗannan ƴan ukun masu masifar kama?ƴa'ƴan wanene?   Abba yace"wannan wani case ne da muke tattaunawa akanshi,shiyasa kika ganmu atsaitsaye,zan sanar dake komai bayan mun dawo daga sallar magrib naga lokaci ya ƙarato,"   Ya ƙarasa maganar tare da kallon azmee yace"Ki wuce da sehrish ɗakinta,sannan waɗannan ƴan uwan nata ki sama masu ɗakin da zasu zauna kafin mu dawo daga sallah,"   Omar yace"a'a Abba banaso arabasu,yaran nan sun kwallafa rai akan ƴar uwarsu,jiya saboda murnar jin cewa tana a gidan nan,ko bacci basuyi ba,kuma basu ci abinci ba,saboda sunyi alƙawarin cewa atare da ƴar uwarsu zasu ci abinci,don haka inaso a haɗasu ɗaki ɗaya da ita,kuma ashirya masu lafiyayyen abinci suci tare da ita,ko tana so ko bataso," Jinjina kai Abba yayi tare da cewa"Shikenan,hakan ma yayi Azmee ki tabbatar da kin haɗasu wuri ɗaya tare da ƴar uwarsu,"   "Insha Allah zanyi hakan,"ta amsa mashi,sannan ta kalli su jahad da hosana tace"ku biyoni mu tafi," tayi maganar tare da ruƙe hannun sehrish dake ta faman faɗin bataso bataso a haɗata ɗaki ɗaya dasu,ahaka suka wuce bedroom ɗinta,   Bayin Allah,duk sunji sun tsani kansu saboda juya masu bayan da sehrish tayi,duk irin ɗoki da murnar ganinta da sukeyi amma ta nuna batasan su ba,kamar wasu bare haka take kallonsu,haƙiƙa zuciyoyinsu ba ƙaramin karaya sukayi ba,    Bayan azmee ta tafi dasu Jahad,anan su abba suka tsaya suna ƙara tattaunawa atsakaninsu,abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yayi ba,lamarin ya rikirkitasu,bakomai yafi tsaya masu aransu ba,face yarda Sehrish ta nuna batasan ƴan uwanta ba,bayan ga shaidunan sun bayyana karara nacewar ƴan uwanta ne su,kome yasa haka!? "Wai ni ina Uncle abusufyan yake ne!ko kun lura da yanayin da ya shiga lokacin da yayi tozali da Sehrish!"Khaleed ne yayi maganar yana kallon fuskar Abban nasu,   Fawan yace"Nima nayi mamakin razanar da naga yayi lokacin daya ganta,"   Jahan yace"ku ka sani ko kwalliyar da tayi ne,yasa ya tsorata da ganin kyawun fuskar.....'bai ƙarasa maganar ba saboda kallon da Sgr yayi mashi,tsit yayi da bakinshi,   "Gaskiya bana tunanin haka jahan,!sae dae wani abun na daban ne yasa shi firgita,"acewar Ayaan,kowa dae da abunda yake tunani acikin ranshi,   Marshal Omar yace"Kowa ya wuce yayi shirin sallah,kafin a fara kira,"   Amsa mashi sukayi da toh,sannan suka kama gabansu kowa ya nufi room dinshi,jikinsu duk a mace,sun jima basuji tausayin wani ɗan adam ba kamar yarda sukaji tausayin su sehrish,sun tausaya masu sosai ganin irin halin rayuwar da yaran suka shiga,   Bayan tafiyarsu,falon ya rage daga Abbansu sai Omar da Sgr sai kuma kanal yousouf,    "Ni fa ina zargin Uncle Abusufyan abba!kamanninshi da yaran nan yayi yawa abun is over,komai na fuskarsu irin nashi ne!kuma tun daga kan yarda ya firgita da ganin sehrish yasa na tabbatar da cewa akwai wani abu aƙasa,bayan wannan kuma akan idona uncle abusufyan yabar wurin nan agigice jikinshi na rawa ganin ƴan uwan yarinyar nan,ya kamata muje muga a wane hali yake ciki,sannan kuma muji dalilin dayasa ya razana da ganin yaran,"!   Jinjina kai Abbansu yayi jin abunda kanal yousouf yace,Tabbas ya yarda da maganarshi,don shi kanshi ya lura da halin da ƙanin nashi ya shiga,yana son jin meyasa shi firgita da ganin yaran!   Batare da 6ata lokaci ba,Suka nufi ɗakin Abusufyan atare, Lokacin da suka tura ƙopar ɗakin nashi suka shiga ciki,samunshi sukayi zaune dirshen a ƙasa gefen gado yana ta faman sharar hawaye hannunshi dafe da kanshi,sae faman sambatu yakeyi shi kadae, Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,musamman Abbansu,da sauri ya ƙarasa wurinshi,tare da zubewa kasa daga gefenshi yace"abusufyan meya same ka ne!meya faru!me yasaka zubar da hawayenka har haka ne?dan Allah ka faɗamun wlh hankalina ya tashi sosai........'gaba daya duk ya ruɗe ganin halin da abusufyan ke ciki,   Daga gefen gadon Sgr da Omar suka zauna suna kallonsu,yayin da kanal yousouf yake tsaye ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi,turo ƙopar aka kumayi,Hajiya azeema ce tabiyo bayansu, "Subhanallahi Meya faru ne!naga Abusufyan na kuka?wani abu ya sameshi ne"?fuskarta ɗauke da damuwa tayi maganar ayayin da take ƙarasawa ciki ta samu wuri saman stool na gaban dressing mirror ɗinshi ta zauna tana fuskantar su, gaba daya suka haɗu suna tambayarshi dalilin yin kukan nashi, Sai faman share hawaye yake yi,ya gaza buɗe baki yayi magana,   "Uncle dan Allah kadaina kukan nan,duk ka sanyamu acikin damuwa,idan akwai wani abu dake damunka dan Allah ka sanar damu,koda bamu da maganin damuwar taka,zamu taya ka da addu'a akan Allah ya yaye maka ita,"Marshal omar ne yayi maganar cikin tausasa murya, Hajiya azeema tace"Ƙanina dan Allah ka sanar damu mana,meyasa ka ware kanka anan kana kuka kai kaɗae kamar wani ƙaramin yaro?mu fa nan danginka ne wanda baka da kamarsu aduniyar nan,dan haka kada kaji komai ka faɗa mana damuwarka insha Allah,zamu nemi mafita atare,'   ɗagowa yayi da idanuwanshi wadanda sukayi jawur suka kumbura saboda kukan da yasha ya kalli yayan nashi la66ansa na kerma yace"ƴa'ƴana yaya,Su ne damuwata,saboda su ne nake zubar da hawayen nan,na cuci rayuwarsu akan idona rayuwarsu ta wulakanta batare da na ɗauki mataki ba.........'   Hankali atashe Abba da Azeema suka haɗa baki wurin cewa"Ƴa'ƴa kuma!wasu ƴa'ƴa kake magana akai kenan!"   ganin yarda suka razana da jin maganarshi yasa jikinshi yin sanyi dama yasan dole suyi mamakin jin cewa yana da ƴa'ƴa, Sgr da Omar kuwa shiru sukayi suna sauraran abunda Uncle ɗin nasu ke cewa,   Jin yayi masu shiru yasa ran Abban nasu 6aci a fadace yace"ba zaka buɗe baki kayimana magana ba! Sam ya rasa ta yarda zai fara sanar dashi game da ƴa'ƴan da yake magana akai,tsoranshi karya ƙi amincewa da zancen shi,yana fargabar abunda zai biyo baya in ya sanar dasu cewa yaran nan ƴa'ƴanshi ne,   "Kai nake sauraro abusufyan!ka sanar mun akan wasu ƴa'ƴa ne kake magana!'wannan karan a rikice abba keyi mashi magana,   cikin sanyin murya Abusufyan yace"Yaya hossein,ina magana akan ƴa'ƴana ne,waɗanda na haifa,na haifi ƴa'ƴa batare da saninku ba...........' A razane abbansu junaid ya miƙe tsaye yana kallonshi yace"What!!abusufyan kai da kanka kake faɗamun cewa kana da ƴa'ƴa naka na kanka!?Anya ba kunne na ne ke jiyomun ba dai dai ba,"yayi tambayar fuskarshi da alamun ruɗu acikinta, jiki na rawa abusufyan ya miƙe tare da ruƙo hannun abban acikin nashi yace"dan Allah ka zauna yaya,zanyi maka bayanin komai,tabbas dagaske ne ina da ƴa'ƴa abba,kuma suna nan araye,jini na ne su,'   dafe kai Abba yayi saboda wani irin jiri daya ji yana niyar kwasar shi,dakyar ya iya buɗe baki yana ambaton"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!abusufyan ka cuce mu Kuma ka yaudare mu ka zubda ƙimar family dinmu!ashe dama abunda ka aikata kenan shiyasa ka gudu kabar ƙasar nan!?saboda kayi ma wasu ciki kana tsoran asirinka ya tonu shine ka tattara kabar ƙasar nan!"ƙarasa maganar yayi yayin da hawaye ke gangarowa daga cikin idanunshi,abun ba ƙaramin gigita su yayi ba gaba dayansu,basu ta6a tunanin cewa abusufyan dinsu zai iya aikata wannan mummunan abun ba, A faɗace yaci gaba da magana"ka faɗamun gaskiyar lamarin tun kafin ranka ya 6aci!tun yaushe wannan abun ya faru baka sanar mun ba!wacece ko kuma suwa kayi ma ciki har aka haifa maka ƴa'ƴa!kuma ina ƴa'ƴan suke,   gaba ɗaya abusufyan yasha jinin jikinshi ƙoƙari yake yayi mashi bayani amma  ya kasa, Marshal Omar ne yace"Abba,pls mubi komai asannu har mu samu uncle  ya warware mana komai,Ni ina da tabbacin cewa Uncle abusufyan bazai ta6a aikata abunda muke zarginshi dashi ba,dole akwae wani dalilin.   Girgiza kai Abbansu ya shiga yi ranshi atsananin 6ace yace"Kabarni Kawai Omar,abusufyan ya gama da mu,bansan iya zunubin da ya aikata ba,da yasa harya gudu yabar ƙasar nan tsawon lokaci, Amman tunda ni bazai sanar dani gaskiyar Lamarin ba, bari na kira Ammi a waya na sanar da ita abunda ya aikata,may be ita zai iya yi mata bayani tunda ni bazaka faɗamun ba!"   Yana ƙarasa maganar ya zura hannu acikin aljihun wandon shi yana ƙoƙarin curo wayarshi don ya kira ammi,   Cikin sauri abusufyan ya ruƙo hannunshi muryar shi har kerma takeyi wurin cewa"ya..ya hossein ka saurareni dan Allah,ina ƙoƙarin na fahimtar dakai ne,muddin ka sanar ma ammi wannan maganar zan tattara kayana nabar gidan nan ne!saboda bazata ta6a fahimtata ba,kamar yarda kai zaka fahimceni.......'   jikin Abbane yayi sanyi ganin yarda Abusufyan ke ta faman zubar da hawayenshi,   Sassauta muryarshi yayi cikin lallami yace"ka sanar dani Abusufyan!taya akai ka samu ƴa'ƴa"?   Hannuwanshi duka biyun yasa ya rike kanshi da yake jin kamar zai fashe,ga wata uwar zufa da ke zubo mashi har ta jika wuyan shaddar jikinshi,sai faman girgiza kanshi yake ya rasa ta ina zai fara komae ya dagule masa,da ka kalle shi zaka fahimci bai cikin hayyacin shi,    Kanal yousouf ne ya dan yi gyaran murya kafin yace"Abba ni ina ganin muje muyi sallah kilan uncle zai samu natsuwa yayi cikakken bayani don na fahimci kaman bai acikin hayyacin shi ma" jinjina kai Abban yayi don shima ya fahimci hakan,ya mika masa hannu tare da cewa"taso muje muyi sallah amman in muka dawo dole kayi mana cikakken bayani" daga masa kai Uncle Abusufyan yayi alamar ya amince daga haka suka fito gaba dayansu suka nufi masallaci kowa da abunda yake sakawa a ransa. Zamu so muji yarda wannan al'amarin ya faru,taya akai abusufyan da bai ta6a aure ba ya samu ƴa'ƴa',taya akai yayi aure batare da sanin Danginshi ba?suwaye ƴa'ƴan nashi da yake magana akai,amsoshin duka wadannan tambayoyin na a bakin Abusufyan,batare da 6ata lokaci ba zamu nutsa cikin labarin da Abusufyan zai ba yayan nashi hossein da zarar sun dawo daga masallacin. A6angaren su Sehrish kuwa,tunda azmee ta shigar dasu hosana da jahad a ɗakinta,gaba ɗaya ta takure kanta saman gado,jikinta sae kerma yakeyi ko son ganinsu bata yi,hakan ba ƙaramin raunata zuciyoyinsu yayi ba,zuba mata ido kawai sukayi suna kallonta yayin da hawaye ke zuba a fuskokinsu,a gefen gadon nata suka zauna,   Jahad tace"banta6a tunanin cewa zakiyi mana haka ba sehrish,nayi tunanin zakiyi murnar ganinmu bayan tsawon lokaci da bamu haɗu ba,amman sae gashi kin juya mana baya,agaban mutane kika nuna cewa baki san mu b....!"   Tunkan takai ƙarshen maganar Sehrish ta kwatsa mata tsawa tana cewa"Karki ƙara yi mun magana!ni ko muryoyinku bana son ji wlh,bansan su wanene ku ba,kawai kunzo don ku takura ma rayuwata ne..,...'   Cikin shessheƙar kuka hosana tace"dan Allah sehrish ki daina faɗin hakan!bana jin daɗi,meyasa zakiyi mana haka?Yanzu kin manta da hosanarki?ga kuma jahad?rishi dan Allah kidaina yi mana wannan wasan,' Hannu sehrish tasa tare da toshe kunnuwanta alamar bata jin ma abunda suke cewa........'     Duk wannan budurin da akeyi Hayaam na kumshe aɗakinta batasan meke wakana ba,tsoranta karta fito su haɗu da Babban yaya awaje,don tasan muddin yaganta acikin gidan sai yasa an wurgar mashi da ita waje,wannan dalilin ya hana ta fitowa, Amani kuwa har sun kammala kimtsawa ita da Amal zasu zo gidan,sai ga Abbas ya shigo gidan,a lokacin suna tsaye ita da Amal acikin falon gidan, tarar shi tayi tare da cewa"Kai fa muke ta jira tun ɗazu mun kammala shiryawa,"   Abbas yace"sai dai kuyi haƙuri,yanzun nan Abba ya kira ni awaya ya sanar dani cewa wani babban al'amari na faruwa agidan,inyi sauri inxo Suna jira na,bana tunanin cewa suna yin wannan walimar ma,"   Jiki asanyaye tace"Allah yasa dae ba wani abunne ya faru ba,bari mu hakura to in komai ya dai dai ta munje,"daga haka Abbas ya shige ciki yayi abunda zai yi ya fice.   Wannan ne abunda ya hana su Amani zuwa gidan, Bayan sun kammala Sallar magrib,atare suka dawo a nan babban falon suka Hallara gaba ɗayansu banda Azmee da Hayaam da kuma su Sehrish,a lokacin Shima C.g Abbas ya ƙaraso gidan,kowa ya samu wuri ya zauna,Su fawan jabeer da kuma Irfan suna zaune a 3 seater,Abbansu tare da Uncle abusufyan suna zaune asaman 2 seater,Omar kuma tare da Sgr da Kanal yousouf suna xaune ne aɗayar 3 seater ɗin,Abbas da khaleed suma suna zaune asaman 2 seater,sai Aunty azeema dasu jahan kowanne na akan one seater, Gyaran murya Abba yayi tare da kallon Abusufyan dake zaune zugudum agefenshi yace"kamar yarda ka buƙaci mu hallara gaba ɗayanmu a falo,gashi nan duk mun haɗu a wuri ɗaya kai muke sauraro," Nannauyar Ajiyar zuciya Abusufyan ya sauke kafin ya soma magana calmy yace"abunda yasa nace ku haɗu ku dukan ku wuri ɗaya,saboda inaso in bayyana maku cewa ina da ƴa'ƴa,kuma ƴa'ƴan nan na same su ne ta hanyar daya dace,Banaso wani ya zargeni ne da laifin aikata zina,wlh ni tunda nake arayuwata ban ta6a kusantar zina ba,ban ta6a kasancewa tare da matar da ba muharramata ba ina nufin ba matata ba.......'   Shiru yayi na ɗan wani lokaci alamar yana nazarin wani abu,duk suka kasa kunne suna sauraron shi,kowa burinshi yaji taya akai Abusufyan ɗinsu ya samu ƴa'ƴa,kuma suwaye ƴa'ƴan nashi!? "Shekara ashirin da ƴan kai da suka gabata,mun samu sa6ani da Ammi saboda rashin jin maganata,babu jituwa atsakanina da ita,bakomai yake haɗani da ita ba,face irin rayuwar dana taso inayi,abota da mata,na maidasu tamkar maza awurina yarda nake friendship da mata ko maza bana kulawa haka,wannan abunne ke 6ata mata rai,saboda ta tsani ta ganni tare da ƴan mata,ko in aka bata labarin cewa anganni tare da mace acikin mota,nan fa hankalinta zai tashi,a ƙarshe data rasa yarda za tayi dani shine,ta tattara mun kayana gaba ɗaya tace in koma Kano wurin ƙanwarta Hajiya Ameena inci gaba da zama acan,saboda nafi ƙarfinta ba zata iya dani ba don ta lura kaina rawa yakeyi,amma tana da tabbacin cewa in na koma wurin ƙanwarta zan shiryu in dawo dai dai, Wannan ne farkon abunda ya rabani da gidanmu na koma wurin goggon mu da zama gaba daya,don ta gyaramun tarbiyyata kamar yadda ku su yaya hossein kuka sani,maimakon hakan sai ta sangarta ni saboda tsananin son da takeyi mun wanda ko ɗanta a wannan lokacin bata nuna mashi irin son da takeyi mun,komai nakeso shi takeyi mun,wankane kawai ba tayi mun,idan nayi laifi kuwa ko na janyo faɗa awaje rufe ido takeyi taita zazzaga masifa kuma tana sane cewa ni ne mai laifin,in mun shiga gida tayi ta lallashina tana bani haƙuri, TUSHEN LABARIN, Alhaji nuraddeen mai dala,hamshaƙin mai kuɗi ne kuma attajirin gaske,na bugawa a jarida,babban ɗan kasuwa ne wanda yayi kaurin suna a harkar kasuwancin saye da siyarwa atsakanin ƙasashe daban daban,haifaffen garin zariya ne,kuma yana ɗaya daga cikin Aminnan Salahuddeen,aiki ne ya kawo shi katsina kafin daga baya lokacin daya fara kasuwanci ya yanke shawarar komawa garin kano da zama saboda kasuwancinshi yafi ƙarfi acan,wannan dalilin ne yasa shi tattarawa ya dawo gaba ɗaya da zama anan kano tare da iyalanshi a katafaren gidanshi dake a unguwar Nasarawa g.r.a anan jihar kano,farkon haɗuwarshi da hajiya Amina kanwar Ammi wato goggon katsina,tun lokacin da suka je ɗaurin auren Salahuddeen da Ammi a jihar yobe damaturu,acan ya ganota ya ƙyasa,basu baro wurin ɗaurin auren ba sae da aka shafa fatiharsu su duka biyun a lokaci guda, Yaronsu ɗaya wanda sai da sukayi aure da jimawa kafin Allah ya albarkace su dashi,ba kowa bane wannan face Dr haris babban likita,shine ɗa ɗaya tilo da suke dashi,kafin Ammi ta mallaka mata Abusufyan don tagyara mata tarbiyarshi,sae suka kasance su biyu ne ƴa'ƴan dake a wurinta,ɗanta da kuma ɗan yayarta abusufyan,tom da kuma jerry,don gaba ɗayansu basa jin magana a wannan lokacin,ƴan abi yarima asha kiɗane,atare suke fita yawon dare,sun iya zuwa club a haɗu da ƴan mata ayita rawa,zuwa wurin party kuwa koba a gayyace su ba sai sunje,wannan shine rashin jin da ammi ta tsana na abusufyan,shi dae haka rayuwarshi take baida burin daya wuce afita yawo tare da ƴan mata akashe masu kuɗi,kullum yana manne dasu,shi dai kawai yaji mace akusa dashi ba namiji ba,kuma bawai don yayi wani abu da ita ba,sam shi wannan bai agabansa, Ana haka su Abusufyan suka samu hutun makaranta,atare da dr haris suka je kai ziyara zariya wurin danginsu, Bayan tafiyarsu ne,Hajiya Amina da Mijinta alhaji nuraddeen suka tafi umra,dama tun kafin su tafi alhaji ya sallami mai gadin gidansu baba buzu don yaje ƙasarsu niger ya gano danginshi kafin su dawo, Ba ƙaramin daɗi yaji ba,saboda dama atakure yake na rashin ganin ƴar shi tilo da yake da ita,kullum yana cikin damuwar rashin yarinyar a kusa dashi,saboda halin da ya barota acan,basu da kowa danginsu duk sun tarwatse ba haɗin kai,ga talauci dake damun kowannansu,ita kanta yarinyar ya barta ne a hannun matar babanshi,tunda baida kowa iyayenshi duk sun rasu,matar nan ta tsani yarinyar ta takurama rayuwarta gata irin tsoffin nan ne masu mitar tsiya,duk wani aiki yarinyar take ɗauramawa,girki,sharar gida,wanki,ɗebo ruwa,kuma ƙarama ce alokacin bazata wuce 16 years ba, Koda baba buzu yazo niger ganin gida,zuwan bazata yayi masu bai sanar ma kowa da maganar zuwan nashi ba,saboda yana so yaba Abu mamaki kuma yaga irin farin cikin da zatayi idan ta ganshi,kwatsam yana shiga gidan ya samu matar baban nan tashi zaune saman abu ta danneta a tsakar gida,yarinyar sai ihu takeyi tana wutsil wutsil da ƙafafunta,ita kuma matar sae sambatu takeyi tana cewa"Babu abunda zai hana inƙi kasheki acikin gidan nan Abu,dan ubanki ni zakiyi ma asarar tsintsiya?kin barta a ƙasa har ruwan sama ya jiƙata baki ɗauketa ba!ko don kina taƙamar ubanki ne ke turo mana da kuɗi muna siyan kayan abinci....' Hankalin baba buzu ba ƙaramin tashi yayi ba a wannan lokacin,ganin zai rasa ƴarshi ɗaya tilo akan tsintsiyar shara da bata wuce naira hamsin ba,ba ƙaramin fusata yayi ba,a ranar ko zama gidan baiyi ba ya ɗauki ƴarshi ya tafi da ita gidan wani amininshi,tamkar ya zubar mata da hawaye haka yaji a wannan lokacin,yarinyar duk ta rame ta fige ta ƙanjame kamar ba mutun ba,yarinyar da duk garinsu babu wanda ya kama ƙafarta a wurin kyau,tun lokacin da mahaifiyarta ta haifa mashi ita,Allah yayi mata rasuwa tabar mashi ita ƴar jinjira da ita,shi yaci gaba da kula da yarinyar,mutane sunsha zuwa suna nuna mashi kuɗi don ya bar musu yarinyar su ruƙe awurinsu amma yaƙi amincewa da hakan,saboda son da yake yi mata, Bayan hajiya Amina sun dawo nigeria ita da mijinta,Baba buzu ya shirya tafiya tare da ƴarsa abu,babu yarda abokinshi baiyi dashi ba akan ya bar mashi Abu suci gaba da kular mashi da yarinyar a hannunsu,amma ina yace ae ƙafarshi kafar abu,bazai ƙara gangancin barinta a wurin wani ba,kwara ta kasance atare dashi,yana jin motsinta a kusa dashi,zaifi samun kwanciyar hankali, Da daddare suka ƙaraso nigeria bayan uwar tafiyar da suka sha agalabaice suka iso cikin gidan,ruƙe da hannun Abu ya shigo cikin falon gidan,lokacin hajiya ameena na zaune saman kujera mai mazaunin mutun uku tana kallo a tv,tun da sukayi sallama ta dago ta kellesu ganin baba buzu yasa ta saki fara'a tana cewa"marhabun lale ƙaraso ciki mutumina,ashe kana kan hanya banyi tsammanin zuwan.....'bata ƙarasa maganar ba,saboda ganin yarinyar dake ruke da hannunshi, .mikewa tayi tare da zame farin glass ɗin dake a fuskarta tace"baba buzu wannan yarinyar fa?yar waye kazo da ita,"   bai bata amsa ba,sae da suka ƙarasa wurin kujerar da take tsaye,suka zauna kasa saman carpet,sannan ya soma magana"hajiya shannunku da dawowa,ya gajiyar tafiya,' "Lafiyalou Alhmdulillah," Taƙarasa maganar har lokacin idanunta na akan abu,komawa tayi tare da zama saman kujerar sannan tace"bakayi mun bayani game da yarinyar nan ba,"Tayi maganar tana nuna Abu dake ƙankame jikin abbanta   Fargabarsa kada ya sanar dasu cewa ƴarshi ce,suƙi kar6arta baisan inda zai kai yarinyar ba,ya kwaso yarinya ya kawo masu batare da ya sanar dasu ba, dakyar ya iya buɗe baki muryarshi kamar zaiyi kuka yace"yarinyar wurina ce hajiya sunanta Abu,ina neman alfarmar ku taimaka mun ta zauna awurina,saboda bata da kowa acan niger,dama a hannun kishiyar babata take zaune,matar bata da imani naje na shame ta tana gallazama yarinyar nan,ban ta6a sanin abunda ke faruwa ba,sai da nayi masu zuwan bazatan nan.......'komai ya kawashe ya sanar ma hajiya ameena,   Kamar jira takeyi ya kai ƙarshen maganar tashi,nan ta rufe shi da faɗa tana cewa"Amma baba buzu ka bani mamaki wlh,yanzu duk irin shaƙuwar dake tsakaninmu dakai,duk irin yarda muka ɗaukeka tamkar ɗanuwanmu,hakan baisa ka sanar damu cewa kana da ƴa ba,meyasa tun lokacin daka fara aiki agidan nan baka ɗauko yarinyar ka kawota gidan nan ba!....'ta inda take shiga bata nan take fita ba, Jin waɗannan kalaman na Hajiya ameena yasa baba buzu fashewa da kuka yana cewa"na cuci kaina da ban sanar maku ba,ban ta6a tunanin cewa zaku kar6i yarinyar nan hannu bibbiyu ba hajia,da tuni na jima da kawo maku ita,kullum ina cikin takaicin rashinta a kusa dani,saboda itace kaɗai nake gani inji dadi aduniyar nan......'sosai baba buzu ke zubda hawayenshi,   Abu kuwa ganin mahaifinta na kuka yasa itama ta fashe da kukan,jikin hajiya ameena ne yayi sanyi,tausayinsu duk ya kamata, tausasa muryarta tayi tace"baba buzu kukan ya isa hakanan,naji daɗin dawowarka musamman daka kawo mana wannan ƴar kyakkyawar yarinyar taka,kuma insha Allahu zamu bata kyakkyawar kulawa,zata zama tamkar ƴar cikina,dama kuma banda ƴa' mace,gashi inason ƴa mace,Ashe da rabon zan samu......'   Share hawayen shi ya shiga yi yana yi mata godiya,   "Yanzu abunda nakeso dakai,ka wuce ɗakinka kayi wanka zansa akawo maka abinci,nasan kun kwaso gajiya sosai kuna bukatar hutu,ita abu kabarta awurina,zan gyara maka ita sosai da anjima zata zo ta gaishe ka,"   Cikin shesshekar kuka baba buzu yace"hajiya bansan da wani irin kalamai zan gode maku ba,kunyi mun abinda bazan iya saka maku ba,kun jima kuna ɗawainiya dani kuma yanzu gashi zaku ɗauki ɗawainiyar yarinyata,Allah yasa ka maku da mafifincin alkhairinsa.....'sosai baba buzu ya shiga yi masu addu'o'i hakan ba ƙaramin dadi yayi ma Hajiya ameena ba, Tun daga wannan lokacin Abu tazama tamkar ƴa awurin hajiya Ameena,baka ta6a gane cewa ba ƴar cikinta bace saboda yadda suke ruƙe ta hannu bibbiyu duk wata ɗawainiyarta tadawo kansu,hatta makarantar islamiyya dana boko babu wanda basu sakata ba,dama yarinyar akwai hazaƙa sosai,akwai son karatun addini,kullum zaka ganta rungume da kur'ani a hannunta tana karatu,ko aiki takeyi zaka ji tana ta rero karatun haddar da aka basu,bata ta6a zama bakinta shiru batare da tana karatu ba,wannan abun ba ƙaramin burge hajiya ameena yake ba,shiyasa batajin wuyar kashe mata kuɗi,saboda ita ta ɗauko malamin da zai dinga zuwa gida yanayi mata karatu,malamin makarantar islamiyyarsu wanda suke kira da Ya sayyadi,tun da zainab tafara zuwa makarantar islamiyyar asatin farko kullum sai yazo gaishe da hajiya ameenatu,idan yazo yayi ta zuzuta zainab awurinta yana yaba irin ƙoƙarin dake gare ta,hajiya Ameenatu najin daɗin hakan,Amma mahaifin Abu,baba buzu mai gadi mutumin bai kwanta mashi araiba,ya tsani yaga malamin nan yazo wurin Abu zai koya mata karatu,shisshigin da yake yi ma yarinyar yayi yawa,kullum sai yazo da ɗan rugwagwar mashin ɗinshi ƙopar gate din gidan wurinta,hakan ba ƙaramin ƙona ma Baba buzu rai yake ba,shiru kawai yake yi don bai da yadda zaiyi ya hana shi zuwa gidan,tunda hajiya ameenatu ta ɗauke shi amatsayin malamin da zai dinga koyama Abu karatu,tun Abu na da wata daya acikin gidan haris ya dawo batare da Abusufyan ba,saboda shi yace bazai dawo ba sai daddy mijin Aunty ameenatu ya bashi haƙuri,saboda yace shi yake 6ata tarbiyyar Haris,rashin jin maganar shi yayi yawa,koda haris ya hadu da Abu acikin gidan saiya mayar da ita tamkar ƙanwarshi,idan aka bata assignment na school shike zama ya fidda mata shi,harma ya koya mata karatu. *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari*, Bayan wani lokaci Tafiya takeyi tamkar batason taka ƙasa,jikinta na sanye da uniform na islamiyya,dogon hijab Brown colour har wuce guiwarta,wandon kuma milk colour,ta rufe fuskarta da nikab,yayin da hannayenta ke ruƙe da jakar makarantarta,da gudun gaske wata danƙareriyar mota ash colour ta faɗo cikin layin da take tafiya,gadan gadan mai motar ya tunkari inda Abu taja ta tsaya,waro ido waje tayi tare da ja da baya jikinta na kerma,koda mai motar nan ya ƙaraso inda take,sai ya shiga zagaye ta da motar gaba ɗaya ya tada mata ƙura,   Ƙanƙame jikinta tayi gabanta ya faɗi rass,tsoronta kar ace sace ta aka zo yi,   Sai da ya tabbatar da cewa ta gama tsorata sannan ya tsayar da motar wuri guda ta tsaya cak,   A ɗan tsorace abu ta buɗe idanunta tana kallon motar cikin ranta tana tunanin wanene wannan bawan Allahn daya firgitar da ita haka,   Bata ƙarasa zancen zucin nata ba taga ya zuge glass ɗin motar,lokacin da tayi arba da kyakkyawar fuskarshi sae da gabanta ya faɗi rasss!matashi ne wanda bazai gaza shekara 20 ba zuwa ashirin da daya,kana kallonshi zaka ga ƙuruciya atare dashi,jikinshi na sanye da crazy jeans sae farar t shirt agaban rigar an rubuta Am crazy,'da alama bashi kaɗae bane acikin motar,akwai wani agefen shi, Muryar mace tajiyo daga cikin motar tashi tana cewa"Hey,ƴan mata,mun tsorata ki ko?ki yi haƙuri Babyn nawa ne sae a hankali,wai kin burge shi ne,shiyasa yayi maki wannan wasan,'.     rai atsananin 6ace take kallon fuskokinsu ta cikin niqab din fuskarta,bakowa yafi bata haushi ba face shi saurayin daya yi mata wannan ɗanyen aikin,arayuwarta ta tsani mutane masu wayewa irin tasu,kallo guda tayi masu ta gane cewa ba mata da miji bane,amma sun manne ma juna acikin motar kamar zasu haɗe su zama ɗaya,    jinjina kai kawai tayi tare da zuƙunnawa ta ɗauki jakar islamiyyarta da ta fadi,cikin sauri ta kama hanyar zuwa gida,biyo ta sukayi da motarsu,hakan yasa hankalinta ya tashi,saboda gudun kada Abbanta ya ga motar dake biye da ita,don kullum yana ja mata kunne akan karta kuskura wani ya tsaidata akan hanya ta tsaya,yanzu in ya ganta tare da wannan jibgegiyar motar dake bin bayanta batasan wane hukunci zaiyi mata ba,dole ya tuhume ta akan ina ta samo su,    "Baby,kana ganin zata faɗa mana address ɗinta kuwa?da alama yarinyar kamar za tayi ji da kai nake gani,kasan ƴan islamiyyan nan,ji su keyi kamar sunfi kowa tsoran Allah,suyi ta kame kansu acikin hijabi,suna yi ma mutane kallon shaiɗanu,'matashiyar dake acikin motar ce tayi wannan maganar,kuma duk akan kunnan Abu,   Saurayin yace"ae ko bata faɗa mana address ɗinta ba,zamuyi ta bin bayanta ne har mu gano gidansu,"   Jin wannan maganar yasa,yarinyar zuƙunnawa tare da kwale takalman ƙafafunta,kafin su ankara ta watsa da gudun gaske kamar zata tashi sama,ko waiwayensu batayi,har ta 6ace ma ganinsu,,   Tun daga nesa Baba buzu mai gadin dake a zaune saman benchi yana sauraron radiyo dake ruke a hannunshi,ya hango ta sai faman tsala gudu takeyi,hankali tashe ya miƙe tsaye yana jiran ƙarasowarta,koda ta ƙaraso a galabaice ta zube agabanshi,saman guiwowinta tana faman haki,   "Abu meya faru ne naga kina gudu haka?waye ya biyo ki"? Muryar mahaifin nata ne ta dawo da ita cikin hayyacinta,   daƙyar ta iya cewa"wasu ne a mota,bansan kosu wanene ba,sae faman bibiyata sukeyi,shine na watso da gudu don karsu gane gidan da nake,"   Jin wannan maganar yasa ran buzun mai gadin ya 6aci sosai nan fa yashiga zazzaga masifa yana cewa"da kin bari sun ƙaraso don ubansu dana koya masu hankali,shikenan ba dama yarinya ta ɗan fita ɗauko karatu sae an samu wanda ya takura rayuwarta!zan yi maganin koma wane ɗan ja'irin ne yake son cutar mun dake.....'ta inda yake shiga batanan yake fita ba, a ƙarshe dae yace"tashi ki shiga ciki,kiyi wanka kici abinci ki kwanta ki huta kafin akira sallar magariba,ki kwantar da hankalinki kinji Abunah,ina nan ina jiran Koma wane ɗan iskan ne,saina koya masu hankali,'   Ajiyar zuciya abu ta sauke tare da miƙewa tayi mashi sallama,sannan ta shiga cikin gidan ta ƙopar gate ɗinsa, Lokacin da ta shiga cikin main palour ɗin gidan babu kowa,alamar suna can upstairs bedrooms ɗinsu,don haka ta wuce nata ɗakin kai tsaye, Bayan ta ajiye jakar islamiyyarta,ta cire hijab ɗin jikinta,ta ninketa tare da turata cikin wardrobe na kayanta,shaf shaf ta kammala cire kayan islamiyan nata ta wuce cikin toilet don tayi wanka, After some minutes,ta fito daga cikin toilet ɗin jikinta ɗaure da farin towel,jikin nan nata har wani ƙalli yakeyi saboda hasken fatarta ga gyaran da take sha,agaban mirror ta tsaya tana ɗaure sumar kanta mai tsayi da yawan gaske,tana da yalwataccen gashin kai wanda yakai har qugunta,tana cikin ɗaure gashin kan nan nata kwatsam taji anyi mata gyaran murya abayanta,a firgice tajiyo don ta ga kowanene,lokacin da tayi arba da mutumin da yayi mata gyaran muryar acikin ɗakinta nan take ta zazzaro ido amatuƙar tsorace take kallonshi,   kwance yake asaman gadonta,ya miƙe ƙafafunshi yayin da hannunshi ke ruƙe da brazier ɗinta da ta cire kafin tashiga toilet,sae faman latsa breast curve ɗin yakeyi cike da tsokana,   Hankali a matukar tashe abu tace"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un...Nashiga uku....!'gaba daya taba ma ranta cewa al'jani ne shi,ba kowa bane wannan face saurayin nan daya tsoratar da ita da motarshi akan hanyarta ta dawowa daga islamiyya,shi da budurwarshi, Muryarta na rawa tace"wa..wanene...kai dan Allah!me kakeso a wurina ne!taya akai kasan gidan mu har ka biyoni ɗakina"?   Ƙayataccen murmushi ya saki tare da cewa"bani da amsar tambayoyinki,ni dai kawai nagani inaso,in kika yi mun biyayya mu rabu lafiya,koda yake bazama mu ta6a rabuwa ba,saboda kinyi mun wlh," ya ƙarasa maganar tare da kai bakinsa ya manna ma bra ɗinta kiss   Runtse ido abu tayi agigice ta fasa ihu tana neman ɗauki,akan azo a fidda mata aljanin dake aɗakinta,   Da gudu ta watsa waje babban falon jikinta na kerma ta shiga cewa"Mommy!!mommy!!ya haris!daddy!!dan Allah kuzo ku taimake ni,Aljani aɗakina saman gadona....'   Jin sautin kukan Abu yasa hankalin Hajiya ameena tashi,da saurin gaske ta sauko downstairs ta nufi wurinta tana cewa"Abu meya faru ne kike ta kwaɗa ihu? Cikin shessheƙar kuka tace"Wani ne acikin ɗakina saman gadona,bansan ko wanene shi ba,a kan hanyar dawowata daga islamiyya ya tsoratar dani da motarshi,shine yanzu kuma bayan na fito daga wanka na ganshi kwance saman gadona,'   Cike da mamaki hajiya Ameena tace"Wani kuma!acikin gidan nan saman gadonki?taya akai har ya samu damar shigowa cikin gidan nan....'   Ba ta kaiga ƙarasa maganar ba,sae ga Abusufyan ya fito daga cikin ɗakin abun,fuskarshi ɗauke da murmushi,   Ganin shi yasa abu yin saurin nuna shi da hannu tace"Ga shi nan mommy....wlh shine ..Aljani ne," murmushi hajiya Ameenatu tayi tana kallon Abusufyan tace"Son sai yau kaga damar dawowa gidan?irin wannan zuwan bazata haka?ka tafi kabarmu da kewarka ko?ko tunanin makaranta bakayi ba,ka kama hanya ka tafi kan abunda bai kai ya kawo ba,'   Langwa6e kai abusufyan yayi yana tsuke bakinshi alamar an 6ata mashi rai, ...zuru abu tayi tana kallon ikon Allah,aranta tana cewa"Ashe ɗan masu gidan nan ne,ni duk atunanina aljani ne shi,amma dae da alama baijin magana sosai,'   "Pls mom just forget about it,komai ya wuce tunda dae nadawo," Jinjina kai hajiya ameenatu tayi,kafin ta mayar da idanunta kan Abu dake tsaye sototo tana kallonsu tace"Calm down ur mind Abuna,wannan da kike gani ɗan yayata ne,sunan shi Abusufyan,bai jin magana amma kada wannan ya hanaki sakewa dashi,shima ki ɗauke shi tamkar Yayanki Haris,'   Jiki asanyaye tace"insha Allah mommy,"kafin ta ɗan wurga ido ta kallo shi har lokacin kashe mata ido yakeyi,hakan ba ƙaramin haushi yake bata ba,har tafara jin tsanarshi, Tun daga ranar da Abusufyan ya dawo cikin gidan abu ta shiga uku dashi,ya hana rayuwarta sakat,duk inda ta sanya ƙafarta yana biye da ita,toilet ne kawai bai binta shi dai kawai burinshi ta sake dashi kamar yarda take shiri da haris,ita kuma tace bazata ta6a ɗaukarshi yayanta ba,saboda bai da kamun kai,bakomai yaja mashi hakan ba face Abubuwan da yake yi mata na rashin kunya,da kuma ƴan mata da take ganinshi tare dasu manne da juna,hakan ba ƙaramin ƙona mata rae yake yi ba,duk a tunaninta Abusufyan ɗan iska ne kamar yana bin mata,saboda ita tayi believing da abunda idanuwanta ke nuna mata, Ana haka wata rana malamin nan nasu Sayyadi ya ɗaukota daga islamiyya asaman machine dinsa super cub,tun suna akan hanya motar abusufyan ke bin bayansu saboda ya hangota abayan mashin ɗin malamin,ranshi yayi mugun 6aci wani irin kashi ne ya lullu6e shi,saboda ya lura akwai soyayya tsakaninta da malamin nan nasu,babu yarda abusufyan baiyi da ita ba akan ta bari ya dinga kaita school amma taƙiya,da yake tana da kafiya sosai,mace ce mai wuyar sha'ani, A bakin gate ɗin gidan sayyadi ya tsayar da mashine ɗinsa,abu ta sauko hannunta ruƙe da jakarta,tsayawa tayi suna ƙara gaisawa dashi, "Abu har yanzu baki bani amsa ta ba"? Sunnar da kai ta ɗanyi tana murmushi tace"amsar me kenan"?   sayyadi yace"oh har kin manta kenan?abu kinfa san ina sonki sosai,kuma kema kina sona,bana buƙatar mu 6ata lokaci atare da juna batare da munyi aure ba,banda burin daya wuce wannan, in ganki amatsayin matar aure na,'   Cike da jin kunyarshi abu tace"dan Allah ka ƙara mun lokaci,zanyi tunani akan hakan,'   Kafin sayyadi ya buɗe baki ya ƙara yin wata maganar,suka ji dirar motar Abusufyan agefensu,tun daga kan yarda yayi parking ɗin motar ya tabbatar masu da cewar ba'a hayyacinshi yake ba, .zuba ma motar ido sayyadi yayi kafin ya mayar da idonshi kan abu yace"wanene acikin motar nan"? Muryarta na rawa tace"yayana ne Abusufyan,' ɗan ta6e bakinshi yayi yana jinjina kai, Atsiyace abusufyan ya buɗe murfin motar ya fito,jikinshi sai faman rawa yake yi,kai tsaye wurinsu ya nufo sai faman huci yake yi,   Wani irin mugun kallo ya jefa mata tare da nuna mata hanyar gida yace"Ke wuce ciki!tun kafin ranki ya 6aci shashasha kawai wadda batasan ciwon kanta ba!ki rasa da wa zakiyi mu'amala sae wannan ƙarmasasshen mutumin,ko uban miye abun so ajikinshi!mutumin da ya kusa tsaran ubanki!"   Hankalin abu ba ƙaramin tashi yayi ba jiki na rawa ta kama hanyar shiga gida, Muryar sayyadi ce ta dakatar da ita"Abu kada ki tafi!bangama magana dake ba,"   Zuba ido abusufyan yayi yana kallon ikon Allah,tsayawa abu tayi saboda umarnin da sayyadi ya bata akan karta tafi, Rai amatuƙar 6ace Abusufyan ya daka mata tsawa tare da cewa"ke!har ni zan baki umarni kiƙiyi mun biyayya saboda wannan munafukin mutumin malamin ƙarya!"   Waro ido waje sayyadi yayi yana kallonshi, Abu kuwa jin an ta6a masoyinta yasa tace"Abusufyan ya isa haka!karka ƙara zagar mun malamina,wannan mutumin da kake gani yafi mun kai so dubu,saboda yana da ilimin addini kuma shi yake koyamun karatu,mutum ne shi mai kamun kai ba kamar kai ba....'jin kalaman abu akan shi yasa sayyadi ya shiga sakin murmushi yana kallon Abusufyan dake tsaye zuciyarshi na tafarfasa, Tuni idanunshi sun ciko tab da kwalla saboda bai iya jurar 6acin rai ba,Zainab ta bada shi awurin malaminsu,   daƙyar yake iya haɗiyar yawun bakinshi da ya gama ƙafewa,jinjina kanshi ya shiga yi kafin daga bisani ya soma magana cikin sanyin murya"Naji duk abunda kika ce abu,amma inaso ki sani bakowane malami bane yake zama mutumin kirki,don kawai ya ruɗe ki da karatun kur'ani yana jawo miki aya da hadisi yana fassara maki su,shine yasa kike tunanin cewa shi mutumin kirki ne?mutun nawa kika sani yana da haddar al'qur'ani akanshi amma hakan bai hana shi aikata zunubin daya ga dama ba....."?   ɗaure fuska sayyadi yayi yace"Kaga ɗan saurayi yarinyar nan ta nuna cewa bata sonka,dan Allah karabu da rayuwarta mana haba,ita malami takeso mahaddacin al'qur'ani ba ɗan tasha ba mai yawo da mata acikin gari,'   Wannan maganar ba ƙaramin fusata Abusufyan yayi ba,har baisan lokacin da ya ware tafin hannunshi ba ya kifa ma sayyadi mari asaman kuncinshi,kafin abusufyan ya zame hannunshi daga kan fuskar Sayyadi yaji saukar mari ɗauuuu a kan fuskarshi agigice ya juya yana kallonta hankalinshi amatuƙar tashe bai ta6a tunanin cewa abu zata iya ɗaga hannu ta mareshi ba,tunda yake arayuwarshi ko dunguri wannan wani bai ta6a gigin yi mashi ba,sai yau da Abu ta mare shi saboda ya mari sayyadinta, Hawaye ne suka soma gangarowa daga cikin idanuwanshi,muryarshi har kerma takeyi wurin cewa"A..ab..bu..ni kika mara saboda na mari wannan ƙasƙantaccen mutumin mai fuska biyu!?   ɗaga hannu tayi zata ƙara kwasa mashi mari,kamar daga sama taji an ruke hannunta kafin tayi wani aune kuma taji saukar mari zazzafan gaske akuncinta,   A firgice ta juya tana kallon shi,bakowa bane ya mare ta ba,face mahaifinta shi da kanshi baba buzu, Fashewa tayi da matsanancin kuka tana cewa"baba...yau kai da kanka ka mare ni?" A faɗace yace"idan kika sake buɗe baki kikayi magana saina kikkifa maki wasu marukan,sakarya kawai wadda batasan halacci ba,yanzu saboda wannan mutumin kika mari abusufyan ko?   wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarshi jin yarda mahaifinta ya goya mashi baya,sayyadi kuwa ranshi ba ƙaramin 6aci yayi ba,sae faman mazurai yake yi,   Kafin yace"haba baba buzu,ni kake kira da wannan mutumin?ka manta matsayin da nake dashi awurin ƴarka?nifa ne malamin dake koya mata karatun addini,ya kamata ka darajani,kuma abunda abu tayi ba kuskure bane,yaron nan rashin kunya yayi mani dole ranta ya 6aci,dan Allah kaja mashi kunne ya daina yi mana shisshigi saboda ni da abu son juna mukeyi kuma aure zamuyi......'   Tunkan ya ƙarasa maganar baba buzu ya daka mashi tsawa tare da cewa"ubanwa zai auraka maka ita!ko ita take da ikon aurar da kanta ne!Ni ne mahaifinta kuma ni nake da ikon na aurar da ita ga wanda naso,kuma naga ya dace da rayuwarta,don haka tun yau inaso ka cire ta aranka,abu nayi mata miji,kuma ba kowa bane mijin nata ba face ABUSUFYAN!muddin ina numfashi abu bazata ta6a auran wani ba in ba shi ba!!!   Hankali tashe abu ke kallon mahaifinta da idanuwanta da sukayi jawur saboda kukan da tasha,mayar da idonta tayi kan Abusufyan dake ta faman sakin murmushi,girgiza kai tashiga yi tana cewa"baba...ni banason abusufyan,bai dace da rayuwata ba,ba mutumin kirki bane shi,bai da kamun kai,kuma baida ilmin addini,boko kawai yasa agaba,wayewarshi tayi yawa baba.....'   Ganin yarda mahaifinta ya harzuƙo zai rufe ta da duka yasa ta watsa aguje cikin gidan tana kuka,   "Yanzu abunda kayi ya dace baba buzu?yarinyar nan ta nuna tana son malamin addini mahaddaccin al'qur'ani saboda ya tarbiyantar da ƴa'ƴanta,ta san cewa idan ta aure ni zan bata kyakkyawar kulawa kuma zan ilmantar da ita da kuma ƴa'ƴan mu saboda me zaka hana ta aure ni!?kafi son ta auri wannan sangartaccen da baisan komai ba sai yawo da ƴan mata acikin gari?ahaka kake tunanin zai bama ƴarka tarbiyya in ya aure ta? sayyadi nakai ƙarshen maganarshi baba buzu yace"Ka gama sambatun naka?to kama hanya kabar ƙopar gidan nan tun kafin raina ya 6aci,banason ganinka tare da abu,don ban yarda dakai ba,akwai wata mummunar manufa atare dakai na son cutar da ƴa ta,shiyasa naji baka kwanta mun araina ba,amma abusufyan ya kwantamin araina,duk da ya kasance yana da ƙananun shekaru amma ina da tabbacin cewa yafi ka hankali da tunani........'   Jin wannan maganar ta baba buzu yasa hawaye sauka a idon sayyadi muryarshi a kasalance yace"Wai me nayi maka ne ka tsane ni?me na tsare maka ne?dama tunda na fara zuwa gidan nan ina koya ma abu karatu na lura da irin kallon da kakeyi mun,meyasa baba buzu?ko don na kasance malamin makaranta banda arziƙin da zan iya siyen zuciyarka ne?saboda banda kuɗin da zan dinga baka cin hanci don ka auramun ƴarka zainab,sae shi daya taso gidan naira,kasan cewa idan ka aura mashi abu tattalin arziƙinka zai bunƙasa,baba buzu ka tabka babban kuskure arayuwarka muddin ka aura ma abu wannan sangartaccen yaron........' Yana kai ƙarshen maganar shi ya tada rugwagwar mashin dinshi yabar wurin,   matsawa baba buzu yayi tare da dafa kafadar Abusufyan cikin rarrashi yace"kayi haƙuri abusufyan,duk sai naji na tsani kaina da abu ta ɗaga hannu ta mare ka,ni ina da tabbacin cewa wannan malamin dake bibiyar rayuwarta ba mutumin kirki bane,ba don Allah yake son abu ba,tabbas akwai wani abu dayake son cimmawa atare da ita,' Abusufyan yace"baba kada ka damu komai ya wuce,kuma ina baka haƙuri game da kalaman da sayyadi yayi maka,banji daɗinsu ba,'   Baba buzu yace"babu komai yaje don kanshi,Allah na gani ba don komai yasa nakeson ka auri abu ba,sai don saboda in saka ma mahaifiyarku da irin ɗawainiyar da take damu ni da ƴa ta abu,wlh bani da burin daya wuce wani acikin ƴa'ƴanta ya nuna yana son abu ni kuma in aura mashi ita,wannan ce kawai hanyar da nake da ita da zan iya sakamata,'   Murmushi abusufyan yayi tare da cewa"Baba yanzu in na nemi auran abu a wurinka zaka aura mun ita?a yadda nake da ƙananun shekarun nan"?   baba buzu yace"mai zai hana?ni lokacin da iyaye na sukayi mun aure ban kai shekarunka ba,kuma muka zauna da matata lafiya har Allah ya al'barkace mu da samun zainab,abusufyan in har dagaske kana son abu,kuma zaka ruƙe mun ita amana,na amince kayi ma Abbanku magana ya nema maka auranta awurina nikuma zan baka ita,kai tun ma yanzu inaso ka sama ranka cewa abu ta zama matarka,saboda na mallaka maka ita,sadaki kawai zaku biya a aura maka ita,'   wani iri farin cikine ya lullu6e abusufyan,saboda tsabar farin ciki baisan lokacin daya ɗauki baba buzu ba ya daga shi sama yana jujjuya shi,dariya sosai baba buzu yayi yana cewa"Abusufyan ka sauke ni mana!ko nauyi na baka ji!duk murnar na mallaka maka abu ne yasa ka ɗauke ni haka kamar diyar roba,   Sosai sukayi nishaɗi atsakaninsu, Lokacin da abu ta shiga falon gidan tana faman zabga kuka,hajiya Ameena na ganinta ta tashi daga zaunen da take saman kujera ta tunkareta tana tambayarta lafiya,   adai dai lokacin Mijinta Alhaji nuraddeen yana kan saukowa ƙasa daga saman bene,tun kan yaƙaraso yake tambayarsu me akayi ma abu take kuka,   cikin shessheƙar kuka tace"Baba ne yace zai auramun abusufyan kuma ni bashi nakeso ba sayyadi nakeso in aura......' Jin wannan maganar ta abu yasa hajiya ameena ta ɗaure fuskarta tace"Abu yanzu saboda mahaifinki ya za6a maki abusufyan amatsayin mijin da zaki aura shine kike kuka!meyasa bakya son shi ne?   Muryar daddy ce ta katse mata hanzarinta"Wannan abun bazai ta6a yiyuwa ba!babu yarda za'ae abu ta auri Abusufyan yaron da bai gama mallakar hankalinshi ba!ban goyi bayan wannan maganarba,zanje na samu mahaifin naki muyi magana dashi,indai aure yakeson yi maki sai dae ya aura maki sayyadi saboda shi ya mallaki hankalinshi zai iya kula dake amma ba abusufyan ba,' Wurga mashi wani kallo mai kama da harara hajiya Ameenatu tayi tare da cewa"Wannan abun bai shafeka ba alhaji!babu ruwanka da shiga shirgin Abusufyan,tunda ubanta da kanshi ya mallaka mashi ita,babu wanda ya isa ya dakatar dashi daga auranta!aure kamar anyi an gama ne'   murmushi kawai alhaji nuraddenn yayi yana girgiza kai yace"oh kema kin goyi bayan Abu ta auri abusufyan?bayan kinsan halin shi sarai bai jin magana,kuma yarinyar nan ta nuna cewa bata son shi,dan Allah karku takura rayuwarta,ku bari ta auri za6in ranta karku tilasta mata!kuma sannan ke kin manta da cewa Yayarki hajiya Aishat bazata bari abusufyan yayi aure da ƙuruciyarshi ba!kuma kin manta da tsarinta na ƙin auren bare"? ta6e baki hajiya ameenatu tayi kafin tace"ni wannan bai dame ni ba,ba'a auran bare ita ta auri amininka salahuddeen?ko tana da alaƙa dashi ne?ba haɗuwar barikin sojoji bace,'tayi tambayar tana kallonshi,   Cigaba da magana tayi,"idan kuma kuruciyarshi kake magana,kai kamanta kana da shekara nawa na aure ka?wasan ƴar 6urun 6urun muka dinga yi dakai adaren farkon mu ko ka manta da wannan"? Bakin Alhaji fa ya mutu shiru yayi bai tanka mata ba,don bai da amsar da zai bata,   guntun tsoki taja kasa² tare da mayar da idanunta kan abu dake tsaye hankali tashe tana kallon mommyn jin ta goyi bayan auranta da abusufyan,   "Abu,kiyi hakuri ki bi za6in da mahaifinki yayi maki,ni ina da tabbacin cewa bazaki ta6a dana sanin auran abusufyan ba!nasan kina yi mashi kallon mutumin banza ne saboda son mu'amalarshi da mata,amma inaso ki sani abusufyan ɗina ba ɗan iska bane,kuma shima yana da ilmin addini fiye da tunaninki,shigar ƙananun kaya da yake yi da kuma yawan manne ma matan da yakeyi hakan ba yana nufin cewa shi mutumin banza bane,zainab abunda nakeso ki sani,bata suttura kota kalaman baki ake gane mutumin kirki kona banza ba,wannan azuciya yake,zaki iya ganin mutum malamin addini mai haddar al'qur'ani kanshi kullum sanye cikin jallabiya yana wa'azi bainar nasi,alhalin zuciyarshi baƙa ce yana aikata wasu muna nan abubuwan a6oye batare da sanin kowa ba sai mahalincinshi ,haka zalika zaki iya samun mutumin da kullum yake ɗabi'u irin na turai,sanya ƙananun kaya,hulɗa da mata rashin jin magana da sauransu amma kuma zaki samu zuciyarshi kyakkyawa ce tsarkakakkiya bai sa6ama ubangijinshi,ki daina yarda da abunda idanuwanki suke nuna maki abu,tun farko kinyi ma abusufyan mummunan zato shiyasa kika tsane shi,amma ni nasan cewa kina sonshi kamar yarda yake sonki,bansan me malamin can ya faɗa maki agame dashi ba,dayasa har kika za6e shi akan jini na,to inaso ki sani muddin kinason ganin farin cikina,tun daga rana irin ta yau ki cire soyayyar wancan mutumin aranki,ki fara koyama kanki soyayyar Abusufyan,kafin aɗaura auranku.,.......'   Murya na rawa abu tace"..mo..mommy..ke ma kin amince in auri abusufyan in rabu da sayyadina? Jinjina mata kai hajiya Ameenatu tayi alamar Eh, Fashewa da kuka Abu tayi tare da watsa wa da gudu ta shige ɗakinta saman gado tana kuka tana faɗin"Ni bani sonshi bana son abusufyan bazan aure shi ba,sayyadi nakeso,'kamar zautacciya haka tashiga sambatu har bacci ya ɗauketa, Alhaji dae bai ƙara tanka masu ba saboda baisan 6acin ran matarshi,ya zuba ma sarautar Allah ido,yana kallon ikon Allah, Batare da 6ata lokaci ba,hajiya Ameenatu ta biya sadakin abu dubu ɗari ta damƙa ma mahaifinta,shi kuma ya damka ma zainab kuɗin a hannunta,daƙyar ta kar6i kuɗin,ko da ta koma ɗakinta dasu,wurgi tayi dasu asaman gadonta,ta koma tana sharar kwalla, Duk wannan budurin da akeyi,iyayen Abusufyan basu son da zancen auren abusufyan ba,tun lokacin da Hajiya ameenatu ta kira Ammi awaya take sanar da ita cewa Abusufyan yaga yarinyar mai gadin gidansu yana so,tun kafin ta rufe bakinta ammi ta katseta a fadace tace"Kar na sake jin wannan zancen,ki rabashi da yarinyar don karya sama ranshi ita,ni bazan ta6a aura mashi yar mai gadi ba mara asali,ƴa'ƴana bazasu auri bare ba,auran zumunci zanyi masu,"tun da hajiya Ameenatu taji wannan zancen na yayarta ta tabbatar da cewar bafa zata amince abusufyan ya auri abu ba,saboda ita kaifi ɗaya ce in ta furta abu babu wanda ya isa ya dakatar dashi! Koda Hajiya ameenatu ta sanar ma Abusufyan abunda mahaifiyarshi tace na ƙin amincewa da aurenshi da abu,ranar har zazza6i yayi yaƙi cin abinci kuma,duk yabi ya hargitse ya shiga damuwa sosai,hakan yasa hankalin hajiya yayi mugun tashi saboda ta mutu akan son Abusufyan,batason ganin damuwarshi,shiyasa ta yanke shawarar aura mashi abu batare da sanin iyayenshi ba,ko wani daga cikin danginsu don kar Ammi ta samu labari,a wata ranar juma'a ne bayan an kammala salla,aka ɗaura igiyoyin auransu dubban jama'a suka shaida,daga ciki hada ni hafsat bature muhammad,da kuma makaranta wannan littafin, Tun lokacin da labarin auren Abu da abusufyan yaje kunnan sayyadi,tun daga ranar bai ƙara takawa yaje gidan ba,abun ya ɗaure mashi kai,yarda suka shirya komai batare da saninshi ba,suka aurar da yarinyar da yake mutuwar so,har gadon asibiti sai da ya kwanta yayi jinya, Bayan aurensu da sati guda hajiya Ameenatu ta ware masu katafaren ɗakin da zasu zauna anan cikin gidansu,ta zuba masu duk wani abu na more rayuwa acikinshi,duk don ta faranta ma abusufyan dinta,hatta lefen kayan abu duk ita ta siya mata komai da kayan ɗakinsu, Duk yadda abusufyan yaso ya shawo kanta ta amince suyi rayuwar aurensu amma abu taƙi amincewa dashi,har yau ganinshi takeyi tamkar ba mijinta ba,saboda bata son shi ita sayyadi takeso,kullum Abusufyan yayi yunƙurin ta6a ta,hana shi takeyi tana cewa ba tayi tanadin kanta  saboda shi ba sai don sayyadinta,'wannan maganar ba ƙaramin ƙona mashi rai takeyi ba,gashi Allah ya jarabce shi da tsananin sonta,duk wulaƙancin da abu keyi mashi,bai ta6a sanarma kowa ba,jurewa kawai yake yi donnya rufa mata asiri,yasan muddin ya sanar ma mommyn shi aminatu ko mahaifinta baba buzu sae ranta yayi mugun 6aci don mahaifinta har bugunta zai iyayi,saboda ya tsani yaji tana maganar sayyadin nan, Wuraren ƙarfe sha biyu na dare,tana kwance saman gadonsu tana bacci,ta dinga jin shessheƙar kukan mutum akusa da ita,buɗe idanunta tayi masu ɗauke da bacci,tare da miƙewa daga zaune tana kallonshi,   Ya tasa ta gaba ya zabga uban tagumi yana ta faman zubda hawaye,gabanta ne taji ya faɗi rass ganin abusufyan na kuka da idanunshi,zuba mashi ido tayi tana kallonshi batare da tace mashi komai ba,   Cikin shesshekar kuka yace"Abu dagaske baki sona?meyasa kika tsane ni ne?   buɗe baki tayi tare da cewa"ba kaine ke bana so ba,ɗabi'unka da halayanka ne ke bana so,na tsani naganka kana mu'amala da wasu matan da sunan abokantaka,kuma natsani naganka kana sanya irin waɗannan kayan ajikinka,kuma baka da kunya abusufyan agaban kowa kake faɗin duk abunda yazo bakin ka,ni nafison kamilin mutun natsastse mai ilimin addini,'     cikin sanyin murya yace"zan canza halaye na saboda son da nake yi maki ne kawai,'   "Kayi mun alƙawarin bazaka ƙara kula wata mace ba in ba ni ba?   ɗaga mata kai yayi alamar eh yace"Nayi maki alƙawari abu,zan daina,daga rana irin ta yau bazan ƙara hulɗa da mata ba,zan kame kaina kamar yarda kikeso,zan zama irin mutumin da kikeso,'ya ƙarasa maganar yana kallon cikin idanunta, Jinjina kai tayi tace"idan kuma ka sa6a fa?ka yadda na yanke duk hukuncin dana ga dama akanka"? "Na amince"ya bata amsa, Ajiyar zuciya ta sauke tare da miƙa hannunta ta ɗauko al'qur'anin dake ajiye asaman side drawer dinta ta miƙa mashi,yasa hannu biyu ya kar6a cike da mamakin me zaiyi da al'qur'anin da ta bashi,gabanshi ne ya shiga faɗuwa tsoranshi kar tace ya rantse da al'qur'ani don bazai iya rantsuwa dashi ba,   "Me kike nufi da wannan qur'anin da kika bani,"   Murmushi ta saki kafin tace"so nake ka rantse dashi cewa ba zaka ƙara hulɗa da wata ƴa mace ba aduniyar nan in ba ni ba,babu ruwanka da mace indai ba ƴar uwarka bace sai kuma ni da nake matarka,in kuma harka sa6a hakan na kama ka tare da wata ƴa mace zaka sake ni saki ukku!ka amince da hakan!!"   Shiru abusufyan yayi gabanshi na faɗuwa,aranshi yana zullumin amincewa da maganarta,saboda baisan halin da zai tsinci kanshi ba anan gaba,tsautsayi zai iya afkawa dashi a lokacin da baiyi tsammani ba, "Dan Allah abu ki janye maganar rantsuwa da qur'ani,banaso kuma ma babu kyau yin rantsuwa dashi,kiyi haƙuri pls,wlh nayi maki alƙawarin bazan ƙara kula mata ba,komai zan daina,"cikin sanyin murya yayi maganar yana kallonta,   ɗaure mashi fuska tayi tare da cewa"Abusufyan dole fa sai ka rantse mun da qur_'anin nan sannan zan yarda dakai!ƙin amincewa da hakan zaici gaba da haddasa rashin zaman lafiya atsakaninmu!"   babu yarda ya iya da ita,saboda aƙagare yake da su fara kasancewa amatsayin ma'aurata tare da ita,baison 6acin ranta ko kadan,baida burin daya wuce yaga suna zaman lafiya da ita,wannan dalilin ne yasa shi yin rantsuwar da har yau yake danasaninta, Hannu tasa tare da kar6ar qur'anin ta maida shi saman drawer ta ajiye shi,   "Yanzu zaki bani haƙƙina kenan"?ya tambaya yana kallonta,   jinjina mashi kai tayi alamar eh,kafin ta sanya hannunta tare da cire rigar jikinta,ya rage daga ita sae bra,nan fa hankalin Abusufyan ya tashi haikam da ganin surar ƙirjinta,gaba daya ya afka mata,suka manne ma juna,gaba daya suka zautar da junansu,sosai Abusufyan ya biya bukatarshi da ita,sai lokacin ta gane ba ƙaramin cutar kanta takeyi ba,na ƙin amincewa dashi tun ranar farko da aka ɗaura masu aurensu,ba ƙaramin so ya nuna mata ba awannan daren,kuka sosai abusufyan yayi mata saboda tsantsar farin cikin da yaji na kasancewarshi mutun na farko daya fara kar6ar budurcinta, Tun daga wannan lokacin soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakaninta dashi,saboda irin tarairayar da yake yi mata,da kuma irin kulawar da yake nuna mata,kullum yana tare da ita yana faranta mata,da kanshi yake kaita school sannan ya wuce tashi makarantar,idan an tashe su shi yake zuwa yaje ya ɗaukota ya kaita gida,tamkar romeo da juliet haka suka koma,har acikin mota soyayya suke sha,idan tana aiki a kitchen haka zai bita yana tayata aiki,gyaran ɗakinsu duk shi ke yi in yana gida,hatta gugar kayan makarantarta shi ke zama ya goge mata su,duk wannan soyayyar da suke sha akan idon Hajiya Ameenatu,dama itace ta bama soyayyar tasu wurin zama,in taga sunyi kwana biyu basu fita yawon shakatawa ba,da kanta take ɗauko kudi tabasu tace su tafi shan ice cream,ko suje suyi siyayyar abunda suke so,shi dai Alhaji nuraddeen har lokacin zuba masu ido kawai yake yi,mahaifin abu kuwa baba buzu mai gadi,hankalinshi ba ƙaramin kwanciya yayi ba,ganin yadda Abusufyan ke kular mashi da yarinyarshi,yanzu baida sauran damuwa sae fatan cikawa da kyau da IMANI, Bayan wata guda da sati uku da yin auransu.................. Suna zaune a cikin class ɗinsu na islamiyya,ƙawayenta na kewaye da ita,tana basu labarin irin soyayyar da suke sha ita da abusufyan ɗinta,dama bata da wata magana sai ta Abusufyan,suna cikin firar nan sai ga malamin nan nasu sayyadi ya faɗo cikin ajin a fujajen yana ta faman huci,suna haɗa ido da abu ya kwaɗa mata kira"Zo nan zainab," ƙin zuwa tayi sai da wata ƙawarta tace mata"Abu kije ya sayyadi na kira,"ba don taso ba ta miƙe tare da zuwa inda yake,waje suka fita daga gefen ajin nasu, "Yanzu abu kin kyauta abunda kikayi mun?kawai sae dai naji agari an ɗaura auranki da abusufyan"? Muryar shi tamkar zaiyi kuka yayi maganar, "Dama Allah ya ƙaddara cewa kai ba mijina bane Sayyad,Abusufyan shine mijina,don haka ina baka haƙuri kuma ina yi maka fatan Allah ya baka mace tagari wadda ta fini,"tana faɗin hakan ta juya zaka koma class cikin sauri yasha gabanta tamkar zai rungumeta,ɗan ja da baya tayi tana kallonshi a tsorace, Rai amatuƙar 6ace yace"Zainab!kada kiyi mun haka kin manta alƙawarin da mukayi ma juna,zamu yi aure mu haifi ƴa'ƴa mu tarbiyantar dasu atare?abu ni fa kikeso ba Abusufyan ba?me zakiyi da namiji mai bin mata?ke da kanki kika sanar dani cewa Abusufyan mutumin banza ne mai hulɗa da mata,kuma bai da tarbiyya sannan baida ilmin addini rayuwar turae yasa agaba bai damu da addinin shi ba....' Abu tace"hakane ni na faɗa maka haka da bakina,tabbas munyi alƙawari dakai sai gashi Allah bai nufa ba,tunda bani ke iko dakaina ba,mahaifina shiya za6amun Abusufyan kaga dole nayi masa biyayya,malam kaida kanka kake yi mana nasiha akan mubi iyayenmu muyi musu biyayya,don haka bai kamata kaga laifina ba,don nabi umarnin mahaifina ba,sannan zancen cewa abusufyan na bin mata,rashin sani ne yasa nayi mashi mummmunar fahimtar nan,amma ni mijina baya bin mata,abusufyan mutumin kirki ne,yana mu'amala da mata amma bai ta6a kusantar su da sunan aikata zina ba,iya friendship yake yi dasu,maganar ilmin addini kuwa abusufyan shima malami ne mai zaman kanshi,da farko na dauka boko ya sanya agaba,amma yanzu nagane cewa yana da ilmin addini sosai,bai cika bayyanawa bane agaban mutane,amma shi da kanshi yake ƙara mun karatun hadda in aka bani a makaranta,kuma yana tashi na muyi sallar dare dashi,kuma muyi karatun alƙur'ani atare.......' Tunda tasoma magana sayyadi ke ta faman huci kamar ya rufe ta da bugu haka ya dinga ji,sae da ta kai ƙarshen maganarta sannan yace"yanzu kin haƙura da duk wasu munanan dabi'u nasa kin amince zaki cigaba da zama dashi yana hulɗa da mata," ɗaga mashi kai tayi alamar eh tace"Abusufyan yayi mun rantsuwa da alƙur'ani cewa bazai ƙara mu'amala da wata ƴa mace ba in bani ba,in kuma har yayi hakan zai sake ni ne mu rabu," tun daga kan yarda abu ke magana zakasan cewa akwai ƙuruciya sosae atare da ita, Jin maganarta yasa sayyadi jinjina kai tare da matsa mata hanya yace"ki koma aji," sallama tayi mashi sannan ta wuce cikin class, Bayan shigarta aji,murmushi ya shiga saki yana cewa"ta kwana gidan sauƙi,"yana fadin hakan ya ƙara gaba. *Zuwa gobe insha allah zamu kammala labarinsu sehrish ataƙaice sannan mu ɗaura daga inda muka tsaya*   *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari*, ❤🤍❤ Da wuri bayan an tashe su daga islamiyyar Abusufyan yazo ɗaukarta,ƙawayenta sae santin shi sukeyi,dama haka kullum suke zuzuta kyanshi da kuma gulmar wankan da yake ɗauka na tsadaddun kaya,ba ƙaramin tafiya yake yi dasu ba,   Shiga cikin motar abu tayi tare da rufe motar,sannan ta juya tana kallonshi,ya kifa kanshi asaman sitiyarin motar da alamun damuwa atattare dashi,   Hannu tasa tare da shafa sumar kanshi tace"Mijina,meya faru ne naganka kamar cikin damuwa," ɗagowa yayi daga kan sitiyarin ya kalli fuskarta tare da cewa"babu komai abuna,yau dai hakanan nake jin gabana na faduwa kamar wani mummunan abu zai faru dani,dan Allah ki tayani da addu'a ko zan samu zuciyata ta daina yi mun bugun da takeyi,   jin wannan maganar ta abusufyan yasa hankalinta tashi,matsawa tayi kusa dashi suna fuskantar juna tace"Insha Allah babu abunda zai faru mijina uban ƴa'ƴana,zan tayaka da addu'a kuma inaso kaci gaba da Ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'in,insha Allah komai zai tafi dai dai,'    Murmushi ya ɗan saki tare da haɗa fuskokinsu wuri guda suna shaƙar numfashin junansu,   Cikin wata irin kasalalliyar murya yace"Kiyimun alƙawarin ba zaki ta6a rabuwa dani ba abuna,wlh ina sonki sosai fiye da yadda nakeson kaina,banda burin daya wuce na ƙare rayuwata tare dake,daga ni har ke akwai ƙuruciya atattare damu,ina fatan mu girma tare,mu kara wayau atare sannan mu tsufa kuma atare,'   Kalamanshi ba ƙaramin kashe mata jiki sukayi ba,nan take taji soyayyarshi na ƙara ninkuwa acikin zuciyarta, Cikin sanyin murya tace"bazan rabu dakai ba Abusufyan ɗina,i luv u so much,more than my life,bazan ta6a bijire maka ba,yanzu na gane cewa bani da masoyin da ya wuce kai aduniyar nan abusufyan,ina fatan Allah yabarmun kai,'ta ƙarasa maganar tare da hugging ɗinshi sosai ta kwantar da kanta asaman wide chest dinshi,dama tubarkallah duk da kananun shekarunsa yana da cikar kira ga hutu daya ratsa shi,hannunshi ya zura acikin hijabin jikinta yana shafa sumar kanta,sun jima a wannan yanayin kusan 30mins,kafin ya tashi motar ya miƙi hanyar komawa dasu gida,a kasalance yake yin driving ɗin,saboda sakonnin da abu ke aika mashi ajikinshi,duk ta jefa shi cikin wani irin yanayi,   koda suka koma gida atare Suka ci abincin da Hajiya Ameenatu ta girka masu abun gwanin burgewa,bayin Allah ashe duk na bankwana ne,sukeyi ma juna basu sani ba, lokacin kiran sallar magrib,abusufyan ya fito daga cikin toilet,jikinshi da danshin ruwa alamar alwala yayi,a lokacin abu na zaune gefen gadonsu tana jiran fitowarshi,jin alamar buɗe ƙopar shi yasa ta ɗan dago ta kalleshi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Sannu da fitowa hayatyna," Ƙarasawa yayi wurinta tare da zama daga gefenta yace"me kika tanadar mun yau idan nadawo gida da daddare? Abu tace"komai kakeso," "To ki tanadar mun kan ki,yau zan baki mamaki,awashe gari zaki haifa mun babies bama ɗaya ba....'   Dariya tayi sosai jin abunda yace kafin ya tashi yayi mata sallama tare da fucewa,' Lokacin da aka kira sallar isha'e bayan tayi wanka ta ɗauro da alwala,sai da ta kammala sallar sannan ta shiga shirya kanta,tun tana shafa mai ajikinta take tunano kalamam abusufyan nacewa zata haifa mashi babies awashe garin ranar,ta lura ba ƙaramin son ƴa'ƴa gare shi ba,kusan kullum ne sai yayi mata maganar yaushe zasu haihu,wani lokacin har cewa yakeyi wai ko dae basu isa haihuwa bane shiyasa bata samu ciki ba,duk irin ƙoƙarin da yakeyi, don ba ƙaramin jarababbe bane, Murmushi tayi tare da cewa"Nikaina aƙagare nake dana ga ƴa'ƴan da zamu haifa ni da abusufyan ɗina,nasan yaran zasu zama kyawawan gaske in dai suka ɗauko kyawun fuskar kowannanmu,amma ni dae nafi son su ɗauko fuskar shi,saboda koda wata rana in yayi tafiya mai nisa,zan dinga kallon fuskarsu a matsayin tashi,hakan zai ɗebe mun kewa, Gaba ɗaya ɗakin ya gauraye da ƙamshin turaren da abu ta feshe jikinta dashi,bayan ta gama shafe shi da haɗaɗdun mayukan jikinta,komawa tayi gaban wardrobe ɗin kayansu ta buɗe tana tunanin wasu kaya zata sanya waɗanda zasu zautar da abusufyan,ta jima atsaye tana ruwan ido kafin ta hango wata rigar bacci Babby doll black color,net ne ajikin rigar shara shara ana kallon komai na jikin mutun,tamkar ma mutun bai sanya kaya bane saboda yadda take fitar da tsiraici,ba ƙaramin kyau rigar tayi mata ba,zubo da gashin kanta tayi ya sauko har wurin waist ɗinta,komawa tayi gaban mirror ta shafa jan baki red abakinta, Bayan ta kammala shirin nata,ta shiga zagayen ɗakin tana jiran dawowar abusufyan,tana yi tana kallon wall clock dake manne a bango tana duba time,abu kamar wasa har ƙarfe 10 na dare babu abusufyan,shi da ya saba dawowa da zarar an kammala isha'e,baiwar Allah har ta fara gajiya da yawon,komawa tayi ta zauna gefen gadon tana sa ran dawowarshi,da zarar taji motsin mutun ya shigo cikin gidan sai ta miƙe jiki na rawa ta leƙa taga wanene  ashe Haris ne ya dawo,na biyu kuma data leƙa Abbansu ne ya dawo,ƙarshe dae bacci ya kwashe ta,wuraren goma sha biyu ta farka,ganin har lokacin bai dawo ba,yasa hankalinta yayi mugun tashi,saukowa tayi daga saman gadon ta ɗauko hijabi ta zura ajikinta,sannan ta fito daga ɗakin ta wuce bedroom ɗin haris,   A ƙofar ɗakin ta tsaya tana kwankwasawa,   Cikin bacci haris ya jiyo bugun ƙopar ɗakin nashi,muryarshi akasalance yace"Wanene,"   Abu tace"ni ce Zainab,' Saukowa yayi daga saman gadonshi yazo bakin ƙopar ya buɗe mata tare da cewa"lfy,meya faru ne abu?   Abu tace"ɗan uwanka abusufyan har yanzu fa bai dawo cikin gidan nan ba,hankalina ya tashi sosai,bansan ko kana da masaniya akan inda yaje ba,"   Cike da mamaki Haris yace"wai kina nufin bro ɗina bai dawo gida ba?tare dashi fa muka je masallaci,amma ba tare muka dawo ba,saboda yace mun yana sauri yazo wurinki ne,ni kuma na biya gidansu abokinmu ne,"   Jin wannan maganar yasa hankalin abu ya ƙara tashi haikam,tuni idanunta sun cicciko da kwalla,dama bata da wuyar yin kuka,fargabarta kar ace wani abu ne ya faru da mijinta,   Lallashinta haris yayi tare da cewa"just calm down ur mind,duk inda abusufyan yake yana atare damu,bana so ki tashi su mommy daga bacci game da maganar nan,hankalinsu zai tashi ne,bari na jaraba kiran numbar shi muga in zata shiga,"ya ƙarasa maganar tare da juyawa ya shiga cikin ɗakin nashi,   Sai gashi ya dawo hannun shi ruƙe da wayarshi yana dannata,numbar shi ya kira,tana fara ringing abun mamaki akayi picking kiran,   Da sauri haris ya kara wayar a kunnan shi yace"bros kana ina ne wai?har 12 baka dawo gida ba?duk ka tayar mana da hankali,"   Gaban haris ne ya faɗi rass jin muryar mace tana cewa"mai wayar ya shiga wanka ne,'   rejecting kiran yayi cikin sauri gudun kar abu tajiyo muryar macen da yaji,don ya santa da kishi,   "Me ya ce maka"! Ta tambaya tana kallonshi,   Daƙyar ya iya cewa"Am..um...kin gane wani aiki ne ya tsayar dasu a company,sai zuwa gobe ko da asuba zai dawo,dan Allah ki ƙara hakuri....'   Tunkan yakai ƙarshen maganar tashi abu ta watsa da gudu ixuwa ɗakinsu ta faɗa saman gado tana kuka,tasha kuka sosai a ƙarshe bacci ya ɗauke ta, Koda ta farka sallar asuba,abusufyan bai dawo ba,bayan tayi salla ta zauna tana karatun al'qur'ani don kar bacci ya kuma ɗaukarta,wuraren ƙarfe 7:30 tayi shirin zuwa islamiyya,duk da halin da take ciki na damuwar rashinshi,    batare da sanin kowa ba ta fice ko breakfast ba tayi ba,a bakin gate suka haɗe da baba buzu,    Zuƙunnawa tayi tare da gaishe shi"ina kwana baba,kun tashi lafiya,"   Baba buzu yace"me ya faru abuna?naga fuskarki tayi jawur ta kumbura kamar kinsha kuka"?   cikin sauri tace"a'a babu komai baba,lafiya ta lou,'ta bashi amsa tare da miƙewa tsaye,   "Ina abusfyan ɗin yake ne yau bazai kai ki makarantar bane"?   Shiru tayi tana tunanin amsar da zata bashi,    Bai kawo komai aranshi ba,yace"kada ki makara ki wuce ki tafi," Amsa mashi tayi da toh sannan ta fito waje ta kama hanya tana tafiya ita kaɗae cike da damuwa,   Kwatsam!kamar ance ta waiga ta hango Motar abusufyan yayi parking ɗinta a gefen hanya,mamaki ne ya kamata, Jiki na rawa ta nufi wurin motar tare da sanya hannunta ta kwankwasa glass ɗin shi,   Zuge glass ɗin akayi a slow,a gigice Abu ta zaro ido waje tana kallonsu,abun tamkar a mafarki, sun manne da juna abusufyan ɗin da take ta haukan nema tare da wata matashiyar budurwa cikin motar,budurwar ko kayan kirki babu ajikinta,inners ne kawai ta bari,da alama ma basu acikin hayyacinsu sunyi nisa cikin harkar tasu,   Hankali amatuƙar tashe abu ta aza hannunta akai tana fadin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'una....!' Tana ƙarasa faɗar hakan ta yanke jiki ta faɗi a sume ƙasa,zubewarta ƙasa ke da wuya,Motar nan tabar wurin tamkar bata ta6a bayyana ba,   Adai dai lokacin kuma Motar Abusufyan ta shigo layin da gudun gaske,tunkan ya ƙaraso ya hangi abu sume a ƙasa cikin uniform dinta,gabansa ne ya faɗi rass,da sauri ya tsayar da motar tare da buɗe ta ya fito yana faɗin"kai!me nake gani haka?kodai idanuna ne suke nuna mun ba dai dai ba!abuna ce kwance a ƙasa!taya akai hakan ya faru!"   ƙarasawa yayi tare da zuƙunnawa agabanta yana shafa fuskarta,ya jima yana mamakin yadda akai abu ta sume ƙasa,kuma tabbas itace,   Hannu yasa ya ɗaukota ya nufi mota da ita bayan ya kwantar da ita abayan motar ya shiga gaban motar ya tashe ta suka nufi gida, Lokacin da abusufyan ya shigo da abu a hannunshi,Hajiya Ameena suna xaune saman dining chairs ita da alhaji da kuma haris suna yin breakfast, Hankali atashe suka nufo shi suna tambayarshi lafiya!meya faru da ita! Hajiya tace"Yaushe kuka fita tare da ita batare da sanina ba!? Abusufyan yace"mommy ba atare muka fita ba,ni jiya ban kwana agida ba,bacci ya ɗauke ni acikin mota ban ƙara sanin inda kai na yake ba sai da safen nan,kuma wayata ma an sace ta banganta ba," Mamaki ne ya kamasu su duka,musamman Haris kanshi ya ɗaure jin cewa an sace wayar abusufyan hakan na nufin cewa jiya wayar bata a hannunshi wasu ne suka ɗauke wayar,to garin yaya hakan ya faru,   Hajiya tace"Haba abusufyan ɗina garin yaya har bacci ya ɗauke ka acikin mota,kuma aka sace maka waya,duk ta yaya hakan ya faru"?   Muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"wlh mommy ni kaina bansani ba,wayata tun a masallaci aka sace ta,ban tashi ankara ba sai da na shiga cikin motata bayan mun rabu da haris,na kamo hanyar zuwa gida na dinga ganin biji biji acikin idanuna,dalilin dayasa na dakatar da driving ɗin nayi parking na motar,tun daga nan ban ƙara sanin inda kaina yake ba,sai yanzu dana farka,na biyo hanyar gida kenan naga abu a kwance ƙasa,ina tunanin wani abune ya tsoratar da ita shiyasa ta sume' Alhaji yace"kaɗan daga cikin sakarcin kane sufyan!in ba shashasha ba taya zaka bar bacci ya ɗauke ka acikin mota har ka kwana awaje,ko tsoron wani abu ya faru dakai baka ji!salon kaja ma mutane bala'e ko!?   Ganin ya rufe shi da fada yasa mommy ta 6ata fuska tare da kallon Abusufyan tace"Ka shiga da ita ciki"   Amsa mata yayi kafin ya wuce da abu cikin ɗakinsu,   "Dama ae kin saba goya mashi baya!yaron nan yayi laifi me yasa ba zaki bari ayi mashi faɗa ba!ke kina da tabbacin cewar baccin ne ya kwashe shi akan hanya har ya kwana waje?ni ban yarda da zancen nan nashi bama,akwai dae inda yaje,".    Rai a6ace Hajiya Ameena tace"ya isa haka Alhaji!kasan irin kalaman da zaka dinga faɗi akan abusufyan ɗina,in ba haka ba,ranmu xai 6aci ne gaba daya, Tamkar zasuyi faɗa atsakaninsu,ganin haka yasa Haris cewa"pls mommy dan Allah kudaina mana,banaso inga kuna faɗa akan abusufyan,wai meyasa kuke haka ne?daddy kaima ka daina sanya baki akan lamarinshi mana tunda mommy bataso,ba shikenan ba,'.   Jinjina kai kawai Alhaji yayi tare da kama hanya ya wuce upstairs,haris ya ruƙo hannun mommynshi suka koma don su ƙarasa yin breakfast ɗinsu, A6angarensu abu da abusufyan kuwa,bayan ya kwantar da ita saman gadonsu,ruwa ya dauko a roba ya ɗebo ya yayyafa mata a saman fuskarta,a hankali ta shiga mutsu mutsun buɗe idanunta,zuba mata ido yayi yana kallon fuskarta cike da tausayinta don yaga alamar jirwayen hawaye a fuskarta kuma ta ɗan kumbura, Ware idanunta tayi akanshi koda taga shine a firgice ta miƙe zaune saman gadon tana ja da baya,ƙure ma head board ɗin gadon tayi tana faman zazzare mashi idanu,   Cikin sanyin murya yace"Abuna,am really sorry jiya nasan kinyi kewata sosai,na kwana awaje ban dawo gida ba,nima ba da son raina hakan ya faru ba,"   Yana kai ƙarshen maganar tashi abu ta fashe da matsanancin kuka tana cewa"ka cuce ni abusufyan,ka yaudare ni!kayi mun ƙaryar cewa zaka daina mu'amala da mata ashe ƙarya kakeyi,har yanzu kana tare dasu,da idona nagani kuma na shaida,hakan ya tabbatar mun da cewar a hotel ka kwana kai da karuwar daka ajiye tana biya maka buƙata,tunda ni ban isheka ba....'   Hankalin abusufyan ba ƙaramin tashi yayi ba,a ruɗe yace"abu bangane akan me kike magana ba!dan Allah ki fahimtar dani!"   Cikin shesshekar kuka ta sake maimaita mashi abunda tace   Hannu ya aza akai yana fadin"innalillahi'wa inna ilaihirraji'un! Ya Allah kasa mafarki nake yi ba gaske ba,abu yau ke da kanki kike jifa na da waɗannan munanan kalaman!abu bani kika gani ba,wlh bani bane ni ban yi mu'amala da wata mace ba,ban haɗu da kowa ba,waɗanda kika gani acikin motar nan bani bane, wasu ne can daban,idanunki ne suka gwada maki ba dai dai ba....'   A tsiwace tace"Abusufyan!nagama yarda dakai,saboda kai maƙaryaci ne kuma fasiƙi mazinaci.......'   Bai bari taƙarasa maganarba afusace ya kwashe ta da mari,dafe kuncinta ta tayi ko gizau batayi ba taci gaba da cewa"Ni ka mara da hannunka saboda na faɗi gaskiya?koda yake yanzu har buguna ma zaka iyayi ai saboda ka samu wadda tafi ni,' Kallonta yake yi yayin da idanunshi sukayi jawur jikinshi har rawa yakeyi saboda tsananin 6acin ran da ta sanya shi,   Muryarshi akausashe yace"Abu kada ki sake kirana da mazina ci!ban ta6a aikata zina ba arayuwata,ko sunanta bana son inji an ambata balle har nayi yunƙurin aikatata,wlh kika ƙara kirana da sunanta saina sa6a maki......'   duk wannan budurin da akeyi Hajiya da haris basu sani ba,saboda akwai tazara tsakanin bedroom ɗinsu abusufyan da kuma inda suke, Harara ta wurga mashi har lokacin hawaye naci gaba da zuba a idanunta huci kawai takeyi saboda 6acin rai,   daƙyar ta iya furta"Ka sake ni!saboda bazan iya cigaba da rayuwa dakai ba!kayi mun alƙawarin cewa zaka daina mu'amala da mata,kuma har rantsuwa kayi da al'qur'ani cewa in har ka sake kula mata,zaka sake ni saki uku!!!'   Tsananin 6acin rai da takaici yasa abusufyan ya fashe da matsanancin kuka yana cewa"Zainab baki a cikin hayyacinki!wlh ba ke bace,nasan cewa ba yin kanki bane,aljanune suka shiga jikinki,"   "Abusufyan ka sake ni!in ba haka ba zan illata kaina kowa ya rasa,"tayi maganar babu wasa a fuskarta,   "Wlh bazan sake ki ba abu,bazan iya ba,saboda ni banyi maki laifin komai ba,zargina kawai kikeyi amma baki da shaida akaina,dan Allah abu kidaina wannan maganar zuciyata zata iya bugawa in mutu,kiyi haƙuri mu sasanta tsakaninmu nasan zaki fahimce ni,'   Babu alamar sassauci a fuskarta,tamkar yana ƙara tunzurata haka taci gaba da faɗin ya sake ta,   Ganin yaƙi sakinta yasa ta mika hannu tare da janyo drawer chest,sabuwar reza ta ciro daga cikin drawer ɗinta,   Hankali tashe abusufyan yace"me zakiyi da ita abu?     Fuskarta aɗaure tace"zaka sake ni ko bazaka sake ni ba!" shi kanshi sai da ya tsorata da yanayin yadda take magana,ganin yadda hijabin jikinta ya jiƙe sharkaf da zufa,kuma babu zafi aɗakin nasu,ga idanuwanta sunyi jawur dasu luhu luhu,jikinta kuma sai kerma yakeyi,   Cikin sanyin murya yace"Abu pls ki saurare ni,zan fahimtar dake..kinsan ina sonki bazanso abunda zai cutar dake ba,bazan iya cin amanarki ba abu,   damƙar hijabin jikinta tayi tare da cireta tayi wurgi da ita gefe guda,a fusace ta Sanya rezar nan abakin tafin hannunta na dama,ta tsarga wurin nan take jini ya soma tsastsafowa daga wurin   Agigice abusufyan ya yunƙura zai kwace rezar hannunta,dakatar dashi tayi da cewa"Idan har ka kuskura ka matso zan kashe kaina ne!"   Cikin shessheƙar kuka Abusufyan yashiga yi mata magiya yana roƙonta akan ta daina tsaga jikinta amma kamar yana tunzurata ne,   Saboda taurin kai da kafiya irin nata ko zafin rezar bata ji ajikinta,kafin yayi wani yunƙurin abu ta sanya rezar asaman wuyanta ta shiga tsarga wurin jini ya shiga bulbulowa,   A wannan lokacin ne abusufyan ya furta mata saki har ukku batare da saninshi ba,saboda tsoran karta kashe kanta,a gigice yace"ABU NA SAKE KI!NA SAKE KI!NA SAKE KI," 😭 Adai dai lokacin Hajiya da haris suka faɗo dakin kamar an jefo su,sakamakon Sautin ƙarar da abu ta saki da kuma kukan da abusufyan ya saki na fitar hayyaci,zubewa tayi saman gadon asume tana billayi saboda radaɗin rezar daya shigeta, Gaba daya suka rufar mata suna ambaton Sunanta suna tambayar meya faru,a lokacin shima abusufyan ya yanke jiki asaman gadon ya sume, Bayan wannan lokacin sai da abu tayi jinya agadon asibiti,inda Allah yaso rezar bata shiga cikin wuyan sosai ba amma ta tsaga fatar wurin sosai, Bayan an sallameta sun dawo gida anan fa suka hadu su duka a falon gidan don jin abunda ya haddasa faɗan daya shiga tsakaninsu,Zainab bata 6oye komai ba ta basu labari hada sakin da abusufyan yayi mata,hankali atashe Abusufyan ya shiga rantsuwar cewar shi bai sake ta ba,saboda baya acikin hayyacinshi baisan ya furta mata ba,gaba dayansu babu wanda baiyi takaicin faruwan wannan al'amarin ba,musamman mahaifinta baba buzu,tun daga ranar da aka sallameta daga asibiti ko kallonta bai ƙara yi ba,in ma tagaishe dashi bai amsawa,ta 6ata mashi rai sosai,bai ta6a tunanin abu zata aikata abunda ta aikata ba saboda kishi daya rufe mata idanunta, Abusufyan kuwa har ciwon zuciya sai da ya kusa kama shi a wannan lokacin,ba arziƙi hajiya Ameena tasa aka fitar dashi ƙasar turkey,wurin wata aminiyarta kuma abokiyar kasuwancinta,hajiya maimunatu dake zaune acan instanbul,a wurinta yaci gaba da zama,ta nisanta shi da nigeria ne saboda ta gusar da damuwar dake ƙoƙarin haddasa mashi Ciwon zuciya, Bayan abusufyan ya koma ƙasar turkey da sati guda kacal,sai ga sayyadi yazo yi ma Abu jajen mutuwar aurenta,tun abakin gate ɗin gidan baba buzu yayi mashi korar kare,wannan abun ba ƙaramin ƙona mashi rai yayi ba, Ana haka kuma abu ta koma yar gidan jiya,soyayyar sayyadi ta dawo sabuwa fal acikin ranta,ko bacci bata iyayi batare da tayi mafarkinshi ba,ko sallah takeyi sai ta dinga kawo zancenshi acikin zuciyarta,Tashin hankali,zuciyarta ta dinga azalzalarta akan son ta sanyashi acikin idanunta gashi an hanata fita ko nan da bakin gate bata iya zuwa saboda mahaifinta dake fushi da ita,da zarar ya ganta awaje zai nufeta afusace da nufin ya bugeta sai ta watsa da gudu ta koma ciki,hajiya da alhaji nuraddeen har haƙuri suka bashi akan komai ya wuce amma yaƙiyi,burinshi ya damƙeta a hannunshi yayi mata mugun bugu,don ya huce haushinta da yake ji,Abu ta ƙumsa mashi baƙin ciki sosai, Ana haka,wata rana ƙawar abu ta islamiyyarsu wadda suke kira da Maryam ta kawo mata ziyara acikin gidansu, A falo suka fara gaisawa dasu mommy kafin suka shiga cikin ɗakin abu,anan take sanar da ita cewa Sayyadine ya aiko ta a 6oye don ta kawo mata wayar da zasu dinga gaisawa dashi,'hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma abu ba, Nokia ce ƙarama maryam ta ciro daga cikin handbag dinta ta miƙa ma Abu,cike da farin ciki ta kar6i wayar,   Tafiyar maryam ke da wuya,sai ga kiran sayyadi ya shigo cikin wayar,jiki na rawa ta ɗaga kiran tare da yi mashi sallama,   ko amsa sallamar baiyi ba yace"Hmmmm abu kenan!yanzu kin tabbatar da abunda nake faɗa maki akan Abusufyan ko?ae tun farko saida naja kunnanki akan ki rabu dashi ba mutumin kirki bane amma kika ƙi jin maganata,' Abu tace"dan Allah mubar wannan maganar,ni ko sunanshi ma bana son ji,yanzu kaine araina,banda burin daya wuce muyi aure yanzu,dan Allah sayyadina ka turo gidanmu asanya ranar auranmu,'   Dariya sayyadi yayi kafin yace"kin manta da cewa idda kikeyi yanzu," Cike da damuwa abu tace"Nasani,amma ni bansan ya zanyi ba,so nake kawai mu kasance atare amatsayin ma'aurata,"   Shu'umin murmushi sayyadi ya saki aranshi yace"yarinya kinzo hannu,"   A fili kuma yace"yanzu ya za muyi abu?nikaina aƙagare nake da naga wannan lokacin,na ƙosa naganki amatsayin matata uwar ƴa'ƴana kuma,"   Suna cikin wayar yunƙurin amai yazo mata,da gudu ta miƙe tare da faɗawa cikin toilet wayar na ahannunta,ta karasa gaban fanfo tana kwarara aman,   Hankalin sayyadi ba ƙaramin tashi yayi ba,jin abu na amai,wannan ya tabbatar mashi da cewa Akwai Cikin abusufyan ajikinta,kuma muddin ya bayyana kowa ya sani babu shi babu abu,kafin ya cimma burinshi za'a ɗauki tsawon lokaci ne,   Kunna fanfon tayi,ruwa ya zubo ta ɗebo tana kuskure bakinta da ɗayan hannun,   Bayan ta kammala aman tadawo ɗakin a gefen gadon ta zauna sannan ta mayar da wayar a kunnanta tace"kayi hakuri sayyadina,wlh bana jin daɗin jikina ne,"   Muryarshi har kerma takeyi wurin cewa"Faɗamun Abu!kamarya kike ji ajikin ki"?   Abu tace"zuciyata ce ke tashi,ga wata irin kasala da nake ji.....'   Tun kafin ta ƙarasa maganar sayyadi ya katse ta da cewa"Abu!banason ki fada ma kowa yanayin da kike ji ajikin ki!kinji ko"?   Amsa mashi tayi da toh bazan faɗa ba,   Yaci gaba da cewa"Ni zanyi maki maganin lalurarki,addu'a kike buƙata,insha Allah yanzu bada jimawa ba,zaki ji sauƙi ajikinki,"   'Nagode sosai,"ta fadi kafin ta kashe wayar ta koma ta kwanta, Kafin wani lokaci abu ta daina jin tashin zuciyar da take ji,kasalar nan duk babu ita komai ya dawo mata dai dai,har abu ta kammala iddarta babu ciki ajikinta,kuma aranar data kammala iddar aranar sayyadi yazo neman auranta wurin baba buzu,tun abakin gate baba buzu yace"meya kawoka gidan nan!" Sayyadi yace"Naji cewa abu ta kammala iddarta,shine nazo neman auranta a wurinka,dan Allah kada ka hanani,tunda dae yarinyar nan ta nuna tana sona,kabarni kawai muyi auranmu,nayi maka alƙawarin zan kula maka da ƴarka,'   Wani irin kallo baba buzu yayi mashi kafin yace"har abada bazaka ta6a auran abuba,indai har nine ubanta,muddin ina numfashi bazan ta6a aura maka ita ba,"   Shu'umin murmushi sayyadi ya saki tare da jinjina kanshi yace"Idan kuma baka araye fa?ka isa ka hanani auranta?   Shiru baba buzu yayi yana kallonshi,dariya sayyadi yayi yana girgiza kai yace"shiyasa tun farko naso ace ka bini ta lalama ka auramun ita,amma saboda taurin kai da kafiya irin taka,yasa ka hanani auran abu,har marin abu kayi saboda ta sanya hannu ta mari abusufyan,sannan kayimun korar wulaƙanci saboda nazo wurin ƴarka,dama tara ka nake yi,yau zaka mutu baba buzu,kuma a sati mai zuwa zan auri abu,'_   Gabanshi ne yayi mugun bugu jin abunda sayyadi yace,nan take jikinshi ya shiga kerma yana rawa,wata irin zufa ce ta shiga gangarowa daga cikin ƙofofin hudar gashin jikinshi,   Muryarshi na kerma yace"Wanene kai!ka faɗamun!meyasa kake son abu,saboda me ka shiga rayuwarta!"   murmushi sayyadi ya saki tare da takawa ya matsa dab da Baba buzu suna fuskantar juna yace"Ni ba rayuwar zainab na shiga ba!rayuwar abusufyan nashiga,bansan zainab ba,abusufyan nasani!shisshiginka da bin ƙwaƙƙwafinka yau sun ja maka zaka rasa ranka baba buzu!kana tunanin cewa bansan bibiyata da kakeyi ba?don kawai kasan wanene ni!da wata manufa nake son ƴarka!shiyasa ba'ason mutun ya tsananta bincike wala tajassasu,da alama bakasan da hadisin ba,koda yake kaifa babu ilmin addini akanka.......'    Tunda sayyadi ya soma magana,baba buzu ya dinga jin tsigar jikinshi na tashi,tamkar ana tsige gashin jikinshi,nan take ya zube saman guiwarshi,idanunshi sukayi jawur muryarshi na rawa yace"Kada ka kashe ni,ka barni da raina!inason nasake ganin abu a idanuna,"   Fashewa da dariya sayyadi yayi tare da cewa"zaka iya ganin abu amma a lokacin da dukkan wasu kalaman bakinka suka daina aiki,ko uffan ba zaka iya furta mata ba,sae dai ka bita da ido kafin azare ranka,sannan kuma inaso nayi maka wani albishir baba buzu,Abu tana ɗauke da cikin Abusufyan,amma na 6oye hakan,zata haife shi ne acikin gidana kuma amatsayin ɗana.....'cike da shaƙiyanci sayyadi ke maganar,   Jin cewa abu nada ciki yasa baba buzu jin hawaye na sauka a idanunshi,dama yaji ma yana mamakin yadda akai babu ciki ajikin abu,ashe sayyadine ya kwantar da cikin don karsu gani su hanashi auranta,"   "Kaji tsoran Allah!kada ka cutar mun da ƴata!don Allah ka fita daga rayuwarta,wai lafin me mukayi maka ne?menene haɗinka da rayuwarmu,Ni da abu bamu ta6a cutar da kowa ba,mun taso mu biyu muke rayuwa bamu da kowa,Na roƙe ka akan ka ƙyale mun ƴa ta,koda zaka kashe ni amma kada ka ta6a abu,'   Bakomai zai baka mamaki ba face yadda ɗai-ɗaikun mutane ke giftawa a wurin amma babu wanda hankalinshi ke kaiwa wurinsu,hatta haris sai da yazo ya wuce ta gate ɗin gidan amma bai kai idonshi wurinsu ba,kuma wannan duk aikin sayyadine,    Juyawa sayyadi yayi ya nufi rugwagwar mashin ɗinshi dake ajiye inda yayi parking dinshi hawa yayi sannan yana kallon baba buzu yace"Zanyi amfani da abu ne don in ƙuntata rayuwar abusufyan,zan kuma yi amfani da yaron da abu zata haifa don in tarwatsa farin cikin zuri'arsu kamar yadda suka tarwatsa farin cikin namu family ɗin,nabarka lafiya,"yana ƙarasa maganar tashi ya tashi mashin ɗin da gudu yabar anguwar,   Barin unguwar tashi ke da wuya baba buzu ya yanke jiki ya faɗi,yana mirgina mirgina a ƙasa,kumfa na fitowa daga bakinshi,sai lokacin mutane suka dawo hayyacinsu suka lura da baba buzu dake kwance yana ta harba ƙafafunshi,   Lokaci guda mutane suka taru a kopar gidan sukayi dandazo suna kallonshi wasu na tambayar lafiya,wasu kuma nayi mashi addu'a,kafin su yanke shawarar kiran wani acikin gidan,    Koda aka sanarma su hajiya ameena abunda ke faruwa jiki na rawa suka kwaso gaba dayansu suka zo wajen gate din gidan,   Lokacin da abu tayi arba da mahaifinta dake kwance ƙasa yana ta birgima,zukunnawa tayi agabanshi tana jijjiga jikinshi tana faɗin'baba baba...meya faru dakai!baba dan Allah ka tashi....wayyo Allah na,nashiga uku......'haka ta dinga sambatu tana jijjiga,bawan Allah sai ƙoƙarin buɗe baki yake yi don ya sanar mata da cewa sayyadi ba mutumin kirki bane,kuma tana ɗauke da cikin abusufyan amma hakan ya faskara,anan dae rai yayi halinshi,baba buzu ya riga mu gidan gaskiya.........'   A ranar abu kamar ta zauce saboda tsabar tashin hankalin rashin mahaifinta da tayi,haka hajiya Ameena da alhaji babu wanda baiji mutuwarshi ba,sun jima suna tunanin menene yayi silar mutuwarshi amma basu gano hakan ba,kowa ranshi na bashi cewa kamar guba ce saboda wannan kumfar da bakinshi ke fitar wa, One week da rasuwarshi ko zaman makoki ba'a kammala ba,abu ta bijiro da maganar auran sayyadi,babu wanda baiji haushinta ba,don hajiya kamar ta rufe ta da bugu,a ƙarshe dae Alhaji nuraddeen ne ya goya mata baya,dama shi ya yarda da sayyadi kallon mutumin kirki yake yi mashi, Batare da 6ata lokaci ba,aka ɗaura auren abu da sayyad'    Kunji yadda akai Abu ta shiga gidan sayyad da cikin abusufyan,aurensu ko One month bai cika ba sai ga ciki ya bayyana ajikinta kuma cikin ba ƙarami ba,yayi watanni,nan fa mutane suka soma tsegumi akan cikin nata,abun ya ɗaure masu kai,aure ko wata baiyi ba ciki ya bayyana,dama ƙarami ne cikin da sauƙi,amma wannan cikin da girmanshi fa,ya haura 4 months, Tun zuwan da tayi gida,wurin Hajiya ameenatu don ta gaishe da ita,kallo daya hajiya tayi ma cikin nata,ranta ya bata cewa cikin abusufyan ne!duk da lokacin da suka rabu da abusufyan babu ciki ajikinta babu alamarshi, "Abu wannan cikin na jikin ki,kamar na abusufyan ne!raina yana bani haka,dama mutane na kawomin tsegumin cewa cikin jikinki yayi saurin girma daga yin aure ko wata baiyi ba sai  ya bayyana kuma da girma har haka"?   Tur6une fuska abu tayi tare da cewa"Mommy dan Allah kidaina maganar nan,taya za'ace cikin abusufyan ne?idan cikinshi ne meyasa bai bayyana ba tun lokacin da muna tare dashi,sai bayan watanni kuma har nayi aure sannan zai fito"?   Hajiya ameena tace"abu kenan,kika san ikon Allah?koda yake ba zanyi maki gardama ba,amma ni raina na bani cewa cikinshi ne,Amma zamu zuba ido muga lokacin da zaki haife shi,in har cikin nan yayi wata tara toh na sayyadine,amma in har kika haifeshi nan da 5 months,to na Abusufyan ne,'   Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Mommy nifa ba cikin abusufyan bane!na sayyadine,dan Allah mudaina maganar nan,'   Hajiya tace"naji zan bar maganar amma ina nan ina zuba ido,kuma in aka haifi yaron zamu je ayi mashi gwajin jini don a tabbatar da yaron wanene shi............'   Bayan abu ta koma gida cike da damuwar abunda mommy ta sanar mata,sayyadi na dawowa ta kwashe duk abunda suka tattauna ita da hajiyarsu ta sanar mashi,   Aikuwa tun daga ranar bakin mutane ya mutu murus,babu wanda ya ƙara tanka mata game da cikin dake a jikinta,abun ya ɗaure mata kai,sa6anin da da mutane ke tsegumin ta amma yanzu ko maganar cikin babu maiyi,   Kuma tun daga ranar Hajiya Ameena,ta fara samun ta6in hankali,na yawan mantuwa,yawan sambatu ita kaɗae da dai sauransu,a ƙarshe ma taji ta tsani zama a kano gaba ɗaya tamkar korarta ake,haka ta tattara ta koma katsina da zama,dama suna da katafaren gidansu acan wanda suka bari amma duk in suka zo garin a gidan suke zama,ita kaɗae ta koma gidan tana rayuwa acikinshi,tare da mai aikinta,kafin daga baya haris ya dawo wurinta,mahaifinsu kuma yana zuwa akai akai don ya dubasu, After 5 months A tsakar dare naƙuda ta taso ma abu,gashi ita kaɗae ce a gidan babu kowa,sayyadi bai dawo ba,dama wani lokacin in ya fita sai tsakar dare yake dawowa kamar aljani, Tun daga saman gadon ta faɗo ƙasa tana faman dafe cikinta tana cizon la66anta tana kuma ambaton sunan Allah abakinta,sosai cikin ya shiga murɗa mata tare da matsanancin ciwo. Daga ƙarshe ta zube anan wurin,bata tashi farkawa ba sai asaman gadon asibiti,kukan jariran da ta haifa ne suka tashe ta daga dogon baccin daya ɗauketa sakamakon allurar baccin da Dr yayi mata,a hankali ta buɗe idanunta ta ware su akan fuskar sayyadi dake tsaye hannunshi ɗauke da jariri naɗe acikin towel,murmushi ya sakar mata tare da cewa"Barka da sauka my wife,ina tayaki murna kin haifa mana kyawawan ƴa'ƴa," yunkurawa abu tayi ta miƙe daga zaune tana kallon yaran dake jere a gefenta guda biyu nade cikin towel ga kuma ɗaya a hannun sayyadi,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,saboda tsabar murna bakinta yaƙi rufuwa,muryarta na kerma tace"Wannan duk nawa ne?ƴa'ƴana ne ni kaɗai"? sayyadi yace"namu dae,naji kina cewa duk ƴa'ƴanki ne,bayan duk ƙoƙarin nawa ne,nakudarsu ne kawai kikayi,"cikin zolaya yayi mata maganar, Hannu tasa tare da daukar ɗaya daga cikin jariran ta buɗe fuskarta tana kallonta,gabanta ne taji ya faɗi rasss! ganin jaririyar na kama da Abusufyan,maimakon taga kamanninta kona sayyadi a fuskar yarinyar sai taga fuskar abusufyan, bin fuskarta da kallo sayyadi yayi ganin kamar tana cikin damuwa yace"meya faru ne?yanzu fa naga kina farin cikin samun ƴan uku,lokaci guda kuma naga kin canza? "Babu komai,"ta bashi amsa muryarta a kasalance, Haihuwar tazo mata cikin sauƙi,a ranar aka sallame ta,suka koma gida,bakomai yafi damun abu ba face yadda mutane suka ƙi zuwa yi mata barkan samun ƴan uku,ko leƙo gidanta babu wanda yayi,tayi tsammanin danginshi zasu zo amma abun mamaki babu wanda ya leƙo da sunan ɗan uwanshi yazo duba yaranta,jikinta yayi mugun sanyi,duk taji ta tsani kanta,amma daga ta kalli ƴan ukunta sai taji farin ciki aranta,suka dae ne dangin da take dasu aduniyar nan,su take gani taji daɗi aranta,lokacin da yaran suka kai wata ɗaya aduniya,aranar wata ƴar uwarshi tazo kawo mata ziyara,ita ta taimaka wurin yi mata wankan jego,da kuma yi ma yaran wanka,duk yadda abu taso taja ta da fira don taji a ina suke da zama suna da dangi,amma matar nan da shegen wayau ko uffan bata ce mata ba,a haka har suka kammala wankan jegon matar ta koma garinsu, Abu ba ƙaramar wahala tasha ba,wurin rainon ƴan ukunta,babu mai taimakonta,itace yi masu wanka har sau biyu arana safe da kuma dare in zata kwantar dasu,wankin kayansu da suka 6ata,ɗawainiyarsu da kuma ɗawainiyar kanta,abun duk ya jagule mata,ga sayyadi ko tsinke bai ta6a sanya hannu ya kawar mata ba,bayan kafin suyi aure shi da kanshi yake sanar da ita cewa in sukayi aure duk ranar da yake hutu bai aiki har girki sai yayi mata ashe duk ƙaryace yake yi mata,Abusufyan kuwa muddin yana agida bai barinta tayi aiki,sai dai yayi shi kaɗae ko kuma suyi atare,da kanshi yake cewa"Abuna idan har kika haifa mana ƴa'ƴa ni da kaina zan dinga yi masu wanka,idan mata ne zan dinga sharce masu gashin kansu ina gyara masu shi,bazan bari kisha wahala ba,'in ta tuna waɗannan kalaman nashi sai ta fashe da kuka,dama ita dana sani bata da daɗi,Allah ka rabamu da aikin dana sani,Amin Kunji yadda akai Abusufyan ya auri abu,da kuma yadda akai yabar nigeria da kuma yadda akai ta haifi ƴa'ƴanshi agidan wani wanda ya taso amatsayin ubansu, 💋Boss Bature💋 Lokacin da Abusufyan yakai ƙarshen labarin nashi sai ya fashe da matsanancin kuka kamar ƙaramin yaro,cikin sauri Abba ya janyoshi jikinshi yana lallashin shi,bashi kaɗae ba hatta su fawan,jabeer,irfan,khaleed dasu twins sai da idanunsu suka cicciko da kwalla,Sgr da Omar kuwa jinjina kai kawai sukeyi,Abbas ne yace"Yanzu ina ƴa'ƴan suke?suna raye ko sun mutu ne"? "Nima abunda nakeso na tambaya kenan,"acewar hajiya azeema da jikinta ya gama mutuwa,kowa mamakinshi ta yadda akai waɗannan abubuwan suka faru batare da Abusufyan da kuma goggon katsina sun sanar ma kowa ba, cikin sanyin murya Abba yace"ka faɗa mana ina ƴa'ƴan suke yanzu"? ɗagowa abusufyan yayi da idanunshi waɗanda sukayi jawur yace"ni kaina bazan iya cewa ga inda suke ba,a lokacin can baya ina bibiyar rayuwarsu,ta hanyar haris shiya kira ni a waya yake sanar dani cewa abu ta haifi ƴa'ƴa kuma yaran dani suke kama sosai,tun daga lokacin na sanya shi akan ya dinga bibiyar rayuwar yaran yana sanar dani duk wani abu dake faruwa arayuwarsu,shine yake turo mun da hotunansu ina ganinsu a wulakance,yara ne mata guda ukku wani lokacin babu kallabi a kawunansu kuma babu takalma a ƙafafunsu,tun lokacin nake tsananin jin tausayinsu,kuma raina yake bani cewa tabbas ƴa'ƴana ne su.....saboda akwai wani lokaci da nazo nigeria zuwan bazata batare da sanin kowa ba............." Bai ƙarasa maganar ba suka jiyo muryar goggon katsina tana sambatu tana cewa"ƙarfen nasara ba tabbas,Allah ka tsine ma baturen daya ƙirƙiri motar harisu,shegiyar motar kamar da katako akayita,tun safe muke a hanya take ta bamu matsala mtsswwwwww haba ina dalili,tafiya daga katsina zuwa abuja sai kace mutun zashi saudia a ƙasa?ae dana san haka zata faru da a kafa na tako wlh,shegen maƙo irin nashi,maimakon ya biya mana kuɗin jirgi,ya nace sai mun hau waccen rugwagwar motar tashi..........'kasa ƙarasa maganar tayi ganin yadda matasan gidan suka taru a falon gidan,ga kuma Abusufyan ɗinta dake ta faman sharar kwalla, Don bala'e,a hannu ta ruƙo zaninta daga ita sae dogon undi fari ajikinta,ta cire zanin gaba ɗaya,ranta ba ƙaramin 6aci yayi ba,da alama, Tsayawa tayi cak baki asake tace"Na shiga uku ni yau,abun dae ba sa'a,Allah yasa dae ba wani ya mutu ba,wlh yanzu inyi kwana in koma katsina don ni ban shirya ganin gawa ba,dan Allah ku faɗa mun maiya faru"? Miƙewa sukayi gaba dayansu suna kallonta cike da tuhuma,adaidai lokacin kuma Dr haris ya shigo tare da Saude,suma duk suka tsaya cirko-cirko ana kallon kallon, Koda Abusufyan yayi arba da goggon katsina,jiki na rawa ya tunkareta,tare da faɗawa jikinta ya rungumota sosai yana cigaba da kukan, Nan fa hankalin goggon katsina ya tashi,hannu bibbiyu tasa tare da ɗago da fuskarshi daga jikinta tana cewa"Abusufyan ɗina meya faru?meyasa kake kuka?kai da zanga kana farin ciki?ko Omar bai nuna maka ƴa'ƴanka bane.....? cike da mamaki kowa ya zuba ido yana kallonta,Abusufyan dake kuka nan take ya dakatar da kukan nashi yana cewa"Mommyna...ina abu take ne?ina yaran da ta haifa suke?suna ina? Bata bashi amsa ba,sae ta kalli Omar dake tsaye yana kallonsu tace"Omaru ina kakai mashi ƴa'ƴanshi ne?yaran nan fa da kazo dasu gidana ƴa'ƴan abusufyan dina ne dama saida na faɗa maka,dan Allah ku nuna mashi ƴa'ƴanshi ya gansu yaga yadda suka girma ko hankalinshi ya kwanta banson ganinshi yana kukan nan" Tashin hankali! Nan fa kowa ya ruɗe yana tunanin su wanene yaran da gwaggon katsina take magana akai, "Gwaggo kina nufin cewa hosana da jahad ƴa'ƴan abusufyan ne!"?Omar ne yayi mata tambayar fuskarshi ɗauke da mamaki, goggo tace"Eh mana,sune ƴa'ƴan abusufyan ɗina,suna ina ne.....' Kafin wani ya buɗe baki ya ƙara magana,sai ga Jahad da hosana sun fito da gudun gaske jin muryar gwaggon katsina data karade gidan,tana ganinsu ta washe baki tana cewa"Yawwwa ga ƴa'ƴan abusufyan ɗina nan sun ƙaraso,maza ku ƙaraso in rungume ku ajikina,' ƙarasawa sukayi tare da faɗawa jikinta,ta hada su duka ta rungume ajikinta,tana ta faman murmushi, Fawan ne yace"Anya gwaggo tasan me take cewa kuwa?taya waɗannan yaran zasu kasance Ƴa'ƴan uncle ɗinmu?hakan na nufin cewa Sehrish itama ƴar shi ce kuma,su jinin mu ne? Cikin sanyin murya abusufyan ya juya tare da kallon fawan da yayi maganar yace"Tabbas su ƴa'ƴana ne!nasan zakuyi kokwanton maganarta ne saboda tana da ta6in hankali,to inaso ku sani cewa mommyna tana acikin hayyacinta,tasan me takeyi duk da akwai ta6in hankalin atare da ita,amma ba kowane lokaci bane take kasancewa dashi ba,' Jin maganarshi yasa Hosana da jahad suka juyo suna kallonshi yayin da zuciyoyinsu ke cigaba da bugawa da ƙarfi da ƙarfi, Kowa fa ya shiga ruɗani,wasu ma saboda tsabar mamaki sun gaza magana,irin su Sgr da kuma su Jahan, "Yanzu duk ba wannan ba!dole muji ya akai kasan cewa su ɗin ƴa'ƴanka ne!kuma ya akai kuka bar rayuwarsu ta wulaƙanta batare da kun sanar mana ba!sannan dole muji ta bakin yaran game da irin ruƙon da wannan mutumin yayi masu!'acewar Abbansu junaid,ranshi a6ace yake maganar, Gwaggo dae bata gane inda zancen nasu ya dosa ba,amma tana da tabbacin cewar abusufyan ya fasa abunda suka jima suna 6oyewa,hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,dama ta gaji da 6oyon al'amarin da sukeyi,saboda ganin irin wahalar da yaran suke sha a hannun mugun mutumin nan, Omar yace"Abunda ya kamata shine,yanzu naga anata kiran sallar isha'e yakamata muje muyi sallah,kafin mu dawo nasan gwaggo ta ɗan rage gajiya,sai mu zauna ayita taƙare kawai,in yaso sai jahad tayi mana bayanin komai tunda itace mai cikakken hankali acikinsu,Sehrish ita kanta bana tunanin tana acikin hayyacinta yanzu, Kowa ya amince da maganar omar,batare da 6ata lokaci ba,suka wuje bedrooms ɗinsu domin yin alwala,hajiya azeema ce ta shigar da Gwaggon katsina cikin ɗakinta tare da saude kafin agyara masu inda zasu zauna, Yau dae gidan Abban sojoji a hargitse yake,Wlh ni kaina a hargitse nake,sai addu'a kawai, Abbansu na fitowa daga cikin toilet,junaid ya faɗo mashi acikin ranshi,nan fa gaban shi ya faɗi rasss,sae lokacin ya tuna da cewar babu junaid fa acikin gidan tun ɗazu,duk wannan budurin da akeyi babu shi acikinsu, Hankalinshi amatuƙar tashe ya tunkari wayarshi dake ajiye saman side drawer ya dauketa,tare da lalubo numbar junaid ya danna mashi kira cikin sa'a wayar tashiga tana ringing amma ba'a ɗaga ba,kusan sau huɗu yana kira ba'a ɗagawa, Ana biyar ɗinne aka ɗaga wayar,kara wayar yayi kunnanshi yana cewa"Junaid ina ka shiga ne!!"shiru yaji ba'a tanka mashi na,nan fa yabi ya rikice, "Junaid wai baka jina ina magana ne?bazaka amsa mun ba?junaid kodae wani abu ya faru da kaine? Nan ma shiru ba'a bashi amsa ba, Muryarshi tamkar zaiyi kuka ya kuma cewa"don Allah babyn Abbanshi kayi mun magana mana! Muryar mace ce ta amsa mashi da cewar"ka duba whatsapp ɗinka,zaka ga video mun tura maka," Jikinshi har kerma yakeyi wurin katse kiran ya shiga whatsapp ɗinshi,new number ya gani tayi mashi message da video, Saboda tsabar fargaba,tun kafin ya buɗe video ɗin zufa tashiga gangarowa a fuskarshi,dukkan ilahirin jikinshi ya shiga yin kerma,idanunshi sukayi jawur tsoranshi kar a videon yaga junaid cikin wani yanayi,bazai iya jurar wannan ba, Runtse idanunshi yayi yana karanto addu'o'i abakinshi,kafin daga bisani ya daure ya cije ya buɗe videon, Zazzare idanunshi yayi waje tamkar kwayar idanunshi zata faɗo ƙasa, A ƙarshe kuma ya fashe da dariya,tare da zubewa saman guiwowinshi yana tikar dariya, Bakomai bane acikin video ɗin nan ba,face Mommynsu junaid Alexandra rungume da junaid asaman gado,suna kwance abunsu,da alama ma kamar bacci yake yi ajikinta.......   *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari*, 😔 Abunda ya faru,lokacin da wata mata ta kira junaid da sunan mommynshi don yazo ya ɗauketa a airport,jiki na rawa junaid ya shige cikin motarshi ya kama hanyar zuwa airport bayan ya fita daga gidanne ya tuna da tace in ya fito ya sanar da ita,fiddo wayarsa yayi da niyyar kiranta,tunanin taya zai kirata ma ba number ya shiga yi,adaidai lokacin ta sake kira tambayarshi tayi ya fito ne,ya amsa mata da eh yana a akan hanyar zuwa,cigaba da tafiya yayi zuciyarshi cike fal da son ganin mommynshi,driving yake yi yana ayyana farkon haɗuwarshi da mommynsu baisan wani irin runguma zaiyi mata ba,yayi zurfi acikin tunaninshi kwatsam sae ga wasu jerin motoci sun kusa goma sha biyu,baƙaƙe kuma da black tinted,da gudun gaske suka nufo inda junaid yake,koda junaid ya lura da motocin nan fa hankalinshi yayi mugun tashi,ƙarasowarsu ke da wuya suka zagaye motar shi,yadda bazai iya kubce masu ba,nan fa hankalin junaid yayi mugun tashi,jikinshi ya shiga rawa,tsoranshi kar ace mutanen da mommy azeema ta sanar dashi cewa suna bibiyar rayuwarshi ne,zama yayi acikin motar hankali a matukar tashe, ɗaya daga cikin motocin aka buɗe,sae ga wani gabjejen mutun faffaɗan gaske sanye cikin suits,kai tsaye ya nufi motar junaid hannu yasa tare da knocking glass ɗin motar,zuge glass ɗin junaid yayi atsorace yana kallonsu sae faman haɗiyar yawu yake yi da kyar, kafin yayi wani yunƙuri Mutumin nan ya buɗe motar tashi,gaba ɗaya ya cakumi junaid ya toshe mashi baki,ya nufi cikin motarshi dashi,bayan ya sanyashi acikin motor,atare suka tashi motocin da gudun gaske suka bar wurin, junaid dake a back seat na motar tuni ido ya raina fata,hawaye suka shiga wanke mashi face ɗinshi,muryar shi tamkar zaiyi kuka yace"Su wanene ku?laifin me na aikata maku?dan Allah kada ku rabani da rai na,inason na sake ganin Abbana.....'bai kai ƙarshen maganar tashi ba,ɗaya daga cikinsu ya daka mashi tsawa tare da cewa"Shut up!ko tari ka ƙara yi saina fille maka kai," Jin haka yasa junaid yayi tsit zuciyarshi na bugawa da ƙarfi da ƙarfi, Wani katafaren gida suka shiga tare da shi,bayan sunyi parking ɗin motocin,ɗaya daga cikinsu ya buɗe motar tare da ɗauko junaid asaman kafaɗar shi,ya wuce dashi cikin gidan,a babban falon gidan ya sauke shi,sannan ya juya ya fuce, To fa,tsayawa junaid yayi cikin tashin hankali yake kallon haɗaɗɗen falon komai a gyare tsaf,tunani ya shiga yi mai yasa suka kawo shi nan suka ajiye shi?ko dae kidnapping ɗinshi sukayi ne?hannu yasa yana share hawayen shi,bai kammala wiping ɗinsu ba,yajiyo takun takalmi kwas kwas, A firgice ya ɗago don yaga wanene,zuba mata ido yayi yana kallonta,daga saman stairs take saukowa down,jikinta na sanye da doguwar riga fara mai shegen kyau tabi shape ɗin jikinta,ƙafafunta kuma na sanye da takalma high hills farare duk da tsayin da take dashi don sam ba gajera bace,ba ƙaramin kyau shigan tayi mata ba,kasancewarta farar fata,wuyanta na sanye da ziririyar sarƙa fara ta diamond,hannunta kuma na sanye da Zobe ɗaya kacal a middle finger,shima na diamond ne,ta ɗaure gashin kanta abaya,mai tsayi wanda launinsa yake tamkar golden yellow, A hankali ta ƙarasa saukowa daga saman benen,sannan ta tsaya tana kallonshi daga inda yake tsaye,duk da akwai tazara atsakaninsu amma suna iya ganin juna sosai,ƙare mashi kallo tashiga yi,burinta junaid ya fara shaida ita wacece kafin ta sanar mashi, hakanan ya dinga jin gabanshi na faɗuwa rass rasss,batare da jin tsoro ba ya tunkareta sai da ya kusa kaiwa inda take sannan ya tsaya yana kallonta,ƙwayar idanunta yabi da kallo blue colour wanda hakan ya tabbatar mashi da cewar mommynsu ce, dama kuma yasan ta a hoto,komai na fuskarta irin na Babban yayansu ne,duk da ta kwana biyu aduniya amma hakan bai 6oye kyawun fuskarta ba,tamkar ƴar shekara 30 haka fuskarta take,hatta jikinta yana nan yadda yake da kyau da kuma diri, A hankali junaid ya furta"Mommy!is you? jinjina mashi kai tayi alamar eh,da gudun gaske ya ƙarasa tare da faɗawa jikinta,sosai ya ƙankameta saboda tsabar farin ciki ya fashe mata da kuka,nan take itama kukan yazo mata atare suka shiga yin kukan babu mai lallashin wani,tamkar zasu haɗe jikin junansu su koma ɗaya haka suka ƙanƙame kansu,daƙyar Alexandra ta iya dakatar da kukan nata,ta sanya hannayenta tare da ɗago da fuskar junaid tana kallonshi,hawaye sun wanke mashi fuskarshi tass, muryarta na rawa ta ambaci sunan shi"Ro..meo.ɗina,' Cikin shessheƙar kuka junaid yace"Mommy,ashe zan sanyaki acikin idanuna,bansan da wasu kalmomin zan bayyana maki irin farin cikin da nake ciki ba,i luv u so much mom....' Jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,duk irin watsin da tayi dashi tabar Nigeria,hakan bai hana shi sonta ba, Kwantar dashi ta sake yi asaman ƙirjinta,ta sanya hannayenta tana ɗan bubbuga bayanshi,kafin ta mayar da hannunta ɗaya acikin sumar kanshi,ta jima tana mamakin girman shi,ta tafi ta barshi a lokacin da yake ɗan jinjiri dashi,amma yanzu tadawo ta same shi ya girma ya zama babba,ba ƙaramin farin ciki taji ba,mara misaltuwa, ɗago dashi ta kuma yi daga jikinta cikin sanyin murya tace"romeo ɗina,kayi haƙuri ka daina wannan kukan duk da nasan na farin cikin ganina ne,ni kaina bazan iya misalta farin cikin dana ji ba,wai yau ni ce tare da babyn dana bari yana jinjirinshi,ya girma ya zama babba,nayi danasanin tafiya nabarka romeo,nayi kewarka sosai,hakanan na raba kaina dakai,ba don bana sonka ba romeo,zan iya cewa nafi sonka fiye da kowa aduniyar nan.....na godema Allah daya nunamin wannan ranar....inaso na sake neman yafiya a wurinka saboda na cutar da rayuwarka sosai,ko wani yaro lokacin da yake jinjiri burinshi yaji dumin mahaifiyarshi,ya kasance atare da ita don samun kulawa daga gareta a koda yaushe,koda ace yana da uba,amma kai baka samu wannan gatancin ba,ka tashi hannun maza ba'a hannun mahaifiyarka ba,baka samu soyayyar nan ba,duk da mahaifinka yayi ƙoƙari sosai wurin gina rayuwarka tayi kyau,haka ƴan uwanka ma ba su bari ka zubar da hawayenka ba,amma duk da haka nasan abun ya jima yana maka Ciwo..." Tana ƙarasa maganar,ta zube saman guiwowinta agabanshi,tana roƙon yafiyarshi,hakan ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba,cikin sauri shima ya zube saman guiwowinshi suna fuskantar juna ita dashi, "Mommy dan Allah ki tashi,banason kina duƙamin,komai ya wuce yanzu tun da kin dawo wurinmu da ranki kuma da lafiyarki,har yanzu kina da sauran damar da zaki gyara kuskuren da kikayi abaya mommy," ashagwa6e ya ƙarasa maganar,murmushi ta saki tana kallonshi,ji take yi da tana da ikon da zata mayar dashi cikin cikinta,taƙara haifo shi da tayi,don kawai ta bashi wannan kulawar daya rasa, Sun jima a wannan yanayin,kafin daga bisani suka miƙe tare,ta ruƙo hannunshi cikin nata,ta wuce dashi upstairs ɗaya daga cikin bedrooms ɗin dake a wurin suka shiga,ɗakin ya haɗu sosai, "Mommy me yasa ba kije gidaba?wurinsu Abba su ganki? Yayi tambaryar yana kallonta, "I just came because of u junaid,inaso mu samu lokaci sosai atare,ka ganni dakyau nima na ganka da kyau,tun yanzu in fara aikina na baka kyakkwayar kulawa kamar jariri,in yaso gobe zamu shiga gidan da safe ko? Murmushin jin dadi junaid yayi tare da cewa"Eh,mommy,dama ni yakamata in fara ganinki tunda dama nine ban sanki ba a zahiri" "Bansani ba ko kana jin yunwa,amma zansa akawo mana abinci,in baka abaki kaci ka ƙoshi,yau dae atare da babyna zamu kwana,' Dariya junaid yayi,ba ƙaramin daɗin maganarta yaji ba,sosai mommynshi ta shiga bashi kulawa a wannan lokacin, Kunji yadda akai junaid ya kasance tare da mommynshi,har ta ɗauko ma Abbansu video ɗinsu saman gado ta tura mashi,abunda yasa kuma Abban bai gane Voice ɗinta ba,shine da kanta tayi amfani da wayarta wurin canza muryarta don ta tsoratar da Abbansu. 💋Boss Bature💋 fitowa Abbansu yayi daga cikin ɗakin nashi fuskar nan tashi awashe saboda tsabar farin cikin dawowar Alexandra,bakomai yafi faranta mashi rae ba face Junaid daya gani rungume ajikinta,yaji daɗi sosai,ko ba komai Junaid dae ya haɗu da mommynshi,hankalinshi zai ƙara kwanciya, Bai sanar masu da zuwan nata ba,saboda sunyi waya da ita ta sanar dashi cewar till tomorrow zasu shigo gidan don tana bukatar kasancewa da junaid don su kara fuskantar juna sosae,hakan yasa ya bari kawai sae goben sannan su ganta unexpected,duk da a kagare idanunshi suke da suyi tozali da ita. Gaba daya suka haɗu atare suka wuce masallaci, Jin shiru hayaam bata fito ba tsawon lokaci,yasa Azmee leƙawa ɗakinta,anan ta same ta zaune dirshan gefen gadon ta zabga uban tagumi,jin motsin mutun yasa ta ɗagowa fuskarnan a yamutse ta kalli azmee, "Hayaam wai dama duk budurin nan da akeyi acikin gidan nan kina ɗaki ƙumshe"? Jin abunda azmee tace yasa tace"hmmmm,to ina zani Aunty azmee?babban yaya ya kore ni daga gidan nan,nasan muddin na leƙa waje ya ganni sai yasa an kora ni daga gidan nan,' Cike da mamaki azmee tace"Subhanallahi!taya akai hakan ya faru?laifin me kika aikata mashi da har ya koreki daga gidan nan?shi da ma bai damu da mutane ba" ta6e baki hayaam tayi kafin tace"Ni banyi mashi laifin komai ba,Sehrish ce ta shiryamun makircin da yasa har ya kore ni,batare da nayi mashi laifin komai ba," Tunda tasoma magana azmee ke kallonta,ga rashin gaskiya nan ya bayyana ƙarara a fuskarta,taya akai ma Sgr yasan da zamanta da har zai kore ta?dole sai in itace tayi mashi shisshigin da yasa har ya ganeta kuma ya kore ta, "Allah ya kyauta toh,!yanzu ya zakiyi kenan?kinfa san halin shi!dole fa ki tattara kibar gidan nan!in ba haka ba wlh zaki fuskanci mummunan hukunci daga wurinshi,' Hankali tashe hayaam ta miƙe tsaye tana kallon Azmee tamkar za tayi kuka tace"don Allah aunty azmee ki taimaka mun,wlh banso in bar gidan nan!na saba da zama acikinshi,anan nake samun duk wani jin daɗin da nakeso,acan gidanmu duk babu waɗannan kayayyakin more rayuwar,nasan zaki taimaka mun," Dariya azmee tayi tana kallonta ko yaushe tazo da har zata ce tayi sabo da mutanen gidan ta ayyana a ranta, "Aunty azmee dan Allah ki taimaka mun,in xauna acikin gidan nan,nasan yana jin maganarki,ki roƙa mun shi akan yabar ni in cigaba da zama,wlh bazan ƙara shiga shirgin kowa ba,zanyi rayuwata cikin salama," Azmee tace"Tabɗijancan!so kike kija mun bala'e ko?ina zaman lafiyata agidan nan,Wacece ni?da har kike tunanin Sgr zaiji maganata?kin manta matsayina ne acikin gidan nan?kefa kike da alaƙa dasu ko kin manta ne"? Da biyu azmee tayi mata maganar saboda wulaƙancin da hayaam tayi mata, Magiya hayaam ta shiga yi mata tana roƙonta akan ta nema mata mafita tamkar zata zuƙunna mata saman guiwarta,don ita sam bata shirya barin gidan yanzu ba,tabb yo mima akai kenan"ta fada cikin ranta. Sosai abun yaba azmee dariya, "Hanya ɗaya ce hayaam in zaki iya!idan har kinason cigaba da zama acikin gidan nan"! jiki na rawa hayaam tace"Ina sauraronki aunty azmee,wlh koma manene zan iya ni," Azmee taci gaba da cewa"daga yau zaki dinga yin shigar maza,kinasa gashin baki kamar yadda sehrish tayi a lokacin da tafara aiki acikin gidan nan kinga sai kizama kamar sabon mai tayani aiki" Waro ido waje Hayaam tayi tare da cewa"Haba Aunty azmee ni zanyi shigar maza?so kike na ƙasƙantar da kaina har yarinyar can ta raina ni" Azmee tace"that's the only solution,if not sai dae fa ki tattara kayanki ki bar gidan nan!"ta karasa maganar tana jiran jin ta bakin hayaam din don tasan da kyar zata amince dama shiyasa ta fadi mata hakan, gyaɗa kai hayaam tayi tace"shikenan zanyi tunani in ga in zan iya,kafin nan zanci gaba da 6oye ma ganinshi" Azmee tace"to shikenan kiyi yadda kika ga yafi maki,ni dai gaskiya ba ruwana,kuma fa dole ki rika futowa kina taya ni aiki,indai kina a cikin gidan nan, don bazai yiwu ba ki zaune a daki baki komae gaskia " Hannu hayaam ta aza akanta tana faɗin"Nashiga uku! dariya Azmee tayi kafin ta kuma cewa"hayaam zamanki fa bazaiyiyu acikin gidan nan ba,Sgr ya riga da ya kore ki!muddin ya sake ganin fuskarki dole ya hukuntaki,kuma kinga gwaggonsu ta katsina tazo,!matar nan bazata ta6a bari ki zauna acikin gidan nan ba,in har taji cewa ke ƙanwar matar yayyansu ce,nan zaki ga tashin hankali,sae ta kunyataki acikin jama'a,shiyasa nace kiyi shigar maza kawai,Ni zan taimaka maki muna yin aiki atare inyaso duk wanda ya tambayeni xance mashi abokin aiki ne na samo,nasan babu wanda zai zargi wani abu, Komawa hayaam tayi ta zauna gefen gadon cike da damuwa,gaba ɗaya taji ta tsani kanta,da tana zaman lafiyarta acikin gidan,kwaɗayinta da zalamarta su suka ja mata,gashi ita gskia bata jin zata iya yin wani shigar maza wannan ai kaskanci ne, "Na manta ban sanar maki ba!" Rai a6ace hayaam tace"Menene!" Azmee tace"SEHRISH TAGA ƳAN UWANTA,ASHE ƳAN UKUNE SU,YANZU HAKA SUNA ACIKIN GIDAN NAN!BAKI GANSU BA,ABUN FARIN CIKI KAMANNINSU IRI ƊAYA SAK!BAKI TA6A BANBANTA SU," A razane Hayaam ta miƙe tsaye hannunta dafe da saitin zuciyarta tace"WAI DAGASKE AUNTY AZMEE? AZMEE TACE"Zan maki ƙarya ne?yaran suna nan,kyawawan gaske,HOSANA DA JAHAD!!!!!" Jiki amace hayaam ta koma ta zauna,gabanta na faɗuwa rasss rasss!tama rasa ina zata tsoma ranta taji dadi, Murmushi azmee ta saki tare da juyawa ta kama hanyar fita daga ɗakin,buɗe kopar tayi tare da sa kai ta fuce, Kamar jira take azmee ta fita,nan fa ta fashe da kuka kamar ranta zai fita,saboda tsabar 6acin rai,wani irin ƙululun baƙin ciki ne taji ya tokare mata maƙoshinta,komae ya jagule mata,tabbas tana bukatar tayi magana da Aunty laila,lokaci guda yadda sukai da yaya babbar ya shiga dawo mata, sambatu tashiga yi tana bugun bed mattress kamar wata zautacciya, Bayan kammala sallar isha'e,atare suka dawo cikin gidan,a babban falon suka kuma zama kamar ɗazu dae, Gyaran murya Abbansu yayi kafin yace"Ina yaran suke ne?wani yaje ya kira mana su,domin jin ta bakinsu" Miƙewa fawan yayi kamar dama jira yake yi,wucewa ɗakin sehrish yayi bayan ya isa ya kwankwasa masu ƙopa,jahad ce ta buɗe mashi kopar jikinta na sanye da hijabi da alama bata jima da kammala salla ba, Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Abba nason ganinku,idan ba damuwa ku fito mu tafi atare," Jahad tace"Toh,bari na kirasu,"ta fadi hakan tare da juyawa ciki ta kira hosana da sehrish wadda har lokacin bata motsaba,tana nan saman gadon ta ƙanƙame jikinta, "Hosana kuzo Abbansu na son ganinmu!hada sehrish kema ki taso," Maƙe kafaɗa sehrish tayi alamar bazata taso ba, "Sehrish dan Allah kidaina abunda kikeyi,nasan duk don saboda ganinmu ne,idan har baki so zuwanmu ba zamu bar gidan nan,"acewar jahad, ɗaure fuska Sehrish tayi tare da kawar da fuskarta gefe tana faman hura hanci, babu yadda basuyi ba akan sehrish tabiyo su amma taƙi binsu,har fawan sae da ya leko yayi mata magana amma ko kallo ma bai isheta ba, A ƙarshe suka ƙyaleta,suka bi bayan fawan ya shiga babban falon tare dasu, gaba daya hankalin kowa ya dawo kansu,musamman Abusufyan dake zaune agefen abbansu,ji yake kamar ya tashi ya rungumosu ajikinsa,su twins kuwa dasu irfan zuba masu ido kawai sukayi suna kallonsu,haka Omar da Abbas da kuma hajiya azeema,kowa burinshi yaran su tabbata ƴa'ƴan abusufyan ne,duk sun ƙagu suji cewa yaransa ne,tabbas da ba ƙaramin farin ciki zasu ji ba, Sgr dae tunda ya ɗago ya kallesu ya gane cewa babu sehrish acikinsu,bayan yaji cewar dukansu Abbansu yace a kira mashi, Abbansu ne yace"Ina ɗayar take ne?ni bana gane ma wacece babu acikin ku! Omar yace"waɗannan hosana da jahad ne!sehrish ce babu acikinsu," Abbas yace"Masha Allah,gaskiya banta6a ganin yara masu kamanni irin nasu ba,Allah dae yasa mu tabbatar da abunda muke hasashe akansu....' "Meya hanata zuwa"?muryar Sgr ce ta karaɗe kunnuwansu,har sae da su jahad suka ɗan tsorata dashi,dama tunda sukazo hankalinsu ke kanshi saboda launin kwayar idonshi ba ƙaramin ɗaukar hankali takeyi ba, Fawan yace"Ba yadda bamu yi da ita ba,amma tace bazata zo ba,kamar tana cikin damuwa sosai,ko kallona fa batayi ba,da naje kiransu,' A zafafe Sgr ya yunkura tare da miƙewa daga saman kujerar da yake ya nufi sashensu Azmee, "Kuzo ku xauna kusa dani,"hajiya azeema ce tayi masu magana yayin da takeyi masu nuni da hannunta, Hannunsu ruƙe cikin na juna,suka ƙarasa wurin sofa ɗin da hajiya azeema take,a gefenta suka zauna,duk jikinsu asanyaye saboda basu saba dasu ba,tunda suka zauna jahad ke kallon Abusufyan,saboda tunawa da maganar gwaggon katsina da tayi ɗazu na cewa shine mahaifinsu,kanta ya gama ɗaurewa,tashiga tambayar kanta taya akai hakan zata kasance?meke shirin faruwa da rayuwarsu ne?dama suna da dangi ne?wai su wanene su?ya akai rayuwarsu take a birkice ne? tambayoyi iri iri tashiga yi ma kanta waɗanda bata da amsar su, ƙasa ƙasa hosana tayi da muryarta tare da kai bakinta saitin kunnan jahad tace"Wancan mutumin sai kallonmu yake yi jahad,ni duk nabi na tsargu wlh,tsoranshi nake ji,shi da wannan kyakkyawan mai wasu kalar kwayar idanu kaman aljani....' "Dan Allah hosana ki daina mun magana a kunne na,wai ke bakya ganin mutanene kuma duk idanunsu na akanmu,ni kaina atsorace nake wlh,yaya Omar kaɗae nake kallo naji dan sauki,da ace baya a wurin nan da tuni na gudu...'jahad ce tayi wannan maganar,cikin raɗa tayi mata ita don kar aji su, A lokacin da Sgr ya ƙarasa bedroom dinta,tura ƙopar yayi tare da faɗawa ciki,tsayawa yayi yana kallonta,ta takure kanta,jikinta sae kerma yakeyi yayin da hawaye ke saukowa daga cikin idanunta,sam bata lura dashi ba har sae da yayi gyaran murya,a firgice ta wurga idanunta akan fuskarshi,gabanta ne taji ya faɗi rass,nan take kermar jikinta ya ƙaru sosai, "Taso muje"!babu wasa a fuskarshi yayi maganar,girgiza mashi kai tashiga yi tana cewa"bazan iya tafiya ba,ƙafafuna ciwo suke yi mun,dan Allah kuyi haƙuri ku ƙyaleni,inji da abunda ke damu na,' Abun ya ɗaure mashi kai,yadda take yi mashi jayayya,tabbas akwai matsala hakanan dae yarinyar bazata ƙi bin umarninshi ba, Bai tsaya wani 6ata lokaci ba,ya ƙarasa shiga cikin ɗakin har saman gadonta ya bita,sai faman ja da baya takeyi,gaba daya ya ɗaukota tare da azata asaman kafaɗarshi ya fito da ita,sai kuka takeyi mashi tana cewa ya sauketa ita bazata je ba,su rabu da rayuwarta,suna ƙuntata mata,har bugun bayanshi ta dinga yi da hannayenta don ya sauketa,duk yana jinta, tashin hankalin da ba'a sama shi date! "Ga babban yaya nan ɗauke da sehrish din daman nasan sai dae ya ɗaukota,"acewar fawan,jin sautin kukanta yasa kowa yakai hankalinshi wurinsu,abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yayi ba,ƙiri-ƙiri tana gudun ƴan uwanta,bayan duk alamu sun nuna cewa su ɗin fa ƴan ukune, Koda Sgr ya ƙaraso wurinsu, a tsakiyar inda kowannansu yake,sai ya sauko da ita,Kamar dama jira takeyi ya sauke ta ƙasa da gudu ta kama hanya zata bar wurin,aikuwa a zafafe ya damƙo waist ɗinta da ƙarfi ya maido ta jikinshi, Har Abbanshi na cewa"ka bi ta a hankali don Allah,ta tsorata sosai,bansan meke damunta bane, ko ƴan uwan nata ne ke batasan gani "abusufyan kuwa runtse idanunshi yayi,har cikin ranshi yake jin soyayyar yaran, Cikin shessheƙar kuka take faɗin"Na bani,na shiga uku!Na lalace!dan Allah ku rabu dani!ku barni na tafi, banason ganinsu!ni ba ƴan uwana bane!ciwon kai suke sani idan ina kallonsu,raɗaɗi nake ji acikin zuciyata kamar ana ƙonata...." Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba jin abunda sehrish ke cewa,yanayin yadda take maganar zai tabbatar maka da cewar da gaske take tana jin duk wani abu da ta faɗi,musamman Sgr daya ruƙota,yaji jikinta da wani irin Zafi,har shi kanshi zafin na shafar jikinshi, Abusufyan ne yace"kuyi mata addu'a don Allah,zai iya yiyuwa akwai sihiri ajikinta,wani zai iya shiga tsakaninta da ƴan uwanta saboda ni shaidane akan yadda suke son junansu!nagani da idona,basa rabuwa da junansu kullum suna manne da juna,banta6a ganin ƴan uwa masu son junansu ba irin yaran nan,tun kafin su mallaki hankalinsu suke tsananin son junansu.....' Cike da mamaki Abba yace"meyasa kake tunanin cewa akwai sihiri ajikinta? kowa ya kasa kunne yana sauraronshi, "In har da gaske sune ƴa'ƴana kamar yadda nake hasashe to tabbas an shiga tsakaninsu ne,saboda mutumin da suka taso awurinshi,nayi bincike akanshi,bama haka ba shi da kanshi ya rabani da bibiyar rayuwarsu da nake yi,kowa zaiyi mamakin taya nabar yaran rayuwarsu ta wulaƙanta batare dana taimaka ma rayuwarsu ba,ko kuma na sanar ma wani daga cikin dangina don a taimaki rayuwarsu,ba laifina bane tursasamun akayi........' Kasa ƙarasa maganar yayi saboda hawayen da suka shiga kwaranyowa daga cikin idanunshi, Abbas yace"Akwai sauran labari kenan, bari mu gyara zama don a idasa warware mana komai," ɗagowa yayi da idanunshi da suka yi jawur har sun dan fara kumbura ya kalli sgr tare da cewa"idan ba damuwa,inaso ka zauna tare da ita akusa dakai,saboda ka ruƙeta karta gudu,in yaso sai kayi mata addu'ar koda bata dawo hayyacinta ba,zataji sauƙin radaɗin ciwon kan da takeyi, "Okey,"ya amsa tare da samun wuri ya xauna,asaman laps ɗinshi ya zaunar da Sehrish,sosai ya ruƙota jikinshi,tunda ta kwantar da kanta asaman wide chest ɗinshi,numfashinta ya fara daidaita,a hankali kuma zafin jikinta ya soma raguwa,saitin kunnanta yakai ƙaramin bakinshi yana karanta mata addu'o'i,bugun zuciyarta ne ya soma raguwa,jikinta kuma ya rage kermar nan da yake yi, "Ina gwaggon take ne?naga bata fito ba inaso ayi komai agabanta tare da Dr haris kuma"abusufyan ne yayi maganar yana kallon Abban nasu Fawan ne ya kuma miƙewa tare da cewa"Bari naje na kirasu,' cike da zolaya jahan yace"Messenger,aikinka na kyau,"murmushi kawai yayi tare da wucewa ciki,ae yau ji yake kamar ya zuba ruwa ƙasa yasha don murna don kuwa ranshi ya gama bashi cewa su jahad din yan'uwansu ne. Ba da jimawa ba,sae ga Gwaggon katsina ta fito har yanzu undin nan ne ajikinta Allah ma yasa irin dogon nan ne mai kauri,tana biye da bayan fawan tana dungurin keyarshi tana cewa"Shegen bisa,da kanshi kamar na tamola,baccin ma baza abar mutun yayi ba,matsalar mutun yazo gidan jikoki kenan duk subi su addabi rayuwarshi.....' Muryar Abba ce ta katse ta da cewa"gwaggo ku samu wuri ku zauna,magana ce mai muhimmanci zamuyi," Har zata zauna idonta suka sauka karaf akan Sehrish dake zaune asaman laps ɗin Sgr,hankali tashe tace"mun shiga uku!yanzu agabanku ake wannan aika-aikar amma babu wanda ya tanka?hosana ce ko jahad?wacece acikinsu?wlh bazan bari a lalatamun ƴa'ƴan Abusufyan ɗina ba,dasu zamu koma katsina ayau.......' ..da sauri Haris ya katseta da cewa"Dan Allah gwaggo kidaina wannan sambatun naki,bakiji abunda abba yace ba!magana mai mahimmanci za'ayi,ki samu wuri ki zauna kuma kiyi shiru,' Wurga mashi harara tayi kafin ta wuce tare da samun wuri ta zauna,shima haris ya zauna agefenta,sai da suka xauna sannan ta lura da hosana da jahad dake zaune gefen hajiya azeema, Da sauri ta mayar da idonta kan sehrish don taga wacece ita,ko dae idanunta ne suka fara samun matsala don taga kamar kamanninsu iri ɗaya sak, "Harisu,kana ganin abunda nake gani kuwa,wai yaran nan har nawa ne masu fuska iri ɗaya"? A dan ƙule haris yace"Eh,su uku ne!ko kinmanta su nawa ne,na faɗa maku Abu ta haifa!wannan ae cikon ƴar ukun tasu ce,' "Oh to,yanzu nagane"ta fadi tana faman gyara zamanta, Sae da kowa ya natsu sannan abusufyan ya kalli su hosana da jahad yace"Ya sunan mahaifiyarku ne?kuma waye mahaifinku"? Yayi masu tambayar ne don ya fara tabbatar da cewar sune ɗin dai dagaske, Har suna haɗa baki wurin cewa"Sunanta Zainab,amma anace mata abu ƴar buzuwa,sannan mahaifinmu kuma sunanshi Sayyadi.......'tunkan taƙarasa maganar kowanne daga cikinsu ya shiga sakin murmushi,jin sun ambaci dai dai da sunayen da abusufyan ya gama bada labari akansu,tunkan aje ko ina suka tabbatar da cewar sune dae ƴa'ƴan abusufyan ɗinsu, "Ina mahaifiyarku take yanzu"?ya kuma tambayarsu, Jahad tace"bamu son inda take ba,amma koma a ina take bata acikin hayyacinta,lokacin da tabarmu tasamu ta6in hankali,' jiki asanyaye ta ƙarasa maganar, "Yanzu zaki iya bamu labarin abubuwan da suka faru arayuwarku gaba daya,har izuwa lokacin da kuka rabu da junanku"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh, Kafin abusufyan ya ƙara cewa wani abu,Abba ya katse mashi hanzarinshi da cewa"Yakamata,ka fara sanar dasu game da alaƙar da take tsakaninka da mahaifiyarsu" Jinjina kai abusufyan yayi kafin yace"zaku iya tunawa da mutumin daya ta6a zuwa wurinku lokacin kuna ƴan ƙanana,har ya ɗauke ku hoto a wayarshi?lokacin da zan tafi kuka dinga kuka kuna cewa na tafi daku baku son zama da mahaifinku"? A razane hosana da jahad suke kallonshi yayin da suke ƙoƙarin tunawa da wannan lokacin......' Murmushi abusufyan yayi tare da cewa"nasan ba zaku iya tunawa da wannan lokacin ba!,amma mun sha haɗuwa daku wani lokacin kuna ku kadae,wani lokacin kuma tare da mahaifiyarku........' Batare da 6ata lokaci ba,abusufyan ya basu labarin rayuwarshi da abu a takaice yadda zasu fahimta,sai lokacin suka san asalin mahaifinsu da kuma kakansu baba buzu daya rasu,da kuma irin rayuwar da abu tayi tare da abusufyan kafin su rabu,ta auri ya sayyadi,sunsha kuka sosai,aransu suna jin ƙuncin abunda mahaifiyarsu tayi masu,ashe duk itace taja masu bala'en da suka fuskanta, Kowa yayi shiru na wani lokaci suna sauraron kukan dasu hosana da jahad sukeyi gwanin ban tausai,banda sehrish wanda tayi lamo ajikin Sgr,duk wani abu da suke faɗi acikin kunnanta,amma bata ɗago ta kallesu ba,har yanzu dae bata dawo dai dai ba, Daƙyar su Omar suka lallashe su,kafin daga bisani Abbansu yace"Jahad yanzu ke muke sauraro!munaso muji irin rayuwar da kukayi a hannun mutumin nan!" Duk wannan abun dake faruwa akan kunnan Haroon,ya jima da shigowa batare da sanin kowa ba ya la6e yana jin labarin da abusufyan ke ba su jahad,na rayuwarshi da mahaifiyarsu,hankalin shi yayi mugun tashi,gaba ɗaya ya tsorata ya rikice,wata irin zufa ce tashiga gangarowa a fuskarshi,bakomai ya razanar dashi ba face ganin Ƴan ukun gaba ɗayansu sun haɗu acikin gidan kuma ga Ubansu da kanshi ya gane cewa ƴa'ƴanshi ne wannan alama ce dake nuna cewar asirinsu ya kusa tonuwa, Tuni zufa tasoma tsastsafo mashi acikin jikinshi,sharkaf ta jiƙa t shirt ɗin jikinshi duk kuwa da ba zafi,jan ƙafarshi yayi tare da lalla6awa cikin sanɗa ya wuce bedroom ɗinshi, Zagaye ya shiga yi acikin ɗakin,gaba ɗaya jikinshi sae faman rawa yakeyi,yama rasa inda zai tsoma kanshi kamar wani zautacce haka ya koma,a fusace ya dunƙule hannunshi tare da kai ma madubin ɗakin naushi,nan take glass ɗin jikinshi ya tsastsage ya zube ƙasa, Hannunshi ya shiga fitar da jini,ko kaɗan baiji xafin hakan ba,raɗaɗin da zuciyarshi ke yi mashi yafi raɗaɗin glass ɗin daya shige shi, Da ƙarfi ya furta"That's impossible!ƙaryane ba gaske bane!!wlh bazan rasa rayuwata ba!dole na rayu ko da kowa zai rasa ranshi,zanyi komai zan yi don ganin na kwaci kaina!! Yana magana yana sakin huci,idanuwan nan nashi sunyi jawur dasu luhu luhu, Cikin sauri ya zura hannunshi tare da ciro wayarshi daga cikin aljihun jeans dinshi ya danna ma wata number kira,cikin sa'a aka ɗaga kiran! Wata irin muryace ta karaɗe kunnanshi mai tsoratarwa"Ba saida nace maka karka sake kira na ba!Tun farko ya mukayi dakai? hankali atashe haroon yace"Ni ba wannan maganar tasa na kira ka ba!ka faɗamun taya akai kukayi gangancin barin yaran nan har suka haɗu da danginsu!!!!!!! "Wasu yara kenan!" Haroon yace"Ƴan ukun nan!na gansu da idona acikin gidan nan!yanzu haka gasu can a falon gidan nan sun taru suna jin labarin rayuwar yaran nan! Nan take muryar mutumin da suke waya dashi ta canza, "Wai kana nufin hosana!jahad!sehrish!duk sun haɗu anan cikin gidan naku ko mi"? A ƙule haroon yace"Eh mana!akansu nake magana,wlh kowa yayi ta kanshi!saboda yarinyar nan dole ta ambaci sunanka acikin labarin da zata bayar kuma kasan cewa muddin waɗannan namun dawan guda biyu sukaji mugayen abubuwan da kuka aikata dole su binciko ka duk inda ka shiga kuwa,kuma koda a ƙarƙashin ƙasa ka 6oye,! Fashewa da dariya mutumin yayi kafin ya tsagaita da yin dariyar yace"Baza su ta6a iya gano ni ba!nafi ƙarfinsu nesa ba kusa ba!zanyi amfani da ƙarfin sihirina wurin dakatar da tunaninsu.......' Tun kan ya ƙarasa maganar haroon ya daka mashi tsawa tare da cewa"Ya Isa haka!!zancen ku iri ɗaya da ita!daga kai har ita daga anyi magana sai kuce ƙarfin sihiri,zakuyi amfani da sihiri ku asirce mutun!angaya maku cewa kowane lokaci sihiri ke yin tasiri ne!sam babu Allah aran kowannanku don haka babu wanda zai tsira acikinmu!ko ka manta da irin mutuwar da mahaifinku yayi ne?duk wani sihiri da kuke taƙama dashi ae a wurinshi kuka gado shi,akan idon kowannanku yayi mummunar mutuwa sakamakon farmakar shi da kakanmu salahuddeen sukayi,ku baku da tunani ne?me yasa shi a lokacin baiyi amfani da ƙarfin sihirin shi ba don ya hana kanshi mutuwa?ko don saboda ya tsufa ne yasa nashi sihirin baiyi aiki bane? Gaba daya haroon ya rufe shi da faɗa ta inda yake shiga batanan yake fita ba,ba don komai ba sai don saboda yasan cewa bazai kai labari ba,sun ja mashi bala'e da masifa, Wata irin gigitacciyar tsawa mutumin ya daka mashi wadda tayi silar dawowarshi cikin hayyacinshi,yayi tsit yana faman sauke ajiyar zuciya, "haroon!ya kamata ka iya bakinka!kasan dawa kake magana!duk wannan tada jijiyoyin wuyan da kakeyi bazai hana kaga mutuwarka ba!zaifi kyau ka mayar da hankali wurin ganin ka sama ma kanka abokan tafiya,kada ka yarda wannan abun ya tayar maka da hankalinka,babu wanda ya isa ya ta6a ka acikinsu,!abu ɗaya kawai mukeso awurinka!muddin ka aikata hakan komai yazo ƙarshe zaka tsira kuma muma zamu tsira,sannan farin cikin gidansu zai tarwatse na har abada,......................' Natsuwa haroon yayi yana sauraron bayanan da mutumin yake kora mashi,sae amsa mashi yake yi da to,toh Alamar ya amince da abunda suke so ya akaitan, Acan main palour ɗin kuwa,kowa ya kasa kunne yana sauraron Jahad, **** *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.      *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari*, 2 pages ne hada na monday *CIGABAN LABARI* Abu ba ƙaramar wahala tasha ba a hannun Ya sayyadi,daga ita har yaran bai raga masu ba,tun yana 6oye mata mugayen halayenshi,har ya fara bayyana mata su,babban tashin hankalin da ta fara fuskanta a wurinshi shine shigo mata da Manyan Alhazan da yake yi acikin gidansu,in suka shiga ɗaki sai suyi fiye da 6hrs basu fito ba,wani sa'in har gurnani take ji ya cika gidan tamkar namun dawa na yaƙi,wannan abun ba ƙaramin razanar da ita yake yi ba,kuma duk in ta tambayeshi me suke zuwa yi a wurinshi sai yace mata *Wala tajassasu*kuma ta tsaya a iya matsayinta kar tace zatayi mashi shisshigi irin na mahaifinta,tarasa uban me sukeyi acikin ɗakin,abun ba ƙaramin damunta yake yi ba,tun tana iya jurewa har dae wata rana ta yi masu la6e a window ɗin ɗakin shi,a ranar abu taga tashin hankalin da bata ta6a gani ba da idonta tunda uwarta ta haife ta,wani irin yunƙurin amai ne yazo mata da gudun gaske tabar leƙen sun da takeyi ta koma bakin fanfo tana kwarara amai tamkar ƴan hanjin cikinta zasu fito,agaban fanfon ta zuƙunna tare da fashewa da kuka,ta dafe kanta da hannunta saboda raɗaɗin da yake yi mata,gaba ɗaya rayuwarta ta shiga ƙunci taji ta tsani kanta,kamar ta kashe kanta haka ta dinga ji a lokacin, ta jima abakin fanfon kafin ta koma cikin ɗakinta,a lokacin triplets ɗinta suna kwance sae sharar bacci sukeyi,komawa tayi daga gefen gadon ta zauna tare da ɗan russinawa dai dai saitin fuskokinsu tana kallonsu,yadda suke sharar baccin su zai tabbatar maka da cewar suna cikin kwanciyar hankali,tasa su gaba tayi tana faman shessheƙar kuka muryarta na rawa ta dinga cewa"Na cuci kaina!Kuma nacuci rayuwar ƴa'ƴana,Haƙƙin mahaifina kadae bazai ƙyale ni ba,na bijire mashi na ƙuntata mashi duk don saboda in auri sayyadi,haƙiƙa na tafka babban kuskuren da bazan ta6a gyarashi ba,Ni duk a zato na kowane mutun daya iya jan ayar kur'ani ya fassarata kuma yayi wa'azi abainar jama'a,mutumin kirki ne bai aikata zunubi tsarkakakke ne shi,ashe ba haka bane,ko acikin malaman akwai nagari akwai kuma na banza,wanda suke amfani da iliminsu na addini don su cutar da mutane,Mommy saida ta gargaɗe ni akan hakan amma na bijire mata saboda na makance akan soyayyar sayyadi,Ni ban tsaya nayi bincike akan rayuwarshi ba,kawai natashi na aure shi,kuma na ƙuntata ma mahaifina duk don saboda shi,na kuma ƙuntatama Mijina mai sona da gaskiya,wlh na cuci rayuwata....!kaicona.......' Sosai abu ke shassheƙar kukan,sautin kukan da takeyi ne ya farkar da Sehrish sai faman mutsustsuka idanunta takeyi da hannayenta,hannu abu takai tare da ɗauko ta,ta zaunar da ita asaman cinyoyinta,shafa fuskarta tayi tare da cewa"Rishina kin farka?kina jin yunwa ne"?   A hankali ta ware kyawawan idanuwanta akan fuskar mahaifiyarsu,koda taga hawaye na zuba a idanun oumman tasu,sae ta sanya tafin hannunta tana share mata su tana cewa"oum ki daina,banasho,nima inyi kuka,'tayi maganar da hausarta ta ƴan koyon magana,hada ta6e la66anta zatayi kuka, Hakan da tayi yasa abu ta fashe da dariyar karfin hali tana kallonta,kwantar da kanta tayi asaman ƙirjinta tana shafa sumar kanta tace"na tambayeki kina jin yunwa baki faɗa mun ba,' Cikin shagwa6a tace"inaji,amma tare dashu usana da johad anci.  '   Abu tace"shikenan,bari mu jira su farka daga baccin sai in dafa maku ko indomie ce kuci,bayan kun gama ci sai inyi maku wanka,in shafa maku mai in canza maku kaya sannan in kaiku gidan maman sadeeq ku tayata fira,kina son zuwa ko?   Inasho,ta bata amsa, Suna cikin yin fira da ita sai ga sayyadi ya faɗo cikin ɗakin nata,tana ganinshi gabanta ya faɗi rass don yanzu yafi yi mata kama da ibliss,   Yadda ya nufo ta a fusace yasa tayi saurin sauke sehrish daga jikinta ta miƙe tsaye tana kallonshi fuskarta da alamun tsoro, Nuna ta yayi da hannunshi yana huci yace"Abu!uban me ya kaiki yin la6e aɗakin can!angaya maki banganki bane?duk wani motsin ki acikin gidan nan,acikin kunne na nake jinshi,basai da na faɗa maki cewa kada ki tsananta bincike akaina ba!   duk da tsoranshi da take ji hakan bai hanata tanka mashi ba, "Saboda baka da gaskiya shiyasa ka hana inyi bincike akanka!yau naga komai da idanuna ashe kai ba sayyadi bane!baƙin shaiɗan ne wanda ke 6oye mugayen halayansa!wlh nayi danasanin auranka sayyadi yafi sau aƙirga,banta6a sanin cewa kai dabba bane sae yau!wlh sai ka sake ni don bazan iya cigaba da zama da fasiƙin mutun irinka ba......'   Tunkan ta ƙarasa maganar sayyad ya fashe da dariya hada dafe cikinshi,abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,shiru tayi tana kallonshi,   Sai da ya gama tiƙar dariyarshi sannan ya sassauta muryarshi tamkar zai lallashe ta yace"My wife,yau da bakinki kike jifana da waɗannan munanan kalaman?nifa ne sayyadin nan naki da kika kwallafa rai akai,ban wani canza ba,'tundaga kan yadda yake yi mata magana ta gane cewa ba karamin gogaggen ɗan bariki ba ne,ya kware wurin iya sarrafa harshe dama da irin kalaman nan nashi ya yaudareta tun farko,in yazo zance ya tsareta da idanunshi yana yi mata nasiha,   daƙyar ta iya haɗiye miyan dake bakinta,cikin sanyin murya tace"Kaji tsoran Allah!meyasa kayi amfani da ilmin da kake dashi na addini wurin cutar da rayuwata?saboda kasan cewa inason malamin addini mahaddacin al'qur'ani shiyasa ka biyomin ta wannan sigar don ka yaudare ni,laifin me nayi maka da har na cancanci hakan a wurinka"?   shu'umin murmushin nan nashi ya saki kafin yace"Ae malaman ma suna muka tara!abu kinyi kuskuren yadda da cewar kowane malamin addini mutumin kirki ne,wasu malam ne nagaske wasu kuma suna yin amfani da maluntar tasu da wata manufa don su Cimma burinsu kamar ni kenan!saboda kawai kin ganni malami ina yin shigar mutunci in yi wa'azi in janyo aya in fassara gani kuma mahaddacin kur'ani sai akace maki ni mutumin kirki ne?An rubuta a goshi na ne?me yasa kuke yin believing da abunda idanuwanku suka gwada maku ne?duk wani ɗan adam da kika sani aduniyar nan bai da tabbas!duk yadda kikaso ki gane mutun na gari kona banza abun zaiyi matuƙar wuya agare ki,saboda akwai masu fuska biyu,zaki ga mutumin banza yana aikata abunda yaga dama agaban kowa baijin kunyar kowa zai aikata zina zaiyi sata,zai zalunci wani zai sha giya,zai yi kaza yayi kaza,kinga shi wannan ya bayyana asalin suffarshi,wani kuwa zaki ganshi babban malami ne mahaddacin al'qur'ani wanda ya saba wa'azi agaban dubban jama'a yana faɗakar dasu cewa suji tsoran Allah kar suyi kaza idan sukayi kaza zasu shiga wuta idan sukayi kaza kuma zasu shiga Aljanna,idan kika bincika kuma wannan malamin ɗabi'unsa da halayansa iri ɗaya ne dana wannan mutumin dana fara kwatanta maki!amma shi bai bayyana suffarshi ta asali ba,yazo da sigar maluntaka don ya cimma wata manufa tashi ta hanyar yin amfani da ilmin addinin da yake dashi,wani kuma zaki ga malamin ne nagaske akwai ilmin addinin Akanshi amma baki ta6a ganewa, kamar dae Abusufyan yaron kirki,abusufyan tun yana da shekara sha wani abu aduniya ya haddace al'qur'ani mai girma tare da manya manyan littattafai na addini,amma ya ɗabi'unsa da halayansa suke?babu mai iya gane cewa yana da ilmin addini akanshi indae ba anyi mu'amala dashi ba,saboda irin rayuwar daya taso yanayi,abota da mata da kuma rashin kunya baijin kunyar furta kalami abakinsa ko gaban wanene 6arota kawai yake yi,kowa zaiyi tunanin cewa shi jahilin addini ne ashe ba haka bane,yasan me yakeyi kuma yana da kyakkyawar zuciya ba kamar sayyadi ba, *dawa zamu yadda aduniyar nan?lalube kawai mukeyi acikin duhu,musamman zamanin nan da muke ciki,Zaiyi wuya ka gane mutun na gari dana banza,shiyasa da yawa mata muke shan wahala wurin neman miji na gari da zamuyi rayuwa dashi,tunda bamu da tabbas akansu Mazan!haka matan ma bamu da tabbas mu kanmu,da mazan da matan wahala kowa ke sha wurin neman righteous life partners,A ƙarshe nidae shawarar da zan ba mutun shine ya dage da addu'a kawai,sannan ya gyara rayuwarshi in ma akwai wani kuskuren da yake aikatawa ko min ƙankantarshi,saboda da yawa wasu abubuwan wlh mu muke ja ma kanmu batare da mun sani ba,muyi ta ganin ba dai dai ba arayuwarmu,dole sai mun gyara sannan zamu ga dai dai mu kanmu,Allah yasa mu dace,Amin. Haƙiƙa su Sehrish sunga rayuwa fiye da tunanin mai tunani,uƙuba babu irin wadda basu sha ba a hannun mutumin nan,tun kafin su mallaki hankalinsu suke jin wannan sautin abun da mahaifinsu ke aikata shi da manyan alhazawan nan dake kawo mashi ziyara,abun ba ƙaramin tsoratar dasu yake yi ba,duk subi su gigice,babu yadda abu batayi ba akan ya daina shigo mata dasu cikin gidan amma ko ajikinshi,in ma ta takura mashi sai ya kwatseta da cewa ae gidan bana Ubanta bane,da kuɗinshi ya siyi gidan, Abu har ya fara affecting ɗinsu sehrish daga sunji gurnanin nan sai subi su gigice su firgice suna yi mata kuka suna cewa Oumma dodo,dodo,ta rasa yadda zatayi dasu baiwar Allah,ƙarshe ta dinga kaisu gidan makwabciyarta suna yini acan wani sa'en ma har kwana suke yi agidanta, Lokacin da Sayyadi ya gane hakan,ba ƙaramin faɗa yayi mata ba akan tadaina kai mashi ƴa'ƴanshi gidan makwabtansu,dama basu shiri da Mijin maman sadeeq,shima malamine sosai amma malamin gaske ba irin sayyadi ba,shiyasa ya tsane shi,saboda ya sanya mashi ido sosai akan lamurran rayuwarshi duk da bai ta6a tarar shi da sunan zaiyi mashi magana ba,babu wanda ke tanka ma wani acikinsu,ƙaryace ta haɗu da gaskiya,kuma a makarantar islamiyya ɗaya suke koyarwa,tun lokacin da sayyadi ke tarayya da abu,sae da ya ta6a kiranta ya gargaɗeta akan ta daina kulashi,su kansu basu san asalinshi ba,kuma basu yadda dashi ba acikin malaman makarantar amma abu taƙi jin maganarshi saboda ta makance akan son shi,maganin marasa jin maganar malamansu kenan da kuma iyayensu kai harma da mazajansu,babu wanda acikinsu bai ja mata kunne ba amma tayi kunnan uwar shaggu dasu ita ga Juliet,yanzu dae ga romeo nan yana ta gasa mata aya a hannu,duk da dae akwai aikin sihiri,Allah ya kara karemu da kariyarsa,Amin A kwana a tashi babu wuya wurin Allah su Sehrish suka kai shekara 5 a duniya,daga lokacin ne fa sayyadi ya fara sanya masu ido saboda kyawunsu dake fusgarshi,nan fa ya fara saƙa wani abu aranshi, Wani sabon salo ya 6ullo mata dashi,na horon yunwa kwata kwata yadaina kawo masu abinci acikin gidan,yaran suyita fama da yunwa,wani lokacin kamar zasu rasa ransu in suka fara billayi suna kuka,hankalinta yabi ya tashi ta rasa inda zata tsoma ranta taji daɗi,gashi bata da kuɗi bata da hanyar da zata same su balle tace zata ɗauki nauyin ciyar dasu,kamar maroƙiya haka ta koma bi gida gida na makwabtansu akansu ƴan mata abinci taba yaranta,tun tana samu suna ɗan mata har aka fara tseguminta abayan idonta,tun suna gulmarta a6oye har aka farayi agabanta,ƙarshe ma da zarar su sehrish sun leƙa kopar gida za'a fara gulmarsu ana cewa ga ƴa'ƴan abu almajira nan sun fito,haka zasu koma sunayi mata kuka,saboda tsokanarsu da akeyi,har jan gashin kansu akeyi ayita dungurin goshinsu,gaba daya mutane suka ɗauki karan tsana suka ɗaurama yaran,duk irin kyan dake garesu,kowa ya daina taimakonsu,bakomai yafi ɗaga ma abu hankali ba face yadda mutane suka tsani ƴa'ƴanta,babu damar su fita waje da sunan zasuyi wasa cikin ƴan uwansu yara sai ta gansu sun watso da gudu cikin gidan suna kuka,haka zata haɗasu a ƙirjinta ta rungumesu tana kuka,duk wannan abun dake faruwa sayyadi yana sane saboda shine silar komai dake faruwa dasu, Gaba ɗaya kowa ya ɗauki karan tsana ya ɗaura masu,mutun biyu ne kaɗae suke tausayin rayuwarsu,Maman sadeeq da kuma Mijinta,kullum cikin tausaya masu sukeyi,a kullum su hosana suka shiga gidan yunwa ta koro su,ita ke zama ta girka masu abinci,har ta kaiga in zatayi girki tare dasu take auna abincin don tasan zasu zo nema ne,ita kaɗae ce take kwantar ma abu da hankali, A ƙarshe dae da abun ya fara yi mata yawa da kanta ta tunkari sayyadi a ɗakinshi lokacin yana a gida baije aiki ba,tunda ta shigo ɗakin ya ɗaure fuskarshi yana daga kishingiɗe saman gadonshi, Wuri tasamu daga gefe ta zauna ta gaishe shi daƙyar ya amsa mata ma,yadda kasan auren ƙiyayya sukayi dashi, "Meyasa kake barin mu da yunwa baka ajiye mana abinci acikin gidan nan yanzu? ta6e bakinshi yayi tare da cewa"Yaushe rabon da kiban haƙƙina na aure?hakanan zan zauna ina ciyar dake da ƴa'ƴanki ne saboda haihuwata kukayi? "Allah ya kiyaye in ƙara haɗa shimfiɗa dakai sayyad!rashin sani ne yasa ko lokacin baya nake baka haɗin kai,amma yanzu nagane ko kai wanene.... ' Murmushi ya saki yana kallonta batare da ya ƙara tanka mata ba, Cigaba da magana tayi"bai kamata laifina ya shafe su ba,su fa ƴa'ƴanka ne jininka ne!meyasa zakayi masu horon yunwa saboda laifin da nina maka?haba sayyad sai kace ba ƴa'ƴanka ba?akan idonka ake wulaƙantasu amma ko ajikinka,narasa gane wannan abun.........'takaici ne yasa ta kasa ƙarasa maganar ta fashe mashi da kuka,cikin shessheƙar kuka taci gaba da cewa"tun da na haifi yaran baka ta6a nuna masu soyayya irin ta mahaifi ba,tun satin farko da suka zo duniya,ko ɗaukarsu bakason yi,me yasa dan Allah?kayan sawar su ma duk sun tsufa sunyi masu kaɗan,amma baka ta6a ɗaukar ko fallan atampha ba wannan kace gashi a ɗinka masu,wai kai wani irin mutun ne!? Da buɗar bakinshi sai cewa yayi"Dabba!" Shiru abu tayi tana kallonshi kamar ta rufe shi da duka haka take ji,   "Ko kin manta munanan kalaman da kika jefe ni dasu ne?da bakinki fa kika kirani da sunan dabba,"   "Dan Allah to kayi hakuri komai ya wuce,ni so nake kawai ka daina yi mana horon yunwa ko dan saboda yaran nan,koda ace ni ba zaka bani ba,su yara ne basu san komai ba,ba zasu iya jurar yunwa ba,sannan kuma ya kamata ka sanyasu makaranta tunda bakinsu yafara buɗewa sosai suna magana,"ba don taso ba haka ta dinga lallashi akan ya taimaki yaran,   Sai da ya mula ya sha iska sannan yace"ni bazan iya ɗaukar nauyin karatunsu ba,saboda ni ban fito gidan arziƙi ba kamar Abusufyan,kinsan cewa Ni malamin makaranta ne,makarantar ma ta islamiyya,salary ɗina bai wuci 20k ba,idan har kinason kula da yaranki ki tashi tsaye ki nemi kuɗinki mana,'   Fuskarta ɗauke da damuwa tace"Meyasa zakayi mun haka sayyad!idan kasan cewa ba zaka iya ɗaukar nauyin su ba,meyasa ka bari na haifesu....   '   Yunƙurawa yayi tare da miƙewa yabar mata ɗakin yana faman buga tsoki,ta jima zaune jugum aɗakin nashi,kafin ta miƙe ta koma bedroom ɗinta,zirga zirga tashiga yi tana neman mafitar yadda zata samu kuɗi don ta tallafama rayuwarsu,bakowa bane ya faɗo mata aranta ba face Ya haris,tana da tabbacin cewa in yaji halin da take ciki zasu iya taimaka mata duk da tana jin kunyar tunkararsu amman bata da wata mafitar data wuce wnn,addu'a ta shiga yi Allah yasa har yanzu da number shi data sani yake amfani, Da wayar makwabciyarta tayi amfani wurin kiran Haris,cikin sa'a ta shiga,lokacin daya ɗaga kiran taji muryarshi sai ta fashe mashi da kuka,nan fa hankalinshi ya tashi ya shiga tambayarta ko lpy,bata 6oye mashi komai ba,game da halin rayuwar da suke ciki ita da ya'yanta,haris yayi mata al'ƙawarin zai taimaka masu,su bashi lokaci, Bayan wasu ƴan kwanaki haris yayi mata aiken kuɗi masu yawa,dasu tayi amfani wurin nema masu makarantar boko da kuma islamiyya,wani lokacin har zama takeyi da kanta ta koya masu karatu,sun ɗan samu sauƙi a wannan lokacin kafin sayyadi ya sake ƙunsa masu wani baƙin cikin,ya kwashe mata Sehrish da jahad 6at aka neme su aka rasa,kamar abu zata yi hauka wurin nemansu,ashe zuwa yayi ya saida ma ƙungiyarsu yaran don suyi amfani dasu,shi kuma suka bashi makudan kuɗi,Mijin maman sadeeq ne ya tona mashi asiri a wurinta,saboda yaga lokacin daya gudu da yaran a 6oye ya tafi dasu,ranar kaca kaca sukayi dashi har bugunta sai da yayi saboda shaƙo kwalar rigarshi da tayi tana jifanshi da munanan kalamai,a ƙarshe tace zata haɗa shi da Allah in bai dawo mata da ƴa'ƴanta ba,tun daga ranar ta fara sallar dare tana kai kukanta wurin Allah,duk yadda sayyadi yaso ya juye mata tunani akan ta daina ibadar nan amma abun yaci tura,ko yayi nufin yi mata asiri babu abunda ke yin tasiri ajikinta, A ƙarshe dae sae gashi a tsakar dare aka dawo mata dasu sun fita hayyacinsu sunyi jaga-jaga dasu,kamar an jefosu haka ta gansu sun faɗo ɗakinta,sae kuka sukeyi ko sutura babu ajikinsu,ga miyau na zalala abakunansu,hankalin abu ba ƙaramin tashi yayi ba,sai lokacin taƙara sanin wanene sayyadi,kuma ta fara kokwanton cewa Anya ƴa'ƴanshi ne,gaba ɗaya kuɗinta sae da suka ƙare wurin nema masu magani don tunda suka dawo ciwon kai,ciwon ido,ciwon ciki,ciwuka iri-iri haka suka dinga fama dasu,har gadon asibiti aka kwantar dasu sukayi jinya duk ita ke faman ɗawainiya dasu tare da Maman sadeeq,har mijin ta yana zuwa dubasu a asibitin sannan ya taimaka masu da wani abun hadi da addu'oi,amma Sayyadi kuwa ko leƙo asibitin baiyi ba,koda aka sallame su suka dawo gidama basu same shi ba,haka abu taci gaba da shan wahalar rayuwa,ko makarantarma acikin sati bai wuci sau biyu suke zuwa ba,saboda rashin lafiyar da suke ta fama da ita,kuma duk in sukaje makarantar da kuka suke dawowa,saboda yara dake tsokanarsu akan cewa mahaifinsu ɗan mafiya ne mai yankar kawunan mutane,wannan abun ba ƙaramin cutar da rayuwarsu yake yi ba,shiyasa duk suka tsani zuwa makarantar, Akwai wani lokaci da Sehrish ta fito waje cikin unguwarsu ta miƙi hanya tana tafiya tana kuka abun duniya yayi mata,kwata kwata basu jin daɗin rayuwarsu ta ko'ina a ƙuntace suke,a daidai wannan lokacin Wata danƙareriyar mota tayi parking a gefenta,cikin sauri matashin dake cikin motar ya buɗe ya fito ya tunkareta,sam bata lura da shi ba har sae da ya ruƙo hannunta,a firgice ta juyo tana kallonshi da idanunta waɗanda sukayi jawur saboda kukan da tasha,ga majina duk fuskarta ta 6aci,zuƙunnawa yayi agabanta yana kallonta,gwanin ban tausayi ƴar ƙaramar yarinya ko kallabi babu akanta balle takalma,ga kayan jikinta duk sun 6aci, Kamar yadda yake kallonta haka itama take kallonshi,ɗan gayu dashi yasha wankan suit ajikinshi, Cikin sanyin murya yace"Ya sunanki"? ..cikin shessheƙar kuka tace"dan Allah ni ka rabu dani,ka ƙyale ni in tafiyana,' Abun yaso ya bashi dariya,shafo fuskarta yayi tare da cewa"Faɗamun me yasa kike kuka?idan kika faɗa mun zan taimake ki,' A ƙule tace"Nidai ka ƙyale ni dan Allah,kawai ka rabu dani,kona faɗa maka babu abunda zaka iyayi mana saboda babu mai sonmu Allah ne kawai ke son mu,' Tuni yaji hawaye sun cicciko mashi acikin idanunshi,Haris dake zaune cikin mota yana hangensu ta glass ɗin motar ba ƙaramin tausayi yarinyar ta bashi ba, lallashinta ya shiga yi yana cewa"kiyi haƙuri kinji?bakowa ne baisonku ba,Nima gani kuma ina sonku sosai,ashirye nake dana taimake ku indae kunaso,zan ɗauke ku mu gudu mu bar ƙasar nan,in tafi tare daku can wani wuri mai daɗi kuyi rayuwarku ko baki so? "dagaske kake"?muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar, ɗaga mata kai yayi alamar eh,tare da cewa"yanzu ki biyoni mu tafi batare da kowa ya ganmu ba," Girgiza mashi kai tayi tare da cewa"Su hosana fa?su bazaka tafi tare dasu ba?Oummanmu fa?itama anan zaka barta, "Kada ki damu suma duk zanzo in ɗaukesu daga baya," Maƙe mashi kafaɗa tayi tace"a'a ni bazan bika ba,sae dae inje in kirasu Johad da hosana,mu tafi atare," "Shikenan zan jiraki ki kirasu,kada ki faɗa ma kowa babu wanda zai san mun tafi," Amsa mashi tayi da toh sannan jiki na rawa ta juya da gudu ta koma gidan, Sai lokacin haris ya fito daga cikin motar jikinshi a sanyaye ya ƙarasa inda abusufyan yake zuƙunne,hannu yasa tare da ɗan bubbuga kafaɗarshi yace"Yanzu ka tabbatar da abunda nake faɗa maka ko? Muryarshi tamkar zai fashe da kuka yace"Haris yaran nan fa ƴa'ƴana ne!ina ji ajikina,hatta kamannin fuskarsu ma irin nawa ne,bansan ya akai hakan ya faru ba,mutumin nan baida Imani dama na jima ina zarginshi,kuma zanyi bincike akanshi,bazan ƙyaleshi ba haris,ni babban abunda yafi damuna yadda yake tafiyar da rayuwar yaran,kamar sunfi kowa rashin gata aduniya,ƴar ƙaramar yarinya kamar wannan har tasan cewa kowa baison su,tama rasa ina zata tsoma ranta saboda ƙuncin da take ji,so yake su kamu da ciwon zuciya tunda ƙuruciyarsu," ƙarasa maganar yayi tare da miƙewa tsaye yana share kwallar data zubo mashi, "Akwai matsala fa,muddin rayuwar yaran nan taci gaba da tafiya ahaka,yakamata muyi gaggawar sanar da Abbanku domin ashawo kan matsalar tun kafin ka rasa yaran nan!amma inaso yanzu idan suka zo mu fara biyawa asibiti domin ayi masu gwajin jini don mu tabbatar da cewar ƴa'ƴanka ne," Yana kai ƙarshen maganar tashi,sae ga Sehrish ruƙe da hannun Hosana da jahad,ta ruƙo hannun kowannansu sun fito daga gidan,ko abu batasan da fitar su ba,saboda ta shiga makwabtansu wurin maman sadeeq don ta samo masu abincin da zasu ci, Wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyar abusufyan lokacin da yayi arba dasu,ruƙe da hannun juna,kamar jira yake yi su ƙaraso wurinshi,ya zuƙunna tare da haɗasu duka ya rungumesu a ƙirjinshi,ya jima dasu a haka kafin ya raba jikinshi da nasu,anan ne yayi masu hoto da wayarshi,ya ɗaukesu a yadda suke kaca kaca dasu da niyyar ya nuna ma gwaggon katsina don taga halin da yaran suke,ko zasu nemi mafita, Akan idon mijin maman sadeeq mlm nura,abusufyan ya sanya su sehrish acikin motarshi,a back seat suka zauna,haris kuma shike driving ɗinsu, Shi kanshi yayi mamakin yadda yaran suka amince suka biyo shi,ko mahaifiyarsu basu nema ba,duk irin shaƙuwar dake tsakaninsu da ita wannan zai tabbatar maka da cewar ta kansu sukeyi,sun gaji da komai, A katafaren gidan nan nasu inda sukayi rayuwa shi da abu,tare dasu hajiya Ameena anan yakai yaran,cikin gidan ya shiga tare dasu,ya rage kayan jikinshi,sannan ya bisu ɗaya bayan ɗaya da kanshi yayi masu wanka acikin toilet,ya wankesu tass ya kuma wanke masu gashin kansu da shampoo,bayan ya kammala yi masu wankan,anan bedroom ɗinshi,ya shafe masu jikinsu da mai,ya gyara masu sumar kansu,sai da yabi kowaccensu yayi mata kalaba guda biyu akanta,ba ƙaramin kyau sukayi ba,bayan ya gama yi masu kitson ya hau saman gadon tare dasu ya kunna masu cartoon awayarshi na tom and jerry suna kallo, Shigowa haris yayi cikin ɗakin hannunshi ɗauke da manyan ledoji guda biyu,lokacin daya samu abusufyan kwance saman gadon tare da ƴan ukunnan duk sun manne mashi suna kallo,abun ba ƙaramin burgeshi yayi ba,sae yaji aranshi dama a wurin abusufyan yaran suka taso,da sun ji daɗin rayuwarsu, Ƙarasawa yayi tare da miƙa mashi ledar kayan,ya taso ya kar6a,kayan sawa ne daya siyo masu,sai kuma ledar abincin da yayi masu take away a restaurant, Bayan haris ya fito daga ɗakin ya fito falo yana jiran Abusufyan ya kammala shirya yaran su tafi asibitin, Sanya masu kayan abusufyan yayi,sannan ya fiddo masu da take away ɗin abincin suka zauna suna ta turawa a bakunansu,zuba masu ido yayi yana kallonsu,ganin ya kura masu ido yasa Hosana ta ɗebo abincin a hannunta takai mashi abakinshi don yaci shima, Murmushi abusufyan yayi ya buɗe bakinshi ta sanya mashi abincin,a haka har suka kammala cin abincin, Yayin da suke nan,Abu nacan tana haukan neman ƴa'ƴanta,gida gida haka ta dinga bi tana neman su hosana,har sai da Allah ya haɗa ta da Mijin maman sadeeq shi ne yake sanar da ita cewa wani matashin saurayi ne mai kama da yaran yazo ya ɗaukesu,tunda taji hakan ranta ya bata cewar Abusufyan ne,jiki asanyaye ta koma cikin gidan,gefen gadonta ta zauna addu'a tashiga yi Allah yasa shine,in ma dagaske shinen Allah yasa karya dawo mata dasu hosana ya tafi dasu kawai duk inda zaije,tabar mashi su, Lokacin da sukaje asibitin akayi masu gwajin jini,result ɗin ya nuna cewa yaransa ne,nan fa suka shiga murna shi da haris,duk da sunyi mamakin taya akai yaran suka kasance nashi!hakan na nufin da cikinshi abu tayi aure, Haris ne ya bashi shawarar su ɗauke yaran kawai karsu maidasu gidan nan,Abusufyan shima ya amince da hakan,bai maida su sehrish ba ya koma dasu gidansu,kusan kwana uku su sehrish sukayi awurin Shi,acikin waɗannan kwanakin sun samu kyakkywar kulawa a wurinshi,kullum sai sunce mashi yaje ya ɗauko oummansu itama ta dawo gidan,sai yace masu su ƙara haƙuri zai kawo masu ita, Ana haka sayyadi yadawo tun bayan da aka sallami su sehrish da jahad daga asibiti bai ƙara leƙo gidan ba sae a wannan lokacin yayi ma abu zuwan bazata,tun aranar ya soma tambayarta ina ƴa'ƴanshi suke,banza takeyi mashi bata bashi amsa,jinjina kanshi yayi tare da cewa duk ma inda takai su zasu dawo ne da ƙafafunsu, Aranar da yayi maganar,tsakar dare suna kwance abusufyan ne tsakiyarsu,hosana da jahad suna gefe da gefenshi,Sehrish kuma na kwance saman jikinshi duka ya sanya hannunshi ya dafe su, Kwatsam yaji kukansu acikin kunnuwanshi,a firgice ya farka nan fa yaga tashin hankalin da bai ta6a gani ba,sai birgima sukeyi idanunsu sun canza launi,kowacce ta dafe kunnanta sae ihu takeyi,saboda sunansu da ake ambata da wani irin sauti mara daɗin ji,hankalin abusufyan ba ƙaramin tashi yayi ba,tsoranshi kar yaran su mutu,wata irin zufa ce ke tsastsafowa daga jikinsu,sharkaf suka jiƙe, Faɗowa cikin ɗakin haris yayi jikinshi na kerma,abusufyan na ganinshi muryarshi na rawa yace"Haris kalli yaran nan ka gani wlh bansan me ya same su ba,ko zamu kai su asibiti ne"? Girgiza kai haris yayi tare da cewa"Ko mun kaisu asibiti babu abunda zasu iya yi masu!yanzun nan sayyadi ya kirani awaya ya sanar dani cewa mu dawo mashi da ƴa'ƴanshi in ba haka ba zasu mutu a hannun mu ne,kuma zaiyi shari'a damu akan laifin mun kashe mashi ƴa'ƴanshi,ina da tabbacin cewar duk shirinshi ne wannan," Jiki na rawa abusufyan ya sauko daga saman gadon ya ɗauko hosana da jahad a hannnunshi,haris kuma ya ɗauko sehrish, Cikin mota suka sanyasu,sannan haris yaja motar suka nufi gidan Ya sayyadi,wuraren ƙarfe sha biyu kenan na dare,tun kan su ƙarasa ƙopar gidan suka hango sayyadi atsaye jikinshi sanye da jallabiya,ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi, Parking ɗin Motar sukayi,da sauri suka ɗauko mashi yaran suka kai mashi,abun mamaki suna ƙarasawa inda yake sai gashi sun dawo cikin hayyacinsu,tun daga nan kowa yasha jinin jikinshi, koda suka saukesu ƙasa,suna ta faman murza idanunsu,suna yin arba da sayyadi,jikinsu na kerma suka ƙanƙame abusufyan suka manne mashi tamkar zasu koma jikinshi, Hasken fitilar kwan dake a kopar gidajensu da kuma hasken motar su abusufyan dake ajiye,shi ya taimaka masu wurin ganin junansu da kyau, Kallon kallo aka shiga yi tsakanin Sayyad da kuma Abusufyan,maƙiya sun haɗu, Haris ne yace"kaji tsoran Allah,laifin me abu tayi maka ita da yaranta da har kake son cutar da rayuwarta? Murmushi kawai sayyadi yayi yana kallonsu yace"nagode sosai,da irin kulawar da kuka ba ƴa'ƴana,naga an canza masu kaya,an kuma saya masu takalma,abu yayi kyau,kaga masu Ji da naira,ba kamar mu ba ƴa'ƴan malam shehu.......' . afusace abusufyan ya katse shi da cewa"Kai malam!ka faɗamun taya akai ka auri abu da ciki na!don bincike ya nuna cewa yaran nan ƴa'ƴana ne!ba naka ba!dama najima ina zarginka wlh!kai ba mutumin kirki bane!" shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da cewa"Oh kanaso kasan yadda akai na auri abu da cikin ka"? Har suna haɗa baki shi da haris wurin cewa Eh, Dariya sayyad yayi kafin ya matso dab da Abusufyan suna fuskantar juna ido cikin ido yace"tabbas Ƴan ukun nan ba ƴa'ƴana bane!naka ne halak malak,tun lokacin da kuka rabu da abu ta sanar dani cewa tana jin tashin zuciya,anan nagane cewa tana ɗauke da cikinka,shine na kwantar da cikin ta hanyar yin amfani da sihiri na,babu wanda yasan cewa tana da ciki har na aureta,sannan na bayyanar da cikin a jikinta,don su taso amatsayin ƴa'ƴana.......' Katse shi haris yayi da cewa"meyasa kayi hakan toh"? Sayyadi yace"bana faɗin dalili sai dae kawai in bada amsa,' Jiki asanyaye abusufyan yakai idanunshi kansu hosana dake manne ajikinshi sun ƙankameshi,alamar basu so yabarsu anan,tuni yaji hawaye sun cicciko mashi a idanunshi aranshi yace ashe dae dagaske jini na ne su, "Amma meyasa ka auri abu?yanzu nake kokwanton cewa anya don kana sonta ka aure ta"? sayyad yace"ina fa?ni sam mace bata gabana!namiji kawai,da maza nake mu'amalata,Na auri abu ne duk don saboda in samu hanyar da zan shiga rayuwarka,kuma na samu,'yayi maganar yana nuna su sehrish dake ƙankame da jikinshi, Rae a6ace haris ya cakumi wuyan rigar sayyadi yana cewa"wlh bazamu ƙyaleka ba,mugu azzalumi!zamuyi ƙararka kotu akan yaran nan,' Dariya yayi tare da cewa"nafi ƙarfin kotu haris!babu abunda zasu iyayi mun,' ""Idan ka fi ƙarfin kotu ae baka fi ƙarfin Allah ba,zamu kai ƙararka wurinshi,kuma insha Allahu sayyad ba zakayi kyakkywan ƙarshe ba,sae kayi mummunan mutuwa kamar yadda mahaifinku kakah yayi......' Buge hannun haris yayi daga cakumar wuyan rigarshi da yayi,cike da mamaki yace"Oh ashe ka gane ni!" jinjina kai Abusufyan yayi tare da cewa"bangane kaba,amma tunda ka ambaci cewa kana son shiga rayuwata na gane cewa kai daga family ɗinsu kakah kake,Azzaluman mutane,mugaye waɗanda suka mayar da zalunci hanyar cin abincinsu,masu tada ƙayar baya a ƙasarmu,asannu asirinka zai tonu kamar yadda na ubanku ya tonu kuma insha Allah,Abbana da kuma yayana Hussein,kai bama su kaɗae ba nayi maka alƙawarin cewa a hannun ɗaya daga cikin jikokin Amminmu zaka Mutu,mummunar mutuwa kuma a wulaƙance kamar dabba haka zakayi ta,idan Allah ya nuna mun wannan ranar ni kuma zan tuna maka waɗannan kalaman da nayi maka, Hannu Abusufyan yasa tare da dafa kawunansu sehrish dake manne da jikinshi yace"idan Allah yasa su kayi tsawancin kwana basu mutu a hannunka ba,A gabansu za'ayi komai," Fashewa da dariya sayyadi yayi hada dafe cikinshi,lokaci guda kuma ya tamke fuskarshi tamkar bai ta6a yin dariya ba yace"kai fa ƙaramin ɗan iska ne mai kwana da wando,har yanzu bakasan wanene sayyadi ba,labarina kawai kake ji,nafi ƙarfin duk wanda kake tunanin zai iya ɗaukar fansa akaina!danginku gaba ɗaga babu wanda zai iya ɗaga mun yatsa,kuma inaso na sanar maka cewa muna nan muna shirin tarwatsa farin cikin zuri'arku,muna nan muna shirya maku maƙarƙashiya,bani kaɗae bane yawa gare mu kuma muna nan kewaye daku,' Kallon juna haris da Abusufyan sukayi kafin su mayar da idanunsu kan Sayyadi, "Daga rana irin ta yau!ina mai gargaɗinka da cewa kada ka kuskura ka ƙara yunƙurin zuwa ɗaukar yaran nan!wlh in har ka ƙara takowa kazo inda suke!ko kuma ka turo wani naka da niyyar ya taimakesu!koma wanene sai ya Mutu!!!!na sanya katanga a tsakaninku dasu,zaku iya tafiya," Ya ƙarasa maganar tare da nuna masu hanyar inda motarsu take da hannunshi,hannu abusufyan ya sanya yana ƙoƙarin raba su hosana da jikinshi kuka suka fashe dashi suna roƙonshi akan karya tafi yabarsu a hannun wannan mutumin basu son zama dashi........'wata irin tsawa ya sayyadi ya daka masu a gigice suka raba jikinsu dana abusufyan suka shige gida da gudu suna kuka,ashe Abu tana a la6e a zauren gidan tana sauraronsu,tun lokacin da abusufyan yazo da su hosana,tasha kuka kamar taje ta rungumoshi ajikinta haka ta dinga ji,kamar ta zauce tayi hauka,su hosana na shigowa ta haɗasu duka ta wuce dasu ɗakinta,anan suka zauna suna ta sharar kwalla, Jiki asanyaye abusufyan da haris suka shige cikin motarsu,tun daga wannan lokacin ne abusufyan yabar Nigeria ya koma Turkey gaba ɗaya,bai ƙara leƙo nigeria ba,ya nesanta kanshi da kowa ne saboda bazai juri zuwa nigeria ba,yayin da ƴa'ƴanshi suke rayuwa awulakance baida ikon taimakonsu ko ya sanya a taimakesu,sai dae Addu'a da yake binsu da ita. Haka su sehrish suka ci gaba da shan wahalar rayuwa a hannun mutumin nan,wani tashin hankalinma sayyadi  ya fara kwaɗaita dasu,ya dinga nemansu a 6oye abu bata sani ba,duk in tayi kuskuren fita ta barsu acikin gidan yazo ya same su haka zai ƙumshe su aɗakin yana tsoratar dasu akan susha mashi gabanshi,duk abu bata ankare ba,sae wata rana da ta ta6a dawowa ta same su suna ta kwarara amai wani irin abu mai yauƙi yauƙi yana fitowa abakinsu,tsare su tayi da tambaya akan me suka sha ne ya 6ata masu ciki,ƙin faɗa mata sukayi saboda tsoran kada Abbansu ya kasheta kamar yadda yayi masu barazana in suka faɗa mata,ganin sunƙi faɗa mata yasa ta ɗauko wuƙa a kitchen ta nuna su da ita tana cewa"Ko ku faɗa mun ko in kashe ku a wurin nan,"gaba daya suka tsorata,sehrish ce ta buɗe baki ta sanar da ita abunda mahaifinsu ke sanyasu suna yi mashi,saboda tashin hankali nan take ta yanke jiki ta faɗi asume, Kukan da suka fashe dashi ne yasa makwabciyarsu shigowa gidan don taga meke faruwa ne,anan ta samu abu a sume ruwa ta ɗebo ta yayyafa mata ta farka,miƙewa tayi zaune tare da sanya hannu ta dafe saitin zuciyarta tana ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!ya Allah ka ɗauki raina tun kafin baƙin cikin mutumin nan ya kashe ni,Sayyadi ka cuci rayuwata ka gama dani nashiga uku! Wayyo Allah na!   Tasha kuka kamar ta zauce,daƙyar maman sadeeq ta lallashe ta bayan ta tsagaita da yin kukan take tambayarta meya faru,bata 6oye mata komai ba ta kwashe ta sanar mata,a lokacin maman sadeeq har hawaye sai da ta zubar masu saboda tsabar tausayin yaran,ranar yini sukayi suna jimamin abunda ya faru atare kuma suka duba yaran don su tabbatar in bai lalata su ba,duk da sun tambayesu ko ya masu wani abu a wurin sunce a'a,bayan tafiyar maman sadeeq ta koma gida mijinta ta samu tayi mashi magana akan Yayi ma sayyadi magana akan abunda yake aikatawa saboda abun yayi yawa,yana cutar da rayuwar yaran, nan gaba zai iya lalata masu rayuwarsu gaba ɗaya har ma yayi silar Rasa ransu,   Jinjina kai Malam yayi tare da cewa"Hmmmm taya zan tunkari mutumin nan?me zan iya yi mashi?Mutumin da kana ja mashi aya yana fassarata!taya zai fahimci cewa badai dai yake aikatawa ba?bayan yasani kuma yake take sanin!Tabbas na tausaya ma rayuwarsu amma babu ta yadda zan iya taimakon rayuwarsu sae dae na bisu da addu'a kawai,Allah shine zaiyi maganinshi"shi kanshi Abban sadeeq sae da ya zubar masu da kwalla,ya tausaya ma rayuwar yaran,tabbas suna cikin masifa, Bari in taƙaice maku labarin,sayyadi shine yayi sanadiyar ta6in hankalin hosana,a tsakar dare suna bacci ya ɗauketa batare da sanin kowa ba,ya kaita gidan wani Babban ɗan siyasa kamar yadda suka tsara dashi akan cewa zai kai mashi ita yayi amfani da ita don cin nasarar za6en shi,sam batasan ya ɗaukota ba sae dae kawai ta ganta asaman gadon mutumin,fasa ihu tayi da sauri ta diro daga saman gadon tana ƙanƙame jikinta,mutumin nan babu kunya babu tsoran Allah ya shiga tu6e kayan jikinshi agabanta,a tsorace tace mashi fitsari take ji,ya nuna mata hanyar toilet taje tayi fitsarin yana jiranta, Jiki na rawa ta shige cikin toilet ɗin ta rufo ƙopar,Kunna fanfo tayi don kar yaji ƙarar abunda zatayi,zagaye tashiga yi acikin toilet din tana neman abunda zata fasa window ɗin kewayen,annan ƙasa ta samu wasu ƙarafuna masu ɗan tsayi kamar an ta6ayin gyaran wani abu a toilet ɗin aka ajesu nan,   Hannu tasa ta ɗauka jiki na rawa ta haye saman toilet seat ɗin dake a rufe,ta faffasa windown da sauri da sauri duk mutumin nan baijiyota ba,sai da ta fasa glass din ya tarwatse sannan ta biyo ta windown duk batayi tunanin cewa bayan yana da tsayi ba,kawai ta afka,gaba ɗaya ta bugi floor ɗin da ƙarfi kanta ya fashe,hancinta da bakinta duk suka bugu ga sauran kananun glass da suka yayyanketa ta,gigitacciyar ƙara ta saki saboda azabar da tasha,amma hakan bai hanata yunƙurawa ta miƙe da gudun gaske ta nufi hanyar fita daga gidan,mai gadin gidan na sallar dare ta samu ta fice da gudu ta karamar kopa tana kuka ta miƙi hanya gashi dare ne, Acan kuwa tsakar dare Oummansu na bacci ta jiyo muryar jahad tana cewa"oumma ki tashi,hosana bata a gida fa,banganta ba,har kewaye na duba amma babu ita bansan ina taje ba,hankali atashe abu ta farka,a lokacin itama sehrish ta tashi,gaba daya suka shiga nemanta,duk sayyadi na ɗakinshi yana jiyo hayaniyarsu bai tanka masu ba,da suka duba ko ina basu ganta ba,anan fa hankalinsu ya ƙara tashi,fitowa sukayi suna bi gidaje suna tambayarta wasu a amsa masu da bata nan,wasu gidajenma ba mai zuwa balle ya basu amsa,kai tsaye suka miƙi hanya suna duddubawa ko wani mummunan abu ya faru da ita ne,lokacin da suka hau gefen titi suna tafiya........    Adai dai time ɗin Hosana ta shigo kan hanyar da gudu tana kuka hannunta dafe da kanta dake ta zubar da jini,tana ambaton oumma, oumma,    a gigice suka kai idanunsu wurinta,da gudun gaske suka tunkareta,abu na ƙoƙarin dakatar da ita akan ta kauce daga saman titin amma sam bata a cikin hayyacinta,wata mota ce ta bugeta da ƙarfin gaske gaba ɗaya ta kife ƙasa,mai motar na bugeta yaja motar da gudu yabar wurin alamar cewa da gangan ya bugeta,ashe ɗan siyasan nan ne yabiyo ta,bayan ya jima yana jiranta ta fito daga toilet bata fito ba,kawai ya afka ciki anan ya samu ta fasa glass ta gudu,yana huci ya fito ya mayar da kayanshi,ya bi bayanta cikin motarshi,don karta tona mashi asiri yasa yayi mata haka don ta mutu,   Zubewa sukayi agabanta suna ta kuka suna ta faman jijjigata a ƙarshe Abu ta sanya hannu ta ɗauketa,a ƙafa suka taka da sauri da sauri saboda babu abun hawa,gashi sae bleeding takeyi,suna cikin tafiyar nan sai ga Mijin maman sadeeq cikin napep,ashe tun lokacin da suka je gidan neman Hosana,bayan tafiyarsu ya gaza samun natsuwa shine ya biyo bayansu,napep ɗin ma bata shi bace arota yayi,saboda mashin ɗinshi babu mai,   Adai dai inda suke ya tsayar da abun hawan nashi,tunda yaga halin da hosana ke ciki bai tsaya tambayar ba'asi ba yace su shiga ciki,   A daren ranar suka kaita asibiti,likitoci suka shiga duba ta,tun nan aka sanar dasu cewa Sai anyi mata aiki,ana buƙatar kuɗi miliyan ɗaya da rabi,nan fa hankalinsu ya tashi,saboda ko sisi basu da ita, Har washe garin ranar ana kan abu ɗaya,andai samu an fara treating ɗin raunukan jikin nata,aikin dai ne ya gagara,sun jima a asibitin nan ana neman taimakon kuɗin da za'ayi mata aiki amma ba'a samu ba,sayyadi ko leƙo asibitin baiyi ba,bayan shine silar komai don ubanshi, Sanadin haukacewar mahaifiyarsu kuwa,lokacin anata neman yarda za'a harhaɗa kuɗin aikin hosanan,duk wani abu mai dan amfani tasa an sayar dama ba wasu abun kirki suka rage mata ba,don duk ta siyar da kayayyakinta wurin kula dasu Sehrish,a lokacin abu duk ta gama fita hayyacinta ta kode ta rame,duk da dae kyawunta na nan,amman inka ganta zaka yi tunanin ta girmi shekarunta saboda wahalar rayuwa, ta yanke shawarar zuwa gidan ta duba taga idan sayyadi yana nan jin shiru bai neme su ba,ko labarin kwanciyar hosana asibiti baije mashi bane,   Tana sa ƙafarta tsakar gidan nanfa ta dinga jin wannan gurnanin abunda sukeyi mara daɗin ji,ranta yayi mugun 6aci,kitchen ta nufa ta ɗauko tukunya ta zubo ruwa a fanfo kusan rabin tukunyar mai fadi,bayan ta ɗaura ruwan sai da ta jira ruwan ya tafasa sosai yana huci sannan ta sauke shi,tsumma ta ɗauko ta ruƙo tukunyar dashi,ta nufi ɗakin nashi,cikin sa'a sun bar ƙopar a buɗe dama da yawan lokutta basa rufe ƙopa turo ta kawai sukeyi,   Faɗawa cikin ɗakin abu tayi,mutun shida ta samu kamar wasu mayu manne da juna,aikuwa tana ƙarasawa wurin gadon,ta ɗaga tukunyar gaba ɗaya ta maka masu ruwan zafin ajikinsu,wa'iyazubillah,agigice suka rabe da junasu,wata irin gigitacciyar ƙara suka shiga saki ta azabar radaɗin tafasasshen ruwan zafin nan da abu ta watsa musu,ihu suka dinga yi suna birgima,fatar jikinsu duk ta ɗame ta lalace,   Duk atunaninta hada sayyadi acikinsu ashe yana acikin toilet,razananniyar ƙarar daya jiyo daga cikin bedroom ɗinshi ne yasa shi fitowa daga cikin toilet din,Waro ido waje Sayyadi yayi tare da aza hannunshi akai yana ambaton"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Abu baki da hankali ne!!kinsan ko me kika aikata?   Idanunta jawur ta kalleshi rai amatuƙar 6ace tace"Na sani,kuma ina cikin hayyacina,wlh naso ace hada kai acikinsu na haɗa na ƙona,uban kowa ya huta da wannan masifar.....' Bai bari ta ƙarasa maganar ba ya kifa mata mari zazzafan gaske har sae da gefen bakinta ya fashe,   Ɗagowa tayi da idanunta dake zubar da hawaye tace"Banji zafin marin da kayi mun ba!ada inajin shakkarka amma yanzu bana jin tsoranka acikin zuciyata,Wlh saina tona maku asiri duniya tasan me kuke aikatawa,daga nan in na fita gidan radio zanje in yaɗa duk wani mugun abunda kuke aikatawa,'   Wani irin huci ya shiga yi zufa na gangarowa daga jikinshi sae tsuma yake yi,hannu yakai tare da shaƙo wuyanta ya bugata jikin wardrobe ɗin dakin,   Sannan ya soma magana da wata irin murya mara daɗin ji yace"Ke daƙiƙiyace har yanzu bakisan ciwon kanki ba!kina tunanin cewa zan bari ki tona mun asiri ne!!kafin na juya maki tunaninki,inaso nasanar dake cewa Hosana jahad da sehrish ba ƴa'ƴa na bane!Da cikin abusufyan na aure ki!kuma nine na kashe mahaifinki baba buzu,saboda yana ƙoƙarin hanani auranki!' Wasu irin hawaye ne masu zafin gaske suka shiga gangarowa a fuskarta,tsabar baƙin ciki da takaici yasa ta gaza magana,saboda wani irin ƙululun baƙin ciki daya tokare mata maƙoshinta,    ƴa'ƴan naki ma bazan barsu ba!ɗaya bayan ɗaya saina kashe su!'   Yana faɗin hakan ya saki wuyanta,da gudun gaske abu ta fito daga cikin ɗakin nashi tana kuka,a ƙopar gidan ta tsaya tana faman ambaton sunan baba buzu tana cewa babana ka kashe mun ka raba shi da ranshi,ka kashe mun babana ko,kuma zaka rabani da ƴa'ƴana suma ka kashe su ko......'haka ta dinga sambatu ita kaɗae,   Tun daga wannan lokacin abu ta haukace ta miƙi santa tana faman sambatu, Wannan shine silar rabuwarsu da mahaifiyarsu basu ƙara sanin inda take ba, Abunda kuma yayi silar komawarsu katsina,labarin neman da mahaifinsu yake yi masu don ya kashe su kamar yadda ya fada ma abu,ya isar masu maman sadeeq,ko aikin ba'ayi ma hosana ba,amma ta miƙe saidae babu hankali ko kaɗan,da taimakon Mijin maman sadeeq ya sanyasu a mota tare da damka ma direban amanarsu,bayan yasa anyi ma hosana allurar bacci ya bama Sehrish address ɗin gidan tsohuwar nan,wadda ta kasance kishiyar mahaifiyarshi ce anan suke zaune,tsohuwa mai kirki koda yayi mata bayanin halin da yaran suke ciki ta tausaya masu sosae ta kuma ce zata rike su da tsakani da Allah,shima kuma yayi alkawarin zai rinka turo da dan abunda Allah ya hore,   Da daddare suka isa unguwar ba tare da sanin kowa ba,sai da aka taimaka masu kafin aka samu suka shiga da hosana gidan,a ɗaki ake rufeta saboda haukan da takeyi,na bugun mutane da jefe jefe,tsaf zata iya kashe mutun,    Wannan shine silar komawarsu gidan tsohuwar nan,tayi masu halarci arayuwa,ita ta dinga nema masu tallafi don a maida hosana asibiti ayi mata aiki,haka sehrish ma bata zauna ba,har wankau suke yi suyi guga itada jahad suna tara kuɗin da za'a kai hosana aiki,kafin tsotsai ya ritsa da jahad,      Akwai wani lokaci da suka je gidan wani ɗan majalissa jin labarin cewa yana taimaka ma marasa lafiya waɗanda ake buƙatar kuɗin da za'ayi masu aiki,tsohuwa da sehrish suka je gidan mutumin,yayin da suka bar jahad a gida tana aikin wanki,   Tana cikin yin wankin nan ta dinga jin kukan hosana gwanin ban tausayi tana cewa dan Allah su buɗe mata ƙopa su taimaki rayuwarta mutuwa za tayi,tana son ganin ƴan uwanta,me yasa kullum suke ƙumsheta a ɗaki,zafi ya isheta,itafa tana da hankalinta,ba mahaukaciya ce ita ba,tana da hankalinta,   Natsuwa jahad tayi tana sauraranta,yanayin yadda hosana ke kalamanta yasa tayi tunanin cewa kodai ta samu lafiya ne,tun tana tsoran buɗe mata ƙopar har dae tausayinta ya kamata sosai,da sauri taje ta buɗe mata ƙopar,   Kamar jira take a buɗe da ƙarfi ta damƙi wuyan jahad da hannunta,ta janyota cikin ɗakin,tana cewa"dama kece kika sace ni ko?kika rufe ni acikin ɗakin nan kina cutar dani!yau Allah ya kamaki!wlh saina rama,   Duk yadda jahad taso ta kwaci kanta a hannun hosana abun yaci tura saboda wani irin mahaukacin ƙarfi ne ke gareta,buga kan jahad tashiga yi ajikin bango,jahad ta fasa ihu saboda azabar da taji,nan take jini ya shiga bulbulowa daga goshinta,kuma hakan baisa hosana ta daina bugunta ba,har saida taga jahad ta daina motsi sannan ta saketa, Adai dai lokacin tsohuwa da sehrish suka dawo cikin gidan,da gudu suka faɗo ɗakin da hosana take ganinshi a buɗe nan suka samu jahad wanwar ƙasa jini na zuba,itama hosanar tana baje ƙasa sai faman mirgina-mirgina takeyi numfashinta na fita sama sama, Wannan shine silar da aka kwantar da hosana da jahad asibiti,har akayi ma jahad ƙarin jini,ita za ayi mata aiki,   Inda Allah ya taimakesu asibitin suna da wata ƙungiya wadda manyan masu kuɗi ke tallafawa marasa lafiyan da za'ayi ma aiki da wani parcentage,sun samu kuɗin amma akwai cikon da zasu yi dubu ɗari tara likitocin suka buƙata a wurinsu,    Sehrish tasha wahala sosai wurin neman cikon kuɗin nan,duk inda taje neman taimako sae an nemi ta bada kanta sannan abata kuɗin,anan ne wata mata dake jinyar wata a ward din da aka kwantar dasu hosana take ba sehrish labarin hajjaju dake ɗaukar ƴan aiki tana samo masu aikatau suna yi kuma suna samun alheri dayawa,saboda gidajen manyan masu kuɗi take samo masu aiki,matar tace in taci sa'a ma,aranar da tafara zuwa aiki sai tace ma masu gidan su bata kuɗin aikinta na shekera ko biyu ne,in aka dace zasu bata kuɗin,bayan matar ta bata address din gidan,tun daga ranar sehrish kullum sai taje ƙopar gidan hajjaju nemanta,har Allah yasa ta samu ganinta, Atakaice tarihin su sehrish hosana da jahad kenan,duk da bakomai aka fayyace ba, amma mutun zai gane inda aka dosa, 💋Boss Bature💋 Jikin kowa yayi mugun sanyi,masu raunin zuciya acikinsu tuni sun soma zubar da hawaye,hatta jahan dake da taurin kai sai da ya matse kwalla,Abusufyan kuwa tuni ya fashe da kuka,haka gwaggon katsina kamar ƙaramar yarinya haka ta dinga kuka tana fadin"Allah ka tsine ma Sayyadi da duk zuri'arshi!Allah ya wulaƙanta rayuwarshi kamar yadda ya wulakanta rayuwar ƴa'ƴan abusufyan ɗina, Hatta Abbansu sae da ya matse kwalla shi da Abbas da su fawan,kowa ya harzuƙa ransu yayi mugun 6aci,tsananin tausayin su Jahad hosana da sehrish ne ya kamasu,marshal Omar kuwa sunnar da kanshi ƙasa yayi idanunshi sunyi jawur jikinshi sai kerma yake yi,zuciyarshi har wani tafarfasa takeyi saboda tsabar 6acin rai,   Sehrish kuwa lokacin da Jahad ta kammala bada labarin tasa kuka ita da Hosana,   Nan take ta miƙe daga jikin Sgr,hankali a matuƙar tashe take kallonsu yayin da zuciyarta ke bugawa da ƙarfi da ƙarfi,kowa zuba mata ido yayi yana kallonta ganin yadda jikinta ke rawa tana kallonsu hosana da jahad,   Muryarta na rawa ta ambaci sunansu"Hosana jahad kune.........'tana faɗin hakan ta yanke jiki ta faɗi asume,   Da sauri abusufyan da hajiya azeema sukayo kanta hada su jahad ɗin,   Sam Sgr bazai iya jurewa ba,yunƙurawa yayi azafafe ya juya tare da nufar upstairs ya koma bedroom ɗinshi,agaban mirror ya tsaya yana kallon fuskarshi wadda take daure tamau,gaba daya jikinshi sae kerma yake yi saboda tsabar 6acin ran da yake ciki,wata irin zufa ce tashiga gangaro mashi daga gefe da gefen fuskarshi,tabbas idonshi Idon Sayyadi............................... *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.   *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* Zagayeta su kayi gaba ɗayansu,su jahad na ambatar sunanta,fawan ne ya ɗauko masu ruwa a fridge ya dawo ya miƙa ma uncle ɗinsu,kar6a yayi tare da buɗe murfin ya ɗebo ruwan hannunshi nata kerma ya watsa mata shi a fuskarta,nan take ta farka tana faman yin atishawa,Alhamdulillah suka shiga faɗi suna kallonta,yunkurawa tayi ta tashi daga zaune tana bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya kafin ta mayar da idanunta akan Su hosana da jahad da suka zuba mata ido,    Muryarta na rawa tace"jaj..jahad hos...sana...ku ne?ko dae idona ne ke nuna mun ba dai dai ba?   Ba ƙaramin farin ciki ne ya lullu6esu ba sehrish ta dawo cikin hayyacinta ta gane su,atare suka faɗa jikinta suka rungume juna suna kuka,   Murmushi kawai Abusufyan ke saki bashi kaɗae ba ma fuskar kowannansu na ɗauke da murmushi,musamman Abbansu junaid farin ciki kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha,haka hajiya azeemarsu har cewa take yi"yanzu nan waɗannan ƴan ukun duka namu ne?ƴa'ƴan mu ne?Allah abun godiya,yau dole in yi nafilar dare don miƙa godiyata ga Allah S.W.A daya nuna mun ƴa'ƴan abusufyan ɗinmu da ranmu kuma da lafiyarmu,Ashe dae da rabon yara suga danginsu,bayin Allah sun sha wahalar rayuwa,amma bakomai har yanzu lokaci bai ƙure mana ba,zamu nuna maku soyayyar da baku samu ba arayuwarku,Zamu baku duk wani jin daɗi na duniya da kuka rasa,zamu gatanta ku,sai mun cika ku da farin cikin da zaisa ku manta duk wani ƙunci da kuka ta6a fuskanta arayuwarku,waɗanda kuma sukayi silar jefa rayuwarku cikin hatsari tabbas sai sun ɗanɗani kuɗarsu sai sunji dama ba'a halicce su cikin duniyar nan ba, Abbansu junaid ya kar6e da cewa"Ae daga rana irin ta yau su fara ƙirgen kwanakin mutuwarsu,saboda ƙarshen su yazo,sun tabka babban kuskuren ta6a jinin SALAHUDDEEEN HUSSEIN!Wallahi thumma tallahi ɗaya daga cikinsu bazai sha ba!' ranshi amatuƙar 6ace yayi maganar,    Abbas yace"Abba ina ganin yakamata yaran nan suje su kwanta dare yayi sosai,suna buƙatar hutu,in yaso koma menene gobe zamu ida tattauna akai,'    Jinjina kai Abbansu yayi tare da mayar da idanunshi kansu sehrish dake manne da juna suna kuka,    Gyaran murya ya ɗan yi masu,atare suka ɗago suna kallonshi da idanunsu dake zubar da hawaye,   "Kuyi kuka yara bazan hanaku ba,dole kuyi kuka domin kuwa an cuci rayuwarku,an zalunce ku,an ƙuntata maku,an rabaku da mahaifinku na asali kuma an rabaku da danginku,duk akan laifin da baku kuka aikata ba,saboda son zuciya irin na mutanan nan su rasa akan wa zasu ɗauki fansar su sae akan waɗannan bayin Allahn....  'Shiru ya ɗanyi yana faman sauke ajiyar zuciya,   abusufyan na zuƙunne akusa dasu ya sunnar da kanshi ƙasa,hakanan ya dinga jin kunyar yaran yana ji aranshi tamkar duk shi ne silar jefa su cikin halin da suka shiga,   Su fawan kuwa dasu twins irfan jabeer da sauransu duk suna atsaye kowannansu jikinshi asanyaye kamar waɗanda aka zare ma lakka,lokaci guda sukaji tsananin Son yaran ya kamasu,   duk wannan abun dake faruwa gwaggon katsina,na zaune saman kujera tana ta faman matsar kwalla,har lokacin bata daina tsinar dangin Sayyadi ba,haris sai faman lallashinta yake yi tana buge mashi hannu tana faɗin"ka rabu dani Harisu!abun da ciwo wlh,Zuciyata tafarfasa takeyi,ƴa'ƴan abusufyan ɗina aka wulaƙanta kamar dabbobi?wlh bazan ta6a daina tsinewa Sayyadi ba,munafuki algungumi ɗan wuta,Ya Allah ka tsine ma sayyadi da duk zuriyarshi harda unguwar zomar da ta yanke mashi cibinshi, Ya Allah kayi mana maganinsu,Sayyadi ko ɗan iska,uwarshi ta haifa mana masifa....munafuki lokacin da yake zuwa wurin abu har ƙasa yake zukunnawa ya gaishe Ni,da wata guntuwar jallabiyarshi ta gado,ƙafafun nan nashi kaman shebur sanye cikin silifar ɗan ta shegiya...Muna yi mashi kallon Biri yana yi mana kallon ayaba.....'   sai faman sambatu takeyi abun ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,can kuma tace"Allah sarki abu,nasan yanzu ta gane cewa Allah ɗaya ne,yarinyar nan akwai taurin kai kamar kwallon goruba ga kafiya,kunnuwan nan nata kamar na Zoman daji falo falo dasu,ba irin jan kunnan da banyi mata ba,amma taƙi ji na,Ae ga irinta nan yanzu majnun ya koya mata hankali yanzu tana can Saman bola tana sambatu baiwar Allah,wama yasan uwa duniyar data shiga.......'   "Sehrish ku tashi ku tafi ɗaki ku kwanta,gobe zamu ƙarasa magana daku," Abbansu ne yayi maganar,   Miƙewa sukayi tsaye tare da yi masu sallama sannan suka wuce ɗakin nata,gaba ɗaya sehrish ta ɗan shiga ruɗu,batasan meya faru ba,amma bakomai yafi ɗaure mata kai ba face ganinsu hosana da jahad,taya akai suka San inda take har suka zo wurinta?abun kamar a mafarki take ganinshi,   Atare suka shiga cikin ɗakin,anan fa suka tsaya suna kallon juna fuskar kowaccen su ɗauke da tsantsar farin ciki mara misaltuwa, "Sehrish Ashe da rabon zamu sake ganinki a duniyar nan"?jahad ce tayi maganar yayin da hawaye ke sauka a fuskarta, ta ɗaura da cewa "Sehrish munyi kewarki sosai,munyi kukan rashinki atare damu,munsha wahala sosai,abubuwa marasa daɗi sun faru damu bayan rabuwar mu dake,amma duk wani hali da muka shiga hakan baisa mun manta dake ba sehrish kullum kina aranmu,koda yaushe muna cikin zullumin a wane hali kike?kina raye kuwa?kina jin daɗin rayuwarki?kina da ƙoshin lpy ko akasin hakan ....'   jin wannan maganar ta Jahad yasa ta fashe da kuka mai cin rai,janyota jahad tayi jikinta sosai ta rungumeta,itama hosana ta matsa tare da sanya hannayenta ta bayansu,suka haɗe su ukun,sun jima a wannan yanayin kafin daga bisani suka haye saman gadon su duka ukun suka zagaye junansu suna fuskantar juna a zaune   Sai lokacin sehrish ta buɗe bakinta tare da cewa"inaso ku faɗamun meya faru na daina samun wayar tsohuwa,sannan kuma inason jin yadda akai har ku ka san inda nake,nayi mamakin yadda na manta daku gaba ɗaya acikin rayuwata,nasan ban kyauta maku ba,Amma kuyi haƙuri ku yafe mun........'   ta ƙarasa maganar tare da kai hannunta ta shafo gefen fuskar hosana tana kallonta da idanunta waɗanda suka canza launi sosai,sai lokacin ta gane cewa ashe sune yaran da Marshal Omar ke ruƙo a wurinshi,rashin sani yafi dare duhu,har waya suka yi dasu jahad amma bata ganesu ba,saboda bata acikin hayyacinta,   Jahad ce ta kwashe dukkan abunda ya faru tun daga kan Jefa wayar tsohuwa da hosana tayi acikin Masai da kuma mutuwar tsohuwa,da kuma zamansu acikin cell,haɗuwarsu da Marshal Omar,zamansu a wurin gwaggon katsina da kuma rayuwarsu agidan Aunty babba,komai ta sanar mata, Sosai sehrish tayi kuka tamkar ranta zai fita,har zazza6i saida ya lullu6eta nan take,bakomai yafi girgiza ta ba face mutuwar tsohuwa,da kuma zamansu hosana a gidan Aunty babba,abun ba ƙaramin ta6a zuciyarta yayi ba,wani irin ciwon kai ne ya rufar mata mai raɗaɗin gaske,rarrafawa tayi ta koma gefe guda saman bed mattress ɗin ta kwanta tare da janyo pillow ta rufe fuskarta dashi,Wurinta su jahad suka koma tare da kwantawa kusa da ita,kowanannsu na acikin yanayi,tabbas sunga rayuwa...... Daƙyar bacci 6arawo ya sace su,amma fa dukkansu babu wanda babu zazza6i ajikinshi, Kowa fa ya manta da cikinshi saboda lamarin su hosana,a gidan babu wanda yaci abincin daren shi,saboda ƙunci da takaicin yadda rayuwar ƴa'ƴan uncle ɗinsu ta kasance, Lokacin da Azmee ta turo ƙopar ɗakin nasu samun su tayi kwance suna bacci kowacce fuskarta ɗauke da hawaye,bacci sukeyi amma hawayen basu daina zuba daga idanunsu ba,ba ƙaramin tausayinsu taji ba,ta jima tana kallonsu kafin ta rufe masu ƙopar ta koma bedroom ɗinta, Kwance yake asaman katafaren gadonshi,tunda ya dawo bedroom ɗinshi,ya shiga toilet yayi wanka,ya dawo ya kwanta yana tunanin duniya,juyi kawai yake yi asaman gadon bacci yaƙi ɗaukarshi,har lokacin zuciyarshi bata sauka ba,abun ya dame shi sosae,ya tsani zalunci arayuwarshi,ya tsani mugun mutun mai hali irin na dabbobi,tabbas idan har sayyadi ya bari ya shigo hannunshi sai ya ɗanɗani kuɗarshi,daga baya kuma ya dawo yana tunanin wai yanzu ƴar yarinyar nan da take yi mashi aiki,ashe ƴar uwarshi ce?jinin shi?ɗiyar Uncle ɗinsu?hakan na nufin cewa ita ƙanwarshi ce...? "Wonders shall neva end'ya furta hakan tare da lumshe idanunshi,nan take kuma ya tuna da hoton da Uncle abusufyan ya basu lokacin da suke a U.s,hakan na nufin cewa Hoton yaran ne ya basu lokacin da suke ƙanana,zan tambayi uncle hoton wacece nai selecting acikinsu,as I promised then zan taimaketa da kuɗi ta sayi duk abunda takeso bazan fasa ba...... ' Wasu dae sunyi bacci a wannan daren yayin da wasu kuma Baccin ya ƙaurace ma idanunsu,a tsaye Abusufyan ya kwana idanunshi sun ƙanƙance saboda raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi,bawan Allah,wlh abunda ciwo,taya ma zai iya bacci?yasha kuka dae,ga wani irin Matsanancin ciwon kai da yake fama dashi,yawo yake ta yi acikin dakin yama rasa tunanin da zai yi yayin da tafin hannunshi na dama ke dafe da saitin zuciyarshi,wani irin bugawa takeyi mashi mara daɗi, Yana cikin tsayuwar ne har aka kira sallar asuba bai ankare ba,sae da Yaji ana mashi knocking ƙopa,muryarshi ashaƙe yace"Wanene," "Ni ne"muryar Abban su junaid ce, Hakan yasa shi cewa"ƙopar abuɗe take yaya ka shigo daga ciki,".  Tura ƙopar Abba yayi ya shiga ciki yana ganin Abusufyan atsaye yace"dama saida rai na ya bani cewar baka yi bacci ba abusufyan,'   Yayi maganar tare da ƙarasawa ya dafa kafaɗarshi yana kallon fuskarshi da hawaye suka wanke ta sharkaf, Cikin sanyin murya yace"duk wanda yace maka kayi haƙuri tamkar ya cuce kane!amma ya zakayi abusufyan?dole haƙurin nan shi zakayi,nasan abun da ciwo,raɗaɗinshi na iya zarce na ƙunar wuta,abusufyan bazan ce kayi laifi ba,amma kasan cewa dole ne dama kaga badai dai ba!kayi aure batare da sanin mahaifiyarka ba,baka sanar mata ba balle tasanya albarka acikin auren naku,kunyi komai a6oye kai da gwaggon katsina,sai gashi yau Allah ya bayyana mana komai,nasan kai kanka kayi mamakin ganin Ƴa'ƴanka su duka ukun a ƙarƙashin kulawar gidan mu,kaɗan daga cikin Ikon Allah kenan!kwata kwata yaran basu san suna da dangi ba,garari kawai sukeyi a wulaƙance cikin gari,mu ma haka bamu son cewa akwai wasu ƴa'ƴa waɗanda suka kasance jinin mu ne su ba,babu wanda yasan haka,amma cikin ikon Allah da yake shi hakimun ne,sai gashi silar aikatau ɗaya ta faɗo hannunmu,yayin da silar ciwon ɗaya daga cikinsu da aka kai asibiti Allah ya ƙaddara haɗuwarsu da Omar yayin da shi kuma yaje wurin ɗan uwanshi Dr haris,lamarin ubangiji girma gare shi!gaba ɗaya Allah ya haɗa yaran a wurinmu ta hanyar da bamu ta6a tsammani ba,kamar yadda kai da gwaggon katsina baku yi tsammanin abunda kuka aikata asirrance zai tonu ba,tunda baku sanar mana ba sae gashi Allah ya sanar damu,su kansu yaran basu yi tsammanin zasu haɗu da dangin ubansu na asali ba,su dama basu da masaniya akan wanine ubansu......' Dakatawa abba yayi da maganar yana kallon abusufyan dake ta faman shessheƙar kuka muryarshi na kerma ya shiga cewa"Ya Allah ka yafe mun kuskuren dana aikata na auren abu batare da sanin mahaifiyata ba da kuma dangina ba......tun farko nine silar jefa rayuwarsu Cikin halin da suka tsinci kansu,da ace ban 6oye ma kowa ba,duk da ammi bazata barni in auri abu ba amma ina da tabbacin cewar Abbanmu salahuddeen zai aura mun ita inna nasanar mashi,iyakaci dae Ammi zata zangwameta ne daga baya kuma nasan zata fara sonta,wlh ni sam tunanin hakan baizo mani ba a wannan lokacin,idona ya makance,kuma ba laifin gwaggon katsina bane,Son da takeyi mun ne yasa ta aikata hakan don ta faranta mun ganin halin da na shiga a lokacin jin cewar Mommynmu ba zata bari in auri abu ba,gashi na mutu akan sonta kaicona.......'fashewa yayi da wani sabon kukan,dana sani kenan irin wadda ba'ason yinta,abun yayi ta maka ciwo azuciyarka,shiyasa kullum muke cewa Allah ya tsare mu daga aikata aikin danasani,saboda bai da daɗi,ɗaci gare shi,     Ba ƙaramin tausayi yaba Abba ba,tuni shima hawaye suka fara sauka akan fuskarshi,janyo abusufyan yayi ajikinshi sosai ya rungume shi yana lallashinshi,   A ƙarshe yace"Abusufyan ka manta da duk wani abu daya faru dazun,yanzu lokacin farin cikine,yakamata ka nuna godiyarka ga Allah subhanahu wata ala daya nuna maka wannan ranar da ya haɗaka da triplet ɗinka dukkansu da ransu kuma da lafiyarsu!wlh abusufyan dana ga yaran nan amatsayin ƴa'ƴanka kaɗan ya hana in buga tsalle saboda murna.....'yayi maganar yayin da suka raba jikinsu dana juna,   tallabo fuskarshi abba yayi cike da zolaya yace"Kasan me?   Abusufyan ya girgiza mashi kai alamar a'a,   Abba yace"nifa ɗazu dana ga ka firgita da ganin yarinyar nan nayi tunanin cewa ko ka ƙyasa ne,har ina cewa shikenan lokacin barin gwaurantakar abusufyan yayi aduniya ashe ashe uban ne gaba ɗaya........'   Ya ƙarasa maganar yana dariya,murmushi abusufyan ya ɗanyi,   Abba ya kuma cewa"Wai yanzu nan duk aikinka ne waɗannan abusufyan?ashe dae ƙanin nawa bana wasa bane...'   fashewa da dariya abusufyan yayi tare da sunnar da kanshi ƙasa,   Hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Abba ba,dama so yake ya sanyashi farin ciki don ya gusar mashi da damuwar da yake ciki,   dafa kaɗarshi abba ya kuma yi tare da cewa"duk haihuwata ya'ya goma sha takwas akan su jahan ne kawai na samu ƴan biyu,amma kai da yake mai sa'a ne,na ku ba irin namu bane sai gashi ka haifa mana ƴan uku reras!ko Ya ammi zata ji in taga ƴa'ƴan mara jin maganar nan nata abusufyan....nasan zata ce shegen bisa zai aika ae,   Wannan karan atare suka fashe da dariya, Daga bisani Abusufyan yace"yaya hussein inaso naga yaran nan sosai,na damu dasu wlh....'   Wani irin kallon rainin wayau Abba yayi mashi kafin yace"yau naga ikon Allah!ni kake fadama kana son ganin ƴa'ƴanka?Yaran nan fa naka ne halak malak,ae ni nama yi tunanin a wurinsu zaka kwana,saboda suna buƙatarka sosai atare dasu,yanzu basu da burin daya wuce suga mahaifinsu atare dasu,"   Wani irin daɗi ne ya lullu6e abusufyan yace   "Zan iya zuwa wurinsu yanzu"? Abba yace"Ka bari mu dawo daga masallaci inyaso kai tsaye kawai sai ka wuce wurinsu,"   Fuskar shi ɗauke da farin ciki yace"okey,bari naje nayi alwala,"   Abba yace"muna jiranka a main palour in ka kammala,ka same mu acan,"   Yana ƙarasa maganar tashi ya juya tare da nufar ƙopar ɗakin nashi ya fuce tare da tura masa ƙopar,   Toilet abusufyan ya shiga batare da 6ata lokaci ba,ya ɗauro alwalar, Lokacin daya fito babban falon anan ya same su kowannansu ka kalla zakaga alamun damuwa a fuskokinsu,wasu ma da alama basuyi bacci ba,musamman Marshal Omar babu alamar yayi bacci adaren jiya,hatta Sgr ma akwai alamun rashin isasshen bacci atattare dashi,taya zaiyi bacci sayyadi na yawo acikin gari,shi fa in ya ƙullaci mutun irin haka har sai yaga bayanshi sannan yake samun kwanciyar hankali,su twins kuwa fuskokinsu sunyi jawur su da fawan,kowa dae da damuwa aranshi, Bayan sun kammala haɗuwa suka wuce masallaci atare, Tura ƙopar ɗakin nasu azmee tayi don ta tashe su sallar asuba,ba ƙaramin mamaki tayi ba,ganinsu ajere suna sallah,kowaccensu na sanye da dogon hijabi a jikinta hijjaban sehrish ne hosana da jahad suka sanya,abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,dama indae suna tare su ukun,musamman in akace maka akwai jahad atare dasu tofa basa wasa da ibada,duk da itama Sehrish ɗin ba daga baya ba,amma jahad ɗin itace kan gaba,saboda ita ba'a tashinta sallar asuba da zarar anfara kiran sallar asuba duk nisan baccin da tayi zata farka ne da kanta,abun sama rai ne da kuma sabo da yi,da kuma imanin mutun, *Murmushi kawai azmee ke saki tana kallonsu gwanin ban sha'awa,ƴa'ƴan abusufyan,jikokin Ammi da salahuddeeen,ƴa'ƴan ƙanin Abban sojoji Abusufyan,ƙanne ga Marshal Da Sgr duk su kaɗae,abun farin ciki abun murna!yanzu su sun zama abunso wlh,yayyansu gaba ɗaya sojoji har goma sha takwas,ko sauro ne yayi gigin Cixon fatar jikinsu sae yaji saukar alburushin bindiga asaman goshin shi* 🤣 Azmee na tsaye tana kallonsu taji alamun motsin mutun a bayanta,jin an dafa ta yasa tayi firgit ta ɗan juya,Hajiya azeema ce jikinta sanye da hijabi blue,hannunta ruƙe da carbi,fuskar nan ɗauke da murmushi tace"Nazo ganin ƴa'ƴanmu ne,idan ba damuwa ki bani hanya in wuce ciki,"   Murmushi azmee tayi tare da matsa mata hanya ta wuce ciki,sai da ta shiga ciki sannan azmee tabi bayanta tana cewa"sallah nazo in tashe su suyi,shi ne na same su ashe har sun tashi ma,abun ba ƙaramin burgeni yayi ba dana gansu ajere su ukun suna sallah,'   Murmushi hajiya azeema tayi ayayin da take zama daga gefen gadon su tace"Albishirinki,"tayi maganar tana kallon azmee,   Azmee tace"Goro," "Fari ko ja,"cike da zolaya tayi maganar,   "Fari dae,shi ne ke tare da alkhairi,wannan launin jan alamace ta hatsari," Dariya hajiya azeema tayi kafin tace"Tab jiya anyi babu ke!Labari da ɗumi ɗuminsa!zazzafan gaske....'   A ƙagare azmee tace"Meya faru"! A lokacin su jahad sun sallame sallah,suna zaune saman dardumar suna sauraransu, Nuna su hajiya azeema tayi tare da cewa"Ke wai ashe yaran nan ƴa'ƴan abusufyan ne!!!"   Gaban azmee ne ya faɗi Rasss!saboda yadda maganar ta dirar mata kai tsaye acikin kunnuwanta,   "Wai dagaske"?tayi tambayar cike da mamaki,   Hajiya azeema tace"hmmmm ke dae bari,wani iko sai ubangiji,dagaske fa nake,babu wanda baiyi mamakin wannan abun al'ajabin ba,yara dae ƴa'ƴan ƙaninmu ne sufyan,'   Juyawa azmee tayi tana kallonsu sehrish da sukayi zuru suna kallonsu musamman Sehrish da batasan kan zancen ba,saboda bata a hayyacinta lokacin da akayi maganar,amma lokacin da jahad ke bada labarin rayuwarsu taji komai a kunnanta kuma daga nan ne Sihirin jikinta ya lalace saboda tunaninta daya rinjayi kwalwarta harta tariyo dukkan abunda ya faru arayuwarsu ga kuma addu'ar da Sgr keta yi mata acikin kunne, Cike da mamaki azmee tace"taya akai hakan ya faru?dama abusufyan ya ta6a aure ne kenan?    Ataƙaice azeema ta bata labarin yadda abusufyan ya auri abu batare da saninsu ba,har suka samu ƙaruwar ƴan uku,'   Wani irin farin cikine ya lullu6e azmee saboda tsabar farin ciki bakinta yaƙi rufuwa,    "Jahad!dagaske ne abunda kunne na ke jiyo mun"?sehrish ce tayi maganar tana kallon jahad da tsananin mamaki,   Murmushi jahad tayi ta jinjina mata kai alamar eh,ta ƙara da cewar"jiya duk baki a hayyacinki,abun farin cikin nan ya faru,Mun jima muna wahalar rayuwa ashe muna da dangi mai girma irin wannan bamu sani ba,cikin ikon Allah kuma sai gashi Allah ya haɗa mu dasu ta hanyar da bamuyi tsammani ba,ina tunanin addu'ar da muka jima munayi ne Allah ya kar6a mana,Ashe oumman mu sai da ta fara auren uncle ɗin su abusufyan sannan ta auri wannan fasiƙin mutumin sayyadi,da cikinmu ta shiga gidan shi........'   Aruɗe sehrish tace"taya hakan zai yiwu?   Hajiya azeema ce ta katse ta da cewar tabbas zancenta gaskiya ne sehrish!ku ƴa'ƴan ƙaninmu ne Abusufyan,sai da ya fara auren mahaifiyarku sannan Mugun mutumin nan daya ƙuntata rayuwarku ya aureta.......'gaba ɗaya hajiya azeema ta kwashe labarin rayuwar mahaifiyarsu agidan gwaggon katsina da kuma haɗuwarsu da abusufyan har izuwa rabuwar aurensu ta auri sayyadi ta sanar ma Sehrish,'   tun kan takai ƙarshen labarin nata,Sehrish tayi sujjada,tana shessheƙar kuka,saboda tsabar farin ciki,Ashe ita ɗiyar uncle ɗinsu ce abusufyan?hakan na nufin su Babban yaya ƴan uwanta ne na jini!haba no wonder ae shaƙuwar dake tsakaninta da junaid tayi yawa,kai kana ganin abun zakasan cewar akwai alaƙa ta jini ajikinsu,ta damu da mutanen gidan sosai,ashe danginta ne su ɗin,   Jikin azmee ba ƙaramin sanyi yayi ba bayan hajiya azeema ta sanar mata irin zaluncin da sayyadi yayi ma su Sehrish,har idanunta sai da suka cicciko da kwalla saboda tausayinsu da taji,ta jima tana tsinar sayyadi acikin zuciyarta, Muryarta tamkar zatayi kuka tace"dama ina ta son mu samu lokaci Sehrish ta bani tarihinta wllh,ashe haka suka sha ukubar rayuwa bayin Allah,kai koma wanene wannan mugun mutumin ya cika babban azzalumi,saboda tsabar zalunci ya raba yara da mahaifinsu ya kuma ƙuntata rayuwarsu,duniya ina zaki damu.......'azmee na cikin magana,Abusufyan ya turo ƙopar ɗakin bakinshi ɗauke da sallama,gaba ɗaya hankalin su sehrish ya dawo kanshi,shi ma kuma yana ɗago idanunshi suka sauka akan ƴan ukun nashi,kwata kwata ma bai lura da hajiya azeema da kuma azmee dake a ɗakin ba,Su sehrish kawai yake kallo cike da so da ƙauna,ko kyaftawa baiyi,kamar ya haɗiye su haka yake ji,kamar yadda yake jinsu haka suma suke jinsu,sae ƙare mashi kallo suke yi kamar su watsa a guje su rungumo shi haka suka dinga ji,ta wani 6angaren kuwa abun ba ƙaramin yawo yake yi masu akai ba,Wai nan mahaifinsu ne halak malak,ubansu wanda yayi silar zuwansu duniwa,dama suna da uba da dangi a duniya?tambayoyi iri iri suke shiga yiwa kansu,   Ganin sun zubama juna ido tsakanin Abusufyan da kuma su sehrish dake zaune saman darduma suna kallon shi,hakan yasa hajiya azeema tayi masu gyaran murya hankalinsu ya dawo kanta sannan tace"Zaman me kuke yi ne?baku ga mahaifin naku bane?ba zaku zo ku rungume shi ba,kuji ɗumin mahaifinku a jikinku?   jin wannan maganar ta hajiya azeema yasa su miƙewa gaba dayansu jiki na rawa suka ƙarasa wurin shi, Tunkan su ƙaraso ya buɗe masu hannayenshi alamar su shiga ciki,haɗasu yayi dukansu ya rungume su sosai ajikinshi kamar zai maidasu cikin cikinshi,hawaye ne suka shiga gangarowa a idanuwanshi da kuma idanuwansu sehrish,bai ta6a tunanin zaiga wannan ranar ba,yau gashi ga ƴa'ƴanshi sun dawo wurinshi,tabbas Allah ne ya kar6i addu'ar daya jima yana yi,atare suka ɗago idonsu cike tab da hawaye suka haɗa baki wurin cewa"Abba," Har cikin zuciyarshi yaji wani irin sanyi ya ratsa shi,muryarshi akasalance yace"Ku sake maimaitawa banji ba," "Abba,"suka maimaita mashi kamar yadda ya umarta, "Wlh kunyarku nake ji!duk wani abu daya faru arayuwarku ni ne sila,Na cuci rayuwarku,Naji na tsani kaina ƴa'ƴana suna a wani hali na rayuwa amma nagaza taimakonsu,zan iya zuƙunnawa saman guiwaowina agabanku domin in nemi gafararku.....,'tunkan ya ƙara maganar gaba ɗaya ya tafi zai zuƙunna saman guiwowins,cikin sauri suka rurruƙe shi suna cewa"Abba dan Allah kada kayi mana haka bamu so,ka daina ɗaura laifin akanka,dama Allah ya riga da ya ƙaddara faruwar hakan,dan Allah kada ka zuƙunna agabanmu,mu fa ƴa'ƴanka ne, Ganin dagaske kneel down zaiyi agabansu yasa suka riga shi zube wa saman guiwowinsu,tsayawa daga tsaye yayi yana kallonsu,Azmee da hajiya azeema duk suna kallon abunda ke faruwa,ba ƙaramin tausayi suka basu ba,   "Abusufyan"! Hajiya azeema ce ta ambaci sunanshi,amsawa yayi yayin da ya mayar da idanunshi akanta,   Anatse ta soma magana"yanzu ba lokacin baƙin ciki bane ko lokacin tuna baya,Lokacin farin ciki ne wannan,dariya yakamata in dinga gani a fuskar kowannanku ba hawaye ba,ko ba haka ba azmee?tayi tambayar tare da mayar da idanunta kan azmee, Murmushi azmee tayi kafin tace"Wannan haka yake,Abusufyan ina tayaka Murna sosai,nayi farin ciki mara misaltuwa,naji daɗi da sehrish ta kasance ƴarka ce,ko ince suka kasance ƴa'ƴanka ne,lamarin ubangiji da girma yake,babu wanda ya ta6a tsammanin haka,naji ma ina ganin kamannin fuskarka a fuskar sehrish ashe ƴar kace.....'magana take hawayen farin ciki na gangarowa daga fuskarta,    Murmushi kawai abusufyan ke saki,a lokacin harsu Sehrish sun miƙe tsaye suna tsaye akusa dashi,hosana ta rurruƙe hanunshi kamar wani zai kwace mata shi, Hajiya azeema ce tace"Azmee yakamata mu basu wuri su gana da juna,don na lura da yadda Uban ƴan ukun nan ke zumuɗi akan ƴa'ƴanshi,"cike da zolaya ta ƙarasa maganar tare da miƙewa taja hannun azmee suka fuce suna dariya,   Ajiyar zuciya ya sauke tare da mayar da idanunshi kansu jahad yace"kun samu bacci kuwa jiya?ya tambayesu ne saboda fuskokinsu daya gani duk a yamutse,musamman idanunsu sun ƙanƙance, Haɗa baki sukayi wurin cewa"Eh,"   Hosana tace"abba,dagaske kaine Abban mu ko?   "Ga zahiri kin gani,"yayi maganar yana yi mata nuni da fuskarshi,murmushi suka saki gaba ɗayansu,   Sun jima atsaye tare dashi suna magana jefi jefi saboda basu saba da juna ba,duk jin abun suke wani iri haka,kamar mafarki ne suke yi ba gaske ba,    "Ku koma ku kwanta,kuyi bacci ku huta,idan har akwai inda keyi maku ciwo ku sanar mun zansa aduba ku yanzun nan....'wannan maganar tashi ba ƙaramin sanyaya masu jiki tayi ba,   "Abba,lafiyarmu qalau,babu abunda ke damun mu,'suka faɗi hakan atare, Gyaɗa kanshi yayi tare da kama hanya zai juya da nufi yabar ɗakin nasu, Cikin sauri jahad ta ruƙo hannunshi tare da cewa"Abba,dan Alla kada ka tafi kabarmu,muna buƙatarka a kusa damu,muna so mu kasance tare da mahaifinmu,' Sehrish ta kar6e da cewa"hakane Abba,ka dawo mu zauna atare dakai,muna buƙatar kyakkyawar kulawa daga wurinka,' tana kai ƙarshen maganar hosana tace"Abba pls,ko don saboda Ni," Wani irin murmushin farin ciki abusufyan ya saki yana kallonta,batare da 6ata lokaci ba,suka wuce saman gadon nasu,a tsakiya suka sanya abusufyan,yayin da suka kwanta gefe da gefenshi,sosai ya rungume hosana ajikinshi,duk in ya tuna labarin yada ta samu ta6in hankalinta nan take sai yaji idonshi sun ciko da kwalla, "Idan Allah ya kaimu gobe,da kaina zan gyara maku gashin kanku inyi maku kalaba guda biyu,kamar yadda na ta6ayi maku Lokacin da kuna yara,nasan ba zaku iya tunawa ba,' Jikinsu ne yayi wani irin sanyi, wani irin yanayi suka shiga gaba ɗayansu,    *💋Boss Bature💋* "Allah ya kaimu lpy,Abba,'jahad da sehrish ne suka haɗa baki wurin bashi amsa, Abusufyan yace"ba abba zaku dinga kirana ba,saboda ana kiran Yaya hossein da Abba,abun zai dinga ruɗa mutane ne arasa gane wani abban kuke nufi,amma ku dinga kirana Daddy,saboda a bambanta sunan,ina fata haka yayi maku? "Eh daddy,"suka haɗa baki wurin bashi amsa,hakan ba ƙaramin daɗi yayi mashi ba,   "Abba ita Oumman mu fa?dagaske ne ta haukace kuma tana saman bola tana hauka kamar yadda gwaggon katsina tace?kuma wanene majnun ɗin da naji gwaggo tace shi ya koya ma oummanmu hankali,'hosana ce tayi maganar,jahad tace"Ke fa matsalarki kenan baki da kan gado,tunda kika ji ance Majnun ae kinsan wa ake nufi,'Murmushi Abusufyan yayi yana sauraronsu,   Sehrish tace"dan Allah ku daina magana,kuna takurama daddynmu bacci fa yake ji,baku ga idanunshi ba,    Mayar da idanunshi yayi kan sehrish data aza kanta asaman kafaɗarshi,kafin ya mayar da idanunshi kan jahad itama tana manne dashi,ga hosana kuma data manne mashi asaman chest ɗinshi,kamar zata koma ciki,Allah kaɗai yasan irin farin cikin da yake ji acikin ranshi,daɗi kamar ya kashe shi,babban burinshi Ammi tazo taga yaran daga zarar ta amince dasu,bai da wata sauran damu,zancen sayyadi kuma ya gama sama ranshi lokacin mutuwarshi yazo,Saboda Case ɗinshi na hannun Zaki da damusa,tabbas sai ya ɗandani kuɗarsa,   "Daddy,bakace komai ba!oumman mu fa muna so mu sake ganinta atare,"muryar hosana ce ta dawo dashi daga zurfin tunanin daya shiga,firgit ya danyi tare da sanya hannunshi ya shafa kanta yace"Kada ku damu,insha Allah komai yazo ƙarshe,Oumman ku duk inda take bi'iznillahi za'a ganota ne,inason komai ya lafa ne,daga ni har ku mu samu kwanciyar hankali sosai,sannan zan fara sanyawa a binciko mun makwabtan nan naku,ina da tabbacin cewa za'a samu wasu bayanai masu muhimmanci a wurinsu,"   Ba ƙaramin daɗi suka ji ba,burinsu oummansu itama tashigo cikin wannan daular suci gaba da rayuwa acikin family ɗin Abbansu,   "Daddy Allah ya taimaka,kuma ya baku sa'a akan duk wani yunƙuri da zakuyi na ganin kun kawo ƙarshen Mugun mutumin nan dashi da duk wani wanda yake da hannu akan cutar da zuri'armu,Allah ya tonu asirinsu,kuma Allah ya bayyanar da Oumman mu da ranta,Insha Allah daga rana irin ta yau zamu kasance kullum muna taya ku addu'a saboda asamu nasarar kama ya sayyadi,'murmushi abusufyan yayi yana sauraran maganar jahad,bayan ta kammala maganar Sehrish tace"insha Allah daddy zamu tayaku da addu'a kuma zamu jajirce wurin ganin mun bada gudummawa wurin binciken gano waɗanda ke da hannu akan cutar da zuri'armu,duk da mu mata ne muna da rauni,amma hakan bazai hanamu miƙewa tsaye ba wurin kawo ƙarshen Ya sayyadi da kuma ire irensa,shaiɗanun dake take masa baya,'   tana kai ƙarshen maganarta hosana tace"Abba don Allah Idan kun gano ya sayyadi,inaso abani damar da zan fasa mashi tsakiyar goshin shi da bindiga,ko in harbi saitin zuciyarshi ta daina bugawa,"   Dariya sosai abusufyan yayi yana sauraron kalaman hosana,   "Hosana,ae idan ya mutu ta hanyar harsashin bindiga sai inga kamar yayi mutuwar sauƙi ne,nafi so ya rayu tamkar matacce,gashi da rai amma baida wani sauran amfani,shi kanshi sai ya dinga roƙon Allah ya ɗauki ranshi ya mutu ya huta,a tunanina ba,amma abunda nake gani yakamata mu shirya mashi mummunan ƙarshe,wacece acikinku zata bamu idea?yayi tambayar yana jiran amsoshinsu,   Kowacce da irin shawarar da take bayarwa akan yadda za'a shiryama ya sayyadi mummunan ƙarshe,bad ending kenan,ba kamar hosana tafi kowa bada mummunar shawara,daga bisani kuma suka fara tsara ma kansu Happy life bayan an kashe ya sayyadi da tawagarsa,zasu fita ƙasashe daban daban yawon shaƙatawa tare da daddynsu,oummansu da kuma ƴan uwansu,araina nace hada mazajanku ko abun kamar zaifi bada citta harda kanunfari.......' Bacci ne ya ɗaukesu atare manne da juna saman gadon,abun gwanin burgewa uba da ƴa'ƴanshi masu kama guda. Har wuraren ƙarfe goma na safe basu farka ba,dama sun tara bacci sosai a idanunsu,har Abbansu junaid sai da ya leƙo ɗakin ya same su a baje suna sharar bacci murmushi ya saki,tare da curo wayar shi daga Aljihun rigar jikinshi,hoto ya ɗaukesu kusan guda uku,bayan ya kammala ya maida masu ƙopar ɗakin ya rufe, Bayan ya fita daga sashen su kitchen ya nufa a lokacin Azmee harta kusa kammala aikin breakfast,yayi mamakin ganinta ita kadae tana ta faman aiki,   Tana ganinshi ta ajiye aikin da takeyi ta ƙaraso gaban shi tare da gaishe shi cikin girmamawa tace"barka da safiya Abba,antashi lpy?jiya sai muka ji abun farin ciki,Hajiya azeema ke sanar dani wai ashe su sehrish ƴa'ƴan Abusufyan ne,Wlh nayi farin ciki sosai,dama na jima ina ganin kamanninta da Shi,'. Fukarshi asake yace"wllh Alhmdllh,mun Samu ƙaruwar ƴan uku,ni dai ince jiya banganki ba,ae naso ace agabanki akayi komai,kema kiji wannan abun al'ajabin da kuma tashin hankalin,labarin dae babu daɗin ji,Amma ta wani 6angaren kuma mun gode ma Allah da ya bayyana mana yaran nan amatsayin jinin mu,munyi farin ciki sosai,har Walima ma nake so asake shirya mana saboda yaran nan,' Murmushi azmee tayi tare da cewa"Yaushe kenan?ko yau zamu fara shiryawa ne"?   Girgiza kai Abba yayi alamar a'a sannan yace"Wannan walimar ta musammance,gagarumin shagali za'ayi,akwai buƙatar kwanciyar hankali kafin lokacin,amma zanyi shawara da Abusufyan,idan har muka tsara komai,zan sanar maki,don ku shirya tarbar baƙi,zamu sa aƙaro wadanda zasu tayaki aiki.....'   Tunkan yakai ƙarshen maganar azmee tace"a'a Abba,zan iya ni kaɗai,basai an ƙaro masu aiki ba'   "Okey,ba damuwa naga kina ta wahala ke kadae,wai nikam ina yarinyar nan take ne?wata ƴar fara kanwarsu laila?naga kamar atare kuke aikin girki da ita ko ta koma gida ne"?   Azmee tace"a'a bata koma ba,bata jin daɗin jikinta ne,shine nace mata ta huta kawai,in taji sauƙi taci gaba da tayani,saboda yarinyar akwai son aiki,' Jinjina kai Abba yayi tare da cewa"Allah ya bata lpy,bari zanyi ma Kanal yousouf magana ya dubata...'   Cikin sauri azmee tace"A'a....ae na bata magani dama ciwon ciki ne,insha Allah zata warke,'    "Okey,' ya ambaci hakan tare da fucewa ya wuce cikin main palour dinsu,   Zama yayi saman sofa yana murmushi,bakomai yake tunawa ba face yadda yaga abusufyan tare da ƴan ukunsa,aranshi yace"Allah sarki,rayuwa kenan komai mai wucewa ne in bawa yasa haƙuri aransa,junaid tun yana jinjiri rabonshi da mahaifiyarshi,sai gashi jiya rungume da ita yana bacci,ƴan ukun abusufyan tun suna ciki rabonsu da ubansu, tun kafin cikinsu ya bayyana ma,sun sha wahalar rayuwa amma sai gashi komai na rayuwarsu ya canza yanzu tamkar basu ta6a shiga wani ƙuncin rayuwa ba,sannu a hankali zasu manta da duk wata uƙuba da suka sha arayuwarsu,Yau dae gasu can rungume da mahaifinsu suna bacci,Allah sarki, A ƙarshe kuma yace"Oh,ni kuma gani nan babu mai rungumata,abusufyan nacen rungume da ƴa'ƴan shi,junaid ma na can manne da mommynsu,gaskiya nayi kewarsu sosai......' "Abba!" karaf kiran ya sauka a kunnanshi a ɗan firgice ya juya don yaga wanene,bakowa bane face Junaid yana tsaye hannunshi ruƙe da waist ɗinshi,har yanzu shaddar jiya ce ajikinshi,fuskar nan tashi cike da annuri sai faman zabga murmushi yake yi yadda kasan wanda akayi mashi albishir da gidan Aljana,   Wani irin farin ciki ne ya lullu6e abbansu,yunkurawa yayi zai miƙe tunkan ya ƙarasa miƙewar junaid ya watsa da gudu kai tsaye ya faɗa jikinshi sosai ya rungume shi yana faɗin"I really miss u Abba,'   "Nima junaid nayi kewarka sosai,jiya da tunaninka na kwana araina,'yayi maganar yana ɗan bubbuga bayanshi,    raba jikinsu sukayi dana juna,ganin abbansu na kallon bayanshi yasa shi cewa"Abba mommy ko?   murmushi yayi tare da cewa"Ashe ka gane,ta ina ne?ko ba tare kuka zo ba?   ɗan ta6e baki junaid yayi nan fa hankalin abbansu ya tashi,. Jiki asanyaye yace"Junaid bazata zo ba ko?Allah yasa dae ba Australlia ta koma ba,dama tunda na ganka kai kadae gabana ya fadi,don nasan halinta,'   Fashewa da dariya junaid yayi ganin yadda Abban nasu ya tashi hankalinshi don baiga mommynsu ba,   ɗaure fuskarshi yayi"oh ka ɗauki abun wasa ko?ba zaka faɗamun ina take ba,' Yana cikin maganar ya jiyo takun takalminta,baisan lokacin daya janye junaid gefe ɗaya ba,Zuba mata ido yayi yana kallonta fuskarshi ɗauke da murmushi,tsayawa tayi tana ƙare mashi kallo,ba ƙaramin kyau tayi ba saboda kwalliyar da junaid yayi mata,da kanshi ya shafa mata janbaki ya gyara mata jagirar idonta,duk da haskenta sai da yashafa mata hoda,wai don Abbansu ya ganta da kyau,kuma shi da kanshi ya za6a mata rigar da zata sanya,jallabiya ce brown colour mai kyan gaske tayi rolling mayafi akanta,kamar wata balarabiya,tayi haske sosai kamar wata fatalwa,ga tsayi dake gareta kamar Sgr,    Komawa junaid yayi saman sofa yana kallonsu,jira yake yaga mai zasu yi,sun wani ƙura ma juna ido,sae murmushi yake saki, Cigaba da tafiya tayi harta ƙaraso kusa dashi suna fuskantar juna,   Waro ido waje junaid yayi tare da cewa"Anshiga uku,Abba kaga yadda ka koma agaban mommy,wai dama ahaka kukayi aure Wayyo Allahna'   maganar junaid tasa suka fashe da dariya gaba ɗayansu,shi abunda ya bashi mamaki tsawonta agaban abban nasu,sae yaga abban nasu ya koma mashi guntu,   Sun jima suna sakar ma juna murmushi kafin daga bisani suka rungume juna sosai,kamar zasu zama daya,ba ƙaramin kewar juna sukayi ba,duk da akwanakin can baya yana kai mata ziyara Australlia,daga bayane ya daina zuwa saboda abubuwa da sukayi mashi yawa,   Kasa rabuwa sukayi da junansu,junaid kuwa ya tasa su gaba yana kallonsu kamar wanda ya samu television,   Adai dai lokacin twins suka shigo cikin falon,sakamakon Yunwa data ciwo su,karaf idanunsu suka sauka akan Mommynsu dake rungume da Abbansu,har suna haɗa baki wurin Cewa"Mommy!" Cikin sauri suka raba jikinsu dana juna,wurga idanunta tayi akansu jahan da ayaan dake tsaye suna kallonta fuskar kowannansu ɗauke da farin ciki,   Da gudun gaske suka ƙarasa inda take gaba ɗaya suka faɗa jikinta,haɗasu tayi duka ta rungume ajikinta,tuni taji hawaye sun cicciko a idanunta,tayi kewar ƴa'ƴanta sosai,muryoyinsu tamkar zasu yi kuka suka haɗa baki wurin cewa"we really missed u mom!ashe zamu sake ganinki acikin gidanmu,'suka ƙarasa maganar ayayin da suke raba jikinsu da nata,   Hawaye tagani a idanunsu,cikin sauri ta sanya hannunta tana share masu hawayen muryarta na rawa saboda kukan daya zo mata daƙyar ta iya cewa"i missed u too my twins,nasan ban kyauta maku..... '   Jahan ya katseta"Mommy abubuwa da yawa sun faru,wanda da ace kina tare damu na tabbatar cewar bazasu faru ba,mun yi rashinki akusa damu mommy,munyi kewarki......'   "Mommy..amma dae ba zaki sake komawa ba ko"?acewar ayaan Jinjina mashi kai tayi alamar eh sannan tace"nadawo kenan bazan sake komawa ba,I will be with u,for the rest of my life....."   Murmushi kawai Abbansu ke saki yana kallon uwa da ƴa'ƴanta,abubuwan farin ciki dae sai faruwa sukeyi acikin gidan,   "Mommy,kinga junaid ko ya girma sosai,yayi kukan rashinki sosai lokacin da baki nan,amma yanzu nasan cewar zaki bashi kulawa,dan Allah mommy ki bashi kyakkyawar kulawa saboda yafi kowa buƙatarki,'ayaan ne yayi maganar yana kallon junaid dake zaune yana ta faman murmushi, Itama kallon nashi tayi tare da cewa"Insha Allah ayaan,daga yanzu junaid zai canza gaba ɗaya,zan bashi kyakkyawar kulawa,bama shi kadae ba hada ku gaba dayanku,Amma banga fawan ba dasu Irfan,and kanal yousouf ko duk suna ciki ne"?   Jahan yace"basu tashi daga bacci ba,bari naje na kira maki fawan ɗin,' Dakatar dashi tayi da cewa"A'a kada ka tashe shi daga bacci,nasan daga ya farka yaji labarin zuwa na zaizo ne,but where is Alexander?   Atare suka haɗa baki wurin cewa"Mommy wanene Alexander kuma"?   Dariya Abbansu yayi tare da cewa"tana nufin Babban yayanku,ae sunan data raɗa mashi kenan ko kun manta,'   "Ae mun saba da kiranshi da babban yaya,mun manta da wannan sunan,shima yana a bedroom ɗinshi,duk bacci sukeyi saboda jiya bamu samu isasshen bacci ba,   Abba ne yayi mata nuni da 3 seater din dake gefensu yace"bismillahi,ki zauna mana ko baki gaji da tsayuwa bane,ko da yake na tuna fa Soja ce matar tawa,'yayi maganar cikin zolaya,   Murmushi kawai tayi tare da samun wuri ta zauna,shima abban nasu ya zauna daga gefenta,wuri su ayaan suka samu saman 2 seater suka zauna, Cike da kulawa tace"Amma meya hanaku samun bacci da wuri ne?naji kunce baku samu isasshen bacci ba ko wani abu ya faru ne'?    Ayaan yace"abun farin cikine ya faru jiya agidan nan mommy,nasan kin kwaso gajiyar tafiya,idan kika huta nasan cewa Abba zai baki labari anjima,"   Da sauri junaid yace"meya faru ne?dan Allah ayaan ka faɗa mana yanzu kawai,Mommy fa tun jiya tazo ƙasar nan,muna acan tare da ita agidanta ma muka kwana,bata sanar ma kowa ba,sae abban mu,'   Baki sake jahan yace"Wai dagaske?mommy abun ƴar haka ce,wato shine mu ba'a sanar mana da zuwan naki ba,junaid kawai kika sanar mawa,no wonder shiyasa jiya ban ganka ba,abun ya tsayamun araina,ba don abunda ya faru ba na bayyanar ƴa'ƴan uncle ɗinmu daba abunda zai hana mu nemeka a wannan lokacin,duk wannan abun shiya ɗauke mana hankalinmu....."tunkan ya ƙarasa maganar Junaid yace"Ƴa'ƴan uncle?wani uncle ɗin kenan"?aɗan rude yayi maganar,   Miƙewa Ayaan yayi tare da ruƙo hannun junaid yabar wurin tare dashi,sai da suka samu wurin da bakowa sannan yace"kai kasan meya faru jiya"?   Cike da zumuɗi junaid yace"taya za'ae in sani,ni da bana agida,don Allah ka sanar dani har naƙosa naji,' Ayaan yace"hmmmmm,labari da ɗumi ɗuminsa,ko kasan cewa yarinyar nan Sehrish ɗiyar uncle ɗinmu ce Abusufyan?   Gaban junaid ne ya faɗi rasss!saboda yadda maganar ta dira a kunnanshi,can kuma ya ɗan ɗaure fuskarshi yace"pls Ya ayaan dan Allah ka daina jamun rai,ni dae ka faɗimun gaskiyar abunda ya faru,'   Ayaan yace"kai nifa bada wasa nake maka ba,na ta6a maka wasa irin wannan ne!Sehrish ɗiyar uncle ɗinmu ce abusufyan,   Tur6une fuska junaid yayi tare da ɗan bubbuga ƙafarshi rai a6ace yace"yaushe uncle ya ta6a aure da har zai haifi ƴa'ƴa,kuma ma ƴar tashi ka rasa wadda zaka ce sae sehrish,kaji tsoran Allah ya Ayaan,babu kyau ƙarya,'   Rai a6ace Ayaan ya dunguri goshin junaid tare da cewa"Shashasha,ana ƙoƙarin a fahimtar dakai amma kaƙi yadda,don ubanka kaje ɗakin nasu ka leƙa,zaka ga abun mamaki,'   Turo baki junaid yayi tare da juyawa ya nufi hanyar xuwa ɗakin sehrish yana cewa"mai ƙarya dae ɗan wuta,'   Murmushi ayaan yayi yana kallon bayanshi,yasan cewa muddin junaid yaga Sehrish da ƴan uwanta sai ya haukace masu,farat ɗaya bazaiyi tunanin ƴan uku bane,sae ranshi ya fara bashi cewar Aljanune, aikuwa,junaid na ƙarasawa kopar dakin,a hankali ya sanya hannunshi tare da tura ƙopar dama a buɗe take,zura ƙafarshi ya fara yi kafin ya ƙarasa shiga bedroom ɗin,koda baby junaid ya shiga ciki bai kai idanunshi kansu ba,sae da ya fara rufe ƙopar ɗakin sannan ya juyo fuskarshi a washe,Karaf idanunshi suka sauka akan abusufyan dake rungume da hosana suna bacci,gabanshi ne ya faɗi rass cike da mamaki yace"Kai uncle tare da rishi ɗina,kwance saman gado suna bacci,Anya kuwa bansamu matsalar idanu ba......'   "Junaid!" Jin an ambaci sunanshi yasa shi juyawa a firgice yaci karo da Sehrish dake zaune gaban mirror tana shafa powder a fuskarta,sae faman sakar mashi murmushi take yi,waro ido waje junaid yayi a tsananin tsorace ya mayar da idanunshi kan hosana dake rungume da abusufyan ya kalleta ya sake juyowa ya kalli wadda ke zaune agaban mirror,   Muryarshi na rawa yace"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Nashiga ukuna!wai meyake damuna ne!meyake shirin faruwa dani ne!kodai nafara gamo da aljanu ne......'bai kai ƙarshen maganar tashi ba yaji an buɗe ƙopar toilet ɗin dakin,da sauri ya wurga idanunshi wurin,   Jahad ce ta fito,jikinta sanye da bathrobe,alamar wanka tayi,   Tashin hankalin da ba'a sa mashi date,   Hankali amatuƙar tashe junaid ya dinga kallonsu ɗaya bayan daya,idan ya kalli jahad sai ya kalli sehrish dake zaune gaban mirror,sae ya kuma juya ya kalli Hosana dake manne da uncle ɗinsu, Tunkarar shi jahad tayi fuskarta ɗauke da murmushi,sehrish kuma na cewa"Junaid nice fa,baka gane ni ba,"   Ae ina,a gigice junaid ya fasa wata uwar ƙara wadda tayi sanadiyar tashin Abusufyan da hosana daga dogon baccin daya ɗaukesu, Da gudun gaske junaid ya damƙi handle din ƙopar ɗakin tamkar zai balle ta,buɗewa yayi tare da watsa wa da gudu har yanayin tuntube,tun kan ya fito daga corridor din dakin,Abbansu da mommynsu dasu twins suka nufo wurin saboda jin sautin razananniyar ƙarar da junaid ya saki,   A sukwane ya faɗo wurinsu,hankalin Abbansu ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin yadda junaid ke gudu duk tsigar jikinshi ta tashi,   Daƙyar suka samu suka damƙoshi saboda ƙokarin guduwa yake yi daga cikin gidan, Hatta Marshal Omar da Sgr sai da suka jiyo ƙarar junaid,duk wani mai bacci acikin gidan sai da ya farka,ɗaya bayan ɗaya suka shiga fitowa suna tambayar ko lafiya,   Jikinshi sae kerma yake yi duk yabi ya firgice,tambayarshi suka shiga yi ko lafiya,   Muryarshi na kerma yace"Abba rishi uku acikin ɗakinta,Abba na mutu wlh aljanune ke bibiyata......'yana faɗin hakan ya sume ajikin Abban nasu,   Tunda sukaji haka ransu ya basu Cewar yaje ɗakin Sehrish ne,Abbansu baiso hakan ba,dama yasan shi firgitacce ne,yaso ace tun farko saida ya fara yi mashi bayani anatse sannan yaje ɗakin nasu,   Ayaan kuwa tun lokacin da yaji junaid ya fasa ƙara,ya ƙumshe dariya abakinsa,saboda yasan tsiyar daya tsula mashi,zaiyi wuya junaid ya yarda cewar Sehrish ƴan uku ne,ba kasafai yake fahimtar irin waɗannan abubuwan ba,sai an zaunar dashi cikin lalama anyi mashi bayani dalla dalla,sannan ake samu ya yadda, "Junaid ne ko"?abusufyan ne yayi tambayar,yayin da yake daga zaune saman gadon,   Sehrish tace"Shine daddy,ya ruɗe ne saboda ya ganmu mu uku,ya tsorata sosai naso na fahimtar dashi amma sai naga ya watsa aguje,'jin haka yasa abusufyan yin hanzarin saukowa daga saman gadon ya fuce daga ɗakin,   Jikin jahad ba ƙaramin sanyi yayi ba,ganin halin da junaid ya shiga saboda ya gansu su uku,tsoronta kar wani abu ya same shi,ganin yadda ya watsa waje aguje,    "Inaso naje naga halin da yake ciki,bansan meyasa ya firgita ba har haka,"sehrish ce tayi maganar a yayin da take miƙewa daga saman stool,jikinta na sanye da farar riga da dogon wando fari,kanta kuma na sanye da hula fara ta roba,buɗe ƙopar dakin tayi ta fuce tare da nufar inda suke, Komawa jahad tayi ta zauna saman kujerar gaban mirror,hannu tasa tare da ɗaukar man shafawar sehrish ta buɗe shi tana lakuto shi a hannunta tana shafa ma jikinta, "Jahad wai meya faru ne?naji sautin ƙara a kunne na," hosana ce tayi maganar,tana zaune tsakiyar gadon sae faman hamma takeyi saboda yunwar da take ji, "Ƙanin Ya Omar ne,junaid ya shigo ɗakin nan,ina tunanin ya tsorata ne da ganinmu shiyasa ya firgita,saboda yaga fuskokinmu iri ɗaya dana sehrish," sauko da ƙafafunta tayi ƙasa tana cewa"bari naje naga meke faruwa a wajen," Da sauri jahad tace"Kada ki fita hosana!sehrish ta fita muddin ya ƙara yin arba dake zai zauce ne,ki bari sehrish tadawo sai muji daga bakinta,idan an fahimtar dashi ya fahimta,sai mu fita atare, Hosana tace"amma fa Yunwa nake ji sosai aciki na,' "Bari daddy ya dawo zanyi mashi magana,nasan zai sa ashirya mana breakfast ɗinmu,'acewar jahad, Murmushi hosana tayi tare da cewa"jahad bakiji irin farin cikin da nayi ba jiyan nan!,wlh inason Daddynmu sosai,tun lokacin da gwaggon katsina tace mu ƴa'ƴan abusufyan ɗinta ne,ta kuma kirashi awaya tabamu mu gaisa dashi,tun daga lokacin nake jinshi araina,na dinga addu'ar Allah yasa ya zama mahaifinmun duk da alokacin nasan wanene mahaifin namu......' "Nikaina hosana a lokacin,da muka fara waya dashi sai da naji jikina yayi sanyi,naji wani irin yanayi atattare dani ashe dae dagaske mahaifin namu ne,gaskiya munyi dacen uba,yana da kirki sosai duk da ban zauna dashi na wani lokaci ba,amma tun daga kan Fuskarshi zakasan cewar mutumin kirki ne,ashe lokacin da muna yara har zuwa ya ta6ayi ya ɗauke mu yakaimu gidansu yayi mana wanka sannan yayi mana kitson kalaba,bawan Allah,Allah kaɗai yasan yadda yaji acikin zuciyarshi lokacin da wannan baƙin mugun ya rabashi damu,' Hosana ta ƙara da cewa"Mummuna kawai,fuskarshi kamar ɗuwawu saboda rashin kyau,har naqosa naga yadda Ya omar ɗina zai karairaya ƙasusuwan jikinshi,"ta ƙarasa maganar tana yin nuni da hannayenta,yadda takeso Omar yayi ma Ya sayyadi, Ta cikin mirror jahad ke kallonta tana dariya tace"ae ba ƴa'ƴa Omar kaɗae ba,baki lura da yadda wannan mai blue eyes ɗin nan yayi ba,wani fari kyakkyawa mai ƙirar nan,har ni sai da na tsorata dashi ganin yadda ya zabura yabar wurin yana huci......' Hosana tace"ae nagane shi,Ni wlh tsoran idanunshi nake ji, kaman aljani,wai shima yanzu ɗan uwanmu ne ko?duk ƴan gidansu ya Omar ne ko? "Yayanmu zaki ce,ae yanzu duk wanda kika gani acikin gidan nan,to yayan mu ne,jiya baki lura da wani matashi acikinsu ba wani fari,mai mutunci wanda yazo ya kira mu,lokacin da alAbbansu ke neman mu"? Murmushi hosana tayi alamar tagane shi tace"daga gani zaiyi sauƙin kai sosai,kuma da alama ba ƙaramin farin ciki yake damu ba,mun gode ma Allah jahad daya haɗamu da dangin mu,'  Lokacin da sehrish ta shiga main palour din nasu,anan ta samu matasan gidan duk tsaitsaye akan junaid,dake kwance saman doguwar sofa ɗin da Abbansu ya kwantar dashi,a lokacin har sun yayyafa mashi ruwa ya farfaɗo,bakinsa sai faman kerma yake yi kuma har lokacin bai daina faɗin "Rishi guda uku"ba,   Abusufyan yace"bawan Allah,nidai naji an saki ƙara ashe wai junaid ne,bansan time ɗin daya shigo ba,lokacin ina bacci ne,ae da ban bari hakan ya faru ba,da tun lokacin na fahimtar dashi,ashe har yanzu junaid na nan da wannan firgitar tashi,ae nayi tunanin ya daina,'   Shafa gefen fuskarshi abba yayi a yayin da yake zaune daga gefen daman kujerar yace"Ya tsorata ne sosai,ae ni kaina banyi tsammanin zaije ɗakin nata bane,naso ace saida na fara yi mashi albishir sannan yaje wurinsu,'   Jahan dake tsaye yace"Aikin ayaan ne,shine ya tura shi ɗakin nata,'ya ƙarasa maganar yana hararar ayaan dake tsaye yana dariya,   Duk Alexandra na tsaye tana sauraronsu,sam batasan inda zancen nasu ya dosa ba,   Koda sehrish ta ƙaraso,zuba mata ido Alexandra tayi tana kallonta,gaban sehrish ne ya faɗi lokacin da tayi arba da ita,har sai da ta ambaci Innalillahi acikin zuciyarta,ba komae ya firgitar da ita ba face ganin fuskar sgr a fuskar matar,kuma batasan da ita acikin gidan ba, sai dai lokaci guda taji aranta kaman ta ta6a ganin hoton matar,   Cike da mamaki Alexandra tace"wacece wannan kuma"?tayi maganar tare da yin nuni da sehrish wadda tuni ta koma bayan abusufyan ta tsaya,   Jahan ne ya bata amsa da cewa"Ƴan ukun uncle abusufyan ne,'.   "Abusufyan kuma?dama ya ta6a aure ne?   "Eh,ya ta6a aure batare da sanin kowa ba,sai daga baya abun ya bayyana cewar ƴa'ƴansa ne,kuma ƴan ukune kamanninsu iri ɗaya sak,abunda yasa kika ga junaid ya ruɗe kenan,baisan cewa su uku bane,ɗaya ya sani acikinsu,muma sai jiya Allah yasa mukasan da zamansu muka san cewa ƴa'ƴanshi ne,Nasan abba zai sanar dake komai,'   Jinjina kai Alexandra tayi tare da ɗan ta6e bakinta,yayin da ta janye idanunta daga kan sehrish ta mayar dasu kan junaid dake ta faman sambatu,   "Abba pls ku fahimtar dani mana!meyasa nake ganin Sehrish guda uku?ko na samu ta6in hankali ne,'   "Junaid u should calm down ur mind,in baka natsu ba taya zamu fahimtar dakai,"acewar abbansu,   Jin hannun mutun acikin nata yasata yin saurin juyawa,sai lokacin ta lura dashi sam bata ga fitowarshi ba,   "Mommy,"ya ambaci sunanta cikin sanyin murya,cike da farin ciki tace"Fawan!ka farka daga baccin kenan"?tayi maganar ayayin da take janyo shi jikinta,sosai ta rungume shi,   "Mommy tun yaushe kika zo ba'a sanar mun ba?sae dai na fito na ganki unexpected"   "Tun jiya nazo fawan,muna tare da junaid acan gidana muka kwana tare dashi sai yau da safe muka dawo atare,da fatan na sameka cikin ƙoshin lapiya,'   "Alhamdulillah mommy munyi missing ɗinki sosai da sosai,'   "Nima nayi missing ɗinku fawan,'magana suka cigaba dayi atsakaninsu,   Duk wannan abun dake faruwa alexandra bata tanka ma abusufyan ba,shima kuma bai tanka mata ba,tun lokacin daya shigo falon yayi arba da ita,yaga ta kawar da kanta gefe tun daga lokacin shima ya share ta,dama bata shiri dashi,tun lokacin da Abba ya aurota,ya ta6a zama agidan,yanayin yadda take wahalar da yayanshi ne yasa yayi mata rashin kunyar da ta haddasa gaba atsakaninsu,saboda shi bakinshi bai rufuwa muddin yaga tana gaya ma Yayanshi hossein magana saiya mayar mata da martani mai zafi,wannan dalilin ne yasa Abba yace ya tattara ya koma wurin ammi don bazai iya jurar zama dashi ba,kullum haɗa mashi Bomb yakeyi acikin gida,shiyasa abusufyan bai zauna agidan yayan nashi ba,kuma ammi bata kawo shi gidan ba lokacin daya addabeta da rashin jin maganarshi,kawai ta yanke shawarar kai shi gidan hajiya Ameenatu,    Kowa daya fito tun daga kan su irfan jabeer,khaleed da kanal yousouf babu wanda baiyi farin cikin zuwan mommynsu junaid ba,daya bayan ɗaya saida tayi hugging ɗinsu ajikinta,kanal yousouf ne kawai ta manna ma kiss a gefen fuskarshi,ji suke tamkar mahaifiyarsu ce Maryam ta dawo gidan,Allah sarki Allah ya jiƙan rai,tun daga yanayin yadda alexandra ta kar6esu hannu bibbiyu tana rungumarsu ransu ya basu cewar ta shiryu yanzu,da alama babu wannan girman kan nata da kuma Zafin ran nan,    Sehrish dae duk jikinta yayi sanyi tun daga kan irin kallon da taga Mommynsu junaid nayi mata,ranta ya bata cewar akwai matsala,sam fuskarta babu yabo babu fallasa lokacin da Jahan ke sanar da ita cewar ɗiyar uncle ɗinsu ce,   Abbansu na ƙoƙarin fahimtar da junaid,suka jiyo muryar sgr yana tambayar"Meya faru ne!"yayi maganar ne ayayin da yake saukowa daga saman stairs ɗin,jikinshi na sanye da shirt fara ta ɗame jikinshi sai kuma dogon wando jeans,ba ƙaramin kyau yayi ba, Gaba daya suka juyo suna kallonshi,Marshal Omar na biye dashi abayanshi,atare suka sauko,   Wani irin farin ciki ne ya lullu6e alexandra lokacin da tayi arba da first born dinta wato Surgeon General Rafayet,gaba ɗaya tagaza rufe bakinta saboda ba ƙaramin so take mashi ba,tana matuƙar alfahari dashi,   Sehrish kuwa tunda taji muryarshi taji gabanta ya faɗi rass,tabbas tayi kewarshi sosai,jiya abubuwan da suka faru ne suka hana takai mashi dinner ɗinshi,tasan cewa daƙyar ne idan yaci wani abu ajiyan nan,   Aranta tace"bansani ba ko yana farin ciki da kasancewata ƴar uwarshi,ɗiyar ƙanin Mahaifinshi,ko yaya yaji aranshi"?    Jahan ne ya sanar dasu abunda ya faru da junaid,   ƙarasawa Sgr yayi wurin Mommyn tasu,ita tafara manna mashi kiss a gefe da gefen fuskarshi sannan shima yayi mata kamar yadda tayi mashi,daga bisani kuma suka rungume junansu, Abun ba ƙaramin burge sehrish yayi ba,har sai da ta ɗan saki murmushi kaɗan a fuskarta,   "Am really glad to see u mom,"ya furta hakan ayayin da suka raba jikinsu daga na juna,   Shafa gefen fuskarshi tayi tare da cewa"Yanzu ka kyauta mun?tun yaushe rabon dana sanya ka a idanuna Alex?ka daina zuwa wurina,kusan 1 year kenan baka tako ƙafarka kazo ba,'   Ganin hawaye sun cicciko a idanunta yasashi yin saurin ruko hannayenta tare da cewa"pls mom just forget about the past,nasan ban kyauta ba,amma kullum kina araina,kuma ina kiranki awaya muna gaisawa....'   Abbansu ne ya katse firar tasu da cewa"Ashe ba daɗi,Rama mun yayi Nima,ƙiri ƙiri kin rabani da aurena kinsa anata yi mun kallon Tazuru,'   Dariya sukayi gaba ɗayansu,banda sehrish dake tsaye jugum tana sauraronsu,   Matsawa Omar yayi cike da zolaya yace"Oh Mommy abun ƴar wariyar launin fata ce ko?atare da bro ɗina muka fito,amma ko kulani bakiyi ba...'yayi maganar yana ɗan ɗaure fuskarshi,   murmushi alexandra tayi tare da komawa wurin marshal,ta manna mashi kiss agefen fuskarshi sannan ta dafa shoulders ɗinshi tare da cewa"Omar ni bazan iya cewa komai ba,so nake nafara huce haushina akanshi kafin nadawo kanka,dama kaine mai ɗan son zumuncin,duk lokacin da kuka samu hutun aiki kana janyo shi kuzo wurina,amma yanzu duk kun juya mun baya,ni nasan duk shirin Abbanku ne yasan cewa dole nayi kewarku....'   Omar yace"no ba haka bane mommy,rayuwarce sai a slow,bamu manta dake ba,kuma kamar yadda rafayet ya fadi,muna kiran ki fa awaya kullum mu tambayi lpyrki,da ace kin ƙara 1 week baki zo nigeria ba,da kin ganmu munzo,ba don ma aiyuka da sukayi mana yawa ba,ae da mun rigaki zuwa....'   Ba ƙaramin daɗin kalaman Omar taji ba,yasan duk wata hanya da zaibi don ya kare kansu a wurinta,ba kamar SGR ba,shi kai tsaye kawai yake maganarshi ba wata kwana kwana,'   Sai da suka samu natsuwa sosai,sannan suka tattara hankalinsu kan junaid,    "Ina sehrish take ne"?Abbansu ne ya ambaci sunanta,saboda yaga gifcinta a wurin,   Da sauri ta amsa mashi da cewa"Gani nan Abba,"tayi maganar tare da fitowa daga tsayen da take abayan daddynsu,    Haɗa ido sukayi da Sgr,da sauri ta kawar da idonta,zuciyarta na harbawa da ƙarfi da ƙarfi,daƙyar ta iya ƙarasawa wurin abban nasu ta gaishe shi,   Bayan ya amsa mata yace"ki fahimtar da junaid,ina tunanin in yaji daga bakinki zaifi yadda cewa ku ƴan uku ne,'    Murmushi sehrish ta ɗan yi tana kallon fuskar junaid wanda ke kwance saman kujerar duk yabi ya rikita kanshi,tunda tayi magana yasan cewa itace saboda yaji muryarta,    Cikin sanyin murya ta soma magana,   "Junaid ka manta kwanaki na ta6a sanar dakai cewa Ina da ƴan uwa?waɗanda nake kira da wayarka? "Amma ai kince mun baki da wasu ƴan uwa lokacin da muka yi maki magana akansu ni da aunty azmee,"yayi maganar yana faman hura hanci,   "Junaid a lokacin bana cikin hayyacina bansan ya akai na manta dasu ba,amma yanzu nadawo hayyacina kuma Zan iya tuna komai a game dasu,idan baka yadda dani ba,bari na tuna maka,ko ka tuna Yarinyar daka ɗauko a school cikin motarka?tun lokacin saida nayi ƙoƙarin fahimtar dakai cewar bani bace,ni ina a makaranta ka barni,shine dalilin da yasa nasha wahala aranar,'   Jin wannan maganar ta sehrish yasa junaid miƙewa daga zaune,bakomai ne ya faɗo mashi aranshi ba face,yadda jahad ta kasa sakewa dashi,kuma launin gashin kanta baƙi ne ba irin na sehrish ba,hatta muryarsu ma akwai ɗan bambanci,haba no wonder shi dae ya jima yana tunanin cewa al'jana ya ɗauko a motarshi ashe ashe mutunce,indae dagaske ne xancen sehrish hakan na nufin cewa ƴar uwartace ya ɗauko a motarshi?to kodai sune yaran da Ya Omar ɗinsu yasa su gyarama gidan uncle ɗinsu zai kawosu suyi rayuwa aciki......'bai ƙarasa zancen zucin nashi ba,Muryar Omar ta katse Hanzarin shi"Junaid!maganar da take faɗa maka dagaske ne!they're triplet,kuma ƴa'ƴan uncle abusufyan ne,dukanmu bamu son da haka ba sai jiya Allah ya bayyana mana komai,'   Yana kai ƙarshen maganar tashi ya juya tare da kallon fawan yace"Kaje ka kira mun su hosana da jahad suzo ya gansu da idanunshi don ya shaida cewar mutane ne ba aljanu ba,'   Cike da zumuɗi fawan ya wuce bedroom ɗin sehrish a lokacin har jahad ta kammala shirya kanta cikin riga da skirt na sehrish,ba ƙaramin kyau tayi ba,   Kwankwasa ƙopar fawan yayi kafin ya turo tare da cewa"Ya omar nason ganinku yanzu,'jin haka yasa sukayi saurin kimtsawa,duk suka yafa gyala a kansu,   Atare da fawan suka shigo cikin main palour ɗin,    Jerawa sukayi kusa da sehrish duk sun sha jinin jikinsu tsoransu kar ace wani abun ne kuma ya taso,   zuba masu ido junaid yayi yana kallonsu,idan ya kalli jahad sai ya kalli hosana,   A ƙarshe ya tsaida idanunshi kan jahad,ta hanyar gashin girarta ya gane cewa itace ya ɗauko a motarshi,har suka sha Love,   Dafe kanshi yayi tare da cewa"OMG!Abba kenan reesh ƴar uwata ce,jini na,ɗiyar uncle ɗinmu abusufyan!taya hakan ya faru?kuma dama rishi ƴan uku ne su ba ita kaɗae bace!idan har dagaske ne meyasa basu taso atare damu ba!!!!!!!_ Karaf maganganun da junaid ke faɗi suka dira a kunnan Hayaam,wadda fitowarta kenan,yunwa ta korota daga bedroom ɗinta ta gaza jurewa shine ta lalla6a ta fito don ta shiga kitchen,   Gabanta ne yayi wani irin bugu ji kake rasss!rarasss!hankali amatuƙar tashe ta ɗago da idanunta ta sauke su akan Mutanen dake tsaitsaye acikin falon,waro ido waje tayi ganin Sehrish dasu jahad,anan ta tuna abunda azmee ta faɗa mata jiya na cewa ƴan uku ne su,kuma kamanninsu iri ɗaya sak,a fili ta ambaci"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!Ya Allah ka rabani da mugun Ji da kuma mugun gani!nashiga uku Ni yau Hayaam,bari dae na ƙara kasa kunne naji uban da suke tattaunawa,ya Allah kasa korar shaggun za'ayi daga gidan, "Junaid sehrish ɗin daka sani da kuma waɗannan biyun masu kama da ita sak,ƴa'ƴana ne,ni ne mahaifinsu,Na auri mahaifiyarsu ne ba tare da sanin kowa ba........'ataƙaice Abusufyan ya fayyace ma Junaid komai, Saboda tsabar kiɗima hayaam ƙiris ya rage ta fasa ƙara a wurin,ta matukar firgita da jin abunda abusufyan ya sanar ma jahad,tashin hankalin da ba'a sama shi date,gudu gudu,sauri sauri hada tuntube wurin komawarta cikin bedroom ɗinta,jikinta sae faman kerma yake yi kamar wadda sanyi ya kama,hannu ta aza asaman kanta tana faɗin"nashiga uku!na bani na lalace!ƙarshe na yazo acikin gidan nan!taya akai haka ya faru duk ina nan sake da baki bansani ba,wai yanzu dagaske yarinyar nan mai aikin gidan dana raina,nake ganinta ƙaskantacciya yar wurin uncle ɗinsu ce Abusufyan,Tabɗijancan,Kallo ya koma sama!kai anya kuwa banyi kuskure wurin sauraran maganar shi ba? Turo ƙopar da akayi ne yasa ta yin firgit ta juya, Tana ganin azmee hannunta ɗauke da plate na breakfast ɗin da ta kawo mata, Jiki na rawa hayaam ta ƙarasa wurinta tare da cewa"Aunty Azmee wai dagaske ne Seh...seh..rish ɗiyar uncle ɗinsu ce abusufyan!" Ƙayataccen murmushi azmee ta saki tare da cewa"Dagaske ne mana!Nima sai da asuba nakejin wannan labarin a wurin Hajiya azeemarsu....'tunda azmee ta soma magana hayaam ta fita hayyacinta, Har sai da azmee ta ambaci sunanta"Hayaam!naga kamar kin tafi duniyar tunani ne?lafiyarki kuwa? Murmushin yaƙe ta saki tana ƙoƙarin danne damuwarta tace"Azmee bana jin daɗi ne,zuciyata tafarfasa takeyi ne," .azmee tace"Allah sarki,dama saida raina ya bani cewa baki lafiya,To Allah ya sawake,yanzu dae ga wannan ki fara karyawa nasan kina jin yunwa.....' Wani irin bugu Hayaam takai ma plate ɗin dake hannun azmee nan take yayi gefe guda ya tarwatse ƙasa,snacks ɗin dake aciki suka 6are, Ita kanta hayaam sai da ta firgita saboda ba'a cikin hayyacinta tayi hakan ba,tsananin 6acin rai ne da ƙiɗimar da tayi, Hankali tashe azmee tace"Hayaam!!' Tunkan ta karasa maganar hayamm ta zukunna jiki na rawa tashiga kwashe snacks ɗin dake zube aƙasa tana mayarwa cikin plate din, Muryarta na rawa tace"dan Allah aunty azmee ki tafi kawai,nagode sosai zanci....' Ƙiris ya rage azmee ta fashe da dariya,ganin yadda la66an hayaam ke kerma kamar gandar nama,tasan cewa duk akansu sehrish ne, "Allah ya baki lafiya,"ta ambaci hakan tare da juyawa tabar mata ɗakin, Azmee na fita hayaam ta jefar da plate ɗin, . miƙewa tsaye tayi nan fa tashiga safa da marwa tana zagaye ɗakin,bakowa ne ya faɗo mata aranta ba face Aunty laila,tabbas ya kamata tayi gaggawar sanar da ita halin da ake ciki, Jiki na rawa ta ɗauko wayarta dake ajiye saman mirror,tana danna wayar yatsun hannunta na kakarwa,daƙyar ta tsaida hankalinta wuri guda ta danna ma Aunty Babba kira.        *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari sannan a kula wannan itace numbar wayata,Wasu suna ɗaukar numbar Wanda suka bani tallarsu kayansu suna kiransu a matsayin ni,bayan ni ga numbar dana bada nan itace numberta_ *Nagode sosai da addu'o'inku agare ni,da kuma uzurin da kukayimun,har zuwa wannan lokacin,Allah yabar zumunci a tsakaninmu daga nan har *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari sannan a kula wannan itace numbar wayata,Wasu suna ɗaukar numbar Wanda suka bani tallarsu kayansu suna kiransu a matsayin ni,bayan ni ga numbar dana bada nan itace numberta_ *Nagode sosai da addu'o'inku agare ni,da kuma uzurin da kukayimun,har zuwa wannan lokacin,Allah yabar zumunci a tsakaninmu daga nan har gidan aljanna💃* *nace ba Masu satar littafi suna fitarwa ta bayan fage,mai yasa baku ƙarasa masu labarin ba?kuma kenan saida kuka jira ni?ae nayi tunanin cewa zaku ƙarasa masu labarin ne ashe dai sai anjira Boss*😂🤣😅 Bismillah Kai tsaye sautin ringing ɗin wayar ya daki dodon kunnan Aunty babba dake baje saman gadonsu tana Bacci,a lokacin ko yatsanta bata jin xata iya motsawa saboda baccin dake a idanunta,yatsina fuska tayi alamar an takura mata,    Ishaq dake tsaye agaban mirror yana gyara jikinshi ya ɗan gyara murya tare da cewa"Madam ki daure ki tashi ki ɗaga kiran nan!da alama kira ne mai muhimmanci tun ɗazu wayar ke ta ringing,"   Uban tsoki Aunty babba ta buga tare da yunƙurawa daƙyar ta tashi daga zaune,jikinta na sanye da sleeping dress,riga da wando purple colour,   Fuskar nan tayi suntum kamar wadda aka nausa,hannu takai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman bedside drawer,duba screen ɗin wayar tayi ganin sunan Hayaam ya bayyana yasa ta ƙara tamke fuska kamar ta shanu,ɗaga kiran tayi tare da kara wayar a kunnanta,rai a6ace tace"Meyasa kika kirani fitsararra!ko kin kira ne don ki ƙarasa yimun rashin kunyar taki don ubanki,"   on the other hand hayam tace"haba aunty laila,ni harna manta da abunda ya faru atsakanin mu.....'tunkan hayaam ta ƙarasa maganar Aunty babba ta katse mata hanzarinta da cewa"Idan kin manta ae ni ban manta ba,Ki faɗamun uban miyasa kika kira ni,idan ba haka ba ni zan kashe wayar,   Zuba mata ido Ishaq yayi yana kallonta aransa yace"Zagi kamar ƴar maguzawa,ko kunyata bata ji,sae faman ɗura ashar take yi,ni dae Allah ya haɗani da Guyaba,'      cike da damuwa hayaam ta sassauta muryarta,tare da cewa"Aunty laila,na shiga uku,ko ince mun shiga uku,Akwai gagarumar matsala,Gaba daya duk wani plan ɗinmu ya tashi aiki,'   Tunda Aunty babba taji hakan,gabanta ya faɗi rasss,ƙasa ƙasa da murya tayi tace"Hayaam meya faru?wata irin matsala kike magana akai?   "Aunty laila,Ashe yarinyar nan mai aikin gidansu,ɗiyar uncle ɗinsu ce Abusufyan!!!!!" tamkar saukar aradu haka aunty babba taji maganar Hayaam aikuwa a matuƙar gigice ta miƙe tsaye tana cewa   "kutumar uba!inji ubanwa!yaushe Abusufyan ya ta6a aure,Wlh ƙaryane koma wani ɗan ƙaniyar ne ya faɗi maki hakan babban maƙaryaci ne....'   Gaba daya hankalin ishaq ya dawo kanta,maganar dayaji tana fadi ta tsaya mashi aranshi,    "Wani abusufyan din kuke magana akai,"   Firgit Aunty babba tayi tare da ware ido tana kallonshi sam ta manta da cewar yana acikin ɗakin,   Hankali a matuƙar tashe ta miƙe tsaye da nufin ta fuce daga cikin ɗakin,Saboda tsabar ruɗu ta nufi hanyar shiga toilet,   gyaran murya ishaq yayi mata tare da cewa"kada fa ki shiga toilet da waya a kunnanki,'   A zabure ta juya ta kuma nufi wardrobe da alama ruɗu yasa ta manta hanyar fita daga ɗakin,zuba mata ido yayi yana mai mamakin irin kiɗimar da tayi,to ko lafiya?ya tambayi kansa,    Bata ankara ba sae da goshinta ya bugi jikin wardrobe din kayan nasu,sannan ta gane inda ta dosa,Rai a6ace ta kama hanya ta fuce daga dakin,saukowa downstairs tayi ta miƙi hanyar wannan tsohon store ɗin data ta6a garƙame su hosana aciki,anan corridor ɗin ta tsaya tana sauraran Hayaam,   "Wlh Aunty laila da gaske ne,Ni shaidace,Naji komai lokacin da Uncle ɗin nasu yake korama junaid bayani,bama haka ba Aunty azmee da kanta ta gasgata mun hakan,Babban abunda yafi rikitar dani Yaran fa triplet ne ashe,kuma dukkansu Mata ne kyawawan gaske,kamannin su sak iri ɗaya,Kuma kina kallonsu zaki gane cewa ƴa'ƴanshi ne......'   Hannu ɗaya Aunty babba tasa ta dafe tsakiyar kanta,yayin da dayan hannun ke ruƙe da wayarta data kara a kunnanta,   "Hayaam bazan ta6a yarda da zancenki ba,Taya hakan ma zata faru!mutumin da bai ta6a yin aure ba,Shi za'ace yana da ƴa'ƴa har ƴan uku!Cikin shege kenan ya ta6a yima wata harya same su!Ni ban yarda da kalamanki ba,Hayaam kinsan cewa babu kyau tsoratar da musulmi,Idan wasa kike mun ki daina!!!!! 6acin raine yasa hayaam ta kashe wayar   Fashewa da kuka tayi saboda ƙululun baƙin cikin daya tokare mata maƙoshinta,ga zuciyarta dake ta faman tafarfasa,Gaba daya bata jin daɗin jikinta,   Zubama wayar ido Aunty babba tayi tana kallonta,   Tsoki taja tana jinjina kai tace"dama saida raina ya bani cewa ƙarya take yi mun,tayi mun hakan ne saboda ta tsoratar dani don in saukko,Shashasha kawai,     "Mommy kin farka kenan" Muryar hafsat ce ta katse mata zancen zucin nata,   Juyowa tayi tana kallonta,atsaye take fuskar nan ɗauke da murmushi jikinta na sanye da riga da wando na jeans,ta ɗaure sumar kanta da ribbom,yayin da hannunta ke ruƙe da Cup mai ɗauke da Tea mai zafi sai faman tiriri yake yi,   Tunda Aunty babba taga hafsat na murmushi tasan cewa akwai matsala,hakanan dae ba zakaga fuskar hafsat da murmushi ba tunda farar safiya,   ƙaƙalo murmushin yaƙe Aunty babba tayi tare da cewa"Lafiya naga kina murmushi"?   "Lafiya lou mommy,kawai wani abun farin ciki ne ya faru,nasan cewa muddin kema kika ji,zaki yi farin ciki sosai,'   Murya asanyaye aunty babba tace"Faɗamun daughter har na ƙosa naji wannan abun farin cikin?halan an ƙara maku albashi ne?ko matsayi aka ƙara maki wurin aiki"?   Dariya hafsat tayi tana girgiza kai tace"Mommy baki canka dai dai ba,wannan albishir ɗin da nakeso inyi maki yafi ƙarfin duk waɗannan abubuwan da kika lissafo,kar6i tea ɗin nan ki fara korawa kafin na faɗa maki,"   Hannunta na kerma ta kar6i kofin da hafsat take miƙa mata,a hankali takai cup din bakinta ta kur6i Tea ɗin,kusan sau uku tana kur6arsa,kafin ta ɗan jinkirta bayan ta janye kofin daga bakinta tace"daughter dan Allah ki faɗamun wannan wani abun farin ciki ne!wlh duk na ƙosa naji,'   "Zan faɗa maki mommy amma mu shiga daga cikin palour mu zauna,'   "Ba inda zanje,idan zaki faɗamun ki faɗamun kawai,Sae ja mun rai kikeyi," tayi maganar tana faman tamke fuska,   Hafsat tace"bada jimawa ba,Na kira Aunty azeema,don in gaishe da ita,Anan take sanar dani cewa ƴa'ƴan uncle abusufyan Sun bayyana...!   Tunkan ta ƙarasa maganar a gigice Aunty babba ta saki kofin dake hannunta,Ya tarwatse ƙasa,Ruwan tean dake ciki ya fallatsar masu a ƙafa,   ja da baya hafsat ta ɗanyi tana kallonta tace"haba mommy,so kike ki ƙonamin ƙafa ta,daga faɗin abun farin ciki?   Rai amatuƙar 6ace tace"Ki 6ace mun da gani sakarya kawai,Maƙaryatan banza,bazan ta6a yadda da kalamanku ba,duk bakinku ɗaya da Hayaam,' Ta faɗi hakan tare da kama hanya fuuuuu kamar zata tashi sama,ranta duk a jagule,bin bayanta hafsat tayi da kallo harta haye upstairs,ta6e baki tayi tare da watsa hannayenta tace"I don't care, Ni dae farin ciki nakeyi,Daddy ma nake jira in tambayeshi yaushe zamu je gidan saboda a qagare nake dana ga ƴa'ƴan uncle ɗinmu Abusufyan,tunkan na gansu har naji ina sonsu sosai,in ma na tashi tafiya hada tsaraba zan tafin masu dashi,'   Cike da farin ciki hafsat take maganar,zuƙunnawa tayi tana tattare kofin da aunty babba ta fasa, Lokacin da Aunty babba ta ƙarasa bedroom ɗin nasu,har ta ɗaga ƙafarta zata zura acikin ɗakin taji muryar ishaq yana cewa"Alhamdulillah!Alhamdulillah!Alhamdulillah!Abba nayi farin ciki sosai,Meyasa tun jiya ba'a sanar dani ba,ae da tunda sanyin safiya zanyi maku dirarr mikiya,Amma ina taya uncle murnar ganin ƴa'ƴanshi,kuma ina tayamu murnar samuwar ƴan uku acikin zuri'ar mu,gaskiya bazan ma iya jurewa ba,Zan shirya nazo ne kawai,saboda na qosa naga ƴan ukun mu bayin Allah....       Abba yace"wani abun ma sai kayi tozali da yaran,kyawawan ƴan mata dasu,Yadda kasan photo copy ɗin abusufyan haka suke,kamanninsu sak iri ɗaya da nashi,'   Murmushi Ishaq yayi tamkar yana agabanshi yace"Abba kafin na ƙaraso,dan Allah a isar musu da saƙon gaisuwata,Ace yayansu General ishaq yana gaishe su sosai da sosai,kuma saboda suma zaiyi zuwa na musamman,'   "Insha Allah zan sanar masu yanzun nan,Allah ya kawoka lfy,"   "Ameen Abbana," Sun jima suna waya kafin sukayi sallama ishaq ya ajiye wayar,   tashin hankalin da ba'a sama shi date!!!!!!!   Magana dae ta tabbata da gaske ne zancen da hayaam da hafsat suka faɗa mata,Tabɗijancan,   Dakyar ta iya shiga cikin ɗakin,lokaci guda ta rasa kuzarin jikinta kamar wadda tayi Zazza6i na sati ɗaya,   Jin takun tafiyarta yasa ishaq juyawa yana kallonta fuskarshi a washe har ya kammala shiryawa cikin haɗaɗɗiyar shadda,   Ganin yana ƙoƙarin buɗe baki yayi mata magana yasa tayi saurin katse shi da cewa"Naji abunda ya faru,Hafsat ta sanar dani komai,ina tayaku murna,'ko amsar shi bata tsaya ji ba,ta faɗa cikin toilet,   Tana juyo muryarshi daga cikin bedroom ɗin yana cewa"Ni yanzu zan wuce Abuja ne,inyaso kun biyo ni daga baya ko zuwa gobe ko jibi haka,duk dae yanda kuka yanke shawara keda hafsat,   daga cikin toilet tace"Allah ya sauke ka lpy,in anje agaishe mana da mutanen gidan,"    "zasuji insha Allah," ya amsa mata tare da kama hanyar fita daga ɗakin. ❤🤍❤ Acan 6angaren kuwa har lokacin suna a falon kan junaid da Uncle abusufyan ya gama fahimtar dashi game da Su Hosana da jahad, jiki asanyaye yace"Amma meyasa su ba suyi rayuwa atare damu ba?meyasa Abba?uncle why?cike da tuhuma yake maganar yana kallonsu,yayin da fuskarshi ke ɗauke da damuwa, abban su ne yace"Junaid,mu kanmu bamu san dasu ba,da ace munsan da zamansu da bamu bari hakan ya faru ba,ƙaddara ce kawai ta riga fata,"   Shiru junaid ya ɗanyi yana ƙare ma su Jahad kallo,yaso ace tun fil azal tare da yaran ya taso,da ba ƙaramin kulawa zasu samu a wurin ƴan uwansu ba,Allah sarki rayuwa kenan,Rashin sani yafi dare duhu,su kansu su Sehrish sae dama dama suke da sun san cewa suna da wannan family ɗin daba abunda zai hana su nemi danginsu,Tabbas an cuci rayuwarsu ƙiri ƙiri an rabasu da Ubansu kuma an hanasu danginsu,wata shari'ar dae sae a lahira, "Nasan yanzu kowa yana jin yunwa,saboda halin da muka shiga jiya babu wanda ya samu damar cin abinci acikin mu,Yakamata yanzu komai ya wuce,Lokacin farin ciki ne,Za'a shirya gagarumar walima saboda ƴan ukun mu,munaso su manta da duk wani abu da ya faru a rayuwarsu kuma su ƙaddara cewa tamkar yau ne suka faɗo duniya,ko ba haka ba"? Ya yi maganar yana kallon matasan gidan dake atsaye,Kowannansu fuskarshi asake,su fawan ne suka haɗa baki wurin cewa"Wannan haka yake Abba,In sha Allah zamu nuna masu soyayyar ƴan uwantaka,har sai sun manta da dukkan wani ƙunci da suka fuskanta na rayuwarsu,' murmushi kawai Abusufyan ke saki don ba ƙaramin daɗi yaji ba, Marshal Omar yace "Sannan kuma muna ƙara baku haƙuri game da halin da kuka tsinci kanku,duk da ba laifin mu bane,amma mun ɗaura ma kanmu laifin,Muna neman afwarku,Hosana Sehrish and Jahad,forgive us pls,'   gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi,lokaci guda kuma sukaji wata irin soyayyar ƴan uwansu ta kamasu, Jahad ce tayi ƙoƙarin cewa"duk wani abu daya faru damu dama can rubutaccen ne!Allah ya riga da ya ƙaddara faruwan hakan,mun gode ma Allah da muka cinye wannan jarabawar,da juriya kuma da haƙuri,yanzu gashi gaba ɗayanmu muna farin cikin wannan rana da Allah ya haɗamu da danginmu,Babban abun farin cikin ma da ya kasance Uncle abusufyan shine mahaifinmu ba waccen fasiƙin mutumin ba.......'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya zo mata,Janyota Abusufyan yayi tare da rungumeta ajikinshi,yana ɗan bubbuga bayanta,   "Ya Omar," hosana ce ta ambaci sunan shi,tana faman kumshe dariya abakinta,gaba ɗaya suka mayar da hankalinsu akanta,nuna shi tayi da yatsanta sannan ta nuna kanta,kafin ta haɗe yatsun wuri guda ta ƙullasu,Alamar ita dashi sun zama  ƴan uwan juna, ƙayataccen murmushi Marshal ya saki yana kallonta, Duk wannan abun dake wakana akan idon Sgr dake atsaye,ya goya hannayenshi asaman wide chest ɗinsa,Har lokacin bai sauko ba,hankalinsa fa bazai kwanta ba har sai yayi tozali da YA SAYYADI, Suna cikin magana muryar azmee ta katse su da cewa"Abba an kammala shirya breakfast ɗin,yakamata ku hallara a dining ɗin," tana magana idonta na akan su jahad fuskar nan ɗauke da murmushi,    Batare da 6ata lokaci ba,gaba ɗayansu suka hallara asaman zungureran dining table ɗin wanda ke shake cike tab maƙil da kayan makwalashe naci dana sha,mutun goma shabiyu yake ɗauka,akwai kuma wanda Abban su junaid yasa aka ƙara cikin wanda aka shirya walimar jiya dasu,Ansanya shi a gefen nasu mai mazaunin mutun shida,Aunty azmee ta jera wasu kayan kalacin asaman shi,anan Abusufyan ya zauna tare da su sehrish jahad da hosana, Tun daga kan yadda kowa ke zuba abinci acikinshi zai tabbatar maka da cewar ba ƙaramar yunwa suke ji ba,ko azmee basu jiya tayi serving ɗinsu ba suka shiga zuba abincin da kansu,Sgr ne kawai tayi serving ɗinsa sae kuma Abbansu,amma sauran ba wanda ya tsaya jira,wurin yayi tsit bakajin hayaniyar komai,sai sautin Cokulla,kwas kwas kwakwasss, ɗagowa Marshal omar yayi karaf idonshi yaci karo dana hosana,ta zuba mashi ido ko kyaftawa batayi,kasancewar table ɗinsu na kusa dana juna,tazarar kadan ce,   Da cokalin hannunshi yayi mata nuni da plate din gabanta,alamar ta mayar da hankalinta kan abunda take ci,   murmushi tayi tare da kai hannu ta dauki lemu tana korawa,   Junaid kuwa duk ya rasa samun natsuwa sam ya gaza cin abincin dake a gabanshi sae faman juya cokalin yake yi acikin plate,duk in ya tuna abunda yayi ma Jahad acikin mota amatsayin Sehrish sai yaji gabanshi ya faɗi rass,fargabar shi kada jahad tayi tunanin ko ɗan iska ne shi,tunda ba sanin shi tayi ba,kar kuma tace zata sanar ma wani abunda yayi mata,tunawa yayi da lokacin daya tsoma harshenshi acikin bakinta ya ƙanƙameta yana kissing lips ɗinta,ba iya nan ba ya tsaya har hannunshi saida ya zura ackin hijabinta   Hankali tashe junaid ya miƙe yana ƙoƙarin barin dining ɗin,hankalin kowa ya koma kanshi,   Har suna haɗa baki wurin tambayar shi ina zashi,   fuskarshi ɗauke da damuwa yace"Abba,bana jin yunwa,dama munyi breakfast tare da Mommy,zanje wurinta yanzu" Abbansu yake ma magana amma hankalinshi na akan Jahad dake shan farfesun da azmee ta zuba mata a plate,da alama ba ƙaramin daɗi farfesun yayi mata ba,duba da yadda ta mayar da hankali akanshi,   "Okey,zaka iya tafiya," ya bashi amsa,cikin sauri junaid ya kama hanyar zuwa bedroom ɗin Abbansu don acan ta sauka,yana tafiya yana waiwayen su jahad aranshi yana cewa"wayyo Allah na,bansan me zai biyo baya ba,nasan cewa dole ta sanar ma Uncle abunda nayi mata,idan ta faɗa mashi shi kuma zai faɗa ma Abban mu ne,Abban mu kuma zai faɗa ma Babban yayanmu ne,shi kuma zaice wuyana ya isa yanka tunda har na iya Sumbatar mace daga nan zaiyi tunanin turani aikin Soja abunda banso,shikenan tawa ta ƙare'   ranta ne ya bata cewar ana kallonta,hakan yasa ta tsagaita daga shan farfesun da takeyi,ta ɗan ɗago idanunta,kai tsaye suka sauka akan junaid dake can nesa dasu yana kallonsu, Mamaki ne ya kamata ganin yadda ya ƙura mata ido yana kallonta,aranta tace"bansan meyasa yake kallona ba,tsorana kar ace baisan ganina ne,'   "Allah yasa halinta irin na Sehrish ne,idan takasance mai sauƙin kai irin na rishi ɗina nasan cewa zata rufa mun asiri,amma anya zatayi sauƙin kai?Nasan me zanyi daga yanzu zan dinga ɗaure mata fuska,in nuna kamar na tsane ta,nasan hakan ne kawai zaisa taji tsorona taƙi faɗa masu abunda ya faru atsakaninmu!good idea",   Yana kai ƙarshen zancen zucin nashi ya watsa mata harara tare da murguɗa mata baki,ya juya ya nufi bedroom ɗin abbansu,    Jiki asanyaye jahad ta ɗauke idanunta daga kallon bayanshi da take yi,lokaci guda taji komai ya fita ranta ba don komai ba sai don kallon da taga junaid yayi mata,maganarta ta tabbata,Junaid baison ganinta,tunda gashi ya harare ta kuma hada murguɗa mata baki,   Muryar daddynsu ce ta katse ta da cewa"Jahad,meya faru ne?naga kin daina shan farfesun ina fata lafiya?   firgit ta ɗanyi tare da wurga eye balls ɗinta akanshi tace"Am ok daddy,'   jinjina kansa yayi kafin yace"Ku saki jikinku,kuci abinci sosai,kada kuji komai,nasan baku saba ba,don na lura akwai rashin sabo atattare daku,amma a hankali zaku saba da ƴan uwanku,'   hosana tace"Abba ae ni,nama saba da kowa,baka ga yadda nake ta cika cikina da abinci ba,jahad ce ke jin kunya,ni bana jin kunyar kowa,'   Dariya sukayi gaba ɗayansu,Sehrish na cikin sakin dariyar nan,Karaf idanunta suka haɗu dana Sgr,ɗagowar shi kenan yayi arba da ita,gabanta ne taji ya faɗi rass saboda fuskarshi a murtuke take ba annuri,nan take dariyar da takeyi ta koma ciki,ganin ta zuba mashi ido,yasa shi jefa mata harara,a hanzarce ta kawar da idanunta daga kallon fuskarshi da take yi,jikinta kuma yayi sanyi,ta shiga tambayar kanta dalilin hararar da taga big bro yayi mata,kodai baya farin ciki ne da kasancewarta JININ SA!?tabbas hakan zai iya faruwa,Wataƙil kodan ya saba ganinta a matsayin ƴar aikinsa,baiwarsa,ƙasƙantacciya shiyasa yanzu Yake nuna 6acin ranshi don yana ganinta tamkar a matsayi ɗaya suke dashi,Ƴa'ƴan Wa da ƙani,da alama hakan baiyi masa ba, "Idan har dagaske ne abunda nake hasashe,insha Allah zan tattara na bar masu gidan,saboda bana son 6acin ranshi,zan iya yin komai don farin cikin shi," ta ƙarasa zancen zucin nata tare da sake ɗagowa a hankali don ta saci kallonshi,adai dai lokacin shima ya ƙara ɗagowa da kyawawan idanuwanshi kai tsaye suka shiga cikin nata,nan take taji gabanta ya kuma faɗuwa rass,kasa janye idanuwanshi yayi daga kallonta da yake yi,a yayin da yake jujjuya spoon ɗin dake hannunsa acikin plate ɗin abincin gabansa,har Yanzu bai daina mamakin kasantuwarta ƴar uwarshi ba,ta jininsa,tamkar a mafarki haka yake ganin abun,ganin ta zuba mashi ido batare da ta janyesu ba yasa shi ɗaure fuskarshi yasha murrr,saboda kada ma yarinya taga fuska har tayi tunanin raina sa don tasamu matsayi,    "U will still remain who u are,wadda take aiki a ƙarƙashina,Matsayin dana baki kenan,"ya fada a ransa   Murmushi Abusufyan yayi tare da cewa"bazasu kara wahala ba,bazan ta6a bari hakan ya faru ba,tunda dae har yaran nan suka bayyana a matsayin ƴa'ƴana,In sha Allah bazan ƙara bari suyi aikin wahala ba,ko cokali bazan ƙara bari ɗaya daga cikinsu ta ɗauko ba acikin gidan nan,rayuwar hutu kawai nake so suyi rayuwar ƴanci," ya ƙarasa zancen zucin nashi a yayin da yake bin kowaccen su da kallo cike da so da ƙaunar ƴa'ƴan nashi,'   Janye idanunshi yayi daga kan nata,kafin ya miƙa hannu tare da ɗaukar Glass cup mai ɗauke da abun sha me sanyi ya kai shi saitin mouth dinsa yana sipping ɗinshi anatse,yayin da sanyin lemun ke ratsa throat ɗinsa,a hankali ya lumshe idanunsa tare da ɗan ware su kaɗan,again suka ƙara sauka akan na sehrish a karo na uku kenan,agaggauce tayi hanzarin janye idanunta daga kan fuskarshi ta mayar dasu akan plate ɗin abincin dake a gabanta, Hannu Sgr ya sanya tare da yago tissue ya goge bakinsa,kafin ya miƙe tare da juyawa ya nufi upstairs,Miƙewa Marshal yayi da alama shima ya kammala breakfast Ɗin nasa,shima upstairs ya nufa, Fitowar Hajiya azeema keda wuya daga cikin bedroon ɗinta,ta jiyo muryar gwaggon katsina tana ta faman sambatu tana cewa"Tsiyarta kenan mutun yazo gidan ƴan gayu,Ni bazan iya rayuwar turawan nan ba,taya za akai ma mutun salalar biredi tare da tea rabin kofi kamar wata ƴar iska ace in sha"?   Tafiya take tana sambatu zaninta a hannu sai ɗan undi ajikinta,kanta kuwa ta kifa wannan ɗaurin ɗan kwalin nata mai kama da helmert,   har zata gifta hajiya azeema tayi gyaran murya tare da ambaton sunanta"Goggo," fuska a yamutse ta juyo tana kallonta,dawowa tayi daga gefenta suna fuskantar juna tace"Yawwa azeema,wai nikam inaso in tambayeki,' Natsuwa hajiya azeema tayi tare da cewa"ina sauraronki gwaggo,"   "Jiya nayi wani mafarki,ƴa'ƴan abusufyan sun bayyana,wasu ƴan uku kyawawan gaske,da nayi tunanin koda gaske ne abun ya faru amma daga baya na gane ba gaskiya bane,in ba haka ba,yaushe abusufyan ya ta6a yin aure"? Tayi tambayar tana kallon hajiya azeema,wadda ta saki baki tana kallon gwaggon,   Ganin azeema tayi sototo tana kallonta yasa tayi tunanin cewa ko abunda ta faɗa ya bata mata rai ne,   "Nasan dole kiyi mamaki kema,Mafarkin fa kamar dagaske,ɗaya daga cikinsu har tana sharara mana labarin ƙarya waisu ƴa'ƴan wata zainabu ne,kuma ma acikin labarin hada wata hajiya Ameena,in banda shaiɗan ina abusufyan ina ƴa'ƴa"?   Ƙiris ya rage Azeema ta fashe da dariya agaban gwaggon katsina,ganin yadda ta haƙiƙance tana kora mata bayani,kuma babu alamun wasa a fuskarta, Ƙunshe dariyar bakinta tayi tare da basar da ita tace"Gwaggo Anya kina shan maganinki kuwa?ina Dr harris yake?gaskiya inason ganinshi,'   Tsoki gwaggon katsina taja tare da cewa"Harrisun daya zama ɗan iska," Waro ido waje azeema tayi tace"gwaggo harris ne ɗan iska"?   ta6e baki tayi tare da cewa"Zan masa ƙarya ne?ba ɗan cikina bane"?nasha wahalar yima yarona tarbiya amma waccen sauden.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya ciyota,zanin hannunta takai saitin idonta tana ƙoƙarin goge hawayenta,   Zuru harris yayi wanda fitowarshi kenan kuma atare da saude suka fito,jin maganar gwaggone ma yasa yayi hanzarin cire hannunshi daga cikin na sauden,   Hajiya azeema tace"gwaggo faɗamun me harris ɗin ya akaita,?   Hankali tashe Saude tace"ya harris pls kada ka bari gwaggo ta faɗa mata abunda muka aikata,kasan gwaggo yadda take ɗaukaka abu,inta tashi faɗi saita ƙara ma miya gishiri,'   Dr harris yace"just don't worry ur self,insha Allah bazata faɗa mata ba," Faɗin hakan keda wuya gwaggon Katsina tace"Azeema abun da ciwo,yanzu yunwa nake ji,shiyasa ma kika ga nafito ina sambatu,Wurin waccen matar zani,wlh ba azmee ba Allah yasa ramadan ce ita yau saina zazzaga mata rashin mutunci!Ni zata raina ma hankali tunda safe,takawo mun tea rabin kofi da salalar biredi wai in fara da wannan,don ta raina mun hankali,nayi mata kama da kusu ne?   Rai a6ace tayi maganar,aikuwa atare haris da saude suka fashe da dariya,a hanzarce ta juyo sakamakon jin sautin dariyar tasu,nan take ta tsuke fuska ganin shi tare da saude,   Murmushi Hajiya azeema tayi tare da cewa"haba gwaggo baki fahimce ta bane,cewa fa tayi ki fara da wannan tana nufin kafin ki tashi fitowa zuwa yin breakfast ɗin,yanzu haka yana can an shirya mana mu kawai ake jira muje muci namu kalacin,"   Hajiya azeema ta ƙarasa maganar tare da ruƙo zanin hannun gwaggon tace"Bari na taimaka maki ki ɗaura shi,"   Girgiza kai tayi tare da cewa"Barmin shi a hannuna,nafison inji iska na shiga ta ko'ina,"murmushi hajiya azeema tayi kafin tace"hakan ma yayi gwaggo,ae under skirt din ma bamai sharashara bane,yana da kauri,amma duk da haka dae ki ɗaura zanin yadda zaki fito da kyau tunda ga rigarshi kin sanya ajikinki,Kuma kinga Abusufyan na nan,Ga kuma ƴa'ƴansa,bazasu so suga gwaggonsu a haka ba,"   wani irin ƙayataccen murmushi gwaggon katsina tasaki tare da cewa"Kenan dagaske ne Mafarkin da nayi jiya"?   Jinjina kai Azeema tayi tace"Ae suna nan,duk abunda ya faru jiya dagaske ne,ba mafarki kikayi ba,agabanki akayi komai kin dai shafa'a ne,'   Jin haka yasa tayi saurin mayar da zanin ajikinta tana ɗaure shi tana cewa"Allah sarki ƴa'ƴan abusufyan ɗina,bayin Allah,sunsha wahala a hannun wannan fasiƙin mutumin baƙin shaiɗani,Allah mutumin nan ƙaho ne kawai bai fito masa aka ba,amma ina tantama anya ba Irin shaiɗan bane"?    "gwaggo kidaina maganarsa ma,Ni wlh ko zancen shi ma bana so anayi,Na tsani mutumin nan kamar yadda natsani mutuwa ta,"acewar hajiya azeema,tayi maganar ne a yayin da take kama hanyar Zuwa Dining area ɗin nasu,bin bayanta Gwaggon tayi tana cewa"Ae ko sai dai ki toshe kunnanki,don zancen sayyadi ya zama dole,in har ba'a kawo min kansa ba,bazan daina faɗan sunan shi ba,'   Murmushi kawai hajiya azeema tayi,atare suka ƙarasa dining area din,    Gaggaisawa suka fara yi da junansu,su jahad na ganin saude suka tashi atare suka nufe ta,dama Jiya basu samu damar gaisawa da ita ba,saboda yanayin da suka shiga gaba ɗayansu,haɗasu tayi ta rungume ajikinta,cike da farin ciki tace"Ina tayaku murna sosai,nayi farin ciki sosai,Ya harris ya sanar dani komai agame daku,ashe ku jininsu ne,'ta ƙarasa maganar ayayin da take raba jikinta daga nasu,kowannansu fuskarshi ɗauke da murmushi,Jahad tace"Aunty saude kinga ikon Allah ko?munsha wahala sosai,mu kanmu bamu ta6a tunanin cewa muna da dangi ba,amma sai gashi ƙaddara ta haɗamu da ya Omar,Ita kuma ƴar uwarmu Sehrish ƙaddarar aikine ya kawota gidan nan,Muna tare da ƴan uwanmu ba tare da mun sani ba,sae gashi rana ɗaya Allah ya bayyana mana komai,'   Saude tace"Congratulations Once again,ina ƙara tayaku murna sosai da kuka fito daga tsatson wannan Family ɗin,abun alfahari ne wannan"kafin ta mayar da idanunta kan Hosana,Cike da zolaya taja kumatunta tare da cewa"Hosana Kinga yadda kika canza?kamar ba wannan Sha takwas sha taran ba,mai ɗan kai,kinyi kumatu kamar Balon balon,Ga haske gaskiya ya Omar ya Iya raino," Fashewa da dariya hosana tayi tana faman sunnar dakai, "Kiyi ma sister ɗinku mana,Ita bazata taso mu gaisa ba"?tayi maganar tana kallon sehrish dake zaune,tana faman kallonsu ɗaya bayan ɗaya, Murmushi jahad tayi tare da juyawa tayi mata alamar ta taso da hannunta, Miƙewa sehrish tayi tare da nufar inda suke,koda ta ƙaraso saude ta sanya hannu tare da janyota ta rungumeta,kafin ta raba jikinta dana sehrish tace"Masha Allah,gaskiya ban ta6a ganin triplet,masu kama iri ɗaya sak kamar taku ba,ina taya ki murna sosai da Allah ya haɗaki da ƴan uwanki,da kuma mahaifinku,da kuma danginku,' Fuskar sehrish ɗauke da murmushi tace"Ngde sosai," "Allah ya tsare mana ku,Ya Albarkaci rayuwarku ya kuma kare ku daga sharrin maƙiya,' Atare suka amsa mata da Ameen,bama su kadae ba,hadasu Abba dake sauraron maganganun nasu, Kamar yadda Abba yayi alƙawarin shirya gagarumar walima na bayyanar ƴa'ƴan ƙaninsa Abusufyan,Da kanshi ya fidda date ɗin da za'a gabatar da ita,Kuma tun aranar ya fara kiran Ƴan uwa da abokanan arziƙi yana sanar dasu game da ƴa'ƴan abusufyan da suka bayyana,Babu wanda bai bari ba,kowa kira yake tun daga kan danginsu na Zaria,na damaturu dana sauran states ɗin da kuma waɗanda ke zaune Ƙasashen waje,kowa saidaya sanar mawa,Bayan Abbas ya koma gidane da safe Amani ke tambayarshi meya faru ne jiya ya hanasu zuwa gidansu,Anan ya kwashe duka abunda ya faru game da su Sehrish ya sanar mata,wani irin farin ciki ne ya cika ta,Ba don komai ba sai don sanin cewa plan ɗin Aunty babba ya gama Tarwatsewa,ae tunda taji cewar ƴan mata ne kuma sun kai shekara goma sha bakwai zuwa sha takwas kyawawan gaske,Nan fa ta kwashe da dariyar mugunta aranta tana cewa Naga yadda za'ae Aunty laila ta cimma burinta,Gida bai ƙoshi ba taya za'a ba na waje,Ae tuwona maina za'ayi,Haba ae xance ya ƙare, ita kanta Amani ta ƙosa ranar walimar tazo saboda suje gidan,saboda taji cewar Aranar Aunty babba da hafsat zasu zo Abuja,babban burinta taga tashin hankalin da aunty babba zata fuskanta inta gansu, Ranar walimar kuma yayi dai dai da ranar da Ammi zata zo,tare da wasu daga cikin danginsu,haka zalika captain Najeeb da kuma Talal suma duk a ranar zasu dawo gida,ba don komai ba sai don su sanya ƴa'ƴan uncle ɗinsu abusufyan acikin idanunsu,Kowa ɗokin ganinsu yake yi kamar kamar me,musamman da sukaji irin rayuwar da yaran sukayi a wulaƙance sai suji wani irin tausayinsu da kuma ƙaunarsu ya shiga cikin ransu,kuma duk aranar MG Osman da kuma Captain Adam suma zasu dawo gida,wanda tun dawowarsu daga U.s suka tafi sada zumunci,Gaskiya wannan Babbar rana ce,Hakan yasa ma Zamuyi shiri na musamman ni da makaranta littafina don mu halarci gidan amatsayin gayyar soɗi tunda ba'a gayyace mu ba,Sa kaine kawai, Cikin ƴan kwanakin nan wata irin rayuwar farin ciki suke gudanarwa tare da Daddynsu,kullum yana manne dasu,Da kanshi ya zauna yayi masu kitson kalaba guda bibbiyu akansu kamar yadda ya ta6a yi masu suna yara,koda yazo kan Sehrish,Cike da mamaki yace"Ya akai naga gashin kanki guntu?ko kinyi wani ciwo ne dayasa aka datse maki gashin,"girgixa kai tayi tare da cewa"a'a Laifi nayi ma Babba yaya shine ya yanke mun gashin da almakashi," da buɗar bakin Abusufyan sai cewa yayi"Yayiwa kanshi ai," murmushi sehrish tayi duk da batasan me daddyn nasu yake nufi da hakan ba,duk a wannan kwanakin basu je school ba,Abusufyan da kanshi yace kada su damu shi da kanshi zai kaisu makarantar don karma a tuhume su, A 6angaren Sir Commander haroon kuwa,tamkar munafuki haka ya koma acikin gidan,ba kowa ma ke sanin lokacin da yake shigowa gidan ba,da kuma lokacin da yake fita,Da alama dae akwai wani abu da yake shiryawa a 6oye, *AMRISH* Zaune take acikin class ɗin gaba daya ta shiga damuwar rashin ganin Sehrish kwana biyu ko layinta ta kira bata samu,hatta wayar junaid ta jaraba kira shima ba'a ɗagawa,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,tagumi tayi idonta cike tab da hawaye saboda damuwar da take ciki,taso ace sehrish na nan atlease zata ɗebe mata kewa,tana cikin wannan tunanin har malam ya shigo cikin class ɗin nasu bata sani ba,bayan ya kammala amsar gaisuwa daga wurin student din,kai tsaye ya ƙarasa seat ɗin da Amrish take,hannun shi yakai wanda ke ruƙe da maker ya ɗan bubbugi desk ɗinta,a firgice takai idanunta akanshi,Yunƙurawa tayi tare da miƙewa ganin Ya mu'allim,wanda tun ranar daya ba sehrish Ruwan addu'ar nan bai ƙara zuwa makarantar ba,duk da sun samu labarin cewar Ya tafi Umra ne,shiyasa aka musanya masu shi, Murmushi ya ɗan saki afuskarshi yana kallonta yace"tunanin me kike yi ne?har na shigo cikin class ɗin baki sani ba? Muryarta na rawa tace"Ayimun afwa ya mu'allim,Bana jin daɗi ne bansan ka shigo ba, Jinjina kanshi yayi tare da ɗan kai idanunshi kan Seat ɗin sehrish yace"Ina yarinyar nan take?ƴar family ɗin Salahuddeeen hussein naga kamar bata a class ɗin"? fuskarta ɗauke da damuwa tace"Batazo ba,yau kusan kwana huɗu kenan bata zo school ba,kuma nayi trying kiran layinta amma bana samu,har brother ɗinta na kira,shima layinsa ba'a samu,' Jin hakan yasa shi fargabar to kodai wani abu ya faru da yarinyar?Yaso yaji ya tayi da ruwan addu'ar daya bata,shin tasha ko bata sha ba? Jinjina kanshi yayi tare da juyawa yace"Allah yasa dae lafiya,in har batazo ba,zuwa sati mai zuwa zan je gidansu don na binciki dalilin rashin zuwan nata,' Jiki asanyaye Amrish ta koma ta zauna,saman seat ɗin nata,jikinta har ya fara kerma saboda tsoran kar ace wani abune ya faru da Sehrish, A ƙarshe dae ta yanke shawarar neman gidansu don taje ta ganta da kanta. *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. Sai faman safa da marwa takeyi acikin bedroom ɗinta,gaba ɗaya ta rasa samun natsuwa,hakanan ta dinga jin fargabar zuwa abuja,ga zumuɗin zuwan da takeyi amma kuma tana zullumin abunda zai biyo baya,hakanan ta dinga jin kamar wani abu mara daɗi zai faru,ƙafafunta har sun fara ciwo saboda zaryar da take ta faman yi,tun bayan da ta kammala sallar asuba bata koma bacci ba,Jikinta na sanye da Zumbuleliyar riga doguwa brown,sae guntun hijabin da ta kammala sallah dashi,hannunta na ruƙe da wayarta,wani tunani ne ya fado mata aranta,cikin sauri ta shiga danna wayar dake hannunta,Hayaam ta buga ma waya,nan take kiran ya shiga,batare da 6ata lokaci ba hayaam ta ɗaga kiran,daƙyar take magana saboda ta katse mata baccinta,rai a6ace tace"Lafiya kika kira Ni?bayan kin gama kwashe mun albarka"!   Cikin lallami Aunty babba tace"Dan Allah hayaam komai ya wuce kinji ƙanwata?nasan ban kyauta ba,amma kiyi haƙuri,"   Tsoki hayaam taja tare da cewa"hmmm,halan yanzu kin gasgata maganata ne?shiyasa kika kira don jin ƙarin bayani?   Aunty babba tace"EH,hakane,na yadda da abunda kika faɗamun,tuntuni shiyasa ma na kira ki,"   Hayaam tace"Yanzu ya kenan?ya zamuyi?don gaskiya akwai matsala aunty laila,burin mu bazai ta6a cika ba,muddin yaran nan suna nan!"   Jinjina kai Aunty babba tayi tana cewa"babban takaicina yaran da suka kasance mata ne!har ƴan uku,gaskiya abusufyan bai kyauta mana ba tsakani da Allah,haka ake?kawai sai yaje yayi aure a 6oye batare da sanin kowa ba?wai kuma da sanin ammi kuwa"?   Hayamm tace"Anya,gaskiya ina tunanin Ammi bata sani ba,'   Jin haka yasa Aunty babba cewa"Allah yasa in tazo tace bata amince da yaran ba,kinsanta Jarababbiyace,musamman ma da yayi auren bada saninta ba,Wai shin su yaran ina mahaifiyarsu take ne?tana da asali kuwa"?tayi tambayar cike da son jin ƙarin bayani,   Hayamm tace"Ina fa,ae rannan na tambayi azmee game da mahaifiyarsu,shine take sanar dani cewa mahaifiyar yaran Ƴar fa mai gadin gidan gwaggon katsina ne!basu da wani asali,buzaye ne ƴan niger,"   Aunty babba tace"tabɗijancan aikuwa Ammi bazata ta6a yarda dasu ba,kinsanta ta tsani mutun mara asali,gata ita kaifi ɗaya ce muddin tace bata yarda dasu ba amatsayin ƴa'ƴan Abusufyan to fa korasu zatayi daga gidan,yakamata muyi wani abu akai,tun kafin takai ga zuwa,"   Hayaam tace"meke nan zamuyi?kinsan fa gobene walimar kuma gobe zata zo,"   "Abunda zamuyi shine,Ae ina da numbar Ammin a wayata,zanyi amfani da sabon sim ɗina,wanda ban fara amfani dashi ba,zan kirata na sanar da ita game dasu tunkan taji a wurin wani,"acewar Aunty babba   dariya hayaam tayi tare da cewa"Gaskiya aunty laila kin iya haɗa tuggu,ni sam banyi tunanin hakan ba,wannan ce hanyar da zamu bi wurin tarwatsasu,idan kika kirata awayar ki tunzurata sosai,ki ɗaurata akan network har sai ta amince da kalamanki,ki sanar da ita cewa yaran shaggu ne,abusufyan yayi ma mahaifiyarsu ciki a 6oye,shine suka so su 6oye mata,don karta sani,"   Murmushi Aunty babba ta saki tana cewa"hakan yayi sosai,zan tsara komai yanzu........."tana cikin maganar taji alamar dirar motar ishaq,   Cikin sauri tace"Hayaam inaso ki ɗauko min hoton yaran kafin muzo gobe,zan kashe wayar yanzu ishaq ya dawo,   "Toh aunty laila,zanyi ƙoƙarin ɗauko maki hoton nasu," Daga haka sukayi sallama da juna, Ajiyar zuciya aunty babba ta sauke,har taji wani sanyi a ranta saboda ta samu mafita, Bayan sun kammala wayar hayaam ta buɗe ƙopar ɗakinta tare da fitowa,cikin sanɗa hayam take tafiya don kar wani ya ganta,a haka har ta ƙarasa bedroom ɗinsu sehrish,tura ƙopar tayi cikin sa'a ta samu ƙopar ɗakin a buɗe,leƙa kanta ta fara yi anan ta same su,suna ta sharar bacci wanda tun bayan sallar Asuba da suka tashi suka koma suna yin baccin, Murmushi ta saki tare da sa kai ta shige ciki,adai dai bakin gadon nasu ta tsaya tare da ɗago da wayarta dama already a cikin camera take,Saita fuskarsu tayi dama kuma duk suna facing ɗin ceilling,kyakkyawan hoton fuskokinsu ta ɗauka,bayan ta kammala ɗaukar hoton,ta lalla6a batare da kowa ya ganta ba,ta koma bedroom ɗinta,cikin sauri ta tura ma Aunty babba hoton ta whatsapp ɗinta, ❤🤍❤ Wuraren karfe takwas,suka farka daga bacci,sehrish ce ta fara shiga toilet tayi wanka,bayan ta fito daga wankan jahad ta shiga ciki,gaban dressing mirror ta zauna ta gama shafe jikinta,ta feshe shi da turare,sannan ta koma ta ɗauko Jallabiya fara ta zura ajikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,musamman adon dake jikin rigar na stones,shiya ƙara ƙawata rigar,bayan tayi rolling kanta da mayafin rigar,ta fito daga cikin bedroom ɗin nasu ta wuce kitchen,cike da zumuɗin kaima babban yaya breakfast ɗinshi gaba ɗaya ta manta da abunda Uncle abusufyan ya faɗa mata, A kitchen ta samu azmee,har ta kusa kammala girkin,ganin yadda take ta aiki ita kaɗae yasa sehrish taji duk ba daɗi,muryarta a sanyaye tace"Ina kwana Aunty azmee," Juyowa tayi daga tsayen da take gaban gas cooker,fuskar nan ɗauke da murmushi tace"Lafiya lou ƴan matan abusufyan,fatan kun tashi lafiya"   "Lafiya lou,amma aunty azmee gaskiya banajin daɗi in naga kina aiki ke kaɗae,meyasa baki tashe mu ba,munzo mun tayaki aikin"?tayi maganar yayin da take ƙarasa shiga cikin kitchen ɗin,   Azmee tace"kada ki damu,na riga na saba da aiki,wannan ba wani abu bane,Abba ma ya nemi daya ƙaro masu aiki amma nace mashi ya barshi kawai,saboda na saba da yin aiki ni kadae," Girgiza kai sehrish tayi tare da cewa"that's impossible,gaskiya in har ba zaki amince a ƙaro masu aiki ba,to daga yau Ni dasu jahad zamu dinga tayaki aiki,don bazaiyiwu ba kiyi ta wahala ke kaɗai,"   murmushi kawai azmee tayi batare da tace Komai ba,    "Aunty azmee idan akwai abunda kika kammala inaso zan fara kaiwa dining in jera,kinga na rage maki wani aikin,"   "Ban kaiga shiryasu ba,amma sai dai idan zaki kaima Sgr nashi,sae na haɗa maki,ki kai mashi,"   Murmushi ta saki tare da cewa"Toh," Shirya mata breakfast azmee tayi acikin ƙayataccen tray,bayan ta kammala,sehrish ta ɗauki tray ɗin tare da fucewa daga kitchen ɗin, tana cikin tafiya harta kusa hayewa upstairs taji anyi mata gyaran murya abayanta,cikin sauri ta juya don taga Wanene,ganin Uncle abusufyan yasa gabanta faɗuwa,saboda tana kallonshi ta tunano da abunda ya faɗa mata a daren jiya, Muryarta na rawa ta furta"Daddy,"ƙarasawa yayi wurinta tare da tsayawa dab da ita fuskarshi a ɗaure yace"Me na faɗa maki jiya?tun yanzu zaki fara sa6amun"? Hankali tashe sehrish tace"a'a daddy,wlh mantawa nayi,bazan ƙara ba,dan Allah kayi haƙuri,"    "Zo ki wuce ki mayar da kayan abincin kitchen,inyaso azmee taje takai masa,"   Jiki asanyaye Sehrish ta juya tare da kama hanyar komawa kitchen,duk wannan abun daya faru akan idon,Mommynsu junaid alexandra,tana tsaye abakin part ɗinsu na downstairs tana kallonsu, Haka ta koma kitchen da kayan abincin idonta cike tab da hawaye,taci burin ta ganshi yau,amma Uncle abusufyan yayi mata tsiya, Tamkar wadda aka zarewa laka haka ta shiga kitchen ɗin,Azmee na ganinta dauke da tray a hannu tace"Lafiya naga kin dawo da kayan abincin"?tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,muryarta tamkar zatayi kuka tace"Uncle ne ya hanani zuwa part dinsa da sunan aiki,tun jiya da daddare ya gargaɗeni akan Karna kuskura na ƙara yin aiki a ƙarkashinsa,bansan meyasa ya hanani ba," Cike da mamaki azmee tace"to fa!ko meyasa yayi hakan?kuma kin tabbata bakiyi wani laifin ba wanda yajawo har ya hanaki aiki a part ɗinsa"?   "Aunty azmee ni banyi laifin komai ba,"ta ƙarasa maganar a yayin da take ajiye tray ɗin hannunta,   Shiru azmee tayi aranta tana mai mamakin hukuncin da Abusufyan ya yanke ma sehrish,to kodai don saboda basa shiri da Alexandra ne?tabbas zai iya yiyuwa hakane!tunda akwai gaba atsakaninsu,dole kuwa ya hana Sehrish tayi ma Sgr aiki,don bazai ta6a yarda ƴarsa tazama baiwarsa ba,   "Aunty azmee ko zaki iya nema mun alfarma a wurinsa yabarni in cigaba da aiki acikin gidan nan kamar yadda na saba,"muryar Sehrish ce ta katse mata tunaninta,   zaro ido azmee tayi tare da cewa"Ni ƴar ubanwa?na isa in shiga tsakaninki da mahaifinki?bazaiyiwu ba sehrish,shawarar da zan baki shine kawai ki bi Umarnin mahaifinki ki xauna lafiya,Shi kaɗae yasan dalilinshi na yin hakan,kuma in har kika yi mashi biyayya zakiga ribar yin hakan,"   ɗakyar ta iya haɗiye yawun bakinta,ga hawaye sae faman zarya sukeyi a fuskarta,     "Wannan hukuncin da mahaifinki ya yanke,yayi mun dai dai,don koda bai dakatar dake daga yi mashi aiki ba,to ni dakaina zan hanaki!"   Gaban Sehrish ne ya faɗi rass jin muryar Mommynsu junaid abayanta,Azmee kuwa na ganinta tasha jinin jikinta don tasanta sarai bata da mutunci ta wani 6angaren,   Juyawa sehrish tayi da sauri tana kallonta,   A hankali take tunkararsu yayin da take ci gaba da magana"Banason kusancinki dashi ko kaɗan!just maintain a good distance between u and him,In ba haka ba,You will see the trouble!!"Jikin sehrish har kerma yake yi don ba ƙaramin tsoranta takeyi ba,koƙarin 6oyewa a bayan Azmee takeyi,don gani take tamkar Alexandra zata bugeta ne,   Koda ta ƙaraso dab dasu,harara ta wurga ma azmee tare da cewa"Matsa daga gabana,da ita nakeson magana,"jiki na rawa azmee ta janye jikinta gefe guda,aranta tace"tashin hankali ashe har yanzu matar nan,bata canza ba,lallai akwai matsala,"    goya hannayenta tayi asaman ƙirjinta,yayin da suke fuskantar juna ita da Sehrish,saboda tsabar tsoro ƙiris ya rage sehrish ta saki fitsari,ko idonta bata iya dagawa ta kalleta saboda yadda tayi mata tsaye aka,   Wani irin kallo Alexandra ke bin Sehrish dashi,tun daga ƙasa har sama,yatsina fuska tayi tare da cewa"Ur name"?   Murya na kerma tace"Sehrish,"   Jinjina kai alexandra tayi tare da cewa"saboda daddynki ya hanaki aiki a part ɗin rafayet shine kike kuka?why? ..girgiza kai sehrish tashiga yi tana cewa"a'a..ba saboda haka nake kuka ba...."   "Kukan menene toh"?ta sake jefa mata tambaya a karo na biyu,   "Babu komai,"ta bata amsa tana faman zazzare idanu,   Murmushin gefen fuska alexandra ta saki kafin ta kuma cewa"dama ana kuka ne just without any reason?ki faɗamun gaskiya mana,kodai kin faɗa tarkon shi ne"?   Waro ido waje Sehrish tayi hankali tashe tace"a'a ba haka bane,kawai ina kuka ne saboda tsoron hukuncin da babban yaya zai yanke mun in ya gane cewa na daina yi masa aiki,"   Ta6e baki alex tayi tare da cewa"Just calm down ur mind,Bama zai ta6a damuwa akan hakan ba,kiyi ma mahaifinki biyayya,kuma ki nisanta kanki dashi kamar yadda nace,hakan zaifi maki kwanciyar hankali,"tana kai ƙarshen maganarta,ta juya cike da isa tare da fucewa daga kitchen ɗin, Fitarta keda wuya Azmee ta mayar da idonta kan sehrish saboda ta lallashe ta,amma ina,tuni sehrish ta watsa da gudu tabar kitchen ɗin, A bakin ƙopar dakinsu ta tsaya tana faman shessheƙar kuka,zuciyarta har wani tafarfasa takeyi mata,dole tayi kuka saboda tasan cewa ta rasa Sgr na har abada,tunda mahaifiyarshi ta nuna bata sonta,zuƙunnawa tayi a ƙopar ɗakin tana cigaba da kukan nata,ta jima zuƙunne a wurin cikin wani irin yanayi mara daɗin ji,tana jiyo muryarsu jahad acikin bedroom ɗin,suna tattaunawa kan wankan da zasu ɗauka gobe ranar walima,hada zancen saloon ɗin da daddynsu yace zai kaisu ayau,   gaba ɗaya taji komai ya fita ranta,don har wani zazza6i taji ya saukar mata ajikinta,ita kaɗae tasan raɗaɗin da takeji acikin zuciyarta,hannu tasa tare da share hawayenta sosai don karsu hosana su gane cewa tayi kuka,bayan ta kammala goge hawayen ta miƙe,tare da buɗe ƙopar ɗakin tashiga ciki,   Jahad na zaune gaban mirror tana shafa powder a fuskarta,hosana kuma na tsaye gaban wardrobe tana cewa"Nama rasa wani kaya zansa yau,saboda inaso in na kammala shiryawa inje in tashi Ya Omar daga bacci don nasan cewa bai kaiga tashi daga bacci ba,"ta ƙarasa maganar tare da ɗan juyawa ta kalli jahad tace"daddy yace yau zai kaimu Saloon ko?to da yaushe zamu fita?donni hada ƙunshi za'ayimun a hannuna,yanzu ma in naje ɗakin ya Omar zan tambayeshi wani kalar ƙunshi yakeso ayimun baƙi ko ja," jahad tace"Soyayya daɗi,kunshin ma sai an tambayi ya omar wani kala yakeso kenan?to gyaran gashin fa?shi bazaki tambayeshi wani kala yakeso ba?   murmushi hosana tasaki tare da cewa"dole ma in tambayeshi wani kalar gyaran gashi yakeso ayi mun,"_   Suna cikin magana muryar Sehrish ta katse su da cewa"Ƴan uwana rabin raina,me kuke tattaunawa akai ne?naji kamar ana gulmar ƴa omar,ko kunnena ne,'tayi maganar tana ƙoƙarin danne damuwarta,gefen gadon ta samu ta zauna,tana faman sauke ajiyar zuciya, .juyowa sukayi suna kallonta,hosana tace"Sehrish ina kika je,na tashi ban ganki ba,har naji tsoran kada ace wannan halittarce mai ƴan idanu ta ɗauke mana ke"   Dariya sehrish tayi tare da cewa"ni harna manta da wannan abun,koda na tashi daga bacci ban iya tuna abunda ya faru jiya ba,sae naji kamar duk a mafarki ne,"   Hosana tace"Ae taji tsoro ta gudu,yau da daddare in tadawo,zan aro bindigar yaya Omar in harba mata bullet acikin idanunta,"atare suka fashe da dariya jin abinda hosana tace,hada kwatantawa da hannunta yadda zatayi shooting din guguwar,   Jahad tace"Cika baki kawai,kin manta kukan da ki kayi mana ajiya?kinfi kowa tsorata,ba don nayi maki addu'ar ɗaukewar fitsari ba,da ba'asan me zai biyo baya ba....'dakyar ta ƙarasa maganar saboda dariyar da tazo mata,   cike da nishaɗi suke yin firar tasu,kafin lokacin yin breakfast yayi atare suka fita,Hosana ta wuce part ɗin Omar,yayin da su kuma suka wuce dining,Sehrish dae jurewa kawai takeyi,suk ta gaza sakewa saboda rashin sanya sgr a idanunta,gashi bai sauko downstairs ba,saboda Azmee takai mashi nashi a part ɗinsu,kuma sam bai tambayeta akan Sehrish ba,Hakan na nufin cewa Sgr bai damu da ita ba ko kaɗan,dama haroon yace Iskace ke wahalar da mai kayan kara, Yana kwance yana sharar bacci,hosana ta shiga bedroom ɗin nashi,lalla6awa tayi ta haye saman gadon har wurinshi ta ƙarasa,saitin fuskarshi tana kallon zunzurutun kyawunsa, Hura mashi iska tayi a fuskarshi,nan take ya ɗan motsa tare da yatsina fuskarshi,murmushi hosana ta saki tare da kai hannu ta toshe mashi hancin shi,aikuwa a gigice ya farka batare da ya sani ba ya tattara dukkanin ƙarfinshi ya cakumi hosana tare da yin wurgi da ita,gaba daya ta tafi yaraf ta kife ƙasan tiles ɗin daga gefen gadon,nan take ta fashe da kuka saboda hancinta daya daki ƙasa,shi duk atunaninshi wani ne ya kawo mashi hari shiyasa yayi mata haka,kuma yana yin wurgin da ita,yaci gaba da baccinsa,dama duk a cikin magagin bacci ne yayi mata hakan, Cikin baccinshi ya jiyo sautin kukanta tana cewa"Wayyo Allah,hanci na ya fashe,ya Omar ka kashe ni," A firgice ya ware idanunshi tare da miƙewa daga zaune yakai idanunshi wurin da sautin kukan ke fita,anan ya samu hosana dafe da hancinta a zaune dirshan tana kuka, Hankali atashe ya sauko daga saman gadon ya zukunna agabanta yana tambayarta lafiya?garin yaya taji ciwo a hancinta, Cikin shessheƙar kuka tace"bakaine ka cakume ni ba,kayi wurgi dani daga saman gado na faɗo ƙasa har hancina ya bugu," Waro ido waje yayi tare da cewa"Ni kuma dakaina"? Jinjina kanta tayi tare da cewa"Eh mana,saboda kawai na toshe maka hanci,   🙏🙏🙏   *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* ❤🤍❤ *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Hannu yasa tare da tallabo fuskarta yace"Hosana bada sani na nayi maki hakan ba,laifin ki ne,meyasa zaki toshe mun hancina?so kike na mutu'? Girgiza kai tayi"a'a,banso ka mutu,ae ni wasa nayi maka ko,"tayi maganar tana satar kallon fuskarshi,   "Faɗa mun me ya kawoki bedroom ɗina har saman gadona"?    A ƙule tace"nifa nazo ne na tashe ka don kaje ka ci abinci,naga kowa ya fito banda kai,kuma zasu iya cinye abincin duka," fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Waya faɗa maki za'a cinye abincin,ae ko ban fita ba Azmee zata kawo mun ne har cikin part ɗina,"     Shiru tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,ɗagowa ta ƙara yi zata saci kallonshi suka haɗa ido,ganin yadda yake kallonta ko ƙyaftawa baiyi hakan yasa ta ɗaure fuska cikin shagwa6a tace"Ya omar wannan kallon fa,ka wani tsare ni da ido,"   yadda tayi maganar ba ƙaramin burgeshi tayi ba,ya jima yana kallonta batare da yace wani abu ba,har sai da ta hasala rai a6ace tace"shikenan tunda ba zaka mun magana ba,bari na tashi na tafi,dama ko abincina banci ba,saboda kawai inzo in tashe ka daga bacci,amma ko farin ciki ba kayi ba,'   Ajiyar zuciya ya sauke tare da ruƙo hannunta cikin nashi"Hosana,so nake ki faɗa mun gaskiya,kina sona da gaske?kuma zaki aure ni? Waro ido waje hosana tayi tana kyakkyaftasu kamar na ƴar tsana jin abunda yace,a ruɗe tace"Ya Omar!aure fa!"_ Jinjina mata kai yayi tare da cewa"eh,aure hosana ko baki shirya ba,"   Turo baki ta ɗanyi tana ƙunƙuni ƙasa ƙasa,hankalinsa kam harya ɗan tashi saboda ganin yadda ta tsorata don yayi mata zancen aure,dama fargabarsa kada sai anje wurin nema mashi auranta tace bata shirya ba,don yasan ba cikakken hankali gare ta ba, Lalla6ata ya shiga yi"pls hosana,ki faɗamun gaskiya,zaki aure ni"?   daƙyar ta iya buɗe baki tace"Ni yanzu tashi zanyi in tafi,dama zuwa nayi fa don in tambayeka,wani kalar ƙunshi kake so ayimun baƙi ko ja,"    ya lura cewa batason zancen auren shiyasa ta kawo maganar ƙunshin,cikin sanyin murya yace"Nafison jan lalle zai fi yi maki kyau,kuma ba mai yawa ba ƙunshin,ƴar flower kawai za'a zana maki mai kyau,"   Yana kai ƙarshen maganar,hosana ta miƙe tana faman shan ƙamshi,da sauri ta juya ta bar bedroom ɗin nashi,bin bayanta yayi da kallo har ta fuce,jiki asanyaye ya miƙe tare da nufar toilet ya shige,    Hosana na fita daga cikin bedroom ɗin nashi,a falonsa ta tsaya tana faman zabga murmushi,tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,Yau ya Omar ya nuna yana sonta harma yanayi mata zancen aure,ta rasa ma wa zata fara faɗamawa,sai faman zagaye zagaye takeyi a cikin falon, Wuraren ƙarfe biyu da rabi na rana,Abusufyan ya ɗaukesu acikin motarshi kamar yadda yayi masu alƙwarin kaisu wurin saloon da kanshi,hosana da jahad suna a bayan motar duk sun ɗau wankan jallabiya sun laga mayafi,Sehrish na agaban motar kusa da driver seat inda Uncle abusufyan ke zaune yana driving ɗinsu anatse,Su jahad da hosana sae fira sukeyi tare dashi,amma ita ko uffan bata tanka masu ba,dama tunda ta shigo cikin motar Abusufyan ya lura da yanayinta, gyaran murya yayi mata hakan yasa ta ɗan dago da kanta ta kalle shi,   "Meyake damunki ne Daughter?tunda kika shigo cikin motar nan baki tanka mana ba,ga ƴan uwanki suna ta fira a tsakaninsu amma ban dake".   Muryarta asanyaye tace"Babu komai,"   "ko don saboda na hana ki kai ma Sgr abinci ne"? Yayi maganar batare daya kalleta,   Cikin sauri tace"a'a ba haka bane,kawai bana jin daɗin jikina ne,"   "Ban yarda ba daughter,saboda shi ne yasa kika shiga damuwa,"_   Shiru tayi bata ce komai ba,murmushi abusufyan yayi kafin yace"banyi hakan don na takura maki ba,face don na ɗaukaka darajarki,nasan ba zaki fahimce ni ba a yanzu amma nan gaba da kanki zakiyi mun godiya akan hakan,idan kuma hakan ya 6ata maki rai,kiyi haƙuri,'ya ƙarasa maganar adai dai lokacin da suka ƙaraso wurin Saloon ɗin,parking ɗin motar yayi jahad da hosana suka fita waje,tana ƙoƙarin buɗe motar ta fita ya ambaci sunanta"Sehrish,"juyowa tayi tare da kallon fuskar daddyn nasu tace"Na'am daddy,"   "Murmushi kawai nakeso kiyi mun kafin ki fita," fashewa tayi da dariya har fararen hakoranta suka bayyana,duk a tunaninta wani abu mai muhimmanci ne yasa ya kirata,ashe kawai don ya tambayi murmushinta ne,shima dariyar yakeyi,kafin su fita daga cikin motar atare, ************** Fitowarshi kenan daga wanka,yana cikin shirya kanshi cikin riga da wandon jeans,yaji an kwankwasa ƙopar ɗakinshi,daga muryarshi yayi tare da cewa"ƙopar a buɗe take,"yayi maganar tare da juyawa yana kallon mai shigowar,   Cike da mamaki yace"Ya HAROON!kaine!dama kana nan," Shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da ƙarasa shiga cikin bedroom ɗin nashi yana cewa"Ina nan mana junaid,kaine ka manta dani,kowa ma ya manta dani,"   "Ya haroon ba haka bane,wlh ni ban manta dakai ba,kana araina,"   ta6e baki haroon yayi alokacin da yake tsayawa agaban junaid suna fuskantar juna yace"Ka ƙara kyau da haske,hankalinka kwance baka da wata damuwa,ba kamar ni ba,kullum cikin damuwa nake,zuciyata har nauyi takeyi mun saboda halin da nake ciki amma babu wanda ya damu dani,yau ko mutuwa nayi babu wanda zai damu,sae ma farin ciki da za'ayi,"   Jin wannan maganar ta haroon yasa jikin junaid yin sanyi,wani irin tausayin shi ya kamashi,muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"pls Ya haroon dan Allah kadaina faɗin wannan maganganun,wlh bana jin daɗi,"   "Junaid ƙarya nayi ne?an damu dani acikin gidan nan ne?kowa yayi watsi dani,babu wanda ke damuwa dani,tamkar bare haka nakeyin rayuwata,hatta azmee da take ƴar aiki acikin gidan nan ta fi ni muhimmanci tunda ita ana damuwa da ita,ni kuwa fa?   Hawaye ne suka cicciko a idanun junaid,dama shi akwai tausayi,gaba ɗaya tausayin haroon ya kamashi,saboda duk abunda ya faɗi gaskiya ne,ba'a damu dashi ba,ko zancen shi ma babu maiyi acikin gidan,idan zai share wata a waje babu mai tambayar ina yaje,   "Tamkar maraya ni fa haka nake acikin gidan nan,kalli kaga yadda na koma duk na rame saboda damuwa,gaskiya ni bazan iya cigaba da rayuwa ba junaid,zan kashe kaina ne kowa ya huta," yana kai ƙarshen maganarshi ya juya da sauri zai bar ɗakin,   Da gudun gaske junaid ya rungumoshi ta baya tare da fashewa da matsanancin kuka yana cewa"Meyasa ya Haroon!pls stop saying that,banason jin kana zancen mutuwa,ko kowa bai damu dakai ba,Ni nadamu dakai,ko don saboda ni ya haroon kada ka aikata hakan,idan ka kashe kanka,nima bazan rayuwa ba,zan bi ka mu tafi tare,"   Wannan kalaman na junaid ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya su kayi ba,cire hannunshi yayi daga ruƙon da yayi ma waist dinshi,sannan ya juya suna fuskantar juna yace"Junaid dagaske ne ka damu dani?kuma bakaso in mutu"?   cikin shessheƙar kuka junaid yace"Eh ya haroon bana so pls,"   Hannu haroon yasa yana share mashi hawayenshi,kafin daga bisani ya janyo shi ajikinshi tare da rungume shi sosai ajikinshi,kamar zai mayar dashi cikin shi,saitin kunnanshi yakai bakinshi tare da cewa"I love u so much junaid,cos you're so special,in dai zan kasance tare dakai bazan ta6a shiga wani ƙunci na rayuwa ba,kallon ka kawai zai iya sanya farin ciki a cikin zuciyata,daga yanzu inason ka zama abokina junaid,saboda ka dinga ɗebe mun kewa,muna fita yawo atare,don bani da aboki,nifa kowa gudu na yake yi,bansan meyasa ba,'ya ƙarasa maganar tare da janye junaid daga jikinshi,   "Junaid!ka amince zaka zama abokina"? Jinjia kai junaid yayi tare da cewa"Eh,na amince,amma dan Allah ya haroon kadaina zancen zaka kashe kanka,banjin daɗi banso pls,"   "Shikenan na daina,daga yau kome kakeso ma zanyi,am sorry na sanyaka zubar da hawayenka,"   "Ya haroon ni zanje nayi ma Abba magana akanka,nasan abba zai fahimce ni,"   cikin sauri haroon ya ruƙo hannun shi tare da cewa"A'a junaid,just leave it,banason kowa yasan meke tsakanina dakai,kada kayi ma kowa maganata don ba lalle su fahimce ni kaman yadda kai ka fahimce ni ba,"   "Shikenan bazan faɗa ba," "Yawwa junaid ɗina,Yanzu zan barka ka ƙarasa shiryawa,"   Yana faɗin hakan ya juya tare da fucewa daga ɗakin junaid,ya koma bedroom ɗinsa,agaban dressing mirror ɗinshi ya tsaya yana ƙarewa fuskarshi kallo,   A hankali wannan mugun murmushin nashi ya soma bayyana akan fuskarshi,fashewa yayi da dariya kafin daga bisani ya ɗaure fuskarshi,kalaman junaid ya shiga tariyowa,tuni jikinshi yayi sanyi,ta wani 6angaren ji yake tamkar bazai iya ba,amma bai da wata mafita daya wuce wannan!   "Junaid kada ka damu zamu mutu atare,"ya faɗi hakan tare da komawa ya zauna daga gefen gadonshi, Bayan junaid ya kammala shiryawa,saukowa downstairs yayi har lokacin jikinshi ba kwari,haroon ba ƙaramin tausayi ya bashi ba,A main palor ya samu Abbansu tare da Momnynsu dasu Twins suna fira atsakaninsu,tunkararsu yayi fuskarshi ɗauke da murmushi,suna haɗa ido da Abbansu ya watsa mashi harara,sunnar da kai ƙasa junaid yayi da wurin Abban yaso ya fara zuwa amma wannan hararar da yayi mashi ce tasa ya fasa zuwa ya wuce wurin mommynsu,dukawa yayi tare da manna mata kiss kafin ya rungumeta,fuskarta asake tace"My romeo,"Amsa mata yayi da mommy,a lokacin daya koma wurinsu twins suna gaisawa,Jahan yace"Ina zuwa naga key ɗin mota a hannunka," "Zanbi su uncle ne," ayaan yace"Kada ka bari Mommy taji to,in ba haka ba bazata bari kabi su ba,"     "Saboda me"?ya tambaya yana kallonshi,Jahan ne ya bashi amsa da cewa"Saboda bazata barka ba,idan ta tambayeka ina zaka je,sae kace mata gidan abokinka zakaje,"duk wannan maganar da sukeyi a kunnan abbansu saboda yana kusa dasu,kallonsu kawai yakeyi,juyawa junaid ya ɗanyi tare da satar kallon mommyn,idonta na akanshi hakan ya tabbatar mashi da cewar so take taji me suke cewa,'   "Ka tafi kawai,"acewar ayaan,   harya juya zai tafi ya tuna da Abbansu,dawowa yayi tare da zuƙunnawa agabanshi yace"Abba,"ɗaure fuska abba yayi batare da ya tanka mashi ba,   "dan Allah kayi haƙuri abba in na 6ata maka rai,bazan ƙara ba,"   Ta6e baki abba yayi tare da cewa"Junaid kenan,ae ni yanzu babu ruwana dakai,kafi ƙarfi na,"_   Ashagwa6e ya kuma cewa"pls abba,kayi hakuri,ka manta da abunda ya faru jiya,bazan ƙara ba,"     "Naji,tashi ka tafi,ka kulamun da kanka,"   Murmushi junaid ya saki tare da mikewa ya manna mashi kiss a fuskarshi,sannan cikin sauri ya kama hanyar fita,   "Junaid ina zuwa"? Jin muryar Momnynsu yasa shi dakatawa da tafiyar da yake yi,    tsayawa yayi tare da juyawo ya kalleta,    "Mommy gidansu abokina zani je,"   "Kai da wa?waye zai kai ka? Nuna mata key ɗin motarshi yayi kafin yace"Ni zan kai kaina," Jinjina kai tayi tare da cewa"Okey,u can go," da sauri ya fuce daga cikin gidan,   Mayar da idanunta tayi akan abbansu tace"Dama inaso inyi magana dakai,wai meyasa kuka bar romeo yana Driving da kanshi?Also babu wani security guard dake tsaronsa,Shi kadae yake yawonshi,"   Abba yace"Allah xai tsare mana shi," Alexandra tace"Nasan da wannan,Amma wannan babban ganganci ne,koda ace kowanne daga cikinsu zaiyi yawonshi batare da security guards ba,amma bai kamata ace kamar junaid ƙaramin yaro yana yawo shi kaɗae ba,ba wani tsaro atare dashi,Especially yadda kowa ya sanya mashi ido,gaskiya ni hakan bai kwanta mun araina ba!!" shiru abbansu yayi yana nazarin maganarta,   Jahan yace"Gaskiya Abba,maganar mommy gaskiya ne,yakamata ace junaid akwai security guards dake tsaronsa duk inda zaije,musamman a wannan yanayin da muke ciki,bibiyar rayuwarmu akeyi don kawai acutar damu,junaid kuma yafi kowa ƙaranta acikinmu,yana buƙatar security,"   "Abunda nake ƙoƙarin fahimtar dashi kenan,"acewar mommnynsu,   jinjina kai Abba yayi tare da cewa"hakane,zanyi wani abu akai',    daga nan suka cigaba da tattauna a tsakaninsu, *Boss Bature* Tun bayan da Hayaam ta tura ma Aunty babba hotonsu hosana,bata samu damar duba hoton nasu ba,ko whatsapp ɗinta bata shiga ba,wayarma tana ajiye cikin bedroom ɗinta,Shirye shiryen zuwa walima kawai sukeyi,atare da hafsat suka fita saloon daga nan za'ayi masu ƙunshi,bayan nan kuma zasu biya Shopping mall,saboda siyayyar da tace zatayi ma Ƴa'ƴan uncle ɗinsu,basu suka dawo gidan ba sai wuraren karfe shida na yamma agajiye suka dawo,kowa ya wuce bedroom ɗinshi,Aunty babba na shiga ɗakinta,kai tsaye ta faɗa saman gadonta ta shiga sharar bacci,Hafsa kuwa saida ta fara yin wanka,ta canza kayan jikinta izuwa riga da skirt marasa nauyi,sannan ta fito falo ta kwashe shopping bags ɗin da suka bari a falo,takaisu ɗakinta,tana cikin dudduba kayan wayarta dake ajiye gaban mirror ta shiga ringing,hannu takai tare da ɗaukar wayar tana kallon screen ɗinta,ganin Sunan Aunty Hayaam ya bayyana akan secreen ɗin wayar,yasa ta ɗaga kiran tare da karawa a kunnanta,   "Assalamu Alaikum aunty hayaam,' Ko amsa mata sallamar batayi ba tace"Hafsat ina Aunty laila take ne?tun da sassafe na tura mata hoton bata duba ba,har nagaji da jira,"   Hafsat tace"yanzu muka dawo daga kasuwa agajiye,tana a bedroom ɗinta ina jin bacci ne ya dauketa,ko inyi mata magana ne"?   Hayaam tace"A'a,kawai idan ta tashi ki sanar da ita cewa na tura mata hoton ƴa'ƴan abusufyan ɗin,ta duba ta whatsapp ɗinta,"   Wani irin farin ciki ne ya lullu6e hafsat,muryarta na rawa tace"hoton ƴa'ƴan Abusufyan dinmu!zan sanar mata kuwa,"   Rejecting call ɗin tayi,da gudu ta fito daga bedroom ɗinta,kai tsaye ta haye upstairs ɗakin aunty babba,tura kopar ɗakin tayi tare da shigewa ciki,a kwance ta samu aunty babba saman gadonta sai sharar bacci takeyi,ga wayarta ajiye agefenta,   Cikin sanɗa takai hannu tare da ɗaukar wayar,ta danna power ɗinta ta kawo haske,ganin akwai password yasa ta ɗan bubbuga kafarta tana cewa"Kai mommy,yanzu dole sae kin tashi sannan zan samu damar ganin hoton babies ɗinmu!gaskiya ni a ƙagare nake,"   Tana cikin maganar,ta tuna da finger print ɗin dake akwai ajikin wayar,nan take zuciyarta ta bata shawarar cewar me zai hana,ta lalla6a ta hau saman gadon,ta dangwalo yatsan aunty babba,kota samu wayar ta buɗe,Good idea,ta furta hakan tare da lalla6awa ta hau saman gadon,cikin sanɗa ta ƙarasa inda aunty babbar take,hannunta ta ruƙo tare da sanya yatsan hannunta a wurin,ya rubuta mata wrong,haka ta dinga bin yatsun hannun aunty babba tana jarabawa,har sai da taci nasarar buɗe wayar,saukowa tayi daga saman gadon,ta tsaya atsaye,hannunta har kerma sukeyi wurin daddana wayar,tsoranta kar Aunty babba tafarka saboda tasan halin Mommyn nata,ta tsani wani ya ɗaukar mata wayarta,kamar mara gaskiya,    Tana shiga whatsapp ɗinta,sai ga wani security ɗin,rai a6ace tace"Mommy kamar mara gaskiya,duk tabi waya ta garƙame da security,"   Allah yaso shima finger print ne,komawa tayi tare da dangwalo yatsan aunty babba,whatsapp ɗin ya buɗe,   Kaitsaye ta shiga chat ɗinsu da Hayaam,anan taga hoton da Hayaam ta tura mata,bai buɗe ba hoton saboda data a kashe take,cikin sauri hafsat ta kunna data ɗin,nan take yashiga loading yana ƙoƙarin budewa,a hankali hoton ya soma bayyana,ƙura ido hafsat tayi tana jiran hoton ya kammala buɗewa,   Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu ji kake Daram!!Dararam!!tamkar ana buga ganga,Waro ido waje hafsat tayi agigice a matukar razane,tamkar wadda taga Zombie,hankali a matuƙar tashe tace"Kai!!!"   Hannunta har kerma yakeyi wurin yin zooming ɗin hoton nasu ta matso dashi kusa don tagani dakyau,gaba ɗaya tagama kiɗima,wata irin zufa ce  ta soma tsattsafo mata agefen fuskarta,daƙyar take iya haɗiye yawun bakinta saboda maƙoshinta daya bushe ƙamas,juyawa tayi ta kalli Aunty baba dake ta faman mutsu-mutsu alamar zata farka daga baccin da takeyi,aikuwa cikin sauri tayi deleting ɗin hoton gaba daya,sannan ta rufe wayar,tayi wurgi da ita asaman gadon,jikinta na kerma ta fuce daga dakin,gudu gudu sauri sauri haka take tattaka stairs ɗin ƙiris ya rage ma tayi tuntu6e saboda yadda jikinta ke rawa kafkaf kamar wadda sanyi ya kama,   Bedroom ɗinta ta koma,tana shiga ta aza hannu akai tana faɗin"Tashin hankali!In har dagaske ne abunda idanuna suka gane mun acikin hoton nan kenan hakan na nufin cewa HOSANA DA JAHAD Suna araye kuma suna a gidansu daddy!taya hakan ya faru?Kenan Ya Omar shine ya ɗaukesu?Ina wannan tsohon mutumin da mommy tasa ya kwashe su da nufin ya zubar dasu?Taya akai hosana da jahad suka kasance ƴa'ƴan uncle ɗinmu!?wacece ita ɗayar yarinyar mai kama dasu sak!dama su ƴan uku ne?Tabɗijancan,akwai matsala,   Komawa tayi gefen gadonta ta zauna tare da kifa hannunta asaman fuskarta,hosana da jahad suna raye,suna gidan abban mu,wayyo Allah na,ina farin ciki sosai,duk da ina tsoran abunda zai biyo baya,Ashe jinina ne su!shiyasa akace rashin sani yafi dare duhu,mun cutar dasu sosai,mun zalunce su bayin Allah,mutuwa ce kawai batazo ta daukesu ba acikin gidan nan amma sunsha wahala,sun ƙuntata,tabbas Mommy mun shiga uku,idan Abba yaji,daga ni harke ba wanda zai tsira,kwara ni hukuncina mai sauƙi ne tunda na nuna masu soyayya daga baya amma ita mommy itace silar fitar dasu daga gidan nan don azubar dasu,Wayyo Allah na!,   Yatsun hannunta sae faman kerma sukeyi,jiki na rawa ta ɗauki wayarta tare da lalubar numbar junaid ta danna mashi kira,   A lokacin junaid yana tare dasu Uncle abusufyan,dama sai daya fara kiranshi a waya ya tambayi address ɗin inda suke ya bashi,har an kammala yi masu saloon tuntuni,anyi masu ƙunshin jan lalle a hannuwansu,daga can suka wuce shoprite siyayya,bayan sun kammala siyayyar,suka biya gidan Uncle ɗin nasu wuraren 6,saboda su kwaso wasu daga cikin kayansu Jahad da hosana wanda zasuyi kwalliyar walima dasu,   A bayan motar junaid aka sanya trolley ɗin kayan nasu,sannan Sehrish da hosana suka shige motar abusufyan,jahad kuma ta shiga motar junaid,atare motocinsu suka fita daga cikin gidan,   Tunda jahad ta shiga motarshi,ya ɗaure fuskarshi,dama tun wurin siyayyar yake ta shan mur yana murtuke mata fuska,amma hakan bai hana tayi masa magana ba,duk in ta ɗauko abu sai ta gwada mashi ta tambayeshi zaiyi mata kyau,daƙyar yake amsa mata da eh,ko a'a,sai dae kawai tayi murmushi ta girgiza kai,     Kiran Hafsat na shigowa a wayarshi,yace"ki ɗauki wayar,ki amsa wayar sai ki sanyata a handsfree,"    hannu jahad tasa tare da ciro wayar daga aljihun gaban rigarshi,picking call ɗin tayi bayan ta sanyata handsfree sannan tayi Mata sallama,    Muryar hafsat ce ta karaɗe kunnansu"Junaid!kana ina ne"? Gaban jahad ne ya faɗi rass saboda jin muryar hafsat,duk da bata tabbatar da cewar ita bace,amma muryar tayi mata kama da ta sister hafsat,   "Ina akan hanyar komawa gida ne yanzu hakan,"    Hafsat tace"junaid dan Allah so nake in tambayeka,waɗannan yaran ƴa'ƴan uncle abusufyan Ƴan uku ne"?   "Of course they are triplet,"ya bata amsa a yayin da yake ƙoƙarin juya sitiyarin motar,ya karya kwana,   Hafsat tace"Ya sunan su"! Juyowa yayi ya ɗan kalli jahad da idanunta ke akan shi,kafin ya mayar da idanunshi kan driving din da yakeyi,a jere ya ambaci sunayensu"Hosana Sehrish Jahad"!hafsat na jin haka,a gigice ta kashe wayar,   "kiran ya katse,"Jahad ta faɗi tana ƙare ma wayar kallo,   "May be network ne,idan na koma gidan zan kirata,"    "In mayar maka da wayar"?   "A'a ki ruƙe a wurinki,idan mun isa gida zan kar6a,"   ta amsa mashi da toh, Gallery ɗinshi ta shiga tana kallon kyawawan hotunanshi da yayi,tare da videos,yawanci duk na ban dariya ne,wasu yana a kwance,wasu ya zullo harshe waje,wasu hotunan ya kashe idanunshi,   Dariya ta dinga yi a yayin da take kallon videos ɗinshi na tiktok,duk yana sauraron sautin dariyarta,wani lokacin har satar kallon fuskarta yakeyi,ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,musamman inta tuntsire da dariya,wani sa'in hada kifa kanta saman laps dinta saboda tsabar dariya,murmushi kawai yayi tare da mayar da hankalinshi akan driving ɗin da yake yi,a haka har suka ƙarasa gida, Bayan hafsat ta katse kiran,ta Kifa kanta asaman pillow ɗinta,tare da fashewa da wani irin matsanancin kuka,dama ance dana sani ƙeya ce, Farkawa Aunty babba tayi da wata irin matsiyaciyar yunwa,sae faman hamma takeyi,tashi tayi daga zaune tare da kai hannu ta ɗauki wayarta tana cewa"Ko hayam ta tura mun da hoton?bari na duba na gani,Allah yasa dai bata manta ba,"   shiga cikin whatsapp ɗinta tayi tare da duba chat ɗinsu da hayaam,rai a6ace taja dogon tsoki tare da cewa"Wai dama bata turamun hoton ba!harfa ƙara nanata mata nayi akan ta tura mun hoton amma bata turo ba," ta ƙarasa maganar tare da yin wurgi da wayar saman gadon,   Saukowa tayi daga saman gadon,fita tayi daga cikin bedroom din ta sauko ƙasa,kai tsaye ta nufi kitchen,   Batare da 6ata lokaci ba,ta shiga harhaɗa kayan da zatayi amfani dasu,bayan ta ɗaura girkin,ta ɗebo snacks a plate ta haɗo da coke mai sanyi ta dawo falo,ta zauna,tana ci tana kallo a plasma hankalinta kwance, jin motsin mutun a gefenta yasa tayi firgit tare da juyawa don taga wanene,ashe hafsat ce atsaye yanayinta kamar na wadda tayi amai da zawo,fuskar nan tayi gwanin ban tausayi,idanunta sun ƙankance saboda kukan da tasha,   "Hafsat!lafiya naga fuskarki tayi jawur?kinyi kuka ne"?   Girgiza kai hafsat tayi tare da cewa"Babu komai mommy,wani film nake kallo acikin wayata,shine ya sanya ni kuka,"   Tsoki Aunty babba taja"shirmen banza,kawai daga kallon film saiki kama kuka kamar wata sakarya,"   murmushin takaici hafsat tayi tare da samun wuri daga gefen aunty babba ta zauna,batare da tace komai ba,    Aunty babba taci gaba da cewa"gaskiya kowane film ne wannan ya ciri tuta tunda har ya iya sanyaki zubar da hawayenki,yadda kike da shegen taurin kai,     "Mommy ba zaki gane bane," "Taya za'ae in gane?tunda bakiyi mun bayanin meya faru ,acikin film ɗin ba,ki ɗan bani labari mana,"   Gyara zama hafsat tayi kafin ta soma bata labarin kamar haka"wata matace fa,mijinta ya kawo mata wasu marayun yara donta rainesu a wurinta,tun ranar da mijin ya kawosu gidan shi kuma yayi tafiya,ae kuwa matar nan,ta shiga gana masu azaba,ta hanasu abinci yunwa kamar zata kashesu,har bugunsu takeyi,sannan kuma ta dinga sanyasu aikin wahala,har saida suka kusa rasa rayuwarsu,mommy kinsan meya faru"?   Dakatawa Aunty babba tayi daga shan lemun hannunta da takeyi tace"a'a saikin faɗa,"   "Hmmm,Mommy ƙarshe fa matar nan,tasa aka kwashe yaran nan,aka 6atar dasu saboda kawai kar asirinta ya tonu a wurin mijinta...'   "Hakan da tayi yayi mun dai dai,"Acewar aunty babba, Murmushi hafsa tayi kamin tace"Ae ban ƙarasa maki labarin film ɗin ba,bayan tasa an zubar da yaran nan,ita duk a tunaninta sun mutu ma,Ashe can wurin gararin rayuwar da sukeyi a daji Allah ya haɗasu da kanin mijinta har ya taimakesu ya kaisu gidansu mijin,da akayi bincike aka gano cewar yaran ƴa'ƴan kawunsu ne wato ƙanin mahaifinsu,"   Aunty babba tace"tashin hankali!ita ko wannan ya zatayi da kanta?   Dariya hafsat tayi tare da cewa"Nima abunda nake tunani kenan!amma Mommy idan kece ya zakiyi,"   shiru Aunty babba tayi tana tunani kafin daga bisani tace"Ae kawai tunkan asirina ya tonu zan gudu ne,a neme ni arasa,amma nikam hafsat wai ya sunan Film ɗin nan ne?tayi tambayar tare da kallon hafsat ɗin wadda itama kallonta takeyi,mikewa hafsat tayi tsaye tare da cewa"An fara kiran sallar magriba,bari naje nayi salla,"   "Amma baki faɗamun sunan film ɗin ba!"Aunty babba ce ta sake nanata mata tambayar da tayi mata,     *AN YANKA TA TASHI* shine sunan film ɗin mommy,yanzu na kalleshi a tashar youtube,tana kai ƙarshen maganarta,ta juya da sauri ta wuce bedroom ɗinta,   Zugudum Aunty babba tayi tana maimaita sunan film ɗin da hafsat ta faɗa mata,wato An yanka ta tashi,   Aranta tace"gaskiya ya kamata in kalli film ɗin nan,Inaso inga yadda matar nan zata ƙare,ko ya mijinta zaiyi da ita?tabɗijancan,akwai badaƙala,"tayi maganar tare da mikewa ta wuce kitchen domin ta duba girkin da ta ɗaura, Bayan ta kuma fitowa daga kitchen ɗin,upstairs ta wuce bedroom ɗinta,gefen gadon ta zauna tare da miƙa hannunta ajikin drawer chest ta janyo gidan farko,sabon sim ne ta ɗauko tare da daukar wayarta dake ajiye saman gadon,zura sim card ɗin tayi aciki,sannan ta lalubo lambar wayar Ammi wadda tayi copying kan phone,danna mata kira tayi,nan take kiran ya shiga,kusan sau uku kiran na katsewa batare da anyi picking ɗinsa ba,tana kira a karo na hutu Ammi ta ɗaga kiran 😳 ɗan zaro ido Aunty babba tayi kafin ta gyara natsuwarta tare da zabga sallama"Assalamu Alaikum Ammi barka da warhaka,"ta maƙe muryarta yadda ammi bazata iya gane muryar wacece ba,   on the other hand Ammi ta amsa mata da cewa"Wa'alaikumus salam,barkanki dai,zan iya sanin dawa nake magana"a dake take magana, Aunty babba tace"Nasan bakisan dawa kike magana ba,saboda baki sanni ba,Ni matar abokin Abusufyan ce,wadda ke zaune a ƙasar turkey,"   Shiru ammi tayi tana sauraran me magana,   Aunty babba taci gaba da cewa"akwai wani mummunan abu da abusufyan ya aikata a 6oye baison kowa ya sani,shiyasa na kira don in sanar dake,don banason abunda zai ta6a mutuncin family ɗinku,wannan abun kunya ne,muddin ya fita waje mutane sukaji to fa,zaku rasa duk wata ƙima da martaba da kuke da ita....'   tana cikin magana Ammi ta dakatar da ita"Ya isa haka!banason wata kwanana,ki faɗamun abunda kikeson sanar dani!me Abusufyan ya aikata?wani laifi ne wannan da har kike ikirarin zai ta6a ƙimar family ɗinmu a idon jama'a,"?   Wani irin wahalallen yawu aunty babba ta haɗiye kafin daƙyar ta soma kora mata jawabi kamar haka    "Shekarun baya da dadewa,Abusufyan yayi ma wata fyaɗe,harta samu ciki....."   Wata irin tsawa da Ammi ta daka mata har sae da takusa sakin fitsari a wando,a tsiwace tace"Dakata!ki iya bakinki!kinaso ki shiga tsakanina da ɗana ne!wacece ke,kada kiyi tunanin kin kirani da 6oyayyiyar number,zan iya sa agano munke duk inda kike,"   Muryar Aunty babba na kerma tashiga faɗin"wlh dagaske nake ammi ba ƙarya nake ba,gobe idan kinzo abuja wurin walima,zaki ga yaran,ae suna nan gidan Abba,Sun jima suna 6oye maki gaskiya,saboda tsoron hukuncin da zaki yanke ma Abusufyan,yanzu haka maganar da nake maki,sun gama shirya yi maki ƙaryar cewar yaran ba shaggu bane ta hanyar aure aka haife su bayan ba haka bane,suna nan yaran ƴan uku ne mata,sun girma sosai,' tana kai ƙarshen maganar Ammi tace"Kin gama"?   Shiru Aunty babba tayi tana faman mazurai aranta tace"Wannan tsohuwa badae taurin kai ba,bansan ya zanyi na fahimtar da ita ba,ta cika jaraba,"   tana cikin wannan zancen zucin Ammi ta katse kiran,   Wurgi Aunty babba tayi da wayarta,tare da mikewa tana cewa"Ae shikenan,nasan cewa gobe tana ganin yaran zata tuna da kalamai na,daga nan saita ɗauki hukuncin daya dace," ❤🤍❤ *Boss Bature* Zaune yake asaman Sofa mai mazaunin mutun uku,gaba ɗaya ya tattara hankalinshi akan Laptop ɗinshi da yake daddawana anatse,jikin shi na sanye da linen tank top,blue colour tabi shape din jikinsa,sick pack din nan nasa ya bayyana ajikin rigar,trouser ɗin jikinsa kuma white colour ne,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga kowani sashe na jikinsa, Shigowa Azmee tayi part ɗin nasa da sallama a bakinta,yayin da hannunta ke ruke da tray,amsa mata sallamar yayi batare daya ɗago ya kalleta ba,ƙarasawa azmee tayi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman empty table din dake a gefenshi,hannu takai tare da ciro plate ta daukko serving spoon tana ƙokarin buɗe warmer,muryarshi ta katse mata hanzarinta da cewa"ɗazu da safe meyasa kika kawomin breakfast?kuma kika gyaramun bedroom ɗina,dama kece ke gyara mun part ɗina ne"? gabanta ne taji ya faɗi rass,muryarta na kerma tace"A'a bani bace,Sehrish ce," "Meya hanata yi mun aiki,"?yana magana yana danna laptop dinsa har time ɗin bai ɗago da idonshi ba ya kalle ta, Azmee tace"Am...um...dama..."bata ƙarasa maganar ba,ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannunshi,cikin sauri ta shiga taitayinta, Cike da bada Umarni yace"Call her right now," Jiki na rawa azmee ta juya tare da fucewa daga part dinsa,downstairs ta saukko,babu kowa a falon duk suna a bedroom ɗinsu,wasu ma sunyi bacci, Kai tsaye ɗakinsu Sehrish taje,tsayawa tayi abakin ƙopar ɗakin tana kwankwasawa,sai faman knocking takeyi amma ba'a buɗe mata kopar ba,da alama sun jima da yin bacci, Har sae da ta fidda rai da za'a buɗe mata kopar,tana kokarin juyawa tabar wurin,taji alamun za'a buɗe kopar,Jahad ce ta buɗe ɗakin tana tambayar wanene, Ganin azmee yasa tayi saurin gaishe da ita cikin girmamawa, Azmee da nan take ta gane ba sehrish bace tace"kiyi hakuri na tashe ki kina bacci,Sehrish nake nema,dan Allah ki sanar da ita cewa SGR yana nemanta a part ɗinsa," Jahad tace"tayi bacci,bari na tashe ta,"tayi maganar tare da juyawa cikin sauri ta shiga cikin ɗakin, Wucewa azmee tayi ta koma kitchen,cike da zullumin mai zai biyo ba idan Sehrish ta sanar ma Sgr cewa Uncle abusufyan ne ya hanata yin aiki a part ɗinsa,tabbas za'a kwashi ƴan kwallo, "Sehrish!ki tashi babban yaya yana son ganinki a part ɗinsa,dan Allah ki tashi kije,"jahad ce keta kokarin tashinta daga bacci,sehrish kuwa sai faman mutsu mutsu takeyi,daƙyar ta iya cewa"Wanene ke nema ne'? Jahad tace"babban yaya," Jin sunanshi yasa Sehrish buɗe idanunta ta wurgasu kan jahad dake tsaye,yatsina fuska tayi tare da maimaita sunan nashi"babban yaya?shike nema na,waya faɗa maki"? "Aunty azmee,yanzun nan bata jima da tafiya ba,naga kamar ma bata acikin natsuwarta," Jin hakan yasa gaban sehrish faɗuwa rass,yunkurawa tayi tare da mikewa zaune,ta saukko da ƙafafunta ƙasa,kafin ta miƙe tsaye,saboda tsabar saurin ta fita ko Mayafi bata ɗauka ba,gashi kanta ko kallabi babu,sumar kanta ce da tasha gyara,an mayar mata da gashin mai gazar gazar ya sauko har kafaɗarta,a hankali gashin kan nata ke toho yana fitowa,har ta launin gashin anyi mata dying dinsa ya koma 2 colour,Kayan bacci ne ajikinta riga da wando sharara suke,farare masu laushin gaske,irin waɗanda kana sanyasu ajikinka,Ko baka jin bacci nan take zai zo maka, Tunkan ta ƙarasa shiga falon nashi take jin ɗar ɗar acikin zuciyarta,tun jiya rabon da ta sanyashi acikin idanunta,daƙyar ta iya yi mashi sallama tare da kutsa kai cikin falon nashi,bai amsa sallamarta ba,har ta ƙarasa inda yake,atsaye muryarta na rawa tace"Gani,"bai dago ba kuma bai tanka mata ba,sae ma cigaba da danna system ɗinshi da yake yi,lokaci bayan lokaci yakan kai hannunshi ya dauki Coffee ya kur6a,zuba mashi ido tayi tana kallon kyakkyawar fuskarshi,ba ƙaramin kewarshi tayi ba,sam batayi tunanin ma zai nemeta ba, sai da ta ƙara cewa"babban yaya gani,Aunty azmee tace kana kira na,"sannan ya soma magana anatse"yau da safe,meya hanaki zuwa part ɗina"? Shiru tayi gabanta na faɗuwa,batasan amsar da zata bashi ba,saboda tsoran abunda zai biyo baya, "Kinsan bana maimaita magana,amsarki nake jira," Runtse idanunta tayi aranta tana fadin"nashiga uku,!Allah ka kawomin ɗauki,bansan me zan faɗa masa ba,"shirun da tayi mashi ne ya fusata shi,aikuwa a zafafe ya daka mata tsawa,har sai da ta zura da gudu saboda yarda ta tsorata,kama hanyar fita tayi saboda ruɗewar da tayi,hakan yasa ya miƙe tsaye tare da bin bayanta,ruƙo hannunta yayi tare da fusgota ta dawo saitin shi,Waro ido waje tayi tare da ja da baya da baya,har suka ƙure ma bangon,runtse idonta tayi muryarta na kerma tashiga faɗin"Am so sorry babban yaya,I can explain,zan faɗa maka," A hankali ya ware blue eyes ɗinshi akan fuskarta,sumar kanta yabi da kallo,yayi mamakin ganin yadda gashin yayi tsayi cikin ƙankanin lokaci har ya kamo kafaɗarta,gyaran gashin da akayi mata ya ƙara fiddo da kyawun fuskarta,mayar da idanunshi yayi akan La66anta dake ta faman kerma duk tabi ta gigice,lokaci guda ya tsinci kanshi cikin wani irin yanayi mara misaltuwa,moving ya ƙarayi gaba ɗaya yayi mata rumfa da faffaɗan ƙirjinshi,lokacin da taji tsinin hancinshi na gogar nata,nan take gabanta ya kuma bugawa daramm,jikinta ya shiga yin kerma ta ko'ina,gaba ɗaya duk tabi ta susuce har lokacin ta gaza buɗe idanunta saboda tsabar tsoro,jin saukar hannunshi asaman ƙirjinta yasa ta yin saurin ware idanunta arazane,kai tsaye suka sauka cikin nashi,face to face,Eyes to eyes,nose to nose,mouth to mouth!!, A firgice ta janye idanunta daga kan fuskarshi ta mayar dasu akan ƙirjinta,Ashe gaban rigarta ne ta bari a buɗe ta manta bata sanya links ɗin rigar ba,Shine ya sanya hannunshi a wurin yana manne mata su,jurewa kawai takeyi amma ba ƙaramin yanayi Sgr ya jefa mata ba,musamman yadda hannunshi ke nutsewa a cikin boobs ɗinta,ba ita kaɗae ba,hatta shi kanshi daya kai hannunshi wurin saida yayi regretting,saboda wani abu daya dinga jin yana fisgarshi yadda kasan magnet,mayen karfe ba, daƙyar ya iya zame hannunshi daga saman ƙirjin nata,bayan ya kammala sanya mata links ɗin,Sannan cikin sanyin murya yace"tell me the reason why baki zo yi mun aiki da safe ba!bakisan bana son sharing a aiki na ba!? Magana yakeyi amma idanunshi sae ƙokarin lumshewa sukeyi tamkar mai jin bacci,wanda kuma ba kowa ne yajawo hakan ba face Sehrish, Cikin en ena tace"Kayi haƙuri ba laifina bane,Daddy ne ya hanani zuwa" Cike da mamaki yace"Kina nufin Uncle ne ya hanaki zuwa," Jinjina mashi kai tayi alamar eh,yayin da take ta faman haɗiyar yawu, . "just without any reason ya hanaki aiki a ƙarƙashi na"? daga mashi kai tayi alamar eh, Cije pink lips ɗinsa yayi tare da tsoma hannunshi acikin sumar kanshi yana cakuɗata,ranshi a matuƙar 6ace yace"hakan bazai ta6a yiyuwa ba,dole kiyi aiki a ƙarƙashina!ban damu da matsayinshi a wurinki ba,dole ne ayimun biyayya!!!!!!!!* *Tashin hankalin da ba'a sama shi date!* Gobe walima,suwa suka shirya zuwa💃💃💃💃 *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.   *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Ƙarasa fitowa tayi daga cikin motar,jikinta na sanye da wani jigunannan lace,anyi mata riga da zani,rigar takai har guiwarta,ta coge ɗaurin ɗankwalin nan ture kaga tsiya,tun daga kan wuyanta zuwa hannayenta,duk zinari ne,tsohuwa mai ran ƙarfe,hajiya Ammi kenan Ummu Hossein,Ummu Azeema,Ummu Abusufyan,kaka ga su junaidu da kuma sehrish,fara ce tass bafullatanar asali doguwa kuma siririya,tsufanta bai hanata yin gayu ba,tsohuwar soja ce wadda tasha gwagwarmaya,kuma itace mace ta farko a lokacinsu data fara ruƙe muƙamin Major General,kaifi ɗaya ce ita,mace mai wuyar sha'ani,mutum mai tsananin haƙuri ne kawai zai iya jurar zama da ita,hannunta ɗaya na ruke da sandar karfe ta alfarma,yayin da ɗayan kuma yake ruƙe da sigari,tana tafiya tana busa ta,har ta hanci hayaƙin ke fitowa, Babu wanda yayi tunanin cewar zatazo da wuri,bata sanarma kowa ƙarfe nawa zata zo ba,duk sunyi tunanin sae wuraren marece zata ƙaraso,Atare da MG Osman da Captain Adam suka zo,sae Hajiya Sarah ƴar wurin yayanta Modibbo,tare da ya'yanta mata su biyu Yasmeen da noor,dukkansu ba zasu wuce shekara ashirin da biyu ba,tunda matasan gidan sukaji zuwan ammi nan fa kowa yasha jinin jikinshi don sun san zuwanta bai cika zama alkhairi ba,duk in tazo sai wani abu ya faru,wannan karan basu san dame tazo ba,gaba ɗayansu sun hallara a main palour ɗin suna jiran ƙarasowarta ciki,mutun ɗaya ne bai fito wurin tarbarta ba,bakowa bane face Abusufyan,tun da yaji zuwanta ya kasa samun sukuni,sae faman safa da marwa yakeyi acikin bedroom ɗinshi,jikinshi nata kerma ba don komai ba sai don zullumin abunda zai biyo baya,idan tayi arba da triplet ɗinshi,duk da yayi ma kanshi alƙawarin cewar,koda ace ta koresu to tabbas ƙafarsu ƙafarshi,bazai ƙara barin rayuwarsu ta wulaƙanta ba,duk inda zasu je zai kasance atare dasu, hayamm kuwa tana la6e jikin window tana leƙen Ammi,tun fitowarta daga mota,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta saboda tana sa ran cewar tuggun da suka shirya,zaiyi aiki, Lokacin da suka shiga falon,nan fa kowa ya shiga miƙa gaisuwa,abun da zai baka mamaki,ko amsawa wannan batayi kamar mai fama da ciwon baki,sai dae ta ɗaga masu hannu,Azmee ce ta kaisu ɗakunan da aka gyara masu,domin su sauke gajiyar da suka kwaso,kafin zuwa anjima,kowa sai da ya kara zuwa gaishe ta ɗaya bayan ɗaya har ɗakin data sauka,mutun uku ne kawai basuje gaishe ta ba,Sgr,Abusufyan sae junaid wanda bai kaiga fitowa ba daga bedroom ɗinshi, Mg Osman kuwa a nan falon suka zauna tare da Marshal Omar,suna gaggaisawa,saboda anjima ba'a haɗu ba sunyi kewar junansu sosai, Hayaam tana ƙoƙarin zuge glass ɗin windon da take leƙe sai ga Motar Abbas tayi parking cikin gidan,tsayawa tayi tana jiran ganin su wanene kuma suka ƙara zuwa,kodai Aunty laila ce ta ƙaraso ne,bata ƙarasa zancen zucin nata ba,Abbas ya fito daga cikin motar,daga bisani kuma Amani da Amal suka fito atare daga cikin motar, Ƙura ido Hayaam tayi tana ƙare ma Amal kallo,cike da mamakin wacece wannan Kyakkyawar yarinyar da Amani tazo da ita,A iya saninta dae Amani bata ta6a haihuwa ba,balle harta haifi ƴa kamar wannan,duk yadda taso ta gane wacece yarinyar nan amma hakan ya gagara,kwakwalwarta a toshe take,saboda tsabar mugunta irin tasu tun Amal na ƙarama suka canza mata kamanni saboda uƙubar da take sha a hannunsa,dole hayamm ta kasa gane wacece ita, "Hayam!"muryar Azmee ce ta karaɗe kunnanta,da sauri ta rufe glass ɗin windown tare da juyowa tana kallon Azmee,shigowarta kenan ɗakin jikinta na Sanye da jallabiya baƙa,anyi mata kwalliyar zanen flower blue,veil ɗin data yafa ma blue ne,ba ƙaramin kyau azmee tayi ba,ta wanku sosai,   Ƙarasawa hayaam tayi wurinta tana faɗin"Aunty Azmee sae yanzu za'a tuna dani?yunwa kamar zata kashe ni,kowa yana rayuwarshi acikin gidan nan sai ni duk a ƙuntace,"   "Ke kika so ki ƙuntata kanki hayam,Sgr yanzu haka ya manta da cewar ya koreki daga gidan nan,zai iya yiwuwa ma ya manta dake gaba ɗaya,kuma kinga yau ranar Walima ne mutane duk sunzo,ba dole bane ya ankara dake ba,bama haka ba mutumin da kafin ya ɗaga ido ya kalli wani aiki ne a wurinsa,don haka ina baki shawarar ki daina kullan kanki,"    Tun kan azmee ta ƙarasa maganar hayaam ta soma washe baki,la66anta har rawa sukeyi wurin cewa"An..aunty Azmee kina nufin sgr ya manta da laifin da nayi mashi kuma zan iya fita inyi yawo na acikin gidan nan kamar kowa,'   Jinjina kai azmee tayi tare da cewa"Of course,amma fa hayaam koda gigin wasa kada ki kuskura ki ƙara yunƙurin zuwa sashen shi!duk yawon da zakiyi ki tsaya a downstairs babu ruwanki da abunda ya shafi upstairs ina fata kin gane"? yatsina fuska tayi tana fadin"dama ni Aunty azmee me zai kai ni,waccen karan ma tsautsayi ne da ƙaddara," "Sannan kuma,kada ki kuskura ki ƙara shiga shirgin Sehrish!kinsan dai yanzu tafi ƙarfinki nesa ba kusa ba,ƴar masu gida ce ita,kuma shalelen daddynsu,ga kuma yayyanta maza muddin kikace zaki ta6ata wlh zaki ta6o ma kanki ne,akanta sae abaki Red card na barin gidan nan,"   ta6e baki hayaam tayi,tana faman hura hanci,maganar ba ƙaramin ƙona mata rai tayi ba,don bata da yadda zatayi ne,   Murmushi azmee tasaki tare da juyawa ta kama hanyar fita tana faɗin"Yakamata kiyi wanka,ki shirya saiki fito ayi shagalin dake,"   Cikin sauri ta ruƙo rigar Azmee tace"Aunty Azmee don Allah ki taimakamun wlh yunwa nake ji,tun jiya da daddare rabona da Abinci,"   "Its Okey,zan kawo maki yanzu," Komawa ciki hayaam tayi tana jiran azmee ta kawo mata abinci taci,kafin tayi wanka ta kimtsa, bayan su Amani sun shigo cikin main palour ɗin,anan suka zauna suna gaisawa dasu kanal yousouf,kafin tabar wurin tare da Amal,wurin Azmee taje suka gaisa tayi masu kwatancen ɗakin Hajiya Azeema da kuma na gwaggo,duk saida tabisu ta gaishe su,hatta ɗakin Abusufyan saida suka je,sukayi mashi Allah sanya Alkhairi,daga nan suka dawo kitchen,lokacin Azmee tana haɗa ma Hayaam lunch ɗin da zata kai mata,     Juyowa tayi jin sallamarsu tace"har kun dawo"? Amani tace"Eh,duk naje nayi masu Allah sanya alkhairi,yanzu abunda ya rage mun inason zuwa wurin dasu yaran suke,bansan a wani ɗaki suke ba,' Azmee tace"Ae suna nan ɗakin da Sehrish take,ae kinsan ɗakinta wanda ke a kusa da namu,yakamata kuje wurinsu,'   Murmushi Amani ta saki aranta tace"ba dole inje ba,ni da nakeson na gyara tsakanina da Sehrish,"   A fili kuma tace"okey,nagane ɗakin bari muje wurinsu,"    Juyawa sukayi atare da Amal suka nufi ɗakinsu sehrish,abakin ƙopar ɗakin suka tsaya,Amani ta kwankwasa ƙopar,jahad ce ta buɗe kopar,ba ƙaramin kyau tayi ba,wankan swiss lace ne ajikinta wanda aka haɗa da bazin shadda,stones work ne ajikin kayan wanda ya ƙara fito da ɗinkin sosai,   Murmushi Amani ta sakar mata tare da cewa"Sehrish ce ko"?ta tambaya ne saboda Abbas ya sanar da ita cewar kamanninsu ɗaya sak,   Martanin murmushin jahad ta mayar mata kafin tace"A'a,ba ita bace,tana ciki in kira maki ita ne,"ta ƙarasa maganar tana kallon Amal wadda itama jahad ɗin take ta kallo,    Amani tace"bari mu shiga daga ciki,sai mu gaisa,"   Matsa mata hanya jahad tayi suka shiga cikin ɗakin,    A lokacin Sehrish na kwance saman gadon ta ɗan kishingiɗa,tana hutawa,saboda ba ƙaramin gajiya tayi ba,sun sha zurga zurga,gashi Anjima za'a fara walimar bayan Sallar la'asar,shiyasa ta dawo ɗaki don ta huta,kafin lokaci yayi,ganin Amani yasa ta miƙewa daga zaune tana kallonsu,   Wuri Amani ta samu daga gefen gadon ta zauna,Amal ma ta zauna,tun kafin ma Amanin tace wani abu sehrish tace"Sannunku da zuwa,"hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Amani ba,tayi tunanin zata ga akasin haka ne,   "Yawwa,fatan mun same ku cikin koshin lafiya"? Sehrish tace"Lafiya lou Alhmdllh," Amani tace"kin gane ni ko"?murmushi kawai sehrish ta saki,taya za'ae ta manta da matar da tace zata iya rasa ranta idan ta cigaba da shisshige ma matasan gidan,   "Ina fata dai baki ruƙe ni aranki ba?dan Allah ki manta da komai dana ta6a faɗa maki,komai ya wuce,yanzu zumunci ya ƙullu atsakaninmu,ko wancen karon ma da nayi maki wannan maganar,wlh bada wata manufa na faɗa maki hakan ba,"   Jinjina kai Sehrish tayi tare da cewa"babu komai,ae ya riga ya wuce,"   Ba ƙaramin daɗi Amani taji ba,juyawa tayi tare da kallon jahad dake tsaye tace"zo ki zauna mana,inaso muyi fira tare daku,"zagayawa jahad tayi ta 6angaren hannun hagu ta zauna daga gefen gadon, Amani tace"ina cikon ta ukun take ne?Abbas ya faɗamun cewa ku ƴan uku ne,"   Jahad tace"hakane,hosana ce babu,taje wurin yaya Omar ne" shiru Amani ta ɗan yi tana maimaita sunan hosana a cikin zuciyarta,kamar ta ta6a jin sunan abakin wani,"ke ya sunanki"? "Ni sunana jahad," jinjina kai amani tayi tare da cewa"Suna mai daɗi,amma nifa bansan komai ba,agame daku,sehrish kawai nasani tana aiki a gidan nan,"   Jahad tace"ae mu muna a wurin ya Omar ne,shi ya taimake mu a lokacin da muke cikin mawuyacin hali,bayan ƙaddara ta rabamu da ƴar uwarmu," ..A ruɗe Amani tace"Hannun Ya Omar" Jahad tace"eh,"   Cike da son jin ƙarin bayani Amani ta kuma cewa"Kun zauna a kaduna ne"?   Ita kanta jahad sai da gabanta ya faɗi jin Amani ta ambaci kaduna kai tsaye,taya akai tasan cewa sun zauna a kaduna,   Daƙyar ta iya bata amsa da cewa"Eh,mun zauna acan,daga baya ne Ya Omar ya dawo damu Abuja,gidan daddynmu,"   Tashin hankali,miƙewa amani tayi da sauri jikinta na rawa tace"Ga Amal nan ƙanwata ce,in ba damuwa ta zauna a wurinku,"   Amsa mata sukayi da toh,cikin sauri ta fuce daga ɗakin,kallon juna jahad da Sehrish suka yi atare,duk sun lura da yadda Amani ta ruɗe,    "Wacece wannan Sehrish"?jahad ce tayi mata tambayar,sehrish tace"matar yaya Abbas ce,Aunty Amani,"   Taso ta ƙara tambayarta,amma saboda Amal dake zaune a wurin yasa tayi shiru,tabbas ta so taga kamannin Aunty babba kaɗan a fuskar Amani,duk da Amani tafi kyau sosai,kuma ita bata da jiki irin na Aunty Babba,miƙewa jahad tayi tare da cewa"Zan fita yanzu zan dawo," Sehrish tace"adawo lafiya," Bayan jahad ta fita,Sehrish ta kalli Amal dake zaune,rashin sabo yasa ta kame kanta wuri guda,   Murmushi tasakar mata tare da cewa"ki saki jikinki mana,naga duk kin gaza samun natsuwa,ko dan bamu ta6a haɗuwa bane?"   Sunnar da kai Amal tayi tana murmushi,wata irin kunyace da ita,daƙyar ta iya cewa"banta6a zuwa nan ba,yau nafara zuwa,bazan iya sakin jikina ba,tunda bansan kowa anan ba,"   Sehrish tace"Ae kuwa yanzun nan zansa ki saba dani,da farko dai ki dinga kirana da Aunty Sehrish,saboda ina kallon ƙaramar fuskar nan taki nasan cewa na girme ki,tsawo ne kawai gare ki,amma a shekaru ba zaki wuce sha huɗu ba,ko nayi ƙarya"? dariya Amal tayi tana girgixa kai tace"A'a bakiyi ƙarya ba,shekarata sha huɗu amma na kusa kai shekara goma sha biyar,nan bada jimawa ba,"   "Kice zamu zo yanka cake ko"?acewar sehrish,   Amal tace"Eh,zan gayyace ku idan lokacin yayi,"   Sehrish tace"Nima na kusa cika shekara sha takwas,banma sani ba ko na kai shekara sha takwas ko ban kai ba,nifa banma son ranar da aka jefo ni duniya ba,ni dai kawai na ganni ina yawo na ne....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda dariyar da Amal ta kwashe da ita,abu kamar wasa sai gashi cikin lokaci ƙankani sun saba da juna,nan suka zauna suna ta fira atsakaninsu, Amani kuwa tun bayan da ta fita daga ɗakinsu sehrish,tarasa inda zata tsoma kanta,abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,Aunty babba ta sanar da ita cewar tasa an zubar da yaran da Omar ya kawo mata,kuma tace mata ƴan biyu ne yaran,hakan na nufin cewar jahad ne da hosana a wurinshi?kamar yadda jahad ta sanar da ita cewa su A wurin yaya Omar suke,indae dagaske hakane to taya akai Yaran suka dawo wajen Marshal Omar bayan tasa an zubar dasu!?kodai Omar ya sanya ɗan leƙen asiri ne acikin gidan?tabbas hakan zai iya faruwa,indai kuwa hakane Watan cin uban Aunty laila ya tsaya,Zuwa maiduguri ba fashi,   Acewar Amani wadda ke ta faman yin safa da Marwa a tsakanin corridor ɗin ɗakunansu sehrish,daga bisani tace"Allah yaso ni ban tsoma hannu na ba,a wurin cutar dasu ba,ashe da rabon aure na yayi lasting,Aunty babba kam ta shiga uku,taja ma kanta bala'e,kwara ma da hakan ya faru,da nayi niyyar ɗaukar ma Amal fansa,amma yanzu na fasa,zan zuba idone kawai inga yadda dramar nan zata kaya,"ta ƙarasa zancen zucin nata,fuskarta ɗauke da murmushi,ba komai take hangowa ba face yadda rayuwar Aunty babba zata ƙare,........' Bayan fitar jahad,kitchen ta wuce ta shirya lunch acikin tray,kamar ita zata ci,upstairs ta wuce dashi,adai dai ƙopar ɗakin junaid ta tsaya tare da sanya hannunta ɗaya,ta ɗan bubbuga ƙopar ɗakin,wata murya taji daga cikin ɗakin ta amsa mata da cewa"Wanene"?muryar kuma bata junaid bace,   "Ni ce," ta bashi amsa ataikace "Kece wa"? "Jahad,"shiru taji anyi mata kafin,harta fidda rai da za'a buɗe mata,tana ƙoƙarin barin wurin taji alamun ana buɗe ƙopar,tsayawa tayi har ya kammala bude kopar,ganin fuskar wani daban bata junaid ba yasa tasha jinin jikinta,musamman yadda taga fuskar mutumin a murtuke babu fara'a ko misƙala zarratin, "Wa kike nema"? Muryarta na rawa tace"Wurin junaid nazo,naga ban ganshi ba duk yau," "Shine kika zo kawo mashi abinci?yace maki yana jin yunwa ne"?shiru jahad tayi masa batace komai ba,da alama dae wannan ba ƙaramin masifaffe bane, "Wuce ki shiga,"ya faɗi hakan tare da matsa mata hanya ta wuce ciki,shi kuma ya fuce daga ɗakin, jikinta sai kerma yakeyi saboda tsoran mutumin da tayi arba dashi,hakanan taji tsanarshi aranta,kuma sam baiyi mata kama da mutanen kirki ba, Lokacin da ta ƙarasa shiga ɗakin a kwance ta samu junaid,daga shi sai farar shirt da short fari a jikinshi,ya kwantar da kanshi asaman pillow,idanunshi na arufe,ajiye mashi tray ɗin tayi asaman front table ɗin gadon nasa,sannan ta samu wuri daga gefen gadon ta zauna tare da ambaton sunanshi"junaid," A hankali ya buɗe idanunshi tare da azasu akan fuskar jahad,yanayin shi ya nuna tamkar baijin daɗin jikinshi,idanunshi kansu sun marairaice, Bai tanka mata ba sae da ya gama ƙare mata kallo sosai,saboda ya tantance wacece acikinsu,tashi yayi daga zaune sannan yace"Jahad ko"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh,sannan ta ƙara da cewa"duk yau ban ganka ba,shiyasa nace bari nazo na duba ka,hada abinci ma nazo maka dashi,duk da bansan ko kana jin yunwa ba," "Thanks for your caring,duk yau babu wanda ya damu dani,sai ke kawai,naji daɗi sosai,"yayi maganar tare da sauko da ƙafafunshi ƙasa,hannu yakai zai ɗauki jug,ta riga shi ɗaukar jug ɗin tare da cewa"bari na zuba maka,"dakatawa yayi ta tsiyaya mashi lemu mai sanyi acikin cup,sannan ta miƙa mashi,yasa hannu ya kar6a,tare da kai cup ɗin saitin bakinshi yana kur6a, binshi tayi da kallo,yayi wani irin haske fari fat,kamar mara jini a jiki,hakanan ta dinga jin wani irin tausayinshi na shigarta,ga tsananin ƙaunarshi da takeyi kamar kamar me, Har ya kammala shan lemun bata sani ba,juyawar da zaiyi suka haɗa ido dashi,kawar da idonta tayi gefe guda tare da yin saurin cewa"Kamar baka lafiya ko"? "Me kika gani"? "Kawai yanayinka na gani,kamar na wanda bashi da ƙoshin lafiya," "Lafiyata ƙalou,don inajin yunwa ne shiyasa kika ganni haka,amma da zarar naci na ƙoshi,zan dawo dai dai," "Kasan kana jin yunwa amma meyasa baka tashi ka nemi abinci ba"?tayi maganar a yayin da take janyo plate ta shiga zuba mashi fried rice aciki, "Tun safe fa naketa yin bacci,ni kaina bansan ya akai nayi bacci mai tsayi ba,kuma dana tashi jikina duk ba ƙwari,shiyasa bansamu na sauko downstairs ba,saboda kasalar data baibaye ni, "Kuma baka sha wani abu ba?kamar maganin bacci"? Shiru junaid ya ɗanyi yana tunani kafin yace"a'a bansha komai ba,amma ya haroon ya kawo mun wani tea a cup wuraren ƙarfe takwas yace mun insha,kuma saida na tambayeshi maganin menene yace mun maganin ƙara kuzari ne,shine nasha,tun daga lokacin nidai ban ƙara sanin meke wakana ba,yanzu ma da kika ganni a kwance tashi na kenan,kuma shi ya tashe ni,yace mun in tashi inyi wanka in shirya,lokacin walima ya kusa," ɗagowa jahad tayi tare da kallon fuskarshi tace"Wannan mutumin daya fita yanzu shine Ya haroon"!? ɗaga mata kai yayi alamar eh, ta kuma cewa"Wanene shi?don ban ta6a ganinshi ba a gidan," Junaid yace"Shima yayan mu ne,bai cika zama gida bane shiyasa baki ta6a ganinshi ba," "Kada na cika ka da surutu,ka fara cin abincin," Maƙe hannayensa yayi tare da cewa"Hannu na ciwo yakeyi mun,"murmushi ta saki tare da kai hannu ta ɗauki cokali tana faɗin"bari na baka abaki to," ɗebowa ta dinga yi tana tura mashi abakinshi yana Ci suna fira,gwanin ban sha'awa,a haka harta samu yaci abincin sosai,sannan ya tashi ya shiga toilet wanka,zama tayi tana jiran fitowarshi saboda yace ta jira shi,su fita atare,hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,a sannu a sannu dai junaid ya fara sakewa da ita,Allah sarki *Boss Bature* Bayan Sallar la'asar,kowa ya ɗauki wani sabon wankan,Amani da kanta tayi masu Jahad makeup ita da Hosana da Sehrish,gaba ɗayansu suka sanya Swiss lace ajikinsu,wanda aka ɗinka masu shi domin su sanya a aranar walimar,riga da skirt ne ba ƙaramin kyau kayan sukayi masu ba,sun wanku iya wankuwa,yadda kasan dollar wurin kyau haka suka koma,Suna acikin ɗakin nasu Su huɗu hada Amal,in aka haɗa da Amani sun zama su biyar kenan,zama tayi tana ƙarasa gyara masu ɗaurin ɗan kwalin da tayi masu, A Can ciki kuwa Matasan gidan duk sun hallara,Azmee da Saude ne suke ta ɗawainiyar bin kowani table dake a wurin suna Jejjera abinci kala kala,daga bayane hayaam ta samu damar fitowa daƙyar,tun tana ƴan kame kame kamar mara gaskiya har dae ta fara sakewa,tashiga tayasu Azmee kai ma baƙi lemu, A hankali Motarsu Aunty Babba,ta shararo izuwa cikin gidan,a dai dai parking space,hafsat ta tsayar da motar,tare da juyawa ta kalli fuskar Mommyn nata dake ta faman jan minshari,tunda suka taho ta kama bacci acikin motar,hannu hafsat tasa tare da bubbuga kafadarta,a firgice Aunty babba ta farka tana fadin"Har mun ƙaraso ne,"   Hafsat tace"eh mana,gamu acikin gidan ma,kin barni da driving kina ta sharar bacci,' Yamutsa fuska Aunty babba tayi tare da buɗe motar tana faɗin,wlh agajiye nake,ga baccin ma bai isheni ba,kuma yunwa ma nake ji,'    Bayan motar ta tsaya tare da buɗe Boot ɗin motar,ta curo trolley ɗin kayansu,tare da saukko dashi ƙasa,    Sai da hafsat ta sanya niqabin da ta siya a hanya sannan ta buɗe motar ta fito,hannunta ruƙe da ƴar purse ɗinta,ganinta da niqabi yasa Aunty babba jan guntun tsoki tare da fadin"Yau naga ikon Allah,kamar wata Munafuka,kin nace dae yau sai kin sanya wannan baƙin abun a fuskarki,kamar wata ƴar shi'a"    "Mommy ba zaki gane bane," Tayi maganar tare da kama hanyar shiga cikin gidan,bin bayanta aunty baba tayi tana fadin"ba zaki zo ki kar6i trolley ɗin ba"   "Haba Mommy,Duk aikin driving ɗin da nayi,kuma sai na wani ɗauki trolley,ae ke yakamata ki janyoshi,tun fa da muka kamo hanya kike ta bacci,kika barni da aiki,nima agajiye nake bazan iya ɗaukar shi ba,"    "Kar Allah yasa ki ɗauka toh,"suna tafe suna magana har suka shiga cikin Main palour ɗin,Hayaam najin sallamar Aunty babba,ta wani saki ihu har saida hankalin kowa ya dawo kanta,da gudu taje ta rungumota tana faɗin"Wayyo Allah aunty laila,tun dazu nake ta baza ido inga zuwanku amma shiru,har na fara fidda rai da zuwanku ashe kuna hanya,"tayi maganar tare da raba jikinta daga na aunty babba,fuskar nan awashe Aunty babba tace"Mezai hana mu zuwa,naso na sanar maki wlh mantawa nayi,koda yake bacci fa nayi a mota,hada ƙarin haka yasa ban samu na kira ki awaya ba,'   "Gaskiya nayi kewar ku sosai,"acewar hayaam tayi maganar a yayin da take mayar da idanunta akan Hafsat dake sanye da niqabi,a ruɗe tace"Kai!wai hafsat ce sanye da niqabi,"   Hannu hafsat ta sanya tare da ɗan ɗage niqabin tace"Nice mana,gaba ɗaya hankalinki na akan mommy dayake kinfi damuwa da ita,"   Washe baki hayaam ta kuma yi tare da rungumo hafsat ajikinta tana faɗin"Sorry bangane ki bane wlh,kema ce kin sanya niqabi kamar wata mara gaskiya,"   Suna cikin magana muryar Azmee ta katse su da cewa"maraba da manyan baƙi,Yau su hajiya laila ne a gidan namu,wata sabon gani,yau za'ayi ruwa da ƙanƙara,"   Dariya sukayi gaba ɗayansu,kafin daga bisani Aunty babba tace"Ae wannan zuwan na musamman ne,Har sai kun gaji damu Allah,"tana magana hafsat na zungurinta alamar ta daina faɗin zasu jima,amma zafin ɗumi yasa ko lura batayi ba balle ta ankare,   "Ae tunda na ganku da trolley ɗin kayan nan nasan cewa zaku jima mana anan,wataƙil ma har sai an aurar da ƴa'ƴan namu tukunna,kunga sai ayi agabanku,'   Gaban aunty babba ne ya faɗi rass,a razane tace"Auren wasu ƴa'ƴa kenan"?   dariya azmee tayi tare da cewa"Ƴa'ƴanku mana na wurin Abusufyan,"   ɗaure fuska Aunty babba tayi tana fadin"haba dae,wani aure kuma ana zaman lafiya,daga ganin yaran kuma sai ki fara yi masu fatan yin aure,duka nawa suke,bana ji ance ƴan shekara sha bane,'   kafin azmee ta kuma cewa wani abu hafsat tace"Dan Allah mu shiga ciki mu zauna,wlh agajiye nake,gashi ko salla ma ba muyi ba,"  Atare suka ƙarasa shiga ciki,bayan sun kammala gaisawa da mutanen dake zaune a babban falon,daga bisani hayaam takaisu bedroom ɗinta,suna shiga ciki hafsat ta cire niqabin data sanya,tai wurgi dashi saman gadon,tashige toilet don ta ɗauro alwala,a ƙagare take da tayi arba dasu jahad,duk da tsoran karsu canza mata,musamman in suka tuna abubuwan da sukayi masu a gidansu,tana cikin toilet tajiyo muryar hayaam tana fadin"Tun jiya fa na tura maki hotunan nasu,baki gani bane,kuma har hafsat saida na kira a waya na sanar da ita don ta tunasar dake,'   Aunty babba tace"Gaskiya ni banga wani hoto ba da kika turamun a whatsapp ɗina,mu barma zancen tunda dae gani acikin gidan zan gansu da ido,batare da nasha wata wahala ba,'   Hayaam tace"Ae yanzu haka suna can cikin ɗakinsu tare da Amani...'   Cike da mamaki Aunty babba tace"Amani kuma?Ubanme ya haɗata dasu da har take shiga ɗakinsu?Oh ni yau naji ikon Allah,wannan shisshigi da kutsu irin na Amani,"   "Nima azmee ce ke sanar dani cewa tana a ɗakinsu wai tanayi masu kwalliya,ni duk bama wannan bane damuwata ba,Akwai wata kyakkyawar yarinya fara da Amani tazo da ita,na rasa gane wacece yarinyar nan,kuma fuskar yarinyar sak irinta amanin ce,"   Aunty babba tace"To fa,ko ina tasamu yarinya,zai iya yuwuwa fa daga gidan marayu Abbas ya ɗaukko masu ita don su raina,kinfa son cewa basu ta6a haihuwa ba,'    "Bari naje ciki,kada azmee taji ni shiru,ina ɗan tayata aiki ne,'acewar hayaam   Harara Aunty babba ta watsa mata tare da cewa"dama aiki na turoki kiyi acikin gidan?shiyasa naga duk kin zabge,nida zanzo inga ko'ina na jikinki ya cicciko,amma sai uban ƙasusuwan wuya,kamar wadda tayi jinya,'   Tsuke fuska hayaam tayi tana faɗin"Bakisan halin dana shiga bane,shiyasa zaki ce haka,tunfa da Sgr ya kore ni daga gidan nan,ban ƙara samun kwanciyar hankali ba,kullum ina ƙumshe acikin ɗaki saboda tsoran kar muyi arba dashi,ga ciwon yunwa dake damuna,ba don azmee ba ae da tuni na jima da sheƙawa,itafa ce take kawomun abinci har ɗakina,wani lokacin in ta manta bata kawo mun ba,sae dai fa in dare yayi kowa yayi bacci in saci hanya inje kitchen in ɗebo abinci,gaskiya nasha wahala sosai,   "Laifinki ne hayaam,kina zaman zaman lafiyarki acikin gidan nan,Amma kika toƙano masifa,kirasa wa zaki kaima hari sai Sgr,ae wlh ki godema Allah dabai kakkaryaki ba,nikaina nayi mamaki da kikace iya korarki yayi kawai,'   Tur6une fuska hayaam tayi tare da juyawa tana fadin"Ni dae mu bar maganar ae yariga da ya wuce,kuma ma ae ya yafe mun,bakiga yanzu ina yawo na hankali kwance acikin gidan ba,"   Aunty babba tace"Allah yasa dagaske ne cewar ya yafe maki ɗin,sai kiyi taka tsantsan kafin mu samu Allah ya cika mana burin mu,don wannan karon da shirina nazo,Bazan bar gidan nan ba,har sai naga an shafa fatihar aurenki,keda Sgr," Cike da farin ciki hayaam ta sanya tafin hannunta tare da rufe fuskarta tana sakin dariyar farin ciki,    "Aunty laila kina ganin hakan zai yiwu kuwa?ga Yaran nan ƴa'ƴan abusufyan,wlh ba ƙananu bane balle ace basu isa aure ba,Sun kaifa sha Takwas inaji,kuma wlh bakiga surar jikinsu ba,matane sosai,ni tunda nagansu ma duk sai naji na tsani kaina,kuma kinga su ƴan gidane za'a iya tunanin haɗasu auren Zumunci...'   Tunkan ta ƙarasa maganar aunty babba tace"Impossible!wlh bazai ta6a yiwuwa ba!Muddin ina numfashi ɗaya daga cikinsu bazata ta6a auren Sgr ba,kwara ma Omar abra saita haƙura amma Allah sgr ya Haramta agaresu na haramta masu shi,da bala'e sai ya aureki,ko anaso ko ba'aso,babu wani shege daya isa ya hana wlh,babu shi,"yadda Aunty babba ke cika baki tana magana ba ƙaramin dariya ya so yaba hafsat ba dake acikin toilet tana sauraronsu,ita batasan halin da suke ciki ba,sae faman kuri take tana cika baki,    Ita kuwa hayaam sae faman washe baki takeyi,gaba daya ta miƙa yardar ta ga Aunty babba,ae gani takeyi zata iya aikata komai don ta mallaka mata Sgr,      Bayan fitar hayaam daga ɗakin Hafsat ta fito daga cikin toilet din,idonta na akan Aunty babba data ɗan kishingiɗa asaman gadon,   "Mommy yakamata kije kiyi sallah,kinsan fa yanzu za'a hallara gaba ɗaya wurin waleemar yakamata ki hanzarta yin sallar,"    yatsina fuska tayi tare da cewa"Anya zan iya yin sallar nan kuwa,nagaji sosai,zuwa anjima dai nayi sai in haɗa da magriba duka inyi,"   girgiza kai kawai hafsat tayi batare da ta ƙara cewa komai ba,don ba yau ta saba yin haka ba,ita kanta hafsat ɗin zamanta dasu jahad ne ta fara yin sallah cikin lokacinta,   Zaune yake agefen gadonshi ya zabga uban tagumi,tun bayan da suka dawo daga sallar la'asar,yadawo ɗakinshi atakure,turo kopar ɗakin nashi Abba yayi tare da shigowa ciki,ba ƙaramin tausayi abusufyan ya bashi ba,wuri ya samu tare da zama daga gefenshi sannan yace"Bana faɗa maka cewa ka kwantar da hankalinka ba?jibi yadda duk kabi ka tukura kanka,"   ɗagowa yayi tare da kai idanunshi kan abba,muryarshi asanyaye yace"bansan ya zanyi bane,hankalina yaƙi kwanciya wlh,bansan wane hukunci Ammi zata yanke mun ba,ni tsorona kada tace bata yarda cewar da aure na samu su jahad ba,kasan halinta yaya hossein,tana da wuyar sha'ani," Abba yace"hakane,amma insha Allah zanyi iyakar bakin ƙoƙarina wurin ganin na fahimtar da ita,kaima kasan cewa bazan ta6a bari yaran nan su tozarta ba akan idon kowa,Ammi tana buƙatar hujjoji masu ƙarfi kafin ta gasgata abu,zamuyi kokari wurin ganin cewa munyi amfani da hujjojin da muke dasu a hannu wurin fahimtar da ita,abunda nakeso dakai yanzu ka saki jikinka,nasan cewa da anjima kaɗan idan ta farka daga bacci zata fito nan babban falon,so nake kazo da ƙwarin guiwarka ka gaishe da ita,kasan kun jima baku haɗu ba,kuma dama can kai mai laifi ne a wurinta,'   fuskar Abusufyan cike da damuwa yace"Hada ƙarin hakan yasa nake fargabar haɗuwa da ita,Ni kullum mai laifi ne a wurinta,ko kirana ma bata ɗagawa,tunda nabar nigeria shekara goma sha,amma mommy bata ta6a ɗaukar waya da sunan zata kira ni ba,kuma ko na kirata bata ɗagawa,ni ina ganin kamar bata so na ne,shiyasa takeyi mun haka,'    ruƙe hannunshi abba yayi acikin nashi"abunda kake tunani ba haka bane,zanma iya cewa tafi sonka fiye da kowa,kuma ta damu da kai sosai,babban laifin da kayi mata shine naƙin sanar da ita dalilin da yasa kabar Nigeria,ammi batasan komai game da tafiyarka ba,tayi kewarka sosai,don akwai lokacin da ta kirani a waya,kuka ne kawai batayi ba a lokacin,saboda ka tafi batare da saninta ba,wannan dalilin ne yasa take fushi dakai,amma yanzu ina da tabbacin cewar in har muka sanar da ita dalilin tafiyarka,zata fahimce mu,kuma zata kar6i yaran nan hannu bibbiyu,kuma zata yafe maka"   Jiki asanyaye abusufyan yace"Allah yasa,dana fi kowa farin ciki,"   Murmushi abba yayi tare da miƙewa tsaye ruke da hannun abusufyan yana cewa"Tashi muje ciki,nasan yanzu haka triplet ɗinka suna nan,sun ɗau wanka suna jiran daddynsu don suyi hoto tare dashi,"   Jin haka yasa Abusufyan sakin fara'a a fuskarshi nan take yaji damuwarshi ta ragu saboda an ambaci ƴan ukunshi,    atare da abba suka fito daga cikin ɗakin,adai dai lokacin Hajiya Azeema da gwaggon katsina da saude suma duk sun fito,kowa yasha kwalliya a fuskarshi,ga harris shima tare da Marshal Omar duk sun hallara anan falon,A jere su Sehrish suka fito su uku Ita dasu jahad hosana,sae Amal dake abayansu tare da Amani,   Ae tunda suka shigo cikin falon hankalin kowa ya dawo kansu,yadda kasan wasu taurari haka suka bayyana,kai tsaye wurin abusufyan suka nufa,haɗasu yayi su duka ya rungumesu sosai,bayan ya sakesu,suka gaishe da Abba tare dasu Marshal Omar dake tsaitsaye a wurin,Hannu abba yasa tare da jan kumatun hosana yace"Amaryar Omar,irin wannan kyau haka,"da sauri tasa hannu tare da rufe fuskarta,tana dariya,kawar da kai gefe Omar yayi yana ɗan sakin Murmushi,da zasu bashi dama da ba abunda zai hana ya rungumota don ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,matsowa kanal yousouf yayi kusa dasu yana fadin"Uncle ni wacce za'a bani acikinsu tunda ya Omar yayi kamun tashi,kada su ƙare ni in rasa,"dariya sukayi gaba dayan su,Uncle abusufyan yace"Layi zaka bi,don mutun ko da kuɗinshi saida rabonshi," Abba ya kar6e da cewa"kwarai kuwa,sae wanda ya dage da sallar dare zamu bamawa," daga bayansu suka jiyo muryar junaid yana cewa"Kamar ni kenan,duk gidan nan babu wanda yakai ni tashi yin sallar dare,"ya ƙarasa maganar tare da ruƙe qugunshi,fuskar nan ɗauke da wannan kyakkyawan murmushin nashi,yayin da idanunshi ke akan jahad, fashewa suka kumayi da dariya,kanal yousouf yace"haba junaid,cewa zakayi duk gidan nan babu wanda yakai ka,sharar bacci idan dare yayi,mutumin da daƙyar ake tashin shi sallar asuba shine yake cika baki yana faɗin yafi kowa sallar dare," bubbuga ƙafa junaid yayi cike da shagwa6a yace"Kai yaya yousouf dan Allah ka daina faɗin haka,kada kasa araina ni," "Raini kuma na yaushe junaid!agabansu fa kake bubbuga ƙafa kamar ƙaramin yaro kana shagwa6a,a haka kake cewa kar araina ka,wace mace ce zata so ta auri shagwa6a66an namiji irinka?acewar kanal yousouf, Tur6une fuska junaid yayi yana faman zumbura baki,juyawa yayi tare da kai idanunshi kan abusufyan yace"Uncle,ae dai zaka bani kyautar ɗaya ko"? Abusufyan yace"mezai hana junaid?ko sisi bana buƙata,duk wacce kakeso acikinsu,zan baka ita kyauta,basai ka biya sadaki ba," gwalo yayi ma kanal yousouf yana fadin"ae dae Uncle yace zai bani,kuma a kyauta ma," Hakan ba ƙaramin dariya ya basu ba,duk wannan rashin wayon da Junaid ke yi akan idon jahad,zubama sarautar Allah ido tayi,aranta tace wai dama haka yake?saboda ita bata ta6a ganin junaid na shagwa6a agabanta ba,hada su gwalo ɗabi'unsa kamar na yaron goye,kaɗan kika gani Cike da nishaɗi sukeyin firar tasu,adai dai lokacin General ishaq da Abbas suka shigo cikin main palour ɗin,sae faman sakin fara'a suke yi,ƙarasa shigowa sukayi kai tsaye suka nufi inda su Abba ke tsaye,gaishe da abba sukayi,kafin su jahad suka haɗa baki wurin gaisar dasu, Fuskar ishaq ɗauke da murmushi yace"Masha Allah,nama rasa abunda zance,yanzu wannan duk namu ne"?yayi maganar yana nuna su hosana,Abba ne ya bashi amsar cewa"Naku ne ishaq,halak malak Allah ya mallaka maku,gasu nan harsu uku," Abbas yace"kamar yadda Allah ya nuna mana wannan ranar da ranmu kuma da lafiyarmu,ina fata Allah ya ƙara haɗamu a ranar auransu kamar haka dae........' haɗa baki su Abba suka yi wurin cewa"Ameen,"banda abusufyan wanda ya sunnar da kanshi ƙasa yana murmushi,Sehrish da jahad kuwa duk kunya ta gama rufesu, Abba yace"ko baku son auren ne"? Shiru su kayi suna faman ƙumshe dariya, "Sun ma isa suce basa so?ga yayyansu nan duk tazurai,ae dole su bada hadin Kai asamu a rufa ma juna asiri," cike da zolaya ishaq yayi maganar,yayi matuƙar basu dariya, Adai dai lokacin Aunty babba ta shigo cikin falon ita da hafsat,😲 *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Gaba ɗaya Aunty babba idonta bai hango mata su hosana ba,kutsa kai kawai takeyi cikin falon,hafsat dai tana la6e a bayanta,cike da fargaba, Ƙarasawa sukayi wurinsu,daga bayansu Sehrish suka tsaya,hakan yasa bata samu damar ganin fuskokinsu ba,sai faman washe baki take yi,gaishe dasu Abba suka farayi,fuskar kowannansu awashe,"Ishaq shine baka sanar dani zuwansu ba,"acewar Abba,General ishaq yace"Ni kaina bansan sun karaso ba,nadaisan munyi dasu kan cewa zasu taho," Abusufyan yace"masha Allah hafsat ta girma sosai,ba don ina ganin hoton ta ba,da bazan iya gane ta ba,   Sunnar da kai ƙasa hafsat tayi tana murmushi ƙasa ƙasa,yayin da zuciyarta ke a cunkushe,   duk su hosana basu ɗauki muryarta ba,amma da zarar tayi magana sai sunji tamkar sun ta6a jin muryar matar dake magana,     "Muna taya ka murna Abusufyan,ƴa'ƴa har ƴan uku Allah ya albarkaci rayuwarsu,Alla ya.........'bata ƙarasa maganar ba sakamakon juyowar da sehrish tayi,Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu ji kake daram!!!dararam!!!yadda kasan ana buga ganga,Saboda tsabar kiɗima bata san lokacin da ta furta"Kutumar Uba...."gaba ɗaya hankalin kowa ya dawo kanta,jin ashar ɗin data buga,Hakan yasa Jahad da Hosana juyowa atare,Waro ido waje tayi hankalinta a matuƙar tashe,lokaci guda duk tabi ta gigice ta ruɗe ta rikice ta fita hayyacinta abunda batayi tsammani ba,la66anta har kerma sukeyi wurin nuna su da hannu tana ƙoƙarin tayi magana amma kermar da bakinta keyi ya hanata cewa komai,   Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin matar da ta azabtar da rayuwarsu,ta ƙuntata masu ta kusa halakasu,hosana kuwa a matuƙar tsorace ta faɗa bayan Marshal Omar ta ƙanƙame shi tana faɗin"Ya Omar,bansan ganinta,tsoranta nake ji,itace matar da ta azabtar da rayuwarmu,itace tasa aje a jefar damu cikin daji,har wannan tsohon mutumin ya kusa cutar dani,don Allah ya Omar ku kureta,azzaluma ce macuciya ce,bata tsoran Allah,bata da tausayi kuma bata da Imani, Hankalin kowa dake a wurin ya dawo kansu,gaba daya Abba dasu Abusufyan da sauran mutanen dake a wurin duk sun ruɗe sun gaza gane inda zancen nata ya dosa,Ishaq kuwa tun da yaga jikin Aunty babba na kerma,zufa na keto mata,ranshi ya bashi cewar tabbas ta aikata wani abu ne,saboda yasan halinta,muguwace kuma bata da gaskiya,Bashi ba hatta Marshal jikinshi yayi mugun sanyi,musamman da yaji hosana na fadin ta cutar da rayuwarsu nan ya fara tunanin Wasu abubuwa da yake zargi a lokacin baya,da kuma maganar da major ya ta6a sanar dashi na cewar baya son ya shiga tsakaninshi da matar Yayan shi, hannu Aunty babba ta aza akanta tana faɗin"Shikenan An yanka ta tashi,amaimakon ta mutu,nashiga ukku ni laila,Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wani tsautsayi ne da ƙaddara suka kawo ni gidan nan,' Tunda Abbansu junaid yaji hakan yasan cewa tabbas akwai wani abu daya ta6a faruwa a tsakaninsu,koma dae menene bai kamata,su tuhumeta ba agaban ƙannen mijinta,a bainar jama'a kuma,ko ba komai Matar babban yayansu ce,   "Ya Omar dan Allah,tabar wurin nan wlh bansan ganinta,kashe mu take son yi,shiyasa ta biyo mu har nan,"gaba ɗaya kukan hosana ya cika kunnuwansu,'   Wani irin wahalallan yawu Aunty babba tazo haɗiyewa,nan take ta yanke jiki a wurin ta faɗi asume,da sauri hafsat ta tsugunna tare da tallabo ta,tana jijjjigata, Gaba ɗaya duk sun kashe ma ishaq baki yama rasa abun cewa,tsananin baƙin ciki da takaici ya hanashi cewa uffan,jikinshi sae faman tsuma yake yi,burinshi kawai yaji abunda suka aikata ma yaran,da har suka tsorata da ganinsu,tabbas sai sunci Ubansu,muddin yaji wani da ba dai dai ba,don bazai yarda suja mashi tozarta ba a idon ƴan uwanshi, Aunty Azmee ce ta taimaka wurin ɗebo ruwa suka yayyafa ma Aunty babba a fuskarta,ae tana farfaɗowa kamar wata zautacciya tayi zumbur ta miƙe,ko waiwayonsu ba tayi ba,ta watsa aguje,tayi cikin gidan,Allah kaɗae yasan inda ta kutsa kanta, A fusace General ishaq zai bi bayanta,Abbansu junaid yayi saurin ruƙo hannunshi tare da cewa"kada ka bita,yakamata mubi komai a sannu,yanzu bamu kaɗai bane a wurin nan ba,akwai ƙannenka kuma akwai bare a wurin nan,"   Jinjina kanshi kawai yayi ba don ya haƙuri ba,   Batare da sanin kowa ba,hafsat ta zame jiki daga wurin,saboda wani irin mugun kallo da taga Daddynta nayi mata,bashi kaɗae ba hatta Marshal kallon tuhuma yake yi mata,hakan ne yasata ta sulale tabar wurin,sauƙinta ma basu ambaci sunanta ba,amma tasan dole sunanta ya fito aciki,kuma daddynta in ya tashi yanke hukunci hada ita zai haɗa ya yanke mawa,tabbas tayi dana sanin biye ma mahaifiyarta wurin cutar dasu hosana,gayanan sunja ma kansu,   Ruƙo hannun hosana yayi tare da janyota,ta dawo ta gabanshi,fuskarnan tayi jawur,sae faman kuka takeyi tana faɗin"ya Omar a koreta tabar gidan nan,bana son ganinta,bata da Imani,itace ta rufe mu acikin store tayi mana horon yunwa,ta dinga bugunmu da bulala,kuma ta dinga samu aiki,har gadon asibiti sai da aka kwantar dani.......' Cikin sauri Omar ya sanya tafin hannunshi ya toshe mata baki,cikin lallashi yace"its ok hosana,na fahimce ki,zansa sojoji su koreta daga gidan nan hakan yayi maki,"   ɗaga mashi kai tayi alamar eh,sannan yace"kada na sake jin kukan ki to,ya isa haka,kalli fa ki gani duk kin 6ata kwalliyarki da hawaye,"   Curo handkerchief Abusufyan yayi daga gaban aljihunsa,ya ruƙo hosana,tare da sanyashi a fuskarta yana goge mata hawayenta,"Daddy matar can bata da Imani ko kaɗan,taso ta kashe ni,dan Allah ku sakar mata karnuka su rakata bakin gate,tabar gidan nan,"   Muryar abusufyan tamkar zaiyi kuka yace"Kiyi haƙuri kinji hosanata,zansa a koreta kamar yadda kikeso,amma yanzu kiyi shiru da bakinki,ki daina magana,banason ganin hawayenki,"   "Daddy bakasan yadda nakeji bane,zuciyata tafarfasa takeyi,raɗaɗi takeyi mun kamar ana rura garwashin wuta acikinta,wlh daddy waccen matar bazata ga Manzon Allah ba,sai ta shiga wuta,' Hankali atashe Marshal ya daka mata tsawa har saida ta dawo cikin hayyacinta,fuskarshi a daure yace"kar na sake jin kince uffan a wurin nan,surutun ya isa haka!banace za'a kore ta ba,"   Saboda tsoratar da tayi da tsawar da yayi mata ne yasa ta faɗa jikin daddyn nasu ta ƙankameshi,tana faman sauke ajiyar zuciya,'   jikin kowa yayi sanyi,musamman Ishaq,bawan Allah duk yabi ya takure kansa,idanunshi sunyi jawur saboda tsabar 6acin rai,    Abba ne yayi ƙoƙari wurin dawo dasu daidai daga yanayin da suka shiga,daƙyar aka samu hosana ta zauna itama amma duk da haka tana yawan firgita wannan ya ƙara tabbatar masu da cewa ba ƙaramin Abu Aunty laila ta aikata masu ba,wuri kowa ya samu ya zauna agaban table ɗin dake a wurin wanda ke shaqe da abinci kala kala,nan fa kowa ya shiga bama cikinsa abinci,jikin Sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,saboda ta gane dalilin dayasa su jahad suka tsorata da ganin matar,wato itace matar da Omar ya kaisu gidanta,wadda ta azabtar da rayuwarsu,kamar yadda jahad ta bata labarinta,kowa ya lura da yanayin yaran,sun kasa sakewa suci abinci sosai,ƙarshe sai dae Abusufyan ya dinga binsu one by one yana sanya masu abinci abakinsu suna ci,a haka har ya samu suka ci sosai,bayan sun kammala cin abincin,Junaid ya ɗaukko Camera ɗinsa,nan fa aka shiga ɗaukar hotuna,abun gwanin burgewa,Happy family,kowa sai da ya fito Hajiya azeema,su gwaggon katsina Saude,Dr harris,hatta ƴan matan da hajiya sarah tazo dasu,sae da suka fito akayi masu hotuna,mutun uku ne kawai babu a wurin Ammi wadda kowa ke fargabar fitowarta,bayan ita sae Haroon wanda ke ƙumshe acikin ɗakinsa,Sgr kuwa baya cikin gidan,tun wuraren ƙarfe uku yabar gidan,   Anyi masu hoto tare da mahaifinsu sun sanyashi atsakiya,sae wanda akayi masu tare da Abbansu junaid tare dashi kanshi junaid ɗin,kowa saida yayi hoto tare dasu,hatta Su twins da fawan dasu irfan,kowannansu sae da yayi hoto dasu,sun sha hotuna ba ƙadan ba, Basu suka kammala ba sae wuraren sallar magrib,sannan kowa ya shige ciki domin yin alwala, Kamar jira jahad takeyi su shiga ɗaki ta rufe hosana da faɗa,tamkar zata bugeta,"Sai yanzu na tabbatar da cewar ke cikakkar zararriyace baki da hankali,meyasa ba zakiyi shiru da bakin ki ba?don me zaki tona mata asiri agaban mutane"? Fashewa da kuka hosana tayi tana faɗin"kada ki ƙara cemun zararriya,kuma naje na tona mata asirin,Ni bazan ta6a yafe mata ba wlh,kamar yadda ta cutar da rayuwarmu itama sai ta fuskanci sakamakon abunda ta aikata mana,' "Hosana,karna sake jin kin tada wannan maganar,idan ba so kike ranki ya 6aci ba,"   "Wlh saina faɗima Daddy da Abba,kuma saina faɗa ma yaya Omar,sai dai duk abunda zai faru ya faru,'   rai a6ace tayi maganar,cakumar rigarta jahad tayi,tare da yin wurgi da ita,ta faɗa saman gadon tana kuka,fitowa Sehrish tayi daga cikin toilet,ganin jahad na ƙoƙarin bugun hosana yasa tayi saurin zuwa tare da ruƙo hannunta"karki kuskura kice zaki hukunta hosana!abunda tayi dai dai ne,koda ace ita bata faɗa masu ba,to ni saina faɗa masu abunda waccan matar ta aikata maku,saboda bata da Imani,muguwace ita,muddin akace za'a cigaba da yafe ma mutane irinta to tabbas bazasu ta6a canza halinsu ba!Suna buƙatar a ladabtar dasu,a hukuntasu,idan suka aikata ba dai dai ba,Ni hakan da hosana tayi ta burgeni,!"   Shiru jahad tayi,ta wani 6angaren zancen sehrish gaskiya ne,muddin ba'a ɗauki mataki ba akanta taga an ƙyaleta to tabbas bazata ta6a canzawa ba,amma yanzu idan suka hukunta ta dole nan gaba taji shakkar ƙara yin irin kuskuren da tayi abaya,   "Kin faɗi gaskiya sehrish,ni banyi tunanin hakan ba,kuma koda nake yi ma hosana faɗa,saboda 6arin zancen da tayi ne agaban mutane,bai kamata ta yi magana akan idon kowa ba,in ma faɗin ne Ya Omar yakamata ta sanar mawa,sae su yanke mata hukuncin da suka ga ya dace da ita," Ta ƙarasa maganar tare da ɗauke idonta daga kan sehrish ta mayar dasu kan hosana dake baje saman gadon tana kuka,nan take taji bata kyauta mata ba,hawa saman gadon tayi tare da janyota jikinta,tana lallashinta,daƙyar ta samu tayi shiru,daga bisani suka tashi domin yin sallar magrib, *Aunty Babba* Tunda ta watsa a gujen nan,ɗakin hayaam ta faɗa,jikinta sae faman rawa yakeyi,zagaye tashiga yi a ɗakin tana tunanin hanyar da zata bi ta gudu daga cikin gidan tun kafin ishaq ya waiwayeta,tsoranta karya bata takardar saki,don bata shirya yin zawarci ba,hannu ta aza aka tana fadin"Nashiga uku ni laila,na jama kaina masifa da bala'e,Ina zan tsoma raina inji daɗi,"tana cikin zancen zucin nan,hafsat ta shigo ɗakin,kamar jira takeyi nan ta shiga balbaleta da faɗa ta inda take shiga bata nan take fita ba, "Don ubanki ki faɗa mun taya akai yaran nan suka rayu!nasan kinsan komai munafuka algunguma!"hafsat na ƙokarin buɗe baki,Aunty babba takai mata naushi a kumatunta,har sai da le6enta ya ɗan fashe,idonta jawur ta ɗago tare da kallon Mommyn nata idanunta cike taf da hawaye tace"Mommy!ni kika buga saboda zunubin da bani na aikata ba? A faɗace Aunty babba tace"Zanci ubanki ko ki rufe mun baki,wlh hafsat kin cuce ni!Allah ya isa tsakanina dake!ae kinsan da zaman yaran nan acikin gidan nan, shiyasa don munafunci kika sanyo nikabi uban meyasa baki sanar dani ba tuntuni don inyi takaina!Kece kika tseratar dasu daga hannun baba alamu,in ba haka ba taya akai har suka kawo kansu cikin gidan nan"!? Girgiza kai hafsat ta shiga yi yayin da idanunta ke fitar da wasu irin hawaye masu ɗumi,cikin shessheƙar kuka tace"banta6a dana sanin kasancewarki mahaifiyata ba sai yau!Kin jefani acikin masifa kin kuma zo kina neman ƙala mun sharrin cewa ni na tseratar dasu daga hannunshi,wlh Mommy bakiyi ba!duk wasu magayen ɗabi'u da halayen dana ɗauko naki ne,baki ta6a cemun nayi badai dai ba,baki bani tarbiya mai kyau ba,kullum gur6atamun tunani na kikeyi,saboda kar in dauko halayyar mahaifina,Ni banta6a ganin uwa irinki ba,Yanzu gashi nan daga ni harke wa gari ya waya?kuma inaso ki sani mommy,Ni bansan komai agame dasu hosana ba,bansan ya akai suka dawo hannun Ya Omar ba,Na faɗa maki hakan ne ba don ina jin tsoranki ba,sai don kisan cewar Bani na aikata hakan ba,Allah ne Ya Kamaki,ba yadda banyi ba don ki kyale yaran nan karki salwantar da rayuwarsu kika ki,kuma ni ce da hannuna na goge hotunan da hayaam ta tura maki a wayarki,saboda nafi son ki tako da ƙafafunki don ki gir6i abunda kika shuka......" ..saboda tsabar tsuma jikinta har kerma yakeyi,shaƙo wuyan rigar hafsat tayi da ƙarfin gaske,gadan gadan kasheta zatayi,kiciniyar kwace wa hafsat tashiga yi,suna cikin wannan halin,Amani da hayaam suka faɗo cikin ɗakin da gudun gaske sukayi kansu,daƙyar suka kwaci hafsat daga hannun Aunty babba,dafe maƙoshinta tayi tana faman yarfa hannu tana ambaton"ruwa!ruwa' Da sauri hayaam ta fita waje,sai gata ta dawo da bottle water a hannunta mai sanyi,miƙa ma Hafsat ruwan tayi,jiki na rawa ta cire marfin robar tare da yin wurgi dashi,ta kafa robar abakinta tana kwankwaɗar ruwan,hayaam ce ta zauna a wurinta,tana lallashinta, Rai amatuƙar 6ace tashiga fadin"ae da kun barni na kasheta don ubanta,wlh hafsat baƙin cikinki bazai ta6a kashe ni ba,Muguwa kawai,nafi kowa dana sanin haihuwarki,Ni ina kokwanton cewar Anya ba'a asibiti akayimun musanyarki ba," Fashewa da dariya Amani tayi tana tafa hannayenta, Nan take Aunty babba ta ɗaure fuska,tana jifarta da harara, Tsagaitawa tayi daga yin dariyar da takeyi masu sannan tace"Wannan abun daya faru nafi kowa farin cikinsa,tamkar na zuba ruwa a ƙasa na sha," "Amani baki da hankaline?kinsan me kike faɗi kuwa?wannan abun fa ya shafi kowannanmu,bai kamata ki dinga yi mana dariya ba,"Acewar Aunty babba, wurga mata harara amani tayi tare da cewa"yadai shafe ku!karki kuskura ki ƙara mentioning ɗina aciki,domin kuwa bansan anyi ba,lokacin da kuka tsara muguntarku kuka cutar dasu,kunyi shawara dani ne?Kuma ae har shawara saida na baki akan ki daina azabtar da yaran amma kika ƙi ji ke ga shugabar azzalumai,wlh baku da imani zuciyarku ta bushe,kwakwalwarku a toshe take,tamkar ana zuba maku dussa acikin kawunanku saboda ɗabi'unku sak irin na kafuran farko ne,....." Waro ido waje Aunty babba tayi tare da faɗin"Ni kike faɗama wannan maganar!" Amani tace"Kwarai kuwa dake nake,Muguwa macuciya kuma Azzaluma,zuciyarku ta ƙeƙashe Zalunci kawai kuka sa agaba,daku da uwarku Mammy,tsohuwar banza me shegen son kuɗin tsiya,wlh kunji haushin rayuwarku,shegen kwaɗayin abun duniya,ga baƙar zuciya,ga dogon burin tsiya ko tsoran mutuwa bakwayi..." Tunkan amani ta ƙarasa maganar Aunty babba ta kwashe ta da tagwayen maruka,ji kake tasss tatasss!'kafin Aunty babba ta janye hannunta daga kan kuncin Amani,itama ta daddage da iya ƙarfinta na ƙarshe ta kikkifa mata maruka a jere kusan uku ji kake fass tasss taaasss! dafe kumatu aunty babba tayi yayin da idanunta sukayi jawur,tunda take arayuwarta ba'a ta6a yi mata irin marin da Amani tayi mata ba,hasalima Amani shakkarta take ji,amma sai gashi yau ta cire yatsunta guda biyar cuf,ta kikkifa mata maruka, Koda ganin haka,sae hayaam ta miƙe tare da ɗaga hannu zata sharara ma Amani mari,aikuwa hafsat ta yunkura tare da miƙewa ta damƙo hannun hayaam tana faɗin"baki da hankaline?matar da ta iya ɗaga hannu ta mari mommy har sau uku,itace zaki mara?kina tunanin cewa zaki iya rama mata ne," dariya Amani tayi tare da cewa"ki barta inga ƙarshen rashin kunya,wlh dai dai nake da kowane shege acikin ku,Bana jin tsoranku a yanzu,tun ranar da Amal ta sanar dani komai game da ukubar da kukeyi mata tun daga ranar na ɗaura ɗamarar yin yaƙi daku," Hankali tashe hayaam da aunty babba suka kalli juna jin ta ambaci sunan Amal, Hafsat ce tace"Amal na wurinki ne"!? Jinjina kai amani tayi tare da cewa"Amal tana wurina!itace yarinyar dana zo da ita cikin gidan nan,kun so ku kashe mun ƙanwata,Amma Allah bai baku nasara akanta ba,Amal ta tako da ƙafafunta ta kawo kanta har cikin garin nan," Shiru duk sukayi suna sauraronta, "Haƙƙin Amal kaɗai ya isa ya jefa rayuwarku cikin masifa,laifin me Amal tayi maku da har kuka wulaƙantar da rayuwarta?yarinya ƴar ƙanƙanuwa amma kukayi mata taron dangi wurin azabtar da ita,saboda tsabar mugunta irin taku,ƙiri ƙiri kuka hanani ganin Amal,ku ka yi mun ƙaryar cewar Amal ta 6ace ba'a ganta ba,mugaye kawai ashe gidan makwabtanmu kuke kaita kuna rufeta,duk in nazo har in bar garin,tana can arufe kamar akuya,ko abinci ma baku bata,wai ku wasu irin mutanene?wace irin zuciya gare ku...? Kasa ƙarasa maganar Amani tayi saboda kukan daya ciyota,nan take ta fashe da wani irin matsanancin kuka,ba ita kaɗae bama hatta hafsat sai da ta zubar mata da kwalla,baƙin ciki kamar ta binne kanta,abun kunyar da mommynta ta aikata ba ƙaramin illa yayi ma zuciyarta ba, Hayaam kuwa sae faman mazurai takeyi ita da aunty babba sunyi wuƙi wuƙi,basu da abun cewa,dama ance rana dubu ta 6arawo,rana ɗaya ta me kaya, "Wlh kaɗan kuka fara gani!haƙƙin Amal da kuma haƙƙin waɗannan bayin Allahn da kuka cutar bazai ta6a barinku ku zauna lafiya ba,in har ba zaku canza waɗannan munanan ɗabi'un naku ba,mugunta da kwaɗayin abun duniya,dogon buri,rayuwar ƙarya,duk ku kadae gashi har yau Allah bai ta6a baku nasara ba,mutumin da bai ta6a sa Allah alamurransa ba taya zaiga dai dai"? Tsoki Aunty babba ta buga tare da nuna mata hanyar fita daga ɗakin tace"zo ki fuce ki bamu wuri tun kafin ranki ya 6aci a wurin nan!shashasha kawai kina tunanin cewa kalamanki zasu iya tankwarani ne?duk duniya ba ayi mutumin da zai zauna yanayi mun nasiha ba,wlh ba ayi shi ba," Girgiza kai amani tayi tare da juyawa a fusace tabar ɗakin tana faɗin"Jiki magayi," Komawa Aunty babba tayi yaraf ta zauna gefen gadon tana faman cizon yatsa,miƙewa hafsat tayi tare da fucewa daga ɗakin, Fitar ta keda wuya,Hayaam ta dawo gefen aunty babba ta zauna tana faɗin"Yanzu menene mafita"? ..fuskarta a hargitse tace"mafita ta wuce mu gudu salin alin batare da sanin kowa ba," "Saboda me zamu gudu?hakan na nufin cewa sun ci nasara akanmu kenan"? "Hayaam ba zaki gane ba,ina tsoran in sake yin arba da hosana ne,bata da hankali,zata ci gaba da tona mun asirine a bainar jama'a" "Amma Aunty laila,taya akai yaran suka zauna a wurinki har hakan ya faru?meyasa baki kashesu ba tun lokacin"? Guntun tsoki taja tare da kawar da kanta gefe cike da takaici tace"sai yanzu nake danasanin barinsu araye,meyasa ban kashesu ba tun lokacin da suke a wurina ba?wancan shashashan mutumin dana bama aikin zubar mun dasu a daji bansan ya akai yayi sakacin da har suka ku6uta daga hannunshi ba,kuma tun ranar dana bashi su nake ta jaraba kiran wayarshi akashe kullum har na gaji na daina kira,duk shi ya kwafsamin wlh,yanzu yawo acikin gidan nan ma ya haramta agareni,Allah yaso Hafsat ta siya niqabi a kasuwa,zan kar6e shine in sanya a fuskata saboda gudun kar waccen mai ta6in hankalin cikin sun ta ganni.....' Shiru suka ɗanyi na wani lokaci,zurfin tunani ta shiga yi kwatsam ta tuna da maganar nan da hajjaju ta ta6a sanar da ita kwanakin baya can da suka wuce lokacin su hosana na a gidan, "Idan kin toshe waɗannan hanyoyin,ita kuma waccen ɗayar hanyar da ta riga isa inda baki so fa ya zakiyi da ita' Jinjina kai Aunty babba tayi tare da faɗin"Allah ya isa tsakanina da hajjaju,sarai tasan komai game da rayuwar yaran nan amma taƙi sanar dani,babu yadda banyi da ita ba,amma taƙiya saboda tsabar baƙin hali irin nata,da tun farko ta sanar dani cewa ƴan ukune yaran akwai ɗaya dake aiki a gidan da tuni nasan abunyi, wannan masifar har ina"? "Amma kina ganin Ammi zata barsu ne acikin gidan nan?Jiya munyi plan ɗin cewa zaki kirata a waya ki sanar da ita cewa yaran shaggu ne,kin sanar da ita hakan," ta ƙarasa maganar tana kallon fuskar aunty babba wadda ke a hargitse,jin maganar hayaam yasa ta ɗan jinkirta,kamar me nazarin wani abu can ta ɗan washe baki tare da cewa"Hakane!Wannan ita kaɗae ce hanyar da ta rage mun,jiya na kira ammi a waya kuma na sanar da ita cewar Abusufyan ne ya ta6a yi ma wata fyaɗe harta samu ciki ta haifesu,ina da tabbacin cewar AMMI bazata barsu su zauna ba,dole ta koresu ƴan jakar uban,wlh na tsani yaran can,na tsani mahaifinsu duk shine silar komai,ya tashi yayi aure batare da sanin kowa ba,gayanan ya jefa mu acikin masifa,ni duk bama wannan ba,taya akai AMAL ta gudo daga gida tazo Abuja wurin waccen baƙar munafukar?ta ya akai Mammy da Abrah su kayi gangancin da har AMAL ta gudu daga gida ta dawo wurin Amani? Hayaam tace"Nima abunda nake tunani kenan,don ko aranar da zan bar gidan Amal na ƙunƙume aɗakinmu,zazza6i ya rufeta,Ni babban baƙin cikina ma,muna nan sake da baki,Amal na iya zuwa ta aure wani daga cikin matasan gidan,kinga ae shikenan mukuma tamu ta ƙare,maƙiyanmu za suyi ta cin nasara akan mu,'   "Insha Allah hakan ma bazata faru ba,in har ɗaya daga cikinku ke da abra bai auri ɗaya daga cikin matasan gidan ba,to sai dai ayi Ragas,Uban kowa ya rasa,itama Amal ɗin tarasa,ita kuma waccen ƴar iskar sai nayi silar mutuwan aurenta,tunda har ta iya ɗaga hannu ta kikkifamun mari,wlh saita gane kuranta,kuma wlh billahil azeemu,muddin Ishaq ya sake ni,itama sai Abbas ya sake ta,inyaso sai muyi zawarcin atare,"ta ƙarasa maganar tana faman sakin huci,tayi danasanin zuwanta gidannan!    *Boss Bature*       ❤🤍❤ turo ƙofar ɗakin da ammi ta sauka akayi,Azmee ce ta shigo hannunta ɗauke da kakkauran tea ɗin data haɗa mata,a zaune ta same ta saman darduma jikinta sanye da hijabi,yayin da hannunta ke ruƙe da cazbaha,da alama sallah ta kammala yi,   Cike da girmamawa azmee ta ƙarasa tare da zuƙunnawa ta gaishe ta,"Ina yini Ammi,ya gajiyar tafiya,"   da buɗar bakinta sae cewa tayi"Ina Abusufyan yake"? Azmee tace"sun fita sallar magrib,amma nasan yanzu suna kan hanyar dawowa gida,nan bada jimawa ba nasan zasu shigo ciki,"   Jinjina kai tayi tare da kai hannu ta ɗauki cup ɗin da azmee ta miƙa mata,abaki takai cup din ta kur6e sa kusan sau uku sannan tace"Idan sun dawo,kice su jira ni a palour gaba ɗayansu,inason ganinsu,"   Tuni Azmee tasha jinin jikinta,aranta tace"tashin hankali,'a fili kuma tayi saurin cewa"Za'a sanar masu,"sannan ta mike ta kama hanyar fita daga ɗakin,har azmee ta ruƙe handle din ƙopar zata fita,muryar Ammi ta katse mata hanzarinta da cewa"Next time idan zaki haɗamun tea,bana son sugar yayi yawa,sannan madarar tafi bornvitan yawa,da fatan za'a kiyaye,' "insha Allah za'a kiyaye,ko akwai wani abu da kike buƙata"?   "Idan ina buƙata zan sanar dake ne,basai kin tambaye ni ba,zaki iya tafiya,"   jinjina kai azmee tayi kafin ta buɗe kopar ɗakin ta fuce,babban falo ta nufa tana tafiya tana jinjina wa izza irin ta Ammi,saboda tsabar masifa,ko bornvita azmee bata zuba a tea din ba,madara kawai ta sanya mata amma saboda hali irin na ammi,da ba'a iya yi mata gwaninta,ta buga warning akan madara tafi bornvita yawa,ko ta ina taga bornvitan"?akan tea ma tayi ƙorafin anyi ba dai dai ba,inaga In taji abunda Abusufyan ya aikata batare da saninta ba,tabbas akwai matsala,rayuwarsu sehrish tana cikin garari,don wannan guyababbiyar matar bazata barsu su zauna lafiya ba,acikin gidan nan, Jin sautin muryoyinsu,yasa Azmee dawowa daga zurfin tunanin da ta shiga,dawowarsu kenan daga masallaci kowa bakin shi ɗauke da sallama suka shigo cikin Main palour din,Abba ne tare da Abusufyan sae junaid atare,bayansu kuma su Abbas ne da ishaq,Mg Osman da kuma Captain Adam,sai kanal yousouf da kuma Marshal wanda ke tare da Dr harris,a bayansu kuma akwai Fawan,twins,jabeer,irfan,khaleed dukansu dai suka shigo ciki,   ƙarasawa Azmee tayi wurinsu tanayi masu sannu da dawowa,daga bisani ta isar masu da saƙon ammi,nan fa kowa ya shiga fargabar dalilin tarasu da Ammi tace ayi,musamman Abusufyan yafi kowa shiga damuwa,tsayawa su kayi a tsaye kowa yana ta zullumin fitowarta,Abba dae sai ƙarfafa ma abusufyan gwiwa yake,akan ya jure,kada tsoro ya hanashi yi ma Ammi bayanin komai yadda zata fahimta, Jin takun takalminta kwas kwas!yasa su yin saurin kai idanunsu akanta,fuskarta na manne da farin glass,kwata kwata babu annuri a fuskarta,yayin da hannunta ke ruƙe da sandar nan ta alfarma,Ƙarasowa tayi tare da samun wuri ta zauna saman 3 seater,sannan ta aza ƙafarta ɗaya bisa ɗaya,tare da kallonsu tace"Ku zauna,"   A ƙasa su fawan suka zauna,yayin da Abbansu junaid,da abusufyan suka zauna asaman ɗayar 3 seater ɗin,ishaq da abbas suka zauna asaman 2 seater,Dr harris da Omar suka zauna a ɗayar 2 seater,dama 2 set ne na sofa a babban falon,manyan ne suka zauna saman kujerun,yayin da ƙananan daga kan Kanal yousouf suka zauna aƙasa, Tsit falon yayi na wani lokaci,kai kace mutuwa ce ta gifta,ko motsin mutun bakaji a wurin,kowa ya kame kanshi,   ɗaya bayan ɗaya Ammi ta dinga binsu da kallo,kowa sae faman noƙe kai yake,shi dai abusufyan ya gaza sakewa,don ko idonshi bai ɗago ya kalle taba,   ɗaga sandar hannunta tayi tare da nuna Ayan tace"wannan dogon gashin fa?sai kace wani ɗan daudu meyasa baka aske shi ba? cikin sauri Ayan yace"ƙuraje ne ke fitomun akaina duk in nayi yunƙurin aske gashin"   Ta6e la66anta tayi,kafin ta janye idonta daga kan Ayaan ta mayar dasu kan fawan,sunnar da kai ƙasa yayi yana ƴan kame kame,   "Ƴa'ƴan fatima kenan,ba zaku ta6a canzawa ba,yadda kasan sun haɗa jinsi da ibliss,ji bi ɗan iskan askin dake akanshi,hada kala ma ka canza mashi kaiga ƙeƙasasshe ko"?   Fawan akeyi ma faɗan Amma Abbansu ne ke jin maganar har cikin zuciyarshi,bakomai ya ɗan 6ata mashi rai ba,sai kalmar data faɗi na cewar kamar sun haɗa jinsi da iblis,abun ya tsaya mashi arai,jurewa kawai yakeyi,   ɗaya bayan ɗaya haka ta dinga sharrance su,har sai da tazo kan junaid wanda keta faman sakin murmushi kamar wani zautacce,   "Iko sai Allah!kai zonan,"da sandar hannunta tayi mashi nuni da yazo,miƙewa junaid yayi ya koma ƙasan kujerar da take ya zauna,hannu tasa tare da jan kunnanshi tace"Bakasan nazo bane?kowa na zuwa ya gaishe ni,amma banda kai,Abbanku ya sangarta ka ko?shiyasa ka fara jin kanka wani shege,"dafe hannunta yayi yana dariya yace"Ammi dan Allah ki sakarmin kunne na,Da zafi fa,Abba kana gani ko,"?   "Me Abban naku zai iya yimun bakasan cewa ni na tsugunna na haifesa ba,"   Zumbura mata baki junaid yayi tare da murguɗa mata baki,   "Fiye da haka ma zaka iya yimun tunda ubanka ya ɗaure maka mazauni,dole ka murguɗamun baki,ae bazan bar gidan nan ba,sae nasa an tura ka aikin soja,sannan hankalina zai kwanta,"   Bubbuga ƙafa junaid ya shigayi yana yi mata ƙunƙuni,hakan ba ƙaramin dariya yaso ya bata ba,amma bata bayyana hakan akan fuskarta ba,"   Shiru ta ɗanyi na wani lokacin kafin tace"kai irfan,tashi ka kiramun gwaggonku,tare da Auntynku Azeema inason ganinsu,"cikin sauri irfan ya miƙe tare da barin wurin ya wuce ɗakinsu gwaggo,   Bada jimawa ba,sae gashi ya dawo tare da gwaggo da hajiya azeema abayan shi,duk wannan surutun na gwaggon katsina,yau tsit kake jin bakinta,sae faman wurga ido take,wuri suka samu suka zauna,a saman sofas ɗin dake cin mutun ɗaya,   Bayan kowannansu ya natsu,Ammi ta tsayar da idanunta akan Abusufyan,wanda tunda suka zauna a falon,bai ɗago ya kalleta ba,   gyaran murya ta ɗan yi tare da ambaton sunanshi"Abusufyan"a firgice ya ɗago yana kallonta,bawan Allah harya fara haɗa gumi,ga yatsun hannunshi dake ta kerma,duk wasu alamu na rashin gaskiya sun bayyana a tattare dashi,Abba sai tausarshi yakeyi yana faɗin"ka kwantar da hankalinka,ka natsu dan Allah,duk kabi ka firgice,hakan ma zaisa taƙi yadda da hujjojin da zamu bata,"ƙasa ƙasa yake yi mashi maganar don karta ji shi,    ɗakyar Abusufyan ya iya amsa kiran da tayi mashi"Na'am Mommy,"   "Meyasa kabar ƙasar nan,batare da ka sanar mun ba?laifin me na aikata maka da har kake gudu na?sai kace bani na haifeka ba?bansan me ka ɗaukeni ba,'   muryarshi na rawa yace"Kiyi haƙuri Ammi,Nima bada son raina na tafi na bar ƙasar nan ba,nasan ni mai laifine a wurinki,ki yafe mun....'saukowa yayi daga saman sofa ɗin ya dawo ƙasa ya zuƙunna yana bata haƙuri,    "idan har dagaske kasan cewar kai mai laifine,meyasa da ka dawo Nigeria bakazo gida ka same ni ba,don ka nemi yafiyata ba"?    Shiru yayi yayin da idanunshi ke cike tab da kwalla,gaba ɗaya ya rasa inda zai tsoma ranshi,babbar damuwarshi shine,yadda zai fara yi mata zancensu sehrish, ..hmmmm ta furta sautin tare da mayar da idanunta kan gwaggon katsina tace"Saboda yardar da nayi dake ne yasa na ɗamƙa maki Amanarshi,don ki ladabtar mun dashi,a tunanina zaki canzamin shi,ashe bansan nayi aikin banza ba," ɗaure fuska gwaggon katsina tayi,alamar ranta ya 6aci,     "Ammi dan Allah komai ya wuce,just forget about the past,haba dan Allah,komai ya wuce mana,taya za'a zauna ana ta faman nanata abunda ya riga ya faru.,.,.."   Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,jin abunda Jahan ke cewa,yadda kasan wanda yasha giya haka ya shiga sambatu yana faman jan guntun tsoki ƙasa kasa,yunƙurawa Marshal yayi da nufin ya buge masa baki,Ammi ta dakatar dashi"basshi ya ƙarasa,ba laifinsa bane,gado yayi wurin Uwarsa,ae ni bansan yaushe ne ƴa'ƴan fatima zasu fara girmamani ba,amatsayina na wadda ta haifi ubansu,"   Rai a6ace jahan ya miƙe zai bar wurin Abbansu ya daka mashi tsawa tare da korosa yace"Koma ka zauna,Allah yasa inga ka ƙara cewa uffan a wurin nan,"   Komawa yayi gefen ayaan ya zauna yana faman hura hanci, Jinjina kai Ammi tayi tana kallonshi tace"Nan gaba fa,in ban bi asannu ba,bugu yaran nan zasu fara kaimun,To Allah ya kyauta gaba,"   Abba yace'Insha Allah hakan ma bazata ta6a faruwa ba"   Shidai abusufyan har lokacin yana zuƙunne asaman guiwowinsa,cike da zullumin me zai biyo baya,   "Uncle ka tashi ka koma ka zauna,jikinka sai kerma yakeyi,Ammi fa ba abunda zata iyayi maka,"Sakin baki abbansu yayi yana kallon junaid dake magana,yana ƙoƙarin kashe wutar da jahan ke ƙoƙarin kunnawa shi kuma zai hura wata wutar,   Girgiza kai Ammi tayi tare da wurga ma Abbansu harara tace"Bazan iya zama agidan nan ba,yaranka sunfi ƙarfina,"sunnar da kai ƙasa abba yayi kafin ya ɗago yana kallon junaid da yayi maganar ya ɗan jefa mashi harara,   Suna cikin wannan Zaman sai ga hosana ta shigo cikin falon,tana neman warin ɗan kunnanta daya faɗi,'tashin hankali,gaba ɗaya hankalin kowa ya koma kanta,abusufyan kuwa arazane ya ɗago yana kallonta,ammi duk bata lura da ita ba har sai da Hosana ta buɗe baki tayi magana"Daddy ɗan kunnena ya faɗi a falon nan ban ganshi ba,'juyawa ammi tayi tare da kai idanunta kan hosana dake tsaye tana magana,a wani slow ta sanya hannu ta zame glass ɗin dake a fuskarta,tashiga ƙare ma hosana kallo,cike da mamaki tace"Ina kuka samu matashiyar yarinya acikin gidan nan"?sunnar da kai ƙasa Abusufyan yayi yana faman zare ido zuciyarshi tamkar zata faso kirjinshi ta fito saboda razana,   Shiru kowa yayi mata aka rasa wanda zai buɗe baki ya bata amsa,   Jin sunyi banza da ita yasa ta kira hosana da hannunta"Zo nan,"   Shiga ciki hosana tayi tare da tsayawa agaban Ammi tace"Gani,"   "Wanene mahaifinki a wurin nan"tayi maganar tana nunasu da sandar hannunta, ...murmushi hosana ta saki tare da ɗaga yatsan hannunta ta nuna abusufyan sannan tace"Gashi nan,shine daddynmu,ni dasu Sehrish da Jahad," ..a wayance Ammi tace"Oh harku nawa ne a wurinshi"?   Hosana tace"Ƴan ukune mu,ko in kira maki su jahad ki gansu?" Cike da mamaki Ammi tace"kira mun su in gansu,"da gudu hosana ta nufi ɗakinsu don ta kira su jahad,    Tashin hankali, Wani irin gumi ne ya shiga fesowa daga jikin abusufyan,gaba ɗaya duk yabi ya kama kansa,jikinshi sae faman kerma yakeyi,bashi kaɗae ba hatta sauran dake a wurin zaune,kowa saida yasha jinin jikinsa,musamman Kallon da Ammi ta dinga binsu dashi ɗaya bayan ɗaya,kallon tuhuma,   Lokacin da hosana ta faɗa corridor ɗin ɗakunansu,hayaam na tsaye a wurin,tana ganinta tasha gabanta tare da cewa"daga ina kike"?   Murguɗa mata baki hosana tayi kafin tace"Ni bansan wacece keba,ki bani hanya in wuce,su jahad zan kira,wata tsohuwa ce fara tass take son ganinsu,"    Jin haka yasa hayaam ta gane cewa cewa AMMI ce ke son ganinsu,shu'umin murmushin nan nata tasaki,kafin ta matsa ma hosana hanya ta wuce,jinjina kai hayaam tayi tana faɗin"hada wani zumuɗin Ammi ta kirasu,basu son cewa watan korarsu daga gidan yayi ba,"tana ƙarasa maganar ta nufi ɗakin da Aunty babba take,tana shiga ta sanar da ita cewar ga Ammi can tasa a kira mata ƴa'ƴan Abusufyan,jiki na rawa Aunty babba ta taso,suka fito daga ɗakin domin suje yin la6e,don su ga irin korar karen da ammi zatasa ayi ma su Sehrish, Bada jimawa ba,Hosana ta fito hannunta ruƙe dana sehrish,ɗayan hannun kuma ruƙe da hannun Jahad,jikinsu na sanye da hijab don tunda su kayi sallar Magrib basu ciresu ba,hosana ce kawai ta cire hijabin jikinta,ta yafa mayafi akanta, da sallama a bakunansu suka shigo cikin falon,ya salam ae tuni Abusufyan ya zauna ƙasa dirshan yana lazimi,Abba kuwa sae faman jinjina kai yakeyi,gwaggon katsina kuwa tana ganinsu jahad ta shiga zare na mazurai don tasan cewa ƙarshe abun kanta zai ƙare ita da ta sanya mashi hannu ta ɗaure mashi mazaunai wurin yin auren batare da sanin Ammi ba,kowa dai yashiga zullumin abunda zai biyo baya,   Aunty babba kuwa suna la6e ita da hayaam sun kasa kunne suna jiran jin mai zai biyo baya,jikinsu sae faman tsuma yakeyi,   Zuba masu ido Ammi tayi tana kallonsu,one by one,ganin yadda matar ta ƙura masu ido yasa duk suka sha jinin jikinsu,daƙyar suka iya haɗa baki wurin gaishe da ita"Ina yini,"   Bata amsa masu gaisuwar tasu ba,sae nuni da tayi masu da sandar hannunta alamar su zauna,wuri suka samu agaban kujerar da su Omar ke zaune,suka zauna daga ƙasa tare da lankwashe ƙafafunsu,zaman cin tuwo,    Nuna Sehrish tayi da sandar hannunta tace"Ya sunanki"   Jiki asanyaye sehrish ta bata amsa da cewa"Sunana Sehrish,"   Ammi ta kuma cewa"wanene mahaifinki"?   wurga idanunta tayi akan Abusufyan ta nuna shi da hannu tare da cewa"Gashi nan,shine mahaifinmu"   jinjina kai Ammi tayi tare da kallon abusufyan wanda keta faman zubda gumi a fuskarsa,duk sanyin A.c din dake akwai a falon, ...hmmmm janye idanunta tayi daga kan Sehrish ta mayar dasu kan Jahad tace"Kefa ya sunanki"? "Sunana jahad," "Wanene mahaifinki acikinsu," Juyawa jahad tayi tare dakai hannu ta nuna abusufyan tace"Shine daddynmu," Rai amatukar 6ace Ammi ta daka masu tsawar da ta gigitasu gaba ɗayansu duk suka razana,a tsiwace tace"Kowa ya zuba mun ido yana kallona,ba zaku faɗamun a ina kuka samo su ba?taya akai Abusufyan ya zama ubansu!" Abba ne yayi ƙoƙarin buɗe baki yace"Ya'yanshi ne dagaske,kamar yadda suka faɗa Ammi," Aruɗe Ammi tace "Ni kake faɗama cewa ƴa'ƴanshi ne?kada ku raina mun hankali ta gidan ubanwa Abusufyan yayi aure da har zai haifi waɗannan balagaggun ƴan matan!"? Fashewa da kuka hosana tayi,sehrish da jahad kuwa tuni hawaye sun soma wanke masu fuskarsu,jikin Marshal ba ƙaramin sanyi yayi ba,haka zalika sauran dake zaune a wurin, "Abusufyan!ka faɗamun taya akai ka samu yaran nan?Na yarda cewa ƴa'ƴanka ne koda basu faɗamun da bakinsu ba,saboda ina ganinsu nasan cewa Jinina ne su,ko ba don kamanninka dake akan fuskarsu ba,So nake naji TAKUN hanyar da aka Same su!?nasan halinka tun fil azal baka rabuwa da mata,ka faɗamun gaskiya,ka ta6a yin mu'amala da wata ƴa' mace ne har ta samu cikinka"? A kiɗime abusufyan ya shiga yi mata rantsuwa yana faɗin"Wlh Ammi tunda nake arayuwata ban ta6a kusantar zina ba,Nasan cewa zaiyi wuya ki yadda dani,amma wlh saida na auri mahaifiyarsu sannan na same su,ga gwaggonan itace shaidata,"   Tamkar zata rufashi da duka haka tashiga balbaleshi da masifa"Bazan ta6a yadda da kalamanka ba,karka kuskura ka ƙara cewa ta hanyar aure ka same su,in ba haka ba saina ci maka mutunci a wurin nan!dama najima ina zarginka abusufyan,banta6a tunanin zakayi mun haka ba,ka cuce ni,bazan ta6a yafe maka ba,rashin jin maganarka har yakai ka kawo mun Shaggu acikin zuri'ata,bazan ta6a lamun ta ba......'   Rai a6ace gwaggon katsina ta katse mata hanzarinta da cewa"Ya isa haka,babu laifin abusufyan acikin wannan lamarin,Nice na aura mashi yarinyar da ta haifa mashi waɗannan ƴa'ƴan,don haka kidaina ambaton sunansu da shaggu saboda baki da hujjar yin hakan,bazan ta6a yarda a tozarta ƴa'ƴan abusufyan ɗina a gabana ba ehe," kowa yayi mamakin yadda gwaggon katsina ta mayar ma Ammi martani,tamkar wata mai cikakken hankali,   "Dan Allah Ammi ki daure ki fahimce shi,rashin sanar maki da basuyi ba,shine babban kuskuren da Abusufyan da gwaggo suka yi,Gwaggo ta aikata hakanne saboda son da takeyi ma abusufyan wannan dalilin ne yasa ta aura mashi mahaifiyarsu batare da saninki ba,saboda tasan halinki,kin tsani auren bare,gashi shi kuma abusufyan ya kwallafa rai akan yarinyar,wannan ne yasa ta aura mashi ita,saboda gudun karya faɗa halaka.....  "Wani irin kallo da Ammi ta jefa mashi ne yasa shi dakatawa da yin maganar da yake,wato Abbansu junaid,   Aunty babba dake la6e ita da hayaam suna sauraronsu,saboda tsabar farin ciki kamar su zuba ruwa a ƙasa su sha,burinsu kawai Ammi ta koresu Jahad,   Kowa saida ranshi ya 6aci a wurin nan,saboda yadda ammi ta haƙiƙance akan cewar bazata kar6i shaggu ba acikin zuri'arta,a ƙarshe tace"na riga da na yanke hukuncin korarsu daga cikin zuri'ata,banason ganinsu,kuma duk wanda yayi yunƙurin binsu acikinku wlh saina tsine mashi yabi duniya,kuma zan yafe shine acikin ƴa'ƴa Na,   Wani irin matsanancin kuka su jahad suka fashe dashi,haka abusufyan ma kuka yake yi tamkar ƙaramin yaro,ƙiri kiri za'a rabashi da ƴa'ƴanshi,su Abba kuwa gaba ɗaya jikinsu yayi mugun sanyi,Hankalin Omar ba ƙaramin tashi yayi ba,haka zalika sauran kowa hankalinshi yayi mugun tashi,   Su aunty babba kuwa dake la6e,jin an kori su sehrish,yasa suka daka uban tsallen farin ciki,saboda tsabar dariyar mugunta,hada hawaye,da gudu suka koma cikin ɗaki,suna faman dariya,burinsu ya cika, "Ku tashi ku fuce daga cikin gidan nan tunkafin insa ayi waje daku,"jiki asanyaye suka miƙe tsaye jahad ta ruƙo hannun sehrish da jahad acikin nata,tafiya sukeyi kamar wanda aka zarewa laka,yayin da hawaye ke gangarowa daga idanuwansu,yunƙurawa abusufyan yayi da sauri zaibi bayansu,aikuwa abba yayi hanzarin damƙo rigarshi ya janyoshi,ya dawo da shi saman sofa din,a haukace ya shiga kiciniyar kwace kanshi yana fadin"Ka barni yaya hossein wlh sai dai ta tsinemun amma bazan bari rayuwar ƴa'ƴana ta wulakanta ba,duk inda zasu je ƙafata kafarsu,"ganin abusufyan na ƙoƙarin zaucewa yasa su Marshal Omar dasu ishaq da abbas suka rurrukeshi,sai faman hargowa yakeyi,yana kokarin kwacewa don yabi bayansu sehrish, bazasu iya jurar ganin halin da mahaifinsu ke ciki ba,hakan ne yasa suka fuce waje da gudu suna kuka,tamkar ransu zai fita,sae faman shessheƙar kuka sukeyi, Suna cikin wannan yanayin Motar SGR,ta shararo da gudu cikin gidan,a tsiyace su kayi parking ɗin motar,tunkan Amstrong ya buɗe mashi motar,ya sanya kafarshi tare da harba murfin motar,ya fito daga ciki,kai tsaye ya nufi wurinsu Sehrish dake a tsaye suna kuka,kwata kwata basu lura dashi ba,sae dai suka ji an ruko hannayensu,Jahad da hosana,a firgice suka ɗago suna kallonshi,"ku wuce mu shiga ciki,"yayi maganar tare da jan hannunsu,sehrish ma tabi bayansu suka koma cikin falon,jin sallamar Sgr yasa hankalin kowa komawa kansu,ganin ya dawo dasu sehrish yasa kowa ya shiga sauke ajiyar zuciya,Zuba mashi ido Ammi tayi tana kallon ikon Allah,   ƙarasawa cikin falon yayi tare ce masu sehrish"Ku samu wuri ku zauna,"jiki asanyaye suka samu wuri ƙasa suka zauna,suna faman sauke ajiyar zuciya,   Zama sgr yayi asaman sofa,tare da aza ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya,yayin da yake fuskantar Ammi wadda ta zuba ma sarautar Allah ido,   Sai da ya mula yasha iska sannan ya soma magana    "dama saida raina ya bani cewa hakan zata iya faruwa,that's the reason why na tanadin hujja ɗaya kuma kwakkwara wadda zata wanke zargin da kikeyi akan abusufyan da kuma waɗannan triplet ɗin,"   Ƙarasa maganar yayi tare da sanya hannunshi cikin aljihun wandon jeans ɗin dake ajikinshi,ya zaro wayar shi,      *mu haɗu On monday don jin yadda zata kaya,* _har yanzu wasu basu gode mun akan long page ɗin da nake sawa,in banda ma rashin godiyar Allah irinta ɗan adam,a ƙalla yawan one page da nake sawa Yayi fiye da 3 page na wasu masu rubutan,Allah har mamaki nakeyi in naga page ɗin wasu writers din,duk read More 3 ne amma ni kaga page mai read more 9 har 12 ina sakawa,ƙaramin page ɗina shine zaka ga read more 6,zama nakeyi inyi rubutu kamar zan kashe kaina,amma wasu saboda rashin godiyar Allah suna zuwa sunayi mun complain ɗin wai adinga posting sau biyu?a iya sanina Vip ne ma ake sanya 2 page,amma ni ina sanya maku kusan 3 page a hade duk da hakan baiyi maku,idan so kuke sai in dinga raba maku shi uku,saboda na lura hakan yafi maku,kunfiso ku ganshi arabe,bakomai ne yasa ma nakeyin page masu tsayi ba face don in samu intakaita labarin saboda yana da tsayi,idan kuma aka cigaba da raina abunda nake sanyawa wlh zan mayar dashi ne read more uku in tafi dai dai da kowa👍_   *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Tofah nan fa kowa ya shiga tunanin wata hujja ce Sgr ke da ita?kanga wayar yayi a kunnansa,then Calmly ya furta"Ku ƙaraso ciki,"jin haka yasa kowa kai idanunshi kan ƙopar shigowa falon,don ganin su wanene zasu shigo ciki, Bada jimawa ba,wata haɗaɗɗiyar Wheel chair Golden Colour mai ɗauke da wani dattijo tsoho tukuf fari tass hatta sumar kanshi furfura ce fara tass babu zaren gashi ko ɗaya daya kasance launin baƙi,hatta gashin girarsa dana idonsa fari ne tass duk furfura ta mamaye ko'ina,wani matashi ne ke ruƙe da ita yana turashi a nutse,tashin hankali ae koda Ammi tayi Arba da mutumin dake a saman wheel chair ɗin nan,hankalinta gaba ɗaya ya tashi haikam,ba ita ba Hatta su Abba dasu Gwaggo da Azeema sunyi matuƙar mamakin ganinshi,saboda a iya saninsu baya qasar,a Saudi Arabia yake da zama,amma sai gashi yau Unexpected yazo,wannan wani irin zuwan bazata ne? Lokacin da matashin ya ƙaraso dashi ciki Ammi ta tabbatar da cewar dagaske dae shine,a kiɗime ta miƙe tsaye muryarta na in,ina ta ambaci sunan shi"Mo...moddibo" Wani irin kallo tsohon ya wurga mata,kallon zakiyi bayani,gwaggon katsina kuwa wani irin farin ciki ne ya lullu6e ta,saboda tasan cewa tunda Modibbo ya tako da ƙafafunsa yazo Nigeria to tabbas za'a samu maslaha,saboda duk duniyar nan babu wanda ke taka ma Ammi burki in ta burkice sai Shi!mugun shakkar shi take ji,saboda shi tamkar Ubane agareta,a hannunshi ta taso,shiyasa yasan hanyoyi da dama da zai iya tankwarata,kuma duk wasu halaye nata da ɗabi'unta nashi ne sak ta ɗaukko,amma shi da ya manyanta ya ajiye wannan jin kan,' Bayan saurayin ya tsayar da wheel chair ɗin,Modibbo ya yunƙura tare da miƙewa da sandar hannunshi,cikin sauri suka bashi wuri,ya samu wuri ya zauna a hakimce saman sofa,nan kowa ya shiga gaishe dashi suna yi mashi sannu da zuwa,fuskar nan tashi asake yake amsa masu,ba ƙaramin daɗin zuwan modibbo suka ji ba,bayan ya kammala kar6ar gaisuwarsu ɗaya bayan ɗaya,   Sannan Ammi tace"Yaya sannu da zuwa,ya gajiyar tafiya"    Fuskarshi aɗaure yace"Gajiya tabi jiki,ae ba yau nazo ba,tun shekaran jiya ina ƙasar nan,zuwa ne kawai banyi ba,kuma ba don kowa nazo ba sai don saboda ke!"   Jin haka yasa ta koma ta zauna,jiki asanyaye, Cikin sauri Abba ya kalli su fawan tare dayi masu alamar su tashi su bar wurin,"mikewa su kayi dama Jahan a ƙagare yake daya bar wurin,duk ji yake kamar ya ɗosa mazannansa akan wuta,atare suka miƙe tare da barin wurin,Ya rage daga Gwaggon katsina,Abbansu,hajiya Azeema,General ishaq,da Cg Abbas,Uncle Abusufyan,marshal Omar da Sgr,bayan su kuma sae su Jahad dake zaune ƙasa,duk sunyi zuru rayuwarsu a hannun Allah,basu san su wanene waɗannan tsoffin ba,amma sun tsorata dasu,musamman Ammi data tayar masu da Hankali,har tana ƙoƙarin korarsu daga gidan, Bayan su jahan sun shiga ciki,ya fashe da dariya hada dafe ciki yana faɗin"Dama ance GABA DA GABANTA ALJANI YA TAKA WUTA"💥 Junaid kuwa,bedroom ɗin Abbansu ya wuce,anan ya samu mommynsu tsaye agaban drawer,jikinta sanye da doguwar riga,tana ƙoƙarin sanya mayafi akanta,   Sam bata lura dashi ba,har saida ya ƙarasa bayanta tare da rungumota,hannu tasa tare da janyoshi ta dawo dashi ta gabanta,a shagwa6e ya ambaci sunanta"Mommy dama kina a ɗaki,bakisan meke faruwa ba a babban falo,"   Hannu tasa tare da shafa fuskarshi tace"Romeo,bani da alaƙa da abunda ke faruwa acan,yanzu faɗamun naga fuskarka kamar akwai damuwa,"   "Mommy,ba Ammi bace take son korar su Jahad daga gidan nan ba,"   "To menene damuwarka aciki don ta kore su"?   Sakin baki junaid yayi yana kallonta kafin ya ɗaure fuskarshi yace"Haba Mommy,ƴa'ƴan uncle ɗinmu fa ne,taya ba zan damu ba,uncle fa yana sonmu sosai,muma dole mu so ya'yanshi,kuma su jinin mu ne,nidai wlh banso ta koresu,kuma Allah koda ace ta koresu,wlh saina bisu.....'ya ƙarasa maganar yana zum6ura baki,   Hannu tasa taja kumatunsa"Ni kuma an gaya maka zan barka ne?zansa a ɗauke mun kaine,in kaika U.s mu cigaba da rayuwarmu acan,ko ba zaka bi mommynka bane,"    Bubbuga ƙafarsa yayi tare da cewa"I wanna fallow u Mom,amma Allah sai dai mu tafi mu duka tare dasu sehrish,jahad da hosana,"    "Dole dai saina je dasu"? ɗaga mata kai yayi alamar eh,janyo shi tayi ta rungumeshi ajikinta,"don't worry dear kome kakeso zanyi,indae hakan zai faranta maka rai,yanzu mu zauna ka tayani fira,inaso mu tattauna wata magana dakai mai mahimmanci,"   Komawa sukayi tare da zama daga saman gadon,suka ci gaba da tattaunawa a tsakaninsu, *Aunty Babba* Lokacin da suka faɗa cikin ɗakin suna murna ita da hayaam,tsayawa sukayi daga tsaye,suna tattaunawa,Aunty babba tace"Ae dama saida raina ya bani cewar Ammi bazata barsu su zauna a gidan nan ba!gaskiya matar nan ta burge ni wlh,yadda ta zagesu tass ta kirasu da shaggu hakan ba ƙaramin nishaɗi ya sani ba,in banda ma shashasha irin Abusufyan taya zaka kawo ƴa'ƴa daga sama kace ya'yanka ne,kuma kayi tunanin cewa kowa zai yarda dakai?Ae ni wlh tayi mun dai dai matar nan," Ta ƙarasa maganar tana faman sakin shu'umin murmushin nan nata, Hayaam tace"Nima ba ƙaramin burgeni tayi ba,naci dariya lokacin data korasu suka watsa aguje suna kuka,ƴan jakar uban,yanzu sai muga ina zasu dosa,dama su kashe kansu kawai su huta muma kuma munsamu natsuwa," cike da nishaɗi take maganar tana watsa hannu alamar ita ko ajikinta,   "Dama abunda yasa nake son Ammi ta koresu,kinga na farko zasu fita daga cikin zuri'arsu ne gaba ɗaya,babu su babu auren ɗaya daga cikin ƴa'ƴan Abba,saboda Ammi bazata bari su auri bare ba,balle kuma yaran da ta ambaci sunansu da shaggu,Secondly kuma wannan korar da tayi masu,zai hana Ishaq da Omar su tuhume ni akan tonan asirin da waccen Zararrar taso tayi mun a bainar jama'a,kinga riba biyu kenan,"   Tana kai karshen maganarta,hayaam ta ɗaura da cewar"wannan haka yake Auntyna,mu ɗin jinin nasara ne,duk abunda muka sa agaba sai munga bayanshi koma uban menene shi,"   Dariyar mugunta Aunty babba ta kuma saki kafin tace"Bazan ƙyalesu haka nan ba,saboda Omar zai iya bin bayansu don ya taimakesu,dole in samu wanda zaibi takansu da mota su mutu kawai,kowa ya huta,"   Hayaam tace"faƙat!kinga babu su a duniyarma balle ayi dasu," .......duk wannan surutan da suke yi,Amani na la6e a ƙopar ɗakinsu wadda bata idasa rufewa ba,tana recording ɗin muryoyinsu a wayarta,don taci alwashin saita tarwatsa duk wani plan nasu,Ni boss nace kinyi mun dai dai, *Boss Bature* The genius   ❤🤍❤ bari mu leƙa falo muga meke wakana,shin ansamu cigaba ko kuwa ana nan yadda ake? Natsuwa su kayi gaba ɗayansu,wurin yayi tsit tamkar mutuwa ta gifta,kowa ya natsu ya nabba'a tamkar ɗalibai ne agaban ya sayyadi,bafa sayyadi mijin abu ba,ina nufin malami,kar ayimun wata fahimta, "Waɗannan sune ƴan ukun Abusufyan ɗin"modibbo ne yayi maganar yayin da idanunshi ke akan Su jahad dake zaune sunyi zuru zuru,'   Har suna haɗa baki wurin cewa"Sune," Jinjina kai yayi tare da mayar da idanunshi kan Ammi yace"Ki kace yaran shaggu ne ko?Wata hujja gare ki na cewar bada aure ya haifesu ba?   Fuskarta aɗaure tace"Ina da hujja,saboda nice mahaifiyarshi,kuma ni bansan an ɗaura mashi aure da kowa ba,"   Girgiza kai modibbo yayi,sannan yace"hannunki ya taso ne?ko kuwa wurin ki kaɗae za'a iya ɗaura mashi aure ne"?   Shiru tayi batace masa uffan ba,cigaba da magana yayi"don haka baki da wata hujja ta cewar abusufyan yayi aure ko baiyi aure ba,ya samu ƴa'ƴa,wlh Aisha kin ban mamaki!wai har yaushe ne zaki ajiye waɗannan makaman yaƙin naki ne?ke fa yanzu ba yarinya bace,kin tara ya'ya da jikoki amma har yau bazaki ajiye wannan zafin ran naki ba,sai yaushe ne ya'yanki da kuma jikokinki zasu ji daɗin zama dake ne?yanzu ni ba misali bane agareki?ko bakisan wanene modibbo ba?kinfi kowa sanina bani da wasa ko miskala zarratin,duk wani kangararre acikinku,keda ƴan uwanki nine nan nake tankwarashi,amma yanzu saboda na manyata,na tara ya'ya da jikoki,duk na ajiye waɗannan ɗabi'un,Na canza kaina ne ba don komai ba sai don saboda ya'yana da kuma jikokina suji daɗin zama dani,kuma suyi alfahari dani amatsayina na kakansu,bawai su dinga tsoro na ba,suna gudu na harma su dinga yi mun fatan mutuwa,kamar ke ɗin nan dai.....'yayi maganar yana nuna ta da sandar hannunshi,sunnar dakai Ammi tayi tana faman jinjina kai, Canza harshe modibbo yayi izuwa harshen fulatanci,yayi hakan ne saboda kada faɗan da zaiyi mata ya zama tamkar tozarci ne agaban jikokinta,   "Gaba ɗaya kin takurawa rayuwar ya'yanki,da ta jikokinki,kin hanasu sakat,ko irin wasan dake tsakanin kaka da jikan nan bakya yi masu,kullum burinki ki ƙuntata rayuwarsu,shin menene ribarki idan kinyi hakan? Ya ɗan dakata da maganar yana kallonta,kafin yaci gaba da cewa"Yanzu jibi yaran nan ƴan wurin fatima,hakanan kika ɗaura karan tsana kika ɗaura masu sai kace ba jininki ba!in ma saboda mahaifiyarsu ne,ke kin ta6a ganin inda laifin wani ke shafar wani ne?in kuwa haka ne ae da dukkanmu mun shiga uku,saboda wancan zaiyi sata ne a ɗaura maka laifin bayan bakai ne ka aikata ba,"   Katse shi tayi cikin harshen fulatanci tace"Amma yaya modibbo ni meyasa ya'yana basu jin maganata ne?basu ɗaukeni mahaifiyarsu ba,suna yin abu gamon kansu batare da sun sanar mun ba,Hossein ya ƙetare ƙasar nan yaje yayi aure batare da sani na ba,sai dai kawai na ganshi da mata ya dawomin,matar kuma ma farar fata ba jinsun mu ba,sannan kuma Abusufyan shima yayi aure batare da sani na ba,saboda me zasuyi mun haka ne? anzo dai dai wajen,acewar modibbo gyara zama yayi sannan yace"kin manta yadda akai kika auri salahuddeen ne?to idan kin manta bari na tuna maki,dama duk wanda ya bijire ma iyayensa ko ba daɗe ko ba jima sai shima yaga ba dai dai ba,na farko bada sa hannun iyayenmu ba,kika shiga aikin Soja,babu irin yadda ba'ayi dake ba don ana ganin bai dace dake ba,ba kaman daya kasance ke bafullatana ce,amma kika ƙeƙashe ƙasa kikace sai kinyi aikin soja,a ƙarshe da aka takura maki,shine kika tattara kayan ki kika dawo gidana da zama saboda kina tunanin cewar ni zan goya maki baya don ki samu abunda kikeso,da kika zo wurina a lokacin na nuna cewar nima bazansa hannu na ba acikin lamarin tunda har iyayenmu sun nuna basu so,a ƙarshe sai kika gudu batare da sanin kowa ba,kika shiga aikin Soja,sae dai kwatsam muka ganki da kakin Soja ajikinki,ko ba haka akayi ba"? Wata irin zufa ce ta shiga wankowa a fuskar Ammi sam bata ta6a tsammanin cewa wannan ƙaramin kuskuren data aikata na bijirema iyayensu,zai dinga bibiyar rayuwarta bane, "Akan wannan aikin sojan da kika shiga,babu wanda baiyi kuka dake ba,saboda kafiya,da taurin kai irin naki,ga jinkai dake gareki,iyayenmu basu isa su baki umarni kai tsaye kiyi abu ba,sai sun biyo ta wurina saboda shakkarki da suke ji,bayan wannan kuma,baki sanar ma kowa ba game da salahuddeen lokacin da kuka fara soyayya dashi ba,sai daga baya ne muka fahimci shi ya hure maki kunne har kika bijire mana kika shiga aikin sojan,hakan kuma yasa duk muka ki amincewa da farko ki aure shi,amman da yake Allah ya kaddaro aure tsakaninku ba yadda muka iya dole muka kyale ki ko don kafewar da kika yi da kuma rabon itama Ameena anan zata samu mijin, ko ba haka akayi ba"?   Jinjina kai Ammi tashiga yi yayin da idanunta suka cicciko tab da kwalla amma bata bari sun zuba ba, Gwaggon katsina kuwa,sae faman sakin murmushi takeyi,tana faɗin"kwarai kuwa,haka akayi,"Abban su junaid kuwa da hajiya azeema duk jikinsu yayi mugun sanyi,sae yanzu suka gane daga inda matsalar take,dama duk in mutun yaga rayuwarshi tana tafiya ba dai dai ba,kuma bai akaita wani zunubi,toWlh ya binciki kanshi!ya tuhumi kanshi ahankali zai gano dalili, Su jahad dae suna nan tsugunne sun kasa kunne suna sauraronsu,sai dai subi bakin modibbo da kallo,daga bisani in Ammi na magana subi ta da kallo saboda basu iya fulatanci ba,haka Marshal Omar dasu ishaq duk basa jin fulatanci,haka zalika Sgr baya jin harshen nasu,dama shi ko hausa daƙyar ya koye ta,kuma har yau in yana magana da harshen hausa sai ka gane cewar ɗan koyo ne don sam hausarsa bata nuna ba shiyasa bai fiye yin magana da hausa zalla ba saiya haɗa da turanci ko spanish,amma kuma hausar tashi ba ƙaramin daɗi takeyi ma mutane ba,   Murmushi Modibbo ya ɗan saki kafin yaci gaba da cewa"ina fata yanzu kin tuna komai"?   Siraran hawayen da take 6oyewa ne suka gangaro a saman fuskarta,muryarta ƙasa ƙasa tace"Na tuna,"   Modibbo yace"Tunda kin tuna bari na ƙara ɗaura ki akan hanya,irin abunda kika aikata ne yasa shima ɗan cikinki da kika haifa yaje yayi aure batare da saninki ba,saboda gudun kada ya fara sanar dake ki hana shi yin auren,hossein ya auri Alala..kunzandariya...."kasa ƙarasa maganar yayi saboda bai iya ambaton sunanta ba,abun yaso yaba Sgr dariya,amma ya basar da ita tare da gyara mashi sunan yace"Alexandra ne sunan," Modibbo yace"yawwa ɗan gari,bazan dai iya Ambaton sunan nata ba,a barshi a fatima,tunda ae ta ta6a musulunta,kuma muna sa ran zata ƙara musulunta insha Allah,"   Suka ɗanyi dariya,kafin ya ɗaura da cewar"Hossein ya auri fatima batare da saninki ba,saboda yasan halinki sarai kin tsani jinsin da ba naki ba,gudun kar ya sanar dake kiƙi amince masa yasa shi yin hakan,sannan......"modibbo bai ƙarasa maganar ba,ammi ta kuma katse mashi hanzarinshi da cewa"Yaya modibbo amma ae ni harsu biyu sukayi mun haka!bayan ni,ni kaɗai ce na bijire ma iyayenmu haka,"   wannan maganar ta Ammi yasa shi yin dariya,tare da girgiza kai yace"in kikayi wata maganar kina tunamin da ƙuruciyarki wlh,dama ita irin sakayyar nan tamkar ramuwar gayya haka take,kuma ita ramuwar gayya tafi ta gayyar zafi,sakamakon abunda kika shuka ne,yasa kika girbi kyakkyawan sakamakon da ya zarta nakin,kuma tunda har kika iya ƙyale hossein bayan laifin daya aikata maki na auren bare kuma farar fata ae yaci ace kin yafe ma Abusufyan tunda shi da ƙuruciyarshi ya auri yarinyar,kuma hada sa hannun gwaggonshi,kuma kinsan wacece ita a wurinki,da mahaifinmu da nata uwa daya uba daya,kuma saboda yardar da kikayi da itane yasa kika damƙa mata amanarshi,ita kuma ƙaunar da take yi maki ne ya shafi ɗanki da kika haifa,hakan yasa ba zataso wani abu ya cutar dashi ba,Yaro ya nuna yana son ƴar mai gadin gidansu,ke kuma kin tsani auren bare mara asali,gashi shi kuma yaron ya kwallafa rai akan yarinyar,don lokacin da ita Aminatu taso ta sanar dake game da yarinyar balbaleta kikayi da masifa,kina cewa karta kuskura ta bari alaƙarsu tayi nisa,ta raba tsakaninshi da yarinyar,a ranar saida Abusufyan ya suma jin za'a raba shi da abunda yakeso,wannan dalilin ne yasa hajiya ameenatu ta aura mashi yarinyar batare da ta sanarma kowa ba,sai ni ɗinnan da nake magana,"   ɗagowa Ammi tayi tana kallonshi cike da mamaki,   Jaddada mata maganar yayi"kwarai kuwa ta sanar dani,nasan da zancen auren,kuma aranar da aka ɗaura auren Abusufyan da zainabu abu,ina ɗaya daga cikin waɗanda suka halarci ɗaurin auren batare da sanin kowa ba,ita kanta hajiya ameenatu batasan na halarci ɗaurin auren nasu ba,a iya waya kawai ta sanar dani,sae kuma akaci sa'a ina da wani taron manyan malamai da zamu halarta anan jihar kano,wannan ne babban maƙasudin daya kaini garin harna shaida wannan ɗaurin auren....." Ae tunkan modibbo yakai ƙarshen maganar wani irin murmushin farin ciki ya bayyana akan fuskar kowannansu,saboda yayi maganar ne cikin harshen da zasuji,wata irin nauyayyiyar ajiyar zuciya abusufyan ya shiga saukewa,nan take yaji wani irin sanyi ya ratsa zuciyarshi,duk da yayi mamakin zuwan modibbo wurin ɗaurin auran nashi saboda bai ganshi ba,amma tunawa da irin dubban al'ummar dake a masallacin kuma ya kasance ranar juma'a ne ana kammala salla aka ɗaura auren nasu,tabbas bazai iya tantance kowa dake a wurin ba,amma ko a lokacin bayan an ɗaura auren sun koma gida sai da baba buzu ya kirashi gefe guda yake sanar dashi cewa"Wani babban malami,yayi mashi alheri bayan sun fito daga masallaci,kuma yana tunanin cewar Kamar jininsu ne saboda yaga kamannin Hajiya ameena a fuskarshi,a lokacin Abusufyan bai gane wanene ba,sai yau da modibbo yayi maganar nan kwatsam ya zancen ya faɗo mashi aranshi bayan ya shiga zurfin tunani,tabbas kuwa modibbo ne,   Murmushi modibbo yayi tare da kallon Abusufyan yace"nasan zakayi mamaki,saboda nazo ɗaurin auren ka batare da sanin kowa ba,uzuri ne ke gare ni a lokacin shiyasa ban nemeka ba,don nasan muddin ka ganni a lokacin saika nace akan in tsaya,"   ya ƙarasa maganar tare da mayar da idanunshi kan Ammi,tun kafin ya kuma cewa wani abu,muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"Amma yaya kasan da maganar auren nashi shine ba'a sanar dani ba?saboda me?   "Saboda halinki"! Kai tsaye ya bata amsa,   "Tabbas naso in sanar dake ko alokacin,saboda kinsan cewa ni bana jin shakkarki,hajiya ameenace ta rokeni akan cewar karna sanar dake,saboda hakan zai iyasa ki fusata harma ki yanke ma Abusufyan hukunci mai tsanani,kuma a ƙarshe zumuncin dake tsakaninki da ita ya tarwatse,dana nace akan zan sanar dake har kuka saida tayi mun,wannan dalilin ne yasa ban sanar dake ba,kuma ana haka daga baya kwatsam naji labarin mutuwar auren Abusufyan ɗin,hada ƙarin haka yasa akabar zancen gaba ɗaya,ashe yarinya ta fita da cikinsa ta auri wani,to kinji dalilin dayasa mu kanmu bamu san da ya'yan nashi ba,har suka kai wannan girman a hannun mijin da ta aura daga baya,"   Dakatawa yayi da maganar,falon yayi shiru na wani lokaci,kafin ya mayar da idanunshi kan Sgr dake zaune,yace mashi"ka kunna mata audio din nan daka kunna mun itama ta saurare shi,"   "Okey,"ya amsa mashi tare da,daddana wayar hannunshi,ya shiga audio din tare da kunnashi,sannan ya miƙe tare da ƙarasawa kusa da kujerar da Ammi ke zaune ya miƙa mata wayar,yatsun hannunta na kerma tasa hannu ta kar6i wayar tashi,ta ajiye asaman hannun sofa ɗin tana sauraronshi,wannan audio din na labarin da abusufyan ya bayar ne da kuma Labarin dasu sehrish suka bayar na irin ukubar da suka sha a hannun ya sayyadi,ashe ranar da abun ya faru,Sgr ya ɗauki audio na maganganun da sukayi kaf acikin wayarshi,tabbas shi ba ƙaramin jami'in Soja bane!yana Aikinsa wani lokacin tamkar jami'in sirri,Na jinjina masa,da irin baiwar da Allah yayi mashi da kuma irin kwazon dake gare shi,ta ko ina Sgr ya haɗa,shiyasa nace maku shi ɗin komai nasa Extraodinary ne~~~ Miƙewa junaid yayi tare da ruƙo hannun Mommynsu yace"Shikenan mommy tunda mun kammala discussion din,ki taso muje falo pls,kada kice baki zuwa,in ba haka ba raina zai 6aci,wlh ko abincin dare bazanci ba,indai kika ƙi zuwa gaishe da modibbo," Cike da mamaki tace"Modibbo?kana nufin mahaifin maryam oummunsu Omar?   daga mata kai yayi alamar eh, Shiru tayi tana wani tunani,a iya saninta modibbo mutunne mai mutunci sosai,saboda shine ya taka ma Ammi burki a lokacin da taso Abba ya sake ta,tabbas bazata ta6a mantawa da halarcin da modibbo yayi mata ba, Ganin ta miƙe yasa junaid sakin murmushi yace"mommy zaki ko"? Jinjina mashi kai tayi alamar eh, Janyo hannunta yayi har suka ƙaraso falon,ganin hankalin mutanen dake acikin falon gaba daya yana akan Audio din da ammi ke saurare,hakan yasa itama ta samu wuri ta zauna,junaid ma ya zauna gefenta,yayin da idanunshi ke akan su sehrish,sam basu lura dashi ba saboda hankalinsu duk ya tashi,a sakamakon Audio din da aka kunna,saboda sun tsani jin labarin rayuwarsu,ko miskala zarratin,   Kowa ya natsu yana sauraron audio ɗin,lokacin da Abusufyan ya kammala bada tarihin rayuwarshi da abu,sai next audio ɗin ya shiga wanda Jahad ke bada labarin rayuwarsu,nan take hankalin AMMI yayi mugun tashi,jikinta har tsuma yakeyi,tuni wasu siraran hawaye suka shiga zarya a kuncinta,ita kanta Alexandra jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,tunda take arayuwarta bata ta6a jin tausayin wani ɗan adam ba,daga ita har ammin kamar yadda sukaji tausayin waɗannan bayin Allahn ba,Very heart touching story,wanda duk wani mai imani In ya saurareshi dole ya zubda hawaye,in ma baiyi kuka ba,    Ganin yadda hawaye ke sintiri akan fuskar AMMI yasa Omar ya cire hanky daga aljihunsa ya miƙa mata,dama kamar yasan cikin buƙatarshi take,a fuskarta ta kifa hankacif ɗin,ta fashe da matsanancin kuka mai cin rai,kowa yayi mamakin yadda Ammi ke kuka,cikin shessheƙar tace"ku kashe mun audio din nan ya isa haka,kunnuwa na bazasu iya jurar jin wannan tashin hankalin ba,'   dama Audio ɗin yazo ƙarshe,junaid ne ya mike ya ɗauki wayar,tare da miƙa ma babban yayansu ita,ya kashe audio ɗin,   "Shiyasa akeso ko da yaushe mutun ya kasance mai sauƙin kai,kada ya cika tsaurara al'amurransa,yanzu da ace banzo ba,da shikenan,haka zaki kora yaran nan,ke baki tsaya kinyi bincike ba,kuma baki saurari bayani daga gurin kowannansu ba kawai kin tashi kin yanke hukunci,sai daga baya kuma kizo kina danasani"   daƙyar ammi ta iya furta"Astagfurullah Allah na tuba!ka yafe mun,rashin sani ne yasa na kirasu da shaggu,game da halin da yaran nan suka tsinci kansu,duk laifin mahaifinsu ne,shine silar komai,duk da daman Allah ya ƙaddara faruwar hakan babu wanda ya isa ya hana,amma Abusufyan bai kyauta ma rayuwarsu ba,meyasa bai sanar ma kowa ba don aɗauki mataki?saboda kawai yayi mashi barazana?Amma dai Allah ya tsine ma fasiƙin mutumin nan,Wlh bazan barsu ba,saboda me laifin kakansu zai shafe su?wannan wata irin mugunta ce mara kan gado,?bai tsaya a iya kan ya'yan salahudeen ba,hada jikokin duka yake ɗaukar fansa akansu,?kuma shima salahudeen ɗin daya kashe mahaifinsu ae don saboda mugayen laifukan da aka kamasu dashi ne,ɗaukar fansar ta mutun ukuce suke ɗauka,mahaifinsu da kuma mahaifiyarsu,da kuma wannan ɗan koran nasu,dukkansu Allah zai toni asirinsu,'   Jinjina kai modibbo yayi yana sauraronta saida takai ƙarshen maganarta,tukunna yace"ba komai ne yasa na tako nazo ƙasar nan ba,face don abu uku,kuma ina fata zaki bani haɗin kai domin asamu maslaha atsakaninku gaba daya,saboda baza a ta6a cin nasarar gano waɗannan masu ɗaukar fansar ba,har sai ku na cikin gidan kun fara haɗa kanku,in ba haka ba,munafukan dake shirya maku zagwan ƙasa zasu samu nasarar cin galaba akanku,ta hanyar rarraba kawunanku,saboda ni inaji araina cewar masu shirya wannan maƙarƙashiyar suna ATARE DAKU!sun shiga cikinku,suna acikin rayuwarku!' Wannan maganar ba ƙaramin jijjigasu tayi ba,don sai da kowannansu ya ɗago yana kallon fuskar modibbon, "Nasan zakuyi mamaki amma nan gaba sannu a hankali zaku shaida maganata,yanzu dae bari inyi abunda ya kawoni," "AISHA" Ya ambaci sunan Ammi,muryarta asanyaye ta amsa mashi da Na'am, "Banaso in ƙarajin wani ƙorafi akanki!wannan ne na farko kuma wannan ne na ƙarshe!idan har kinaso ki zauna lafiya,to ki gyara tsakaninki da ya'yanki!da kuma tsakaninki da Jikokinki,na uku kuma shine tsakaninki da surukarki fatima,"ya ƙarasa maganar yana nuna Alexandra da sandar hannunshi,ɗagowa ammi tayi tare da kai idonta kan Mommynsu junaid wadda itama kallon nata takeyi,kawar da kanta tayi gefe batare da tace komai ba, Cigaba da magana modibbo yayi,"Allah ma mukanyi masa laifi kuma ya yafe mana,balle mu ƴan adam,fatima bata yi maki laifin komai ba,tun farko koda kike mata magana take mayar maki saboda kin nemi cin zarafinta ne!wanda kuma ba kowa ne zai iya jurewa ba,balle ita da take jar fata,yanayin rayuwarsu ko ince tarbiyarsu ba irin tamu bace,don da a ƙasarsu ne kikayi mata haka zata kaiki ƙara kotu ne a yanke maki hukunci,babu ruwanta da Cewar ke surukarta ce,sannan kuma bai kamata ki nuna mata ƙiyayya ba,duk maison naka ae masoyinka ne!ɗanki fa takeso,kuma saboda son da take mashi tabar iyayenta da kowa nata tazo ƙasar nan,inda bata san kowa ba,ko tsoron acutar da ita batayi ba,bakowa ne ma zai iya wannan kasadar ba,don haka yakamata ki so fatima saboda masoyiyarki ce,ba maƙiyiyarki ba,idan don ta kasance farar fata ce,damu dasu shin ba Allah bane ya halicce mu ba?ya banbanta mu ne?ko wani yafi wani ne"? Ya ɗan jinkirta da maganar yana kallonta, Kafin ya ɗaura da cewar"Yakamata ki ajiye wannan gabar dake tsakaninki da ita,Yanzu fatima ta wuce suruka a wurinki,tamkar ƴ'a take a wurinki,tunda ta hayayyafa da ɗanki,yakamata kiyi alfahari da ita saboda itace ta haifa maki ɗaya daga cikin jikokinki wanda duniya take alfahari dasu,waɗanda suka ɗaukaka darajar mu a idon duniya,"   Nauyayyiyar ajiyar zuciya Ammi tasaki tare da gyaɗa kai tace"Insha Allah komai ya wuce,"   Murmushi Abba ya saki ranshi fari tass kamar an yi mashi albishir da gidan aljanna,   "Sannan kema Fatima inaso ki ajiye dukkan wasu makaman yaƙin ki,kibi surukarki tamkar mahaifiyarki,kiyi mata biyayya amatsayinta na wadda ta tsugunna ta haifi uban ya'yanki,"   Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Nima a wurina komai ya wuce,dama saboda ƙiyayyar da take nunamin ni da ya'yana ne yasa nima nake ƙinta,amma daga yanzu insha Allah babu wanda zai ƙara jinkan mu,"   Tana kai ƙarshen maganar junaid yace"Gaskiya,wannan sulhun bai cika yadda akeson shi ba,Mommy da Ammi basu ta6a yin koda musabaha ba,yakamata yau su tashi su rungume junansu ta hakan ne zamu gane cewar sun shirya da junansu,"   Gaba ɗayansu suka saki murmushi,miƙewa Alexandra ta farayi kamin Ammi itama ta miƙe,suka ƙarasa tare da rungume juna,tafi su Abba suka shiga yi wanda hakan yaja hankalin sauran matasan gidan,har suka firfito cikin falon don suga me ke wakana,ae koda su kayi arba da Ammi da Alexandra rungume da juna,nan fa suka shiga sowa,abun ba ƙaramin farin ciki ya sanyasu ba,musamman su Fawan don sun jima suna jiran wannan ranar tazo,ashe da rabon zasu ganta da idanuwansu,   "Ki yafe mun duk abubuwan da nayi maki,kuma inaso ki sani ba don bana sonki bane yasa nayi maki hakan ba,kawai haline irin nawa,da kuma sharrin shaiɗan" Ammi ce tayi maganar ayayin da take raba jikinta daga na alexandra,fuskar kowanansu ɗauke da siraran hawaye,   Murmushi alex ta saki kafin tace"Allah ya yafe mana gaba ɗaya,inaji kamar nafi kowa farin cikin wannan ranar,"tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya,suna cikin rahar nan sukaji ana ɗaukarsu hoto ket ket!!   Da sauri suka waiga don su ga wanene,ashe wai fawan ne ya ɗauko camera ɗinsu,yana ɗaukarsu hoto yana faɗin"yau a daily trust dole su buga wannan gagarumin labarin,zazzafan gaske,Ammin mu wato kakarmu a yau ta rungumi surukarta wadda ta kasance mahaifiyarmu bayan sun dade suna shan gwagwarmaya ,"   Dariya sosai su kayi,ganin ya sanyasu raha,yasa shi cewa"Abba mu shigo ciki a ƙarasa tattaunawar tare damu?   Fuskar Abbansu ɗauke da murmushi yace"why not,a yanzu an sasanta komai,an samu maslaha,zaku iya zuwa ku zauna,"   Jin haka yasa suka ƙaraso ciki,gaba ɗayansu ne hada su twins jabeer,khaleed irfan dasu kanal,wuri suka samu suka zazzauna a ƙasa,   Junaid yace"Yawwa Amminmu,yanzu saura Uncle ɗinmu bawan Allah,yayi missing ɗinki sosai yakamata shima ki rungumeshi,ko yaji sanyi aranshi,"ya karasa yana langa6ar da kai.    Juyawa Ammi tayi tare da kallon abusufyan wanda ke a zaune,idonshi na kallon ƙasa,   Gyaran murya ta ɗan yi mashi,ya ɗago da idonshi ya kalleta,cike da zolaya tace"So kake sai nace ka taso"?   Fashewa yayi da dariya,kafin ya miƙe da sauri ya faɗa jikinta,sosai ta rungume shi ajikinta,tana ɗan bubbuga hannunta a bayanshi tace"nayi kewarka sosai,ka sani kuka Abusufyan,fiye da tunaninka,hakanan ka tafi ka barni shekara da shekaru...."tana maganar hawaye na fita a idanunta,   ɗagowa yayi daga jikinta,idonshi na fitar da kwalla yace"Ki yafe mun Ammi,nasan ban kyauta maki ba,nayi maki abubuwa da dama wanda bakyaso,nasan cewa hada haƙƙinki ne ke bibiyar rayuwata shiyasa ma harya shafi ya'yana,...."     Hannu tasa tana share mashi hawayenshi tace"Na yafe maka abusufyan,dama ni burina shine ka dawo kusa dani,kuma Alhamdulillah,gashinan ka dawo cikin yan uwanka,naji daɗin hakan sosai,Allah ya ƙara haɗamun kanku,"   gaba ɗaya suka amsa da Ammin, "AMMI saura su rishi,su baki rungumesu ba,kalli fa kiga yadda duk suka shiga damuwa,bayin Allah," junaid ne ya sake yin maganar yana raku6e fuska,alamar tausayi    Kallonsu Ammi tayi,sun cunkushe wuri guda kamar kifin gwangwani,musamman Sehrish jikinta har lokacin sae kerma yake,a hankali Ammi ta taka izuwa inda suke,ta zuƙunna agabansu,sannan takai hannunta tare da shafa fuskokinsu,kafin tace"dole in nemi yafiyarku,saboda na jefebku da mummunan kalma,bisa rashin sani,ina mai matuƙar baku Haƙuri akan abunda ya faru a rayuwarku!ba laifinku bane laifin wasu ne akeso a ɗaura maku shiyasa aka biyo ta hanyarku duk don a ƙuntata mana,amma nayi maku alƙwarin cewa ɗaya daga cikin waɗanda sukayi sanadiyar wulaƙanta rayuwarku,Wlh bazai sha ba!daga rana irin ta yau zansa a fara bincike akansu har sai Allah ya tonu asirin kowannansu,kuma nayi maku alƙawarin cewa,zansa akawo maku wannan fasiƙin mutumin har inda kuke don ku wanke mun mummunar fuskarshi da tafukan hannayenku,"   Jin wannan maganar ta Ammi yasa Hosana fashewa da dariya,har white teeth ɗinta suka bayyana,dimples ɗin fuskarta suka lotsa,Jahad ma murmushi ne ya bayyana a fuskarta,sehrish ce kawai batayi murmushi ba,da alama kamar akwai wani abu dake damunta,duba da yanayin jikinta dake ta kerma,   Ruƙo hannayensu ammi tayi tare da miƙar dasu tsaye sannan ta haɗasu duka ta rungumesu sosai,ajikinta, Wani irin matashin murmushi ne ya bayyana a fuskar kowannansu dake a falon,haƙika sunji daɗin wannan ranar,tsakaninsu da Allah sai godiya daya bar Modibbo a raye har zuwa wannan lokacin,saboda shine silar komai daya faru ayanzu,da bai zo ba da akasin hakan ne zai faru,    Addu'oi' Ammi ta shiga karantowa tana tottofa masu akawunansu,a ƙarshe tace"Allah yayi maku ALBARKA,"suka amsa mata da Amin,   Komawa su kayi kowa ya zauna,itama ammin ta zauna,bayan kowa ya natsu Modibbo yace"ko akwai mai magana acikinku"?   Da sauri Abbansu junaid yace"Ina da magana," Modibbo yace"faɗi kai tsaye muna sauraronka,"    "Yawwa kawuna,dama akan maganar fatima ne da Abusufyan!har yanzu basu shiri a tsakaninsu,tun wani sa6ani da suka ta6a samu a lokacin baya,to har yanzu basa jituwa,yakamata aduba lamarin,' Sunnar dakai ƙasa Abusufyan yayi,kamar yadda itama alexandran tayi, "Ae yanzu ko banyi masu magana ba,zasu shirya kansu ne ko don zumuncin dake a tsakaninsu,da kuma ƴa'ƴayensu," Murmushi kowannansu,yayi abusufyan yace"Insha Allah komai ya wuce a wurina,dama can ni ban ta6a ruƙeta araina ba,nasan rashin kunyar da nakeyi mata ne a lokacin baya yasa take fushi dani har yanzu,amma ina neman afuwarta," Yana kai ƙarshen maganarshi,Alexandra tace"Nima komai ya wuce a wurina,Allah ya yafe mana baki ɗaya,kuma ya ƙara haɗa kawunanmu," Wani irin ihu junaid ya fasa,saboda tsabar farin ciki,hankalin kowa ya koma kanshi,ganin sun zuba mashi ido yasa shi sanya tafin hannunshi ya rufe fuskarshi,saboda kunyar data rufe shi,ƙasa ƙasa yake sakin dariya,bakomai ne yasa shi wannan farin cikin ba,face Shiryawar da Momnynsu tayi da Uncle ɗinsu,ko ba komai zai samu amincewarta wurin auren ɗaya daga cikinsu,💃 "Gobe da safe zan wuce damaturu,tunda naci nasarar haɗa kawunanku,ina fata zaku kasance a haka ko bayan tafiyata," atare suka amsa mashi da cewa"Insha Allah," "Amma mun jima bamu haɗu ba,bazaka ƙara kwanaki ba"? Ammi ce tayi maganar, murmushi modibbo yayi kafin yace"kada ki damu,tun da dai na shigo ƙasar zaku dinga ganina ne akai akai,insha Allah," Alhamdulillah,The end🥱🤣😂😅 nan bada jimawa ba,zan rubuta hakan insha Allah,nasan wasu har gabansu ya faɗi rass......... *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.     *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _Ga duk mai son karanta littafin Abban sojoji,kai tsaye ya tuntu6eni ta numbar wayata 08103884440_ Special thanks to hafsat Usman Abubakar🥰, "Koda ace baka samu zuwa ba,xamu zo nan damaturun,dama mu ya dace ace mun je can gaba ɗayan mu bayan komai ya lafa,ko don saboda ƴan ukun abusufyan,zamu je dasu don suma suga danginsu dake acan da kuma na zariyya,dana sauran state,"acewar ammi, Modibbo yace"hakan ma yayi,Allah yayi maku albarka gaba ɗayanku,"suka haɗa baki wurin amsa mashi da ameeeen, Duk wannan abun dake faruwa Aunty babba da hayaam suna acikin ɗaki,kowannansu ya dafi waya sai danna yake yi,gaba ɗaya tunaninsu ya tafi akan cewa An kori su sehrish,hakan yasa hankalinsu ya kwanta luf, miƙewa zaune aunty babba tayi daga kishingiɗen da take,fuskar nan a washe tace"Oh ni ƴasu,ko ina waɗannan ƴan ukun suka dosa yanzu? Hayaam tace"Wama ya sanin masu,suna can suna gagari acikin gari,ƙarshenta ma a samu wata babbar mota zubin ɗan gotte tayi mana awon gaba da kawunansu,"   Fashewa su kayi da dariya,sai da suka tsagaita dayin dariyar Aunty babba tace"duba mun ƙarfe nawa yanzu,agogon wayata ba saiti,"    "kusan Ƙarfe tara fa yanzu,gashi ko abincin dare ma ba mu nema ba,"   Tsoki taja"mtsww,wannan wani irin gidane!A tunani na Azmee ya kamata ace ta kawo mana dinner ɗin mu har cikin ɗaki,ni bansan menene amfanin matar nan ba a cikin gidan nan,bata wani aiki,sae dae ta dafa masu abinci,ta zauna taci ta ƙoshi ta tara tumbi,ta mayar da gidan kamar na ubanta,"   Hayaam ta ɗaura da cewa"Ae kwanaki har magana taso ta gayamun,saboda waccen korarriyar yarinyar,Sehrish take da suna ko wa ma......."dakatawa tayi da yin maganar sakamakon turo ƙopar da taji anyi,atare suka kai idanunsu wurin,   Azmee ce ta shigo hannunta ɗauke da tray,koda su kayi arba da ita,nan fa suka shiga yin ƴan kame kame na rashin gaskiya,    Basu amsa mata sallamar da tayi masu ba,ƙarasawa tayi ta ajiye masu tray ɗin a ƙasa,sannan tace"abinci ne na kawo maku,bansan ko kuna buƙata ba,naga baku fito kun nema ba,shine nace bari na kawo maku a ɗaki," Washe baki suka shiga yi,hankalinsu harya kwanta,da alama bataji gossiping ɗinta da sukeyi ba,   "Mun gode sosae Azmee,wlh kina ƙoƙari sosai acikin gidan nan,ke kaɗae kike duk wasu aikace aikace na gidan nan,shekara da shekaru,baki ta6a gajiyawa ba,kin mayar da dangin nan tamkar naki,bansan meyasa har yanzu kike tare dasu ba,wahalar tayi yawa,yaci ace yanzu kin nemi miji kinyi aure,amma in kika cigaba da zama a haka,rayuwarki zata ƙare ne a matsayin baiwa kuma bazawara,ba wani cigaba,"   Tunda Aunty babba tafara magana azmee ta zuba mata ido tana kallonta,batare da ta ƙyafta idanunta ba,har sai da Aunty babba takai ƙarshen maganar,sannan tace"Bani da amsar da zan baki Laila,amma inaso ki sani dangin nan basu ɗaukeni kamar yadda kikayi tsammani ba,kuma ni bana gajiya da aiki a ƙarƙashinsu,saboda sunyi mun halarcin da bazan ta6a mantawa ba,"   Juyawa azmee tayi da sauri ta kama hanyar fita daga ɗakin,harta ruƙe handle ɗin ƙopar zata buɗe muryar aunty babba ta katse mata hanzarinta da cewa"har yaushe ne zaki cigaba da danne abunda ke zuciyarki?   "Mekenan"!azmee ta tambaya a yayin da ta juyo da kanta tana kallonta,   "Azmee nafa son komai!na son cewa akwai wanda kikeso acikin gidan nan!saboda kin ta6a sanar dani a lokacin baya,ko kin manta"?   Baza kunne hayaam tayi tana sauraronsu,   "Hakane,na ta6a sanar dake,amma yanzu babu wannan a zuciyata,kuma ko a lokacin dana so shi,saboda irin kyautatawar da yake yi mun ne,kuma da tausayin shi da nakeji,na rashin matarshi a kusa dashi,Amma yanzu Alhamdulillah,uwar ƴa'yanshi tana a kusa dashi,babu wata sauran damuwa, Murmushi aunty babba ta saki tare da miƙewa daga zaunen da take a gefen gadon,ta tunkari azmee tana cewa"Yanzu ke sai ki haƙura dashi?baki kwaɗayin ki aure shi,ki samu ƙaruwa dashi,ko don ki samu gado acikin gidan nan"? Da alama Aunty babba so take ta tunzura azmee,   Girgiza kai azmee tayi"ni bani da buri akan tara dukiya,bana kwaɗayin abun duniya,saboda sanin cewa komai na tara ƙarshe a gidan duniyar nan zan barshi!albashin da nake samu acikin gidan nan ya isheni in ƙarashe rayuwata dashi,"    Ta6e baki aunty babba tayi,fuskar nan ɗauke da shu'umin murmushin nan tace"Yanzu shikenan kin za6i ki ƙarashe rayuwarki a ƙarkashin wasu kenan?ke baki da ƴancin kanki?wlh azmee bakisan ciwon kanki ba,ban ta6a ganin ƴar wahala irin ki ba,kin ƙuntata rayuwarki,kin ƙasƙantar da kanki,duk don saboda ki faranta ma wasu!har yau babu wani cigaba a arayuwarki,yakamata ace yanxu kin mallaki katafaren gida naki na kanki,kin kuma mallaki mota,kinje hajji da umrah,kin kuma je yawon shaƙatawa dubai da sauran ƙasashe,haba azmee yakamata kiyima kanki adalci,wlh kina cutar kanki,Nidai shawara nake ba......"   Tsawar da azmee ta daka mata ne yasa ta kasa ƙarasa maganar,ba ƙaramin razana tayi da tsawar ba,tamkar ba abakin azmee ta fito ba,    "Ke baki isa ki tunzurani ba,laila!ki iya bakin ki,in ba so kike kija ma kanki ba,ki tsaya a iya matsayinki,nima in tsaya a nawa,idan ki kayi kuskuren shiga gonata wlh ranki zaiyi mugun 6aci," tana ƙarasa maganar,ta janyo ƙopar da sauri ta fuce,   "Hmmmm Aunty laila,matar nan fa ba zaki ta6a iya canza mata ra'ayi ba,don na lura itama kaifi ɗaya ce,"   Jinjina kai aunty babba tayi aranta tana mai mamakin irin yadda azmee ta daka mata tsawa,sai kace batasan matsayinta agidan Ba,!    Komawa tayi cikin ɗakin ta zauna dirshan a gefen gadon,ranta ba ƙaramin 6aci yayi ba,taso ace taci nasara akan azmee ko don su sami haɗin kanta wurin Cimma burinsu,guntun tsoki taja tare da cewa"Ƴar wahala,sai kace tafi kowa tsoron Allah,kullum haka zaki ganta da cazbi a hannunta tana yawo," Ta ƙarasa maganar tare da mayar da idonta kan tray ɗin abincin da azmeen ta kawo masu,yatsina fuska tayi tare da kai hannu ta buɗe warmer ɗin,dambun shinkafa ne yaji kayan haɗi sai ƙamshi yake yi,a plate ta zuba masu nan suka zauna,suna ci ita da hayaam kamar wanda yunwa ta koro, Azmee kuwa bayan fitarta daga ɗakin nasu,jiki a sanyaye ta wuce ɗakinta,kalaman aunty babba ba ƙaramin 6ata mata rai su kayi ba,zuciyarta ta sosu sosai,daure wa kawai takeyi,da ace bata kai zuciyarta nesa ba da ba abunda zai hana ta wanke fuskar laila da mari! Sam ta manta da hafsat dake kwance a ɗakinta,baiwar Allah tun bayan fitarta daga ɗakin hayaam,ta wuce ɗakin azmee batare da sanin kowa ba azmee ce kaɗae tasan cewa tana a ɗakinta,anan tayi wanka,ta kuma ci abinci ta kwanta,saboda wani irin zazza6i daya saukar mata ajikinta,kwata kwata zuciyarta ba daɗi,tayi danasanin rayuwarta fiye da a ƙirga,idanunta na tsananin son ganin Su Jahad,amma tsoran tunkararsu takeyi,gashi har tsaraba tayi masu don ta basu hmmm,duk in ta tuna irin uƙubar da suka sha a hannunsu,sae ta fashe da matsanancin kuka,tun azmee na rarrashinta har ta gaji ta ƙyaleta,idanunta sun kumbura suntum haka la66anta ma,bakomai take yi ma fargaba ba,fa ce irin hukuncin da Mahaifinta zai yanke mata,don kuwa tasan muddin yaji abunda suka aikata masu jahad,Wlh ba zasu sha ba,su dukan su sae sun fuskanci mummunan hukunci a wurinsa,gaba ɗaya tayi nisa cikin zurfin tunani,taji shigowar azmee cikin ɗakin,buɗe idanunta tayi tana kallon azmee dake shigowa,yanayin yadda taga fuskar azmee ya tabbatar mata da cewar tana cikin damuwa,gefen gadon ta zauna zugudum yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,   "AUNTY AZMEE" muryar hafsat ce ta dawo da ita cikin hayyacinta,juyawa tayi bayanta tare da kai idanunta kan fuskar hafsat dake kawance,ƙoƙarin 6oye damuwarta tayi kafin tace"har yanzu bakiyi bacci ba?   Miƙewa hafsat tayi daga zaune,sannan tace"Bazan iyayin bacci ba aunty azmee,inajin tsoron abunda zai biyo baya,nasan cewa daddy bazai ƙyaleni ba,"ta ƙarasa maganar tana faman matse kwallon dake gangarowa akan fuskarta,     "Kidaina sa damuwa aranki hafsat,a yadda kika bani labarin irin ruƙon da kuka yi masu jahad,da farko atare kuka azabtar da rayuwarsu ke da mahaifiyarki amma kuma daga baya kin nuna masu soyayya,ina mai tabbatar maki da cewar wannan soyayyar da kika nuna masu daga baya itace zata cece ki a hannun mahaifinki...."   "Taya kike tunanin hakan zai zame mun mafita aunty azmee?bayan ni ce dakaina,na ɗauki su jahad acikin mota ta,na fitar dasu daga cikin gidan,na damƙa su a hannun wannan mugun mutumin wanda mommy tasa ya zubar mata dasu a daji!"tana magana hawaye na zuba a fuskarta,   "Amma Ae kin sanar dani cewar,Mommynki yaudararki tayi akan cewar gidan marayu zaki kai su ashe zubar dasu take so ayi,"   "Hakane aunty azmee,amma ae su hosana basu son da haka ba!nasan cewa sun tsaneni yanzu,kallon mayaudariya suke yi mun,kuma ba kowa ne ya jawo mun haka ba,fa ce Mommy,"    Ta ƙarasa maganar tare da fashewa da wani sabon kukan,    "Ga shawara"! Cikin shessheƙar kuka Hafsat tace"Ina...sauraronki,koma wata irin shawarace inaso,"   "Gobe da safe tun kafin Abbanki ko Omar suyi yunƙurin tunkarar Su jahad akan maganar,ke ki fara yin hanzarin zuwa wurinsu ki nemi yafiyarsu sannan kiyi masu bayanin cewar bada saninki ba,wannan mutumin ya ɗauke su ya kaisu daji don ya zubar dasu ba,Mommynki ce ta yaudareki akan cewar gidan marayu zai kai su....."   "Aunty azmee kina ganin in na faɗa masu hakan zasu yarda dani?hosana fa tana da ta6in hankali,daƙyar zata fahimce ni," .."kada ki damu,zasu fahimce ki,ki kwantar da hankalinki kawai,kamar kina acikin jirgi mai ya qare,"murmushi hafsat ta ɗan saki,har taji sanyi aranta,fatan ta Allah yasa gobe in taje wurin su Jahad,su fahimce ta, Sun jima suna tattaunawa atsakaninsu kafin daga bisani,azmee tabar ɗakin hafsat kuwa bargo taja ta lullu6e kanta,sannu a hankali bacci ya ɗauke ta,    Acan falo kuwa bayan komi ya lafa,Ammi tace"Yakamata kowa yaje yayi sallah,ya kwanta ya huta,"amsa mata suka yi da toh,sannan kowannansu ya miƙe tare da nufar Bedrooms ɗinsu,atare Su jahad suka miƙe,saida suka fara yi ma su ammi sallama,ta amsa masu fuskarta asake tare da tunasar dasu akan in zasu kwanta kar su manta suyi addu'a,a ƙarshe dae falon ya rage babu kowa cikinsa,irfan shiya jagoranci Modibbo har zuwa ɗakin da zai zauna kafin gobe,Bayan ya kaishi ɗakin,Azmee ta shirya mashi kayan tea takai masa,kamar yadda ya buƙata, *Boss Bature*   🤍❤? A 6angarensu sehrish kuwa,bayan sun koma bedroom ɗinsu,alwala kowannansu yayi sannan su kayi salla atare,bayan sun kammala suka haye saman gadonsu,cikin ƙanƙanin lokaci bacci ya ɗauki Jahad da Hosana,banda sehrish wadda bacci ya ƙaurace ma idanunta,tabbas ɗazu ta tsorata sosai da Ammi ta koresu,abun ya razanar da ita,ta kuma ji matuƙar tausayin Daddynsu,duk in tazo rufe ido,fuskarshi take gani a lokacin daya fashe da kuka yana faɗin cewa sai dai ta tsine mashi amma sai yabi ƴa'ƴan shi,bazai bari rayuwarsu ta wulaƙanta ba,tabbas ba ƙaramin so yake yi masu ba,yana tsananin ƙaunarsu fiye da tunaninsu,lokaci guda abunda ya faru a babban falo ya shiga dawo mata acikin kanta,mikewa tayi daga zaune,ta jingina bayanta a headboard din gadon,yayin da hannayenta ke rungume da pillow,a hankali tashiga tariyo abunda ammi tayi,na bijirema umarnin iyayenta,wanda hakan yasa ita ma ƴa'ƴanta suke bijire mata,Wannan abun ba ƙaramin tsoratar da sehrish yayi ba,saboda tunawa da Umarnin da mahaifinta ya bata na hana ta zuwa sashen sgr da sunan yi mashi aiki,amma taƙi bin umarninsa,hakanan ta dinga jin gabanta na faduwa,runtse idanunta tayi tare da buɗesu a hankali,wasu siraran hawaye ne suka shiga gangaro mata a fuskarta,a hankali la66anta suka soma motsi,ƙasa ƙasa take magana,matsar da kunne na nayi don inji me take cewa, _Ya Allah ka yafemun!bani da hankali nayi kuskure,saboda kawai son wanda baisan inayi ba,saboda na faranta ma wanda nakeso,naƙi bin umarnin mahaifina,wlh bazan ƙara ba,inajin tsoron nima ƴa'ƴan da zan haifa suƙi bin umarni na,bana fatan hakan ya faru,zan daure nayi mashi biyayya_   Tafin hannunta tasa ta goge hawayen dake zuba a idanunta,bakomai idanunta ke hango mata ba,fa ce kyakkyawar fuskar SGR,tabbas yau yayi masu abunda ba zasu ta6a mantawa ba arayuwarsu,yana da matuƙar kirki sosai,bakowa ne zai gane hakan ba farat ɗaya,shi na musamman ne,samun mutun mai irin kyakkyawar zuciyarshi a wannan zamanin da muke ciki,zaiyi matuƙar wuya,   Zuro ƙafafunta tayi ƙasa daga saman gadon,ta miƙe tsaye,jikinta na sanye da riga da wando na bacci,milk colour,takawa tayi izuwa gaban door ɗin dakin,ta buɗe bayan ta fita ta janyo masu ƙopar ta rufe,   A hankali take tafiya,ga wani irin sanyi dake ɗan ratsa sassan jikinta,amma sam bata jin sanyin,saboda daɗinshi take ji,zura hannayenta tayi acikin aljihun wandon jikinta,kai tsaye ta wuce main palour din,wayaam taga babu kowa kamar yadda tayi tsammani,da alama ma mutanen gidan duk sunyi bacci,hakanan taji tana marmarin tasha Cornflakes acikin wannan daren,juyawa tayi da sauri ta nufi kitchen,within minutes ta fito hannunta ɗauke da Cup,ta cika shi da cornflakes haɗi na musamman tayi mashi,ta zuba uwar madara da bornvita duka ta sanya,ta kuma Tsula sugar,'   Dawowa tayi falon,ta zauna saman sofa tare da aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,nace sannu ƴar masu gidan,   Motsa cornflakes ɗin ta shiga yi,da cokalin hannunta sae faman jujjuyashi takeyi aciki,kafin daga bisani ta shiga ɗebowa tana kaiwa abakinta tana sha,tana taunarsa kunnuwanta na motsi saboda daɗin da yayi,bakowa ne ya faɗo mata aranta ba fa ce junaid,abokin shiriritarta,murmushi tayi tare da cewa ɗan uwana rabin raina nasan yanzu haka yana can yana sharar baccinshi,da ace idonshi biyu da atare zamu sha wannan cornflakes din,i really missed u junaid,rashin kwanciyar hankali yasa,mun nisanta da juna,amma insha Allah tunda komai ya dai²ta,yanzu bamu da sauran wata damuwa,zamu dinga fita yawan shaƙatawa atare mu dukkan mu, Ita kaɗae abunta sai faman sambatu takeyi,kamar wata zautacciya,tana cikin shan cornflakes ɗinnan,ta wutsiyar idonta ta hango mutun a tsaye ƙiƙam,aikuwa hankalinta yayi mugun tashi,kasa juyawa tayi saboda tsoron kar ace dodo ne,tuni jikinta ya fara kerma,dama gata da shegen tsoro,zuciyarta ta shiga bugawa da ƙarfi da ƙarfi,tunaninta wanene mutumin data hango tsaye a upstairs,tsabar tsoro ya hana ta juyawa ta kalleshi da kyau,wani irin wahalallan yawu ta haɗiye,ajiye cup ɗin dake hannunta tayi,sannan ta lalla6e tare da saukowa daga saman sofa ɗin,ta durƙushe ƙasa tayi sujjada,kamar maiyin sallah,duk don saboda kar dodon ya ganta,a hankali ta shiga rarrafawa a ƙoƙarinta na tabar falon,ta koma ɗakinsu,   Shikuwa mutumin dake tsaye goye da hannayenshi asaman ƙirjinshi,zuba ma sarautar Allah ido yayi,abun ba ƙaramin mamaki ya bashi ba,tsoran yarinyar harya so yayi yawa,ko kallon inda ya ke bata yi ba,ta wutsiyar ido kawai taga inuwarsa amma ta sama ranta cewar wani mugun abunne,sam baiso ta tsorata ba,don bada niyar wannan yazo wurin ba,   Wani abune ya faɗo mashi aransa,cikin sauri ya koma cikin part ɗinsa,jimmm kaɗan sai gashi ya dawo hannunshi ɗauke da wayarsa,tsayawa yayi tare da saita wurin da take yana ɗaukarta video kasancewar akwai haske sosai a main falo din,   Ba ƙaramar wahala sehrish tasha ba,da wannan rarrafen ta ƙarasa har wurin da zata shiga corridor ɗin ɗakinsu,gaba ɗaya zufa ta wanke mata fuskarta,tana ƙokarin shiga,wani abu ya faɗo mata aranta,tsayawa tayi tana tunanin kodai ta juya taga wanene shi tunda dae ta iso wurin da zata shiga ɗakinsu,koma menene ai bai isa ya cutar da ita ba,da zarar ta juya taga dodo ne,sae ta watsa da gudu ta shige ɗakinsu,taja ƙopa ta rufe,fakat,   Jikinta na kerma,amma ahaka ta daure ta ɗan juyo da kanta,takai idanunta saman upstairs din,ae batasan lokacin da taƙarasa juyowa gaba ɗaya ba,ta baza idanunta donta tabbatarma kanta abunda take gani,ƙura ido tayi tana son gano wanene saboda yayi mata nisa,wannan hasken fatar nashi ne ya fara sa ta tunanin kamar sgr ne,ƙara zuba ido tayi anan ta hango wannan doguwar sunar kan tashi,tabbas kuwa shine,ajiyar zuciya ta shiga saukewa a fili tace"Ashe babban yaya ne,nasha wahalar banxa,Allah yasa dai ban zubar da cornflakes ɗina ba,   ganin tana kallonshi,yasa ya janye phone dinsa,ya kashe camera ɗin ya tura wayar a short pocket dinsa,da hannu yayi mata Alamar taxo,   Waro ido tayi tare da nuna kanta,don ta tabbatar in ita yake kira,nuna ta ya kuma yi da hannunshi,   Gabanta ba ƙaramin faɗuwa yayi ba rasss,tsoranta kar ya tuhumeta akan meya hanata zuwa part ɗinsa kai mashi Cofee don yau bata je ba,   Miƙewa tayi kamar wata mara gaskiya,haka ta tunkaresa,kamar an zare mata lakar jikinta,a hankali take tattaka matattakalar stairs ɗin,harta ƙarasa ɗan nesa dashi tukunna ta tsaya,tunda ta saci kallonshi sau ɗaya,tayi arba da faffaɗan ƙirjin nan nashi,gashi babu shirt ajikinsa,Shorts ne kawai black colour ya sanya,kuma ma dai ba ƙaramin kyau yayi masa ba,   Ganin ta tsoge wuri guda,yasa shi moving ya ƙarasa inda take dab da ita,don har saida ta ɗan ja da baya,saboda ƙure matan da yayi,   Lokaci guda tarasa natsuwarta,sai ƴan kame kame take,a ƙarshe ma ta zura hannunta acikin sumar kanta,tana ɗan sosawa,ƙamshin turaren jikinshi ba ƙaramin illa yake yi mata ba,saboda wani yanayin da take tsintar kanta aciki,      gaba ɗaya idanunshi na akan lips ɗinta,mutsu mutsun da takeyi da bakinta,ba ƙaramin tafiya yake yi dashi ba,    Almost 5 mins suna a haka sannan ya buɗe baki da wannan Sexy voice ɗin tasa yace"Meyasa baki yi bacci ba"?   Muryarta na kerma tace"bana jin bacci ne,"   "Okey,that's y You came out to disturb those who are sleeping"? sunnar dakai ƙasa tayi tana girgiza mashi kai,alamar a'a,ganin ta dage sai faman sosa gashin kanta takeyi,yasa shi kai hannunsa ya damƙo wrist ɗin hannunta da ta zura acikin sumar kanta yace"ƙaiƙayi kike ji ne"?   A ruɗe tace"eh," Jinjina kanshi yayi tare da sakin hannun nata, .."lemme help u.......'ɗagowa tayi a razane jin abunda yace,ko amsarta bai tsaya ji ba,ya sanya hannunshi tare da zagayo dashi ta gefen waist ɗinta ya tallabota sosai, ya janyota gaba ɗaya ta faɗa asaman wide chest ɗinsa,nan fa hankalinta yabi ya tashi,ta susuce ta zauce ta rasa uwar ubanta,a hankali ya ɗago da right hand dinsa,ya tsoma shi acikin lallausar sumar kanta,wani irin massage ya shiga yi mata,wanda ya haifar mata da wata irin matsananciyar kasala ajikinta,ita kanta batasan lokacin da ta zagaye waist ɗinshi ba da hannayenta duka,ta ƙankame shi sosai kamar zata koma cikin cikinshi,yana jin yadda numfashinta ke fita da zafi zafi,tausasan la66anta sai gogar masa fatarsa suke,sosai sehrish ke shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinshi,tana jin kanta a wata irin duniya,wadda ba kalar tamu ba,just like in the dream haka take kallon lamarin,ta rasa gane wai shin SGR sosa mata kanta yake yi ko kuwa,saboda daɗin dake ratsa jikinta yafi ƙarfin a kirashi da daɗin susa kawai,tamkar zata zauce haka take ji,ga wani irin abu dake yi mata yawo a jikinta tamkar zufa,' Duƙar da kansa ya ɗanyi tare da kai hancinsa ya cusa sa shi acikin sumar kanta,ƙamshin man da take shafama kanta ne ya daki hancinsa sosai ya shaƙe sa,lumshe idanunsa yayi tare da ɗan ware su a hankali ya buɗe su,kafin ya mayar da la66ansa asaman fatar kunnanta,tamkar mai yin whispering haka ya shiga yi mata magana"tell me What did you do in the kitchen when you entered"? Yayi maganar tare da raba jikinshi daga nata,idanunshi tamkar na mai jin bacci,   "Cornflakes na haɗa,saboda in sha,"ta bashi amsa a yayin da idanunta ke kallon yatsun hannunta data haɗesu wuri guda tana wasa dasu,.   "Okey,ɗaukomin cornflakes ɗin,inaso nasha nima,"   Batare da musu ba,ta juyawa da sauri da sauri ta sauka downstairs,a nan saman table,ta ɗauko cup ɗin da ta ajiye,sannan ta dawowa upstairs ɗin ta kawo mashi,miƙa mashi tayi,ya sanya hannu tare da kar6ar kofin,spoon ɗin ya ɗauka tare da ɗan jujjuya shi,kafin ya ciko cokalin yana ƙokarin kaiwa bakinsa yaji tace"Kamar yayi yawa,'ɗan ɗagowa yayi da idanunshi ya kalli fuskarta da sauri ta kawar da nata idanun gefe,saboda taga ya ɗebo da yawa ne kuma mouth ɗinsa is too small shiyasa tayi mashi magana,a ganinta cokalin bazai iya wuce wa ba,ta cikin bakinsa,amma sai gashi ya shanye abunsa,bayan ya tauna cornflakes din,ya ɗan dakata tare da cewa"Bana shan sugar sosai,sannan milk ɗin ma tayi yawa acikinsa,meyasa kika sanya da yawa har haka"? . shiru tayi tana faman wurga ido, Miƙa mata cup ɗin yayi tare da cewa"Kar6i kayan ki"hannu tasa ta kar6a,sannan tace"Zan iya tafiya,"?   Hanya ya nuna mata tare da cewa"na ruƙe ki ne"?   Ajiyar zuciya ta sauke,kafin ta juya da sauri da sauri ta sauka donwstairs,duk yana binta da kallo,kitchen ta shiga a tsaye ta ƙarasa shanye cornflakes din ta ajiye cup ɗin,sannan ta fito tare da kai idanunta Upstairs taga in yana nan,a tsaye ta same shi,idanunshi a lumshe,   Juyawa tayi ta kama hanyar zuwa bedroom ɗinsu,adai² corridor din ta kuma tsayawa tare da ɗan waiwayawa don taga in yana nan koya tafi,Again ta ƙara ganinshi a tsaye kuma da alama ita yake kallo,ranta ne ya bata cewar kodai tayi masa bye bye da hannunta,may be ya mayar mata da martani,   ɗaga hannunta tayi tare dayi mashi bye bye,abun mamaki sai gashi ya ɗaga mata hannu yana yi mata bye bye din shima,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,har batasan lokacin da ta fashe da dariya ba,da gudu ta juya tare da faɗawa bedroom dinsu,    Ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa ya koma cikin part dinsa,bayan ya shiga bedroom ɗinsa,toilet ya fara shiga,bada jimawa ba,ya fito tare da hayewa saman shimfiɗeɗen gadonshi ya kwanta,tare da janyo pillow ya rungume shi asaman wide chest dinsa,yayin da blue eyes ɗinsa ke kallon haɗaɗɗen ceilling ɗin ɗakinsa,ya rasa gane meke damun shi,amma tabbas yana jin missing ɗin wani abu sosai atattare dashi,yana tsananin buƙatar wani abu,wanda baisan menene shi ba~~~~~~~   *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Saman Gadon ta haye ta kwanta tare da jan bargo ta lullu6e,zuciyarta cike da wani irin farin ciki,sai faman sakin kayataccen murmushi take,daƙyar bacci 6arawo yayi awon gaba da ita,? Wuraren sallar asuba,jahad ta farka tare da tashin su hosana,atare bayan sunyi alwala su kayi salla,bayan sun kammala suka koma saman gadon suka dasa wani sabon baccin don bai ishe su ba, Ƙarasowa hafsat tayi ƙopar bedroom ɗin nasu,jikinta sanye da dogon hijabi,hannu tasa ta ɗan bubbuga ƙopar ɗakin,shiru ba'a buɗe ba,ƙara bugawa tayi,bugun ya isa cikin kunnan sehrish,cikin bacci tace"Wanene"? Hafsat tace"Ni ce," "Kece wa"? Sehrish ta tambaya a yayin da ta miƙe tare da tunkarar ƙopar ta buɗe,Tun daga ƙasa har sama sehrish ke bin ta da kallo don batasan wacece ita ba,amma tabbas ta ta6a ganin fuskarta,kuma jiya taga gifcinta acikin gidan,ga kuma kamannin fuskar Yaya ishaq a fuskarta,   ƴan kame kame hafsat ta shiga yi,muryarta na inda inda tace"am...um..jahad.." katse ta sehrish tayi da cewa"ba ita bace,Ni sunana sehrish,jahad tana ciki tana bacci,"   "In ba damuwa inason ganinta," Matsa mata hanya sehrish tayi,ta shiga cikin ɗakin nasu,rufe ƙopar sehrish tayi sannan ta koma ciki itama,sae faman kallon kallo suke ita da hafsat,duk tabi ta kama kanta,kana ganin fuskarta zaka fahimci cewar bata da gaskiya,   Wuri ta samu gefen gadonsu ta zauna,idanunta na akan su jahad da hosana dake ta sharar bacci,   Muryarta a sanyaye tace"in ba damuwa,dan Allah ki tashe su daga baccin inason yin wata magana dasu mai mahimmanci,"   Batare da musu ba,Sehrish tace toh,sannan ta haye saman gadon tana ambatan sunayensu,gami da bubbuga ƙafafuwansu"jahad!hosana!ku tashi ana son ganinku,"   cikin bacci hosana ta buga tsoki tana fadin"dan Allah a ƙyale ni,kar a takuramin,"   Jahad kuwa tuni ta farka,tana faman mutsustsuka idanuwanta,wurga idanunta tayi kan sehrish tace"Wai lafiya"?   "Wannan ce ke son magana daku,"tayi maganar tana nuna hafsat dake zaune,   Juyawa jahad tayi tana kallonta,cike da mamaki ta ambaci sunanta"Aunty hafsat!" sunnar dakai ƙasa hafsat tayi,fuskarta dauke da matsananciyar damuwa,daƙyar ta iya amsa mata"Na'am jahad,"tashi zaune jahad tayi,suna fuskantar juna ta sake ambatar sunanta"Aunty hafsat,"   "Kinsanta ne"? Sehrish ce tayi tambayar,jahad tace"Niko na santa,itace ɗiyar wannan matar da nake faɗa maki wadda ta azabtar da rayuwarmu,kuma wannan itace ta ɗauke mu acikin motarta,ni da Hosana ta kai mu hannun wannan mugun mutumin wanda ya kai mu daji har yayi ƙoƙarin cutar da Hosana,"   Jin wannan maganar yasa ran sehrish ya 6aci,harara ta wurga ma hafsat tare da nuna mata hanyar fita daga ɗakin tace"Dan Allah malama tashi ki fita ki bamu wuri!bamu son ganinki!mugaye kawai Azzalumai,kun cutar da rayuwar ƴan uwana,saboda son zuciya irin naku,basuyi maku laifin komai ba,Amma kuka tsangwamesu,saboda kunga basu da gata,Insha Allah sai kunga sakayyar da Allah zaiyi masu,kuma sai kun ɗanɗana irin uƙubar da kukayi masu,"   Hawaye ne suka shiga zarya a fuskar hafsat,dama saida ranta ya bata cewar dakyar ne su yafe mata,   Janye idanunta tayi daga kan sehrish ta mayar dasu kan Jahad,cikin shessheƙar kuka tace"dan Allah ku yafe mun Jahad,nasan mun cutar daku,amma inaso ku sani bada son raina ba,na kaiku wurin wannan mutumin,Mommy ce ta sanar dani cewa Gidan marayu za'a kaiku,shiyasa har na ɗauke ku,kuma nayi hakan ne saboda tsoran karta halakar daku acikin gidan nan don ba yadda banyi ba akan ta kyale ku amman ta kiya,shiyasa ma na amince da akaiku gidan marayun ashe zubar daku tasa ayi,'   "Ba zamu ta6a yarda da kalamanki ba,saboda tun farko baki nuna kina son mu zauna acikin gidan ba,ke da mommynki,shiyasa kuka haɗa baki ke da ita,kika fara yaudararmu kina nuna kamar kina son mu ashe,so kuke ku fitar damu daga cikin gidan,saboda rashin Imani Aunty hafsat kika damƙa mu a hannun wannan mutumin,to bari kiji Ya Omar ya kashe shi har lahira!!   Gabanta ne ya faɗi rassss!hankalinta yayi mugun tashi,a kiɗime tace"Ya kashe shi!"   Jahad tace"kwarai kuwa Ya Omar shi ne ya kama shi da hannun shi acikin gidan gonarsa,lokacin da yake ƙoƙarin keta haddin hosana,aikuwa ya fasa mashi kai,anan wurin ya zama gawa,'     Tana kai ƙarshen maganarta sehrish ta ɗaura da cewar"tun yanzu kwara kusan inda dare yayi maku!don wlh Ya Omar bazai sassauta maku ba!muddin yaji cewar kune kukayi silar da har wannan mutumin ya ɗauki su jahad ya kaisu daji,sannan ku fara tunanin irin hukuncin da kuma zaku fuskanta a wurinshi!"   Wani irin wahalallan yawu hafsat ta haɗiya,tsananin tsoro ne ya bayyana akan fuskarta,ba don komai ba sai don jin cewa An kashe mutumin nan!tun da har Omar zai iya kashe rai akan su hosana,tabbas ba ƙaramin so yake masu ba,kuma akansu zai iya hukunta kowa,yanzu su menene sakamakonsu?   "Baku da wata mafita,shawara nake baku tun kafin hosana tayi maku tonan asiri,kwara kusan abunyi,don tace saita sanar ma Daddy da Ya Omar abunda kukayi mana!" jahad ce tayi maganar,   Gaba ɗaya duk sun bi sun tsoratar da ita,la66anta har kerma suke wurin rokonsu tana cewa"Dan Allah ku yafe mun,wlh nayi dana sanin duk wani abu da mu kayi maku,har ga Allah ni bada sanina ba,mommy ce ta shirya duk wannan,Allah shine shaidata,bazan yi maku ƙarya ba,"sosai hafsat ke kuka, Ruko hannun jahad tayi acikin nata tana fadin"jahad nasan kina da sauƙin kai,dan Allah ki yafe mun,wlh nayi nadamar abunda mu kayi maku ni da mommyna,nasan naƙi ku da farko amma daga baya naso ku sosai,kuma nayi kukan rashinku atare dani,lokacin da nagane cewa Mommy ba gidan marayu tasa akaiku ba,har faɗa sai da mu kayi da ita,ko isasshen bacci bana samu a lokacin saboda tunanin wani hali kuke ciki......"ƙarasa maganar tayi tare da sanya hannu tana share hawayen dake zuba a kan fuskarta,   Shiru su kayi da alama jikinsu ya ɗanyi sanyi,Sehrish tace"Jahad,idan kinyi niyya ki yafe mata,'jinjina kai jahad tayi tare da cewa"Ni dama ban ruƙe ki araina ba Aunty hafsat,na yafe maki Allah ya yafe mana gaba ɗaya,"   Amsawa tayi da "Amin,sannan tace"Hosana fa?dan Allah ku tashe ta inaso in nemi yafiyarta,"   Hannu Sehrish takai tare da bubbuga ƙafarta,farkawa hosana tayi,idanunta sunyi suntum saboda bacci,   "Hosana ki tashi,ga Aunty hafsat nan tana son magana dake,"jin an ambaci sunan Aunty hafsat yasa ta wartsakewa ta miƙe daga zaune,koda idanunta su kayi arba da fuskar hafsat,nan take ta murtuke fuska rai a6ace tace"Ni bana son ganinta,na tsaneta kamar yadda suka tsane mu ita da Mommynta,Aunty hafsat muguwace bata tsoron Allah,itace takai mu wurin wannan mummunan mutumin wanda yakusa kashe ....."katse ta jahad tayi da cewa"pls hosana just forget about the past,forgive her pls,Aunty hafsat tayi nadama,kuma bada son ranta ba ta kaimu wurin mutumin nan ba,Mommynta ce ta shirya wannan,"   Maƙe kafaɗa hosana tayi alamar bata yarda ba,harara ta wurga ma hafsat ɗin tana murguɗa mata baki tace"Allah saina faɗama Ya Omar da daddy,ko kukan jini zatayi sai dai tayi,amma saina faɗa,saboda rashin Imani kamar wasu dabbobi haka kuka rufe mu acikin store babu abinci ga ƙishin ruwa,ko iska babu,amma ko ajikin ku mu rayu ko mu mutu wannan ba matsalarku bace,zafi kamar zai kashe mu,adaren ranar da muka kwana a store,ba don jahad tayi mun fifita ba da Allah kaɗae yasan me zai biyo baya don rashin imani ku kuna can kuna shan A.c,wlh saina faɗama daddy....."fashewa hosana tayi da kuka,hada bubbuga ƙafarta,daga gani abun ba ƙaramin ciwo yake yi mata ba,ya tsaya mata arai,   Gaba ɗaya jikinsu yayi wani irin sanyi,musamman hafsat,duk yadda taso ta shawo kanta amma abun yaci tura,hosana ta rantse ta maya akan cewar saita faɗa ma Ya Omar,hatta jahad sai da taso ta lallasheta,amma ina ƙarshe sai ta dinga ƙoƙarin bugun jahad din,   Ganin haka yasa sehrish kallon hafsat tare da cewa"dan Allah kiyi haƙuri ki tafi kawai,hosana batasan ganinki,idan tana kallonki haukanta zai iya tashi,"     Jiki asanyaye Hafsat ta mike,tana tafiya tana waiwayonsu yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,a haka har ta isa ƙopar ɗakin ta buɗe ta fuce da gudu tana kuka,   Hannu Sehrish tasa tare da janyo hosana ta rungumeta sosai ajikinta tana lallashinta,da ƙyar ta samu hosana tayi shiru,sai faman sauke ajiyar zuciya take yi,komawa su kayi suka kwanta kowa da abunda yake saƙawa aranshi, *Aunty Babba* Suna kwance ita da hayaam sai faman sharar bacci sukeyi suna jan minshari yadda kasan bijimayen sa,sun cika gadon su biyu kawai,babu wanda ya farka acikinsu balle suyi tunanin yin sallar asuba,can cikin bacci Hayaam ta dinga jin ana bugun ƙopar ɗakin nasu tamkar za'a balle ta,dogon tsoki taja tana faman yatsina fuska alamar an takurata,a ƙule tace"Wai dallah wanene ke buga ƙopar ɗakin nan"!?   Muryar hafsat tajiyo daga waje cikin shessheƙar kuka tace"Ni ce,ki zo ki buɗe mun ƙopa,"   Jiki na rawa hayaam ta saukko daga saman gadon ta ƙarasa tare da buɗe ƙopar,gabanta ba ƙaramin faduwa yayi ba ganin fuskar hafsat sharkaf da hawaye,hankali atashe tace"Meya faru ne kike kuka"?   A tsiwace hafsat tace"Ba dole inyi kuka ba!kun jefani cikin masifa!ki bani hanya na wuce,Da Mommy nake so inyi magana,"tana faɗin hakan ta bangaje hayaam tare da wuce wa ciki,duk tabi ta ruɗe,wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare ma hafsat maƙoshinta,lokacin da tayi arba da Aunty babba,baje saman gadon tana sharar bacci,wato hankalinta kwance ita,batasan wainar da ake toyawa ba,   Da karfi ta ambaci sunanta"Mommy!Mommyyyyyyyy!   A firgice Aunty babba ta farka,agigice ta tashi zaune tana faɗin"Lafiya hafsat kike mun irin wannan kiran"?   "Ina fa lafiya mommy!ashe ke kina nan kina sharar bacci,ni kin barni cikin tashin hankali,jiya ko isasshen bacci ban samu ba,saboda tunanin hukuncin da Ya Omar da daddy zasu yanke mana..."   Jin wannan maganar yasa Aunty babba fashewa da dariya tana tafa hannu,   Hakan ba ƙaramin fusata hafsat yayi ba,muryarta na rawa tace"Mom...my dariya ma kike yi"? Aunty babba tace"to me kikeso inyi in banda dariya,ke bakisan meya faru ba jiya"?   Zuba mata ido hafsat tayi tana kallonta,   "Hayaam zo ki faɗa mata da alama batasan meya faru ba,ae mu yanzu bamu da sauran damuwa,hankalinmu a  kwance yake kamar muna cikin jirgi gobara ta kama," tana magana tana faman washe baki,   Ƙarasowa inda hafsat take a tsaye,hayaam tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli hafsat tare da cewa"ke bakisan cewa jiya Ammi ta kori su Jahad daga gidan nan ba?korar ma korar wulaƙanci,ae shiyasa kika ga mun saki baki muna bacci hankalinmu kwance,saboda bamu da sauran damuwa yanzu,"   Wani irin kallo hafsat ta wurga mata tare da cewa"Amma dae a mafarki hakan ya faru ko"?   Aunty babba tace"Wani mafarki,jiya agabanmu Ammi ta korasu,da gudu suka fita daga gidan nan suna kuka,"   Tsabar takaici ya hana hafsat cewa komai,     Hayaam tace"Ae kawai ki kwantar da hankalin ki kema,babu mai tuhumarki akansu,Yaran da yanzu ba'asan ma inda suke ba,"    "Mommy!dama tunanin da kuke kenan?shiyasa baku damu ba,ko kaɗan"   ""Kwarai kuwa akan me zamu damu"? Hannu hafsat tasa tare da dafe kanta,tana faɗin"Ya salam!Wlh Mommy idan mafarki kike toh ki farka!domin kuwa jahad da hosana suna acikin Gidan nan!babu inda suka je!!   Wani irin bugu zuciyar Aunty babba tayi ji kake daraam,a ruɗe tace"Kamar ya kenan"?   "Mommy Jahad da hosana suna nan!Yanzu haka daga bedroom ɗinsu nake,naje ne domin in nemi yafiyarsu akan laifin da muka aikata masu,"   Saboda tsabar tashin hankali har suna haɗa baki Ita da hayaam wurin cewa"Jahad da hosana suna acikin gidan nan!!!"   Jinjina kai Hafsat tayi kafin ta ɗaura da cewar"mun shiga uku mommy,mun ja ma kanmu bala'e da masifa!Ashe Ya Omar shine ya taimake su hosana acikin gidan Gonar mutumin nan,kuma a dai dai lokacin da yake ƙoƙarin yin raping ɗin hosana!   Hannu Aunty babba ta aza aka tana fadin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"   Hayaam kuwa sai faman zazzare ido take,   "Mommy,bugu da ƙari,a nan wurin Ya Omar ya tarwatsa kan mutumin nan ya mutu har Lahira,"tunkan hafsat ta ƙarasa maganar Aunty babba ta saukko daga saman gadon,hannayenta asaman kanta take fadin"Nashiga ukuna,Na bani na lalace,na ru6e!hafsat dan Allah ki faɗamun gaskiya,!dagaske baba alamu ya mutu!kuma Omar ne ya kashe shi saboda su Hosana!ashe shiyasa kenan naita neman number wayansa daga baya ban samu,wannan wata irin masifa ce!,    Zarya tashiga yi acikin ɗakin tana faman cizon yatsa,Hayaam tace"Aunty laila don Allah ki kwantar da hanlinki...."   Hankali tashe Aunty babba tace"taya zaki ce in kwantar da hankalina?bayan ga kashi cike a wandona,ni bansan wani irin hukunci Omar zai yanke mun ba" tana magana zufa na gangarowa a fuskarta,   Ita kanta hayaam,duk a tsorace take duk da ba ita ta aikata laifin ba,amma ta razana da jin cewar Omar ya kashe mutumin da Aunty babba tasa ya zubar mata da yaran,   "Yanzu hafsat menene mafita"!tayi maganar muryarta tamkar zata fashe da kuka,   Kafin hafsat tace wani abu hayaam ta rigata cewa"Ni ina ganin kawai Aunty laila,ku tattara kawai kubar gidan nan ke da hafsat,"   Wani irin kallon rainin wayau hafsat tayi mata tare da cewa"Mu tattara mubar gidan nan fa kika ce?ke kuma fa?ko kina tunanin cewa In asirin mu ya tonu,ke bazai shafe ki bane?tun wuri kusan inda dare yayi maku ke da Mommy!saboda kune baku da alaƙa da gidan nan!Ni kuwa ba inda zanje saboda nasan cewa duk hukuncin da daddy zai yanke mun bazai ta6a korata ba a gidan nan,saboda Ni ƴarsa ce,nan kuma gidan kakana ne,"   Zuru zuru hayaam tayi jin abunda Hafsat tace,Aunty babba kuwa batasan ma me suke magana akai ba,saboda kanta ya ɗau chargy,sae faman zagaye ɗakin takeyi,ta rasa inda zata tsoma ranta taji daɗi,    "Wlh da nasan yaran nan suna acikin gidan nan,da tun jiya da daddare zanbi dare,in taushe masu hanci da pillow har sai sun bar duniya don ubansu,yara sun zame man bala'e!"   Girgiza kai hafsat tayi tana kallonta,har yanzu dae babu alamun dana sani atattare da ita,   "Tunda nake ban ta6a shiga tashin hankali ba arayuwata sai akan waɗannan yaran!komai nasa agaba sai naci nasara akanshi,amma waɗannan tsinannun yaran sun tarwatsa mun duk wani plan ɗina,Ba kowa nafi jin haushi ba,face Ubansu,duk shine silar daya auri uwarsu a 6oye harta haifo mana mugun abu,Allah danasan da zaman yaran tun suna cikin ciki zansa a markaɗe munsu,don karsu duniya,'   "Mommy dan Allah kidaina wannan soki burutsin!kin ishemu da surutu kamar wata zautacciya,duk waye ya jefa mu cikin halin nan in ba ke ba?maimakon ma kiyi tunanin sama mana mafita,Sai wasu sambatu kike marasa kan gado,ni bazan iya jurar jin waɗannan munanen kalaman da kike jifar su jahad dashi ba,inaso ki sani su ɗin ƴan uwana ne,"   Juyowa Aunty babba tayi tamkar zata rufe hafsat da bugu,"Don Ubanki Har ni zaki faɗama cewar ƴan uwanki ne!sun fini kusanci dake ne?Ko ciki ɗaya kuka fito tare dasu ne?   "Wlh mommy da ace ciki ɗaya na fito dasu dana fi kowa farin ciki,tun daga kan halayansu da ɗabi'unsu zai tabbatar maka da cewar mahaifiyarsu ta basu tarbiyyar daya dace,kuma ita mai kyakkyawar zuciyace shiyasa ƴa'ƴanta ma suka kasance masu kamar yadda take,Ni ce dai nayi babbar asara,dana fito daga jikin ki!gashi nan yanzu sai danasani nake....."kasa ƙarasa maganar tayi,a hanzarce ta watsa da gudu tabar ɗakin,saboda yadda taga Aunty babba ta tunkarota azafafe,yadda ranta ya 6aci ɗinnan komai zata iya aikatawa, ƙafafunta ne suka fara yi mata raɗaɗi ba arziƙi ta koma daga gefen gadon ta zauna,idanunta sunyi jawur saboda tsabar 6acin rai,zuciyarta sae faman tafarfasa takeyi mata,tamkar zata fasa ƙirjinta ta fito waje,zama hayaam tayi daga gefenta,kowannansu yayi zuru zuru,   "Aunty laila!ni ina ganin kawai ki gudu batare da sanin kowa ba,in ba haka ba,inajiye maki tsoron abunda zai biyo baya,"    Cike da takaici Aunty babba tace"Hayaam naso ace hada Amani muka aikata wannan laifin,saboda banaso taci galaba akaina,yanzu in ishaq ya sake ni,ni kaɗae zanyi zawarci na,bakowa nafi jin haushi ba face hosana!mahaukaciyar banza,ina zaman zamana lafiya na,ta nemi tozarta ni agaban kannen mijina,wlh in har ta tona mun asiri,ni kuma sai nayi silar mutuwarta!!!!!!!!!!!!!!   "Dan Allah Aunty laila kidaina kira mana mutuwa,muji da abunda ke damun mu,duk yadda za'ae yanzu kada ki bari kuyi arba da hosana ɗin, yunwa nata cinsu,amma saboda gudun haɗuwarta da Omar ko Ishaq,yasa ta gaza ko ɗan leƙawa waje, Bayan fitar Hafsat tashi suka yi suka zura Hijabs ajikinsu,sannan suka fito atare suka nufi ɗakin daddynsu,kamar yadda Sehrish ta basu shawarar su je su gaishe da daddynsu da Ammi da su hajiya Azeema, Abusufyan na kwance saman gadonshi yaji ana knocking door ɗin ɗakinsa,miƙewa yayi tare da ajiye wayar hannunshi saman side drawer,ƙarasawa yayi yasa hannu ya buɗe ƙopar,zuba masu ido yayi yana kallonsu,sam baiyi tsammanin zai gansu ba,abun ba ƙaramin burgeshi yayi ba sunsha hijabai ajikinsu,sae faman murmushi suke sakar mashi,   "My triplets"ya ambaci hakan tare da basu hanya don su shiga ciki,rufe ƙopar yayi bayan sun shiga daga ciki,   Saman gadonshi hosana ta haye,jahad da sehrish kuwa a ƙasa suka lankwashe ƙafafunsu suka zauna,   Wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana kallonsu,   "Ina kwana daddy,an tashi lafiya," Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Lafiya lou my daughters,Nayi mamakin ganinku,waye acikinku ya bada shawarar azo agaishe ni ne"?yayi maganar yana kallon fuskokinsu, Jahad ce ta nuna sehrish da hannu,   "Kinyi tunani mai kyau,dama yanzu nake shirin zuwa in taso ku,don muje ku gaishe da Modibbo,da Ammi da sauransu,abunda ya dace ne,kullum da safe ku dinga zuwa kuna gaishe dasu,"   Atare suka haɗa baki wurin cewa"In shaa Allah zamuyi hakan daddy,"   Juyawa yayi tare da kallon hosana dake kwance,hada rufe ido tana minsharin ƙarya,don yayi tunanin cewa bacci ne ya ɗauke ta,   Hannu yasa tare da jan kumatunta,nan take ta fashe da dariya,shima dariyar yayi kafin daga bisani,yace"ku tashi mu tafi ɗakin Ammin atare don ku gaisar da ita, Saukowa hosana tayi daga saman gadon,ya ruqo hannunta dana jahad,suka jera tare suka fuce, Suna tsaye a ƙopar ɗakin Ammi,sae ga Junaid,yana hangosu ya shiga sakin murmushin nan nashi,jiki na rawa ya nufi wurinsu,Gaisar da Abusufyan ya fara yi"Gm Uncle,"cike da zolaya Abusufyan yace"a haka zan baka auren ƴa ta?kana gaisar dani daga tsaye sai kace wani tsaranka ba wani respect"?jin haka yasa junaid saurin duƙawa ƙasa,sannan yace"Ina kwana Uncle"? Dariya su kayi gaba ɗayansu,ganin yadda ya zuƙunna,   "Lafiya lou in law ɗina,ko kaifa,miƙe tsaye toh tunda ka ƙaraso sae mu shiga ciki atare,"mikewa yayi fuskarshi a washe,duk a tunanin Abusufyan junaid wasa yake yi masa yawan zancen zai bashi auren ɗaya daga cikinsu,baisan dagaske shi kamu yake yi ba da sallama a bakunansu suka shiga cikin ɗakin,koda ammi taji muryoyinsu,da sauri ta kashe tabar da take zuƙa,ta sanya ta acikin Ashtray dake ajiye ƙasa,da ƙafarta ta tura shi ƙarƙashin gado,duk akan idon Abusufyan abun yaso ya bashi dariya,lallai Ammi ta kimtsu tunda har ta fara jin kunyar jikokinta su ganta tana zuqar sigari,    A saman carpet,kowannansu ya zauna tare da lankwashe ƙafa,Abusufyan ne ya fara gaisar da ita"Ina kwana Ammi,kun tashi lafiya?Ya gajiyar tafiya"? "Lafiya lou Alhamdulillah,"ta amsa mashi,Sannan su Jahad suka haɗa baki wurin miƙa gaisuwarsu,da murmushi a fuskarta ta shiga amsa masu ɗaya bayan ɗaya,a ƙarshe ta tsayar da idanunta kan Hosana tace"Kin tashi lafiya"?   Murmushi hosana ta saki tana faman noƙe kai tace"lafiya lou,"       Janye idonta tayi daga kan hosana ta mayar dashi kan junaid tace"Sarkin Murmushi,Angona nakaina naga kayi kyau sosai ka kuma ƙara haske,faɗamun menene sirrin"?   "Kishiya zanyi maki ne"yayi maganar yana murmura mata ido,ɗan waro ido waje tayi tare da cewa"Wacece ita"?   ɗagowa yayi yana kallonsu,Sehrish har sai da ya gano jahad sannan ya nuna ta da hannu yace"Gatanan,"   Ammi tace"Kin shirya yin kishi dani ko"?   Girgiza kai jahad ta shiga yi alamar a'a,   "To kaji bazata iya kishi dani ba,sai ka haƙura da auren gaba ɗaya,don ni bazan zauna da kishiya ba,"   "A'a wlh Ammi sai dai ki haƙura dani in aurota," Yadda yayi maganar ba ƙaramin dariya ya basu ba,don har saida suka dara, Ammi tace"wato Ni zaka juya ma baya ko?saboda ka samu zankaɗeɗiyar budurwa sabuwa gal cikin leda,Ni kuma nayi maka tsufa,"gyaɗa kai tayi tare da cewa"bakomai na haƙura,"   Murmushi suka saki gaba ɗayansu,mayar da idonta tayi kan Abusufyan"Yanzu ya ake ciki game da zancen Mahaifiyar yaran nan"?   Jin an sako zancen abu yasa shi gyara zama,sannan yace"Muna nan muna shirya waɗanda zasu je kano domin binciko gidan da suka zauna acikinsa,saboda muna sa ran zamu samu wasu muhimman bayanai a wurin makwabtansu,"   Jinjina kai Ammi tayi"hakan yayi kyau,banason a tsaya 6ata lokaci nafi son ayi komai tun da wuri don ba'a san halin da take ciki ba,"   "In sha Allah zamuyi hakan,daga nan suka miƙe tare da yi mata sallama suka wuce ɗakin Modibbo,ba ƙaramin daɗi yaji ba daya gansu,sun jima a wurinshi,kafin daga bisani suka wuce ɗakin gwaggon katsina,sun sha barkwanci a wurinta,daƙyar suka samu tabarsu suka fito,ɗakin hajiya azeema suka wuce,sun jima a wurinta suna shan fira,ɗaya bayan ɗaya haka suka dinga bin ɗakunansu kafin daga bisani,Lokacin yin breakfast yayi suka hallara gaba ɗayansu a dining,kowa saida yazo banda Sgr,saboda yasa ma ranshi cewar za'a kawo mashi ne har part ɗinsa,Azmee ce takai mashi,saboda Sehrish ta sanar da ita cewar,bazata samu damar kai mashi ba,tana so tabi Umarnin mahaifinta ne, Lokacin da Azmee ta shiga part ɗinsa,yana daga kishingiɗe saman Sofa mai mazaunin mutun ukku,jikinshi na sanye da jallabiya,shigowa ciki tayi gabanta na faɗuwa don tasan cewa dole ya tuhumeta akan me ya hana sehrish zuwa,lalla6awa tayi ta ajiye masa tray ɗin a asaman table,gudun karya tuhumeta yasa tayi saurin ja da baya zata gudu tabar ɗakin,har takai baƙin ƙopar ɗakin tajiyo muryarshi yana fadin"ke zo nan,"dakatawa tayi da tafiyar hannunta dafe da saitin zuciyarta,jiki asanyaye ta dawo ta tsaya agabanshi,kwata kwata idanunshi na a lumshe,wayarshi na ajiye asaman wide chest ɗinsa,   dakyar ta iya cewa gani yalla6ai, "Bana ce kar na sake ganinki a part ɗina ba da sunan aiki?ko bata faɗa maki bane"?   Shiru azmee tayi,tana faman zazzare ido,ranta ne ya bata cewar kawai ta sanar dashi gaskiyar zance, Don haka tace"Sehrish ta sanar dani cewar bazata ƙara aiki a part ɗin ka ba...."tunkan ta ƙarasa maganar ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu,nan take azmee tasha jinin jikinta,   "Ita da bakin ta,ta faɗi hakan"? Muryarta na kerma tace"Eh,   Ya kuma cewa"ta faɗa maki dalilin yin hakan"? "Eh,tace tana son bin Umarnin mahaifinta ne,"    ɗan ciza gefen la66ansa yayi tare da cewa"its Okey,just leave........" da sauri azmee ta juya tare da kama hanya ta fuce daga part ɗin nasa, Wuraren ƙarfe goma sha biyu modibbo ya shirya tafiya,Kanal yousouf ne tare dasu Irfan suka kai shi har Airpot ya hau jirgi, Yinin Ranar Aunty babba na ƙumshe a cikin ɗakin Hayaam,tsoro ya hanata fitowa waje,da yunwa ta addabe ta Hayaam ce ta ɗebo mata abinci ta kawo mata a ɗakin,hosana kuwa kar take dasu,don taci alwashin sai ta tona masu asiri wurin daddynsu,da kuma Ya omar, Hankalin sehrish ba ƙaramin kwanciya yayi ba,jin Cewa sgr bai nemeta ba,duk da ta damu akan son ganinshi,jurewa kawai takeyi, A ranar Talal Da captain najeeb suka ƙaraso,murna a wurin ƴan uwansu kamar zasu haɗiye su don farin ciki,musamman junaid daya kasance rival ɗinsa ne ya dawo wato Talal,da yake shima autane a ɗakinsu Omar, After 1 day *Boss Bature* Around 2:00 pm, Zaune take a hakimce saman 2 seater,jikinta na sanye da turkish dress Riga da wando,a launin fata fara ce amma hasken nata hada na bleaching tayi 6au sosai,babbar mace ce a ƙalla zata kai shekara 35,gaba ɗaya idanunta na akan plasma tv din da take kallo aciki,yayin da hannunta ke ɗauke da cup na coffee,lokaci bayan lokaci take kur6asa,ta aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,wuyan kafarta na sanye da ziririyar sarƙa,sai faman karkaɗa kafar takeyi,Tana da manyan idanu dara dara,ga dogon hanci wanda ke manne da nose ring,kai kana ganinta zaka san cewar cikakkiyar ƴar bariki ce, Jin ringing din wayarta dake ajiye asaman hannun kujerar da take ne yasa ta Ajiye cup din hannunta asaman madaidaicin table din dake a kusa da ita,sannan tasa hannu ta dauki wayar,hidden number ce aka kirata da ita,picking call ɗin tayi ta kanga wayar a kunnanta,cikin harshen fulatanci take magana, Tana cikin yin wayar taga inuwar mutun tsaye akanta,ɗagowa tayi a hankali don taga wanene,sauke ajiyar zuciya tayi ganin Amrish ce,jikinta na sanye da uniform,ta goya school bag dinta a abayanta,dawowarta kenan daga school,fuskarta a ɗaure kwata kwata babu annuri acikinta, Rejecting call ɗin tayi tare da ajiye wayar asaman sofa din,sannan ta mayar da hankalinta sosai akan Amrish,   "Welcome back my daughter,Am really glad to see u,"   Tayi maganar tana buɗe mata hannunwanta don tazo ta rungume ta,rai a6ace tace"Mommy na tsani ganinki wlh,banason ki,saboda baki da halin kirki,so kike ki kashe mun rayuwata da hannunki,"tana maganar hawaye na gangarowa akan fuskarta,   Maimakon ta nuna damuwarta akan hakan sai ma ɗan ta6e la66anta tare da cewa"Kamar yadda baki so na,Nima haka bana son ki,donni a tsarin rayuwata ban shirya haihuwa ba saboda bana son ƴa'ƴa don su takura ne,na samu cikinki batare dana shirya ba,babu yadda banyi ba don na zubar da cikin,amma ya liƙe ya nace sai ya zauna a mahaifata,a ƙarshe nayi deciding zuwa ƙasar waje a markaɗe mun shi,mahaifinki ya hana hakan,nayi takaici a wannan lokacin kamar nayi suicide,"   Hankalin Amrish ba ƙaramin tashi yayi ba,jin abunda mahaifiyarta ke faɗi da bakinta,tuni wasu zafafan hawaye suka shiga wankowa a saman fuskarta,cikin shessheƙar kuka tace"ki faɗamun!Su wanene iyaye na!don ina da tabbacin cewar bake kika haife ni ba,"   Fashewa da dariya matar tayi yayin da take karkaɗa kafafunta, Jin tayi banza da ita yasa ta daka mata tsawa tare da cewa"Mommy ki faɗamun su wanene iyaye na?In ba haka ba zan je na kashe kaina!" Yunkurawa mommyn tayi tare da mikewa tsaye ta daddage ta kifa ma Amrish mari tare da cewa"Sai me idan kin kashe kanki!?wa kikayi ma asara!shashasha kawai," Fashewa da kuka Amrish tayi yayin da zuciyarta ke tafarfasa tace"Mommy yau ke da kanki kika mare ni"? Dogon tsoki taja tare da cewa"Har kashe ki ma zan iyayi,Saboda kinyi mun tsawa,ko iyayena da suka haife ni basu ta6a gigin daka mun tsawa ba,balle ke ƴar dana haifa,idiot" Ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta ɗauki wayarta,sannan tabar falon tana fadin"kafin gobe in samu gawarki dan Allah,"tayi maganar cikin halin ko in kula, Da gudu Amrish ta watsa,izuwa bedroom dinta dake a upstairs,datse ƙopar ɗakin tayi,bayan tayi wurgi da school bag dinta,ta shiga neman igiyar da zata shaƙe kanta don ta mutu,ganin bata samu ba yasa ta buɗe kopar ɗakin,ta fita,bada jimawa ba sai gata ta dawo cikin ɗakin hannunta dauke da insect powder,buɗe murfin tayi da sauri sauri ta daga robar tare da zazzagawa acikin bakinta, Mommyn na acikin bedroom ɗinta,ta jiyo wata irin razananniyar ƙara mai rikitarwa,sakin wayar dake hannunta tayi,da gudun gaske ta fito daga bedroom ɗinta dake a downstairs,tamkar za tayi tuntu6e ta fadi kasa haka take gudun,lokacin da ta ƙarasa bedroom din Amrish,hannu tasa ta dinga bubbuga ƙopar tana faɗin"AMRISH!AMRISH!!baki da hankali ne,bakisan wasa ba,me kika aikatawa kanki!ba zaki zo ki buɗe mun ƙopa ba!!Amrish gaba daya duk tabi ta rikice, Shiru amrish bata buɗe mata ƙopar ba,hakan yasa ta dawowa wurin window ɗin ɗakin ta buɗe ta don ta gane ma idonta, A gigice ta fasa uwar ƙara tare da aza hannyenta asaman kanta tana fadin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!na shiga uku!!!!zubewa tayi ƙasa saman guiwowinta tana faman zabga kuka,hawaye jaga jaga a fuskarta,tana cikin wannan yanayin,taji shigowarsu Zeenat da sofia ƙawayen Amrish cikin falon gidan,mikewa tayi da sauri har tana tuntu6e ta saukko downstairs,tunkararsu tayi tana fadin"Nashiga uku!!Amrish ta kashe kanta!!bansan ya zanyi da rayuwata ba!! Kallon juna sukayi hankalinsu a matukar tashe suka haɗa baki wurin cewa"Am...Amrish!!meya faru da ita!taya akai ta kashe kanta!!! Kasa bude baki tayi don tayi masu magana,da hannu ta dinga nuna masu bedroom ɗinta,nan suka gane cewar tana acikin ɗakinta,da gudu suka nufi upstairs ɗin,itama tabi bayansu,nan fa suka shiga ƙoƙarin 6alle ƙopar ɗakin nata,         *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Saman Gadon ta haye ta kwanta tare da jan bargo ta lullu6e,zuciyarta cike da wani irin farin ciki,sai faman sakin kayataccen murmushi take,daƙyar bacci 6arawo yayi awon gaba da ita,? Wuraren sallar asuba,jahad ta farka tare da tashin su hosana,atare bayan sunyi alwala su kayi salla,bayan sun kammala suka koma saman gadon suka dasa wani sabon baccin don bai ishe su ba, Ƙarasowa hafsat tayi ƙopar bedroom ɗin nasu,jikinta sanye da dogon hijabi,hannu tasa ta ɗan bubbuga ƙopar ɗakin,shiru ba'a buɗe ba,ƙara bugawa tayi,bugun ya isa cikin kunnan sehrish,cikin bacci tace"Wanene"? Hafsat tace"Ni ce," "Kece wa"? Sehrish ta tambaya a yayin da ta miƙe tare da tunkarar ƙopar ta buɗe,Tun daga ƙasa har sama sehrish ke bin ta da kallo don batasan wacece ita ba,amma tabbas ta ta6a ganin fuskarta,kuma jiya taga gifcinta acikin gidan,ga kuma kamannin fuskar Yaya ishaq a fuskarta,   ƴan kame kame hafsat ta shiga yi,muryarta na inda inda tace"am...um..jahad.." katse ta sehrish tayi da cewa"ba ita bace,Ni sunana sehrish,jahad tana ciki tana bacci,"   "In ba damuwa inason ganinta," Matsa mata hanya sehrish tayi,ta shiga cikin ɗakin nasu,rufe ƙopar sehrish tayi sannan ta koma ciki itama,sae faman kallon kallo suke ita da hafsat,duk tabi ta kama kanta,kana ganin fuskarta zaka fahimci cewar bata da gaskiya,   Wuri ta samu gefen gadonsu ta zauna,idanunta na akan su jahad da hosana dake ta sharar bacci,   Muryarta a sanyaye tace"in ba damuwa,dan Allah ki tashe su daga baccin inason yin wata magana dasu mai mahimmanci,"   Batare da musu ba,Sehrish tace toh,sannan ta haye saman gadon tana ambatan sunayensu,gami da bubbuga ƙafafuwansu"jahad!hosana!ku tashi ana son ganinku,"   cikin bacci hosana ta buga tsoki tana fadin"dan Allah a ƙyale ni,kar a takuramin,"   Jahad kuwa tuni ta farka,tana faman mutsustsuka idanuwanta,wurga idanunta tayi kan sehrish tace"Wai lafiya"?   "Wannan ce ke son magana daku,"tayi maganar tana nuna hafsat dake zaune,   Juyawa jahad tayi tana kallonta,cike da mamaki ta ambaci sunanta"Aunty hafsat!" sunnar dakai ƙasa hafsat tayi,fuskarta dauke da matsananciyar damuwa,daƙyar ta iya amsa mata"Na'am jahad,"tashi zaune jahad tayi,suna fuskantar juna ta sake ambatar sunanta"Aunty hafsat,"   "Kinsanta ne"? Sehrish ce tayi tambayar,jahad tace"Niko na santa,itace ɗiyar wannan matar da nake faɗa maki wadda ta azabtar da rayuwarmu,kuma wannan itace ta ɗauke mu acikin motarta,ni da Hosana ta kai mu hannun wannan mugun mutumin wanda ya kai mu daji har yayi ƙoƙarin cutar da Hosana,"   Jin wannan maganar yasa ran sehrish ya 6aci,harara ta wurga ma hafsat tare da nuna mata hanyar fita daga ɗakin tace"Dan Allah malama tashi ki fita ki bamu wuri!bamu son ganinki!mugaye kawai Azzalumai,kun cutar da rayuwar ƴan uwana,saboda son zuciya irin naku,basuyi maku laifin komai ba,Amma kuka tsangwamesu,saboda kunga basu da gata,Insha Allah sai kunga sakayyar da Allah zaiyi masu,kuma sai kun ɗanɗana irin uƙubar da kukayi masu,"   Hawaye ne suka shiga zarya a fuskar hafsat,dama saida ranta ya bata cewar dakyar ne su yafe mata,   Janye idanunta tayi daga kan sehrish ta mayar dasu kan Jahad,cikin shessheƙar kuka tace"dan Allah ku yafe mun Jahad,nasan mun cutar daku,amma inaso ku sani bada son raina ba,na kaiku wurin wannan mutumin,Mommy ce ta sanar dani cewa Gidan marayu za'a kaiku,shiyasa har na ɗauke ku,kuma nayi hakan ne saboda tsoran karta halakar daku acikin gidan nan don ba yadda banyi ba akan ta kyale ku amman ta kiya,shiyasa ma na amince da akaiku gidan marayun ashe zubar daku tasa ayi,'   "Ba zamu ta6a yarda da kalamanki ba,saboda tun farko baki nuna kina son mu zauna acikin gidan ba,ke da mommynki,shiyasa kuka haɗa baki ke da ita,kika fara yaudararmu kina nuna kamar kina son mu ashe,so kuke ku fitar damu daga cikin gidan,saboda rashin Imani Aunty hafsat kika damƙa mu a hannun wannan mutumin,to bari kiji Ya Omar ya kashe shi har lahira!!   Gabanta ne ya faɗi rassss!hankalinta yayi mugun tashi,a kiɗime tace"Ya kashe shi!"   Jahad tace"kwarai kuwa Ya Omar shi ne ya kama shi da hannun shi acikin gidan gonarsa,lokacin da yake ƙoƙarin keta haddin hosana,aikuwa ya fasa mashi kai,anan wurin ya zama gawa,'     Tana kai ƙarshen maganarta sehrish ta ɗaura da cewar"tun yanzu kwara kusan inda dare yayi maku!don wlh Ya Omar bazai sassauta maku ba!muddin yaji cewar kune kukayi silar da har wannan mutumin ya ɗauki su jahad ya kaisu daji,sannan ku fara tunanin irin hukuncin da kuma zaku fuskanta a wurinshi!"   Wani irin wahalallan yawu hafsat ta haɗiya,tsananin tsoro ne ya bayyana akan fuskarta,ba don komai ba sai don jin cewa An kashe mutumin nan!tun da har Omar zai iya kashe rai akan su hosana,tabbas ba ƙaramin so yake masu ba,kuma akansu zai iya hukunta kowa,yanzu su menene sakamakonsu?   "Baku da wata mafita,shawara nake baku tun kafin hosana tayi maku tonan asiri,kwara kusan abunyi,don tace saita sanar ma Daddy da Ya Omar abunda kukayi mana!" jahad ce tayi maganar,   Gaba ɗaya duk sun bi sun tsoratar da ita,la66anta har kerma suke wurin rokonsu tana cewa"Dan Allah ku yafe mun,wlh nayi dana sanin duk wani abu da mu kayi maku,har ga Allah ni bada sanina ba,mommy ce ta shirya duk wannan,Allah shine shaidata,bazan yi maku ƙarya ba,"sosai hafsat ke kuka, Ruko hannun jahad tayi acikin nata tana fadin"jahad nasan kina da sauƙin kai,dan Allah ki yafe mun,wlh nayi nadamar abunda mu kayi maku ni da mommyna,nasan naƙi ku da farko amma daga baya naso ku sosai,kuma nayi kukan rashinku atare dani,lokacin da nagane cewa Mommy ba gidan marayu tasa akaiku ba,har faɗa sai da mu kayi da ita,ko isasshen bacci bana samu a lokacin saboda tunanin wani hali kuke ciki......"ƙarasa maganar tayi tare da sanya hannu tana share hawayen dake zuba a kan fuskarta,   Shiru su kayi da alama jikinsu ya ɗanyi sanyi,Sehrish tace"Jahad,idan kinyi niyya ki yafe mata,'jinjina kai jahad tayi tare da cewa"Ni dama ban ruƙe ki araina ba Aunty hafsat,na yafe maki Allah ya yafe mana gaba ɗaya,"   Amsawa tayi da "Amin,sannan tace"Hosana fa?dan Allah ku tashe ta inaso in nemi yafiyarta,"   Hannu Sehrish takai tare da bubbuga ƙafarta,farkawa hosana tayi,idanunta sunyi suntum saboda bacci,   "Hosana ki tashi,ga Aunty hafsat nan tana son magana dake,"jin an ambaci sunan Aunty hafsat yasa ta wartsakewa ta miƙe daga zaune,koda idanunta su kayi arba da fuskar hafsat,nan take ta murtuke fuska rai a6ace tace"Ni bana son ganinta,na tsaneta kamar yadda suka tsane mu ita da Mommynta,Aunty hafsat muguwace bata tsoron Allah,itace takai mu wurin wannan mummunan mutumin wanda yakusa kashe ....."katse ta jahad tayi da cewa"pls hosana just forget about the past,forgive her pls,Aunty hafsat tayi nadama,kuma bada son ranta ba ta kaimu wurin mutumin nan ba,Mommynta ce ta shirya wannan,"   Maƙe kafaɗa hosana tayi alamar bata yarda ba,harara ta wurga ma hafsat ɗin tana murguɗa mata baki tace"Allah saina faɗama Ya Omar da daddy,ko kukan jini zatayi sai dai tayi,amma saina faɗa,saboda rashin Imani kamar wasu dabbobi haka kuka rufe mu acikin store babu abinci ga ƙishin ruwa,ko iska babu,amma ko ajikin ku mu rayu ko mu mutu wannan ba matsalarku bace,zafi kamar zai kashe mu,adaren ranar da muka kwana a store,ba don jahad tayi mun fifita ba da Allah kaɗae yasan me zai biyo baya don rashin imani ku kuna can kuna shan A.c,wlh saina faɗama daddy....."fashewa hosana tayi da kuka,hada bubbuga ƙafarta,daga gani abun ba ƙaramin ciwo yake yi mata ba,ya tsaya mata arai,   Gaba ɗaya jikinsu yayi wani irin sanyi,musamman hafsat,duk yadda taso ta shawo kanta amma abun yaci tura,hosana ta rantse ta maya akan cewar saita faɗa ma Ya Omar,hatta jahad sai da taso ta lallasheta,amma ina ƙarshe sai ta dinga ƙoƙarin bugun jahad din,   Ganin haka yasa sehrish kallon hafsat tare da cewa"dan Allah kiyi haƙuri ki tafi kawai,hosana batasan ganinki,idan tana kallonki haukanta zai iya tashi,"     Jiki asanyaye Hafsat ta mike,tana tafiya tana waiwayonsu yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,a haka har ta isa ƙopar ɗakin ta buɗe ta fuce da gudu tana kuka,   Hannu Sehrish tasa tare da janyo hosana ta rungumeta sosai ajikinta tana lallashinta,da ƙyar ta samu hosana tayi shiru,sai faman sauke ajiyar zuciya take yi,komawa su kayi suka kwanta kowa da abunda yake saƙawa aranshi, *Aunty Babba* Suna kwance ita da hayaam sai faman sharar bacci sukeyi suna jan minshari yadda kasan bijimayen sa,sun cika gadon su biyu kawai,babu wanda ya farka acikinsu balle suyi tunanin yin sallar asuba,can cikin bacci Hayaam ta dinga jin ana bugun ƙopar ɗakin nasu tamkar za'a balle ta,dogon tsoki taja tana faman yatsina fuska alamar an takurata,a ƙule tace"Wai dallah wanene ke buga ƙopar ɗakin nan"!?   Muryar hafsat tajiyo daga waje cikin shessheƙar kuka tace"Ni ce,ki zo ki buɗe mun ƙopa,"   Jiki na rawa hayaam ta saukko daga saman gadon ta ƙarasa tare da buɗe ƙopar,gabanta ba ƙaramin faduwa yayi ba ganin fuskar hafsat sharkaf da hawaye,hankali atashe tace"Meya faru ne kike kuka"?   A tsiwace hafsat tace"Ba dole inyi kuka ba!kun jefani cikin masifa!ki bani hanya na wuce,Da Mommy nake so inyi magana,"tana faɗin hakan ta bangaje hayaam tare da wuce wa ciki,duk tabi ta ruɗe,wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare ma hafsat maƙoshinta,lokacin da tayi arba da Aunty babba,baje saman gadon tana sharar bacci,wato hankalinta kwance ita,batasan wainar da ake toyawa ba,   Da karfi ta ambaci sunanta"Mommy!Mommyyyyyyyy!   A firgice Aunty babba ta farka,agigice ta tashi zaune tana faɗin"Lafiya hafsat kike mun irin wannan kiran"?   "Ina fa lafiya mommy!ashe ke kina nan kina sharar bacci,ni kin barni cikin tashin hankali,jiya ko isasshen bacci ban samu ba,saboda tunanin hukuncin da Ya Omar da daddy zasu yanke mana..."   Jin wannan maganar yasa Aunty babba fashewa da dariya tana tafa hannu,   Hakan ba ƙaramin fusata hafsat yayi ba,muryarta na rawa tace"Mom...my dariya ma kike yi"? Aunty babba tace"to me kikeso inyi in banda dariya,ke bakisan meya faru ba jiya"?   Zuba mata ido hafsat tayi tana kallonta,   "Hayaam zo ki faɗa mata da alama batasan meya faru ba,ae mu yanzu bamu da sauran damuwa,hankalinmu a  kwance yake kamar muna cikin jirgi gobara ta kama," tana magana tana faman washe baki,   Ƙarasowa inda hafsat take a tsaye,hayaam tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli hafsat tare da cewa"ke bakisan cewa jiya Ammi ta kori su Jahad daga gidan nan ba?korar ma korar wulaƙanci,ae shiyasa kika ga mun saki baki muna bacci hankalinmu kwance,saboda bamu da sauran damuwa yanzu,"   Wani irin kallo hafsat ta wurga mata tare da cewa"Amma dae a mafarki hakan ya faru ko"?   Aunty babba tace"Wani mafarki,jiya agabanmu Ammi ta korasu,da gudu suka fita daga gidan nan suna kuka,"   Tsabar takaici ya hana hafsat cewa komai,     Hayaam tace"Ae kawai ki kwantar da hankalin ki kema,babu mai tuhumarki akansu,Yaran da yanzu ba'asan ma inda suke ba,"    "Mommy!dama tunanin da kuke kenan?shiyasa baku damu ba,ko kaɗan"   ""Kwarai kuwa akan me zamu damu"? Hannu hafsat tasa tare da dafe kanta,tana faɗin"Ya salam!Wlh Mommy idan mafarki kike toh ki farka!domin kuwa jahad da hosana suna acikin Gidan nan!babu inda suka je!!   Wani irin bugu zuciyar Aunty babba tayi ji kake daraam,a ruɗe tace"Kamar ya kenan"?   "Mommy Jahad da hosana suna nan!Yanzu haka daga bedroom ɗinsu nake,naje ne domin in nemi yafiyarsu akan laifin da muka aikata masu,"   Saboda tsabar tashin hankali har suna haɗa baki Ita da hayaam wurin cewa"Jahad da hosana suna acikin gidan nan!!!"   Jinjina kai Hafsat tayi kafin ta ɗaura da cewar"mun shiga uku mommy,mun ja ma kanmu bala'e da masifa!Ashe Ya Omar shine ya taimake su hosana acikin gidan Gonar mutumin nan,kuma a dai dai lokacin da yake ƙoƙarin yin raping ɗin hosana!   Hannu Aunty babba ta aza aka tana fadin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"   Hayaam kuwa sai faman zazzare ido take,   "Mommy,bugu da ƙari,a nan wurin Ya Omar ya tarwatsa kan mutumin nan ya mutu har Lahira,"tunkan hafsat ta ƙarasa maganar Aunty babba ta saukko daga saman gadon,hannayenta asaman kanta take fadin"Nashiga ukuna,Na bani na lalace,na ru6e!hafsat dan Allah ki faɗamun gaskiya,!dagaske baba alamu ya mutu!kuma Omar ne ya kashe shi saboda su Hosana!ashe shiyasa kenan naita neman number wayansa daga baya ban samu,wannan wata irin masifa ce!,    Zarya tashiga yi acikin ɗakin tana faman cizon yatsa,Hayaam tace"Aunty laila don Allah ki kwantar da hanlinki...."   Hankali tashe Aunty babba tace"taya zaki ce in kwantar da hankalina?bayan ga kashi cike a wandona,ni bansan wani irin hukunci Omar zai yanke mun ba" tana magana zufa na gangarowa a fuskarta,   Ita kanta hayaam,duk a tsorace take duk da ba ita ta aikata laifin ba,amma ta razana da jin cewar Omar ya kashe mutumin da Aunty babba tasa ya zubar mata da yaran,   "Yanzu hafsat menene mafita"!tayi maganar muryarta tamkar zata fashe da kuka,   Kafin hafsat tace wani abu hayaam ta rigata cewa"Ni ina ganin kawai Aunty laila,ku tattara kawai kubar gidan nan ke da hafsat,"   Wani irin kallon rainin wayau hafsat tayi mata tare da cewa"Mu tattara mubar gidan nan fa kika ce?ke kuma fa?ko kina tunanin cewa In asirin mu ya tonu,ke bazai shafe ki bane?tun wuri kusan inda dare yayi maku ke da Mommy!saboda kune baku da alaƙa da gidan nan!Ni kuwa ba inda zanje saboda nasan cewa duk hukuncin da daddy zai yanke mun bazai ta6a korata ba a gidan nan,saboda Ni ƴarsa ce,nan kuma gidan kakana ne,"   Zuru zuru hayaam tayi jin abunda Hafsat tace,Aunty babba kuwa batasan ma me suke magana akai ba,saboda kanta ya ɗau chargy,sae faman zagaye ɗakin takeyi,ta rasa inda zata tsoma ranta taji daɗi,    "Wlh da nasan yaran nan suna acikin gidan nan,da tun jiya da daddare zanbi dare,in taushe masu hanci da pillow har sai sun bar duniya don ubansu,yara sun zame man bala'e!"   Girgiza kai hafsat tayi tana kallonta,har yanzu dae babu alamun dana sani atattare da ita,   "Tunda nake ban ta6a shiga tashin hankali ba arayuwata sai akan waɗannan yaran!komai nasa agaba sai naci nasara akanshi,amma waɗannan tsinannun yaran sun tarwatsa mun duk wani plan ɗina,Ba kowa nafi jin haushi ba,face Ubansu,duk shine silar daya auri uwarsu a 6oye harta haifo mana mugun abu,Allah danasan da zaman yaran tun suna cikin ciki zansa a markaɗe munsu,don karsu duniya,'   "Mommy dan Allah kidaina wannan soki burutsin!kin ishemu da surutu kamar wata zautacciya,duk waye ya jefa mu cikin halin nan in ba ke ba?maimakon ma kiyi tunanin sama mana mafita,Sai wasu sambatu kike marasa kan gado,ni bazan iya jurar jin waɗannan munanen kalaman da kike jifar su jahad dashi ba,inaso ki sani su ɗin ƴan uwana ne,"   Juyowa Aunty babba tayi tamkar zata rufe hafsat da bugu,"Don Ubanki Har ni zaki faɗama cewar ƴan uwanki ne!sun fini kusanci dake ne?Ko ciki ɗaya kuka fito tare dasu ne?   "Wlh mommy da ace ciki ɗaya na fito dasu dana fi kowa farin ciki,tun daga kan halayansu da ɗabi'unsu zai tabbatar maka da cewar mahaifiyarsu ta basu tarbiyyar daya dace,kuma ita mai kyakkyawar zuciyace shiyasa ƴa'ƴanta ma suka kasance masu kamar yadda take,Ni ce dai nayi babbar asara,dana fito daga jikin ki!gashi nan yanzu sai danasani nake....."kasa ƙarasa maganar tayi,a hanzarce ta watsa da gudu tabar ɗakin,saboda yadda taga Aunty babba ta tunkarota azafafe,yadda ranta ya 6aci ɗinnan komai zata iya aikatawa, ƙafafunta ne suka fara yi mata raɗaɗi ba arziƙi ta koma daga gefen gadon ta zauna,idanunta sunyi jawur saboda tsabar 6acin rai,zuciyarta sae faman tafarfasa takeyi mata,tamkar zata fasa ƙirjinta ta fito waje,zama hayaam tayi daga gefenta,kowannansu yayi zuru zuru,   "Aunty laila!ni ina ganin kawai ki gudu batare da sanin kowa ba,in ba haka ba,inajiye maki tsoron abunda zai biyo baya,"    Cike da takaici Aunty babba tace"Hayaam naso ace hada Amani muka aikata wannan laifin,saboda banaso taci galaba akaina,yanzu in ishaq ya sake ni,ni kaɗae zanyi zawarci na,bakowa nafi jin haushi ba face hosana!mahaukaciyar banza,ina zaman zamana lafiya na,ta nemi tozarta ni agaban kannen mijina,wlh in har ta tona mun asiri,ni kuma sai nayi silar mutuwarta!!!!!!!!!!!!!!   "Dan Allah Aunty laila kidaina kira mana mutuwa,muji da abunda ke damun mu,duk yadda za'ae yanzu kada ki bari kuyi arba da hosana ɗin, yunwa nata cinsu,amma saboda gudun haɗuwarta da Omar ko Ishaq,yasa ta gaza ko ɗan leƙawa waje, Bayan fitar Hafsat tashi suka yi suka zura Hijabs ajikinsu,sannan suka fito atare suka nufi ɗakin daddynsu,kamar yadda Sehrish ta basu shawarar su je su gaishe da daddynsu da Ammi da su hajiya Azeema, Abusufyan na kwance saman gadonshi yaji ana knocking door ɗin ɗakinsa,miƙewa yayi tare da ajiye wayar hannunshi saman side drawer,ƙarasawa yayi yasa hannu ya buɗe ƙopar,zuba masu ido yayi yana kallonsu,sam baiyi tsammanin zai gansu ba,abun ba ƙaramin burgeshi yayi ba sunsha hijabai ajikinsu,sae faman murmushi suke sakar mashi,   "My triplets"ya ambaci hakan tare da basu hanya don su shiga ciki,rufe ƙopar yayi bayan sun shiga daga ciki,   Saman gadonshi hosana ta haye,jahad da sehrish kuwa a ƙasa suka lankwashe ƙafafunsu suka zauna,   Wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana kallonsu,   "Ina kwana daddy,an tashi lafiya," Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Lafiya lou my daughters,Nayi mamakin ganinku,waye acikinku ya bada shawarar azo agaishe ni ne"?yayi maganar yana kallon fuskokinsu, Jahad ce ta nuna sehrish da hannu,   "Kinyi tunani mai kyau,dama yanzu nake shirin zuwa in taso ku,don muje ku gaishe da Modibbo,da Ammi da sauransu,abunda ya dace ne,kullum da safe ku dinga zuwa kuna gaishe dasu,"   Atare suka haɗa baki wurin cewa"In shaa Allah zamuyi hakan daddy,"   Juyawa yayi tare da kallon hosana dake kwance,hada rufe ido tana minsharin ƙarya,don yayi tunanin cewa bacci ne ya ɗauke ta,   Hannu yasa tare da jan kumatunta,nan take ta fashe da dariya,shima dariyar yayi kafin daga bisani,yace"ku tashi mu tafi ɗakin Ammin atare don ku gaisar da ita, Saukowa hosana tayi daga saman gadon,ya ruqo hannunta dana jahad,suka jera tare suka fuce, Suna tsaye a ƙopar ɗakin Ammi,sae ga Junaid,yana hangosu ya shiga sakin murmushin nan nashi,jiki na rawa ya nufi wurinsu,Gaisar da Abusufyan ya fara yi"Gm Uncle,"cike da zolaya Abusufyan yace"a haka zan baka auren ƴa ta?kana gaisar dani daga tsaye sai kace wani tsaranka ba wani respect"?jin haka yasa junaid saurin duƙawa ƙasa,sannan yace"Ina kwana Uncle"? Dariya su kayi gaba ɗayansu,ganin yadda ya zuƙunna,   "Lafiya lou in law ɗina,ko kaifa,miƙe tsaye toh tunda ka ƙaraso sae mu shiga ciki atare,"mikewa yayi fuskarshi a washe,duk a tunanin Abusufyan junaid wasa yake yi masa yawan zancen zai bashi auren ɗaya daga cikinsu,baisan dagaske shi kamu yake yi ba da sallama a bakunansu suka shiga cikin ɗakin,koda ammi taji muryoyinsu,da sauri ta kashe tabar da take zuƙa,ta sanya ta acikin Ashtray dake ajiye ƙasa,da ƙafarta ta tura shi ƙarƙashin gado,duk akan idon Abusufyan abun yaso ya bashi dariya,lallai Ammi ta kimtsu tunda har ta fara jin kunyar jikokinta su ganta tana zuqar sigari,    A saman carpet,kowannansu ya zauna tare da lankwashe ƙafa,Abusufyan ne ya fara gaisar da ita"Ina kwana Ammi,kun tashi lafiya?Ya gajiyar tafiya"? "Lafiya lou Alhamdulillah,"ta amsa mashi,Sannan su Jahad suka haɗa baki wurin miƙa gaisuwarsu,da murmushi a fuskarta ta shiga amsa masu ɗaya bayan ɗaya,a ƙarshe ta tsayar da idanunta kan Hosana tace"Kin tashi lafiya"?   Murmushi hosana ta saki tana faman noƙe kai tace"lafiya lou,"       Janye idonta tayi daga kan hosana ta mayar dashi kan junaid tace"Sarkin Murmushi,Angona nakaina naga kayi kyau sosai ka kuma ƙara haske,faɗamun menene sirrin"?   "Kishiya zanyi maki ne"yayi maganar yana murmura mata ido,ɗan waro ido waje tayi tare da cewa"Wacece ita"?   ɗagowa yayi yana kallonsu,Sehrish har sai da ya gano jahad sannan ya nuna ta da hannu yace"Gatanan,"   Ammi tace"Kin shirya yin kishi dani ko"?   Girgiza kai jahad ta shiga yi alamar a'a,   "To kaji bazata iya kishi dani ba,sai ka haƙura da auren gaba ɗaya,don ni bazan zauna da kishiya ba,"   "A'a wlh Ammi sai dai ki haƙura dani in aurota," Yadda yayi maganar ba ƙaramin dariya ya basu ba,don har saida suka dara, Ammi tace"wato Ni zaka juya ma baya ko?saboda ka samu zankaɗeɗiyar budurwa sabuwa gal cikin leda,Ni kuma nayi maka tsufa,"gyaɗa kai tayi tare da cewa"bakomai na haƙura,"   Murmushi suka saki gaba ɗayansu,mayar da idonta tayi kan Abusufyan"Yanzu ya ake ciki game da zancen Mahaifiyar yaran nan"?   Jin an sako zancen abu yasa shi gyara zama,sannan yace"Muna nan muna shirya waɗanda zasu je kano domin binciko gidan da suka zauna acikinsa,saboda muna sa ran zamu samu wasu muhimman bayanai a wurin makwabtansu,"   Jinjina kai Ammi tayi"hakan yayi kyau,banason a tsaya 6ata lokaci nafi son ayi komai tun da wuri don ba'a san halin da take ciki ba,"   "In sha Allah zamuyi hakan,daga nan suka miƙe tare da yi mata sallama suka wuce ɗakin Modibbo,ba ƙaramin daɗi yaji ba daya gansu,sun jima a wurinshi,kafin daga bisani suka wuce ɗakin gwaggon katsina,sun sha barkwanci a wurinta,daƙyar suka samu tabarsu suka fito,ɗakin hajiya azeema suka wuce,sun jima a wurinta suna shan fira,ɗaya bayan ɗaya haka suka dinga bin ɗakunansu kafin daga bisani,Lokacin yin breakfast yayi suka hallara gaba ɗayansu a dining,kowa saida yazo banda Sgr,saboda yasa ma ranshi cewar za'a kawo mashi ne har part ɗinsa,Azmee ce takai mashi,saboda Sehrish ta sanar da ita cewar,bazata samu damar kai mashi ba,tana so tabi Umarnin mahaifinta ne, Lokacin da Azmee ta shiga part ɗinsa,yana daga kishingiɗe saman Sofa mai mazaunin mutun ukku,jikinshi na sanye da jallabiya,shigowa ciki tayi gabanta na faɗuwa don tasan cewa dole ya tuhumeta akan me ya hana sehrish zuwa,lalla6awa tayi ta ajiye masa tray ɗin a asaman table,gudun karya tuhumeta yasa tayi saurin ja da baya zata gudu tabar ɗakin,har takai baƙin ƙopar ɗakin tajiyo muryarshi yana fadin"ke zo nan,"dakatawa tayi da tafiyar hannunta dafe da saitin zuciyarta,jiki asanyaye ta dawo ta tsaya agabanshi,kwata kwata idanunshi na a lumshe,wayarshi na ajiye asaman wide chest ɗinsa,   dakyar ta iya cewa gani yalla6ai, "Bana ce kar na sake ganinki a part ɗina ba da sunan aiki?ko bata faɗa maki bane"?   Shiru azmee tayi,tana faman zazzare ido,ranta ne ya bata cewar kawai ta sanar dashi gaskiyar zance, Don haka tace"Sehrish ta sanar dani cewar bazata ƙara aiki a part ɗin ka ba...."tunkan ta ƙarasa maganar ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu,nan take azmee tasha jinin jikinta,   "Ita da bakin ta,ta faɗi hakan"? Muryarta na kerma tace"Eh,   Ya kuma cewa"ta faɗa maki dalilin yin hakan"? "Eh,tace tana son bin Umarnin mahaifinta ne,"    ɗan ciza gefen la66ansa yayi tare da cewa"its Okey,just leave........" da sauri azmee ta juya tare da kama hanya ta fuce daga part ɗin nasa, Wuraren ƙarfe goma sha biyu modibbo ya shirya tafiya,Kanal yousouf ne tare dasu Irfan suka kai shi har Airpot ya hau jirgi, Yinin Ranar Aunty babba na ƙumshe a cikin ɗakin Hayaam,tsoro ya hanata fitowa waje,da yunwa ta addabe ta Hayaam ce ta ɗebo mata abinci ta kawo mata a ɗakin,hosana kuwa kar take dasu,don taci alwashin sai ta tona masu asiri wurin daddynsu,da kuma Ya omar, Hankalin sehrish ba ƙaramin kwanciya yayi ba,jin Cewa sgr bai nemeta ba,duk da ta damu akan son ganinshi,jurewa kawai takeyi, A ranar Talal Da captain najeeb suka ƙaraso,murna a wurin ƴan uwansu kamar zasu haɗiye su don farin ciki,musamman junaid daya kasance rival ɗinsa ne ya dawo wato Talal,da yake shima autane a ɗakinsu Omar, After 1 day *Boss Bature* Around 2:00 pm, Zaune take a hakimce saman 2 seater,jikinta na sanye da turkish dress Riga da wando,a launin fata fara ce amma hasken nata hada na bleaching tayi 6au sosai,babbar mace ce a ƙalla zata kai shekara 35,gaba ɗaya idanunta na akan plasma tv din da take kallo aciki,yayin da hannunta ke ɗauke da cup na coffee,lokaci bayan lokaci take kur6asa,ta aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,wuyan kafarta na sanye da ziririyar sarƙa,sai faman karkaɗa kafar takeyi,Tana da manyan idanu dara dara,ga dogon hanci wanda ke manne da nose ring,kai kana ganinta zaka san cewar cikakkiyar ƴar bariki ce, Jin ringing din wayarta dake ajiye asaman hannun kujerar da take ne yasa ta Ajiye cup din hannunta asaman madaidaicin table din dake a kusa da ita,sannan tasa hannu ta dauki wayar,hidden number ce aka kirata da ita,picking call ɗin tayi ta kanga wayar a kunnanta,cikin harshen fulatanci take magana, Tana cikin yin wayar taga inuwar mutun tsaye akanta,ɗagowa tayi a hankali don taga wanene,sauke ajiyar zuciya tayi ganin Amrish ce,jikinta na sanye da uniform,ta goya school bag dinta a abayanta,dawowarta kenan daga school,fuskarta a ɗaure kwata kwata babu annuri acikinta, Rejecting call ɗin tayi tare da ajiye wayar asaman sofa din,sannan ta mayar da hankalinta sosai akan Amrish,   "Welcome back my daughter,Am really glad to see u,"   Tayi maganar tana buɗe mata hannunwanta don tazo ta rungume ta,rai a6ace tace"Mommy na tsani ganinki wlh,banason ki,saboda baki da halin kirki,so kike ki kashe mun rayuwata da hannunki,"tana maganar hawaye na gangarowa akan fuskarta,   Maimakon ta nuna damuwarta akan hakan sai ma ɗan ta6e la66anta tare da cewa"Kamar yadda baki so na,Nima haka bana son ki,donni a tsarin rayuwata ban shirya haihuwa ba saboda bana son ƴa'ƴa don su takura ne,na samu cikinki batare dana shirya ba,babu yadda banyi ba don na zubar da cikin,amma ya liƙe ya nace sai ya zauna a mahaifata,a ƙarshe nayi deciding zuwa ƙasar waje a markaɗe mun shi,mahaifinki ya hana hakan,nayi takaici a wannan lokacin kamar nayi suicide,"   Hankalin Amrish ba ƙaramin tashi yayi ba,jin abunda mahaifiyarta ke faɗi da bakinta,tuni wasu zafafan hawaye suka shiga wankowa a saman fuskarta,cikin shessheƙar kuka tace"ki faɗamun!Su wanene iyaye na!don ina da tabbacin cewar bake kika haife ni ba,"   Fashewa da dariya matar tayi yayin da take karkaɗa kafafunta, Jin tayi banza da ita yasa ta daka mata tsawa tare da cewa"Mommy ki faɗamun su wanene iyaye na?In ba haka ba zan je na kashe kaina!" Yunkurawa mommyn tayi tare da mikewa tsaye ta daddage ta kifa ma Amrish mari tare da cewa"Sai me idan kin kashe kanki!?wa kikayi ma asara!shashasha kawai," Fashewa da kuka Amrish tayi yayin da zuciyarta ke tafarfasa tace"Mommy yau ke da kanki kika mare ni"? Dogon tsoki taja tare da cewa"Har kashe ki ma zan iyayi,Saboda kinyi mun tsawa,ko iyayena da suka haife ni basu ta6a gigin daka mun tsawa ba,balle ke ƴar dana haifa,idiot" Ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta ɗauki wayarta,sannan tabar falon tana fadin"kafin gobe in samu gawarki dan Allah,"tayi maganar cikin halin ko in kula, Da gudu Amrish ta watsa,izuwa bedroom dinta dake a upstairs,datse ƙopar ɗakin tayi,bayan tayi wurgi da school bag dinta,ta shiga neman igiyar da zata shaƙe kanta don ta mutu,ganin bata samu ba yasa ta buɗe kopar ɗakin,ta fita,bada jimawa ba sai gata ta dawo cikin ɗakin hannunta dauke da insect powder,buɗe murfin tayi da sauri sauri ta daga robar tare da zazzagawa acikin bakinta, Mommyn na acikin bedroom ɗinta,ta jiyo wata irin razananniyar ƙara mai rikitarwa,sakin wayar dake hannunta tayi,da gudun gaske ta fito daga bedroom ɗinta dake a downstairs,tamkar za tayi tuntu6e ta fadi kasa haka take gudun,lokacin da ta ƙarasa bedroom din Amrish,hannu tasa ta dinga bubbuga ƙopar tana faɗin"AMRISH!AMRISH!!baki da hankali ne,bakisan wasa ba,me kika aikatawa kanki!ba zaki zo ki buɗe mun ƙopa ba!!Amrish gaba daya duk tabi ta rikice, Shiru amrish bata buɗe mata ƙopar ba,hakan yasa ta dawowa wurin window ɗin ɗakin ta buɗe ta don ta gane ma idonta, A gigice ta fasa uwar ƙara tare da aza hannyenta asaman kanta tana fadin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!na shiga uku!!!!zubewa tayi ƙasa saman guiwowinta tana faman zabga kuka,hawaye jaga jaga a fuskarta,tana cikin wannan yanayin,taji shigowarsu Zeenat da sofia ƙawayen Amrish cikin falon gidan,mikewa tayi da sauri har tana tuntu6e ta saukko downstairs,tunkararsu tayi tana fadin"Nashiga uku!!Amrish ta kashe kanta!!bansan ya zanyi da rayuwata ba!! Kallon juna sukayi hankalinsu a matukar tashe suka haɗa baki wurin cewa"Am...Amrish!!meya faru da ita!taya akai ta kashe kanta!!! Kasa bude baki tayi don tayi masu magana,da hannu ta dinga nuna masu bedroom ɗinta,nan suka gane cewar tana acikin ɗakinta,da gudu suka nufi upstairs ɗin,itama tabi bayansu,nan fa suka shiga ƙoƙarin 6alle ƙopar ɗakin nata,    *💋 Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* ❤🤍❤ Daƙyar suka samu ƙopar ta buɗe nan suka same ta a kwance rai hannun Allah,wani irin ruwan kumfa kumfa ne ke fitowa daga bakinta,gaggawar ɗaukarta su kayi,su biyu suka cuccu6eta sai cikin motar Mommyn,da kanta tayi driving ɗin motar,yatsun hannunta nata kerma tana yi tana dan bugun steering,Su zeenatu kuwa dake a back seat na motar,sae kuka sukeyi suna jijjigata don karta mutu basu isa asibitin ba, Suna ƙarasawa asibitin,da sauri suka cuccu6eta suka shiga da ita mommyn na fadin"Emergency pls doc,nurse....!"reception Nurses ne suka kar6eta da sauri da sauri suka shiga da ita ɗaki,anan aka kwantar da ita,doctors suka taru a kanta. Zama sofia da Zeenatu su kayi asaman waiting seat,yayin da Mommyn Amrish ke ta faman zarya a corridor din,jikinta sai faman kerma yake yi,sam bata ta6a tunanin cewa Amrish zata iya yunkurin kashe kanta ba sai yau da ta tabbatar mata,tasha faɗin cewa zata kashe kanta in bata faɗa mata wanene mahaifinta ba,bata ta6a ɗaukar abun serious ba,sae yau,ta tsorata da irin hukuncin da Amrish ta yanke wa kanta,   "Mommy wai meya faru ne?Nasan cewa Amrish bazata ta6a yunƙurin kashe kanta ba,batare da anyi mata wani abu daya 6ata mata rai ba!" Zeenat ce tayi maganar,yayin da idanunta ke fitar da hawaye,   "Ni banyi mata laifin komai ba,kan dai maganar nan ce da take yawan faɗamun na cewar ta tsane ni bata sona,in faɗa mata su wanene iyayenta ko ta kashe kanta,ta 6ata mun raine yau saboda tayi mun tsawa shiyasa na kwashe ta da mari sannan nace taje kafin gobe in samu gawarta,shine fa ta fusata har ta aikata hakan,"    Cikin shessheƙar kuka zeenat tace"meyasa ba zaki iya lallashinta ba?saboda me zaki sa hannu ki mare ta?kuma kika furta mata cewar taje ta kashe kanta bayan kinsan cewa ita yarinyace ba wayau tacika ba,yanzu gashinan kinja zamu rasa ta gaba ɗaya"cike da takaici Zeenatu ta ƙarasa maganar tare da komawa saman waiting seat ɗin ta zauna tare da kifa kanta saman laps ɗinta tana cigaba da matsar kwalla,hannu sofia tasa tana ɗan bubbuga bayanta,ɗagowa tayi da idanunta waɗanda suka rune jawur dasu,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Mommy yakamata ki sanar da yayanta halin da ake ciki,tun kafin rai yayi halinsa,"    A tsananin tsorace Mommyn tace"bazan sanar da kowa ba,idan ma ta mutu bazan bari wani ya sani ba,guduwa kawai zanyi in yaso daga baya sunji labari,don wlh bazasu ƙyaleni ba,"   "Saboda me kika ce haka mommy"? "Zeenat mubar zancen kawai,ni kaɗai nasan halin da nake ciki,"tayi maganar tare da kifa kanta jikin bangon da take tsaye,   Jikinsu ba ƙaramin sanyi yayi ba, "Amma mommy meyasa kike 6oye mana abubuwa da dama game da Amrish?har yau bamu ta6a ganin mahaifinta ba,bayan wannan bamu ta6a ganin wani acikin dangin ku ba,sae mutun ɗaya kawai,yayanta dake zuwa wurinta ...."   Kasa ƙarasa maganar tayi saboda ganin irin juyowar da mommyn Amrish tayi a ruɗe,la66anta har rawa sukeyi wurin cewa"Kar na kuskura na ƙara jin kinyi mun wannan maganar!baida amfani sanin wanene mahaifin Amrish!Ni ɗin nan ni ce Mahaifinta kuma ni ce mahaifiyarta!!   Shiru sofia tayi,batare da ta ƙara cewa Komai ba,,,,,,,, Ranar dae A asibiti suka yini har dare ya ritsa dasu, *Boss Bature* ❤🤍❤ Fitowarsa kenan daga cikin toilet jikinshi na sanye da bathrobe,hannunsa kuma na ruƙe da short towel yana ɗan matse sumar kanshi,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga jikinshi,tamkar wanda aka tsamo daga ruwan turare,saboda ƙamshi,gaban dresssing mirror ya tsaya yana ƙarasa tsane sumar kan tashi,ɗan dakatawa yayi tare da wurga eye balls ɗinsa ta cikin mirror yana kallon Shimfiɗeɗen gadonsa,bedsheet ɗin duk yayi  squeezing,ga blanket ɗinsa dake a cukurkuɗe saman gadon,komai ya hargitse ba don komai ba sai don rashin mai gyara,2 days kenan ba'a gyara mashi part ɗinsa ba,a ƙa'ida duk rana sai an canza mashi bedsheet da Blanket amma yau har 2 days ba'a musanyasu ba,mutun ne shi mai tsaftar gaske,ga ƙyanƙyami,gashi ko kaɗan baijin zai iya ɗaga yatsanshi da sunan zai gyara bed ɗin nasa,ba don komai ba,sae don saboda kasancewar shi mutun mai matuƙar Ji da kanshi,a wurinshi wannan tamkar ƙasƙanci ne da matsayinshi ya zuƙunna da sunan zai gyara bedroom ɗinsa,tamkar ƙaskanci ne namiji yayi aikin da mace ya dace tayi shi,ko ba don wannan ba shi tun yana yaro ko tsinke wannan acikin gida kawar masa shi akeyi,sam bai iya aikin gida ba,wanka ne kawai yakeyi ma kanshi,amma da zarar ya fito daga toilet akwai masu taimaka mashi wurin yin dressing na Outfits ɗin da zaisa, Yana cikin tsayuwar nan,Yaji sallamar Azmee daga cikin palour ɗinsa,bai amsa mata sallamar ba,hannu yasa tare da ɗaure igiyar Bathrobe ɗinsa sosai,sannan ya juya tare da nufar ƙopar fita daga bedroom ɗin,adai dai bakin ƙopar ya tsaya tare da goya hannayenshi asaman wide chest ɗinsa, Azmee kuwa tunda taga ya fito gabanta ya shiga faɗuwa,dama zuwa tayi don ta gyara mashi part ɗinsa,   "Where's she"? Ya tambaya batare da ya aza eyes ɗinsa akantaa ba,   Tunda ya ambaci hakan ta gane cewa akan sehrish yake magana,don haka tace"Tana a bedroom ɗinsu,"   "Okey,call her right now," Yayi maganar cike da bada Umarni sannan ya juya tare da shigewa cikin bedroom ɗinsa,.    Juyawa Azmee tayi da sauri ta fuce daga part ɗin nasa,downstairs ta saukko kai tsaye ta nufi ɗakinsu Sehrish,hannu tasa tare da knocing ƙopar,a lokacin duk sunyi nisa acikin baccinsu,can cikin bacci Sehrish taji bugun ƙopar ɗakin nasu,buɗe idanunta tayi a hankali sunyi mata nauyi saboda wani irin bacci da take ji,jikinta a kasalance ta yunƙura daƙyar ta sauko daga saman gadon ta buɗe ƙopar tana tambayar wanene, Tunda taga Azmee taji gabanta ya faɗi rass,duk da batasan meya kawota ba, "Aunty azmee lafiya?tayi tambayar tana yin hamma, Azmee tace"ina fa lafiya,Sgr ne ke son ganin ki,yace in kira mashi ke yanzun nan" Daram taƙara jin gabanta ya faɗi,"nashiga uku ni yau,"ta faɗi hakan tana yarfa hannu,    "Yakamata kiyi sauri kije tun kafin ya hasala,don da alama yau ranshi a 6ace yake,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta bar ƙopar ɗakin nasu,   Jiki a sanyaye sehrish ta koma cikin bedroom ɗin nasu,gaban wardrobe taje,ta buɗe ta ɗauko mayafi ta yafa shi asaman kanta,kayan bacci ne ajikinta, Fitowa tayi daga ɗakin,ƙafarta na sanye da slipper,tana tafiya cike da zullumin me zai biyo baya,ba komai take hangowa ba face tafin hannun Sgr,ya wanka mata mari,har runtse ido takeyi saboda ganin abun take kamar dagaske,tana ƙoƙarin giftawa ta babban falon ta wuce sama,kwatsam Abusufyan ya fito daga bedroom ɗinsa ya hango gifcinta,tsayawa yayi yana ƙare mata kallo daga inda yake,jinjina kanshi yayi tare da lalla6awa yabi bayanta,cikin sanɗa batare da ta sani ba,   Hayewa tayi saman stairs ɗin,sannan ta wuce part ɗinsa,bakinta ɗauke da sallama ta shiga ciki,babu kowa a falon nasa,tsayawa tayi a tsakiyar Sofas ɗin,don bazatayi gangancin shiga bedroom ɗinsa ba,ƙwara daganan idan taga ya harzuƙa ta watsa da gudu,amma in can ciki ne zai iya kama ta,   Tana cikin tsayuwar nan zuciyarta na ɗar ɗar,taji motsinshi da sauri takai idanunta kan ƙopar bedroom ɗinsa,gabanta ne ya faɗi rass ganin shi a tsaye,hannunshi ɗaya ruƙe da waist ɗinshi,yayin da yake sanye cikin sleeping dress white color ba ƙaramin kyau su kayi mashi ba,Amma fuskar nan fa babu annuri ko misƙala zarratin,   Da hannu yayi mata alamar tazo,hakan yasa ta nufi wurinshi ɗan nesa dashi ta tsaya sannan tace"Gani," Hakan da tayi ba ƙaramin 6ata mashi rai yayi ba,maimakon tazo kusa dashi saita tsaya nesa dashi,    "Ni kike so in ƙaraso inda kike"!? Girgiza kai tayi alamar a'a,jinjina kanshi yayi tare da matsa mata hanya yace"shiga ki gyara mun bedroom ɗina,"   kasa motsawa tayi saboda alƙawarin da ta ɗaukarwa kanta na cewar bazata ƙara zuwa part ɗinsa ba,da sunan yin aiki,saboda umarnin mahaifinta,   Ja da baya ta ɗanyi tare da girgiza mashi kai gabanta na faɗuwa ga tsoro amma ahaka ta daure ta cije tace"daddy ya hanani," Wani irin kallo da yayi mata ita kanta saida ta girgiza,tausasan la66ansa har kerma sukayi wurin furta"Ni kike faɗama cewa Daddy ya hanaki"? ..shiru tayi tana faman zare ido,hakan ya ƙara fusata shi,gadan gadan ya tunkarota,ƙoƙarin juyawa tayi amma ina kafin tayi wani yunƙuri tuni ya ruƙo mayafinta nan take ya zame ƙasa,kwakkwaran damƙa yayi ma gashin kanta,hakan yasa tayi screaming saboda Zafin da taji,   Jijjiga kan nata yayi,tamkar wata Ƴar babyn roba haka ya ɗaga ta gaba ɗayanta da hannu guda,kuma ta hanyar gashin kanta daya damƙa,wutsil wutsil tashiga yi da ƙafafunta,hawayen azaba na gangarowa akan  fuskarta,fashe mashi da kuka tayi muryarta na rawa ta shiga faɗin"Wayyo Allah na!Babban yaya dan Allah kayi haƙuri ka sauke ni ƙasa,wlh bazan ƙara ba,zan gyara maka ɗakin,'   Zuba mata ido yayi yana kallonta tun daga ƙasa har sama,wata ƴar ƙarama da ita,mamakinsa a ina ta samu ƙwarin guiwar gaya masa magana batare da jin shakkarshi ba,   "Babban yaya dan Allah ka sauke ni!Wayyo Allah da.. daddy,nashiga uku,zai kashe ni,gashin kaina zafi,zai cire mun gashina,"saboda tsabar kuka hada majina,fuskarta tayi jaga jaga da hawaye,sai da ta galabaita sosai sannan ya saki gashin kan nata,gaba daya ta zube saman guiwowinta saboda jikinta da ba ƙwari,      Zura hannayenshi yayi acikin aljihun dogon wandon dake ajikinsa,sannan yace"Tashi ki shiga ciki,ki gyaramun bedroom ɗina"   Jikinta na kerma ta miƙe da sauri da sauri ta tunkari ɗakin nashi tana faman shessheƙar kuka,tana ɗaga ƙafarta zata shiga ɗakin taji an dakatar da ita,   "Karki kuskura ki shiga ɗakin nan"!!!! Rass taji gabanta ya faɗi jin Muryar daddynsu,a firgice ta juyo don ta shaidawa idanunta,   Shigowarshi kenan cikin palourn yayi maganar,a wani sukwane Sgr ya wurga eye balls ɗinsa akanshi,takawa yayi har zuwa gabanshi ya tsaya suna Facing ɗin juna,sannan yace"meyasa kake son takura rayuwarta ne?yarinyar nan ba ƴar aiki bace,ƴata ce!kuma ni ne na bata Umarnin cewa ta daina aiki acikin gidan nan!akan me kakeso ta fifita Umarninka akan na mahaifinta?matsayinmu ɗaya ne a wurinta ne"? Wannan maganar ta Abusufyan ba ƙaramin Fusata shi tayi ba,Yadda kasan zaki haka ya shiga fitar da huci ta hancinsa,ya ma rasa amsar da zai ba Uncle ɗin,saboda zuciyarshi da ta hasala,don har bugu zai iya kai mashi,muryarshi na kerma yace"Un...cle!Are u telling me dat matsayinmu ba ɗaya ba a wurinta!"jinjina kanshi ya shiga yi yana fama ciccije la66ansa,ran manya ya 6aci,yaci gaba da cewa   "Of course our position is not the same,but she's my younger sis,ina da right ɗin da zan sanyata aiki tayi mun,why kake so kajamin raini a wurinta"! daƙyar voice ɗinshi ke fita saboda tsabar 6acin rai zuciyarshi har wani tafarfasa takeyi,   "Ba raini nakeso naja maka ba a wurinta!tabbas ƙanwarka ce ita halak malak,kuma kana da ikon da zaka sanyata abu tayi maka,wannan gaskiya ne,amma Ni mahaifinta na hana haka!ban amince ba,tayi aiki a ƙarƙashin kowa ba,Azmee itace mai aikin gidan nan!ita yakamata ace tana yin duk wani aikin daya dace,idan ma Aikin azmeen ke baka so,Zan iya sawa a ƙaro wasu masu aikin da zasu rika yi maka,amma ba ƴa taba,saboda ita ba ƴar aiki bace......"tunkan ya ƙarasa maganar Sgr ya daka mashi wata irin gigitacciyar tsawa,a tsiwace yasa hannu tare da toshe ears dinsa yana faɗin"ENOUGH!Enough!banason ji,banaso,she must execute my Command,that's may final say" ya karasa maganar yayin da idanunshi ke aruntse ruff ya rufesu   Abusufyan yayi ma tsawar,amma gigitar da sehrish tayi,tamkar zata zauce,ƙanƙame jikinta tayi,cike da fargaba,    Zuba mashi ido abusufyan yayi yana kallonshi,a hankali ya zame tafin hannayensa daga toshe kunnuwansa da yayi,a hankali ya ɗan ware blue eyes ɗinsa,tare da juyawa ya kalli wurin da Sehrish ke tsaye a ƙopar ɗakinsa yace"Wuce ciki ki gyaramun bedroom ɗina"!babu wasa a fuskarshi yayi maganar,wannan ƙarfin halin na Sgr ba ƙaramin mamaki yaba Abusufyan ba,a tsananin tsorace ta wurga idanunta kan daddynsu don taji me zaice,    "Karki kuskura ki sanya ƙafarki a ɗakin nan!idan har na isa dake"!!wannan shi ake kira da tashin hankali,zazzare idonta tayi tana kallonsu,ta rasa Umarnin wa zata bi,A zarihi dae tafi tsoran Sgr,a baɗini kuwa tafi son tabi umarnin mahaifinta saboda sanin matsayin da yake dashi a wurinta,sa6a mashi zai iya haifar mata da gagarumar matsala a rayuwarta,haka zalika sa6ama sgr ba ƙaramar matsala zaija ma kanta ba,ta rasa inda zata tsayar da kwayar idonta,idan ta kalli Sgr sai ta kalli abusufyan,kowannansu ita yake kallo,daga ganin fuskar Abusufyan zaka san cewar hankalinsa ba a kwance yake ba,babban abunda yake fargaba shine Sehrish taƙi bin Umarninsa,duba da yadda ta gaza motsa jikinta,tabbas zai kunyata sosai kuma darajar da yake da ita ta mahaifinta zai zube ne a idon sgr,zai cigaba da ganin kanshi ne amatsayin Sarki,wanda ke bada Umarni kuma dole abi,   Wata irin tsawa sgr ya daka mata,wadda har sai da jikinta ya girgiza sosai tabi ta rikice,a fusace yace"won't u go in!"   Yana rufe bakinsa,Abusufyan yace"idan har kika kuskura kika shiga ciki,zan yafe ki ne acikin ƴa'ƴana,babu ni babu ke!"   Jin wannan maganar yasa ta fashe da matsanancin kuka,baiwar Allah tana a cikin tsaka mai wuya,yarfa hannunta tashiga yi tana faɗin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un Ya Allah ka kawomun ɗauki!daddy!!babban yaya!!bansan ya kukeso inyi da kaina ba!!dan Allah ku ƙyale ni!kubarni in ba haka ba zuciyata zata iya bugawa in mutu,"   Tuni jikin Abusufyan yayi wani irin sanyi,idanunshi suka cika tab da hawaye,tsananin tausayinta ne ya kamashi,kamar yaje ya rungumota ajikinshi ya lallasheta,Amma yaci alwashin cewa bazai ta6a bari Sgr yaci nasara akanshi ba,   A 6angaren Sgr kuwa,ya gama hasala tunda yake a rayuwarshi bai ta6a bada umarni aka tsaya yi mashi jayayya ba sai yau,sau ɗaya yake bada command kuma dole abi batare da anyi mashi musu ba,runtse idanunshi yayi tare da tura yatsun hannayenshi cikin sumar kanshi yana cakuɗata,yayin da yake ɗan cizon lips ɗinsa,wani irin huci ke fita daga hancinsa,wannan ɗabi'arsa ce aduk lokacin da ranshi ya 6aci sosai,steps uku ne matakin hauhawarshi,idan yakai step na ƙarshen the most dangerous kenan don tamkar aljani yake komawa kuma kowaye gabanshi bai gani tamkar makaho yake komawa,a wannan step ɗin idan ya damƙi mutun a hannunshi yana bugunshi sae yaga gawarshi,kuma babu mai iya control ɗinsa har sai lokacin da Allah yasa zai dawo hayyacinsa,amma zaiyi wuya yakai wannan step ɗin sai in ya damƙi mai laifi zai hukunta shi,iya step na biyu yake tsayawa,mataki na farko shine zaka ga yana huci yana zagaye wuri,na biyu kuma Shine yake cizon la66ansa sosai,ya runtse idonshi ya kuma cusa yatsun hannunshi acikin sumar kanshi yana faman sakin huci tamkar mayunwacin zaki, Jini ne ya shiga ɗiɗɗigowa daga saman pink lips ɗinsa hakan ba ƙaramin tayar ma sehrish da hankali yayi ba,ita da bata saba ganin yana yi ba,Abusufyan kuwa hankalinshi kwance saboda yasan sgr sarai tun yana yaro yasan shi da wannan baƙar zuciyar,idan ya cije la66ansa har sai ya fasa su,    Fashewa ta kuma yi da wani sabon kukan cikin shessheƙar kuka tashiga cewa"Dad..ddy dan Allah ka ce mashi ya daina,yana fasa la66ansa da kanshi,!"Shi yake fasa la66ansa amma raɗaɗin ita take jinshi ajikinta saboda tsabar ƙaunar da takeyi mashi,   Da wata irin murya ya kuma cewa"ki wuce ciki nace,karki bari na ƙara maimaita maki hakan!" saboda tsabar ruɗu ta juya zata shiga ɗaƙin,aikuwa abusufyan ya daka mata tsawa,a ruɗe ta juyo tana kallonshi yayin da hawaye ke fita a idanunta,hanya ya nuna mata da hannunshi yace"Zoki wuce"   A tsorace take kallon Sgr wanda idanunshi ke arufe,sosai ya runtse su,ganin haka yasa tayi tunanin watsawa da gudu tabar ɗakin don tabi Umarnin mahaifinta,tasan cewa kafin ya buɗe idanunshi tabar falon,   Daddagewa tayi da gudun gaske ta watsa aguje ta nufi hanyar fita daga falon,sae dai ina kafin ta ankara sgr ya zabura a hargitse yabita,abusufyan na ƙokarin taroshi aikuwa yayi wurgi dashi gaba ɗaya,yayi gefe guda ƙasa,A zafafe ya damƙi waist ɗinta,wani irin ruƙo yayi mata ruƙo bana wasa ba,ya ɗaɗɗagota sosai ya manna ta da jikinshi,bedroom ɗin shi ya nufa da ita,wannan ƙarfin halin har ina,ran abusufyan ba ƙaramin 6aci yayi ba,miƙewa yayi da sauri ya tari Sgr kiciniyar kwace Sehrish ya shiga yi da hannunshi,nan fa suka kacame ma juna,   "Subhanallahi me nake gani haka"!!muryar Abba ce ta karaɗe kunnuwansu,gaba ɗaya suka juyo kowa na huci suna kallonshi,a lokacin Sgr ya saki sehrish daga hannunshi,da gudu ta miƙe tana kuka,ta nufi wurin Abba,gaba daya ta faɗa jikinshi,rungumeta yayi yana ɗan bubbuga bayanta,yayin da idanunshi ke akan Sgr da Abusufyan,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,yadda sgr ya manta wanene abusufyan a wurinshi,har yake ƙoƙarin yin dambe dashi,hauka maganinka Allah, "Abusufyan da hankalinka kake kokoyi da Rafayet kamar wasu tsararrakin juna?duk akan menene kuke wannan faɗan"?   Yayi tambayar tare da mayar da idanunshi kan Sgr wanda ke tsaye har lokacin sama yake bai sakko ba"Rafayet ka bani mamaki!ka rasa dawa zakayi dambe sae Kawunka,ƙanin mahaifinka!Anya baka fara shaye shaye ba?nafara zarginka," afusace ya juya tare da shigewa cikin bedroom ɗinshi yaja ƙopa ya rufe, "Bansan me rafayet ya ke ɗaukar kanshi ba,Taya zan ba yarinya umarni A matsayina na mahaifinta sannan yace dole saita take umarni na don tabi nashi?saboda haka fa ya ke ƙoƙarin buguna sai kace wani tsaransa"da alama ran abusufyan ya 6aci sosai,yana maganar yana nufo inda su Abban suke tsaye shi da sehrish,hannunta na ruƙe cikin na abban,wani irin zazza6i ne ya rufar mata mai zafin gaske,ga ciwon kai mai tsanani da take fama dashi,duk don saboda tashin hankalin da suka jefa ta ciki,kuma har lokacin kukan take yi, Sam Abba baiji daɗin abunda ya faru ba,"kayi haƙuri Abusufyan abunda yayi bai kyauta ba,duk da ba laifinsa bane irin rayuwar da aka saba mashi da ita kenan tun yana yaro,komai yi mashi akeyi,kuma in ya bada Umarni bi akeyi duk don tsoran kada ranshi ya 6aci," Gyaɗa kai kawai Abusufyan yayi tare da cewa"babu komai,Ae nasan halinshi sarai shiyasa banji zafin abun sosai ba,inayi mashi uziri ne,"    Ya ƙarasa maganar tare da kallon sehrish wadda ke ta faman matse kwalla,suna haɗa ido dashi ta sunnar dakai ƙasa,   "am really sorry my daugher,banyi hakan don na 6ata maki rai ba," Cikin shessheƙar tace"Ammm..ma daddy,cewa fa kayi zaka yafe ni acikin ƴa'ƴanka,idan har nabi umarninsa,"    Murmushi ya ɗan saki akan fuskarshi kafin yace"wasa fa nake maki,banda hankali ne,ae koda ace kin bi umarnin nasa bazan faɗi hakan ba,zan dai ji ɗaci araina,na faɗi hakan saboda ina gudun ki ƙi bin Umarni na,"   "Daddy nidai banason wannan wasan,dan Allah kada ka ƙara faɗamun hakan," yadda tayi maganar ba ƙaramin dariya yaso ya basu ba,don har sai da ta bubbuga ƙafafunta ƙasa,don ya tabbatar da cewar bataso,   "In sha Allah bazan ƙara ba,kinyi haƙuri ko"?   ɗaga mashi kai tayi alamar Eh, "Wato kun sasanta tsakaninku,ni kuma kun barmun yaro na,cikin wani hali ko"?Abba ne yayi maganar cikin zolaya,hada ɗaure fuskarshi,   Abusufyan yace"Yaya ai kai kaɗai kasan yadda zaka shawo kanshi,don yanzu duk wanda yayi gigin zuwa wurinshi,ba ƙaramar matsala za'a samu ba," Murmushi Abba yayi kafin yace"Shikenan zanje in lallashi abuna,kai kuma kaja ƴarka ku wuce ku bamu wuri,"   Hannun Sehrish Abusufyan ya ruƙe,tare da janta suka bar part ɗin yana dariya,   A bakin ƙopar bedroom ɗinsa ya tsaya cike da zullumin taya zai shawo kan sgr,hannu yasa yayi knocking ƙopar,shiru Sgr bai buɗe masa ƙopan ba,hannu yasa ya ƙara knocking ɗin ƙopar yana kiran sunanshi"Rafayet!ka zo ka buɗe mun ƙopa,inason magana dakai,"shiru bai ji motsinshi ba,babu alamun zai buɗe masa ƙopar,kwantar dakai abba yayi ajikin ƙopar cikin lallashi ya soma magana"haba rafayet ɗina,ni fa ne abbanka,so kake yau in gaza runtsawa?idan har bakazo ka buɗe mun ba anan zan kwana,"ya ƙarasa maganar tare da zuƙunnawa ƙopar ɗakin nashi,abu kamar wasa ya fara gyangyaɗin bacci,duk in ya ɗan farka sai ya ambaci sunan Shi Rafayet ka buɗe mun ƙopa,so kake na kwana anan? Duk wannan surutan da Abbansu ke yi kaf a kunnan sgr,wanda ke zaune saman front chair na dressing mirror ɗinshi,ya kifa kanshi asaman Dressing mirror,gaba ɗaya sumar kanshi ta rufe mashi side by side na fuskarshi,zuciyarshi ba ƙaramin tafarfasa take mashi ba,ranshi yayi mugun 6aci wai har shi zai bada Command aƙi bin umarninsa?bakowa yafi ji ma haushi ba fa ce Uncle ɗin nasu,don me zaiyi iko da Sehrish?saboda kawai ya haifeta?wani irin huci ne ke fita akanshi tabbas sai ya nemi matsayin dake asama dana mahaifinta ba don komai ba sai don yayi iko da ita,akan idon mahaifinta kuma,   Yana cikin yin wannan zancen zucin yaji Muryar Abbansu kamar ta wanda yasha giya,saurarawa yayi yana sauraron waƙar da Abbansu ke rera masa daga waje,tun yana yaro idan aka 6ata mashi rai,ya fusata da gudu yake shiga bedroom ɗinsa ya rufe ƙopa,idan abbansu naso ya sauko daga fushin da yake yi sai yazo ƙopar ɗakinshi yana kwankwasawa yana raira masa waƙa,cikin ƙankanin lokaci yake saukowa daga wannan fushin,   Jikinshi ba ƙaramin sanyi yayi ba,ɗan ɗagowa yayi da kanshi ya wurga eyes ɗinshi kan agogon bangon dake a manne ƙarfe kusan ɗaya na dare,Abbansu na waje yaƙi tafiya,kuma in har bai buɗe mashi ƙopar nan ba,to anan wurin zai kwana,saboda ya ta6a yi mashi haka,miƙewa yayi jikin shi babu ƙwari ya ƙarasa tare da jan ƙopar ya buɗe mashi,jin an buɗe ƙopar yasa Abbansu miƙewa jiki na rawa,suna haɗa ido da sgr,yasa hannunshi a idanunshi yana yi mashi kukan ƙarya wai ya barshi a waje,sanyi ya bugeshi,hakan da yayi ba ƙaramin dariya yaso ya ba Sgr ba,     Juyawa Sgr yayi tare da shigewa cikin bedroom ɗin,abban yabi bayanshi,a gefen gadon suka zauna suna fuskantar juna,   "Yanzu faɗamun,me yake damunka"? Shiru ya ɗanyi tamkar bazai tanka masa ba,daƙyar ya iya buɗe bakinshi yace"Abba,Uncle ya gama dani!har ni zan ba yarinyar can Umarni,ya hanata,don kawai yana taƙamar cewar shi mahaifinta ne"?yana magana muryarshi na shaƙewa saboda tsabar 6acin rai, "Rafayet!ni bansan me zance maka ba,ka san dai inason farin cikinka,duk wani abu da kake so ni mai iya yi maka shi ne,amma banda wannan!zan iya iko da Abusufyan amma bazan iya iko da ƴarsa ba,shi mahaifinta ne dole tabi Umarninsa tayi mashi biyayya,bijire mashi zai iya sa ta fuskanci matsala arayuwarta....." Bai ƙarasa maganar ba Sgr yace"That means ba wanda ya isa yayi iko da ita sai shi kawai?kenan Ni bani da wani matsayi a wurinta?bamu isa mu sata abu ba tayi kenan? Jinjina kai abbansu yayi tare da cewa"Hakane!maganar gaskiya babu wanda ya isa yayi iko da ita a halin yanzu bayan mahaifiyarta sai kuma shi" "Abba babu wani sama dasu wanda zai iya iko da ita fiye da mahaifanta"?yayi maganar ranshi a ɗan 6ace yana kallon Abban nasu, Gyara zama abbansu yayi,fuskar nan tashi ɗauke da wani 6oyayyen murmushi yace"duk duniyar nan bayansu mutun ɗaya ne!wanda zai iya yin iko da ita,fiye da iyayenta!' "Wanene shi"?ya tambaya Yana jiran jin amsar da Abban nasu zai bashi, "MIJINTA,shine wanda zai iya yin iko da ita fiye da iyayenta!Mahaifinta zai iya kiranta tazo gida mijinta ya hana,kuma dole ta hanu,ko tana so ko bataso," Hannu Sgr yasa tare da dafe gefen kanshi,yana faman sauke ajiyar zuciya,muryarshi ƙasa kasa yace"Abba!babu wata hanyar sai wannan"? Jinjina kai Abbansu yayi tare da cewa"that's the Only solution,"! Ya ƙarasa maganar yana kallon fuskar SGR,Acikin zuciyarshi kuwa Allah Allah yake akan ya amince zai auretan,Shikenan burinshi zai cika ganin cewa Rafayet yayi aure, "She's too young for me,Ni bazan iya auren yarinyar da ko Secondry school bata kammala ba,wannan abun kunya ne agare ni,da matsayi na in aureta?da wani ido duniya zata kalleni"? Zuru Abbansu yayi yana sauraronshi,wato Sgr har yanzu yana nan da wannan ji da kan nashi, Hannu Abbansu yasa tare da dafa shoulder ɗinshi sannan yace"Rafayet!nima ban goyi bayan hakan ba!idan har ka aureta girmanka zai faɗi ne!Amma ga wata shawara"? ɗan ɗagowa yayi da idanunshi masu ɗauke da bacci ya kalli abban nasu"Wane shawara ne wannan"?muryarshi a akasalance yayi maganar, Abba yace"Me zai hana kuyi auren yarjejeniya atsakaninka da ita yarinyar"? "Kamarya kenan"? Ƙayataccen murmushi Abbansu ya saki yana kallonshi kafin ya ɗaura da cewar"Wata nawa ya rage maku ku koma U.S"? "Remain 3 Months,"ya bashi amsa, Abba yace"Yawwa,before 3 months ɗin nan su cika,me zai hana ka aureta,a matsayin Contract marriage,don tayi maka aiki kawai na tsawon wata uku,kamar yadda kake so da zarar time ɗin ya cika,kawai saika bata divorce letter ɗinta,Amma ya kake gani"? Shiru Sgr ya ɗan yi yana nazarin maganar Abban nasu,kafin yace"Abba bacci nake ji,i will think about it before tomorrow," "Ba damuwa,kafin gobe dae yakamata kayi tunanin abunda ya dace,zan jira jin amsarka da safe," ya ƙarasa maganar tare da juyawa ya fuce daga ɗakin nashi, Blanket ɗinsa yaja ya lullu6e jikinshi har zuwa neck ɗinsa,maganar Abbansu ce ke tayi mashi yawo acikin kanshi,ga bacci yana ji amma yaƙi ɗaukarsa,sae faman juyi yake yi asaman gadon,tabbas in ya aureta zaici galaba akan Uncle ɗinsu Abusufyan,yana so ya dinga commanding ɗinta akan idon mahaifinta kuma ba yadda zaiyi dashi,na biyu kuma Yana so yarinyar taci gaba da aiki a ƙarkashin ikonshi,har zuwa lokacin da zai koma U.S!!idan har yana so hakan ya faru kenan dole sai ya aureta!?OMG! "That could not be possible for me as a Surgeon General to marry a young girl who has not even finished her secondary school,"ya furta hakan tare da jan blanket dinsa ya rufe fuskarshi daƙyar bacci 6arawo yayi awon gaba dashi, *Boss Bature* Saukowa down abba yayi fuskar nan tashi ɗauke da murmushi,anan ya samu abusufyan tsaye yana jiranshi,yana ganin ya tunkare shi,   "Ina sehrish ɗin take ne"? Abusufyan yace"Tun ɗazu ta wuce ɗakinsu,Nima kai nake jira muyi sallama kafin inje in kwanta,Amma ya kuka ƙare da rafayet ɗin?ina fata dai ya sauko daga fushin nan nashi"? Fuskar abba ɗauke da murmushi yace"daƙyar na shawo kanshi,yanzu haka ma ya kwanta,sae kayi haƙuri da surukin naka,"   Dariya abusufyan yayi kafin yace"ae ni bansan ya zamu ƙare da rafayet ba,lamarin ya fara bani tsoro,ƙoƙarin buguna fa yake yi ne?ahaka zan zama surukinsa?yana yi mun kallon tsaransa?Lokacin dana shiga ɗakin nasa samun shi nayi fa ya damƙi gashin kanta ya ɗaga ta sama kamar wata ƴar babyn Roba,yarinya sae kuka take tana bashi haƙuri amma ko ajikinshi,"    Abba yace"Ae rafayet sae addu'a,amma abun nashi ƙara gaba yake yi,yana ji Da ƙarfin nan nasa,bakowa zai iya jure zama dashi ba," suna tafiya suna fira har suka zo ƙofar ɗakin Abba,anan su kayi sallama da abusufyan ya wuce nashi ɗakin,    Fuskarshi a washe ya shiga ɗakin kamar ance ya ɗaga idanunshi karaf suka sauka akan Junaid dake baje saman gadon yana bacci,ga Mommynsa agefe,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,daga fitarsa har ya shigo ɗakinshi,Anya kuwa junaid shi kaɗai ne?yaro kamar mai iska,har leƙa ɗakinshi yayi ya same shi kwance yana sharar bacci shi da Talal,amma yanzu daga dawowarshi ya same shi a ɗakinshi,   Cike da takaici ya shiga cikin ɗakin,gefen gadon ya zauna tare dasa hannu ya bubbugga ƙafarɗarshi""Junaid!junaid"! Da ƙarfi yake ambaton sunan nashi,yatsina fuska junaid ya shiga yi yana faɗin"Wai wanene ke son takuramin"!   Yayi maganar yana ɗan ware idanunshi masu ɗauke da bacci,   Harara abbansu yaa jefa mashi tare da cewa"Ubanka ne,buɗe idonka ka gani mara matunci" koda yaji muryar. abbansu sae ya ƙara tamke fuska,yana faman murguɗa masa baki,Abba yace "Eyyyeh!ni kake murguɗa ma baki," zumbura masa baki yayi,hada sa hannu ya toshe kunnuwansa don karma yaji muryar abban nasu,   "Nasan maganinka yaro"yayi maganar tare da kai hannunshi saman side drawer ya ɗauko bottle water ɗin dake ajiye a sama,buɗe murfin robar ya shiga yi yana faɗin"Zaka tashi ko saina watsa maka ruwan nan,"   Wuri wuri yayi masa da ido,yana jira yaga in dagaske abban nasu ruwan zai watsa mashi,   Jin yayi banza dashi yasa shi ɗebo ruwan a murfin robar,ya watsa masa shi da sanyinsa asaman fuskarshi,aikuwa a gigice ya tashi zaune jikin shi na kerma,hankalin abbansu ba ƙaramin tashi yayi ba ganin yadda ya tsorata daga watsa mashi ruwa a fuska,abu kamar wasa sai ga junaid yana kuka hawaye jaga jaga a fuskarshi,   Tsawa abbansu ya ɗan daka mashi tare da cewa"Yi mun shiri rigimamme kawai,"   Wannan maganar da abbansu yayi ba ƙaramin ƙona mashi rai tayi ba,saukowa yayi daga saman gadon yana shassheƙar kuka yace""kuma Allah tunda ka kore ni,ɗakinsu sehrish zanje na kwana,"yayi maganar tare da bubbuga ƙafarshi ya fuce,   Sakin baki abbansu yayi yana kallonshi har ya fuce daga ɗakin,girgiza kai kawai yayi tare da gyara kwanciyarshi, Junaid kuwa bayan fitarshi daga ɗakin Abbansu,bedroom ɗinsu sehrish ya wuce kai tsaye,cikin sa'a ya samu ƙopar ɗakin a buɗe,hannu yasa ya tura door din,sannan ya shige ciki, Sun cika gadon su uku abunsu,sae faman sharar bacci sukeyi banda mutun ɗaya wadda ta rufe idanunta tamkar maiyin bacci, gaba daya hosana ta yaye masu bargon da suka lullu6e dashi,dama ita bata iya kwanciyar bacci ba,zaiyi wuya ta kwanta batare da ta faɗo ƙasa ba,dalilin dayasa suke sanyata tsakiya kenan saboda gudun karta faɗo,sehrish na kwance a left hand,hosana tana a middle ɗinsu,yayin da jahad ke a right hand,saitin inda yake tsaye,hannu yasa tare da kashe masu hasken ɗakin da sehrish ta bari a kunne,lalla6awa yayi ya haye saman gadon,gefen jahad ya kwanta, tare da ja masu bargon ya lullu6esu duka,cikin ƙankanin lokaci bacci ya ɗaukeshi,tabbas Sehrish taji lokacin da aka kashe masu hasken ɗakinsu,amma batayi tunanin ta buɗe idanunta ba don taga wanene,saboda halin da ta shiga,Zuciyarta ba tayi mata daɗi ga hawaye sae faman shararowa suke yi daga cikin idanunta,babban abunda ke damunta shine wani hali sgr yake ciki?Yayi bacci ko idonshi biyu?bataso abunda ya faru ba,sai dae ba yadda ta iya dole tabi umarnin mahaifinta da wannan zancen zucin bacci ya sace ta, tashin hankali,Junaid fa ya shige acikinsu sae faman sharar baccinsa yake,sun manne ma juna shi da jahad,duk a tunaninta sehrish ce,hada ƙara rungumoshi ajikinta,    *mu haɗu on monday donjin yadda zata kaya don kuwa akwai ƙura! Amrish zata Rayu ko kuwa akasin hakan?Wai ma wacece Amrish ɗin nan?su waye iyayenta?shin Sgr zai amince da auren sehrish?a yadda yake jin kanshi ɗin nan?Me zai faru idansu jahad suka Tsinci junaid acikin ɗakinsu saman gadonsu?*😨😱    *Su aunty babba manya Naki na nan tafe*🤣 *💋 Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Wuraren ƙarfe 3:00 na dare,Jahad tayi wani kwakkwaran juyi cikin bacci zata gyara kwanciyarta,aikuwa taji an ƙanƙameta sosai an matse ta,numfashinta har wani kokawar ɗaukewa yake yi,ƙoƙarin janye jikinta ta shiga yi amman hakan ya faskara,saboda ruƙon da akayi mata bana wasa bane,cikin baccin ta dinga faɗin"Sehrish!ki sake Ni!kin matseni,numfashi na zai ɗauke" daƙyar sound ɗin ke fita saboda throat ɗinta da ke abushe,saboda thirsty da take ji,tun tana ambaton hakan ƙasa kasa har takai ga ɗaga muryarta "Sehrish!!dan Allah ki sake ni,baki ji nace kin matse ni ba? Shiru babu mai bata amsa domin kuwa duk bacci suke yi, Jahad kuwa tuni ta gama galabaita hakan yasa ta tattare iya ƙarfinta na ƙarshe ta ingije junaid daga jikinta,ya ɗan yi baya,hakan yasa ta samu sarari,hannu tasa tare da zame bargon ta fiddo da kanta,tana faman sauke ajiyar zuciya,zufa duk ta wanke mata jikinta duk da weather ɗin nasu akwai sanyi,matsuwar da tayi ne yasa ta zubda gumi,juyawa ta ɗan yi tare da kallon gefen hannun hagunta,kasancewar akwai hasken electric bulbs ɗin da suka gauraye gidan daga waje da kuma na corridor ɗinsu gana main palour,Sune suka ɗan bama ɗakinsu haske,duk da an kashe Globe ɗin ɗakin nasu,dama kuma Sehrish ta lalata bedside lamp ɗin ɗakin,lokacin baya data kwala ma Haroon a goshinsa, Ƙura ido jahad tayi tana ƙare masu kallo,gani take tamkar idonta ba dai dai suke nuna mata ba kamar mutun biyu ne kwance a gefen hagunta,hannunta ta miƙe tare da yaye masu Sehrish bargon da suka rufa dashi,gabanta ne ya faɗi rass!ganin Sehrish ga kuma hosana baje suna ta sharar bacci,nan take hankalinta yayi mugun tashi,wani irin tsoro ne ya lullu6eta,tabbas akwai mutun ɗaya 6angaren damanta,wanda suka kwana rungume da juna a ƙanƙame,wanda yayi silar taushe numfashinta,tashin hankali! kasa juyawa tayi don taga wanene saboda tsabar tsoro,sae dai ta zura hannayenta dake ta faman kerma ta laluba don taji in da gaske wani ne kwance a wurin,Sumar kan junaid ta shafo da hannunta,a razane ta zame hannunta,la66anta na kerma ta shiga furta"La'Ila ha'illah Anta subhanaka,Inni kuntu minazzalumin,"daga bisani ta shiga faɗin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un!!, Muryarta na kerma ta shiga kwalama su sehrish kira kaɗan kaɗan don kada aljanin ya farka,"Hosana!Sehrish!!dan Allah ku tashi!Mutum mutumi acikin ɗakinmu saman gadonmu!ina tunanin Aljani ne ya faɗo ɗakinmu don ya cutar damu,Wayyo Allah na" babban tashin hankalinta aljanin na akusa da ita,in ma cutar dasu yazo yayi toh ta kanta zai fara tunda itace a kusa dashi, Tuni zufa ta gama wanko mata a fuskarta,numfashi kanshi daƙyar take fitar dashi don kada aljanin yaji yasan cewar idonta biyu,   "Sehrish!Sehrish!!hosana!wai ba zaku tashi ba?dan Allah ku tashi kuga abunda na gani,asaman gadon mu,"tana magana hawaye na sauka daga idonta,don ita ta riga ta sallamawa kanta cewar ajalinta ne yazo,    Duk wannan surutan da Jahad ke yi kaf a kunnan Sehrish,wadda ke lamo tayi nisa cikin zurfin tunanin da take yi,Duk a tunaninta Jahad mafarki takeyi shiyasa take sambatu,wannan dalilin ne yasa bata motsa ba,kuma bata tanka mata ba,idanunta ne kawae ke arufe amma idonta biyu,likimo kawai tayi, Jahad na cikin wannan yanayin taji an aza mata hannu asaman waist ɗinta,a wani irin Firgice ta fashe da wata irin gigitacciyar ƙara,wadda tayi silar tashin hosana daga bacci,hatta sehrish sai da ta razana,a tare suka tashi zaune ita da hosana suna kallon Jahad dake ta ihun neman agaji,ai koda Hosana da sehrish suka ga hannun mutum a saman qugun jahad,a gigice suka duro daga saman gadon da gudun gaske har suna tuntu6e wurin tunkarar ƙopar ɗakin don su buɗe ta su gudu,jahad kuwa sam taƙi motsawa,sai ihu take tana kuka,waɗanda take tunanin cewa zasu taimaketa sun gudu sun barta asaman gadon ita kaɗai,jikinsu sae faman kerma yakeyi burinsu su buɗe ƙopar su gudu amma taƙi buɗuwa,hakan yasa Sehrish watsawa da gudu,ta shige toilet taja ƙopar ta rufe,ganin haka yasa hosana tunkarar wardrobe ɗinsu,ta buɗe gidan ƙasa da babu kaya sosai acikinsa sae bedsheets,Ta faɗa ciki tare da jan murfin wardrobe ɗin ta rufe shi,kowa yayi ta kansa kenan,duk wannan budurin da akeyi Junaid bai sani ba,domin kuwa ba ƙaramin abune ke iya tashinshi daga bacci ba,irin mutanen nan ne masu nauyin baccin tsiya, Jahad na cikin wannan halin na firgici,taji an aza mata ƙafa asaman jikinta,firgitar da tayi ne yasa tayi wurgi da junaid gaba ɗaya,ya tafi dama yana dab da bakin gadon,aikuwa ji kake timmmm!ya ƙundumo ƙasa kanshi ya bugu sosai saman tiles, raɗaɗin da yaji ne yasa shi farkawa daga baccin,ya fashe da matsanancin kuka,    Gaban jahad ne ya faɗi rass!!jin sautin kukan Junaid,rarrafowa tayi ta dawo gefen gadon tare da ɗan leƙawa don ta tabbatar ma kanta abunda kunnuwanta ke ji,Zaro ido waje tayi cike da mamaki take kallonshi,yadda kasan wani jinjiri ya 6are baki sai kuka yake yi,da ƙarfi ta ambaci sunanshi"JUNAID"dakatawa yayi daga yin kukan da yakeyi jin an ambaci sunanshi,wurga idanunshi yayi akan jahad,yayi mata wuri wuri da ido yana kallonta,   Muryarta na rawa tace"juj..junaid!dama kai Ne?me kake yi acikin ɗakin mu? cikin shessheƙar kuka yace"Nifa Zuwa kawai nayi don in taya ku kwana," ...zuba mashi ido kawai tayi tana  kallon fuskarshi don abun ya fi ƙarfinta,   Daga cikin toilet ta jiyo Muryar Sehrish tana ce wa"Jahad wai dagaske junaid ne?Naji kin ambaci sunanshi"?   A ƙule jahad tace"Bansani ba,ku fito ku gane ma idonku,kunaji ina kukan neman taimako amma duk kuka watsa a guje kuka barni,yanzu da wani mugun abunne ba junaid ba,da Allah kaɗae yasan me zai biyo baya,"   buɗe ƙopar sehrish tayi tare da fitowa daga cikin toilet ɗin,hosana ma ta buɗe wardrobe ɗin tare da fitowa daga ciki,suka tunkari inda junaid yake kwance yana faman sauke ajiyar zuciya,sae faman lumshe ido yakeyi,saboda baccin dake a idanunshi,   "Junaid!" sehrish ce ta kira sunanshi,ware idanunshi yayi akanta yana kallonta, .."junaid me kake yi a ɗakin mu?waya kawo ka?anya baka fara shan ƙwaya ba"   Harara ya wurga mata tare da murguɗa mata baki yace"bansani ba,duk kun bi kun takura rayuwata,hakanan kawai ina baccina kun tashe ni,laifi ne in na kwana aɗakinku,ni ba ɗan uwanku bane"? Sakin baki sukayi suna kallonshi,hosana tace"wlh saina faɗa ma Daddy da Ya Omar,ince ka shigo ɗakinmu ka kwanta mana asaman gadonmu,ƙato dakai,"tana kai ƙarshen maganarta,junaid yace"idan kin tashi ki faɗama Kaka ƙarewar daddyn,mai kan kurciya kawai" wannan maganar ba ƙaramin fusata hosana tayi ba,jikinta har rawa yakeyi wurin dauko pillow daga saman gadonsu,ta buga mashi asaman fuskarshi,koda ganin hakan,sehrish ma ta ɗauko pillow ta shiga taya hosana,jahad tace"wlh nima bazan ƙyale ka ba,junaid saboda ka bani tsoro,kuma babu kyau ma tsoratar da musulmi,"tasa hannu ta ɗauko pillow itama,nan fa suka tasa junaid kamar sun samu jaki,suka dingi jibgarshi da pillows,tun yana yi masu magiyar su daina har ya sake fashe masu da kuka yana bubbuga ƙafafunshi,suna cikin bugun nan nashi,suka ji tsit junaid ya daina motsi,cikin sauri Jahad ta kalli jikin pillown hannunta,Ɗigon jini ta gani,ɗagowa tayi da nufin ta nuna ma su Sehrish aikuwa karaf idonta ya sauka akan pillown dake hannun sehrish da hosana,duk ɗigon jini ne ajikin pillown hannunsu,Tashin Hankali!   Gaba ɗayansu ba ƙaramin kiɗima suka yi ba,ƴan hanjin cikinsu suka kaɗa,zagaye shi su kayi a zuƙunne suna kallon fuskarshi,   Fashewa hosana tayi da kuka tana faɗin"Wlh babu ruwa na!bani na kashe junaid ba!"maganar da tayi ba ƙaramin tsoratar dasu tayi ba,tuni ido ya raina fata,daga wasa!?   Jijjigashi suka shiga yi atare suna ambaton sunanshi"Junaid!junaid!!!ka tashi!dan Allah junaid ka tashi!!Wayyo Allah munshiga ukun mu!!dan Allah baby junaid ka tashi," ko motsi wannan junaid baiyi ba,matsawa sehrish tayi tare da kanga kunnanta asaman hancinshi don taji in yana numfashi,ɗufff taji babu numfashi da sauri ta sanya tafin hannunta asaman kirjinshi saitin zuciyarshi nan ma taji zuciyar tashi tadaina bugawa,a wani irin sukwane ta ɗago da idanunta waɗanda sukayi luhu luhu cike tab da hawaye tana kallonsu Jahad da hosana,jiki a mace tace"ZUCIYAR JUNAID BATA BUGAWA HAKAN NA NUFIN MUNYI SILAR MUTUWAR JUNAID"!!!   Girgiza kai jahad ta shiga yi tana cewa"Junaid bai mutu ba,dan Allah ki daina faɗan hakan,kada ya tabbata dagaske,"tayi maganar a yayin da take kai hannu tana tatta6a fuskarshi"junaid!junaid!ka tashi dan Allah ka tashi junaid,"    Ganin yaƙi motsi yasa suka fidda rai da cewar junaid zai tashi,kifa kai sukayi su duka ukun suna shessheƙar kuka,ɗan ɗagowa jahad tayi tare da kai idonta kan fuskarshi,Abun mamaki sae ga murmushi ya bayyana akan fuskarshi,dimples ɗinsa guda biyu sun lotsa,Wani irin ihun farin ciki ta saki tana fadin"Bai mutu ba!junaid wasa yake yi mana,gayanan yana murmushi,'jin haka yasa su sehrish saurin ɗagowa da kawunansu suna kallonshi,sae faman wangale baki yakeyi yana dariya,abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yayi ba,   "Junaid"sehrish ce ta ambaci sunanshi,a hankali ya buɗe manyan idanunshi yana kallonsu one by one,sai faman 6a66aka dariya yakeyi,   Har suna haɗa baki wurin cewa"Kai junaid!meyasa zakayi mana haka?wlh ka tsoratar damu sosai,"   "Wanda yasa kuka bugeni,ko tausayina bakuji,kun wani taru akaina kuna jibgata kamar kunsamu jaki amale,shiyasa nima na rama da gangan na ɗauke numfashina don kuyi tsammanin kona mutu"yayi maganar yana murguɗa masu baki,Ajiyar zuciya suka shiga saukewa,   "Junaid dan Allah kayi haƙuri,bazan ƙara bugunka ba,kada ka faɗama kowa,"acewar hosana,   Harara ya jefa mata tare da ƙara tamke fuskarshi,   Cikin sanyin murya jahad tace"junaid baka da lafiya ne?mun ga jini ajikin pillow lokacin da muke bugunka,kuma da alama daga hancinka muka gogo shi,"   Shiru ya ɗan yi yana kallonta kafin yace"Lafiyata ƙalau Ni,nose bleeding ne ba wani abu ba dama ina yawan yinshi,yafi zuwa mun da daddare,shiyasa baku ta6a gani ba"   "Amma ka faɗama Abba ko wani game da nose bleeding din"? Girgiza kai yayi alamar a'a,da alama baison maganar,don haka yace"pls nidai mubar wannan zancen,kusan yadda za kuyi dani don Allah bazan iya komawa bedroom ɗina ba,tsoro ma nakeji,"yayi maganar ashagwa6e,   Jiki asanyaye jahad ta kalli su sehrish tace"kuje ku kwanta,bari ni na rakashi ɗakin nashi," mikewa su kayi atare da ita da hosana suka koma kan gadon suka kwanta,tare da jan bargo suka lullu6e,     Miƙewa daga zaune junaid yayi yana cewa"Allah sai dai ki goyani,don na riga dana faɗa maki cewa ƙafafuna ciwo suke yi mun bazan iya taka stairs ba,"   Murmushi jahad tayi tare da cewa"shikenan,zan goya ka amma ka bari sai munje wurin benen tukunna in goya ka," amsa mata yayi da toh,sannan ya mike tare da ruƙo hannunta cikin nashi yace"Tashi muje,"mikewa tayi suka fita atare,suna tafiya tana satar kallon gefen fuskarshi kamar wani zautacce sai faman sakin murmushi yake yi,hakanan ta dinga jin gabanta na faɗuwa,lamarinsa ba ƙaramin mamaki yake bata ba,kokonto ta shiga yi anya wannan ɗigon jinin da suka gani na ha6o ne? Yanayin yadda abun ya afku tamkar ba jinin ha6o bane,tabbas akwai dae wani abu dake damunshi wanda baison kowa ya sani, Tana cikin zancen zucin nata taji yace"Mun ƙaraso wurin stairs ɗin,yanzu ki goyani,ki kaini har bedroom ɗina,kuma ki kwantar dani,"   Amsa mashi tayi da toh,sannan ta zuƙunna,ya daddage ya haye saman bayanta,tare da kwantar da kanshi luff kamar wani jinjiri,zagayo da hannayenshi yayi ta saman stomach ɗinta,hakan ba ƙaramin yanayi ya jefa ta ba,ji tayi tamkar bazata iya miƙewa tsaye ba,saitin kunnanta taji daddaɗar muryar nan tashi mai haɗe da shagwa6a"jahad ki tashi mu tafi,bacci nake ji,"   Daƙyar ta iya mikewa tsaye goye dashi abayanta,hannu tasa ta tallaboshi sosai,sannan ta haye saman benen,tana tafiya tana tangal tangal har ta ƙaraso ɗakin nashi,hannu tasa ta ɗan tura ƙopar sannan ta shige ciki,Talal suka samu kwance yana ta sharar bacci,ƙarasawa tayi tare da sauke junaid saman gadon,ya gyara kwanciyarshi,bargo taja ta rufe mashi body ɗinsa zuwa neck ɗinsa,tana ƙoƙarin juyawa tabar wurin,taji ya ruƙo hannunta cikin nashi,jimmm tayi tana jiran jin me zaice mata,   "Jahad"ya ambaci sunanta da wata irin murya ta mai jin bacci,   "Na'am,"ta amsa mashi kiran a yayin da take juyowa" murmushi ya sakar mata tare da sanya yatsan hannunshi acikin dimple ɗin fuskarshi yace"Kiss me pls," bakomai ya faɗo mata aranta ba,face abunda ya ta6a faruwa atsakaninsu,cikin motarshi,daga zuwa manna mashi kiss a side face ɗinsa,bakinta ya goce izuwa cikin bakinsa,a ranar zauce mata yayi,   Maƙe masa kafaɗa tayi alamar bazatayi mashi kiss ɗin ba,bubbuga ƙafarshi ya shiga yi yana yi mata shagwa6a,hakan ba ƙaramin burgeta yayi ba,saboda wani irin kyau da yake bayyana akan fuskarshi aduk lokacin da yake shagwa6a,tamkar tayi hugging ɗinshi ajikinta haka ta dinga ji,    "Baza kiyi mun ba ko"?yayi maganar.yayin da idanunshi ke ƙoƙarin lumshewa,    "Shikenan,zanyi maka,amma ka rufe idanunka," da sauri ya rufe su yana jiran jin la66anta asaman fuskarshi,tsayawa tayi asaman kanshi,tana karanto addu'o'i tana tattofa mashi akan fuskarshi,daga ƙarshe ta haɗe yatsun hannunta guda biyu na hannun damanta,a hankali ta aza yatsun nata asaman la66ansa,sannan ta furta sautin kiss ɗin da bakinta,wani irin farinciki ne ya lullu6e junaid,duk a tunaninshi bakinta ne ta aza asaman nashi,baisan cewa wayau tayi mashi ba,tasa yatsun hannunta amatsayin la66anta, rufe mashi fuskarshi tayi da bargon,sannan ta kama hanyar fita daga bedroom ɗin,    "I Love u so much jahad," muryar junaid ce ta katse mata hanzarinta,dakatawa tayi tare da ɗan juyawa tana kallonshi,yana acikin bargon ya furta mata wannan kalmar,    "Kina sona jahad"? Wani irin ƙayataccen murmushi ne ya sauka akan fuskarta,bata bashi amsar tambayarba,cikin sauri ta fuce daga ɗakin nashi,ta koma bedroom ɗinsu ta kwanta zuciyarta cike fal da farin ciki,ta ji daɗin kalmar da junaid ya furta mata,duk da bata da tabbacin cewar ko dagaske yake yi mata," da wannan tunanin bacci ya ɗauketa,   *Boss Bature*     🤍❤? Washe Gari, Kwance take asaman katifarsu,ta saki baki tana ta sharar baccinta,sae faman jan minshari takeyi kamar Ragon layya ga miyan bacci dake gangarowa ta cikin bakinta da ta bari a buɗe,tana cikin baccin nan taji Ringing ɗin wayarta da ƙarfin gaske har cikin dodon kunnanta,hannu tasa tare da toshe kunnanta tana faman buga tsoki,alamar an takura mata,bata ɗaga kiran ba,har ya katse kuma sai ga wani kiran ya ƙara shigowa,a hargitse Abra ta miƙe ranta a matuƙar 6ace,tasa hannu ta dauki wayar dake ajiye gefenta,picking call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta Cike da masifa tace"Wai Uban wanene ke kirana tunda sanyin safiya"?   Kafin ta rufe bakinta taji ance"Ubanki ne!" har sai da gaban abrah ya faɗi rasss,cikin sauri ta janye wayar daga kunnanta tare da kallon screen ɗin wayar don ta shaida mai kiran nata,Sunan Aunty babba ta gani,yatsina fuska tayi kafin ta mayar da wayar a kunnanta,"ina kwana aunty,an tashi lafiya"   Rai a6ace Aunty babba tace"Ruƙe gaisuwarki,sakarya daƙiƙiya zaman uban mi kike ke da Mammy da har kuka bari AMAL ta gudo daga mai duguri tazo Abuja wurin Amani?!" jin wannan maganar yasa abrah ta zabura,don har sai da ta daki ƙirjinta da hannunta,Hankali atashe tace"Aunty laila dagaske Amal tana abuja wurin Amani!"   "Ƙarya zan maki ne?Kuna nan sake da baki har yarinya ƙarama tayi maku wayau ta gudu,Yanzu baki ga yadda Amal ta koma ba,Yarinya ta zama ƴar hutu kamar wadda ta taso a gidan naira,Tamkar bata ta6a shan wahala ba,Irin rayuwar dana so ace ke kika same ta,sae gashi ƴar kishiyar da muka tsana ita ta samu wannan damar,ina nan dake in har mu kayi sake AMAL sai ta auri ɗaya daga cikin ƴa'ƴan Alexandra,"   Saboda tsabar takaici Hannu ɗaya abra ta aza asaman kanta tana faɗin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un! Aunty babba tace"kaɗan ma kika gani!duk laifinku ne!da alama su Amani sunfi mu Jinin Nasara,shiyasa suke ta cin galaba akan mu,"   Muryar abra tamkar zatayi kuka tace"Wlh aunty laila har shawara sai da naba mammy tun kafin amal ta gudu nace mata mu 6alle ƙafarta guda ɗaya,don ta zama gurguwa kinga in mukayi hakan ba yadda za'ae ta gudu,Amma saboda shegen son kuɗi irin na mammy tace Wai mu barta da ƙafafunta,saboda tana so Amal ta auri mai kuɗi don ta rinƙa tatso mana kuɗi a wurinta,Yanzu gashi nan Mammy taja mana"   Shiru suka ɗanyi na wani lokaci kafin Aunty babba tace"Abra inaso kiyi gaggawar tattara kayanki kibar gidan nan!kema ki dawo Abuja gidan surukanmu da zama!wannan kaɗae ce hanyar da zamu iya cin nasara akansu,"   "Aunty in dawo nan fa kika ce?Aunty hayaam fa?zata dawo gida ne"? "Bazata dawo ba,zama ma yanzu ta fara shi har sai an shafa fatihar aurenta da Babban yayansu,kawai abunda nakeso dake,ki tattara kayanki ki dawo gidan da zama,saboda ni bani da tabbacin cewar zama na zaiyiyu acikinsa,atakure nake,"   Jinjina kai Abra tayi tamkar tana agabanta tace"Shikenan Aunty laila,da yaushe kikeso inzo nan ne?kuma ya zamuyi da mammy?kinsan fa bata da lafiya tana can kwance,"   Dogon tsoki Aunty babba taja tare da cewa"Wake ta wani mammy?ae kawai ki tattara kayanki yanzun nan ki biyo motar Abuja ta kawoki,Ita kuma mammy Allah ya bata lafiya shine kawai,"   Fuskar Abra ɗauke da murmushi tace"aikuwa yanzun nan zan shirya,zan ma iya sa ɗaya daga cikin samari na,ya kawoni gidan don duk suna da Mota,"   Aunty babba tace"Yawwa cikin sauƙi ma,ki kira ɗaya daga cikinsu,ya kawoki,"   "In sha Allah Auntyna," abra ta amsa mata kafin sukayi sallama, Duk wannan wayar da Aunty babba keyi kaf a kunnan Hafsat da hayaam dake kwance saman gado,ita kuma tana zaune asaman Stool dake agaban mirror,    "Mommy wannan abun kunyar har ina?taya zaki ce abra tadawo gidan nan da zama?bayan ga hayaam kuma!Nan fa gidan surukanku ne ba gidan ƙanin mahaifinku ba...." a fusace Aunty babba ta jefa ma hafsat wayar hannunta cikin sa'a tasamu gefen goshinta,dafe wurin hafsat tayi saboda zafin da taji,   Rai a6ace tace"Hafsat ki fita daga idona in rufe!kina yimun shisshigi acikin lamurrana,Ina ruwanki da zaman su Abra acikin gidan nan?ke zaki ciyar dasu ne?ko saman kanki zasu zauna ne"?   Shiru hafsat tayi batare da ta tanka mata ba,hayaam dae bata sanya masu baki ba,saboda gudun rashin kunyar hafsat don bata raga ma kowa acikinsu, Wuraren ƙarfe tara,Azmee da Saude suka kammala girke girken breakfast na gidan,yanzu ta samu sauƙi wurin yin aiki don Saude ba ƙaramin taimaka mata takeyi ba,dayake itama kwararriyace wurin iya girki tana son yin girki,bayan sun kammala,Azmee ta shiga jera mata Warmers acikin tray tana kaiwa saman dining table,cikin lokaci ƙanƙani suka kammala jera abincin, ɗaya bayan ɗaya matasan gidan suka shiga fitowa daga bedroom ɗinsu,su Kanal yousouf,Irfan jabeer khaleed twins,fawan,sune waɗanda suka fara hallara daga baya,Abbansu tare da Mommynsu junaid suka fito,kafin wani lokaci kowa ya fito,hadasu Dr haris su Captain adam,najeeb talal da kuma junaid,da sauransu duka dai,Mutun ɗaya ne bai fito ba,bakowa bane fa ce Surgeon general Rafayet, Bayan matasan sun hallara Azmee taje ɗakinsu Sehrish ta taso su daga bacci,atare suka fito bayan sunyi brush su uku kowacce sanye da hijabi ajikinta,tun ta sallar asuba ce da suka sanya ajikinsu basu cireta ba,bacci yayi awon gaba dasu,   Gaishe dasu Abba suka fara yi,fuskar kowannansu ɗauke da murmushi haka suka shiga amsa masu gaisuwar,daga bisani suka shiga gaisar da yayyensu,kowa da irin yadda yake amsa masu gaisuwar cike da zolaya,don wasu ma hada kwaikwayon Muryarsu,hakan ba ƙaramin nishaɗi ya sanyasu ba, Komawa su kayi tare da samun wuri suka zauna a dining chairs ɗin da Abusufyan ke zaune,atare suka haɗa baki wurin cewa"Daddy ina kwana?ka tashi lafiya," ɗagowa yayi tare da kallon fuskokinsu ɗaya bayan ɗaya kafin yace"Lafiyalou Alhamdulillah!" Natsuwa kowa yayi,yayin da Azmee da saude suka shiga zuzzuba masu abincin,kowa na faɗin abunda yake so yaci,   Gyaran murya Abba yayi tare da kallon azmee yace"An kai ma Ammi nata breakfast ɗin"!?   azmee tace"Eh nakai masu,a ɗakin gwaggo don acan tace mun zatayi kalacinta,ita da ƴar uwarta,"   Murmushi ya ɗan yi don ba ƙaramin daɗi yaji ba,   "Azeema fa"? Ya kuma tambayarta, "Itama tana atare dasu,can ɗakin gwaggon," Jinjina kai abba yayi kafin ya kuma cewa"Aunty saratu fa?da ƴanmatan ta suma ankai masu nasu"?   Saude ce ta kar6e da cewa"Ni nakai masu a ɗakinsu,"   Abba yace"Aikin ku yayi kyau,"ya ƙarasa maganar tare da kai hannu ya ɗauki plate ɗin dake hannunsa yaci gaba da cin abincinsa da azmee ta zuba mashi,   Abbas yace"Azmee banga su Amal ba?ko ankai masu nasu ne"?yayi maganar ayayin da yake ƙoƙarin ajiye spoon ɗin dake hannunshi,?       "Na kai masu a bedroom ɗinsu," ta bashi amsa,   Ganin Abbas ya tambayi iyalinsa ne yasa Ishaq yin gyaran murya yace"Azmee wai ni ina ƴata hafsat ne?ko an manta dasu ne?naga ban gansu ba!?   "Ni kaina inata so in tambayesu,tun shekaran jiya rabon da in Sanya su a cikin idona,tamkar basa a cikin gidan nan"!Acewar Abbansu,   "Bari na kirasu,"Azmee ta faɗi hakan tare da juyawa ta nufi ɗakinsu laila,   abinci take ci,amma hankalinta ba akwance yake ba,Yau tunda ta tashi daga bacci gabanta ke ta faɗuwa rasss!rasss!mafi yawancin lokutta in taji gabanta na yawan faɗuwa to tabbas wani abune zai faru da ita!mai kyau ko mara kyau,sam takasa cin abincinta,sae faman jujjuya cokalin hannunta takeyi acikin plate ɗin dake agabanta,    A hankali ta ɗago da idanunta tare da azasu akan Hosana dake ta faman cunkusa Burger acikin bakinta,yadda kasan zata 6ara bakin ko gajiya da Ci ba tayi,Allah sarki rayuwa kenan,Allah mai yadda yaso,kamar basu bane waɗannan yaran ba,masu yawo babu takalmi a ƙafafunsu,kawunansu babu ɗan kwali,Kayan jikinsu duk a yayyage,babu mai son su,rayuwarsu a wulaƙance kowa gudunsu yakeyi,Amma yanzu komai ya canza!Yanzu gasu acikin danginsu,kowa sonsu yakeyi,suci mai kyau su sha mai kyau,su kwana a mai kyau,suturar sawa ma sai sun za6i wadda suke so su sanya ajikinsu,duk mai yajawo wannan, haƙuri!sun rungumi ƙaddararsu sun cinye jarabawar da Allah yayi masu,basuyi gajan haƙuri ba,kullum cikin kai kukan su wurin Allah suke,saboda sun san cewa shi kaɗai ne zai iya share masu hawayensu,duk irin ƙuncin rayuwar dasu Sehrish suka shiga,basu ta6a ƙasƙantar da kansu ba don suyi bara,ko su siyar da mutuncinsu don su samu kuɗi,kamar yadda wasu mutanen keyi, Janye idanunta tayi daga kan hosana ta mayar dasu kan jahad,wadda ke ruƙe da bread a hannunta,tana goga mashi butter,abun ya ɗaure mata kai kowa sai cin abinci yake yi hankali kwance,amma ita takasa Cin nata,to ko dai bata da lafiya ne? ta ƙarasa zancen zucin tare da juyawa,karaf idanunta suka sauka akan Fuskar Abusufyan wanda ke kallonta,har sai da ta ɗan razana kaɗan,sunanshi ta ambata abakinta a hankali"daddy," ..murmushi ya ɗan sakar mata tare da cewa"Daughter,tun ɗazu ina kallonki,kin ƙi cin abincinki,kin tasa ƴan uwanki gaba kinata kallonsu ɗaya bayan ɗaya,faɗamun meke damunki ne'?   "Daddy am not feeling well,gabana sai faɗuwa yakeyi,bansan meyasa ba,shiyasa ma nagaza cin abincin"muryarta akasalance tayi maganar,   Jahad tace"Daddy,jiya ma batayi wani isasshen bacci ba,"   "Saboda me"?yayi tambayar yana kallonta,   "Nikaina bansan meyasa ba,kawai bana jin daɗi ne,"   Jinjina kai yayi tare da cewa"Kada ki damu in sha Allah wannan faɗuwar gaban da kikeji Alkhairi ne zai faru dake,"   "Allah yasa haka ne daddy" ta ƙarasa maganar tare da kai hannu ta ɗauki cup of tea ɗin dake agabanta,ta shiga kur6arsa a hankali,ba don tana jin daɗinsa ba, Suna cikin cin abincin nan,sae ga Azmee tare da hafsat,sun shigo dining area ɗin,Aunty babba na a bayansu ta sanya Niqab a fuskarta,hayaam dai bata fito ba,saboda gudun karsu haɗu da Sgr a wurin,da hannu Azmee tayi masu nuni da su zauna a inda su Jahad suke,saboda nan ke akwai empty chairs guda biyu da suka rage,da yake table ɗin mai mazaunin mutun Shida ne,   Tunda suka zo wurin,idon kowa ya koma akan Aunty babba dake sanye da niqabi,abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yayi ba,sai da suka fara gaishe dasu Abba,sannan suka samu wuri suka zauna,hankalin Aunty babba sam ba'a kwance yake ba,bata so fitowa ba,Azmee ce ta sanar da ita cewa Ishaq yace su fito dining suci abinci,tayi mata hakan ne saboda ta rama Wulaƙancin da sukayi mata, Daƙyar ta iya gaishe da Abusufyan,batare daya ɗago ya kalleta ba ya amsa mata,hafsat tace"Uncle ina kwana,"? "Lafiya lou hafsat,ashe kuna acikin gidan,ae nayi tunanin kun koma Kaduna ne," Murmushin yaƙe tayi,sae faman zazzare ido takeyi,duk sunbi sun tsargu,ita da mommynta,ita dai Sehrish ta zuba ma sarautar Allah ido,so take taga ta yadda Aunty babba zataci abinci da niqabi a fuskarta,ba ita kaɗae ba hatta jahad abunda take jira kenan,Ishaq kuwa tuni ranshi yayi mugun 6aci,sarai yasan cewa da gangan ta zura niqabi a fuskarta bayan tasan cewar abinci zata ci,alamun rashin gaskiya duk sun bayyana atattare dasu,ita da hafsat, Serving ɗinsu Aunty azmee tayi,ta tura masu plate ɗin abincin agabansu,hafsat dai tayi kokarin cin abincin,kaɗan kaɗan take tura chips abakinta,Aunty babba kuwa kamar gunki haka ta ƙame saman kujerar taƙi motsi,fargabarta kada hosana ta gane cewa itace, Murmushin mugunta sehrish ta saki,tare da yin gyaran Murya tace"Aunty,ki cire niqabin mana,in ba haka ba,bazaki ji daɗin cin abincin ba,gashi yana ta hucewa,bazaiyi maki daɗin ci ba inya salafce," Mazurai Aunty babba tashiga yi ta cikin niqabin,ƙululun baƙin ciki kamar ta shaqo sehrish ta rufe ta da bugu,ƙin magana tayi saboda gudun kar Hosana taji Muryarta,ta kara tona mata asiri,hakan yasa Jahad cewa"Na ji tayi shiru,kodai bacci ne bai isheta ba"?tayi maganar tana faman ƙumshe dariya abakinta,sehrish tace"inaji tayi bacci ne a zaune,bari na cire mata niqabin don tasha iska kada numfashinta ya sarƙe," yunƙurawa Sehrish tayi tare da kai hannu zata zame niqabin dake a fuskar Aunty babba,ae kuwa a firgice Aunty babba ta zabura ta miƙe tsaye tana faɗin"Karki kuskura ki ta6amun niqabi na," rai a6ace tayi maganar,aikuwa Hosana najin Muryarta,ta daddage ta fasa uwar ƙara,tare da yin wurgi da kofin dake a hannunta,a gigice ta miƙe tana ƙokarin guduwa,gaba daya hankalin kowa ya dawo kanta,Omar ne ya miƙe da sauri ya ruƙo hannunta yana tambayarta lafiya, A tsorace tashiga fadin"Banason ta!na tsane ta!wlh ya Omar muguwace matar nan,tazo nan ne don ta kashe mu,dan Allah ku koreta daga gidan nan,wayyo Allah na....."ta fashe da matsanancin kuka,tashin hankalin da ba'a samashi date!nan fa kowa ya miƙe tsaye yana bin Aunty babba da kallo,saboda tsabar ruɗu muryarta na kerma tashiga cewa"wa...wallahi Billahil azimu Ni bansanta ba!bansan laifin me na aikata mata ba,yarinyar nan fa mahaukaciya ce tana da ta6in hankali,shiyasa take wannan sambatun...."tunkan ta ƙarasa maganar Abusufyan ya daka mata tsawa tare da cewa"karki kuskura ki ƙara kiran ƴata da sunan mahaukaciya!in ba haka ba ranki zai 6aci a wurin nan ne!hosana bazata ta6a tsangwamar mutun hakanan ba batare daya aikata mata wani mugun abun ba," ya karasa maganar tare da jan dogon tsoki, "Ya Omar dan Allah ku sakar mata karnuka su fiddata daga cikin gidan nan,wlh babu Allah aranta!so take takashe maka hosanarka,"cikin shesshekar kuka take maganar,Marshal sai ƙokarin rufe mata bakinta yakeyi don ta daina amma ina hosana taƙi rufe bakin,don har cizon hannunshi takeyi,in yayi ƙoƙarin toshe mata baki,Aunty babba kuwa sae faman zabga salati takeyi,jikinta sae kerma yakeyi,tuni zufa ta jika ta sharkaf,ƴan hanjin cikinta kuwa sae faman kaɗawa sukeyi,hankalin General ishaq ba ƙaramin tashi yayi ba,tsoranshi kada ace wani mugun abunne laila ta aikata ma yarinyar da har take tsoron ganinta, Lalla6awa Aunty babba tayi da gudu tabar dining area ɗin ta koma cikin dakinsu,tana shiga ciki ta aza hannayenta asaman kanta tana faɗin"Na shiga uku!Na bani!na lalace!Waccen mahaukaciyar yarinyar tana son taja mun bala'e ina zaman zaman lafiyata,"tana magana tana cizon yatsan hannunta,"Aunty laila meya faru,"hayaam ce tayi mata tambayar, "Hayaam ta faru ta ƙare!yarinyar can ta gama dani!"muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,hannu tasa tare da zame niqabin fuskarta,tayi wurgi dashi ƙasa,sannan tashiga zagaye ɗakin tana faman cizon yatsanta, "Dan Allah kowa yayi haƙuri ya koma ya zauna,ina tunanin ciwon hosana ne ya motsa,ba wani abu ba shiyasa take ta sambatu,"Omar ne yayi maganar don ya kwantar masu da hankalinsu, Fashewa da wani sabon kukan hosana tayi tana faɗin "Wlh ya Omar Ni da hankalina,da tunani na!nasan me nakeyi,wannan matar itace ta...."kasa ƙarasa maganar tayi saboda tsawar da Omar ya daka mata "Shut up hosana!bana son na ƙara jin maganarki a wurin nan!in ba haka ba saina sa6a maki," tafin hannunta tasa tare da toshe bakinta,tana yin kuka ƙasa kasa, "Ka daina yi mata tsawa Omar,tabbas akwai abunda akayi ma yarinyar nan,wanda ya ƙona mata zuciya shiyasa take wannan sambatun,ya kamata mu lallasheta,muji menene matsalarta"? Acewar Abba, Ishaq yace"hakane,In ba damuwa Inason ganinka Omar tare kuma da yaran," Ya ƙarasa maganar tare da shigewa gaba,Omar yabi bayansa hannunshi ruƙe dana hosana,jahad kuma na abayansu, Bayan tafiyarsu,kowa ya koma ya zauna,wasu suka cigaba da cin abincinsu,wasu kuma suka bar dining ɗin waɗanda suka ƙoshi da abincin kenan,wurin yayi tsit kowa da abunda yake saƙawa aranshi, A 6angarensu General ishaq kuwa,a farfajiyar gidan suka zauna saman wasu ƙayatattun kujeru na shakatawa,kowa ya zauna,Hosana da jahad suna fuskantar Ya Omar da kuma ya ishaq, Gyaran murya ya ɗan yi tare da kallonsu yace"dalilin dayasa na buƙaci ganinku,saboda inason jin menene alaƙar dake atsakaninku da Laila matata?shin taya akai hosana ta santa da har take tsoran ganinta"? Kafin su bashi amsa Omar yayi hanzarin cewa"Ae farko sun ta6a zama a wurinta,Ni na kaisu gidanka,a lokacin kayi tafiya,na damƙa amanarsu a wurin laila,saboda ina da tabbacin cewar zasu samu kyakkyawar kulawa a wurinta,tun da ita mace ce,zasu fi sakewa a wurinta," Tunda ishaq yaji hakan gabanshi ya fadi,saboda yasan halin laila sarai,bata da mutunci,saboda mugun halinta yasa masu aiki suke gudun gidan,duk ƴar aikin da sukayi ƙarshe guduwa takeyi daga gidan saboda masifarta, janye idonshi yayi daga kan Omar dake magana,ya mayar dasu kansu jahad da hosana,yace"Ina sauraronku?A zaman da kukayi tare da laila me ya faru? Jahad tace"babu komai,munyi zaman lafiya tare da ita,"tana rufe bakinta hosana tace"wlh ƙaryane!jahad ƙarya takeyi maku,batason ta faɗi gaskiya ne,"ta ƙarasa maganar tana matse kwallar data zubo mata a idanunta, "Jahad!kinsan banason wasa!faɗamun gaskiyar abunda ya faru acikin gidan,bayan na barku," Marshal ne yayi maganar fuskarshi a ɗaure babu alamun wasa tattare dashi,hakan ne yasa jahad ta natsu ta shiga kora masu bayani, "Ya Omar,tun lokacin da ka tafi kabarmu a gidan,Aunty laila ta rufe mu acikin wani tsohon store,babu ci babu sha,iska kanta daƙyar muke shaƙarta saboda wurin a ƙuntace yake,babu window,ga ƙwari dake yawo acikin store ɗin,ranar acikinsa muka kwana,hosana ko bacci bata samu ba......"gaba ɗaya jahad ta kwashe duk abunda ya faru dasu agidan Aunty babba,tun daga A har Z ta sanar masu,a ƙarshe ta fashe da kuka, Ishaq kuwa ba abunda ke fitowa daga bakinshi sai kalmar innalillahi'wa inna ilaihirraji'un,'Muryarshi har kerma takeyi wurin cewa"Omar meyasa ka kaisu gidana ne?wlh da ace ka sanar dani tunda farko,da banbari ka kaisu wurin laila ba,saboda nasan halinta,hakanan nake zaune da ita,matar nan bata da imani!muguwace!yanzu ni bansan ya zanyi ba!da wani ido zan kalli Abusufyan da sauran ƴan uwana idan sukaji wannan Zaluncin da laila ta aikata ma Yaran nan!! Yana magana,huci na fitowa daga bakinshi,ranshi yayi mugun 6aci idanuwanshi sunyi jawur, Marshal Omar kuwa saboda tsabar 6acin rai,ya gaza buɗe baki yayi magana,tamkar ya haɗiyi zuciya ya mutu saboda takaicin abunda laila ta aikata ma su jahad,yaran da ya damƙa mata amanarsu,sai yanzu ya gane dalilin da yasa duk in yaje gidan a lokacin da suke wurinta,sai yaga fuskokinsu babu walwala ashe bayin Allah azabtar dasu takeyi, Daƙyar ya iya buɗe baki yace"Amma Laila ta cuce Ni!ban ta6a tunanin zatayi mun haka ba,Meyasa zatayi mun haka?laifin me kuka aikata mata?kawai saboda taga baku da gata ne,don nace mata marayu ne ku shine ta ƙuntata rayuwarku?Ashe itace ta sanya wannan fasiƙin mutumin ya ɗauke ku acikin motarshi don ya zubar mata daku acikin dajin,har yayi ƙoƙarin Yima hosana fyaɗe acikin gidan gonarshi.... " sai yanzu ya gane dalilin da yasa Major yaƙi sanar dashi gaskiyar lamarin daya afku,koda ya tambayeshi a lokacin baya sai cewa yayi yalla6ai banso in shiga tsakaninka da Matar yayanka ne,Ashe mugun abu ta aikata masu, A fusace Ishaq ya daki table ɗin dake agabansu,ya miƙe azabure yana ƙokarin zame belt ɗin wandonshi,a ƙoƙarinshi na ya shiga cikin gidan yayi ma Aunty babba bugun tsiya, Da sauri Omar ya ruƙo hannunshi,"Ya ishaq,ba anan yakamata ka yanke mata hukunci ba,koba komai ita uwar ƴa'ƴanka ce,mutuncinta zai zube agaban kannenmu,da sauran mutanen gidan,inaso taci albarkacin wannan," Runtse ido ishaq yayi wani irin huci ke fita daga bakinsa,damƙar hannun Omar yayi tare da janye shi daga ruƙon da yayi mashi,ko waiwayenshi baiyi ba ya shige cikin gidan, Jiki ansayaye Omar ya mayar da idanunshi kan su hosana dake tsaye,wani irin tausayinsu ne ya lullu6eshi,matsawa yayi tare da janyosu ya rungumesu ajikinshi,tamkar ya zubar masu da hawaye haka yake ji,Yayi danasanin kaisu wurin laila,bakomai ne yaja hakan ba fa ce rashin sani,cikin sanyin Murya yace"kuyi haƙuri ku yafe mun,duk laifina ne dana kaiku wurinta,wlh danasani kai tsaye Abuja na kawoku gidanmu,Ni duk atunanina zaku fi samun kulawa a wurinta,ƙaddarace kawai ta riga fata,Amma wlh da ace kun sanar dani tun lokacin da nake zuwa gidan,da saita ɗanɗani kuɗarta," ya ƙarasa maganar a lokacin da yake ƙoƙarin raba jikinshi daga nasu, Jahad tace"Ya Omar kadaina ɗaura ma kanka laifi,dama can Allah ya ruga da ya ƙaddara faruwar hakan,kuma yanzu ae komai ya wuce,ni wlh ba don hosana ta fara tona mata asiri ba,da babu wanda zaiji wannan maganar abakina,don har gargaɗin hosana nayi akan kada ta sanarma kowa amma bataji ba," Murmushi Omar ya ɗan yi tare da kallon hosana dake ta faman sauke ajiyar zuciya,ruƙo hannunta yayi cikin nashi sannan yace"Hosana tayi mun dai dai jahad!idan har aka biye ta taki,bazaki ta6a bari a hukunta mara gaskiya ba,saboda tausayinki,abunda nakeso ki gane jahad,Irin waɗannan mutanen masu baƙar zuciya,idan har ba'a dinga hukunta su ba,to basu ta6a gane kuskurensu,balle har suyi nadamar abunda suke aikatawa su daina," jinjina kai jahad tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Hakane ya Omar,kayi gaskiya,Sehrish ma ta ta6a fadamun hakan,lokacin da nayi ƙokarin hukunta hosana akan tonan asirin da taso tayi ma matar Ya ishaq,' sun jima atsaye suna magana kafin daga bisani Omar ya ruƙo hannayensu tare da shigowa dasu cikin gidan, Hankalin aunty babba fa yaƙi kwanciya,babban abunda takeyi ma fargaba shine kada Hosana ta tona mata asiri agaban surukansu,kusan sau uku tana shiga toilet saboda cikinta daya katsa,har wurin ƙarfe 2:30,bata daina safa da marwar nan ba,acikin ɗakin,ƙafafunta har sai da suka fara yi mata raɗaɗi sannan ta samu wuri ta zauna daga gefen gadon tana faman sakin huci,shigowa hafsat tayi cikin ɗakin,fuskarta jawur sae faman kuka takeyi,aunty babba na ganinta ta miƙe hankalinta a matuƙar tashe ta shiga tambayarta Meya faru,Cikin shessheƙar kuka hafsat tace"daddy ne,Yayi mun faɗa sosai akan abunda muka aikata masu hosana,har mari na sai da yayi,kuma yace daga yanzu babu ni babu shi,In nemi wani uban,!" Hannu aunty babba ta aza asaman kanta tana ambaton"Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un!wayyo!nashiga uku!shikenan Hosana ta gama dani ta tona mun asiri wurinsu ishaq,Wayyo Ni laila,Zawarci ba fashi," tana magana tana cizon yatsanta,   Fitowar hayaam kenan daga cikin toilet taji suna wannan maganar,jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,babban abunda take ji ma tsoro shine Ishaq ya saki Laila,saboda tasan cewa muddin ya saki aunty babba,to zamanta a gidan ya qare!!tunda bata da wata aƙala dasu,!Tashin hankali,ishaq bai ta6a gigin ta6a jikin hafsat ba,duk irin girman laifin da take aikatawa,amma yau akansu hosana Tasha mari,idan har hakane menene hukuncin aunty babba?ita da ta ɗauki nauyin shirin gaba daya,OMG!! Rungumota hayaam tayi ajikinta tana lallashinta,daƙyar ta samu hafsat tayi shiru, *Boss Bature*   ❤🤍❤💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Wuraren ƙarfe shida na marece,ta fito daga cikin toilet,jikinta na sanye da towel fari ta ɗaure shi a saman ƙirjinta,da alama wanka tayi aciki,jahad ta samu zaune saman gadonsu,hannunta ɗauke da wayarta tana ɗan daddanawa,tsayawa tayi a ƙopar toilet ɗin ta ruqe ƙugunta tare da ɗan ɗaure fuskarta tace"Jahad!bana hanaki ɗaukarmin waya ba?kin manta abunda ya faru ran nan?kika kusa kashe mun waya gaba ɗaya!,yanzu da ace ta lalace dashi kenan wa zai siyamun wata"?   Fuskar jahad ɗauke da murmushi tace"Daddy mana!ae yace zai siya mana Phones gaba ɗayanmu,hada ke ma zai canza maki wata,hada ma laptop xai siya mana,"   Washe baki Sehrish tayi tare da cewa"Wai dagaske"?   "Eh,mana,shi da kanshi ya faɗi hakan,Kuma yace next week zamu koma school da kanshi zai mayar damu,don kada wani ya ɗaga mana yatsa,"ta ƙarasa maganar fuskarta dauke da dariya,sehrish kuwa tunda jahad tayi maganar school ba kowa ya faɗo mata aranta ba,face ƙawarta AMRISH,lokaci guda ta faɗo mata acikin ranta,nan take kuma taji gabanta ya faɗi rass,   Ganin fuskarta da alamun damuwa atattare da ita,yasa jahad kiran sunanta"Sehrish,meya faru ne?maimakon inga kina farin ciki?ko baki son komawa school ne?baki gaji da zaman kashe wando ba acikin gida?    Muryarta asanyaye tace"ba haka bane jahad,kawai na tuna da wata school friend ɗita ne,Nayi missing ɗinta sosai,Yarinyar tana sona sosai,itace take ƙarfafa mun guiwa akan in ringa yin karatu,in daina bacci a class,Gaskiya banyi mata adalci ba,sam na manta da ita,ni nasan cewa amrish ta neme ni har ta gaji,"   Jahad tace"Eyya,gaskiya baki kyauta mata ba,gashi sunan ku shigen iri ɗaya ke da ita,ni tun kafin ma in ganta har naji ina sonta,saboda tana son ƴar uwata sosai,Amma meyasa ba zaki jaraba kiranta ba tunda ga waya ko baki da numbarta ne?   "Ina da numbarta,kinsan kwanakin nan hankali na duk ba'a kwance yake ba,tun lokacin da muka daina zuwa school,ban ƙara bi takan wayar ba,sai ma na ganta a hannunki ne sannan nake tunawa da cewar ina da waya,Allah sarki Amrish ɗina,bansan wani hali take ciki ba,gashi bansan gidansu ba,"   Mikewa jahad tayi ta nufi wurin da Sehrish take tsaye,mika mata wayar tayi tare da cewa"Ki jaraba kiranta mana,sai mu gaisa,"   Kar6ar wayar Sehrish tayi,ta shiga cikin contacts ɗinta,ta lalubo numbar amrish,sae dai kash tana kiran layin taji wayar akashe,ɗayan layinta na Airtel ta kira shima akashe yake,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,    "Bansan meyasa ba'a samun layinta ba,amma mu bari da anjima sae mu jaraba kiranta mu gani kilan ta kunna wayar,"tayi maganar tare da miƙa ma jahad wayar ta kar6a,sannan ta koma gefen gadon ta zauna,ita kuma ta wuce gaban wardrobe tana lalubar kayan da zata sanya,   Turo ƙopar ɗakin nasu hosana tayi,da sallama abakinta,juyowa sehrish tayi tana kallonta haka itama jahad,   Nuna Sehrish tayi da yatsanta manuni,kafin tace"RISHI KIZO INJI DADDYN MU YACE KI SAME SHI A ƊAKIN SHI,KADA KI WUCE MINTI BIYAR"   Rasss!taji gabanta ya faɗi, "Hosana dagaske ni daddy ke kira?kuma ni kaɗai yace inzo"?   "Eh,ke kaɗae yake son gani," Cikin sauri ta juya tare da zura hannunta cikin wardrobe ɗin,ta lalubo wasu pakistan riga da wando,rigar fara ce,har guiwa daga ƙasanta kwalliyar duwatsu ne,wandon kuma pink colour ne,bai da kwalliya ajikinsa,irin falazun nan ne burgujeje,mayafin kayan ta yafa Shima pink colour,gaban madubi ta koma ta ɗauki flower bomb ɗinta,ta feshe jikinta dashi,sai da ta fara kallon fuskarta a mirror ta ɗan sakarwa kanta murmushi,sannan ta kama hanyar fita daga ɗakin, Jahad tace"Allah yasa alkhairi ne!kullum in daddy zai kiramu atare yake kiranmu amma yau ke kaɗae kawai yake son gani,"ta ƙarasa maganar tana nuna bayan sehrish da hannunta,   Murmushi kawai ta saki kafin ta buɗe ƙopar ta fuce, Da sauri da sauri take tafiya don karta wuce minti biyar ɗin da Hosana tace,tana ƙarasawa baƙin ƙopar ɗakin takai hannu kenan zata buɗe,taga an ja ƙopar daga cikin ɗakin,da alama wani ne zai fito,zubama dogayen yatsun hannunshi ido tayi,farare tass ya ruƙe handle ɗin ƙopar dasu,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga ɗakin,nan take ta gane Cewa BABBAN YAYA NE,mamaki ta shiga yi mai ya kawo babban yaya a ɗakin daddynsu?bayan sa6anin da suka samu a tsakaninsu,ko sun shirya ne,? Bata ƙarasa zancen zucin nata ba,SGR ya ƙarasa fitowa daga cikin ɗakin Abusufyan,wankan suit ne ajikinshi farare,kyau iya kyau,    Tsayawa yayi cak kamar an dakatar dashi,Sehrish kuwa tuni gabanta ya shiga faɗuwa,tun daga ƙasa har sama yabi ta da kallo,Yarinyar ko ƙafaɗarshi tsayinta bai kai ba,   Daƙyar sehrish ta iya buɗe baki tace mashi"Ina yini"   Tamkar bazai amsa mata ba,don har sai da ya wuceta ya ɗan yi nisa sannan taji yace"Lafiya,"yana faɗin hakan ya ƙara gaba,su babban yaya irin wannan shan ƙamshi haka,    Jiki asanyaye ta shiga cikin ɗakin da sallama abakinta,A zaune ta samu Uncle abusufyan,daga gefen gadonshi,juyowa yayi tare da kallonta fuskar nan tashi ɗauke da murmushi yace"Daughter,"   "Na'am daddy,ta amsa mashi tare da ƙarasawa,ta samu wuri saman sofa ɗin dake fuskantar gadonshi ta zauna,suna facing ɗin juna ita dashi,sannan tace"gani daddy hosana ce ta sanar dani cewa kana nema na," "Eh hakane,ni na ce ta kira mun ke,"    Natsuwa tayi tana jiran jin me zaice mata,sae faman wasa takeyi da yatsun hannunta,    "Gobe yaushe"?yayi tambayar yana kallonta, ..fuskarta ɗauke da murmushi tace"Friday," jinjina kanshi yayi tare da cewa"Masha Allah,Juma'a babbar rana,zaifi kyau in aka kafa tarihi aranar juma'a,ina tunanin kamar zai yi wuya a manta dashi,ko ba haka ba daughter?   Dariya sehrish tayi kafin tace"gaskiya ne daddy,juma'a itace babbar rana,duk abunda ya faru a ranar friday,zaiyi wuya a manta dashi,"   Abusufyan yace"Shiyasa nake so gobe na ɗaura maki aure,ko bakya so"?   Da sauri tasa tafukan hannunta tare da rufe fuskarta,tana dariya,     "Na ƙosa na fara ganin ƴan jikoki na," cikin zolaya yayi mata maganar,   "Dan Allah daddy,ka daina faɗin haka wlh kunya nake ji," cikin shagawa6a tayi maganar har lokacin bata zame tafin hannunta daga saman fuskarta ba,   Miƙa hannu Abusufyan yayi tare da janyo drawer chest ɗinsa gida na tsakiya,ya ɗauko wani small box Golden Colour mai shegen kyau,sae faman ƙyalli yake yi yadda kasan da Zallar Zinari akayi shi,    Ruƙo shi yayi a hannunshi yana jujjuya shi,ɗan ɗagowa yayi yana kallon sehrish wadda ta rufe fuskarta,   Gyaran murya yayi mata tare da cewa"Buɗe fuskarki mana," a hankali ta zame hannunta daga kan fuskarta,kai tsaye idanunta suka sauka kan small box ɗin dake hannun Daddynsu,ɗan zaro idanunta tayi tana ƙare mashi kallo,akwatin ya burgeta sosai,jikinshi sae ƙyalli yakeyi mai matuƙar ɗaukar ido,da jan hankali,cike da zumuɗi tace"daddy wannan fa?wlh yayi kyau sosai,ban ta6a ganin irin shi ba,"   Ƴar dariya Abusufyan yayi tare da cewa"koya burge ki ne"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh, Jujjuya akwatin yayi tare da cewa"Sadakin wata Ne,aka biya da Gold,"   Waro ido waje sehrish tayi cike da mamaki tace"daddy!dagaske ka ke dowry ne aka biya da Gold,but daddy who's she? Dariya abusufyan ya kuma yi ganin yadda tabi ta ruɗe da jin abunda yace,   "Dagaske nake ba wasa ba,sadakin wata Mai sa'a ce,Jinin nasara,"   "Daddy,can i see it pls"? Miƙa mata small box ɗin yayi hannunta har kerma yake yi wurin kar6arsa,janyewa Abusufyan yayi fuskar nan tashi ɗauke da dariya yace"Da hannun hagu kuma?hannu biyu zaki sa ki kar6a,sannan in zaki kar6a ki tabbatar da kinyi bismillah,don Abun yayi albarka,"   Murmushi sehrish tayi tare da gyara natsuwarta,sannan ta miƙa hannanyenta duka biyun,tayi bismillah kafin ta kar6e shi daga hannun abusufyan,wani irin sanyi ne taji ya ratsata,jujjuya akwatin ta shiga yi tana ƙare mashi kallo,yana da nauyi duk da ƙarantar shi,hakan ya tabbatar mata da cewar,abune mai daraja acikinsa,ƙoƙarin buɗe akwatin ta shiga yi,da sauri Abusufyan ya dakatar da ita"kada ki buɗe shi,ki adana shi a wurinki,bana so kowa ya gani,kuma kada kowa yasan inda kika ajiye shi," Abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,   "Amma daddy,sadakin wata ne fa?kuma naji ka ce in ajiye shi a wurina,saboda Me"?    Bai bata amsa ba,sae ma kwantar da bayanshi da yayi saman gadon nashi,ya ɗan kishingiɗa,ya aza kansa saman pillow,yana kallonta,ta zuba mashi ido tana jiran jin amsar da zai bata,    Ƙayataccen murmushi ne ya bayyana akan fuskar Abusufyan,ya jima ahaka suna kallon kallo shi da Ƴar tashi,kafin yace"Zaki samu amsar tambayarki,amma ba yanzu ba,ki bani lokaci zan neme ki,yanzu zaki iya tafiya,"ya ƙarasa maganar yana nuna mata hanyar fita daga ɗakin,   Tamkar wadda aka zarewa lakar jikinta,haka ta miƙe jiki ba kwari,wani irin faɗuwar gaba kawai take ji,daƙyar ta iya ɗaga ƙafarta,tana tafiya tana waiwayen daddyn nasu,daya zuba mata ido yana kallonta,tabbas akwai wani abu da yake 6oye mata,sai da takai bakin ƙopar ɗakin,tana ƙoƙarin buɗe kopar ta fita,taji ya ambaci sunanta   "SEHRISH" da sauri ta juya tana kallonshi,    "Game da abunda ya faru tsakaninki da babban yayanku,Nasan ranshi ya 6aci sosai,ya baki Umarnin kiyi mashi aiki,amma na hanaki a matsayina na mahaifin ki,inaso kije ki bashi haƙuri,'   Waro ido waje sehrish tayi a ɗan tsorace tace"daddy in bashi haƙuri fa ka ce?wlh tsoro nake ji,jiya ranshi ya 6aci sosai,idan na kuskura naje wurinshi yau karya ni zaiyi nasan,"   Yadda tayi maganar ba ƙaramin dariya yaso ya bashi ba,fuskarta tamkar zatayi kuka,   "Don't worry ur self,SGR bazai ta6a gigin bugunki ba,saboda ba halayyarsa bace,"   Haɗiyar yawu tayi,tana sauraronshi,ɗan dakatawa yayi da yin maganar,kafin ya ɗaura da cewa"daga yanzu inaso,ki cigaba da aiki a ƙarkashinsa....' tunkan ya ƙarasa maganar Sehrish tace"Amma daddy,ka hanani zuwa part ɗinsa fa"   "A yanzu na soke wannan!inaso ki yi mashi biyayya,ki bishi sau da ƙafa,komai yake so kiyi mashi kawai!part ɗinsa kuma koda wani lokaci zaki iya zuwa ki shiga,even in the midnight,indai ya buƙaci ganinki ki je kawai,"   Gaba ɗaya Abusufyan ya gama ruɗar da ita,la66anta har kerma sukeyi wurin cewa"dad..dy!bangane me kake nufi ba,dan Allah ka fahimtar dani,"      "Ki tafi kawai kiyi duk abunda nace maki,idan lokaci yayi zan sanar maki,"    Juyawa tayi tare da zura ƙafarta,tabar bedroom ɗin nashi,lumshe idanunshi yayi tare da buɗesu,ya ƙurama ceilling ɗin sama ido yana kallonshi tamkar mai karanta wani abu ajikinshi,tunani ya shiga yi acikin zuciyarshi,ya shiga tariyo abunda yaji a kunnuwansa,   _Na amince zan aureta,bana son abun ya ɗauki lokaci,bana son taron mutane,kuma banaso kowa ya sani,saboda ba auren dundundun bane,nan da wata uku zan sake ta,zan aureta ne ba don ina sonta matsayin matata ba,sae don tayi mun aiki kafin na bar nigeria_   Hannu Abusufyan yasa tare da ɗaukar wata takarda dake ajiye saman side drawer ɗinshi,zuba ma takardar ido yayi yana kallonta,Agreement paper ce (Takardar yarjejeniya)mai ɗauke da signatures na mutun uku,"   Ajiyar zuciya ya sauke tare da zura ta cikin drawer chest ɗin daya fiddo akwatin nan da ya bama sehrish ya sanya takardar aciki ya ajiyeta,sannan ya mayar da ita ya datse,rufe idanunshi yayi bakowa bane ya faɗo mashi arai ba face ABU,nan take yaji kewarta ta lullu6e shi,Allah sarki abu,tana raye kota mutu? A 6angaren Sehrish kuwa bayan fitarta daga bedroom ɗin Abusufyan,a ƙopar ɗakinsu ta tsaya,warware mayafin da ta laga akanta tayi,sannan ta lullu6e small box ɗin dake hannunta don kada wani ya gani,tura ƙopar ɗakin tayi sannan ta shiga daga ciki,babu kowa acikin ɗakin,sautin ruwan da taji ne daga cikin toilet ya tabbatar mata da cewar Jahad ce ke wanka,cikin sauri ta lalla6a gaban dressing mirror ɗinsu,ta zuƙunna gaban drawer ɗin dake ɗauke da mirror ɗin,ta janyo gida na ƙarshe,ta tura small box ɗin acikinsa can ƙurya ta turashi,sannan ta rufe,tana faman sauke ajiyar zuciya,miƙewa tsaye tayi har lokacin bata daina mamakin abubuwan da Uncle ya faɗa mata ba,abun ya ɗaure mata kai sosai, Safa da marwa ta shiga yi acikin ɗakin,takasa zama saboda yanayin da ta tsinci kanta aciki, *Boss Bature* ❤🤍❤ AMRISH, Tun jiya da daddare data farka,tana bullayi asaman gadon bayan an samu nasarar ceto rayuwarta,doctor yayi mata allurar bacci bata ƙara farkawa ba,yini tayi a kwance tana bacci kamar matacciya,hankalinsu zeenatu ba ƙaramin kwanciya yayi ba,musamman Mommyn Amrish ɗin,bata ta6a tunanin amrish zata rayu ba,amma cikin ikon Allah sae gashi taji sauƙi sosai,poison ɗin da tasha bai kaiga yi mata illa ba,sunyi gaggawar kaita asibitin kuma likotoci sun taru akanta wurin ceto rayuwarta,wannan ne yasa bata jigata ba sosae,amma still da sauranta don ba ƙaramin galabaita tayi ba,yanzu haka ma ƙarin ruwa ne aka sanya mata, Mommynta na zaune asaman plastic chair din dake agaban gadonta,fuskar nan tayi jawur da alama ba ƙaramin kuka tasha ba,ga rashin baccin da basu samu ba adaren jiya,gaba ɗaya hankalinta na akan Amrish dake kwance magashiyan tana bacci, Zeenatu na a zaune daga gefen gadon da amrish ɗin take kwance,duk sunyi zuru suna kallonta,tunda safe Sofia ta koma gidansu,ita kaɗae ta rage saboda tace bazata koma gidansu ba har sai Amrish taji sauƙi sun koma gida, Suna cikin zaman nan,kwatsam Amrish ta buɗe idanunta ta zazzaresu a wani irin firgice ta sanya hannu ta fizge robar ƙarin ruwan da akeyi mata,hankali atashe Zeenatu tace"Mommy amrish ta farka!ta cire ƙarin ruwan da aka sa mata,"jin wannan maganar yasa Mommyn yin firgit ta dawo cikin hayyacinta daga zurfin tunanin da ta shiga,sai dai kafin suyi wani yunƙuri,tuni Amrish ta diro daga saman gadon,ta watsa aguje,zeenatu na ƙoƙarin tarota,takai mata wani kakkwaran naushi a saitin Cikinta,nan take zeenatu ta zube ƙasa hannunta dafe da cikin,ta fasa uwar ƙara tana faɗin"Wayyo Allah na!cikina!nashiga uku, Ko waiwayonta amrish batayi ba,hanyar fita kawai ta nufa,da gudu ta fice daga ɗakin,bin bayanta Mommyn tayi tana yarfa hannu a ruɗe take faɗin"Help!help!!dan Allah jama'a ataimaka a taro mun ita!mara lafiyace zata gudu,'     Da gudu wasu nurses suka bi bayan amrish,hada wasu daga cikin masu zuwa dubiya,    "Amrish dan Allah ki tsaya!wai meke damunki ne!bakiji ina magana ba!ina zaki je ne!," hankali tashe mommyn ke magana,amma ko sauraronta amrish bata yi ba,duk wanda ma yayi ƙoƙarin tarota bugu take kai mashi kamar ƴar wrestling,gashi wani irin ƙarfine da ita kamar na Doki,in ta daki mutun sai ya kusa zaucewa,duk yadda suka so su kama amrish,amma abun yaci tura,domin kuwa 6att suka neme ta suka rasa acikin asibitin,saƙo da lungu babu inda basu duba ba,amma babu ita babu alamarta,ko mai kama da ita ma babu,nan fa hankalin kowa ya tashi,hatta security guards ɗin dake tsaron gate ɗin asibitin,sae da aka tambayesu,sun tabbatar da cewar basu ga fitarta daga asibitin ba,sae dai ko a wani wurin ta 6oye,Hatta Cctv footage sae da aka bincika,amma ba aga ta hanyar da Amrish tabar cikin hospital ɗin ba,kuma ba'aga wurin da ta 6oye ba,wannan abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yayi ba,yarinya kamar mai iskokai?babban abunda zai baka mamaki ƙarfin daya zo mata,mutumin dake kwance magashiyan a gadon asibiti,amma ya tashi farat daya da irin ƙarfin nan a jikinshi? Saboda tsabar tashin hankalin da Mommyn Amrish ta shiga,nan take ta yanke jiki ta faɗi ƙasa asume,sai dai nurses suka cuccu6eta aka shiga da ita ciki,suka kwantar,itama zeenatu sae da suka kwantar da ita don kuwa ba ƙaramin buguwa tayi ba,naushi ɗaya tayi mata aciki,amma sae da jini ya zuba a bakinta, *ANA WATA GA WATA!JAMA'A INA AMRISH TA SHIGA NE*?😳😳😳 *Aunty Babba* Fitowarta kenan daga cikin toilet tana faman dafe cikinta,ɗagowa tayi tana kallon hayaam dake zaune gefen gadon ta zabga uban tagumi da hannayenta biyu,Hafsat kuwa na asaman gadon kwance ta lullu6e da bargo jikinta sae kerma yake yi,wani irin zazza6ine mai zafi ya rufar mata,tunda rana tagaza motsa jikinta,abun gwanin ban tausayi, Kwatsam!sukaji an banko ƙopar ɗakin nasu,dafe ƙirji Aunty babba tayi tana kallonshi,sae faman huci yakeyi yadda kasan mayunwacin zaki,da ƙafarsa ya tura ƙopar ɗakin ta rufe,hayaam na ganinshi a razane ta haye saman gadon,jiki na rawa ta wuntsila daga ƙasan gadon ta 6oye,tana faman zazzare ido,   Cikin inda inda ta ambaci sunan shi"I..ishaq!"   A zafafe ya ƙarasa inda take,kwakkwarar damƙa yakai ma wuyanta,ya shaqeta sosai,yadda ko ihu bazata iyayi ba,saboda tsabar raɗaɗin da taji nan take ta saki fitsari a wando,wani irin gumi ne ya shiga tsattsafowa daga gefen fuskarta,idanunta sunyi jawur cike tab da kwalla,ƙwayar idon tamkar zata zazzago ƙasa,   A ruɗe hafsat ta fasa uwar ƙara,ganin abunda daddynta ke ƙoƙarin yi,gadan gadan so yake ya kashe Mommynta,da gudun gaske ta duro daga saman gadon tana kuka,   "Kafin ki kashe su!Ni zan fara kashe ki!muguwa kawai!Nayi danasanin aurenki laila!nayi danasanin saninki da nayi,Nayi danasanin haɗa zuri'a ɗaya dake,Allah ya isa tsakani na dake!Na tsaneki!kin fita araina!ban sonki!bansan ganinki!"daƙyar sautin muryarshi ke fita saboda tsabar 6acin rai,a fusace ya buga kanta jikin bango,nan take Aunty babba ta baje ƙasa a sume,'   Juyawa yayi tare da aza idanunshi akan hafsat dake tsaye tana faman zabga uban kuka fuskarnan tayi jaga jaga da hawaye hada majina,nunata yayi da yatsan hannunshi sannan yace"dake da uwarki!ku tattara kayanku ku bar gidan nan!tun kafin inyi sanadin mutuwarku!muguye kawai waɗanda ba Allah aransu,"   Hannu hafsat ta aza akanta tana ambaton"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un!"   Juyawa ishaq yayi da sauri zai bar ɗakin,da gudun gaske ta ruƙo rigar jikinshi tare da zubewa saman guiwowinta tana kuka tana yi mashi magiya akan,karya koreta,    "Daddy dan Allah kayi haƙuri ka yafe mun!wlh ba laifina bane,nasan mun cutar dasu,amma inaso ka sani daga baya na ƙaunace su,Daddy ka yarda dani Mommy itace take azabtar dasu,kuma itace tayi silar barin....'bata ƙarasa maganar ba sakamakon bugun daya kai mata da ƙafarshi,da sauri ta dafe gefen bakinta daya buga wurin har ya fashe,jini ya shiga ɗiɗɗigowa,dogon tsoki ishaq yaja tare da cewa"Kada ki kuskura ki ƙara kirana da sunan daddy!don ni ban haifi wata ƴa mai suna hafsat ba!tunda har kin za6i ki bi mugun hali irin na mommynki,don haka gaki ga ita,duk in da zata je ƙafarki ƙafarta,karku kuskura Dare yayi maku acikin gidan nan!don wlh sai kunyi danasanin haihuwarku da akayi acikin duniyar nan!don bazan raga maku ba,tamkar ban sanku ba,haka zan hukunta ku!kuma idan ta farka daga suman da tayi ki sanar da ita cewa NI ISHAQ NA SAKE TA,!!!! Wani irin bugu zuciyar hayaam tayi ji kake daramm!!kamar an buga ganga,nan take ido ya raina fata,sae faman mazurai takeyi abayan gadon da ta la6e,Na shiga uku Ni hayaam An saki Aunty laila!Shikenan komai ya ƙare komai ya lalace!mun gama yawo!!   Ya ƙarasa maganar tare da kai hannu tamkar zai 6alle ƙofar ya fuce,Amani dake la6e tana sauraronsu da gudun gaske ta watsa,sae cikin ɗakin da suka sauka,Tana shiga cikin ɗakin ta daka tsalle,bakinta awashe saboda tsabar dariyar mugunta hada hawaye ke fita a idonta,Amal dake zaune saman gado tana buga game a wayar amani,ganin yadda amani keta dariya kamar wata zautacciya,yasa ta ɗan dakata da buga game ɗin tare da cewa"Aunty Amani meya sanyaki farin ciki har haka"?   Daƙyar ta iya dakatawa da yin dariyar tace"Amal ba zaki gane bane,Wani buri da nake dashi ne ya cika ayau ɗin nan!!waɗanda suka jima suna ƙuntata rayuwarmu,tun yau zasu fara gir6ar abunda suka shuka," tana magana tana dariya,   Murmushi kawai Amal tayi tare da mayar da hankalinta kan game ɗin da take bugawa, General ishaq na fita daga ɗakin,hayaam ta lalla6a ta fito,yadda kasan lagwanin fitila haka take tafiya,jikin taƙaura yayi la'asar wannan hada magriba ma,zuƙunnawa tayi gaban Aunty babba dake baje ƙasa,ta fashe da wani irin matsanancin kuka,Hafsat na kuka itama tana kuka,babu mai lallashin wani,kowa takansa yake yi, Cikin shessheƙar kuka hafsat ta soma magana"Allah ya isa tsakanina dake Aunty hayaam,kun cuci rayuwata duk don saboda ku ne mommy ta aikata abunda ta aikata don taga ta cika muku burinku,gashi nan yanzu abun ya shafe ni,kunja daddyna ya kore ni,Ni bansan ku wasu irin mutane bane!sam baku da zuciya kare ya lashe,kun nace kun liƙe dole sai kunyi arziƙi da gumin wasu,ku bazaku tashi ku nemi na kanku ba,sam babu Allah aranku,mugunta kawai kukasa agaba,shiyasa har yau babu wani cigaba acikin lamurranku!wlh yanzu ma kuka fara gani!indai bazaku koma ga Allah ba,,ku tsaya a iya matsayin da Allah ya ajiye ku,ku daina hangen na wasu,wannan dogon burin da kwaɗayin abun duniyar ba inda zai kai ku face ya jefa ku ga halaka....." Itadae hayaam bata tanka mata ba,saboda bata da abun cewa,har wani zazza6i take ji ajikinta,saboda tsabar tashin hankalin da take ciki,komai ya jagule masu, Miƙewa hafsat tayi,jiki ba ƙwari ta ƙarasa tare da janyo trolley ɗin kayansu da suka zo dashi,janshi tayi izuwa gaban wardrobe ɗin hayaam,ta buɗeta,kayansu dake aciki tashiga fitowa tana ninkesu,Cikin trolley ɗin take jerasu, Miƙewa hayaam tayi tana tunanin inda zata samu ruwa ta yayyafa ma Aunty babba,saboda babu ruwa acikin ɗakin,kuma tana jin tsoron ta fita waje suci karo da mutumin,tana cikin wannan tunanin ta tuna da akwai fanfo cikin toilet,da sauri ta shiga ciki a tafin hannayenta ta tarbo ruwan,da sauri da sauri tazo ta yarfa mata shi a fuskarta,dogon numfashi Aunty babba taja,tun kafin ta buɗe idanunta ta shiga fadin"Ruwa!Ruwa!" jin haka yasa hayaam yin tunanin ta fita waje ta samo mata ruwan,buɗe kopar dakin tayi cikin sanɗa ta fito tana tafiya acikin corridor din dakunan nasu,cikin sa'a ta taras babu kowa a main palour din,ƙarasawa tayi wurin fridge ɗinsu,ta bude jikinta na kerma ta ɗauko robar ruwa,da gudu ta koma cikin ɗakin,    Ƙarasawa tayi tare da taimaka ma Aunty babba ta tashi zaune sannan ta miƙa mata bottle water ɗin,A tsiyace ta 6alle murfin robar,ta kafata a bakinta,yadda kasan zata haɗa da robar duka ta cinye,abun kamar yaƙi,ta damƙi robar,sae kwankwaɗar ruwan take,kwatt!kwatt!!har sae da ta shanye ruwan duka tass,sannan ta saki robar ƙasa,sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi,hannunta na dafe da kakkauran wuyanta sae faman Murzarshi takeyi,wurin sae raɗaɗi yake yi mata kamar an barbaɗa mata attarugu,idanuwan nan nata sunyi jawur luhu luhu,sae da tadawo cikin hayyacinta sosai sannan ta kalli Hayaam tare da cewa"hayaam meya faru dani ne?ya akai na ganni akwance ƙasa?   Kafin hayaam ta buɗe baki tayi magana,tuni hafsat ta katse mata hanzarinta da cewa"Mommy!kina nufin cewa kin manta duk abunda ya faru?idan ma kin manta bari na tuna maki,Dadddy ne ya damƙi wuyanki ya shaqeki,sannan ya bugaki ajikin bango har saida kika suma,"   Shiru aunty babba tayi tana tariyo abunda ya faru, "kuma yace mu tattara kayanmu mubar gidan nan,kada mu bari dare yayi mana,bayan haka kuma ya dankara maki saki ɗaya"rai a6ace hafsat ke maganar, Wata irin mahaukaciyar dariya Aunty babba ta kwashe da ita kamar wata zautacciya,hakan ba ƙaramin mamaki ya basu ba,miƙewa tsaye tayi tana gyara ɗaurin ɗankwalinta tace"Da sauƙi ma,Ni nayi tunanin wani mummunan hukunci zai yanke mun,sai me don ya kore ni?sakin ma da yayi mun wlh ko ajikina,yayi a banza Ae akwai sauran igiyoyi guda biyu,Ni nasan cewa muddin Abbansu yaji cewar ya sake ni,sae yasa ya mayar dani,Ae ni wlh gaba takaini gobarar titi A jos!" To fa, sakin baki hafsat tayi galala tana kallonta,ba ita kaɗae ba hatta hayaam abun ya ɗaure mata kai,sunyi tunanin cewa in taji ishaq ya sake ta,xata haukace masu ne,amma sae gashi ko ajikinta!zuciyar ta bushe,   Sae faman tiƙar dariya takeyi kamar sabon shiga a fagen hauka,lokaci guda kuma ta murtuke fuskarta,tare da kallon hayaam tace"Maza ki tattara kayanki,don atare dake zamu tafi,"   Hankali tashe hayaam tace"Ni kuma?saboda me zamu tafi atare"?   Shu'umin murmushin nan nata tasaki kafin tace"Saboda inaso,muje wurin bokan nan baba ibliss!wannan karan ba fashi,Dole in kawo ƙarshen auren Amani!kamar yadda zanyi zawarci itama haka nakeso tayi shi,sannan waccen mahaukaciyar yarinyar da tayi silar tona mun asiri har ishaq ya sanya hannunshi ya shaqe mun wuyana na kusa sheqawa barzahu wlh saina yi Ajalinta!!!sannan kuma aurenki da Sgr ba fashi!Wlh ko ta halin ƙaƙa!ko suna so ko basa so sai an ɗaura shi!In har kika ga ba'ayi auren nan ba!To sai dai in bana a doron duniyar nan!ko kuma shi RAFAYET ɗin Ya daina numfashi ne acikinta!sai dai kowa ya rasa wlh!da alama har yanzu basu san wacece Ni ba!zan nuna masu true colour ɗina!Ni dasu shege ka fasa!!" tana magana tana fitar da huci,   Mugun abu kokayi bacci?yace idona biyu 👀!ANA WATA GA WATA, Zuru hafsat tayi tana kallonta,abun yafi ƙarfinta,lamarin Mommyn nata sae addu'a,tunani ta shiga yi anya Mommynta bata fara shaye shaye ba?kodai tana da iskokai ne? Suna cikin wannan tsayuwar,aka kwankwaso ƙopar ɗakin nasu,a tsiwace Aunty babba tace"Wanene"?   "OMAR NE" koda jin muryar marshal Omar nan fa kowa ya shiga taitayinsa,   "Hayaam je ki buɗe mashi ƙopa,muji dame yazo!in shima zuwa yayi don yaci mutunci na to bismillah!kowani shege dai dai nake dashi,"kamar wata ƴar daba haka take maganar,   Buɗe mashi ƙopa Hayaaam tayi,tun daga irin kallon da taga Omar ya watsa mata tuni tashiga ƴan kame kame tana sunnar da kai,   Shiga cikin ɗakin nasu yayi,yayin da idanunshi ke akan Aunty babba wadda ke tsaye ta ruƙe qugu,sae faman jijjiga jikinta takeyi kamar wata ƴar bori,   Janye idanunshi yayi daga kanta ya mayar dasu kan hafsat,wadda ke tsaye ruƙe da trolley ɗin kayansu,ganin yana kallonta ne yasa ta ɗukar da kanta ƙasa cike da jin kunyarshi,   "Ina zaki je ne"? Yayi maganar fuskarshi a ɗaure,   Muryarta na rawa tace"dad..dy ne yace mu tattara kayanmu mubar gidan nan kada mu kuskura mu bari dare yayi mana anan,"   "Ban da ke!su kaɗai zasu tafi," Wani irin farin ciki ne ya lullu6e hafsat,har ta gaza rufe bakinta saboda tsabar farin ciki,"   Mayar da idanunshi yayi kan Aunty babba dake tsaye ruqe da qugu yace"Major na awaje yana jiranku,idan kun kammala shiryawa ku same shi,Nayi mashi magana zai kai ku hotel ɗin da zaku kwana kafin gobe da safe sae ku wuce maiduguri,Amma fa in kuna so kenan,sannan kuma....'ya ɗan dakata da yin maganar tare da zura hannunshi cikin aljihun jeans ɗin dake ajikinshi ya zaro bendir ɗin kuɗi na ƴan dubu dubu,a ƙalla zasu yi dubu ɗari ɗaya,ya miƙa masu,jiki na rawa hayaam ta kar6e kuɗin tana yi mashi godiya, ...murmushi Marshal Omar ya saki tare da cewa"No,ba sai kin gode mun ba,nayi ne don Allah,'   Yana kai ƙarshen maganar ya juya tare da fucewa daga dakin yana dariya gami da girgiza kanshi,   Bayan fitarshi aunty babba ta buga tsoki,tana faman hura hanci tace ma hayaam"maza ki shirya mana kayanmu,naji ana kiran sallar magrib,zae fi mu lalla6a mu fuce daga gidan batare da kowa ya ganmu ba,nasan duk sun tafi salla,"   Amsa mata hayaam tayi da toh,sannan ta juya tare da shigewa cikin toilet,   Hankalin hafsat ba ƙaramin kwanciya yayi ba,wuri ta samu gefen gadon ta zauna tana faman sakin murmushi,dama babban tashin hankalinta shine idan tabi su Aunty babba maiduguri bazata iya rayuwa cikin gidansu ba,sau ɗaya ta ta6a zuwa,bataji daɗin zama agidan ba,muggan talakawa ne,babu wani abu na more rayuwa acikin gidan,sae ma abun haushi da takaici da zaka taras,   Kusan minti Goma shabiyar sai ga aunty babba ta fito daga cikin toilet ɗin,da alama wanka tayi,xanin atampar jikinta ne tayi ɗaurin gaba dashi,ya jiƙe sharkaf saboda ta ɗauraye shi acikin toilet da ta shiga,   Batare da 6ata lokaci ba,suka shirya tsaf ita da hayaam,dogayen riguna suka sanya ajikinsu,sannan suka aza mayafi daga sama,kama hanyar fita daga ɗakin sukayi,ɗan juyowa aunty babba tayi tare da kallon hafsat tace"sannu hakima yayi maki dai dai wato hankalinki kwance zaki rabu da Mommynki ko rakiya babu"?   Miƙewa hafsat tayi tare da bin bayansu,suka fuce daga cikin ɗakin,ta ƙopar baya suka bi don kada wani yaga fitarsu,a waje suka samu Major tsaye jikin motarshi,ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi,yana ganin sun fito da sauri ya buɗe masu motar,    "Allah ya kiyaye hanya mommy,in sha Allah gobe da safe kafin ku wuce maidugurin zan kiraki a waya,"   Harara aunty babba ta watsa mata kafin tace"Munafuka!Hada wani raku6e fuska kamar irin zakiyi kewata ɗinnan!Ae kada ki damu ki sha kuruminki in dai ni ce zan dawo ne!nan bada jimawa ba,"tayi maganar tare da kutsa kai ta shiga cikin Motar,   "Aunty hayaam Allah ya tsare hanya,Ni dai zan wuce ciki,"   Murmushin yaƙe hayaam tayi,tare da janyota ta rungumeta,daga bisani ta shiga cikin motar,batare da 6ata lokaci ba,Mojar ya shiga mazaunin driver,yayi ma motar key,yaja ta da gudun gaske,Fashewa da kuka hayaam tayi tana leƙen gidan ta cikin gilashin motar,aunty babba sai lallashinta takeyi tana cewa"ke fa banzace,menene abun kuka anan?karki wani damu kanki,Ae babu inda zamuje,ko cikin garin nan bazamu bari ba,Ni nasan me nake shiryawa,AI YANZU WASAN YA FARA,    Cikin shessheƙar kuka hayaam tace"Aunty laila bazaki gane bane,wlh banson inyi nesa da gidan nan!ji nake kamar zan rasa shine gaba ɗaya,na kwallafa raina akan Sgr,duk da bana ganinsa amma zaman da nakeyi acikin gidan nan,yana kwantar min da hankalina,at lease muna kusa da juna,ko ba don haka ba,A yanzu ni banajin zan iya rayuwa acikin gidanmu,kwara nan gidan wlh,kaci mai kyau kasha mai kyau ka kwana a mai kyau,duk da atakure nake kwara nan ɗin da can gidan mu,Jarabar mammy kaɗae ta isa ta Ramar da mutun,babban takaici na,korar wulaƙancin da nayi ma Sofwan nasan cewa yanzu kona nemi taimako awajensa bazai kulani ba,"hannu tasa tana share hawayenta,   Tsoki aunty babba taja mtsww kefa matsakarki kenan!nace maki ki kwantar da hankalinki,ba inda zamuje amma duk kin bi kin tashi hankalinki,sannan in dai akan sgr ne ni nayi maki alƙwarin cewar saina mallaka maki shi,in dai kika ga sgr bai aureki ba to ki tabbatar cewar rayuwarshi a tazuranci zata ƙare,kuma naji kina maganar wani sofwan,uban me zaiyi mana?Ko kin manta cewar Muna da jari atare damu?daga ke harni babu namijin da zai kallemu ya kawar da kansa,Allah ya bamu hasken fata,ga dogon gashi,duk wani abu dake jan hankalin ɗa Namiji ae muna dashi Allah ya bamu,Kinga kuwa muna da hanyar da zamu samu kuɗi,don biyan buƙatunmu,' Gaba ɗaya duk wannan surutun da sukeyi a kunnan Major,ya kasa kunne yana sauraron su,Sae faman ƙumshe dariya yakeyi acikin bakinsa,abun ban haushi abun ban dariya,      *Boss Bature*          ❤REESHRAF? A hankali take hawan upstairs ɗin,yayin da zuciyarta ke tariyo mata abunda daddynsu ya sanar da ita,na cewa taci gaba da aiki a part ɗin SGR,kuma tayi mashi biyayya sau da ƙafa,me hakan ke nufi?small box ɗin da daddynsu ya bata,dowry ɗin wanene?ya sanar dani cewa sadakin wata ne,amma dai koma wacece wannan ba ƙaramar mai sa'a bace,halan tafi kowa kyau a duniya ne?shiyasa Aka biya sadakinta da Gold,dama ni wlh,'   Kamar wata zautacciya,sae faman surutai takeyi ita kadae abunta, Ƙarasa hawa up din tayi,kai tsaye ta wuce part ɗin babban yaya,bata tashi jin faduwar gaba ba,sae da tazo ƙopar shiga falonsa,sannan ta tsaya tana karanto addu'o'in neman tsari,duk don kada ta fuskanci hukunci a wurinsa,bayan ta kammala addu'ar,ta shafa asaman fuskarta da kuma jikinta,kafin tasa ƙafarta ta shiga cikin falon cike da kwarin guiwa,sauke ajiyar zuciya tayi ganin babu shi acikin falon,sae dai daddaɗan ƙamshin turarensa,mai ratsa zuciya,bin falon nasa tayi da kallo,kusan 3 days kenan babu gyara,dama da shirin aiki tazo,wuce wa cikin bedroom ɗinshi tayi,nan ma babu shi aciki,da alama basu dawo daga sallar magrib ba,may be sae after isha,ko kuma ƙarfe goma sha biyun dare daya saba dawowa gida,   Shimfiɗeɗen gadonshi tabi da kallo,zanin gadon duk yayi squeezing,ga blanket ɗinsa ma nannaɗe asaman gadon,bai ɗaukeshi ba,   Hannu tasa tare da zame mayafin sarin dake ajikinta,ta ɗaure shi a qugunta,kwantacciyar sumar kanta na ɗaure acikin ribbon,saman gadon ta haye tare da sanya hannayenta tashiga ƙoƙarin tattaro bedsheet din nasa,Zancen zucin da takeyi ne ya fito fili,   "Matar babban yaya ta shiga uku,na tausaya mata Allah,mutun kullum fuskarshi a daure,kamar ta sa,babu fara'a ko kaɗan,in tayi mashi laifi kuwa zata sha zallan kwaɗi,in kuwa ta fusata shi,ɗaukar ta zaiyi kamar haka,   Tayi maganar tana tattaro bargonsa,ta ɗaga bargon sama tare da yin wurgi dashi,sannan tace"Ya jefar da ita,ko kuma yayi mata irin yadda yayi mun jiya,kamar wata ɗiyar Roba haka zai ruko wutsiyoyin gashin kanta,ya ɗaga ta sama!yana jujjuyata, Tana cikin wannan sambatun nata,taji anyi mata gyaran Murya,a wani irin firgice ta juya don taga WANENE  * Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Waro ido waje tayi tana kallonshi,la66anta har rawa sukeyi wurin furta"bab..babban..yaya," tsananin tsoro ne ya bayyana akan fuskarta,babban abunda ya tayar mata da hankali shine batasan tun yaushe yake tsaye abakin ƙopar ɗakin ba!in kuwa har ya jima a tsaye to tabbas yaji duk abunda tace, Yana tsaye a bakin ƙopar,ya goya hannayenshi asaman faffaɗan ƙirjinshi,farar shirt ce ajikinsa mai dogon hannu tare da wandon suits ɗinsa fari,hannun nan nashi na sanye da agogon diamond ɗinsa,Ya ɗaure sumar kansa ta baya,fuskar nan babu annuri ko misƙala zarratin,ya ɗaureta tamau,a hankali ya furta"On My bed!" Jiki na rawa Sehrish ta sauko ƙasa daga saman gadon,cikin in ena tace"am..umm..dama gyara gadon nake yi,shine na hau sama don in samu in tattaro zanin gadon da bar....' bata ƙarasa maganar ba,ya dakatar da ita"Shut up!banason jin komai"ya ƙarasa maganar tare da shigewa cikin ɗakin,kama hanyar fita daga ɗakin tayi,muryarshi ce ta kuma katseta da cewa"are u done"? "A'a bangama ba,"ta bashi amsa, "Okey,"ya ambaci hakan a yayin da yake zame agogon dake hannunshi, Komawa ciki tayi,sannan taci gaba da gyaran gadon,tana jin lokacin daya shige cikin toilet,da alama wanka zaiyi,ajiyar zuciya ta sauke aranta tace"Allah yaso ni baiji abunda nace ba,dana shiga uku yau,nasan cewa dole ya sanyani tsallan kwaɗi,"shaf shaf ta kammala gyara tamfatsetsen gadon,ta canza mashi bedsheet,ta kuma canza mashi bargon da zai lullu6a dashi,in ya tashi kwanciya,bayan ta kammala gyara bedroom ɗin,ta dawo falo,nan ma ta shiga gyara mashi falon,Cikin ƙankanin lokaci ta kammala gyaran,ko'ina ya koma tamkar sabo,sae ƙamshi ke tashi, Fitowa tayi daga part ɗin nashi,ta wuce kitchen don ta shirya mashi dinner ɗinsa,a kitchen ta samu Azmee ita da Saude,sun kammala dinner suna gyara kitchen ɗin,gaishe dasu ta fara yi,fuskokinsu a sake suka amsa mata, "Aunty azmee a shirya mun dinner ɗin babban yaya,inaso zan kai mashi ne," Murmushi Azmee tasaki tare da cewa"Masha Allah,ki ce Anyi welcome back kenan," Dariya sehrish tayi har fararen hakoranta suka bayyana,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"ae daddy,Ya amince na cigaba da zuwa part ɗinsa,inayi mashi aiki," "Amma naji daɗin jin hakan sosai,yanzu bari na shirya maki dinner ɗin," Amsa mata tayi da toh,sannan ta tsaya tana jiranta, Batare da 6ata lokaci ba,Azmee ta kammala shirya mata a warmers da sauran food stuffs asaman tray,ta miƙa mata,kar6a sehrish tayi tare da kama hanyar fita daga kitchen ɗin tana faɗin"nagode Aunty azmee," Babu kowa a main palour ɗin,yawanci duk basu kaiga dawowa cikin gidan ba,wasu kuma suna acikin ɗakunansu,tana cikin tafiya hannunta ɗauke da tray,taji maganar mutun abayanta, "Ƴar shila,"a ɗan firgice ta juya don taga kowanene,gabanta ne ya faɗi Rassss!cike da mamaki take bin shi da kallo yaushe rabon da ta sanyashi acikin idanunta harta manta,ita duk a tunaninta ma an tura shi aikine,ashe yana nan cikin gidan, Fuskar nan tashi ɗauke da wannan shu'umin Murmushin nashi,ya ƙarasa tare da cin burki ya tsaya tagabanta,Face to face suka fuskanci juna, Jikinshi na sanye da rigar ankara har guiwarsa,sae wandon jeans,sumar kan nan nashi yayi mata ɗan iskan gyaran gashin nan daya saba yi,an saisaye gefe da gefe na kan,tsakiyar kuma anbar sumar a tsaye ba ladabi, "Nayi kewarki sosai,abubuwa da yawa sun faru,bansamu isasshen lokacin da zamuyi magana ba,naso nazo na taya ki Murna na kasancewarki ƴar wurin Uncle ɗinmu Abusufyan,abun ya ƙayartar dani," Sakin baki sehrish tayi tana kallonshi,abun ya ɗaure mata kai,Yadda yake tsara kalami kamar ba wannan mashayin giyar ba,wata irin natsuwa wadda bata saba ganinshi da ita ba,har wani kyau ya ƙara,yayi haske abunshi,duk da ramar da ya ɗanyi, "Naji kinyi shiru baki ce komai ba" Jin muryarshi yasa ta dawo daga zurfin tunanin da tashiga,muryarta a ɗan ruɗe tace"amma kaine dagaske?ko an yi musayarka ne," Wani ƙayataccen murmushi ya saki na gefen fuska,kafin yace"Ni ne mana HAROON ɗin da kika sani,koda yake na canza a yanzu,nayi ma kaina karatun ta natsu,saboda inaso in zama mutumin kirki,kamar kowa,inaso na shiryu,don na samu mace ta gari,a kwanakin baya kin ta6a yi mun nasiha akan cewa kinaso nazama tamkar ƴan uwana,naji daɗin maganar nan da kikayi mun,kuma nayi amfani da hakan gashi yanzu ni kaina inajin daɗin sauyawar da nayi," Zuba mashi ido sehrish tayi tana ƙare mashi kallo har yakai ƙarshen maganar tashi,tayi matuƙar mamakin jin abunda haroon ke faɗa mata,kokwanto ta shiga yi anya haroon ba wani plan yake shirya mata ba? Ganin ta tsaya tana kallonshi yasa shi gane cewar kokwanto takeyi akanshi,Cikin sauri yace"nasan zaiyi wuya ki yadda dani,saboda sanin da kikayi mun ada,amma na canza ayanzu fiye da tunaninki," "Amma na daina ganinka acikin gidan nan"? "Masallaci nake kwana,shiya sanya baki cika ganina ba,yanzu bana jin daɗin zama ko ina,in ba masallaci ba,acan nake rayuwata,in kinga na fita daga cikin masallaci to wani abu mai muhimmanci ne ya fidda ni,kinsan na tara zunubi sosai shiyasa nake kusanta kaina da ubangiji sosae,saboda in samu yafiyarshi...." Yanayin yadda haroon yayi mata maganar ba ƙaramin tausayi ya bata ba,domin kuwa har hawaye sun taru acikin idanunshi,wata siririyar ƙwalla ce ta gangaro cikin idonshi,da sauri ya sanya hannu ya shareta, "Yaya haroon,ka daina zubar da kwallarka,tunda dai har ka shiryu ka koma ga Allah,zai kar6i tubanka ne,fata na shine Allah yasa ka daina duk wani abu mara kyau da kake aikatawa," Tana kai ƙarshen maganarta,yace"In sha Allah nadaina,bazan ƙara ba,Ni dai yanzu babban burin da nake dashi arayuwata shine in samu mace tagari inyi aure,zan fi samun kwanciyar hankali," "Kada ka damu,in sha Allah zaka samu," Tana kai karshen maganar ta kama hanya da sauri ta nufi upstairs, Bin bayanta da kallo haroon yayi har sai da ta 6ace ma ganinshi,fashewa yayi da dariya,a fili yace"Mata kenan!zuciyarku da rauni take,wannan alƙawari ne na ɗaukar ma kaina,Sai na cimma burina ko da ace shikaɗae ne abunda zan aikata kafin in bar duniya,"yana faɗin hakan ya wuce bedroom ɗinshi, Sehrish kuwa,tun bayan da tabar wurin,zuciyarta ke cike tab da tausayin Haroon,bakomai take tunawa ba fa ce fuskarshi,yadda yayi mata magana yau ba ƙaramin kashe mata jiki yayi ba,sanya ƙafarta tayi acikin falon Sgr,sannan ta shiga da sallama abakinta,ganin bai fito falon ba,yasa ta wuce bedroom ɗin nashi,sanin cewa ya shiga wanka,yasa ta shiga cikin bedroom ɗin kaitsaye batare da yin sallama ba, Gabanta ne ya fadi rass!!ganinshi tsaye gaban mirror daga shi sai short ajikinshi,hannunshi ruƙe da comb yana taje doguwar sumar kanshi, Juyawa tayi da sauri zata koma falon,ta cikin mirror ya hangota,gyaran Muryar da yayi ne yasa ta ɗan dakata daga ƙoƙarin da takeyi na fita daga bedroom ɗin nashi, "Where are u going?" Muryarta na kerma tace"Falo,dama dinner ne na kawo maka," "Okey,idan kin kai abincin falo,kizo inason ganinki" Da sauri ta amsa mashi da toh,fita daga cikin bedroom ɗin tayi,a saman table ta ajiye mashi tray din kayan abincin,sai da ta bada kusan minti 10 sannan ta koma bedroom ɗin nashi,A lokacin har ya kammala zura sleeping dress ɗinshi,Red colour sun fito da natural beauty dinshi,gefen gadonshi ya zauna,tare da aza ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya,yana karkaɗa ƙafarshi ta hannun dama wadda ya aza asaman ta hagun,yayin da hannunshi ke ruƙe da wayarshi yana daddanawa Da yatsan hannunshi yayi mata nuni da tazo gabanshi,cike da fargaba ta ƙarasa tare da tsayawa a tsaye tana faman zare ido, "Haka ya dace ki tsaya gabana?C'mon Kneel down"! Hankali atashe ta zube saman guiwowinta,jikinta nata faman kerma, Tun kafin ya kuma cewa wani abu,tayi saurin cewa"Am sorry babban yaya,daddy yace na baka haƙuri game da abunda ya faru jiya,dan Allah kayi haƙuri," Banza yayi da ita tamkar baiji abunda tace ba,gaba ɗaya hankalinsa na akan wayar hannunshi,sae da ya mula yasha iska sannan yace"Wanene SA"? Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,hannu ta aza akai tana fadin"Innalillahi!nashiga uku,"ƙasa ƙasa tayi maganar tuni ido ya raina fata, "Idan har kika bari na maimaita tambayar da nayi maki,jikinki ne zai gaya maki", Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"Wlh babban yaya ba dakai nake ba,su6ul da baka ne nayi bansan nace ba,kuma Allah bakai nace ma sa ba,Ni kawai nasan dai nace kullum fuska a ɗaure kamar sa,Kuma fa waƙa ce nake rairawa..." Bata ƙarasa maganar ba,ya katseta da cewa"Just one answer nakeso!ki faɗamun menene ma'anar kalmar SA da kika faɗi,if not u will be in serious trouble,"tashin hankali! Nan fa sehrish tashiga mazurai,shin tayaya zatayi mashi bayanin cewa shanu take nufi da sa!tabɗijancan,hauka ma takeyi da zata sanar dashi ainihin mai kalmar SA ke nufi,ta fahimci cewa baisan menene SA ɗin ke nufi ba,shiyasa har ya tambayeta don yaji ma'anarta,yadda zaiji daɗin hukunta ta, Shirun da tayi mashi ne ya 6ata mashi rai,tsawa ya daka mata wadda ta firgitar da ita,a ruɗe tace"SIR na Yalla6ai nake nufi,wani malamin mu ne na makaranta,muke kiranshi da SA,kuna kama dashi sosai,kyakkyawa ne shima,shiyasa nace fuskarka irin tashi," Guntun tsoki SGR yaja,kafin yace"Tashi kiban wuri,"da sauri ta miƙe,ta fito daga bedroom ɗin nashi,gaba daya ma tabar masa part ɗin,don ta lura yau kamar asama yake, Bedroom ɗinsu ta koma hannu tasa tare da tura ƙopar ta shiga ciki,Jahad ta samu a zaune saman gadon nasu hannunta ruƙe da wayarta,ta ƙurama screen ɗin wayar ido da alama wani abu take karantawa wanda yaja hankalinta har bata ji shigowar Sehrish ɗin ba,hosana kuwa tuni bacci yayi awon gaba da ita,tana kwance naɗe cikin bargo, Kamar daga sama taji an fisge wayar,a ɗan firgice ta juya don taga wanene ganin sehrish yasa ta sauke a jiyar zuciya tare da cewa"Ashe ke ce,wlh har kin bani tsoro,ƙoƙarin hawa gadon sehrish tayi tana cewa"Halan karatun Novel ɗinne?tayi maganar ayayin da ta aza idonta kan screen ɗin wayar,Ganin rubutun ƙur'ani yasata cewa"Oh ashe karatun qur'ani kikeyi hakan yayi kyau sosai,' "Ina kika je ne?tun ɗazu ina jiranki,kizo muyi fira don bana jin bacci yanzu," Shiru sehrish ta ɗan yi da alamun damuwa a fuskarta,hakan yasa jahad ta kuma cewa"faɗamun meya faru ne?na tambayeki kinyi shiru baki bani amsa ba,ko akwai wani abu ne dake damunki"? Shaking head sehrish ta ɗan yi kafin tace"bakomai jahad,naje part din babban yaya ne,nayi masa gyaran ɗaki dana falo,shiyasa na jima ban dawo ba,' Jinjina kai jahad tayi tare da cewa"amma duk da haka akwai sauran wani abu da ki ke ƙoƙarin 6oye mun,ko kin manta cewa ni ƴar uwarki ce,rabin ranki,koma nace ranki gaba ɗaya" Dariya sehrish tayi jin abunda jahad tace, "Jahad,akwai abunda ke damuna amma na barshi acikin zuciyata ne kawai,saboda baida amfani kona furta shi,kawai ki tayani addu'a " Ruƙo hannunta jahad tayi acikin nata,sannan tace"in sha Allah,rishi zan tayaki da addu'a,dama kuma kullum cikin yi maku addu'a nake yi gaba ɗayanku,"ta ƙarasa maganar,jikinta asanyaye saboda tunawa da mahaifiyarsu,a hankali taci gaba da magana"Ko wani hali Oumman mu take ciki a yanzu?nadamu sosai akan rashin mahaifiyarmu a kusa damu,baiwar Allah bazan ta6a mantawa da wasu kalami nata ba,tana yawan cewa ina sonku sosai ƴan ukuna,a duk lokacin dana kalleku,sai inji wani sanyi ya ratsa zuciyata,ku kaɗae ne dangin da nake dasu a duniyar nan,ina addu'a akan Allah ya raya mun ku......."kasa ƙarasa maganar jahad tayi saboda hawayen da suka shiga gangarowa daga cikin idanunta,ita sehrish nan take taji hawaye sun shiga wanke mata fuskarta, Sehrish ce ta ɗaura da cewar"babu tabbacin cewa zanyi tsawancin kwana,baƙin cikin wannan mutumin ma kaɗai ya isa ya halakar dani,zanyi kuka sosai,naci buri akan naga girmanku amma zaiyi matuƙar wuya hakan ya faru.........."duk wannan zancen da suke yi gaba daya kaf kalaman da mahaifiyarsu ke yawan faɗi masu ne,tun suna yara,dama kuma yaro akwai shi da ruƙo,in ya ruƙe abu aranshi da wuya ya manta shi har girmanshi,kuka sosai suka shiga yi babu mai lallashin wani,cikin shessheƙar kuka jahad tace"Oumman mu ta ta6a sanar dani cewa mu ba ƴan uku bane,Ƴan shida ne ɗaya ta mutu,biyu kuma Ya sayyadi ya kwashe su ya siyar ma ƙungiyarsu don ya samu kuɗi ........"hannu tasa tana share hawayenta a yayin da takai ƙarshen maganarta,,   Girgiza kai sehrish ta shiga yi yayin da hawayen idanunta ke cigaba da zuba,    "Jahad,wannan maganar ba gaskiya bace,nacewa mu ba ƴan uku bane!daga baya Oumma ta tabbatar mun da cewa mu ƴan ukune ta haifa,Ya sayyadine yayi mata ƙaryar cewar mu ƴan shida ne ta haifa,ɗaya ta mutu biyu kuma ya kwashe su ya siyar ma ƙungiyarsu,da farko ta yadda da kalamanshi saboda ta sanar dani cewa a lokacin da ta haife mu ba'a hayyacinta take ba saboda matsanancin ciwon nakuda daya taso mata gashi ita kadai ce a gidan,sae dai kawai ta farka a gadon asibiti,taga jarirai guda uku a gefenta,a yayin da shi kuma yake tsaye akanta,batasan meya faru ba,wannan dalilin ne yasa ta yarda da maganarshi daya faɗa mata,Ashe yayi hakanne kawai don ya ƙona mata rai,dama kuma rabi da kwata na kalaman ya sayyadi ƙaryane,zaiyi wuya ya faɗi gaskiya a bakinshi,mugun maƙaryaci ne,hakanan ma yana iya tsara ƙarya,ya mayar da ita tamkar gaskiya,don haka ki cire wannan aranki!"   Wata nauyayyiyar ajiyar Zuciya jahad ta sauke,muryarta ɗauke da tsantsar farin ciki tace"Har hankalina ya kwanta wlh,bakiji yadda naji ba,ashe ƙaryane ba gaskiya ba,Amma gaskiya mutumin nan baya tsoran Allah,ni fa duk a tunani na dagaske mu ba ƴan uku bane,akwai wasu suna nan a raye,kullum zullumin da nakeyi shine Suna ina?A wane hali suke ciki su ma?kamannin fuskarsu irin namu ne sak ko kuwa?Ashe duk ƙanzan kurege ne,Ya sayyadi dai ya shiga uku,in ya mutu yana aikata waɗannan mugayen halayan nashi,' Sehrish ta ɗaura da cewa"ae wannan mutumin bazai kai labari ba,irinsu tun a gidan duniya suke fara gir6ar abunda suka shuka,ƙaddara ce kawai tasa Oumman mu ta aureshi,Ashe shima da wani mugun nufin ya aureta,In sha Allah asirinshi sae ya tonu,kuma Ammi tayi mana al'ƙawarin cewa in aka kamoshi sae mun wanke mata mummunar fuskarshi da mari,Ranar kawai nake jira,in da rai da lafiya,nasan rayuwarmu a hannun Allah take,amma zan roƙi Allah akan ya nuna mun wannan lokacin,koda ace shikaɗae ne burina na ƙarshe da zan cika kafin in bar duniya!!"   Jahad tace"Ni dai koda ace bana raye aka kamo ya sayyadi,alhakin marina na akan ki,Ki haɗa da nawa duka ki kifa mashi su a fuskarshi,"   "Allah shikaɗae yasan wanene gawar fari acikinmu jahad,nima idan bana raye,Alhakin Marina na akanki Jahad,ki haɗa da nawa da naki ki kifa mashi su a fuskarsa,"ta ƙarasa maganar tana nuna ma jahad yadda zata kifa ma ya sayyadi mari a fuskarshi,   "Allah ya kiyaye in ta6a fatar fuskarshi da hannuna!wannan ƙazamin mutumin,sai dai in sanya glove a hannuna,"jahad ce tayi maganar,tare da 6ata fuskarta,   Sun jima suna fira atsakaninsu,kafin daga bisani,jahad ta kwanta,Sehrish kuma ta wuce toilet,bayan ta fito tayi alwala tayi sallah,komawa saman gadon tayi tare da ja musu bargo ta lullu6esu hadi da tofa masu addu'oi.                 *Aunty Babba* A 6angarensu Aunty babba kuwa,sam bacci ya ƙaurace ma idanunta,tsabar baƙin ciki ne ƙumshe acikin zuciyarta,tagaza samun natsuwa,tun bayan da Major ya ajiyesu a hotel ɗin,suka shiga ɗakin da aka kama masu,bata samu ta zauna ba,sae faman safa da marwa takeyi acikin ɗakin,Hayaam kuwa tuni bacci yayi awon gaba da ita asaman gadon, Allah kaɗae yasan mugun abunda take ƙullawa acikin ranta,don kuwa taci alwashin cewa,a gobe goben nan zasu wuce dajin nan na enugu inda wannan ƙasurgumin fasiƙin bokan yake,Wato Baba Ibliss,kuɗi ne matsalarsu,amma ta yanke shawarar cewa zata siyar da sarƙar gold ɗinta da kuma awarwaron sarƙar,hadda Earrings duka zata siyar don su samu tunkarar Bokan,    *Allah yaba mai rabo sa'a* *Boss Bature*    ❤🤍❤ *A washe garin Juma'a, Cikin bacci Sehrish ta dinga jin sautin waƙa ƙasa kasa"Takusa Aure ƙara faɗa breaker!ta kusa aure ƙara faɗa breaker,"sae faman mutsu mutsu takeyi acikin bargo,ga baccin bai isheta ba,gashi kuma an takura mata,Ranta yayi mugun 6aci,shiru kawai tayi acikin bargon tayi lamo tana tunanin wani shaiɗani ne tunda sanyin safe yake raira masu waƙa acikin ɗaki,ta kasa gane muryar wacece kamar hosana kamar kuma Muryar jahad,a ƙarshe ta tsayar da tunaninta akan cewa Hosana ce,saboda itace gwanar iya raira waƙa,da wuya kaji waƙa a bakin jahad sae dai karatun ƙur'ani,bata ƙarasa zancen zucin nata ba,taji an ƙara Volume hada ma kiɗa gangan gangan acikin kunnanta"Takusa aure ƙara faɗa breaker!takusa aure ƙara faɗa breaker," a fusace sehrish ta yaye bargon da ta lullu6a dashi,karaf idanunta suka sauka akan hosana,dake zaune saman front chair ɗin dressing mirror ɗinsu,ta dage da iya ƙarfinta na ƙarshe,sae faman kiɗa takeyi da hannayenta,   "OMG!!!" pillow ta raruma ta daddage ta jefa ma Hosana,cikin sa'a ya samu tsakiyar kanta,amma ko ajikinta da alama bata ji pillown ba,lalubo wani pillow ɗin sehrish tayi da ƙarfi ta wurga mata shi,Ya daki kanta,a firgice hosana ta juya don taga menene,pillows ta gani guda biyu a ƙasa,a hankali ta ɗago da idanunta kan wanda ya jefo mata da filon,   Daƙuwa Sehrish tayi mata da hannunta"Ungo nan don ubanki!Dama sai da raina ya bani cewa kece,Saboda baki da hankali,Mahaukaciya ce ke,Tunda sanyin safiya kin addabi mutane kin takurawa rayuwarsu,saboda tsabar rashin hankali waqa kike rairawa hada kiɗa,maimakon ki kama azkhar ɗin safe kinayi abakinki,.....".   Muryar jahad ce ta katse mata hanzarinta da cewa"Wai dama hosana ce ke raira mana waƙa da kiɗa!Nifa nayi tunanin cewa ko ringing ɗin wayarki ne,Amma dae hosana baki da hankali bakisan ciwon kanki ba!shiyasa har yanzu haukan naki ƙara gaba yakeyi,babu abunda zai hana in yiwa Daddy magana akai ki asibitin mahaukata,don abincika notikan kwakwalwarki da suka kwance a ɗauɗaure maki su,"tana magana tana kwatanta yadda za'a ɗaure mata notikan kan nata da hannunta,   Tashin ta kenan itama daga bacci,Kiɗan hosana ne ya farkar da ita,    Tunda suka fara maganar hosana ta zuba masu ido tana kallonsu tsabar bakin ciki ya hanata tanka masu,zuciyarta sae faman tafarfasa takeyi,arayuwarta ta tsani ace mata zararra ko mahaukaciya,fuskarta tacika fam ta kumbura kamar alkubus,a ƙule tace"Ni ce Zararra ko?kuma mahaukaciya"?   Har suna haɗa baki wurin cewa"Eh ance zararra kuma mahaukaciya kiyi abunda zakiyi,"hakan da sukayi ba ƙaramin tunzurata sukayi ba,miƙewa tayi daga saman kujerar,ta shiga nannaɗe hannun rigarta,hakan ya tabbatar masu da cewar dambe zasuyi,   Tana kammala naɗe hannun rigar,ta danƙara da gudu,ta daka uban tsalle ta haye saman gadon,kafin suyi wani yunƙuri,gaba ɗaya ta haɗe kawunansu ta bugasu jikin na juna,ƙara suka saki saboda zafin da sukaji,Ransu yayi mugun 6aci,Aikuwa gaba ɗaya suka tarar ma hosana suka shiga bugunta,ita ma kuma ta shiga kai masu naushi bana wasa ba,dama tafisu ƙarfi,don bala'e suna kuka suna faɗa su duka ukun,gashi babu mai rabasu, hafsat ce ta nufo bedroom ɗin nasu tun kafin ta ƙaraso ƙopar ɗakin,taji sautin kukansu da kuma sautin buge bugen da sukeyi,   Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,bugun ƙopar tashiga yi amma arufe take,sun datse ƙopar tun jiya da daddare da zasu kwanta Next page na nan tafe,amma fa in mutun najin bacci ya kwanta,don zai iya kai 10,😟💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,bugun ƙopar tashiga yi amma arufe take,sun datse ƙopar tun jiya da daddare da zasu kwanta,tana cikin bugun ƙopar ɗakin nasu sai ga Azmee ta shigo corridor ɗin ɗakin nasu,da alama daga kitchen take,ganin hafsat a ƙopar ɗakinsu sehrish tana ta faman yi masu magiya akan su buɗe mata ƙopar,yasa azmee yin hanzarin ƙarasawa kusa da ita tana tambayar ko lafiya,tun kafin ma hafsat ta bata amsa ta jiyo sautin kukansu Jahad acikin ɗakin,kuka fa bana wasa ba,hankali atashe azmee tace"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Meke faruwa ne!meyasa su ke kuka"?   Fuskar hafsat ɗauke da damuwa tace"Wlh bansani ba,zuwana kenan najiyo sautin kukansu hada ma buge buge da alama faɗa suke atsakaninsu,Ni tsorona ma kada su lahanta junansu,'   A ruɗe Azmee ta shiga bugun ƙopar tana kwala masu kira"Jahad!Sehrish!hosana!wai bazaku daina ba!Me kukeyi haka!kuzo ku buɗe ƙopar nan tun kafin ranku ya 6aci," duk wannan kwakwazon da azmee keyi a banza domin kuwa babu mai sauraronta,hasalima basu son tana yi ba saboda basu a hayyacinsu,   "Hafsat!kije ki sanar da Daddynsu ko wani daga cikin yayyensu game da abunda ke faruwa,su taimaka suzo ko ƙopar ce a 6alle,tun kafin yaran nan su halaka kansu,"acewar Azmee wadda hankalinta ya gama tashi,   Da gudun gaske hafsat ta fita daga corridor ɗin ɗakin,A main palour ta samu Mommynsu junaid tare da Abbansu da kuma Hajiya Azeema suna tattaunawa,wurinsu ta tunkara tana faman yarfa hannu idonta cike tab da kwalla,   Tun kafin tayi magana suna ganinta suka miƙe tsaye suna tambayar ko lafiya,   Muryarta na kerma tace"Su jahad ne,suke faɗa acikin ɗakinsu,gashi can suna ƙoƙarin halaka kansu,munyi munyi su buɗe ƙopar sunƙi buɗewa sae dai sautin kukansu kawai da muke ji,"   Tun kafin ma ta karasa maganar,Jiki na rawa suka nufi ɗakin nasu,hajiya azeema hada tuntu6e saboda tsabar sauri,a ƙopar dakin nasu suka tsaya,bubbuga ƙopar ɗakin Abbansu ya shiga yi a tsawace yake ambaton sunayensu,amma shiru babu wadda ta amsa masa,sae dai sautin kukan nan da suke ji na tashin hankali,    "Ina ganin bari na kira mahaifinsu wata'ƙil idan yayi masu magana sun ji maganar shi,'Abba ne yayi maganar tare da zura hannu cikin aljihun wandonshi ya ɗauko wayarshi,yatsun hannunshi har kerma sukeyi wurin lalubo number Abusufyan,ya danna mashi kira ta soma ringing,   Hajiya Azeema da Alexandra duk sun bi sun ruɗe,   "Ni babban tashin hankalina ma kada yaran nan su illata kansu,Wlh abun ya tsoratar dani sosai ya tayar mun da hankalina,"Hajiya azeema ce tayi maganar,fuskarta tamkar zata fashe da kuka,   Hafsat kuwa tana acikin main palour ɗin,Sae faman kuka takeyi,kwatsamm taji takun takalmi,da sauri takai idanunta wurin MARSHAL OMAR ne ke saukowa daga upstairs da gudun gaske ta tunkare shi tana fadin"Ya Omar,gasu jahad can suna faɗa acikin ɗakinsu,kuma sun kulle ƙopa,anyi anyi su buɗe sun ƙi su buɗe....."   Jin wannan maganar yasa hankalin Omar mugun tashi,da sauri ya nufi bedroom ɗin nasu,lokaci guda kowa na gidan labarin abunda ke faruwa yaje musu,hatta su Junaid dake ɗakunansu suna bacci sae da suka tashi,su fawan twins,dasu Irfan,hada Dr hariis da gwaggon katsina,da Ammi,dukkansu kowa fa amma banda Sgr dake a bedroom ɗinshi,   A ƙopar ɗakin nasu sukayi cirko cirko,Abusufyan yafi kowa shiga damuwa bawan Allah,kamar ya zauce haka yake bugun ƙopar ɗakin nasu yana roƙonsu akan su daina kokoyin da sukeyi suzo su buɗe mashi ƙopa amma shiru babu wanda ya tanka mashi,Haka Marshal Omar ma,Tamkar zai 6alle ƙopar haka ya dinga bugun ƙopar ɗakin nasu,amma duk abanza,Junaid kuwa tuni ya fashe da kuka,yadda kasan wani ƙaramin yaro,   Cikin shessheƙar kuka Gwaggon katsina tace"nashiga uku..Wayyo Allah na,wlh nasan duk sharrin Ya sayyadine bazai barsu hakanan ba,yanzu haka shine ya shiga tsakaninsu,Ya Allah kayi mana maganin wannan baƙin shaiɗanin....'kuka takeyi hada majina,    Lokaci guda sukaji shiru tsit cikin bedroom ɗin nasu babu wani gunjin kuka,hakan ya tabbatar masu da cewar wani mummunan abunne ya faru dasu,nan fa kowa ya shiga kallon kallo,yayin da zuciyoyinsu keta bugawa da karfi,    Jiki asanyaye Abusufyan ya zame ƙasa,tare da aza hannayenshi saman kanshi,yayin da bakinsa ke furta kalmar"Innalillahi wa'Inna ilaihirraji'un,'   "Abba,ina ganin kawai a 6alle ƙopar," acewar kanal yousouf, Omar yace"Nima abunda nake tunani kenan,amma ƙopar fa ta cije sosai,na buga na buga amman ko motsi batayi,duk irin ƙarfin da nake dashi,"   Cikin shesshekar kuka junaid yace"Bari naje na ɗauko zarto sai a datse kubar,"    Ya ambaci hakan tare da watsawa da gudu ya nufi weapons Room ɗinsu (ɗakin ajiye makamansu,"A rufe ya samu ɗakin,sam ya manta cewar key ɗin yana a wurin babban yayansu,sae da yayi arba da ƙopar a rufe sannan yasha kwana ya dawo da gudu ya haye upstairs ɗin,   Faɗawa part ɗin SGR yayi,a rikice ya shiga bedroom ɗinshi,a lokacin Sgr na kwance saman shimfiɗeɗen gadonshi yana bacci,   Junaid baibi takanshi ba saboda a ruɗe yake,side drawer ɗinsa ya tunkara,ya shiga bubbuɗeta yana neman key ɗin,duk inda ya duba babu key ɗin,saman gadon ya hau,yana kiran sunanshi"Babban yaya!Babban yaya!pls wake up!babban yaya ka tashi dan Allah,'   Cikin bacci rafayet yaji muryar junaid dake ta faman kiran sunanshi,a hankali ya buɗe idanunshi kai tsaye suka sauka kan fuskar junaid,ganin hawaye jaga jaga a fuskar junaid yasa Sgr yin hanzarin miƙewa daga zaune,hankalinshi aɗan tashe yake kallon junaid,da wata irin kasalalliyar murya ya ambaci sunanshi"Junaid!what are u crying for?meya faru ne?.     "Babban yaya,key nake nema na weapon's room,inaso in ɗauko saw ne,za'a 6alle ƙopar ɗakinsu Sehrish"   Cike da mamaki Sgr yace"For what reason?wani abu ya samu door ɗin da za'a 6alleta"?   Ganin bai fahimci inda zancen nashi ya dosa ba,yasa shi yi mashi bayanin abunda ke faruwa,    Saukowa Sgr yayi daga saman gadon nashi,junaid na biye da bayanshi suka fito daga part ɗin nasa,da sauri da sauri suke saukowa down stairs,    Lokacin da suka shigo Corridor(doguwar hanyar) da ɗakunnansu sehrish suke a jere,Hankalin Sgr ya ɗan tashi musamman daya ga dandazon matasan gidan,ga kuma su Abbansu kowa atsaye cirko cirko,fuskokinsu sun nuna alamun damuwa atattare dasu,'   Abbansu na ganinshi yayi saurin ruƙe hannunshi yana fadin"Yawwa rafayet,nasan zaku iya kai da Omar,dan Allah ku haɗu ku 6alle ƙopar nan,ko mun samu muga meke faruwa aciki,'   A hanzarce kowa ya dare ya basu wuri,da iya ƙarfinsu Na ƙarshe suka daddage suka kaima ƙopar wani irin kwakkwaran bugu ji kake daraamm!nan take Sakatar ciki ta zame da kanta,ƙopar ta buɗe,gaba daya suka afka ciki,   Ba ƙaramin girgiza sukayi ba,gaba dayansu musamman Abusufyan,abunda suka gani yayi matuƙar tayar masu da hankali,Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un!!!wannan shine abunda suke ambato a bakunansu,   Sun tarwatsa komai na bedroom ɗin nasu,ɗigon jini jinin da suka gani shi yafi komai tayar masu da hankali, Jahad ce kwance ƙasan gadon saman tiles,damtsen hannunta duk sawun cizo ne,wurin duk ya farfashe,hatta saman kumatunta cizon ne,daga can saman gadon kuwa hosana ce,baje hannunta dafe da kanta ta toshe kunnuwanta sae faman mutsu mutsu takeyi da ƙafafuwanta,alamar idonta biyu,Sehrish kuwa basu san ina ta lula ba,   Zubewa Abusufyan yayi agaban Jahad dake kwance,hannu yasa yana jijjigata yana ambaton sunanta saboda ya gane itace,hawaye sae faman sintiri sukeyi akan fuskarshi,    Jikin kowa yayi sanyi,zukunnawa Abbansu yayi agaban Abusufyan din yana kallon jahad dake kwance,Sawun haƙoran dake asaman fatar jahad ya tabbatar mashi da cewar faɗa ne ya 6arke a tsakaninsu har sukayi kokoyin nan,    "Ina tunanin suma tayi ne,wani ya ɗauko mun ruwa dan Allah,"Abbansu ne yayi maganar,da sauri fawan ya fuce daga dakin,ya nufi babban falo don ya ɗauko masu ruwan da za'a yayyafa mata, ....a hankali Sgr yake bin ɗakin nasu da kallo,sunyi mashi kaca kaca,damben daga saman gadon nasu ya fara,Hatta bargon lullu6arsu duk sun jefo shi ƙasa,zagayawa yayi ta dayan gefen gadon,6angaren hannun hagu,tunkan ya ƙarasa ya hango ƙafafun mutun,hakan ya tabbatar mashi da cewar cikon ta ukunsu ce,ta wuntsila ta baya,lokacin daya ƙarasa wurin a kwance ya samu Sehrish,gefen bakinta ya ɗan fashe,ga kuma sawun haƙora asaman ƙirjinta,da kuma damtsen hannunta,zuƙunnawa yayi agabanta yana ƙare mata kallo,   "Rafayet!wacece anan?ko cikon ƴar ukun tasu ce"?Ishaq ne yayi maganar ganin rafayet ɗin zuƙunne a wurin,   "Itace," ya bashi amsa atakaice,da sauri Abusufyan ya miƙe tare da sauran suka nufo wurin don suga a wani hali take ciki,   Tun kafin su ƙaraso Sgr yayi saurin kai hannunshi gaban rigarta yaja rigar ya lullu6e mata ƙirjinta daya fito sosai,   Fashewa da kuka gwaggon katsina tayi tana fadin"Wayyo Allah ƴa'ƴan Abusufyan ɗina!ni nasan cewa ba yin kanku bane,Wlh sai Allah ya saka maku,Bayin Allah sunji jiki,kowanene yayi masu wannan ɗanyen aikin,jibi yadda aka ciccije masu fata,Yanzu haka ya sayyadine yazo masu da suffar kura yayi masu wannan aika... aikan,' Harris ne ya katseta da cewa"pls gwaggo kibarmu muji da abunda ke damunmu idan ma kina magana ƙara masu zafin ciwon kikeyi,   Jin haka yasa tayi saurin rufe bakinta,tana cigaba da matsar kwalla a idonta,    "Abun ya ɗaure mun kai!garin yaya haka ya faru?gaba daya kowannansu sawun cizo ne a fatar jikinsu",Abbansu junaid ne yayi maganar,a yayin da suke tsaye gaban sehrish,Sgr kuma na a zuƙunne,    Hafsat ce ta basu amsa da cewa"lokacin da nazo ƙopar dakinsu,naji sautin Kukansu acikin ɗakin da kuma sautin bugu kamar suna dambe a tsakaninsu,ina tunanin cewa faɗa sukeyi a tsakaninsu,'   Jinjina kai marshal Omar yayi tare da cewa"Tabbas sunyi sa insa a tsakaninsu ne har abun yakai ga fada,Kuma wannan cizon dake asaman fatar jikinsu,ba kowa bace tayi masu shi ba fa ce HOSANA!saboda nima ta ta6a cizo na a kwanakin baya,da ranta ya 6aci a asibiti,ta cije ni kuma ba ƙaramin zafi naji ba a lokacin,"   Abba yace"No wonder!in kuka lura babu sawun cizo a fatar jikinta,indai itace kwance asaman gadonsu,ku kalli jikinta dakyau,kuma bata jigata ba,kamar yarda ƴan uwan nata suka jigata,"    Suna cikin maganar nan,Fawan ya shigo hannunshi ɗauke da robar ruwan daya dauko masu a fridge,da sauri kanal yousouf ya kar6i bottle water din,ya 6alle murfin,tare da tarbo ruwan a tafin hannunsa na dama,ya watsa shi a fuskar jahad,Nan take taja dogon numfashi tana ambaton sunan Allah abakinta,ajiyar zuciya suka shiga saukewa,da sauri Abusufyan ya dawo wurinta,tare da zukunnawa agabanta,ya ɗago da ita ajikinshi yana ambaton sunanta"Jahad!Jahad!"koda jahad ta buɗe idanunta tayi tozali da fuskar Daddynsu saita fashe da matsanancin kuka tana cewa"daddy kaga abunda hosana tayi mana?kawai daga magana ta hau bugunmu ni da Sehrish,duk tabi ta gartsa mana ciwo a fatar jikinmu....'tana magana hawaye na zuba a idanunta,   Runtse ido Abusufyan yayi tare da buɗesu a hankali,abun ba ƙaramin ta6a mashi zuciya yayi ba,   Hannu Omar yasa tare da kar6ar Robar ruwan dake hannun Kanal yousouf ya taka izuwa inda Sgr ke a zuƙunne ya miƙa mashi ita,Kar6a Sgr yayi tare da kur6ar ruwan abakinshi,ya fesar dashi akan fuskar Sehrish,a firgice ta farka gami da mikewa zaune tana faman zazzare idanunta,one by one tabi su da kallo,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin Sgr,ga kuma su hajiya azeema tsaye duk akanta,tafin hannuwanta tasa tare da rufe fuskarta,tana kuka,    "Wani ya ɗauko min FA box a medical room"Sgr ne ya ambaci hakan,da sauri irfan ya fuce daga ɗakin don zuwa ɗauko akwatin,ruƙo hannun Sehrish Hajiya azeema tayi tare da zaunar da ita gefen gadon,"sannu kinji,yi shiru ki daina kuka,"cikin lallashi takeyi mata maganar,      Hawa saman gadon nasu Hafsat tayi,tare da kai hannunta ta ɗago da hosana ajikinta,sae faman kerma jikinta yakeyi,ciwonta ya motsa,da alama an rabu da shan magani,duk a tunanin su abun yayi sauƙi,ashe da sauranta,tabbas hosana tana buƙatar ganin likitan mahaukata,   A faɗace Omar ya daka masu tsawa gaba dayansu yace"wai duk menene yajawo hakan!ba zaku buɗe baki kuyi ma mutane bayani ba!"    Cikin shessheƙar kuka Sehrish tace"Hosana ce,tunda sanyin safiya tafarka,tana raira mana waƙar takusa aure ƙara faɗa breaker,kuma hada kiɗa take raira waƙar duk ta takura kunnuwanmu,har muka farka daga bacci,Don munyi mata faɗa shine ta naɗe hannun rigarta ta hau mu da bugu da cizo kamar ta samu jakuna....'   Cike da mamaki kowa ke kallon sehrish dake kora masu bayani,Ishaq yace"Wai yanzu duk don saboda wannan ku ka kusa illata junanku?gaskiya akwai gagarumar matsala babba ma kuwa,'    Abbas yace"dama da wuya kaga ƴan biyu ko ƴan uku suna zaman lafiya a tsakaninsu,zakaga suna tsananin son junansu,amma ta wani 6angaren basu jituwa,don akwai labarin dana ta6a ji shigen irin wannan daga kokowa suka kashe kawunansu,"   Jin wannan maganar ta Abbas ya ƙara daga masu hankali,Abba yace"in sha Allah,ba zamu bari hakan ta faru ba!tunda abun har yakai ga faɗa da jima juna ciwo,dole a raba masu wurin kwana,shine kawai mafita,"   "Abunda nake ƙokarin cewa kenan"acewar hajiya azeema,   Ammi dai abun yafi ƙarfinta daga ita har Alexandra da hajiya Saratu suna atsaye sun zuba ma sarautar Allah ido,Lamarin yaran yayi matukar daure masu kai,    Dawowa cikin ɗakin nasu Irfan yayi hannunshi ɗauke da First aid box ɗin,ya ƙaraso tare da miƙa ma Sgr akwatin,hannu yasa ya kar6e shi tare da ajiye shi a ƙasa,    Sannan ya zauna,daga gefen gadon,suna fuskantar juna shi da sehrish,wadda ke ta faman shessheƙar kuka,wani irin kallo daya jefa mata,tuni ta nemi kukan da takeyi ta rasa,    "Close ur eyes,"da sauri ta rufe idanunta kamar yarda ya umarta,tana ji yasa mata audiga a wurin ciwon yana goge mata jinin,a sannu ya shiga yi mata dressing din ciwon da taji,bayan ya kammala da ita,Abusufyan ya ruƙo hannun jahad,ya dawo da ita gefen Sgr ya zaunar da ita,cikin lokaci ƙankani Sgr ya kammala yi mata dressing ɗin itama,    "Ita kuma hosana ya zamuyi da ita?kodai asibiti zamu kai ta?Acewar Abusufyan,   Omar yace"Rafayet zai iya duba mana ita anan gida ma"    "Omar am not a psychiatric doctor,though i've experience about their work,zan iya duba ta,Amma a ƙa'ida,psychiatric doctor ya kamata yayi checking ɗinta,bazan shiga aikin da banawa ba,"kaji turawa,ƴan bin ƙa'ida,   Jinjina kai Omar yayi fuskarshi ɗauke da murmushi,ya juya tare da kallon Dr harris dake tsaye ya goya hannayenshi saman ƙirjinshi yace"Bismillah,"yayi maganar yayin da yake yi mashi nuni da hosana wadda ke kwance ajikin hafsat,idanunta sun birkice sae farar kwayar idon kawai,yatsunta kuwa sae faman kerma sukeyi,hada na kafafunta,   Kallonta kawai Dr harris yayi batare daya ta6a jikinta ba,ya faɗi sunan allurar da take buƙata ayi mata,   Da sauri Omar ya ciro wayarshi tare daddana wasu numbobi,ya kira Dr Emran na asibitin Sgr,kiran na shiga emran ya ɗauka,don haka Omar ya miƙa ma Dr harris wayar don suyi magana,   Bayan sun kammala wayar,ya dago tare da kallon Marshal yace"Ya sanar dani cewa within 15 mins zaizo tare da allurar da kuma medicine ɗinta," Omar yace"Okey,Allah ya kawo shi lafiya, "Ku kwanta saman gadon,itama mara lafiyar a kwantar da ita before doctor din yazo,Azmee ki shirya masu breakfast dinsu,yanzu haka ma Yunwa ce ke Cinsu,shiyasa su kayi wannan damban," sae yanzu ammi ta tanka masu,saboda tsabar gatanci maimakon asamu wanda xaiyi masu faɗa da tsumagiya a Zane su, amma kowa ya rufe ido,sae lalla6a su akeyi,diyanso kenan,shalelen abusufyan, miƙewa sgr yayi daga zaunen da yake,sannan yayi masu nuni da su kwanta,a hankali kowaccensu ta kwanta yadda kasan waɗanda suka yi wata suna Jinya don sunji jiki,a hankali Hafsat ta janye Hosana daga  jikinta ta kwantar da ita,har lokacin bata dawo hayyacinta ba,sae faman fari takeyi da idanuwanta,yatsun hannunta dana ƙafafunta sae kerma suke yi, Haɗa baki su fawan su kayi wurin yi masu ya jiki,kafin daga bisani matasan  suka fita daga ɗakin nasu tare da Ammi da hajiya saratu,Ya rage daga Sgr sae Marshal Omar,Hajiya azeema da kuma abusufyan da kuma gwaggwon katsina sae hafsat,Azmee ta wuce kitchen don ta shirya masu breakfast ɗinsu,within 15 mins,Dr Emran ya ƙaraso gidan,a cikin motarshi yazo,tun a waje ya haďu da dr Harris tare da kanal Yusuf a tsaye,dama shi suke jira,fitowa yayi daga cikin Motar hannunshi dauke da Ledar maganin Hosana da kuma injection din da xa'ayi mata,gaisawa suka fara yi  fuskar kowannansu dauke da murmushi,canal Yusuf ne ya kar6i Ledar da Emran din yaxo da ita,sun so ya shigo daga ciki suyi breakfast atare dashi,Amma ya sanar dasu uzurinshi,hakan yasa suka ƙyale shi,sallama sukayi da juna sannan suka koma ciki da sauri, Cikin bedroom din nasu,Dr Harris ya shigo ganinshi yasa Omar da Sgr suka bashi wuri donya ƙarasa gaban gadon,batare da 6ata lokaci ba,ya ɗura ruwan allurar acikin syringe,aikuwa kamar akan idon Hosana yana kai hannu zai ruƙota ta zabura,tashiga yan buge²,ganin haka yasa sgr da Omar matsawa kusa dashi,sae da suka rurruketa dakyar aka samu yayi mata allurar,yana  kammala yi mata allurar,nan take zufa ta Shiga tsastsafowa daga jikinta,Kafin wani lokaci tuni bacci yayi awon gaba da ita,hankalinsu ba ƙaramin kwanciya yayi ba,   Juyawa dr Harris yayi tare da kallonsu Omar yace"in sha Allah,Zata ji sauƙin jikin nata,sannan idan ta farka,ga medicines ɗinta nan,bayan taci abinci,akwai direction ajikin kowani magani sae a duba,idan za'a bata," Amsa mashi sukayi da toh,Omar yace"aikin ka na kyau dr,"sannan ya mayar da idanunshi kan hajiya azeema tunkafin yayi mata magana tace"Zan kula dasu,idan tafarka zan bata maganin da yardar Allah,"murmushi ya saki tare da juyawa ya kalli sgr,"Muje ko?time karya ƙure mana,naga yanzu har 12 ta kusa,nan da wani lokaci xa'a shafa fati.....'bai ƙarasa maganar ba ganin irin kallon da rafayet ya jefa mashi,Dariya Omar yayi yana faɗin"Sorry bro,kada ranka ya 6aci mana,Yau fa ranar farin ciki ce agaremu,murmushi yakamata a gani akan fuskokinmu,ɗanyi murmushi mana,cike da zolaya Omar keyi mashi magana,shi kuwa Namijin sae faman tamke fuska yake yi,daga bisani suka fita daga ɗakin atare da dr harris, Komawa hajiya azeema tayi tare da samun wuri gefen gadon ta zauna tana kallonsu,duk sun rufe idanunsu kamar masu yin bacci,    "Bismillah gwaggo ku zauna mana,"azeema ce tayi maganar tare da yi mata nuni da saman bedside drawer dinsu,jiki asanyaye gwaggon katsina ta karasa ta zauna saman drawer din,ita dae har  yanzu bata yarda Cewar Hosana ce ta ciccijesu ba,    "Azeeme yanzu kema kin yarda cewa yarinyar nan itace da kanta ta gartsa ma ƴan uwanta cizo har haka?Ni nafi tunanin cewa Ya Sayyadine yazo da suffar kura yayi masu wannan aika aikar,mutumin nan fa ba ƙaramin Taƙadari  bane,banbancinshi da shaiďan kaho ne kawai da babu,"wannan maganar da gwaggon katsina tayi ba karamin dariya tabasu ba,    Girgiza kai hajiya azeema tayi fuskarta ɗauke da dariya tace"gwaggon shagali,ae in ma shine to ta Allah ba tashi ba,ki kwantar da hankalinki,Sayyadi yake kowa,ba abunda ya isa yayi masu bi'iznillahi,"   Washe Baki gwaggo tayi da alama taji dadin abunda Azeema tace mata,   "Allah yayi mana maganin la'ananne," Azeema ta amsa mata da ameen, Sae wuraren karfe sha biyu da rabi Hosana ta farka jikinta da sauki sosai,kuma tana bude ido ta fashe da kuka tana ambaton  sunansu sehrish da jahad,sae da aka nuna mata su sannan hankalinta ya kwanta, Tuni azmee ta kawo masu breakfast ɗinsu acikin dakin,da taimakon Hafsat da kuma hajiya azeema suka ci abincin,bayan sun kammala cin abincin,Hajiya azeema da gwaggo suka bar dakin,ya rage saura hafsat ita kaɗai,gyara masu bedroom din nasu ta Shiga yi,komai yadawo normal Ba kamar daba da suka hargitsa dakin,bayan ta kammala gyaran ɗakin,wuri tasamu saman side drawer dinsu ta zauna tana kallonsu,   "Hosana ki ji tsoran Allah,jibi yadda kika raunata mu sae kace ba yan uwanki ba,"jahad ce tayi maganar ranta a6ace,   A kule hosana tace"ae laifin ku ne,saboda me zakuyi mun rashin kunya?ni ba yayarku bace?oumma tace ni ce babba acikin ku,saboda majnun ya faɗa mata cewa ni ce na fara zuwa duniya,sae da na shaƙi iskar duniya da minti biyar sannan ke kika zo daga ke kuma sae waccen uwar tsiwar" "dakyar take magana,saboda har yanxu jikin nata da sauranshi,   Guntun tsoki sehrish taja"karki kara ce mun uwar tsiwa,in ba haka ba zan nuna maki kalar nawa haukan,mara mutunci kawai,kuranya mai cin naman ýan uwanta..."   Tunkan ta ƙarasa maganar,da Sauri jahad ta toshe mata bakinta,"Dan Allah ya isa haka,da alama baki ji jiki ba,shiyasa kike ƙoƙarin tsokanota,salon Kija mana jinyar  ta koma a gadon asibiti,"    Hafsat dake zaune tana sauraronsu,sae faman kunshe Dariya takeyi, *Boss Bature*   ❤🤍❤ Gaba ďaya matasan gidan,kowa ya Shiga yin wankan juma'a,Kafin wani lokaci duk sun shirya halarta Sallar Juma'a tsaf,kowa ya ɗauki wanka na mutunci wankan shadda,abun sai wanda ya gani,bakowa ne yasan da zancen ɗaurin auren babban yayan nasu ba ko acikin matasan  gidan,manyan su ne kawai suka son da ɗaurin auren,sauran kuwa koda zasu san da auren sai dai suji  a masallaci a yayin da ake sanarwa. Zuba mashi ido Alexandra tayi ganin yadda  yake ta rawar jiki,yaci uban ado cikin farar shadda,ya zura malunmalun,ya sanya sabuwar hula akanshi,ga agogo sabuwa ya Sanya a hannunshi,ga haɗaɗɗun takalma masu tsadar gaske ya zura a kafafunshi,sae faman sakin Fara'a ya keyi kamar wani sabon ango,yana tsaye agaban mirror hannunshi dauke da kwalbar Turare sae bin jikinshi yakeyi ko ina yana feshe shi saƙo da lungu na jikinshi tamkar  zai ƙarar da turaren dukansa,   Abun ya ɗaure mata kai cike da mamaki tace"Darling,irin wannan daukar wanka haka?kaji tsoran Allah kodai kishiya Zaka ƙaromin ne"? dariya abbansu yayi tare da ďan juyawa ya kalli wurin da take zaune gafen gadonsu,ta kura  mashi ido ko kyaftawa batayi,     "Ni da nake da Alexandra,Me zanyi da wata ya' mace?Ni na isa ma nayi maki kishiya?kefa ta dabance ko acikin mata,shiyasa lokacin da kika tafi kika barni nagaza samun natsuwa,kuma naqi kula kowa,saboda son da nake yi maki,"    ƴar hararar wasa ta jefa mashi tare da cewa"daɗin baki zakayi mun ko?    "No,ba haka bane,am serious fa,taya zanyi aure baki sani ba?kamar dai wani munafuki,wannan fa wankar sallar juma'a ne,ko kin manta cewa Yau juma'a ne"?   Shiru ta ɗanyi tana kallonshi,kafin ta ɗan ta6e bakinta tare da cewa"Okey,natuna,nidae duk da haka ban yarda dakai ba Allah,ji nake kamar na bika masallacin nan,"   Dariya sosai abba yayi,bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"Ashe kina kishi ne?shine kuma kika tafi kika barni,ba kiyi tunanin cewa zan iya ƙara aure ba,a bayan idonki ba"?   "Ae nasan cewa ba zaka iya ƙara aure ba,that's why ban damu akan haka ba,nasan wanene mijina,kuma na yarda da irin son da yake yi mun,bazai haɗa ni da wata ba," acikin zuciyarta kuwa cewa takeyi"Mutun ma ya kuskura yayi mun kishi,da kuwa na tashi gidan nan da bomb,kowa ya rasa,"    Suna cikin magana,sae ga junaid ya faɗo cikin ɗakin,jikinshi na sanye da farar shadda,sae ƙamshi ke tashi ajikinshi,hannunshi na ruke da hularshi,mommynsu na ganinshi ta miƙe jiki na rawa,ta rungumoshi tana shafa sumar kanshi, "My baby boy,U look so beautiful,Har ma kaso kafi daddynku kyau,"ta ƙarasa maganar a yayin da take raba jikinta daga nashi, Ashagwa6e yace"Mommy,yanzu kina nufin Abba ya fi ni kyau?kallar ni fa dakyau ki gani tun daga ƙasa har sama,son kowa ƙin wanda ya rasa," Dariya sukayi gaba ɗayansu,Abbansu yace"To fa!junaid kishi kake dani"? Turo baki yayi yana faman ƙunƙuni,irin na shagwa6a66un nan, Alexandra tace"wasa nake nima,kafi shi kyau nesa ba kusa ba," Ƙayataccen murmushi ya saki jin abunda tace, Mayar da hankalinshi yayi kan abban nasu tare da cewa"Abba mu tafi,kada lokaci ya ƙure mana," "Toh,Uban sauri,mu tafi," yayi maganar tare da ruƙo hannunshi, "Madam mu zamu wuce" Murmushi tasaki tare da ɗaga masu hannu tace"Adawo lafiya,in anje anyi mana addu'a," Junaid yace"kada ki damu mommy zanyi maki addu'a akan Allah yasa daddy ya ƙara maki kishiya," ɗan zaro ido waje tayi tana kallonshi,da sauri yaja hannun abbansu suka fuce suna dariya, A main palour Matasan gidan suka hallara ga6a dayansu,sae ƙamshi ke tashi,kowannansu fuskarshi na ɗauke da murmushi,musamman abusufyan,shigowa abba yayi cikin falon hannunshi cikin na junaid,tunkan ya ƙaraso ya lura cewa babu Rafayet acikinsu, Kowa sai tambayar ina babban yaya yake,saboda sun saba tafiya masallacin juma'a atare,gaba ɗayansu suke hallara a babban falon nasu duk juma'a before su wuce masallaci,shiru babu rafayet,sae Faman duba agogon hannuwansu sukeyi suna kallon lokaci,har sai da Marshal Omar yace"bari naje bedroom ɗinshi yanzu haka bai kammala shiryawa bane,"da sauri ya tunkari upstairs ɗin yana ƙoƙarin hawa saman benen,Suka jiyo sautin takalmansa, Gaba ɗayansu suka ɗaga idanunsu sama suna kallonshi,Cike da tsananin mamaki,tunda suke arayuwarsu basu ta6a ganin sgr ya sanya shadda ajikinshi ba,this is the first time daya fara sanya shadda ajikinshi,tabarakallahu ahsanul khaliƙin,Getzner ce sky blue mai ɗaukar ido,wadda sehrish ta ta6a ɗauko mashi a kwanakin baya,donya sanya amma yaƙi sanyawa,To yau dai itace ya sanya ajikinshi,Babu hula akanshi amma ba ƙaramin kyau sumar kanshi tayi ba,yayi mata gyara na musamman,hannunshi kuwa na sanye da Wannan diamond watch ɗin tashi,yayin da ƙafarshi ke sanye da penny loafers,tunkan ya ƙaraso down stairs din ƙamshin turarenshi ya gauraye ko'ina,yadda kasan tauraro acikin taurari haka ya bayyana,tafiya yakeyi gently tamkar baisan taka ƙasa,fuskar nan tashi aɗaure babu fara'a ko miskala zarratin,sae kace ba yau zai angwance ba, A hankali yake tattaka stairs ɗin, yayin da yake manna links ɗin hannun rigarshi,koda ya ƙaraso cikin falon,batare daya kalli kowannansu ba,ya nufi hanyar fita daga main falo ɗin,Murmushi abbansu ya saki aranshi yace"Rafayet kenan" batare da 6ata lokaci ba,Suka fito waje gaba dayansu,dama already motocinsu na nan a jere,Nan kowa ya buɗe motarshi ya shiga,A jere motocin suka fuce daga cikin gidan ɗauke da jiniya, *💃💃💃ALHAMDULILLAH, A YAU JUMA'A DUBBAN JAMA'A SUN SHAIDA ƊAURIN AUREN RAFAYET SALAHUDDEEN HOSSEIN,TARE DA AMARYARSA SEHRISH SALAHUDDEEEN ABUSUFYAN💃💃💃*, bayan kammala sallar juma'a aka ɗaura auren nasu,Sae dai muce Allah ya basu zaman Lafiya atsakaninsu? *Finally Rafayet weds sehrish*🥳🥳🥳😘💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina 08103884440❤_ Fitowarta kenan daga cikin toilet taji gabanta ya faɗi rasss!da sauri takai hannu ta dafe saitin zuciyarta,ƙamewa tayi abakin toilet ɗin batare da ta motsa ba,jahad dake zaune saman darduma,da alama ta kammala sallah,jikinta na a sanye da hijab Maroon colour,ta ɗaga hannayenta sama tana addu'a,tunkan ta kammala ta lura da halin da Sehrish ke ciki,tana shafa addu'ar da sauri ta miƙe ta tunkareta,     "Sehrish!lafiya meya faru ne? A ɗan ruɗe ta tambayeta,    Sehrish kuwa sam ta gaza buɗe bakinta tayi magana,saboda yanayin da ta shiga,gaba ɗaya jikinta yayi wani irin sanyi,     Ruƙo hannunta jahad tayi tare da cewa"sehrish!wai lafiya?ki amsa mun mana"?   Lumshe ido sehrish tayi a hankali ta shiga sauke ajiyar zuciya,daga bisani ta ɗan ware idanunta tana kallon fuskar jahad,dake tsaye agabanta,   "Ko kin fama ciwonki ne"? Girgiza kai sehrish tayi alamar a'a,tukunna tace"Jahad,ina fitowa daga cikin toilet ɗinnan,naji gabana ya faɗi rass,kuma naji jikina gaba ɗaya yayi mun sanyi,bansan meya jawo hakan ba,"    "Ki cigaba da ambaton Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un acikin zuciyarki,In sha Allah babu abunda zai faru dake fa ce alkhairi,"ta ƙarasa maganar tare da janyo sehrish ɗin har izuwa gefen gadonsu ta zaunar da ita sannan tace"Ki kwantar da hankalinki,bari na ɗauko maki kayan da zaki sanya,".    Amsa mata tayi da toh,kafin ta mayar da idanunta kan farin towel ɗin dake sanye ajikinta ta ƙura mashi ido tana kallonshi zuciyarta cike fal da fargaba,ita kanta batasan dalilin faruwar hakan ba, Jin an turo ƙopar ɗakinsu yasa tayi saurin ɗagowa don taga wanene,Hajiya azeema ce ta shigo hannunta ruƙe da shopping bag fara fuskar nan ɗauke da murmushi kamar wadda akayi ma albishir da gidan aljanna,murmushi sehrish ta saki da sauri ta miƙe tsaye tana gaisheta"Ina yini Aunty azeema,"   Bata amsa mata gaisuwar ba sae cewa tayi"me nake gani haka?Amarya sanye da towel,ko baki san cewa an ɗaura ba"?   A ruɗe sehrish tace"Aunty azeema,bangane me kike nufi ba,naji kince an ɗaura"?   dariya azeema tayi tare da cewa"su6ul da baka ne fa,Bansan ma na faɗa ba,inaso ince ko an ɗaura abincin lunch ne,ashe azmeen bata a cikin ɗakin nan,"     "Ina yini Aunty azeema,"jahad ce tayi maganar a yayin da take ƙarasowa wurinsu hannunta ruƙe da wasu riga da wando na turkey,da ta ɗaukko ma sehrish,    "Lafiya lou jahad,in ce ko ke zaki sanya waɗannan kayan na hannunki,"   Girgiza kai jahad tayi tare da nuna sehrish tace"A'a bani zan sanya ba,Sehrish na ɗauko masu don ta sanya"    Cike da Zolaya Aunty azeeema tace"kin ta6a ganin inda Amarya ta sanya waɗannan kayan a ranar ɗaurin aurenta"?   Cike da mamaki suka haɗa baki wurin cewa"AMARYA KUMA!!"? da sauri Azeema tace"Kai,mantawa fa nakeyi,wani film na kalla yanzu,to yarinyar cikin film ɗince aka ɗaura ma aure,a yau juma'a batare da saninta ba,abunne ya tsayamun arai shiyasa nake ta sako zancen,"   Murmushi suka saki gaba ɗayansu,Jahad tace"Amma gaskiya na tausaya mata Aunty,meyasa za'ayi mata aure batare da saninta ba?To idan ita bata son Mijin da aka aura mata zata iya kashe kanta fa,'?yanayin yadda jahad tayi maganar fuskarta da alamun tausayi,   Sehrish tace"Nima abunda nakeson cewa kenan,zai iya yiwuwa akwai wanda take so,hakan ba ƙaramin illa zaiyi mata ba,"   Murmushi hajiya azeema tayi tana kallonsu,har sai da suka kai ƙarshen maganar tasu,sannan tace"kun ce wani abu anan,amma idan mijin ya kasance kamar babban yayan ku fa?kuna tunanin akwai macen da zata iya rejecting ɗin aurenshi"?   Kallon juna suka kuma yi,kafin jahad tace"Gaskiya zaiyi wuya Aunty azeema,ae babban yayanmu na daban ne shi ko acikin maza,zan iya cewa ma duk macen da ta mallake shi ba ƙaramar mai sa'a bace,ƴar baiwar ce,kuma ita jinin nasara ce,da ƙafar dama ta shigo duniya,"   Dariya sosai hajiya azeema tayi,jin yadda jahad ke zuzuta SGR,    "Duk da ance abincin wani gubar wani,Zai iya yuwuwa ita yarinyar bata ra'ayin namiji irinsa,ba wai don bai kai ba...."   Katseta hajiya azeema tayi da cewa"kamar ya kenan"?   Sehrish taci gaba da cewa"yanzu kamar ace ita yarinyar,tafi son baƙin namiji dogo,sannan wanda baya tara sumar kai,kuma tafi son namiji mai yawan fara'a a fuskar shi,ko kuma ace ita yarinyar tafi son ta auri wanda bai ruƙe da muƙamin soja,Ya abun zai kasance?zatayi farin ciki idan ta samu kamar babban yayanmu,amma ta wani 6angaren baiyi dai dai da ra'ayinta ba,"   Tana kai ƙarshen maganar,Azeema tace"kamar ke kenan!kina nufin bakison namiji kamar babban yayan ku"? Tayi tambayar cike da fargabar amsar da Sehrish zata bata,   Sunnar dakai ƙasa sehrish tayi tana wasa da yatsun hannunta,yayin da fuskarta ke ɗauke da ƙayataccen murmushi,wannan ya tabbatar mata da cewa Tana RA'AYINSA,   Dariya hajiya azeema tayi tare da ɗago da shopping bag ɗin dake hannunta ta miƙe ma sehrish,   "Wedding gown ce aciki,tare da takalmanta,Zuwa bayan la'asar,da zarar an kammala sallar,Zanzo in taimaka maki wurin sanya rigar,sannan da kaina zanyi maki kwalliya,"   A ruɗe sehrish ke kallonta don bata gane inda zancen nata ya dosa ba,ita kanta jahad abun ya ɗaure mata kai,   Ganin yadda suka saki baki suna kallonta,yasa tayi saurin cewa"Oh,na manta ban sanar daku ba,Wani wasan kwaikwayone zamu yi yau acikin gidan nan don nishadi,that's why we choose you to be our bride in the drama," Wani irin farin cikine ya lullu6e sehrish,cike da zumuɗi ta kar6i bag ɗin,tana fadin"Amma abun zai ƙayatar sosai,dama inason inga na sanya wedding gown,Ashe da rabon yau in sanyata,   Jahad tace"gaskiya abun zai bada citta,yau kam zamu sha hotuna,"    "Har ma video idan kunaso zaku iyayi,Ni bari na wuce kitchen wurin Azmee,".   Tana ƙoƙarin fita,ta tuna da hosana da sauri ta juyo tare da kallonsu tace"Ya jikin hosana?naga sae bacci take tayi tunda nashigo,da alama jikin yayi sauƙi kenan"?   Jahad tace"eh,taji sauƙi sosai,"   "To,ku ya jikin naku"? "Ae mu munji sauƙi,"suka haɗa baki wurin bata amsa,   Jinjina kai tayi tare da kama hanyar fita tana cewa"Allah ya ƙaro sauƙi," Suka amsa mata da cewa"Ameen,"    A saman gado sehrish ta ajiye shopping bag ɗin,sannan ta kar6i kayan da jahad,ta ɗauko mata batare da 6ata lokaci ba ta zura riga da wandon ajikinta Red colour ne ba ƙaramin kyau suka yi mata ba,gaban dressing mirror taje wurin da ta ajiye ribbom ɗinta before ta shiga wanka ɗaukarsa tayi tare da zura shi acikin hannunta,sai da tafara tattara gashin kafin ta sanya ribbom ɗin ta ɗaure shi tamau,   "Ko dai in tashi hosana,tayi wanka itama?kin ga ko sallah batayi ba,"acewar jahad,   Sehrish tace"ko baki tasheta ba,Yunwa zata tayar da ita,kibarta kawai,kada ki tado mana jangwamgwam,"   "Baiwar Allah ni tausayi take bani,duk in na tuna yadda ta samu ciwon haukanta,sai inji idanuna sun cika tab da kwalla,"acewar jahad,   Sehrish tace"Ni kaina ina tausaya mata sosai,Amma inaji araina cewa,Wata rana hosana zata dawo cikin hankalinta ne,sannu a hankali,Haka muke fata in sha Allah,   Suna cikin magana,Jiniyar motocin dake shigowa cikin gidan ta karaɗe kunnuwansu,da ƙarar gaske har cikin dodon kunnuwansu,    "Su babban yaya ne suka dawo daga sallar juma'a,bari in leƙa inga wankan daya ɗauka yau,!"   Cike da farin ciki sehrish tayi maganar tare da juyawa ta nufi window,jahad ma tabi bayanta,janye labulan sukayi sannan ta zuge masu glass ɗin,Baza idanunsu sukayi suna kallon abunda ke wakana a farfajiyar gidan,   Da gudun gaske motocinsu ke shararowa saman titin da zai kawo ka har wurin parking space na gidan,tun daga bakin gate titin ya fara,   "Wlh abun kamar a shirin film" jahad ce tayi maganar,abun ba ƙaramin burgesu yayi ba,    Lokacin da motocin suka ƙaraso ciki,a wani slow suka tsaya a jere,    "Ko wanene zai fara fitowa,bari mu zuba ido muga wankan su babban yaya,"acewar sehrish,   Jahad tace"Ni har na ƙosa,in ga wankan da daddynmu ya dauka yau da kuma wankan Baby junaid,"     Suna cikin magana,wani gabjejen soja mai ƙirar samudawa,ya buɗe motar farko,Abbansu junaid ne ya fito,other side ɗin kuma Uncle Abusufyan ne,fuskokinsu ɗauke da murmushi,yadda kasan Gonar auduga, Bayansu kuma sae motar da ke bin bayan tasu,Abokin Abbansu ne Tafeeda tare da abokin Omar,Adams da kuma shattima,daga motarsu sae motar Marshal Omar,zuba ido su Sehrish su kayi suna kallon Ya Omar dinsu,ganin ya fito daga cikin motar ya kuma zura hannayenshi acikin motar,jimm kaɗan sae gashi ya kinkimo junaid tare da aza shi asaman kafaɗarshi,   Waro ido waje su sehrish sukayi Jahad tace"Mun shiga uku!meya faru da baby junaid ɗinmu?kodai bashi da lafiya ne?kalli fa yadda ya Omar ya ɗaukoshi asaman kafaɗarshi,"    "Yanzu haka rigimarshi ce,nasan junaid sarai,har goyashi zai iya cewa ayi,yadda yake jin kanshi kamar jinjiri,"Sehrish ce tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya,   Jahad tace"wannan fa ba abun dariya bane,tunda kika ga an ɗaukoshi asaman kafaɗa to tabbas akwai abunda ya faru dashi,nidai Allah yasa kafiyarshi ƙalau,   Sehrish na ƙoƙarin buɗe baki tayi magana,ta hango Amstrong ya fito daga cikin motar Sgr,da sauri ya zagaya tare da buɗe mashi motar,zuba ido tayi tana jiran fitowarshi,   A hankali ya zuro ƙafarsa ɗaya waje,almost 5 mins,tukunna ya ƙarasa fitowa daga cikin motar gaba ɗaya,   Gabanta ne taji ya faɗi rass!ba ita kaɗae ba hatta jahad ya tafi da imaninta,a rude sehrish ta shiga yarfa hannu tama rasa abunda zata ce,just speechless,   Jahad ce tayi ƙoƙarin cewa"Tabarakallahu Ahsanul khaliqin!gaskiya babban yayanmu duniya ne!Irin wannan ɗaukar wanka haka!Ni tunda nake a rayuwata ban ta6a ganin mutumin da shadda tayima kyau sosai irin Babban yayanmu sae kuma Ya Omar,Wankan shadda ba ƙaramin kyau yake yi masu ba,ko don suna da ƙirar jiki mai kyau ne,!koda yake shima fa Ya yusouf ba ƙaramin kyau shadda takeyi mashi ba,kinsan shi wani irin sanyin kyau ne dashi na miskilai,hatta su twins da fawan kowa ma yana yin kyau idan suka sanya shadda amma ba kamar yaya Rafayet ba,da ya Omar,junaid kuwa na dabanne shi,"    Jahad sae faman zuzuta su takeyi,duk a tunaninta Sehrish na sauraronta,batasan cewa sehrish ta lula wata duniyar ba,gaba ɗaya Sgr ya tafi da Imaninta,ya janye hankalinta,babban farin cikinta shaddar daya sanya ajikinsa,saboda tana kwaɗayin son tagan shi sanye cikin kayan hausawa,kuma ta gane cewa shaddar nan ce wadda ta ta6a dauko mashi a kwanakin baya,Ya ƙi sanyawa saboda baya sanya kayan hausawa sai nasu na turawa,    Yadda kasan tauraro acikin taurari haka ya bayyana,fuskar nan babu annuri,ya tamketa tamau,kamar wanda aka ɗaura ma aure da Mutuwa,hannunshi na ruƙe da hular da abbansu ya sanya mashi kafin su shiga masallaci,don a ganshi da mutunci,amma ɗan tahalikin nan kamar jira yakeyi a kammala sallar,suna fitowa daga masallacin bayan ɗaurin auren ya tumbuƙe hular,don shi arayuwarshi ya tsani duk wani abu da zai rufe mashi sumar kanshi,ba ƙaramin ji yake da ita ba,zaiyi wuya kaga Sgr da hula akanshi,sai dai Facing cap ko kuma in ya sanya jacket mai hula ajikinta shine zakaga ya sanya hula,hatta shaddar dake ajikinshi atakure yake da ita duk da shi kanshi ya shaida irin kyan da yayi acikinta,ya saba da kayansu marasa nauyi shiyasa yake jinshi duk atakure,Ƴan uwanshi kowa farin ciki yake yi gashi ya hana kowa ya furta kalmar nan Wato ango kasha kamshi,ya tsani yaji an ambaci hakan,ko kuma a kirashi da sunan Ango,kowa so yake ya ɗanyi mashi wasa da dariyar nan da ƴar zolayar nan da akeyi ma angwaye amma rafayet ya hana hakan!yaƙi jinin akirashi da sunan ango, Gaba ɗaya suka tunkari ƙopar da zata sadaka da babban palourn gidan,"    Jiki asanyaye sehrish ta zuge glass ɗin windown,ta gyara labulen,      Zuba mata ido jahad tayi tana kallonta,ganin yadda ta sauya lokaci guda kamar wadda aka zarewa lakar jikinta,   Gefen gadon ta koma ta zauna,sam tagaza samun natsuwa acikin zuciyarta,ganin rafayet da tayi ya fama mata ciwon dake acikin zuciyarta,   "Sehrish wai meya faru ne?Yanzun nan fa muke raha dake,amma lokaci guda kin canza,ko baki lafiya ne"? Ta ƙarasa maganar,tare da samun wuri gefen sehrish ɗin ta zauna,    Muryarta tamkar zata yi kuka tace"bakomai,kawai zuciyata ce har yanzu bana jin daɗinta,"    "Dan Allah ki kwantar da hankalinki rishi,Ki saki jikinki,ko zaki kwanta ne?ki ɗan samu bacci may be Ki samu natsuwa acikin zuciyarki,"cike da kulawa jahad keyi mata maganar, ..Sehrish na ƙoƙarin buɗe baki tayi magana,suka ji an kwankwaso ƙopar ɗakin nasu,   Da sauri Jahad ta miƙe tare da tunkarar ƙopar tana tambayar wanene,   Daga waje taji ance"Daddynku ne" Jin haka yasa jahad yin saurin buɗe mashi ƙopar,    Shigowa ciki Abusufyan yayi fuskarshi ɗauke da ƙayataccen murmushi,zuba mashi ido jahad tayi tana kallonshi baki asake,from head to toe,irin kallon ƙurullar nan,   A ruɗe tace"daddy!kaine!"   Dariya ya ɗan saki tare da cewa"Ni ne mana,me kika gani"   A susuce tace"Wow daddy kayi kyau Over,kamar matashin saurayi ɗan shekara ashirin da biyar,"   Wannan maganar ta jahad,ba ƙaramin dariya ta bashi ba,ta wani 6angaren yaji daɗin yabon da tayi mashi,    Miƙewa Sehrish tayi jin maganar daddynsu nufo wurinsu tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Masha Allah,daddy kayi kyau sosai Allah,kamar irin sabbin ƴan dubu dubu ɗin nan,kasan yadda suke da ɗaukar ido,ga kyau,gasu da burgewa,"   Fashewa da dariya Abusufyan ya kuma yi bakin shi yaƙi rufuwa sai faman hura mashi kai sukeyi,   daƙyar ya samu ya tsagaita da dariyar yace"har kun tuna mun da mommyn ku,duk in naje ɗaukarta daga islamiyya in aka tashe su,Ƙawayenta suyi ta santin wankan da na ɗauka,Har leƙena akeyi ta cikin mota ana nuna ni ga mijin abu nan yazo,Ya iya ɗaukar wanka,ya haɗu sosai,Mommynku ta tsani taji suna yabona,abun haushi yake bata,idan na kuskura na fito daga mota ina jiranta,haka zasu zagaye ni suna kallona,harma suyi mun magana mu gaisa,da zarar abu tazo fuskarta a ɗaure,a fusace take ruƙo hannuna ta tura ni cikin mota,mu tafi,hakan ba ƙaramin dariya yake bani ba Inajin daɗin kishina da takeyi sosai,amma kishin da takeyi mun yajawo rabuwarmu da ita ba don naso ba......"kasa ƙarasa maganar yayi,saboda wani abu da yaji ya taso mashi mara daɗin ji acikin zuciyarshi,tuni idanunshi sun cicciko da kwalla,   tsananin tausayin Abbansu ne ya kamasu duk jikinsu yayi sanyi,daƙyar jahad ta iya buɗe baki tace"daddy,dan Allah kayi haƙuri da duk abunda ya faru tsakaninka da Oumman mu,nasan cewa abun yana yi maka ciwo acikin zuciyarka,Oumman mu bata kyauta maka ba,gashi sanadin hakan ta jefa rayuwarta cikin haɗari da kuma rayuwarmu,sau dayawa takan zauna tayi ta kuka,musamman da daddare ko runtsawa bata iya yi,kullum cikin ambaton sunanka takeyi tana cewa haƙƙin Abusufyan ne yake bibiyar rayuwarta,na cutar dashi sosai,Mijina yana so na amma na butulce mashi,saboda baƙin kishi na,nayi danasanin rabuwa dashi sosai,Ya Allah ka yafemun,mu lokacin duk bamu san abunda take nufi ba...."tuni hawaye sun shiga wanke mata fuskarta,itama sehrish hawayen ne suka soma shararowa daga cikin idanunta,Hannu Abusufyan ya sanya tare da janyo su ya rungumesu sosai ajikinshi,sae lokacin ƙwallar dake cike taf cikin idanunshi ta shiga wanke mashi fuskarshi,muryarshi a kasalance ya soma magana"Oummanku yarinya ce sosai,Ko a lokacin ban ruƙe ta a raina ba,saboda akwai ƙuruciya sosai atattare da ita,Nasha wahala sosai akanta,saboda Allah ya jarabce ni da tsananin sonta,ina sonta sosai,har yanzu soyayyar da nake yi mata na nan yadda take,babu abunda ya canza,Nayi kukan zuciya a lokacin dana rasa ta,kamar in zauce,lokacin dana ji zancen aurenta da sayyadi,Allah kaɗae yasan ƙuncin dana ji acikin zuciyata,bakomai nake tunawa ba,fa ce Amanarta da mahaifinta ya damƙa mun,ya yarda dani sosai baba buzu,yasan cewa banajin magana,ga ƙuruciya dake ɗibana amma a haka ya toshe kunnuwansa Ya aura mun ƴarsa,Naji daɗi sosai,A lokacin kamar kamar me,Allah ya jiƙanshi,   Atare suka amsa mashi da Ameen,ɗagowa dasu yayi daga jikinshi yana ƙoƙarin kai hannu ya share hawayen dake zuba akan fuskarshi,da sauri suka riga shi sanya tafukan hannyensu suna goge mashi hawayenshi,   Murmushi ya saki,don ba ƙaramin daɗin hakan yaji ba,    "Dama nasani wata rana zaku share mun hawaye na,gashi Allah ya nuna mun ranar da raina kuma da lafiyata,"    Yayi maganar tare da sanya hannayenshi duka biyu,asaman fuskokinsu yana share masu hawayensu,bayan ya kammala goge masu hawayen,yace"oh namanta,ban baku tsarabar masallaci ba,"da sauri ya zura hannunshi cikin aljihun wandon jikinshi,   Farar leda ce ya curo mai ɗauke da dabino da goro,   Miƙa masu yayi tare da cewa"hada aya da kwakwa nasiyo maku amma ta hosana ce ita kaɗae zan bamawa,wannan dai gashi ku raba a tsakaninku,"   Kar6ar ladar jahad tayi fuskarta ɗauke da murmushi,sehrish tace"dama na lura kafi ji da hosana,"    Abusufyan yace"eh mana,saboda itace autarku a yanzu,nafi sonta,kuma nafi ji da ita,"   Zumbura baki sehrish tayi tare da cewa"yanzu duk irin cizon da tayi mana a jikinmu baka gani ba?   "Nagani mana,ae gwaggo ta tabbatar mun da cewar ba yin kanta bane,Ya sayyadi ne yazo da suffar kura yayi maku wannan aika aikar....."karasa maganar yayi tare da fashewa da dariya,suma dariyarce ta kufce masu,     Wucewa cikin ɗakin nasu,yayi tare da zama daga gefen gadon yana kallon hosana dake kwance tana bacci,baki a buɗe,    Da sauri ya sanya hannunshi,a cikin aljihun ya curo ledar dake ɗauke da yankakkar kwakwa da ƙullin aya acikinta,     Kwakwar ya ciro,cike da tsokana ya zurata cikin bakin hosana,cikin bacci hosana ta kama kwakwar ta shiga taunarta abakinta,   Dariya sosai sukayi abun ba ƙaramin nishaɗi ya basu ba,    Wuri suka samu suka zauna,suna kallon tsokanar da Daddynsu ke yi ma Hosana,    gaba ɗaya ta cinye kwakwar daya sanya mata abakinta,wata kwakwar ya kuma curowa,tare da zura mata abakinta,kamar wata kura haka ta kama kwakwar tana gartsa,tana taunewa acikin bakinta,   "Daddy,ɗan janye kwakwar mu gani ya zatayi,"acewar jahad,   A hankali ya shiga ƙoƙarin janye kwakwar daga cikin bakinta,ta cije ta da haƙoranta,yana ja tana rurruƙeta,dariya sosai Abusufyan yake yi abun ba ƙaramin nishaɗi yake sanyashi ba,    Da ƙarfi ya janye kwakwar aikuwa a firgice hosana ta farka,fuskarta a yamutse,zuba mashi ido tayi tana kallonshi,muryarta a kasalance ta ambaci sunanshi"daddy!"   "Na'am,hosana,"ya amsa mata,yunƙurawa tayi dakyar ta miƙe daga zaune tana ƙare mashi kallo kafin ta kwantar da kanta asaman kafaɗarshi,tana faman lumshe ido saboda baccin da tasha,    "Kin tashi lafiya?ko baccin bai isheki bane?   A shagwa6e tace"Ya isheni,yunwa ma nake ji,Cikina babu komai,gashi ko wanka banyi ba,Su jahad duk sunyi wanka basu tashe ni ba,balle inyi nima,"ta ƙarasa maganar tana kallonsu sehrish dake a bakin gadon,murguɗa masu baki tayi tare da harararsu,    "Shikenan,bari in na fita yanzu zanyi ma azmee magana,sae ta shirya maki lunch ko"? ..ɗaga mashi kai tayi alamar eh,   Miƙa mata ledar kwakwar yayi"kar6i nan,tsarabarki ce,ta masallaci kada ki ɗanma kowa kinji ko"?   Fuskarta ɗauke da murmushi ta kar6i ledar daga hannunshi      "Nagode sosai daddyna,kuma bazan ɗan masu ba,"    Wurga mata harara jahad tayi tare da cewa"Sannu ko?daddynmu zakice ba daddyna ba,ae bake kaɗae bace a wurinshi ba,"   Gatsina mata hanci hosana tayi tare da ƙara rungumo Abusufyan ajikinta don suji haushi,hakan ba ƙaramin dariya ya bashi ba,    "Daddy,ƙamshin turaren jikinka akwai daɗi sosai Allah,"tayi maganar tare da sanya hancinta ajikin rigar shaddar jikinshi tana shaƙar ƙamshin turaren kamar wata mayya,    "Idan kinaso ma,zan ɗauko maki kwalbar turaren gaba ɗaya,sae ki dinga shafawa kema hakan yayi maki"?    Girgiza kai tayi"a'a daddy,kabarshi kawai,Ya Omar ya hanani shafa turare,idan na shafa wannan turaren zaiyi ƙamshi sosai,kuma idan Yaji bazaiji daɗi ba,zaice hosana bakijin maganata ko?to daga yau babu ni babu ke,ni bazan zauna da mai kunnan 6era ba,'   Fashewa da dariya su jahad sukayi,tuni hosana ta ɗaure fuskarta tana harararsu,Abusufyan yace"yayi kyau babyn Omar,yana da kyau ki dinga jin maganarshi,kina yi mashi biyayya,kada ranshi ya 6aci,"    Cike da jin kunya hosana ta janye jikinta daga na Daddynsu,ta janyo pillow ta rufe fuskarta dashi,    Wayar Abusufyan ce ta shiga yin ringing,har lokacin fuskarshi ɗauke da murmushi,yace"Bari na shiga ciki,zansa azmee ta shirya maku launch,"   "To daddy,"suka amsa mashi da sauri ya fuce,    *JUNAID ROMEO* Tashin hankalin da ba'a sama shi date,Tun wurin ɗaurin aure da junaid yaji sanarwar ɗaurin auren Babban yayansu,tare da Rishi ɗinsa,acikin masallacin ya yanke jiki ya faɗi a sume,saboda baisan da zancen ɗaurin auren ba,kwatsam yaji ana sanarwar, A bedroom ɗinsa Omar ya kwantar dashi,bayan sun yayyafa mashi ruwa ya farfaɗo,koda ya buɗe idanunshi yaga Abbansu ga kuma yayyansu Isha da Abbas,ga Marshal Omar da sauran matasan duk suna tsaye akanshi,Fashewa yayi da matsanancin kuka mai cin rai,Cikin shesshekar kuka yace"Wayyo Allah na!Wlh an cuce ni,Abba kana sane da cewar ni ke son sehrish amma ka aura ma babban yayan mu ita,wlh bazan yarda ba,Ae ni na fara sonta,don me za'a aura mashi ita!ashe baku sona,hakanan kuke nuna mun soyayya,Wlh nidai bazan yarda ba,abba ka cuce ni sau nawa ina faɗa maka cewar inasonta,Ita nake da burin in aura amma....." bai ƙarasa maganar ba,Omar ya daka mashi tsawa wadda ta gigitar dashi,    "Rufe ma mutane baki junaid!shashasha kawai!Abban ne kaka cewa ya cuce ka?kai ko kunyar yin zancen aure agaban mu baka ji?ubanwa zaiyi maka aure da ƙananun shekarunka?kai da ita waye zai raini wani in anyi maku auren"?   Tafin hannayensa ya sanya tare da rufe fuskarshi,yana cigaba da kukan kuma hakan baisa ya daina sambatun da yake yi ba,    "Ya omar ba zaka gane bane,Abun da ciwo,wlh ina sonta sosai,ina son rishi,kuma itama tana sona,wlh ba babban yayanmu take so ba,Ni take so,don me za'a aura mata shi..."   A zafafe Omar ya zabura zai kai mashi mari a kan fuskarshi,da sauri Abba ya ruƙo hannunshi tare da cewa"Kuyi mashi uziri,wlh nasan yana sonta sosai,banta6a tunanin cewa junaid ya san so ba,ni duk a tunani na wasa yake yi mun,ashe dagaske yakeyi,dole yaji ciwo acikin zuciyarshi saboda ya saba da ita sosai," muryarshi a sanyaye yayi maganar,Abun ya ta6a mashi zuciyarshi,tsananin tausayin junaid ne ya kamashi,    Shi kanshi marshal Omar jikinshi ba ƙaramin sanyi yayi ba,kowa yasan da irin shakuwar dake atsakaninshi da sehrish amma ba suyi tsammanin cewar dagaske sonta yakeyi ba,   Hatta su ishaq dake tsaitsaiye cirko cirko agaban gadon nashi ba ƙaramin tausayi ya basu ba,duk yabi ya burkice,fuskar nan tayi jawur da ita,jijiyoyin jikinshi duk sun bayyana,    Adai dai lokacin da Abusufyan ya ƙaraso kopar ɗakin junaid ɗin,kasa shiga ciki yayi saboda jin maganganun da sukeyi aciki,hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,jin cewar junaid sehrish yake so,kuma adalilinta ne ya suma a masallaci,    Duk yadda suka so su shawo kan junaid da lallashi don yayi shiru abun ya faskara,hancinsa har ya fara bleeding,hankalinsu yayi mugun tashi,     Matsawa sukayi kusa dashi suna lallashinsa,Ja da baya ya dinga yi asaman gadon har ya ƙure ma head board ɗin gadon,sautin muryarshi ashake saboda tsabar kukan daya sha,   "Ku rabu dani,bana son ganin kowa!ba kunfi so na mutu ba!to zan mutu ne yanzun nan sae hankalinku ya kwanta,"   Hawaye ne suka cicciko tab a idanuwan kowannansu,   "Junaid dan Allah kayi haƙuri,Allah ya riga daya ƙaddara faruwan hakan,dama can ita ba matarka bace," Acewar Abbas,   Girgiza kai ya shiga yi yana cewa"yaya abbas,bazaku gane bane,bakusan yadda nake ji acikin zuciyata bane,tafarfasa take yi mun,wlh bazan iya jurewa ba,inason rishi sosai,idan har kuna so kuga farin ciki na,to akwance ɗaurin aurenta da babban yayanmu a aura mun ita shine kawai,in ba haka ba mutuwa zanyi,Wayyo Allah rishi ɗina,"yana magana yana shessheƙar kuka,     Abbas yace"Calm down ur mind junaid,akwai mata da yawa agari suna yawo kyawawan gaske,ga ƙanwar matata nan Amal,baka ganta ba ƴar ƙarama dai dai kai,idan kayi hakuri zaka samu wadda tafi ta ma,"   Bubbuga kafafunshi yayi asaman gadon tare da cewa"Ya Abbas wlh banson kowace mace in ba ita ba,Sehrish itace juliet ɗina ita kawai nakeso,kodai aban rishi ko kuma in haɗiyi zuciya in mutu,"to fa,!junaid ya tashi hankalin kowa,yaƙi saurarar kowa,yau an ta6a romeo shugaban ƴan soyayya,    Cikin lallashi Abbansu ya ambaci sunanshi"Babyn Abbanshi,"   Wani irin kallo ya wurga ma abban nasu idanuwan nan sunyi luhu luhu saboda tsabar kukan daya sha,    "Ni ba babynka bane,Romeo ɗin mommynsa ne,saboda baka sona Abba,"ya karasa maganar yana faman matse kwallar dake sharara daga cikin idanuwanshi,   Shiru Abbansu yayi bai ƙarasa maganar tashi ba,junaid yafi jin haushinshi akan kowa,saboda yasan da cewar yana sonta amma ya ɗaura mata aure,duk da shi bai ɗauki maganar tashi serious ba,sae yau daya haukace masu,    Turo ƙopar Abusufyan yayi jikinshi duk ya mutu,tsabar tausayin junaid ne ya kamashi,   Juyowa suka yi suna kallonshi,matsa mashi hanya sukayi ya wuce,har izuwa gaban gadon junaid din,    Zuba mashi ido yayi yana kallonshi,duk ya fita cikin hayyacinshi ya zama abun ban tausayi,wannan ya tabbatar mashi da cewar ba ƙaramin son sehrish yake yi ba,   ɗagowa junaid yayi tare da kallon Uncle ɗin nasu,Cikin shessheƙar kuka yace"Un..cle!hada kai aka ɗaura ma rishi ɗina aure da babban yayan mu,bayan kunsan cewa ina sonta sosai,"    Hawa saman gadon abusufyan yayi tare da janyo junaid ya rungumoshi ajikinshi yana ɗan bubbuga bayanshi da hannunshi,cikin lallashi yace"Junaid,Ni bansan cewa kana sonta ba,da banyi kuskuren aura ma rafayet ita ba,kasan cewa inason ka sosai,kowa ma yana sonka,kuma zamu iya yin komai saboda farin cikinka,hatta rayukan mu ma zamu iya badawa domin ceto rayuwarka,balle kuma ƴar uwarka?sae ita zata gagara?"   "Amma..uncle..meyasa ku ka ɗaura mata aure da babban yayan mu?maimakon ni"?daƙyar yake magana,    "Kayi haƙuri junaid,dama Allah ya ƙaddara cewar ita ba matarka bace,Matar babban yayanku ce,"    ɗagowa yayi daga jikin Abusufyan din fuskarshi jaga jaga da hawaye hada majina,yana kallon uncle ɗin yace"yanzu kuna nufin cewa,babu ni babu rishi?in haƙura da ita kawai?kun za6i ku rasa ni kenan"?   ruƙo hannunshi abusufyan yayi tare da sassauta muryarshi yace"haba junaid,in sha Allah ba zamu rasa ka ba saboda sehrish,ae ba ita kaɗai bace ba,Ko ka manta cewar su ƴan ukune?kuma kamanninsu ɗaya,Idan kayi haƙuri zan baka auren ɗaya daga cikinsu,"   Da sauri Marshal Omar ya katse mashi hanzarinshi da cewar"Wacce acikinsu,"?   dariya abbansu yayi ganin yadda omar ya ɗan tashi hankalinshi,   Abbas yace"Uncle,kada fa kayi mashi alƙawarin auren ɗaya daga cikinsu,saboda junaid bai da wayau baisan wasa ba,kuma koda za'ayi mashi aure ba yanzu ba,sae yayi hankali nan da in ya kai shekara talatin,"yana kai ƙarshen maganarshi,Ishaq ya ɗaura da cewar"Bazai yiwu ba ayi ma junaid aure a yanzu,bayan ga yayyensa nan duk sun manyanta kowa na bukatar aure,yayi haƙuri dai akwai matar abokina na nan,yanzu haka tana dauke da ciki,idan ta haifi jinjirin muka ga mace ce,sae ayi masu magana,su ajiye mashi ita,in ta girma lokacin yayi hankali sai a aura mashi ita,"   Suna cikin maganar nan,Junaid ya sume,a jikin Abusufyan,a ruɗe abusufyan ya shiga jijjiga shi yana kiran sunanshi"Junaid!Junaid!!"   Hankalin Abbansu atashe yace"Duk laifinku ne!meyasa bazakuyi shiru da bakinku ba,gashi nan ya ƙara sumewa,kuma ina da tabbacin cewar maganganun da kuke gaya masa ne suka ƙona mashi rai,"   Hannu Omar yasa tare da ɗauko bottle water ɗin dake ajiye saman side drawer dinsa,ya cire murfin tare da mika ma abusufyan,A hannu ya tar6o ruwan sannan ya watsa mashi a fuskarshi,   Dogon numfashi yaja tare da sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya,   Shafa fuskarshi Abusufyan yayi tare da cewa"Junaid,"    Tunkafin ya buɗe idanunshi yace"Uncle mutuwa zanyi,"   "Junaid dan Allah kadaina kira mana mutuwa,Indai kan sehrish ne,NI NAYI MAKA ALƘAWARIN CEWA ZAN AURA MAKA ƊAYA DAGA CIKINSU IN HAR TANA SONKA,"   Muryarshi a kasalance yace"Uncle nasan wasa kake yi mun,kada kayi mun alƙwarin da bazaka iya cika mun ba,Zan haƙura kawai in rungumi ƙaddarata,"_    Wannan maganar da junaid yayi ba ƙaramin kashe masu jiki tayi ba, Tuni hawaye suka cicciko a idanuwan Abusufyan,muryarshi na kerma yace"meyasa kace haka junaid"?   "Uncle,bani da wayau,ni yaro ne har yanzu,kowa yana yi mun kallon sakarai,kuma bani da aikin yi,a haka zaka bani auren ƴarka""?    A hankali wasu siraran hawaye suka shiga gangarowa a saman fuskar Abusufyan,daƙyar ya iya buɗe baki yace"Junaid!duk rashin wayonka baka kaini ba lokacin da ina yaro,bana jin magana har sa'insa nake yi da Mahaifiyata,na iya rashin kunya saboda ni bana jin kunyar kowa,ni ina mu'amala da mata muje party,muje night club,Ka faɗamun ɗaya daga cikinsu wanne kake yi?   "Ko ɗaya bana yi"ya bashi amsa, Murmushi abusufyan yayi kafin ya cigaba da cewa"kana da kyakkyawar zuciya junaid kai mutumin kirki ne,kana son kaga farin ciki a fuskar kowannan mu,saboda me Ni zan gaza sanya ka farin ciki?Duk da banajin magana amma ahaka Mahaifin Oummansu Sehrish ya bani auren ƴarsa,Nima don haka daga yau ka sanya aranka cewar na baka Auren JAHAD!idan ma akwai mai sonta cikin yayyenka sai dai yayi haƙuri yabar maka,    Wani irin Farin Ciki ne ya lullu6e junaid,lokaci guda ya nemi kukan da yake yi ya rasa,bashi kaɗae ba hatta sauran ƴan uwan nasa dake tsaye a wurin ba ƙaramin daɗi suka ji ba,Musamman Abbansu,Yaji daɗi har cikin ranshi,    Cike da zolaya abusufyan ya kallesu tare da cewa"Ko akwai mai ja acikin ku ne"?    Fashewa sukayi da dariya gaba ɗayansu,tare da haɗa baki aurin cewa"Mu mun isa?Uba ya mallaka ma ɗansa auren ƴarsa?waya isa yaja daku?ae magana ta ƙare"    Sae lokacin junaid ya fashe da dariya har fararen haƙoransa suka bayyana masu ɗauke da matsakaiciyar wushirya siririya,mai kyan gaske,   "Surukina,fadamun me kakeso yanzu"?   Cikin shagwa6a junaid yace"Maganin ciwon kai,sannan ina jin yunwa sosai,"    "Bari inyi ma jahad magana takawo maka,hakan yayi maka"?   Cike da jin kunya junaid ya rufe fuskarshi da tafukan hannayenshi,yana dariya ƙasa ƙasa,    Zolayarshi suka shiga yi,har sai da suka sanya shi farin ciki sosai,sannan suka bar cikin bedroom ɗin nashi,ya kasance shi kaɗae ne acikin ɗakin kwance asaman gadon,kamar wani zautacce sae faman sakin murmushi yake yi,bakinshi yaƙi rufuwa,    Turo ƙopar ɗakin nashi,akayi da sauri yakai idanunshi wurin,Azmee ce ta shigo hannunta ruke da tray,lunch ne ta shirya mashi,ƙarasawa tayi tare da ajiye mashi tray ɗin saman front table din gadonshi,   Mikewa yayi daga zaune,yana gaisar da ita,    "Ina yini Aunty azmee,ya aiki,"   Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Lafiya lou junaid Alhamdulillah," Ta karasa maganar tare da ɗaukar plate ta buɗe warmer mai dauke da chicken pepper soup serving spoon ta sanya tana ɗaukar cinyar kazar tana sanya mashi a plate,kallonta yakeyi sae ya dinga ganin kamar jahad ce,saboda tsabar son ya ganta musamman da yaji an mallaka mashi ita, "Idan ka kammala ci,ga magani nan Uncle ɗinku ne yace na baka kasha,"tayi maganar tana nuna mashi maganin dake ajiye asaman tray ɗin, "Nagode sosai Aunty azmee," "Na lura kamar kana cikin farin ciki sosai yau,"_ Murmushi ya saki tare da cewa"Aunty azmee,Am so,so happy today,Uncle abusufyan ya bani auren Jahad,Ya mallaka mun ita," Waro ido waje Azmee tayi cike da mamaki tace"Wai dagaske"? ɗaga mata kai yayi alamar eh,Hannayenta ta daga sama cike da tsantsar farin ciki tace"Alhamdulillah!Allah na gode maka!ashe dae ina da rabon ganin aurenka junaid,Allah ya nuna mana lokacin," "Ameen ameen,"ya amsa mata, "Dan Allah kaci abincin nan sosai,kaci ka koshi angon jahad," Rufe fuskarshi yayi yana dariya ƙasa ƙasa, itama dariyar ce ɗauke akan fuskarta har ta kammala zuba mashi abincin,sannan ta kama hanyar fita daga ɗakin,sae da junaid yaji alamun ta bar bedroom ɗin nashi sannan ya buɗe fuskarshi yana faman sakin murmushi   *Haroon* Motarshi na qoqarin shiga cikin hotel yaji an ambaci sunanshi"Ya Haroon,"gabansa ne ya faɗi rass jin Muryar mutum mai mahimmanci a wurinshi,da sauri yaci burki tare da zuge glass ɗin motar a slow,    Tsaye take jikinta na asanye da Uniform,yadda kasan mahaukaciya,gashin kanta duk ya tarwatse ya hargitse,babu gyara,ƙafafunta babu takalma,tayi buɗu buɗu da ita,waro ido waje haroon yayi yana kallonta,tamkar a mafarki,kusan minti 5 kafin ya buɗe motar,ya fito har lokacin kayan jiya ne ajikinshi,a hankali yake tunkararta yana ƙare mata kallo,ita kuwa da gudun gaske ta tunkareshi,faɗawa tayi saman ƙirjinshi tare da zagayo da hanneyenta ta bayanshi,ta ƙanƙame shi sosai,lokaci guda ta fashe da matsanancin kuka,   Lumshe idanunshi yayi tare da sanya hannunshi abayanta,yana ɗan bubbuga bayan nata,a hankali ya ambaci sunanta"AMRISH"    Boss tabarku da tunani,Bashin friday ne na biyaku,kowa yasan cewa weekend banayin posting,Don haka mu haɗu On monday,in Allah yakaimu da rai da lafiya,don jin Yadda zata kaya👍     *SALON NA DABANNE🔥* *kada fa ku manta har yanzu muna acikin Littafin Abban Sojoji ne Takun ƙarshe wanda Ni hafsat Bature Na rubuta* 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina pls banda kiran waya,bana amsa shi,Just message za'ayi mun ta whatsapp in sha Allah zan amsa,don bana shariya indai ina online 08103884440❤Masu kirana ƙarfe goma na dare kuna son jamun wlh😡_ Cikin shessheƙar kuka ta amsa mashi"na..am yaya haroon" raba ta yayi daga jikinshi tare da sanya hannayenshi ya tallabo fuskarta,daƙyar take iya buɗe idanunta waɗanda ke jike sharkaf da hawaye,zuba mata ido yayi yana kalllonta,fuskarta duk ta kumbura tayi haske,gashi ta ɗan yi rama wannan ya tabbatar mashi da cewar tana cikin matsananciyar damuwa,yana ƙoƙarin buɗe baki yayi mata magana idonshi ya sauka akan hannunta,kanula ya gani,a ruɗe yace"Amrish!Wannan fa?faɗa mun meya faru?Kinyi rashin lafiya ne"?    daƙyar ta iya buɗe baki tace"Poison nasha,Saboda na gaji da zaman duniyar nan,Mommy ta 6atamun rai,ba ta sona ba ta damu dani ba......".   Bata ƙarasa maganar ba,yaja hannunta izuwa wurin motarshi,buɗe mata motar yayi ta shiga back seat ta zauna sannan shima ya shiga mazaunin driver,shiga cikin Hotel ɗin ya ƙarasa shiga da ita,bayan yayi parking ɗin Motar ya fito ya buɗe wurin da amrish take ya shiga daga ciki,    Cikin sanyin Murya yace"faɗamun abunda ya faru tsakanin ki da ita"?   Nan ta labarta mashi abunda ya faru tsakaninta da mommynta tun daga farko har ƙarshe,      "Amrish!ashe baki da hankali?saboda kawai ta gaya maki wannan ƴar maganar sai ki nemi kashe kan ki?suwa kika yi ma asara?   Shiru tayi yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,     "So kike narasa ki ko"?da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a,    "Bazan ƙara ba,yaya haroon mommy ce ta 6ata mun rai,kuma ni bansan zama wurinta,Na tsaneta bata kwanta mun araina ba,dan Allah kada ka mayar dani wurinta,ka kaini gidanku kawai in zauna tare daku,"   Waro idonshi ya ɗan yi kafin yace"gidan mu!in kaiki a matsayin wa?so kike kija mun?yayyena fa gaba ɗayansu maza ne kuma sojoji ne,bazaiyiwu ba ki zauna acan,"   Fuskarta tamkar zata yi kuka tace"Ya kake so nayi da rayuwata ne?ni babu wurin da nake jin daɗin zama,Ka kaini kawai gidan ku in zauna,idan ina ganinka sai hankalina yafi kwanciya,amma ni bazan koma wurin mommy ba,in ba so kake ka rasa ni ba gaba ɗaya,"tayi maganar aɗan shagwa6e,    Shiru ya ɗan yi yana tunanin mafita,don kuwa ya santa da baƙar zuciyar nan ta gado,in har yaƙi yi mata abunda take so to tabbas zata aikata abunda ta faɗa ne,    Ajiyar zuciya ya sauke tare da kallonta yace"It's Okey,zan kai ki gidan mu amma kafin nan,Ki fara zama a wurina,Ni abunda ya ɗaure mun kai,taya ya har kika gano inda nake?"   Sae lokacin ta ɗan saki murmushi akan fuskarta,kafin tace"Ae nasan duk wani wuri da kake zuwa,kaine baka sani ba....".     "Wato bibiyata kikeyi ko"? Dariya tayi,tana ɗaga mashi gira,     "Zanyi maganinki,mai ɗan kumatu,"   Sosai ya shiga zolayarta,har sai da yaga farin ciki akan fuskarta,atare suka fito daga cikin Motar hannunshi acikin nata,wucewa yayi da ita VIP,inda room ɗinsa daya kama a hotel ɗin yake,bayan sun shiga ciki wanka ya sanyata tayi sannan ya daukko mata kayan da zata sanya ajikinta,dama ɗakin nasa na sharholiyarsa ne,akwai duk wani abu da mace zata buƙata,tunda nan yake kawo ƴan matansa da samarinsa duka dae,bayan ta kammala shirya kanta,order ya bada na abincin da zataci,   Bayan an kawo mata abincin,taci ta ƙoshi,sannan yace ta kwanta ta huta,Cikin ƙankanin lokaci bacci ya ɗauke ta asaman gadonshi,   Safa da marwa ya shiga yi acikin ɗakin tunanin shi,taya za'ae yakai amrish gidansu!?Yasan cewa ba wani abun tashin hankali bane,kuma in ya kaita zasu kar6eta hannu bibbiyu,amma bazai bari su ganshi ba da sunan wanda ya kawota,in ba haka ba zai zama abun zargi a wurin ƴan uwansu,   Sae faman zirga zirga yakeyi acikin ɗakin,lokaci zuwa lokaci yakan ɗan juya ya kalli amrish dake kwance saman gadon nashi,hankalinta kwance sae sharar bacci take yi,bai ta6a ganin yarinyar da ta yarda dashi ba kamar amrish,kwata kwata ba ta jin tsoranshi don ta rungumeshi,ba wani abu bane a wurinta,duk da shi ya koya mata hakan,har kwana saman gado ɗaya suna yi da ita,amma wani abu bai ta6a shiga tsakaninsu ba,sae dai ƙawayenta su Zeenatu,babu wadda bai yi lalata da ita ba acikinsu,kuma har yanzu yana tare da kowaccensu,duk in ya buƙace su zasu kawo mashi kansu ne, ❤🤍❤ After La'asar, Tsaye take agaban dressing mirror tana ƙare ma kanta kallo yadda kasan wadda za ta je gasar Kyawun duniya,Wedding gown ce a jikinta  fara ƙal,tabi shape ɗin jikinta,hips ɗinta ya fito sosai kamar zai fasa rigar haka daga saman rigar net ne,sosai fatar ƙirjinta ta fito mai matuƙar jan hankali,Daga bayan Rigar lace tattoo ne wanda ya ƙara fito da kyawun rigar,fuskarta na ɗauke da light makeup,ta shafa jan baki red colour,Hannunta na sanye da haɗaɗɗiyar wrist watch ta diamond da Aunty azeeema ta saka mata,mai haɗe da ring da kuma chain ƴar ziririya fara,ga earrings ɗinta,wani irin daddaɗan kamshi ne ke fitowa daga jikinta Kamar wadda aka tsamo daga cikin ƙogin turare,gaba ɗaya bedroom ɗin nasu Ƙamshin turarenta ne ya karaɗe ko'ina,ƙafarta na sanye da stilleto,matsiyacin high heels ne mai shegen tsini,shima launin rigar jikinta ne,ƙafafunta sun fito ɗass acikinsa,    "Wow masha Allah,Tabarakallahu Ahsanul khaliƙin!"hajiya azeema ce ta ambaci hakan,jahad kuwa hannunta na ɗauke da Wayar sehrish ta shiga Camera sae video take yi mata,ita ma hosana hannunta na ruqe da wayar hajiya azeema I phone 13,Sun taru sai video suke ɗaukar sehrish, Ƙoƙarin juyowa tayi da sauri hajiya azeema ta dakatar da ita"Kada ki juyo yanzu,bari na aza maki net ɗin nan asaman kanki zai ƙara maki kyau sosai,Bayan ta kammala sanya mata mayafin sannan tace"Sannu a hankali zaki juyo ba da sauri ba," a natse Sehrish ta soma juyowa a wani slow,Hosana na kallonta ta cikin camera sai faman sakin Murmushi take yi,   Hajiya azeema tace"Yawwa My photographers ku ɗaukarmun ita da kyau,ta fito sosai acikin Video ɗin,yadda zanji daɗin ɗaurawa a status ɗina,   Ƙarasa juyowa sehrish tayi,fuskar nan ɗauke da ƙayataccen Murmushi,ita kanta tasan tayi kyau over,Zuciyarta cike fal da farin ciki,kamar wadda akayima albishir da gidan Aljanna,dama hannunta akwai zanen jan lallen da akayi masu na walima,yana nan raɗau a hannunta bai goge ba,ta ruƙe yar purse ɗinta a hannunta,   Tun daga ƙasa Hosana ta fara ɗaukarta ta cikin camera ɗin har izuwa saman fuskarta,    "Turn ur back,yadda zasu ji daɗin ɗaukarki da kyau,"acewar Azeema,   Juyawa sehrish tayi a hankali suka ɗauki bayan,sannan ta sake juyowa,Jahad sae faman zuzuta ta take yi tana cewa"wlh yadda kasan Amaryar Gaske,Sehrish kinyi kyau sosai kamar dollars"   Dariya hajiya azeema tayi jin abunda jahad tace,   tace"Wato kuɗi sune suka fi komai kyau kenan?shiyasa ake kwantanta su da mutumin da yayi kyau ko"?tayi maganar tana kallon Jahad dariya sukayi gaba ɗayansu,   Suna cikin rahar nan wayar hajiya azeema tayi ringing,sunan Abba ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,da sauri hosana ta miƙa mata wayar,hannu tasa ta kar6i wayar bayan ta ɗaga kiran ta kara wayar a kunnanta,    Tun kafin tayi sallama taji muryar abba yace"Azeema kina ina ne"?    "Ina a ɗakinsu sehrish ne yanzu haka,na kammala yi mata kwalliya ne harma ta sanya rigar amaren...."   Katse ta yayi da cewa"Karki kuskura,kice zaki kai yarinyar nan ɗakin Rafayet!".     Hankalinta atashe tace"Saboda me Yaya hossein"?tun daga kan muryar Abba ta tabbatar da cewar yana cikin matsananciyar damuwa,    "Tun farko sai da na faɗa maki cewar wannan auren na sirri ne,kuma na faɗa maki dalilin dayasa ya aureta ba don yana sonta ba fa ce don tayi mashi aiki,.." a ɗan ruɗe hajiya azeema ta dago tana kallon Sehrish,jikinta ne yayi wani irin sanyi har cikin zuciyarta taji babu daɗi,   Da sauri tace masu"Ina zuwa" tana faɗin hakan ta fuce daga ɗakin,a nan cikin corridor din ta tsaya,Muryarta asanyaye tace"Yanzu yaya kana nufin cewa yarinyar nan bazata tare aɗakin Mijinta ba!"    "Azeema so nake ki fahimce ni,!ki natsu ki saurare ni,!rafayet wani irin bauɗaɗɗan mutunne mai wuyar sha'ani,Wlh bazai bari yarinyar nan ta zauna a part ɗinsa ba,da sunan amaryarshi,Yanzu haka zancen da nake yi maki,Ya hana uban kowa ya ɗauki hoto tare dashi!gaba ɗaya babu wanda ranshi bai 6aci ba saboda rafayet!"    Muryar hajiya azeema tamkar zatayi kuka tace"Amma ba'ayi ma yarinyar nan adalci ba!Meyasa tun farko ba'a shawarce ta ba?kafin a ɗaura mata aure dashi!yakamata ace tasan da zancen auren da za'ayi mata da kuma dalilin yin auren!me kuke tunanin zai faru idan har yarinyar nan taji cewar an aurar da ita ne don tayi aiki kawai a ƙarkashinsa"?   Shiru Abba yayi batare daya ce mata komai ba,   Jinjina kai kawai hajiya azeema tayi tare da cewa "Shikenan kawai,Zansa ta cire rigar dana sanya mata,Amma dae banji daɗi ba,Kuma in sha Allah rafayet sai yayi danasanin yin hakan da yayi!"tana kai ƙarshen maganarta,tayi rejecting kiran,Tuni idanunta sun cicciko da kwalla,Ranta yayi mugun 6aci,     "Aunty azeema!"hosana ce ta ambaci sunanta,da sauri takai idanunta ƙopar ɗakin nasu,tsaye take fuskar nan ɗauke da murmushi tace"Munata jiranki,Kince zamu je kai amarya,"    "Kada ki damu hosana,Yanzu zan shigo ciki,"   Amsa mata tayi da toh,sannan ta koma cikin ɗakin,Kusan 15 mins hajiya azeema tana tsaye batare da ta motsa ba,sae da zuciyarta ta lafa,sannan ta wuce cikin ɗakin nasu,     A tsaitsaye ta samesu suna jiran dawowarta,gaba ɗaya duk sai taji ba daɗi,Musamman yadda taga Sehrish sae faman sakin Murmushi takeyi,tsananin tausayinta ne ya kamata,Shin wata irin rayuwa yarinyar zatayi a ƙarƙashin Sgr?mutumin da baisan Soyayya ba,Tabbas zata sha wahala a hannunshi,Domin kuwa zai mayar da ita tamkar baiwarshi ne,su yaya hossein sunyi kuskuren aura mashi ita,da sunan tayi mashi aiki,wannan tamkar ƙasƙanci ne,kuma yarinyar bazata ji daɗi ba,ranta zai 6aci sosai idan ta gano cewar aure akayi mata,auren ma na sirri,tamkar wata mara gata,babu walima babu wani party,babu taron mutane,babu wedding pics,dole abun ya ta6a Zuciyarta,na biyu da sa hannun iyayenta suka aura mata shi da sunan tayi aiki a ƙarƙashinsa ba matsayin matarshi ba,tabbas an gama cutar da ita,     Mamaki abun ya ba su Jahad ganin hajiya azeema tayi tsaye agabansu,kuma ta ƙurawa sehrish ido tana kallonta,Kamar mai nazarin wani abu,    Jahad ce ta ambaci sunanta"Aunty azeema,"   Firgita tayi lokaci guda ta ɗan saki murmushin yaƙe tare da cewa"Am sorry fa,wlh na shafa'a ne,Yanzu mai ya rage mana muyi"?    Hosana tace"Kai amarya mana,ki faɗa mana a ina zamu kai rishi ɗin,"    Hajiya azeema tace"Ae wannan shirin drama ne!ba dagaske ba,A nan zakuyi wasan ga wayata ma idan kuna buƙatar yin hotuna,Ni yanzu inaso zan wuce ciki ne,"   Da sauri Hosana ta kar6i wayar daga hannun hajiya azeeman,sallama tayi masu da sauri ta fuce daga cikin ɗakin,   "Kamar yanayinta ya canza ko"?jahad ce tayi maganar tana kallon sehrish,    "Nima na lura da hakan,Hosana wanene ya kira ta a waya nasan kinga sunan daya bayyana akan screen ɗin,Zai iya yiwuwa wani abu aka sanar da ita wanda ya 6ata mata rai,"acewar sehrish,    Hosana tace"Ni dai naga Sunan Yaya hossein,amma bansan wanene ba,"   "Sunan Abbansu Junaid ne,Allah yasa dae ba wani abu ya faru ba,"sehrish tayi maganar fuskarta ɗauke da damuwa,   "Kodai naje najiyo mana abunda ke faruwa cikin gidan"?Hosanar tayi tambayar tana kallonsu,   Jahad tace"A'a,babu ruwanki,tunda ba kiran mu akayi ba," Cigaba da ɗaukar hotuna sukayi acikin ɗakin,Shigowa junaid yayi fuskar nan tashi ɗauke da murmushi,Suna ganinshi suka haɗa baki wurin cewa"Baby Junaid!"   Ɗaure fuskarshi yayi tare da ɗan turo bakinshi ashagwa6e yace"Ni ku daina Kirana da sunan baby,In ba haka ba,ran kowa zai 6aci a wurin nan,"ya ƙarasa maganar tare da aza idanunshi kan Sehrish dake tsaye tasha Kwalliya abunta,sakin baki yayi galala yana kallonta,a ruɗe ya ambaci sunanta"Reesh,"   Murmushi Sehrish ta sakar mashi,tare da yi mashi fari da ido,sannan tace"Na'am,Junaid ya kaga wankan nawa,"?    daƙyar ya iya cewa"reesh,yanzu kina sane aka ɗaura maki aure da babban yayan mu bayan kinsan da cewar Ina sonki"?   Gabanta ne ya faɗi rassss!!Ba ita ba hatta su Jahad da hosana a ruɗe suka haɗa baki wurin cewa"Aure kuma,da Babban yayan mu!"   Shi kanshi junaid ɗin sae da gabanshi ya faɗi,tunani ya shiga yi anya Sehrish tasan da auren kuwa?Yanayin yadda ya ga ta razana ya tabbatar mashi da cewar batasan da zancen auren ba!acikin ranshi yace"meke faruwa ne?Mommy batasan da auren babban yaya ba,kuma itama rishi dasu jahad basu san da auren ba!Abba ya 6oye masu kenan!aikuwa saina tona masu asiri kowa yaji,dama ya 6ata mun raina yau,duk irin amanar dake tsakanina da Abba ya rasa dame zai sakamun sai da wannan,"   "Junaid dan Allah kayi mana bayani dalla dalla yadda zamu fahimta!"acewar jahad,    Kallon fuskar sehrish yayi ganin ta zuba mashi ido tana kallonshi,kalmar daya furta masu ce take ta maimaitawa acikin zuciyarta    "nidai baza aji mutuwar sarki abakina ba,Abba yace kar na faɗama kowa cewa an ɗaura aurensu,"yayi maganar tare da sanya hannu ya toshe bakinshi,   Hankali atashe suka shiga kallon juna atsakaninsu,   "Don Allah junaid ka faɗamun auren wa aka ɗaura"? muryarta tamkar zata yi kuka tayi maganar,    "Sehrish kiyi haƙuri bazan iya sanar dake ba,Amma idan kina son samun ƙarin bayani,kije wurin Uncle ki tambayeshi,   Jiki na rawa sehrish ta kama hanyar fita da sauri Hosana tabi bayanta,suka fita atare,     Matsawa yayi kusa da jahad,tare da ruƙo hannayenta yace"Jahad!Albishirinki"? "Goro,"ta bashi amsa fuskarta ɗauke da murmushi, "Fari ko Ja"? Wurga ido ta ɗan yi sama kafin tace"Fari,"     "Uncle ya bani aurenki,"jin wannan maganar yasa hankalin jahad ya tashi,lokaci guda ta ɗaure fuskarta,tare da fisge hannunta daga cikin nashi,    Gabansa ne ya faɗi,ganin yadda ta canza mashi lokaci guda tsoranshi kada ace jahad ba son shi take yi ba,   "Jahad baki sona?bakison ki aure ni ko"?   Shiru jahad tayi tana ƙare mashi kallo daga ƙasa har sama,    Tuni idanunshi sun cicciko da kwalla,fargabarshi wata amsa jahad zata bashi,in har bata amince ba shikenan zai rasa damar da yake da ita,na mayar da gurbin rishi ɗinsa daya rasa,    Motsi ta soma yi da la66anta daƙyar ta iya cewa"Junaid!dagaske kake mun ko wasa?tell me the truth pls,i know u are just teasing me,'     Girgiza kai yayi tare da cewa"Am serious jahad,Bazan 6oye maki ba,da farko sehrish nake so sosai,in har ba zaki manta ba,lokacin dana ɗauko ki a school matsayin sehrish,idan zaki iya tunawa sunanta nake ambata a matsayin ke,nayi tunanin itace shiya sanya na sanar dake abunda ke acikin zuciyata,Amma yau batare da sani na ba,A masallaci naji sanarwar ɗaurin Auren Sehrish da babban yayan mu,har sai da na kusa zaucewa ƙarshe a masallacin na yanke jiki na fa....."   A razane jahad ta katse shi da cewa"Wai dagaske an ɗaura auren Sehrish!kuma da babban yayan mu!?    ɗaga mata kai yayi alamar eh,kafin ya ɗaura da cewa"Ni kaina bansan da zancen auren nasu ba sae a masallaci dana ji ana sanarwar,abun ba ƙaramin ta6a zuciyata yayi ba,na shaqu sosai da sehrish,   Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba,jin zancen auren Sehrish da Sgr,ta rasa gane a wane yanayi take ciki,farin ciki ko kuwa akasin hakan!babban abunda ya ɗaure mata kai shine yadda aka 6oye masu ba'a sanar dasu ba,Ko meyasa?Yanzu shikenan an ɗaura auren rishi ɗinsu?ta zama married woman?    Runtse idanuwanta tayi tare da sanya hannu ɗaya ta dafe gefen goshinta,a hankali ta furta"Ya salaam,"    "Jahad,inason naji amsar tambayar da nayi maki"?muryarshi a kasalance yayi maganar,don ya qagara yaji amsar da zata bashi,    A hankali ta ware kyawawan idanuwanta akan fuskar junaid,tana kallonshi tace"junaid Daddy da kanshi ya baka aure na?kuma ya tabbatar maka da cewar bada wasa yake maka ba"?    Bubbuga ƙafafunshi yayi saboda hasalar da yayi,a ƙule yace"eh mana,shi da kanshi ya mallaka mun ke agaban kowa da kowa,yaji tausayina ne saboda halin dana shiga," .....fuskarta aɗaure tace"Meyasa daddy zai yi mun haka?nace mashi ina sonka ne?kuma ya rasa ma wazai ba aure na sai kai?junaid kayi mun ƙanƙanta!Ni bazan iya zaman aure dakai ba,nafison namijin daya mallaki hankalinshi ba shagwa6a66e ba sangartacce irinka...."tun kafin takai ƙarshen maganarta,hawaye suka fara wanke mashi fuskarshi,cikin shessheƙar kuka yace"au haka ma zaki ce jahad?shikenan babu komai,"da sauri junaid ya juya tare da nufar kopar ɗakin nasu gwanin ban tausayi,   Yana ƙoƙarin kai hannu ya buɗe ƙopar,da gudu jahad ta faɗa bayanshi tare da rungumoshi sosai tana dariya,wata irin nauyayyiyar ajiyar zuciya junaid ya sauke,kwantar da kanta tayi asaman bayanshi,magana ta soma yi mashi anatse"junaid,ko da yake yanzu na canza maka suna,Ka tashi daga junaid ka koma Babyn jahad,Ina fata hakan yayi maka,"   Tafin hannayenshi ya sanya tare da share hawayenshi,wani irin sanyi ne ya ratsa cikin zuciyarshi,Calmly ya ambaci sunanta"Jahad,Kin amince da aure na?a yadda nake?zaki iya haƙuri dani?ki zauna dani amatsayin Mijin ki uban ƴa'ƴanki kuma"?   Lumshe idanunta tayi yayin da hancinta ke shinshinar ƙamshin turaren jikinshi,    "I accept ur love junaid,I love u so much,nayi farin ciki sosai da daddy ya baka aurena,a ashirye nake dana baka kulawar daya dace junaid,"   Saboda tsabar farin ciki bakin junaid yaƙi rufuwa,hannunta ya ruƙo tare da zagayo da ita,ta dawo gabanshi suna facing ɗin junansu,zuba ma juna ido sukayi na wani lokaci,batare da sun sha Wahala ba,Sun amince ma junansu kowa ya samu abunda zuciyarshi ke muradi,janyota yayi ta faɗa asaman ƙirjinshi,zagayo da hannayenshi yayi ta bayanta,sosai ya rungumeta,tamkar zai mayar da ita cikin cikinshi,lokaci guda suka kamu da tsananin son kasancewa da junansu,   *Boss Bature*   ❤🤍❤   "Rafayet!Ka 6ata mun rai!ka ƙuntatamun!Amma kai ko ajikin ka?meyasa zakayi mun haka"?Abbansu ne yayi maganar a yayin da yake tsaye acikin bedroom ɗin Sgr,Idanuwanshi sun cika tab da hawaye,   "Abba,don me zaka tashi hankalin ka akan auren nan!You know the reason why I married her,Saboda inaso taci gaba dayin aiki a ƙarƙashina,ni ban shirya yin rayuwar aure ba,Babu wannan a tsari na," yana magana huci na fita a bakinshi,saboda tsabar 6acin ran da ya ke ciki,ji yake gaba ɗaya sun takura rayuwarshi,ba don komai ba sai don saboda sun nemi Alfarmar ya taimaka yayi koda hoto ɗaya ne shi da Sehrish don su ajiye na tarihi,   Gyaɗa kai Abbansu yayi tare da cewa"A haka kakeso kai ayi maka biyayya,bayan Ni ban isa na sanya ka abu kayi mun ba,narasa gane kai wani irin mutunne!ka ce yarinya bazata zauna a part ɗinka ba!kuma ba zaka ɗauki hoto ba atare da ita,nasan meyasa kayi hakan!saboda kada hotonku ya shiga duniya a dinga nunata a matsayin matarka!saboda kai a wurinka wannan ƙasƙancine aganta a matsayin matarka,saboda ka fi ƙarfin ta ko"?   Yayi maganar ranshi a 6ace,Sgr kuwa ko ajikinshi,yana daga tsaye agaban dressing mirror ɗinshi ya juya ma Abbansu baya,har lokacin bai canza kayan jikinshi ba,babu wanda baizo yayi mashi magana ba akan ya amince da buƙatar mahaifinsu amma yaƙi yarda,hatta Ishaq da Abbas sunyi sunyi har sun gaji sun ƙyale shi,haka Marshal Omar sunyi barambaram dashi,saboda ya 6ata masu rai,   "Zan tafi na bar maka ɗakin ka,Amma inaso na ƙara tunasar dakai cewa Abusufyan ya baka tsawon wata ɗaya kacal akan ka canza ra'ayinka game da auren yarjejeniyar nan,Zaka iya soke shi in har kana so acikin ƴan kwanakin nan,Amma idan har ka bari wata ɗaya ya wuce baka canza ra'ayin ka ba,duk abunda ya biyo baya kada kayi kuka da kowa ka kuka da kanka!kuma babu ruwana Na zame hannu na aciki,   A fusace Sgr ya juyo tare da kallon Abban nasu yace"bazan ta6a canza ra'ayi na ba akan hakan!Idan ma yana tunanin hakan to ya daina!Bana buƙatar wani time nayin tunani!wata uku na cika zan sallame ta ne!   Abba na ƙoƙarin buɗe baki yayi magana,ta wutsiyar idonshi ya hango mutun atsaye,a ɗan firgice ya juya don yaga wanene,   Sehrish ce atsaye tana kallonsu,gaba ɗaya jikinta ya gama mutuwa,domin kuwa taji duk abunda suka ce kaf acikin kunnanta,Jikinta har kerma yakeyi,wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga gangarowa akan fuskarta,   Jin shessheƙar kukanta yasa Sgr Juyawa tare dakai idanunshi wurin da take tsaye a ƙopar ɗakin nashi,tun daga ƙasa har sama yabita da kallo,   A hankali Abbansu ya ambaci sunanta"Sehrish!"   Juyawa tayi da gudun gaske tabar ƙopar ɗakin nashi,gaba ɗaya tabar part ɗin nashi,saukkowa tayi downstairs,Su fawan ne tsaitsaye acikin babban falon,koda suka ji shessheƙar kukanta sae hankalinsu ya koma akanta,kowa ya shiga tambayarta lafiya,   Bata tsaya sauraronsu ba,da gudu ta wuce bedroom ɗinsu,tana shiga ciki ta samu junaid da jahad azaune gefen gadonsu suna shan soyayya,jin shigowarta yasa suka mike tsaye hankali atashe suka shiga tambayarta Lafiya,   Bata basu amsa ba,kai tsaye ta nufi toilet ta buɗe ƙopar ta shige ciki,da ƙarfi ta datse ƙopar,sannan ta tsugunna ƙasa tana kuka tamkar ranta zai fita, Gaba ɗaya Jahad da Junaid suka nufi ƙopar,Suna kwankwasawa suna kiran sunanta"Sehrish!Sehrish!dan Allah Rishi ki buɗe mana kopa!   Turo kopar ɗakin nasu akayi,Abusufyan ne tare da hajiya azeema suka shigo ciki hankalinsu atashe,basu jima da shigowa ba,sai ga Abbansu junaid,dama tunda yaga ta watsa aguje tana kuka ya biyo bayanta,   A bakin kopar shiga toilet ɗin suka tsaitsaya cirko cirko    "Dama nasan abunda zai biyo baya kenan!"acewar hajiya azeema,   Abusufyan yace"Ni bansan waya faɗa mata ba,Naso ace ni na fara sanar da ita,"   Fuskar Abba a yamutse yace"wlh bansan da ita ba!Yanzun nan fa naganta a ɗakin Rafayet,muna cikin magana dashi akan zancen auren nasu,kawai naji shessheƙar kukanta,ashe duk taji abunda muka ce,"    Jikinsu ba ƙaramin sanyi yayi ba,musamman Abusufyan har cikin zuciyarshi ya ke jin kukan nata,    Ƙoƙarin lallashinta suka shiga yi amma ina,Sehrish taƙi sauraron kowa kuka sosai takeyi kamar ranta zai fita,tana jin muryoyinsu a waje sai faman yi mata magiya sukeyi akan ta buɗe masu ƙopar,    Junaid duk yabi ya ruɗe sam baisan cewa abun zai ta6a zuciyarta ba har haka,Ita kanta jahad ba ƙaramin tausayin Sehrish taji ba,kowa sai da yasha jinin jikinshi,babban abunda suke ji ma tsoro kada ta illata kanta, Bakomai ne ya ƙona mata rai ba,Fa ce abunda kunnuwanta suka jiyo mata,gaba ɗaya taji ta tsani kanta,komai ya fita aranta,tabbas tana son Sgr sosai har cikin ranta,kuma babu abunda ya canza acikin zuciyarta,tayi farin ciki mara misaltuwa na kasancewarta matarshi,wannan babbar kyauta ce agareta,sae dai kash bataso ya aureta batare da yana sonta ba!Sam bata ta6a ra'ayin hakan ba,tafi son ta auri wanda take so kuma yake sonta,bawai wanda takeso ba,Shi baya sonta,bugu da ƙari kuma ya aureta ne don taci gaba da aiki a ƙarkashinshi na wata uku kacal!     "Idan ba damuwa inaso ku ɗan bani wuri in shawo kanta,"hajiya azeema ce tayi maganar,    Abusufyan yace"kina ganin zaki iya shawo kanta kuwa?   "Ku je kawai,Ni nasan yadda zanyi da ita,ku ɗan bamu wuri,"   Kama hanya sukayi gaba ɗayansu hadasu jahad suka bata wuri,kamar yadda ta bukaci su fita daga dakin,   Zuƙunnawa hajiya azeema tayi abakin ƙopar toilet ɗin,Saboda ranta ya bata cewar sehrish tana zuƙunne a ƙasa,ta gane hakan ne ta hanyar sautin kukan nata,   Cikin lallami ta ambaci sunanta"Sehrish,"   Cikin shessheƙar kuka tace"Na'am,"   "Inason magana dake!dan Allah ki bani haɗin kai,kada ki bani kunya,inaso kizo ki buɗe mun ƙopar nan!,"    Miƙewa sehrish tayi,jikinta sai faman kerma yake yi,daƙyar ta iya sanya hannu ta buɗe kopar toilet ɗin,   Sauke ajiyar zuciya hajiya azeema tayi tare da mikewa tsaye tana kallonta,fuskar nan tayi suntum da ita,gaja gaja da hawaye,idanun sun kumbura,janbakin da ta shafa duk ya 6ata mata fuskarta,mascara ɗin da aka shafa mata asaman eye lashes ɗinta,duk ya jike sharkaf da hawayenta ya 6ata fuskar da baƙin,kayan jikinta ne kawai basu 6aci ba,   Ruƙo hannunta hajiya azeema tayi tare da zaunar da ita daga gefen gadon nasu,itama ta zauna suna fuskantar juna, "Haba amaryar babban yaya,kuka bana ki bane,Farin ciki ya kamata na gani akan fuskarki,"cike da zolaya hajiya azeema tayi mata maganar hada jan kumatunta, Fashewa ta kuma yi da wani sabon kukan cikin shesshekar kuka tace"Am...amma..Aunty azeema..meyasa za'ayi mun haka?saboda me za'a ɗaura mun aure tare da babban yayanmu batare da an sanar dani ba?Nasan cewa sun isa dani!Amma yakamata ayi mun adalci,Auren wata uku fa?kawai saboda buƙatar kanshi"?   Ruƙo hannunta hajiya azeema tayi cikin sanyin murya tace"Inaso na tambayeki wani abu,amsa ɗaya kawai nakeso ki bani,kuma ki faɗamun gaskiya,' Dakatawa sehrish tayi da yin kukan tare da mayar da hankalinta kan Aunty azeema tana sauraronta,    "Inaso ki faɗamun gaskiya,Shin kina son Sgr ko bakya son shi ne"?   Shiru sehrish tayi yayin da idanunta ke akan yatsun hannunta da ta harɗesu wuri guda tana murzasu,   "Kinyi shiru baki ban amsa ba"? ƙasa kasa tayi da muryarta tare da cewa"bazan 6oye maki ba Aunty azeema,ina son Yaya rafayet sosai,fiye da yadda nake son kaina,"    Murmushi hajiya azeema ta ɗan yi,dama saida ranta ya bata cewar tana sonshi,   "In har dagaske kina son shi bai kamata kiyi kuka ba don an ɗaura maki aure dashi,"   "Aunty azeema ba baƙin ciki nake yi ba,bakomai ne ya 6ata mun rai ba fa ce irin auren da akayi mun dashi,Saboda kawai nayi  aiki a ƙarƙashinshi,na tsawon wata uku?meyasa za'ayi mun haka?idan aka barni ma zan iya yin aiki a ƙarkashinshi ba sai ansa ya aure ni ba,ba bisa son ranshi ba,tunda ba sona yake yi ba,ni kaɗaice nake ɗawainiya da son shi tun kafin nasan wanene shi,Wahala kawai zansha a hannunshi,Ni ban ta6a son na aureshi ba batare da yana Sona ba,"   Jinjina kai hajiya azeema tayi tare da cewa"hakane kin faɗi gaskiya,ba'ayi maki adalci ba,Ni kaina bansan dalilin yin auren ba sai daga baya nake ji a wurin Abbanku,Amma kiyi haƙuri dan Allah kada hakan yasa ki bijire ma iyayenki,kiyi masu biyayya in sha Allah zaki ci ribar yin hakan,"   Batare da musu ba Sehrish tace'Shikenan,in sha Allah zanyi masu biyayya,kamar yadda kika ce,kuma koda baki faɗamun haka ba,Ni bazan yi kuskuren bijire masu ba,"   Murmushi hajiya azeema tayi tare da sanya hannunta ta shafa gefen fuskar sehrish, "Good girl,Naji daɗi sosai da kika amince zakiyi masu biyayya,Ni kuma nayi maki alƙwarin cewa atare zamu yaƙi sgr,acikin waɗannan watannin guda uku kacal,Zamu canza mashi ra'ayinshi,don ya gane kuskurenshi,kinsan ance DUK ƘYAN TAKALMI ƘAFA CE KE TAKASHI,So nake ki take mun wannan tsadaddan takalmin da ƙafafun nan naki ya taku sosae," Sae lokacin Sehrish ta fashe da dariya,har hakoranta suka bayyana,maganar da hajiya azeema tayi mata ta ƙarshen nan ba ƙaramin dariya ta bata ba, Cigaba da magana hajiya azeema tayi"domin aikin mu yayi kyau muna buƙatar mu shirya plan A da kuma plan b zuwa c,zamu fara jaraba plan A,idan har akaci nasara akan shi kinga basai mun buƙaci plan B ba,Abunda nakeso dake yanzu shine muna buƙatar satar amsa,kuma ke kaɗae ce zaki iya samo mana wannan satar amsar da muke buƙata a wurinshi, A tsorace sehrish tace"Ni kuma!"hajiya azeema tace"kwarai kuwa,ba wani abun tashin hankali bane,just akwai bukatar musan me yake so da kuma abunda baya so don mu kiyayesu,Ni dae a iya sanina Sgr mutunne maison abi umarninshi ba'ayi mashi musu,yafi so ayi mashi biyayya abishi sau da ƙafa,sannan mutunne shi mai tsaftar gaske,ya tsani ƙazanta,bayan haka kuma Yana son abinci mai daɗi,shiyasa yake cin girkin azmee saboda tana da tsafta kuma ta iya girki,yakama ki koyi kalar girke girkenta," "Ae na fara koyo a wurinta,Kuma na iya waɗansu,amma zanyi mata magana akan ta ƙara koyamun wanda ban iyaba," "Yawwa haka nakeson ji,ki dage sosai,Nidae ta 6angarena zan baki gudummuwa sosai,"" Sun jima suna fira atsakinsu tamkar ba uwa da ƴa ba,har sae da aka fara kiran sallar Magrib,sannan aunty azeema tayi mata sallama, Hankalin sehrish ba ƙaramin kwanciya yayi ba,ta samu ƙwarin guiwa sosai a wurin Hajiya azeema kuma taci alwashin zata ɗaura ɗamarar zama da sgr,har na tsawon wata ukun *Boss Bature* Wuraren ƙarfe 12 na dare,tana a tsaye cikin ɗakinsu,sae faman zagaye zagaye takeyi,tana jiran dawowar Sgr,tun bayan sallar isha'e bai dawo cikin gidan ba,har lokacin wedding gown ɗince a jikinta,ta gyara kwalliyar fuskarta,sannan ta daure gashin kanta da ribbom, Jahad da hosana sun jima da yin bacci ita kaɗae ta rage batayi bacci ba,zuciyarta cike take da damuwa,sam tagaza samun natsuwa babban abunda takeyi ma fargaba shine taya zata fara tunkarar SGR a matsayin Mijinta?shin zata iya jure zama dashi?tasan cewa dole ta fuskanci ƙalubale dayawa a wurinshi, Tana cikin wannan zancen zucin taji shigowar motocinsu,ajiyar zuciya ta sauke tare da komawa gefen gadonsu ta zauna tana jiran su ƙarasa shigowa cikin gidan, Almost 30 mins,sannan ta miƙe tare da buɗe ƙopar ɗakin ta fito waje,babu kowa kai tsaye ta nufi kitchen,batare da 6ata lokaci ba,ta shirya mashi dinner ɗinshi a saman ƙayataccen tray ta ruƙo shi da hannayenta,a hankali take tafiya saboda tsinin takalman dake a ƙafafunta,bata saba tafiya da irinshi ba,babu kowa a main palour ɗin hakan yasa ta wuce upstairs part ɗinsa, Da sallama abakinta tashiga falon,babu kowa aciki sae dae kamshin turaren nan nashi,kama hanyar zuwa bedroom ɗinshi tayi,a bakin ƙopar ta tsaya tare da yin sallama"Assalamu alaikum" "Who's there"abunda taji yace kenan, daƙyar ta iya cewa"Ni ce" "Okey,Come in" A hankali ta zura ƙafarta cikin ɗakin nashi,samun shi tayin kwance asaman katafaren gadon nan nashi na mulki,ko takalman ƙafarshi bai cire ba,still shaddar ce ajikinshi, Ƙarasa shiga ciki tayi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman table,kamar wata mara gaskiya ta juya zata kama hanyar fita daga ɗakin muryarshi ta katse mata hanzarinta da cewa"Baki iya gaisuwa bane?" dakatawa tayi tare da ɗan juyo ta saci kallon fuskarshi,A lumshe ta samu idanunshi tamkar maijin bacci, Muryarta na rawa tace"Ina yini" Ta6e la66ansa yayi tare da cewa'zonan"" Jiki asanyaye ta tunkareshi,da hannu ya nuna mata gaban gadon nashi,sannan yace"kneel down" Tattare rigar jikinta tayi,tare da zubewa saman guiwowinta, "Kukan me kikeyi ɗazu?ko don saboda kinji abunda muke tattauna da Abba ne?" Girgixa kai tayi'a'a ba haka bane,"" "Okey," Shiru ya ɗanyi na wani lokacin kafin yaci gaba da magana"Na aureki ne saboda inaso ki cigaba da aiki a ƙarƙashin ikona!Idan har bakya ra'ayin hakan zan iya sakin ki,"Ya ɗan dakata da yin maganar yana jiran jin 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina 08103884440❤_ Not edited, "zan cigaba da aiki a ƙarƙashin ka,"ta ƙarasa maganar,tana faman sauke ajiyar zuciya,   "Good,"ya furta hakan tare da miƙe wa daga zaune,Ya jingina bayanshi a jikin pillow,har time ɗin idanuwanshi na a lumshe bai buɗesu ba,    "Now you are under my control, you must follow my rules,"dakatawa yayi da yin maganar,tare da kai hannu ya zaro hanky daga front pocket na rigar shaddar jikinshi,   Miƙa mata yayi tare da cewa"Oya,goge wannan fentin dake a saman lips ɗinki,from now bana buƙatar naga make up a face ɗinki,in dai zakiyi aiki a part ɗina,"    Hannu tasa ta kar6i hanky ɗin,tare da kaishi saman lips ɗinta,a hankali ta shiga goge jan bakin da tasha fa,    Cigaba da magana yayi"i won't restrict ur life,You still ave ur right,don na aure ki ba hakan yana nufin zaki ɗauki kanki as a married women ba,No just normally zakiyi rayuwarki,Kuma zaki iya kula duk wanda kikeso koda namiji ne i don't care about that,'   Zaro ido waje sehrish tayi tana kallon fuskarshi,cike da mamakin jin abunda yace mata,Lamarin sgr ya fara bata tsoro,sae ka ce ba musulmi ba!da aurenta kuma ya amince mata ta kula duk wanda takeso?Anya bai fara shaye shaye ba?kodai yana da Iska ne ajikinshi?Abun yayi confusing ɗinta sosai,   "Idan ma kina da tsafta ki ƙara akan wadda kike da ita,part ɗina ya kasance kullum a tsaftace ya ke,"   Kasa kunne sehrish tayi tana sauraron shi,guiwowinta har sun fara yi mata raɗaɗi,magana yake yi tamkar baisan motsa la66ansa,balle har yayi sauri ya kammala ko ta samu ta miƙe,    "Banason wani ya ƙara girkamin abincin da zanci,da hannunki zaki girka mun,sannan ba kowani kalar abinci nake ci ba,Ki nemi bayani a wurin Asmee,"   Dakatawa ya ɗanyi da maganar,hannu ya miƙa tare da ɗauko wayarshi dake ajiye saman side drawer ɗinshi,ya shiga daddanata,    Ganin haka yasa sehrish tayi sauri Zama dirshin a ƙasan,kota rage raɗaɗin da guiwarta keyi mata,      "Where's ur phone"?yayi tambayar tare da ɗan dakawata,da dannar wayar da yake yi,    Da sauri tace"na barta a bedroom ɗinmu,"   "Okey,"ya ambaci hakan tare da kai hannu ya buɗe drawer chest,memo ya ɗauko tare da biro,Ya buɗe empty page,a natse ya shiga yin rubutu asaman paper ɗin,.   Zugudum sehrish tayi,aranta tana tunanin ko taya zata iya gane hand writting ɗinshi?kwanakin baya,daya ta6a yi mata rubutu bata iya gane komai ya rubuta ba,har haroon ya yaudareta,    Bayan ya kammala rubutun,Yayi tearing paper ɗin tare da miƙa mata,hannu tasa ta kar6a,    "Phone number ɗina ne,Cos at anytime zan iya kiranki,even in the midnight indai ina buƙatar wani abu"    Amsa mashi tayi da toh, "Your work will start from tomorrow!U can leave now,"   Jiki asanyaye sehrish ta miƙe dakyar take ɗangyasa ƙafarta tana tafiya,har sae da takai bakin ƙopar bedroom ɗin nashi sannan ta ɗan dakata da yin tafiyar,juyowa tayi tare da aza idonta akanshi,a lokacin harya sauko daga saman gadon,yana ƙokarin cire kayan jikinshi,da alama wanka zaiyi,    Gyaɗa kai kawai tayi tare da sanya ƙafa ta fito daga bedroom ɗin nashi,   Bata tashi jin hawaye ba,sae da ta hau saman staircase din,tana taka benen a hankali,bakomai yafi ƙona mata rai ba fa ce abunda ya ce mata,Zata iya kula duk wanda takeso koda Namiji ne shi bai damu ba,tsabar takaici kamar ta haɗiyi zuciyarta haka take ji,taci alwashin saita koya mashi hankali,kuma zata jajurce ne wurin ganin ta gudanar da aikinta kamar yadda yakeso,daga baya kuma ta shiga tunanin komai yasa ya hanata shiga part ɗinshi da makeup?mai jan bakinta yayi mashi ne da zaisa ta goge?da alama so yake ya dinga ganinta kamar gardi,shiyasa yayi mata hakan, Ƙarasa saukowa tayi daga saman stairs din,sannan ta tsaya tare da juyawa tana kallon upstairs ɗin" In sha Allah,Wata rana Sai kayi kneel down agabana,Kamar yadda ka saba sanya ni in duka agabanka,koda baka zubar da hawayenka ba,zakayi kukan zuciya ne wanda yafi ciwo,Wannan alwashine na ɗaukarma kaina,In har ban tabbatar da faruwar hakan ba,To ni ba jinin Abusufyan bace da abu!!kuma ban cika mace ba,"   Tana magana hawaye na shararowa akan fuskarta,ranta ya 6aci sosai   *ATAƘAICE* Acikin waɗannan ƴan kwanakin Sehrish ba ƙaramin jiki taji ba,domin kuwa sgr baiyi mata da sauƙi,Aiki takeyi tuƙuru,ba ƙaramin ƙoƙari take yi ba wurin ganin ta kiyaye duk wani abu da zai haɗa ta dashi,Aranar monday abusufyan ya mayar dasu school,da kanshi yakaisu acikin motarshi,basu samu matsala ba,sae dai an wuce su abubuwa da dama,Domin kuwa suna dab da fara'a Exams,abubuwa duk sun haɗe mata,ko karatu takeyi hankalinta na akan agogo,don kada ta shiga lokacin aikinta batare da ta sani ba,tun da sanyin safiya take shiga part dinshi tunkafin ma ya tashi daga bacci,ta gyara mashi toilet ɗinshi da falonshi,bayan ya tashi daga bacci ya shiga wanka,ta zauna ta gyara bedroom ɗin nashi,Sannan ta shiga kitchen ta haɗa mashi breakfast ɗinshi,Mafi yawancin lokutta a makare take zuwa makaranta,Saboda aikin sgr,Sae yaga damar sallamarta tukunna,abun ba ƙaramin 6ata ma abusufyan rai yakeyi ba,sae daga baya ya dinga danasanin ƙulla auren yarjejeniyar da sukayi,kullum Shi yake ja masu yin late a school,saboda dole sai sun jira sehrish ta kammala aiki a part din sgr,sannan su wuce school,baiwar Allah suna dawowa daga school da zarar tayi sallah,ko abinci bata ci,indai sgr na a cikin gidan sae ta fara zuwa ta gyara mashi part ɗinshi ta kuma kai mashi lunch ɗinshi,ta kuma yi serving ɗinshi abincinshi har sai ya mula yasha iska tukunna ya sallame ta,sannan fa take samun damar cin abincinta,Cikin lokaci ƙankani sehrish ta soma fita hayyacinta,Duk ta rame,kullum ne sai ta farka tsakar dare,ta zauna tayi ta kuka ba wanda ya sani,ita kaɗae tasan irin raɗaɗin da take ji acikin zuciyarta,gashi in tayi kuskuren yi mashi laifi,Hukunta ta yakeyi da tsallan kwaɗi,babu wanda bai fara jin tausayinta ba acikin gidan,shiru kawai sukeyi,bakomai ne ya jawo mata hakan ba fa ce rashin Hajiya azeema domin kuwa tun sati daya da yin auren,Tabar ƙasar izuwa dubai inda tasaba yin harkokin kasuwancinta,Amma tayi mata alƙawarin cewa bazata wuce One month ba zata dawo nigeria saboda ita kawai,Duk da haka kullum sai sunyi waya da ita,kuma tana ƙara ƙarfafa mata guiwa,kullum tana kara tunasar da ita akan cewa Karta kuskura ta karaya tun yanzu,Taci gaba da hakuri wata rana sai labari,mahaƙurci mawadaci ne,Sannan ta dage da addu'a kuma taci gaba da kyautata mashi,sgr bai tsaya a iya nan ba,idan dare yayi dama wannan ƙa'ida ne saita kai mashi coffee da kayan marmari around 12,toh yanzu takai ga,sae tana bacci wuraren 1:30 na dare ko biyu,ringing ɗin wayarshi ke tashinta daga bacci,daga ta ɗaga zaice mata Coffeee,yana furta hakan zai katse kiran,Dolenta ne ta tashi takai mashi ga bacci a idanunta,duk in taje part dinsa a wannan lokacin zata same shi ne yana yin nafilfilin dare,ko kuma ta same shi bayan ya kammala yin sallar yana karatun alƙur'ani,a rana ta farko data fara ganinshi yana karatun kur'ani abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,Ita duk a tunaninta babu ilmin addini akanshi,Ashe kullum saiya tashi in midnight don yayi sallar dare da kuma karatun alƙur'ani,tun daga ranar da ta fara ganinshi yana yin sallar nan,itama sai ta koma yin sallar daren da karatun al'kur'nin,saboda su dinga samun ladar atare,tunda ya katse mata baccinta, A 6angaren Amrish kuwa,Daƙyar haroon ya samu ta amince zata koma wurin Mommynta da zama,Da kanshi ya mayar da ita gidansu,Sannan ya gargaɗi mommynta akan ta kiyaye 6acin ranta,itama amrishi ɗin sai da yaja mata kunne akan karta ƙara yunkurin kashe kanta,da haka ya samu ya sasanta tsakaninsu,har ta koma school,Ranar da suka haɗu da sehrish a makaranta kamar zasu haɗiye junansu saboda tsabar farin ciki,sun sha kuka sosai,saboda sunyi kewar junansu,abun ba'a magana, Soyayyar junaid da jahad kuwa kullum ƙara ninkuwa takeyi acikin zukatansu,sun shaƙu sosai koda yaushe suna manne da junansu,baya gajiya da ɗaukarta su fita shan ice cream,Junaid ya iya soyayya sosau,yaci sunanshi romeo,saboda ya iya caring,ga zumuɗi kamar sabon ango,A ƙagare yake da aɗaura mashi aure da jahad,Bawan Allah duk safiyar Allah sai yayi shiga ta mutunci yaje gaisar da Abusufyan,hakan ba ƙaramin daɗi yakeyi ma abusufyan ba,tun daga haka ya gane cewa junaid zai ruke mashi ƴarshi dakyau duk da ƙuruciyarshi,amma yana da hankali sosai, A 6angaren Marshal Omar kuwa,Hosana ta tada mashi 6alli,saboda sehrish tayi aure ita bai aure ta ba,duk yadda yaso ya shawo kan hosana akan ta bashi lokaci amma yarinyar nan taƙi yarda,ƙarshe tace mashi in har baije anyi maganar aurensu ba,zata tona mashi asiri ne,gabanshi ya faɗi ya shiga tunanin wani asiri ne hosana take ikirarin zata tona mashi,koda ya matsa mata akan ta faɗa mashi abunda take 6oyewa,sae cewa tayi ae Ya ta6a yi mata fyaɗe hada nuna mashi Zoben diamond ɗinshi daya manta a ranar,kuma tace zata sanar dasu Abbansu ne,Hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,ƙoƙarin fahimtar da ita ya shiga yi akan cewa shi fa ba fyade yayi mata ba,kawai tsautsayine yasa yayi ƙoƙarin raping ɗinta a lokacin,daƙyar ya samu ya lallasheta,sannan ta haƙura,a hakan ma sai da yayi mata alƙawarin cewa za'a daura masu aure, lokacin da Haroon Ya ji Auren Sehrish da sgr,tamkar zai zauce saboda tsabar tashin hankalin daya shiga,don shi dagaske son Sehrish yake yi,daga baya ne ya gano cewar Auren Nasu na wata uku ne,tunda yaji hakan sai hankalinshi ya kwanta,Kuma yaci alwashin cewa Sai ya samu soyayyar Sehrish,in ba haka ba sai yabi duk hanyar da zai bi wurin ganin ya biya bukatarshi da ita,don ya jima da kwaɗayin son kasancewa da ita,tashin hankali, Wannan kenan A ranar wata Juma'a ne,Allah yayi ma modibbo rasuwa,Mutuwarshi tayi matuƙar girgizasu gaba ɗayansu,Musaman Ammi kamar zata zauce don kuwa har suma saida tayi lokacin da saƙon mutuwar nashi ya isar masu,Rashin lafiya yayi na rana ɗaya kuma Allah ya kar6i abunshi,Sunji mutuwarnan kamar kamar me,Ashe babu rabon komawarshi saudiya,duk da yaci nasara akan abunda ya kawo shi nigeria ya haɗa kan zuri'arsu,ya ƙulla zumunci mai ƙarfi atsakaninsu,Allah ya jiƙan Modibbo, Gaba ɗayansu suka shirya zuwa Damaturu domin halartar jana'izarshi,Banda su sehrish saboda Exams da sukeyi a school ta Second term,amma matasan gidan dukansu abbansu ya tattarasu sun tafi can,gidan ya rage daga Azmee sae su sehrish,baƙaramin daɗin tafiyar sgr sehrish taji ba,Duk da ranta na bata cewar daƙyar zai wuce 1 week bai dawo cikin gidan ba,ta dan samu hutu,Kullum daga taji dirar mota jiki na rawa zata je ta leƙa ta window taga wanene ya dawo,Fargabarta kar ace shine ya dawo,da zarar taga bashi bane,Daɗi take ji,duk da tayi kewar shi sosai,Ko bacci takeyi sai ta dinga jin muryarshi acikin kunnanta yana cewa"Oya kneel down" har mafarkinshi takeyi,?   Yau Ya kasance wata ɗaya cuf da yin aurensu,batare da sgr ya soke yarjejeniyar ba,yanzu kwana biyar kenan da tafiyarsu Damaturu,dama abbansu yace sai sun zaga dangi,tunda sun jima basu je sun sada zumunci ba, *Boss Bature*    ❤🤍❤ Wuraren ƙarfe 3 na rana,sehrish na kwance saman gadonsu,tayi nisa acikin baccinta,baiwar Allah ba ƙaramar gajiya ta kwaso ba,Yau suka kammala Exams ɗinsu,tunda suka dawo daga school Ko Uniform ɗin jikinta bata samu ta cire ba,ga yunwa na cinta amma ahaka ta kwanta saboda baccin da take ji, Jahad kuwa tana a garden suna video call da junaid,tun bayan da suka tafi,kullum ne saiya kirata video Call,idan suka fara wayar nan sai sunyi fiye da one hour suna magana,Idan da daddare ne kuwa ya kirata suna kaiwa har wurin asuba,basu runtsa ba,Soyayyarsu ba ƙaramin burge sehrish takeyi ba,wani sa'in sai taji dama itace take samun irin kulawar a wurin sgr,ɗan tahalikin nan tunda suka tafi kullum ne saita tura mashi Text message amma babu reply,bai ta6a mayar mata da amsa ba,kuma hakan baisa ta daina tura mashi ba, Cikin bacci ta dinga jin jiniyar motoci acikin kunnanta,A firgice ta farka tana faman zare ido,tsoranta kada ace Sgr ne yadawo Cikin gidan,Sai da tadawo cikin hayyacinta sosai sannan ta gane cewa ashe wayarta ce ke ringing,Wata irin nauyayiyar ajiyar zuciya ta sauke,Hannu takai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman pillow,sae hamma takeyi saboda yunwar da take ji,duba screen ɗin wayar tayi,Sunan Daddy ne ya bayyana,Murmushi ta ɗan saki tare da answer kiran,ta kara wayar a kunnanta,    "Assalamu Alalikum daddy," Muryar abusufyance ta amsa mata da cewa"Wa'alaikum salam,Daughter ya kike?tun ɗazu inata jaraba kiran wayar jahad line busy,ke ma kuma na kira wayarki kusan sau biyu tana ringing ba'a ɗaga ba,dafatan kuna lafiya,"    "Bacci nakeyi ne shiyasa banga kiranka ba,Jahad kuma tunkafin na kwanta,ta sanar dani cewa junaid ya kirata,nasan yanzu haka dashi takeyin waya a garden,"    "Okey,hosana fa?tana ina ne?itama na kira layinta a switch off,"    "Daddy hosana fa,bata amfani da wayarta,tun ranar daka siya mana su bata ƙara bi takanta ba,tafi mayar da hankali akan laptop ɗinmu,yanzu haka ma kallo takeyi acikinta,"_   Abusufyan yace"Na kira ne dama don inji ya ku ke,"   Murmushi tayi kafin tace"Alhamdulillah daddy,muna lafiya,fatan kaima haka"? .."ina lafiya nima,Ya Exams ɗin taku?kunyi abun kirki ko?   dariya ta ɗanyi tare da cewa"Yau dai muka kammala,Result muke jira yanzu,amma fa daddy kasan a ƙurarren lokaci muka koma school,duk an wuce mu a karatu,duk yadda kaga result ɗinmu kawai kayi shiru da bakinka,ka sanya mana albarka,"   Tana jiyo muryar abusufyan ta cikin wayar yana dariya,bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"Oh,kina nufin cewa ba kuyi abun kirki ba ko?oh ni abusufyan kada ace ƴa'ƴana basu da ƙoƙari,"    "A'a daddy ae ba laifinmu bane,yakamata ayi mana uziri,saura fa two weeks a fara exam ka mayar damu school,"    Abusufyan yace"hakane kuma fa,baki tambayeni yaushe zan dawo ba?ko bakiyi missing ɗina bane"?    Muryarta da ƴar shagwa6a tace"I really missed u alot daddy,kamar na janyoka ta cikin wayar nan,inyi hugging ɗinki,"   Dariya yayi sosai kafin yace"this Week zamu dawo ae,zuwan bazata zanyi,kuma a washe garin ranar da nadawo zamuje kano,Zan ɗauki ɗaya daga cikin ku mu tafi kano,saboda inaso muje gidan makwabtan nan naku ya ma sunansu?   Da sauri tace"gidansu maman sadeeq"?   Yace"eh nan nake nufi,zamu je ne domin munyi bincike akan mahaifiyarku,Nasan zamu samu ƙarin bayani a wurinsu,"   Wani irin farin cikine ya bayyana akan fuskar sehrish,fuskarta dauke da murmushi tace"daddy inaso dan Allah ku tafi tare dani mana,"   "Kina tunanin cewa Babban yayanku zai bari na tafi tare dake ne"?   Shiru tayi tuni idanunta sun ciko da kwalla,muryarta tamkar zatayi kuka tace"Amma daddy,ni ya kamata a tafi tare dani,saboda zanfi gane kwantancen gidan nasu,"   "Shikenan idan har kinason mu tafi tare dake,toh ki fara sanar da babban yayanku,idan har ya amince zamu tafi atare,in kuwa ya hanaki zuwa sai dai ki haƙura mu tafi tare da Jahad,"    Jikinta ne yayi sanyi harma ta fidda rai don kuwa tasan cewa Daƙyar ne sgr ya barta ta tafi kano,   Cikin sanyin murya tace"Shikenan daddy,zan jaraba tambayarshi idan ya dawo,Allah yasa yabarni,wlh dana ji sosai,"   Sun jima suna waya dashi kafin sukayi sallama,ajiye wayar tayi asaman side drawer,sannan ta sauko daga saman gadon,direct ta wuce toilet domin yin wanka,within mins ta fito jikinta sanye da bathrobe,ta saki gashin kanta a bayanta,yanzu tsayinshi yakai har mid back ɗinta,   Gaban mirror ta tsaya,tare da ruƙe qugunta,bakowa bane ya faɗo mata a ranta ba fa ce Sgr,a duk lokacin daya sanya bathrobe ɗinshi ba ƙaramin kyau rigar take yi mashi ba,yadda kasan donshi akayi rigar,    Hannu tasa tare da janyo gashin kan nata,ta dawo dashi ta gabanta,tana kwaikwayon yadda sgr yakeyi in ya fito daga wanka,ta daure fuskarta kamar yadda yake tamke fuskarshi,a ƙarshe ta fashe da dariya,   Tana cikin rahar nan,hosana ta turo ƙopar ɗakin nasu,Ta cikin mirror take hangenta,Hannunta na ruke da system ɗinsu,jikinta na sanye da doguwar riga ta material,    "Sehrish ga lunch ɗinki can a dining,Aunty azmee ta ce idan kin gama baccin lalacin naki kije ki ci,"    Ta ƙarasa maganar a yayin da take zama daga gefen gadon nasu,    Juyowa sehrish tayi tare da kallon hosana tace"daddy ya kira wayarki a switch off,wai ina kike ajiye ta ne"?   Yatsina fuska hosana tayi kafin tace"Oho,nima bansan inda take ba,nemanta na keyi ruwa ajallo,dan Allah ki tayani nemanta,inaso in kira Ya Omar,nayi nayi da jahad ta kira munshi amma taƙiya,dama kece mai ɗan mutuncin,"   Harara sehrish ta watsa mata tare da cewa"Sai yau kikasan da haka?bayan kinsaba cewa nafi kowa tsiwa,bayan duk acikinmu ni ce innocent,"   Marairaice mata fuska hosana tayi,"pls rishi komai ya wuce,dan Allah ki bani aron wayarki yanzu dai in kira Ya omar,2 days banji Voice ɗinshi ba,Ni fushi nakeyi dashi ma,ko ya kira yaji ya nake,amma bai kira ba,"rai a6ace tayi maganar,    "Kada ki isheni da surutu,don nasanki bakya gajiya,ga wayar nan ki ɗauka,salon ki cinyemun katina,"    Cike da zumuɗi hosana ta ajiye system ɗin asaman gadon,sannan ta ɗauki wayar da sauri ta fuce daga ɗakin,    Gaban wardrobe ta koma tare da buɗewa,tana neman kayan da zata sanya,shirt ce ta ɗauko off shoulder Ash colour tare da dogon wandon Jeans,batare da 6ata lokaci ba ta zura kayan ajikinta,bayan ta kammala sanya kayan ta koma gaban mirror, tana shafa powder,sannan ta ɗan shafa lip gloss,murza la66an tayi,tana cikin sharce sumar kanta,Jahad ta turo ƙopar ɗakin,    Hannunta ruƙe da wayarta,fuskar nan awashe sae faman sakin murmushi take yi,    Juyowa sehrish tayi tare da kallonta tace"Sai yanzu kika kammala shan Love ɗin?Ni wannan soyayyarta ku tana ɗaure mun kai wlh,ko gajiya bakuyi,yadda kasan Romeo da juliet,kullum kuna a manne da juna,"   Jahad tace"da alama baƙin ciki kikeyi mun Allah,"    "In rasa dawa zanyi baƙin ciki sae dake?kin manta wa nake aure?Ni fa matar Surgeon general ce,ke fa?Ni har kunya ma nake ji,ki rasa dawa zakiyi soyayya sae wannan shagwa6a66an..."   Tunkan takai ƙarshen maganar jahad tace"Auren da yanzu saura 2 month ya mutu!dashi har kike tutiya,"   Gaban sehrish ne ya faɗi rasss!lokaci guda jikinta yayi wani irin sanyi,yayin da idanunta suka ciko tab da kwalla,    Ita kanta jahad,bataso ta faɗi hakan ba,ranta ne ya 6aci saboda ta tsani a kushe mata baby Junaid ɗinta,Wannan ne yasa har ta faɗi maganar da tayi,   "Jahad!ni kike faɗa ma haka"? Da sauri jahad tace"dan Allah kiyi haƙuri,wlh bansan na faɗi hakan ba,raina ne ya ɗan sosu,"   "Kinayi mun fatan aurena ya mutu kenan"? Tayi tambayar hankalinta aɗan tashe   "Dan Allah rishi kidaina faɗin wannan maganar,nace maki ba a son raina na faɗi hakan ba,"tayi maganar tare da ƙarasawa wurin sehrish ɗin,ta ruƙo hannunta,    "Pls kada ki bari hawayen nan sun fito daga cikin idanunki,kinsan cewa bazan ta6a yi maki fatan aurenki ya mutu ba,kuma wlh ban faɗi hakan ba donna 6ata maki rai ba," fuskar jahad tamkar zatayi kuka saboda tausayin sehrish,    Tuni hawaye sun shiga wanke mata fuskarta,cikin sanyin murya ta wanda ya karaya tace"kin faɗi gaskiya jahad,bai kamata inyi prouding da aurenshi ba,Ni sam na manta ashe yau saura 2 month babban yaya ya sake ni,ni nama ƙosa ya sake ni in huta,'    Hannu jahad tasanya tana share mata hawayenta"in sha Allah Babban yaya bazai ta6a sakin ki ba,banayi maku fatan rabuwa da junanku,Nafison ku kasance atare na har abada,Daso samu ne kawai wani abu ya shiga atsakaninku,Ana saura sati daya auren ya mutu,aga kina amai kinga shikenan babu zancen saki,Sae dai a fara tanadin suna,"cike da zolaya jahad tayi maganar,aikuwa nan take sehrish ta fashe da dariya,   Ganin tafara dariya yasa jahad taci gaba da tsokanarta"gaskiya naƙosa in ganki da ciki,cikin ma na babban yayanmu,Wayyo Allah na bansan wani irin farin ciki zanyi ba aranar,zanso naga babynku,wlh ba ƙaramin kyau zaiyi ba,idan ya biyo kowannanku,"   Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Najima ina burin wannan ranar,bazan 6oye maki ba jahad,inaso inga nima na haifi ɗan babbyna,Amma nasan ba yanzu ba,"    "Dont worry ur self,Very soon zaki haifa ma babban yayanmu twins ko triplet,tunda muma triplet ne,nasan acikinmu baza'a rasa wadda zata haifi ƴan biyu ba ko ƴan uku,"Acewar jahad,   Shiru sehrish ta ɗanyi tana murmushi,duk da tasan abune mai wuya amma taji daɗin maganar nan ta jahad,    "Inaso naje naci abinci,yunwa nake ji,"    Ta ƙarasa maganar tare da kama hanyar fita daga ɗakin,Bin bayanta jahad tayi da sauri tare da ruƙo hannunta cikin nata,    "Mu tafi atare,nima ae banci abincin ba,"   Dining suka nufa,Wuri suka samu asaman dining chairs ɗin kowa ya zauna,Tray ne mai faɗi azmee ta ajiye masu asaman dining ɗin,Warmers ne guda biyu babba da ƙarama ta miya ajiye asaman shi tare da plate,sae drinks data ɗauko masu,    Da yake mutanen gidan duk basu nan shiyasa bata girka abinci dayawa ba kamar yadda ta saba,ita kanta ta ɗan samu hutu yanzu,    "Munyi waya da daddy,"sehrish ce tayi maganar a yayin da take ƙoƙarin buɗe warmer ɗin,    "Ya faɗa maki ranar da zasu dawo ne"?_   "A'a bai faɗamun ba,sai dai yayi mun albishir mai daɗi,"   Cike da zumuɗi jahad tace"Wani albishir kenan"?    Murmushi ta ɗanyi a lokacin ta kammala buɗe warmer ɗin,wainar shinkafa ce acikinta,    "Ya sanar dani cewa da zarar sun dawo daga damaturu,A washe garin ranar zasu tafi kano,wurin nemo oumman mu,"   Maimakon taga farin ciki akan fuskar jahad,sai taga idanunta sun ɗan ciko daa kwalla,    "Meyasa bakya farin ciki ne"? "Sehrish farin ciki fa kika ce?Bana Farin ciki,Idan har kika ga nayi farin ciki,toh An samu oummaan mu ne da ranta kuma da lafiyarta,ina fargabar abunda zaibiyo baya,idan suka je nemanta,Kinsan yadda oumman mu take tsananin son mu sosai,Amma lokaci guda aka nemeta aka rasa,tsorona kada ace ya sayyadi ne yayi mata wani abun,dama yasha faɗin cewa zai kashe ta idan har bata daina bin ƙwaƙƙwafin da takeyi mashi ba....."dakatawa jahad tayi da yin maganar,jikinsu duk yayi sanyi,    "Addu'a yakamata muyi mata akan Allah yasa su samota,Amma nikaina ina fargabar a wani hali zasu same ta,"     Duk sunsha jinin jikinsu,zuba masu wainar tayi acikin plate,sannan ta buɗe ƙaramar warmer ɗin,Miyar ganye ce,taji ganda lu6u lu6u acikin,Tuni ƙamshinta ya gauraye wurin,    Daƙyar suke iya cin abincin,kamar waɗanda akayi ma dole suci,    *HAROON* Fitowarshi kenan daga cikin bedroom ɗinshi,yana ƙokarin barin wurin,Yaji an ambaci sunanshi"Haroon"!gabanshi ne ya fadi,duk a tunaninshi Amrish ce ta kuma biyo shi,da sauri ya juya don yaga wacece,tun daga ƙasa har sama ya soma binta da kallo,Jikinta na sanye da atampa,riga da skirt ne sun matseta sosai,gaba ɗaya surar jikinta ta fito ɗass,bakowa bace wannan fa ce Hayaam,fitowarta kenan daga ɗakinsu na hotel da Omar ya kama masu,Ashe tun ranar basu tafi ba,Zama suka cigaba dayi acikinshi sun ƙara biyan kuɗin ɗakin,don aunty babba taci alwashin cewa babu inda zasu tafi,daga abuja sai Enugu wurin bokan nan,Yanzu haka kuɗi suke harhaɗawa,duk ta siyar da gold ɗinta,yanzu ma shirye shiryen tafiya sukeyi,   Sakin baki haroon yayi yana kallonta,da wata irin kasalalliyar Murya yace"Ke!me kikeyi anan"!?   Cike da kwarkwasa Hayaam ta ƙarasa gabanshi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Kayi mamakin ganina ne?nikaina bansan da zamanka anan ba,yanzu kawai ina fitowa na ganka,kana ƙoƙarin fitowa daga ɗakinka,"    Lokaci guda haroon ya saki wannan shu'umin murmushin nashi,a wayance yace"Amma nadaina ganinki a gidanmu,nayi tsammanin cewa kin koma gidanku ne?but me kikeyi acikin hotel ɗin nan"?    Shiru ta danyi tana tunanin abunda zata faɗa mashi, Shi kuwa gogan gaba daya ya aza kwartayen idanuwan nan nashi akan Ƙirjinta,    "Naji kin yi shiru,idan ba damuwa mu shiga daga ciki mana,"yayi maganar yana nuna mata ƙopar daƙinshi,   Gaba yayi tabi bayanshi,buɗe masu ɗakin yayi suka shiga ciki,    A gefen gadonshi suka zauna,suna fuskantar juna,    "Kinyi kyau sosai,"yayi maganar yana wasa da harshen shi asaman la66ansa,   Murmushi hayaam tayi,batare da tace mashi komai ba,   "Ko kina buƙatar abunsha ne kona ci haka insa akawo maki"?   Girgiza kai tayi"a'a,a ƙoshe nake,bana jin yunwa,   ta6e bakinsa ya ɗanyi,kafin ya kuma cewa"Ƙamshin turarenki yayi mun,"   Dariya tayi tare da cewa"Allah ko"?   "Da zaki bani dama ko sau ɗaya ne,just inaso in ɗan shaƙi ƙamshinne a hancina,"    Batasan wanene haroon ba,saboda tasan halayen matasan gidansu,tayi tunanin cewa shima duk irinsu ne,hakan yasa tace mashi"Mezai hana,"   Matsawa yayi kusa da ita,tare da kai hancinshi saman fatar ƙirjinta,yana ɗan shinshinar ƙamshin turaren,nan take taji wani irin yanayi atattare da ita,zagayawa yayi da hannunshi ta bayan rigarta,abu kamar wasa,ya zuge zeep ɗin rigarta a hankali,saboda tafara fita hayyacinta,   ɗagowa yayi da hancinshi izuwa saman wuyanta kamar wani maye,haka ya shiga shinshina wuyan nata,da wata irin kasalalliyar murya yace,"Wannan turaren na wani company ne"     Shiru tayi batare da ta bashi amsar tambayarshi ba,dama da biyu yayi mata maganar don yaji idan har lokacin tana acikin hayyacinta,Shirun da tayi mashi ne ya tabbatar mashi da cewar,tafara fita hayyacinta,    Bata ankara ba,taji hannunshi ta cikin rigarta saman boobs ɗinta,A zabure ta kwace kanta daga jikinshi tare da ja da baya,tana ƙokarin gyara rigarta,ɗagowa tayi tana kallonshi,Murmushi ta gani akan fuskarshi,    Hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ma,duk a tunaninta mutumin kirki ne shi ashe shima ɗan harka ne,    Miƙewa tayi da sauri ta nufi hanyar fita daga ɗakin,Hannu tasa ta ruƙo kopar zata buɗe,taji ƙopar adatse,hakan yasa tayi saurin juyawa tare da kallonshi,Nuna mata key ɗin yayi a hannunshi yana dariya,    Fuskarta aɗan ɗaure tace"pls,ka buɗe mun kopa inaso na tafi,Aunty laila na jirana,"   Mikewa haroon yayi tare da takawa izuwa gabanta ya tsaya,sannan yace"Ganinki da nayi gaba daya kin tayarmun da sha'awata,na kwaɗaitu da son kasancewa tare dake,kallo ɗaya da nayi maki na gane cewa ke ba ƙaramar ƴar bariki bace,Don haka kada ki 6oye mun true colour ɗinki,kizo kawai muyi harka,"   Zuba mashi ido tayi tana tunanin ta wata hanya zata 6ullowa haroon don ta samu ta tsere mashi,bakomai take ji ma tsoro ba fa ce aunty babba,saboda ta hanata kula maza,'     "Koda ace ina kula maza,bazan kula irinka ba,Kuma ni ba ƴar iska bace kamar yadda kake tsammani,Ka buɗe mun kopa in fita,in ba haka ba zanyi maka illa,"a tsiwace tayi maganar hada rufe idanunta,   Dariya haroon yayi tare da sanya hannushi ya ɗaga wandon jikinshi,ya tura key din acikinsa,sannan yace mata"Zoki ɗauki key din idan kin isa,ƙaramar ƴar tasha kafin kiyimun illa ni zan illata ki idan har baki taimaki kanki ba"   Tsabar takaici ne ya cika hayaam,tayi danasanin yi mashi magana,da duk hakan bata faru 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina pls banda phone call just message ta whatsapp,08103884440❤_ *Aunty Babba* Guntun tsoki taja,yayin da idanunta ke kallon agogon dake manne acikin ɗakin,kusan ƙarfe 6 na marece babu hayaam babu alamarta,har ta fara gajiya da jiranta,tun ɗazu take traying numbar wayarta amma Still Switch off,hakan ba ƙaramin 6ata mata rai yayi ba,tunani tashiga yi ko ina ta shiga?daga zuwa curo kuɗi a banki shiru kake ji wai malam yaci shirwa, Ruƙe qugu tayi tare da yin ƙwafa,ta koma gefen gadon ta zauna,tana jiran shigowarta,tuntana sa ran dawowarta harta fara fidda rai,lokaci sai gudu yake yi har wurin ƙarfe 7,hayaam bata dawo ba,duk tana azaune har 8 ta buga, "Allah yasa ba gantalin nata ta tafi ba,daga zuwa curo kuɗi a banki kamar na aiketa wata uwa duniya,tabi duk ta rufe layinta,Mtsww"ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki, Yayin da aunty babba ke zaman jiran hayaam,ita kuma tana can rai hannun Allah a ɗakin haroon,Lokacin daya hanata fita daga ɗakin ya zura key a wondonshi yace ta taimaki kanta,tayi tsammanin cewa zata iya kwatar kanta saboda tasa ba gara sofwan saurayinta,hakan yasa cikin salon wayau ta zura hannunta acikin jakarta,batare da ya ankare ba,Ta curo kwalbar turare ta fesa mashi asaman fuskarshi,kai tsaye ya ta6a idanuwanshi,raɗaɗi yasa yayi saurin kai hannu yana murza idanun nashi,ganin ya fita hayyacinshi yasa tayi ƙoƙarin zura hannunta acikin wandonshi,aikuwa batayi wani aune ba yayi mata ƙwaƙƙwarar damƙa,Ya yayyaga kayan jikinta da hannunshi,tundaga tsaye ya fara biyan buƙatarshi da ita,cikin rashin imani haroon yayi mata kaca kaca,Karshe yayi wurgi da ita saman gadonshi,Ya tu6e kayan jikinshi kamar yadda ya cire nata gaba ɗaya,sannan yabi ya danneta kamar wani bakure haka yakai mata Hari,wa'iyazubillah duk yadda taso ta ƙwaci kanta amma hakan ya faskara,Tun tana ihu tana kuka har bakinta ya mutu ƙarshe ta sume....." *Boss Bature* ❤🤍❤ *SEHRISH* Wuraren ƙarfe 10 na dare,tana a kwance saman gadonsu,ta ƙudundune cikin bargo,bacci harya fara ɗaukarta,tajiyo ringing ɗin wayarta,a hankali ta zame bargon tare da miƙa hannu ta dauki wayar dake ajiye saman mattress din,daƙyar ta iya buɗe idanunta masu ɗauke da bacci,ƙurawa screen ɗin ido tayi yayin ta zuciyarta ke bugawa,Sunan My Boss Man ne ya bayyana da manyan haruffa,Gabanta ne yayi wani irin bugu rass!lokaci guda ta miƙe daga zaune tana faman zare ido,hannayenta har kerma sukeyi,Amsa kiran tayi tare da kara wayar a kunnata,Tunkafin tayi sallama Sexy voice ɗinshi ta katse mata hanzarinta da cewa"Am back,"yana faɗin hakan yayi rejecting call ɗin,    Yadda kasan gunki haka sehrish tayi kasaƙai,fuskarnan tamkar ta fashe da kuka,ɗan hutun da ta samu na kwana biyu ya ƙare,    Jiki asanyaye ta sauko daga saman gadon bayan tayi wurgi da wayar saman mattress ɗin,Sleeping dress ne ajikinta white colour masu ɗige ɗigen baƙi ajikinsu,sunyi matuƙar yi mata kyau,Riga da wando ne, Kaitsaye ta nufi wurin windown don ta leƙa taga idan dagaske ya dawo din,hannu tasa ta janye labulen tare da zuqe glass ɗinta,    daga inda take ta hango motorshi a parkin space,wannan ya tabbatar mata da cewar ya dawo yana a cikin gidan,hannu tasa tare da dafe goshinta a hankali ta furta"OMG!"   Gyaɗa kawai tayi tare da cewa"Ae shikenan,Za'a koma ƴar gidan jiya kenan,    Juyawa tayi ta nufi shoe rock ɗinsu,flat shoe ta ɗauko ta zura a ƙafafunta,sannan ta nufi hanyar fita daga ɗakin,buɗe kopar ɗakin tayi bayan ta fita ta datse ɗakin,    Fitowa tayi daga corridor din ta wuce kitchen,gidan tsit babu kowa,duk babu daɗi,tayi kewarsu sosai,musamman ɗan baby junaid ɗinsu,    Batasan ko zai buƙaci abinci ba,tun da yanzu ya dawo,Hakan yasa ta hado mashi Coffee kawai don tasan dole ya bukace shi,a cikin plate ta aza cup ɗin,ta fito daga kitchen ɗin,ta nufi upstairs,tunani tashiga yi ko ina su jahad suke,yanzu haka suna a ɗakin aunty azmee dama kwana biyun nan,duk in dare yayi suna zuwa fira ɗakinta,wani lokacin acan bacci yake ɗaukarsu,sae wurin asuba suke dawowa dakinsu,   A hankali take taka staircase ɗin harta haura sama,wuce wa part ɗinshi tayi,a baƙin kopar shiga falon ta tsaya,kamar yadda tasa ba,sae da fara karanta addu'o'in neman tsari daga sharrinshi sannan ta shiga ciki da sallama abakinta,   Babu kowa acikin falon,bedroom dinshi ta wuce zuciyarta na ɗar ɗar,sallama tayi mashi,daga ciki taji ya amsa mata,tare da bata Iznin shiga, Shiga cikin ɗakin tayi cike da fargabar ganin fuskarshi,agaban mirror ta same shi tsaye,yana sanye da bathrobe,jikinshi da alamun danshin ruwan da yayi wanka,bata samu damar ganin fuskarshi ba saboda ya juya mata baya,   Ƙarasawa ciki tayi tare da ajiye mashi coffee ɗin saman table sannan tace"Sannu da dawowa babban yaya ya gajiyar tafiya"?    Tamkar bazai amsa mata ba,har sai da ta fidda rai da zaiyi mata magana sannan yace"Am ok,"ɗaya daga cikin abunda ke ƙona mata rai kenan,Saita saki baki tayi mashi magana mai tsayi ya bata amsa in short,    "Ga coffee nan,bansan ko zaka buƙaci wani abu ba,bayan wannan,"     "No,need,"ya ambaci hakan tare da juyowa ya koma daga gefen gadon ya zauna,tsayawa tayi saboda tasan halinshi,in har bashi ya sallameta ba,toh bata isa ta tafi ba,    Ɗagowa tayi ahankali ta saci kallon fuskarshi,yayi haske sosai la66an nan nashi sunyi pink tamkar ya shafa jan baki,ya ɗaure fuskar tamau kamar wanda aka aiko ma saƙon mutuwa,    Mayar da idanuwanta tayi akan fatar ƙirjinshi,ganin yana ƙokarin dagowa yasa tayi saurin kawar da idonta gefe guda,      Hannu yasa tare da daukar Cup of coffee din,sae faman tiririn zafi yake yi,saitin bakinsa yakai cup ɗin a hankali yake kur6arshi,    ɗan dakatawa yayi da shan coffee ɗin batare da ya ɗago ya kalleta ba yace"Ɗaukomin sleeping dress ɗin da zan sanya,"   Amsa mashi tayi da toh,Sannan ta juya,kamar ance ya ɗago idonshi karaf ya sauka akan Wandon jikinta,ɗigon jinin daya gani ne yasa shi yin wurgi da Cup ɗin hannunshi ya faɗi ƙasa ya fashe,wani irin tashin zuciya ne yazo mashi,da gudun gaske ya mike tare da tunkarar toilet ya faɗa ciki,   Hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,batasan meyasa shi jin amai ba,ita dae kawai taga yayi wurgi da cup kuma ya nufi toilet,tuni tasha jinin jikinta,tsananin tsoro ne ya bayyana kan fuskarta,tunkafin ma taji meyasa shi yin amai,   Gaban Basin ya tsaya,sae faman kakarin amai yakeyi,tamakar ƴan hanjin Cikinshi zasu fito waje,Wani irin ƙyanƙyami ne dashi,gaba ɗaya duk yabi ya burkice,almost 8 mins yana acikin toilet ɗin,tanajiyo sautin aman da yake yi,zugudum tayi tana jiran fitowarshi,   Hannu yasa tare da buɗe ƙopar toilet ɗin ya fito,jikinshi sae kerma yake yi saboda tsabar 6acin rai,idanuwanshi har sun canza launi,    A zafafe ya tunkareta,ganin haka yasa sehrish tashi ga ƙoƙarin ja da baya,tana ƙoƙarin guduwa daga bedroom ɗin nashi, damƙo wuyan rigar jikinta yayi,tare da janyota yayi wurgi da ita,ta bugi bangon ɗakin,    Raɗaɗin da taji ne yasa ta fashe da matsanancin kuka,ware hannayensa yayi da nufin ya mare ta,runtse idanuwanta tayi da sauri tana kuka,   Yarfar da hannun yayi gefe guda,tsabar 6acin rai ya hana ya buɗe baki yayi mata magana balle har tasan laifin data aikata mashi,cikin shesshekar kuka tace"Dan Allah kayi haƙuri bansan laifin dana aikata maka ba,"     Tamkar ya rufe ta bugu haka yake ji,daƙyar ya iya buɗe baki yace"karki kuskura ki ƙara shigomin part ɗina da wannan ƙazantar a jikinki!ki tsaya har saikin kammala"   a ruɗe sehrish tashiga tunanin wata ƙazanta ce yake magana akai,da sauri ta shiga bin jikinta da kallo,a ƙoƙarinta nata gano abunda ya kira da ƙazanta, .  hakan ba ƙaramin fusata shi yayi ba,a fusace ya buga mata tsawa wadda tayi matuƙar girgizata,ta zaburar da ita kuma ta tsoratar da ita,Nan take taji zubar jini acan under ɗinta,tare da matsanancin ciwon mara lokaci guda ya farmata,Sae lokacin ta gane cewa period ɗinta ne yazo mata,jinin ne ya fara zuwa shiyasa batayi noticing ɗinshi ba,sae daga baya raɗaɗin ciwon ya taso mata,   Dogon tsoki yaja,tare da juyawa ya nufi cikin ɗakin,    Sehrish kuwa tuni ta soma fita hayyacinta,idanuwanta sunyi jawur da su,kamar daga sama yaji tace"AMMA BAKA DA IMANI"_    gabanshi ne ya faɗi rass,dakatawa yayi da yin tafiyar tamkar antokare shi,    "Tunda nake arayuwata banta6a ganin mutun mara imani mara tausayi ba irinka!Jinin daka gani ajikina lalura ce bani na ɗaurama kaina ba,nikaina bansan dashi ba,da bazan bari ya zuba ajikin kayana ba balle har ka gani,duk irin ƙoƙarin da nakeyi wurin ganin na faranta maka rai baka ta6a gani ba,Nifa ba tsoranka nake ji ba!Allah kaɗae nake tsoro,Idan taƙamarka ƙarfi kazo ka buge ni,kaga in zan mutu,Na rayu da wanda yafi ka rashin Imani da tausayi,Kuma na jure zama dashi,naga tashin hankalin daya fi wanda nagani a wurinka,kuma duk na jure hakan....."   Tashin hankali,Sanƙamewa sgr yayi atsaye,hankalinshi yayi matuƙar tashi,a arazane ya juyo don ya tabbatarwa kanshi da abunda kunnuwanshi ke juyo mashi,Jikinshi sae faman tsuma yakeyi,abun yayi matuƙar girgizashi,abun Yayi mugu mugun ɗaure mashi rai,Zuba mata ido yayi yana kallonta cike da mamaki,   "Dame ka ke taƙama ne?kaifa mutunne ɗan adam,mai hannu biyu mai ƙafa biyu,hancin ɗaya,da baki ɗaya,idanuwa guda biyu kamar nawa,Wanda idan yayi bacci sai yarda akayi dashi,idan ya mutu kuwa duk  kyanshi duk mun dukiyarshi duk ji dakanshi acikin farin yadi mafi arha za'ayi mashi sutura,ƙarshe ya zama abincin tsutsa,"    Waro ido waje sgr yayi hankali atashe yake kallonta,tunda yake arayuwarshi wata ƴa mace bata ta6a tsayawa agabanshi ba,kamar haka tana gaya mashi magana,Ido cikin ido batare da jin shakkarshi ba,yadda kasan mai iskokai haka sehrish ta rufe shi da faɗa,abun yayi matuƙar ɗaure mashi kai,har ya fara tunanin kodae Tasha ƙwaya ne?to ae ko wanda yasha ya bugi da giya bai ta6a kallon cikin idonshi ba ya gaya mashi magana,    "Burin ka kawai ka wulaƙanta rayuwata,shiyasa ka aure ni don in cigaba da aiki a ƙarƙashinka,Inayi maka biyayya ne ba don inajin tsoranka ba,kaima ka sani,ni ba baiwarka bace baiwar Allah ce,Kuma idan yau naga dama zan iya barin gidan nan,kuma baka isa ka dawo dani ba,dana so tuntuni wlh dana tafi nabar gidan nan,Ƴanci nane," .. Tana magana hawaye na shararowa asaman fuskarta,with confidence takeyin maganar,batare data girgixa ba,    "Zan tafi kuma kada kayi tunanin cewa idan na kammala ƙazantar zan dawo part ɗinka da sunan aiki,Bazan ƙara zuwa ba,kuma kada kayi tunanin cewa zanji tsoranka in gudu daga gidan nan ko inzo in baka haƙuri,Wlh bazan ta6a karaya ba,ka yi duk abunda kaga dama,ƙarshe kace zaka hukuntani ko,Idan ka tashi dan Allah kada kabarni da raina,ka kashe ni,"   Ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki,a fusace ta juya tabar cikin bedroom ɗin nashi,    Sai lokacin sgr ya runtse idanunshi,la66ansa sae kerma sukeyi kaf kaf,saboda tsabar 6acin rai,Hannunshi ya cusa acikin sumar kanshi ya shiga cakuɗata,gaba ɗaya ya hargitsar da gashin kan nashi,Cizon la66ansa ya shiga yi,nan take le6en ya fashe jini ya soma ɗiɗɗigowa daga jikinsu,Zuciyarshi har wani boiling take tana burning,wani irin zafi ne ya taso mashi gadan gadan,jiri ya dinga gani acikin idanunshi harya fara tangal tangal zai faɗi ƙasa,   Daƙyar ya iya takawa izuwa gafen gadonshi ya zube ƙasa saman guiwowinshi tare da aza kanshi saman gadon,Tashin hankali Ran manya ya 6aci sosai,ƙoƙari yakeyi ya dakatar da bad temper ɗinshi saboda gudun karya aikata kisan kai,don muddin yakai matakin ƙarshe zaibi bayanta ne kuma sai yayi mata mummunar illa,   A hankali ya shiga furta"Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un"!ya ambaci hakan kusan sau talatin, Sehrish kuwa bayan ta fita daga part ɗinshi,daƙyar take ɗaga ƙafafunta saboda matsanancin ciwon marar da takeyi,Gaba ɗaya duk wannan maganganun da ta gaya ma Sgr ba'a cikin hayyacinta tayi su ba,batasan ma ta furta mashi su ba,Zafin raɗaɗin ciwo ne yasa ta zazzaga mashi masifa,dama kuma a ƙule take dashi saboda ya ƙuntata mata sosai,kuma ya kira jinin da takeyi da ƙazanta abun yayi matuƙar ƙona mata rai,hada ƙarin hakan yasa ta balbaleshi da faɗa, Tun tana tafiya da ƙafafunta har suka gaza ɗaukarta,ƙarshe a bakin shiga corridor ɗin ɗakinsu,ta yanke jiki ta faɗi ƙasa saman tiles tana birgima,hannunta dafe da mararta,gashi babu wani a kusa balle ya kawo mata agaji, Kamar yadda sehrish ta kwana waje saman tiles,haka sgr ya kwana zuƙunne saman guiwowinsa,kanshi na asaman gadonshi,Aranar bai runtsa ba,bacci ya ƙauracewa idanuwanshi, Wuraren sallar asuba,Jahad ta fito daga ɗakin azmee tana ƙoƙarin shiga bedroom ɗinsu,idonta suka sauka akan sehrish dake kwance a ƙasa,gashin kanta duk ya rufe fuskarta,da ƙarfi ta ambaci Sunanta SEHRISH,da gudun gaske ta ƙarasa tare da zubewa saman guiwowinta agaban sehrish ɗin,   "Innalallahi'wa'innalairrahiji un,Sehrish!meya faru dake ne!nashiga uku!Aunty Azmee!!!"duk tabi ta ruɗe,musamman data ga jini ya 6ata wandon sehrish ɗin,sai tayi tsammanin kodai taji wani mummunan rauni ne,Jijjiga jikinta tashiga yi tana cigaba da kwalama Azmee kira,    "Aunty azmee!Hosana!dan Allah kuzo ku dubamin!meya faru da sehrish ne!"    A ruɗe ta miƙe tare da tunkarar ɗakin azmee,tura ƙopar tayi ta faɗa ciki a hargitse,Adai dai lokacin Azmee ta kammala sallar asuba,juyowa tayi tana kallon jahad ganin hawaye asaman fuskarta yasa ta miƙe da sauri ta tunkareta tana tambayarta    "Jahad lafiya meya faru ne"   Muryarta har shaƙewa takeyi wurin ambaton sunan sehrish"Aunty azmee sehrish!bansan meya faru da ita ba,gata can kwance a ƙasa bata motsi,ga jini a jikin wandonta....."tunkan taƙarasa maganar Azmee ta zabura da gudu ta fita daga ɗakin,itama jahad ɗin tabi bayanta da sauri,   Ƙarasawa azmee tayi wurin da sehrish take akwance,ta zuƙunna tana ƙare ma jikinta kallo,tsananin tausayinta ne ya kamata,Allah kaɗae yasan tun yaushe take kwance a wurin cikin halin ha'ula'e,    Hannu tasa tare da shafa fuskarta,busassun hawayene asaman fuskarta,la66anta duk sun bushe ƙamas dasu, ɗagowa tayi tare da kallon jahad dake tsaye tana kuka,    "Ki kwantar da hankalin ki,ina tunanin suma tayi ne sakamakon Ciwon cikin da tayi,Jinin dake ajikinta na al'ada ne,"   Jin haka yasa jahad ta tsagaita da yin kukan,har hankalinta ya ɗan kwanta duk da akwai sauran damuwa atattare da ita,   "Aunty azmee duk laifin mu ne ni da hosana,da ace bamu tafi mun barta a ɗaki ita kaɗai ba,da duk hakan bata faru ba,Allah kaɗae yasan tun yaushe take kwance a wurin nan,"    "ɗaukomin ruwa,in yayyafa mata," Da sauri jahad ta nufi fridge dinsu,hannunta har kerma yakeyi wurin yin saurin ta buɗe,bottle water ta ɗauko,sannan ta dawo wurin azmee ta miƙa mata,kar6a tayi ta 6alle murfin ta ɗan kur6i ruwan abakinta sannan ta fesar dashi asaman fuskar sehrish,   Dogon Numfashi taja,tare da sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya,muryarta ƙasa ƙasa tashiga fadin"Cikina zafi,Ciwo yakeyi mun!dan Allah abani magani nasha,kada na mutu,"   "Jahad dauko mata magani,yana nan ajiye saman drawer ɗina,"juya jahad tayi da gudu ta nufi ɗakin azmee,     Hannu azmee tasa tare da ɗago da kan sehrish ta azata asaman laps ɗinta,kafa mata ruwan tayi abakinta,a hankali tashiga kwankwaɗar ruwan,dama makoshinta a bushe yake,    Dawowa jahad tayi hannunta ɗauke da maganin ta miƙa ma Azmee, bayan ta kar6a ta curo mata shi guda biyu ta sanya mata abakinta,tare da ruwan ta haɗiya,   Bayan ta kammala sha,ta mika ma jahad robar ruwan"ki mayar dashi a fridge,bari na taimakata mu shiga daga ciki,"    Dakyar ta cuccu6i sehrish,don ma ba wani nauyi ne da ita ba,cikin bedroom ɗin nasu ta shiga da ita,Jahad tabi bayansu,   Toilet tashiga da ita,jahad sae faman zirga zirga take yi acikin bedroom ɗin nasu,duk wannan budurin da akeyi hosana nacan ɗakin azmee naɗe cikin bargo tana bacci,    Muryar azmee tajiyo daga cikin toilet ɗin tana yi mata magana"Pad zaki miko mun,tare da pant ɗinta,"_   Jiki na rawa jahad,ta ƙarasa gaban wardrobe ɗinsu,wurin kayan sehrish ta ɗauko mata pant,sannan ta haɗo mata tare da pads,    Abakin ƙopar toilet din ta tsaya tare da ɗan knocking kopar,zuro hannu azmee tayi ta kar6i kayan,   Komawa jahad tayi saman gadonsu,ta zauna tana jiran fitowarsu daga cikin toilet ɗin,   Within mins,Azmee ta fito daga cikin toilet ɗin,hannunta dafe da sehrish,duk ta rurruketa gudun karta faɗi,Waist dinta na ɗaure da farin towel,sae faman cizon la66anta takeyi,saboda raɗaɗin da take ji har lokacin bata dawo cikin hayyacinta ba,   Asaman bed ɗinsu Azmee ta kwantar da ita,jahad ta yafa mata bargo asaman jikinta ta lullu6eta,   "Sannu sehrish,Allah ya baki lafiya," acewar jahad,    Dama ance ciwon ƴa mace na ƴa mace ne,su da suka son zafin abun gashinan sun taimaka mata,saboda suma sunayi kuma sunsan cewa lalurace,sannan sunsan irin raɗaɗin da takeji ajikinta,dayawa Wasu mazan basu son ya abun yake ba,tunda bayi sukeyi ba,shiyasa har suke ganinshi amatsayin ƙazanta,kuma basu yi ma mata uziri,aduk lokacin da sukayi kuskuren da jini ya bayyana ajikinsu,Wasu mazan nake nufi ba duka aka taru aka zama ɗaya ba,Haka matan ba,bakowa bace ke taimakon ƴar uwarta ba,acikin irin wannan yanayin na period,    "Sannu Allah ya baki lafiya,"azmee ce tayi maganar,yayin da idanuwanta ke akan sehrish,wadda ta runtse idanunta tana ta faman ciccije la66anta,    Bata bar ɗakin nasu ba,har saida bacci ya ɗauki sehrish sannan tayi masu sallama,   Kwanciya jahad tayi agafenta,suna fuskantar juna,zuba mata ido tayi tana kallonta,cike da so da ƙauna,    A haka har bacci ya dauketa, A 6angaren Sgr kuwa,ko sallar asuba bai samu ya halarta ba,Acikin bedroom ɗinshi yayi sallar,komawa yayi saman katafaren gadonshi ya kwanta yayin da blue eyes dinshi ke kallon Ceilling,Kalaman sehrish ne suka shiga dawo mashi acikin zuciyarshi,bakomai ne yafi tsaya mashi aranshi ba fa ce kalmomin nan guda biyu da ta kirashi dasu,MARA TAUSAYI MARA IMANI!sannan kuma tayi comparing ɗinshi da wannan fasiƙin mutumin, yaji raɗaɗin abun sosai acikin zuciyarshi,tayi matuƙar ɗaure mashi kai,Ko a ina tasamu ƙwarin guiwar gaya mashi magana?duk irin yadda take jin shakkarshi?yarinyar da ko cikin idonshi tsoran kallo takeyi,balle har ta ɗaga mashi yatsa,     Gyara kwanciyarshi yayi,ya koma yana fuskantar right hand ɗinshi,sannu a hankali bacci ya dauke shi batare da ya shirya yin shi ba,   Wuraren ƙarfe Takwas na safe,jahad na cikin bacci,taji shessheƙar kuka acikin kunnuwanta,buɗe idanuwanta tayi tare da wurgasu wurin da take jin sautin kukan,Sehrish ta gani zaune ta jingina bayanta a head board ɗin gadon,sae kuka takeyi kamar wadda ta rasa wani mai mahimmanci arayuwarta,   Da sauri jahad ta miƙe zaune,tana kallonta tace"Sehrish!lafiya kike kuka?ko haryanzu ciwon cikin ne"?   Girgiza kanta tayi alamar a'a, "To ki faɗamun meke damunki ne"?da damuwa a fuskarta tayi maganar,   Cikin shesshekar kuka Sehrish ta soma magana,    "Jahad!na shiga uku!najama kaina bala'e,Jiya nayi ma babban yayanmu rashin kunya,batare da sanina ba,wlh sai yau da safe na tuna duk abunda ya faru,nasan cewa bazai ƙyaleni ba,Dole ya hukunta ni"ta karasa maganar tare da sa hannu tana matsar hancinta,   Hankali atashe jahad tace"Sehrish!kodai mafarki kikayi ne?ae babban yayanmu bai dawo ba,kin manta sun tafi damaturu ne"?tayi maganar tana ƙoƙarin fahimtar da ita,   "Wlh jahad ba mafarki nayi ba,jiya ya dawo acikin gidan nan,yana nan a part dinsa,"    Hannu jahad tasa tare da dafe saitin zuciyarta adan tsorace tace"Munshiga Uku!garin yaya har kikayi mashi rashin kunya?kuma kina acikin hayyacinki babu magagin bacci atare dake"?   "Bana acikin hayyacina jahad,zafin ciwone yasa na balbaleshi da masifa,har ina nuna shi da yatsa..."kaf ta kwashe duk abunda ya faru a tsakaninsu ta sanar ma jahad,    Hannu jahad tashiga tafawa tana faɗin"wlh babu ruwana!sehrish kin shiga uku,mai kwatarki a hannunshi yau sai Allah,hukuncinki yafi ƙarfin ayi maki shi acikin gidan nan sai dai yakai ki can headquater dinsu," Jin wannan maganar,ya ƙara ɗaga hankalinta,fashewa ta kuma yi da kuka,   Lallashinta jahad ta shiga yi"Am sorry,zolayarki nakeyi,amma gaskiya sehrish Anya baki sha Codine ba?Yo ni ko giyar wake nasha,ae bazan iya tunkarar babban yayanmu ba,balle har in gaya mashi irin zafafa kalaman da kika yada mashi,"    Cikin shesshekar kuka tace"dan Allah jahad ki bani shawara,kodai in gudu in bar gidanne?kinga su daddy basu nan,zai iya kashe ni,"    Shiru jahad tayi tana saƙa wani abu aranta,sehrish kuwa ta zuba mata ido tana jiran jin shawarar da zata bata,   "Kinsan me!kada ki kuskura kije bashi haƙuri,Dama kin faɗa mashi cewa kada yayi tunanin zaki gudu kibar gidan ne,ko kuma zaki zo bashi hakuri,Sannan kuma kince mashi ba zaki ƙara zuwa part dinshi ba koda ace kin kammala ƙazantar ne,Inaso ya tabbatar da cewar dagaske kike mashi bada wasa ba,hakan zaisa abun ya tsaya mashi acikin ranshi kuma zaiji shakkar ƙara faɗa maki irin waɗannan kalaman saboda gudun kar girmanshi ya faɗi,sannan idan yaga kwana biyu baki je yi mashi aiki ba,ina da tabbacin cewar zai nemeki ne,Amma muddin kika je bashi hakuri,wlh sai kinyi danasani ne,"   "Amma jahad,rashin kunya fa nayi mashi,yakamata na bashi hakuri in ba haka ba Zai gane cewa ina acikin hayyacina na gaya mashi magana,kuma zai dinga yi mun kallon mara kunya ƙarshe ma ya tsane ni gaba daya,"   Murmushi jahad tayi tare da cewa"indai bazai ta6a lafiyar jikinka ba toh da sauki,ƙwara yayi maki kallon mara kunyar,akan dai kije bashi haƙuri,nasan bazaki fahimce ni ba,A yanzu amma nan gaba zaki ga amfanin yin hakan da kikayi,"_   Zugudum sehrish tayi tana doubting akan abunda jahad ta faɗa mata,Anya kuwa jahad ba hanyar banza takeson ɗaurata ba?in ba haka ba saboda me zata hana ta zuwa bashi haƙuri,bayan itace mai laifi,A matsayin shi na mijinta kuma yayanta,bai kamata tayi mashi hakan ba,sannan kuma taƙi zuwa bashi hakuri, Shigowar azmee ne ya katse mata zancen zucin nata,atare suka juya suna kallonta,    "An kammala breakfast,yana a dining yana jiranku,"   Ta karasa maganar tare da kai idanunta kan sehrish tace"Ya jikin naki"? "da sauƙi alhamdullah,nagode ssai da irin kulawar da kuka bani,"   "Kada ki damu ae duk yiwa kaine,Amma naga kamar hawaye akan fuskarki,Ko haryanzu akwai ciwon ne"?   "A'a,naji sauƙi sosai," Murmushi azmee ta saki,kafin ta juya ta fuce daga ɗakin,    "Jahad kije kawai kuyi breakfast ɗin,Ni zan zauna a ɗakine,kada mu haɗu da babban yaya,Don nasan bazaiyi mun da kyau ba,"     "kada kisa damuwa aranki mana,duk kin bi kin tashi hankalin ki,Da yunwa zakiyi ta zama ne?bazaki ci komai ba"?    Shiru tayi ba tare da tace komai ba,   "Okey,zan kawo maki breakfast ɗin aɗaki sai kici hakan yayi maki"?   Ɗaga mata kai sehrish tayi"Eh,ki kawomin anan,zan fi samun kwanciyar hankali,akan in fita wajen,"   Saukowa jahad tayi daga saman gadon,ta buɗe kopa ta fuce daga dakin,   Ajiyar zuciya sehrish ta sauke,tunani ta shiga yi ko a wani hali babban yaya yake ciki,Yayi bacci jiya ko baiyi ba,Allah yasa dai kalamanta basu ta6a mashi zuciyarshi ba, shigowa jahad ta kumayi hannunta ɗauke da madaidaicin tray,kayan tea ne sai chips da sauran abunda baza a rasa ba,Asaman drawer ta ajiye mata shi,sannan ta juya ta fuce daga ɗakin,   Matsawa tayi kusa da trayn,sannan takai hannu ta ɗauki cup of tea ɗin tana ɗan kur6arshi,    Cikin ƙankanin lokaci ta kammala yin breakfast ɗin nata,    Zama tayi cike da fargabar abunda zai biyo baya,    Ranta ne ya bata cewar,ta jaraba kiran aunty azeema ta sanar da ita abunda ya faru atsakaninta da sgr,may be ta samu shawara mai kyau a wurinta,   Da sauri ta ɗauki wayarta dake ajiye saman gadon,contact ta shiga ta lalubo numbarta,ta danna mata kira,tana fara ringing,Azeema ta ɗaga kiran nata,   Tunkafin tafara magana hajiya azeema tace"2 days ba hello ba hi ko?har kin fara mantawa dani ko,"   Murmushi sehrish tayi tare da cewa"ba haka bane,Aunty azeema kusan kullum ne saina nemi layinki,amma baya shiga,"   Azeema tace"Hakane fa,nifa wayata indai bani na kira mutun ba,da wuya ne a same shi,kullum busy nake,"   Shiru sehrish tayi tana tunanin ta ina zata fara kora mata jawabi,   "Ina sauraronki,Har yanzu ba wani cigaba a zamanki dashi"?_    Nan fa sehrish ta samu ƙwarin guiwar sanar da ita duk abunda ya faru atsakaninsu daren jiya,   Tayi tunanin aunty azeema zatayi mata faɗa ne,amma da buɗar bakinta sai cewa tayi"Very Good!hakan da kikayi mashi yayi mun dai dai wlh,"    Sakin baki sehrish tayi tamkar tana agabanta,kusan bakinsu ɗaya da jahad,   "Kada ki kuskura kije bashi haƙuri!nafi so ya gasgata kalamanki"   Cike da mamaki sehrish tace"Aunty azeema dagaske kike?kada na bashi haƙuri"?   "Ƙwarai kuwa,ina goyon bayan hakan ɗari bisa ɗari,kuma kada ki kuskura kije part dinshi da sunan aiki,Ki rabu dashi,dama ae yace kada ki koma mashi har saikin kammala kazantar kibarshi a hakan,kada ki wani ji tsoro,"   Lumshe ido sehrish tayi tare da ware su fuskarta da dan murmushi tace"Shikenan aunty azeema bazanje ba in sha Allah,"   "Namanta ban sanar dake ba,nafa dawo nigeria,tun jiya amma na wuce damaturu,bazan samu zuwa nan ba yanzu saboda abunda ya faru na rasuwar modibbo,amma kada ki damu zan bada saƙo ta wurin junaid,naji yace zai biyo Abusufyan idan ya tashi dawowa,zan bashi ya kawo maki har gida,Sannan zanyi maki bayanin yadda zakiyi amfani dasu,koda ta wayane,"    "Nagode sosai Aunty azeema,Allah yasaka da alkhairi,Amma yaushe zaki dawo nan?don nayi kewarki sosai,"   Dariya hajiya azeema tayi tare da cewa"Very soon zan dawo,"   Sehrish tace"to shikenan,Allah ya kaimu lokacin," "Ameen my daughter,"   Sun jima suna waya kafin daga bisani ta ajiye wayar,har hankalinta ya kwanta,duk da akwai sauran fargaba atare da ita, saukowa tayi daga saman gadon,Wardrobe ta nufa,hannu tasa ta buɗe,Arab gown ce ta ɗauko pink colour,tare da mayafinta shima pink ne amma bai ciza ba,kamar na rigar,zura kayan tayi ajikinta,sannan ta koma gaban mirror ta zauna,zuba ma mirror din ido tayi tana kallon fuskarta,ta cikin madubin,yayin da zuciyarta ke tariyo mata abunda ya faru adaren jiya, A 6angaren Sgr kuwa,wata irin matsiyaciyar yunwa ce ta farkar dashi daga bacci,saukowa yayi daga saman gadon,Jallabiya ce ajikinshi,wuce wa yayi wurin closet ɗinshi,withins mins ya shirya kanshi cikin jeans da t shirt Maroon colour,rigar ta fito da surar jikinshi saboda ta ɗanyi tighting ɗinshi,Ƙafarshi na sanye cikin Canvas sneakers,    fitowa yayi daga part ɗinsa,Ya nufi downatairs,a natse yake taka staircase din har ya sauko down,Su jahad na zaune ita da hosana saman Sofa mai mazaunin mutun uku,suka jiyo takun takalmanshi,   ɗagowa sukayi atare suna kallonshi,lokacin da ya ƙaraso wurinsu,da sauri suka haɗa baki wurin gaisar dashi,   Batare daya kallesu ba,Ya amsa masu gaisuwarta su,fuce wa yayi daga cikin main palour ɗin,Kaitsaye Motarshi ya nufa,Amstrong na ganin shi da sauri ya ƙarasa tare da buɗe mashi motar ya shiga daga ciki,sannan shima ya bude driver seat ya zauna,    Kafin ya tashi motar,ya ɗan dago tare da kallonshi ta cikon mirror yace"Sir,Where are we going"?    "Restaurant,"ya bashi amsa atakaice,     Shiru amstrong yayi batare daya tashi motar ba,Hakan yasa shi cewa"what are u waiting for"?   Cikin harshen turanci amstrong yace"Sir,kayi haƙuri da abunda zance,Amma zuwa restaurant ba naka bane,da matsayinka aganka a restaurant ka je cin abinci?kaida ya kamata ace a gida ake girka maka,idan ba damuwa zanje nakawo maka,ka koma ciki pls"    Tunda ya soma magana sgr yayi shiru yana sauraronshi,saboda amstrong yana ɗaya daga cikin waɗanda suke Control dinshi,"   Amsa mashi yayi da okey,sannan ya buɗe motar ya fuce,   Duk wannan abun dake faruwa sehrish na tsaye a wurin window tana leƙen motarshi,taga lokacin daya shiga cikin motar,kuma sai taga ya fito daga ciki,   Aranta tashiga tunanin ko lafiya, Dawowa cikin gidan yayi,Part ɗinshi ya koma ya zauna saman sofa yana jiran dawowar Amstrong,dan bala'e ga abinci acikin gidan amma yafi ƙarfin yayi ma wani magana ya kawo mashi abincin,tunda ya ƙori mai aikin tashi,   Cikin minti goma sha biyar,Amstrong ya shigo cikin gidan hannunshi dauke da ledojin,Su jahad na ganinshi suka shiga gaisar dashi,fuskarshi ɗauke da murmushi ya amsa mashi,sannan ya wuce upstairs sashen sgr,   Yana barin wurin da gudu jahad ta nufi ɗakinsu,tura kopar tayi ta shiga ciki tana faman ƙwala ma sehrish kira,    tsaye ta same ta hannunta ruke da wayarta,ganin jahad ta faɗo ɗakin babu sallama yasa tace"Lafiya"?    Jahad tace"Yanzu naga wannan sojan wanda yake yin driving ɗin babban yayanmu,Hannunshi dauke da ledojin kuma na restaurant ne don naga sunan ajiki,"    Cike da mamaki sehrish tace"to fa!ko meyasa ya aika akawo mashi abinci bayan ga wanda aka girka agida"?   Jahad tace"Yanzu haka saboda abunda ya faru atsakaninku ne jiya,shiyasa yaƙi cin abincin gidan,"    Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,    "Yanzu haka,saboda yana ƙyamar girkina ne saboda ina yin period,shiyasa bazaici abincin gidan ba,"acewar sehrish,   Jahad tace"Amma ae bake kikayi girkin ba,Aunty azmee ce ta girka,Gaskiya nafi tunanin cewa wani abunne daban yasa bazaici abincin gidan nan ba,"    Murmushi sehrish ta ɗanyi tare da cewa"kinsan Allah babban yaya bazai iya cin abincin nan ba,Ina nan dake ƙarshe sai dai azubar da shi abanza"      Jahad tace"Mu zuba ido mu gani,zaici ko bazaici ba," *** Excuse sir!muryar amstrong ce ta dawo dashi daga zurfin tunanin da ya faɗa,    Muryarshi a kasalance yace mashi"Come in,"   Shiga ciki yayi tare da ajiye mashi asaman table dinshi,Sannan ya sara mashi,kafin ya fuce daga ɗakin,     Kusan minti 5 bai motsa ba,kamar ba yunwa yake ji ba,Hannu yasa tare da curo bugger daga ciki,yana ƙokarin kaita a bakinshi ,Ya tuna da jinin daya gani ajikin wandon sehrish,aikuwa nan take Ya sake ta ta faɗi saman table din,Wani irin yunƙurin amai ne ya taso mashi,da sauri ya miƙe ya nufi cikin toilet,ya shiga kwara amai agaban basin,Ba ƙaramin galabaita yayi ba,ƙyanƘyami ya hana yaci abincin ga yunwa na cinshi,har zazza6i ya fara kamashi, Tap ya kunna ruwa ya shiga kwararowa,tarba hannayenshi yayi ya shiga kuskure bakinsa,kafin ya wanke face ɗinshi,    Fitowa yayi daga cikin toilet,yana faman sauke ajiyar zuciya,komawa yayi saman gadonshi ya kwanta,wasa wasa Zazza6i ya rufe shi,temperature ɗin jikinshi yayi zafi sosai, Kasa samun natsuwa sehrish tayi,tunda taga an kira sallar magrib da isha'e,sgr bai fito daga part ɗinsa ba,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankalinta yayi ba,jiki na rawa ta fito daga ɗakinsu ta wuce kitchen,Anan ta samu azmee tana ƙarasa gyara kitchen din ita da hosana, Ganinta yasa azmee tace"Ya jikin naki"? "Da sauƙi aunty azmee,sai dai...."shiru ta ɗanyi bata ƙarasa maganar ba, Tunkarota azmee tayi tare da ruƙo hannunta suka ja daga gefe sannan tashiga tambayarta meya faru, "Aunty azmee,wani abu ya faru jiya tsakanina da babban yaya ban sanar maki ba," "Faɗamun meya faru,Allah yasa dae ba wani laifin kika aikata masa ba," Nan sehrish ta kwashe duk abunda ya faru ta sanar mata, "Ya salaam,' azmee ta ambaci hakan hankalinta aɗan tashe tayi maganar, "Wlh aunty azmee ba laifina bane,bana acikin hayyacina ne,shiyasa nayi mashi rashin kunya," Muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar, Cigaba da magana tayi"Ni babban abunda yafi tayar mun da hankali,har aka kammala sallar magrib da isha'e,banga ya fito daga cikin part dinshi ba,kuma inajin tsoran in tunkare shi,saboda nasan dole ya hukunta ni,kuma nayi shawara da aunty azeema tace kada na kuskura naje bashi haƙuri,haka jahad ma tace mun," "Sehrish idan kikace zaki ɗauki shawarar Azeema,zata kaiki ta baroki ne,saboda ita wata irin wayayyiyar maca ce,Bazan hana ki ɗauki shawararta ba,amma inaso ki tuna matsayinshi a wurinki,Yayanki ne shi kuma Mijinki,jiya ya kwana da fushinki acikin zuciyarshi haka yauma ya tashi da fushinki,tabbas zaki jefa kanki cikin matsala ne,in har bakiyi hanzarin neman afuwarsa ba,Yakamata kije ki bashi haƙuri,kuma ki sanar dashi cewa ba a hayyacinki kike ba!" . "yanzu aunty azmee kina nufin inje in bashi haƙuri"? "Eh,haka nake nufi," "Amma fa yace mun kada na kuskura na ƙara zuwa part ɗinshi har saina kammala period ɗina," "Kada ki damu da wannan kije kawai,in sha Allah babu abunda zai faru," Tashin hankalin da ba'a sama shi date,Shin shawarar wa kuke tunanin zatayi ma sehrish amfani?Shawarar Azeema da Jahad,ko kuwa shawarar Aunty Azmee,  💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana ta whatsapp dan Allah banda kiran wayar,bana ɗagawa 08103884440❤_ Nagode da shawararki Aunty azmee,in sha Allah zanyi amfani da ita"    "Yawwa haka nake son ji" azmee tayi maganar tare da komawa cikin kitchen,Sehrish kuwa bata wuce part ɗinshi ba,bedroom ɗinsu ta wuce,sam takasa samun natsuwa,ta rasa shawarar wa zata ɗauka acikinsu,bakomai yafi sata fargaba ba,fa ce abunda zai biyo baya idan tayi kuskuren zuwa sashen shi, Har wuraren ƙarfe goma sha biyu na dare bata runtsa ba,tana zaune saman gadon nasu,yayin da wayarta ke ruƙe a hannunta,Hosana na kwance a gefenta tana bacci cikin bargo hankalinta kwance,Jahad kuma na can ɗakin azmee,    Wani tunani ne yazo mata acikin zuciyarta,da sauri ta shiga contacts ta lalubo layin Aunty azeema,ta danna mata kira,cikin sa'a ta ɗaga kiran nata,   Kara wayar tayi a kunnanta,tare da yi mata sallama,    "Assalamu Alaikum," Aunty azeema tace"Wa'alaikum salam daughter,me kikeyi har yanzu baki yi bacci ba,"?    "Na kasa yin bacci ne,ina cikin damuwa"acewar Sehrish,   Azeema tace"kodai duk fargabar babban yayan naku ne? "Ba haka bane,Aunty azeema,na ɗan shiga damuwa ne,yau babban yaya bai fito daga part ɗinshi ba,har akayi sallar La'asar da magrib,bai fito ba,"   Maganar sehrish ta ɗan tashi hankalin hajiya azeema,   "Amma ya ci abinci kuwa"? Sehrish tace"baici abincin gida ba,ɗazu dai yasa an kawo mashi abincin restaurant,amma bani da masaniya akan yaci ko bai ci ba,"   Shiru hajiya azeema tayi na wani dan lokaci,haka itama sehrish ɗin,Kowa da abunda yake saƙawa aranshi,   "Kina jina"muryar hajiya azeema ce ta katse mata zancen zucin da ta shiga,   "Ina sauraronki Aunty," "Gaskiya akwai matsala,saboda ba ƙaramin abu bane zai hana Sgr zuwa masallaci ba,Ina da tabbacin cewa zuciyarshi ta motsa,Allah kaɗae yasan halin da yake ciki,gashi babu kowa agidan idan baku ba,dama ace su Abbanku suna nan ne ko Omar zasu iya shawo kan matsalar,Amma yanzu haɗari ne wani ya tunkare shi,tunda ba'asan halin da yake ciki ba,wani irin zafin zuciyane dashi idan ya fusata kowa tsoran tunkararshi yake yi,Amma idan akaci sa'a,Ya yanke jiki ya faɗi ya suma a lokacin da zuciyar tashi ta motsa,to tabbas koda ya farfaɗo bazai tashi da wannan fushin ba......"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar,tana sauke ajiyar zuciya,   "Yanzu ya zamuyi kenan"?sehrish ta tambaya,fuskarta dauke da damuwa,   "Abunda za'ae yanzu shine,inaso kije part ɗin nashi kiga a wani hali yake ciki,Amma fa kada ki bari ya ganki,a 6oye zaki je,in ba haka ba a tsinto ƙasusuwanki a dakinshi,"ta karasa maganar cike da zolaya,   Dariya sehrish ta dan yi duk da tsoron daya kamata,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Shikenan Aunty azeema,zanje in sha Allah,"   Azeema tace"yawwa daughter,idan kin dawo duk abunda ya faru ki sanar dani pls,"   "Toh Aunty," Daga nan sukayi sallama,saukowa daga saman gadon Sehrish tayi,bayan ta ajiye wayar saman side drawer,ta zura slipper ɗinta dake ajiye nan ƙasan,ta gyara mayafin jikinta sannan ta fito daga dakin nasu,   Tunkafin ma ta hau upstairs din gabanta ke faɗuwa rass rasss,tamkar wadda zata tunkari wani zombie, A hankali take taka staircase ɗin harta samu ta haura sama,tana tafiya tana ambaton"La'ilah ha illa antas subhanaka inni kuntu minazzalimin,"har tazo bakin ƙopar part dinshi,kamar wata 6arauniya haka ta leƙa cikin falon,ganin baya ciki yasa ta sauke ajiyar zuciya,cikin sanɗa ta zura ƙafarta ciki,a hankali take tafiya,gudun kada yaji sautin takalminta yasa ta zuƙunna tare da ciresu ta ruƙesu a hannunta, A ƙopar bedroom ɗinshi ta tsaya,har lokacin bata daina ambaton La'ila ha illah anta subhanala inni kuntu minazzalimin,acikin zuciyarta ba,saboda tsabar tsoro,zuciyarta tamkar zata fito daga ƙirjinta,saboda bugun da take yi mata,daraam!daraaam,     A hankali ta ɗan zura kanta tare da leƙawa cikin ɗakin nashi,   Kwance yake saman gadon,gangar jikin na asaman gadon,yayin da head ɗinsa zuwa wuyanshi suka zuro daga gefen gadon,Sumar kanshi ta zubo har saman floor,   Gabanta ne ya faɗi rasss!tun daga kan yadda yayi kwanciyar ta gane cewa babu lafiya,gaba ɗaya zufa ta wanke jikinshi tamkar wanda ya watsa ruwa ajikinshi,ta ko'ina zufar ke tsastsafo mashi,gaba ɗaya ga66an jikinshi sun sake,    Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,batasan ko bacci yake yi ba,ko suma yayi,Allah wa'alamu,    Zura ƙafarta tayi yayin da gabanta ke ci gaba da faduwa,Shiga cikin bedroom ɗin tayi,har zuwa wurin gadon nashi,Yanayin kwanciyar tashi ma,Zata iya haifar mashi da matsanancin ciwon wuya,saboda yadda ya yi sadda kai,     Zuba mashi ido tayi tana kallon fuskarshi,daga gani ba ƙaramin jiki yaji ba,    Tunani ta shiga yi,kodai ta ɗaukko ruwa ta yayyafa mashi,duk da bata da tabbacin cewar ko suman yayi ne,amma ga dukkan alamu ya suma ne......  ,   Da sauri ta juya ta koma palour,fridge ta nufa da sauri sauri ta buɗe shi ta ɗauko robar ruwa,Sannan ta dawo cikin ɗakin nashi,Tashin hankali,Tsayawa tayi tana tunanin taya ma zata fara yayyafa mashi ruwan batare daya ganta ba?kyau tana watsa mashi ta watsa da gudu kafin ya murmure,    Jikinta sae kerma yake yi,a haka ta buɗe robar ruwan,ta tarfa ruwan a hannunta,Ja da baya ta ɗan yi,sai da taba da interval sosai a tsakaninsu,daga inda take ta yarfa mashi ruwan akan fuskarshi,yaraf!ya saukar mashi,Aikuwa nan take ya shiga sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya,da gudun gaske sehrish ta 6oye acikin labulen ɗakin nashi,zuciyarta na ɗar ɗar,   Sannu a hankali ya buɗe blue eyes ɗinshi,yana faman sauke ajiyar zuciya,bin kasan bedroom ɗin nashi yayi da kallo,kafin yayi yunƙurin mayar da kanshi saman Gadon nashi,saman pillow ya aza kanshi,yasa hannu yana murza wuyanshi saboda raɗaɗin da ya ji a wurin,lumshe idanuwanshi yayi tare da sake buɗesu,jikinshi babu ƙwari amma zazza6in ya sauka daga jikinshi,dakyar ya iya miƙewa daga zaune,ya jingina bayanshi a head board ɗin gadon,Yayin da idanuwanshi ke a lumshe,   Sehrish dake 6oye bayan curtains ɗin ɗakin,tana jin duk wani moving ɗinshi,ta toshe bakinta da hancinta da tafin hannunta,saboda gudun kar ya gane akwai mutun aɗakin nashi,    Almost 15 mins yana a zaune bai motsa ba,tun da yake a arayuwarshi bai ta6a shiga matsanancin halin daya shiga ba irin na yau,kamar wani mara gata,sae kace ba Surgeon General ba,Yau ya ɗanɗani zafin kadaici,duk a sanadin kalaman da sehrish ta gaya mashi,    Saukowa yayi daga saman gadon,Ya tsaya atsaye tare da sanya hannu ya tu6e shirt ɗin dake ajikinta,Yayi wurgi da ita saman gadon,Zame belt ɗin wandonshi yayi ya jefar dashi saman rigar,sannan ya zame dogon wandon,Ya rage daga shi sai short light blue,    yana tafiya cike da rashin ƙwarin jiki,a haka har ya buɗe toilet ya shige ciki,Sehrish na jin motsin buɗe kopar toilet,Jiki na rawa ta lalla6a,saɗaf saɗaf ta fito daga cikin bedroom din,Hannunta riƙe da bottle water din,Saman fridge ta ajiye robar ruwan sannan ta kama hanyar fita daga falon,Har ta kai bakin kopar dakin ta juyo ta kalli kayan Breakfast ɗin da Armstrong ya kawo mashi,nan ta gane cewa bai ci komai ba,    Fitowa tayi daga part ɗin nashi,ta saukko downstairs da sauri ta nufi ɗakinsu,bayan ta shiga ciki ta ɗauki wayarta,tare da danna ma Aunty azeema kira,nan take ta ɗaga kiran,   Da sauri ta sanya wayar a kunnanta,tun kafin tayi magana Hajiya azeema tace"Ya ake ciki ne?   Sehrish tace"Naje part ɗin nashi,na same shi a sume saman gadonshi,gaskiya ba ƙaramin jiki yaji ba,nasamu dae na yayyafa mashi ruwa batare da ya ganni ba,na lalla6a na fito daga ɗakin nasa,naji ya shiga toilet da alama wanka zaiyi,Amma fa naga kayan abincin da aka kawo mashi daga restaurant,Da alama bai ci komai ba,"   Hajiya azeema tace"Good!,naji daɗi da bai ganki ba,Kuma naji daɗin suman nan da yayi,saboda zai samu sauƙi acikin zuciyarshi,duk da nasan dole ya ƙullace ki a aranshi,"   Murmushi sehrish ta ɗan yi kafin ta kuma cewa"duk yau baici komai ba," "Kada ki damu da wannan,ita yunwa bata da hankali,Ina nan dake wannan abincin da ya bari wanda aka kawo mashi na restaurant,Shi zai nema ina nan dake,yanzu dae ki kwanta kiyi bacci',   Hankalin sehrish ba ƙaramin kwanciya yayi ba,    "Ki kwanta kiyi bacci,Sae Allah ya kaimu gobe zamuyi magana," sallama sukayi da ita,Sehrish ta kwanta saman gadon tare da ajiye wayarta saman stomach ɗinta,yayin da idanuwanta ke fuskantar ceilling ɗin dakin, Sgr kuwa,bayan ya fito daga wankan da ya shiga,jallabiya ya zura ajikinshi ash colour,har wani jiri yake gani saboda tsabar yunwar da ya ke ji,ba arziƙi ya dawo palour saman sofa ya zauna,tare da kai hannu ya ɗauki burger ɗin nan,da ya ajiye saman table,Turata yayi cikin bakinsa ya shiga cin ta har yana shaƙewa,a ƙa'ida baya cin abincin da ya sha iska wanda aka bari a buɗe,Amma yau ba kanta,Ci kawai yakeyi,tass ya cinyeta,Miƙewa yayi da sauri ya nufi wurin fridge don ya daukko drink din da zaisha,hannu yakai tare da ɗaukar bottle water ɗin da Sehrish ta bari asaman fridge ɗin,6alle marfin yayi ya kafata a bakinshi yana kwankwadar ruwan,sae da yayi rabin ruwan dake acikinta,sannan ya dakata da shan ruwan da yake yi,Sai lokacin ya ankara da inda ya ɗauki robar ruwan,Shiru ya ɗan yi tare da zubawa robar ruwan dake hannunshi ido yana kallonta,Shi dai yasan bai ajiye ruwa asaman fridge ba,tunani ya shiga yi,Yanayin yarda ya farka duk da akwai zufa ajikinshi,amma tabbas yaji Saukar ruwa akan fuskarshi wannan ya tabbatar mashi da cewar wani ya shigo cikin part ɗinsa,Hannu yasa tare da buɗe fridge ɗin ya saka robar ciki,Sannan ya ɗauki coke mai sanyi,   Komawa yayi saman sofa din,ya zauna tare da kai hannu ya buɗe daya daga cikin ledojin,take away ya curo ya buɗe shi Chips ne aciki duk yayi sanyi,amma ahaka ya shiga turashi acikin bakinshi yana ci,bai ta6a shiga yanayi irin wannan ba a rayuwarshi,tass ya cinye duk wani abu dake a wurin,bayan ya kammala cin abincin,mikewa yayi ya koma cikin bedroom ɗin shi,ya ɗauko wayarshi,Sannan ya dawo saman sofa ɗin ya kwanta tare da miƙar da ƙafafunshi saman hannun kujerar,   Zubama screen ɗin wayar ido yayi yana kallonshi batare da ƙyaftawar ido ba,yama rasa wa zai kira yaji sanyi aranshi,numbar Abbansu ya lalubo ya danna mashi call,Ringing din farko Abbansu ya ɗaga kiran nashi muryarshi da alamun bacci yace"My son,Me kake yi har yanzu baka yi bacci ba"?    batare da ya amsa mashi tambayarshi yace"Daddy,when zaku dawo?gida duk ba daɗi,"   Tsananin mamakine ya kama Abbansu,Yau Sgr da kanshi yake cewa Gida babu daɗi saboda basu nan,ta wani 6angaren kuma yaji daɗin hakan sosai,    "Kayi missing ɗinmu ne"?Abba ya tambayeshi, muryarshi akasalance yace"Yeah,especially you,I missed u so much,"   Farin ciki ne ya cika Abbansu,kamar ya janyoshi ta cikin wayar ya rungumeshi,     "Pls Daddy,just come back home,if not zan biyoku damaturun ne,in yaso saimu dawo atare,"   Sgr na jiyo sautin muryar Abbansu yana tiƙar dariya,    "Are u laughing at me"? Tsagaitawa Abbansu yayi da yin dariyar yace"dole nayi dariyar Farin ciki mana,Yau ya kasance rana ta farko daka nuna kayi kewarmu sosai,naji muryarka wani iri tamkar zaka yi kuka,tell me what's wrong with u,wani ya ta6a mun kaine"?   Sgr yace"bana jin daɗin zuciyata ne,ko zaka sanyani farin ciki?   Abba yace"yanzun nan kuwa,bari na tuna maka wani abu,lokacin da kana ɗan jinjiri dakai cikin towel,kyakkyawa da kai,Na ƙwallafa rai sosai akan ka, kai kuma ga kyuyar tsiya,ka ƙi jinin baƙin mutun ya ɗauke ka,koni da nake mahaifinka ban isa na ɗauke ka ba,in ba bacci ya ɗaukeka ba,Sae in lalla6a in shiga ɗakinka,In zauna saman gadon in zuba maka ido inta kallonka,araina ina cewa Yanzu wannan mallakina ne,Allah ya bani Halak malak,Haka zan tasaka gaba ina kallonka,da zarar ka farka kuwa,mukayi ido biyu,kamar kaga wani 6arawo haka zaka fasa ihu kana ambaton sunan Mommynka,"    Lumshe ido Sgr yayi yana sauraron Abbansu,fuskarshi asake tamkar zaiyi murmushi,wata irin natsuwa yaji acikin zuciyarshi,   "Amma daga baya,saboda irin kulawar da nake baka sae ka gane cewa ni mahaifinka ne,kuma inason ka sosai fiye da kowa,sae gashi da kanka,kake zuwa wurina don in ɗauke ka,mu tafi yawo atare,"    jikin Sgr ba ƙaramin sanyi yayi ba,kalaman Abbansu sunyi matuƙar ta6a mashi zuciya,    "Amma ni sai inga kamar baka sona,baka damu dani ba kamar yadda na damu da kai...."   Tunkan ya ƙarasa maganar Sgr ya katse shi da cewa"Daddy kadaina faɗan hakan bana jin daɗi,duk duniya bani da tamkarka,kaine mahaifina,Jigona kuma ginshiƙi na,Abun alfaharina,madubin dubawana....".   Wani irin farin cikine ya lullu6e Abbansu,bai ta6a jin irin wannan yabon daga bakin Sgr ba,sai yau har ya fara tunanin anya kuwa cikin hayyacinshi yake gaya mashi waɗannan kalaman?ko kuwa ya ɗan kora wani abune,Gashi ya saki jiki sai surutu yake yi mashi kamar ba wannan miskilin ba..."   "Pls Rafayet,ka maimaita mun kalaman nan daka faɗamun,inaso nayi recording ɗinsu,"   fashewa da dariya Sgr yayi,hakan ba ƙaramin ɗaurewa Abbansu kai yayi ba,   Cike da mamaki yace"Rafayet,dariya kakeyi mun,dan Allah faɗamun kodai kasha kwaya ne yau,"    "Daddy bansha komai ba,lafiyana ƙalou,kawai ina jin daɗin waya da kaine,ka bari idan ka dawo gida zan sake maimaita maka sai kaji a kunnanka,"   Cikin raha sukayi wayar gwanin ban sha'awa hira irin ta da da mahaifi suka yi wadanda suke cikin begen juna,a karshe sukayi sallama,sauke ajiyar zuciya yayi tare da aza wayar saman chest ɗinshi,wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarshi,still kalaman Sehrish nadawo mashi acikin ranshi,waɗannan kalaman dae su suka fi ta6a mashi zuciya,Mara tausayi mara Imani,da kuma danganta shi da ya sayyadi, Tariyo abunda ya faru tsakaninsu ya shiga yi cikin ranshi,Yadda ya damƙo wuyan rigarta tare da yin wurgi da ita ta bugi bango,har ta fashe da kuka saboda zafin da taji,da kuma munanan kalaman da ta jefa mashi,da alama nazarin wani abu yake yi,dangane da abunda ya faru jiya atsakaninsu, Ya jima asaman Sofa ɗin,kafin daga bisani ya koma cikin bedroom ɗinshi,darduma ya dauƙo ya shimfiɗa tare da kabbara salla,Sae da ya fara biyan bashin sallolin da baiyi ba,sannan ya ɗaura da yin nafilfilin daren daya saba yi,bayan ya kammala ya ɗauki qur'ani ya shiga karantawa,nan take yaji natsuwa tazo mashi acikin zuciyarshi,bashi ya kwanta bacci ba,har sae wuraren ƙarfe biyu na dare,sannan ya haye saman gadonshi ya kwanta,bacci 6arawo yayi awon gaba dashi, Itama Sehrish,sae da tayi sallar daren,kafin ta kwanta bacci, Abunda ya faru daren jiya da Aunty babba ta zauna zaman jiran Hayaam.... tunda ƙarfe goma ta buga hayaam bata dawo ba,nan hankalinta yayi mugun tashi,fitowa tayi daga bedroom ɗinsu,ta shiga zarya acikin hotel ɗin,ko Allah zaisa taga gifcinta,amma shiru babu ita har receptionists taje ta tambaya ko sunga fitarta suka tabbatar mata da basu ganta ba,ƙarshe da ta gaji da biɗiɗin nemanta,komawa tayi ɗakin nasu zuciyarta a ƙuntace ta kwanta,duk da halin da ta shiga na rashin hayaam,hakan bai hanata yin bacci ba,harda minshari,   Haroon kuwa tun da ya kammala yi mata wannan aika aikar,ya tattara yabar Hotel ɗin ya gudu gaba ɗaya,don kuwa daƙyar in hayaam zata ƙara moruwa,Ya naƙasata sosai,a saman gadon ya barta a yashe, Wuraren Sallar asuba,Wayar Aunty babba dake ajiye gefenta ta soma ringing,can cikin bacci ta dinga jin ringing ɗin wayar,dama ta kwana da tunanin hayaam zata iya kiran ta in ta buɗe wayarta,hakan yasa ta farka da sauri takai hannu ta ɗauki wayar,duba screen ɗin wayar tayi da 6oyayyiyar lamba aka kirata,cike da mamaki tace"To fa,waye ya kirani a irin wannan lokacin da 6oyayyiyar number?kodai hayaam ce ta kira,bari na ɗaga na ji,    Picking call ɗin tayi ta kara wayar a kunnanta,   Tun kafin tayi sallama taji ance"Madam,barka da warhaka"   gabanta ne ya ɗan faɗi rass,amma ta dake tace"yawwa,dan Allah wanene ke magana,"    "Babu bukatar ki sani,dama na kira ne don in yi aikin lada,Nasan kina ta neman hayaam ido a rufe,to hayaam dae a halin yanzu addu'arki take buƙata,idan kina son sanin inda take,yanzu zan turo maki da message na address ɗin inda take,sae ki hanzarta zuwa don ki kai mata agaji,Allah ya bata lafiya,idan ta samu ciki dan Allah a ajiyemun abuna,inaso" yana faɗin haka,yayi rejecting kiran,"   Waro ido waje Aunty babba tayi,a hargitse ta saukko daga saman gadon hannunta riƙe da wayar,jikinta har kerma yakeyi,zarya ta shiga yi acikin ɗakin tana jiran shigowar saƙon,   A fili tace"Allah yasa dae hayaam ba wani taje taba ma kanta ba yayi amfani da ita,Sae da naja mata kunne akan ta daina kula maza,amma da ya ke karya ce gaya nan tana son ja mun bala'e,ina zaman zaman lafiyana," Tana cikin wannan zullumin,taji ƙarar shigowar message da sauri ta duba top of the screen ɗin wayar,   "Vip,Room 34,"shine abunda taga an rubuta acikin message ɗin,kuma babu numbar wanda ya tura,anyi hidden number,    Sai da tayi zurfin tunani sannan ta gane cewa numbar ɗakin hotel ne aka turo mata,hakan na nufin cewa hayaam tana acikin hotel ɗin,    Jiki na rawa ta ƙarasa wurin trolley ɗin kayansu dake ajiye,gefen wardrobe,buɗe wa tayi ta dauko mayafi ta lullu6a asaman kanta,    Sannan ta tura kopar ɗakin ta fito,tafiya takeyi cike da zullumin abunda zai biyo baya,sae bin ɗakunan dake a wurin takeyi tana bin numbobin jikinsu,cikin sa'a batare da tasha wahala ba tazo kan numbar ɗakin da aka turo mata,sae da ta duba dakyau taga Room 34 ne,Hada key aka ajiye mata ajikin ƙopar,wannan ya tabbatar mata da cewa da gangan aka sanya key ɗin,saboda in tazo ta buɗe ta shiga,    Gabanta sae faɗuwa yakeyi,a hankali ta sanya hannunta ta ɗan murza key ɗin ɗakin ya buɗe,cike da fargaba ta tura ƙopar ɗakin a wani slow kopar ta soma buɗewa ƙiiiiiii,tun kafin ma ta sanya kafarta acikin ɗakin ta hango pant yashe a saman tiles,Rass taji gabanta ya faɗi,wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,dakyar ta shiga cikin ɗakin,karaf Idanuwanta suka hango mata Bra din hayaam dake sagale ajikin mirror,tun daga nan tasha jinin jikinta,wurga idonta tayi gefen hagunta,Handbag ɗin hayaam ta hango yashe a kasa,da alama wurgi akayi da jakar kayan cikinta suka watse akasa,hada wayarta ma duk screen ɗin ya fashe, ..arazane Aunty babba takai idonta saman gadon,mutunne a kwance an lullu6e shi da bargo,   A tsananin tsorace ta ƙarasa gaban gadon,sanya hannunta tayi tare da zame bargon a hankali,tana buɗe bargon da sauri ta mayar ta rufe,saboda tashin hankalin da ta gani,hannu ta aza akai ta fasa ihu tana faɗin"Nashiga uku!Wayyo Allah na,Hayaam wani marar imanin ne yayi maki wannan aika aikar!hayaam waye ya yashe ki haka!La'ila ha'illallahu muhammadur rasulillahi!Amma kowaye wannan anyi haihuwar asara,Uwarshi ta haifo mana Bala'e" ta inda take shiga bata nan take fita ba,Muryarta har shaƙewa takeyi saboda tsabar baƙin ciki,tamkar ta haɗiyi zuciya ta mutu, ..a karshe ta fashe da matsanancin kuka,tare da hayewa saman gadon,tana cigaba da sambatu,da alama ta fara zaucewa,    "mun shiga uku mu yau,Wllh dana san haka zata faru da bamu zauna a hotel ɗin nan ba,ƙaddara ce kawai ta riga fata,Hayaam kowaye wannan ya gama damu,ɗan jarin da muke taƙama dashi ya kwashe komai babu,ya yashe ki,ya karya mana tattalin arziƙin da yayi mana saura,Ya takaita mu don ubanshi,wlh koma wani jarababben ne,Sae Allah ya toni asirinshi,Ni na ta6a ganin jaraba irin wannan,bai bar komai ba,yayi mata wanwar ɗan jakar uban,haihuwar asara haihuwar titi,haihuwar kwararo...."kasa ƙarasa maganar tayi,wani irin ƙululun baƙin cikine ya tokare mata maƙoshinta,nan tashiga yin kakarin amai,ta saukko daga saman gadon agalabaice ta nufi toilet ɗin cikin ɗakin ta shiga,Sosai tayi amai tamkar ƴan hanjin cikinta zasu fito waje,ta jima acikin toilet ɗin kafin ta fito,tana tafiya ƙafafunta na harɗewa,   Fitowa tayi daga ɗakin ta koma ɗakinsu,Trolley ɗin kayansu ta buɗe,Jallabiya ta ɗaukowa hayaam tare da Mayafi,Sannan ta koma can ɗakin,taci wahala haka ta kinkimi hayaam ta shiga da ita toilet,wani wurin ma ajikinta,baya ta6uwa sae dai anje asibiti duk ya jagule babu kyan gani,hatta la66anta duk sun faffashe hada busasshen jini,nipple ɗinta na right breast kuwa,sai jini yake yi,ƙiris ya rage ya 6alle,haƙika haroon ya cutar da ita,ya zalunce ta,Da mugunta yayi mata hakan,Dama babu Imani aranshi,duk ya faffasa mata skin ɗinta da Nails ɗinshi,saboda baya yanke akaifa,doguwar ƙumba ne dashi,   Aunty babba tasha kuka,Tuntana kukan fili har ta koma yin kukan zuciya,wanda yafi ciwo,Sai da ta nemi taimako a hotel ɗin,sannan ta samu aka ɗauki hayaam,Suka kaita wani private hospital saidai sam bata sanar dasu haƙiƙanin abunda ya sameta ba don tasan karshe reporting za'ace ayi wurin yansanda ita kuma bata son asirinsu ya tonu har abun ya kai kunnan su Ishaq,tafi son in hayaam din ta farfado ta fadi wanda yayi mata hakan don ta tabbatar ba da karfi aka jata dakin ba don wanda ya kira ta ya sanar da ita halin da take ciki har sunan hayaam din ya ambata hakan kuma na nufin ya santa ne,  Tunda aka shiga da ita ciki,Likitoci suka taru akanta,Aunty babba na zaune zugudum saman waiting seat,tashin farko sae da suka fara kar6ar kuɗin gadon kusan Naira dubu 50,Sannan za'ayi mata aiki ciki da waje a ƙalla za'a cajesu kuɗi kusan Dubu ɗari biyar,Bayan haka akwai alluran da za'ayi mata ajikinta kuɗinsu ya kai kimanin dubu 20,   Abun yayi matuƙar girgizata,ita babbar damuwarta,ba halin da hayaam ke ciki ba,Kuɗinsu da suke tattalawa zasu je wurin boka,Har an yashe kusan rabinsu,wasu mutanen dai ba imani aransu,ɗaya daga cikin halin ɗan adam kenan,Duk yadda take da hayaam same parents,Amma harta fara tunanin guduwa ta barta a asibitin saboda gudun kar su talauta ta,Kuma ta yanke shawarar zata yi ma Abra magana tazo su tafi wurin bokan tare da ita,Tunda ita hayaam ta gama lalacewa,babu wani amfanin da zata yi mata,ƙarshe ma taja masu asara,yini tayi a asibitin tana zirga zirga,Yayin da zuciyarta ke saƙa mata,ta gudu tabar asibitin,tun da ta samu ta biya mata kuɗin aikin Can su ƙarata, Har wuraren ƙarfe Goma na dare,lokacin an kammala yiwa hayaam aikin,Amma bata farfaɗo ba,tsayawa Aunty babba tayi abakin ƙopar shiga ɗakin tana kallon hayaam dake kwance,hancinta na sanye da Oxygen,   Komawa tayi saman waiting seat din,inda tabar handbag ɗinta,ɗaukar jakar tayi ta buɗe ta,biro ta curo tare da memo,aza takardar tayi saman kujerar sannan ta soma rubutu Kamar haka   _Hayaam sae dai kiyi haƙuri,Wlh bazan iya cigaba da zama acikin asibitin nan ba,duk laifinki ne,Sai da na gargaɗeki akan karki kuskura ki ƙara kula wani ɗa namiji,amma da yake ke karyace ba'a raba ki da maza,Gashi nan kin jawowa kanki wanda yafi ƙarfinki,Ya gama dake yayi maki kankat,babu abunda yayi saura ajikinki balle har insa ran zakiyi mun amfani,Shiyasa na yanke shawarar zanyi ma Abra magana,zamuje wurin bokan tare da ita,Don bazan bari burina yaƙi cika ba har su Amani suyi nasara,In dana gode ma Allah bake kaɗai bace ƙanwar da nake da ita ba,Wlh dana ji kunya_   Tana kammala rubuta short note ɗin,Ta ɗauki handbag ɗinta,Sannan ta shiga cikin ɗakin da aka kwantar da hayaam ɗin,A gefenta ta ajiye wasiƙar,Sannan ta curo bandir ɗin kuɗi dubu hamsin ta ajiye mata a gefenta,a hankali ta furta Allah ya baki lafiya hayaam,Idan kuma kin riga mu gidan Gaskiya,Allah ya jiƙanki da rahama,   Tana kai ƙarshen maganar,da sauri ta juya tabar ɗakin,batare da 6ata lokaci ba,ta gudu tabar asibitin,   Rayuwa kenan, *Boss Bature*    ❤🤍❤ Tunda sanyin safiya ringing ɗin wayarta ya farkar da ita daga bacci,cikin bacci takai hannu tana laluban wayar harta samu ta cafkota,janyota tayi cikin bargon tare da buɗe idanunta masu ɗauke da bacci,Sunan Mommy Azeema ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,da sauri ta miƙe daga zaune,har time ɗin doguwar rigar jiyace a jikinta pink ɗin nan,picking call ɗin tayi ta kara wayar a kunnanta,   "Assalamu alaikum," On the other hand Aunty Azeema tace"Babyn Rafayet,kin tashi lafiya,"   Murmushi sehrish ta ɗan yi tare da cewa"lafiya qalou Alhamdulillah," "Yawwa my Daughter,dama na kira ne about abunda ya faru a tsakaninki da Rafayet,"   Natsuwa Sehrish tayi tana sauraronta   Ci gaba da magana tayi,"Jiya na hana ki bashi haƙuri,Saboda nasan cewa yana cikin fushi,kuma haɗari ne ki tunkareshi a wannan lokacin,kafin nan abunda nakeso in sanar dake,duk yadda kike tunanin rafayet ba haka yake ba,mutunne shi mai ƙyanƙyami sosai,kuma yana da zuciya shiyasa a lokacin ranshi ya 6aci ne sosai,har yayi yunƙurin bugunki,kinsan in ran mutun ya 6aci zai iya aikata komai ba'a hayyacinshi ba,sae yadawo cikin hankalinshi kuma yazo yana danasani,Akwai ire irensu,Ni nasan ba ason ranshi yayi maki hakan ba,don ba halinshi bane wulaƙanta mace,Zuciya ce ta fisge shi har yayi wurgi dake,ya kuma yi yunƙurin marinki......"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar na wani lokaci kafin ta ɗaura da cewa"Kin riga da kin faɗi abunda ke cikin ranki ba'a hayyacinki ba,ina mai tabbatar maki da cewar yanzu zai yi ƙoƙarin gyara mu'amularshi dake ne,Saboda ki daina yi mashi kallon mugu,Amma fa idan har kina son hakan ta faru dole sai kinje kin bashi haƙuri,sai daga baya na zauna nayi wani tunani,muddin baki bashi haƙuri ba,to akwai gagarumar matsala,tunda bai fara sonki ba,zai iya aikata komai daga ciki hada divorce tun kafin ma lokacin ya cika kin ga mu kuma ba haka muke so ba,Kuma idan kin bashi haƙuri ba hakan yana nufin cewa kin zubda ajinki bane,Darajarki zata ƙara daukaka a wurinshi,zai san cewa tabbas kina da hankali sosai tunda har kinsan kiyi laifi kuma ki nemi yafiya,kawai abunda nake so dake koda kinje bashi haƙuri karki nuna cewa ba'a hayyacinki kikayi maganar ba,"   Zuru sehrish tayi tana sauraronta,hankalinta yayi mugun tashi,Shin ta yaya zata tunkari Sgr da sunan zata bashi haƙuri?   "Aunty azeema,still akwai matsala,Babban yaya ya hanani zuwa part ɗinshi fa,saboda period ɗin da nake yi,Nasan idan ya ganni zai tuna da jinin da ya gani ajikin wandona ƙarshema yayi mun korar kare in bai bugeni ba,"muryarta tamkar zata yi kuka haka tayi maganar,   "Kada ki damu da wannan,In sha Allah babu abunda zai faru dake,sannan idan zaki je part ɗin nashi,ki gyara jikin naki sosai,Kuma ki shafe shi da turare"   Gyaɗa kai kawai tayi tare da cewa"Shikenan zanje in sha Allah,duk yadda mukayi dashi zan sanar maki,"    "Okey,saina ji ki," Tayi rejecting kiran,Ajiye wayar sehrish tayi saman gadon,Saukkowa tayi tare da nufar toilet ta shiga,Cikin mintina tayi wanka ta fito jikinta sanye da undy taja shi saman ƙirjinta,hannunta ruƙe da Short towel,Goge ruwan jikinta tayi dashi,bayan ta kammala,ta zauna gaban mirror tana shafa body cream ɗinta,Bayan ta gama ta shafa powder afuskarta,tare da murza man baki,Comb ta ɗauka tana sharce gashin kanta,   Turo kopar akayi,ta cikin mirror ta kalli wurin ƙopar don taga wanene,Jahad ce ta shigo hannunta ɗauke da plate meat balls ne aciki tare da Cup na coffee,   "Allah yasa nawa ne,"acewar Sehrish,   Murmushi jahad ta saki tare da cewa"Naki ne mana,nayi tunanin ma baki tashi daga bacci ba," tayi maganar tare da nufar wurin mirror ɗin ta tsaya,hannu tasa ta ɗauki meat ball din guda daya tace"Buɗe bakinki in saka maki,kiji idan yayi daɗi,"   Buɗe baki Sehrish tayi,Jahad ta tura mata shi cikin bakinta,taunarshi ta shiga yi tana jinjina kai alamar daɗinshi yana kai mata karo,   "Baby junaid nayi mawa,Ya kika ji ɗanɗanon"? .Sehrish tace"Bangane ba,wani junaid ɗin bayan basu nan?ko kin manta ne"?    Jahad tace"Ae munyi waya dashi,Ya sanar dani cewa,Yau ko gobe zasu dawo,Amma basu duka ba,Shi dai yace bazai iya jure rashina ba,In ma basu dawo dashi ba,ko a ƙafa ne sai ya tako," ..fashewa da dariya Sehrish tayi,itama jahad ɗin dariyar ce akan fuskarta,   "Gaskiya junaid na dabanne,yaci sunanshi Romeo,ga kuma juliet ɗinshi tsaye agabana,"   Tayi maganar tana nuna Jahad dake atsaye, Murmushi jahad ta saki tare da cewa"Oh Ni sehrish,Wlh bansan ya zamu qare da junaid ba,idan munyi aure,Kina ganinshi ɗan ustazi ko,ba ƙaramin jarababbe bane,"   Sehrish tace"gaskiya sai kin jure don kula da junaid ba abu bane mai sauki,a kwanakin baya can da jimawa,lokacin daya gane cewa ni mace ce,Mun ta6a yi dashi zamu haɗu a garden,Ni kuma na manta,kinsan Allah tun wurin magrib junaid ya zauna a garden ɗin nan yana jiran zuwana,maimakon da ya ji ni shiru ya dawo cikin gida,sae yaƙi shigowa saboda munyi alkawarin haɗuwa dashi,Ni kuma na manta,ɗan tahalikin nan,tsakar dare akayi ta nemanshi aka rasa,ashe yana can garden yana jirana,ga asthma ɗinshi ta tashi,da ace ban tuna ba naje wurin nan ba,da Allah kaɗae yasan abunda zai faru dashi....."   Jin wannan maganar ba ƙaramin tayarwa jahad da hankali tayi ba,   "Kice Majnun zan aura ba Romeo ba,junaid bashi da hankali wlh,"acewar jahad,   Sehrish tace"yana da hankali mana,Junaid yana da mutunci sosai,ya kyautatamun sosai,bazan ta6a mantawa da halaccin da yayi mun ba,ina taya ki murna jahad,idan har kika auri junaid,babu ke babu yin aikin wahala,zan so naga rayuwar aurenku,tamkar comedy haka zata kasance,Zaki samu nishaɗi sosai,"   Ba ƙaramin farin ciki jahad taji ba,sae faman sakin murmushi takeyi,   Hannu sehrish tasa tare da ɗaukar cup ta kaishi bakinta tana kur6ar coffee,sae da ta shanye sannan taci gaba da ɗaukar Meatballs ɗin tana jefawa a bakinta,Duk jahad na atsaye ta ruƙe mata plate ɗin,    "ki zauna mana,ƙafafunki basu ciwo ne"?    "A'a,So nake in koma kitchen,Ina taya Aunty azmee aikin gida ne,"   "Hosana fa?tunda mukayi sallar Asuba,dana koma bacci ban ganta ba lokacin dana farka,"tayi maganar a yayin da takai hannu gaban mirror,ta yago tissue tana goge bakinta,   Jahad tace"Tana a dining,kinsan ta bata gajiya da ci,Ae ina tausayin Ya Omar,Don hosana saita ƙarar mashi da duk wani tattalin arziƙin da yake dashi,Gashi don ubanta ko girki bata wani iya ba,ci kawai ta sani,"   Dariya Sehrish tayi sosai kafin tace"Sauƙinta ma,Ya Omar mutunne mai haƙuri,Kuma yana da kyakkyawar zuciya,Shi kaɗai ne zai iya control ɗinta,Amma fa zaiyi fama wlh,"tayi maganar tare da miƙewa ta koma gaban wardrobe,   Buɗewa tayi tana neman kayan da zata sanya ajikinta,   Suna cikin magana,Hosana ta faɗo ɗakin tana kuka,bakinta cunkushe da Donuts,Ga wani a hannunta ta ruƙo,ɗayan hannun na ruƙe da wayarta,   Juyowa sukayi atare suna kallonta,hankali atashe suka tunkareta har suna haɗa baki wurin cewa"Hosana,Me ya faru!me kikeyi ma kuka haka?Wani ne ya rasu"?   Ɗaga masu kai tayi alamar eh, Gabansu ya faɗi rass,A sukwane suka kalli juna,kafin suka mayar da idanuwansu kanta,   "Hosana faɗamun!waye ya rasu!"jahad tayi maganar jikinta na kerma,   Sehrish tace"ki buɗe baki kiyi mana magana,ko wani ne bashi da lafiya,"?   Sae lokacin ta taune donut ɗin bakinta tana matsar kwalla tace"Yayi Hatsarin Mota ya mutu"!   Kallon juna sukayi atare kafin su kuma mayar da idanuwansu kanta,arazane suka haɗa baki wurin cewa"Wa? ..cusa donut ɗin hannunta tayi acikin bakinta,Cikin shessheƙar kuka tace"wani Mai yin comedy,Yanzu nake gani acikin wayata,yayi hatsarin mota ya rasu"   Sauke ajiyar zuciya su kayi atare,Duk atunaninsu wani ne ya rasu Cikin waɗanda suka tafi damaturu,   "Hosana ba kuka zakiyi mashi ba,Addu'a yakamata kiyi mashi don ita yake bukata,Allah ya jiƙanshi,Ya gafarta mashi zunubban shi,Allah yasa aljanna ce makomarshi,Amma idan kikayi mashi kuka to ke ba cikakkiyar masoyiyarshi bace,"   "Nadaina kukan,Idan nayi sallah zanyi mashi addu'a,"    ta ƙarasa maganar,tana cigaba da taunar donut ɗin dake a bakinta,sannan ta juya ta fuce daga ɗakin,   Jiki asanyaye Jahad ta koma gefen gadonsu ta zauna,Sehrish kuma ta koma wurin wadrobe ɗin,Tana ɗaukar kayan da zata sanya,   "Hosana ta tayar mun da hankalina sosai,Jikina duk yayi sanyi,"   "Kin gane wa take nufi ne"?sehrish tayi mata tambayar,ayayin da take zura skirt ajikinta,   "Kamal Aboki take nufi mana,Wanda yayi wannan comedy ɗin nan,na matar soja,yana rera waƙar india shi da wani,akwae ma wani wanda yake cewa gayuna kun ga Alert,su kuma sauran sai suce a'a,kin tuna shi"?   Shiru sehrish tayi tana ƙoƙarin tuna comedy ɗinsa,can tace"Nagane shi,ya iya comedy sosai,Na ta6a ganin video ɗinshi a wayar Amrish,dayake ita mayyar kallon Comedy ce,Ni kinsan bancika amfani da waya ba,"    Jahad tace"naji mutuwarshi sosai,ya tsaya mun araina,rayuwar kenan kana taka Allah yana nashi,shiyasa wasu mutanen in suna aikata abunda suka ga dama har mamaki suke bani,sun manta cewa duniyar nan ba wurin zama bane,Jin daɗinta ƙalilan ne,da zarar ka mutu za'a kai ka grave ɗinka,daga kai sai Halinka,mai kyau ne ko mara kyau,idan na tuna cewa zan mutu in bar duniyar nan,ko inaso ko banso sai inji komai ya fita raina,ina rage duk wani dogon burin da nake dashi akan duniyar nan,Kuma ina ƙara kusanta kaina wurin Allah,...'    Sehrish tace"Wata rana muma babu mu,masu karanta labarin ma babu su,Mai bada labarin ma babu ita,Allah yasa dae mu cika da kyau da imani"_   Jahad ta amsa mata da"Ameen" sannan ta miƙe tare da nufar ƙopar fita daga ɗakin tana cewa"Ni zan wuce wurin Aunty azmee,kada mu barta da aiki ita kaɗae,"   "Nima idan na kammala shiryawar zanzo na tayaku aikin"acewar sehrish,"    Shaf shaf ta kammala shirya kanta,Cikin Skirt red colour,Asymmetrical Yana da baza ajikinshi,Gaban skirt ɗin bai kai bayanshi tsayi ba,yayi matuƙar yi mata kyau,Halter shirt ta sanya ajikinta white colour tayi tighting ɗinta,Red & white abun ba'a magana,Takalma ta zura a ƙafarta t-strap yana da ɗan tsini amma ba sosai ba,Launin skirt ɗinta ne,komawa tayi gaban mirror ɗin,ta ɗauki kwalbar turarenta tabi jikinta ta feshe ko'ina,saƙo da lungu,nan take ƙamshin ya gauraye ko'ina,bata sanya mayafi akanta ba,sai gashin kanta da yayi mata rumfa abayanta,   Fitowa tayi daga ɗakin,ta shiga cikin palour bata samu kowa ba,Suna can cikin gidan suna gyare gyare,   Tunda ta hau saman staircases(matattakalar bene)gabanta ya shiga faɗuwa,lokacin da ta ƙarasa part ɗin nashi bata shiga daga ciki ba, Gabanta sae faɗuwa yake yi rass rass!leƙawa tayi ciki babu kowa Sae dae kayan abincin nan daya ci,' Runtse idanuwanta tayi tare da ɗaga hannayenta izuwa saitin fuskarta, "Ya Allah Kana ganin baiwarka,acikin wani hali na firgici da tsoro,Allah ka tsare ni,Wllh idan naga ya nufo ni zai bugeni,Sae in watsa da gudu,Amma takalmana masu tsini ne,kada suja inyi tuntu6e in faɗi ƙasa," Dakatawa tayi da yin zancen zucin nata,Sannan ta ɗan buɗe idanuwanta tana ƙara leƙa cikin palourn nashi, Jaraba yadda zata bashi haƙuri ta shiga yi, _babban yaya,Am sorry bazan ƙara ba,nasan nayi maka laifi,amma banyi hakan da niyyar na 6ata maka rai ba,Ba yin kaina bane,kuma ba hali na bane,Allah shine shaidata,ni bana yi ma na gaba dani rashin kunya,tsautsayine kawai da ƙaddara,A iya nan zan tsaya na baka haƙuri,saboda ka hanani shiga part ɗinka,har saina kammala period ɗina,Shiyasa bazan samu damar shigowa daga ciki in baka haƙuri ba_ Tana cikin tsara yadda zata sanar dashi,Kwatsam taji ƙamshin turarensa acikin hancinta,gabanta ne ya faɗi Rasss!waro ido tayi waje,ta zazzaresu,hankalinta yayi mugun tashi, Kasa juyawa tayi ta kalli bayanta,saboda tana da tabbacin cewar,SGR YANA TSAYE ABAYANTA!Ashe baya cikin part ɗin nasa,Tashin hankalin da ba'a sa mashi date! Ko ya sehrish zata ƙare!? Sanƙamewa tayi a tsaye,ko motsi ta gaza yi,jira kawai take taji yayi wurgi da ita,    "Excuse me,"muryarshi ce ta katseta,jiki na rawa taja gefe guda,yayin da idanuwanta ke kallon ƙasa taƙi yarda ta ɗago balle har su haɗa ido dashi,jikinshi na sanye da kaftan shirt har guiwa tare da trouser ɗinta brown colour,ya saki sumar kanshi ta baya,wani irin daddaɗan ƙamshine ke fitowa daga jikinshi,Slowly ya wuce cikin palourn batare da ya kalleta ba,abun ya yi matuƙar bata mamaki,tayi tsammanin tashin farko zai daka mata tsawa ne ya shako wuyanta,Sae gashi ko kallon inda take bai yi ba,Wuri ya samu saman Sofa ya zauna,tare da jingina bayanshi a jikinta,    Tunani Sehrish ta shiga yi Ko ya ji abunda tace ko baiji ba Oho,Allah Wa'alamu,ranta ne ya bata cewar ta juya ta tafi kawai,tunda ba damar ta shiga ciki,ya riga da ya hanata,tana ƙoƙarin barin wurin,kwatsam taji yace"Zo nan,"   Rasss taji gabanta ya faɗi,nan take taji fitsari ya matseta,daƙyar ta daure ta cije,ta dake sannan ta juya ta shiga cikin palourn,nesa dashi ta tsaya,saboda gudun kar ya shaƙota,     Idanuwanshi na akan agogon hannunshi daya dafa sofa hand dashi,   "Laifin me na aikata maki,da har na cancanci a kira ni,da mara IMANI mara TAUSAYI"?he said calmly,    Wuƙi wuƙi sehrish tayi da ido,sae faman murza yatsun hannunta take yi,batasan amsar da zata bashi ba,    "Also,kinyi comparing ɗina da wannan fasiƙin mutumin,Why"?   Shiru tayi tana ta faman mazurai, Miƙewa yayi daga zaunen da yake gadan gadan ya nufi wurinta,ja da baya Sehrish ta shiga yi tamkar ta watsa da gudu tabar falon sai dai ba dama,har saida suka ƙurewa bangon falon sannan ta tsaya,tare da ƙankame jikinta,tsoronta kada yace zai bugeta,    Rumfa yayi mata da faffaɗan ƙirjinshi,duk tabi tasha jinin jikinta,Acikin zuciyarta sae faman ambaton La'ila ha'illah anta subhanaka inni kuntu minazzalimin takeyi,gaba ɗaya ƙamshin turaren jikinshi ya hanata sukuni,ga fargabar da ta shiga,     "look at my face!nayi maki kama da mara tausayi,Mara imani"? Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,dakyar ta iya buɗe baki tace"A'a,?    "But Why u said so"? Girgiza kai ta shiga yi,batare da ta furta komai ba,     "Shekarunki nawa"? Muryarta na kerma tace"Na shiga sha takwas,"    Gwauron numfashi ya saki tare da zura hannunshi na dama cikin sumar kanshi a hankali ya furta"Ya Allah"!abun yayi mashi ciwo,ƙaramar yarinya na so ta caja mashi kwalwa,     Zame hannun yayi daga cikin sumar,tare da dafe bangon da tafin hannun,    "In my life,Wata ƴa mace bata ta6a gigin gaya mun magana ido cikin ido ba,batare jin shakkata ba,Sae ke,"yayi maganar yana nuna ta from head to toe,     Hankalin Sehrish yayi mugun tashi,Hukuncin da zai yanke mata kawai take jira,"    "A ina kika samu ƙwarin guiwar yin hakan"?yayi tambayar yana kallon fuskarta,   Shiru tayi,tana faman haɗiyar yawu,    Jinjina kanshi yayi tare da ja da baya ya juya,Saman sofa ya koma ya zauna,    "Come close"ya furta hakan yana nuna mata gefen table ɗin dake agabanshi,   A hankali ta tako tazo gabanshi ta tsaya,sae lokacin ta ɗan saci kallon fuskarshi,karaf idanuwansu suka shiga cikin na juna,irin kallon da taga yanayi mata ne yasa tayi saurin duƙar da kanta ƙasa,ta ƙurawa takalman ƙafarta ido,    "Don't judge me,till u know me well,"   Jinjina kanta tayi,batare da ta ɗago ba,     "Idan har akwai abunda nake maki,Wanda yasa kike yi mun kallon wicked,mara tausayi mara Imani,lemme know,"    Da sauri tace"babu komai," "I don't trust u,If u can't say it,ki rubuta mun a Text message"   Abun yayi matuƙar ɗaure mata kai,yadda tayi tsammani ba haka ta gani ba,kokonto ta shiga yi anya Sgr ɗin da ta sani ne kuwa?kodae mafarki take yi ne,ta kasa yarda cewa da gaske ne shi yake yi mata,     A hankali ta furta mashi toh, Juyawa tayi ta kama hanyar fita daga falon,tafiya take yi tana wasi wasi acikin zuciyarta,    "Idan ina takura maki ne,Remain just 2 months na bar ƙasar,Zan sallame ki ne,kiyi rayuwarki kamar yadda kika saba,".     dakatawa tayi da yin tafiyar ta ɗan juya tare da kallonshi, ba ita yake kallo ba,idanuwanshi na a lumshe,ci gaba da magana yayi"Ki dawo ki ci gaba,da yin aikin ki a part ɗina," Tayi matuƙar yin mamakin abunda yace mata,hatta kalamansa ya tausasasu bakamar yadda yake yi mata magana ba ada, "Am waiting for my breakfast,then bedroom ɗina yana buƙatar gyara," "Amma ka hanani yin aiki a part ɗinka ayanzu," "Nayi cancelling," Nauyayyiyar ajiyar zuciya ta sauke,ta wani 6angaren taji daɗi sosai,duk da bata ji daɗin kalaman da ta faɗa mashi ba a jiyan nan,da alama sun ta6a mashi zuciyarshi sosai, Komawa cikin falon tayi,gaban table ɗin sa taje,ta kwashe ledojin nan da aka kawo mashi na restaurant, Sannan ta juya ta nufi ƙopar fita daga falon,tana tafiya tana waiwayenshi har wani ƙara leƙen fuskarshi takeyi,Saboda abun ya ɗaure mata💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Batare da 6ata lokaci ba,ta shirya mashi breakfast ɗinshi,takai mashi a falonsa,yadda tabarshi haka ta same shi a zaune,Sae da tayi serving ɗinshi ya ci ya ƙoshi,Sannan ta wuce bedroom ɗinshi,Ta shiga gyara mashi,lokacin da ta kammala gyara Bedroom ɗinsa da Toilet,ta fito palourn, Komawa cikin bedroom ɗin yayi after some minutes ya fito jikinshi sanye da trouser na army tare da shirt,tana cikin gyaran yazo ya wuce ta,Gyara palourn tayi ko'ina yayi fess sae ƙamshi dake ta tashi,turo mashi ƙopar falon ta ɗan yi,Sannan ta saukko down da sauri ta wuce bedroom ɗinsu jiki na rawa,Don a ƙagare take da ta sanar Wa Aunty Azeema,   Tura ƙopar ɗakin tayi tare da sa ƙafa ta shiga ciki,jahad ce kwance saman gadon Kunnanta manne da waya,suna waya da junaid,juyowa ta ɗan yi tare da kallon ƙopar don taga wanene ya shigo,Ganin Sehrish yasa ta mayar da kanta inda take fuskanta taci gaba da yin wayar,    Wayarta dake ajiye saman drawer ta dauko,contact ta shiga ta lalubo layin hajiya Azeema ta danna mata kira,Wayar na shiga ta ɗaga kiran ,   "Daughter,ya ake ciki ne?tun ɗazu  nake tasa ran ganin kiran ki,"Aunty Azeema tace,   Murmushi sehrish ta ɗan saki tare da cewa"Yau babban yaya yayi matuƙar bani mamaki,Abun da ban ta6a tsammani ba,'_    "har na ƙosa naji meya faru,ae tunda naji muryarki,nasan cewa an dace,halan bai yi maki komai ba"?   "Baiyi mun komai ba,ƙarshe ma cewa yayi in rubuta mashi duk wani abu da yake yi mun wanda bana so in tura mashi ta message da ya tambaye ni abunda yake man nace ba komae,Sannan kuma yace in ci gaba da aiki a part ɗinsa,"ta ɗan dakata da yin maganar,tana jiran jin me Auntyn zata ce,Sautin dariyarta tajiyo ta cikin wayar,    "Dama sae da raina ya bani cewar Rafayet,bazai yi maki komai ba,Gaskiya naji daɗin hakan sosai,wannan ma wani matakin nasarar ne,Yanzu me kika yanke shawara akai"?    Sehrish tace"game da me kenan"? "Ina nufin me zaki rubuta mashi"    "Nikaina,bansan me zan rubuta mashi ba,amma ki bani shawara,"ta ƙarasa maganar tare da samun wuri,saman drawer ɗin ta zauna,tana ci gaba da sauraronta, "abunda nakeso dake,kada ki ji tsoron komai,ki natsu ki kwantar da hankalinki,ki rubuta mashi duk wani abu da kika sani wanda baki so yana yi maki,wannan dama ce kika samu,"_    Ajiyar zuciya ta sauke tare da gyaɗa kai tace"shikenan,Zan rubuta mashi yanzu,"   "Yawwa my daughter,take care of ur self for me,Sai kinji daga gare ni,"   Daga nan sukayi sallama tayi rejecting kiran,    Juyawa tayi gefen hagunta tare da kallon jahad tace"Juliet,inason magana dake,idan kin kammala wayar,"   Juyowa jahad tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Ae mun kammala yin wayar ma tun ɗazu,wayarce kawai ban cire a kunne na ba,saboda ban gajiya da jin Voice ɗinshi,Expecially idan yanayi Mun shagawa6ar nan tashi,kamar in janyoshi ta cikin wayar,in manna mashi kiss,"   Fashewa Sehrish tayi da dariya,gami da girgiza kai,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Gaskiya ne,Juliet Matar Romeo,abun naku azimunne,"ta ƙarasa maganar a yayin da take komawa gefen gadon ta zauna,kafin ta kuma cewa"Am looking for ur advise,My lovely sis,"jin haka yasa jahad ta miƙe zaune daga kwancen da take,ta jingina bayanta jikin head board ɗin gadon,tana facing sehrish sannan tace"Shawarar me kike so in baki ne"?   Calmly sehrish tace"yau naje bama babban yaya haƙuri,Kinsan meya faru"? Hankali aɗan tashe jahad tace"Sae kin faɗa,"   Murmushi sehrish ta ɗan saki kafin ta cigaba da cewa"bai yi mun komai ba,ko yatsa bai ɗaga mun ba,Yanzu haka ma zancen da nake maki,Yace na rubuta mashi text message na duk abunda banso yana yi mun,"_   Wani irin ihun farin ciki jahad ta saki tare da furta"Yess!yess!"da alama abun ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,    "Wlh naji daɗi sosai!dama nifa koda nace kada kije ki bashi haƙuri saboda tsoran karya Bugeki ne,Amma yanzu Alhamdulillah,komai ya wuce,gashi har an samu ci gaba," "Yanzu me kike ganin ya dace na rubuta mashi?Mommy azeema tace kada naji tsoran komai na rubuta duk abunda nake so ya daina yi mun," Murmushi jahad tayi,tare da cewa"ta kwana gidan sauƙi,Ae yanzun nan zamu tsara mashi text message,Amma inaga kamar mu rubuta mashi ta whatsapp ko?zaifi tsayi rubutun ba kamar na text message ba,   Sehrish tace"Ni damuwata ma,kada musha wahalar rubutawa yaƙi karantawa,Saboda na ta6a tura mashi message,bai rubutomin reply ba,"   Jahad tace"kinsan shi mutunne mai jama'a,mutun mai farin jini irinshi bazai rasa dubban saƙonnin Masoyanshi ba,Shawarar da zan baki shine,Idan kin rubuta mashi message ɗin saiki jaraba kiran layinshi,idan ya ɗaga saiki sanar dashi cewa kin tura mashi,"   Jinjina kai Sehrish tayi,"kin kawo shawara mai kyau,"   "Yanzu dame dame Yake yi maki wanda bakya so"?Jahad tayi tambayar tana kallon fuskar Sehrish dake kallonta,   "Abu na farko,nidai bana son wannan tsawar da yake yi mun,na biyu bana son tsallan kwaɗin da yake sanya ni don ba ƙaramar wahala nake sha ba duk in nayi shi,Na uku kuma,banason yana hana ni zuwa part ɗinshi da make-up a fuskata....,"haka Sehrish ta shiga lissafa mata abubuwan da bataso,Bakomai yafi bama jahad dariya ba,fa ce Make-up da sehrish tace bata so yana hanata,cike da zolaya tace"in banda abunki,bashi kike yiwa kwalliyar ba?kuma yace bayaso,sae ki daina kawai,Kinsan ba ko wani namiji bane keson wannan ƙyaleƙyalen namu na mata,wani namijin ma baison ƙamshin turare,kowa fa da irin nashi ra'ayin,"   Harara sehrish ta ɗan wurga mata tare da cewa"Amma lokacin baya before wedding ɗinmu,ina yin make-up in shiga part ɗinsa bai ta6a hanani ba,sae bayan da aka ɗaura auren," Jahad tace"saboda yanzu ne yake da cikakken iko akan ki,Shiyasa ya hana ki,'   Ta6e baki sehrish tayi kafin ta mayar da idanuwanta kan wayar,Ta shiga whatsapp ɗinta,Contact ɗinsa ta nemo wanda tayi mashi saving da *My Boss man*,ta shiga Cikin Chat ɗinsa,sau ɗaya ta ta6a yi mashi sallama,bai duba ba,"   A hankali ta soma rubuta mashi saƙon,    "Sehrish,me zai hanaki ki ɗan rubuta mashi cewa,ya dinga sakar maki fuska,koda bazaiyi murmushi ba"?   Wani bazawarin kallo sehrish ta jefa ma Jahad,a ƙule tace"idan ya tashi cin ubana,ae baki a kusa balle ki kawo min agaji,Ni na isa in sanya wannan fuskar tashi,ta dinga yi mun murmushi,?kina ganin ko su Abba in yana tare dasu baya murmushi,shifa naturally haka face ɗinshi take,a tamke," Dariya jahad tayi tare da kai hannu ta dafa shoulder ɗin Sehrish "Kada ki damu My own sister,Very soon fuskar yaya rafayet,zata koma kullum a washe,amma fa sai ranar da kika haifa mashi baby,"   Fashewa tayi da dariya,jin abunda jahad tace mata,   Can kuma tace"Anya,Babban yaya yana son ƴa'ƴa kuwa?irinsu fa kamar basu damu da haihuwa ba,yawanci ma basu son matansu su haihu,Akwai wani American film dana ta6a kallo,Bature ne mutumin har yakai shekara 80 bai ta6a haihuwa ba,Saboda yana da wani ɗan karensa,shiya ruƙa a matsayin ɗansa,yawanci kuma zaki ga basu son haihuwa da yawa,ɗaya zuwa biyu,sae kiga sun kwallafa rai akan ƴa'ƴan nan,"   Jahad tace"Amma shi Half cast ne!(ruwa biyu)ba dole bane komai ace irin nasu ya ɗauko,Duk da yafi ƙarfi ta 6angaren Mommynsu,kuma acan ya taso duk ɗabi'unsa da halayansa,in kika lura irin nasu ne,Amma daga gani kamar zaiso ƴan babies,ke in ma baiso,to akan ki zai fara son ƴa'ƴa,"ta ƙarasa maganar tana dariya Murmushi sehrish tayi a yayin da idanuwanta ke akan screen ɗin wayarta,har tayi nisa cikin rubuta mashi saƙon,   "Jahad,bansan meyasa kikeso in samu ciki ba,kullum baki da zance sai na in samu ciki,in haifa ma babban yaya baby,bayan kinsan cewa nan da wani ɗan lokaci auren zai mutu,"tayi maganar muryarta a sanyaye,   Jahad tace"saboda na ta6a yin mafarki ne,kuma acikin mafarkin na ganki da ƙaton ciki,sai gashi kuma kin haihu,Kinsan me?tayi tambayar batare da tajira amsar sehrish ɗin ba taci gaba da cewa"babyn da kika haifa Triplets ne kuma dukkansu maza ne,Ƙwayar idonsu blue ce kalar ta babban yayanmu,gashin kansu ma kwantacce ne irin nashi,hasken fatarsu da komi irin nashi ne.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda jin saukar pillow da tayi asaman fuskarta,wanda Sehrish ta jefa mata shi,   "Maƙaryaciya kawai,daga jin wannan ƙirƙirarran labari ne,babu wani mafarkin da kika yi,"_   Dariya sosai sukayi,ba ƙaramin nishaɗi suka samu ba Bayan ta kammala rubuta mashi saƙon,Miƙa ma jahad wayar tayi don ta duba ta gani in akwai abunda ya dace su ƙara,Kar6ar wayar jahad tayi tana karanta message ɗin har yazo karshe,Sannan tace"komai yayi yadda akeso,tura mashi sakon sai ki kirashi,"   Tura saƙon sehrish tayi bayan ta kunna WI-FI ɗinta,nan take saƙon ya isar mashi,phone call ta shiga tare da danna mashi kira,    Kusan sau biyar tana kira ba'ayi picking ba, Jahad tace"mu haƙura zuwa anjima yanzu haka suna aikine," *Boss Bature* Wuraren ƙarfe 6 na marece,wata danƙareriyar mota tayi parking a cikin wani katafaren hotel,a parking space motar ta tsaya,jim kaɗan wata matashiyar budurwa ta fito daga cikin motar,jikinta na sanye da riga bubu ta material,ƙafarta kuwa na sanye cikin high hills,ta coge ɗaurin kallabin nan na rashin ɗa'a,Sae faman taunar cingam takeyi abakinta,    Hannunta na ruƙe da ƴar purse ɗinta,ta sagala mayafin asaman kafadarta, ....fitowa wani matashi yayi daga gaban motar,daga ganinsa zakasan cewa ba ƙaramin shege bane,kuma tantirin ɗan iska,   Zagayawa yayi tare da buɗe boot ɗin motar ya ɗauko mata trolley ɗin kayanta,sannan ya kalleta tare da cewa"Babe,Mu shiga ciki ko?in ɗan taka maki" Murmushi Abrah,ta saki tare da nuna mashi hanya tace"bismillah,"gaba tayi yabi bayanta,suna tafiya yana yi mata sambatu,"Gaskiya zanyi kewarki sosai baby,bansan ya rayuwata zaka kasance ba,idan babu ke,zan zama tamkar maraya,"_   Abra tace"hmm,dama ka daina yi mun wannan daɗin bakin naka wlh,Don na sanka,mayen mata ne,Allah kaɗai yasan yawan matan da kake mu'amala dasu,Ni bansan ma tanawa bace,"_    "Subhanallah,Zargina kikeyi ma kenan?babu kyaufa,"   "Ba zarginka nake yi ba,zahiran na gani ae,"suna magana suna tafiya har suka shiga cikin reception,mutane ne ke ta safa da marwa a wurin,Batare da sun sha wahala ba,ta hango Aunty babba tana tunkarosu,Fuskar nan aɗaure babu annuri,Amma tana hango saurayin da Abra tazo dashi,nan take ta ɗan saki fuskarta,ƙarasowa tayi wurinsu,   "Sannunku da zuwa ya gajiyar tafiya,"    Saurayin ya amsa mata"Alhamdulillah,Mun same ku lafiya,"   "Lafiya lou,"kafin ta mayar da idonta kan abra tace"Wanene wannan kuma?yakamata a gabatar mun dashi,ko da yake bari mu shiga daga ciki,'tayi maganar tana yi masu nuni da hannunta,   Saurayin yace"kash,bazan samu shiga ciki ba,ina sauri ne zan wuce wurin wani uncle ɗina dake anan,Urgently yake nemana,"    Aunty babba tace"Amma banji dadi ba,duk irin wannan ɗawainiyar da kayi mana,bazaka shigo daga ciki ba ka huta,ko lemu ne ka ɗan sha,'   "Kada ki damu Aunty,Idan kuka dawo daga tafiyar zanzo ne sai mu gaisa dakyau,"    "Aunty wannan shine Bobby ɗin da nake baki labarinshi,Yana da kirki sosai,Saboda yana kyautatamun,"ta ƙarasa maganar,fuskarta dauke da murmushi,   Aunty babba tace"Ma sha Allah,naji daɗin ganinka sosai,Allah dae ya nuna mana ranar aurenku,Musha biki,'   Murmushi ya saki yana faman shafa keyarshi da hannunshi,     "Bari mu shiga daga ciki,Sae munyi waya,"acewar Abra,    "Okey babe,ki kulamun da kanki,Sae kinga saƙona,"    Ya ƙarasa maganar tare da juyawa yabar reception din,Aunty babba tayi gaba Abra tabi bayanta,Har izuwa cikin ɗakin da ta kama,     Suna shiga cikin ɗakin abra ta saki trolley din kayan,ta faɗa saman gadon ta kwanta tana faman sauke ajiyar zuciya,     Daga gefen gadon Aunty babba ta zauna,tare da kallonta tace"kun sha tafiya,toh ya ku ka baro su mammyn'?   "Tana can,rai hannun Allah,ae na faɗa maki cewa bata da lafiya,Amma da sauƙi dae,tunda tana ɗan mikewa har ma ta zauna,Matsalar dae babu mai kula da ita,Shima Abie ya tattara yana shi yana shi yabar gidan,yanzu ita kaɗai ce acikin gidan,bansan ya zata ƙare ba,"hankalinta kwance take yin maganar,   Shiru Aunty babba ta ɗan yi,batare da ta janye idanuwanta daga kan fuskar abra ba,   "Aunty kinyi shiru,ba kice komai ba?wai nikam Ina Aunty hayaam ne'?nayi tunanin zan ganku atare ne,kuma nayi mamakin ganinki a hotel"    Harara ta ɗan watsa mata tare da cewa"in ba a hotel ba,a ina kikeson ki ganni ne?Ko bakisan cewa aure na ya mutu ba"? ...ƙumshe dariya Abra tayi,     "Kiyi mai isarki lokacinki ne ƴar rainin hankali,Muna nan cikin tashin hankali,ke kina can kina holewarki,wato kin samu duniya ko"?   Turo baki abra tayi tana fadin"matsalar kenan fa,yanzu nasha wahalar tafiya,ko ruwa ban sha ba,Amma zaki fara yi mun faɗa,Allah in naji ban iyawa,sae dai ki neme ni ki rasa,"    Sakin baki Aunty babba tayi tana kallonta,kafin tace"lallaine wuyanki ya isa yanka,fiye da haka ma zaki iya faɗamun,"     murguɗa baki abra tayi tare da cewa"na tambaye ki Aunty hayaam amma baki ce komai ba,tana ina,"?    Ta6e baki Aunty babba tayi kafin tace"Ae hayaam ni kaina bansan inda take ba,kinsanta bata gajiya da yawo,yau kusan kwana uku banganta ba,sae dai ta kirani mu gaisa,Amma ni kona kirata a kashe nake samun wayarta,"   Saboda rashin tsoran Allah,Aunty babba ta zauna tana shirgawa Abra ƙarya,don tasan cewa muddin Abra taji cewa,hayaam na kwance gadon asibiti ba lafia,baza ta ta6a yarda suyi tafiyar nan da ita ba,Sai ta tsaya tayi jinyarta,kuma in taji cewar ta bar ƴar uwarta a asibiti babu mai kula da ita,to tabbas ranta zai 6aci sosai,"    "Kai Aunty hayaam,ita ma dae kamar wadda taci ƙafar kare,bata nan bata can,"   Aunty babba tace"Ni duk ba wannan ba,Kinsan dai dalilin dayasa nace kizo ko"?   "Eh nasani,"ta bata amsa, "Yawwa,Jibi nakeso mu shirya mu tafi,lokacin kin huta sosai,"   Yatsina fuska Abra tayi,tana ɗan gatsina hanci tace"Oh ni,yanzu haka zamu kwasa mu tafi wurin boka har enugu,cikin dajin Allah,Kamar waɗanda basu da mafaɗi,Kuma dae babu tsoran Allah..... "   Tunkan ta ƙarasa maganar Aunty babba tace"Rufe mun baki,Uwar surutu sai kace aku,Duk ba don ku akeyi ba?don rayuwarku tayi kyau," fuskarta aɗaure tayi maganar,   Zumbura baki abra tayi,tare da yin ƙasa ƙasa da muryarta tace"mutun yayi sallar dare mana,ya roƙa wurin wanda ya halicce shi sai wani boka can"   "Me kikace"Aunty babba tayi tambayar tana kallonta,Don tajiyo ƙusƙus ɗin da take yi,  Abra tace"Ni Bance komai ba,idan ma nayi magana to akan abinci ne,yunwa nake ji,"ta ƙarasa maganar tana shafa stomach ɗinta,    "Okey,bari nayi mana order,sae muci atare,don nima banci komai ba,"    Wuraren ƙarfe 7,Motoci guda biyu suka shigo cikin gidan a jere,a lokacin Jahad da Sehrish suna a kitchen tare da Aunty azmee suna tayata aiki,Azmee na agaban gas cooker,Sehrish da jahad,suna yanke yanken kayan lambu,   Jin dirar motacin nan yasa Sehrish saurin cewa"Ga babban yaya nan ya ƙaraso gida,"   Jahad tace"Anya kuwa shi ne?Junaid fa ya sanar dani cewa yau ko gobe zasu dawo,Allah yasa su ne,kada abunda na haɗa mashi ya lalace,"   Murmushi sehrish ta saki,tana cewa"Mrs romeo,Ae koda bai dawo ba,mu zamu cinye kayan daɗin da kika haɗa mashi,".   Muryar azmee suka jiyo daga bayansu tana cewa"Nima hadani za'aci daɗin,"   Dariya su kayi gaba dayansu, Jahad tace"idan zaki ci Aunty azmee babu damuwa,Amma Allah koda bai dawo yau ba,ƙwara na zuba shi a dustbin da dai inba su rishi suci"   Harara sehrish ta ɗan watsa mata da yake suna facing ɗin juna na,tace"saboda baƙin hali irin na ɗan adam,'    "Aunty azmee ina da tambaya dan Allah,"acewar jahad,   Azmee tace"Allah yasa na sani," Murmushi jahad ta yi tare da cewa"Tsakanin babban yaya da Junaid waya fi wani kyau,"   Har sai da gaban azmee ya faɗi rass,Saboda girman tambayar da tayi mata,jinjina kai tayi na wani lokaci kafin tace"tashin hankali,Kuma ni kike so in amsa maki tambayar,"   Jahad tace"Eh,saboda nasan kinsan menene kyau,zaki iya fadin wanda yafi kyau acikinsu,"   Sehrish tuni ta dakata da yankar lettuce ɗin da takeyi,hannunta ruke da wuqa,duk ta qagara taji amsar da azmee zata basu,   "Ni ko a school,ban ta6a haɗuwa da question mai wuyar Amsawa ba irin wannan,To ae dukkansu kyawawane na bugawa a jarida,Junaid kyau rafayet kyau,"   Dariya sukayi jin yadda azmee keta nanata maganar,da alama sun caza mata kai,    "Amma ni a ganina,kamar junaid yafi kyau,saboda shi fuskarshi kullum asake take,Kuma wannan murmushin nashi ba ƙaramin kyau yake ƙara mashi ba,"acewar Sehrish, Jahad tace"Amma ae bai kai yaya rafayet tsayi ba,duk da shi ma dogone,kuma baida irin surar jikin babban yayan mu,"   Sehrish tace"Ae da ace shima junaid ɗin zai dinga motsa jiki,in a short time zaki ga ya koma kamar babban yayan mu,ae su maza daga sun fara ɗaga ƙarfe Jikinsu ke buɗewa,"   Azmee tace"hakane kema kince wani abu anan,Gaskiya dukkansu zan iya cewa babu wanda yafi wani kyau,idan don saboda murmushi zaisa junaid ya ɗare rafayet a kyau,to ae shima rafayet ɗin idan yayi murmushi sai kin kusa zaucewa,kilan bai ta6a yin murmushin bane kun gani,sannan kuma ga surar jiki ta ko'ina dae su duka biyun sai dai ace ma sha Allah..."zugudum sehrish tayi tana sauraron abunda azmee ke cewa,aranta tace"Kutmelesi,Su Aunty azmee har ansan su babban yaya nada kyawun sura,da kyakkyawan murmushi,ba dai kalle mun mijina takeyi ba,"ta ɗan yi maganar hada tamke fuska,can kuma ta fashe da dariya...,   Suna cikin tattaunawar nan,Suka jiyo Muryar Junaid yana sallama,aikuwa jiki na rawa jahad ta ajiye knife din dake hannunta,da gudun gaske ta fito daga kitchen din,   Yana a tsaye,jikinshi sanye da shadda brown colour,hannunshi ruke da trolley,fuskar nan ɗauke da ƙayataccen murmushi,duk a tunaninta shi kaɗai ne,hakan yasa ta nufe shi da gudu zata rungume shi,ƙiris ya rage ta ƙarasa,Sae ga Marshal Omar da Uncle abusufyan sun shigo,da sauri taci burki,tana faman sauke ajiyar zuciya,Fashewa junaid yayi da dariya yana kallonta,saboda ya gane abunda taso tayi,Su uncle sunyi mashi buƙulu, .....hannu tasa ta rufe fuskarta,tana dariya, Murmushi marshal ya saki,haka shima abusufyan ɗin,Jahad sarkin kunya,    Fitowa sehrish tayi daga cikin kitchen ɗin,fuskarta ɗauke da murmushi,da sauri ta ƙarasa wurin abusufyan,hugging ɗinshi tayi tare da cewa"sannu da dawowa Daddy,ya gajiyar tafiya,"?ta ƙarasa maganar tare da ɗagowa daga jikinshi, Hannu yasa tare da shafa fuskarta yace"lafiyalou My Daughter fatan na same ku lafiya,"yayi maganar yana miƙa ma jahad hannu,cike da jin kunya ta ƙarasa wurinshi,ya rungumota ajikinshi,   Marshal Omar yace"Oh ni,babu mai yin hugging dina,daddynku kawai kuka sani,babu komai nasan da hosana na nan,da gudu zata bani hug" dariya sukayi gaba ɗayansu,haɗa baki sukayi wurin gaishe dashi,Ya amsa masu fuskarshi a sake,   "Lah ya Omar,"muryar hosana ce ta katse su,ɗagowa su kayi gaba ɗaya suna kallonta,Da alama daga bacci ta taso,sae faman lumshe ido takeyi,   Kai tsaye ta tunkarosu,kamar yadda yayi tsammani,ko Daddynsu bata runguma ba,wurinshi ta wuce,ta rungumeshi tare da kwantar da kanta saman wide chest ɗinshi,'   Jinjina kai Abusufyan yayi tare da cewa"Hosana ko kallo ban isheki ba ko?,hankalinki na akan Omar," Yayi maganar yana kallonta,    Murmushi ta saki tare da ɗagowa daga jikin Omar ta koma wurinshi,zata rungumo shi da sauri yaja da baya yana cewa"bana so,babu ruwana dake,ki koma wurin Omar ɗin,Ae ni baki damu dani ba,burina kawai in dawo gida don saboda ke,Amma shine kika watsa mun ƙasa a ido,"   Dariya suka shiga yi gaba dayansu,hosana kuwa bubbuga ƙafa ta shiga yi muryarta tamkar zata yi kuka tace"pls daddy,let me hug u,wlh nayi missing ɗinka sosai,kawai dae nayi alƙwarin cewa,zan fara tarbar Ya Omar ne kafin kai,kuma banso in karya alƙawarin dana ɗauka,"    Abusufyan yace"ae gashinan ko?Dama na yafe mashi ke,Ni ga ƴan tagwaye na nan,su da suka damu dani,'yayi maganar yana nuna su sehrish,   Zumbura baki tashiga yi,tana murmura masu baki,   Ruko hannun Omar tayi tare da jan shi tace"Mu tafi ya Omar,kayi wanka kaci abinci,Sannan ka kwanta ka huta,"Bin bayanta Omar yayi fuskarshi ɗauke da Murmushi,   Girgiza kai Abusufyan yayi tare da cewa"Allah ya shirya min ke Hosana,Abun naki sai addu'a,"   Ya ƙarasa maganar tare da ruƙo hannayensu Sehrish suka wuce cikin palourn,sun ɗan zauna anan suka ƙara gaisawa da daddyn nasu kafin daga bisani,suka barshi ya wuce bedroom ɗinshi don ya huta, Wuraren ƙarfe 12 na dare,lokacin har sun kammala dinner ɗinsu tuni,Sun koma cikin bedroom ɗinsu,batare da 6ata lokaci ba,Su ka shirya cikin kayan baccinsu,sun kwanta ajere cikin lallausan bargonsu,   Kwankwasa ƙopar ɗakinsu akayi kwankwan,     "Wanene"?jahad ce tayi tambayar,saboda itace ta rage  idonta a buɗe,   "Zo ki buɗe mun kopa,"da sauri ta saukko daga saman gadon jin muryar junaid,   Hannu tasa tare da buɗe kopar,Yana tsaye cikin sleeping dress dinsa white colour,hannunshi ruƙe da Shopping bag,".    Junaid dama ba kayi bacci ba?tayi tambayar tana ƙare mashi kallo,sae hamma yake saki,    Ashagwa6a yace"Na fara bacci mana,Mommy azeema ce ta tashe ni,saboda kawai wannan saƙon na rishi da tace na kawo mata,"   Yayi maganar yana nuna mata ledar hannunshi,    "Eyya,Amma banji daɗi ba,but am sorry,kawo saƙon na ajiye mata,don har bacci ya ɗauketa,"   Miƙa matar bag din yayi,ta sanya hannu ta kar6a,sannan ta juya zata shiga ciki,da sauri ya ruƙo hannunta tare da janyota ta faɗo jikinshi,hugging ɗinta yayi tightly tare da cewa"I really missed u my Juliet,"   Lumshe ido jahad tayi tana shaƙar ƙamshin turaren jikinshi tace"I missed u too my Romeo,"_ Kiss ya manna mata asaman cheek dinta,sannan ya raba jikinta daga nashi,tare da juyawa yabar bedroom ɗin, Har sai da ya 6ace ma ganinta,Sannan ta tura kopar tare da shigewa ciki,A gefen gadon daga ƙasa ta ajiye bag ɗin,batare da ta buɗe taga menene aciki ba,ta haye saman gadon ta kwanta fuskarta dauke da murmushi,    "Jahad har yanzu yaya rafayet bai dawo ba"!?   Muryar Sehrish ce ta katse ta,da sauri ta juya left hand ɗinta tana kallonta,a rufe ta samu idanuwanta tamkar mai yin bacci ashe likimo tayi,    "My own sis,ashe bakiyi bacci ba,"?   "Idona biyu jahad,baccin ne yaƙi zuwa,"    Jahad tace"Yakamata kiyi bacci,kinsan da anjima idan babban yaya ya dawo zai tashe ki ne,so it's better ki kwanta yanzu,ko kin samu bacci na minti 30,"   "Ae baccin ne yaƙi zuwa,"tayi maganar tana ƙoƙarin buɗe idanuwanta,   "Wanene ya shigo ɗakin nan?ko daddy ne,"?   "Junaid ne,ya kawo saƙo yace naki ne,Inji Aunty azeema"jin haka yasa sehrish miƙewa daga zaune,tana faɗin"ina sakon yake," Hannu jahad tasa tare da ruƙo hannun bag ɗin,ta ɗago da ita,izuwa saman gadon ta miƙa ma Sehrish,hannu tasa ta kar6a,tare da ajiyeta agabanta,tana faman yin hamma,kamar mai jin yunwa,   Buɗe shopping bag ɗin tayi,tare da ɗan leƙa kanta tana kallon kwalaben dake acikinta tare da robobi,aranta tace"ko na menene wannan,bari dai na ajiyesu,zuwa gobe nasan zatayi mun bayani akansu,"ta ƙarasa maganar tare da matsawa ta ajiye bag ɗin saman side drawer,sam bata son bacci ya ɗauketa,saboda tasan cewa lokacin dawowarshi yayi harma ya wuce,jingina bayanta tayi ajikin head board din gadon,Sae faman yin hamma takeyi tana gyangyaɗi amma taƙi yarda bacci ya ɗauketa,tana yi tana kallon wall clock,kusan ƙarfe ɗaya,amma basu dawo cikin gidan ba,duk yadda taso ta hana bacci ɗaukarta,amma hakan ya faskara a zaune ta fara baccin,itama jahad tuni bacci yayi awon gaba da ita,Hosana dama tuntuni ta ƙundundune cikin bargo tana sharar baccinta, A round 1:30 na dare,Motarsu ta shigo cikin gidan da gudun gaske ta shararo har izuwa parking space,tsayar da motar Armstrong yayi tare da fitowa,da hanzarinsa ya zagaya tare da buɗe mashi kopa,a hankali ya zuro da ƙafarshi,after some minutes ya ƙarasa fitowa daga cikinta,Hannunshi na'a dafe da forehead ɗinsa yayin da idanuwanshi ke a lumshe,da alama babu cikakkiyar lafiya atattare dashi,tun daga kan yadda yake fitar da numfashinsa,    "Sorry sir,idan ba damuwa zan iya taka maka,mu shiga daga ciki,naga kamar ba zaka iya ƙarasawa ba".     A hankali ya furta"don't worry ur self,Zan iya tafiya da kaina"yayi maganar tare da kama hanya ya wuce cikin gidan,tsayawa armstrong yayi yana kallonshi har saida yaga shigar shi kopar falon gidan,Sannan yabar wurin motar,   Babu kowa a main palour ɗin,dakyar yake tafiya har ya samu ya hau saman staircases ɗin,Ya wuce part ɗinsu,hannu yasa ya tura kopar,ya shiga daga ciki,Direct ya wuce bedroom ɗinshi,zame t-shirt ɗin dake ajikinshi yayi tare da yin wurgi da ita saman gadon,daƙyar yake fitar da numfashi mai hucin zafi,idanuwanshi kansu daƙyar yake iya buɗe su,.   Hannunshi yakai tare da ruƙo belt ɗin wandon jikinshi ya cireshi,ya duka ya cire takalmansa,sai da ya rage daga shi sae Short ajikinshi,yana ƙoƙarin zame safar ƙafarsa,kira ya shigo cikin wayarshi,hannu yakai tare da daukarta,inda ya ajiyeta saman side drawer dinshi,duba screen ɗin wayar yayi,da hidden number aka kirashi,Abun yayi matuƙar daure mashi kai,muddin aka kirashi da hidden number sai Ainihin sunan mai number ya bayyana,amma wannan kiran a haka ya shigo mashi,    Picking call ɗin yayi tare da kara wayar a kunnanshi,Shiru ba'ayi mashi magana ba,shima kuma bai tanka ba,yana ƙokarin rejecting kiran yaji shessheƙar kukan mace,kuka fa sosai tamkar zai fasa screen ɗin wayar,da sauri ya janye wayar daga kan kunnan shi ya zuba ma screen ɗin wayar ido yana kallonshi,cike da mamakin wacece wannan ta kirashi tana raira mashi kuka a irin wannan lokacin"? Rejecting kiran yayi,yana ƙoƙarin ajiye wayar,text message ya shigo wayarshi,on the top of the screen message din ya bayyana,   Karanta saƙon ya shiga yi kamar haka,   _Rafayet bazan ta6a bari na rasa ka ba,Zan iya yin komai akanka don na mallake ka,koda kuwa kisan kaine,Na jima da sha'awar son kasancewa tare da kai,alƙawarine wannan na ɗaukarwa kaina_   Bai damu da saƙon daya gani ba,Saboda yasha haɗuwa da ire-irensu,sun yi nacin har sun gaji sun daina,Amma wannan baisan dame tazo ba,hada ikirarin zata iya yin kisan kai akanshi,koma wacece wannan ba ƙaramar ƴar daba bace da alama,   wurgi yayi da wayar saman gadonshi,Sannan ya juya daƙyar yake ɗaga ƙafarshi har ya samu ya shige cikin toilet, *Sehrish* Firgit ta farka lokaci guda ta miƙe a hanzarce ta wurga idanuwanta kan agogo,ƙarfe kusan 2 na dare,durowa tayi daga saman gadon hankalinta aɗan tashe,sai da ta fara zuwa window ta leƙa taga Motarsu,sannan ta fito da sauri,riga da wandone ajikinta,kanta kuma na sanye da mayafi ta ɗaureshi amatsayin kallabi,tafiya takeyi tana sambatu ga bacci da bai bar idanuwanta ba, Kitchen ta shiga,jim kaɗan ta fito hannunta ruƙe da tray,Coffee ne asaman shi tare da Fruit,tana ƙokarin hawa upstairs taji ance"Sannu da ƙoƙari," Cak ta tsaya da tafiya,yayin da zuciyarta tayi wani irin bugu ji kake rasss!,a hankali ta juya don taga wanene yayi mata maganar,Waro ido waje tayi ganin babu kowa a babban falon,kuma tabbas taji anyi mata magana,ranta ne ya bata cewa kodai kunnuwanta ne suka jiyo mata hakan,tuna wannan yasa ta sauke ajiyar zuciya ta wuce part dinshi,a bakin kopar shiga bedroom ɗinshi ta tsaya ta fara yin sallama,jin bai amsa mata ba yasa tayi tunanin ko bacci ya ɗauke shine ko kuma ya shiga cikin toilet ne,   Sanya kafa tayi ta shiga cikin ɗakin,Ƙarasawa tayi wurin table ta ajiye mashi tray ɗin,Sannan ta ɗan jinkirta tana jiran fitowarshi daga cikin toilet ɗin,har lokacin bata daina yin hammar bacci ba,idanuwanta kuma na rufewa,da alama baccin zata cigaba da yi atsaye,   Tana cikin tsayuwar nan tajiyo sautin aman shi daga cikin toilet,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,bakomai ya faɗo mata arai ba,fa ce abunda ya faru tsakaninta dashi a daren shekaranjiya,kada ace har yanzu ƙyanƙyamin jinin daya gani ajikinta ne yake sa shi yin amai,Nan take taji jikinta yayi wani irin sanyi.........."bata ƙarasa zancen zucin nata ba,Taji motsin fitowarshi daga toilet,   Tsautsayi da ƙaddara ne yasa Sehrish yunƙurin juyawa don taga a wani hali yake ciki,Aikuwa A gigice ta fasa ƙara,firgitar da tayi ne yasa ta yanke jiki ta faɗi ƙasa a sume,Da sauri Sgr ya koma cikin toilet,tare da jan kopa ya rufe,sam baiyi tsammanin akwai mutun a bedroom ɗin nashi ba,Shiyasa ya fito a naked ɗinsa,babu kaya ajikinshi,Sehrish taga abunda yafi ƙarfin idanuwanta,   Bada jimawa ba,ya kuma fitowa daga cikin toilet ɗin,Waist ɗinshi ɗaure da towel,ya saki sumar kanshi ta baya,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,yadda ta yanke jiki ta faɗi a sume saboda kawai taganshi babu kaya ajikinshi,kamar taga wani mugun abu?ko kaɗan baiji kunyar komai ba da ta ganshi a haka din,sae ma mamakin sumewarta da yayi,sam baya jin ƙarfin jikinshi,Ƙarasawa yayi wurin da take a sume ƙasa,ya zuƙunne saman guiwarsa ɗaya,Hannayensa ya sanya tare da ɗaukkota ya kinkimota A saman shoulder ɗinshi,A ƙoƙarinsa na yakai ta bedroom ɗinsu,yana ƙoƙarin miƙewa tsaye da ita dauke a kafaɗarshi,Cikin rashin sa'a ƙafafunshi suka harɗe a jirkice ya saki jikinshi gaba ɗaya suka faɗa saman katafaren gadon nashi yaraff nan take mayafin da ta rufe hair ɗinta dashi yabar kanta,kwantacciyar sumar kanta ta tarwatse asaman gadon, Tunda suka faɗa saman gadon sehrish ta farfaɗo sakamakon ruwan daya Yarfo mata asaman fuskarta,Ruwan sumar kanshi ne daya fito daga wanka bai tsaneta ba,numfashin mutun ta dinga ji da ɗumi duminsa asaman fatar ƙirjinta,tarasa gane maiya faru da ita,meya ke faruwa ne?taji an danneta,wani irin nauyi tamkar an ɗaɗɗaure jikinta haka ta dinga ji,    A hankali ta buɗe idanuwanta,kai tsaye suka fuskanci ceilling,gabanta ne ya faɗi rass,hannu tasa don taji menene ajikinta,kai tsaye hannunta ya sauka akan lallausar sumar kanshi,shafa sumar ta shiga yi,lokaci guda ta tuna cewa a ɗakin Sgr take,A matuƙar tsorace ta ambaci sunanshi"Ya Rafayet,"shiru bai amsa ba,hakan ba ƙaramin ruɗu ya sanyata ba,    ƙoƙari yake don ya tashi daga jikinta,Amma hakan ya faskara,a karo na biyu yayi yunƙurin miƙewa,ɗagowa yayi da kanshi yana faman cizon la66ansa,a hankali ya ware sexy blue eyes ɗinshi,kai tsaye suka sauka akan ƙirjin sehrish,Nan take ya tsinci kanshi da bin surar kirjinta da kallo,gaba ɗaya rigar jikinta ta zamo,sakamakon faɗawar da sukayi saman gadon da hannunshi ya zame rigar batare daya sani ba alokacin da yake ƙoƙarin ɗaga jikinshi daga nata,dukiyar fulanin nan nata a tsaitsaye dasu tubarkalla ma sha Allah full ɗinsu,gwanin ban sha'awa,   Lokaci guda yabi ya susuce,ya tsinci kanshi a wani irin yanayi,Sehrish kuwa tunda ya ɗago da fuskarshi,hankalinta yayi mugun tashi,duk tabi ta ruɗe ta firgita,jikinta sae kerma yake yi,Sam bata lura da abunda yake kallo ba,sae faman lumshe idanuwanshi yakeyi yana buɗesu a hankali,yayin da maƙoshinshi ke motsi,kamar yana swallowing wani abu,wata irin zufa ce ta shiga tsastsafo mashi a gefen fuskarshi,ganin haka yasa ta ƙara tsorata,saboda tunawa da abunda ya ta6a faruwa a tsakaninsu,lokacin da haroon ya bata allurar nan,tuna wannan yasa hankalinta ya ƙara tashi,la66anta sae kerma sukeyi,a hankali ta furta"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un..."sautin muryarta ne yaja hankalinshi,mayar da idanuwanshi yayi akan fuskarta,wani irin kallo ya shiga bin ta dashi,    Moving face ɗinshi yayi saitin fuskarta,da sauri ta runtse idanuwanta yayin da ta ke ci gaba da ambaton hakan,numfashinsu ne ya shiga haɗuwa dana juna,tana ƙoƙarin buɗe idanuwanta,taji tausasan la66ansa asaman nata la66an,tongue ɗinshi ya zura acikin bakinta,lokaci guda Sehrish tabi ta rikice ta susuce,ta fita hayyacinta,kamar yadda shima ya fita nashi hayyacin,haɗa bakinsu su kayi cikin na juna,suna exchanging saliva ɗinsu,hot french kiss ya shiga mata,tun daga kan lower lip ɗinta ya soma tsotsarshi sosai,laushinsu yasa shi ƙara zabura,gaba ɗaya yabi ya rikice,hannayenshi kuwa tunda ya damƙi boobs ɗinta dasu,ya shiga murzarsu,gaba ɗaya ya kara susucewa,ya zauce ya soma sakin nishi,almost 30 mins ya zame mouth ɗinshi daga nata,ya mayar dashi saman nipples ɗinta,ya kama tamkar jinjiri ya shiga sucking ɗinsu,bada wasa ba,Jikinshi har wani kerma yake yi,tamkar wanda ya shekara da yunwa atattare dashi,raɗaɗin da tafara ji ne ya dawo da ita cikin hayyacinta,a lokacin har yana ƙoƙarin Zame towel ɗin jikinshi bcos all he needs at dat moment was to do it,da alama ya manta halin da amaryar tasa ke ciki na rashin yin salla,a wani irin firgice da iya karfinta na ƙarshe,ta daddage ta ingije Sgr daga jikinta,a wani irin kasalance yayi gefe guda yana faman sauke ajiyar zuciya,jikinta sam babu ƙwari haka ta miƙe da sauri ta dira daga saman gadon,har tana tuntu6e wurin ƙoƙarin guduwa daga bedroom ɗin nashi,tamkar wadda zombie ya biyo,ko mayafinta bata tsaya dauka ba,boobs dinta ma da hannuwanta ta tar6esu sai daga baya ta janyo rigarta da ta zame kasan stomach dinta,ta zura hannun rigar,gudu gudu sauri sauri tabar part ɗinshi,duk ta bi ta ruɗe ta rasa in da zata dosa,Allah dae ne ya kawota ɗakinsu,don kuwa bata cikin hayyacinta,lamarin ya girmi tunaninta,a wani sukwane ta faɗa bedroom ɗinsu,a edge of the bed ɗin,ta zube jikinta naci gaba da yin kerma,hakoranta har gamewa suke yi dana juna kaf kaf,tamkar wadda sanyi yayi ma mugun kamu,ƙanƙame jikinta tayi yayin da idanuwanta ke rurrufewa,wata irin matsananciyar sha'awace ta rufe ta, Ita kenan,A 6angaren Sgr kuwa tun bayan da ta bar part ɗinsa,bai iya motsa koda yatsansa ba,jibgewa yayi saman gadon tamkar kayan wanki,ga wani irin raɗaɗi da yake ji a kasan mararsa,abun da bai ta6a yi ba arayuwarshi yau ya ɗanɗana ma kanshi,bazai iya tantance meke faruwa dashi ba,wata irin kasalace ta rufeshi,ya jima yana juye juye asaman gadon,cikin wani irin mawuyacin hali kafin Allah ya kawo mashi sauƙin jikin nashi,har bacci yayi awon gaba dashi, *Boss Bature* Wuraren sallar asuba,azmee ta kwankwaso ƙopar bedroom ɗinsu,kwankwan,dogon numfashi Sehrish taja tare da buɗe idanuwanta,waɗanda suka canza launi izuwa ja,tamkar wadda tayi ciwon ido,har cikin kunnanta take jin bugun ƙopar ɗakin nasu,amma ta kasa buɗe baki tayi magana,   Jahad ce ta farka daga bacci tana tambayar wanene,Muryar azmee tajiyo daga waje tana cewa"Aunty azmee ce,Lokacin sallah yayi,bansan ko kun tashi ba,"   "Yanzu muka tashi Aunty azmee,muna godiya sosai,"juyawa azmee tayi tare da barin ƙopar dakin,   "ku tashi rishi lokacin sallah yayi,dan Allah a hanzarta tashi,Sallah tafi bacci da minshari alkhairi,"cike da zolaya takeyin maganar kamar yadda ta saba yi in zata tashe su,zura hannunta tayi abayanta tana ƙoƙarin lalubo sehrish dake kwanciya abayanta wayammm taji babu kowa,ranta ne ya bata cewar kodai ta shiga toilet ne,gyara kwanciyarta tayi tana jiran fitowar sehrish daga toilet ko ta samu itama ta shiga tayi al'walar,duk wannan surutun da jahad keyi A kunnan sehrish tana sauraron Muryarta, Lalla6awa tayi da rarrafe ta nufi toilet,daƙyar ta iya miƙewa tsaye,a hankali ta tura kopar ta shige ciki,batare da tabari jahad ta ankara da ita ba, After some minutes,ta fito jikinta ɗaure da towel,jin motsin fitowarta,yasa jahad saukowa daga saman gadon,      Ta nufi wurinta,tunkan ta ƙarasa wurinta taga alamun ruwa ajikinta,yana ɗiɗɗigowa,fuskarta ɗauke da mamaki tace"Wanka da asuba"?shiru sehrish tayi batare da tace komai ba, Jahad ta kuma cewa"da ruwan sanyi kikayi wanka ne?naga jikinki yana ta kerma,"nan ma tayi shiru bata tanka mata ba,    A hasale tace"Sehrish magana fa,nake yi maki,"    Muryarta a kasalance tace"Jahad,Am not feeling well"tayi maganar tare da wucewa izuwa gaban wardrobe,   "Meya ke damunki ne"?jahad tayi tambayar tana binta da kallo,   Shiru tayi ba tare da ta bata amsar komai ba,gyaɗa kai jahad tayi kafin ta wuce cikin toilet,don ta lura kamar sehrish batason zancen,💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Bayan *Jahad* ta fito daga toilet, hijab ta ɗauko cikin wardrobe ta zura ajikinta,wurin gadonsu ta koma ta haye sama tare da kai hannu tana bubbuga hosana,    "Get up hosana,Time ɗin sallah yayi,"   hosana bata motsa ba,sae ma cigaba da jan minsharinta da tayi,   "Hosana ki tashi mana!ba zaki tashi ba wai,kullum sai kin bani wahala idan nazo tashin ki daga bacci"tayi maganar fuskarta a ɗaure,   Hosana kuwa,gyara kwanciyarta ta ƙara yi,har wani ƙara jan minsharin takeyi da ƙarfi don ma jahad tasan cewa tayi nisa a baccinta,alhalin tun a first call da tayi mata ta farka,     A ƙule jahad tace"kada Allah yasa ki tashi,kuma saina faɗa ma ya Omar cewa baki yin....."tunkan taƙarasa maganar,hosana ta diro daga saman gadon da gudun gaske ta nufi toilet ta buɗe ta shige ciki,dariya jahad tayi sosai kafin ta sauka daga saman gadon ta koma ta shimfiɗa carpet ta kabbara sallah, Sehrish kuwa tana a ƙudundune cikin bargo tayi lamo tana faman sauke ajiyar zuciya,kokwanton abunda ya faru tsakaninta da Sgr takeyi,ta kasa gasgata abunda ya faru last night,shin dagaske ne ko kuwa mafarki ne tayi,Don tasan cewa hakan zai yi wuya ya kasance gaskiya,Abun ya matukar ɗaure mata kai,ya caza mata brain ɗinta,tana cikin wannan zancen zucin bacci yayi awon gaba da ita, *Junaid Romeo* Bude ƙopar bedroom ɗinsa yayi tare da fitowa daga ciki,Still kayan baccin jiya ne ajikinshi,ya kara wayarshi a saman kunnanshi,hakan na nuni da cewar waya yake yi,Ashagwa6e yake magana yana faman tura baki,   "Abba pls come back Soon,nafiso na ganka a kusa dani,"ya ɗan yi maganar yana bubbuga ƙafarshi ƙasa,   On the other hand,Abbansu yace"ka ji tsoron Allah junaid!Nafa gano ka,So kake in dawo gida,saboda ayi maganar aurenka ko"?   Murmushi junaid ya saki yana ɗan sosa ƙeyarshi da ɗayan hannunshi"eh dan Allah Abba,nidai duk atakure nake,Allah jina nake kamar a prison,Ayi mun aure kawai in ana son zaman lafiya,"   Abba yace"idan ba'ayi maka auren ba fa"?    Ƙuƙuni ya shiga yi ƙasa ƙasa yana cewa"zan addabi kowa ne,in kuma kama ɗaki a hotel....." Bai ƙarasa maganar ba,Jin dariyar Abbansu ta cikin wayar,ashe duk yaji abunda yake cewa,     "Junaid wa kayi mawa?kasan cewa yayyenka gaba ɗaya soldiers ne,Wlh kayi kuskuren yin badai dai ba,kai kasan inda za'a kai ka,".    Jin wannan maganar ta Abba yasa shi ɗaure fuskarshi,   Yana tafiya yana waya,da alama part ɗin Sgr zai wuce,saboda can ya nufa,   Lokacin daya shiga falonsa,babu kowa,a saman sofa ya zauna,sai da ya kammala yin wayar da Abba,Su kayi sallama,Sannan ya miƙe tare da wuce wa bedroom ɗin Sgr,   Sallama yayi mashi,jin shiru yasa shi shiga cikin ɗakin kaitsaye,a kwance ya same shi saman katafaren gadon nashi,ya lullu6e jikinshi har zuwa chest ɗinshi,jallabiya ce sanye ajikinshi,tun daga kan yadda yake yin baccin nashi zai tabbatar maka da cewa,yana cikin kwanciyar hankali da natsuwa,   Lalla6awa Junaid yayi ya ƙarasa kusa da gadon,yana ƙoƙarin hawa idanuwanshi suka sauka asaman bargon Sgr,turus yayi ya tsaya yana kallon ikon Allah,Ya jima yana tunanin kome ya jawo hakan,abu dai gashi nan kana ganinshi ta cikin bargon,hawa sama yayi har zuwa saitin fuskarshi sannan ya tsaya tare da furta sunanshi a hankali"Babban yayanmu,"shiru bai amsa mashi ba,ƙara ɗaga murya yayi'babban yaya,"   Hannu ya kai tare da shafa gefen fuskarshi ya sake cewa"Babban yaya..,"   Har cikin dodon ears ɗinsa yaji kiran nashi,daƙyar ya iya ware blue eyes ɗinshi,biji biji ya fara gani kafin idanuwan suka ɗan washe,da wata irin kasalalliyar murya ya ambaci sunan shi"Junaid,"   Murmushi junaid yayi tare da cewa"nazo ne don na takura maka,Jiya na jira naga dawowarka,amma baka dawo gida ba,har bacci ya ɗauke ni,'_   Zuba mashi ido Sgr yayi yana kallonshi,    Hakan yasa junaid ya ɗan tsuke fuskarshi yace"haba yaya rafayet,in zauna in tayi maka zuba kamar parrot maimakon ka mayar mun da martani saika zuba min ido kana kallona,"    a hankali ya lumshe idanuwanshi kafin ya sake ɗan waresu akan Fuskar junaid ɗin,   "Me kake so ne"? Muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"Yanzu babban yaya sai inason wani abu zanzo wurinka?jiya fa na dawo daga tafiya,ko farin cikin ganina ma baka yi ba,"   Ruƙo hannunshi Sgr yayi tare da janyoshi ya kwantar da kanshi saman ƙirjinshi,yana ɗan shafa bayanshi yace"Am glad to see you,Ya gajiyan tafiya,?kayi mun tsaraba"?   Ashagwa6e junaid yace"Eh mana,munyi tsarabar fura,da zuma,da sauransu dai,idan kanaso zan yi ma rishi magana ta dama maka fura kasha,Wlh akwai daɗi sosai,nima in nasha kunne na har rawa yake yi,'    Ya ƙarasa maganar tare da ɗagowa daga jikinshi,da buɗar bakin Sgr sai cewa yayi"you mean tafi abun da nasha last night daɗi"? A ruɗe junaid yace"babban yaya,me kasha jiyan?Ae ni bansan shi ba balle in san cewa ko yafi furar daɗi,   Shi kanshi baisan ya furta hakan ba,it was just slip of the tongue,saboda ya kwana da abun aranshi,kuma yanzu haka ma shi yake tariyowa acikin brain ɗinsa,abun ya tsaya mashi arai,yadda har surar jikinta taja ra'ayinshi har ya fita hayyacinshi ya fara romancing ɗinta,ƙiris ya rage jiya ayi abun kunya, (Allah yaso bai ƙarasa headquater ɗin ba,da shikenan an buge boss,(in jini ba,don na lura wasu in ina kara wannan bayanin suna tsammanin cewa Sune sukeyin zancen zucin,sometimes ina ƙarawa da nawa bayanin) "Yaya rafayet,"junaid ne ya ambaci sunanshi,ganin ya shiga zurfin tunani, hankalinshi yayi wani wurin,mayar da idanuwanshi yayi kan junaid tare da cewa"don't disturb me pls,Inaso na ɗan huta junaid,"   Ranshi ya ɗan sosu,jiki asanyaye ya juya zai sauko daga saman gadon,Sgr ya dakatar dashi"Wait,'ɗan tsayawa yayi tare da juyawa yana kallonshi,   "Tell me what do u want from me"? Shiru junaid yayi yana lissafin adadin kuɗin da zai kar6a a wurinshi,Don sunyi da jahad zasu fita yawo,gashi ƴan kuɗaɗen acct ɗinsa duk sun ƙare,Yayi broke,'   ɗaga yatsun hannunshi yayi yana yin lissafin,hakan ba ƙaramin dariya yaso yaba Sgr ba,dama sai da ranshi ya bashi cewar wani abu ne ya kawo shi bedroom ɗinshi,tunda sassafe ko wanka bai yi ba,balle aje ga maganar breakfast,A tsiyacen shi yazo,   "Zan koma bacci,tunda naga lissafin na ka bamai ƙarewa bane,"   Da sauri yace"pls babban yaya kada ka koma bacci,yanzu ma daƙyar na tashe ka,".   ta6e lips ɗinshi yayi tare da nuna wurin dressing mirror ɗinshi da hannunshi,Yace"idan kuɗine kake buƙata a wurina gasu can ka ɗauki iya yadda kakeso,idan ma na cikin nan isn't enough for u,Zan ƙara maka ta acct,hope hakan yayi maka"?yayi tambayar yana kallonshi,.    Washe baki junaid ya shiga yi yana cewa"Babban yaya nagode sosai,wlh duk gidan nan kafi kowa sona,har Daddy ma kafi shi sona,"   Harara Sgr ya ɗan jefa mashi kafin yace"Saboda ina baka kuɗi ko"?_   fashewa junaid yayi da dariya,tare da saukowa daga saman gadon ya nufi wurin dressing mirror, Mayar da idanuwanshi yayi ya lumshe su,shikaɗai yasan irin feelings ɗin da yake ji,kamar yayi hauka,Kuma shi irin mutanan nan ne,waɗanda basa wasa da lafiyar jikinsu,Komai yaji jikinshi na bukata yinshi yake yi don ya samu cikakkiyar lafiya,shiyasa gashi nan ta ko'ina masha Allah,tun daga kan skin ɗinshi zakasan cewa ba ƙaramin gyara take sha ba,haka sumar kanshi,da sauran parts na jikinshi,yanzu kuma ga wani new abu da yake bukata Urgently, Zuƙunnawa junaid yayi agaban drawer ɗin,ya buɗe middle ɗinta,Dollars ne ya gani a jere,cike fam da ita,har wani ƙyalli kuɗin sukeyi acikin idanunshi,murza hannunshi ya shiga yi,har wani ƙaiƙayi suke yi mashi,Bandir ukku ya ɗauko ya tura su daƙyar cikin aljihun wandonshi,duk da haka basu isheshi ba,sae daya ƙara da naira,A gida na ƙarshe daya buɗe ajikin drawer chest din,kuɗin nigeria ne,Suma ya ɗauki Bandir uku na dubu dubu kusan dubu ɗari uku kenan,Ya turasu cikin ɗayan aljihun daƙyar suka shiga,Bayan ya kammala ya rufe mashi ita,yana ƙoƙarin miƙewa,idonshi ya sauka akan hoton daya faɗo ƙasan tiles,baisan daga ina hoton yake ba,duk a tunanin shi hoton Babban yayansu ne,   Zukunnawa yayi tare da kai hannu ya ɗauki hoton da ya kife,ya juyo dashi yadda zai ganshi da kyau,   Da karfi ya furta"Sehrish!"miƙewa yayi tare da tunkarar wurin gadon hannunshi ruƙe da hoton yaci gaba da cewa"wlh itace," jin sambatun da junaid keyi ne yasa Sgr ya ɗan buɗe idanuwanshi tare da wurga eye balls ɗinsa wurin junaid dake tunkaroshi    Zama yayi daga gefen gadon fuskar nan tashi awashe cike fal da farin ciki,ya kuma yace"Wlh itace,Yaya rafayet ina ka samu hoton rishi tana ƴar ƙarama,"   "Junaid what are u talking about"?yayi tambayar a yayin da yake ɗan miƙewa zaune,tare da jingina bayanshi akan gadon,    "Sehrish mana!wadda take yi maka aiki,"   Cike da mamaki Sgr yace"Kana nufin itace a pic ɗin"?   Jinjina kai junaid yayi"ƙwarai kuwa itace,"   Cike da mamaki Sgr ya kuma tambayarshi "taya akai ka gane cewa itace?cos i even asked her last time,amma ta sanar dani cewa ba ita bace'   Junaid yace"ae duk cikinsu,babu mai ɗigon tawada asaman wuyanshi sai ita,duk sauran basu dashi asaman neck ɗinsu,Idan ka kalli hoton nan dakyau,zaka ga ɗigon baki asaman wuyanta,'.   "Lemme see"ya buƙaci ganin hoton,da sauri junaid ya mika mashi,hannu yasa ya kar6a,sannan ya ƙura ma hoton ido yana kallonshi,ɗigon tawadar ya gani asaman wuyanta,closing eyes dinsa ya ɗanyi,yana tariyo kallon da yayi ma ƙirjinta adaren jiya,har izuwa saman wuyanta,tabbas yaga black point ɗin nan,amma abun ya daure mashi kai,ta yadda har ita kanta,bata gane cewa ita bace a hoton, Buɗe idanuwan nashi yayi akan fuskar junaid sannan atsanake yace"Junaid,dama kallonta kakeyi?" cike da tuhuma yayi mashi tambayar,   Sunnar da kai junaid ya ɗan yi yana sosa ƙeyarshi yace"Nifa ba kallonta nake yi ba,tun lokacin baya ne,kafin ta bayyana amatsayin mace,muna da kusanci sosai da ita,shiyasa ma har nayi mata wannan kyakkyawan sanin,"    "Its okey" ya furta hakan,tare da mayar da idanuwanshi kan hoton,Abun ya daure mashi kai,sai lokacin ya shiga tunanin ko meyasa Uncle Abusufyan ya basu hotonsu shi da Omar?   Muryar junaid ce ta katse shi da cewa"Ka taso muje dining muci abinci pls,nasan kana jin yunwa,'   Runƙo hannun Sgr yayi,har sai da ya samu ya sauko daga saman gadon,Sannan suka fito atare,har lokacin hoton na hannunshi,daga bayane ya zura shi cikin aljihun jallabiyarshi Saukowa downstairs suka yi,tunkafin su ƙarasa dining ɗin,suka hango Uncle Abusufyan tare da Marshal Omar,ga Jahad da Hosana ma,duk suna azaune suna cin breakfast ɗinsu,Azmee ce atsaye take yin serving ɗinsu,   koda suka ƙarasa,da sauri su jahad suka gaisar dashi"babban yaya ina kwana,an tashi lafiya,"? "Lafiya,sannunku"ya ambaci hakan kafin ya samu wuri ya zauna,junaid ma ya zauna a kusa dashi,    "Big bro,jiya na jira dawowarka gida baka dawo ba,ina fata kana cikin ƙoshin lafiya,"acewar Marshal Omar,   "Am ok,"ya bashi amsa atakaice,dama fushi yake yi dashi saboda yaso su dawo gida atare,Amma Omar yace sai ya ɗan ƙara kwanaki,   Juyawa ya ɗanyi tare da kallon Abusufyan,wanda shima kallon nashi yake yi,jira yake yaga iya gudun ruwan nashi,zai gaisar dashi ne?ko kuwa jira yake yi shi ya gaishe da shi Ne?    a hankali ya furta"Uncle,ya gajiyar tafiya,jiya kun dawo time ɗin bana nan"   Murmushi Abusufyan ya ɗan saki tare da cewa"lafiyalou Alhamdulillah,gajiya tabi jiki,'   Matsawa azmee tayi ta ɗauki plate ta shiga zuba masu abincin da zasu ci,   Hosana tace"Daddy,rishi fa?kada acinye ita bata ci komai ba,"   Jahad tace"bacci takeyi tun ɗazu,kuma har tashinta nayi tazo muci abinci,amma tace mun in ƙyaleta,bata jin daɗin jikinta,'   "Me ya ke damunta ne"?Omar yayi tambayar,   "Nima bansani ba,tunda asuba dai kamar bata da lafiya,duk ta canza mun,har tambayarta nayi meke damunta amma bata sanar dani ba,"   Abusufyan yace"bai kamata a ƙyaleta ba,yakamata ku kirata tazo muji menene matsalarta,"   Jiki na rawa junaid ya miƙe zaije kiranta,karaf idanuwanshi suka sauka kan fuskar Sgr,wani irin kallo ya wurga mashi mai kama da harara,batare da kowa ya lura ba,komawa junaid yayi ya zauna,tare da cewa"Jahad kije ki kirata mana,"_   "Amsa mashi tayi da toh,kafin ta mike cikin sauri ta wuce bedroom ɗinsu,   Cike da zolaya Marshal yace"Wato har ka fara bata Command ko"?_   Kunyace ta rufe junaid,har ya kasa shan Tea ɗin da ya ke sha cikin cup,Satar kallon Abusufyan yayi,Suna haɗa ido nan fa ya ƙara kame kanshi, Hakan ba ƙaramin dariya ya basu ba,Hosana tace"Ya Omar,wai yaushe ne abun nan?kace idan kuka dawo za'ayi magana nifa na kagara wlh,"   Gabanshi ne ya fadi rass,Hankali aɗan tashe ya ɗago ya kalleta,ko ajikinta sae ma tura pancake takeyi acikin bakinta,wata irin kunyace ta rufe shi,.    Shi kanshi Abusufyan,kunyarce ta rufeshi,sai faman jujjuya fork yake acikin plate,ya kasa cin Abincin,   Sgr kuwa har ɗagowa yayi ya kalli Hosana da tayi maganar,   Ƙiris ya rage azmee ta fashe da dariya,jurewa kawai takeyi,   Junaid ne yayi ƙokarin dakatar da ita ta hanyar yi mata raɗa acikin kunnanta,   "Hosana waike baki da burki ne?meyasa zakiyi mashi haka,Duk kinsa sunji kunya,daga shi har Daddy ɗin naku,bai kamata kice haka ba,"_   Turo baki ta ɗan yi tare da cewa"zunubi na aikata ne?kawai kawai saboda nace....."bata ƙarasa maganar ba,sakamakon kallon da taga Omar yayi mata,nan take ta shiga taitayinta, After some minutes,Jahad ta shigo Dining area ɗin,tunkan ta karaso Junaid yace"ina rishi ɗin take ne"ganin ta dawo ita kaɗai batare da Sehrish ba,   "Tana aciki,yanzu zata fito,"ta karasa maganar tare da samun wuri ta zauna, A hankali ta zuro da kafarta,har yanzu jallabiyar ce ajikinta,ta laga gyale akanta,ƙafarta kuma na sanye da flat shoes,jikinta sae kerma yake yi,saboda zazza6in daya rufar mata,amma bata so kowa ya gane halin da take ciki,hakan yasa tun kafin ta ƙaraso wurinsu,ta daidaita natsuwarta sosai,sannan ta shigo dining area ɗin,takun takalminta ne ya janyo hankalinsu,duk suka juyo suna kallonta,gabanta ne ya faɗi Rasss ganin Sgr zaune,aikuwa a ruɗe ta juya zata koma ciki,.    Abusufyan ya dakatar da ita,ta hanyar ambaton sunanta"Sehrish,"tsayawa tayi cak,batare da ta ƙara ɗaga ƙafarta ba,wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,kafin a hankali ta juyo ta ci gaba da tafiya,hankalinta duk yabi ya tashi kamar taga wani mugun abu,    Wurin Abbansu ta tsaya,tare da gaisar dashi,"daddy ina kwana,".   Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"lafiyalou Daughter,meyasa baki fito ba tun ɗazu,"?    "Bana jin daɗin jikina ne,Amma naji sauƙi yanzu"    "Alhamdulillah,samu wuri ki zauna,"cike da kulawa yayi maganar,   Gabanta sai faɗuwa yakeyi,ta rasa ta ina zata zauna,inda bazata fuskance shi ba,balle har su haɗa ido,   Ganin taƙi samun wuri ta zauna sai ƴan dube dube takeyi,Hakan yasa Omar nuna mata gefenshi yace"Zo ki zauna,"hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,saboda yana a left hand ne kuma suna fuskantar su Sgr dake ta dama,kuma kujerar da zata zauna,ita ke fuskantarshi,jiki a mace ta ƙarasa gefen Marshal ta zauna,muryarta na kerma ta gaisar da Marshal"ina kwana yaya Omar,"   Da fara'a a fuskarshi ya amsa mata,"lafiyalou sister,ya jikin naki,"   "Da sauƙi,"ta bashi amsa, "Allah ya ƙara sauki,"   "Ameen" "Yaya rafayet,ina kwana,"daƙyar ta iya gaishe shi,sai dai ko kallo bata ishe shi ba,balle har tayi tsammanin zai amsa mata gaisuwarta,lokaci guda ta gane dalilin dayasa yaƙi amsa mata gaisuwar saboda bashi ta fara gaisarwa ba,a matsayinshi na boss ɗinta,wanda ke asama da mahaifinta,   "Bro baka ji ana gaishe dakai bane"?acewar Omar    Batare daya ɗago ya kalleshi ba yace"Naji,"yayi maganar tare da ɗaukar cup na coffee yana sha,   Murmushi marshal yayi,saboda ya gane reason ɗin dayasa yaƙi amsa gaisuwarta,    Zagayowa azmee tayi kusa da ita,ta ɗan duƙa saitin kunnan sehrish tace"Amaryarmu,me kikeso a zuba maki ne?farfesun nama ko Snacks,"?     Murmushi sehrish tayi har dimple ɗinta ya lotsa,sannan tace"Aunty azmee pls kidaina zolayata,yanzu idan yaji fa?ni zaki jamawa,"cikin raɗa tayi maganar don kada suji mai take cewa,   Azmee tace"Shikenan Mrs rafayet,na daina,yanzu dai me kikeso"?   Sehrish tace"farfesun zaki samun,saboda bakina babu daɗi,"   Su6ul da baka azmee tayi wurin cewa"kice mun kusa samun ƙaruwar baby kenan,"karaf maganarta ta sauka akan kunnan Sgr,kuma cikin whispering tayi maganar,amma wani iko na Allah yaji abunda tace,ko kuwa yayi amfani da motsin la66anta ne Oho,   Kamar daga sama taji yace"Keee!"a ɗan firgice azmee ta ɗago,ba ita kaɗai ba hatta su Uncle sai da suka ɗago suna kallonshi,ya haɗe fuskar nan babu annuri acikinta,.     Da cokalin hannunshi yayi mata nuni da tabar wurin,Jiki asanyaye azmee ta juya da sauri tabar wurin,   Sam sehrish bata ji daɗin hakan ba,duk sai taji babu daɗi,bata so Sgr ya kori Azmee ba,agaban kowa da kowa wannan kamar Cin fuska ne,Su kansu sauran dake zaune a dining ɗin basu ji daɗin hakan ba,shiru kawai su kayi,tunda basu da yadda zasuyi dashi,    Ganin ya sallami Azmee yasa ta shiga ƙoƙarin yin serving ɗin kanta,plate ta ɗauko acikin jerin plates ɗin dake ajiye saman table din,Warmers din tashiga bubbuɗewa harta buɗo wadda ke ɗauke da farfesun naman kaza,serving spoon ta sanya,ta shiga ɗibarta tana zubawa acikin plate din,sai da tacika shi,sannan ta rufe warmer ɗin, Sosai ta shiga shan farfesun,har wani lasar baki takeyi saboda daɗinshi da takeji,cinyar kaza ta ɗauko tana ƙoƙarin kaiwa bakinta,Sgr ya ɗago da idanuwanshi,karaf suka shiga cikin nata,nan take tasha jinin jikinta,kasa ƙarasa kazar tayi cikin bakinta,cak ta tsaya,tana kallonshi,   Wannan karon kallon da yake yi mata yasha bambam da irin kallon daya saba yi mata a baya,gaba ɗaya sun shagala da kallon junansu,babu wanda ya lura a wurin,tunani tashiga yi komai yasa yake kallonta har haka batare da ya janye idanuwanshi ba?   Shikuwa gogan jira yake ta kawar da idonta daga kallon da takeyi mashi,kada raini ya fara shiga tsakaninsu,saboda abunda ya faru jiya,musamman da ta ganshi tsurararshi babu kaya a jikinshi,    ƴar harara ya watsa mata,tare da janye idanuwanshi daga kanta,kawar da nata idon tayi,mayar da cinyar kazar tayi cikin plate,gaba ɗaya taji komai ya fita ranta,ba don ta ƙoshi ba,ta miƙe zata bar dining ɗin,   "Whe're u going"muryarshi ce ta dakatar da ita,    daƙyar ta iya buɗe baki tace"Na koshi,"   Zuba masu ido Abusufyan yayi yana kallonsu,     "Koma ki zauna,"Yayi maganar yana nuna mata seat ɗinta,Tamkar ta fashe da kuka haka taji,juyawa ta dan yi suka haɗa ido da daddynsu,kafin ta zauna,taci gaba da shan farfesun da ta rage,   Hannu yasa ya yago tissue,yana goge mouth ɗinsa,kafin daga bisani ya miƙe ya wuce part ɗinsa,    Sai da ya bar wurin sannan,ta samu natsuwa,   "Daddy,ya maganar zuwa kano?sehrish ta faɗamun cewa,da zarar kadawo daga damaturu zaku wuce kano,Wurin neman Oumman mu,"jahad ce tayi maganar,   "In sha Allah gobe nake son tafiya,tunda Asuba before ku tashi daga bacci ma"   Yana kai ƙarshen maganarshi,Hosana tayi saurin cewa"daddy,pls dani za'a tafi,wlh inason zuwa kano,"   Harara marshal ya ɗan wurga mata kafin yace"a haka za'a tafi dake?me kika sani?Faɗamun a wata unguwa kuka zauna a kano"    Wurga ido sama tayi tana ƙoƙarin tunano anguwar da suka zauna a kano   Yatsina fuska tayi tare da cewa"Dawanau ko"? me zasuyi in ba dariya ba,gaba ɗayansu suka fashe da dariya,ɗaure fuskarta tayi,don ita ba ta faɗi don ayi mata dariya ba,bilhaƙƙi da gaske take ita,   Jahad tace"kai hosana dawanau fa kika ce?Anan ne muka zauna?,' murguɗa mata baki tayi batare da ta ƙara cewa komai ba,    "Daddy dan Allah ka tafi dani,nafi kowa son naje,"acewar sehrish,   Mayar da idanuwanshi yayi kanta tare da cewa"Kin tambayeshi ne?ko kin manta yadda muka yi dake,"_   Jin haka yasa ta ɗan ɗaure fuskarta don tasan cewa,daƙyar ne Sgr yabarta ta tafi kano,   "Ki je ki tambayeshi,idan ya barki tun yau ki fara shiri don da asuba zamu tafi,idan kuma ya hana to zan tafi da jahad ne"    Tuni idanuwanta suka ciko tab da kwalla saboda tasa ran zuwa kano,   Mikewa tayi daga saman kujerar tace"shikenan daddy,zan tambayeshi,Allah yasa yabarni,"ta ƙarasa maganar tare da barin wurin da sauri ta wuce ciki, Bayan sun kammala yin breakfast ɗin,kowa ya kama gabansa, A 6angarensu Aunty babba,tafiya ta kankama,Domin kuwa tun yau sun kammala shirinsu na tafiya Enugu,sun kimtsa kayansu da zasu tafi dasu,da asussuba zasu bar Abuja,da farko zasu fara sauka a hotel ne,a washe garin ranar zasu wuce,Cikin dajin da Bokan yake,taci alwashin cewa Sai taga bayan Hosana,saboda itace silar tonuwar asirinta,kuma A sanadinta ne tarasa igiyar auranta ɗaya,Bayan haka kuma taci alwashin saita Sanya soyayyar Abra acikin zuciyar Sgr,fiye da yadda ya Ke son iyayenshi,   Tashin hankali!Rayuwar hosana na cikin haɗari, Shin ina hayaam dake a kwance gadon asibiti cikin mawuyacin hali,har yau ba ta dawo cikin hayyacinta ba,Gashi likitocin sun nemi wani makusancinta sun rasa,babu wani atare da ita,baiwar Allah,bamu son ya zata ƙare ba, Gab da sallar magrib,Wayarta dake ajiye saman gadonsu ta shiga ringing,a lokacin tana acikin toilet,Jahad ce kawai acikin bedroom ɗin nasu,tayi zaman cin tuwo saman gadon,ta ƙura ido tana kallon k-drama acikin system dinsu,Hannu tasa tare da daukar wayar Sehrish,ta duba mai kiran nata,Sunan Aunty azeema ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,picking tayi tare da manna wayar a kunnanta,   "Assalamu alaikum,mommy azeema" On the other hand azeema tace"Daughter,kin ga saƙo na"?_ Murmushi jahad tayi kafin tace"Aunty azeema yanzu baki gane muryoyin mu?Jahad fa ce ba rishi ba,"   Hajiya azeema tace"wlh naso in ɗauki muryarki,Ashe second daughter ce,To ya kike"?   "Lafiya lou Alhamdulillah ina lafiya,"   "Madallah,Amaryar junaid," Cike da jin kunya jahad tace"Aunty azeema waya faɗi zancen nan,"    Dariya hajiya azeema tayi kafin tace"oh kin manta matsayina a wurin daddynku ne?Ae shi da kanshi ya sanar dani,kuma naji daɗi wlh,Junaid zai samu kamilar mace wadda zata kula da rayuwarshi,"_ kayataccen murmushi jahad ta saki,ba ƙaramin daɗin maganar taji ba,    "Ina fata zaki kula mana da bugun zuciyar mu?   Dariya jahad tayi tana faɗin"in sha Allah,zan kula maku dashi,"   Hajiya azeema tace"Yawwa My daughter,but akwai abunda nakeso na tattauna tare dake game da junaid!amma ki bari zan kira wayarki,ko zuwa anjima ne,"   "To Aunty Allah yakaimu anjiman lafiya,"   "Ameen daughter,ina sehrish ɗin take ne?inaso nayi magana da ita ne,"   Jahad na ƙoƙarin bude baki tayi magana,sai ga sehrish ta fito daga toilet din,jikinta sanye da bathrobe,wankan marece tayi,dama duk in tana period,kusan sau uku take yin wanka,'    Ganin wayarta a hannun jahad yasa ta tunkarota tana tambayarta wanene ya kirata,   Mika mata wayar jahad tayi"kar6i nan,Mommy azeema ce keson magana dake"   Jiki na rawa ta kar6i wayar,da sauri ta koma gaban mirror,ta zauna saman kujerar,sannan tayi mata sallama,   "Daughter,ya ake ciki ne?ina fata kinga saƙona ko"? ..Sehrish tace"nagani,junaid ya kawomin su,nagode sosai,"   "Yawwa,Zaki ga turarurruka aciki,Tun yanzu zaki fara amfani dasu,akwai wasu sirrika atattare dasu,sannan akwai mayuka na gyaran fata,dana gyaran gashi,Original ne,Cikin one week,kina fara amfani dasu zaki ga sauyi a jikinki,Sannan akwai sauran kayan da ba yanzu zakiyi amfani dasu ba,suna da haɗarin gaske,su kansu turarurrukan nan,Shu'umaine na gaske,Fisgar mutun sukeyi kamar magnet,ƙarfi ne dasu,duk in zaki shafasu ki bari sai in zaki part ɗinsa,idan ba haka ba gaskiya za'a iya samun matsala,"   Natsuwa sehrish tayi tana sauraronta,sun jima suna waya kafin daga bisani su kayi sallama,    Kasa yin amfani da turaren tayi,tsoranshi ma take ji,tunda taji ance fisgar mutun yake yi,kada ta jama kanta bala'e tana zaman zamanta lafiya,    bata shafa turaren ba,Amma ta fara amfani da mayukan gyaran jikin,   Shaf shaf ta shirya cikin Doguwar riga ta material black colour,mai zanen manyan flowers a jikinshi launin ash,rigar tabi shape ɗin jikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba gaban mirror ta koma ta zauna,powder ta murza a fuskarta,Sannan ta shafa man baki,la66anta sae salƙi sukeyi,    Bata yafa komai akanta ba,Iya sumar kanta ce data sauko har gadon bayanta,high hills ta zura a ƙafarta, Kama hanyar fita daga ɗakin tayi da sauri jahad tace"Ina zuwa? "Zanje part ɗin babban yaya ne,Inaso na gyara mashi ne," Murmushi jahad ta saki tare da mayar da idonta kan system ɗin gabanta, "Kinyi kyau sosai,kada fa ki zautar mana da babban yayanmu a rasa gane kanshi," dariya sehrish tayi batare da tace komai ba,ta fuce daga dakin, Babu kowa a falon,da alama duk sun tafi yin sallar magriba ne,tana cikin tafiya,kwatsam taji an ruƙo sumar kanta ta baya,a firgice ta juya don taga wanene,Gabanta ne ya faɗi rass!ganin Haroon kamar wani maye haka ya kama dogon gashin kanta,yakai shi izuwa saitin hancinsa yana shinshinar ƙamshinshi, A wani irin tsorace sehrish ta buge hannunshi,sam batasan cewa zata hadu dashi ba,da batayi kuskuren fitowa daga dakinsu ba,batare da ta sanya mayafi ba, Fuskarta a daure tace"Dan Allah menene haka"? Shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da cewa"Shauƙi," Harara ta watsa mashi,aranta tace"Mai hali bai ta6a canzawa dama saida raina ya bani cewa karyane tuban da yace mun yayi," Guntun tsoki taja,da hanzari ta juya zata wuce saman stairs din,aikuwa da sauri ya sha gabanta ƙiris ya rage ƙirjinta ya daki nashi,hakan ba ƙaramin daga mata hankali yayi ba, "Ka bani wuri na wuce,banason wannan rashin wayon naka,Bakasan cewa ni matar aure bace," Ta6e bakinshi yayi tare da cewa"And then so what idan ke matar aure ce?Nafa son komai,auren yarjejeniya ne,mutumin nan fa da kika kwallafa rai akanshi ba sonki yake yi ba,Ni ne mosayinki,inason ki sosai,kuma ashirye nake dana aureki da zarar ya sake ki...." Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshinta,tuni idanuwanta suka cicciko da kwalla,ta tsani taji ance mata haka, Ranta a matuƙar 6ace tace"Wlh koda ace mazan duniya sun ƙare duka kaf babu su,kai kaɗae ne ka rage sai dabbobi a cikinta,to na ƙwammace in auri Biri da in aure ka," Waro ido waje yayi yana kallonta a hasale yace"Ke!ni kike gayawa wannan maganar?baki da hankali ne?ki rasa dawa zaki haɗani sai biri,kina nufin cewa biri yafi ni mahimmanci a wurinki"? "Ƙwara shi dabbane,kaifa mutunne mai hali irin na dabbo...."_ Bata ƙarasa maganar ba,a fusace haroon ya sanya tafin hannunshi ya ɗauke ta da mari,Sae dai kafin ya janye hannunshi daga saman kuncin ta,yaji shima an dauke shi da wani irin zazzaffan mari,Kuma kafin yayi wani yunƙuri yaji tafukan hannaye again har biyu asaman fuskarshi,Tashin hankalin Wasu irin baƙaƙen taurari ya gani acikin idanuwanshi,tsabar raɗaɗin da ya ji ne yasa shi sakin ihu,yana tangal tangal zai fadi,gaba daya duk yabi ya susuce,har fitsari sae da ya saki a wondonshi,saboda tsabar raɗaɗin daya ji, A galabaice yace"Na shiga uku!Meke faruwa dani ne!dan Allah ataimakamin duhu cikin idanuwana," Shessheƙar kuka kawai sehrish keyi hannunta dafe da kuncinta,mutum biyu ne suka mari haroon,shigowarsu kenan Suka ganshi ya sharara mata mari,aikuwa da gudu Abusufyan ya ƙaraso ya kwashe shi da mari,Marshal Omar kuwa,Hannu biyu yasa ya ɗauke shi da Mari ta baya,hakan yasa yaji duuuuum acikin kunnanshi,babu wani sauti kwata kwata,kamar ya kurmance, Ruko hannunta Marshal yayi"kiyi haƙuri kinji,dan Allah ki daina kuka," side hug yayi mata yana dan bubbuga bayanta,Abusufyan kuwa sam ya kasa magana sai faman huci yakeyi,ranshi yayi mugun 6aci, "Banaso Sgr ya shigo yaji wannan aika aikar da haroon yayi,don wlh sai ya ɗanɗana kuɗarshi,Sehrish ki wuce bedroom ɗinku,ki barni dashi,zaici ubanshi ne," .. Cikin shessheƙar kuka tace"Part din babban yaya zanje in gyara mashi" Tayi maganar tare da wuce wa upstairs da sauri tana ci gaba da yin kukan, "Uncle,dan Allah ka shiga daga ciki,Ni zanji dashi," Jinjina kai kawai Abusufyan yayi tare da juyawa yabar falon, Kwakkwaran damƙa Marshal yayi ma wuyan rigar haroon dake a zube ƙasa yana birgima,ɗaɗɗago dashi yayi ya jashi,har izuwa ɗakin da suke hukunta mai laifi,lallai haroon ya ta6o ma kanshi, Lokacin da sehrish ta faɗa cikin palourn shi,Saman sofa ta zauna tana cigaba da yin kukan,taji zafin marin da haroon yayi mata sosai,abun ya tsaya mata aranta,tsanarshi ta ƙara ninkuwa acikin zuciyarta,ta jima a zaune batare da ta motsa ba,har aka kira sallar isha'e,sae bayan da aka kammala sallar sannan ta miƙe ta wuce cikin bedroom ɗinshi,toilet ta fara shiga ta gyara mashi,kafin ta dawo bedroom ɗin nashi tana gyarawa,har lokacin bata daina yin shessheƙar kukan ba, Bayan ta kammala gyara mashi part ɗin nasa,kasa tafiya tayi saboda a ƙagare take daya dawo,saboda tayi mashi maganar zuwansu kano,Addu'arta Allah yasa yabarta taje,   Safa da marwa ta shiga yi acikin bedroom ɗin nashi,gajiya tafara yi da yin yawon,wuri ta samu daga gefen gadon ta zauna,gyangyaɗi ta fara yi a ƙarshe bacci ya kwasheta,bata ƙara sanin meke wakana ba, *SGR* Around 12 ya dawo cikin gidan,Army trouser ne ajikinshi,sae farar shirt mai dogon hannu,Lokacin daya shiga bedroom ɗinshi bai ankara da ita ba,rage kayan jikinshi yayi kafin ya shiga toilet,bayan ya kammala yin wankan,Ya fito sanye da bathrobe ajikinshi,gaban mirror ya tsaya sai da ya kammala shafe jikinshi da tsadaddun mayukan jikinshi,ya gyara sumar kanshi sosai,kafin ya koma wurin closet ɗinshi,after some minutes ya dawo cikin ɗakin jikinshi sanye da Sleeping dress Red colour,yayi wani fresh dashi,tunanin kiranta yayi a wayarshi don ta kawo mashi dinner ɗinshi before ya kwanta,Yana ƙoƙarin juyawa don yaje ya ɗauki wayarshi daya ajiye saman drawer ɗinshi,wayar ta shiga ruri,da sauri ya ƙarasa tare da ɗaukar wayar,duba screen ɗin wayar yayi sunan*Uncle donald*ne ya bayyana, Picking call ɗin yayi a natse ya kara wayar a kunnanshi,Cikin harshen Spanish suka soma yin maganar,wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana cigaba yin wayar,fuskarshi asake da alama ba ƙaramin farin ciki yake da kiran ba,     Sun jima suna magana da uncle ɗin nashi,kafin sukayi sallama,mayar da wayar yayi saman side drawer ɗin ya ajiyeta,sauke ajiyar zuciya yayi tare da kwantar da bayanshi asaman laps ɗin sehrish batare da saninshi ba,lumshe idanuwanshi yayi a hankali ya ɗan waresu,ƙoƙarin juyawa yayi karaf eyes ɗinshi suka sauka akan hannunta,Har sai da gabanshi ya ɗan faɗi rass saboda baiyi tsammanin ganin  mutum a cikin bedroom ɗinshi ba,kuma farat ɗaya bai gane cewa ita bace,A sukwane ya miƙe zaune yana kallonta,cike da mamaki,Hankalinta kwance sae sharar baccinta takeyi,Abun ya ɗaure mashi kai har saman gadonshi,   Clapping hands ɗinshi yayi,A firgice sehrish ta farka,Sakamakon sautin da taji na tafin da sgr yayi mata,A Ruɗe ta miƙe daga zaune,sumar kanta duk ta yarfo ta saman fuskar ta rufe mata idanuwanta,hakan yasa bata iya tantance wanene ba,Amma ranta na bata cewar mamallakin ɗakinne ya dawo,Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,tsoro ya hana ta janye gashin kanta daya rufe fuskarta don taga wanene,   Shi kuwa boss man ɗin ya zuba ma sarautar Allah ido,ganin ta kaza yin motsi yasa shi yin magana    "Bacci asaman gadona"?wani irin wahallan yawu ta haɗiya,    Muryarta na kerma tace"Am Sorry yaya rafayet,wlh bansan bacci ya ɗauko ni ba,Asaman gadonka,Na tsaya ne saboda inason yin magana dakai,"    Matsawa yayi kusa da ita,ta maƙure ajikin head board ɗin gadon,    A hankali ya sanya hannu tare da ruƙo doguwar sumar kanta,Ya yarfar da ita gefe guda,ta sauka asaman kafaɗarta,runtse idanuwanta tayi da sauri saboda bazata iya jurar kallon cikin nashi idanuwan ba,Ƙwayar idonshi ba ƙaramin rikitar da ita takeyi ba,Hada ƙarin ƙwayar idon yasa take jin tsoranshi,      "Neman me kike yi mun"?yayi tambayar a yayin da yake saukar da idanuwanshi saman lips ɗinta,   "Dama,na tura maka saƙo ta whatsapp ɗinka,bansani ba ko ka gani,"tayi maganar tare da buɗe idanuwanta,suka sauka kan fuskarshi da sauri ta kawar dasu izuwa saman yatsun hannunta data aza asaman laps ɗinta,    "I saw it already,naji complain ɗinki,Bayan wannan tashinki da nake yi in midnight,baya takura maki"?    "A'a,Nima ina samu nayi sallah,"   Jinjina kanshi yayi tare da cewa"Okey,je ki kawomin dinner ɗina,'   Amsa mashi tayi da toh,kafin ta sauko daga saman gadon,tayi mamakin yadda yake yi mata magana cikin sanyin Murya babu wannan faɗan,tayi tunanin cewa,Zai ɗauke ta da mari ne,amma sai taga akasin hakan,   Har ta kusa fita daga bedroom ɗin nashi ta ɗan dakata da yin tafiyar,ta juya tare da kallonshi a lokacin harya kwanta,    "Yaya rafayet"ta ambaci sunanshi, Har cikin kunnanshi,tsayar da idanuwanshi yayi akanta,Yana jiran jin me zatace,      "dama gobe daddy zai tafi kano,kuma yana so ya tafi tare dani,"   Shiru ya ɗanyi na wani lokacin kafin yace"dole sai dake za'a je kano ɗin ne? ba wani wanda zai iya replacing ɗinki"? tunda taji haka,jikinta yayi sanyi,    Muryarta tamkar zata yi kuka tace"Akwai,"   Bai ƙara tanka mata ba,kama hanya tayi ta fuce,sai da ta sauko downstairs sannan ta fashe da wani sabon kukan,Ta kwalfa rai akan son zuwa Kano, *tawaga biyu zasu yi tafiya gobe in Allah yakai mu,Tawaga ta farko zasu tafi neman wani da suka rasa a rayuwarsu,Tawaga ta biyu kuma zasu tafi wurin boka neman sa'a,*😱😳   💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* *RISHRAF* A cikin kitchen ta ƙarasa shan kukan nata,ta matse ƴar kwallarta,kafin ta shirya mashi dinner ɗinshi,Asaman Tray tana kan hanyar komawa upstairs,Kwatsam Sai ga haroon ya faɗo cikin falon,ba daga waje ya shigo ba,Acikin gidan yake,amma batasan daga ina yake ba,har sai da gabanta ya faɗi lokacin da tayi arba dashi,yayi jaga-jaga dashi ya jigata sosai,daƙyar yake iya ɗaga ƙafarsa idanuwan nan sunyi jawur dasu tamkar garwashin wuta yadda kasan na Mujiya sun yi luhu luhu,Jini sai ɗiga yake yi daga hancinshi,   Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,musamman da ya ƙaraso wurinta,duk tabi tasha jinin jikinta,    Tsayawa yayi kusa da ita yana kallonta,nuna mata fuskarshi yayi da yatsan hannunshi yace"haka kike so ko"?    Sunnar da kai ƙasa tayi,jikinta yayi wani irin sanyi,    "Saboda kawai na mareki,Shine aka yanke mun wannan ɗanyen hukuncin,bansan meyasa kowa yake ƙi na ba,An tsane ne ba'a son rayuwata,yau idan na faɗi na mutu alhakina bazai ta6a barinku ba" yana magana yana share hawayen dake shararowa akan fuskarshi,Wani irin tausayinshi ne ya Kamata,   "Nasan nayi laifi,Amma sau ɗaya na mareki su kuma har sau uku suka mare ni,Bayan wannan Hada wani horon aka ƙaramin,just because of You!Kuma laifi kika yi mun,Kin haɗani da dabba dole raina ya 6aci,ni kaina bada son raina na mare ki ba,Kin ƙuleni ne," Tuni idanuwanta suka cicciko da kwalla,muryarta na kerma tace"Dan Allah kayi haƙuri ya haroon....".    Bata ƙarasa maganar ba ya katse ta"Haƙuri fa kika ce?hmmmmm,bansan shi ba,Wlh tunda har suka ta6a lafiyar jikina sae uban kowa ya ɗanɗani kuɗarshi acikin gidan nan!Irin ƙuncin da suka ƙumsa mun acikin zuciyata sai sun ga martanin da zan mayar masu,Sun ta6o ma kansu bala'e da masifa,Zaman lafiya ya ƙare acikin gidan nan!Zan kashe musu farin cikinsu na har abada,Zan ƙuntata rayuwarsu,Zanyi silar da zuciyar wasu zata buga,"   Gabanta ne ya faɗi rass,gaba ɗaya tabi ta razana da kalamansa,Cos in a serious matter yayi maganar,babu wasa a kalamansa,   Jan ƙafarshi yayi daƙyar yake ɗangyasawa,kama hanyar zuwa part ɗinsu yayi,     Har yayi nisa da tafiya ya ɗan dakata tare da juyowa ya kalleta,adai dai lokacin itama ta juyo tana kallonshi,    Nuna ta yayi da yatsanshi"ke kuma!ki kuka da kan ki"!   Yana ambaton hakan yasa kai da sauri yabar wurin,   Tashin hankali! Jikinta har kerma yake,tray ɗin hannunta da ta ruƙo kamar zai faɗi ƙasa,dakyar ta iya ɗaga ƙafarta,jiki amace kamar wadda aka zarewa laka, Lokacin da ta shiga bedroom ɗin nashi,Har ya fara yin bacci,ƙarasawa tayi ta ajiye mashi dinner ɗinsa asaman table,kasa tashin shi tayi daga baccin,sam babu natsuwa atattare da ita,Kalaman haroon sunyi matuƙar girgizata,har cikin ranta take jin fargaban abunda haroon zai shirya masu,Wannan lokaci ne mai haɗarin gaske a rayuwarsu,tayi zurfi acikin tunaninta,Shessheƙar kukan da take yi ne ƙasa ƙasa Sounds ɗin ke kai mashi cikin kunnanshi,a hankali ya ɗan buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci,direct suka sauka akanta,zuba mata ido yayi yana kallon ikon Allah,Hawaye wasu na bin wasu fuskarta ta jiƙe sharkaf,ta shiga wani irin yanayi na tsoran halin da zasu shiga, "Lafiya"?yayi maganar a yayin da yake ƙoƙarin miƙewa zaune,jin tayi shiru bata bashi amsa ba yasa shi kai hannu ya daki table ɗin gabanshi,A firgice ta dawo cikin hayyacinta zuba mashi ido tayi tana kallonshi,da sauri ta sanya tafin hannunta tare da wiping tears ɗinta,   "Hawayen menene asaman fuskarki"? da sauri tace"babu komai,"   "Saboda na hana ki zuwa Kano"? Girgiza mashi kai tayi alamar a''a,   "To na menene"? Shiru tayi saboda ba ta da amsar da zata bashi,taso ace zata iya sanar dashi game da kalaman Haroon Wata'ƙil suyi ƙoƙarin dakatar dashi,Amma ina bazata iya ba don bata san miye zai aikatan ba,jin tayi mashi shiru yasa shi miƙewa tsaye ya koma wurinta ya tsaya,Hannu biyu yasa ya tallabo fuskarta,    "Tell me whats wrong with u?who touch u"?    girgiza mashi kai ta ƙara yi"babu komai,Bana jin daɗin jikina ne,'     "ina ke maki ciwo"? Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,Ae yasan cewa tana period,tuna haka yasa tayi saurin cewa"Marata,ke yi mun ciwo,Amma da sauƙi,"    ta ƙarasa maganar tare da ɗagowa don ta saci kallonshi,idanuwanshi na akanta tamkar zasu lumshe saboda yanayin da yake jin kanshi a lokacin,      Zame hannuwanshi yayi daga kan fuskarta,ya mayar dasu saman waist ɗinta,gabanta ne ya faɗi rass,tunani ta shiga yi komai zai yi mata,ɗaukarta yayi cak tare da sauketa saman katafaren gadon nashi,hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba ga wani irin tsoro da taji,     Ja da baya yayi ya taka izuwa wurin switch ya kashe light ɗin ɗakin gaba ɗaya nan take furniture ɗin ɗakin suka Soma bada haskensu different colours,hatta gadonshi da ya kwantar da ita,tunawa tayi da lokacin da ta ta6a kashe light ɗin ɗakinsa,ranar tayi mamaki sosai abun ya ruɗar da ita kuma ya ƙayatar da ita,Yadda komai na kayan ɗakinshi ke ƙyalli suna bada haske launi launi daban daban da zarar an kashe hasken ɗakin,     daga inda take kwance take hangen fuskarshi ba ƙaramin kyau yayi mata ba,gaban dressing mirror ɗinshi ya tsaya,ya zura hannayensa acikin trouser pocket ɗinsa,ya jima tsaye a wurin,kafin ya dawo saman gadon daga gefe ya zauna,Da kanshi ya shiga yin serving abincin yana ci atsanake,   Lumshe ido Sehrish tayi,tunda take a arayuwarta bata ta6a jin bed mattress mai ɗan bala'en laushi da daɗin kwanciya ba irinta Sgr,irin gadon da mutum ko baya jin bacci ya haushi,nan take baccin zai zo mashi,   tun tana kallonshi biji biji har ya kammala cin dinner ɗin nashi ya miƙe ya wuce cikin toilet daga nan ta fara bacci sama sama,lokacin da taji motsi ta ƙara buɗe idanuwanta,samunshi tayi a tsaye saman Darduma yana yin nafilfilin daya saba,Abun ba ƙaramin tafiya yayi da ita ba,komai nashi burgeta yake yi ba kaɗan ba,a hankali bacci ya ɗauke ta,     tana cikin baccin nan,taji daddaɗan ƙamshin turaren nan nashi acikin hancinta,Slowly ta buɗe idanuwanta Unexpected eyeballs ɗinta suka sauka cikin ƙwayar idonshi a matuƙar tsorace ta buɗe baki zata yi ihu da sauri ya sanya tafin hannunshi ya rufe mata bakin,   Ta tsorata ne da ganin yadda blue eyes ɗin nashi ke shining kuma sunyi blue sosai,dama idan dare yayi kalarsu tana ɗan ƙara cizawa,     "It's me,"a hankali ya furta mata hakan,lokaci guda ta shiga sauke ajiyar zuciya,kallon junansu suka shiga yi,launukan hasken ɗakin dake ƙyalla fuskokinsu ba ƙaramin ƙayatar da abun yayi ba,   A hankali ya zame tafin hannunshi daga bakinta ya maye gurbinsu da tausasan la66ansa,sosai ya shiga kissing lower lip ɗinta,har izuwa upper,gaba ɗaya Sehrish ta soma fita hayyacinta ɗago da ita yayi tare da zagayawa da hannunshi ta baya ya zuge zip ɗin rigar jikinta ya soma shafa bayan romantically,kafin ya ƙarasa zame rigar zuwa saman stomach ɗinta,Lokaci guda yabi ya susuce saboda halittar ƙirjinta ba ƙaramin fisgarshi sukeyi ba,tayar mashi da sha'awarshi suke yi gaba ɗaya,duk da yana ƙoƙarin Controlling ɗin kanshi saboda period ɗin da takeyi,da sauri sauri numfashinsu ke fita,ga wani irin dumi da temperature ɗin jikinsu yayi,moving hands ɗinshi yayi izuwa saman mararta a hankali ya shiga shafa wurin,hakan ba ƙaramin gigitar da ita yayi ba,Lumshe idanuwanta tayi yayin da wasu siraran hawaye ke fitowa daga cikinsu,mayar da harshen shi yayi cikin bakinta,gaba ɗaya suka kacame ma juna,ita kanta batasan ta zura hannayenta cikin sumar kanshi ba,Duk ta hargitsar da ita,ta cukuikuye mashi ita,zame tongue ɗinshi yayi daga cikin mouth ɗinta,passionately ya shiga bata hot kisses asaman wuyanta,runtse idanuwanta tayi sosai kamar ta fasa ihu haka take ji,A wata irin duniya ta fara jin ta wadda bata ta6a ziyarta ba sai a wannan karon,da Yayan Romeo ya fara sanyanta a hanyar zuwanta,    Hucin numfashinshi ta dinga ji asaman wuyanta ya lumshe idanuwanshi yana jin wani irin feelings,da bai ta6a ji ba arayuwarshi,ɗan ta halikin nan ya jima yana cutar rayuwarshi saboda ego,almost 30years duk da bai ƙarasa ba,babu aure ba soyayya ta kowace hanya ya haramta ma kanshi mace,But this time around ya fara dawowa cikin hayyacinshi,ya jima bai motsa ba,almost 15 mins,kafin ya mayar da mouth din sa saman nipple ɗinta,kamawa yayi a hankali ya shiga sucking ɗinshi,A ruɗe Sehrish ta zabura,gudun kada tayi mashi irin na jiya yasa ya rufeta gaba ɗaya babu ta hanyar da zata tsere mashi,Sosai ya shiga biyan buƙatar shi da ita,sama sama cikin wani irin yanayi na shauƙi Bacci ya ɗaukesu a rungume da juna,ƙanƙame fa irin sosai ɗinnan, A 6angaren jahad kuwa ta gaza runtsawa,tunda Daddynsu yace mata ta shirya gobe zasu je kano,kwata kwata bata son zuwa kano,Har acikin ranta ta tsani zuwa garin saboda rayuwar da suka yi acikinshi,Ga fargabar halin da zasu tsinci mahaifiyarsu aciki,Araye ko a Mace?Ko a wani mawuyacin hali na rayuwa,ga kuma babynta Junaid,basu jima da yin waya ba har kuka saida yayi mata akan cewa karta tafi tabarshi saboda ya shirya masu outing gobe,Abubuwa da yawa sun bi sun cunkushe mata,tsaye take acikin ɗakin sai faman safa da marwa ta ke yi,ta gaza kwanciya,har wuraren ƙarfe ɗaya jahad bata runtsa ba,Hosana kuwa tana ƙudundune cikin bargo,hankalinta kwance baiwar Allah,ita da babu cutar so ajikinta, Ta jima a haka kafin daga bisani ta samu Solution na matsalar,komawa tayi saman gadonsu ta kwanta tare da jan bargo ta ƙudundune,taso ta jira dawowar sehrish amma shiru bata dawo ba,bata damu da hakan ba saboda tana da tabbacin cewa duk inda take tana acikin ƙoshin lafiya, *Junaid Romeo*.. In midnight (Cikin tsakar dare) *Wuraren ƙarfe 2:30 na dare* Yayi nisa acikin baccinshi yaji an ambaci sunanshi da ƙarfin gaske da wata irin murya mai matuƙar razanarwa,tashin hankali,A firgice junaid ya ware idanuwanshi shi kaɗae asaman gadonshi,Gabanshi ne ya faɗi rass!sakamakon Mutun daya gani tsaye agaban mirror ɗinshi sanye da baƙar jallabiya mai hula,a wani irin firgice junaid ya miƙe zaune tare da toshe kunnanshi ya fasa ƙara mai sautin gaske yana ambaton sunan Daddynsu maimaikon sunan Allah,    Sosai ya shiga ja da baya,Hankalin shi a matuƙar tashe la66ansa na kerma ya shiga faɗin"Daddy!Mommy!Ya Rafayet!ya Omar!kuzo ku taimake ni!nashiga uku!dodo acikin ɗakina!Kashe ni zaiyi,'    Ƙwayar idonshi tamkar zata faɗo waje saboda tsabar tsoro,    Mutumin dake tsaye agaban madubin,wasu irin zaƙwa zaƙwan Akaifune a hannunshi,tsininsu tamkar na wuƙa,Ga uban gashi ajikin fatar hannunshi,juyowa yayi junaid na ganin fuskarshi ya rikirkice ya ruɗe,uban gashi ne ta ko'ina asaman fuskarshi,Ga wasu irin dogayen haƙora dake gareshi har sun sauko daga bakinshi,Idanuwanshi kuwa wa'iya zubilla,   Gadan gadan ya tunkari junaid,A wani irin Sukwane,junaid ya wuntsilo daga saman gadon har yana tuntu6e wurin ƙoƙarin fitowa daga cikin bedroom ɗinshi,fisgar ƙopar yayi dama a buɗe ya barta,da gudun gaske ya fito tare da nufar bedroom ɗin Sgr yana kuka,Sai dai kafin ya ƙarasa wurin part din nashi,Sai ga wannan Mutumin ya bayyana,A gigice junaid ya fasa ƙara ya canza hanya ya nufi part ɗin marshal Omar,Nan ma kafin ya isa,Sai ga mutun ya ƙara bayyana,A galabaice ya sauko daga downstairs,bawan Allah Ya rasa wurin wa zashi,gashi duk ihun da yake yi yana kuka babu mai jin shi,   *Junaid*! Muryar jahad ce ta katse shi,da sauri ya juya wurin da sautin ya fito,a tsaye take tana kallonshi da gudun gaske ya nufeta tare da faɗawa jikinta ya ƙankameta yana faɗin"dodo!dodo!"    Bugun ƙafarshi da akayi ne yasa shi yin firgit ya farga daga baccin da yake yi,Duk zufa tabi ta jiƙa jikinshi sharkaf,kukan da yake yi acikin mafarkin har azahiri yake yinshi hannunshi rungume da pillow,   Biji biji ya fara gani acikin eyes ɗinshi kafin idon nashi su washe,   A hankali ya ambaci sunanta"Aunty Azmee,"yayi maganar tare da tashi daga zaune yana kallonta,    "Meya faru dakai ne junaid?tunda nashigo nagan ka kana ta koke koke cikin bacci,"ajiyar zuciya ya sauke tare dakai idonshi kan wall clock ƙarfe 9 na safe,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,Ko sallar asuba baiyi ba,   Cike da damuwa yace"Aunty Azmee wani mummunan mafarki nayi wallahi,Na tsorata sosai,Amma dana farka na ganki sae hankalina ya kwanta,Allah na gode maka da ya kasance ba gaske bane,da yanzu shikenan Na rasa rayuwata,"    Zama azmee tayi daga gefen gadon mashi,cike da kulawa tace"Junaid!Anya kayi addu'a kafin ka kwanta bacci?   girgiza mata kai yayi alamar a'a "Ni nasani ae,tun lokacin baya nake fama dakai akan yin addu'ar bacci before ka kwanta,amma kaƙi jin maganata,"   Muryarshi tamkar zai yi kuka yace"Aunty azmee,wlh inaso nima na dinga yin addu'ar,amma bansan meyasa ba,karatu baya zama cikin brain ɗina,bazan 6oye maki ba,ban iya komai ba,ko a karatun sallah iya surori biyarne akaina dasu nake yin sallah,amma bayansu wlh ban iya wani abu ba,komai na karanta bai zama acikin kaina,"   Tsananin tausayinshi ne ya kama azmee,har cikin ranta ta damu da halin da junaid yake ciki,tana jinshi tamkar ɗan cikinta,    "Junaid ita addu'a,zaka iyayinta da ko wani irin Yare,Allah yana ji kuma zai amsa maka ne,Inaso ka dage da yin addu'a,nima kuma zan tayaka in sha Allah,"   Ba ƙaramin daɗin maganarta yaji ba, "In sha Allah Aunty Azmee zan dage da addu'a,nagode sosai da irin kulawar da kike bani,"   Murmushi azmee ta saki tare da cewa"kada ka manta fa,nifa na shayar dakai,Na so ka sosai junaid,tun lokacin da kana jinjirinka,ban mantawa Abban ku ya ke kawomin kai, yini kake a wurina,lokacin yayyanka na zuwa aiki wasu kuma ba su kammala secondary ba,mu kaɗai muke kasancewa acikin gidan,Inyi maka wanka,in shafe maka jikinka da mai in gyara maka sumar kan ka,sannan in canza maka kaya,idan na kammala yi maka wannan,sai in shayar da kai,har bacci ya ɗauke mu saman gado,Kasan me"?   Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"a'a sai kin faɗa,"   Taci gaba da cewa"idan na farka naga babu kai a kusa dani kamar in zauce...."   "Saboda me"?Yayi tambayar da ɗan mamaki a fuskarshi,    "Saboda na tsani araba ni dakai,Su fawan da zarar sun dawo daga school,har ɗakina suke zuwa su ɗauke ka,"   Fashewa yayi da dariya sosai har dimples ɗinshi suka lotsa,Bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"Ni bansan meyasa kowa ke sona ba,Ina da farin jini sosai,ko yau muka haɗu da mutun cikin ƴan mintina sai ki ji yace ina burgeshi,"yayi maganar with proud,   Murmushi Azmee ta saki,kafin tace"Because of ur Glamorous personality,kana da kyakkyawar zuciya,shiyasa ka ke sace zuciyar mutane cikin ƙankanin lokaci," ..cike da zolaya yace"Shiyasa jahad ta zauce akan sona,"yayi maganar yana dafe saitin heart dinshi,   Dariya azmee tayi tare da miƙewa tsaye tana cewa"Ga breakfast can yana jiran ka a dining,Jahad ba ta nan balle ta kawo maka a ɗakinka   Dafe saitin zuciyarshi ya kuma yi hankali a ɗan tashe yace"Aunty Azmee kina nufin cewa,Juliet dina bata nan?yanzu saida Uncle Abusufyan ya tafin mu da ita ko"?a shagwa6e ya ƙarasa maganar yana ɗan bubbuga ƙafarshi,har cikin ranshi baiso tafiyar jahad ba,Yaci burin su fita shan ice cream yau,   Fucewa Azmee tayi daga cikin ɗaƙin tana dariya,   Saukowa yayi daga saman gadon jiki asanyaye ya wuce cikin toilet, *Boss Bature*   ❤🤍❤ *Marshal Omar* Fitowar shi kenan daga cikin toilet,Waist dinshi ɗaure da towel hannunshi kuma na ruke da wani short yana goge ruwan dake ɗiɗɗigowa daga jikinshi,   "Ya Omar"muryar hosana yaji acikin kunnanshi,da sauri ya juya don yaga ko itace,Kwance ya sameta saman gadonshi ko kayan baccinta bata cire ba,   Cike da mamaki yace"Kee!me kike yi acikin bedroom ɗina"?    "Ya Omar nifa zuwa nayi kawai don na gaishe ka"tayi maganar a ɗan shagawa6e,    "Haka ya dace kizo gaishe dani?ko sallama babu,kawai sai dai na fito daga toilet na same ki a kwance saman gadona,"Yayi maganar fuskarshi aɗan daure,   Murguɗa mashi baki tayi tare da cewa"Ae ɗakin Mijina ne"   Harara ya watsa mata"waye mijin naki?Allah ya kiyaye in auri mai ɗan kai irin naki,"   Gwalo tayi mashi tare da cewa"Oho dai,a haka ka gani kuma kake so,"_   ƙiris ya rage ya fashe da dariya,amma sai yayi saurin kawar da dariyar don kada taga kamar ma wasa yake yi mata,    "Get out from my bedroom!"a ɗan tsawace yayi maganar tare da nuna mata hanyar fita daga bedroom ɗin,   Maƙe mashi kafaɗa tayi,"Wlh ba inda zani ya Omar,Kazo ka ɗauke ni,ka fitar dani idan ba ka son gani na,"   girgiza kai kawai yayi tare da ƙarasawa gaban mirror dinshi,    "Kaya fa zansa,pls ki fita daga waje idan na kammala saiki dawo,kin ji My baby"    "Ae wlh ba inda zani je,Ae ba wani abu bane don ka sanya kaya agabana,tunda aure zamuyi,"   Shiru yayi bai kara tanka mata ba, Jin yayi banza da ita yasa ta kuma cewa"Ya Omar"shiru yaƙi amsa mata kiran nata,   Ci gaba da magana tayi"Wai ya Omar,idan munyi aure,to taya zamu haihu muma"?   Banza yayi bai tanka mata ba, Bata damu da hakan ba,sai ma ci gaba da maganar tayi,   "Ya Omar,kana ganin nima zan iya haihuwa?Kuma ma Taya za'ae na samu cikin"?   Hauka maganinka Allah,ya furta hakan acikin Zuciyarshi,    "Ji ya Omar ina magana ka wani share ni,idan baka faɗamun ba,to taya zan sani,"?   Ƙin tanka mata yayi,a hasale tace"Shikenan tunda ba zaka bani Amsa ba,wlh idan Daddy ya dawo zanje in tambayeshi ne,don ni bazan bari ayi abun kunya ba,Ayi mun aure bansan komai ba,   A ƙule ya juyo tare da kallonta yace"Ke,Tashi ki fuce mun daga ɗaki"   Maƙe mashi kafaɗa ta kuma yi"anƙi a fita Ya omar,"   Abun ya ɗaure mashi kai,ita ko shakkarshi bata ji,neman ma abunda zata yi mashi ya bugeta take yi don tasan cewa bazai iya ta6a lafiyar jikinta ba,   "Idan kanaso in fita cikin lalama,to ka fara faɗamun taya zan samu ciki idan munyi aure"   "Shine abunda kikeson sani"?yayi tambayar yana kallonta hadi da dage mata gira,ɗaga mashi kai tayi alamar eh, Aikuwa Nan take ya sanya hannunshi ya zame towel ɗin daya ɗaure qugunshi dashi,   Tashin hankali! A gigice Hosana ta fasa wata irin razananniyar ƙara,Kafin kace me kamar walkiya haka tabar ɗakin da gudu tana kuka,ta firgita sosai   Mayar da towel ɗin yayi ya ɗaure waist ɗin sosai,sai faman tiƙar dariya yake yi,har da dafe cikinshi,   "Maganinki kenan,nasan daga yau ba zaki sake yi mun irin wannan question ɗin ba,Yarinya sai kace mai iskokai,Ni bansan ya zan ƙare da ita ba,A haka dai nakeso,kuma zan kula da abuna"ya ƙarasa zancen zucin fuskarshi ɗauke da murmushi ya wuce wurin wardrobe ɗinshi,sai daga baya ya dinga tunanin kada hosana fa taje ta faɗa ma wani abunda ta gani tunda ba hankali gareta ba,Tuna wannan yasa yayi saurin ɗauko jallabiya ya zura ajikinshi,da sauri ya sauko downstairs yana nemanta, Azmee ya hango tana jera kayan abinci asaman Dining na breakfast dinsu,da sauri ya tunkareta,tunkan ya ƙarasa wurinta tajiyo takun takalmin mutun,ɗagowa tayi tare da kallonshi,ganin Marshal yasa ta saki fuska tare da gaisar dashi,    "Barka da safiya Omar,an tashi lafiya," A gaggauce ya amsa mata"lafiya lou,amman pls ko kinga gifcin Hosana,"?   "kamar dai naso naga giftawarta,lokacin ina ƙoƙarin fitowa daga kitchen,kuma naji kamar shessheƙar kuka ta ke,"   "Ina kike tunanin ta shiga ne," Shiru Azmee ta ɗan yi tana tunanin wurin da taga hosana ta nufa,   "Yawwa,ina tunanin bedroom ɗinsu ta nufa,"   Tunkan ta ƙarasa maganar ya kama hanya da sauri da sauri ya nufi ɗakinsu,a buɗe ƙopar take hannu yasa ya turata,tunkan ya shiga ciki,Ya jiyo shessheƙar kukan Hosana,Yana yin sallama taji muryarshi da gudun gaske ta sauko saman gadonsu ta faɗa toilet ta datse ƙopar,tana ci gaba da yin kukan, ..Sehrish na kwance saman gadon,ta ƙudundune cikin bargo,tun da Asuba da ta farka asaman gadon Sgr lokacin ya shiga toilet domin yin alwala,ta saɗaɗa tabar bedroom ɗin nashi,ta dawo ɗakinsu, Kaitsaye ya wuce ƙopar toilet ɗin ya tsaya tare da ambaton sunanta"Am really sorry Hosana,nasan ban kyauta maki ba,ke ce kin takuramin that's why nayi maki hakan,kuma ni fa amsar tambayarki kawai na baki ba wani abu ba,   Cikin shessheƙar kuka yaji tace"Ya Omar baka da kunya wlh,Ni babu ruwana dakai,Wlh bansan ganinka,bansan ganin wannan abun naka" Hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,   A ruɗe ya shiga faɗin"hosana!baki da hankaline?so kike ki tona mun asiri,har wani ya ji mu?kin manta ni zan aureki,"?    A tsiwace tace"wlh saina faɗama daddy idan ya dawo,ince ka nuna mun abunka,"   Hannu yasa tare da dafe kanshi,ya furta"Wayyo Allah na,Ni Omar,naja ma kaina,"   Ƙasa ƙasa yayi da muryarshi cikin lallashi ya soma magana,    "My Hosana pls,ki yafe mun,bazan ƙara ba wllh,kome kikeso zanyi maki,"    "Wlh ya Omar,ko kukan jini zaka yi saina faɗama daddy cewa kai ɗan iska ne,Ni bazan aure ka ba,"   Tsawa ya daka mata tare da cewa"Ki faɗima duk wanda zaki faɗimawa ƴar rainin hankali,Wlh kuma kika kuskura kika faɗama wani sai na sa6a maki,kuma babu ni babu ke,Ƙasar ma zan bari gaba ɗaya in tafi can in auri baturiya,".    Rai a6ace ya juya tare da barin ɗakin nasu,   Sai da taji alamun fitarshi daga ɗakin,sannan ta wanko fuskarta ta,ta buɗe ƙopar toilet ɗin ta fito waje,abun ya dameta sosai buɗe ƙopar ɗakin tayi ta fuce,A dining ta same shi zaune shi da junaid suna yin breakfast,Azmee na yin serving ɗinsu,   Kamar wadda aka zarewa lakar jikinta haka ta ƙarasa ta samu wuri kusa dashi ta zauna,     "Aunty Azmee ina kwana"?fuskar Azmee ɗauke da murmushi ta amsa mata,"Lafiya lou Jahad,kin tashi lafiya...."da sauri junaid yace"Aunty azmee wannan ce jahad?kalli fa ƴan kumatun fuskarta ki gani,Hosana ce,"   Dariya azmee tayi,shi kanshi Omar yaso ya ɗan dara,ita kuwa tsuke fuska tayi tare da jifarshi da harara tace"ina ruwanka da kumatuna"?    murguɗa mata baki junaid yayi dama basu jituwa atsakaninsu,Ƴar tsama sukeyi,     juyawa ta ɗan yi gefenta tare da kallon Marshal,Ya tamke fuskar nan babu annuri acikinta,    Saitin kunnanshi takai bakinta cikin sanyin murya tace"Ya Omar bazan ƙara ba,kuma bazan tona maka asiri ba,dan Allah kada ka tafi ka barni,"   side smile yayi tare da cewa"Its okey,nima wasa nake yi maki,bazan iya tafiya nabarki ba,"   Murmushi ta saki,har hankalinta ya kwanta,     Hannu Azmee takai zata ɗauki plate ta zuba mata abinci,ganin ta zura hannunta acikin plate ɗin Omar suna ci atare yasa ta fasa,Abun ba ƙaramin burgeta yayi ba, *KANO TA DABO TUMBIN GIWA KODA ME KAZO AN FI KA* acewarsu ba,Don ni ban yarda ba, 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Na biya bashi😏 Masu buƙatar littafin Suyi mun magana direct ta layina amma fa message ta whatsapp kawai,Ko an kira ba'za a samu ba, 08103884440 ❤🤍❤ Tun wuraren ƙarfe Goma,Motarsu Abusufyan tayi dirar mikiya acikin jahar Kano,Da kanshi yake yin driving ɗinsu,Jahad na manne a kafaɗarshi tana sharar baccin da bata ƙarasa ba a gida,   Tunda suka shigo cikin garin murmushi ya wanzu akan fuskarshi,Bakomai yake tunawa ba fa ce irin rayuwar da yayi acikin garin tun lokacin ƙuruciyarshi,    "Jahad!ki tashi mun ƙaraso fa,"cike da farin ciki yayi maganar, Sai da ya ambaci sunanta kusan sau 5 kafin ta amsa mashi,tare da miƙewa daga zaune tana yin hamma,ta cikin face mask ɗin dake a fuskarta,   Buɗe idanuwanta tayi tare da juyawa tana ƙarewa garin kallo ta cikin glass ɗin Motar,hakanan ta dinga jin faɗuwar gaba rass!rasss!lokaci guda kuma tashiga tariyo abunda ya faru acikin rayuwarsu azamansu garin, NASARAWA G.R.A Shine Sunan Unguwar da hajiya Ameenatu Wato Gwaggon katsina tayi rayuwa acikinta tare da ahalinta,a hankali motarsu ta shigo cikin unguwar da matsakaicin gudu,A dai dai jerin wasu manyan gidaje na masu hali,Abusufyan ya tsayar da Motar a bakin gate,    "Daddy wannan gidan wanene'?tayi tambayar tana kallon fuskarshi, murmushi ya ɗan yi tare da cewa"Wannan gidan da kike gani acikinsa nayi rayuwa tare da mahaifiyarku,Kuma anan kakan ku Marigayi baba buzu yayi gadi,Allah ya jiƙanshi da rahama,   Amsa mashi tayi da Ameen,kafin suka fito daga cikin motar,   "Allah sarki,Kullum idan nadawo a wancan lokacin,Baba buzu nake samu zaune saman benci yana dafa ruwan bununsa,da zarar ya hango motata zai fara yi mun kirari,Ya buɗe mun gate don in shiga daga ciki," acewar Abusufyan, Jefi jefi mutane ke giftawa acikin unguwar,tun bayan da suka bar kano a lokacin baya,Mijin Gwaggon katsina ne ke zama a cikin gida kafin Allah yayi mashi rasuwa,Tun daga lokacin kuma babu wanda ya ƙara zaman gidan,ko Dr harris idan yazo kano ya kwammace ya kama hotel ya zauna acikinsa,    Hannu ya zura acikin aljihunshi ya curo key ɗin gidan,Ya ƙarasa tare da zura key ɗin ajikin ƙopar dake manne da gate ɗin gidan,Wurin har ya fara tsatsa,ya ciccije daƙyar ya samu ya buɗe ƙopar,   Ya ruƙo hannunta suka shiga daga ciki,    Zuba ma gidan ido tayi tana kallonshi,A ranta tana ayyana irin rayuwar da mahaifiyarsu tayi acikin gidan,Ya haɗu duk da ginin Ya tsufa sosai,akwai fili sosai,Ga wurin buga ball nasu Abusufyan,Ga moto park,da sauransu, Kaitsaye suka nufi Ƙopar da zata sadaka da Babban falon gidan,ita kuwa ta zuba ido tana ƙarewa gidan kallo,Uwar yanace ta ko'ina yayi datti,ga tarin ƙura musamman ajikin glass ɗin windows dana doors,   Buɗe masu ƙopar yayi da key ɗin hannunshi,Yayi gaba tabi bayanshi,Kamar mai jin tsoro haka ta zura ƙafarta ciki,Matsakaicin falo ne,Yadda kasan bola,ledoji,yayi da sauran tarkace a kasanshi,Tiles ɗin kuwa duk yayi dirty kura ta rufe shi,Sofas ɗin dake a ɗakin duk sun gajarce sunyi ƙanƙanta,yadin jikinsu yayi diƙiƙi,   "Daddy,ina ɗakin da Oumman mu tayi rayuwa acikinshi?ka nuna mun inaso naga ɗakin,"   Da yatsan hannunshi ya nuna mata bedroom ɗin da abu tayi rayuwa,da sauri ta nufi ɗakin,shima yabi bayanta,A datse ƙopar ɗakin take amma babu key ajikinta,da ƙarfi yasa hannu ya turata,ji kake ƙiiiiiiii,ta buɗe a slow,   Faɗawa cikin ɗakin tayi tana bin kayan cikinshi da kallo,labulayen duk sunyi ƙura,sun nannaɗe sun cukuikuye,Carpet ɗin bakin kofar ya fita hayyacinshi,Single bed ne acikin ɗakin,sai wardrobe ta bango,itama duk tayi ƙura,book shelve,Da dressing mirror da sauran tarkace,komai yafita hayyacinshi,    Qur'ani ta hango saman bedside drawer ɗin gadon,   Tun kafin tayi magana Abusufyan yace"Wancen qur'anin da kike gani na mahaifiyarku Ne,mace ce mai son addini tana ƙoƙari sosai,bata wasa da ibada,da haka ta sace mun zuciyata,"   Hawaye ne suka soma sintiri akan fuskarta,ƙarasawa tayi gaban drawer ɗin ta sanya hannu tare da shafa al'qur'anin,ta kakka6e ƙurar dake akanshi,ɗago dashi tayi a hankali ta manna mashi kiss,    "Daddy inason qur'anin nan sosai,zamu tafi dashi,"ta ƙarasa maganar tare da buɗe handbag ɗin dake hannunta,ta zura shi ciki,"   School bags ta hango guda biyu,Anyi hanging ɗinsu a saman bango inda aka bubbuga ƙusa,   Da sauri ta ƙarasa tare da kai hannu ta curo jakunkunan,ta sauko dasu ƙasa,ta zuƙunna tare da buɗe jakar,Littattafan addini ne cikinsu,Ahlari ne,Tajweed,Fiqhu,da sauransu,ɗayar jakar kuma da ta buɗe Littattafanta ne na boko da take zuwa school dasu,komai nata mai tsari,   Abusufyan kuwa wurin wardrobe ɗin kayanta ya wuce,buɗewa yayi yana kallon jerin wasu daga cikin kayanta,Uniform ɗin islamiyyarta ya ɗauko,tare da rungumesu a ƙirjinshi,Sae lokacin hawaye suka shiga zarya akan fuskarshi,    Bazai ta6a mantawa ba,da rana ta farko daya fara sanyata acikin idanuwanshi,a lokacin tana kan hanyar dawowarta daga school,    "Jahad,"ya ambaci sunan ta tare da juyawa yana kallonta   "Na'am Abba,tayi maganar tare da miƙewa ta ƙarasa gabanshi,    "Kin ga waɗannan kayan,dasu ne na fara ganin Oummanku,Uniform ɗinta ne na islamiyya,"   Murmushi ta saki tare da sanya hannu ta kar6i kayan,Rungumesu tayi ajikinta,Sae ta dinga jin tamkar Oumman tasu ta rungume,   6ata lokaci sukayi sosai suna bincike acikin ɗakin Zainabu abu, Daga bisani ne Yunwa ta fara kamasu gashi gidan babu abinci,Yanke shawarar zuwa nemo masu abincin yayi,ya barta acikin gidan,Gyara masu ɗakin oummansu ta shiga yi,Taci baƙar wahala sosai,Bayan ta share ɗakin har wanke shi tayi,A kitchen ta samu bokiti da ledar detergent,ga ruwa available,sosai ta wanke ɗakin sai ga tiles ɗin yayi haske sosai,Cire zanin gadon tayi ta ɗauko wani acikin wadrobe,Ta shimfiɗa masu bayan ta kakka6e gadon,ta goge jikinshi, Hatta glass door din sai da tabi tayi scrubbing ɗinsu,ta goge yanar ɗakin,lokaci guda kamanin ɗakin suka canza,Komai na son gyara,Toilet ta shiga nan ma tataras dashi duk sai a hankali,sae da ta fara gyarashi fess,Sannan ta samu ta ɗan watso ruwa tare da ɗauro alwala,   Darduma ta dauko cikin wadrobe ta shimfiɗata,ta kabbara sallar azhar,A tsanake tayi sallar tana kammalawa,agalabaice bacci ya ɗauketa saman dardumar, Wuraren ƙarfe 2:30 Abusufyan ya shigo cikin gidan hannunshi ɗauke da Ledojin da yayi masu take away na restaurant,   Da sallama ya shiga cikin falon,wuce wa bedroom ɗin yayi,ba ƙaramin mamaki yayi ba,ganin yadda Jahad ta gyara ɗakin tsaf,komai yayi fess,kamar lokacin da Zainabun shi na nan,   Murmushi ya saki tare da samun wuri kasa gefenta ya zauna,Ya ajiye ledojin,Hannu yasa abayanta ya ɗan bubbugi kafaɗarta"Jahad!tashi muci abinci,"   Firgita tayi ta farka tana Sambatu"Ya Rafayet,baisan na taho ba...,"   Ƙiris ya rage yaji abunda tace, Hannu tasa da sauri ta toshe bakinta,tana kallonshi,Shima kallon nata yake yi,    "Me kika ce"?girgiza mashi kai ta shiga yi,tana faɗin"bakomai Daddy,Ashe ka dawo,nagaji ne shi ne na ɗan kwanta don in huta,"   Murmushi yayi tare da cewa"Ae naga aikin da kikayi,kin yi ƙoƙari sosai,"   "Bari na ɗauko mana plate,"ta miƙe tare da nufar hanyar fita daga ɗakin,   Sai da tafito sannan ta dafe saitin zuciyarta tana faman sauke ajiyar zuciya,a ranta tace"Allah yaso daddy baiji abunda nace ba,dashi kenan zai gano ni,"_ Tayi maganar tare da yin saurin wuce wa cikin kitchen ɗin,A cikin kwandon wanke wanke ta samu tray da plates tare da cups,gaban basin taje ta wanke su tass da klin da soso,ta ɗaurayo su,bayan ta kammala wankesu saman tray din ta jera su,Ta ruƙosu a hannunta sannan ta dawo cikin bedroom ɗin,   "Salamu Alaikum"Ta kwaɗa sallama ta shiga ciki,Zuƙunnawa tayi ta ajiye trayn agaban Abusufyan,   Janyo ledar tayi ta buɗe,tare da sanya hannu ta curo fried meat(tsiren nama)ta jera masu shi asaman tray,hannu yasa ya taimaka mata wurin ɗauko sauran kayan,Cool Drinks ne da sauran kayan maƙwalashe,atare suka shiga ci suna fira gwanin ban sha'awa,bayan sun kammala cin abincin,Abusufyan ya tattara kayan abincin da sukayi amfani dashi,Ya wuce dasu kitchen yabarta zaune tana shan lemu,bayan ta shanye,ta sanya robar a dustbin,komawa tayi saman gadon ta kwanta,cikinta yayi haƙe² saboda cin muguntar da ta yi,wani baccin ne ya sake ɗaukarta, *Boss Bature*   ❤🤍❤ Wuraren ƙarfe 3 na rana Sgr ya dawo cikin gidan,Tun bayan da ya fita da safe Ko breakfast bai nema ba,saboda Emergency call ɗin da akayi mashi acan headquater ɗinsu,Jikinshi na sanye da Tank Top,light green,Tare da wandon kaki,Yayin da kunnanshi ke manne da wayarshi,Cikin harshen faransanci yake yin waya,   Da sauri da sauri ya haye upstairs,direct ya wuce part ɗinshi,tunkan ya shiga ciki ya fara jin daddaɗan ƙamshi nakai mashi ziyara acikin hancinshi,gaba daya yayi tsammanin cewa zai same ta ne a part ɗin nashi amma baiga Kowa ba Wayaam,Bedroom ɗinshi ya shiga,Shaf shaf ya rage kayan jikinshi ya faɗa cikin toilet,After some minutes ya fito waist ɗinshi ɗaure da towel,Yana tsaye agaban mirror yaji motsin mutun acikin falonshi,    "Who's there"?yayi tambayar yana jiran amsa,   "Sehrish ce," Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"Come in,"   Hannunta na ruƙe da tray na Lunch ɗinshi da ta shirya mashi,tana tafiya gabanta na faɗuwa rass rass   Sallama ta fara yi mashi ya amsa,kafin ta sanya ƙafa ta shiga ciki,sum sum ta lalla6a ta ajiye mashi tray asaman table,Jiki na rawa ta juya zata bar ɗakin,   Zuba mata ido yayi ta cikin mirror yana kallonta,tana ƙoƙarin ɗaga ƙafarta tabar ɗakin taji ya Ambaci sunanta kai tsaye"JAHAD"   DARAAAM!!!!!!Taji gabanta ya faɗi,sanƙamewa tayi atsaye,hankalinta a matukar tashe,tuni zufa ta shiga wanke mata fuskarta,Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya abakinta,Abun ya ɗaure mata kai,farat ɗaya Sgr ya gane cewa ba Sehrish bace,Hatta junaid yau bai ganeta ba,kowa ɗaukar sehrish yake yi mata,saboda sunsa ma ransu cewa da jahad aka tafi,Shiyasa basu natsu sun gane cewa itace ba,"    Wata irin zufa ce ta shiga gangarowa asaman fuskarta,ƙiris ya rage ta saki fitsari a wando, Slowly ya juyo tare da tunkararta,jikinta sae kerma yake yi,hannunta ya ruƙo tare da juyo da ita ta gabanshi ya kasance suna fuskantar juna,wuƙi wuƙi tayi mashi da idanu tana faman mazurai na rashin gaskiya,    Abun ya ɗaure mashi kai,Wai harshi zasuyi wa wayau,kamar wani soko,An gaya masu cewa a banza yakai muƙamin da yake dashi a yanzu,    goya hannayenshi yayi asaman wide chest ɗinshi,Ya zuba mata ido yana kallon Ikon Allah,    Saboda tsabar rashin gaskiya tun kafin ma yayi mata magana,murya na kerma tace"Amm...um..babban..yaya pls dan Allah kayi haƙuri ka yafe mun,Wayyo Allahna na shiga uku,"a ruɗe tayi maganar,tana yarfa hannuwanta,tsoranta kada ya kwashe ta da mari,   Ruke ha6arsa yayi cike da mamaki yake kallonta from head to toe,    Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,tun kafin ma taji hukuncin da zai yanke mata,Zuciyarta sae bugawa take yi ba ƙaƙƙautawa,    "Where's she"?fuskarshi a ɗaure yayi tambayar,   Sunnar dakai tayi kamar munafuka,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Wlh baban yaya ni bani nace ta tafi ba,yau ne dama da asuba,ta same ni cikin damuwa take tambayata lafiya shi ne na sanar da ita cewa Ni banso nabi Daddy kano,bansan zuwa garin saboda abunda ya faru damu acikinshi...."   Tunkan ta ƙarasa maganar yace"What!tafiya tayi without My Permission,"ranshi a matuƙar 6ace yayi maganar,   "Ya salam"ya furta hakan tare da zura hannunshi cikin sumar kanshi, Ya runtse idanuwanshi, "Am sorry,babban yaya bazan ƙara ba,"_ Jinjina kanshi yayi tare da ware idanuwanshi akan fuskarta,yana kallonta duk tabi ta susuce,    "Kin iya frog jump ko"? Waro ido tayi tana kallonshi,girgiza kai tashiga yi alamar a'a, ...ruko hannunta yayi ya fito da ita cikin falonshi,fuskarshi a daure yace"Oya,start from here,karki kuskura ki tsaya,if not zaki ga abunda zai biyo baya,"    Jahad tamkar zata fashe da kuka,Zuƙunnawa tayi tare da kama kunnanta kamar ɗan kwaɗo haka tafara yin tsallan tana zagaye kujerun,tun a first round jikinta ya fara gaya mata,Komawa yayi cikin bedroom ɗinshi ya ɗauki wayarshi daya bari agaban Mirror,Numbar Uncle Abusufyan ya lalubo,ya danna mashi Call, A lokacin Abusufyan,Na acikin kitchen ya tu6e rigarshi daga shi sai shorts,ya dage sai aikin goge goge yake yi da ƴan wanke wanke,ya gyara kitchen ɗin tsaf,   Fitowa Sehrish tayi hannunta ruƙe da wayarshi,har tuntu6e take yi wurin yin sauri donta kai mashi wayar,tana baccinta mai daɗi ringing ɗin wayar shi ne ya tashe ta, "Daddy,ana kira,"ta ƙarasa maganar yayin da take shiga kitchen ɗin,hannu abusufyan yasa ya kar6i wayar,duba screen din wayar ya fara yi,    *My first in-Law* Shi ne sunan daya bayyana akan screen ɗin,Yayi mamakin ganin kiran Sgr,Picking call ɗin yayi ya kara wayar a kunnanshi,    "Assalamu Alaikum" On the other hand,Sgr ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,Uncle kun isa Lafiya"? .  "lafiya Lou,ae tun ɗazu muka ƙaraso,"    "Okey,inason magana da sehrish ne,tana a kusa"?    Murmushi abusufyan yayi tare da cewa"Ae bada ita muka zo ba,ko ka manta ne?    "Uncle,Da ita ka tafi bada Jahad ba,yanzu haka jahad tana a part dinta,Sunyi musaya ne,"   Cike da mamaki abusufyan yace"Jahad tana a gida!"   Gaban Sehrish ne ya faɗi rass,wuƙi wuƙi tayi da ido,ɗagowa abusufyan yayi tare da kallonta,Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,sai lokacin ya shaida cewa Sehrish ce,ya ɗauko amatsayin Jahad,Ko ya akai suka shirya Wannan batare da kowa ya ankara ba,   Sunnar dakai ƙasa tayi,ganin irin kallon da daddynsu yake yi mata,   Rai a6ace ya miƙa mata wayar"Kar6i nan,"   Hannunta na kerma ta kar6i wayar,hankalinta a matuƙar tashe,ta sanya wayar a kunnanta,muryarta tamkar zata yi kuka tace"Ya rafayet........"    Tunkan ta ƙarasa maganar ya daka mata tsawa"Shut up!"nan take ta shiga taitayinta,     "da iznin wa kika bar garin nan"?_   Idanuwanta ne suka cicciko da kwalla,Sae faman kallon uncle take yi,sam baiji daɗin abunda sehrish tayi ba,don yasan ƙarshe kanshi abun zai ƙare,    "Am sorry ya rafayet,dan Allah kayi haƙuri,Bazan ƙara ba,"   dogon tsoki yaja,Kafin yace"Come back home,In ba haka ba,Ranki zai 6aci,"yana faɗin hakan yayi rejecting kiran,   Fashewa tayi da matsanancin kuka, Hannu abusufyan yasa ya kar6e wayar,   "Koma meya laifinki ne!Ashe baki da hankali Sehrishi!Why kike son Jamin ina zaman lafiyana?,Taya zaki kamo hanya batare da iznin Mijinki ba,?"    Cikin shesshekar tace"dan Allah daddy,kayi haƙuri,na kwallafa raina ne akan son zuwa,nasan nayi laifi,Kuma nayi danasanin yin hakan,Amma dan Allah daddy,Ka roƙan mun alfarma a wurinshi,Yabarni in zauna,Saboda yace in koma gida yau ɗin nan,"ta ƙarasa magana tare da sanya hannu tana share hawayenta,   "I can't Call him Sehrish,rafayet bazai saurari kowa ba a halin yanzu,Kawai kije ki shirya kayanki,in kaiki tasha ki hau mota," Jin haka yasa ta ƙara fashewa da matsanancin kuka,tana faɗin"dan Allah daddy,kada ka mayar dani,Nashiga ukuna,"   Sosai take kuka,Shi kanshi ya tausaya mata,duk yadda take shakkar Sgr amma ta kama hanya ta baro gidan batare da izninshi ba,tabbas ba ƙaramin son zuwa takeyi ba,    Muryarshi a sanyaye yace"Kiyi hakuri daughter,babu yadda zamuyi dole ki bi umarnin Mijinki,lokaci yana ƙurewa,ki je ki shirya kayanki,mu tafi tasha,"   Juyawa tayi da gudun gaske,Ta koma ɗaki,Saman gadon ta faɗa tare da fashewa da wani sabon kukan, Jikin abusufyan ba ƙaramin sanyi yayi ba,yaso ace akwai wata hanyar da zai iya taimaka mata,don ta zauna a kanon,Amma ba halin yin hakan,   yana cikin wannan zancen zucin wayar shi ta shiga ruri,da sauri yakai idonshi kan wayar dake hannunshi don yaga mai kiran nashi,Sunan Yaya Hossein ne ya bayyana akan screen din wayar,   Da sauri ya answer kiran ya kara wayar a kunnanshi"Assalamu Alaikum,Yayana na kaina"_   On the other hand,Abba yace"wa'alaikum salam ƙanina na kaina,Ya kake fatan kun isa kanon lafiya,"   Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Mun ƙaraso tun wuraren goma,"   Abba yace"Madallah,naji daɗi sosai,kai dawa kuka tafi ne"?    Shiru ya ɗanyi yana tunanin halin da sehrish take ciki,ranshi ne ya bashi cewar Ya sanar ma Yayan nashi,May be ya iya dakatar da Sgr ɗin,    Calmly ya soma magana"Ya hossein,Wlh an samu matsala,Da jahad na shirya tafiya,bansan ya akai ba,su ka yi musaya ita da sehrish,dama ta kwallafa rai akan son zuwa kano,To yanzu haka zancen da nakeyi maka,Muna tare da Sehrish ɗin,Kuma Sgr ya gane cewa da ita muka zo kano,ya bada umarnin ta koma yau yau ɗinnan,baiwar Allah tana cikin damuwa,yanzu haka tana can tana kuka,"yaƙarasa jawabin yana jiran jin amsar da abba zai bashi,    "Kada ka damu,Ka lallasheta ta kwantar da hankalinta,Ni zanyi mashi magana,duk yadda mukayi dashi,in sha Allah i will inform you,"_   Ajiyar zuciya abusufyan ya sauke tare da cewa"Nagode sosai,Yayana nakaina Allah yabar zumunci atsakaninmu,"    "Ameen Ameen,ƙanina,"abba ya amsa mashi before suyi sallama,    Har hankalinshi ya ɗan kwanta duk da yana zullumin amsar da abban zai bashi,don yasan halin Sgr wani lokacin idan ya burkice,mai tankwarashi sae Allah, A lokacin da kiran abban ya shiga wayarshi,Yana zaune asaman sofa,ya aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,Yana sanye cikin jeans da t~shirt,yayin da jahad ke zukunne agabanshi,Tayi kneel down fuskar nan tayi jaga jaga da ita,tasha kuka har ta gode wa Allah,    Hannu yakai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman front table din gabanshi yayi picking call ɗin,tare da kara wayar a kunnanshi,Ya furta"assalamu alaikum,"    Acan 6angaren abba ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,My son ya kake ya gida,ya kuma aiki"    "Alhamdulliah" Abba yace"Yawwa,Rafayet dama game da yarainyar nan ne,Sehrish,"tunda yaji ya ambaci sunanta,Ranshi ya bashi cewar sunkai ƙararsa ne,     "Dan Allah rafayet,ka ƙyale yarinyar nan ta zauna,ba jimawa zasuyi acan ba,Yarinyar nan ta kwallafa rai akan son zuwa can shiyasa harta tsallake ta tafi ba tare da saninka ba,Amma kai shaida ne akan yarda takeyi maka biyayya sau da ƙafa,duk wani abu da zai 6ata maka rai,tana ƙoƙari don taga ta faranta maka rai,pls rafayet ta ci albarkacin wannan,"   shiru yayi batare da yace komai ba,   Har sai da abban ya sake cewa"Rafayet naji kayi shiru,"   Ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa"its Okey daddy,na haƙura,"Yanayin yadda yayi maganar,bada son ranshi ba,    Muryar abba ɗauke da farin ciki yace"Ko kaifa,Wlh har naji daɗi acikin raina,Allah yayi maka albarka " "Ameen"daƙyar ya iya furta hakan,Sallama su kayi ya janye wayar daga kunnanshi,   mayar da idanuwanshi yayi kan jahad yace"U can go"   Miƙewa tayi tana faman ɗangyasa ƙafarta,tabar falon nashi,ba ƙaramin jiki taji ba,Saukowa tayi downstairs tana cigaba da yin shessheƙar kukan,   adai dai lokacin junaid ya faɗo cikin falon,Tsayawa yayi yana kallonta,ƙarasawa yayi da sauri wurinta yana faɗin"rishi lafiya meya faru"? ...ɗagowa tayi da idanuwanta waɗanda sukayi ja saboda kukan da tasha,Waro idonshi ya ɗanyi tare da ambaton sunanta"JAHAD"    Cikin shesshekar kuka ta amsa mashi"Na,am"    Hannu yasa ya tallabo fuskarta,"Dama bada ke aka tafi kano ba"?   Jinjina mashi kai tayi alamar eh,sannan tace "Tare da sehrish aka tafi,amma dani muka shirya tafiya,Shine mukayi musaya ni da sehrish,yaya rafayet ya gano ni,Shine ya hukunta ni Hada tsallan kwaɗi ya sani,"    Hannuta ya ruko,tare da samun wuri saman sofa suka zauna,    Ranshi aɗan 6ace yace"Allah dana son da haka bazan bari Babban yaya ya sanyaki yin tsallan kwaɗi ba,Meyasa zai sanya juliet ɗita,Aikin wahala,'?    hannu yasa yana share mata hawayen dake sauka akan fuskarta,cikin lallashi yace"stop crying my juliet,Allah in baki daina zubar da hawayenki ba,Nima zan fara kukan,".    Cike da zolaya,ya sanya hannunshi yana murza idanuwanshi,kamar zaiyi kukan,   Da sauri ta ruƙo hannunshi tana faman sauke ajiyar zuciya tace"Nadaina".   murmushi ya saki tare da cewa"Yaushe zamu fita yawo?Da anjima ko gobe"?   Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Mu bari sai gobe,Yanzu har la'asar tayi,Nafiso mu fita da wuri,mu zaga garin nan,"    "Yadda kikeso haka za'ayi,"ya karasa maganar,tare da kai la66ansa zai sumbaci gefen fuskarta,Karaf idanuwanshi suka sauka akan na SGR dake ƙoƙarin saukowa downstairs,da sauri ya janye la66ansa,ya shiga ƴan kame kame,   girgiza kai kawai sgr yayi don yaga abunda junaid ɗin ke ƙoƙarin yi,Fita yayi daga cikin falon batare daya tanka masu ba,    *Boss Bature* *Sehrish* hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,jin cewa an barta ta zauna a kanon,taji daɗi sosai acikin ranta,duk da tana fargabar hukuncin da Sgr zai yanke mata idon suka koma gida, Bayan sallar la'asar,Suka shirya tsaf domin zuwa hotoro,Unguwar da sukayi rayuwa a cikinta,Abusufyan ne ke driving ɗinsu,tana zaune a gefenshi tana latse latsen wayarta,Yayin da can ƙasan zuciyarta ke cike fal da fargabar zuwa anguwar,A hankali Motar ta shararowa da matsakaicin gudu,izuwa cikin unguwar bai direta a ko'ina ba sai a ƙofar gidansu,don bai manta da kwatancen gidan ba,duk da yaɗan so ya ruɗe saboda sabbin gine ginen dake a wurin,kasa fitowa sehrish tayi daga cikin motar,Saboda yanayin da tashiga,ta tsani yin toxali da unguwar,Saboda bata son duk wani abu da zai tuna mata rayuwarsu ta baya, Fitowa abusufyan yayi daga cikin motar ya zagaya,ya bude mata ƙopar,"Daughter,mun ƙaraso fa,"jiki asanyaye ta fito daga cikin motar,yayin da idanuwanta ke cike tab da kwalla,A wani slow ta wurga kwayar idonta akan gidajensu,Ginin ya tsufa sosai,duk fentin ya ƙoƙe,ya gajarce,An garƙame gidan da ƙaton ƙwaɗo,duk yayi tsatsa,da alama anjima ba'ayi amfani da gidan ba,mayar da idanuwanta tayi akan gidansu maman sadeeq,A rufe yake gidan da makulli,Gidan ya tsufa shima Amma bai kai gidansu tsufa ba,saboda an canza mashi fenti, Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,juyawa ta ɗanyi tare da kallon abusufyan dake tsaye,jikinshi duk yayi sanyi,Saboda tunawa da wasu abubuwa da suka faru a rayuwarshi,   Mutanen dake kai komo acikin Layin nasu sai faman leƙensu sukeyi,musamman ƴan yaran anguwar,   "Daddy,Kamar basu nan fa,naga gidan a rufe,"   Uncle yace"Bari na samu yaro na tambayeshi,Muji ko sun tashi ne,"   Yana ƙoƙarin rufe bakinshi,Yaji anyi mashi sallama ta bayanshi,Muryar wani dattijo ne,juyawa yayi tare da kallon mutumin,tsoho ne amma ba irin tukuf ɗinnan ba,jikinshi na sanye da koɗaɗɗen yadi,ƙafafunshi na sanye da wasu siɗaɗdun silifas duk sun fita hayyacinsu,kamar mahaukaci,    Da sauri abusufyan ya miƙa mashi hannu donsu gaisa,  Dattijon ya maƙe hannunshi tare da cewa"Haba Alhajin Allah,baka ga yadda hannuna yake ba duk datti a haka zaka gaisa dani,"   Murmushi abusufyan ya sakar mashi,"dan Allah kada ka hanani gaisawa dakai,"   Mika mashi hannun tsohon yayi suka gaisa,Sannan yace"bawan Allah,ban ta6a ganinka acikin unguwar nan ba,Kuma da alama kamar wani ku ke nema ko"?   abusufyan yace"ƙwarai kuwa,wannan Ƴa tace,Munzo daga abuja ne,Muna neman..umm....."bai ƙarasa maganar ba,saboda ya manta da sunan mutumin,   Sehrish ce ta ƙarasa mashi maganar"Malam nura muke nema,malamin makarantar islamiyya,"   Dattijon yace"Ae nan ne gidan shi,Sae dai kash,Sunyi tafiya zuwa kankia wurin jana'izar Wani kawunshi daya rasu,"   Jin haka yasa yanayin fuskar abusufyan ta ɗan canza,zuwa damuwa,   "Amma,tun yaushe suka tafi"?   Dattijon yace"tun makon daya gabata,Amma jiya munyi waya dashi ya sanar dani cewa Yau ko gobe zasu dawo,"   Ba ƙaramin daɗi suka ji ba,don har sai da abusufyan ya ɗanyi murmushi,   Hannu yasa cikin aljihunshi ya zaro kuɗi sababbin ƴan dubu dubu kusan dubu goma sha biyar ya miƙa ma dattijon, Washe baki tsohon yayi tare da sanya hannu biyu ya kar6i kuɗin,tare da cewa"yalla6ai kamar ka sani wlh yau gidana da yunwa muka tashi,yara sai kuka sukeyi,Hakanan na gaji da zama cikin gidan, nace bari na fito na nemi na abinci,Ashe arziƙi ne ke kirana,Allah na gode maka,da ka haɗani da wannan bawan naka,Ya Allah kamar yadda ya farantamun rai,kaima ka faranta mashi nashi,ka biya mashi buƙatunshi na alkhairi,'yana addu'ar hada ƴar kwalla akan fuskarshi,    Atare suka dinga haɗa baki suna Amsa mashi"ameen ameen,   Abusufyan yace"baba taimakon da zakayi mana,idan sun dawo dan Allah ayi gaggawar sanar damu,Bari na baka lambar wayata,   Ya ƙarasa maganar tare da zura hannunshi cikin aljihun wandonshi ya ɗauko wayarshi,   Hannu dattijon yasa,a gaban aljihun rigarshi,Ya curo ƴar ƙaramar wayarshi tecno,taji jiki duk tafita hayyacinta,miƙa ma abusufyan wayar yayi"kar6inan yaro,sanya mun numbarka,kayi mun saving ɗinta da sunan Mai mutunci,Zanfi ganewa,Da zarar sun dawo in sha Allah,bi'iznil lahi,koda ƙarfe ɗayan dare ne zan kira in sanar dakai,"   Murmushi suka saki gaba ɗayansu,kar6ar wayar abusufyan yayi,madannan jikinta duk sun nutse ciki,daƙyar ya samu ya rubuta mashi numbar,yayi mashi saving da Mai mutunci,Sanna ya mayar mashi da wayar"Gashi baba,mun gode sosai,Sai naji ka,Allah yasa adace,"   Tsohon ya amsa mashi da ameen ameen,ae tunda ka farantamun raina,Kaima sai Allah ya faranta maka naka,har addu'a sai nayi maka idan nayi sallah,   "Ina godiya sosai,"ya karasa maganar tare da ruƙo hannun sehrish suka shige cikin mota,key yayi ma motar,a hankali yayi reverse,tare da karya kwana,da gudun gaske ya fuce daga cikin unguwar,   Nasarawa suka koma,a bakin gate din gidan ya sauke sehrish,Saboda zuwa masallaci,An fara kiran magrib,Miƙa mata key ɗin gidan yayi"kar6i nan,ki rufe gidan da kyau,Bazan dawo da wuri ba,Saboda inaso naje nayi mana siyayyar kayan abinci,dana amfani,"_   "Toh daddy adawo lafiya"tasa hannu ta kar6i key din,kafin ta juya ta nufi cikin gidan,tsayawa yayi acikin motar yana kallonta,har saida ta 6ace ma ganinshi,ya tabbatar da ta rufe ƙopar gidan,Sannan ya tashi motar ya fuce,    A 6angarensu Aunty babba kuwa,basu isa Enugu ba sai wuraren ƙarfe sha ɗaya na dare,Sunsha uwar tafiya,ba ƙaramin jiki suka ji ba,Acikin garin suka kama ɗaki a hotel,Tunda suka shiga ɗakin,kowaccensu ta baje saman gadon ɗakin,suka shiga sharar bacci kamar wasu matattu,Ga uwar yunwa na cinsu,sai da sukayi bacci mai isarsu,Kafin suka farka neman abunda zasu sama cikinsu,Oder sukayi aka kawo masu lafiyayyan abinci,kamar wasu kuraye haka suka tasarwa abincin suna Ci,Sai da suka ci suka ƙoshi,tukunna suka koma saman gadon,Suka dasa wani sabon baccin,ba tunanin yin sallah,a ƙagare suke washe gari yayi su wuce cikin dajin,   *Boss Bature*    ❤🤍❤ Har Wuraren ƙarfe 12,Abusufyan bai dawo cikin gidan ba,gashi yabarta ita kaɗai,da farko bata damu ba,falo ta dawo ta zauna saman sofa,daya ke akwai nepa,hasken globe ya gauraye ko'ina,hannunta na ɗauke da littafin oummansu tana karantawa,Kalaman soyayya ne acikinshi,a cikin drawer ta samu littafin,Wani page ta buɗo acikin littafin Sunan oummansu ne akai dana Ya sayyadi,Aikuwa rai a6ace ta sanya hannu ta yage takardar tare da yin wurgi da ita,Mayar da hankalinta tayi sosai akan littafin tana karanta love messages ɗin dake aciki,da zarar taga wanda ke ɗauke da sunan ya sayyadi,jikinta har rawa yake yi wurin sanya hannu ta yage shi, Tana cikin wannan karance karance,kwatsam!Aka ɗauke da wutar nepa,nan take duhu ya gauraye ko'ina,babu haske ko misƙala zarratin,gashi ta baro wayarta saman drawer cikin ɗakin,Sanin kanku ne sehrish muguwar matsoraciya ne,Tuni ido ya raina fata,Hankalinta yayi mugun tashi,jikinta ya shiga yin kerma,kamar gunki haka ta ƙame a zaune ta gaza motsawa,tana cikin wannan yanayin na tashin hankali,Tajiyo takun takalmin mutum,A matukar tsorace ta shiga ambaton sunan Daddynsu da ƙarfi"Daddy!daddy!dan Allah kana ina,nashiga uku,'   Gabanta ne ya fadi lokacin da ta tuna cewa,daddynsu da Motarshi ya fita,da ace shine ya dawo cikin gidan to tabbas zata ji sautin ƙarar shigowar motarshi,    Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,jin motsin mutumin na tunkarota,a razane ta saki littafin dake a hannunta,ta miƙe daga saman sofa ɗin tashiga ja da baya,tana tafiya saɗaf saɗaf,hawaye duk sun wanke mata fuskarta,zuƙunnawa tayi ta soma yin rarrafe a hankali tana ƙoƙarin gano ƙopar ɗakin oummansu,cikin rashin sani takai hannunta saman wani gwangwanin maltina,aikuwa ya bada wani irin sauti rakwakwas,a gigice sehrish ta miƙe,gudu gudu sauri sauri,ita kanta batasan inda zata tunkara ba,Unfortunately tayi tuntu6e da wani abu,gaba ɗaya ta tafi zata faɗi ƙasa,ta saki wata irin razananniyar ƙara,   Sai dai kafin takai ƙasa,Taji an damƙi qugunta,kwakkwaran ruƙo akayi mata,kafin aka janyota da ƙarfi,ta faɗa saman ƙirjin mutumin,koma waye wannan ba ƙaramin mutun bane,ƙarƙarfan gaske,   Tashin hankali domin son sanin wanene wannan mutumin,Mu haɗu gobe inda rai da lafiya,In Allah yasa muna da rabon ganinta kenan💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Am really sorry,🙏 Tayi matuƙar tsorata dashi,kasa ɗagowa tayi daga jikinshi,jikinta sae kerma yake yi,lokaci guda daddaɗan ƙamshin turarenshi ya daki hancinta,nan take ta ruɗe tana ƙoƙarin gano a ina tasan ƙamshin nan,duk duniya mutun ɗaya ne ta sani mai irin wannan ƙamshin turaren mai matuƙar ratsa zuciya,Ruɗewa tayi tana so ta canko wanene,kuma tana kokwanton anya hakan zai iya kasancewa gaskiya?zame hannayenta tayi daga saman waist ɗinshi da ta ruƙe,ta matsar dasu har izuwa mid back ɗinshi,Gabanta ne ya faɗi rass jin ta shafo doguwar sumar kanshi,muryarta na kerma ta furta sunanshi"BABBAN YAYA..!"tana ambaton hakan,Wutar ɗakin ta dawo nan take haske ya gauraye ko'ina tamkar da Rana,zuba mashi ido tayi tana kallon kyakkyawar fuskanshi wadda ke sanye cikin face mask black colour,Launin rigar jikinshi ya lumshe idanuwanshi,slowly ya ɗan waresu akan fuskarta,Ae tana ganin blue eyeballs ɗin nan nashi,Ta ƙara tabbatar da hasashenta,abun yayi mugun ɗaure mata kai,kallonta yake yi from head to toe,fuskarta duk tayi zufa saboda tsabar firgicin da ta shiga,ga hawaye jaga jaga a fuskar,duk don saboda an ɗauke da wutar nepa ta ganta acikin duhu, Sai faman sauke ajiyar zuciya take yi,hankalinta har ya kwanta da ta tabbatar cewa shine,Tayi tunanin wani mugunne yazo don ya cutar da ita,tayi farin cikin ganinshi sosai kamar tayi ihu,Amma ta wani 6angaren tsoran hukuncin da zai yanke mata take yi,duk a tunaninta yazo ne don ya hukuntata,tunda ya bata Command taƙi bi,    Ganin irin kallon da yake yi mata ne yasa tayi saurin sunnar da kanta ƙasa,tana wasa da yatsun hannunta,     Hanky ya zaro daga cikin trouser pocket ɗinsa,Ya miƙa mata tare da cewa"Take it,"hannu tasa ta kar6a,ta shiga goge fuskarta sosai,    "In kawo maka ruwa kasha"?cikin sanyin murya ta ambaci hakan,    Girgiza mata kai yayi alamar a'a,kafin ya wuce cikin falon,Ya zura hannayenshi biyu acikin aljihun wandonshi,   juyowa tayi tana kallonshi,A dai dai lokacin suka jiyo sallamar Abusufyan"Assalamu Alaikum",    Amsa mashi su kayi da"Wa'alaikum salaam,"   Shigowa cikin falon yayi,hannunshi ruƙe da key ɗin Motarshi,   Koda yayi arba da Sgr,cike da mamaki yace"Rafayet!Ashe dagaske ne,Abban ku ya sanar dani cewa,zai yi wa Omar magana ko shi ko kai wani yabiyo bayanmu don yaso yana nan muzo dashi,Banyi tsammanin cewa kaine zaka zo ba,Yanzu kawai ina karyo kwana da motata naga sojoji zagaye da gidan nayi ta mamaki cikin raina,Gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba," ya karasa maganar a yayin da yake ƙoƙarin rungumarshi,da alama Abusufyan ba ƙaramin daɗi yaji ba,Sai murmushi yake yi,    "Na same ku lafiya,"? "Lafiya lou Alhmdllh,Naje masallaci ne,na biya naga wani Abokina daga can kuma na wuce wani store zanyi mana siyayyar kayan abinci,Inata fargabar nabar yarinya ita kaɗai acikin gida",   Sgr yace"nayi mamakin ganinta ita kaɗai zaune acikin gidan,time ɗin dana shigo kuma bansan meya faru ba,duhu ko'ina,so sai daga bayane hasken ya dawo,"   Abusufyan yace"Ae ɗaukewa su kayi da wutar ne,yanzu nima ina kan hanyar dawowa naga sun dawo da ita,"   wurga idonshi yayi kan Sehrish dake tsaye hannunta ruƙe da hanky dinsa,ta kammala goge hawayen,   "Daughter,zonan mana,"ya kirata da hannunshi,wurinsu tazo ta tsaya tana facing din Abusufyan,    "Faɗamun meya faru?bayan na tafi"? murmushi ta ɗan yi,batare da tace komai ba,    Mayar da idanuwanshi yayi kan Sgr yace"Amma dai ba nan zaka kwana ba ko"?    "I will spend the night here," Abusufyan yace"ba ka ga yadda gidan yake ba ne?Ni nasan bazaka iya bacci acikinsa ba,Yakamata ka wuce hotel kawai,ina ganin zaifi maka daɗin zama,"   Girgiza mashi kai yayi"No,i wanna stay here," gyaɗa kai abusufyan yayi tare da kallon sehrish yace   "Sehrish ki kaishi bedroom ɗin da kika gyara,ya zauna acan,Amma dai banso ba wlh,Don nasan cewa zaka takura sosai,Ga zafi ga sauro duk da na siyo maganin sauron,Amma bana tunanin zai iya dakatar da saurayen dake acikin gidan nan,"   Amsa mashi tayi da toh,Sannan ta juya tare da kallon Sgr tace"Mu shiga ciki,"   Gaba tayi yabi bayanta,daƙyar yake iya taka kasan palourn,saboda daudar dake a wurin duk da sun gyara shi,   Shiga cikin bedroom ɗin su kayi atare,Wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙarewa ɗakin kallo,   "Kana bukatar wani abu,in kawo maka,"    "No need"ya ambaci hakan a yayin da yake zaro wayarshi daga cikin aljihun wandonshi, "Sehrish!"Abusufyan ne ya kwala mata kira,da sauri ta juya ta fita daga ɗakin,   Komawa tayi cikin palourn A tsaye ta same shi,Ga kayan da yayi masu siyayya hada gass cylinder saboda yin girki,Sojoji ne suka shigo dasu,A cikin buhu guda biyu,sae cylinder ɗin da suka ajiye nan,   Ƙarasawa tayi wurinshi,"Gani Daddy,"    "Kunyi magana dashi ya fada maki ko yana buƙatar wani abu?" "a'a bai bukaci komai ba," Shiru Abusufyan ya dan yi,ganin damuwa akan fuskarshi yasa tace"Meya faru daddy," hannu yasa ya ɗan shafa sumar kanshi kafin yace"Daughter,bazai iya kwana acikin gidan nan ba,Ni nasan waye rafayet,Wlh nayi mamakin ganinshi banyi tsammanin cewa shi zaizo ba,Kalli fa gidan nan ki gani,babu wani shiri da mukayi,yanzu da zarar an ɗauke da wutar nepa,Shikenan zafi zai rufe mu,kuma ko kaɗan baison zafi,Gashi da ƙyankyami toilet idan bana bedroom ɗinshi ba,baya shiga na kowa,Kuma dole ya buƙaci yin wanka,Ni bansan ya zamu ƙare dashi ba,"   Murmushi Sehrish tayi,ita kanta ta jinjina ma ƙarfin hali irin na Sgr,yadda yake da ƙyanƙyamin nan,Amma a haka yace zai kwana acikin gidan,Koya zasu ƙare,?   "Daddy,kada ka damu,tunda yaji ya gani,zai kwana anan ɗin ka ƙyaleshi kawai,"   Gyaɗa kai Abusufyan yayi tare da cewa"Shikenan kawai,Yanzu dai bari na shiga da kayan abincin nan kitchen,"   Yayi maganar tare da sa hannu ya dauki buhu ɗaya,hannu tasa itama ta kama ɗayan buhun,taja shi izuwa cikin kitchen,bayan sun kammala kwashe kayan sunkai kitchen,   Ta dube shi tare da cewa"Zan iya dafa mana ko taliya ce?   Abusufyan yace"Kina jin yunwa ne"?   "A'a,bana ji,saboda kai dama zan dafa,naga bamu ci Dinner ba,   "Ki barshi kawai,akwai kayan tea dana siyo da bread,idan kina jin yunwa ki haɗa ki sha,Yanzu dae bacci nake ji,"   Yayi maganar yana hamma, "A ina zamu kwana"tayi tambayar tana kallonshi, "Ki wuce inda mijinki yake mana,Ni zan kwana a palour ne,Ki dauko mun bargon da zan ɗan shimfiɗa in akwai"   "Toh" ta amsa mashi tare da   Kama hanya ta fuce daga cikin kitchen ɗin,Shima fitowa falon yayi ya tsaya a tsaye yana jiranta, Lokacin da ta shiga bedroom ɗin,A kwance ta samu Sgr yana bacci ya ƙure fankar ɗakin har ƙarshe,iska ta ko'ina,hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,wurin wardrobe ta wuce ta sanya hannu ta buɗeta,daga gida na kasa blanket din suke tare da bedsheet,hada mosquito net,    Bargo ta dauko mashi,Sannan ta koma falon,har lokacin Abusufyan na atsaye,yana jiranta,    Ƙoƙarin shimfiɗa mashi tayi,da sauri yasa hannu ya kar6i bargon tare da cewa"Yawwa My Own Daughter,nagode sosai," "Sae Allah yakaimu Daddy,"fuskarta asake tayi maganar,   "Allah ya kaimu lafiya,take care of my son,don't allow even one mosquito to bite his skin,If not ranki zai 6aci,"cike da zolaya yayi maganar,   Fashewa tayi da dariya,tare da juyawa tana faɗin"don't worry daddy,In sha Allah i will look after him,very well,"   Gyara kwanciyarshi yayi saman sofa ɗin,cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba dashi,   Komawa cikin bedroom ɗin tayi,bedsheet ta dauko acikin wadrobe ta shimfiɗa a kasa,sannan ta matsa wurin gadon,ta ɗauko pillow guda ɗaya ta ajiye shi saman zanin gadon,    Wurin switch taje,ta kashe light ɗin ɗakin,Nan take duhu ya gauraye ɗakin amma ba sosai ba,akwai hasken ƙwan dake a falo guda daya da aka bari akunne,ya ɗan haska ɗakin nasu,     Moving tayi izuwa wurin gadon inda Sgr ke kwance yana bacci,addu'o'i ta shiga karantowa tana ɗan tattofa mashi,bayan ta kammala ta koma saman shimfiɗar da tayi,ta gyara kwanciyarta,sai da itama ta karanta addu'o'in tabi ta shafe jikinta kafin ta rufe idanuwanta,bacci 6arawo yayi awon gaba da ita, Around 1:30 na dare,Ƴan nepa suka yi tsiyar tasu da suka saba,Tashin hankali,Ƴan sakanni da ɗauke wutar fanka ta tsaya cak,Wani irin zafi ya fara ziyarta ɗakin,Sai ga mutanen da gudun gaske sun fara kwararowa cikin ɗakin,Buuuuuuuuuu da wani irin kuka mai sautin gaske,tun yana juyi saman gadon yana kai hannu yana buge sauron dake ƙokarin attacking ɗinshi,har ya fara ƙokarin farkawa,Wata irin zuface ta soma tsastsafo mashi ajikinshi,Sharkaf ya jiƙe,tuni numfashinshi ya soma kokawar fitowa daga hancinshi,kamar an toshe shi,A firgice Sgr ya farka yana faman zazzare blue eyes ɗinshi,Hankalinshi yayi mugun tashi,arayuwarshi ya tsani sauro ko miskala zarratin baisan halittar nan,bai taso a inda ke akwai taba,Amma yasanta sarai a matsayinshi na Dr yasan irin cututtukan da take haifarwa,Gashi ya tsani duk wani abu da zai naƙasa lafiyar jikinshi,tuni jikinshi ya soma kerma,hannu yasa ya ɗebe rigarshi gaba daya,ya shiga kokawar korarsu daga kusa dashi bayan ya kunna fitilar wayarshi dakin yayi haske,ji kake fass fass!kaff kaff!!haka ya dinga bubbugesu,duk yabi ya ruɗe, Cikin bacci Sehrish ta dinga jin muryarshi yana faɗa da sauraye yana fadin"Don't come close to me!Am gonna shoot you"tashin hankali Sgr fa ya zauce da alama,duk sun rikitashi sun mayar dashi ƙaramin mahaukaci,Idan ya sanya riga bala'e biyu,ga zafi ga sauro,idan ya cire rigar kuma Sauraye zasu sha jini,bai da choice,   A firgice ta farka,hankalinta a matukar tashe ta mike daga kwancen da take saman bedsheet ɗin,Wurin shi ta ƙarasa,yanayin da ta ganshi gaba ɗaya ya rikice ba ƙaramin tausayi ya bata ba,gaba daya yabi ya susuce ya hargitsa sumar kanshi,    "Ya Rafayet,"ta ambaci sunan shi da wata irin kasalalliyar murya ta mai bacci,ƙoƙarin hawa saman gadon tayi don ta taimaka mashi ta kore mashi su,kafin su san abunyi,ae tana hawa saman gadon,ya ƙanƙameta ya rungumeta sosai,A faɗace yake ce mata ta kori saurayen su fita su bar ɗakin,ko ya harbesu da bindiga,tuni taji hawaye sun cicciko mata acikin idanuwanta,tsananin tausayinshi ne ya kamata,dama sai da Uncle yace bazai iya kwana a cikin gidan ba,Amma yace zai iya,wani iko na Allah,babu halittar da Sgr ke jin shakkarta irin sauro,Gashi Yau Allah ya haɗasu,ƙananun ƙwari sun firgita babban kwaro,Shaggu sun ga Farar fata,burinsu kawai su tsotsi jininshi,Dama abu tubarkalla masha Allah,   gaba daya hannayenta na asaman bayanshi,ya cusa kanshi a kirjinta,numfashin shi da wani irin huci yake fita,    Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Ya rafayet,dan Allah ka natsu,zanje wurin daddy na kar6o mana maganin sauron,"tayi maganar tana ƙoƙarin janye jikinta daga nashi,ƙin barinta yayi,yaƙi yarda ta motsa daga jikinshi,gani yake kamar in tabar wurin Saurayen zasu shanye mashi jinin jikinshi ne,   Ganin yaƙi sakinta yasa takai hannu ta ɗauki rigarshi da yayi wurgi da ita gefe saman bedmattress ɗin,Ruƙo rigar tayi a hannunta,ta shiga kore mashi saurayen dake akewaye dasu, Duk wannan budurin da akeyi,Abusufyan na kwance saman doguwar kujerar,Shi kanshi zafi ya ishe shi ga saurayen a kewaye dashi,Amma hakan baisa ya farka ba,sae faman juyi yake yi,    (Allah sarki,haka talaka ke fama,da zarar an ɗauke da wutar nepa lokacin zafi,Ya rasa inda zaisa kanshi,ga sauro ga zafi,yayin da masu kuɗi ke can suna shan sanyin A.c,a lokacin zafi,idan kuma na sanyi ne su kunna room heater,Talaka kuma Ya hura garwashin wuta😥) Jikinshi sae kerma yake yi,Duk da ya ɗan ji sauƙin Zafin saboda fiffitar da take yi mashi tana kore mashi saurayen,ko gajiya bata yi baiwar Allah,Haka ta hana idonta bacci,ta zauna tana kula dashi,sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi,har lokacin yana manne da ita,    A hankali bacci yayi awon gaba dashi,kamar wani jinjiri,gyangyaɗi ta fara yi,tana fiffitar bacci na fisgarta,idanuwan nan sunyi jawur dasu,taƙi bari bacci ya ɗauketa,saboda gudun halin da Sgr zai shiga,idan ta daina yi mashi fifitar,    Tafin hannunta ta sanya asaman fine face dinsa,ta shafa gefen fuskarshi har izuwa saman pink lips ɗinshi,kafin ta mayar da hannun saman dogon wuyanshi,fatar wurin tayi haske sosai mai matukar jan hankali,la66anta takai asaman cheek ɗinsa ta manna mashi kiss,ɗagowa tayi tare da aza tsinin hancinta cikin sumar kanshi,daddaɗan ƙamshin dake fitowa daga wurin ta dinga shaƙa,tana faman lumshe idanuwanta,da hannu ɗaya take yi mashi fiffitar,   Tana cikin wannan yanayin,ta galabaita sosai saboda baccin da take ji,Ƴan nepa suka dawo da wutar,a hankali fankar ta soma jujjuyawa,nan take iska ta karaɗe ko'ina na bedroom ɗin,wani irin farin ciki ne ya ratsa zuciyarta,    "Allah na gode maka,da suka dawo da wutar nan,nayi farin ciki sosai,"    Lokaci guda Mosquitoes ɗin nan kowa ya kama gabanshi,saboda wutar mai ƙarfi ce,iska duk ta kaɗa shaggun,   A hankali ta lalla6a ta janye Sgr daga jikinta,ya koma saman mattress ɗin,ta dauki wayanshi ta kashe fitilar ta daura ta saman bedside drawer,gefenshi ta kwanta,tare da jan bargo ta lullu6e jikinta,banda nashi saboda ta lura dashi baisan Zafi ko misƙala zarratin, *Boss Bature* Wuraren Sallar asuba,Abusufyan ya farka,Saukkowa yayi daga saman Sofa ɗin,yana faman murza wuyanshi,Wurin yayi mashi zafi saboda kujerar tayi mashi karanta,ya takure kansa sosai,Ƙopar ɗakinsu yaje tare da sanya hannu yana ɗan kwankwasa ƙopar,    Sehrish ce ta farka,saukowa tayi daga saman gadon,sai da ta fara kunna hasken ɗakin,sannan taje ta buɗe ɗakin,   "Daddy,"ta ambaci sunanshi, "Na'am,Daughter," "Wlh jiya munji jiki daddy,dama haka Yaya Rafayet ke da jin Zafi? Ga sauraye suka takura masa,jiya daga ni harshi bamu samu isasshen bacci ba,"muryarta tamkar zata yi kuka tayi maganar, "Ae dama saida nace mashi,Yaje hotel amma yaƙiya,banji daɗi ba gaskiya,duk ban shirya ma zama gidan ba,dana sani tun kafin muzo,nasa an gyara shi,An sanya generator da A.C an kuma yi mashi feshin maganin sauro,Amma ban yi tunanin hakan ba,Wllh koni jiya naji jiki,"   Ya ƙarasa maganar tare da cewa"Yanzu ya yake?Yana lafiya kuwa,"?yayi tambayar yana jiran amsarta,   "Ya samu bacci,da suka dawo da wutar,bansani ba ko yana lafiya ko kuwa,Still dai bacci yake yi bai farka ba,"   Jinjina kai Abusufyan yayi tare da cewa"je ki taso munshi,Yazo mu tafi masallaci,Lokacin salla yayi,"   "Toh daddy"tayi maganar tare da juyawa ta shige cikin ɗakin, Yadda tabarshi haka ta same shi,kwance yana bacci,   Zama tayi daga gefen gadon,sannan ta ambaci sunanshi"Ya Rafayet"!shiru bai motsa ba,sake kiran nashi tayi"Babban yaya ka tashi,time ɗin sallah yayi,"_   Ganin yaƙi motsawa yasa takai hannunta saman damtsen hannunshi,ta ɗan bubbugashi,dogon numfashi yaja a hankali ya soma ƙoƙarin buɗe idanuwanshi,   Biji biji ya fara ganinta,kafin idanuwan nashi suka washe,   "Ankira sallah,Daddy yana jiranka a palour,"   daƙyar ya iya furta mata Okey,miƙewa yayi daga zaune,yakai hannu ya ɗauki shirt ɗinshi,Ya zurata ajikinshi,Hada ido su kayi da ita,da sauri ta kawar da idonta gefe guda,miƙewa tayi daga tsaye,ta bashi wuri don ya wuce,   Saukowa yayi daga saman gadon,Ya kama hanyar fita daga ɗakin,   "Adawo lafiya," "Okey,"yasa kai ya fuce, Bayan fitarshi,toilet ta shiga,ta ɗauro alwala,bayan ta fito ta ɗauko darduma ta shimfiɗa,a natse ta kabbara Sallah,tana gama yin sallar ta ɗebe hijabin ta ninke dardumar ta turasu cikin wadrobe,   Wani irin bacci take ji acikin idanuwanta,saboda jiya bata samu isasshen bacci ba,Cire doguwar rigar jikinta tayi tare da sagala ta saman Murfin wardrobe ɗin,   Toilet ta wuce,Saboda jikinta duk babu daɗi,After some minutes ta fito jikinta sanye da Brazier,tare da Short,farare,ba ƙaramin kyau su kayi mata ba,dama dasu ta shiga wankan,    Tunda ta fito kuma,baccin ya ya ci gaba da addabarta don ba karamin dadin jikinta taji ba,bata samu ta sanya kaya ajikinta ba,Saman gadon ta haye taja bargo cikin ƙankanin lokaci bacci yayi awon gaba da ita,bata ƙara sanin inda hayyacinta yake ba, *Marshal Omar* Yayi nisa a cikin baccin shi,yajiyo muryar Hosana tana raira mashi waƙa,     _Wataran wata rana_    _za'a kaika gidana_     _matsayin mijina_     _kaine madara na_ _na matsu!na matsu na matsu inga wannan rana_ Cike da jan faɗa take yin wakar hada matsawa saitin kunnanshi,Rai a matuƙar 6ace ya farka,tare da wurga mata uwar harara,tana zaune saman gadon tayi zaman cin tuwo,   A faɗace yace"Hosana!bana hanaki shigomin bedroom ɗina ba?Meyasa baki jin maganata ne"   Hura mashi hanci tayi tare da murguɗa baki tace"Haramun ne idan nashigo ɗakin ɗan uwana,?to idan ma haramun ne,Sai ka aure ni kowa ma ya huta," Hannu yasa tare da dafe kanshi,yana faɗin"Allahumma ajirni fi masibati,wa'aklif ni khairan minha,"   A ƙule tace"Ya Omar,Ni ce masifar"?   Banza yayi da ita bai tanka mata ba,   Jin yayi shiru yana kallonta,yasa tace"haushina kake ji ko?to ka kashe ni mana kowa ya huta,"   Yunƙurawa yayi tare da miƙewa daga zaune,yace"Meyasa kike mun haka ne?kin takurawa rayuwata Hosana,A haka kikeso na"?   Turo baki tayi tana ɗan satar kallonshi,   "Baki son farin cikina,kullum burinki ki addabi rayuwata kib hanani sakat,Zunubin me na akaita maki ne,"    Ashagwa6e tace"Bakomai,"   "Kinfi so ki ga hawaye na ko," Girgiza mashi kai tayi alamar,A'a, Hannu yasa ya rufe fuskarshi yana raira mata kukan ƙarya,   Nan fa hankalinta ya tashi,tabi ta ruɗe,   "Ya Omar bazan ƙara zuwa ba,dan Allah kadaina kukan,yanzu zan tafi na barka,"jiki na rawa ta sauka daga saman gadon tana ja da baya baya tana faɗin"ka gani ko?tafiya zanyi,bazan ƙara dawowa ba,dan Allah ka daina kukan toh,"   Ƙasa ƙasa ya dinga dariya batare da taji shi ba,har sai da ta fuce daga ɗakin sannan ya zame hannunshi aranshi yace"fitinanna,Allah yasa Daddy ya dawo cikin week ɗinnan zansa a ɗaura mana aure,At first night,zan koya maki hankali,duk wani hauka da kike ji asaman kanki saina sauke maki shi,"   Yana maganar yana dariya,a yayin da yake saukowa daga saman gadon,jallabiya ce ajikinshi,toilet ya wuce, Wuraren karfe 8,Sehrish ta farka da wata irin matsananciyar Yunwa,a gaggauce ta miƙe,ta ɗauko jallabiya ta zura a jikinta,kitchen ta wuce,batare da 6ata lokaci ba,ta ɗaura girki,bazata iya jure dafa abu mai wuyar dafuwa ba,Shiyasa ta ɗaura Indomie shaf shaf ta kammala dafuwarta,A cikin plate ta kwasota ta fito daga cikin kitchen ɗin,ta zauna a palour tana ci,sai lokacin ta shiga tunanin ko'ina su Uncle suka tafi?daga fita sallar Asuba har yanzu basu dawo gidan ba,yanke shawarar kiransu tayi idan ta kammala cin taliyar,asaman table tabar plate din da sauran taliyar,ta koma kitchen ta haɗo kakkauran Tea wanda yaji madara da bournvita,dawowa tayi falon ta zauna tana kur6arshi a hankali, Tana cikin shan tea ɗin nan,taji dirar motarsu acikin gidan,Uncle Abusufyan ne ya fara shigowa cikin gidan,Miƙewa tayi da sauri tana fadin"Daddy,sannu da dawowa,"   A gaggauce ya amsa mata"Yawwa Daughter,ɗaukko mayafinki mu tafi,dattijon nan ya kira ni a waya,badajimawa ba,"   Jin haka yasa ta ajiye cup din hannunta asaman table ɗin gabanta,Jiki na rawa ta wuce ɗakin,jimm kaɗan ta dawo sanye da mayafi tayi rolling ɗinshi,hannunta ruƙe da wayarta,   Shigowa cikin palourn tayi batare da 6ata lokaci ba,Abusufyan ya ruƙo hannunta suka fito waje wurin motarshi,Security ta gani suna tsaron gidan,tana ganinsu ta gane cewa mutanen babban yaya ne,    buɗe motar tayi ta shiga,Abusufyan ya shiga ya zauna a mazaunin driver,tashin motar yayi tare da yin reverse ya karya kwana,da gudun gaske ya fuce daga cikin gidan,Kai tsaye suka haura saman titi,hannunshi har kerma yake yi saboda saurin da yake yi,burinshi kawai su ƙarasa cikin unguwar,    "Daddy,ina yaya Rafayet ɗin?naga banganshi ba,"   "Nabarshi a hotel,tun bayan da muka kammala sallar Asuba,Ni kuma na wuce gidan wani Old friend ɗina dake anan,Na jima acan,ina kan hanyar dawowa Dattijon ya kira wayata,Yake sanar dani cewa Malam Nura ya dawo"ya ƙarasa maganar adai dai lokacin da yake ƙoƙarin juya sitiyarin motar,Cikin unguwar suka shiga,a bakin bishiyar bedi yayi parking ɗin Motar cikin layin,tun kafin su fito daga cikin Motar suka hango ƙopar gidan a buɗe,bayan sun fito daga cikin Motar,Abusufyan ya daga hannunshi sama tare da cewa"Ya Allah kasa muji alkhairi!"   Sehrish ta amsa mashi"Ameeen Daddy,"   A ƙopar gidan suka tsaya,Abusufyan ya kwaɗa sallama,cikin sa'a suka ji an amsa masu sallamar tasu,Jimm kaɗan sai ga wani matashin saurayi dogo siriri ya fito daga cikin gidan,jikinshi na sanye da yadi,   Miƙa ma Abusufyan hannu yayi suka gaisa,kafin yace"baƙi mukayi ne,"Abusufyan yace"Eh,baƙine,muna neman Malam nura ne,Allah yasa yana nan,"   Tunda saurayin ya fito idonshi na akan sehrish,kallon sani yake yi ma fuskarta,ita kanta kallon nashi takeyi,kamar taso ta gane shi,da alama tasan shi tun yana da ƙuruciyarshi,Ranta ne ya bata cewar kodai Sadeeq ne ɗansu ya girma haka"!?   "Da ace kun ƙara minti Biyar baku zo ba,da kun rasa shi,don kuwa yanzu yake shirin komawa Islamiyya,"   Wani irin farin cikine ya lullu6e Abusufyan"taimaka kayi mana sallama dashi,".   "Toh,"ya amsa tare da juyawa ya shige cikin gidan,after some minutes ya dawo hannunshi ɗauke da tabarma,A cikin zauren gidan ya shimfiɗa masu ita,    "Ku shigo daga ciki ku zauna,yanzun nan zai fito,"   "Yawwa mun gode ƙwarai,"Abusufyan ne yayi maganar tare da ruƙo hannun Sehrish suka shiga zauren,A saman tabarmar suka zauna,Suna jiran tsammanin ganinshi,   Wayar Abusufyan dake acikin aljihunshi ce ta soma ringing,da sauri ya zaro wayar,yana duba mai kiran nashi Sunan My first in~law ne,Amsa kiran yayi tare da kara wayar a kunanshi,   "Uncle,A ina zan same ku"?Rafayet ne yayi maganar,    Abusufyan yace"muna a hotoro,Amma kaɗan jira kaɗan zan tura maka da address ɗin gidan,Sai kazo,"   Sgr yace"okey,I will be waiting," Rejecting call ɗin yayi,yana ƙoƙarin mayar da wayar cikin aljihunshi,Wani babban mutun ya shigo cikin zauren,bakinshi dauke da sallama"Assalamu Alaikum,"atare suka amsa mashi sallamar,yayin da suka bi shi da kallo,   Daga ganin mutumin ya kwana biyu a duniya,ya manyanta sosai ya fara tsufa,Jikinshi na sanye da shiga ta musulunci,ta waɗanda suka amsa sunansu malamai,hannunshi na ruƙe da cazbaha,kanshi kuwa rawanine,A mutuncen shi yazo,   Kamar yadda suke kallonshi shima haka yake kallonsu,yanayin kallon dayake yi masu kamar kallon sani ne,wuri ya samu agefen tabarmar ya zauna suna fuskantar juna,Shi dasu,   Da sauri Abusufyan ya shiga gaisar dashi"ina kwana baba,mun same ku lafiya,"   Fuskarshi asake ya amsashi lafiya lou,Alhamdulillah"   Gaba daya hankalinshi na akan fuskar Sehrish,kallon ƙurulla ya shiga yi mata,nasan gano a ina yasan fuskar yarinyar,Sunnar da kanta ƙasa tayi tana wasa da yatsun hannunta,    ɗauke idanuwanshi yayi daga kan sehrish ya mayar dasu kan Abusufyan yace"Ince dai lafiya ko?naji kunyi shiru baku gabatarmun da kanku ba,Gashi ni bansan ku ba,"   Murmushi Abusufyan ya ɗan yi tare da gyara zamanshi,Atsanake ya soma kora mashi jawabi,   "Ni sunana Abusufyan,Wannan kuma ƴa tace,Sunanta Sehrish,'   Gabanshi ne ya faɗi rass,aɗan tuɗe ya maimaita sunan"Sehrish"kamar irin ya ta6a jin sunan,   Cigaba da magana Abusufyan yayi"nasan baka gane ta ba,saboda sanin da kayi mata tun na ƙuruciya ne,Amma nasan ba zaka iya mantawa ba,Da ZAINABU ABU BUZUWA MATAR MAKWABCINKA YA SAYYADI,"   Saboda tsabar kiɗima Malam Nura ya zabura tare da miƙewa tsaye yana kallonsu hankalinshi aɗan tashe yace"dan Allah kuyi mun bayanin su wanene ku?menene alaƙarku da zainabu abu da kuma sayyadi"?   Miƙewa Abusufyan yayi yana ƙoƙarin kwantar mashi da hankali yace"pls baba,dan Allah ka koma ka zauna muyi magana atsanake,"   Rai a6ace malam Nura yace"Idan maganar wannan fasiƙin mutumince ta kawoku to ku tattara kubarmin gidana!Banason ganinku,banason ganin duk wani abu daya shafe shi,ku fuce kawai tun kafin ranku ya 6aci a wurin nan "yana magana jikinshi na kerma saboda tsabar 6acin rai,   Ganin yana ƙokarin korarsu yasa sehrish miƙewa tsaye cikin sanyin murya tace"Baban sadeeq,Ka manta da ƴan ukun zainabu abu da ta haifa"?   Mayar da hankalinshi yayi sosai akanta yana kallonta,   "Ni ɗaya ce daga cikinsu,nasan baka manta damu ba,Nice Sehrish ƴar uwarsu Jahad da Hosana"    Cike da mamaki Malam nura ke kallonta,hannunshi na kerma ya nunata da ɗan yatsanshi daƙyar ya iya furta cewa"kek..ke..ƴar wurin zainabu abuce?   Jinjina mashi kai tayi alamar eh,tace"Ni ce SEHRISH Baban sadeeq,su jahad ma suna nan araye,"   Wasu irin zafafan hawaye ne suka soma sauka akan fuskar malam nura,ruƙo hannunta yayi yana kallonta,la66ansa sae kerma sukeyi,yayi matuƙar mamaki ganin yarinyar,bai ta6a tsammanin cewa yaran zasu rayu ba,abun yayi matukar daure mashi kai,   Cikin shessheƙar kuka yace"Allahu akhbar!Wai dagaske ƴa'ƴan abu suna araye a doron duniyar nan?Dagaske ne abunda idona suke gane mun kuma suke jiyomun!Ya Allah kasa ba mafarki nake yi ba,"kuka sosai ya fashe dashi,duk yabi ya ruɗe bawan Allah,   Kama hanyar shiga cikin gidan yayi,yana kwaɗama maman sadeeq kira"Murja!!murjanatu!kina inane kizo dan Allah,Ki ganemun wannan abun al'ajabin,Yau gani ga jinin zainabu abu har cikin gidana,Abun da muka daɗe muna jira,yau Allah ya amsa addu'armu"   Jin wannan maganar ta Baban sadeeq yasa Maman sadeeq ta miƙe zumbur daga zaunen da take saman sallaya,buguzun buguzun ta faɗo cikin zauren,turus ta tsaya abakin zauren tana ƙarewa Abusufyan da Sehrish Kallo,   Malam nura yace"kin gani ko?Yaran nan sun rayu,Wahala batasa sun mutu ba,dama nasha faɗa maki cewa Allah yana tare dasu a duk inda suke,Allah shi zai kula da abunshi,Yau dai maganata ta tabbata,kalli ki gani wannan yarinyar ƴar wurin zainabu abu ce fa,Sehrish ce"yayi maganar yana nuna mata sehrish,   Hannu murja tasa ta daki ƙirjinta tare da Ambaton sunan Sehrish da ƙarfin gaske,   Da gudu sehrish ta ƙarasa wurinta suka rungume juna,tare da fashewa da wani irin matsanancin kuka,kamar ransu zai fita,   Tuni idanuwan Abusufyan sun cicciko da kwalla,shi kanshi baisan lokacin da hawaye suka wanke mashi fuskarshi ba,   Gaba dayansu sun shiga cikin wani irin yanayi na ban tausayi,kowa da abunda yake tunawa acikin ranshi,   Cikin shessheƙar kuka Maman Sadeeq ta dafa kafaɗun Sehrish tana faɗin"Ashe rai kanga rai!Rishi kece kika girma haka?lallai Allah Al musawwir ne,Kalli yadda rayuwa ta sauyaki,Ban manta lokacin da kuke rayuwa a wulakance ko takalma babu a kafafuwanki,Ya Allah na gode maka daka nuna mun wannan ranar,Yau gani ga ƴa'ƴan aminiyata zainabu abu,Wayyo Allah farin ciki,"zubewa ƙasa tayi ta fuskanci gabas tayi sujjada tana kuka tana godewa Allah,hakan ba ƙaramin ta6a masu zuciya yayi ba,   Sun ɗauki tsawon lokaci suna wannan koke koken,kafin daga bisani komai ya lafa,Saman tabarmar suka koma suka zauna,cike da jimami,kowa yayi shiru na ɗan wani lokaci, Kafin Abusufyan ya soma magana"Baba waɗannan ƴaran ƴa'ƴana ne,bana sayyadi ba,Ya yaudaremu ne gaba ɗayanmu ya auri abu da cikina,batare da saninmu ba,Wannan shine silar duk wani abu daya faru a rayuwarsu...."   Tunkan ya ƙarasa maganar Baban sadeeq yace"Dama najima ina zargin cewa,ƴan ukun nan bana shi bane ashe dagaske ne,Ya Allah kayi mana maganin Fasiƙin mutumin nan,Ka kawo mana ƙarshen shi,Mugu azzalumi ya jima yana cutar rayuwar yaran nan,In sha Allah ƙarshen shi bazaiyi kyau ba,"ranshi a 6ace yake yin maganar,   "Sehrish ina Hosana take baiwar Allah"Maman sadeeq ce tayi maganar har lokacin hawaye ne ke shararowa akan fuskarta,   "Duk suna nan lafiyarsu ƙalou muna atare dasu cikin danginmu," Murmushi Maman sadeeq ta saki tare da cewa"Allah sarki,rayuwa kenan,"   "Baba ko kuna da labarin Abu"?Abusufyan ya jefo masu tambayar, Gabansu ne ya faɗi atare suka kalli juna jin tambayar da Abusufyan yayi masu,   Hakan ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba,tun daga kan irin kallon da yaga sunyi ma juna yasa shi shan jinin jikinshi,.    Hankalin Sehrish a matuƙar tashe tace"Dan allah,ku faɗamana a ina Oummanmu take?nasan kuna da masaniya akai,"   Shiru sukayi batare da sun basu amsa ba,nan take Sehrish ta fashe da kuka tana cewa"dama nasani,zai yi wuya mu sameta araye,innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,"   Ƙiriss ya rage zuciyar Abusufyan ta buga,zumbur ya miƙe yana ƙoƙarin barin wurin,hannunshi dafe da saitin zuciyarshi,     Muryar Baban sadeeq ce ta katse mashi hanzarinshi,    "ABU TANA RAYE," jin wannan maganar yasa,Abusufyan komawa dirshan ya zauna,muryarshi har shaƙewa take yi wurin cewa"dagaske abuna tana araye?dan Allah ku faɗamin gaskiya,abu tana raye?tana ina?a ina zan ganta?"   A natse baban sadeeq ya soma kora masu jawabi,   "Tun bayan lokacin da Hosana tayi jinya a asibiti sakamakon Buguwar da kanta yayi harta samu ta6in hankali,nasan kunji labarin nan a wurinsu Sehrish,"ya ɗan dakata dayin maganar yana kallon fuskokinsu,   "Hakane,munji komai a wurinsu,"a ƙagare Abusufyan yayi maganar,jikinshi sae tsuma yake yi,ita kanta sehrish ta ƙosa taji abunda zaice,    "Tun bayan da aka kwantar da Hosana gadon asibiti,lokacin ana ƙoƙarin tattara kuɗin da za'ayi mata aiki,kwatsamm aka nemi mahaifiyarsu aka rasa ƙasa ko sama,tun bayan da ta sanar masu cewa zata je gida ta sanar da sayyadi halin da yarinyar take ciki don tunda aka kwantar da ita bai leko asibitin ba da tunanin ko asamu wani abu daga wurinshi,Don acika ayima yarinyar aiki,tunda ta haura ƙafa tabar asibitin bamu ƙara jin ɗuriyarta ba,"   Shiru ya ɗan yi yana sauke ajiyar zuciya kafin ya daura da cewa"A lokacin Hankalin mu ba ƙaramin tashi yayi ba,ga yarinya ba lafiya kwance gadon asibiti rai hannun Allah,Ga sauran ƴan uwanta dake a cikin ƙuncin rayuwa na rashin ganin mahaifiyarsu da basu yi ba har tsawon kwanaki,wannan yasa muka bazama neman abu acikin unguwar nan,Saƙo da lungu ba'a sameta ba,Gashi gidansu a garkame da kwaɗo,har muka fara tunanin cewa kodai Abu ta gudu ne tabar yaranta,wata'ƙil damuwace tayi mata yawa,shiyasa ta ta tafi tabarsu,Jinyar hosana ta koma hannun Maman sadeeq itace taci gaba da kula dasu a asibiti,"   Dakatawa ya ɗan yi da jawabin,na wani lokaci kafin yaci gaba da cewa"Ana haka,wata rana na dawo daga masallaci,ina ƙoƙarin shiga gidana,sae ga wani yaro nan,Umari ɗan wurin makwabcinmu ne shima,Yana tsaron shagon mahaifinshi abakin hanya,shi ya tare ni yayi mun sallama,Na juya na amsa mashi sallamar,yace mun malam inason magana dakai,game da Matar mutumin nan makwabcinka,Ya sayyadi,koda naji ya ambaci hakan sai na mayar da hankali sosai akanshi nace mashi"ina sauraronka,Anan ne yake sanar dani cewa,Ya gamu da abu akan hanya tana hauka babu takalma a kafafunta babu mayafi a jikinta,tana kuka tana sambatu tana fadin cewa Ya kashe mun babana,Ya rabani da mijina!kuma zai kashe mun ƴa'ƴana,'lokacin da Umari ya sanar dani wannan maganar hankalina ba ƙaramun tashi yayi ba,tun kafin ma ya ƙarasa maganar,jiki na rawa na hau babur ɗina na koma asibiti,a gaggauce na tattara yaran nan,nasa aka kaisu katsina wurin kishiyar babata,bakomai yasa nayi hakan ba,sai don gudun kada kalaman Zainabu abu su tabbata da gaske,Saboda a nazarin da nayi,wannan sambatun da akace tana yi yana da alaƙa da haukanta,Tabbas ya sayyadi shine yayi silar mutuwar mahaifinta,shiyasa har abun ya tsaya mata aranta,kuma ya ta6a mata zuciya har ta samu ta6in hankali,wannan dalilin yasa na ɗauke yaran gaba ɗaya na mayar dasu can,saboda inajin tsoran Ya sayyadi ya halakar dasu," Ganin ya dakata da yin maganar yasa Abusufyan saurin cewa"Yanzu a wani hali abu take ciki?kun samu nasarar gano inda take," Miƙewa Maman sadeeq tayi tare da shigewa cikin gidan,Jim kaɗan ta dawo hannunta ɗauke da tray,ruwa ta ɗebo masu acikin Jug,sae ƴan kofuna guda uku,Ajiyewa tayi agabansu,tare da tsiyaya ruwan ta miƙa ma Baban Sadeeq,hannu yasa ya kar6a tare da kai kofin bakinshi yana sha, Ƙara zuba ruwan tayi a sauran kofunan ta dauka ta miƙa ma Abusufyan,girgiza mata kai yayi tare da cewa"Bazan iya shan komai ba,in har banji a wani hali abu take ciki ba,"sam babu kwanciyar hankali atattare dashi, Miƙa ma Sehrish ruwan tayi,"kar6i kisha ƴata,"hannun sehrish na kerma ta kar6i kofin takai ruwan abakinta tana sha, 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* 💫💥💫💥💫💥💫💥💫💥💫 *_ALBISHIRINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE , SHAHARARRAR KUMA KASAITACCIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WADDA KUKAFI SANI MAMAN YUSUF YAR SOKOTO TANA YI MAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE CIKIN FADIN NIGERIA DA NIGER KARKU MANTA MACE MAI KYARA KANTA BATA BORANCI_* 💃💃💃💃💃💃💃 07069711327 _Akwai zafafan kayan Mata masu kyau da arha cikin sauki da rahusa Kuma duk inda kike zamu aika maki kayanki cikin aminci da yardar Allah ba cuta ba cutarwa don a Dade anayi sai gaskiya uwargida da amarya ku garzayo Kar abaku labari_ Munada kalolin Kaya kamar haka💥💫💥💫💥💫👇🏻👇🏻 Maganin sanyi sahihi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata Maganin gyaran nono domin dawo da martaban nononki hadin gargajiya da bashida illah ajiki Maganin hips Mai tado da hips cikin kankanin lokaci Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko dai dai misali kiyi kyau kema ki shigo cikin jerin Mata masu aji Maganin rage kiba da tumbi Wanda zaisa ki sace ki koma Yar dai dai abin alfaharin kowane namiji, Akwai kalolin gumbuna masu kyau da saukar da ni'ima Maganin matsi masu ciko da gaba da matseki Kamar Yar budurwa uwa uba zasu Baki dandano Mai gamasar da maigida Kalolin garrika masu bawa mace niima da jimawa ajiki Kalolin tsumi Sha yanzu magani yanzu dasa Mai gida ihun Dadi Zumar mallaka Zumar goron Tula Zumar ridi Zumar Mai rubutu Hadin mallaka Turaren mallaka Shu'umar humra Turaren AL'AJABI Matan gaske Ak 49 Sirrin tafin k'afa Turaren fuska Hatsabibin turare Kwallin mallaka Zoben mallaka Jigidar maida tsohuwa yarinya Maltinar Mata Karya gado Yajin Mata (yajin Mai ciko da mace) Yajin maza (domin Karin k'arfi) Muna dahuwar Kaya kamar haka💫💥💫💥👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Dahuwar zabo (mallaka) Kazar Yar gata Yan shila Ciccibi Dambu Zuciya Yan ciki Kwai ukku Tsoka Tara Kifi Da sauransu Akwai sirrika sosai da muke hadawa ga wacce kishiya ta addabeta ko wadda take fama da butsarin namiji ko mafadacin namiji ko namiji Mai yawon dare ko Wanda yake bin Mata insha Allah duk zaku samesu Kuma da yardar Allah za'asamu biyan bukata Muna bada magani ga yarinyar da tsautsayi ya fad'a Mata ta rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji Kuma insha Allah zaadace da yardar Allah Abubuwan da yawa gsky Wanda in nace Zan lissafasu sai nakwashi tsawon lokaci maiso tabini PC don ganin kalolin kayan da muke dasu , Karku manta mace Mai gyara kanta Bata boranci taku ce maman yusuf Yar mutan sokoto 07069711327 . Don Allah wadda Bata shirya ba tabari sai ta shirya sannan tayimun magana🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼ngd 07069711327 *Boss Bature✍️* "Bayan komawarsu hannun kishiyar babata,Sai hankalin mu ya dawo kan tunanin a ina zamu ga uwar yaran nan,Nemanta muka bazama yi acikin unguwar nan ruwa A jallo,duk wasu gidajen masu unguwanni na kewayen mu mun cigita haka ma ofishin yan sanda,tsawon lokaci ana nemanta bamu same ta ba,Hankalinmu ya tashi,Saboda sanin cewa Yarinyar nan bata da kowa,Gashi tabar gida a wani yanayi na ta6in hankali,Ga ƴa'ƴanta dake buƙatarta,hakan yasa bamu yi kasa a gwiwa ba ni da baban umari muka kai cigiya awani gidan Redio amman shiru kake ji ba Abu babu dalilinta Allah kaɗai yasan ina ta nufa don kasan garin kano da faɗi,aƙarshe muka fara zullumin anya Abu na'a garin nan ma kuwa,hakan yasa muka hana idonmu bacci wurin rokon ubangijin sammai da kassai da ya bayyana mana ita cikin aminci ya kareta aduk inda take,tsawon lokaci muna ta rokon Allah ba tare da gajiyawa ba,Ana haka kwatsam wata rana muka samu labarin bayyanar Abu ta hanyar Sanarwa a gidajen radio dana talabijin cewa Ana neman danginta,tare da adireshin asibitin da aka kwantar da ita sakamakon motar wani bawan Allah da ta bugeta a saman titi tana gararanbarta shine ya kaita asibiti ya kuma bada ayi cigiyar danginta,koda sanarwar nan ta isar mana jiki na rawa,Ni da Maman sadeeq tare da yaron nan ɗan wurin makwabcinmu muka kwasa muka tafi asibitin,ba ƙaramin daɗi muka ji ba da muka samu abu zuciyoyinmu suka cika da farinciki,duk da babu hankali atattare da ita,A lokacin likitan dake kula da ita ya buƙaci akawo wani makusancinta,wata'ƙil adace ta dawo cikin hayyacinta idan tayi ido biyu da ƴa'ƴanta da take yawan ambaton sunansu,jin haka yasa na yanke shawarar zuwa katsina domin in taho da yaran nan,ko Allah zaisa adace abu ta dawo cikin hayyacinta,alokacin nayi kokarin kiran lambar tsohuwa don in sanar da ita game da zuwa na don a shirya ma yaran amman a kashe,hakan baisa nayi tunanin wani abu ba,don dama mafi yawancin lokutta wayar tata na kasancewa a rufe sai anyi sa'a ake samu,ahanzarce na shirya zuwa katsina,Sai dai kash!wani mummunan labari ya riskeni a lokacin da naje unguwar da suke,Na rasuwar ita mariƙiyarsu Kishiyar babata tsohuwa,Sannan kuma naji cewa an liƙa masu ƙazafin maita,wai sune suka kashe ta saboda an ga kumfa a bakinta kamar taci guba,Hankalina yayi mugun tashi saboda ina da tabbacin cewar yaran abu bazasu ta6a aikata hakan ba,Ni shaida ne akan yaran,nayi baƙin ciki sosai kamar zan haɗiyi zuciya in mutu lokacin da Makwabcinsu ya rakani police station ɗin da aka kulle yaran,ƴan sandan da muka samu a wannan lokacin sun tabbatar mana da cewa,a nan police station ɗin aka kawo case ɗinsu,sai dai daga baya sun bar hannunsu sakamakon ciwon ɗaya daga cikinsu daya tashi aka kaisu asibiti Anan ne wani babban Jami'en Soja ya kashe Case ɗin gaba ɗaya,Shine silar barinsu asibitin,kamar zanyi hauka alokacin,Saboda tsabar takaici,na nace akan dole ƴan sandan nan su haɗani da mutumin daya kar6i yaran,Amma suka sanar dani cewa su kansu basu san wanene ba,Saboda basu bane asalin waɗanda case ɗin ya mutu ahannunsu ba,waɗancan anyi masu canjin wurin aiki,A ƙarshe dana takura masu na dinga zarya a police station ɗin akan su faɗamun waye wannan jami'en sai su kayi mun barazanar idan na ƙara zuwa zasu ɗaure ni,Tun daga wannan lokacin,jiki a mace nadawo kano alokacin aka sallami Abu bayan likitan dake kula da ita ya bada shawarar amaida ita asibitin masu ta6in hankali amman muka dawo nan gidana da ita da tunanin yi mata addu'oi don alokacin ina ganin kaman harda sihiri atare da ita,haka na dukufa yi mata addu'oi ba dare ba rana amman sauki dai sai wurin Allah,yadda taga rana haka take ganin dare sam bata bacci,sai sambatun Babanta da ya'yanta,in takaice maku dai Abu buge buge ta fara tana kokarin guduwa,Babu yarda muka iya muna ji muna gani haka muka dauki Abu muka kaita Asibitin mahaukata......"daƙyar ya ƙarasa maganar saboda kukan daya zo mashi,yana kai ƙarshen maganar ya fashe da kuka,tuni hawaye sun wanke fuskokinsu gaba ɗaya,Musamman Sehrish sosai take kuka,   Muryar Abusufyan na kerma yace"Ya..yanzu...a wani psychiatric ne aka kaita,"   Maman sadeeq ce ta bashi amsa da cewa"Tana a Dawanau Psychiatric Hospital,ko watan daya gabata sai da muka je gano ta,baiwar Allah tana cikin halin ha'ula'e,gwanin ban tausayi,duk in muka je kai mata ziyara,haka zamu sameta tana ta kuka tana sambatun Ya kashe mata mahaifinta,Ƴa'ƴanta Suna ina,akawo mata ƴa'ƴanta,kada ya kashe mata su," Jin wannan maganar yasa Sehrish ta ƙara sautin kukan nata sosae,   "Inason ganinta yanzu,"Abusufyan ne yayi maganar tare da miƙewa jikinshi na rawa yace"dan Allah idan ba damuwa,Ku taimaka ku jagorance mu izuwa asibitin,"   Miƙewa suka yi gaba ɗayansu,Baban Sadeeq yace"nafi kowa farin cikin wannan ranar,duk da ina da uzuri a makaranta,Zan iya dakatar da komai,dan In raka ku muje a tare,"   Ɗaga hannu Abusufyan yayi sama yana godiya ga Allah,Ita kanta Sehrish tsantsar farin cikine ya rufe ta,   Atare suka fito daga cikin gidan,a ƙopar gidan suka tsaya,Abusufyan ya ɗauko wayarshi tare da dannawa Sgr kira,Bayan ya amsa kiran anan yake sanar dashi cewa Zasu wuce Dawanau Psychiatric Hospital,Sgr yace su haɗu acan," A back seat na motar Baban Sadeeq tare da Maman Sadeeq suka shiga suka zauna,Yayin da Abusufyan ya shiga mazaunin driver,Sehrish na a gefenshi,ganin yadda hannunshi ke ta kerma wurin ƙoƙarin tashin motar yasa tace"Daddy,Anya zaka iya driving ɗin nan"?   A ruɗe yace"Daughter,ki ganni kawai,ba zaki gane halin da nake ciki ba,Am so eager to see her,Kamar nayi fiffike," Murmushi ta ɗan yi,Ita kanta ji take da ace tana da fiffike da ta tashi sama don ta ƙarasa asibitin da wuri, da gudun gaske ya fisgi motar kamar zasu tashi sama,cikin ƙankanin lokaci suka ƙarasa asibitin, *DAWANAU PSYCHIATRIC HOSPITAL* A dai dai lokacin da Abusufyan yake ƙoƙarin shigar da motarsu cikin asibitin,Sai ga Motocin Sgr da jiniya mai sautin gaske,sun shararowa a jere,Jibga jibgan sojoji ne a saman motocin bana wasa ba,ko shugaban ƙasa albarka,tuni mutane suka dare aka bar masu hanyar su kaɗae, A daidai bakin gate din aka tsaida jiniyar,kafin motocin suka shiga cikin Asibitin, Motar Abusufyan ce ta fara shiga sannan nasu suka rufa masa baya,wasu daga cikin sojojin dake a motar ƙarshe ne suka diddiro suka ƙame a bakin gate din shiga sai faman mazurai suke yi kowannansu hannunshi na riƙe da ƙatuwar bindiga gwanin ban tsoro,parking ɗin motocin su kayi,buɗe motar Abusufyan yayi tare da fitowa daga ciki,ya zagaya ya buɗema Su Baban Sadeeq motar suka fito,Sannan itama Sehrish ta fito,tana ƙarewa asibitin kallo,tun kafin ma su shiga ciki,ta fara ayyana yadda zata samu mahaifiyarsu,duk da tana cikin damuwar halin da zasu same ta, Fitowa Armstrong yayi daga cikin Motarsu,ya zagaya tare da bude mashi,A hankali ya zuro ƙafarshi daga cikin motar,Kafin ya ƙarasa saukowa daga cikinta Masha Allah,Open shirt ce sanye a jikinshi white colour,rigar ta bayyana Ƙirar faffaɗan ƙirjin nan nashi,Cos bai sanya button ko ɗaya ba,a buɗe yabarta sai farar vest,Dogon wandon jikinshi black colour ne,Wankan black & white ya ɗauka,ƙafarshi na sanye cikin oxfords shoes,daga saman sumar kanshi kuma ya sanya facing cap black,Eyes ɗinshi na manne da Sunglasses,Wa'iyazubillah Ya haɗu iya haɗuwa,kamar a buga a jarida, Duk da yanayin da suke ciki hakan baisa sun ƙi kallon wankan nashi ba,Musamman Babban sadeeq da kuma Maman sadeeq,tare da sauran jama'ar dake zarya a cikin asibitin,Yayi matuƙar jan hankalinsu,Ita kanta Sehrish sai da ta girgiza da irin wankan da ya ɗauka, Kama hanyar shiga ciki su kayi,Baban sadeeq ne agaba shi da Maman sadeeq,Abusufyan da Sehrish na abayansu,yayin da Sgr tare da Armstrong suke a biye dasu,sai wasu daga cikin security,mutum biyu dake ruƙe da jibga jibgan bindigogi,suna take mashi baya,a bakin OPD suka ƙame,yayin da Sgr da Armstrong wanda ƙugunshi ke manne da bindigu pistol guda biyu suka shiga ciki,batare da sunsha wahala ba saboda su Maman Sadeeq sun san asibitin,suka nufi wurin da nurses suke,wato nurses station,Anan suka taras da Nurses ɗin dake Duty,koda nurses ɗin nan sukayi arba dasu,gaba ɗaya hankalinsu ya koma akan Sgr,kallon ƙurulla suka shiga binshi dashi, Gyaran murya Abusufyan yayi masu hankalinsu ya koma akanshi,A natse ya soma magana"Sannunku da aiki,"   Atare suka haɗa baki wurin amsa mashi"Yawwa yalla6ai,munayi maku barka da zuwa,"    gabatar masu da kanshi yayi tare dasu Sehrish kafin yace"akwai patient ɗinmu dake anan asibitin,munzo dubata ne,'   ɗaya daga cikinsu ce,ta kai hannu gaban drawer chest ɗin dake a jikin table ɗin gabansu,tana ƙoƙarin zaro roster ɗinsu,tace"Zan iya sanin sunan mara lafiyan naku," Abusufyan yace"Sunanta Zainab ibrahim buzuwa,"yayi maganar tare da kallon baban Sadeeq,don yaji idan ya faɗa dai dai,jinjina mashi kai yayi alamar eh,   A saman table ɗin gabansu ta ajiye patients roster ɗin,tana dudduba sunan marasa lafiyan,   "Last week,an canza ma wasu daga cikinsu wurin zama,bansan ko kuna da masaniya akan hakan ba,"acewar nurse ɗin   Kallon juna sukayi hankalinsu aɗan tashe fargabarsu kar ace,an ɗauke abu daga asibitin,   "Yawwa,itace Zainabu ibrahim buzu ko"? Har suna haɗa baki wurin cewa "eh,itace, Murmushi Nurse ɗin tayi tare da cewa"Zainab tana a female ward B,"kallon abokiyar aikinta dake a gefenta tayi tare da cewa"kiyi masu jagora izuwa ɗakin da Zainab buzuwa take,"Amsa mata tayi da toh,sannan ta fito tare da nufar wani corridor,gaba ɗaya suka bi bayanta,kowa da abunda yake saƙawa aranshi,jikin Sehrish dana Abusufyan sae kerma yake yi,duk sun sha jinin jikinsu, Tun kafin su ƙarasa ward ɗin,mahaukatan dake a killace suka fara kwala masu kira,   "Yalla6ai,yalla6ai,"Sehrish ba ƙaramin tsoro taji ba,gasu nan gwanin ban tausayi,sae faman zuru hannuwansu suke yi daga cikin bars ɗin,   "Baiwar Allah!"wata mahaukaciya ce ta kwala ma Sehrish kira,tana nuna ta da hannu,a firgice Sehrish ta juya tana kallonta,Washe mata haƙora tayi tana kashe mata ido ɗaya tace"ki ce wa mijinki ya dinga sanya Niƙabi a fuskarshi,in ba haka ba wlh za'ayi maki kwacenshi,Don mu nan da kike ganin mu ba cikakken hankali ne damu ba,"   Ba sehrish ba,hatta Sgr sai da ya ɗan murmusa,ba ƙaramin dariya ta basu ba,   Suna cikin tafiya wata mahaukaciyar kuma ta ƙara kwala masu kira tana fadin"Wayyo Allah,Farin namiji ko maye ne nidai inaso,Ya Allah ka bani fari dogo kyakkyawa,kalan yan kasan waje,In biya sadakin shi ayi mana aure,"tana magana miyau na zalala a bakinta,   A rude Sehrish tace"Nashiga uku,Wannan wani irin kyau ne da har mahaukata ma suke santinshi"?acikin zuciyarta tayi maganar,bata ƙarasa zancen zucin nata ba,tajiyo wata mahaukaciyar kuma tana tambayar wai nawa ne farashinshi,   "Yalla6ai..."hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,jin yadda suke ta kwaɗa mashi kira,duk da jikinta yayi sanyi,tsananin tausayin mahaukatan ne ya kamata,nan take ta shiga tunanin ko awani hali zasu samu oummansu,   Tana cikin wannan yanayin na damuwa taji hannun Sgr a cikin nata,ɗan juyawa tayi tare da kallonshi,adai dai lokacin shima idon nashi na akan fuskarta,kallon juna suka shiga yi,bakomai ne ya faɗo mata aranta ba,face irin haukan da yayi mata adaren jiya na sauraye,yayin da shima abunda yake tariyowa kenan acikin kanshi,yadda ta tsaya kore mashi saurayen nan,ta ba shi kyakkyawar kulawa har ya samu bacci,ba ƙaramin daɗin hakan yaji ba,   Gaba ɗaya sun shagala da kallon junansu,   Muryar wata mahauciyarce ta kuma katse su da cewa"Ranka shi daɗe,Amma dai sabon aure ne ko?Wlh kunyi kyau kun dace da juna sosai,Wlh har kun tunamin da mijina...."tana faɗin hakan ta fashe da kuka mai sauti,atare suka kai idanunsu wurinta suna kallonta,Cikin shessheƙar kuka tace"Yalla6ai dan Allah ka kula da matarka kuyi zaman lafiya,kada ka wulaƙantata,ka bata kyakkyawar kulawa,Musamman in tasamu ciki,"ta ƙarasa maganar tana matsar kwalla, Wata irin kunyace ta rufe sehrish, Maman sadeeq ce ta kalli mahaukaciyar tare da cewa"baiwar Allah,meya faru da mijin naki?baki bamu labari ba,".   Hannu tasa ta ɗan share hawayenta kafin tace"Naso shi sosai,Munyi aure har mun haifi ƴa'ƴa dashi,babban abun takaici,A wurin haihuwarshi mahaifiyarshi ta mutu da cikinshi,"tana kai ƙarshen zancen nata ta rushe da kuka,.    Gaba ɗaya suka fashe da dariya,hatta Abusufyan dake acikin damuwa sai da ya ɗan yi murmushi,Haka Sgr shi kanshi baisan ya saki wannan kyakkyawan murmushin nashi ba,Zuba mashi ido Sehrish tayi tana kallonshi,dimple har biyu suka lotsa asaman fuskarshi,abun yayi matuƙar tafiya da hankalinta,koda ya gane cewa shi take kallo,nan take ya ɗauke murmushin ya tamke fuskarshi,   A dai dai lokacin da suke ƙoƙarin karya corner su shiga wani ward ɗin,kwatsam suka ji hayaniya na tunkarosu,da sautin takalman mutane,hankalinsu a matuƙar tashe suka kai idanuwansu wurin don suga meke wakana,   Wata mahaukaciya ce,ta 6allo daga wurin da aka killaceta,da gudun gaske,blue uniform din jikinta duk sun yayyage sun fita hayyacinsu,ƙafafunta ba takalma,gashin kanta duk ya hargitse ya rufe fuskarta gaba ɗaya,a bayanta kuwa likitoci ne da wasu ma'aikata suka biyota suma a guje,suna ƙoƙarin dakatar da ita,   "Ki tsaya!ki dakata anan!dan Allah ataimaka ataro mana ita,mara lafiya ce ta kufce mana,"ɗaya daga cikin likitocin dake biye da ita ne yayi maganar,hannunshi na ruƙe da syringe,yayi annoucement ɗinne don asamu wanda zasu taimaka wurin damƙo masu ita,   Duk tabi ta firgita ta ruɗe,ko kallon gabanta batayi,da dukkan ƙarfinta take yin gudun gashi sumar kanta duk ta zubo ta rufe mata har idanuwanta,ita kanta batasan wurin da zata dosa ba,burinta kawai tabar hannun masu fararen kayan dake biye da ita,   Sai gara likitocin takeyi duk sun galabaita,gadan gadan ta tunkari wurin da su Sehrish suke,Naɗe hannun riga Abusufyan ya shiga yi,haka Sgr ma he's ready to help,ba'a maganar Armstrong da yayi shirin yi mata ɗaukan jariri, jira kawai suke ta ƙaraso wurinsu,su cafke ta,   Tunkan ta ƙarasa wurinsu,ƙafafuwanta suka harɗe gaba ɗaya ta tafi a karkace zata kife ƙasa,da sauri Abusufyan ya damƙota,ta faɗa ƙirjinshi ta tsorata sosai,ƙankame shi tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,jikinta sai kerma yake yi,   Ƙarasowa likitocin su kayi suna faman sauke ajiyar zuciya,   "Yalla6ai,mun gode sosai,ba ƙaramin taimako kayi mana ba,baiwar Allah nan,daga shiga yi mata Allura ta kubce mana,ta bamu wahala sosai,"ɗaya daga cikin likitocinne yayi maganar,    Ɗayan doctor ɗin dake a gefenshi yace"Allah ya taƙaita wahala,Da bamu son inda zata dosa ba," ..su uku ne likitocin sae Nurse ɗaya dake a biye dasu,   Hannu Abusufyan yasa yana ƙoƙarin 6an6arota daga jikinshi,ae kuwa a tsorace ta ƙara ƙankameshi tana faɗin"dan Allah kada ka bari su tafi dani,wlh ni ba mahaukaciya bace,da hankalina,ƴa'ƴana nake nema,dan Allah ku kaini wurin ƴa'ƴana kar a kashe mun su suma,koda sau ɗaya ne in sanyasu acikin idanuwana,"   Rasss! yaji gabanshi ya faɗi,Hatta Sehrish sai da gabanta ya faɗi,saboda jin muryar Mahaukaciyar da tayi maganar,"   Ƙarfi yasa ya ɗaɗɗago da kanta,daga saman ƙirjinshi,Hankalinshi a matuƙar tashe yake kallonta,ta runtse idanuwanta jikinta sae faman kerma yake yi,     Bazai ta6a mantawa da fuskar abunshi ba,haddar da yayiwa fuskarta bamai gogewa bace,Bazai ta6a mantawa da ita ba,duk irin canzawar da zatayi,   Muryarshi na kerma ya ambaci sunanta da ƙarfi"ABU"!gaba ɗaya hankalin Sauran ya dawo kansu,    da ƙarfi Sehrish ta Ambaci sunanta"OUMMA!!"a firgice mahaukaciyar ta juya tana kallon Sehrish da tayi magana,duk tabi ta ruɗe,hannu tasa ta dafe kanta wani irin jiri ta dinga gani acikin idanuwanta,Nan take jikinta ya soma kerma,sumewa tayi gaba ɗaya ta tafi zata faɗi ƙasa,da sauri Abusufyan ya dawo da ita jikinshi sosai ya ƙanƙameta,Lokaci guda hawaye suka shiga wanke mashi fuskarshi,Sehrish kuwa tuni ta fashe da matsanancin kuka,Na farin cikin ganin Oummansu,    Kowa fuskanshi ɗauke da farin cikin ganinta da su kayi batare da sunsha Wahala ba,likitocin da suka biyota,duk jikinsu yayi sanyi,musamman yanayin da suka ga mutumin ya shiga,tare da yarinyar dake a gefenshi,ta wani 6angaren kuma fargaba suka fara yi kada ace wa'adin zaman abu ya ƙare a asibitin,Saboda sun saba da ita,ko acikin mahaukatan dake a Gidan,   Gyaran murya Sgr yayi tare da cewa"We don't ave time to waste here,Uncle zamu wuce da ita gida ne,idan yaso Dr ɗin dake kula da ita,Sai ya bi mu can,"   Hankalin ɗaya daga cikin Dr ɗinnan ba ƙaramin tashi yayi ba,yanayin yadda ya furta"tafiya za kuyi da Zainab"?   Jinjina kai Abusufyan yayi tare da cewa"Zamanta acikin asibitin nan ya qare,"ya ƙarasa maganar har lokacin hawayen basu daina sauka akan fuskarshi ba,gashi ya ƙanƙameta ajikinshi,ko warin jikinta baiji,   A ruɗe Dr ɗin yace"Haba yalla6ai,mezai hana ku barta anan acigaba da duba ta,har Allah ya Bata lafi......."kasa ƙarasa maganar yayi ganin irin kallon da Sgr yake yi mashi,duk sai ya sha jinin jikinshi, Sai lokacin Baban sadeeq ya tsoma baki,   "Doctor,Wannan da kake gani Mijinta Ne!wannan kuma ƴarsu ce,yaran da take yawan ambato acikin bakinta,To wannan ɗaya ce daga cikinsu,Ƴan ukune gare ta,ƙaddara ce ta rabasu da ita,Yanzun kuma Allah ya haɗasu da ita,"   Yana kai ƙarshen maganar,likitocin suka haɗa baki wurin cewa"Allahu akhbar!Amma mun tayata Murna sosai,Allah yasa silar samun saukinta kenan" gaba ɗaya suka amsa da Amin,   Sun jima suna magana,a tsaye kafin daga bisani,Abusufyan ya ɗauketa asaman kafaɗarshi,Sai da suka fara shigar da ita medical room likita ya duba ta sosai,tare da yi mata allurorin da aka saba yi mata,aciki hada na bacci,Tsayawa suka yi acikin asibitin suna ciccike wasu mahimman bayanai da ake bukata a wurinsu,harda Malam nura su da suka kawo ta asibitin,kafin Aka mallaka masu ita, 😍 *Boss Bature*   *Hayaaam* Tun da Aunty babba tabarta a asibitin nan magashiyan rai hannun Allah,Sai yau ta dawo cikin Hayyacinta,duk ta bushe ta dishe ta ƙanjame,jikinta duk faci,kamar wadda tayi hatsarin Mota,Komai nata ya ƙare,tayi mamakin ganinta a asibiti kuma babu kowa atare da ita,daƙyar ta iya miƙewa zaune,jikinta sae kerma yake yi,lokaci ɗaya ta shiga tariyo abunda Haroon yayi mata,fashewa tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,duk taji ta tsani kanta kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu,cikin shessheƙar kuka take faɗin"Meyasa na farka ban mutu ba?me yayi mun saura acikin duniyar nan,Natsani kaina,Natsani komai ban sha'awar cigaba da zama acikinta!bazan ta6a yafe mashi ba,mugu azzalumi ya cutar da rayuwata,hannu tasa ta yaye farin yadin da aka rufeta da shi,riga ce ƴar dai dai guiwa aka sanya mata blue colour kamar uniform,yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin ƙoƙarin ɗage rigar don taga menene a wurin,don tana jin kanta kamar ba dai dai ba,   Slowly ta tattare rigar,ta dage ta,koda tayi arba da gabanta,A rikice ta mayar da rigar ta rufe tare da fashewa da wani kukan mai cin rai,   Tana cikin kukan nan,Dr ya shigo tare da Nurse abayanshi,    Lallashinta suka shiga yi har suka samu ta lafa,Sannan Dr ɗin ya soma magana a tsanake,   "Baiwar Allah,Ya jikin naki"?_ Cikin shessheƙar kuka tace"da sauƙi,dan Allah ku faɗamun wanene ya kawo ni asibitin nan,yaushe aka kawoni,"tana magana hawaye na wanko fuskarta,   "ƴar uwarki ce,ta kawoki asibitin nan,Tun last week,Sai dai tun ranar da ta kawoki,Ta gudu tabarki anan bamu ƙara jin ɗuriyarta ba,Mun nemeta sosai ba mu same ta ba,A ƙarshe sai muka samu wannan wasiƙar a gefen gadon ki,bamu karanta abunda ke ciki ba,"ya ƙarasa maganar tare da miƙa mata wasiƙar, Tunkan ta kar6a gabanta ya shiga faɗuwa rasss!rass!buɗe paper ɗin tayi ta soma karanta abunda ke cikinta,tun da ta fara karantawa tafin hannunta ɗaya ke rufe da bakinta,hawaye sai shararowa sukeyi daga cikin idanuwanta,ƙiris ya rage zuciyarta ta buga saboda tsabar takaici,Ba ta ta6a tsammanin cewa Aunty laila zata iya guduwa tabarta a asibitin ba,Taji ciwon kalmar nan da ta kirata,Wato karya wadda ba'a rabata da maza,ta yanke mata hukunci batare da tasan ainihin abunda ya faru da ita ba," Dunƙule takardar tayi ta cukuikuyeta a hannunta,sai faman matsar kwalla take yi,wasu nabin wasu, "Lokacin sallamar ki bai yi ba,Amma ya zama dole muyi discharge ɗinki saboda kuɗin gado da aka biya sun ƙare,Sannan akwai wasu bayanai masu mahimmanci game da lafiyarki,da muke so mu samu wani makusancinki mu sanar dashi,Gashi baki da kowa,Bayan wannan akwai alluran da kike buƙata da kuma magunguna domin bunƙasa lafiyar jikinki,Ko kina da wani wanda zai iya taimaka maki"?   Kuka sosai hayaam take yi,tunani ta shiga yi wa zata kira yanzu don ya taimake ta?Waye take dashi wanda zaiji tausayinta,A iya saninta bata da kowa,in ma akwai babu wanda zai agaza mata saboda sanin Mugun halinta,Shiyasa a koda yaushe akeso mutun ya kasance yana aikata abun kirki a rayuwarshi,ba ka son awani hali zaka tsinci kanka ba a nan gaba ba,duk wani abu da kake taƙama dashi,Walau kyau ko dukiya ko mulki,wata rana Allah zai iya kwace abunshi,Hayaam tayi dana sanin rayuwarta gaba ɗaya,abun ya tsaya mata arai,Wai har ƴar uwarta wadda suka fito ciki ɗaya,Zata iya guduwa tabarta a gadon asibiti rai hannun Allah,ta rayu kota Mutu wannan badamuwarta bace,Wannan wace irin rayuwace?ɗan uwa na gudun ɗan uwanshi,koda yake ɗa ma ya kashe ubansa,Sau nawa akayi? "Baiwar Allah,kin yi shiru ba kice komai ba"?Dr ɗinne ya katse mata zancen zucin da takeyi,   Cikin shessheƙar kuka tace"Dan Allah,ku taimaka mun da waya,inaso na kira ƴar uwata ne,"_ Hannu Dr ɗin yasa a aljihun wandonshi ya zaro wayar shi,Infinix ya miƙa mata,jiki na rawa ta kar6i wayar,sai da ta ruƙeta a hannunta ta shiga tunanin wa zata kira,Bakowa ya faɗo mata aranta ba,Fa ce AMANI,duk da tana jin fargabar kada Amani,ta balbale ta da faɗa sakamakon irin wulaƙancin da sukayi masu,daƙyar ta iya danna numbobin wayar Amani,da yake ta haddace numbarta a kanta,Danna mata kira tayi,nan take ya shiga,gabanta sai faɗuwa yake yi,almost 3 times Amani bata ɗaga ba, A lokacin tana a kitchen tana shirya lunch,tajiyo muryar Amaal tana kwala mata kira,fitowa tayi daga cikin kitchen ɗin ta tunkarota tana tambayar wanene ke kiranta a waya, Amal dake saukkowa downstairs,tace"New number ce,bansan wanene ba,ta ƙarasa maganar tare da miƙa mata wayar,zuba ma numbar ido tayi tana kallonta,a ƙa'ida bata cika ɗaukar bakuwar number ba,amma tunawa da yadda Amal tazo hannunta,ta hanyar kira da bakuwar number,yasa tayi tunanin ɗaga kiran kada ace wani abu mai mahimmanci ne,Sanya wayar tayi a kunnanta bayan ta amsa kiran,sallama tayi"Assalamu alaikum,"   On the other hand Hayaam na jin an ɗaga kiran,jiki na rawa ta kara wayar a kunnanta,cikin shessheƙar kuka ta ambaci sunanta"Aunty Amani,"   Cike da mamaki Amani tace"To fa,kamar muryar Hayaam nake ji," Murya na kerma tace"Ni ce,"shiru amani ta ɗan yi kafin tace"Lafiya kika kirani?fuskarta a ɗaure tayi tambayar kamar tana agabanta,   Cike da fargaba hayaam tace"Aunty Amani ina gadon asibiti,nayi fiye da sati a kwance,babu wani a kusa dani,"    Murmushi Amani ta saki tare da cewa"Sai akai yaya kenan?menene amfanin kira na?ina Laila ne?inasu Abrah?   Jiki asanyaye Hayaam tace"Duk basu atare dani,Aunty laila itace ta kawoni asibitin,Amma ta gudu ta barni ni kaɗai,gashi ina cikin mawuyacin hali,kamar zan mutu,"   tana kai ƙarshen maganar Amani tace"Oh Allah sarki,Allah ya baki lafiya,"   "Dan Allah Aunty Amani ki taimaka mun,Nasan kina da kyakkyawar zuciya,"   Fashewa Amani tayi da dariya mai sautin gaske,hada yin shewa kafin tace"Sai yau kika san inada kyakkyawar zuciya?Kin manta irin rashin mutuncin da kuka shuka mana?Ashe akwai rana irin wannan da zaki nemi taimako a wurina?bakiyi tunanin hakan ba?Saboda tsabar rashin kunya a haka kike tunanin cewa zan taimake ki,Koda yake dama ae ba kunya gare ku ba,"guntun tsoki taja mtswww kafin ta ɗaura da cewa"Karki kuskura ki ƙara kiran layina da sunan taimako,don da in taimaki Mugaye masu kafirar zuciya irin taku,wlh ƙwara na tattara duk wani abu dana mallaka,na kaishi gidan marayu,ko Allah ya bani Lada,Amma taimakon irinku,bakomai zai janyomun ba,fa ce Zunubi!"tana kai ƙarshen maganarta,tun kan taji me Hayaam zata ce mata,Nan take ta katse kiran,   "Aunty Amani meyasa zakiyi mata haka"?Acewar Amal,wadda tuni tausayin hayaam ya kama,   Harara Amani ta watsa mata tare da cewa"Oh harkin manta irin Muguntar da su kayi mana kenan!waɗannan mutanen da baƙin cikinsu mahaifiyar mu ta mutu,Sannan sune su kayi silar Da mahaifinmu ya Zauce,yake rayuwa tamkar mahaukaci,Bayan wannan Sune suka wulaƙantar da rayuwarki suka mayar dake tamkar dabba a haka kike tunanin zan iya taimakonsu!"?    Cikin sanyin murya Amal tace"Aunty Amani be kamata kina tuna abunda ya faru ba,wannan su da Allah,Tunda har hayaam ta kira a waya tana neman taimakonki,Yakamata ki agaza mata,koba komai ita ƴar uwarmu ce,bai kamata mu juya mata baya a irin wannan halin na neman taimako ba,Wata'kil ya zamto silar shiriyarta,dama kuma shine abunda muke fata,duk wani wanda ke aikata badai dai ba,ya gane kuskurenshi ya koma ga Allah..."sosai Amal ta shiga tausar Amani,har ta ɗan fara saukowa, Tunda Amani ta katse mata kira,ta fashe da wani irin matsanancin kukan,mai cin rai,Hada majina,miƙa ma Dr ɗin wayarshi tayi batare da ta iya furta mashi komai ba,Jikinsu ba ƙaramin sanyi yayi ba,shi da nurse ɗin dake atsaye suna kallonta,duk ta fita hayyacinta,   "Am sorry sister,dukkan tsanani yana tare da sauƙi,Ki ci gaba da addu'a in sha Allah,Zaki samu wanda zai taimake ki,"ɗagowa hayaam tayi da idanuwanta waɗanda sukayi jawur tana kallon nurse ɗin da tayi maganar,cikin shessheƙar kuka tace"Allah bazai ta6a yafe mun zunubin da na aikata mashi ba,Sakayyace ke bibiyata,haƙiƙa Nayi danasanin zuwana wannan duniyar,"tana magana hawaye na zuba akan fuskarta,   Nurse ɗin tace"Ki gode ma Allah da kika kasance araye har wannan lokacin da kika gane kuskuren da kika aikata,baki mutu kina mai aikata shi ba,Yanzu dama ce agare ki,da zaki tuba ki koma ga Allah,"   Tana kai ƙarshen maganarta,Tabi bayan Dr ɗin suka fuce daga ɗakin, Sosai hayaam ke yin kuka har kanta ya fara ciwo,Ga uwar yunwa dake cinta,kamar tayi hauka,zama tayi zugudum tana tunanin inda zata dosa idan likita ya sallameta,bata da kowa babu wurin wanda zata je,gashi bata da ko sisi balle ta doshi gida,ko da tana da kudin inama zata iya zaman mota zuwa maiduguri a wannan halin,saboda raunin dake a jikinta,Batajin zata iya taka ƙafafunta ma har taje wani wuri,uban tagumi ta zabga,tare da rufe fuskarta,tana cigaba da shessheƙar kukan, Almost 30 mins bata motsa ba,tana cikin wannan halin,Ta jiyo sautin takalma,Kamar ana shigowa ɗakin da take ciki,    "HAYAAM!"kai tsaye kiran ya shigar mata har cikin dodon kunnanta,a firgice ta ɗago don taga wanene,har sai da gabanta ya faɗi,Abunda batayi tsammani ba,Hannu tasa tana murza idanuwanta,don ta tabbatar da abunda su ke gane mata,   Amani ce atsaye bakin ƙopar,jikinsu na sanye da jallabiya,sunyi rolling veils a kansu,Hannun Amani na ruƙe da Hand bag ɗinta,Amal kuma na ruƙe da Basket mai ɗauke da food stuffs,da suka zo mata dashi,    Sakin baki hayaam tayi tana kallonsu cike da tsananin mamakin ganinsu,Lokaci guda kuma tasake fashewa da wani kukan na farin cikin ganinsu,   Ƙarasa shiga cikin ɗakin sukayi,abayansu kuwa Dr Osman ne a biye dasu,likitan dake kula da ita,    Ashe bayan fitarshi daga ɗakin Hayaam,ya wuce Office ɗinshi,bada jimawa ba,sae ga kiran Sabuwar numbar a wayarshi,Daya ɗaga kiran,suka gaisa da Amani,ta buƙaci ya bata address ɗin asibitin,Ba ƙaramin farin ciki likitan yayi ba,Saboda ya gane cewa ƴar uwar mara lafiyannan ce,Bayan ya tura mata address ɗin asibitin,After some minutes Motarsu Amani ta shigo asibitin,da kanta tayi driving ɗinsu a motarta,Bayan sun ƙaraso ta kira layin doctor ɗin,Da kanshi yazo inda suke,sannan ya jagorance su izuwa Room ɗin da aka kwantar da Hayaam,   Wuri Amani ta samu gefen gadon ta zauna,Amal kuma ta zauna saman plastic chair ɗin dake fuskantar gadon,a ƙasa ta ajiye kwandon hannunta, a ruɗe Amani tace"Hayaam!meya faru dake haka?hatsarin mota kikayi ne"?   Girgiza mata kai hayaam tayi alamar a'a,kasa buɗe baki tayi,saboda bata da amsar da zata basu ga kukan dake cinta,     "Hayaam dan Allah ki sanar dani meya faru dake ne,Nayi mamakin ganinki ke kaɗai a asibiti a wannan halin,batare da Laila ba,"   "Aunty Hayaam,Sannu ya jikin naki"?Amal ce tayi maganar fuskarta da alamun tausayinta,daƙyar ta iya amsa mata,Duk kunya ta rufeta,    Cikin sanyin murya tace"Aunty Amani nayi danasanin rayuwata gaba ɗaya,Na tsani kaina,Komai ya fita raina,Ban yi tsammanin zaki zo ba,Har na fidda rai da cigaba da rayuwa acikin duniyar nan,Amma ganinku da nayi ba ƙaramin farin ciki nayi ba,"tana magana hawaye na zuba,   Juyawa Amani tayi tare da kallon Amal tace"Ki jirani a waje,Zan kira ki,inaso muyi magana da hayaam,ki tafi da wayata,ko game ne ki buga,"   Miƙewa Amal tayi tare da matsawa wurin Amani,ta kar6i wayarta,kafin ta kama hanyar barin ɗakin,    mayar da hankalinta tayi sosai akan Hayaam tace"ina sauraronki,faɗamun meya faru dake?meyasa kike zaune a asibiti ke kaɗai batare da Laila ba?duk me ya jawo hakan"?a ƙagare Amani take da taji amsoshin tambayarta,   Hayaam bata 6oye mata komai ba,Tun daga kan Abunda ya faru tsakaninta da haroon har izuwa farfaɗowarta da tayi a gadon asibiti,Hannu tasa tare da ɗaukar wasiƙar da ta cukuikuye agefenta ta miƙa ma Amani ita,kar6a Amani tayi a atsanake ta shiga karanta wasiƙar da Aunty babba ta rubuta mata,wasu irin hawaye ne suka soma shararowa daga kan fuskarta,Saboda tsabar ƙululun baƙin ciki kamar ta haɗiyi zuciya, "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!wannan wani irin rashin Imani da rashin tausayi ne?Anya kuwa laila tana son tagama da duniya lafiya?yanzu duk don saboda neman abun duniya ta tafi ta barki a gadon asibiti rai hannun Allah?Anya matar nan tana da Hankali kuwa?Ya salam"rai a6ace take maganar,abun ya ƙona mata ranta sosai,   Hayaam tace"bata da imani,wlh duk rashin hankalina,banajin zan iya tafiya in bar Aunty laila a gadon asibiti,Amma haka ta haura ƙafa ta barni,Sai kace ba ciki ɗaya muka fito da ita ba......"kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da yazo mata,   Itama Amanin kukan takeyi sosai,cikin shessheƙar kuka tace"Ha..hayaam ki faɗamun sunan wanda yayi maki wannan aika aikar,inason nasan Wani mara imanin ne"?   Daƙyar hayaam ta tsagaita da yin kukan tace"HAROON ne ɗan gidansu Ya Abbas,Mijinki,"   Saboda tsabar kiɗima a razane Amani ta miƙe tsaye hankalinta a matuƙar tashe take maimaita sunan haroon abakinta,   Hannu ta aza akai tana faɗin"Nashiga Uku!Hayaam kina nufin haroon shine yayi maki wannan ɗanyen aikin"?ɗaga mata kai hayaam tayi Alamar eh,    "Wlh bazan ta6a ƙyaleshi ba,Sai na tona mashi asiri wurin Abbas!Fasiƙi kawai mugu,dama ni bai ta6a kwantamun araina ba,Allah kaɗai yasan abunda yake aikatawa"ta ƙarasa maganar tare da komawa gefen gadon ta zauna,   "Aunty Amani ki ƙyaleshi kawai,kada kice zaki tona mashi asiri,koma me ya faru dani laifina ne,Da ace tun farko na kama mutuncin kaina,da babu namijin da zai nemi aikata fasiƙanci dani,Zan yi haƙuri in rungumi ƙaddarata,Kibarshi kawai,Allah shi zai sakamun,"   girgiza kai Amani ta shiga yi tare da cewa"Wlh bazan ta6a ƙyaleshi ba,Shikenan yaci bulus kenan?wannan mutumin fa,ba ƙaramin mugu bane,bai kamata a dinga ƙyale irinsu ba,Suna aikata abunda suka ga dama,batare da an yanke masu hukunci ba,Yanzu kika san irin matan da ya lalata ta ƙarfi ta tsiya kamar yadda yayi maki?shiru hayaam tayi tana sauraronta,   "Dole ya gane kuskurenshi,kuma ni bazanso duk wani abu da zai 6ata sunan family ɗinsu ba,Yana so ya zubda masu mutuncinsu ne a idon duniya,Don haka dole na ɗauki mataki akanshi,"ranta a 6ace tayi maganar,tare da kai hannunta cikin food basket din da suka zo dashi ta zaro plate tare da warmer,Buɗe kular tayi,Soyayyan naman kaza ne acikinta wanda yaji uban kayan haɗi,sae ƙamshi ke tashi,tuni jikin hayaam ya soma rawa sai faman haɗiyar yawu take yi,kamar ta kaima warmer ɗin wawura haka take ji,.     Acikin plate Amani ta zuba mata naman tare da miƙa mata,Sannan ta dauko mata ruwa mai sanyi na roba,tare da fresh milk,ta shiga tsiyaya mata su acikin Cup,    ganin yadda hayaam ke taunar cinyar kazar hada ƙashin duka take haɗawa,yasa Amani cewa"Ki ci a hankali mana,kada kija ma kanki wata matsalar,"kasa natsuwa tayi saboda yunwar da take ji,   Sosai hayaam taci naman nan,tasha fresh milk ɗin mai sanyin gaske,sai da taci ta ƙoshi,sannan ta samu natsuwa,   "Itama Laila bazan ƙyaleta ba,nasan cewa zata nemi Abra ne don ta rakata wurin bokan,wama yasani ko har sun tafi,Kuma ina da tabbacin cewar,bazata ta6a sanar ma wani cewa tabarki a asibiti ba,don kada a tuhume ta,"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar kafin taci gaba da cewa"muguwar ashe ko ƙannenta da suka fito ciki ɗaya bata iya raga mawa,inajin tsoron tace zata kai Abra wurin fasiƙin Bokannan,don muddin takaita,zaiyi wuya bai nemi ya kusanci ɗaya daga cikinsu ba,"   Jin wannan maganar yasa hankalin hayaam ya tashi,don ita yanzu tayi nadama,kuma tana jin tsoron halin da Aunty babba zata jefa Abra,kamar yadda tayi mata,    "Yanzu ya zamuyi mu dakatar da Abra daga zuwa wurin bokan nan"?hayaam ce tayi maganar,   "Ina ganin idan muka kira Abra muka sanar da ita abunda laila tayi maki na barinki a gadon asibiti,zata fasa bin ta ne,"   Zama suka yi suna yanke shawarar yadda zasu dakatar da Abra,a ƙarshe suka yanke shawarar kiranta a waya, *Boss Bature* *JUNAID* Tsaye yake a gaban dressing mirror,ya ɗauki wankan pakistan ajikinshi masu kyan gaske farare sun ƙara fito da hasken fatarshi,Fuskar nan har wani kyau ta ƙara,ya gyara sumar kanshi sosai ta kwanta luf a bayan wuyanshi,Slowly ya miƙa hannu gaban mirror ɗin ya ɗauki kwalbar turarenshi,yabi ko ina na jikinshi ya feshe shi,bayan ya mayar da ita,ya ɗauko wrist watch ɗinshi ta diamond da Hajiya azeema ta bashi,Yana ƙoƙari sanyata a hannunshi,Wayar shi ta soma ringing,da sauri ya ƙarasa sanya agogon,tare da tunkarar saman gadonshi inda ya ajiye wayar yakai hannu ya ɗauketa,tare da kollon screen ɗin wayar,Sunan Mommyn su ne ya bayyana akai,tur6une fuska yayi kafin ya ɗaga wayar,cike da shagwa6a ya soma magana"Mommy,ni fushi nake yi dake," On the other hand,Alexandra tace"haba romeo ɗina,why are u angry wit me?laifin me na maka da kake fushi dani"    "Mommy,u forgot about me,tunda na dawo baki kira layina ba,babu wanda ya damu dani,"   Cikin lallashi tace"Sorry my own son,pls kadaina fushi dani,"   Bubbuga kafarsa yayi cikin shagwa6e yace"Nidai Mommy indai kina son farin cikina,Ki dawo gida kawai ke da daddy,dasu yaya Fawan,kowa ya dawo gida,nayi missing ɗinku sosai,"    Alexandra tace"shi ne kawai abunda kakeso,"   "Eh,adawo gida,acigaba da rainon baby junaid"yanayin yadda yayi maganar ba ƙaramin dariya ya bata ba,yana jiyo muryarta ta cikin wayar tana dariya, Bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Calm down ur mind,This week zamu dawo,"   Fuskarshi ɗauke da farin ciki yace"Mommy pls,Ki tursasa daddy,ko da baya son dawowa,ni dai ku dawo gida kowa da kowa,tare da su yaya fawan,Twins su irfan and sister hafsat,inason ganin kowa a kusa dani,"   "Don't worry ur self,my romeo kowa zai dawo saboda farin cikinka," Ba ƙaramin daɗi yaji ba   Sun jima suna waya kafin daga bisani,su kayi sallama,ajiyar zuciya ya sauke tare da yin wurgi da wayar saman gadon,kwankwasa ƙopar bedroom ɗinshi akayi,da sauri yace wanene   "My Romeo,its Me ur juliet,am ready for the outing,"wani irin ƙayataccen murmushi ya saki jin muryar jahad,    A ƙagare yake daya ga wankan data ɗauka,jiki na rawa ya ƙarasa tare da buɗe mata ƙopar,Gabanshi ne ya faɗi rass,Tun daga kan takalman ƙafarta ya fara kallonta,High heels ne ƙafarta,farare,abun ya bashi mamaki ganin tayi shigar white gown,launin kayanshi daya sanya,tayi rolling veil akanta,lips ɗinta kuwa Red ta sanya masu,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga jikin ko wannansu,   Ruƙo hannunta junaid yayi tare da janyota cikin bedroom ɗin,lumshe idanuwanshi yayi tamkar maijin bacci,da wata irin kasalalliyar murya,yace"Jahad,You look so beautiful,kayan nan sunyi maki kyau sosai,"   Hannu tasa tare da shafa side face ɗinshi"Duk kyawuna ae bankai ka ba,kaifa na dabanne,ta ko'ina Allah ya baka,".    Aɗan shagwa6a yace"Amma ni bana jin kaina a matsayin cikakken mutun,"   A ɗan ruɗe tace"Saboda me,'? Hugging ɗinta yayi tare da kai lips ɗinsa saitin kunnanta sannan yace"Saboda,ban mallake ki ba,sai dake ne zan zama cikakken mutun,'   Wani irin matashin murmushi jahad ta saki,taji daɗin kalaminsa sosai,    "Nikaina junaid,bana jin kaina amatsayin cikakkiya,har saina mallake ka,"   kalaman soyayya suka shiga gayawa junansu, Duk wannan abunda da suke yi akan idon Haroon wanda ke la6e,ya ɗan buɗe kopar ɗakin ya zuro kanshi yana kallonsu,   Jinjina kanshi yayi tare da cewa"Ta kwana gidan sauƙi,"yana faɗin hakan,ya rufo masu ƙopar ɗakin,hannu yasa tare da zaro wayarshi,Contact ya shiga,Tare da rubuta wasu numbobi,ya danna kira,tare da manna wayar asaman kunnanshi,   Muryar wani kakkauran mutunne yace"Ya haroon,Ya ake ciki ne?ina fata kazo mana da labari me daɗi,"   ƙasa ƙasa da murya haroon yayi don kada wani ya juyo shi,    "Ka saurare ni dakyau,Yanzu junaid zasu fita tare da ƴar wurin uncle ɗinmu,Abunda nakeso daku,Karku kuskura ku ta6a lafiyar jikin yarinyar saboda ba akanta zamuyi aiki ba,Junaid kawai nakeso,Ku bi ta kan motarshi da truck,Yadda ko fuskarshi ba'za a gane ba,idan tayi dameji,"   Fashewa mutun yayi da wata irin Mahaukaciyar dariya,hhhhhhhh kamar zai fasa screen ɗin wayar,Bayan ya tsagaita da yin Dariyar yace"AN GAMA OGA,SAI DAI UWARSHI TA HAIFI WANI," Jinjina kai haroon yayi tare da sakin shu'umin murmushin nan nashi yace"ku kasance a ankare,Yanzu zai fito da motarshi,banaso yaron nan ya dawo gidan nan araye,Gawarsa kawai nakeson gani,jaga jaga da jini," 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* ⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐ *MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI*💃🏻💃🏻 Sis ko kinsan illar rama ajikin mace in tayi yawa ??? Rama Sam batayi ba mijinki kullum yana iya kokarinshi akanki amma da yawa mutane sai suyi maki kallon kina cikin matsala ne saboda ramar da kikeyi , sannan zaki zquna a abushe bawata mat'aba ajikinki 🤣🤣 wannan yasa nazo maki da maganin kiba mai inganci hajiya yadda zaki ciko sosai ki murje abunki bawai kiba mai yawa ba aa zaki ciko dai kikoma yar dai dai misali ke ba katuwaba ke ba ramamma ba yadda kema zakiji dadin yin kwalliyar da zataja hankalin mijinki agareki😉😉 mmn Yusuf fa ta shirya tsaf domin gwangwaje Ku da zafafan kayanta uwayen gida da Amare👍🏼👍🏼👍🏼👍🏼07069711327 *Boss Bature ✍️* *HAROON*na kammala yin wayar,ya mayar da ita cikin aljihun wandonshi,da sauri da sauri ya saukko down kaitsaye ya nufi part ɗinsu,Sautin murya yaji ana raira waƙa da sauri yakai idanuwanshi wurin,Hosana ce zaune saman Sofa,ta aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,ta ɗauki wankan jeans da t shirt ajikinta sam bata lura dashi ba,jinjina kai haroon yayi tare da sakin wannan shu'umin murmushin nashi,A ranshi yace"Zan dawo kanku ne,dake da Omar ɗin,tabbas idan na ta6aki tamkar na ta6a zuciyarshi ne,don haka ta wurinki zan biyo mashi,Saina sa ya zubda hawayenshi kamar yadda nima yasa na zubar da nawa,"ya ƙarasa zancen zucin nashi tare da wuce wa part ɗinsa,bedroom ɗinshi ya shige ya fara zarya acikinshi,burinshi kawai yaji Saƙon mutuwar Junaid~ *JUNHAD* Saukowa sukeyi downstairs hannunsu ruƙe acikin na Juna,    "Tun ɗazu nake kiran Layin Rishi,Amma bata ɗagawa,I don't know why,nashiga damuwa,"jahad ce tayi maganar,fuskarta da ɗan damuwa,   Junaid yace"may be tana busy ne,amma ki bari zuwa anjima sai mu jaraba kiranta,may be ta ɗaga wayar,"   Cikin palour suka saukko,hosana na ganinsu ta miƙe tana sakar masu murmushi,   Ba ƙaramin burgeta su kayi ba yarfa hannu ta shiga yi tana faɗin"Wow,jahad junaid kunyi kyau kamar sabbin kuɗin da Central bank suka fitar,"gaba ɗaya suka fashe da dariya,    camera ta shiga,tare da ɗaukarsu hotuna da wayarta,kafin suka wuce tare da barin palourn,komawa hosana tayi saman sofa ɗin tana jiran dawowar Ya Omar, Wurin motarshi suka nufa,da kanshi ya buɗewa jahad mota,ta shiga,kafin ya zagaya other side ɗin,ya buɗe ma kanshi motar ya shiga, juyawa ta ɗan yi tare da kallon fuskarshi,Murmushi ta samu akan fuskarshi,   Cikin sanyin murya tace"Babyna,"   "Na'am" ya amsa mata tare da wurga idanuwanshi akanta,   Kashe mashi ido ɗaya tayi kafin tace"Junaid,I love u so much,I can sacrifice my life for u,"   Ƙayataccen murmushi ya saki,tare da cewa"Me too,",yana ƙoƙarin tashin motar yaji gabanshi yayi wani irin mugun bugu mai sautin gaske ji kake daraaam!har razana sai da yayi,lokaci guda yanayin fuskarshi ya canza,ganin ya kasa tashin motar yasa jahad,cewa"Babyna,Lafiya naga yanayinka ya canza"?   Ashagwa6e yace"jahad,faduwar gaba nake ji,kamar wani mummunan abu zai faru dani,haka nake ji,"muryarshi a kasalance yayi maganar,   Cikin sanyin murya tace"In sha Allah babu abunda zai faru da kai babyna,idan har fitar nan da zamuyi bata kwanta maka arai ba,ni inaga kawai mu koma gida..."tunkan ta ƙarasa maganar,yace"a'a,Bazamu fasa ba,na sa rai sosai akan fitar nan,"   Jinjina kai jahad ta ɗan yi tare da zura hannu cikin ƴar purse ɗinta dake ajiye saman laps ɗinta,Phone ɗinta ta curo tare da buɗeta,adai adai lokacin app ɗin da take amfani dashi na V muslim wurin yin azkhar yayi mata alert na cewa time ɗin yin evening azkhar yayi,   Juyawa ta ɗanyi tare da kallon junaid,wanda jikinshi duk yayi sanyi,   "Babyna,yakamata muyi azhkar kafin mu fita daga gidan nan,"    Ashagwa6e yace"jahad ni ban iyaba,bansan ya zanyi ba,"   Moving tayi close to him tare da nuna mashi screen ɗin wayarta"kalli ka gani,App ne nake using dashi yana da matuƙar amfani,kuma yana taimaka mun wurin tunasar dani lokuttan yin sallah da kuma yin azhkar,koda ace baka iya ba,zaka iya yi yayin da kake kallo kana karantawa acikin zuciyarka," Murmushi ya ɗan saki kafin yace"Its ok my juliet,mu fara atare,"   Nan suka shiga yin azkhar ɗin acikin zuciyarsu,har suka kammala,tukunna yaja motar da gudu ya nufi hanyar fita daga gate ɗin gidan,a bakin gate ɗin ma sai da jahad ta ƙara tunasar dashi akan yin addu'ar fita daga gida kuma atare suka furta"Bismillah,Tawakkaltu Alallah,wala haula wala ƙuwwata illa billah", Fitar motarsu keda wuya,Sai ga motarsu Marshal Omar na shigowa cikin gidan,Hatta gifcinsu sai da marshal Omar ya gani,   "Yalla6ai,kamar motar junaid ce ta wuce yanzun nan"major ne yayi maganar, Omar dake zaune a back seat na motar yace"I think so,"   "Amma yalla6ai,kada kace nayi shisshigi,ni dai aganina bai kamata junaid na fita yawo shi kaɗai ba without security guards atare dashi,duk da munsan Allah ke tsare bayinsa," shiru Marshal ya ɗan yi yana nazarin wani abu kafin yace"Ni kaina na jima ina tunanin hakan,last time har maganar mu kayi da Rafayet,amma daga baya kowa ya share maganar," Major yace"gaskiya yakamata aduba,saboda yaron yana da farin jini sosai,kuma kowa yasan irin son da kuke yi mashi,duk wani mai hakon family ɗinku zai iya biyowa ta wurinshi ne"_ Jin wannan maganar ta Major,yasa hankalin Omar ya tashi,saboda an sha faɗa masu cewa junaid,Shi ne lagwansu,Duk wani wanda zai kawo masu hari acikin masu son ganin bayansu,dole sai an ƙuntatawa junaid sannan za'a ta6a zuciyoyinsu,   "Major thank u so much for ur advise,and in sha Allah zanyi wani abu akai,' Bayan Major yayi parking ɗin motar,Ya buɗe ya fito tare da zagayawa ya buɗewa Marshal,Saukowa marshal yayi,ya nufi cikin gidan,lokacin da ya shiga babu kowa a main palour ɗin,Bedroom ɗinshi ya wuce,Shaf shaf ya cire kakin dake ajikinshi,Ya wuce cikin toilet,after some minutes ya fito daga cikin toilet ɗin,sanye da short a jikinshi,Agajiye yake ga wani irin bacci da yake ji,Saman gadonshi ya haye,in a short time bacci ya ɗauke shi, A hankali Hosana ta turo ƙopar dakin nashi,tun tana kabbara sallar la'asar ta jiyo shigowar mota cikin gidan,jiki na rawa ta sallame bayan ta gama sallar ta fito,saboda tana da tabbacin cewar Ya Omar ɗinta ne ya dawo,murmushi ta saki ganinshi kwance da gajeran wando ajikinshi,ya baje sai faman sharar bacci yake yi,lalla6awa tayi cikin sanɗa ta haye saman gadon,saman jikinshi ta hau,har zuwa saitin fuskarshi,ta ƙura mashi ido tana kallon kyakkyawar fuskarshi,bata da da burin da ya wuce ta takura mashi arayuwarta,    "Bari nagani,idan na toshe mashi hancinshi da bakinshi,ta ina zai yi numfashin,"   Hannu tasa,cike da mugunta,ta toshe mashi hancinshi da bakinshi,ta danne su da tafin hannunta,aikuwa nan take numfashinshi ya soma tattokarewa,A razane ya farka lokaci guda,ya rarumeta batare da ya ankara ba,yayi wurgi da ita,da iya ƙarfinshi na ƙarshe,kai tsaye hosana ta faɗi ƙasan gadon yaraf!kanta ya bugu sosai,fashewa tayi da matsanancin kuka tana fadin"Wayyo Allah na,Ya Omar ka kashe ni wllh,"   Tunda yaji muryarta,ranshi ya 6aci sosai,saboda ita taja har yayi mata hakan,ko kwanakin baya ta ta6a yi mashi irin hakan har yayi wurgi da ita,miƙewa yayi daga zaune tare da kai idanuwanshi wurin da take yashe a ƙasa tana kuka,   Da wata irin kasalalliyar murya yace"Why Hosana!why!"?    Sai faman shessheƙar kuka take yi,tama gaza ɗagowa da kanta,   Guntun tsoki yaja,kafin ya sauko saman floor ɗin,hannu yasa ya janyota jikinshi ya rungumeta a saman faffaɗan ƙirjinshi,yana ɗan bubbuga bayanta,Cikin lallashi yace"Am so sorry My Hosana,duk laifinki ne,meyasa kike son takuramin ne?   Cikin shesshekar tace"ya..ya..Omar,nifa wasa nake yi maka fa..."   "Haka ake yin wasa a garinku?You are trying to kill me,and u are saying that it was a joke!"    "Ya Omar,nima fa a wani Chinese film ne nagani,Na jakican,shi ne na kwaikwaya,"   A ruɗe ya ɗago da kanta daga saman ƙirjinshi yace"Ke!ashe dagaske baki da hankali,saboda kawai kin kalli film kinga anyi haka sai kice nima zaki jaraba akaina?angaya maki cewa abunda ke cikin film dagaske ne?Su idan sunyi sun rayu,to ni idan kika yi mun kashe ni zakiyi,"   Runtse idanuwanta tayi ganin yadda yake ta surfa mata faɗa,   Tsagaitawa tayi da yin kukan da take yi"Am sorry Ya Omar bazan ƙara ba,"   Harara ya ɗan watsa mata"kinfi kowa iya bada haƙuri,idan kikayi laifi kamar matar aure ta gari,"   Murguɗa mashi baki tayi,lokaci guda ya samu kanshi cikin wani irin yanayi,zuba mata ido yayi yana kallon dress ɗin dake ajikinta,Jeans da t shirt sunyi matuƙar bin shape ɗin jikinta,jin yayi tsit yasa ta ɗan buɗe idanuwanta,ganin ya zuba mata ido ko ƙyaftawa baiyi ba,yasata fara tunanin kome yake kallo ajikinta,Ganin yana kallon ƙirjinta yasa tace"Ya Omar sun ƙara girma ko"? Waro ido ya ɗan yi tare da cewa"Mekenan?" Hannu tasa tana nuna mashi breasts ɗinta,   "Ya salam,"ya furta hakan tare da ɗan rufe idanuwanshi yace"nifa,basu nake kallo ba,kayan jikinki ne suka burgeni,sunyi maki kyau sosai,"ya ƙarasa maganar tare da miƙewa tsaye yana kallonta,    "Idan kana jin yunwa in kawo maka abinci"?tayi tambayar tana kallonshi,    ɗaga mata kai yayi alamar eh,sannan yace"pls,inaso in ɗan kwanta in huta kinga baccin bai ishe ni ba,idan kika kawo mun Lunch ɗin,ki ajiyemun shi saina farka zanci,"   Amsa mashi tayi da toh,kafin ta miƙe da sauri da sauri ta fuce daga ɗakin,saman gadon ya koma ya kwanta,bakomai bane ya faɗo mashi aranshi ba,fa ce maganar da suka yi da Major dangane da Junaid,hakanan ya dinga jin kamar yayi kuskuren barinshi ya wuce da motarshi,dama ya sani tun a time ɗin yasa security sun bi Bayan Motarshi........... *Boss Bature* Ƙarar shigowar Message,da ta ji ne yasa takai hannu tare da ɗaukar wayarta dake ajiye agaban mirror,yayin da take zaune asaman kujerar gabanshi,tana yin makeup,janyo wayar tayi tana karanta message ɗin daya bayyana akan screen ɗin wayar,    _Abra,inason magana dake,amma bana so kowa ya sani,koda Aunty Laila ce_   Mamaki ne ya kamata ganin anyi mata saƙo da new number,kowaye wannan,ɗaukar wayar tayi tare da miƙewa tsaye,a lokacin Aunty babba na cikin toilet tana yin wanka, Arab gown ce ajikinta,pink colour abunka ga fara tass,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,fitowa tayi daga cikin bedroom ɗin nasu,ta miƙi hanya kamar zata fita daga corridor ɗin,Sai da ta bada tazara sosai,Sannan ta dannama numbar kira,tana fara ringing aka ɗaga,   Tun kafin tayi sallama,taji muryar hayaam tace"ABRAH"!tun daga kan yadda ta kira sunanta yasa gabanta ya faɗi rass,    "Aunty hayaam kece"? Bata amsa mata ba,sae ma fashewa da tayi da kuka mai sautin gaske,hakan ya ƙara ɗagawa Abra hankali,a ruɗe ta shiga faɗin"Aunty hayaam meya faru dake ne?meyasa kike kuka?dan Allah kiyi mun bayani," On the other hand,Hayaam ta miƙa ma Amani wayar tare da cewa"kiyi mata bayani,"   Gyaran murya Amani tayi tare da ambaton sunan Abra,   Duk sunbi sun ɗaga mata hankali,muryarta har kerma takeyi wurin cewa"Dan Allah kuyi mun bayani,kun sanyani acikin duhu,"   "Abrah!ki natsu ki saurareni,"jinjina kai abra ta shiga yi tana fadin"ina sauraranki Aunty Amani,meya faru ne naji Aunty hayaam tana kuka,   Amani bata 6oye mata komai ba,game da abunda ya faru da hayaam da kuma guduwar Aunty babba daga asibitin,da kuma wasikar da ta bar mata,wasu irin zafafan hawaye ne suka soma gangarowa akan fuskar Abra,hankalinta a matuƙar tashe tace"Nashiga uku!kenan nima wata rana idan ƙaddara ta same ni,Aunty laila zata iya guduwa ta barni?   Amani tace"ƙwarai kuwa!saboda bata da Imani kuma bata da tausayi,karki so kiga yadda na samu hayaam a asibitin nan a wulakance,kamar wadda tayi hatsarin mota amma a haka laila tabarta,saboda bata da amfanin da zata yi mata,To kema muddin kika kuskura kika bita wurin bokan nan rayuwarki ta faɗa halaka,Kuma wlh da zarar amfaninki ya ƙare a wurinta shikenan kin zama Waste product!Zata yi watsi dake ne,"jin wannan maganar yasa Abra ta fashe da matsanancin kuka,wani irin tsoro ne ya kamata,don Aunty babba ta zama abun tsoro a wurinta,ta girgiza da jin rashin imaninta, Da gangan Amani ta dinga tunzura abra don ta tsoratar da ita akan karta goyi bayan Aunty babba suje wurin bokannan,   "Abra!ina ƙara jan kunnanki,karki kuskura ki bi ta,Kiji tsoron Allah,ki tuna cewa wata rana zaki koma gare shi,kada kiyi silar da za'a cutar da rayuwar wasu,Aunty laila bata da Imani,tanaso ta jefa rayuwarku cikin haɗari ne,kuma tana yin amfani da ku ne don ta cimma burinta,kuma da zarar amfanin ku ya ƙare a wurinta,zata yi watsi daku ne,ta kama gabanta,Ga hayaam nan dai yanzu ta gane kuskuren da tayi,tana mai dana sanin abunda ta aikata,"   Amani nakai ƙarshen maganarta,ta miƙa ma hayaam wayan"kiyi mata magana,"   Kar6ar wayar hayaam tayi tare da karata a kunnanta,Kukan da Abra keyi har cikin zuciyarta,dama tasan dole taji raɗaɗin acikin zuciyarta,ɗan uwa ba wasa ba,   Cikin Sanyin murya tace"Abra,baki ga yadda na koma ba,bani da wani abu daya rage na ƴa mace a jikina,komai ya lalace,Yanzu ma bana jin kaina amatsayin mace,"   Wani sabon kukan Abra ta ƙara fashewa dashi,cikin shessheƙa tace"Aunty hayaam wlh bazan bi ta ba,sai dai taje ita kaɗai,Ashe ba son mu take yi ba,bata ɗauke mu abakin komai ba,Amfani kawai take yi damu don ta cimma burinta,Ni wlh bansani ba Aunty hayaam,harfa tambayarta nayi ina kike amma tace mun wai batasan inda kika tafi ba,kinacan kina yawon gantali,Ashe kina gadon asibiti rai hannun Allah,yanzu haka fa da nake yin maganar nan,tun jiya muka iso Enugu da ita,Yanzu haka ma shirin zuwa wurin bokan muke yi,   Hayaam tace"Abra,ki natsu ki saurare ni,kada ki bari tasan da shirinki naƙin binta wurin boka,saboda bata da imani tana iya kasheki,in kika 6ata mata rai,Abunda nake so dake shi ne,Duk wani kuɗi dake a wurinta,ki tattarasu gaba ɗaya ki sanyo su acikin jakarki,muguwar rabi da kwata na kuɗin dake a hannunta nawa ne,amma saboda tsabar rashin Imani ta kwashe hada nawa ta gudu dasu,"   Jinjina kai Abra tayi yayin da take share hawayenta,   "Aunty hayaam,yanzu tana acikin toilet,bari nayi sauri na tattara kayana,in biyo mota in dawo nan,"   Hayaam tace"Yawwa,kiyi sauri kada fa kiyi kuskuren da zai sa ta gane cewa guduwa zakiyi ki barta,".    "In sha Allah bazan bari ba," .daga haka su kayi sallama, Ajiyar zuciya hayaam ta sauke tare da kallon Amani dake zaune gefen gadon,tace"Har hankalina ya kwanta,So nake Aunty laila ta ɗanɗani kuɗarta,taji irin raɗaɗin dana ji acikin zuciyata,   Murmushi Amani tasaki,tare da cewa"Nafi ki jin daɗi Hayaam,A shirye nake dana taimaka muku wurin ganin kun gyara rayuwarku,"acikin ranta kuma tace"Ita kuma waccen bijimar,Sai nasa ta tsani kanta,duk wani makusancinta saina kwace shi ya dawo a ƙarkashin ikona,So nake ta gane kuskuran da ta aikata arayuwarta," A 6angaren abra kuwa,tun bayan da suka kammala yin wayar,jiki na rawa ta koma Room ɗin nasu,A hankali ta tura ƙopar ta fara leƙawa ciki,don taga ko ta fito daga wankan,Ajiyar zuciya ta sauke,ganin bata fito ba,da sauri ta faɗa cikin ɗakin,Jikinta sai kerma yake yi,asaman bedside drawer,ta samu jakar Aunty babba,hannu tasa ta ɗauki handbag ɗin,tare da zagayawa ta Other side ɗin ta ɗauko ƴar purse ɗinta,saboda tsabar sauri jin Aunty babba na motsi kamar zata fito daga cikin toilet ɗin,aikuwa a gigice ta buɗe ƙopar ɗakin ta fuce,da gudun gaske,mutanen dake kai komo a cikin hotel ɗin sai kallonta sukaye,wasu kallon burgewa suke yi mata saboda rigar jikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,gashi bata sanya mayafi akanta ba,ƙafafunta ko takalma babu, Hankalinta bai kwanta ba,har sai da ta fito daga cikin hotel ɗin,gudu gudu sauri sauri ta miƙi hanya tana tafiya tana waiwayon bayanta kada ace Aunty laila ta biyota,Masu motoci sai parking sukeyi agabanta suna yi mata tayin shiga motarsu,amma taƙi sauraron kowa saboda gudun kada wani ya cutar da rayuwarta,kamar yadda aka yiwa Hayaam,baiwar Allah ta tsorata sosai,gashi babu wanda ta sani a garin,haka bata san ko ina ba,ba ƙaramin galabaita tayi ba,     *Koya Abra zata ƙare?Shin ina Aunty Babba dake a cikin toilet tana wanka?Batasan an yashe ta ba* *Boss Bature*    ❤🤍❤ Kano state Wuraren ƙarfe 6 na marece,Slowly motocin Sgr suka shiga cikin unguwar batare da jiniya ba,saboda patient ɗinsu da suka ɗaukko,a back seat na motar Abusufyan suka kwantar da ita,Abusufyan shi ne ke driving ɗin motar,fuskarnan tashi a washe,kamar wanda aka yima Albishiri da Gidan Aljanna,Sehrish na agefenshi sae faman sakin murmushi take yi tana waiwayawa,bakinta yaƙi rufuwa,a ƙagare take dasu ƙarasa gidan,ko ta samu ta kira sauran ƴan uwa ta sanar dasu cewa An samo Oummansu, Bayan motar su Abusufyan Motar dake ɗauke da Baban Sadeeq ce,tare da Maman Sadeeq,ɗaya daga cikin motocin Sgr ne,wanda wani soja ke driving ɗinsu, Mamaki yaƙi barinsu,musamman Maman sadeeq,abun ya ɗaure mata kai har tagaza rufe bakinta, Kasa kasa tace "Baban Sadeeq kaga wani iko na Ubangiji"?   Murmushi Baban sadeeq yayi tare da kallonta yace"dama ae naji ma ina sanar dake cewa,Allah yana tare dasu,kuma shi zai kula da abunshi,Yau nasan kin shaida maganata," Murmushi ta saki tunawa da wannan kalami na Baban sadeeq,a duk lokacin da ta rufe shi da faɗa kan cewa sunƙi ɗaukar mataki akan Ya sayyadi,yana ta cutar da bayin Allah,an zuba mashi,sai babban sadeeq yace mata"Bazan iya tunkarar mutumin nan ba,Mutumin da kana ja mashi ayar ƙur'ani yana fassara maka?taya zan iya tunkararshi?in dai akan yara ne Allah yana tare dasu,Kuma shi zai kula da abunshi,"   "Amma gaskiya Baban sadeeq,nayi matuƙar mamaki,har yanzu fa ji nake yi kamar mafarki nakeyi wlh,wai yanzu waɗannan danginsu rishi ne?bayin Allah,wlh na tayasu murna sosai,"   Baban sadeeq yace"Ni ji nake kamar nafi kowa farin cikin wannan ranar wlh,Alƙawarin dana ɗaukarwa kaina,Ya cika yau ga abu ga Ƴa'ƴanta,ga kuma danginsu,Godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata'ala," A bayan motarsu dasu Baban sadeeq suka,Motar dake biye da tasu,nurse ce ɗaya tare da Dr,An zo dasu ne don a nuna masu gidan,Saboda sune zasu ci gaba da zuwa suna duba lafiyarta,security guards sun sanya motocinsu a tsakiya,gaba da baya duk motocin Soldiers ɗinne,Sgr baisamu ya biyo bayansu ba,Sun wuce Hotel shi da Armstrong, A parking space suka tsayar da motocin nasu,fitowa Abusufyan yayi tare da zagayawa ya buɗe gidan baya,Hannu yasa ya kinkimo abu,tare da azata asaman kafaɗarshi,gaba ɗaya suka kama hanyar shiga cikin falon gidan,tun kafin su shiga ciki sehrish ta fara ganin canji alamun kamar anyi gyara acikin gidan,shi kanshi Abusufyan yayi noticing hakan, Main palour ɗin suka shiga,Nan fa suka sha mamakin ganin an canza Sofa set ɗin falon izuwa sababbi,Hatta ƙasan falon wani jigunannan carpet ne aka shimfiɗa ya mamaye ko'ina,ga wani irin sanyi na A.c dake ratsa ko'ina cikinshi,Abun ya ɗaure masu kai,    "Abba kodai munyi mistake ne"?Sehrish ce tayi maganar,   "Ba kuskure mu kayi ba sehrish,ni kaina nayi mamaki,daga gani aikin Sgr ne,Shi ya sanya aka gyara gidan,dama ina ta fargabar awani wuri zamu aje Oummanku"yayi maganar,a yayin da suke tunkarar Bedroom ɗin abu,ciki ya shiga da ita,nan ma an sanya A.c ɗin,daga gani duka gidan aka gyara,hatta furniture ɗin duk an canzasu,Naira tayi aiki daga safe zuwa maraice gidan ya koma tamkar na amarya,amaryar ma yar masu fada aji,a hankali ya kwantar da ita saman gadon,wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙare mata kallo cikin zuciyarshi kam hamdala yake tayi,   Sehrish dake tsaye tana kallon fuskar Oumman tasu,sae faman sakin murmushi takeyi,ji take kamar ta faɗa jikinta ta rungumeta sosai,'   Sehrish ki zauna gefenta,bari na fita wurinsu Baban sadeeq,mun barsu a palour,"yayi maganar tare da miƙewa ya fuce daga ɗakin,   Wuri Sehrish ta samu daga gefen gadon ta zauna,tana kallonta,   "Allah ya baki lafiya Oummanmu,Nasan zakiyi farin ciki sosai,idan kika ga yadda ƴan ukunki suka koma,Ashe da rabon mukai wannan lokacin araye,mu dukkanmu"?hawaye ne suka soma saukowa daga saman fuskarta,kwantar da kanta tayi daga gefen Oumman,ta sanya hannunta tare da ruƙo nata, Lokacin da Abusufyan ya koma palourn,A zaune ya samu Malam Nura tare da Maman sadeeq saman 3 seater,Nurse ɗin kuwa tana zaune saman 2 seater ita da Doctor, After few minutes da shigarshi palourn,Sae ga wani Soja ya shigo hannunshi ruke da manya manyan ledoji na restaurant,A bayanshi kuma wani sojan ne hannunshi ruke da Katan katan na lemunsha,Saboda tsabar farin ciki,bakin Abusufyan yaƙi rufuwa,dama tunanin da yake yi kenan,gashi sun shigo da baƙi kowa ya kwaso yunwa gidan kuma ba wani abunsha,Balle abinci,    Ƙarasowa ciki sukayi tare da ajiye kayan a tsakiyar palourn,    Atare suka haɗa baki wurin cewa"Sgr ne,yace a shigo maku dashi,zaizo anjima,"   Murmushi Abusufyan ya ɗan saki tare da cewa"Okey,mun gode sosai,Allah ya kawo shi lafiya," Juyawa su kayi atare suka bar ɗakin,   Sehrish ya kira,ta ɗauki ledojin takaisu kitchen,acan ta haɗo masu kayan abincin A cikin warmers ta jerasu a saman tray,Saman dining table ta jera masu su tare da drinks,Gaba ɗaya nan suka harhadu,dama kowa ya kwaso yunwa,don sun jima a asibitin nan,Nan fa kowa ya shiga ɗurama cikinshi abinci,bayan sun ci sun ƙoshi,daga bisani,wuraren sallar magrib,Nurse ɗin tare da doctor su kayi masu sallama, Abusufyan ne ya ɗauko su acikin motarshi tare da Baban sadeeq saboda zasu wuce masallaci daga nan,' Tun bayan da ta kammala sallar magrib,ta koma saman gadon Oummasu ta zauna tana kallonta,a ƙagare take da ta farka duk da tasan cewa,ba a hayyacinta take ba,batasan wacece ita ba ayanzu,   "Yakamata in sanarwa su Jahad da hosana,"tayi maganar cike da zumuɗi ta dauki wayarta dake ajiye gefenta,   Contacts ta shiga,tare da lalubo numbar jahad ta danna mata kira,Kusan sau uku tana ringing ba'a ɗaga ba,hakan yasa ta tura mata text message,    Layin hosana,ta kira itama wayar bata a kusa da ita,tayi ringing harta katse ba'a ɗaga ba,   Yanke shawarar kiran junaid tayi,cikin rashin sa'a ta samu wayarshi a kashe,   Tur6une fuska tayi ranta a 6ace,taso ace itace zata fara yi masu albishirin ganin Oummansu,Amma duk sun ƙi ɗaga kiran wayarta,   Yunƙurawa ta ɗan yi saitin fuskar Oummansu,ta ɗauketa photo da camera ɗin wayarta,kusan hoto uku tayi mata, ta whatsapp ta tura masu hotunanta,' Motsin mutane taji acikin palourn,ranta ya bata cewa Su Baban sadeeq ne suka dawo,bata leƙa ba,kwanciya tayi a gefen oummantasu, Su biyu suka shigo cikin palourn,zama sukayi saman sofas ɗin suna fuskantar juna,Abusufyan yace"Bamu da wasu kalmomi da zamu iya amfani dasu wurin gode maku,kunyi matuƙar yin ƙoƙari,kun kula da rayuwar abu,tamkar ƴar cikinku,kun damu da ita sosai,Allah ne kaɗai zai iya sakamaku,"   Baban sadeeq yace"duk yiwa kaine,idan ka taimaki rayuwar wani kaima Allah sai ya taimaki ta ka,Naji daɗi sosai,kuma nayi matuƙar farin ciki,daya kasance kaine Mijin Zainab duk da an shiga tsakaninku,kuma mahaifinsu sehrish!hankalina ya kwanta sosai,Abu zata rayu atare da mijinta ga kuma ƴa'ƴanta,uwa uba kuma ga dangin mijinta,Allahu Akhbar,najiye mata daɗi,ƙarshen wahalarta yazo da yardar Allah,"   Murmushi Abusufyan yayi tare da cewa"Amma malam,Ya maganar sayyadi ne!?ko kuna da labarinshi"?   Shiru Malam nura ya ɗanyi na wani lokaci yana tunani kafin yace"Ae Sayyadi tun ranar da aka nemi abu aka rasa,tun daga ranar bamu ƙara sanyashi a idanuwanmu ba,gidan ma a garƙame muka same shi da ƙaton ƙwaɗo,".   dakatawa yayi da yin maganar, Hakan yasa Abusufyan cewa"dama nasan bazai tsaya ba,guduwa zai yi,"   Girgiza kai Baban sadeeq ya ɗan yi tare da cewa"A'a,bana tunanin ya gudu,Munafukin duk inda yake yana acikin garin nan!yanzu haka ba mamaki yasan da zuwanku!ae ba ƙaramin shu'umin mutun bane,"   "Amma taya akai kasan cewa,yana acikin garin nan?ko kun ƙara haɗuwa dashi ne"?acewar Abusufyan,   Baban sadeeq yace"ƙwarai kuwa!Kama tuna min!ae can shekarun baya lokacin da aka nemi abu aka rasata,fitsararran ya tako da waɗannan ƙafafuwan nashi masu kama dana zabbi har ƙopar gidana,   Lokacin na dawo daga sallar asuba,na shiga da mashin cikin gida,nadawo zan rufe ƙopa kenan ina ƙokarin rufewa,Naji an banko mun ƙopar,A firgice na kai idanuwana wurin don inga wani taƙadirinne!aikuwa sai nayi tozali dashi,A tsaye ruƙe da qugu,nan fa nashiga faɗin A'uzubillahi minasshaiɗanir rajim,"sai cewa yayi"Ni ne shaiɗanin"?nace mashi "to ae baku da bambanci da shaiɗan,ƙahonne kawai ke babu!shin me ma yakawo ka ƙopar gidana?ko kazo ne kayi mun futsarar taka daka saba ne?sai yace mun saƙo ne yazo dashi,nace saƙo kuma?yace mun eh,yasa hannu cikin aljihun jallabiyarshi ya zaro wata ƴar doguwar takarda,ya miƙo mun tare da cewa"Saƙon Abu ne,idan mun sameta,A bata wasiƙar," jin cewa sakon na abu ne yasa na amsa,to tun daga wannan lokacin da ya haura ƙafa,ban ƙara sanya sayyadi acikin idanuwana ba,hatta makarantar islamiyyar da muke koyawa atare dashi,ya daina zuwa...."   Lokacin da ya kai ƙarshen labarinshi,Abusufyan yace"Amma kun karanta wasiƙar"?   Baban sadeeq yace"A'a,babu wanda ya ta6a ta,Ae amana ce,yace wasiƙar ta abu ce shiyasa bamu karantata ba,"   A ƙagare Abusufyan yake daya ga wannan wasiƙar,    "Yanzu wasiƙar tana ina ne"? "Tun lokacin dai,bayan tafiyar sayyadi,dana shigo cikin gida,kaitsaye wurin Maman Sadeeq na wuce,ita nabawa ajiyar wasiƙar,"   Ajiyar zuciya Abusufyan ya sauke,   "Gobe,in Allah ya kaimu,sai muje gidan a ɗauko wasikar,yau dai anan zaku kwanan mana,"acewar Abusufyan,    "Akwai yaronmu fa,mun barshi a gida,"Baban Sadeeq ne yayi maganar, "idan mun fita yin sallah,sae mu dawo tare dashi," acewar Abusufyan   Suna cikin tattaunawar nan aka kira sallar isha'e,atare suka fita yin salla daga can zasu wuce gidan,Su ɗaukko Sadeeq, Fitowa Sehrish tayi daga Bedroom ɗin Oummansu,wuraren ƙarfe 8:30 na dare,a palour ta samu Maman sadeeq zaune,jikinta sanye da hijabi,   Tana ganin Sehrish ta mike,tare da tunkararta,   "Rishi,zonan mana,baki bani labarin ya kuka ƙare ba,bayan kun bar nan"tayi maganar tare da ruƙo hannunta,saman 3 seater suka zauna,   Nan fa Sehrish ta shiga bata labarin rayuwarsu,tun daga lokacin da suka koma katsina har ƙarshe,jikin Maman Sadeeq ba ƙaramin sanyi yayi ba,jin irin wahalar da suka sha,ta wani 6angaren kuma ba ƙaramin farin ciki tayi ba,  sun jima suna firar yaushe rabo,kafin suyi sallama kowa ya wuce ɗaki,don ba ƙaramar gajiya suka kwaso ba, Koda Sehrish ta koma ɗaya daga cikin bedrooms ɗinsu da aka gyara masu,wanda ke a upstairs,toilet ta shiga don ta watsa ruwa ajikinta,kafin ta kwanta,Maman sadeeq kuma a downstairs ta zauna,ɗakunan su Dr haris a lokacin baya,    fitowa tayi daga cikin toilet,jikinta sanye da undi ta ja shi har saman kirjinta,ƙarasawa tayi gaban gadon,inda ta ajiye kayan baccin da ta dauko don ta sa,tare da phone ɗinta,   Tana ƙoƙarin kai hannu ta ɗauki wayar,Ta jiyo sautin dirar mota acikin gidan,   "Su Daddy sun dawo kenan"tayi maganar tare da ɗaukar wayar,Har lokacin fuskarta ɗauke da murmushi,bakinta fa ya ƙi rufuwa tunda aka samu Oummansu,babban burinta yanzu bai wuci Oummansu ta dawo cikin hayyacinta ba,waƙa ta kunna ta ƙure Volume,Nan fa ta shiga yin rawa,kamar wata zautacciya,juyi ta dinga yi,iska na kaɗa gashin kanta,duk cikin farin cikin ne,yaushe rabon da tayi dancing irin haka harta manta,dama can ita ba ma'abociyar yin rawa bace,duk da tana son yin rawar,yanayin rayuwane yasa bata samu wannan damar ba,a hankali ta soma bin wakar abakinta, _rawa da girgiza zanyi gabanka,in jujjuya,zanyi maka albishir kayi dace da mai tarbiyya,sannan zan zame maka farin ciki na nan gidan duniya,Nafi kowa saninka acikin abunsha kafi son coffee_ Bata ƙarasa baitin ba,ta tsaya cak sakamakon mutun da ta hango tsaye ta cikin mirror,ya goya hannayensa asaman wide chest ɗinshi,gabanta ne ya faɗi rass,lokaci guda ta shiga taitayinta,duk tabi ta kame kanta kamar wata mara gaskiya, Bakowa bane fa ce Sgr,still dress ɗin ɗazu ne ajikinshi,tun lokacin da ta fara rawar yazo ɗakin,kuma ta hanyar kiɗan wakar da ta kunna ne yasa ya gane cewa akwai mutun a ɗakin,dama kuma ita yake nema saboda ya tayata Murnar ganin mahaifiyarta, tsayawa su kayi suna kallon juna ta cikin mirror,kunya duk ta rufe ta,saboda ɗan undi ɗin dake ajikinta sharara yake,gashi ko bra bata sanya ba, Slowly ya soma takowa izuwa cikin ɗakin,da sauri Sehrish ta nufi wurin gadon tana ƙoƙarin ɗaukar Kayan sawarta,da ta ajiye asaman gadon, Sai dai kafin tayi wani yunƙuri tuni Sgr ya ƙaraso wurin,at same time suka kai hannu saman kayan nata gabanta ne ya faɗi rass,yayin da take kallon hannunshi da ya ruƙo rigarta,a ɗan razane ta cire hannunta tare da ɗan ja da baya tana kallonshi, ɗagowa yayi hannunshi ruke da kayan sawar nata yace"Me zaki yi dasu"? Muryarta na kerma tace"Am..um..sanyawa..zanyi,' Da buɗar bakinsa sai cewa ya yi"bayan na kammala abunda zanyi kenan"? Gabanta ne ya kuma faɗuwa,throwing ɗinsu yayi saman gadon,gadan gadan ya tunkareta,jiki na rawa ta shiga ƙoƙarin ja da baya,muryarta na rawa tace"Dan Allah babban yaya kayi haƙuri,wlh bazan ƙara tafiya ba,without ur permission nasan nayi maka laifi,"ita duk a tunaninta,yazo ne ya yanke mata hukunci,saboda zuwan da tayi kano batare da saninshi ba, "Am sorry Ya Rafayet.."wani irin kallo yake bin ta dashi,wani canji ya fara gani ajikinta,kaitsaye take fisgarshi,sai ƙokarin motsa lips ɗinsa yake yi don ya sanar da ita cewa,ba hukunta ta yazo yi ba,yazo ne don ya tayata murna,Amma ina,sam ya kasa furta hakan,duk zufa ta gama wanke mata fuska,har idanuwanta sun cicciko tab da kwalla, Hannayensa ya sanya asaman belt ɗin wandon jikinshi,Waro ido waje Sehrish tayi,hankalinta yayi mugun tashi,tsoronta kar ace bugunta zai yi, Fashewa tayi da matsanancin kuka,tare da aza hannunta asaman kanta,tana faɗin"Innalillahi,wayyo Allah na," Da gangan Sgr yake zame belt ɗin wandonsa,duk don saboda ya ƙara ruɗar da ita,lokacin da ya ƙare zare belt ɗin daga jikin wandon ya curoshi yana nannaɗe shi a hannunshi,A matuƙar tsorace sehrish ta juya da nufin ta gudu,Da ƙarfi ya kai hannu zai ruƙo undi ɗin jikinta,aikuwa gaba daya,Ya zame undi ɗin daga jikinta ya sulale,kasa gashi bata sanya komai ba,babu pant bare bra,saboda tsabar kiɗima,fasa ƙara tayi sosai ta fashe da kuka,tare da ƙanƙame ƙirjinta da hannuwanta,bangon ɗakin ta ƙankame jikinta na kerma, Duk wannan budirin da akeyi babu wanda yasan meke wakana,saboda sun yi nesa da downstairs, Rumfa yayi mata da faffaɗan ƙirjinshi,ya lullu6eta sosai,nan take taji wata irin natsuwa tazo mata,daddaɗan ƙamshin turarenshi ne ya mamaye hancinta,lokaci guda ta nemi kukan da takeyi tarasa, "Ain't trying to flog u,"ya furta hakan da wata irin kasalalliyar murya,saboda tsabar rawar da jikinta keyi,har a jikinshi yake ji, duƙo da kanshi yayi dai dai saitin wuyanta,slowly ya manna mata kiss,har cikin zuciyarta taji wannan kiss ɗin nashi,kafin tayi wani yunƙuri,taji tafin hannunshi asaman ass ɗinta,laushin fatar wurinne ta soma fisgarshi,har ya fara shafata yana matsarta,almost 3 mins kafin ya zame hannun daga wurin,ya zagayo dasu ta front ɗinta,sosai yayi tighting ɗin ta ajikin wall ɗin kamar zai mayar da ita,cikin cikinshi,lokacin da taji hannunshi saman gabanta,gaba daya tabi ta susuce,ta shiga ƙoƙarin kufce mashi,ruƙon da yayi mata ne yasa ta kasa yin hakan,sosai ya shiga shafa wurin before ya janyo tafin hannun nashi izuwa saman ƙirjinta,duka hannunshi biyu ya sanya,duk irin girman tafin hannunshi,sai da boobs ɗinta suka cika su fam,har babu space,damƙarsu yayi sosai tare da runtse idanuwanshi saboda wani irin yanayi da ya fara tsintar kanshi aciki,muryarshi na kerma ya ambaci sunanta"Reesh.."for the first time da Sgr ya fara furta sunanta,tunda take yi mashi aiki bata ta6a jin ya ambaci sunanta ba,tamkar baima san sunanta ba,sosai ya cusa hancinshi acikin lallausar sumar kanta,batare da ya saki ƙirjin nata ba,da alama fa Sehrish suman tsaye tayi,gaba ɗaya sun shiga cikin wani irin yanayi mara misaltuwa,sautin kiɗan da sehrish ta kunna ne ya ƙara jefasu cikin wani yanayin na sha'awar son kasancewa da junansu,Taken waƙar Love Nwantiti ya shiga,baka jin komai sai sautin breathing dinsu dake fita da zafi zafinshi,yayin da heart ɗinsu ke beating very fast at same time,tamkar zata 6allo daga ƙirjinsu,Ya salaam! *Boss Bature* A 6angaren su Junaid kuwa,sunsha yawo shi da Jahad,wuraren 8 suka kamo hanyar zuwa gida,bacci cike da idanuwansu,driving yake yi slowly kamar baison yin tuƙin, Muryarshi tamkar zai yi kuka yace"Jahad,mun ci komae amman bafa musha ice cream ɗin ba" "Mu haƙura Junaid,hankalina ya koma kan gida,dare yayi yakamata ace tun 6 muna a gida," ..."Jahad,nidai inaso nasha,na kuma baki,saboda shi na fito ma ni," "Asthma fa gare ka,ko ka manta ne?ni bazan so abunda zai cutar mun dakai ba," Tana kai ƙarshen maganar taji,ya dakatar da motar a gefen titi, Juyawa tayi tare da kallonshi,tun kafin ta tambayi dalili yayi saurin cewa"Ga mai ice cream can tsallaken titi,ki jira ni a mota yanzu zanje nadawo,if not wlh bazan yi driving ɗin ba,"zuba mashi ido tayi tana kallonshi, Ashagwa6e ya kuma cewa"kin yi shiru baki ce komai ba, Murmushi ta ɗan saki tare da cewa"Kada ka damu my Romeo tunda kana so,Ni zanje na siya mana ice cream ɗin,ka jira ni a mota,naga kaman bacci ma kake ji,yanzun nan zan dawo,"ta ƙarasa maganar tare da ruƙo ƴar purse ɗin ta, Tana ƙoƙarin fita daga motar,taji ya ruƙo rigarta,tsayawa tayi cak,hakanan ta dinga jin zuciyarta nayi mata wani irin bugu mara daɗin ji, Juyowa ta ɗan yi tare da kallonshi,lumshe idanuwanshi yayi tare da buɗesu,da wata irin murya tamkar bata shi ba,ya furta mata"I LOVE U SO MUCH," har cikin zuciyarta,taji wannan kalamin nashi,dawowa tayi kusa dashi,tare da tallabo fuskarshi ta manna mashi kiss a gefen fuskarshi,tana ƙoƙarin janye la66anta,ya ruƙo waist ɗinta sosai,tare da haɗa bakinsu wuri guda,a susuce suka shiga kissing ɗin junansu sosai,almost 10 mins,kafin jahad ta janye jikinta daga nashi,da sauri ta buɗe murfin motar,ta fita daga cikinta, Tsallaka titin tayi tana tafiya tana waiwayon motarsu,wurin mai ice cream ɗin taje,mutun huɗu ta samu a tsaye suna jiran ya zuba masu,hakan yasa ta ɗan tsaya tana jiran a sallamesu itama a bata nata, "Jahad,"Junaid ne ya kwala mata kira,daga cikin motar,da sauri ta juya tana kallonshi dayake akwai hasken Street light daya haskaka titin, ɗago mata hannu yayi fuskar nan tashi ɗauke da ƙayataccen murmushi,dimples ɗinshi sun lotsa sosai, Murmushi ta sakar mashi itama,sai faman kallon juna suke yi, ..."madam guda nawa za'a baki ne"?muryar mai siyar da ice cream ɗin ce ya katse ta,juyawa tayi tare da kallonshi tace"Guda biyu nake so," Yana cikin zuba mata Corn Ice cream ɗin,ƙarar truck ta karaɗe wurin,Wata jibgegiyar mota ce,gadan dagan ta tunkari motar da junaid ke ciki, Adai dai lokacin mai ice cream ɗin ya sallameta,har ta biyashi kuɗin,tun kan ta juya mai ice cream ɗin nan ya furta"Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un!"a wani firgice jahad ta juya don taga menene ke faruwa,Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,A gigice ta fasa wata irin ƙara mai sautin gaske lokaci guda tayi wurgi da ice cream ɗin dake a hannunta,A zabure ta tunkari wurin da motar junaid take,Sai dai kash ƘADDARA TA RIGA FATA, Don tuni Motar nan,tabi ta kan motar junaid,Gaba ɗaya ta danne motarshi,tayi mata rugu rugu, Da gudun gaske mutane suka taru a wurin suna faman ambaton INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIRRAJI'UN!!!😭😭😭😭 *kullu nafsin za'ikatul maut* 💋Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* SADDEST MOOD, THE Greatest Lost, Gingimarin motar nan,na sauka daga kan Motar junaid,drivern dake tuƙinta ya fusgeta da gudun gaske ko waiwaye babu,kafin mutane suyi wani yunƙuri motar junaid ta kama ci da wuta tamkar Bomb ne ya fashe a cikinta, Wata irin razananniyar ƙara jahad ta fashe da ita,cikin fitar hayyaci ta nufi motar zata faɗa ciki,Mutane duk suka rurruƙeta,kuka takeyi kamar ranta zai fita,idanuwanta sunyi jawur dasu,jijiyoyin wuyanta duk sun firfito waje,Cizo da yakushi ta dinga kaiwa hannun mutanen dake rurruƙe da ita,muryarta adisashe take fadin"Junaid!yana cikin mota!dan allah kada ku bari na rasa shi!dan Allah ku ciro mun ɗan uwana!ina jin sautin kukanshi acikin kunne na,Dan Allah kutaimakeshi wuta tana ƙona sassan jikinshi........"tana kai ƙarshen maganar,ta yanke jiki ta faɗi asume,Mutane sunyi ƙoƙarin kashe wutar amma sai dai kash babu ruwa a kusa,lokacin da motar ƴan kwana kwana ta ƙaraso,tuni Motar junaid ta ƙone ƙurmus,Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Motocin Ƴan sanda ne suka zagaye wurin,tare da ƴan kwana kwanan,sun kashe wutar dake ci a motar tashi but unfortunately,basu samu komai ba dangane da junaid,domin kuwa ya ƙone ƙurmus,sai dai toka,wa'iyazubillah,  Ƴan sandan Sun samu bayani a wurin mai siyar da ice cream ɗin nan,saboda agabanshi komai ya faru,kuma shi ne ya kira Police men ɗin,da kuma motar kwana kwanar ya basu address ɗin wurin, A bincikensu sun gano cewa,koma waye da gangan ya aikata hakan,saboda guduwar da yayi batare da ya tsaya ba,   Ambulance suka kira,aka shigar da jahad cikin motar,kai tsaye suka wuce da ita,asibiti,    Cigaba da bincike ƴan sandan sukayi,ko'ina na wurin suka shiga dubawa,Anan suka samu ƴar purse ɗin jahad,tare da takalmanta,sae kuma ice cream corn ɗin da tayi wurgi dashi, ..wani Inspector ne ya ɗauki,purse ɗinta,ya zaro wayarta,dake ta ringing acikin jakar,Duba screen ɗin wayar yayi,Sunan Ya Omar ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,picking Call ɗin yayi yasa ta Hands free tare da kara wayar a kunnansa,   "Jahad kuna ina ne!har yanzu baku dawo gida ba?nayi trying number ɗin Junaid,but na same ta a kashe," runtse ido ɗan sandar yayi,jikinshi ba ƙaramin sanyi yayi ba,    "Jahad!"Omar ne ya sake kiran sunanta,   Sai lokacin inspector ɗin yace"kana magana da Inspector Mukhtar ne!yarinyar da ka kira wayarta,yanzu haka an wuce da ita asibiti ne,sakamakon motar da suka hau tare da ɗan uwanta,ta hadu da hadari......" Saboda tsabar kiɗima,marshal Omar dake tsaye gaban mirror baisan lokacin da ya saki wayarshi ba,ta faɗi ƙasa,idanuwanshi azazzare yake kallon kanshi ta cikin mirror ɗin gabanshi,tuni jikinshi ya soma kerma kaf kaf kaf,   Saboda tsabar kiɗima hanyar fita daga dakin ya nufa daga shi sai short ajikinshi,sae da ya ruƙo handle ɗin kopar sannan ya tuna cewa babu kayan mutunci a jikinshi,komawa yayi a hanzarce ya ɗauko jallabiya ya zura ajikinshi,sannan ya dauki wayarshi,   Gudu gudu sauri sauri haka ya nufo downstairs,Mojar ya kira a waya tunkan yabar falon,ya sanar dashi cewa,An samu matsala su kasance cikin shiri zasu fita, Da gudun gaske,motoci goma sha biyar na sojoji suka fuce daga cikin gidan,tare da wata irin jiniya mai sautin gaske, Tracking layin Jahad su kayi har suka ƙaraso inda Motar junaid take,tunkan su fito daga cikin motar jikin kowannansu,yayi mugun sanyi, A wani irin sukwane marshal Omar ya fito daga cikin Motar,da sauri mutane suka dinga darewa suna basu hanya don su wuce,Lokacin daya ƙarasa wurin da motar junaid take a ƙarmashe,ta lanƙwashe ta dagargaje,Jikinshi a mace ya zube saman guiwowinshi,komai ya tsaya mashi cak!tsit kake ji,   Girgiza kai ya shiga yi da wata irin razananniyar murya ya shiga faɗin"innallillahi wa'inna ilaihirraji'un"!hannu yasa ya damƙi tokar dake a ƙasan wurin,Nan take ya fashe da wani irin matsanancin kuka,hawaye ne suka soma gangarowa asaman fuskarshi Major dake tsaye akansa,haka zalika sauran Soldiers ɗin dake a wurin kowannansu,idanuwansu cike taf da hawaye,tunda suke a rayuwarsu basu ta6a ganin hawayen Marshal ba sai yau,    Cikin shessheƙar kuka ya furta"ku faɗamun meya faru dasu?ina ƙanina yake?Ina jahad"?   Daƙyar ɗan sandar nan ya iya buɗe baki yace"Yalla6ai,A bayanan da muka samu a wurin mai siyar da ice cream ɗin da yarinyar taje,Sun tsayar da motarsu a bakin titin ne,ita yarinyar itace ta fito daga cikin Motarsu,tabar shi Yaron acikin Motar,ta tsallaka titi,kafin ta dawo ne,babbar mota tabi takan Motar,nan take kuma ta kama da wuta,koda muka iso bamu samu komai daga sassan jikinshi ba,    Hannu Marshal Yasa ya tallabe kanshi,saboda wani irin jiri dake ɗibarshi,sai faman ambaton innalillahi wa'inna ilaihirraji'un yakeyi,Yanke jiki yayi ya faɗi ƙasa a sume, "yalla6ai!"major ne ya ambaci sunanshi da ƙarfi,tare da zuƙunnawa agabanshi,   Suna cikin wannan alhinin saiga Motar journalists ta ƙaraso wurin,aikuwa tun kafin ma su sauko daga cikin motar,sojojin nan suka koresu daga wurin,a hanzarce suka ja motarsu suka koma,   Sau uku suna yayyafa mashi ruwa,yana sake sumewa,hakan yasa suka cuccu6eshi izuwa cikin Motarsu,don su wuce dashi asibiti, Jami'an ƴan sandar nan,sunyi ƙoƙari wurin ganin sun gano yadda abun ya faru,har street Cctv aka bincika,amma kash Camera ɗin ta jima da samun matsala,   *Allah yajiƙan junaid,ya gafarta mashi,mutun mai kyakkywar zuciya irinta junaid,munayi mashi fatan dacewa don yayi mutuwar shahada,bawan Allah naji mutuwarshi sosai,don har hawaye saida na zubar,akan laifin da bashi ya aikata ba,Anyi silar mutuwarshi,saboda Soyayyar da akeyi mashi itace taja mashi,babu komai,wanda sukayi silar mutuwar tashi kowa zai ɗanɗani kuɗarshi ne,masu cewa junaid yayi azkhar da addu'a before ya fita,kada ku manta,idan lokacin mutun yayi koda sallah yake cikin yi ko agaban ka'aba ne hakan bazai hanashi mutuwa ba,yakamata mu tuna da wannan,bawa bai isa ya gujewa ƙaddararsa ba,ko da yayi addu'a in dae anan ajalinsa yake dole ya mutu ba makawa😭*   *Boss Bature* Rishraf, Gabanshi ne yaji yayi wani irin bugu,ba arziƙi ya zame hannunshi daga saman ƙirjin sehrish,ja da baya yayi,yayin da hannunshi ke dafe da saitin zuciyarshi,hankalin shi yayi mugun tashi,lokaci guda ya rasa natsuwarshi,da sauri ya fuce daga ɗakin,hakan yaba Sehrish damar motsawa,ta ɗauki undi ɗinta dake ajiye a ƙasa,ta sanya ajikinta,wata irin kasalace ta baibayeta ga wani irin faɗuwar gaba da take ji,daƙyar ta lalla6a ta haye saman gadon ta kwanta,hannunta rungume da pillow, Saukowa downstairs,yayi hannunshi na kerma ya zaro wayarshi,yama rasa wa zai kira gida,yaji kowa yana lafiya,ko wani abu ya faru ne?don yanaji aranshi cewa,Something is wrong,that's why yake jin bugun zuciyarshi na ƙaruwa,   Layin Marshal Ya kira,a lokacin wayar na a hannun Major,koda yaga kiran Sgr,ƙin ɗaga wayar yayi saboda baisan taya zai fara sanar dashi ba,game da mutuwar junaid, Almost 3 times,wayar na ringing ba'ayi picking ba,layin junaid ya lalubo ya danna mashi kira,lokacin da aka sanar dashi cewa layin daya kira a kashe yake,nan fa hankalinshi ya ƙara tashi sosai,saboda tunda yake a rayuwarshi bai ta6a samun layin junaid a kashe ba sai yau,a ruɗe ya danna ma Abbansu kira,tana fara ringing,Abbansu ya ɗaga tun kafin ma yayi mashi sallama,muryar Abbansu ta katse shi da cewa"Rafayet!wai meke faruwa ne?ina ta kiran Layin junaid akashe!hankalina yaƙi kwanciya,"   Muryar Sgr,a kasalance yace"Daddy,i don't know why nima na kira layinshi,switched off,Na kira layin Omar ma,tayi ringing ba'ayi picking ba"   "Dan Allah rafayet,ka bincikamun meke faruwa a gidan nan,Hankalina bazai kwanta ba,in har banji muryar baby junaid ɗina ba,wlh har bacci ya fara ɗaukata amma na farka,saboda nasama raina zai kirani ne kamar yadda ya saba kirana,duk in dare yayi kafin ya kwanta,"acewar Abbansu,   Jikin Sgr ba ƙaramin sanyi yayi ba,daƙyar ya iya cewa"In sha Allah daddy,zan yi ƙoƙari na haɗa ka dashi,"   Daga haka sukayi sallama,zarya ya shiga yi acikin falon gidan,tunanin zuwa Abuja yake yi,don ji yake in har bai sanya junaid a idonshi ba,to hankalinshi bazai kwanta ba, Ranshi ne ya bashi cewar,ya jaraba kiran layin Haroon may be,yana a gidan,can kuma ya soma tunani Anya ma yana da numbar haroon?tabbas baida ita,layin Major ya kira kaitsaye don ya samu ya haɗa shi da Omar,tunda na hannun daman shi ne,   Lokacin da kiran ya shiga wayar major,suna tsaitsaye cirko cirko a cikin asibitin Sgr,Yana ganin sunan Sgr ya bayyana akan screen ɗin wayarshi,jiki na rawa ya kashe wayar gaba ɗaya,   Abun ba ƙaramin ɗaurewa Sgr kai yai ba,kowa ya kira ba'a picking,shi Major ma kiran ya shiga,daga baya kuma aka kashe wayar,hakan ya ƙarasa shi zargin cewa wani mummunan abunne ya faru,   Komawa Upstairs yayi da sauri bedroom ɗin da Sehrish take ciki,tura kopar yayi ya shiga,a kwance ya sameta rungume da pillow,    "I know u are awake,inaso ki kiramin layin wani daga cikin sisters ɗinki,i wanna talk with them "   Yunƙurawa sehrish tayi tare da kai hannu ta ɗauki wayarta da ta aje gefenta bayan ta kashe wakar,layin jahad ta lalubo ta danna mata kira,A lokacin wayar na a hannun Major ya kar6eta daga hannun police men ɗin,koda yaga kiran My Own sis ya shigo,ta layin jahad,kin daga kiran yayi har ya yanke,hakan yasa sehrish sake kira,sai ya kashe wayar gaba ɗaya,   ɗagowa tayi tare da kallon Sgr,tun kafin tayi magana,ya riga ta cewa"Switch off ko"?ɗaga mashi kai tayi alamar eh,tare da cewa"Bari na kira layin Hosana,"   Numbar hosana ta lalubo,tare da danna mata kira,tana fara ringing hosana ta ɗaga kiran,muryarta da alamun bacci atare da ita,    "Wai wanene ke kira na"? Sehrish tace"ke nice,Ina jahad ne na kira layinta a kashe"?    Hosana tace"tun ɗazu da suka fita da junaid shan ice cream basu dawo ba,inata jiransu har bacci ya ɗauke ni,"kafin Sehrish ta ƙara cewa wani abu,da sauri Sgr ya sanya hannu ya kar6e wayar,   tare da karata a kunnansa"Ina Omar yake"?rass taji gabanta ya faɗi,daga kwance take,amma jin maganar babban yayansu yasa ta miƙe zaune,anatse tace"Wlh bansan inda yake ba,ko yana gida ko yana waje oho,ni dai ina ɗakinmu,"    "Go to his bedroom right now,and see if he's around," Mikewa hosana tayi tare da saukowa daga saman gadon,gudu gudu sauri sauri ta wuce upstairs bedroom ɗin Omar,a buɗe ta samu ƙopar,turawa tayi ta shiga daga ciki,ko'ina ta duba,hada leƙa toilet ɗinsa,ganin babu kowa yasa ta sanya wayar a kunnanta,   "Ya Rafayet,na duba ko'ina,amma banga ya Omar ba,"   "Its okey,ki koma ɗaki,"yana faɗin hakan ya katse kiran,   ɗagowa yayi da lumsassun idanuwanshi masu ɗauke da bacci ya kalli Sehrish itama kallon nashi takeyi,duk jikinsu yayi sanyi mika mata wayar yayi"take ur phone,"hannu tasa ta kar6a,   Da sauri ya juya,jikinshi duk babu ƙwari a lokacin idonshi ya sauka kan belt din shi dake akasa,hannu yakai ya dauka ya fara kokarin maida shi jikinsa tare da fucewa ya nufi downstairs,a dai dai lokacin Abusufyan na fitowa daga ɗakin da suka kwantar da Abu,jikinshi sanye da jallabiya,   Yana jin takun takalmi,yakai idanuwanshi wurin,yana ganin Sgr ya tunkareshi da sauri,   "Rafayet!wai kunyi waya da Junaid ne?i ave been trying his phone number,Amma akashe!nayi traying har nagaji,since evening ya sanar dani cewa,zasu fita tare da jahad shan ice cream,inaso naji ko sun koma gida,itama kuma phone dinta akashe"   Ƙarasa saukkowa daga saman benen Sgr yayi tare da kallon Uncle ɗin nasu yace"Uncle nima bansan meke faruwa ba,kowa na kira layinshi switched off,babu mai picking call ɗina,That's why na yanke shawarar zuwa Abuja yanzun nan zan bi jirgi naje can," ya ƙarasa maganar yana ƙoƙarin wucewa ta gefen Abusufyan,da sauri ya ruƙo damtsen hannunshi tare da cewa"A'a Rafayet!ka haƙura sai gobe mana ka wuce can ɗin,"acewar Abusufyan Girgiza kai ya shiga yi tare da cewa"Bazan iya jurewa ba,inaso nasan meke faruwa ne acan ɗin,na damu akan rashin jin muryar Junaid,daddy ma ya kira ni yanzu,yana cikin damuwa,ko don saboda shi inaso naje can na haɗashi da junaid,if not ko bacci bazai iya yi ba,tunda ya sama ranshi son jin muryar junaid,"   "Zanyi magana da yaya hossein ɗin,ka ajiye tafiyar nan dare yayi,sai zuwa gobe da asuba,"   Ba don ya so ba,a dolenshi ya haƙura,komawa sukayi saman sofa suka zauna jigum jigum,Suna jiran tsammani,kowa da abunda yake saƙawa acikin ranshi,   *HAROON* Around 12 na dare,Yana zaune gefen gadonshi,message ya shigo wayarshi,da sauri yakai hannunshi ya zarota daga cikin trouser pocket ɗinsa,buɗe message ɗin yayi ya soma karanta shi kamar haka,    _Oga Aiki ya kammalu fa!ka duba whatsapp ɗinka,mun tura maka video zazzafan gaske,nasan yau zakayi kwanan farin ciki_   Shu'umin murmushin nan nashi ya saki,jiki na rawa ya shiga whatsapp ɗinshi anan ya samu Video ɗin da suka tura mashi,bayan ya kunna Wi-fi ɗin wayarsa,tunkan video ɗin ya ƙarasa yin loading jikinshi keta tsuma harya ƙagara yaga Videon menene,   Ƙura ido yayi akan screen ɗin wayar,lokacin da video ɗin ya buɗe,motar Junaid ya gani tana ta ci da wuta,ta lomatse ta rakwakkwa6e,Wani irin ihu ya fasa cike da tsantsar farin ciki ya miƙe tsaye yana faɗin"Yess!Yess!!finally Burina ya cika,ko ayanzu na mutu nasan cewa,na gama dasu,na kashe farin cikin da suke taƙama dashi!" Ya ƙarasa maganar tare da fashewa da wata irin mahaukaciyar dariya,lokaci guda kuma ya dakata da yin dariyar,jikinshi ya soma kerma sakamakon Muryar junaid da tayi mashi gizau acikin kunnanshi    _Ya haroon!burinka ya cika ko?ka rabani da rayuwata,laifin me nayi maka?menayi maka dana cancanci wannan ɗanyen hukuncin a wurinka!yanzu shikenan bazan sake ganin ƴan uwana ba?ka rabani da mahaifina kuma kana farin ciki?haƙƙina bazai ta6a barinka ba_   A tsorace Haroon ya shiga waige waige a cikin ɗakin nashi,ba ƙaramin razana yayi ba,ganin baiga kowa ba,yasa shi sauke ajiyar zuciya,   ɗago da wayarshi yayi tare da Calling layin waɗanda yasa su kashe mashi junaid,tana fara ringing aka ɗaga kiran,   Muryarshi asanyaye yace"dagaske ne video ɗin da kuka turomin cewa kun kashe junaid"?   On the other hand,mutumin yace"ƙwarai kuwa!Yaron nan babu shi yanzu a doron duniyar nan!domin kuwa da truck muka take motarshi,bayan mun tabbatar yana acikin Motar,Amma ita yarinyar bata acikin motar kamar yadda ka bamu umarni,ta tsallaka titi zata siya masu ice cream......"   Tunkan ya ƙarasa maganar,haroon ya zube saman guiwowinsa,wata irin zufa ce ta shiga tsatstsafo mashi ajikinshi,tuni ta wanke shi sharkaf,   "Ya Haroon!Kamar baka farin ciki?naji kayi shiru"?   Kasa buɗe baki haroon yayi,la66ansa sae kerma suke yi,   "Hello!hello!Oga haroon!kana a kan layi kuwa"?jin shiru bai tanka masu ba yasa suka katse kiran,   Jikin taƙaura yayi la'asar,gaba ɗaya haroon ya shiga ruɗani,Shin farin ciki yake yi da mutuwar junaid ko kuwa baƙin ciki?Tun yanzu ya fara tsorata da gizan da muryar junaid tayi mashi,   _Laifin me junaid yayi mun?na kasa yarda cewa ni da kaina na bada umarnin a akashe shi_   Runtse idanuwanshi yayi sosai,yana tariyo fuskar junaid,mai ɗauke da kyakkyawan murmushi nan nashi,   Guiwowinsa duk sun sage,ya kasa miƙewa tsaye,yayi fiye da awanni zuƙunne batare daya motsa ba........ *AUNTY BABBA* Tun bayan da Abra ta gudu daga hotel ɗinnan,Tana fitowa daga wanka,jikinta ɗaure da towel,sam bata kawoma ranta komai ba,duk da tayi mamakin ganin babu kowa,Jinjina kai ta shiga yi tana faɗin"Ko gidan ubanwa taje?bayan na sanar da ita cewa Yanzu zamu tafi,zata dawo ta same ni,"ta ambaci hakan tare da samun wuri gefen gadon ta zauna,tun tana sa ran dawowar abra har ta fara fidda rai,tunawa da abunda ya faru da hayaam a hotel yasa hankalinta ya tashi,tsoranta kar ace itama abra,an samu wani ya ƙurmushe ta ne,hakan yasa tayi firgit ta miƙe tsaye,tare da kai hannu saman bedside drawer ta ɗauki wayarta dake ajiye a samanta,   Yanke shawarar kiran Abra tayi,tun kafin ta shiga Contacts ɗinta,saƙon abra ya shigo cikin wayar,on the top of screen ɗin wayar,   Janyo saƙon tayi ta buɗeshi,a tsanake ta soma karanta saƙon   _Aunty laila sai dai kiyi haƙuri,wlh bazan iya zuwa wurin bokan nan ba!saboda ƙaryar da kika yi mun dangane da hayaam,ashe Aunty hayaam tana kwance rai hannun Allan agadon asibiti,amma kika gudu kika barta saboda kawai tsautsayi ya same ta?ashe dama amfani kike yi damu don ki cimma burinki!baki damu da rayuwarmu ba,Naji tsoro ne saboda nasan cewa nima wata rana in irin hakan ta faru dani zaki gujeni ne,ina mai baki haƙuri Aunty laila,bansan ya rayuwarki zata ƙare ba a Enugu,domin kuwa na kwashe duk wasu kuɗi da muka zo dasu,Na tafi da handbag ɗinki gaba ɗayama,kada ki sha wahalar nemanta Aunty hayaam da aunty Amani ne suka sa nayi hakan a ƙarshe ina maki fatan sa'a_   Saboda tsabar kiɗima a hautsine ta jefar da wayar ƙasa,Dafe ƙirjinta tayi hankalinta a matuƙar tashe,ta furta"kutumar Uba!Ni Abra zata yiwa iya shege!Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Ya Allah ka rabani da mugun ji da mugun gani!Ya Allah kasa mafarki ne ba gaske ba,Abra ta yashe ni!ta gama dani!na shiga uku na ni yau! Na gama yawo!   Tuni Ido ya raina fata,cizon yatsanta ta shiga yi,tana faman yarfa hannunta,Duk tabi ta ruɗe ta rasa inda zata tsoma ranta,   Zuƙunnawa tayi ta ɗauki wayar da tayi wurgi da ita ƙasa,layin Abra ta kira,unfortunately ta samu wayar akashe!   "Allahumma Ajirni fil musibati wa'aklifni khairan Minha,Meyasa Abra zatayi mun haka!Nashiga uku ni yau,Wannan wata irin Musiba ce!daga wannan sai wannan?"   Hawaye ne suka soma saukowa daga saman fuskarta,a susuce ta shiga faɗin"Wlh baku isa ba!baku isa ku hanani zuwa wurin bokan nan ba!Wlh sai naje,Allah ya isa tsakanina Da Amani!Munafuka duk ita ta shirya mun wannan,Ita kuma waccen kingin gardawan bamma san ya akai ta farfaɗo ba,don nasan itace ta sanarwa Amani har suka shiryamin wannan tuggun,Wlh bazan ƙyalesu ba....."Aunty babba fa ta zare sai faman sakin sambatu takeyi,da alama ta fara zarewa,zagaye ɗakin tashiga yi tana safa da marwa,hannunta asaman kanta,    Yanke shawarar bin bayan Abra tayi,a gaggauce ta buɗe trolley ɗin kayansu,ta ɗauko doguwar riga ta zura ajikinta,Ta yafa mayafi buɗe ƙopar tayi,jiki na rawa,haka ta shiga zagaye hotel ɗin tana neman Abra,har wurin receptionists taje,ta tambayesu ita,hada yi masu kwatancenta anan suka sanar da ita cewa,sunga gifcinta a lokacin da take ƙoƙarin barin reception ɗin,Jin haka yasa Aunty babba ta zabura da gudu ta fuce daga reception ɗin ta miƙi hanyar fita daga hotel ɗin,gudu gudu sauri sauri haka ta fita waje gefen titi tana Neman Abra,   Hanya ta miƙa tana tafiya tana sambatu,tana ƙoƙarin ta tsallaka titi wata jibgegiyar Mota ƙirar Range rover tayi Awon gaba da ita,Koda mai motar nan yaga aika aikar da yayi jini har asaman glass ɗin motarshi,aikuwa a hanzarce yaja motarshi da gudun gaske ya bata wuta kamar zai tashi sama yabar Wurin!!!   Aunty babba kuwa sai kwala ihu takeyi tana shure shuren ƙafa asaman titi,    "Wayyo Allah!nashiga uku!na bani Na lalace!Ya kashe ni!Ya gama dani!"   Dandazon mutane ne suka taru a kewaye da ita,sun zuba mata ido suna ta kallonta an ransa wanda zai iya taimaka mata,kowa tsoro yake ji kada ace shine yayi silar mutuwarta,Wannan dalilinne yasa aka rasa wanda zai ta6ata,kuma babu wanda yayi tunanin kiran ƴan sanda don yayi reporting akan Incident ɗin,   Tun tana shure shuren kafarta jini na tsargowa ajikinta,har jikinta ya soma saki alamar rai zai yi Halinsa........ DAMATURU, Wuraren karfe 1 na dare,Abba na zaune zugudum tsakiyar gadonsu ya zabga uban tagumi,zuciyarshi sai bugawa take yi,kwakkwaran juyi Alexandra tayi karaf idanuwanta suka sauka akan shi,da ya ke akwai hasken bedside lamp dake a kunne,muryarta adisashe tace"Abban Junaid!lafiya har yanzu bakayi bacci ba,"? Hankalinshi atashe yace"taya zan iya runtsawa?kullum junaid ya saba kirana a waya da daddare kafin ya kwanta yayi bacci,Amma yau shiru wayarshi a kashe,wayar Omar a kashe,na rasa wanda zan samu a gidan in kira shi don ya sanar dani halin da junaid ke ciki," Jin wannan maganar yasa hankalin Alexandra ya tashi haiƙam,mikewa zaune tayi cike da mamaki tace"nikaina nayi mamakin rashin kirana da junaid,baiyi ba amma ban kawo komai araina ba har bacci ya dauke ni" Abba na ƙoƙarin buɗe baki yayi magana,suka ji an ƙwanƙwasa ƙopar ɗakin nasu, Atare suka haɗa baki wurin cewa"Wanene"? Muryar Twins ce ta amsa masu"Mommy mune," Kallon juna sukayi at same time,kafin Abba yace"Ku shigo ciki," Tura ƙopar sukayi atare suka shiga kowannansu sai faman hammar bacci yake yi idanuwansu a lumshe saboda baccin da suke ji, Aruɗe Alexandra tace"is everything alright twins?me kuke yi har yanzu bakuyi bacci ba"? Ayaan yace"mommy wlh ba lafiya,mun kasa runtsawa saboda yau junaid kwata kwata bai kira wayarmu ba,Ko text message ɗin da ya saba tura mana yau bamu gani ba,kuma mun bibiyi layinshi a kashe,har ya Omar mun kira muji ko lapia shima a kashe,taya hankalinmu zai kwanta,"yana kai ƙarshen maganarshi jahan ya ɗaura da cewa"Mommy,Daddy Ni da Ayaan mun yanke shawarar komawa gida gobe,dan Bazamu juri rashin junaid a kusa damu ba," Tashin hankali,zuba masu ido Sukayi suna kallonsu,kowanne yasha sleeping dress ajikinshi, "Ku zauna"Abbansu ne yayi maganar tare da nuna masu doguwar sofa ɗin dake acikin bedroom ɗin,Zama su kayi kowa fuskarshi ɗauke da damuwa, "Mommy!"gabanta ne ya faɗi jin Muryar fawan,da sauri takai idanuwanta bakin ƙopar ɗakin,shigowarshi kenan,idanuwanshi sunyi luhu luhu dasu,ƙarasa shiga ciki yayi daƙyar yake iya ɗaga ƙafarshi saboda bacci, "Fawan!kaima baka yi bacci ba"?Abbansu ne yayi tambayar, ɗaga mashi kai yayi alamar eh,tare da cewa"Abba,junaid fa?ko wani yayi waya dashi acikin ku?duk yau bai kira ni ba,kamar yadda ya saba,har text yana turamun kullum amma yau shiru,ko ta whatsapp bai turo man ba,da abun na kwanta yanzu na farka still banga sakon shi ba, layinshi ma a switched off,duk na damu wlh,' Tashin hankali,abun fa ya fara basu tsoro,wasa wasa one by one su Irfan kowa ya shiga shigowa ɗakin yana tambayar junaid,dayake family house ne,duka danginsu na 6angaren Mahaifinsu,suna acikin katafaren gidan,wanda ya kasance mallakin kakansu,mijin Ammi, Aranar dukkansu babu wanda ya runtsa,mafi yawancinsu a zaune suka kwana,don sunci alwashin dawowa gida,tun da asussuba,Abbansu yafi kowa ƙagara daya dawo yaga meke faru ne,Ya ƙwallafa rai akan son ganin junaid,don da ace yana da fiffike da ba abunda zai hanashi tashi sama atsakar daren nan yadawo gida! *Allah sarki* Kamar yarda su Abba suka kwana a zaune,haka Sgr da Abusufyan suka kwana a zaune,cikin falon gidan,babu wanda ya runtsa acikinsu,haƙika ba ƙaramin so sukeyi wa junaid ba,Rashin kiran da baiyi masu ba a waya yasa duk sun tashi hankalinsu,inaga sunji mutuwarshi?mezai faru?kowa fa yasha jinin jikinshi, Tunda asussuba Jirginsu Sgr da Armstrong ya ɗaga izuwa Abuja, *Sehrish* Bayan sallar asuba,Sehrish ta koma ɗakin Oummansu,har lokacin bata farka ba,Wuri ta samu saman gadon daga gefenta,ta kwanta abubuwa da yawa suna zuwa mata aranta,ita kanta tasan cewa tayi kewar wasu daga cikin mutanen gidan,musamman Su Hosana da Junaid,da Aunty azmee,kowa missing ɗinshi take yi,gashi batasan ranar da zasu koma gida ba,tana cikin wannan zancen zucin nata,tajiyo muryar Oummansu tana sambatu,tana faɗin"kada a ta6a mun ƴa'ƴana,dan Allah abarmun su,su kaɗai nake dasu,sune dangina,sune komai nawa,' Wani irin farin ciki ne ya lullu6e Sehrish,miƙewa tayi zaune tana kallonta,a hankali ta furta"Oumma" slowly abu ta buɗe idanuwanta,tare da wurgasu kan fuskar sehrish,wani irin kallo take bin ta dashi,kallon tuhuma, Murmushi sehrish ta sakar mata tare da ƙoƙarin miƙa hannu zata shafa gefen fuskarta,aikuwa a tsorace Abu ta miƙe zumbur tana ja da baya,girgiza mata kai ta shiga yi tare da zare mata manyan idanuwanta,wai don kada ta ta6ata,. Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba, "Oumma baki gane ni ba?Ni ce fa sehrish!Rishi ɗinki' A ruɗe ta shirga girgiza kanta tana cewa"a'a a'a Ni bansan wacece ke ba,bake bace rishi ɗina ba,Rishi ɗina ƙarama ce," Cikin sanyin murya Sehrish tace"Oumma kallanni dakyau ki gani,nifa ce rishi ɗinki,nasan bazaki manta da kamannin fuskata ba,na ƙara girma ne kaɗan," Harara abu ta watsa mata,dama tun fil azal abu mace ce mai taurin kan tsiya ga kafiya,tun tana da hankalinta balle kuma yanzu da babu hankalin atare da ita, Zubama juna ido sukayi kowa na kallon kowa,taƙi yarda sehrish ta kusantota,da zarar sehrish ta matsa,itama da sauri zata matsa,ganin ta kusa ƙurewa gadon gudun kada ta faɗa ƙasa,yasa Sehrish ta ƙyaleta, Cikin lallashi tace"Oumma!kin tuna da Hosana?da jahad? Girgiza mata kai tayi alamar a'a,"Ni bansan su ba,Ni ki ƙyaleni bansan kowa ba,ƴa'ƴana na sani Nemansu nake yi,yace zai kashe munsu,dan Allah akawo mun ƴa'ƴana kusa dani," Murmushi sehrish ta saki tana kallonta,tsantsar son mahaifiyarsu take ji kamar kamar me,gashi taƙi bari ko rungumarta tayi, "Kiyi haƙuri kinji,Babu wanda zai ta6a maki ƴa'ƴanki,idan har kika bani dama,Ni dakaina zan kawo maki ƴa'ƴanki," Shiru tayi bata tanka mata ba,Sai ma wani kallo da take bin ta dashi,kallon ban yarda dake ba,wayau zakiyi mun, Jin sallamarsu Abusufyan yasa tayi saurin amsa masu tare da saukowa daga saman gadon,ta fito daga ƙopar dakin,Su uku ne suka shigo,Baban sadeeq tare da Abusufyan sai Sadeeq ɗansu da suka ɗauko jiya,Anan ya kwana gidan, Fuskarta ɗauke da fara'a ta gaisar dasu"ina kwananku?Kun tashi lafiya," Atare suka amsa mata"lafiyalou,Alhamdulillah," "Sadeeq ka ganeta kuwa,"?Baban sadeeq ne yayi maganar yana kallon sadeeq ɗin dake tsaye agefenshi,murmushi ya ɗan saki tare da girgiza kai alamar a'a,yace"fuskarta kamar na santa,amma bazan iya tunawa ba,' Abusufyan yace"Ae zaiyi wuya ya ganeta saboda canzawar da tayi,ba kamar daba da yasanta,yanzu ta ɗan ƙara girma," Baban sadeeq yace"Allah sarki,Sadeeq wannan fa ba kowa bace face daya daga cikin waɗannan ƴan ukun na Wurin abu,waɗanda suke yawan zuwa gidanmu su yini wani sa'in ma harsu kwana," Cike da mamaki Sadeeq yace"Wai su rishi,hosana,da jahad"?sae lokacin ya ganeta,baki asake yake kallonta,don bazai manta lokacin da suke yawon zarya acikin gidansu ba,musamman in yunwa ta addabesu,wani sa'in ma shi Mamansu ke aikawa gidansu ya kai masu abinci idan tajiyo kukansu,da zarar ya kai masu abincin,Jiki na rawa suke kar6a su zauna suna ci,' "Rayuwa kenan,banta6a tsammnin rana irin ta yau ba,gani ga rishi,"tuni idonshi sun ɗan cicciko da ƙwalla,haka itama sehrish ɗin Baban sadeeq yace"ka tuna lokacin da kake kuka saboda mamanka taba su rishi abincinka'? Fashewa sukayi da dariya gaba ɗayansu, Kunya duk ta rufeshi daƙyar ya iya buɗe baki yace"Dan Allah Abba,adaina tuna abunda ya wuce,' "Shikenan tunda haka kake so andaina," Wuce wa Abusufyan yayi cikin ɗakin abu,Baban sadeeq ma ya wuce ɗakin da suka sauka,ya rage daga ita sai Sadeeq atsaye,suna fira, "Yanzu shekarunki nawa'?ya tambaya yana kallonta, Wurga ido ta ɗan yi kamar mai tunanin wani abu,kafin tace"sha takwas kaifa"? Hannu yasa tare da ɗan sosa keyarsa yace"Sha tara," harara ta watsa mashi tana ƴar dariya tace"wlh ƙarya kake yi mun nafa son shekarunka,Allah kamar ma mun girmeka,don ka ganka dogo shiyasa zaka 6oye mun shekarunka ko'? Murmushi ya ɗan saki tare da nuna mata sofa ɗin dake a falon yace"Mu zauna mana,nagaji da tsayuwa,baccin ma bai isheni ba Allah,naji daɗin sanyin nan ba kamar gidanmu ba,fankar ɗakina ma,6eraye sun lalata mun ita,"ya ƙarasa maganar tare da samun wuri ya zauna,itama ta zauna suna fuskantar juna, Sae faman bin falon yakeyi da kallo,ƙasa ƙasa yayi da muryarshi ya ambaci sunanta"rishi," "Na'am"ta amsa mashi "Wai wannan mai mutuncin,mai kama dake ɗinnan Yayanku ne"? "Me hali dai bazai ta6a canzawa ba,ashe har yanzu kana nan da wannan tsegumin naka kamar mace"?cike da zolaya tayi maganar,harararta yayi tare da cewa"Ae tsegumin nawa ku ma yayi maku amfani!ko kinmanta ni ne ɗan leƙan asirin Mamanmu?ita ke cewa nazo gidanku najiyo mata idan kun ci abinci,idan nayi la6e naji kuna kukan yunwa sai in watsa da gudu inje in sanar mata.... " Dariya sehrish tayi har haƙoranta suka bayyana,baki asake Sadeeq yace"Wai!madarar kyau!rishi kinga yadda kikayi kyau kuwa da kika washe bakinki Fararen haƙoranki suka fito kamar na Ketrina kef?ba kamar lokacin da ba,Haƙorannan Jawur dasu kona Maclean ma babu," ɗaure fuska sehrish tayi kamar ta rufe shi da bugu tace"kai Sadeeq ɗazu fa naji kana cema baban ku,adaina tuna baya,shine nikuma zaka dinga tunamun abunda ya wuce don wulakanci," Fashewa yayi da dariya,bin shi tayi da kallo bakowa ya faɗo mata arai ba,fa ce junaid ɗinsu,lokaci guda taji tana kewarshi, "Sadeeq,mutumin da kake magana akanshi,ba yayana bane,Shi ne mahaifin mu!"tunkan ta taƙarasa maganar ya katseta da cewa"kutmelesi!Amma dai ƙarya kikeyi mun ko?idan shine mahaifinku,Wanccan mai dogon gemun fa?wanene Shi?cike da tuhuma yayi mata tambayar, Shiru tayi bata bashi amsa ba,tsareta yayi har sai da ta faɗa mashi komai daya faru arayuwarsu,wani Shu'umin murmushi taga yana saki,hakan yasa tace"Wai lafiya"? "Rishi aike yanzu hajiya ce,Ashe dama ku ƴa'ƴan masu kuɗi ne?Ae wlh bazata sa6u ba,Tunda kunyi arziƙi yanzu sai a ramama kura aniyarta koba haka ba"?yayi maganar yana ɗage mata gira,irin na ƴan duniyar nan, Dariya sosai tayi,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Faɗamun dame dame za'a rama maka"? Lissafo mata ya shiga yi"Ragowar abinci na da kuka saba cinye mun,tare da ƴan kayan sawa na da maman mu ke kwashewa tana kaima Oummanku don asanya maku kin tuna'? Shiru sehrish tayi bata bashi amsa ba,bakomai take tunawa ba,fa ce rayuwarsu ta baya,ya tuna mata da lokacin da Maman Sadeeq ke aiko da kayanshi don acanza masu kaya,saboda nasu duk sun yayyage,tun sunayi ma Oummansu kukan bazasu sanya kayan maza ba har suka haƙura ta dinga sanya masu,haka tsoffin takalman sadeeq haka aka dinga kawo masu don su rinka sama kafafunsu, Ganin hawaye akan fuskarta yasa Sadeeq saurin mikewa ya dawo gefenta ya zauna cikin lallashi yace"rishi nifa wasa nake yi maki,wlh ban faɗi hakan ba,da niyyar in 6ata maki rai ba,kawai inaso in sanyaki nishadi ne,saboda yanzu ta ko'ina Allah ya hore maku,' Cikin shessheƙar kuka tace"ni baka 6ata mun rai ba sadeeq,na tuna da irin rayuwar da muka yi ne abaya,kaima kasan dole inyi kuka in na tuna," "Tunda baki so,mu manta da komai,bazan ƙara tuna maki ba,Yanzu dai faɗamun nawa ne acikin asusun bankin ki?nawa kika tara"? Fashewa tayi da dariya jin abunda yace, Da hannu ta nuna mashi yatsunta guda biyar, "ɗari biyar"?yayi guessing yana kallonta,girgiza mashi kai tayi alamar a'a, "Dubu biyar"?ya sake canka,cike da sa ran ya faɗi dai dai, Girgiza mashi kai ta kuma yi, "To dubu ɗari biyar,"nan ma ta girgiza mashi kai Alamar a'a,tur6une fuska ya ɗanyi saboda ya fara tunanin kamar ƙarya takeson ta shirga mashi, A ƙule yace"Miliyan biyar"murmushi ta sakar mashi tare da jinjina mashi kai alamar ya faɗi dai dai, wani kallon rainin wayau ya jefa mata tare da cewa"Alkazzubu haramun," "Wlh dagaske nake maka,Ina da kuɗi sosai sunma fi miliyan biyar amma basa a hannuna,duk suna a wurin Daddyn...."kasa ƙarasa maganar tayi,ganin Sadeeq ya sauko daga saman kujerar ya dawo ƙasa saman carpet ya zauna agabanta tare da lankwashe ƙafafunshi zaman cin tuwo, "Lafiya naga ka dawo ƙasa,"? Hannu yasa tare da ɗan sosa ƙeyarshi yace"Ae matsayinmu ba ɗaya ba,kefa Millionaire ce,ni kuma Faƙiri mamallakin naira ɗari biyar acikin aljihu,bazaiyiwu mu zauna a saman kujera ɗaya ba,abun ma sam babu ladabi acikinsa, Fashewa Sehrish tayi da dariya,Yau sadeeq ya sanyata nishaɗi sosai,komai yayi yana tuna mata da junaid, "Aunty sehrish,kinji nace ina da ɗari biyar ko? ɗaga mashi kai tayi alamar eh , "Yawwa,wlh itama Wanki da guga nayi a shagon wani abokina aka bani ita,Nifa nan da kike gani na sai inyi fiye da wata ɗaya babu ko sisi a aljihuna,Babanmu kuwa idan kinga ya bani kuɗi to sai dai fa,idan naje islamiyya ne,haka itama maman mu,ataƙaice dai bari in fito maki a mutun,wlh Sehrish ko abun hawa bandashi,tunda keke na ya samu matsala ba'a ƙara gyaramun shi ba,naje wurin mai gyara yace sai ya ci dubu uku,tun daga nan na jingine shi gefe guda, Zuba mashi ido sehrish tayi tana kallonshi,yadda kasan ɗan Almajiri haka ya zauna yana zayyano mata matsolilin dayake fama dasu na rashin kuɗi,ta kasa kunne tana sauraronshi, A 6angaren Abusufyan kuwa,lokacin daya shiga yayi arba Da abu a zaune dirshan saman gadon tana faman zazzare idanuwanta,ba ƙaramin daɗi yaji ba,ƙarasa shiga ciki yayi tare da samun wuri daga gefen gadon ya zauna,zuba mashi ido tayi tana kallonshi,    Murmushi ya sakar mata tare da miƙa mata hannunshi,zuba ma tafin hannunshi ido tayi tana kallonshi,ta gane fuskarshi a matsayin wanda ya taimaketa,ta fito daga hannun masu fararen kayan nan,    "Ina ƴa'ƴana suke"?muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,    "Kada ki damu,ƴa'ƴanki suna atare dani zan kaiki wurinsu,kina so ko"?   ɗaga mashi kai tayi alamar eh,   "A ƙarshe dai duk yawace yawacen naki,gashi kin dawo wurina abu,saboda ƙaddararki tana atare dani,kamar yadda kika zama ƙaddarata nima,Ashe da rabon zan sake ganin wannan kyakkyawar fuskartaki"?calmly yayi maganar,tsantsar sonta ne da ƙaunarta ke addabarshi,ji yake yi tamkar ya mayar da ita cikin cikinshi,   "Abu na,Faɗamun har yanzu kina sona kamar yadda nima nakeson ki,"   Wuƙi wuƙi tayi mashi da ido tana kallonshi,sam batasan inda zacen nashi ya dosa ba,    "Kaine ka kashe mun babana ko?kuma ka rabani da ƴa'ƴana ko?Zaka kashe munsu ko"? girgiza kai Abusufyan yayi tare da cewa"ni bani bane na kashe maki mahaifinki ba abu,Nifa ne Abusufyan ɗinki,uban ƴa'ƴanki,ba zaki iya tunawa ba ko kaɗan,"   Kallon dayaga tana binshi dashi ne ya tabbatar mashi da cewar a harzuke take,jira take yayi yunƙurin matsawa kusa da ita,Yasha bugu,   Dariya ya ɗan yi tare dacewa"kwantar da hankalinki, ⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐? *_MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI_* *DOMIN. DAWO DA MARTABAN NONONKI* Shin ko kinsan nono yanada matukar muhimmanci a wajan mai gida ,? Shin ko kinsan babu abunda namiji yafiso yafi daukar hankalinahi kamar cikar k'irji , ? To nono shine babban Martaban mace a wajan mijinta , don babu namijin da zaiso mace mai yakunannen nono kamar silifas ,wannan yasa Nazo maku da sahihi kuma ingantaccen maganin nono Wanda bashida wata matsala hadin gargajiya ne , acikin lokaci kalilan zakisha mamakin yadda nononki zai ciko sosai Wanda wannan cikowar ita zata bashi damar da zai tashi sosai ta yadda kema zaki Shiga cikin jerin mata masu aji agaban mazajensu ........kedai hanzarta ki nemi mmn Yusuf mai kayan mata yar mutan sokoto zaki samu ingantattun kayan mata masu tafiyar da hankalin maigida.......don neman Karin bayani 07069711327 ...... is 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Am sorry🙏 Babu abunda zan yi maki,a haka ma daɗi nake ji,kina kallona ina kallonki,"murguɗa mashi baki tayi tare da kawar da idanuwanta gefe guda, Wuraren ƙarfe 8 na safe,nurse ɗin dake kula da abu ta ƙaraso,taimaka mata tayi wurin yin wanka a toilet ta gyara mata jikinta,da gashin kanta ko'ina ta wanke mata shi,lokaci guda Abu ta fito fess da ita,ƴar doguwar rigar material ta sanya mata,ita kanta abun sai murna takeyi da aka gyara mata gashin kanta da jikinta,taji daɗin jikinta sosai,Sehrish ce ta shirya masu breakfast gaba dayansu suka hallara a falo suka zauna suna ci,banda abu dake zaune a bedroom ɗinta tare da nurse ɗin,saboda ita kaɗai zata iya da ita,dama sune masu kula dasu a gidan mahaukatan,Sun san duk wasu dabaru da zasu bi wurin tafiyar dasu batare da sunsha wahala ba,a baki ta dinga bata abincin kalacinta tana ci,saboda bata iya ci da hannunta ba,Zubarwa takeyi a ƙasa,kamar ƙaramar yarinya haka take yin wasa da abincin,Bayan nurse ɗin ta kammala kimtsata,Dr yazo ya duba ta,bayan tafiyarshi ne ta samu bacci, *SGR* Da gudun gaske motarsu ta shararo izuwa cikin gidan yadda kasan zasu tashi sama,gudu bana wasa ba,Sam ya kasa samun natsuwa acikin zuciyarshi,jikinshi sai tsuma yake yi a ƙagare yake dasu ƙarasa cikin gidan,Armstrong nazaune agefenshi sai faman tausarshi yake yi ganin yadda ya tashi hankalinshi,slowly sojan daya ɗaukkosu from Airport ya rage gudun motar lokacin da ya ƙaraso wurin da zai yi parking ɗinta,saboda tsabar sauri,tun kafin a buɗe mashi ƙopa yasa ƙafarshi azafafe ya harba ƙopar,gudu gudu sauri dauri ya nufi cikin main palour ɗinsu,wayaam babu kowa tsit kake ji,A hanzarce ya haura upstairs direct ya wuce bedroom ɗin junaid,a buɗe ya samu ƙopar ɗakin hannu yasa ya tura tare da shigewa ciki,gabanshi ne ya faɗi rasss ganin babu junaid,saboda yasan cewa junaid bai zuwa ko'ina tunda sanyin safiya,adai irin wannan lokacin zaka same shi kwance saman gadonshi rungume da pillow,   Muryarshi tamkar zata fasa maƙoshinshi haka ya shiga ƙwala mashi kira"JUNAID!JUNAID!!JUNAID!!!"a gaggauce ya nufi toilet ɗinshi yasa hannu ya tura,nan ma yaga wayaam babu kowa,jiki asanyaye ya fito daga ɗakin junaid ya wuce bedroom ɗin Marshal Omar,tura ƙopar yayi ya shiga daga ciki,babu kowa a falonsa,bedroom ɗinshi ya nufa nan ma babu kowa,tashin hankali!   Wani irin wahallallan yawu ya haɗiya,fitowa yayi daga part ɗin Omar ya nufo downstairs,gudu gudu sauri sauri haka yake taka staircases ɗin,yana a second to the last step,yaji shigowar message a wayarshi,dakatawa yayi tare da sanya hannu cikin trouser pocket ɗinsa,duba screen ɗin wayar yayi,bayan ya sanya finger ɗinsa ya buɗe saƙon,a tsanake ya soma karantawa   _Gm Sir,ina fata ban takura maka ba,Marshal yana kwance a gadon asibitin mu yanzu haka_   Message from doctor Emran,Hankalinshi yayi mugun tashi,a ruɗe ya furta"Omar?kwance a gadon asibiti?   Da sauri ya nufi hanyar fita daga falon,fitarshi keda wuya,Hosana ta fito daga bedroom ɗinsu,tasha kuka kamar ranta zai fita,saboda an barta ita kaɗai,babu Jahad babu Sehrish babu Junaid,bugu da ƙari kuma babu Ya Omar,tun ɗazu take ta zaryar zuwa ɗakin shi,don taga ko ya dawo amma babu shi,palour ta dawo ta zauna saman sofa,hawaye wasu na bin wasu,fuskar ta jiƙe sharkaf, "Hosana"!jin muryar Azmee yasa ta miƙe tare da juyowa tana kallonta,sanye take cikin doguwar jallabiya,tayi rolling mayafi akanta,    Tunkararta hosana tayi cikin shessheƙar kuka tace"A...aunty azmee har yanzu basu dawo ba,ni kaɗai aka bari,gidan duk babu daɗi,"    Janyota Azmee tayi tare da rungumeta ajikinta,tana ɗan lallashinta,   "Don't worry ur self,wipe ur tears,in sha Allah nasan nan bada jimawa ba,Ya Omar ɗinki zai dawo cikin gidan nan,Just calm down ur mind,"ta ƙarasa maganar tare da ɗago hosana daga jikinta,    "Aunty azmee,shiru fa since yesterday night,kuma har kiran layinshi nayi wayarshi a kashe,Ni shikenan kowa ya tafi ya barni,dama ba so na akeyi ba,"tana magana hawaye na sharara akan fuskarta,ɗan murmushi Azmee tayi tare da kai hannunta saman fuskar hosana,taja kumatunta tare da cewa"Haba Babyn Omar,shalelen Abusufyan,kinfi kowa sanin yadda ya Omar ɗinki ke tsananin sonki,Ina da tabbacin cewa duk inda yake a yanzu,tunaninki yake yi,ya hosanata ta ke?me take yi a yanzu?tana kewata kuwa?    Murmushi hosana ta saki har hankalinta ya ɗan kwanta jin abunda Azmee tace,   "Aunty azmee kin tabbata cewa ya Omar yana tunani na yanzu haka"?   ɗaga mata kai azmee tayi alamar eh,kafin tace"Kina aransa mana,yanzu abunda za'ayi,me zai hana mu shiga kitchen atare mu haɗa mashi lafiyayyen breakfast,da zarar ya dawo gida kinga sai ki kai mashi,Zaiji daɗi sosai,"   Cike da zumuɗi hosana tace"Mu tafi kitchen ɗin,Hada chocolate zamu haɗa mashi,nasan zaiji daɗinshi sosai"   Ruƙo hannunta Azmee tayi atare suka wuce cikin kitchen,Suna aiki suna fira,gwanin ban sha'awa,   *SGR HOSPITAL* Slowly Motarsu ta shiga cikin katafaren asibitin,bayan Armstrong yayi parking ɗin Motar,buɗewa Sgr yayi a hanzarce ya wuce cikin asibitin da saurin gaske,Armstrong na biye dashi,Tashin hankali,Soldiers ɗin da suka kawo Marshal Omar,Suna yin arba da fuskar Sgr nan fa kowa yasha jinin jikinshi,Hankalinshi a matuƙar tashe yake kallonsu one by one,Sara mashi suka shiga yi,batare da ya tanka masu ba,jiki a sanyaye yake tafiya kamar wanda aka zarewa Lakar jikinshi,tuni ya soma karaya,Zuciyarshi sai tsinkewa take yi,   Lokacin da ya ƙaraso wurin da Major ke tsaye,Suna haɗa ido major ya saddar da kanshi ƙasa,yayin da zuciyarshi ke bugawa,Don yasan cewa dole ya tuhume shi game da kashe mashi waya da yayi,    "Major"da wata irin raunanniyar Murya Sgr ya ambaci sunanshi,    Batare da ya ɗago sun haɗa ido ba yace"Na'am yalla6ai,"    "Where's Omar"? Da hannu major ya nuna mashi medical room ɗin da aka kwantar dashi,batare da ya kuma tambayarshi wani abu ba,Ya wuce cikin ɗakin  har izuwa gaban gadon da Marshal ke kwance,babu alamun sauƙi a jikinshi,   biyo bayanshi Major yayi tare da Armstrong suka tsaya agefe,    Juyowa yayi tare da wurga eyeballs ɗinshi kan fuskar Major,tun kafin yayi magana a ruɗe Major ya dakatar dashi"Am sorry sir,don Allah don sonka da manzon Allah (SAW)kada ka tambayeni komai,saboda bazan iya amsa maka ba,"  gyaɗa kai kawai yayi tare da juyawa daƙyar ya iya ɗaga kafarshi har izuwa gefen gadon ya zauna,yana kallon Omar,ya jima yana mamakin menene silar kwantar dashi gadon asibiti?A iya sanin shi ba ƙaramin abune zaisa a kwantar da Omar gadon asibiti ba,   Turo ƙopa Dr Emran yayi ganin su Armstrong sunyi cirko cirko yasa shima yaja gefe ɗaya ya tsaya,To fa kowa tunani ya shiga yi taya zasu fahimtar da Sgr batare da ya haukace masu ba,   "Major!"ya ambaci sunanshi, Hankali atashe major yace"Na'am Yalla6ai,"   "Meya faru da ɗan uwana ne?"ƴan kame kame major ya shiga yi duk yabi ya susuce ya rasa ta ina zai fara kora mashi bayani,    "Emran!meya faru da Omar ne"?ya sake tambayar Dr emran,Shiru Emran yayi shima ya rasa ta ina zai fara,Jin sunyi mashi shiru yasa zuciyarshi ta hasala,jikinshi na kerma ya miƙe tare da kallonsu,ranshi a matuƙar 6ace yake magana!   "Bazaku amsa mun ba!Kun wani zuba min ido kuna kallona,kun mayar dani tamkar wani shashasha,"hankalinsu ya tashi matuƙa,kowa sai motsa la66ansa yake yi,suna so suyi magana amma fargaba ta hanasu,   Hannu yasa ya daki ƙirjinshi da ƙarfi,lokaci guda idanuwanshi suka juye tamkar ba mutun ba,rarumar plastic chair ɗin dake agaban gadon Marshal yayi azafafe yayi wurgi da ita,nan take kujerar ta yi gefe guda ta daki ƙasan tiles, A razane suke kallonshi,wata irin zufa ce ta soma gangarowa ta gefen fuskarshi,ɗaya bayan ɗaya yake binsu da kallo,jikinsu sai kerma yake yi,Dr Emran ma ƙoƙarin guduwa yake yi,Armstrong kuwa sai lalla6ashi yake yi akan su sanar dashi abunda ke faruwa tun kafin ya birkice masu,    "Rafayet"!muryar Marshal Omar ce ta dawo dashi cikin hayyacinshi,jiki na rawa ya juya yana kallonshi,a hankali Omar ke buɗe idanuwanshi waɗanda sukayi jawur dasu,zufa ta ko'ina ajikinshi duk da sanyin A.c ɗin dake akwai,da sauri Sgr ya koma gefen gadon ya zauna tare da ruƙo hannunshi,   "Omar pls tell me,what's happening wit u?meyasa na ganka a asibiti?Are u not feeling well"?daƙyar Marshal ya samu ya yunƙura tare da mikewa ya zauna,numfashinshi da huci yake fita,bawan Allah yaji jiki sosai,wasu zafafan hawaye ne suka wanke mashi fuskarshi,   Muryarshi na rawa yace"Bro,Yaushe ka dawo Abuja?    Muryar Sgr tamkar zai yi kuka yace"Omar duk ba wannan ba,Where's Junaid?nadamu akan son ganinshi,Daddy ma yana ta kira na saboda rashin samun Junaid a waya..."ya ƙarasa maganar yana faman haɗiyar yawu, Marshal na ƙoƙarin buɗe baki yayi mashi magana,Karaf idanuwanshi suka sauka akan Major dake girgiza mashi kai alamar karya kuskura ya faɗa mashi,kasa magana Omar yayi,sai ma zuba mashi ido da yayi yana kallonshi,   "Wai menene haka?kowa na tambaya sai yayi mun shiru babu magana?meke faruwa ne!in wani abu ne ya faru ba zaku sanar mun ba ne?Ni fa Musulmi ne!nayi imani da ƙaddara mai kyau ko mara kyau,ku faɗa mun mana......"ya ƙarasa maganar fuskarshi ɗauke da matsananciyar damuwa,    Daƙyar Omar ya iya buɗe baki yace"Babu abunda ya faru,Junaid yana lafiya...."tunkan ya ƙarasa maganar Sgr yace"That's impossible!Taya zaka ce mun junaid yana lafiya kuma in yarda?To idan yana nan a nuna mun shi inaso in ganshi!Meyasa layinshi a kashe?meyasa nake ganin hawaye akan fuskarka?   Daurewa kawai Omar keyi,saboda kukan dake cinshi,So yake ya fashe da kuka ko ya samu ya rage raɗaɗin dake acikin zuciyarshi,    Tausasa murya Sgr yayi"pls Omar,ka sanar dani!ina ƙanina yake?wani abu ya faru dashi ne?saboda shi jiya ko bacci ban samu ba,   Da sauri Omar ya sanya tafin hannunshi tare da share hawayenshi,    "Rafayet!I won't hide it for u,Junaid was kidnapped...."daƙyar ya ƙarasa maganar ganin irin kallon da Sgr ke jefa mashi,kallon tuhuma,    "Omar,ni kake faɗama cewa Anyi kidnapping ɗin junaid"?shiru Omar yayi batare da yace mashi komai ba, "Omar,If it is true,Junaid was kidnapped,as a Senior Soldier with the rank of Marshal,you will be brave enough to rescue him,bawai na ganka kwance a gadon asibiti ba kana zubar da hawaye,"tausasa muryarshi yayi"don Allah Omar ka faɗa mun gaskiyar abunda ya faru,kada kasa zuciyata ta buga,Ina junaid ɗina yake?meya faru dashi?yanayin yadda yayi maganar ne yasa jikinsu kara yin sanyi lakwas,   Daƙyar Major ya daure ya cije,ya yi karfin halin bude baki yace"Sir,Junaid ya riga mu gidan gaskiya!junaid ya koma ga mahalicci....."bai ƙarasa maganar ba sakamakon Zaburar da yaga Sgr yayi gadan gadan ya tunkareshi,yana faɗin",repeat what u just said Major!"yana magana yana naɗe hannun rigarshi alamar zaiyi dambe,da sauri Omar ya ambaci sunanshi Rafayet,wanda hakan ya dakatar dashi tare da juyawa yana kallon Omar,   Cikin shesshekar kuka Marshal yace"Junaid has gone forever,wanda yafi mu sonshi ya kar6i abunshi,jiya da daddare around 8,Suna kan hanyar dawowarsu acikin mota shi da jahad,ta fita ta siya masu ice cream tabar junaid acikin Motar,kafin ta dawo,babbar mota tabi ta kan motarshi,Rafayet bamu samu komai daga sassan jikin junaid ba,Ya ƙone ƙurmus acikin motar........"kasa ƙarasa maganar yayi,ya fashe da wani irin matsanancin kuka mai cin rai tare da buga hannuwanshi saman gadon,   Tashin hankali!!!Kasa motsawa Sgr yayi daga tsayen da yake,kamar an dasa mashi aya,Tsit ka ke ji,kowa yasha jinin jikinshi Sgr kawai suke kallo, Almost 15 mins,Kafin ya motsa pink lips ɗinsa a hankali ya furta"Omar!Do you wanna say that Junaid is dead?   Jinjina mashi kai marshal yayi alamar eh,abun mamaki sai suka ga yana murmushi gami da girgiza kanshi yace"I can't believe that junaid is gone,this is a fabricated lie, Omar you're just kidding me and I don't want it...."   Tsananin tausayinshi ne ya kama Omar,dama yasan cewa zaiyi wuya ya yarda cewa Junaid ya mutu,   "Sir,we are really sorry.....'Dr Emran ne ya ambaci hakan,a sukwane Sgr ya juya tare da kallonshi aruɗe yace"Sorry for what"?   Shiru yayi baice komai ba,ɗaya bayan ɗaya yake kallonsu,a wani irin yanayi mara misaltuwa,fuskarshi duk ta hargitse,jikinshi yayi laushi,guiwarshi ta sage,ƙafafuwanshi sun gaza ɗaukarshi,ga6o6in jikinshi duk sun saki,Zuciyarshi ta raunata sosai,    Wani farin ruwa ne ya kwanta luf acikin fararen idanuwanshi,jinjina kanshi kawai yake yi batare da ya furta komai ba,temperature ɗin jikinshi yayi zafi sosai,yadda ko mutun ya matso kusa dashi,sai yaji hucin jikin nashi,wata irin zufa ce ta soma tsastsofa mashi,a jikinshi lokaci guda ya jiƙe sharkaf,gaba ɗaya sun zuba mashi ido suna kallonshi,gwanin ban tausayi,    "Wai Junaid ne ya mutu?tatsuniya ce ko mafarki"?muryarshi na kerma yayi maganar,    "Enough is enough! What do you want me to say to our father? How can I inform him about Junaid's death?saboda shi  ko bacci baiyi ba jiya,Nima haka,meyasa mutuwa zata yi mun yankan ƙauna ne?    Sulalewa yayi saman guiwowinshi wani irin biji biji ya fara gani a idanuwanshi,a hankali ya shiga furta"Innallilahi wa'inna ilaihirraji'un,Ya Allah kasa mafarki nake yi ba gaske ba,meyasa ni bata ɗauke ni ba ta ƙyale Junaid?Why!why!'da sauri Dr Emran tare dasu Major suka kewayeshi suna tottofa mashi addu'o'e asaman kanshi,wani irin jijjiga jikinshi ya soma yi,hakan ba ƙaramin ɗaga masu hankali yayi ba,a Ruɗe marshal ya saukko daga saman gadon ya nufosu jiki ba ƙwari ya zube agaban Sgr wanda tuni ya yanke jiki ya faɗi,kuka sosai Omar yake yi kamar ya haɗiyi zuciya,rungume Sgr yayi sosai ajikinshi,Ya tsorata da jin irin zafin da jikin Sgr ya ɗauka,tamkar hucin wuta ,   "His body temperature was very high,I think he got a heatstroke,yana buƙatar Emergency treatment,"Dr Emran ne yayi maganar,batare da 6ata lokaci ba a gaggauce suka ɗaukeshi izuwa saman medical bed ɗin da Omar ya sauka suka kwantar dashi,doctors ne suka taru akanshi,ga jinin shi ya hau sosai, Daga waje suka koma,Saman waiting seats suka zauna suna jiran tsammani,ɗage kanshi yayi jikin seat din yasa Hanky ya rufe fuskarshi,Allah kaɗai yasan irin raɗaɗin da yake ji acikin Zuciyarshi,bakowa yafi ji ma tausayi ba,Fa ce Abbansu,don muddin yaji irin Mummunar mutuwar da Junaid yayi tofa Zuciyarshi zata buga ne,A rasa duka biyun,Sojojin dake a kewaye dasu,sai tausarshi sukeyi ganin yadda kamanninshi suka sauya saboda damuwa,   "Haƙuri zamuyi yalla6ai,nasan abun da ciwo,raɗaɗinshi yafi ƙunar wuta,Amma ya zamuyi?mutuwa ce tana akan kowa,Junaid addu'armu yake bukata a yanzu,Allah ya jiƙanshi,ya gafarta mashi zunubbanshi,Yasa can yafi mashi nan,Su kuma waɗanda suka shirya mutuwarshi,Allah ya tonu asirinsu,don bazamu ƙyalesu ba,sai sun ɗanɗani kuɗarsu,"sosai Major ya shiga tausarshi yana ƙara ƙarfafa mashi guiwa,   a hankali Omar ya zame hanky ɗin dake akan fuskarshi,ta kumbura sosai la66ansa sunyi suntum,idanuwanshi sunyi jawur dasu luhu luhu,daƙyar ya iya buɗe baki yace"Nagode sosai Major,naji daɗi sosai,kalamanka sun dan sanyaya mun zuciyata,Amma inaso ka sani rashin Junaid atare damu babban gi6i ne,wanda babu wanda zai iya cike sa,he's our weakness!maƙiyanmu sunci galaba akanmu!Sun kashe mana duk wani ƙwarin guiwa da muke dashi!laifin me junaid ya aikata da ya cancanci wannan ɗanyen hukuncin?Yaron da baison komai ba,Soyayyar ƴan uwansa kawai ya sani,burinshi koda yaushe ya sanya kowa farin ciki,amma yau an samu wasu marasa imani,Marasa tausayi,sun yi silar mutuwarshi!wlh ɗaya daga cikinsu bazai shaba,Sai sunyi danasanin haihuwarsu da uwarsu tayi acikin duniyar nan,"yana magana hawaye na wanke mashi fuskarshi, Major na ƙoƙarin buɗe baki yayi magana,Suka jiyo hayaniya daga can cikin asibitin,Sautin kuka suka jiyo mai sautin gaske,Gaban Omar ne ya faɗi rasss jin Muryar jahad wadda tun a jiyan su major suka sa aka maido ta nan,A hanzarce suka miƙe tsaye suna kallon wurin da sautin ke fitowa,da gudun gaske take tunkarosu nurses sun biyota da gudu,sae ihu takeyi tana faɗin"wuta!wuta!Junaid yana acikin wuta,ataimaka a fito mun da ɗan uwana,kada ta ƙona shi,"wannan shine sambatun da takeyi,tashin hankali!   Duk da jikinshi ba ƙwari haka ya nufeta,tare da ruƙota jikinshi,idanuwanta sun juye kwata kwata bata iya gane wanene agabanta,ita dai kawai sunan junaid take ambato acikin bakinta,hankalin Omar ba ƙaramin tashi yayi ba,tsoranshi kar ace ta samu ta6in hankali,don da alama abunda ke shirin faruwa kenan,    "Jahad!ki natsu ki kalleni,Ya Omar ne fa"   Kuka takeyi sosai,jijiyoyin wuyanta duk sun firfito waje,don bala'e Allurar kashe jiki akayi mata,Amma babu abunda allurar tayi mata,tamkar an ƙara mata ƙarfin jikinta,baiwar Allah taga tashin hankalin da bata ta6a gani ba,kuma akan Masoyinta da take tsananin so,   Jijjigata ya shiga yi yana ambaton sunanta"Jahad!Ina zaki je?    Firgita tayi agigice ta dinga faɗin"Gashi can!yana kuka wuta!wuta!ke ci ajikinshi!Yana kuka,Ya Omar a fiddo shi kada ya mutu ya barni,"da ƙarfi take yin maganar tamkar maƙoshinta zai 6allo,ƙoƙarin ƙwacewa take yi daga hannunshi don taje wurin abunda idanuwanta ke hango mata,Ko ina ta kalla,sai taga motar junaid tana ci da wuta,shine abunda idanuwanta ke nuna mata,   Hawaye ne suka kuma wanke mashi fuskarshi,tsananin tausayin jahad ne ya kamashi,gaba ɗaya babu natsuwa atare da ita,ta haukace ta gigice ta firgice,kamar wadda tayi shekara ɗaya tana hauka,    Hannu yasa tare da sa6arta saman kafaɗarshi,saboda rashin ƙwarin jikinshi,har tangal tangal yayi kamar zai faɗi daƙyar ya samu ya tsayar da kanshi,wuce wa nurses ɗin sukayi gaba yabi bayansu,yana jin yadda jahad keta bugun bayanshi,ta dunƙule hannayenta sae ɗumarshi take yi don ya saketa,Allah sarki innocent girl kamar jahad,yau ta zauce har tana bugun Ya Omar ɗinsu,   Er nurses ɗin suka wuce har zuwa room ɗin da aka kwantar da ita,Shiga yayi da ita ciki,a lokacin har jikinta ya fara saki,alluran da aka ɗurka mata sun fara aiki,a hankali ya kwantar da ita saman gadon,kamar matacciya haka ta koma,ko yatsanta bata iya ɗagawa,la66anta sun bushe sosai,sun farfashe sakamakon ciccijesun da tayi,tsayawa yayi daga tsaye yana kallonta,idanuwanta suna a rufe,tunda yake a rayuwarshi bai ta6a fuskantar tashin hankali irin na jiya da kuma yau ba,bai ta6a cin karo da mummunar rana ba,irin ta yau,ta ko'ina babu sauƙi,zuciyarshi har wani tafarfasa takeyi saboda ƙunar da takeyi mashi,   Shigowa cikin ɗakin Major yayi tare da wani baturen Likita,jin sallamarsu yasa Omar juyawa yana kallonsu,da sauri ya tunkari Doctor ɗin yana tambayarshi dangane da jahad,   "She is having a panic attack as a result of the incident"acewar Dr Antony,    Dafe kai Omar yayi da hannu ɗaya ya ɗan runtse idanuwanshi tare da buɗesu,Muryarshi a kasalance yace"Yanzu Doctor babu yadda za'ae yarinyar ta dawo cikin hayyacinta!"   Dr Antony yace"It will be very difficult for us to overcome her now,but we will do our best to see her regain consciousness,"   "Pls Dr,try as much as u can" Jinjina kai Dr antony yayi,tare da dafa kafaɗar Marshal don ya lura baya acikin hayyacinsa    "Calm down ur mind,she will be ok,zamu yi iyakar bakin ƙoƙarinmu wurin ganin mun shawo kanta,"    Daga haka Major ya ruƙo hannunshi suka fito daga waje,zama fa bai gansu ba,Zarya ya shiga yi tsakanin room ɗin da Jahad take ciki dakuma room ɗin Sgr,sam ya kasa samun natsuwarshi tuni ya mance da shima mara lafiya ne,ana cikin wannan tashin hankalin,Tsautsayi yasa Omar ya kar6i wayarshi daga hannun Major,Yana kunnata kwatsam!sai ga kiran Abbansu ya shigo cikin wayar kamar jira yake yi,!   Zubawa screen ɗin wayar ido yayi,tare da ɗagowa ya kalli Major,tun kafin ma yayi magana,major ya riga shi cewa"Abba ne ko"?ɗaga mashi kai yayi alamar eh,    "Seriously I can't pick his calls,saboda bansan amsar da zan bashi ba,if he asks about junaid,"ba don yaso ba haka ya katse kiran Abbansu,Abunda bai ta6a yi ba arayuwarshi, yana ƙoƙarin kashe wayar gaba ɗaya sai ga message ya shigo ta sama,hannunshi na kerma ya buɗe message ɗin,fearfully ya soma karantawa,   _Omar kun kyauta ku dukanku,kowa yaƙi ɗaga kiran wayata,dama inaso in sanar dakai cewa,Yau zamu dawo gida_   Saboda tsabar kiɗima,Omar baisan lokacin daya saki wayarshi ba,ta faɗi ƙasa sosai ta daki tiles ɗin,   "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un!Allahumma ajirni fil masibati wa'aklifni khairan Minha"wannan shine abunda yake ambato acikin bakinshi,    "Major menene mafita?Ka taimaka min!abubuwa sunyi mun yawa,Ya zanyi da rayuwata!Babu Junaid,Jahad ta zauce!Ga Sgr ma a kwance gadon asibiti,Na shiga uku ni yau!wannan wace irin baƙar rana ce!?   Wani irin tausayinshi ne ya lullu6e major,janyoshi yayi ajikinshi ya rungumeshi sosai,dama a buƙace yake da ya samu kafaɗar da zai aza kanshi,Ya zubar da hawayenshi sosai,ko ya rage raɗaɗin dake acikin zuciyarshi,   Cikin shessheƙar kuka yace"Major menene mafita yanzu?Ya zanyi da Abbansu?   Hannu major yasa yana ɗan bubbuga bayanshi yace"Sir,in sha Allah komai zai tafi dai dai,bazamu rasa abunyi ba bi'iznillahi,"    Ruƙo hannun Omar yayi suka koma saman waiting seat ɗin suka zauna,kwantar da kanshi ya kumayi asaman kafadar major,sai faman sauke ajiyar zuciya yakeyi,bakomai yake faɗo mashi arai ba,fa ce Fuskar Baby Junaid ɗinsu,mai ɗauke da wannan kyakkyawan Murmushin,    *Boss Bature* *Sehrish* Around 1:30 na rana, Zaune take asaman Sofa ta zabga Uban tagumi,tunda Daddynsu ya sanar da ita game da tafiyar Sgr Abuja,take jin kanta kamar ba cikakkiyar mutun ba,Bataso tafiyarshi ba,duk da ta yi mamakin tafiyar tashi,kewarshi duk tabi ta lullu6eta,ga kewar gida yau 3 days kenan suna a kano,Yanzu gidan ya rage daga ita sai Oummansu,tun kafin a fara kiran sallah,Maman sadeeq suka koma gidansu,Abusufyan ne ya ɗaukesu acikin motarshi,hannu takai tare da ɗaukar wayarta dake ajiye agefenta,Contact ta shiga tare da lalubo numbar jahad ta buga mata kira,   Guntun tsoki taja,jin layin nata a kashe,Layin Junaid ta kira Shima a kashe,hakan ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba,Layin Hosana ta kira,a lokacin sun kammala haɗama Omar breakfast ɗinshi,har ta koma ɗaki ta shiga toilet tayi wanka,tana zaune gaban mirror tana kwalliya jikinta sanye da gown,wayarta dake ajiye saman drawer ta soma ringing,duk a tunaninta ya Omar ɗinta ne,jiki na rawa ta miƙe hada tuntu6e wurin yin saurin ɗaukar wayar,koda taga kira daga Sehrish ne,jiki na rawa tayi picking call ɗin tare da kara wayar a kunnanta,   Tunkafin Sehrish tayi magana,hosana ta ruga ta cewa"Wai yaushe zaku dawo ne?gidan fa ba kowa ni kaɗaice,    "Hosana wai ina jahad ne?ina kuma junaid?basu dawo daga shan ice cream ɗin bane tun jiya da suka fita?na shiga damuwa saboda rashin samunsu a waya,"   Hosana tace"Nima bansan inda suka je ba,babu fa kowa gida,daga ni sai Aunty azmee,ya Omar bansan shima ina yaje ba,"    Hankalin sehrish yayi matuƙar tashi,la66anta na kerma tace"Hosana!yaya Rafayet baizo nan gidan ba"?   "Eh,baizo ba,ni banga kowa ba," Nan take ranta ya bata cewa wani abu ya faru acikin gidan,kuma bada kowa ya faru ba,fa ce Su Junaid da suka fita shan ice cream,saboda rashin dawowarsu cikin gidan   "Rishi ko breakfast na gaza ci,ina cikin matsananciyar damuwa,"   Ajiyar zuciya Sehrish ta sauke tare da cewa"Hosana ki kwantar da hankalinki,Zasu dawo cikin gidan ne,Yanzu zan sanar dake wani abun farin ciki nasan zaki ji daɗi sosai,    Muryarta aɗan shagwa6e tace"toh faɗamun menene"    Sehrish ta miƙe tare da nufar ɗakin Oummarsu tana faɗin"Nasan Daddy bai sanar dake ba ko"? Hosana tace"meke nan"? Shiga cikin ɗakin tayi wayarta manne a kunnanta,   Video call ta mayar da kiran nasu,bayan ta samu wuri ta zauna gefen Oummansu dake ta bacci hankalinta a kwance,   "Hosana kalli ki gani,Wacece wannan,"tayi maganar tare da saita Screen ɗin wayar saitin fuskar Oummansu,   Ƙura ido hosana tayi tana kallon fuskar oummasu,almost 7 mins,a hankali wani kyakkyawan murmushi ya bayyana akan fuskarta,a ruɗe tace"rishi Oumman mu ce ko?    "Eh itace,naso na sanar dake tun jiya,baki dauki wayan ba kuma bansamu halin sake kiran ba,An samu Oummanmu,Amma bata acikin hayyacinta ta samu ta6in hankali,   Uban tsalle hosana ta daka,da gudun gaske ta fito daga ɗakinsu,kaitsaye ta nufi kitchen inda ta baro Azmee tana gyare gyare,Cikin rashin sani Hosana taci karo da haroon,ta bangaje shi sosai har wayar dake hannunta ta kubce mata,kaitsaye ta faɗi ƙasa ta daki Tiles Screen ɗin ya fashe,   Hannu hosana ta aza asaman kanta ta fashe da wani irin matsanancin kuka,tana faɗin"Wayyo Allah wayata!Ka kashe mun wayata,Wlh bazan yafe maka ba,Allah ya isa,"   Rai a6ace haroon ya ɗaga hannu zai mareta,adai dai lokacin Azmee ta fito daga kitchen ɗin,A ruɗe ta ƙaraso ta damƙi hannunshi,wani mugun kallo daya jefa mata sai da gabanta ya faɗi rass saboda launin idanuwanshi da sukayi jawur dasu,fuskar nan tashi tayi suntum da ita,da sauri azmee ta saki hannunshi,cikin sanyin murya tace"Allah ya huci zuciyarka,"   Harara ya wurga mata tare da jan dogon tsoki mai sautin gaske,matsawa yayi izuwa inda wayar hosana take a ƙasa,Ya sanya faffaɗan tafin kafarsa mai sanye da takalmi,Ya take wayar ya rugurguzata,hakan ba ƙaramin ƙona ma hosana rai yayi ba,Abun ka ga mai ta6in hankali,Kamar kura ta mamayeshi tare da gartsa mashi cizo asaman damtsen hannunshi,Dama ƴar singlet ce ajikinshi,ƙoƙarin janyeta ya dinga yi amma taƙi cire haƙoranta daga saman fatar hannun,har sai da ta fasa shi,jini ya shiga tsastsafowa a wurin,waro ido waje haroon yayi ganin ta fitar mashi da jini a fatar jikinshi,ƙwaƙƙwarar damƙa yakaima Gashin kanta,Hankalin Azmee ba ƙaramin tashi yayi ba,Ga tsoron shiga huruminshi take yi don tasan halinshi ba imani ya cika ba,Yasha ɗaga hannu zai mareta,   Wurgi yayi da hosana,gaba ɗaya ta tafi zata faɗi ƙasa,Azmee takai hannu zata ruƙota,   Tsawa ya daka mata tare da cewa"kika kuskura kika ta6a ta abakin aikin ki cikin gidan nan!uwar shisshigi kawai,ki tsaya a iya matsayinki,"jiki asanyaye azmee ta tsaya tuni idanuwanta suka cicciko tab da ƙwalla,tana ji tana gani haka hosana ta kife ƙasa,fuskarta ta bugu sosai har hancinta ya fashe,    Haura ƙafa yayi ya wuce Can medical room ɗinsu,saboda yayi dressing raunin da taji mashi,   "Hosana"Azmee ce ta ambaci sunanta,tare da zuƙunnawa agabanta,tasa hannu ta janyota ajikinta,Lallashinta ta shiga yi,abun ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,Haroon ya 6ata mata rai,   Cikin shessheƙar kuka tace"Aunty azmee,Kalli yarda ya fasa mun wayata,mutumin can baida imani shi ba jininmu bane,"hannu Azmee tasa tana share mata hawayenta,    "Kiyi hakuri hosana,Allah shi zai saka maki,"   Daƙyar azmee ta samu ta lallasheta,har ta rakata ɗakinsu ta kwantar da ita tana ta ajiyar zuciya,cikin lokaci ƙanƙani bacci ya ɗauketa,   Dawowa falon Azmee tayi wurin da wayar Hosana ta fashe,hannu tasa ta ɗauki wayar tana kallon screen ɗin,Ya dagargaje sosai baka iya ganin komai, A 6angaren Sehrish kuwa,duk tabi ta ruɗe lokacin da taji sautin kukan hosana,kafin haroon ya taka wayar ta ƙarasa mutuwa gaba ɗaya,zumbur ta mike tana zarya acikin ɗakin,kamar tayi tsuntsuwa ta tafi Abuja haka take ji,ta ƙagara tasan meke faruwa acan ɗinne ... .. ' Tashin hankali!Su marshal na zaune zaman jiran tsammani,sae ga Sgr ya fito daga room ɗin da aka kwantar dashi,Ko riga babu ajikinshi ya yageta ya cireta,ƙirar ƙarfin nan tashi mai matuƙar tsoratarwa gata nan a bayyane,Tsokar jikinshi sai rawa takeyi,miƙewa sukayi gaba ɗayansu suna kallonshi,   "Rafayet"!Omar ne ya ambaci sunanshi tare da tunkarar shi,damtsen hannunshi ya ruƙo acikin nashi yana sake ambaton sunanshi   "Omar!I can't believe that junaid has gone,till the day i found out those who planned his death!One by one sai na kashe su da hannuwana,daga nan ne zan yarda cewa Na rasa shi na har abada,wlh in har ban aikata abunda na faɗa ba,Sai na ajiye aiki na"daƙyar yake magana saboda zuciyarshi dake a harzuƙe,jininshi na akan akaifarshi,   ƙoƙarin kama hanya yake yi yabar wurin Omar ya rurruƙeshi saboda baisan inda zai dosa ba,Likitocin dake kula dashi duk sun kewaye shi sae faman tausarshi sukeyi suna lallashi,Amma ina idanuwanshi sun rufe rufff,baya ji baya gani,   "Rafayet ka kwantar da hankalinka mana!Duk yarda ka ke jin radadin mutuwar nan nima haka nake ji,nama fika jin raɗaɗi saboda Gani nake yi kamar ni ne silar mutuwarshi,Akan idona Junaid yabar gidan acikin motarshi na gaza dakatar dashi,Har Major sai da ya bani shawara amma banyi saurin ɗaukar mataki ba,Wlh kamar na haɗiyi zuciyata na mutu haka nake ji,"dakatawa ya ɗan yi da yin maganar yayin da suke kallon juna,shi da Sgr idanuwan kowannansu cike tab da Hawaye ba ƙaramin jiki suke ji ba,   Tausasa muryarshi yayi kafin yaci gaba da cewa"Rafayet!yakamata muyi tunani akan mahaifinmu!mu nemi mafita,domin kuwa ya sanar dani cewa suna akan hanyar dawowa gida yanzu haka,kaima kasan irin yadda yake jin junaid aransa,muddin yaji mutuwarshi tofa zamu rasa shi ne,a yadda shekarunshi suka ja ɗinnan bakomai zai iya jurewa ba,"   Jikin Sgr ba ƙaramin sanyi yayi ba,bawan Allah duk yabi ya susuce ya rasa kuzarin jikinshi,    "Omar,yanzu ina ita yarinyar take ne"?yayi tambayar yana kallonshi,    "Jahad ta zauce yanzu haka an kwantar da ita,ta samu bacci,"   Jinjina kanshi ya ɗan yi,Shiru sukayi na wani lokaci,kafin Major yace"Yakamata mu nemi mafita,lokaci yana ƙure mana!" Doctor Emran ne ya basu shawarar su shiga ɗaya daga cikin resting rooms na asibitin,yadda zasu ji daɗin tsara yadda zasu tunkari Abbansu, Katafaren ɗaki ne ya haɗu sosai,wuri kowannansu ya samu ya zauna,Omar Da Sgr suna zaune daga gefen gadon ɗakin,Major tare da Dr Emran da Armstrong suna zaune asaman doguwar sofa ɗin dake a ɗakin,Sanyin A.c ɗin dake a ɗakin ba karamin sanyaya masu zuciya yayi ba,almost 15 mins kowa yayi shiru babu mai magana acikinsu,Kowa da abunda ke zuwa mashi aranshi,   "Yalla6ai mi zai hana asamu babban malamin addini ya fahimtar dashi ta hanyar tausarshi da daɗaɗan kalamai,tare da janyo mashi ayoyin al kur'ani,"acewar Major Dr Emran yace"that wouldn't be a solution a yanzu dai,gaskiya a yadda naji irin son da yake yi mashi muddin yaji irin mummunar mutuwar da Junaid yayi tofa wannan ba zai yi tasiri ba,zamu rasa shi,Zuciyarshi zata buga ne...."   Armstrong yace"Koda za'a sanar dashi,Ni shawarata kada a faɗa mashi ainihin abunda ya faru,Ina nufin irin mutuwar da Junaid yayi,kawai asanar dashi cewa Ya rasu ne ta hanyar rashin lafiya na rana ɗaya..."tun kan yakai ƙarshen maganar Omar yace"idan ya nemi ganin gawarsa fa?Ya zamuyi kenan"?   Shiru Armstrong yayi can yace"sai ace anyi burying dinta tunda dama ku baku taking time kafin ku rufe deceased" wani kallo Omar yayi mashi yace"kana ganin in ance masa hakan zan yarda ne,alhalin yana araye,sam hakan ma ba mai yuwuwa bane" shiru Armstrong yayi don kuwa bai yi nazari ba kafin ya bada shawarar,   "To yalla6ai mezai hana kawai a 6oye mashi komai game da mutuwar Junaid ɗin!in yaso koda ya tambayeshi sai asanar dashi cewa,Sgr ya tura shi U.s ne,wurin yin training ɗin aikin soja,"Major ne yayi maganar,   Murmushin takaici Omar yayi tare da kallonshi yace"Ita kuma jahad ɗin fa?ko itama mun turata U.s ɗinne training?   Duƙar da kai ƙasa major yayi,Sgr dai bai tanka masu ba shi kaɗai yasan irin tafarfasar da zuciyarshi keyi mashi,   "Gaskiya akwai gagarumar matasala!yanzu idan muka ce an tura Junaid U.s zai kar6i training ɗin soja,Jahad kuma ya zamuyi da ita?Zata tona mana asiri ne,ta hanyar sambatun da takeyi in har bata dawo hayyacinta ba,koba wannan bama Shi Abban zai iya buƙatar yin waya da jubaid!Dole fa ya nemi layin waɗanda ke a u.s don yaji ya lafiyar ɗanshi,duk kuma in hakan bata samu ba zai ce zaije can ne don ya ganshi"Marshal Omar ne yayi wannan jawabin   Armstrong yace"Inaso naji abunda Sgr zaice,Saboda nasan baza a rasa mafita a wurinshi ba,"   Mayar da hankalinsu su kayi akan Sgr wada ya ɗan lumshe idanuwanshi,   Cikin sanyin murya Omar yace"muna sauraronka ya zamuyi yanzu?Daddy yakusa dawowa,kuma da alama bashi kaɗai zai dawo ba,dukkansu zasu dawo",saboda tsabar tashin hankalin da suke ciki,Ko tunanin abinci ma basuyi,bawai don basu jin yunwa ba, Slowly ya buɗe idanuwanshi sai lokacin ya soma magana atsanake    "Duk shawarwarin da kuka bayar ba masu 6ullewa bane,a karshe dai dole mahaifinmu yasan cewa ɗanshi ya mutu,Ba don naso ba,Amma ba yadda zanyi ne,ya zama dole muyi wa mahaifinmu ƙarya a karo na farko don mu ceto rayuwarshi...."dakatawa ya ɗanyi da yin maganar,yana sauke ajiyar zuciya kafin ya ɗaura da cewa"Shawarata shi ne,Za'a sanar dashi cewa,Anyi kidnapping ɗinsu su duka biyun!saboda babu junaid jahad kuma ta zauce,muddin muka mayar da ita gida asirinmu zai tonu ne,kuma mahaifin yarinyar yanzu yana cikin farin cikin ganin mahaifiyarsu,idan har ya dawo ya samu ƴarshi a cikin wannan yanayin yaya kuke tunanin zaiji aranshi?ga kuma babban rashin da mukayi na Junaid!that's the reason why ya zama dole a killace Jahad acikin asibitin nan na tsawon wasu kwanaki har asamu ta dawo cikin hayyacinta,hikimar yin hakan shi ne na farko idan daddy yaji cewa anyi kidnapping ɗinsu,tabbas hankalinshi zai tashi sosai,Amma zai sa ran bayyanar junaid a koda yaushe,kuma zamu sanar dashi cewa Junaid zai dawo Zamuyi ƙoƙari wurin ganin mun ku6utar dashi hakan zaisa Ya ɗan ji sauƙi aranshi duk da zai shiga matsananciyar damuwa,mu kuma zamuyi ƙoƙari wurin ganin mun shawo kanshi,Abu na biyu shi ne bayan wasu ƴan kwanaki idan Allah yasa Jahad ta dawo cikin hayyacinta,Zamu lallasheta ne nasan zata fahimce mu,Zamu fara sakinta ta koma gida a matsayin su kidnappers ɗin suka saketa,Wannan zai ƙara kwantarwa Abbanmu hankali saboda zaisa Ma ranshi cewa shima junaid zasu sako shi,Ta wani 6angaren Abusufyan ma zaiji sauƙi aranshi in yaga dawowar Jahad,may be ma kafin ya dawo daga kano zata koma,so daganan a hankali a hankali zamu cigaba da ƙoƙarin fahimtar da Daddy,koda zaisan cewa junaid ya mutu sai daga baya lokacin komai ya wuce kamar next 1 to 2 month haka,Sae asamu babban malami ya zaunar dashi yayi mashi nasiha sannan ya sanar dashi ainihin abunda ya faru,radaɗin da zaiji aranshi bazai kai raɗaɗin da zaiji ba a yanzu idan aka sanar dashi..."yana kai ƙarshen maganar shi,ya rufe idanuwanshi yayin da zuciyarshi keta harbawa,   "Good Idea"!acewar Armstrong, Major ya ɗaura da cewa"Yanzu yakamata a fara kawar da duk wani abu wanda zaisa Labarin hatsarin daya faru yaje masu,dama an kori ƴan jarida daga wurin,yanzu haka akwai sojojin dake kewaye da wurin an rufe shi,basu bari kowa ya ɗauki video ko hoton abunda ya faru ba,Zamusa su tsananta bincike akan mutanen dake a wurin dama kuma ba wasu mutane da yawa ne su kai witnessing incident din ba,ko masu wuce wa a mota babu sosae,dakuma mai siyar da ice cream ɗin nan,Hatta wayarshi za'a canza mashi saboda gudun kar ace ya dauki rahoto in ma ta kama asa ya canza wuri ne sai ayi hakan,Zamu toshe duk wata hanya da zaisa labarin mutuwar Junaid yaje kunnan mutanen gidan in sha Allah," Jinjina kai Omar yayi tare da cewa"hakan yayi,Yanzu yakamata a hanzarta zuwa yi mashi jana'iza,Yamu yamu zamu halarta wurin yi mashi sallah,mu binne tokarsa awurin,bayan an kammala sai a kawar da ƙarahunan Motar,A shafe duk wani abu da zai nuna cewa Anyi hatsarin mota a wurin,"cikin karyayyar murya ya yi maganar. Sun jima suna tattaunawa akan yadda zasu tafiyar da komai,daga bisani wuraren karfe 2,Suka ɗunguma gaba dayansu zuwa wurin da incident ɗin ya afku,Sgr kamar yayi hauka lokacin daya yi arba da motar Junaid,Yaji mutuwar nan har cikin ranshi,daƙyar suka samu kowa ya dan daidaita natsuwarshi,Alwala su kayi gaba ɗayansu banda Armstrong da wasu da suka kasance ba musulmai ba,Anan sukayi mashi Sallah tare da burying ɗin tokarsa A gefen wata bishiya,bayan sun gama jana'izar,sojoji suka kawar da motarshi daga wurin,jikin kowa fa yayi mugun sanyi,Don suna kammala sallar jana'ixar Sgr ya zukunna gefen ƙabarin Junaid,tare da kwantar da kanshi asaman ƙabarin,Addu'o'e ya shiga jerowa abakinshi yana tottofa mashi,a ƙarshe yace"Allah ya jikanka Junaid,bazan ta6a yafewa kaina ba,idan har ban ɗauki fansa akan irin kisan wulakancin da akayi maka ba,Na ɗaurawa kaina alhakin mutuwarka,Saboda laifina ne Junaid da ban baka kariya ba,na tabka babban kuskuren da har duniya ta naɗe bazan ta6a mantawa dashi ba,"    Kasa ɗagowa yayi daga kan ƙabarinsa,💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥*    Kasa ɗagowa yayi daga kan ƙabarinsa,   Marshal Omar ne ya ɗaura da cewa"In sha Allah junaid na aljanna,muna yi mashi kyakkyawan fata,Allah yasa ƙarshen wahalarshi kenan,"gaba daya basu ji daɗin irin yadda mutuwar junaid ta kasance ba,kamar wani mara gata,babu mahaifinshi akusa babu ƴan uwanshi,   Ruƙo hannun Sgr major yayi,tare da janyoshi,jikinshi duk ya saki,daƙyar ya iya mikewa ya tsayar da kanshi akan ƙafafunshi,   Sojojin dake kewaye da wurin sunyi su 50,Layi sukayi wani na bin wani,kowa yazo wurin ƙabarinsa sai ya tsaya ya tottafa mashi addu'a kafin ya wuce,Na bayan shi yazo shima yayi mashi addu'a a haka har suka kammala,ba tare da mutane sun samu damar tsayawa ganin abunda ke faruwa ba,dama kuma hanyar sam ba mutane sosae.    Basu bar ƙabarin junaid a fili ba,saboda gudun kada mutane su dinga tattake wurin batare da saninsu ba,ko su zauna abakin bishiyar,waya suka sa suka kewaye bishiyar, Sun jima a awurin cike da jimamin mutuwar junaid,kafin wani lokaci suka shige motocinsu suka tafi ba don sunso ba,Kuma duk da haka sai da Sgr ya sanya sojoji guda biyu suka tsaya a wurin,batare da uniform ajikinsu ba,     *RIJF BABY JUNAID* *Boss Bature* Wuraren ƙarfe 5:30 na marece, Slowly motocinsu suka shiga cikin gidan,Bayan sunyi parking ɗinsu Major ya buɗe masu mota,don atare suka zauna shi da Sgr a motar Omar,kowa jiki babu ƙwari haka suka fito daga cikin Motar,kaitsaye suka nufi ƙopar shiga falon, A lokacin hosana na zaune saman Sofa,duk ta takure kanta,tun da tafarka daga bacci take ta faman yin sintiri acikin gidan tana jiran dawowar Omar don ta faɗa mashi abunda haroon yayi mata, Jin motsin shigowarsu yasa tayi saurin miƙewa jiki na rawa ta tunkareshi zata rungumeshi, Da hannu yayi mata alamar karta matso kusa dashi,fuskarshi babu annuri,har cikin ranta bata ji daɗin abunda yayi mata ba,har gaishe dasu tayi amma babu wanda ya kulata,acikinsu,   Upstairs suka wuce atare,kowa ya nufi part ɗinsa,komawa hosana tayi saman sofa ɗin tana kuka,abun ya ƙona mata rai,Yadda Omar ya dakatar da ita don karta ta6a shi,   Faɗawa yayi saman gadonshi yayin da idanuwanshi ke fuskantar Ceiling,Fuskar Junaid ya dinga ganin tana yi mashi gizau,ji yake tamkar abunda ya faru mafarkine ba gaskiya ba,saboda wani sashe na zuciyarshi na raya mashi cewa Junaid yana raye bai mutu ba,Yayin da wani sashen na zuciyar tashi ke gasgata mashi mutuwar junaid,runtse idanuwanshi yayi Allah kaɗai yasan irin raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi daurewa kawai yake yi,ya jima a haka idonshi na kallon sama,kafin daga bisani ya miƙe tare da faɗawa toilet bayan ya rage kayan jikinshi, Kwance yayi tsulundum acikin jacuzzi (kwamin wanka)wanda ke kewaye da glass,da niyyar yin wanka ya shiga toilet ɗin,Amma sai kasala ta baibayeshi ko yatsan shi ya gaza ɗagawa,abubuwa sunyi mashi yawa,tunda yake a rayuwarshi bai ta6a fuskantar mummunar rana irin wannan ba,da ace mutuwa hutu ce agareshi da ba abunda zai hana ya roƙi Allah akan ya ɗauki ranshi ya huta,Yaci alwashin saiya ga bayan waɗanda suka kashe junaid,Alƙawari ne ya ɗaukarwa kanshi,Ko bacci bazai ƙara yi ba,in har bai ɗaukarwa junaid FANSA ba,kamar yadda Sgr yaci Alwashin ɗaukar fansa haka shima Omar ya ɗauka, Kasa jurewa yayi saboda kukan da hosana ke raira mashi ta la6e a ƙopar dakinshi batasan halin da yake ciki ba,   "Hosana,"ya ambaci sunanta,muryarshi a kasalance,   Cikin shessheƙar kuka tace"Na'am,"   "Zonan," Hannu tasa ta tura ƙopar tare da shigewa ciki,Kwance ta same shi saman gadonshi,Ya baje daga shi sai short,kallo guda zakayiwa fuskarshi ka gane cewa yana acikin matsanancin tashin hankali,   har Saman gadon hosana ta hau ta zauna tana kallonshi,lokaci guda ta dakata da yin kukan nata,Ganin dry tears asaman fuskarshi,nan fa hankalinta ya tashi sosai,   "Ya omar,hawaye akan fuskarka?meke damunka ya Omar,Ban ta6a ganin hawayenka ba,Sae yau,"   A hankali ya bude idanuwanshi da sukayi jawur dasu yana kallonta yace"Hosana,ki taimaka mun kaina kamar zai fashe,Ina cikin matsananciyar damuwa,Zuciyata raɗaɗi take yi mun,pray for me hosana kona samu sauƙi acikin zuciyata,   Jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,hannayenta ta sanya tana kokarin janyo shi hakan yasa ya dan matso daura kanshi tayi saman laps ɗinta,Addu'o'i ta shiga karantowa tana tottafa mashi asaman fuskarshi,shafa sumar kanshi ta shiga yi,tana cewa"Ya Allah ga bawanka nan,kai kaɗai kasan meke damunshi,Ya Allah ka yaye mashi damuwarshi,Ka sanyaya mashi zuciyarshi,Alfarmar Annabi Muhammadu (S.A.W),   Ba ƙaramin daɗin maganarta yaji ba,sosai ya gyara kwanciyarshi sama sama bacci ya fara ƙoƙarin daukarshi, Yana jiyo muryarta tana tambayarshi Ko zaici abinci ta kawo mashi,    Daƙyar ya iya amsa mata da cewa"A'a hosana,bana iya cin komai yanzu,"   "Shikenan ya Omar ɗina,kayi baccinka kawai,zanci gaba da yi maka addu'a,har ka farka,"    Shafa sumar kanshi taci gaba da yi,tamkar jinjiri haka ta dinga treating ɗinsa har bacci yayi awon gaba dashi,Yau hosana tayi mashi abunda bai ta6a tsammani ba,Ta bashi kyakkyawar kulawa kamar ba wannan mai ta6in hankalin ba,wani iko na Allah ta so sanar dashi damuwarta,amma tunda ta gane cewa baya a hayyacinshi,Sae kawai ta fasa sanar dashi. *Tashin Hankali!" Jin dirar motoci acikin gidan yasa shi yin firgit ya farka,tare da yunƙurawa ya miƙe zaune,Hosana ya gani kwance tana bacci,asaman gadon ya ɗauketa,   Jiki na rawa ya saukko daga saman gadon ya samu jallabiya ya zura ma jikinshi ya bude ƙopar dakinshi da sauri ya nufi downstairs,Tunkan ya ƙarasa ya jiyo Muryar Abbansu yana ƙwalama Junaid kira,ko sallama baiyi ba,Burinshi kawai yayi tozali da junaid,   "Hasbunallahu wani'e mal wakil"ya furta hakan tamkar zai fashe da kuka,   Yana cikin wannan yanayin sai ga Sgr shima ya fito daga part ɗinsa,jikinshi sanye da jallabiya shima,kallon juna suka yi kowa fuskarshi ayamutse take,    "Daga shigowarshi ko sallama baiyi ba sunan junaid kawai ya ambata,yanzu yaya zamuyi dashi'?omar ne yayi maganar tare da kallon Sgr dake tsaye a gefenshi,    "Yanzu ya dawo yana buƙatar ya huta,yakamata muyi ƙoƙari wurin ganin mun daidaita natsuwarmu,if not za'a samu matsala ne," Shigowa cikin falon suka karasa yi,Abbansu ne sai Mommynsu,tare dasu twins,fawan gaba ɗaya matasan gidan sun dawo,hada kanal yousouf su irfan da sauransu,Banda gwaggon katsina suma sun shirya dawowa tare dasu Ammi,zasu zo daga baya, Agajiye suke kowa ya samu wuri saman Sofa ya zauna,Abba kuwa jiki na rawa ya wuce upstairs,su Sgr najin takun takalminshi hankalinsu ya ƙara tashi,Yana tafiya yana ƙwalawa junaid kira,   "Junaid!Junaid!where are you?Ur dad is back,Nayi missing ɗinka sosai...."    Bai ƙarasa maganar ba,ganinsu Omar atsaye,cirko cirko,ƙaƙaro murmushi suka yi gaba dayansu suka tunkareshi,Sgr ne ya fara yin hugging ɗinshi,Daddy I really missed you,Ya gajiyar tafiya?ya ƙarasa maganar tare da ɗagowa daga jikinshi,Bai amsa mashi gaisuwar tashi ba,yace"Yaushe ka dawo Abuja?ko kun dawo ne'?    "A'a daddy,Wani uziri ne ya kawo ni,Amma zan koma kano ɗinne,"wani kallo da yaga Abbansu na binshi dashi yasa ya ɗan sha jinin jikinshi,   "Abba sannu da dawowa,"Omar ne yayi maganar,wurga idanuwanshi yayi akan fuskar Omar,aɗan ruɗe yace"kunyi rashin lafiya ne?meke faruwa ne?naga fuskokinku duk sun kumbura,fuskar Rafayet tayi jawur da ita,kaima haka...."   Da sauri Omar yace"Am...Abba..I know u are tired,kana buƙatar hutu,yakamata muje bedroom ɗin ka Inyi maka tausa,"   Harara Abban ya ɗan watsa mashi tare da cewa"a ƙule nake dakai Omar,ina ta nemanka jiya,ka tashi ka kashe mun waya hmmmm..."yana kai ƙarshen maganar ya soma ƙoƙarin wuce wa ciki,Saboda tsabar ruɗu Sgr baisan sa'adda ya tarboshi da hannunshi,Zuba ma hannun nashi ido Abbansu yayi,fuskarshi ɗauke da mamaki yace"Rafayet,lafiyarka kuwa?cikina fa ka tarbe,"   Zame hannunshi yayi tare da ɗan sosa ƙeyarshi yace"Am sorry Daddy,pls u need a rest,mu sauka down ka huta mana,ka kwaso gajiya,inaso na baka abinci kaci ka huta,Omar zaiyi maka massage ka ɗan ji daɗin jikinka,   Cike da mamaki Abbansu ke kallonshi,"Rafayet!yau kaine da kanka kake zancen zaka bani abinci a baki na naci?Omar kuma zai yi mun tausa,sae kace wani ƙaramin yaro,"gyaɗa kanshi yayi tare da cewa"Naji toh,Amma saina fara zuwa ɗakin Junaid,idan nadawo sai mu je ɗakin nawa,"yana kai ƙarshen maganar ya wuce tare da nufar ɗakin Junaid yana ƙwala masa kira,   Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,A hankali Abba ya tura ƙopar ɗakin junaid ya shiga daga ciki,Wayaam yaga babu kowa aciki,Bai kawo komai aransa ba,saboda ƙarar saukar ruwa dayaji a toilet,hakan yasa shi tunanin ko ya shiga wanka ne,ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa ya fito daga ɗakin,da niyar idan ya huta zai dawo wurinshi,don yau atare yake son su kwana dashi, Koda suka yi arba da Abbansu yana nufosu sai kowannansu ya shiga ƴan kame kame,fargabarsu kada ace zai tambayesu ina Junaid ya ke,.     Tunkan ya ƙaraso wurinsu suka ji yace"Ashe ya shiga wanka ne,idan ya fito daga wankan pls ku sanar dashi cewa nadawo kuma inason ganinshi,a bedroom ɗina,"   Atare suka haɗa baki wurin cewa"Toh Abba" Saukowa down sukayi atare da abban yana gaba suna a bayanshi,Sae faman sauke ajiyar zuciya suke yi, Lokacin da suka sauko down,Su kanal Yousouf na ganinsu kowa ya miƙe fuskar nan ɗauke da farin ciki,Yayin da su kuma kowannansu ya dabarbarce, Daƙyar suke gaisawa da ƴan uwan nasu,kowa ya lura da yanayinsu shiru kawai su kayi,Su fawan sai tambayar Junaid suke yi,Yana ina?basu ganshi ba,amsa daya suke basu ta yana a cikin toilet yana wanka,Duk wanda yaje ɗakin Junaid yaji sautin saukar ruwa daga cikin toilet,sai yayi tunanin cewa wanka yake yi,Ashe fanfo ne Aka bari a kunne ba'a kashe ba,    Daƙyar suka samu kowa ya haƙura da ganin junaid,Omar yace su wuce ɗakunansu kowa yaje ya huta,an kwaso gajiya,   "Nifa ban yarda dasu babban yaya ba,Shi da ya Omar akwai wani abu da suke 6oye mana Allah,"Acewar Jahan, A yayin da suke shiga bedroom ɗinsu,   Ayaan yace"nikaina na lura da hakan,musamman faces ɗinsu,kamar sunsha kuka Allah,Gaskiya hankalina bazai kwanta ba,sai naga junaid,ni ban yarda wanka yake yi acikin toilet ba,"   Jahan yace"mu bari mu huta,Zuwa dare sai muje ɗakin nashi,nasan lokacin idan ma wankan ne ya gama,"   Ƙarasa shiga cikin ɗakin sukayi,kowa ya shiga rage kayan jikinshi,Jahan ne ya fara shiga waka,Ayaan ya zauna gefen gadon yana jiranshi ya fito shima ya shiga wankan,    A can falo kuwa,Mommynsu ta tsare Sgr da Omar,Tasa su gaba tayi tana binsu da kallo one by one,dama bakowa Sgr yafi ji ba fa ce Mommynsu,tana da wuyar sha'ani,   "Mommy,"Sgr ne ya ambaci sunanta, bata amsa mashi sunan nata daya kira ba,sai cewa tayi"you didn't answer my question,It seems like you are hidding something for us!Rafayet where is junaid!kada kuyi mun ƙarya nasan ba halinku ba ne,just ku faɗamun Gaskiyar abunda ya faru,"   Murya na rawa Omar yace“Am..mommy,Junaid fa yana a toilet yana wanka zai fito ne...m"daƙyar ya ƙarasa maganar ganin irin kallon da take yi mashi,kallon tuhuma,kallon ban yarda dakai ba "Wai taya za ku ce mun junaid yana wanka?Nifa ba ƙaramar yarinya bace,balle kuce zakuyi mun wayau,tun daga kan fuskarku na gane cewa akwai wani abu daya faru dashi...."   Saussauta muryarta tayi,sannan taci gaba da magana"pls idan wani abu ne ya faru da Romeo ɗina ku sanar dani,i will accept it,"yadda tayi maganar yasa su kaji jikinsu ya ƙara mutuwa,   "Am listening to u guys,ku faɗamun meya faru dashi ya mutu ko"?   Gabansu ne ya faɗi rass!da sauri Sgr ya ruƙo hannunta muryarshi na kerma yace"Mommy dan Allah kiyi haƙuri,ki rufa mana asiri,I will explain to u mu shiga daga cikin bedroom ɗin..."   "Rafayet,meyasa zaka sanar da ita"?Omar ne yayi maganar fuskarshi a yamutse,   "To ya kakeso nayi Omar,Mommy bazata ta6a yarda ba,kwara kawai mu faɗa mata gaskiyar abunda ya faru,Ka wuce wurin Daddy,ni zanji da Mommy,'   Ya ƙarasa maganar tare da jan hannunta,Suka wuce upstairs bedroom ɗinshi,   Ajiyar zuciya Omar ya sauke,Ya jima atsaye yana tunanin Yadda zasu ƙare da Abbansu,tsoranshi kada farat ɗaya zuciyarshi ta buga idan yaji cewa Anyi garkuwa da junaid kamar yadda suka tsara,   "Omar,lafiya kuwa,"firgit ya ɗanyi tare da kai idanuwanshi wurinta,Azmee ta nufo shi,Ganinshi a tsaye kamar akwai damuwa atattare dashi,   Dakyar ya ƙaƙaro murmushin yaƙe yace"bakomai,"     "Omar,dama inaso na tambayeka ne,Wai ina junaid ne?tun jiya da suka fita shi da jahad shiru har yau basu dawo ba,nashiga damuwa sosai akan rashin ganinsu,har cewa yayi idan suka je shan ice cream zaiyi min tsaraba," ta ƙarasa maganar tana kallonshi,   "Aunty Azmee,bazan iya 6oye maki ba,Junaid da jahad anyi kidnapping ɗinsu...."jin wannan maganar yasa Azmee ta dafe ƙirjinta da ƙarfi,idanuwanta suka firfito waje,hankalinta yayi mugun tashi,   "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"kusan sau biyar tana maimata kalmar,    siraran hawaye ne suka soma saukowa saman cheeks ɗinta,ji tayi tamkar bazata iya ɗaga ƙafafunta ba,saboda nauyin da sukayi mata,   "Junaid da jahad suna buƙatar addu'armu Azmee,"acewar Omar,   Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Nashiga uku!Yanzu junaid da jahad aka ɗauke mana...." Katse ta Omar yayi'pls Aunty azmee,ki daina ɗaga sautin muryarki,na faɗa maki ne don ki taimaka mana,Wurin kwantar da hankalin sauran mutanen gidan nan,Mun shiga damuwa sosai,saboda gudun halin da zasu shiga,musamman mahaifinmu...."   Cikin shessheƙar kuka tace"Ya Allah ga bayinka nan!ka tsare manasu a duk inda suke,Ya Allah ka ku6utar dasu daga hannun azzaluman da suka yi garkuwa dasu,wannan wata irin masifa ce......"kuka ne yaci ƙarfinta,da gudun gaske ta juya tare da tunkarar kitchen,zama tayi ta dingi kuka kamar ranta zai fita,gani take yi kamar zasu rasa su ne,Ta ƙwallafa rai akan junaid,tana jinshi tamkar ɗan cikinta saboda ta shayar dashi,baiwar Allah,   Jiki asanyaye Omar ya wuce bedroom ɗin Abbansu,tsaye ya same shi har ya zura kayan bacci ajikinshi,ta cikin mirror ya hango Omar,juyowa yayi fuskar shi ɗauke da murmushi yace"halan junaid ya fito daga wankan ne"?yayi tunanin abunda ya kawo shi ne,   "Abba,me kake buƙata na kawo maka"ya tambaye shi ne don ya kawar mashi da tunanin Junaid aranshi Murmushi Abba yayi tare da cewa"Sannu Azmee,Yau kaine ka kar6i aikinta kenan"?   Duk da halin daya ke ciki na fargaba sai da ya ɗan murmusa,jin abunda abban yace,    "No,kawai inaso na baka kyakkyawar kulawa ne saboda nayi kewarka,ka fara faɗamun abunda kakeso sai in kawo maka,"   Murmushi Abba ya ɗan yi kafin yace"shikenan,junaid nake son gani ka kawo mun shi,idan ma ya fara bacci ka ɗauko mun shi,ina jiranka,"ya ƙarasa maganar tare da samun wuri gefen gadonshi,yana kallon Omar da yayi mashi zuru da ido,   "Omar,lafiya ka zubamin ido kana kallona'?   "Babu komai Abba,bari na ɗauko maka junaid ɗin,"yayi maganar tare da juyawa yabar ɗakin,Zaman jiran dawowarshi Abba yayi,sai faman sakin murmushi yake yi,harya ƙosa Omar ya ɗauko mashi Baby Junaid ɗinshi, A 6angaren Omar yana fita daga bedroom ɗin abban nasu,kaitsaye kitchen ya wuce,Anan ya samu azmee zaune saman kujera tana ta matsar kwalla, "haba Aunty azmee,meyasa zakiyi mun haka?Addu'a yakamata kiyi masu akan Allah ya bayyanar mana dasu,kukan da kike yi bazai amfane su ba,"   Zame hannuwanta tayi daga saman fuskarta,idanuwanta sunyi jawur dasu luhu luhu,   "Omar,ba zaka gane bane,dole inyi kukan rashin su junaid,ko ka manta shakuwar dake tsakanina dashi ne'?   Shiru omar yayi yana kallonta,Allah yaso bai sanar da ita gaskiyar abunda ya faru ba,da baisan abunda zai biyo baya ba daga gareta itama, Lallashinta ya shiga yi har ya samu ta saukko,Tsayawa yayi ta shirya mashi dinner asaman tray,ya kar6a ya wuce ɗakin Abbansu,ita kuma ta shiga ɗaukar kayan abincin da ta shirya masu tana kaiwa dining, Lokacin da Omar ya koma bedroom ɗin Abbansu,yana shiga ciki Abbansu yaga tray a hannunshi sai ya ɗaure fuskarshi tare da cewa"Nifa ba yunwa nace maka inaji ba,Junaid nace ka ɗauko mun,"   Saman table omar ya ajiye tray din tare da samun wuri gefenshi ya zauna,ruƙo hannayenshi yayi tare da sassauta muryarshi    "Abba pls,kaci abincin ka ƙoshi,idan ka kammala zamuyi magana dakai,"   Shiru yayi yana kallonshi kamar mai nazarin wani abu yace"Shikenan zuba mun abincin naci,Allah yasa naji alkhairi," Serving ɗinshi Omar ya soma yi,sosai yaci abincin bayan ya gama da abincin,Omar ya tsiyaya mashi Lemu me sanyi a cup,yasha,   "Yanzu ina sauraronka,wata maganace zamuyi,"   "Abba ko zaka ɗan kwanta ne?ina ga kamar hakan zaifi,muna magana inayi maka tausa,"   Abun ya daurewa Abbansu kai,gyara kwanciyarshi yayi saman gadon sannan yace"ina sauraronka toh,"   Hawa saman gadon Omar yayi,A hankali ya fara yi mashi massage ɗin kafarsa,    A tsanake ya soma magana"Abba dama game da junaid ne,nasan ka yarda dani sosai,kuma zaka fahimce ni ne,   Tunda ya ambaci sunan Junaid,Abba ya miƙe daga zaune da sauri yana kallonshi   daurewa Omar yayi tare da cigaba da cewa"mun shiga matsananciyar damuwa Abba,idan ka lura da fuskokinmu duk sun sauya saboda tsabar tashin hankalin da muke ciki...."dakatar dashi Abba yayi ta hanyar ɗaga mashi hannu,    "Ka fito fili ka faɗamun ainihin abunda ke faruwa Omar,sai 6oye 6oye kake yi mun,dama ni tuni sai da raina ya bani cewa wani abu ya faru da junaid,dan Allah ka sanar dani!ina ɗana yake"?hankalinshi atashe yayi maganar,   Cike da fargaba Omar ya ɗaura da cewa"Abba,junaid yana cikin ƙoshin lafiya,sai dai baya atare damu,Jiya bayan fitarsu shan ice cream tare da jahad,kidnappers su kayi garkuwa dasu,bana so ka tashi hankalinka Abba,Ni nayi maka alƙwarin zan dawo maka da ƴa'ƴanka,cikin ƙoshin lafiya batare da sun samu koda ƙwarzane ajikinsu ba....."duk wannan surutan da Omar keyi baisan cewa Abbansu ya jima da sumewa ba,tunda ya ambaci sunan kidnappers sunyi garkuwa dasu,Bai ƙara sanin inda kanshi yake ba,   "Abba!"ya ambaci sunanshi,yayin da yake kallon fuskarshi,Hannu yasa tare da dafe goshinshi,Dama saida ranshi ya bashi cewar hakan zata iya faruwa,   Idanuwanshi ne suka cuccuko da kwalla,kamar ya fasa ihu haka yake ji,ta ko'ina babu sauƙi,dirshan ya zauna saman gadon fuskarshi a yamutse,ya zuba ma Abban nasu ido yana kallonshi, Adai dai Lokacin Sgr ya shigo bedroom ɗin tare da Mommynsu,tasha kuka duk da irin juriyarta,daƙyar ya samu ya shawo kanta,shima ɗin don yayi mata alƙwarin cewa zai dawo mata da ɗanta har gida ba tare da komai ya same shi ba,jin motsin shigowarsu yasa Omar waigawa yana kallonsu,har suka ƙarasa shigowa wurin gadon,Gefen gadon Sgr ya zauna,Mommy ta tsaya daga tsaye tana kallon Abba dake a zaune ido rufe,   "Omar,ka faɗa mashi ne"!?ɗaga mashi kai Omar yayi alamar eh,Ya kuma cewa"ko ya samu bacci ne"?   Girgiza kai yayi tare da cewa"a'a,taya zan faɗa mashi wannan tashin hankalin yayi bacci?Kaima ka sani,tun kafin ma na ƙarasa sanar dashi ya sume a zaune,Na rasa abun yi ne shiyasa nayi zugum ina kallonshi,   Miƙewa Sgr yayi da sauri ya fuce daga ɗakin don ya ɗauko masu ruwan da za'a yayyafa mashi,   "Mommy,dan Allah ku ƙara haƙuri akan 6atansu junaid,in sha Allah we will try our best don muga mun dawo dasu cikin gidan nan," Jinjina kai tayi "Na yarda daku Omar,Nidai burina ku dawo mun dasu cikin gidan nan,Na tambayi Son game da kidnappers ɗin ya sanar dani cewa,Sau ɗaya suka kira waya,Kunyi magana dasu kuma har sun baku Junaid kunyi magana dashi,Naso ace sun bar wata kafa da zatasa ayi tracking layinsu,Amma kashe yace mun Sun kira da hidden number ne,abunda nakeso naji shi ne,basu buƙaci adadin kuɗin da suke so ba?ni koma nawa ne zan bada a kar6ominsu,"   Jikin Omar ba ƙaramin sanyi yayi ba,gwanin ban tausayi haka yake kallonta,Aransa yana ayyana irin tashin hankalin da zata shiga idan taji cewa,Junaid ya mutu ta hanyar take shi da mota,   "Omar kayi shiru baka ce komai ba,"ta jifa mashi tambayar,tana kallonshi,   Girgiza mata kai yayi"A'a Mommy,basu buƙaci komai ba yanzu,Sun sanar damu cewa,Zasu tuntu6emu idan buƙatar hakan ya taso,kuma sunyi warning ɗinmu,kada mu kuskura muyi gigin yin investigation akansu,if not zasu illatasu ne,shiyasa bamu yi wani yunƙuri ba ayanzu,Amma yanzu mu kanmu kiransu muke jira,muji nawa suke buƙata sai a tura masu,"ba don yaso ba haka ya dinga shirga mata ƙarya,kamar yayi kuka wai yau shine ke yin ƙarya,duk da yayi ba'ason ranshi ba,Dole ce tasa su yin hakan,   Turo ƙopar Sgr yayi hannunshi ruƙe da bottle water,ƙarasawa yayi tare da buɗe murfi ya tarfa ruwan asaman tafin hannunshi,Sannan ya shafa fuskar Abban nasu,Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da ware idanuwanshi akansu yana kallonsu ɗaya bayan ɗaya,a hankali ya furta"Ina junaid"?   Omar na ƙoƙarin buɗe baki yayi mashi jawabi,Alexandra ta katse mashi hanzarinshi da cewa"Ku barni dashi,dare yayi sosai yakamata kuje ku kwanta ku huta,kafin gobe,"ta fadi hakan ne don tasan cewa ba karamin tashin hankali suma suke ciki ba da ganin yanayin su,     Saukowa daga saman gadon Omar yayi tare da ruƙo hannun Sgr yace"Mu tafi,"sallama su kayi mata tare da fucewa daga ɗakin, Hawa saman gadon tayi suna fuskantar juna,tallabo fuskarshi tayi da hannayenta biyu,suka zuba ma juna ido,na wani lokaci kafin tace"Hubby,ka natsu ka saurare ni,Nasan zaka fahimce ni,Kuma kai musulmi ne!kayi imani da ƙaddara mai kyau ko mara kyau haka ne"?kamar wani ƙaramin yaro haka ta mayar dashi, Nodding kai yayi mata alamar eh,   Murmushi ta ɗan sakar mashi tare da cewa"haka nake son ji my hubby,"dakatawa ta ɗan yi da yin jawabin tana kallonshi,saboda ta kasa furta mashi abunda take so ta faɗa,farin ruwa ta gani ya kwanta acikin idanuwanshi,la66ansa na kerma yace"Pls tell me the truth,Meya faru ne?kowa ya sauya mun,Dama ni sai da raina ya bani cewa wani abu ya faru da baby junaid ɗina,"jikinshi har ya fara kakarwa kamar wanda sanyi ya kama,    Hawaye ne suka ciko tab a idonta, "Am sorry to say,Junaid yana cikin ƙoshin lafiya,Amma baya atare damu,Rafayet ya sanar dani cewa,since yesterday night around 8 suna kan hanyar dawowarsu gida,kidnappers suka ɗaukesu gaba ɗayansu,"   Jin wannan maganar yasa hankalinshi yayi mugun tashi,wata irin zabura yayi yana ƙoƙarin saukowa daga saman gadon,Da sauri ta ruƙo rigar jikinshi"dan Allah ka natsu ka saurare ne...."    Girgiza kai ya shiga yi yana faɗin"banga ta zama ba,Anyi garkuwa dasu junaid ɗina,Wlh bazata sa6u ba,duk inda junaid da jahad suke adawo mun dasu cikin daren nan in har anason zaman lafiya,wannan wani irin shashanci ne?har junaid ya kwana a hannun kidnappers tun jiya arasa wanda zai ƙwatosu daga hannunsu,Banga amfanin sojojin dana tara acikin gidan nan ba,Nikaina bani da amfani kenan!Kowa ma bai da amfani mun zama tamkar kwankwan ashana,tunda har bazamu iya ceto rayuwarsu ba,"idonshi ya rufe sai faman zazzaga masifa yakeyi,Ƙarasa saukowa yayi daga saman gadon,buguzun buguzun ya kama hanyar fita daga bedroom ɗin nashi,da sauri Alex tabi bayanshi,tana ambaton sunanshi   Ko sauraronta baiyi ba,da alama ya zauce ne,   "Yau ƙafata kafarsu junaid zamu dawo cikin gidan nan duk inda suke saina dawo dasu,abun ban haushi wai anyi garkuwa dasu junaid?sai kace ƴa'ƴan wani me siyar da kifi abakin titi,Ƴa'ƴana ne fa!Ni chief of army staff na Nigeria gaba ɗaya,banga amfanin matsayin da nake dashi ba Allah,tunda har za'a iya yin kidnapping ɗin ya'yana,wlh bazan yafewa kaina ba,in har bandawo da junaid cikin gidan nan ba,"ranshi amatukar 6ace yake yin maganar,jijiyoyin wuyanshi duk sun firfito waje,   "Pls hubby Calm down ur mind,Ina zaka je ne?acikin daren nan!indai akansu junaid ne,na tabbata zasu dawo ne"   Guntun tsoki yaja tare da cewa"baki da hankaline,da alama bakisan zafin haihuwa ba,Shiyasa kike faɗin hakan,"   "Ni fa na haifeshi,taya zaka ce mun bansan zafin haihuwa ba?Ya kake so nayi ne?ka ƙi tsayawa nayi maka bayani,   Su Marshal na zaune asaman sofa,kowa da abunda yake saƙawa aranshi,kwatsam suka jiyo muryoyinsu,nan fa suka miƙe suna kallonsu,    Ganin Abbansu ya nufi hanyar fita daga falon ko takalma babu a ƙafarshi,da sauri suka sha gabanshi,   Rufe ido yayi atsiwace yace"Ku matsa ku bani wuri,wlh Omar ka bani mamaki,ko ince kun bani mamaki,How many hours su junaid na a hannun kidnappers amma baku iya ƙwatomun shi ba,babu wani mataki da kuka ɗauka,to ni zanje in dawo da abuna,"yana magana huci na fitowa daga bakinshi,    Ruƙo shi Omar yayi tare da fashewa da matsanancin kuka,Girgiza mashi kai ya soma yi batare da ya furta mashi komai,jikin Abbansu ba ƙaramin sanyi yayi ba,Cos ya manta when last yaga hawaye a fuskar Omar,tabbas abun na ci masu rai sosai,Mayar da idanuwanshi yayi kan Sgr,Hawaye ya gani kwance Luf acikin idanuwanshi,wanda tunda yake arayuwarshi bai ta6a ganin ruwan hawaye a idon Sgr ba,tun ma da aka haifeshi har suna expecting ko baida cikakkiyar lafiya ne,    "Omar!kuka kake yi mun"?yayi maganar yayin da hawaye suka soma wanko fuskarshi,Kallon Sgr yayi tare da cewa"Kaima kukan zaka yi mun"?   Duƙar da kanshi yayi ƙasa,gaba ɗaya jikin kowannansu yayi sanyi,   "Abba,ka tausaya mana muna cikin matsananciyar damuwa na rashin Su junaid atare damu,Mun rasa yaya zamuyi,munyi tunanin zaka ƙarfafa mana guiwa wurin ganin mun ceto rayuwarsu,Amma sam kaƙi tsayawa kaji abunda muke son mu sanar dakai balle har musa ran zaka fahimce mu...."ya ƙarasa maganar tare da sanya tafin hannunshi yana share hawayen dake sauka a fuskarshi,    "Abba,saboda rashin su junaid,ko bacci ba muyi ba,Yadda muka ga dare haka muka ga rana,Ga rafayet nan saboda shi,Ya baro kano ya dawo Abuja tunda sanyin safiya,dukanmu nan babu wanda ya iya kora koda ruwa ne ta maƙoshinsa,duk don saboda 6atansu junaid...."dakatawa ya ɗan yi da yin maganar yana kallon Abban nasu,da alama ya fara saukowa   "Kaine ka haifemu,kafi kowa sanin su wanene mu!me zamu iya da kuma wanda baza mu iya ba!Nasan ka yarda damu sosai,Idan har akwai wanda zai bada shaida akanmu kaine Abba!meyasa bazaka yi mana uziri ba?idan har bamu bi komai a hankali ba wurin ganin mun ceto rayuwarsu,Toh zamu rasa su ne gaba ɗayansu!"   Juyawa Abba yayi ya soma tafiya cikin falon,Saman sofa ya zauna,ganin haka yasa suma suka dawo saman Sofa ɗin suka zauna suna fuskantarshi,Itama Mommy ta samu wuri daga gefen shi ta zauna, Duk wannan abun dake faruwa akan idon ƙannensu,don tun lokacin da Abbansu ya fito yana sambatun nan,Kowannansu ya fito daga bedroom ɗinshi,Jikin kowannansu yayi mugun sanyi,jin cewa Anyi kidnapping ɗinsu Junaid,Abun ya ta6a masu zuciya sosai, "Har tsawon wani lokaci,kuke so na baku ku dawo mun dasu junaid"?Acewar Abba,   Shiru sukayi gabansu na faɗuwa,Omar ne yayi ƙoƙarin cewa"1 week"a hanzarce Sgr yace"Omar that's impossible,ka manta yarda mu kayi dasu ne?Sunyi mana alƙawarin cewa in dae aka yi masu yadda suke so zasu sakosu,Amma ba a tare ba,saboda suna ganin za'a gano su adau mataki, akwai yiyuwar su fara sauko junaid shi kaɗai acikin satin nan ko kuma su fara sakin Jahad,Ni ina ga kamar one month yayi,Kafin lokacin in sha Allah mun dawo dasu duka acikin gidan,   Girgiza kai Abbansu ya ɗan yi tare da cewa"Har one month!su junaid basa atare damu?idan suka cutar dasu fa?   "Abba sunyi mana alƙawarin cewa in har zamu biyasu yadda suke so,bazasu cutar mana dasu ba,"   "Nawa suka buƙata"yayi tambayar yana kallon faces ɗinsu, "har yanzu dai su muke jira,sunce zasu kira su sanar damu,sannan sunce mu kwantar da hankalinmu,Bazasu ta6a cutar dasu ba,Zasu basu kyakkyawar kulawa,kuɗi kawai suke buƙata ba wani abu ba,"Omar ne ya kora mashi jawabin   Cike da takaici Abba yace"just because of money,suka ɗauke mun ƴa'ƴana?Ae da sun sani sun nemi tallafi a wurinmu konawa ne zamu basu basai sun ɗauke mun su ba,"    Miƙewa yayi sam babu kuzari ajikinshi,tafiya ya soma yi dakyar yake iya ɗaga ƙafarshi,har sai da yabar wurin Sofas ɗin,Sannan ya dakata da yin tafiyar,ya waiwayo tare da kallonsu,gaba ɗaya idanuwansu na akanshi,   Magana ya soma yi masu babu wasa a fuskarshi"Omar!"   "Na'am Abba"ya amsa mashi, "Rafayet"shima ya amsa mashi"Na'am Daddy,"    "Na yarda daku sosai,abu biyu nake tsammani daga wurinku,Na fako ku dawo mun dasu junaid,Cikin ƙoshin lafiya,Na biyu kuma ku kawo mun waɗannan gur6atattun mutanen da sukayi garkuwa dasu,Wallahi thumma tallahi idan har ku kasa yi mun waɗannan abubuwan dana lissafa maku,inaso ku sani Za ku rasa ni ne,NA HAR ABADA,daga yau zuwa 30 ga watan da zamu shiga,a kowace rana zan fara sa ran dawowarsu acikin gidan nan!kuma daga ranar ku fara ƙirgen ranakun da su kayi mun saura acikin duniyar nan   *Tashin hankali!* Mikewa Mommynsu tayi tare da kallonsu gwanin ban tausayi tace"Na yarda daku sosai,ku taimaki rayuwar mahaifinku,Zamu taya ku da Addu'a Har Allah yasa kuyi nasara akan kidnappers ɗin nan,"tana kai ƙarshen maganarta,tabi bayan abbansu,   "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"wannan shi ne abunda ke fitowa daga bakunansu,basu ta6a ganin tashin hankali irin na wannan ranar ba,A tsaye kowannansu ya kwana,har sun fara regretting ɗin ƙaryar da suka shirya ma Abbansu, Acikin waɗannan kwanakin,Komai ya hargitse masu,safe da marece dare da rana,kullum cikin Zullumi suke,Suna cikin tashin hankali,Duk sunbi sun firgice,kallo guda zaka yi masu ga gane cewar basa a hayyacinsu,Don gaba ɗayansu daga Omar ɗin har Sgr babu wanda baiyi rama ba ajikinsu,gidan ya zama tamkar maƙabarta,Babu wani sauran farin ciki daya rage masu,Saboda rashin junaid babu mai samun isasshen bacci acikinsu,Abinci ma har Azmee ta fara gajiya da girka masu saboda Asarar shi da akeyi,Yadda ta ajiye haka take zuwa ta same shi,duk rana ta Allah sai Abbansu ya tunasar dasu Adadin kwanakin daya rage masu na ƙwato su junaid a wurin kidnappers,yayin da suke cikin wannan tashin hankalin,Abusufyan na can suma ba kwanciyar hankali wanda hakan ya ɗauke hankalinshi gaba daya batare da ya fahimci halin da gidan suke ciki ba,Ciwon abu ya tashi gadan gadan,Kullum da daddare sai ta dinga kuka tana buge buge tana faɗin sunan sayyadi,hakan ba ƙaramin ruɗani ya sanyasu ba,har Sehrish ta fara zargin cewa,kodai yafara yi mata gizau ne?Anya ba wani abu ke faruwa ba?duk yadda taso Oummansu ta sanar da ita abunda take gani,Hakan ya faskara saboda bata da hankalin da zata iya fayyace mata komai,a ƙarshe dole sehrish ta koma ɗakinta da kwana,duk in haukan nata ya motsa da zarar ta fara raira mata karatun Alƙur'ani sai ta samu natsuwa,a haka suke samu tayi bacci, A 6angaren Su Hayaam kuwa,ba ƙaramin daɗi suka ji ba,lokacin da Abra ta dawo abuja,Batare da tasha wahala ba,bayan An sallami Hayaam daga Asibiti gidan Amani suka koma,Zasu zauna na ɗan wani lokaci kafin su wuce Maiduguri,duk wannan budurin da sukeyi basu son abunda ke faruwa acan gidansu na maiduguri ba,Sun manta da mahaifiyarsu da suka baro kwance ba lafiya rai hannun Allah, A 6angaren Aunty babba kuwa ba ƙaramin jiki taji ba,tun bayan da mai motar nan ya hankaɗe ta a Enugu,daƙyar aka samu wani bawan Allah ya ɗauketa a motarshi suka kaita asibiti,Taci baƙar wuya kamar bazata rayu ba,tsawon sati tana kwance a gadon asibiti batasan inda kanta yake ba,Komai ya ƙare mata ƙarƙaf,mutumin daya kawota asibitin tun da ya biya kuɗin da za'a yi mata aiki a ƙafarta da ta samu matsala,bai ƙara tako kafarshi yazo ba,Ga ciwo yaƙi ci yaƙi cinyewa,ta ɗuri ruwa,tayi suntum da ita,daga baya ta ru6e sai uban wari dake fitowa daga jikin ƙafar,Likitoci sunyi iya kar bakin ƙoƙarinsu wurin ganin sunyi mata magani,amma abun ya ci tura,da suka gaji gashi babu wani danginta a kusa,kuma babu kuɗin da zasu cigaba da kula da ita,A ƙarshe Suka sallame ta daga asibitin,Tashin hankali!ko ya rayuwar Laila zata kasance"?   Yau Two Weeks kenan da mutuwar Junaid,Wanda ya kasance Wata biyu cuf da sati ɗaya da yin auren Sehrish Abusufyan da Rafayet salahuddeen,duk da muna sa ran kwanakin auren nasu zai ƙara tsayi saboda Sgr ya ɗaga tafiyarshi ta komawa U.s,Zuwa Next One Month,dalilin ɗaga tafiyar tashi saboda Investigation ɗin da sukeyi na ƙoƙarin gano waɗanda suka kashe Junaid,Ga kuma Abbansu daya zuba masu ido yana jiran su dawo mashi da ƴa'ƴanshi,bawan Allah ko bacci bai samu,duk ya rame ya fige,bai samun bacci da daddare saboda sallar daren da yake yi, haka zai zauna saman darduma yayi ta yi masu addu'a,Allah ya dawo mashi da ƴa'ƴanshi,ita kanta Mommynsu junaid tana cikin mawuyacin hali,cos ta fara zargin cewa ba Kidnapping ɗinsu akayi ba,there's something behind da suka 6oye masu,har sun fara fidda rai da dawowarsu,A ranar Litinin sai ga JAHAD ta dawo gidan da ƙafafunta,Murna a wurinsu kamar su haɗiyeta,duk da sun shiga damuwa ganin yadda ta rame ta fige,duk ta fita hayyacinta,ƙashin wuyanta duk ya firfito kamar zai fasa fatar wuyanta,Taji jiki sosai,Idanuwanta duk sun kumbura,duk yadda suka so jahad ta buɗe baki ta faɗa masu ina junaid yake,taƙi magana bakinta a rufe yake,sai dai kawai ta dinga binsu da ido,bakomai ya hanata yin magana ba,fa ce kukan dake cinta,muddin ta buɗe bakinta to zata fashe masu da kuka ne,kuma ta ɗaukarwa Su ya Omar alƙawarin bazata tona masu asiri ba nace wa junaid ya mutu,har sai lokacin da suka shirya sanar dasu,tunda ta dawo gidan nan,Ta zama salihar ƙarfi da yaji,magana saita zama dole sannan take yinta,ko ɗakinsu batasan fitowa daga ciki,tun hosana na lalla6ata don ta faɗa mata abunda ke damunta,saboda kullum sai ta farka ta sameta tsakar dare tana sallah hawaye na gangarowa akan fuskarta,Har tagaji da tambayarta ta ƙyaleta, Kullum ne in zata kwanta da daddare sai ta ɗaukko wannan zanen fuskar junaid da tayi a cikin drawing book ɗinta,ta tasa shi gaba tayi ta kallo,Wani lokacin ta fashe da kuka wani lokacin kuma tayi murmushi,bakomai yafi tsaya mata araiba,kamar rana ta farko da ta fara haɗuwa dashi face to face,Yayi tsammanin Sehrish ce,ya ruƙo hannunta ya turata cikin motarshi,ya tasa ta gaba da wannan kyakkyawan murmushin nashi,jahad tayi kuka tamkar ranta zai fita,har ya bi jikinta,in har bata zubda kwallaba ita kanta bata jin daɗin jikinta,wani sa'in idan raɗaɗin yayi mata yawa ƙur'ani take ɗauka ta zauna tayi ta karantawa har ta samu sauƙi acikin zuciyarta,Sau dayawa Omar yakan kirata a garden su zauna yayi ta lallashinta,yana yi mata nasiha,hakan yasa ta fara samun sauƙin raɗaɗin da zuciyarta keyi mata,har ta fara sakewa da kowa acikin gidan,hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba,Yanzu saura dawowar Junaid suke jira shima Masu garkuwar su sako shi,😥rashin sani yafi dare duhu *Boss Bature* Kano State, Wuraren ƙarfe 8 na dare,Sehrish ta fito daga cikin toilet,chest ɗinta ɗaure da towel,ta canza sosai,duk da babu kwanciyar hankali atare da ita,Ciwon Oummansu ba ƙaramin ɗaga mata hankali yake yi ba,harta fara murnar zasu koma gida,sae kuma abu ya dawo gadan gadan haukan take yi,wardrobe ta nufa tare da buɗewa,ta dauko kayan baccinta riga da wando ta zurasu ajikinta,bayan ta kammala sanya kayan,gaban mirror ta koma ta zauna tana kallon fuskarta acikin madubin,ta ƙara kyau da haske,mayukan da take amfani dasu ba ƙaramin gyara suke yi ma jikinta ba,tunani ta shiga yi yau saura satittika suka rage aurenta ya mutu da Sgr,ta ɗan damu da rashinsa a kusa da ita,kusan kullum ne saita tura mashi text message a wayarshi,Sometimes yana maido mata da reply,harma ya tambayi ya lafiyar Oummansu,hakan ba ƙaramin daɗi yake yi mata ba, Kiran wayane ya shigo,nan take wayarta ta soma ruri,jiki na rawa ta miƙe daga saman kujerar ta nufi inda ta ajiye wayar asaman pillow,hannu tasa ta ɗauki wayar tare da duba sunan mai kiran nata,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta ganin sunan Mommy Azeema ya bayyana akan screen ɗin wayar,Cike da zumuɗi ta ɗaga kiran, "Assalamu alaikum mommy" On the other hand mommy Azeema tace"wa'alaikumus salam my Daughter hope kina lafiya," Shiru Sehrish tayi batare da ta bata amsa ba,ƙasa kasa ta soma shessheƙar kuka, "Daughter,kuka kikeyi koh"?nan ma shiru bata amsa mata ba, "Kinyi missing ɗin mommynki ko?, Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Eh mommy,kin manta dani,ina cikin damuwa sosai,ta ko'ina ba sauƙi,dama kece kike kwantar mun da hankalina,gashi yanzu kona kira baki ɗagawa," "Am sorry daughter,Nasan ban kyauta maki ba,Amma yanzu ki kwantar da hankalinki,In sha Allah this week zamu zo nan Abuja,Munyi waya da Abusufyan ya sanar dani cewa,Zaku dawo tare da Oummanku ko! sehrish tace"Eh," "Naji daɗi sosai,Ban kira na tayaki murnar ganin Oummanku ba,Wlh na yi farin ciki sosai,har ina cewa gwaurancin Abusufyan ya ƙare tunda sanyin idaniyarshi ta dawo," Murmushi sehrish ta saki,hajiya azeema taci gaba da cewa"Baki bani labarin rayuwarki da Sgr ba?ya ake ciki?ko har yanzu babu wani sauyi"? Komawa sehrish tayi gefen gadon ta zauna,A tsanake ta labarta mata irin zaman da sukayi dashi," Hajiya azeema tace"Good,Koba komai ta wani 6angaren hankalinshi ya fara karkata akanki,Wannan ma mataki ne na nasara" Dakatawa tayi da yin maganar tana sauke ajiyar zuciya,kasa kunne sehrish tayi tana jiran jin me zatace mata, "Yaushe zaku dawo kano?kamata yayi ace kuna tare da juna,banji daɗin komawarshi Abuja ba," "Gobe muka shirya komawa gida,Amma ciwon oumman mu sai ƙara gaba yake yi,bansani ba ko tafiyar na nan,ko an fasa,Daddy nake jira ya dawo na tambayeshi," "Kisan yarda zakiyi Ku koma Abuja,if not duk wani shirin mu zai lalace ne,Ita kuma Oummanku,Allah ya bata lafiya,zamu tayaku da addu'a,Zan yi magana da daddy ɗin naku gaskiya ƙwara adawo da ita nan Abuja,zata fi samun caring,ga kuma su hosana da jahad,idan tana ganinku ku uku atare sai inga kamar zata iya dawowa hayyacinta in a short time," Sehrish ta Gamsu da bayaninta ita kanta tayi tunanin hakan, "Nagode sosae Mommy,Allah yabarmun ke,Har na kosa mu hadu,don nayi missing ɗinki sosai da sosai," dariya hajiya azeema tayi tare da cewa"don't worry ur self in dai nice har sai kin gaji da gani na,Am coming back soon,Dani za'ayi yaƙin karshen nan,da makamaina zanzo,mu bazama a filin daga har sai mun cimma nasara,"cike da Zolaya tayi maganar,hakan ba ƙaramin dariya ya ba sehrish ba,hada dafe cikinta,taji daɗin kiran da Hajiya azeema tayi mata,Ta sanyata farin ciki sosai,Sun jima suna waya kafin daga bisani suka yi sallama, Wurgi tayi da wayar saman mattress,fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi,tana cikin Nishaɗin nan ta soma jin faɗuwar gaba rass rass!tunani ta shiga yi ko mai yasa take jin faduwar gaba?kodai wani abu na faruwa ne,tana cikin wannan fargabar taji an kashe ƙwan falo,da farko bata damu ba,tun da ba ita kaɗai bace acikin gidan Akwai security guards zai iya yiwuwa ma Daddynsu ne ya dawo,dama ya sanar da ita cewa after isha' prayer zai wuce gidansu Maman sadeeq, Ƙwala mashi kira ta soma yi don taji idan shi ne ya dawo, "Daddy!Daddy!Daddy Abusufyan"!shiru ba'a amsa mata ba,nan fa ta soma zargin kodai wani ne ya shigo masu,Amma ae akwai security a gidan,kasa jurewa tayi hakan yasa ta mike tsaye,ta tunkari ƙopar ɗakin,a hankali tasa hannu ta buɗe ƙopar ɗakin ta fara leƙawa,ko'ina duhu babu haske a falon,motsin takun takalmi ta fara tsoro ne ya kamata,Zuciyarta sai harbawa take yi da ƙarfi da ƙarfi,wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,Sam takasa Motsawa,tabbas wani ne ya shigo cikin gidan tunda harta Ambaci sunan Daddynsu bai amsa mata ba,A ƙopar ɗakin ta tsaya cak kamar an dasa mata Aya,Saboda duhu ta ko'ina bazata iya hangen meke wakana ba acikin falon,tunanin kiran Abusufyan tayi,da sauri ta juya hannunta na kerma tana ƙoƙarin tura ƙopar ɗakin ta shiga daga ciki,Ta jiyo ihun Oummansu dake a downstairs,A gigice Sehrish ta juya da gudun gaske ta nufi downstairs,cikin rashin sanin ina zata taka saboda duhu ƙafafunta suka harɗe daga saman benen gaba daya ta rubza mashi,mirginowa ta dinga yi daga saman benen har ta faɗo ƙasa ta ƙume goshinta,Sosai taji raɗaɗin buguwar da tayi amma a haka ta jure ta daddage ta mike,tana laluban hanyar zuwa ɗakin Oummansu cikin duhun,Sosai take jiyo sautin koke koken da Oummansu keyi,Duk tabi ta ruɗe ta rasa ina zata dosa,   Da ƙarfi ta soma kwala mata kira"Oumma!Oumma!!"tamkar makoshinta zai 6allo waje,duhu ya hana ta gano kopar ɗakin,Bangon falon tabi ta dinga sanya tafin hannunta tana shasshafawa,da taimakon Koke koken da Oumman keyi ne ta samu ta ruƙo Handle ɗin kopar ɗakin,Da karfin ƙarfe ta sanya ƙafarta tare da Harba ƙopar ɗakin ta buɗe,Bata iya ganin komai ba saboda duhun da ɗakin yayi an kashe Hasken ɗakin kamar yadda aka kashe na Falo,   Shafa bangon tayi dayake tasan inda Switch ɗin yake,Cikin sa'a ta kunno shi ƙitt Haske ya gauraye ko'ina na ɗakin, Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu rasss!ƙwayar idonta tamkar zata faɗo ƙasa saboda Tashin hankalin da sukayi arba dashi,   Ta ko'ina ya mamayeta,ƙokarin rabata da kayan jikinta yakeyi,babu kunya babu tsoron Allah,Wani irin kukan kura Sehrish tayi bata dira a ko'ina ba sai asaman gadon,A hargitse ta Cakumi Wuyan rigar jallabiyar dake ajikinshi,da iya ƙarfinta na ƙarshe tayi wurgi dashi gefe guda,Ya gangara ƙasan gadon,   Fashewa tayi da matsanancin kuka,tana kallon Oummansu wadda tuni ta jima da sumewa asaman gadon,   Jijjiga jikinta sehrish ta shiga yi tana Ambaton sunanta,Dakatawa tayi da yin kukan tare da wurga ƙwayar idonta kan Mutumin wanda ke tsaye a bakin gadon,jallabiyace a jikinshi,kanshi kuwa Rawani ne,Ya sanya face mask a fuskarshi,"   Huci kawai takeyi tana kallonshi, Hannu yasa tare da zame takunkumin dake a fuskarshi,Mummunane sosai bai da kyau ko miskala zarratin,irin mutanen da kallo guda zakayi masu kaji ka tsanesu,Sehrish bazata ta6a mantawa da fuskar wannan fasiƙin mutumin ba,   Ranta a matuƙar 6ace tace"Mugu azzalumi!dama sai da raina ya bani cewa kaine!Ashe har yanzu kana bibiyar rayuwarmu!Wai uban mi muka tsare maka ne!Meyasa bazaka fita arayuwarmu ba!,"   Jinjina kai Ya sayyadi yayi yana kallonta batare da yace komai ba,sai da ta kammala balbaleshi da faɗa sannan yace"kin gama"?banza tayi bata tanka mashi ba,   "Bansan wacece ke acikinsu ba,Amma fitsarar da kikayi mun a yanzu ya tabbatar mun dacewa rishi ce ke,Dama tun kina yarinya kangararra ce ke,balle kuma yanzu da kika samu ƴanci kika zama cikakkar budurwa,har kika samu bakin gayamun magana,Ban zo nan don inyi jayayya dake ba,Wurin uwarku nazo don ta bani haƙƙina na aure dake akanta....." Tunkan ya ƙarasa maganar Sehrish ta Ambaci"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"dafe kanta tayi saboda jirin da take gani,Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata makoshinta,   Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Amma baka da kunya!Tunda nake banta6a ganin ɗan akuya bunsuru ba,wawa jakki ba,kuma daƙiƙi irinka ba!Wai kai wani irin Dabbane....."A fusace Sayyadi ya daka mata tsawa tare da furta"Kalas!karki kuskura ki ƙara jifana da waɗannan munanan kalaman!Ki iya bakinki in ba so kike na keta maki rigar mutunci ba awurin nan!ƙaramar ƴar iska kawai,kin manta lokacin da kuke rayuwa a ƙarkashin ikona?idan kin manta toh bari na tuna maki,"   Yayi maganar cike da sheƙiyanci yakai hannunshi tare da shafa gabanshi dake asandare yace"Ina fata kin tuna,"   Waro ido waje sehrish tayi yayin da idanuwanta suka cicciko tab da ƙwalla ta furta"Nashiga uku!"   Fashewa yayi da dariya kafin ya ɗaura da cewa"kin tuna lokacin da nake damƙar wuyanku in tasa ku gaba sai kun tsotsi gabana"?   Innalillahi wa'inna ilahirraji'un!fashewa tayi da matsanancin kuka na tashin hankali,Tsabar raɗaɗin tunawa da wannan ƙazantar yasa ta fara yunƙurin yin amai ga ƙirjinta da yayi mata zafi sosai,   Muryarta adisashe ta soma magana"Allah ya isa tsakaninmu dakai!Wlh Allah bazai ta6a barinka ba,Sai ya saka mana Cin zalin da kayi mana,in sha Allah tun agidan duniya zaka fara gir6ar abunda ka shuka,Ƙarshenka bazaiyi kyau ba Sayyadi,Sai kayi danasanin haihuwarka da Uwarka tayi acikin duniyar nan!Natsani ganin mummunar fuskarka fiye da yadda na tsani mutuwa,Munafuki,mugu azzalumi,fasiki,Sannan kuma matsoraci!tsabar bakin ciki ya hanaka sakat saboda ganin irin Canjin rayuwar da muka samu,Ni bansan wani tsautsayi bane yasa Oummanmu ta aureka ba,Nasan ba hakanan ka ƙyaleta ba,domin kuwa duk wata mace me hankali da tunani bazata auri dabba,daƙiƙi,bunsuru irinka ba,Jahilin addini jahilin rayuwa,Kana yin amfani da iliminka wurin cutar da rayuwar al'umma, idonta arufe take zazzaga mashi masifa,   Goya hannayenshi yayi asaman ƙirjinshi yana kallonta,maimakon yaji haushin kalaman da ta yada mashi,Sai ma yatsinci kanshi da jin sha'awarta,zuba mata kwartayen idanunwashi yayi yana bin jikinta da kallo batare data ankara ba,Kayan baccin jikinta shara shara suke,Subhanallah,   Sautin dariyar da taji ne yasa ta dakata da yin masifar,ta buɗe idanuwanta da sukayi jawuur dasu,Zuba mashi ido tayi tana kallonshi ganin yana dariya,   "Kin gama naki"?yayi maganar yana sakar mata wani shu'umin murmushi,   Shiru tayi batace mashi komai ba,la66anta duk sun bushe sun ƙame,ga ƙishin ruwa da take ji, "sai yanzu nake danasanin barinku da nayi araye!naso ace tun lokacin da kuke a hannuna na tattaraku gaba ɗaya na aika ku lahira,Amma Allah bai nufa ba,Duk yadda naso Sihiri na yayi tasiri akanku Amma hakan ya faskara,Na bibiyi rayuwarku tun lokacin da Mlm nura ya mayar daku wurin wata tsohuwa mai taurin kan tsiya......"   Tunkan ya ƙarasa maganar Sehrish tace"hakan na nufin cewa,kaine kayi silar mutuwarta"?   shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare dasa hannu yana gyara rawanin kanshi yace"ƙwarai kuwa!ni na kashe ta,saboda na nemi ta bani haɗin kai Wurin ganin na kawar daku,tayi mun gardama harda tofa mun kakin Majina ajikina,Wannan dalilin ne yasa nayi silar mutuwarta,duk da haka ban rabu daku ba,Bayan an kaiku Cell na tura inspector Esha donta tursasa maku akan ku amince Zaku amsa laifin ku kuka kashe ta,har kun amince sai kuma Ciwon Hosana ya tashi,Wanda hakan yasa Ƴan sanda suka kaiku Asibiti,Daga nan ne Allah ya haɗaku da Marshal Omar,har ya taimaki rayuwarku,Naji haushi sosai kamar na binne kaina lokacin,amma ba yadda na iya,Haka naci gaba da bibiyar rayuwarku,har lokacin da Omar yakai ku Kaduna gidan Yayanshi General Ishaq,Nan ma na biku don na kawar daku,babu wanda yasan duk wannan shirin nawa da nayi,Ni na tura matata wurin hafsat ɗiyar Laila,ta bata zunzurutun kuɗi har miliyan shidda donta Zubar mata daku,daga nan na halaka ku,hafsa ta kar6i kuɗin amma bata aiwatar da abunda ta sanyata ba,a ƙarshe ta buƙaci ta dawo mata da kuɗinta in ba haka ba zata yi ƙararsu........." Duk cikin abunda ya sayyadi yake faɗa mata bakomai yafi ɗaga mata hankali ba,fa ce Mutuwar tsohuwa,Ashe dama shi ya kashe ta duk don saboda su?Sosai ta fashe da kuka tana kallonshi hawaye wasu na bin wasu sam ta kasa furta komai,     Ko ajikinshi saima dariya da yake ta faman 6a66akawa kamar wani zautacce,    "Meyasa?meyasa duk kayi wannan"A fadace tayi maganar,jijiyoyin wuyanta duk sun fito ruɗu ruɗu dasu,    Tsagaitawa yayi da yin dariyar yace"ɗaukar fansa nake yi,ko ince mukeyi!Laifi akayi mana wanda bazamu ta6a yafewa ba,gaba ɗaya danginku a tafin hannunmu suke,duk wani motsi naku akan idonmu kuke yin shi,Nasan zaki yi mamaki,kuma zaki yi kokwanton ko ƙarya nake yi....."Hankali atashe sehrish take kallonshi,Ba ƙaramin Caza mata ƙwaƙwalwarta yayi ba,   "Nazo nan ne,Don in kashe mahaifiyarku bawai don in biya bukatata da ita ba,Sai dai kuma ganinki da nayi yasa na canza ra'ayina akan hakan,Surar jikinki ta yi matukar tafiya dani,Yanzu haka da nake magana dake,tsuma kawai nakeyi,kin matukar tayar mun da sha'awata,tunda nake ma ni ban ta6a jin sha'awar mace ba,Sai da nayi tozali da kyakkyawar surar ƙirjinki,Nayi mamakin yadda kika Cika ta ko'ina,ba kamar yadda na sanki ba,Kai gaskiya Abusufyan ya iya raino,Naira ta zauna maki shiyasa kika canza," A ruɗe Sehrish take furta"Allahumma ajirni fil masibati wa'aklifni khairan minha,tsananin tsoro ne ya kamata,ganin ya sanya hannu yana ƙokarin tattare jallabiyar dake ajikinshi,Tashin hankali! ..girgiza kai ta shiga yi tana fadin"karka kuskura kace zaka kusanto ni,Ni matar aure ce,"a ruɗe tayi maganar tana ƙoƙarin saukkowa daga saman gadon'..    "Oh ashe ke matar aure ce,wannan ae ba wani abu bane dan naci amfanin gonar wani,"    Durowa tayi daga saman gadon tare da nufar ƙopar fita daga ɗakin,Aikuwa a zafafe Ya sayyadi ya biyo bayanta,kafin tayi wani yunkuri ya damƙi rigar baccin dake ajikinta,nan take rigar ta zame har izuwa mid back ɗinta,Fashewa ta kuma yi da matsanancin kuka tana ambaton Sunan Daddynsu,ƙoƙarin kwale mata rigar yakeyi gaba dayanta amma ta hana hakan,Ba zato ba tsammani taji yana goga mata abun gabanshi ta bayanta,Wa'iyazu billah,Daddagewa tayi da iya karfinta na ƙarshe,Ta kai mashi naushi a tsakiyar cikinshi,Amma wani abun mamaki ko gezau baiyi ba,Kamar ta naushi ƙarfe,kiciniyar ƙwace kanta ta shiga yi daga hannunshi,Ji take kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu saboda takaici,   Saukar harshenshi taji asaman fatar bayanta,kamar wani maye haka ya dinga lashe shi,   "Wayyo Allah na Oumma!na shiga ukku nabani na lalace!"cikin fitar hayyaci Sehrish ta samu hannunshi daya zagayo dashi ta gabanta,Ta daddage ta gartsa mashi cizo har saida ta fasa fatar hannunshi,raɗaɗin da yaji ne yasa shi yin saurin sakinta,A hanzarce ta sanya hannunta tana ƙoƙarin buɗe ƙopar ɗakin,Sayyadi ya taɗiyo ƙafarta gaba daya ta kife ƙasa,kanta ya bugu sosai,fashewa tayi da matsanancin kuka tana bugun floor ɗin da hannunta,Ta rasa ina zata tsoma ranta,jin motsinshi yasata yin saurin miƙewa zaune tana ja da baya,   Cikin Shesshekar kuka take Ambaton sunan Daddynsu da sunan Oummansu don su kawo mata ɗauki,   Hannayenshi ya sanya tare da tattaro jallabiyar jikinshi ya ɗage ta sama har izuwa saman cikinshi ya naɗe ta,tsikar jikinta ce ta fara tashi,ganin uban cunkoson gashin jikinshi mara kyan gani,hannu yasa ya kwale gajeran wandon nashi,Rasss taji mummunar faɗuwar gaba,   Dariya ya dinga yi yana nuna mata abun nasa yayin da yake tunkararta tana ƙoƙarin ja da baya,   Koke koken da sehrish keyi ne ya fara kai mata ziyara cikin kanta,lokaci guda Kwakwalwarta ta fara tariyo mata kukan ƴa'ƴanta yayin da suke ambaton Sunanta,Oumma Oumma aduk lokacin da suka shiga wani hali,Allah ne ya farfaɗo da ita,Hannu tasa tare da dafe kanta wani irin raɗaɗi ta dinga ji yanayi mata,tunkafin ta buɗe idanuwanta ta soma ambaton Sunayensu Sehrish Hosana Jahad,wani ihu da sehrish ta kurma ne yasa ta yin firgit ta mike zaune daga saman gadon,Zazzare idanuwanta tayi akan sayyadi daya duƙufa akan Sehrish,Ya sanya duka hannayenshi ya tallabo kanta yana ƙokarin Kafa bakinta agabanshi,Hasbunallah!   Kukan kura abu tayi a fujajen ta diro daga saman gadon,a harzuƙe ta rarumi Side drawer ɗin gadon,gaba daya ta kinkimota ta ɗaga sama da gudun gaske,Bata sauketa a ko'ina ba sai akan sayyadi gaba ɗaya Ta rotsa mashi ita asaman kanshi,wani irin jiri ne ya ɗebe shi ya soma tangal tangal zai faɗi,Rawanin kanshi tuni ya yi tsalle ya fadi kasa,   Tsabar raɗaɗin da yaji ne yasa shi sakin Wuyan sehrish,Jallabiyarshi ta sauko ƙasa daga naɗewar dayayi mata,Rawanin kanshi kuwa tuni ya wargaje aƙasa,wani irin jiri ya soma gani kafin ya dawo hayyacinshi,Ganin Abu yasa shi ɗaure fuskarshi tamau,idanuwannan sunyi jawur dasu babu ɗigon Imani akansu,Kallon kallo suka shiga yi,jinjina kanshi ya yi yana huci kamar wani mayunwacin zaki,gadan gadan ya tunkareta,gashin kanta ya damƙo tare da yin wurgi da ita,gaba ɗaya ta kife ƙasa,juyawa yayi ya koma kan Sehrish wadda ke yashe ƙasa a sume,naɗe jallabiyar jikinshi ya soma yi,zukunnawa yayi agabanta yana ƙoƙarin tallabo kanta, Abu dake kwance a ƙasa,ta ɗaɗɗago da kanta,yayin da hawaye ke ta sharorowa akan fuskarta,karaf idanuwanta suka sauka akan Sirinjin Allurar da Likita yayi mata ɗazu da safe,Wani tunani ne yazo mata,matsawa tayi tare da miƙa hannunta,ta Damƙi sirinjin allurar,yunkurawa tayi ta miƙe,cikin sanɗa ta soma tafiya tana tunkararshi,motsin da ya ji abayanshi ne yasa yayi firgit,Juyowar nan da zaiyi don yaga me take ƙokarin yi mashi,Ba zato ba tsammani,Abu ta daddage ta burma mashi Allurar acikin ƙwayar idonshi,Zuruf ta nutse acikin ƙwayar idonshi,Wata irin ƙururuwa Sayyadi yayi,Gaba ɗaya yabi ya firgice ya gigice ya zauce,Wani irin raɗaɗin Azaba mara misaltuwa Yaji mai haɗe da zogi,Caccaka mashi allurar ta dinga yi,gaba daya ta tsiyaye mashi idanuwanshi duka biyun,sulalewa yayi kasa yana burgima,Wata irin ƙururuwa da ya soma yi gaba daya kwaratsin shi ya karaɗe ko'ina na cikin gidan,Abu ta shammace shi,ta naƙasa mashi idanuwanshi wanda ya kasance rauninsu ne,a ƙungiyarsu ta matsafa da zarar member ya rasa idonshi,duk wani sihiri na jikinshi zai rabu dashi ne,Ya dawo normal mutun kamar kowa, Tsananin tsorone ya kama abu ganin yadda jikin ya sayyadi ke fitar da wani irin baƙin hayaki batare da wuta naci ajikinshi ba,kamar tsumma haka ya nannaɗe wuri guda,hannu tasa tare da toshe kunnuwanta,Saboda sautin kururuwar da yake yi tamkar  Ana buga ganga acikin kunnuwan nata haka take ji,sosai ta runtse idanuwanta, Lokacin da ta buɗe su,Sai da ta tsorata,ya 6ace 6aat babu shi acikin ɗakin sai dai Tsummar jallabiyarshi tare da rawaninshi,da kuma sharba sharban Silifas ɗinshi, *Boss Bature* A hankali yake saukowa down stairs,jikinshi na sanye da Jeans tare da t.shirt fara,gaba ɗaya ya canza,komai nashi ya sauya,tamkar ba Sgr ba,kwata kwata babu annuri akan fuskarshi,ya ƙara haske sosai,ya kuma yi rama, Jin takun tafiyarshi yasa suka ɗago suna kallonshi,Tsayawa yayi yana ƙare masu kallo one by One,Fuskarshi ɗauke da matsananciyar damuwa,kullum ne sai sun zauna Zaman jiran dawowar junaid,babu yadda baiyi dasu ba akan su daina hana idonsu bacci Amma sun ƙiya,koda zasu yi baccin to sai dai ya ɗaukesu anan falon,Yayin da suke zaune zaman jiran dawowar junaid, Ƙarasa saukowa yayi daga Saman stairs ɗin Ya nufi wurinsu,tunkan ya isa yace'Bana hanaku zama anan ba"? Shiru sukayi saboda basu da amsar da zasu bashi, Fitowa azmee tayi daga kitchen ta tunkaro wurin da suke,ƙarasowa tayi tana faɗin"Yawwa Rafayet,Dan Allah kayi Masu magana,tun ɗazu nake fama dasu akan suci abinci amma sun ƙiya,narasa yadda zanyi dasu,   Ɗaure fuska jahan yayi tare da cewa'Dan Allah abarmu muji da abunda ya Dame mu,Idan muna jin yunwa zamu taso ne muci,"   Yana kai ƙarshen maganar Fawan yace"Ni wlh komai ya fita raina,Nasaba cin abinci tare da baby junaid ɗinmu,yanzu kuma babu shi,Taya ma zan iya Cin abinci?bayan bansan halin da junaid yake ciki ba,Shin yaci abinci ko bai ci ba,"ya ƙarasa maganar tamkar zai fashe da kuka,    "Allah yasa basu cutar mana dashi ba,Junaid ya saba rayuwarshi acikin ƴan uwanshi,hakanan wasu mugaye marasa imani sun ɗauke mana shi,"Acewar Irfan,   Guntun tsoki jabeer yaja kafin yace"Ni babban takaici na,Duk yawanmu nan,arasa wa za'ayi garkuwa dashi sai junaid,Saboda bakin Hali irin na mutanan nan,wlh duk ranar da sukayi kuskuren da Asirinsu ya tonu sai sun ɗanɗani kuɗarsu," Kasa kunne Sgr yayi yana sauraronsu,tsananin tausayinsu ne ya kamashi,Ita kanta azmee jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba jin maganganun da sukeyi,Banga laifinsu ba,dole ne suyi kukan rashin junaid,yaron ne akwai shiga rai,Ya damu da kowa,kowa nashi ne,   "Wlh bazamu iya jure rashin junaid ba,Ya rafayet dan Allah idan sun ƙara kira,A sanar dasu cewa,Su dawo mana da junaid,Ni su ɗauke ni,In yaso ma su ruƙe ni na har abada,"Ayaan ne yayi maganar,yayin da yake share hawayenshi,   "Yaya rafayet,dan Allah nima idan sun kira ace masu ga wani ƙarin ma,"khaleed ne yayi maganar idonshi arufe Kamar maijin bacci,   "Wlh tun ranar da aka ɗauke mana junaid,ban ƙara yin wanka ba,na ƙuntata rayuwata ne saboda Nima in ɗanɗani irin raɗaɗin da junaid ke ji a hannun waɗancan Azzaluman mutanan"yana kai ƙarshen maganar ya sanya tafin hannunshi tare da rufe fuskarshi yana kuka,abun ya ta6a masu zuciyarsu sosai, Juyawa azmee tayi da sauri ta koma kitchen saboda kukan daya ciyota, Cike da takaici Jahan yace"wai sun ɗauke junaid saboda kuɗi.......... 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Am sorry, "Is Enough!"tsit su kayi basu ƙara cewa uffan ba,   "Kafin nan da 3 minutes inaso inga kowa asaman dining chairs yana cin abinci" Miƙewa suka yi ba don sun so ba suka nufi dining area,kowa yaja kujera ya zauna,wuri ya samu shima ya zauna,tare da ƙwalawa Azmee kira, Fitowa tayi daga cikin kitchen ɗin fuskarta duk alamun hawaye,Serving ɗinsu ta shiga yi,daƙyar suke Cusa abincin abakinsu, "Kunsan Allah!kaf sai kun cinye abincin nan,its better ku saki jikinku," Loma suka soma yi,Suna ci hawaye na zuba,kowa da abunda yake ayyanawa aransa,   "Babban yaya,kaifa?ba zaka ci ba?" Fawan ne yayi maganar, Ɗaga mashi kai kawai yayi batare da yace ƙala ba, Takun takalmi suka jiyo kamar ana tunkarosu,ɗagowa sukayi da idanuwansu suna kallon mai shigowar,Mommy ce jikinta sanye da Sleeping dress,ƙarasowa tayi ta samu wuri gefen Sgr ta zauna,   Hada baki su kayi wurin gaisar da ita Mommy barka da dare,   "Yawwa Sons,"ataƙaice ta amsa masu tare da kallon Fuskar Sgr dake a gefenta,   "My son,har Yanzu ba zaka daina sa damuwa aranka ba?ina fa sane da irin yarda kake rayuwa acikin gidan nan yanzu,Ba abinci ba bacci taya zaka samu natsuwar yin investigation akan Kidnappers ɗin da Suka ɗauke mun Romeo ɗina"idanuwanta cike tab da hawaye ta karasa maganar,   Calmly ya furta"Mommy,don't worry about that,Addu'arki kawai nake buƙata,"   "Kullum haka kake ce mun,why should i not worry?addu'a dama inayi maka,Ni so nake inga kana cin abinci kuma kana bacci",   Bai amsa mata ba sai ma fawan da yayi ma magana"Fawan,Call Jahad for me,"miƙewa fawan yayi jiki ba ƙwari ya nufi bedroom ɗinsu Sehrish, mayar da hankalinshi yayi kan Mommy   "She needs ur caring,tana cikin wani hali na buƙatar uwa atare da ita,Fawan zai kira maki ita,pls ki bata kyakkyawar kulawa,"yana kai ƙarshen maganar ya miƙe da sauri yabar dining ɗin,sam baison anayi mashi magana akan halin da yake ciki, Girgiza kai kawai tayi,ita kanta jurewa kawai takeyi, A bakin ƙopar ɗakinsu Fawan ya tsaya tare da sanya hannu yana kwankwasawa, "Wanene,"muryar hosana ce yaji ta amsa mashi,  "Ya fawan ne,jahad ake kira,"   bude mashi ƙopar Hosana tayi tare da ɗan leƙo da kanta tana kallonshi,   "where is she"? Nuna mashi cikin ɗakin tayi da hannunta,Jahad ya hango kwance saman Darduma,   "Kamar bacci take yi ko"? Jinjina mashi kai tayi"Eh,"   "Ta ci abinci" "A'a,bata ci komai ba," ."Okey taso mun ita," Juyawa tayi ta koma cikin ɗakin zuƙunnawa tayi agaban jahad tare da sanya hannu tana bubbuga bayanta   "Jahad!jahad!"mutsu mutsu ta fara yi kafin ta yunkura ta tashi zaune,ta rame sosai tun daga kan fuskarta zaka lura da hakan,idanuwanta sun ƙanƙance saboda kukan da take sha,   "Hosana bana ce kada ki tashe ni ba,"   "Yaya fawan ne ke kiranki ae,"ta ƙarasa maganar tare da miƙewa ta koma saman gadonsu, jiki ba ƙwari ta miƙe ta nufi ƙopar ɗakin,Fawan na ganinta ya ɗan saki fuskarshi, "Ya fawan,"ta ambaci sunanshi, "Babban yaya ne yace in kira mashi ke," Hannunta ya ruƙo ya jata suka nufi dining area,  Lokacin da suka ƙarasa dining area ɗin,kiranta Alex tayi"jahad,"Amsa mata tayi"na'am mommy,"da hannu Alex tayi mata nuni da tazo kusa da ita ta zauna,zagayawa tayi 6angaren da Alexandra take,taja kujera ta zauna,tana sauke ajiyar zuciya,    "Ya jikin naki,"? jahad tace"Alhamdulillah da sauƙi,"    "Good haka nake son ji," Da kanta tayi serving ɗin jahad,ta shiga bata abincin abaki,dole Jahad ta saki ciki taci Abinci sosai, *Boss Bature* Ajiyar zuciya ta soma saukewa tare da Ambaton"ALHAMDULILLAH"mayar da idanuwanta tayi kan Sehrish dake sume a ƙasa,da Sauri ta ƙarasa wurinta zama tayi daga gefenta sannan ta sanya hannunta tare da janyo Sehrish ta ɗaurata asaman cinyoyinta,lumshe idanuwanta tayi tare da buɗe su akan fuskar Sehrish,Slowly ta ɗaura tafin hannunta asaman fuskar Sehrish tana shafata,kafin ta yarfar da Sumar kanta gefe guda,tayi hakan ne don taga rubutun dake a bayan wuyanta,Wanda tun suna yara Maman Sadeeq ta bata shawarar tayi masu shaida,Sehrish ta sanya mata SB ma'anarshi Sehrish buzuwa,Hosana ma akwai nata rubutun wuyan HB haka ma jahad,kowaccensu tana da shi abayan wuyanta,   "Ya Allah na gode maka,daka dawo dani cikin hayyacina,Adai dai lokacin da ƴata ke buƙatar taimako na,"tana magana hawaye ne shararowa akan fuskarta,waige waige ta soma yi tana kallon ɗakin da suke ciki,Allah sarki lokaci guda ta fashe da kuka Saboda ta gane ɗakinta ne na gidansu Abusufyan,Bazata ta6a mantawa da irin rayuwar farin cikin da tayi ba acikin gidan,Tunawa da mahaifinta Baba buzu mai gadi yasa ta ƙara sautin kukan nata,   "Zainab!Zainabu abu,"haka yake ƙwala mata kira,idan yana nemanta,tayi matukar danasanin bijire mashi da tayi a lokacin da yake raye duk da ta auri za6inshi,bakowa tafi jin kunyar haɗuwa dashi ba,irin Abusufyan batasan da wani ido zata kalleshi ba,Ga kuma Hajiya Ameena,mutanen da suka yi mata halacci ta butulce masu, Ruwan hawayen abu ne suka wanke mata fuskarta,wanda hakan yayi silar farfaɗowarta daga suman da tayi,Yunƙurin amai ta fara yi daga kwancen da take,da sauri abu ta ɗago da ita,nan take aman ya kwararo daga bakinta,tamkar ƴan hanjin cikinta zasu fito waje,hannu abu tasa tana ɗan bubbuga mata bayanta,Sosai ta dinga sharara aman anan ƙasa,ta galabaita sosai ga zazza6in da ya yi mata mugun kamu,   Miƙewa abu tayi da sauri ta fito daga dakin ta shigo palour,fridge ta hango da sauri ta nufe shi,buɗewa tayi tare da zura hannu ta ɗaukko bottle water jiki na rawa ta koma cikin ɗakin,A gaban sehrish ta zuƙunna a lokacin ta kammala kwarara Aman,cire murfin robar tayi tare da tarba tafin hannunta ta debo ruwan tana zuba mata shi abakinta tana kuskurewa,bayan ta gama kuskure bakin Abu ta kafa mata robar ruwan abakinta,Sosai ta shiga kwankwadar ruwan tana sha,sai da ta ƙoshi sannan ta janye bakinta,Har lokacin Sehrish bata dawo hayyacinta ba,jikinta duk ya saki babu ƙwari,     Ajiye robar ruwan abu tayi gefe tana kallon fuskarta,   Gam ta runtse idanuwanta,tana faman ciccije la66anta,   "RISHI"ta furta sunanta, A hankali Sehrish ta ɗan ware idanuwanta akan fuskar abu,wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarta,ganin Oummansu agabanta,kuma da alama tadawo cikin Hayyacinta ne,   "Oumma,"ta ambaci sunanta tare da fashewa da wani sabon kuka,   Ita ma abun fashewa tayi da kuka,Cikin Shesshekar kuka take cewa"Laifina ne!komai ya faru arayuwarku ni ce sila,Ni naja maku...."   "Oumma ba laifin ki bane,ki daina ɗaurawa kanki laifi,Allah ya rigada ya ƙaddara faruwar hakan"   "Rishi bakisan irin raɗaɗin da nake ji acikin zuciyata ba,bansan tsawon lokacin dana ɗauka bana acikin hayyacina ba,bansan ya rayuwarku ta ƙare ba,Nasan dole kunsha Wahala"   Sosai suke yin kukan babu mai lallashin wani acikinsu, Sai da suka yi mai isarsu,Sannan suka tsagaita da yin kukan,    "Ina Hosana take?ina Jahad?duk suna ina?meyasa kike zaune ke kadai acikin gidan nan?Babu kowa atare dake?   ɗagowa Sehrish tayi daga kwancen da take saman ƙirjinta,cikin sanyin murya tace"Hosana da Jahad suna a Abuja wurin danginsu Daddy"   Cike da Mamaki abu ta maimaita sunan Daddy,   Sehrish tace"Eh,mahaifinmu nake nufi,Daddy Abusufyan atare muka zo kano,Tun da ya fita da marece bai dawo ba,kuma akwai security guards dake tsaron gidan,Amma bansan ya akai Ya sayyadi ya shigo ciki ba,"   Tunda Sehrish ta ambaci sunan Abusufyan jikin abu ya kara yin sanyi lakwas,shiru tayi na wani lokaci kafin tace"Kina nufin Abusufyan yana atare daku"?   ɗaga mata kai Sehrish tayi"Eh," Abun yayi matukar ɗaure mata kai,cike da mamaki tace"Taya akai kuka san cewa shi ne mahaifinku?Kuma ya akai kuka haɗu dashi"?har ya kai ku wurin danginshi"?daƙyar take magana saboda Ciwon kan da take ji yana ɗan takura mata,   "Oumma,Labari ne mai dogon zango....,"kasa ƙarasa maganar tayi sakamakon tashin Zuciyar da take ji,   "Sannu kinji,idan muka samu natsuwa sai ki sanar dani"    ta ƙarasa maganar tare da ruƙo hannayen Sehrish Cikin nata,suka mike tsaye suna fuskantar junansu,haɗa ido sukayi lokaci guda suka sakarwa juna murmushi, "Kin girma sosai,komai naki ya canza mun,"duƙar da kai kasa sehrish tayi tana dariya,   "Allah sarki hosana,Ashe da rabon zata rayu"?   "Sai ma kin ganta Oumma,Zaki sha Mamaki Allah,saboda hosana duk tafi mu girman jiki,"  wani irin farin ciki ne ya lullu6eta mara misaltuwa, Sun jima suna tattaunawa atsakaninsu,kafin daga bisani Sehrish ta shiga toilet don tayi wanka,tunda ta rufo ƙopar toilet ɗin,ta sulale ƙasa jikin ƙofar tana kuka ƙasa ƙasa,Abunda ya sayyadi yayi mata ya tsaya mata aranta,yadda ya dinga goga mata Abunshi ajikinta,Da kuma harshenshi da ya sanya yana lasar mata bayanta Ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,runtse idanuwanta tayi sosai,wani irin ɗaci ta dinga ji acikin zuciyarta,lokaci guda ta fara jin ƙyanƙyamin jikinta,hada ƙaiƙayi miƙewa tayi ta soma tu6e kayan baccin dake ajikinta, Lokacin da ta kammala wankan ta fito jikinta ɗaure da towel,bata samu kowa a ɗakin ba,Amma taga an gyara shi,komai ya koma yadda yake,hatta aman da tayi an kwashe shi da tarkacen Ya sayyadi,tasan cewa aikin Oummansu ne, Jiki ba ƙwari ta wuce saman gado ta haye,tare jan bargo ta lullu6e jikinta,bakowa take jiran dawowarshi ba,fa ce Daddynsu,Tayi mamakin jimawarshi awaje,har wuraren 12,Allah yasa dai yana lafiya, Kitchen ta shiga ta ɗauko Ashana,da sauri ta fito ta dawo harabar gidan,inda ta tattara Tsummokaran Ya sayyadi da ya bar masu,ba tare da taji komae ba ta Ƙyasta ashanar ta jefa ta asaman kayan nan take wuta ta soma ci ajikinsu,har sai da ta cinyesu abu na tsaye tana kallonsu, Ajiyar Zuciya ta sauke tare da bin gidan da kallo,mutane ta hango a bakin gate ɗin gidan Sanye da kakin Sojoji,kowannansu a yashe ƙasa sai bacci sukeyi,Abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,ranta ne ya bata cewar Securities ne,Da alama Ya sayyadi ne yasa su yin baccin Dole,don ya samu hanyar shigowa cikin gidan, Girgiza kai kawai tayi tare da komawa cikin falon,Bedroom ɗin ta shiga,tsayawa tayi abakin ƙopar ɗakin tana kallon Sehrish dake ƙumshe cikin bargo,jikinta sae kerma yake yi,  Idasa shiga cikin ɗakin tayi har zuwa gefen gadon ta zauna,tare da Ambaton Sunanta"Sehrish,"   Muryata na kerma tace"Na'am Oumma,"    "Taya zan iya samun Daddynku?inaso nayi magana dashi,"    "Ina da waya,nabarta a ɗaya daga cikin ɗakunan dake a upstairs,"   Da sauri abu ta mike ta fuce daga ɗakin,Upstairs ta wuce,tana neman ɗakin da sehrish ta faɗa mata,Ɗaki ɗaya ta samu a buɗe,tun kafin ta shiga tajiyo ringing ɗin wayar tura ƙopar tayi ta shiga cikinsa,A saman gado ta samu wayar,hannu takai ta ɗauki wayar tare da duba screen ɗin   "My Boss Man,"shi ne sunan daya bayyana akan Screen ɗin wayar,picking call ɗin abu tayi tare da kara wayar a kunnanta,batasan wanene ba kawai ranta ya bata cewar Abusufyan ne,tayi tunanin zai yi mata sallama sai taji shiru,   Batare da ta kawo komai aranta ba,ta soma magana,   "Assalamu Alaikum,Oummansu Sehrish ce ke magana,dan Allah kadawo gida akwai matsala,Sehrish tana cikin wani hali,yanzu haka bata jin daɗin jikinta,duk ta tsorata saboda abunda Ya sayyadi yayi mata,   Sgr dake kwance asaman gadonshi,baisan lokacin da ya mike daga zaune ba,a kiɗime yace"What?meya faru da ita ne?Waye ya shigo"?    Abu bata wayi muryarshi ba,ita dai kawai koma wanene so take akawo masu ɗauki ko dan saboda halin da Sehrish take ciki,   "Ya sayyadi ne ya shigo cikin gidan,bamu san taya akai ya shigo ba,Ya so ya cutar da rayuwarta....."gaba daya abu ta kwashe dukkan abunda ya faru ta sanar dashi a ƙarshe tace"dan Allah idan ka tashi dawowa,Ka biya koda chemist ne asamo mata maganin Zazza6i,ga tashin zuciya da take ji,Tunkan takai ƙarshen maganar,Yayi rejecting Call ɗin,   Hankalinshi yayi mugun mugun tashi,har wani jiri ya soma gani acikin idanuwanshi,a zafafe ya tunkari ƙopar fita daga bedroom ɗinshi,sai ga Marshal ya faɗo cikin ɗakin har karo suka kusan yi,   "Bro whats happening?Where are going?"   Zuciya ce kawai ke fusgarshi,   "Omar,Airport zani je," Damko damtsen hannunshi Omar yayi ganin yana ƙokarin wuce shi ya tafi,   "Haba Rafayet!Airport kuma at this time?Me zakayi acan "   "Pls omar,leave alone,ka bani hanya in wuce,Zuciyana tafarfasa take yi,idan har ban kama wancan fasiƙin mutumin ba,hankalina bazai kwanta ba,"   A ruɗe Marshal yace"Wai wa kake magana akai?ko ka gano waɗanda suka kashe junaid ne"?   Girgiza kai yayi'A'a,ina magana akan wancan Bastard ɗin dake a Kano,Yau ya taka har gidan da Abusufyan yake..wai har...'kasa ƙarasa maganar yayi saboda raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi,   Hankalin Omar ba karamin tashi yayi ba,tun kafin ma ya ƙarasa jin abunda ya faru ɗin,   "Rafayet,pls Calm down ur mind,Kayi mun bayani yadda zan fahimta,'   Mika mashi wayarshi yayi batare daya furta komai ba, Kar6ar wayar Omar yayi, kaitsaye ya shiga call log nashi,   Kiran da Sgr yayi ma sehrish ya fara gani,"Calling ɗin layin yayi, A lokacin abu na acikin falo tana safa da marwa,jiran dawowar Abusufyan kawai takeyi,   Kiran na shiga wayar,da sauri tayi picking tare da zabga sallama,    "Am..sehrish,pls inason sanin meke faruwa anan ne,"?   Abu tace"ba Sehrish bace,Oummansu ce,"   Abun ya ɗan ɗaure mashi kai,jin tace Oummansu ce,a iya saninshi tana da ta6in Hankali,gaisar da ita ya fara yi cike da girmamawa tare da gabatar mata da kanshi a matsayin yayansu sehrish,abu ba ƙaramin daɗi taji ba,   Bata 6oye mashi komai ba,kaf ta kwashe abunda tasan ya faru ta sanar dashi,"   Jinjina kai Omar yayi,jikinshi har tsuma yake yi,daƙyar ya iya furta"Zan yi magana da Abusufyan ɗin,Ki kula da Sehrish ɗin kafin ya dawo gidan,"   amsa mashi tayi da toh,daga bisani su kayi sallama,   Zuba ma juna ido sukayi shi da Sgr, "Bansan wani irin dabban mutun bane wannan,wai ma ina security ɗin dake tsaron gidan ne?aikin me sukeyi ne da har suka barshi Ya samu damar shiga gidan?shi kuma Uncle bansan ya akayi har yayi dare haka ba awaje,"Omar ne yayi maganar ranshi a matukar 6ace,   "Last time ma,Ya ta6a yin irin hakan,Ya tafi ya barta ita kaɗai acikin gidan,"Acewar Sgr, Omar yace"ba don Oummansu na a kusa ba,da bansan mezai biyo baya ba,Amma naji daɗin jarumtar da tayi wurin ceton sehrish ɗin,"   Kar6ar wayar Sgr yayi daga hannunshi,Layin Abusufyan ya kira,   Almost 3 times tana ringing ba'a ɗagawa,   Sauke wayar yayi daga kan kunnanshi,  Omar yace "Allah yasa dai lafiya,hankalina fa duk ya tashi,abunda za'ayi yanzu Kawai gobe da asussuba su dawo gida kawai,nasan kafin lokacin may be Abusufyan ɗin ya dawo,Zan cigaba da trying layinsa,"   Dakyar ya samu ya lalla6a Sgr ya fasa zuwa airport ɗin,Amma fa abun ya tsaya Mashi aranshi,gefen gadonshi ya zauna,Omar ma ya zauna akusa dashi,   "Omar,kodai mun aikata wani zunubi ne da yasa waɗannan abubuwan ke faruwa damu ne?daga wannan sai wannan!   "Rafayet,ba laifin mu bane Laifin wasu ne aka ɗaura mana,ni tunda nake arayuwata ban ta6a fuskantar tashin hankali irin na waɗannan ranakun ba,kuma ban ta6a tunanin cewa rana irin Wannan zata zo mana ba,"   "What's the solution now?time fa yana ƙure mana,Daddy ma harya fara karaya da dawowar junaid,ɗazu da safe da yazo bedroom ɗina,Tsare ni yayi akan in faɗa mashi gaskiya,Junaid zai dawo yaci gaba da sa rai,ko kuwa bazai dawo bane,A lokacin saina kasa buɗe baki inyi mashi magana,"Sgr ne yayi maganar   Omar yace"Wlh nayi regretting ɗin 6oye mashi ainihin abunda ya faru,Duk da munyi hakan ne don mu ceto rayuwarshi,Amma kuma fa mun tabka kuskure babba,Don kuwa duk ranar daya gano cewa Junaid ya mutu,wlh ya gama yarda damu har abada,zuciyarshi zata karaya ne,Inajin tsoron wannan ranar,Rafayet,kodai mu sanar dashi gaskiyar lamarin ne"?   Shiru Sgr ya ɗan yi yana nazarin maganar tashi,girgiza kanshi ya ɗan yi tare da cewa"That's not the solution Omar,koda ace zai sani,yakasance time ɗin da muka kama waɗanda su kayi silar mutuwarshi,Mu gurfanar dasu agabanshi,before mu yanke masu hukunci akan idonshi,ina ganin kamar zaifi jin sauki acikin zuciyarshi,"   Sun jima suna tattaunawa a tsakaninsu kafin daga bisani,Kowannansu ya ɗauro alwala,Suka daidai ta sahu tare da kabbara Sallah, Ataƙaice Abusufyan bai tashi dawowa cikin gidan nan ba sai wuraren sallar asuba,Bawan Allah ashe Bayan ya baro gidan su Maman Sadeeq akan hanyar dawowarshi gida aka turo mashi da saƙo cikin wayarshi cewa za'a kashe Ƴarshi da ya bari acikin gidan,Hankalin shi yayi mugun tashi,Ya kure gudun motarshi,idonshi ya rufe saboda tashin hankalin dayake ciki,Baisan sa'adda ya buge wani Tsoho ba dake ƙoƙarin tsallaka titi,Tsohon yaji mummunan rauni dole ya tsaya don yaji bazai iya daukar alhakin guduwa yabarshi cikin mawuyacin halin da zai iya rasa ransa,mutane suka kama mashi tsohon yasa shi a motarshi suka wuce dashi asibiti,babu yadda ya iya,kamar ya fasa ihu haka yaji saboda tsabar baƙin ciki,duk da wani bangare na zuciyarshi na tunasar dashi akwae security guards a gidan,Bashi ya baro asibitin ba sai wuraren Sallar Asuba Ya dawo cikin gidan,Yayi mamakin ganin komai lafiya,Lokacin daya shiga ɗakin abu kwance ya samesu rungume Saman gadon ita da Sehrish suna ta sharar baccinsu,Hankalinshi ya kwanta sosai ganin babu abunda ya faru dasu, Falo ya koma ya zauna saman sofa,jikinshi duk amace,Ringing ɗin wayarshi dayaji yasa shi zura hannu cikin aljihu ya ɗauko wayar tare da duba sunan mai kiran nashi,Marshal Omar ne,   Picking call ɗin yayi tare da kara wayar a kunnanshi,   "Omar me kake yi har yanzu bakayi bacci ba"?   On the other hand Omar yace"Uncle,Ina ka shiga ne anata nemanka,"?   Nan Abusufyan yake sanar dashi abunda ya faru dashi akan hanyar dawowarshi gidan,    "Yanzu na dawo gidanma,Na same su cikin koshin lafiya suna ta bacci,"   A nan Omar ya kwashe duk abunda Abu ta sanar dasu ya faɗa ma Abusufyan,A zabure ya miƙe tsaye jikinshi na rawa,   "Pls Uncle,ka kwantar da hankalin ka,Tunda ba abunda ya faru dasu,Abunda ya kamata kawai ku dawo gida yau yau ɗin nan zamanku anan baida amfani,dama saboda ciwon Mahaifiyarsu ne Kuma ta samu lafiya,Yakamata ku dawo gida,Hankalinmu sai ya fi kwanciya," ..jinjina kai kawai Abusufyan keyi sam ya kasa buɗe baki yayi magana,Allah kaɗai yasan raɗaɗin da yake ji acikin Zuciyarshi,dakyar ya iya buɗe baki yace"Shikenan Omar,yanzun nan zamu shirya,'   "Allah ya dawo daku Lafiya," "Ameen"daga haka su kayi Sallama, Komawa Bedroom ɗinsu yayi wuraren karfe 6 na asuba,da alama ko sallar asuba basu yi ba,sai sharar bacci sukeyi,   Zagayawa yayi gefen da Sehrish take a kwance ya zauna tare da zuba mata ido yana kallonta,Yayin da hawaye ke sharara akan fuskarshi,tsananin tausayinta ne ya kamashi,baiji daɗin abunda ya faru ba,ta wani 6angaren kuma yaji sanyi aranshi da Allah ya tsare mashi ita,ga kuma Mahaifiyarsu da ta dawo cikin hayyacinta ta silar abunda ya faru,   Shessheƙar kukan da Abusufyan keyi ne ya farkar da Sehrish,buɗe idanuwanta tayi masu ɗauke da bacci,Suna haɗa ido dashi tayi hanzarin mikewa daga zaune tana ambaton sunanshi"Daddy!yaushe ka dawo?meya faru kake kuka,"   "Daughter,Am sorry!am really sorry,duk laifina ne dana tafi nabarki ke kaɗai acikin gidan,"   "Daddy,bangane akan me kake magana ba?nifa babu abunda ya faru dani,"tayi hakan ne don ta 6oye mashi gudun karya sanya damuwa aranshi,batasan cewa ya riga daya ji ba,   "Omar ya sanar dani duk abunda ya faru dangane da zuwan sayyadi cikin gidan nan,"    Mamaki ta shiga yi taya akai Ya Omar yasan abunda ya faru dasu?can kuma ta tuna da lokacin da Oummansu ta nemi yin magana da Abusufyan may be a wurinta yaji komai,   "Dan Allah Daddy,kada kasa damuwa aran ka tunda ba abunda ya faru dani lafiyata kalau,Sai ma wani abun farin ciki da ya faru,Oummanmu ta dawo cikin hayyacinta,Sanadin zuwan ya sayyadi,Kuma ta lalata mashi idanuwanshi,karkaso kaga yarda ya dinga kururuwa yana ihu," Tayi maganar tana kwatanta mashi irin yarda Ya sayyadi yayi ihun,   Hakan ba ƙaramin kwantar mashi da hankali yayi ba,dama tayi hakan ne don ta sanyaya mashi ranshi,   ɗaure fuskarta ta ɗan yi ashagwa6e tace"Daddy banga kana farin ciki da abunda na sanar dakai ba"?   Daƙyar ya ƙaƙaro murmushi akan fuskarshi yace"Ina farin ciki mana,Naji daɗi sosai,kawai dai nadamu ne akan Halin da kika tsinci kanki a lokacin da bana nan,"   ɗaure fuskarta tayi"Why Daddy,bana ce ka kwantar da hankalin ka ba?komai ya wuce,Yanzu lokacin farin ciki ne,Ga ka, Ga Ni,ga Oummanmu kuma,Bari na tashe ta daga bacci kuyi magana,"ta ƙarasa maganar tare da sanya hannu tana ɗan bubbuga kafadar Oummansu,   Murmushi kawai Abusufyan ke saki yana kallonta,   "Oumma!oumma!ki tashi ga Daddynmu nan ya dawo,"   Kasa tashi abu tayi saboda kunyar Abusufyan da take ji,Ashe tun shigowarshi dakin ta farka,tana jinsu suna magana amma tayi likimo, "Nasan cewa idonki biyu abu,bakison gani na ko"?Abusufyan ne yayi maganar ayayin da yake leƙen fuskarta,pillow ta sanya tare da rufe fuskarta dashi,   Murmushi suka saki atare shi da Sehrish,   "Inason magana dake,ki tashi daga zaune,"cike da jin kunyarshi ta cire pillow ɗin tare da tashi daga zaune suna fuskantar juna,Ta kasa ɗagowa su haɗa ido da Abusufyan,kunyarshi ta rufe ta,kamar tayi rami ta binne kanta,          "ZAINAB"ya ambaci sunanta da wata irin kasalalliyar murya,    daƙyar ta iya motsa lips ɗinta wurin amsa mashi,    "Na'am," Murmushi ya saki tare da ɗaga hannunshi sama yana furta"Alhamdulillah!Alhamdulillah,Almost 3 times yana ambaton hakan,Cike da tsantsar farin ciki,    Sai faman sauke ajiyar Zuciya take yi,matsawa yayi kusa da ita tare da sanya hannayenshi biyu ya tallabo fuskarta yana ƙare mata kallo,   Siraran hawaye ne suka soma Zarya akan fuskarta masu ɗumin gaske,    "Hawayen menene wannan"? Cikin Shessheƙar kuka tace"Kayi haƙuri,ka yafe mun,Na gane kuskuren dana yi,Naji jiki Abusufyan,nayi dana sanin butulce maka da nayi,Haƙƙinka ne yake ta bibiyar rayuwata,Ni ce silar duk wani abu daya faru a rayuwarmu nida ƴa'ƴana...."ta ƙarasa maganar tare da fashewa da kuka,Hannu tasa ta zame hannayenshi daga saman fuskarta,kafin ta Sauko daga saman gadon ta zuƙunna saman guiwowinta agabanshi,tana ci gaba da yin kukan....    "Tun da nake arayuwata,ban ta6a ganin mutun mai kyakkyawar Zuciya irin taka ba,duk irin girman laifin dana aikata maka,hakan baisa ka guje ni ba,Sai ma bibiyar rayuwata daka ci gaba dayi duk don kaga Ka taimake ni,Amma na kasa gane hakan,saboda tsabar baƙin kishin da nake dashi na yanke maka hukunci batare dana tsananta bincike ba......"      Ruƙo hannunta Abusufyan yayi tare da ɗago da fuskarta yace"pls bana son muna tuna abunda ya wuce,Ni komai ya wuce a wurina Abu,tabbas naji zafin abunda kika yi mun Amma wlh banta6a ruƙe ki araina ba,kullum burina inga na taimaki rayuwarki saboda baki da kowa abu,Allah kaɗai gare ki,Sai kuma Ni dana haɗa zuri'a dake,Ba zanso rayuwarki ta wulaƙanta ba,ko ba don haka ba Ke amana ce agare Ni," Zuba masu ido Sehrish tayi tana kallonsu fuskarta ɗauke da Murmushi,tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,   "Bansan da wasu kalmomi zanyi amfani ba wurin bayyana maka irin farin cikin da nake ciki ba,Abusufyan Allah kadai ne zai iya biyanka,",addu'oi ta shiga yi mashi yana amsa mata da ameen,Kafin daga bisani Ya nuna mata gefenshi ta miƙe ta zauna,    "nasan kinyi kewar ƴa'ƴanki sosai,In sha Allah Yau ɗinnan zamu wuce Abuja,Zaki ga Hosana da Jahad,da kuma sauran Family ɗinmu," Fira sosai suka shiga yi,Anan ta samu labarin irin wuyar dasu sehrish suka sha bayan 6acewarta,da kuma yadda akai suka haɗu da dangin mahaifinsu da shi kanshi Abusufyan din har kawo yanzu da suke bata labarin,Abu tasha kuka sosai tsananin tausayinsu ne yakamata,ta wani 6angaren kuma tayi farin ciki sosai Da Allah ya nuna mata wannan ranar da ranta kuma da Lafiyarta, Batare da 6ata lokaci ba Suka kammala shirinsu na komawa Abuja,A jere Motocinsu suka fita daga cikin gidan,Motar Abusufyan na atsakiyan motocin security ɗin gidan,Kaitsaye hotoro suka wuce domin yin sallama dasu Maman Sadeeq,   Sunsha kuka sosai,musamman Maman sadeeq da Abu,rungume juna suka yi kamar karsu rabu,babu wanda bai zubda ƙwalla ba acikinsu,kafin su tafi sai da Abusufyan ya damƙa ma Malam Nura key din gidansu dake a nasarawa G.r.a,Ya mallaka masu shi duk da haka sai da ya ƙara masu da zunzurutun kuɗi har miliyan 10,yace ya dauki miliyan bakwai yaba Baban Umari cikon miliyan ukkun,don bai manta da gudunmawar da akace ya bada ba wurin neman abu,anan take ya rubuta ma Malam Nura cheque,Duk da haka bai ƙyalesu ba,Bayan haka kuma yayi masu albishir ɗin cewa tare dasu Za'ayi aikin hajjin bana,Wayyo Allah saboda tsabar farin ciki,kasa bude baki su kayi don suyi mashi godiya,Kuka kawai sukeyi,abun da basu ta6a tsammanin zasu samu a rayuwarsu ba,Yau gashi silar taimakon da sukayi Allah ya ɗaukaka rayuwarsu,   Sehrish kuwa Dama tayi alƙawarin zata taimaka ma Sadeeq ya gyara keken shi,maimakon kuɗin gyaran keken sai Gashi ya samu kyautar danƙareriyar Motar Abusufyan gaba daya ya mallaka mashi ita,kusan zaucewa Sadeeq yayi saboda tsabar farin ciki,sun jima a wurinsu suna bankwana,kafin daga bisani Sukayi masu Sallama,Anyi rabuwar mutunci sai kuma in Allah ya haɗasu wurin shagalin bikin Ƴa'ƴan abu, Ɗaya daga cikin motocin security ɗinsu suka shiga Gidan baya Abu da Sehrish,Abusufyan yana agaban motar,A jere Motocin suka kama hanyar fita daga unguwar, Su Maman Sadeeq na tsaye a kopar gida ita da Mlm nura,tare da sadeeq sai bye bye suke yi masu da hannu,yayin da hawaye ke zuba a fuskar kowannansu, Sehrish sai lekensu takeyi ta glass ɗin motar dake a zuge,har sai da suka 6ace ma ganinta tukunna ta hakuri da leken,Rayuwa kenan in akayi hakuri Komai mai wuce ne, Hannu abu tasa tare da janyo Sehrish ta rungumota ajikinta,a lokacin har motocin sun haura saman titi,Sun miƙi hanyar barin garin da matsakaicin gudu, Da zarar ta ɗago da idonta ta kalli madubin motar,Fuskar Abusufyan take gani yana sakar mata murmushi,Sunnar da kanta ƙasa tayi tana ƴar dariya, Sehrish batasan wainar da suke toyawa ba,domin kuwa ta lumshe idanuwanta da alama bacci ya fara ɗaukarta, Sake ɗagowa abu tayi tare da kallon Mirror ɗin,suka ƙara haɗa ido dashi, Kashe mata ido ɗaya Abusufyan yayi,batasan lokacin da ta fashe da dariya ba cike da tsantsar farin ciki, Shima dariyar yayi,kusan minti 30 bata ƙara dagowa sun haɗa ido ba,saboda baccin da yayi awon gaba da ita, Wasa wasa shima bacci ya ɗauke shi,dama duk basu samu isasshen Bacci ba a adaren Jiya, Wuraren ƙarfe 2 na rana suka ƙaraso Abuja,Slowly motocinsu suka shararo izuwa cikin gidan,tun da Hosana tajiyo sautin shigowar motoci da gudun gaske ta fito daga cikin falon don taga su wanene, Bayan sunyi parking ɗin motocin,Abusufyan ya fito daga cikin motar,hosana na ganinshi ta ƙwala mashi kira"Daddy"!wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,da gudun gaske ta nufe shi tare da faɗawa jikinshi ta ƙankameshi sosai,tana dariya, "Hosana,"ya Ambaci sunanta tare da ɗago da ita daga jikinshi yana kallonta,fuskarshi ɗauke da murmushi, Ɗaure fuskarta ta ɗan yi ashagwa6e tace"Munyi fushi daddy,Sai yau zaku dawo"? Yana ƙokarin buɗe baki ya bata amsa,karaf idanuwanshi suka sauka akan Jahad wadda ta fito daga cikin falon tana tunkaro su, Gabanshi ne ya faɗi rass!Ganin yadda kamanninta suka sauya tamkar ba ita ba,ta rame sosai ,tafiyar kanta ma daƙyar take yinta, Ƙarasawa tayi gabansu ta tsaya batare da tace komai ba,idanuwanta na kallon ƙasa, "Jahad!kinyi rashin lafiya ne"?ɗaga mashi kai tayi alamar eh, "Zazza6i nayi sosae amma naji sauƙi yanzu," Hannu yasa tare da janyota ya rungumeta ajikinshi,Kasa jurewa tayi aikuwa ta fashe mashi da kuka sosai, Hankalinshi ya ƙara tashi, "Jahad kukan menene"? Cikin shessheƙar kuka tace"bakomai Daddy,nayi kewarka sosai," hannu yasa yana ɗan bubbuga bayanta yace"Am Sorry Daughter,pls ki daina kuka kada kisa nima na fara zubar da hawayen nawa," Dakyar ta tsagaita da yin kuka ta ɗago da kanta daga jikinshi tace"Daddy,ina rishi take?ina kuma Oumman mu?Hosana ta sanar dani cewa an ganta," Murmushi ya saki tare da sanya hannunshi ya ɗan kwankwasa glass ɗin motar, Buɗe murfin motar Abu tayi tare da fitowa daga cikin Motar,Zuba mata ido su kayi suna kallonta kamar yadda itama take kallonsu, Atare suka haɗa baki wurin ambaton sunanta"Oumma!" Murmushi ta ɗan sakar masu,tare da buɗe masu hannunwanta don su zo ta rungumesu,Matsawa suka yi tare da faɗawa saman jikinta,ta haɗasu duka ta rungume sosai,fashewa sukayi da matsanancin kuka kamar ransu zai fita,musamman jahad da take cikin wani hali na buƙatar kulawarsu, Itama abun kukan takeyi sosai,babu mai lallashin wani acikinsu,Fitowa Sehrish tayi daga cikin motar ta other side ɗin,jikinta a sanyaye ta zagayo ta wurin da suke,bayansu jahad ta fada ta rungumesu,abu ta haɗa da ita duka ta ƙanƙame abunta, Tuni hawaye sun wanke fuskar Abusufyan,Yau burinshi Ya cika na ganin ya haɗa kan family ɗinshi,wannan rana ce da bazai ta6a mantawa ba arayuwarshi,, Suna cikin wannan yanayin sai ga Abbansu junaid tare da Alexandra sun fito daga cikin gidan,tsayawa su kayi suna kallonsu fuskar kowannansu ɗauke da murmushi, "Bismilla,Ku ƙaraso daga ciki mana,"Abba ne yayi maganar tare da yi masu nuni da hannunshi, Kallonsu Abu yayi tare da yi masu gyaran murya yace"Koke koken sun isa haka,mu shiga daga ciki mana," Raba jikinsu sukayi dana Oummansu,ta ruƙo hannun jahad da hosana acikin nata,Abusufyan kuma ya ruko hannun Sehrish wurinsu Abba dake atsaye, tunkan su ƙaraso Abba yace" masha Allah,Yau family ɗin Abusufyan ya haɗu wuri guda,Ga Uwar Ga uban Ga kuma ƴa'ƴansu,"ya ƙarasa maganar yana dariya, Alex tace "U'r Highly welcome, Abusufyan's Family,Am glad to see guys "ta yi maganar tare da ƙarasawa ta rungumo Abu ajikinta,hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba, Sun jima a waje suna gaisawa kafin daga bisani suka koma babban falon gidan,Kowa dake acikin gidan sai da ya hallara A falon,Abusufyan ya shiga gabatar ma abu kowa,Sun yi farin ciki sosai,duk da tashin hankalin da suke ciki hakan bai hanasu yin Murnar dawowar Uncle ɗinsu ba tare da Oummansu rishi,Abusufyan ya lura da yanayin fuskokinsu,abun ya ɗaure mashi kai,mutanen gidan duk sun rame sunyi duhu,bashi kaɗai ba hatta Sehrish ta ankara da canzawar da mutanen gidan su kayi,Sai faman wurga ido takeyi taga ko junaid zai fito amma shiru babu shi,Ranta ne ya bata cewar ko sun fita tare dasu Babban yaya ne tunda bata gansu ba acikin gidan, Basu tashi sanin halin da Family ɗin suke ciki ba,Sai da suka huce gajiyarsu,tukunna Abba ya sanar da Abusufyan shima ɗin don ya matsa mashi ne akan son ganin junaid,Hankalin shi ba ƙaramin tashi yayi ba,jin anyi garkuwa dasu Junaid,baima son lokacin da ya rufe Abba da faɗa ba saboda ƙin sanar dashi da sukayi,Don me zasu 6oye mashi abunda ke faruwa acikin gidan,abun ya ƙona mashi rai,Har cikin ranshi baiji daɗin hakan ba,har ƙwalla saida ya zubar, Yinin ranar Abu na tare da ƴan ukunta a bedroom ɗinsu,Sun sha firar yaushe rabo,har bacci ya ɗaukesu atare saman gadon,basu suka farka ba sai wuraren Sallar Magriba, Bayan kowannansu yayo alwala Jahad ta shimfiɗa masu darduma suka jera atare da Oummansu,a tsanake sukayi sallar har suka kammala,basu tashi daga saman dardumar ba,ɗaga hannayensu suka yi sama suka shiga karanto addu'o'a abakunansu suna masu kara mika godiyar su ga Allah(S.W.A), Allah Allah Sehrish take yi su kammala Sallar taja jahad gefe saboda ta tambayeta ina junaid yake sannan kuma ta bata Labarin Artabun da suka yi tsakaninsu da ya sayyadi,ita ma jahad ɗin a ƙagare take dasu ke6e ita da Sehrish,Don ta bata labarin mutuwar junaid,kota samu ta rage raɗaɗin dake acikin zuciyarta,bazata iya 6oyema Sehrish ba,duk da An gargaɗeta akan karta fadama kowa, Basu suka samu lokacin kebewa da junansu ba,Sai bayan sallar Isha'e,kowa ya hallara a dining area,Suna cin abincin darensu, Su biyu suka rage acikin bedroom ɗinsu,Zaune daga gefen gadonsu,kowa yayi tsit,na wani lokaci kafin Sehrish tace"Jahad,tun ɗazu nakeso na tambayeki game da canzawar dana ga mutanen gidan nan sunyi,kowa ya rame yayi duhu,musamman ke kamar kin yi ciwo," Cikin sanyin murya Jahad tace"Labari ne mara daɗin ji Sehrish,Zan faɗa maki amma ina gudun na jefa ki cikin tashin hankali," "Kada ki damu jahad,ki faɗamun koma menene,in sha Allah zan jure bazan tashi hankali na ba," "Shikenan zan faɗa maki Amma kafin nan inaso ki yi mun alƙawarin cewa bazaki faɗa ma kowa ba" ..Sehrish tace"I promised you jahad,babu wanda zaiji abunda muka tattauna dake," Shiru jahad ta ɗan yi yayin da take yin wasa da yatsun hannunta, "Ina sauraronki jahad,"ta faɗi hakan ne don a ƙagare take da ta ji abunda jahad zata sanar da ita, "Sehrish!munyi babban rashi,wanda ya raunata zukatanmu," ..tunkan ta ƙarasa maganar sehrish taji gabanta ya faɗi rasss, Aruɗe tace"Jahad kada ki ce mun junaid ya mutu......!" Hawaye ne suka fara saukowa daga cikin idanun Jahad,bata 6oye mata komai ba game da mutuwar Junaid,Abun mamaki sai taga Sehrish na Zabga murmushi kamar wata zautacciya, Bata karaya ba,cigaba da magana tayi"Babu wanda yasan ainihin abunda ya faru,daga ni sai su ya Omar sai kuma Jami'an ƴan sandan da suke je wurin da kuma Sojojin dasu ya Omar suka je dasu," Dakatawa tayi da yin maganar tare da kallon Sehrish,wadda ke ta sakin murmushi, Fashewa da kuka Jahad tayi tare da cewa"Sehrish meyasa kike yin murmushi?na faɗa maki ne don in rage raɗaɗin da nake ji acikin zuciyata,wlh da kinsan halin da muka shiga ni dasu Ya Omar da baki yi mana dariya ba,"tana kai ƙarshen maganar ta ƙara sautin kukan nata, Sai lokacin Sehrish ta tsagaita da yin dariyar,Sannan ta soma magana"Haba Jahad,taya zaki ce mun Junaid ya mutu farat ɗaya in yarda?bazan ƙaryata ki ba,mutuwa na akan kowa babu wanda yafi ƙarfinta,Amma ni dai ban yarda cewa junaid ya mutu ba,tunda banga gawarshi ba,"tuni hawaye sun cicciko acikin idanuwanta, Cikin Shesshekar kuka jahad tace"Taya za'ae kiga gawarshi!nace maki ko ƙashi ba'a samu ba daga sassan jikinshi,Saboda ya ruga da ya ƙone ƙurmus ya zama toka," "Jahad ni ban yarda ba,Allah Junaid ɗinmu bai mutu ba,ki daina wahalar da kanki wurin faɗa mun," Rai a6ace Jahad tace"Wlh dole ki yarda Sehrish!meyasa zakiyi mun haka!Maimakon ki tayani jimamin rashin shi amma shine kike ƙara jefa ni cikin damuwa," Girgiza kai sehrish ta shiga yi tana faɗin'wlh bazan yarda ba,"tashin hankaline yasa Sehrish ta burkice mata, "Ko kin ƙi ko kin so dole ki yarda Sehrish,Junaid has gone forever," Miƙewa Sehrish tayi jiki ba ƙwari ta nufi toilet,Shigewa ciki tayi tare da jan ƙopar ta rufe, Zuƙunnawa tayi ajikin ƙopar,sai lokacin ta fashe da matsanancin kuka kamar ranta zai fita, "Allah sarki Junaid,Allah ya jiƙanka,bazan ta6a mantawa da halarcin da kayi mun ba, 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Zuƙunnawa tayi ajikin ƙopar,sai lokacin ta fashe da matsanancin kuka kamar ranta zai fita, "Allah sarki Junaid,Allah ya jiƙanka,bazan ta6a mantawa da halarcin da kayi mun ba,Allah yasa ƙarshen wahalarka kenan" Sai da tayi mai isarta,Sannan ta miƙe ta nufi basin,Fanfo ta kunna ta wanke fuskarta,bayan ta kashe shi ta fito daga toilet ɗin,Har lokacin Jahad na zaune tana matsar kwalla, Wuri sehrish ta samu gefenta,ta zauna yadda kasan ba ita bace tasha kuka acikin toilet ba,tayi hakan ne saboda batason jahad taga rauninta,hakan zaisa itama jahad ɗin ta ƙara shiga damuwa, "Jahad,kuka bashi ne magani ba,Allah ya jiƙanshi ya gafarta mashi,bazan iya misalta raɗaɗin dana ji acikin Zuciyata ba,Allah sarki junaid,Yayi mun abubuwan da bazan ta6a mantawa ba,"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar,yayin da take tariyo rayuwarsu ta baya ita da junaid, "Muna da kusanci da juna dani dashi tamkar abokai muke,ashe ɗan uwana ne shi," tana magana hawaye na zuba akan fuskarta,jurewa kawai take yi,Zuciyarta tayi mata nauyi sosai ga wani raɗaɗi da take ji,daga ta runtse idanuwanta fuskarshi kawai take gani, Sai lokacin Jahad ta tsagaita da yin kukan nata,kallon sehrish tayi da idanuwanta waɗanda suka yi jawur dasu sun ƙankance saboda yawan kuka, "Yaya rafayet da Ya Omar suna cikin tashin hankali Sehrish,baki ga yadda suka koma ba,Nafi jin tausayinsu akaina,ba don son ransu ba suka 6oye mutuwar junaid,sunyi hakan ne saboda su ceto rayuwar Abba daga rasa shi,sai gashi kuma abun ya fara damunsu,Yanzu kullum mutanen gidan nan suna sa ran dawowar junaid bansan ya zasu ƙare ba duk ranar da suka ji cewa junaid ya mutu ba garkuwa akayi dashi ba,"ƙarasa maganar tayi tare da sanya tafin hannunta saman fuskarta,ta sake fashewa da wani kukan, Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,abun ya ta6a mata zuciyarta sosai, "In sha Allah,Zamu tayasu da addu'a akan Allah ya kawo masu mafita,"Acewar sehrish, Sun jima suna jimamin mutuwar junaid,kafin daga bisani Jahad tace"Baki fadamun labarin rayuwarku a kano ba?Rashin kwanciyar hankaline ya hana in kiraku,Ni ban ma san inda na yarda wayata ba," Nan sehrish ta labarta mata abunda ya faru zuwansu kano har zuwan ya sayyadi," Murmushin takaici jahad ta saki kafin tace"Allah ya tsine ma la'anannan mutumin nan,Dama saida raina ya bani cewa shine ke bibiyar rayuwarmu,ta Allah ba tashi ba,ƙarshen shi ne yazo shiyasa yake bibiyar ajalinshi batare da ya sani ba....." "Jahad,Nifa ina zargin cewa su ne suka kashe Junaid,tabbaci ma nake dashi,tunda yace Family ɗinmu a tafin hannunsu yake,kuma duk motsin mu akan idonsu yake wannan ya tabbatar mun da cewa,Suna Atare damu," Jinjina kai jahad tayi"Nima yanzu shi nake zargi,bayan shi kuma ina tunanin akwai wani mai take masa baya,ko kuma wanda yake take ma baya,Dole akwai wani a kusa damu,Lamarin ma ya fara bani tsoro Rishi,ɗan adam ba abun yarda bane,Ke dai kawai ki kalli mutum," cike da takaici sehrish tace "Wlh ji nake da ina da halin da zan iya taimaka masu Babban yaya dana taimaka masu,Amma zamu tayasu da Addu'a dare da rana,That's the only solution......" Turo ƙopar da akayi ne yasa suka dakata da yin maganar,atare suka ɗago don suga wanene Hosana ce atsaye sai faman lasar hannunta take yi,bakinta duk maikon abinci tace"Waiku ba zaku zo muci abinci ba"? A fusace Jahad ta warci pillow tare da wurga mata shi ya sauka akan fuskarta, "Sakarya kawai,Ci kaɗai kika sani,Ba za'aci abincin ba,sai kace bakisan Halin da ake ciki ba," Harara hosana ta jefa mata,kafin tace"Ae bani na kar zoman ba,Rataya aka bani,"guntun tsoki taja tare da jan ƙopar ta fuce tana raira waƙa, Girgiza kai Sehrish tayi tare da cewa"Allah ya baki lafiya Hosana," "Ameen,"jahad ta amsa a yayin da take gyara kwanciyarta saman gadon, Wuraren ƙarfe Goma Sha biyu na dare,Kowa ya yi shirin kwanciya,A saman gadonsu Abu ta kwanta tare da Hosana da Jahad,Gadon yayi masu kaɗan su kwana su huɗu hakan yasa ta sanar dasu cewa zata wuce ɗakin Aunty Azmee ta kwana acan,fitowa tayi daga cikin dakinsu jikinta sanye da jallabiya, Babu kowa A main palour ɗin,Da alama duk sunyi bacci koda basuyi bacci ba,to suna a bedrooms ɗinsu Ne, Upstairs ta wuce Part ɗin Sgr,hannu tasa ta tura ƙopar tare da shigewa ciki,sai da gabanta ya faɗi ganin irin dattin da falonshi yayi,komai a hargitse,wannan ya ƙara tabbatar mata da cewar babu Lafiya,Mutun mai tsafta irin Sgr bazai bar part ɗinsa da dauɗa ba irin haka, Ashe bata ga komai a falon ba,Sai da ta shiga bedroom ɗinshi,Tashin sense,tun A ƙopar ɗakin ta fara cin karo da robobin lemun da ya sha yayi wurgi dasu a wurin,a hankali take tafiya izuwa cikin ɗakin,haɗaɗɗen gadon nan nashi ya canza kamani,Zanin gadon yayi uban squeezing,komai ya fita hayyacinshi,Pillow har a ƙasa anyi wurgi dashi,tausayinshi ne ya kamata,tuni hawaye sun fara saukowa saman kuncinta,gefen gadonshi ta zauna tana shessheƙar kuka sai da tayi mai isarta,Sannan ta mike tare da cire mayafin dake akanta ta ɗaure ɗamara dashi,toilet ɗinshi ta fara shiga,yayi datti sosai,hada ƙura kamar ba mutun ke amfani da shi ba,batare da 6ata lokaci ba,within 30 minutes Sehrish ta gyara mashi ko'ina ya dawo fes dashi,taci baƙar wuya don ba ƙaramin aiki tasha ba,bayan ta kammala da toilet ta dawo bedroom ɗin ta gyara mashi,ta canza mashi bedsheet da blanket,komai tayi arranging ɗinshi,after ta gama da bedroom ɗin ta Koma falonshi,Nan ma ta gyara mashi shi,Ƴan share share ne,ƴan goge goge ne babu abunda ta bari, A galabaice ta fito daga part ɗinshi lokacin da ta kammala gyaran,saukowa downstairs tayi tana tafiya kamar an zare mata lakar jikinta,kitchen ta wuce da niyyar ta ɗaura mashi girki duk da jahad ta sanar da ita cewa bai cika cin abinci ba,kuma bata da tabbacin zai dawo gidan ko bazai dawo ba, Within 30 mins,ta kammala shirya mashi dinner ɗinshi,fitowa tayi daga kitchen ɗin ta koma bedroom ɗinsu,A hankali ta tura ƙopar ɗakin ta shiga ciki, Murmushi ta saki yayin da idanuwanta ke kallon Oummansu dake rungume da Jahad suna bacci,Hosana ma na manne da ita,ta rungumeta ta baya, "Allah sarki,Rayuwa kenan,ko kusa banta6a tunanin zanga wannan ranar ba,Ya Allah ka ƙara haɗa kan zuri'armu," Na amsa mata da Ameeen, Wall clock ta duba kusan ƙarfe 1:30 na dare,toilet ta wuce,within few mins,ta watso ruwa, Fitowa tayi da ɗaurin gaba,Gaban dressing mirror ta zauna saman front chair ɗinshi,har lokacin Junaid na faɗo mata aranta,jin mutuwarshi take yi kamar ba a gaske ba, Hannu takai jikin drawer chest na mirror ɗin gida na ƙarshe ta janyo shi,kayan da Aunty Azeema ta aiko mata dasu ne,a nan ta jerasu,tare da wasu daga ciki ta tafi kano na gyaran jiki,amma bata fara amfani da turarurrukan ba, Ɗauko turaren tayi hadi da wasu haɗaɗɗun mayukan shafawa na jiki ta ajiyesu agaban madubin Ko'ina na jikinta tabi ta mulke shi da mayukan,bayan ta gama kuma ta feshe jikinta da turarurrukan,powder ta shafa a fuskarta,Sannan ta murza man baki mai ƙyalli asaman la66anta,Wow ta yi kyau ba kaɗan ba,kamar Aljana haka ta zauna tana kwalliya,ko tsoro bata ji ita kaɗai cikin daren nan, Ta ƙwallafa rai akan son ganin Sgr,ta damu sosai akan rashin baccin da taji Ance baya yi,da kuma rashin cin abinci,Yafi kowa shiga damuwa akan rashin Junaid, Miƙewa tayi tsaye tare da nufar wardrobe ɗinsu,buɗewa tayi tana laluben kayan baccin da zata sanya a jikinta,Night gown ta ɗauko red colour,tsayin rigar bazai wuce dai dai guiwarta ba,launinta kuma maroon colour ce, Zura rigar tayi ajikinta,ta ɗauko mayafi ta yafa asaman kanta,komawa tayi gaban mirror ɗin,turarurrukan ta ƙara fesawa ajikinta,wani irin fragrance mai sanyaya zuciya jikinta ke fitarwa, Zirga zirga ta soma yi acikin bedroom ɗin har ta fara fidda ran zasu dawo cikin gidan,Gaban window ta koma ta janyen labulen tare da zuge glass ɗin tana leƙen harabar gidan, Gajiya tayi da tsayuwa ta koma daga gefen gadon ta zauna,gyangyaɗin bacci ta fara yi,a hankali ta ɗan kwanta a takure daga gefen gadon,in a short time bacci ya ɗauke ta, Minti goma sha biyar da fara yin baccinta,Sai ga Motocinsu sun shararo da gudun gaske cikin gidan,motarsu marshal Omar ce farko,Sai Motar Sgr dake biye da tasu,Da alama dai wani bincike suke yi wanda yasa har sukayi dare a waje, Parking ɗin motocin suka yi,At same time Major da Armstrong suka fito tare da buɗe masu motar, Atare suka fito kowannansu na sanye da army trouser,tare da Long sleeve shirt green colour,sallama suka yi masu Armstrong kafin suka Nufi ƙopar shiga Main palour ɗin,hannunsu ruke cikin na juna,Upstairs suka haye bayan sunyi sallama da junansu,kowa ya wuce part ɗinshi, Tunkan ya shiga falon ya fara jin daddaɗan kamshin na kai mashi ziyara cikin hancinshi,Tura kopar yayi slowly ta buɗe,Shiga daga cikin falon yayi abun yayi matuƙar ɗaure mashi kai,Ganin an gyara mashi falonshi an canza mashi kamanni,ko'ina yayi fess,da farko yayi tunanin ko Azmee ce ta gyara mashi ɗakin,afterwards ya fara doubting ko Yarinyarshi ce ta dawo,Cos ya hana Azmee yi mashi aiki ko part ɗinshi ma bata Zuwa,ranshi ne ya bashi cewar Uncle ɗinsu ya dawo, Walking slowly ya nufi bedroom ɗinshi,Lokacin da ya shiga cikin ɗakin nan ma yaga angyara mashi ɗakin,Har cikin ranshi yaji daɗi sosai,ƙarasawa ciki yayi tare da rage kayan jikinshi,Ya shiga toilet domin yayi wanka,cikin minti Goma sha biyar ya fito jikinshi sanye da bathrobe,hannunshi na ruqe da short towel fari yana tsane ruwan dake acikin sumar kanshi,bayan ya kammala ya koma gefen gadonshi ya Zauna,ya jima ahaka kafin ya gyara kwanciyarshi asaman gadon batare da ya cire Bathrobe ɗin ba ya sanya night dress ɗinshi, damuwa tayi mashi yawa,a kowace daƙiƙa gabanshi faɗuwa yake yi,saboda gudun da lokacin keyi,yau har ya rage saura 1 week da ƴan kwanaki su bayyanar da Junaid agaban Abbansu, _Ya Allah makes it easy for me_Ya furta hakan yayin da idanuwanshi ke kallon Ceiling,ya ƙura mashi ido fuskar junaid kawai yake gani tana yi mashi gizau,babu alamun bacci a idanuwanshi don kuwa tuni ya ƙaurace mashi, "Assalamu Alaikum,"kamar daga sama yaji muryarta acikin kunnanshi,Wurga eyeballs ɗinshi yayi akanta batare da ya ɗago daga kwancen da yake ba,tun daga ƙasa har sama yake bin ta da kallo,. Tsaye take abakin ƙopar ɗakin,hannunta ruƙe da tray wanda ta shirya mashi dinner ɗinshi, Amsa mata sallamar yayi tare da bata izinin shiga daga cikin ɗakin, Ƙarasawa cikin ɗakin tayi,asaman table ɗin gadonshi ta ajiye mashi tray ɗin, Lumshe idanuwanshi yayi,ƙamshin turarenta sai kai mashi attack yake yi, Gaisar dashi tayi"Ya rafayet,how are u and how work" batare da ya buɗe idanuwanshi ba yace"Alhamdulillah,Am well,"iya abunda ya furta mata kenan, Jiki asanyaye ta juya zata bar ɗakin,bai tanka mata ba sai da takai bakin ƙopar fita daga ɗakin sannan taji yace"wannan food stuffs ɗin fa?wa kika ajiye mawa"? Dakyar ta iya bashi amsa da cewa"Kai na kawo mawa,". "Okey,bana jin yunwa,Zo ki kwashe su,". Sam bata ji daɗin jin hakan daga gare shi ba,at least koda ace yana cikin damuwa bai kamata ya yi mata haka ba,how many days basa atare almost 2 weeks,ko irin sannu da zuwa babu,tayi mashi uziri ne kawai saboda tasan halin da yake ciki, komawa cikin ɗakin tayi idonta cike tab da ƙwalla,tasha wahalar girka mashi abinci don ta damu da halin da yake ciki,amma ya watsa mata ƙasa a ido, Hannu tasa zata ɗauki tray ɗin kayan abinci,a hankali ya ɗan buɗe idanuwanshi ya saci kallon fuskarta,kallon ta ya shiga yi batare da ta sani ba,especially lips ɗinta dake matuƙar jan hankalinshi,tunawa yayi da halin da yake ciki,tabbas yana buƙatar natsuwa sosai,kuma yana jin cewa a wurinta ne kawai zai iya samun wannan natsuwar da kwanciyar hankali,harma da Lafiya,"Hold On!ya dakatar da ita da hannunshi a lokacin har ta juya zata tafi, "ajiye mun,ki tsaya ki yi serving ɗina before ki tafi," juyawa tayi asanyaye tare da ajiye mashi tray ɗin asaman table, Yunƙurawa yayi ya tashi daga zaune,ya saukko da ƙafafunshi ƙasa, "Me zan zuba maka,"? "Abunda kika san ya dace naci," A tsanake ta soma yin Serving ɗinshi,sosai ya ci abincin, yaushe rabon da ya sanya abincin kirki acikinshi har ya manta,sai da yaci ya ƙoshi,Sannan ya kalleta yace"faɗamun meya faru tsakanin ki da wannan bastard ɗin a Kano"? Gabanta ne ya faɗi rasss,mamakinta taya akai zancen yazo kunnanshiWayyo Allah! Girgiza kai ta ɗan yi "babu komai,babu abunda ya faru tsakanina dashi", "Ƙarya zaki yi mun"?rai a6ace yayi maganar tare da miƙewa tsaye,aikuwa a tsorace sehrish tace"wlh baiyi mun komai ba,ba ƙarya nake yi maka,bazan iya yi maka ƙarya ba," Wani irin kallo taga yana yi mata,tarasa gane kallon menene,ganin yana ƙoƙarin zagayowa ta gabanta yasa ta soma ƙoƙarin ja da baya, Daga zarar ya matso saita ja da baya,a haka har suka ƙurewa bangon ɗakin,rumfa yayi mata da faffaɗan kirjinshi,lokaci guda ƙamshin turaren jikinta ya gama kashe mashi jiki, Da wata irin kasalalliyar murya,yace"tell me,me yayi maki?ya cutar dake?" Muryarta na kerma tace"A'a,bai yi mun komai ba,wlh dagaske nake," "Its okey,"ya ambaci hakan tare da lumshe idanuwanshi,yayin da yake ci gaba da shakar kamshin turarenta,ganin ya rufe idanuwanshi yasa ta soma satar kallonshi,yayi haske sosai ga ramar da yayi,la66ansa sun ƙara cizawa sosai, Ganin yana ƙoƙarin buɗe idanuwan yasa tayi saurin kawar da nata idon,tun daga kan eye lashes ɗinta ya soma kallonta har izuwa saman hancinta,da kuma siraran la66anta,moving face ɗinshi yayi close to her face,tsinin hancinshi ya soma goga mata asaman hancinta,lokaci guda numfashinta ya fara canzawa,hannayenshi ya sanya tare da ruƙo waist ɗinta,sosai ya damƙi ƙugun,soft lips dinshi ya manna da nata a hankali ya zura tongue ɗinshi acikin bakinta,a gigice ya shiga kissing ɗinta kamar zai cinye mata la66anta,ƙanƙame juna sukayi kamar boss tace zata raba su,hannayenta gaba ɗaya suna acikin sumar kanshi tana hargitsa mashi ita,kasa jurewa yayi da tsayuwar,gaba ɗaya Ya sa6eta asaman shoulder ɗinshi,wurin switch ɗin ɗakin ya nufa ya kashe light ɗin,furniture ɗin dakin suka soma bada nasu hasken mai canza launi,ƙarasawa yayi saman gadon tare da sauketa,jikinshi har kerma yakeyi duk yabi ya susuce ya rasa tunaninshi,Rumfa ya yi mata ta ko'ina ya lullu6eta da ƙirjinshi,harshen shi ya mayar acikin bakinta,hot french kisses ya shiga bata,gaba ɗaya suka haukace ma juna,Dama bathrobe ce ajikinshi short ne kawai ya sanya daga ciki,zame mata rigar baccin jikinta ya soma yi da hannunshi,tun daga saman kafadarta ya sabule rigar har izuwa saman cikinta,Nan fa hankalinshi ya ƙara tashi haikan,kamar sabon jinjiri haka ya kama boobs ɗinta yana sha,kamar zai cire mata nipples ɗinta,sosai ta ƙankameshi,daɗin da take ji ya hana taji raɗaɗin sucking ɗin da Sgr keyi mata,Tuni Zufa ta wanke masu jikinsu duk da sanyin A.c ɗin dake a ɗakin,wani irin gurnani Sgr keyi kamar mayunwacin zakin daya jima baici namun dawa ba,Cikin fitar hayyaci Sehrish ta zura hannayenta acikin short ɗin Sgr,tunda yaji hannunta ruƙe da Ak47 ɗinshi Ya ƙara haukacewa,a ruɗe ya shiga furta"Keep doing it Reesh,you're giving me fire, baisan lokacin da ya yayyage rigar jikinta ba gaba ɗaya yayi wurgi da rigar,damƙar pant ɗin jikinta yayi azafafe ya yage shi gida biyu,yayi wurgi dashi, idonshi ya rufe jikinshi sae kerma yakeyi He became uncontrollable,ya gama fita hayyacinshi,Zame short ɗin jikinshi yayi gaba daya ya cire shi,tashin hankali! Man at work,ƙoƙarin penetrating ɗinta yake da ƙarfin gaske bada wasa ba,Saboda baya acikin hayyacinshi,wata irin razananniyar kara Sehrish ta saki saboda raɗaɗin da taji har cikin tsakiyan kanta,a gigice ta tureshi ta Zabura ta mike jiki na 6ari ta nufi hanyar sauka daga gadon,Rukota yayi da ƙarfin gaske yayi wurgi da ita,a galabaice ta koma saman gadon,Fashewa tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,Ta tsorata sosai,gani take yi kamar mutuwa zatayi,ruƙo kafafuwanta yayi yana ƙokarin buɗesu,Ta ƙara burkice mashi,lokaci guda jikinshi ya saki wata irin kasala ta baibayeshi,da alama ya dawo cikin hayyacinshi,jiki amace ya mayar da short ɗinshi,saukkowa yayi daga saman gadon yana tafiya a wani irin yanayi Mara misaltuwa,toilet ya faɗa tare da turo ƙopar ya datse ta, Within mins ya fito daga cikin toilet ɗin,a bakin ƙopar ya tsaya yana kallonta yayin da idanuwanshi ke rurrufewa,ƙarasawa yayi gaban gadon,tare da sanya hannunshi ya ɗauketa gaba daya ya aza asaman kafadarshi,Ya Wuce da ita cikin toilet ɗinshi, Within 15 mins ya fito dauke da ita,irin ɗaukar da akeyiwa jarirai na hannu biyu ɗinnan,ya ɗaura mata towel a Chest ɗinta,mayar da ita yayi saman shoulder dinshi sannan ya sanya hannunshi tare da janye bedsheet ɗin ya nannaɗe shi, A hankali ya kwantar da ita saman mattress ɗin,ɗaukar zanin gadon yayi ya tafi dashi izuwa laundry yayi datti,Wani sabon bedsheet ya ɗaukko ya shimfiɗa masu,bai kwanta ba sai da ya Sanya Sleeping dress ɗinshi white colour tukunna ya dawo saman gadon ya kwanta tare da janyota jikinshi yayi hugging ɗinta asaman wide chest ɗinshi, Gaba daya ya zura hannayenshi acikin towel yana shafa ƙirjinta,duk tana jin motsin hannayenshi ajikinta tayi likimo saboda kunyar shi da take ji,haɗe jikinsu yayi sosai,yadda duk wani motsi nata yake jinshi ajikinsa,ba zato ba tsammani bacci yayi awon gaba dasu,yaushe rabonshi da yayi bacci haka sati biyu kenan da ƴan kwanaki,Sai gashi yau a sanadin natsuwar da ya samu tare da Sehrish bacci ya ɗaukeshi batare daya ankare ba, Tun daga kan yarda suke yin baccinsu zai tabbatar maka da cewa suna acikin yanayi mai daɗi, *Boss Bature* Can cikin dare wuraren sallar Asuba,ƙasa ƙasa ta dinga jin sambatun Sgr yana ambaton sunan junaid,yana faɗin remain two weeks ya rage mashi,Ya sanya damuwa aranshi ne shiyasa har yake yawan yin mafarki,ware idanuwanta tayi akan fuskarshi La66anshi sai kerma sukeyi, Tafin hannunta ta sanya tare da shafa gefen fuskarshi,tsananin tausayinshi ne yakamata,taso ace tana da wata hanyar da zata iya taimaka mashi da ba abunda zai hana tayi hakan, Zame jikinta tayi daga jikinshi a hankali,ta saukko daga saman gadon,tana neman Night gown ɗinta,a can ƙasa ta hango rigar inda yayi wurgi da ita,ga kuma pant ɗinta da ya yaga mata shi biyu, Tsugunnawa tayi ta sanya hannu ta tattarasu,kafin ta miƙe da sauri ta fita daga bedroom din nashi, Cikin sanɗa take taka staircases ɗin,gudun kada wani ya fito yayi arba da ita a halin da take ciki,Daga ita sai Towel ajikinta, Saukowa cikin palourn tayi babu kowa anan,gudu gudu sauri sauri ta wuce bedroom ɗinsu,Hannu tasa ta tura ƙopar sae da ta fara leƙawa taga basu farka daga bacci ba,Sannan ta kutsa kanta cikin ɗakin,toilet ta shiga da kayan jim kaɗan ta fito tare da nufar wardrobe ɗinsu,turkish dress ta ɗaukko riga da wando ta zura ajikinta,cikin sanɗa ta fito daga ɗakin ta wuce bedroom ɗin Azmee kamar yarda tayi dasu cewa acan zata kwana, Turo ƙopar tayi ta shiga,a kwance ta samu azmee tana ta sharar baccinta hankali kwance hada minshari,lalla6awa Sehrish tayi cikin sanɗa ta nufi gadon tare da hayewa gefen azmee ta kwanta tare da jan bargo ta lullubesu,ajiyar zuciya ta shiga saukewa yayin da brain ɗinta ke tariyo mata abunda ya faru Tsakaninta da SGR,Namijin Duniya,bazata iya misalta irin halin da ta shiga ba,aduk lokacin da suke tare dashi,wata irin natsuwa take samu a wurinshi, Junaid ne ya faɗo mata aranta,nan take kuma ta shiga tariyo memories ɗinsu lokacin da yana araye,tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,tana cikin wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita, Lokacin da aka fara kiran sallar Asuba,azmee ta farka,har sai da ta tsorata da taga mutum kwance a gadonta,Ajiyar zuciya ta sauke lokacin da ta gane cewa ashe Sehrish ce, Hannu tasa tare da dan bubbugata"Sehrish!Sehrish!" Daƙyar Sehrish ta amsa mata"Na'am," "Lokacin sallah yayi,ki tashi kiyi sallah," "Toh"ta amsa mata batare da tayi yunkurin tashi ba,saukowa daga saman gadon Azmee tayi ta nufi toilet, Har Azmee ta kammala salla Sehrish bata motsa ba,bacci ne mai nauyi yake ɗawainiya da ita, Buɗe ɗakin Azmee tayi ta fuce tabar sehrish aciki,Sai da ta fara zuwa ɗakinsu Jahad ta kwankwasa masu ƙopa,taji alamun sun tashi,Sannan ta wuce kitchen, Tunda wuri ta fara shirye shiryen ɗaura girki, Sehrish kuwa sai da ta mula tasha iska kafin ta miƙe zaune,a hankali ta sauko daga saman gadon ta wuce toilet,bada jimawa ba tafito tana faman Yarfe hannunta,har lokacin akwai kasala atattare da ita, Buɗe wardrobe ɗin Aunty Azmee tayi tana neman Hijabin da zata sanya tayi sallah,a gida na farko Cikin jerin hijabanta Sehrish takai hannu ta janyo wata maroon colour,Abayar ta gogu sosai ga ninkin da akayi mata, Tana kammala janyo hijabin,Ba zato ba tsammani taji sautin faɗowar wani abu ƙasa kamar ƙarfe ƙarfe haka sautin ya bada,wurga eyeballs ɗinta tayi ƙasan tiles ɗin don taga menene,ƙura ido tayi tana kallon Diamond ring ɗin da ya faɗo ƙasa,A sukwane Sehrish ta tsugunna saman guiwowonta,tare da sanya hannunta ta ɗaukko zoben,Stone ɗin jikinshi sai faman ƙyalli yake yi, Kamar ta ta6a ganin zoben a hannun wani,zurfin tunani ta shiga yi tana ƙoƙarin gano inda ta ta6a ganin Zoben ko kuma hannun wanda ta ta6a gani, Lokaci guda kanta ya ɗauki Caji,Almost 15 mins bata motsa ba,Jujjuya zoben take yi tana kallonshi,ta kasa tunawa amma tabbas ta ta6a ganinshi, Matso da zoben tayi saitin idanuwanta,Harafin da ke ajikin Dutsen Zoben ta ƙura wa ido,Harafin *J* ne,Duk yadda Sehrish taso ta gano a ina tasan zoben Sam ta kasa,miƙewa tayi hannunta ruke dashi, "Kodai in tambayi Aunty Azmee nawa ne farashinsa,Yayi mun kyau sosai,"ta ƙarasa maganar tare da tura zoben cikin wadrobe ɗin wurin da take tunanin tanan ciki ya faɗo, Darduma ta ɗauko ta shimfiɗa a ƙasa,A tsanake ta kabbara Sallah,Bayan ta kammala ta zauna saman dardumar tana Addu'a, Hannayenta ta ɗaga sama"Ya Allah kaine gatan mu!Da kai kadai muka dogara!Ya Allah kana ganin halin da muke ciki,Ya Allah ka kawo mana ɗauki! "Ya Allah kaji ƙan Junaid,ka gafarta mashi kurakurenshi,Ya Allah Kasa can yafi mashi nan,Allah ka tonu asirin wadanda suka kashe shi....."sosai ta shiga yi ma junaid addu'a,bayan ta kammala sallar ta naɗe sallayar tare da hijabin da ta cire ta mayar dasu inda ta daukkosu ta ajiyesu, Bude kopar tayi ta fuce daga cikin ɗakin, Ɗakinsu ta koma,da sallama abakinta ta shiga cikin ɗakin, "Assalamu Alaikum" "Wa'alaikum Salam,"muryar Oummansu ce ta Amsa mata, Murmushi ta saki tana kallonsu,gaba ɗaya suna zaune saman gadon sun zagaye juna da alama fira suke yi, Ƙarasawa cikin ɗakin tayi tare da samun wuri saman gadon ta zauna itama, "Oumma ina kwana,kin tashi lafiya,"murmushi abu ta sakar mata tare da cewa"lafiya qalou rishi,ina fata kin tashi cikin ƙoshin Lafiya" "Alhamdulillah Oumma," Hosana tace"Yawwa rishi ƙwara da kika zo wlh,wai Oumma taƙi yarda cewa Ya Omar Saurayina ne shi zan aura," Dariya Sehrish tayi tare da cewa"Amma baki da kunya Allah,Oumman kike faɗama cewa kina da saurayi,"? Zumbura baki hosana tayi a ɗan shagwa6e tace"ai ƙwara ni,saurayi gare ni,ke da ma kike da au. "bata ƙarasa maganar ba,Sehrish ta buge mata baki,"shashasha karki kuskura ki faɗa wlh ranki zai 6aci ne,' A harzuƙe tace"Wlh sai an faɗa," Jahad tace"ki fada ɗin,Ni kuma in faɗawa ya Omar cewa baki respecting ɗinmu," Tsuke baki Hosana tayi tana gatsina masu hanci, Ita dai Oummansu sai bin su takeyi da kallo,gwanin ban sha'awa, "Oumma,Jiya kinsha farfesun Aunty Azmee ko?ya kika ji ɗanɗanon girkinta,"Sehrish ce tayi maganar don ta kawar ma Hosana zancen da takeyi na son tona mata asiri, "Yayi daɗi sosai,ɗanɗanon girkin na musamman ne,Amma sai dai bansan wacece Azmeen ba,saboda banga fuskarta ba jiya da kyau,kodai itama Auntyn ku ce"?tayi maganar tana kallon fuskar Sehrish, Girgiza mata kai tayi alamar a'a, "Ba Auntyn mu bace,Amma kuma matsayin Auntynmu take,ta jima tana aiki acikin gidan nan,tana da mutunci sosai,zan haɗa ki da ita ku gaisa kuma kiyi Mata godiya,saboda ta bani kyakkyawar kulawa lokacin da nake cikin mawuyacin hali," Fuskar Abu ɗauke da murmushi tace"Allah sarki,har naji ta kwantamin arai na,na kosa na ganta ma," "Ae yanzu haka tana aiki a kitchen,bari muje mu tayata aiki idan muka haɗu wurin yin Breakfast zaki ganta ne,Sai ku gaisa," Abu tace"To shikenan,Yanzu kuje ku tayata aiki ke da Hosana,Jahad ta zauna a wurina tunda bata da ƙoshin Lafiya," Maƙe kafaɗa Hosana tayi"Ni bazanje wani kitchen ba,Ae ni ba ƴar aiki bace," Dariya su kayi gaba ɗayansu,sehrish tace"Sha zamanki,Ni kaɗai na isa na tayata aikin har mu kammala,"ta ƙarasa maganar a yayin da take ƙoƙarin sauka daga saman gadon. Fitowa tayi daga cikin ɗakin ta nufi kitchen,azmee ta samu acikin kitchen tana aikace aikacenta, "Assalamu Alaikum,"sehrish ce tayi sallamar a yayin da take shiga daga cikin kitchen ɗin, Juyowa azmee tayi fuskarta asake tace"Mutanen kano,An tashi lafiya'?   "Lafiya lou Aunty azmee,Nayi missing ɗinki sosai,"   Azmee tace"i missed u too,jiya naso mu haɗu dake,In tayaki murnar ganin Oummanku,Amma bansamu halin yin hakan ba,"   "Nima jiya naso nazo ɗakinki mu gaisa Amma gajiya ta hana,"acewar Sehrish,   "Ae na ganki da asuba,kinso ki tsoratar dani Allah,sam Ni banyi tsammanin akwai mutun a kwance  gefena ba,Ashe ke ce,"   Dariya Sehrish ta ɗanyi kafin tace"Oh,aunty Azmee ashe kema kina da tsoro kamar ni,"    "Ni ba mutun bace"ta ɗanyi maganar tana hararar sehrish    Murmushi kawai tayi batare da tace komai ba   Takowa azmee tayi izuwa kusa da ita,hannunta ta ruƙo cikinta   "Sehrish,kinji abunda ya faru ko"? Cikin sanyin murya tace"Eh,jahad ta sanar dani komai,dangane da garkuwar da akayi dasu,nasha kuka sosai na gode wa Allah,Fatana shine Allah ya bayyanar da Junaid,"tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla,    "Wlh aunty azmee na karaya sosai,jikina yayi mugun yin sanyi,Allah sarki Junaid,bawan Allah,Yaso ni sosai,Ya bani kyakkyawar kulawa,"    Gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi, "Sehrish akwai abunda na manta ban sanar dake ba,koda yake junaid ne Ya hana in faɗa maki tun lokacin bayaa yanzu tunda baya nan inaso na sanar dake,"    "Menene aunty azmee"tayi maganar yayin da take kallonta,    'A lokacin baya,farko farkon zuwanki gidan nan,Zaki iya tuna ranar da kikayi Ciwon ciki mai tsanani?har kika sanar dani cewa Aljani ne yazo maki a daren ranar"? .shiru sehrish ta ɗanyi tana ƙoƙarin tunawa da ranar,Can tace"Na tuna,"   Ajiyar zuciya azmee ta sauke kafin ta ɗaura da cewa"JUNAID NE ba Aljani ba!Sehrish shi ne ya taimake ki a wannan ranar,Ya sanar dani komai,kuma tun a lokacin yake ta ɗawainiya da sonki acikin zuciyarshi,"   Fashewa sehrish tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,Cikin shessheƙar kuka tace"Dama junaid ne aunty azmee,Wayyo Allah na,Meyasa tuntuni baki sanar dani ba?meyasa aunty azmee!   Hawaye ne ke shararowa akan fuskar Azmee,   "Shiya ce karna faɗa maki Sehrish,saboda yana tsoron kiji haushinshi,Saboda ya gane cewa ke maca ce,After that,Sehrish junaid Shi ne ya siya maki wannan wayar taki ta farko,Tecno Camon 18,Wayarshi sabuwa ya mallaka maki ita,Bayan haka kuma Shi ne Silar da aka sanyaki Makarantar Boko,da kuɗinshi kuma,Wanda babban yayansu ya bashi don yayi Celebrating birthday ɗinshi,Amma ya fasa yin murnar ranar haihuwarshi Duk don saboda Ke!Na faɗa maki ne saboda in sauke nauyin dake akaina," Gaba ɗaya jikin Sehrish ya gama mutuwa,Kasa motsawa tayi daga tsayen da take,Ta ƙame kamar gunki,yayin da hawaye ke ta wanke mata fuskarta,masu ɗumi wasu nabin wasu,kamar wadda aka zarewa lakar jikinta,Ta rasa duk wani ƙarfi na jikinta,Abun da Ciwo acan ƙasan Zuciya,raɗaɗinshi yafi na zafin wuta, Hannu tasa tare da dafe saitin Zuciyarta,ji take tamkar zata 6allo daga ƙirjinta, Dafa shoulders ɗinta Azmee tayi tare da cewa"Sehrish!meya faru naga duk kin Canza?ban faɗa maki hakan ba don na tashi hankalinki,Na Sauke nauyin dake akaina ne,Junaid addu'armu yake buƙata Allah ya bayyanar dashi,Ni sai ma nake ji araina kamar bazai dawo ba,"   Sai lokacin Sehrish taja dogon numfashi,daƙyar ta iya ɗaga ƙafarta tana tafiya,Ta fuce daga cikin kitchen ɗin,Har lokacin babu kowa a falon duk basu fito ba,kewar junaid duk ta baibayeta,tsananin sonshi ne ya kamata,komai ya fita ranta a yanzu junaid kawai take son gani a yanzu,Gashi ya tafi ya barta,Tafiya ta har ABADA,   Garden ɗin gidan ta shiga,slowly take tafiya saman korayen Ciyayin dake aƙasan wurin,bakomai take tunawa ba,Fa ce irin rayuwar da sukayi da junaid,musamman ranar da suka fara haɗuwa a garden,Ranar da yazo zai bayyana mata kanshi amatsayin mutun na farko daya gane cewa ita maca ce,harya sanya hannu yana cire mata gashin bakinta,da kuma ranar da suka shirya zasu haɗu dashi a garden har yayi ta zaman jiranta bata fito ba,har dare Yayi akayi ta nemanshi acikin gida,   Duk duniya bata da masoyi daya wuce junaid,kifa kanta tayi asaman table ɗin gabanta,Sosai ta fashe da kuka mai cin rai,taso ace tuntuni junaid ya bayyana mata soyayyarshi da babu abunda zai hana ta aure shi, ...tashin sense...... Mu haɗu on monday 💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* 💋💋💋 Kwance yake asaman doguwar sofa mai mazaunin mutun ukku,da alama bacci ne ya ɗauke shi,daga shi sai gajeran wando ajikinshi, Sautin bugun ƙopar falon ne ya farkar dashi daga baccin da yake yi,tun kafin ya buɗe idanuwanshi yace"Who is Knocking!"   From ouside the door yaji an ce"Afternoon sir!Kunyi bakuwa ne tana a waje tana jira,"   "Ka sanar da ita cewa Matar gidan bata nan,"har lokacin bai buɗe idanuwanshi ba, Jim kaɗan har ya koma baccin nashi,Yaji an sake kwankwasa ƙopar,rai a6ace yace"Sergeant!"   "Am Sorry sir,matar ta nace akan tana son yin magana da matarka Laila,"   Guntun tsoki General Ishaq yaja kafin yace"Let her Come in," "Okey,Sir," A ƙule yake dama sam ƙawayen Laila ba burgeshi suke yi ba,duk yawancinsu irinta ne,masu mugun hali,' Kwankwasa kopar yaji anyi,muryarshi a kasalance yace"Who is knocking"   "Hajiya Rabi'atu ce,ƙawar Laila,"har cikin dodon kunnanshi ya jiyo daddaɗar muryarta,sai gashi ya buɗe idanuwanshi,Saukowa yayi daga saman Sofa ɗin da sauri ya nufi bedroom ɗinshi dake a upstairs,Jim kaɗan yadawo jikinshi sanye da Jallabiya, Hannu yasa tare da buɗe mata ƙopar,tun kafin ma ya kalleta,Wani irin daddaɗan ƙamshin turare mai ratsa sassan jiki da sanyaya zuciya ya daki hancinshi,from down ya soma kallonta,Highhills ne a ƙafarta,Jikinta kuma na sanye da Code lace milk colour riga bubuce ajikinta,ta aza mayafin asaman kafaɗarta,duka hannayenta da wuyanta na sanye da sarƙar gold,light make up ne akan fuskarta Koda General Ishaq,ya yi arba da kyakkyawar fuskarta,farat ɗaya ya waye ta,   da niyyar rashin mutunci ya buɗe ƙopar,Amma sai gashi yana sakar mata murmushi,A wayance yace"Hajjaju ko"?   Mayar mashi da martanin murmusin tayi tare da ɗaga mashi kai alamar eh,   "Ina fata ban takura maka ba,dama na shigo garin naku ne,Shi ne nace bari na leƙo mu gaisa da ƙawar tawa,nata trying layinta amma akashe I don't why,nashiga damuwa,"   Matsa mata hanya Ishaq yayi"mu shiga daga ciki mana,sai muyi magana"   "Toh"ta amsa mashi tare da bi ta gefenshi ta nufi cikin palourn,Shima yabi bayanta,Sai ƙara bin ta da kallo yake yi,from head to toe,wankan lace ɗin da ta ɗauka ba ƙaramin tafiya yayi dashi ba,musamman da ta kasance dirarrar mace, Wuri ta samu saman 2 seater ta zauna,Ishaq ya zauna saman 3 seater, A tsanake ta soma magana bayan sun gaisa"Am Lailan tana ciki ne"?   "A'a,bata nan fa,bata sanar dake bane"?   "No Bata sanar dani komai ba,ai na faɗa maka ina ta trying layinta a kashe,"magana takeyi tamkar bata son motsa la66anta,dama hajjaju anji wayewa,ishaq kuwa sai ƙara kalleta yake yi,    "bazan 6oye maki ba,Zancen gaskiya mun rabu da laila,Ni banma son inda take ba ayanzu ha...."bai ƙarasa maganar ba ganin yadda ta zabura ta miƙe tsaye tana faɗin"ka rabu da laila"? Murmushi Ishaq ya ɗan yi kafin yace"Calm down ur mind,koma ki zauna,"   Muryarta tamkar zatayi kuka tace'haba Ishaq,taya zaka ce mun in zauna?zaman me zan yi kuma,bayan ka rabu da laila!amma gaskiya banji daɗin wannan maganar ba,"   Zuba mata ido yayi yana kallonta,sai da ta kai ƙarshen maganarta,sannan yace"pls ki koma ki zauna,I will explain to you,"   Fuskarta aɗaure ta koma ta zauna tare da cewa'wlh Ishaq ka bani mamaki,sam ni baka yi mun kama da irin mazan dake sakin matansu ba,meyasa zaka yiwa laila haka?idan ma laifi tayi maka,at least kodan saboda Hafsat ai bai kamata ka rabu da ita ba" ..shiru ya ɗan yi batare da yace komai ba,har sai da ta hasala,ta soma ƙoƙarin miƙewa"Ni zan wuce,dama saboda Laila nazo,tun da kayi mana tsiyar taku ta maza,banga amfanin zama na ba,"   "Pls kada ki tafi,i will explain to u as i said,"Yanayin yadda ya furta maganar kamar akwai damuwa atattare dashi,hakan yasa ta gyara zamanta,tare da cewa"ina sauraronka," .."Ban cika son ina faɗin sirrikan matata ba,kuma bana ɗaya daga cikin mazajen da suke fallasa sirrin dake tsakaninsu da matayensu,so kamar yadda kika ce,banyi maki kama da mazajen da suke sakin matayensu ba,inaso ki ci gaba da yi mun wannan kyakkyawon zaton,Sam ni a tsari na babu sakin mace,kuma ke shaidace!kinsan wacece laila,kinsan halinta,bakowani namiji bane zai iya jure zama da mace irinta ba,amma haka ni na daure na rufe idona na zauna da ita,bayan duk irin Girman laifukan da take yi mun,Laila ta kaini maƙura ne,shiyasa har na zartar mata hukuncin saki........"Anan Ishaq ya kwashe dukkan Abunda ya faru tsakaninshi da laila game da irin Zaluncin da ta yiwa ƴa'ƴan Uncle ɗinshi ya sanar mata,   Saboda tsabar tashin hankali,Hajjaju ta shiga zabga salati tana faɗi "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Dama su Sehrish ƴa'ƴan Abusufyan ne?"   Cike da mamaki Ishaq yace"Dama kin sansu ne"?   "Nasan su mana,Ae ni ce silar tura ita Sehrish din aikatau a anan gidanku,Ashe dama jininku ne su?Ya salaaam,"ta ƙarasa maganar tana dafe kanta da hannunta ɗaya,   "Wlh Nayi danasanin rashin sanar dakai da ban yi ba,Nazo naga Hosana da Jahad,acikin gidan nan,tunda na kallesu dama nasan cewa suna cikin mawuyacin hali,bayin Allah,"   "Dama kinsan da zamansu acikin gidan nan?kuma baki sanar damu ba?bayan kinsan halin ƙawartaki"?   Idanuwanta cike tab da kwalla tace"Wlh banyi dabarar yin hakan ba,Amma ae komai ya wuce,kuma wlh nayi murna nayi farin ciki sosai da kasancewarsu ƴa'ƴan Abusufyan,in sha Allah idan na samu zuwa can abujan zanje na kai masu ziyara," Sun jima suna tattaunawa akan su Sehrish,bayan sun kammala firar tasu ne,Hajajju tace"Yanzu,mu dawo kan laila,"da sauri Ishaq ya katse ta da cewa"karfa kice zaki bani shawarar in mayar da ita,"   Girgiza kai tayi"a'a ni na isa,kawai dai yakamata kayi zurfin tunani,banso ka yanke mata hukuncin saki ba,ka jima tare da laila,kodan albarkacin hafsat bai kamata ka rabu da ita,Ya kakeso rayuwar hafsat ta kasance babu uwa atare da ita"?tayi maganar tana kallonshi,   "Hajjaju kenan!hafsat ba ƙaramar yarinya bace,ta mallaki hankalinta,ba zata yi maraicin uwa ba,zan iya sawa ayi mata transfer ta koma Abuja da aiki,in yaso sai ta zauna a wurinsu Abba,"   "Kai kuma fa?ba zakayi maraicin rashin mace atare dakai ba?nasan dole ka buƙaci kulawa,gashi gidan ma ko mai aiki babu,"tayi maganar tana ƙarewa gidan kallo,   Wani ƙayataccen murmushi Ishaq ya saki,anzo wurin da ya fi so,    Jingina bayanshi yayi ajikin sofa ɗin tare da cewa"kin faɗi gaskiya,ina buƙatar mace atare dani,musamman wadda ta iya ɗaukar wankan lace,ta iya kashe ɗaurin kallabi,Sai dai ina jin tsoran na sake yin aure,saboda matan ne basu da tabbas,"    "Ba duka aka taru aka zama ɗaya ba,kada ka yanke hukunci akan abunda baka da masaniya akanshi,Dole akwai na gari kuma akwai na banza,shiyasa kafin mutun yayi aure yake da kyau ya tsananta bincike,Don ya sama ma ƴa'ƴanshi uwa ta gari,haka mu ma matan,"   Sam bata kawo komai aranta ba,tana kai ƙarshen maganar ta ɗauki hand bag ɗinta tare da mikewa"Ni zan wuce,"bata jira amsarshi ba,ta nufi hanyar fita daga falon,   Da sauri Ishaq ya miƙe tare da yin hazarin shan gabanta,ba arziki ta tsaya tana kallonshi,    Marairaice mata fuska yayi"pls Kada kiyi mun haka mana,nasan kin fahimci abunda nake nufi,koda ban fito na bayyana maki ba,"ya ɗan daka da yin maganar yana jiran amsarta,   "Sauri nake yi,dan Allah ka bani hanya na wuce,ae kasan alaƙata da laila,So bai kamata kayi mun wannan maganar ba,"   "Ita laila ɗin ciki ɗaya kuka fito da ita ne"?yayi maganar tare da tamke fuskarshi,   Girgiza kai tayi alamar a'a,   "Ko akwai wani hadisi ko aya daya haramta wa namiji ya auri ƙawar matarshi"?   Nan ma ta sake girgiza mashi kai"ko ɗaya babu,Amma ae ana barin halas ko dan kunya,Ishaq idan ma da wannan manufar kazo mun,Ni bazan iya aurenka ba gaskiya,ba wai don ka ta6a auren ƙawata bane,No kawai bana ra'ayin ƙara kasancewa da wani ɗa namiji ne,"   "Koda ace ni ne"?yayi tambayar fuskarshi da alamun damuwa,shiru tayi bata tanka mashi ba,a qagare take ma daya bata hanya ta wuce,     Cikin sanyin murya yaci gaba da cewa"Na jima da dakon sonki acikin zuciyata,Yanzu ne nasamu ƙwarin guiwar sanar dake,ko alokacin baya nayi kawaici ne kawai don saboda nasan bazaki amince da soyayyata ba,Saboda Ƙawanccan dake tsakaninki da laila,Amma yanzu babu Laila,meyasa zaki haramtawa kanki ƙara yin aure ne?nafa san komai agame da rayuwarki,lokacin da mijinki yayi hatsarin mota tare da ɗanki,hada ni cikin waɗanda suka halarci jana'izarsu,Nasan abun dole ya ta6a maki zuciya sosai,Amma Ya zakiyi?mutuwa ce kuma tana akan kowa...."   Tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,cikin shessheƙar kuka tace"Dan Allah ka bani hanya na wuce"daƙyar sautin maganarta ke fita,   "Zan baki hanya ki wuce,Amma kafin nan ki tsaya ki saurari maganata,kina buƙatar wanda zai maye maki gurbin mijinki,kuma ni ashirye nake dana zama madadinshi,zan baki kyakkyawar kulawa in har kika amince kika aure ni,ke kinsan wanene ni basai na faɗa maki ba,bazan yabi kaina ba,Amma nasan kinsan komai a wurin ƙawarki laila,kuma nima a wurinta nake jin labarinki,"   Natsuwa tayi tana sauraran kalamanshi,yayin da take ta wasi wasi acikin zuciyarta,   "Daga ni har ke,babu yaro acikinmu dukkanninmu mun mallaki hankalinmu,Ki amince kawai nasan ba zaki rasa manema ba,Ni late comer ne,Amma da shiri na nazo bada wasa ba,inaso na haɗa zuri'a dake,Yaronki da kika rasa,Zaki samu madadinshi atare dani....."bazata iya jure sauraron kalaman Ishaq ba,da sauri tabi ta gefenshi da gudu ta buɗe kopar falon ta fuce tana kuka,Ya fama mata tsohon ciwon daya daɗe acikin Zuciyarta, Jiki asanyaye Ishaq ya koma saman sofa ya zauna tamkar ya fashe da kuka haka yake ji,bai yi tunanin zata ƙi amince mashi ba,gashi tunda yayi arba da ita ya rasa natsuwarshi,    *Marshal Omar* Abun ya ɗaure mashi kai!tunda ya shigo bedroom ɗinshi ya same shi kwance yana ta sharar bacci,Yaushe rabon daya ga Sgr yana bacci irin wannan,tun kafin mutuwar Junaid,wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙare mashi kallo,Har cikin ranshi ba ƙaramin daɗi yaji ba daya samu Sgr yana bacci,da alama tun da yadawo daga sallar Asuba yake kwance yana bacci,don bai cire jallabiyar jikinshi ba, Zuba mashi ido omar yayi yana kallonshi,yayi hugging ɗin pillow sosai a ƙirjinshi,kasa tashin shi daga baccin Omar yayi,don bazai so ya katse shi ba tunda an samu baccin ya ɗaukeshi,don yafi kowa shiga matsananciyar damuwa akan rashin Junaid,da kuma Alƙawarin da sukayi ma mahaifinsu, Motsi ya soma yi da la66ansa da alama mafarki yake yi,matsawa Omar yayi kusa dashi ya kasa kunne don yaji me yake cewa,Sambatu ne yake yi yana ambaton sunan Reesh,abun ya ɗaure mashi kai,instead yaji yana sambatu akan Halin da suke ciki kaman yadda yai tunani amma sai yaji yana ambaton sunan reesh,Wai ma sunan menene reesh ɗin nan?ya tambayi kanshi tare da kallon sama yana ƙokarin tunano inda yasan sunan,   Sai da yayi zurfin tunani sannan ya gane cewa sunan Sehrish ne ya maida reesh,   Ƙayataccen murmushi Omar ya saki,aranshi yace"shegen bisa na,Allah ya toni asirinka,Allah kadai yasan me ya aikata ma ƴar mutane jiya da har yake sambatu akanta,Haba no wonder!ba banza ba yake ta sharar bacci,mutumin da saboda tsabar tashin hankalin da muke ciki ko runtsawa baiyi amma yau gashi ya baje yayi ɗai dai saman gado yana ta bacci," Motsi Sgr ya fara yi alamar zai farka,slowly ya ɗan ware blue eyes ɗinshi ceiling ya fara kallo na wani lokaci,kafin ya wurga idonshi kan Omar daya ƙura mashi ido yana ta faman sakin murmushi,   Muryarshi da alamun bacci bai ishe shi ba yace"Bro,yaushe ka shigo?   "Ban jima da shigowa ba,nazo na taras da abun farin ciki,Na same ka kana ta sharar bacci,hankalinka kwance kamar kana cikin jirgi mai ya ƙare,"   yatsina fuska Sgr yayi batare daya ce komai ba,   "Ka gama shan ƙamshin naka,Nasan komai,babu abunda zaka 6oye mun,"cike da zolaya Omar yayi maganar,   "What are u talking about"?Sgr ya tambaya fuska a ɗaure yana kallonshi,    Murmushi Omar ya saki tare da kashe mashi ido ɗaya irin na ƴan duniyan nan,    "Tell me,Wacece reesh da naji kana faɗi acikin baccinka"?   A hasale Sgr yace"bansani ba,Omar yaushe ka fara sa ido,"   Dariya Omar yayi tare da cewa"basa ido bane,its just a question pls ka faɗamun sunan wa naji kana faɗi acikin baccinka,"   Harararshi Sgr yayi"I don't know," "Kada kayi tunanin zaka 6oye mun wani abu,saboda alamu sun bayyana ajikinka,"   Jin haka yasa Sgr yayi saurin kai hannunshi saman short ɗin jikinshi,   A ƙule ya furta"And then so what Omar!,Yau ka fara gani ne"?a fadace yake magana,dama ance wai da bori ake naɗe tabarmar kunya,   Sosai Omar ya 6a66ake da dariya,daƙyar ya samu ya tsagaita da yin dariyar    "I know this is a normal thing,but akan ka ni ban saba gani ba,gaskiya in ma na ta6a gani to na yau dai na musamman ne fa,Kalli fa ka gani,Tayi tsaye ba ladabi ba biyayya....."kasa ƙarasa maganar yayi saboda dariyar da ta ciyoshi,Rai amatuƙar yace Sgr ya miƙe daga zaune tare da kai hannu ya warci pillow ya wurga ma Omar asaman fuskarshi,da sauri Omar ya ruƙo pillown ya janye shi daga fuskarshi yana yi mashi gwalo,    "May be it needs a second round shiyasa taki relax,ɗan rainin hankali,kayi ta shan ƙamshi wai kai baka buƙatar mace a arayuwarka ko?Yanzun wannan menene? Yayi tambayar cike da tuhuma, Sgr was speechless,Zuba mashi ido kawai yayi yana kallonshi without saying anything,    Omar kuwa daɗin zolayar tashi yake ji,    "Tell me the truth!meya faru jiya da daddare atsakaninka da ita"? cizon tausasan la66ansa ya shiga yi yayin da yake kallon Omar,kamar ya shaqe shi Haka yake ji,    "Tunda bazaka faɗamun ba,Al'qur'an saina faɗama Uncle ince ka fara taushe mashi ɗiyarsa,ni ban ta6a ganin mara kunya irinka ba Allah,nan nan fa ka auri yarinyar nan don tayi maka aiki,ƴan share share da goge,Ashe muka maida shashashu,"" "Is enough Omar!kana so ka 6atamin raina ko?U know why i married her,yarjejeniyace akan zatayi mun aiki,so this is also part of her work," ya ƙarasa maganar tare da saukowa daga saman gadon yana faman hura hanci,   Dariya sosai Omar keyi,hada kwantawa saman gadon Sgr ɗin,Yau da jan faɗa yazo,    "Naji abunda kace,Amma pls kaga yarinya ce,Ya kamata ka dinga ɗan riritata,kana tarairayarta kamar new born baby,don nasan halinka Allah,kullum fuska a ɗaure,ita kanta bazata samu sakewa dakai ba,halan ma ƙarfi kake nuna mata?shiyasa har take baka"?   Dakatawa Sgr yayi daga yin tafiyar da yakeyi,Omar ya ƙule shi a hasale ya juyo yana kallonshi........   Ɗaga mashi gira ɗaya Omar yayi tare da cewa"what do u think if she becomes pregnant?kaga shikenan Abba zai samu little Junaid,hakan zai ɗebe mashi kewar Babynmu da muka rasa,"   Har cikin zuciyarshi yaji maganar Omar,shi kanshi Omar da yayi maganar sai da yaji wani iri acikin zuciyarshi,   Bai dai tanka mashi ba,ya shige cikin toilet tare da turo ƙopar ya rufe, *Boss Bature* A 6angaren Sehrish kuwa,bayan ta kammala shan kukan nata,Bacci ne ya ɗauke ta acikin garden ɗin yayin da take zaune asaman garden Chair ɗin,ta aza kanta asaman table ɗin gabanshi, Kukan tsuntsayen dake shawagi a wurin ne ya farkar da ita,a hankali ta buɗe idanuwanta,tare da miƙewa zaune tana bin tsuntsayen da kallo,jikinta duk ya saki,kewar junaid duk ta baibayeta,daƙyar ta iya miƙewa tsaye ta juya tana tafiya iska na kaɗa sumar kanta,cikin gidan ta koma ta ƙopar da ta fito,ƙopar da idan ka shiga zata kaika direct corridor ɗin dakunansu, Lokacin da ta ƙaraso bedroom ɗinsu,hannu tasa ta tura ƙopar ta shiga daga ciki,babu kowa da alama sun fita yin breakfast ne, Rage kayan jikinta tayi,kafin ta shige cikin toilet don tayi wanka,almost 30 mins sannan ta fito daga ciki,jikinta sanye da white underwear ɗinta,gaban wadrobe ta nufa tare da sanya hannu ta buɗe tana neman kayan da zata sanya, Wata gown ce ta ɗauko,Doguwa Red colour mai bazar net daga ƙasanta,daga sama kuma hannu ɗaya gareta siriri,rigar ta haɗu sosai,sanya rigar tayi ajikinta ta zauna mata sosai tabi shape ɗin jikinta,saukko da gashin kanta tayi ta sanya hannu ta barbazo dashi ya rufe bayanta,gaban mirror ta koma ta zauna da niyyar yin kwalliya amma sai ta shiga tunanin wai ma wa zatayi ma kwalliya? Tana cikin wannan tunanin wayarta dake ajiye saman gadonsu ta soma ringing,miƙewa tayi jiki ba ƙwari ta ƙarasa tare da ɗaukar wayar,ta duba sunan mai kiran nata,Ajiyar zucia ta sauke tare da picking call ɗin ta kara wayar a kunnanta"Mommyna,kin tashi lafiya,"   On the other hand Aunty azeema tace"Lafiya lou Daughter Alhamdulillah,Ya kike ya gida!ya jikin Oumman taku?Abba ya sanar dani cewa taji sauƙi,harma kun dawo gida," . "eh,jiya muka dawo,"   "Allah sarki,to Allah ya ƙara mata lafiya," Ta amsa mata da Ameen,   "Inason magana dake ne shiyasa na kira,"jin haka yasa Sehrish ta samu wuri gefen gadonsu ta zauna tare da wayar manne a kunnanta,   "Mommy ina sauraronki,"   Hajiya azeema tace"Yawwa,dama inaso naji ya tsakaninki da Rafayet?   "Shiru sehrish tayi saboda kunyar da take ji,tuntuni taso ta fayyace mata abunda ya fara shiga tsakaninta da Sgr amma kunya ta hanata,   "Kada kiji kunyar komai,ki ɗauke ni tamkar ƙawarki aminiyarki,inaso ki sanar dani komai,"Acewar hajiya azeema don ta ganota,kunyarta take ji shiyasa tayi shiru bata tanka mata ba,   Cike da jin kunya Sehrish ta sanar da ita duk wani abu dake wakana atsakaninta dashi,   Lokacin da ta kai ƙarshen maganar,tana jiyo sautin dariyar hajiya azeema ta cikin wayar,da alama abun ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,sai da tayi mai isarta sannan tace"amma Rafayet baida ta ido,in banda ma baturen mutun,ka auri yarinya don tayi maka aiki,kuma ka 6uge da neman biyan buƙatarka,'   Sunnar dabkai Sehrish tayi,gani take yi kamar Mommy azeeman tana agabanta ne,   "Am sorry fa,karki ji inata yi maki dariya,abunne ya sanya ni nishaɗi,kina ji na ko"?   ɗaga kai sehrish tayi kamar tana agabanta"ina sauraronki Aunty,"   "Yawwa inaso ki natsu ki saurare ni,nasan kina jin tsoron Sgr sosai,saboda yanayinsa,Yawan ɗaure fuska,rashin fara'a da sauransu,wannan tsoron shi nake so ki cire!   Ɗan waro ido sehrish tayi hankalinta atashe tace"Aunty,taya zan daina jin shakkarshi"?   "Na farko dai mutunne kamarki,ba aljani ba,dole sai kin cire kunya idan har kina so kija ra'ayinshi agare ki,har yanzu fa Sgr baisan so ba,sha'awarki kawai yake yi shiyasa ya fara kulaki,koda ace ma yana sonki bazai iya gane hakan ba,har sai kin koyar dashi,"   "Amma Aunty taya zan iya koyar dashi soyayya"?muryarta sanyaye tayi maganar   "Yanzu Sgr ya fara sha'awarki,bazaiyi wasa dake ba,zaki ga canji atattare dashi,zai fara baki kulawa ta musamman kuma zai damu dake,ba don komai ba sai don saboda yasan cewa ta wurinki ne kawai zai samu natsuwa aduk lokacin da desire dinshi ta motsa,zai dinga tarairayarki ne yana baki kulawa sosae,ko tari kika yi zai tambayeki lafiya?Sanin cewa in fa baki da ƙoshin lafiya,abun zai shafe shi ne shiyasa zai dinga tambayarki da zarar yaga canji atattare dake,daga yanzu inaso ki lura dakyau ki gano wurin da yafi ra'ayin ta6awa ajikinki,saboda ta hakanne zaki gane lagwansa,sannan a duk lokacin da zaki je part ɗinshi,ki dinga ɗaukar wanka kuma kada ki dinga sanya manyan kaya irin atampa ko shadda wannan sai za'aje unguwa,ko cikin gida,ki dinga sanya kayan da zasu bayyana surar jikinki,Yadda zai dinga ganin komai Zahiran har ya gaza samun kwanciyar hankali,amma fa idan zaki sanya kalar wannan kayan ki tabbatar da kin sanya hijab ajikinki saboda akwai maza agidan,daga baya idan kinje part ɗinshi sai ki cire kina jina ko"?   "Eh,"ta amsa mata, "Yawwa,nasan dai basai na ƙara tunasar dake ba,game da tsafta duk kina yin wannan,Amma shagwa6a fa kin ta6a jaraba yi mashi...."tunkan ta ƙarasa maganar,Sehrish ta 6a66ake da dariya,   Hajiya azeema tace"Allah kuwa,bafa wasa nake yi maki ba,shagwa6a tana ɗaya daga cikin abunda ke jan hankalin ɗa namiji zuwa ga mace,da kuma salon magana,da tafiya,da sauransu,"   "Aunty azeema shagwa6a fa kika ce,babban yaya zan yiwa shagwa6a aikuwa da rabon insha Mari,"daƙyar ta ƙarasa maganar saboda dariyar data zo mata,   Itama azeema dariyar take yi,sai da suka tsagaita da yin dariyar tukunna tace"Don kina jin tsoranshi ne shiyasa kike jin wani banbarakwai,ai ba wani abu bane,ko da yake kufa Majority ɗinku kunya ke hanaku nunawa miji soyayya,ba zaku iya sakin jiki ku nuna ma miji Soyayya ba,ga kuma girman kai,duk da nasan ke baki da wannam girman kan,kunyar dai ce kawai da kuma tsoro,'   Murmushi kawai Sehrish keyi tana sauraronta,aranta kuwa tana aayyana abunda zai faru idan tayi kuskuren yi ma Sgr shagwa6a,    "Ki ƙaddara cewa,Sgr jinjiri ne aka baki shi don ki kula da rayuwarshi,komai kece zaki koya mashi,kamar soyayya da bai iyaba zaki iya koya Mashi,duk abunda kika saba mashi,to shima ko bai iyaba zai fara kwatanta yi maki ne,"sosai Aunty azeema ta shiga koyar da ita,Yadda zata jawo hankalin Sgr,suna cikin magana ta wurga idonta kan Wall Clock,sam ta manta bata kai mashi breakfast ɗinshi ba,"   Aruɗe tace"Aunty azeema,na manta ban kai mashi breakfast ɗinshi ba"   "Okey,ki kwantar da hankalinki pls,Zamuyi Magana anjima," . sallama Su kayi da ita,jiki na rawa Sehrish ta koma gaban mirror,janbaki ta ɗauko red colour ta murza ma la66anta suka ciza sosai,turarenta ta ɗauka ta feshe jikinta dashi,   Komawa tayi gaban wardrobe ta ɗauko babban mayafi ta lullu6e jikinta dashi tun daga saman kanta, High heels ta sanya a ƙafarta launin rigar jikinta,ƙarasawa tayi tare da buɗe ƙopar ɗakin ta fito,tun kafin ta ƙarasa fitowa daga cikin corridor ɗin ta soma jin sautin ƙarar Cokula,alamar abinci suke ci, Kamar karta fito haka ta dinga ji,batasan taya zata nufi part ɗinshi ba,ga mutane a dining area kuma dole ne in zata gifta sai sun ganta har ma su nemi jin ba'asin rashin fitowarta cin abincin, Daƙyar ta ɗaure,ta nufi dining ɗin kaitsaye,tun kafin ta isa sautin takalmanta yaja hankalinsu,gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta   "Daugher!dama idonki biyu?amma shi ne baki fito kin ci abinci ba"?Abusufyan ne yayi maganar,   "Ni nayi tunanin ma ko bacci takeyi shiyasa banyi magana ba,"acewar Abba,wanda ya tasa plate ɗin abinci agabanshi sam ya kasa cin abinci,har yanzu kewar junaid ke ɗawainiya dashi,   "Ina kwananku,"ta gaisar dasu cikin girmamawa atare suka amsa mata,   Duka matasan gidan nan suka hallara,dogon table ɗin mai mazaunin mutun 12,anan Abbansu yake tare da Mommynsu,Fawan,Irfan, Jabeer,Khaleed,sai kanal Yousouf tare dasu Talal,Najeeb da twins, Ɗayan table ɗin kuma mai mazaunin mutun 6,Oummansu ce tare da Abusufyan sai su Jahad da Hosana,idan ka kalli fuskokin matasan gidan sai sun baka tausayi,don kuwa kamar anyi masu dole don suci abinci,musamman fawan jujjuya cokalin hannunshi kawai yake yi,har yau ya hana kanshi jin daɗi duk don saboda Junaid, "Samu wuri ki zauna mana"Mommynsu Junaid ce tayi mata magana ganin ta tsaya atsaye kiƙam,   Sunkuyar da kanta ƙasa tayi,tana wasa da yatsun hannunta sam taƙi motsawa,   "Ki zauna mana baki ji ana magana ba"Abusufyan ne ya tunasar da ita,   Tafiya ta soma yi zata zagaya ta zauna,   "Ina azmee take ne?naga yau tunda ta jera abinci,bata fito tayi serving ɗinmu ba kamar yadda ta saba,kodai bata lafiya ne"Abba ne yayi maganar cike da son jin ƙarin bayani daga wurinsu Abusufyan yace"Nima tun ɗazu na lura bata a wurin nan,yakamata a dubo ta aji ko lafiya," "Bari naje na kirata,"Ko sauraron amsarsu batayi ba,dama so take ta gudu daga Dining area ɗin,   Gudu gudu sauri sauri ta nufi corridor ɗin ɗakinsu,a ƙopar ɗakin azmee ta tsaya tare da sanya hannu ta kwankwasa ƙopar,kusan sau uku tana buga ƙopar,ana ƙarshe ne tajiyo muryar azmee daga cikin ɗakin tana tambayar wanene,   "Sehrish ce Aunty azmee,su daddy ne ke nemanki,Sun ji shiru shi ne suka ce a kirawo ki,"   "Okey,gani nan zuwa,bana jin daɗi ne,"   Tsayawa sehrish tayi a bakin ƙopar ɗakin har saida azmee ta fito jikinta sanye da hijabi,   "Aunty azmee ya jikin naki"? Daƙyar ta iya buɗe baki"da sauki,ciwon kai ne,kuma nasha magani,"   "Allah ya ƙaro sauki Aunty azmee,"ta ƙarasa maganar tare da ruko hannun azmee cikin nata,suka kama hanyar zuwa dining ɗin atare, Lokacin da suka ƙaraso dining area ɗin,hankalin kowa ya dawo kansu, "Oumma ga Aunty azmee nan,kallatta ki gani,itace muke baki labarinta jiya mai girka mana abinci"a wani slow abu ta wurga eyeballs ɗinta akan fuskar Azmee,karaf idanuwansu suka shiga cikin na juna,Zumbur abu ta miƙe tsaye tana kallonta,kallon kamar nasanki,Itama Azmeen kallon Sani take yi mata,   Ganin sun ƙurawa juna ido,babu mai magana acikinsu,yasa Abusufyan tanka masu"Ko kunsan juna ne"?   Girgiza kai abu tayi"a'a gani nake yi kamar na santa ne,tayi mun kama da wata dana ta6a sani arayuwata,Amma bazan iya tunawa ba,   "Aunty azmee kefa?kinsan Oumma ne"?Sehrish ce tayi mata tambayar,girgiza kai azmeen tayi"A'a nima dai kallon sani nake yi mata,kamar na ta6a sanin wata mai irin fuskarta,amma dai ba ita bace ba,sunyi kama ne"   Murmushi sehrish ta ɗan saki tare da cewa,"tunda baku san juna ba,bari na gabatar da kowannanku,"   "Aunty Azmee wannan itace Oummanmu,mahaifiyarmu,"   Sannan ta nuna Azmee"Oumma ga Aunty azmeen da muke baki labarinta jiya,ba iya girki kaɗai ta iya ba,tana da kyakkyawar zuciya,mutuniyar kirki ce ita,"   Murmushi abu ta saki tare da miƙa ma azmee hannu suka gaisa da juna,kowa fuskarshi ɗauke da murmushi, Ajiyar zuciya Sehrish ta sauke,ganin hankalin kowa ya koma kansu yasa tayi saurin lalla6awa ta wuce kitchen,shaf shaf ta shiga haɗa mashi breakfast ɗinshi, "Sehrish ta faɗamun irin halarcin da kikayi mata,bansan da wasu kalmomi zanyi amfani dasu ba wurin gode maki,Allah ne kaɗai zai iya saka maki"   Murmushi Azmee tayi"Ae duk yiwa kaine,na dauki sehrish tamkar ƴar cikina,"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar,ta mayar da idonta kan Abusufyan"ina tayaka murna sosai,Allah ya ƙara haɗa kan zuri'arku,"addu'o'i ta shiga yi masu suna amsa mata da Ameen,kafin daga bisani Abba yace"Samu wuri ki zauna,Ke ma Azmee daga yanzu bana so kina wannan tsayuwar,don yanzu kinfi ƙarfin ƴar aiki a wurinmu,pls kada kiyi mun musu kamar yadda kika saba," Murmushi Azmee tayi tare da samun wuri a table ɗinsu Abusufyan ta zauna,Abu ma ta zauna,a tsanake kowa yake cin abincinshi,Abunda zai ɗaure maka kai,ya baka mamaki shine duk bayan ƴan mintina sai abu ta saci kallon Azmee,da alama dai tasanta ne,kuma tana ƙoƙarin tuna wurin da suka ta6a haɗuwa,itama Azmeen satar kallon nata take yi,kowa da abunda yake sakawa aranshi, Fitowa tayi daga cikin kitchen ɗin hannunta ruƙe da ƙayataccen tray,hannu bibbiyu ta ruƙo shi,cikin sanɗa ta wuce upstairs,direct ta nufi part ɗin Sgr,a bakin ƙopar shiga falon ta tsaya sallama tayi jin shiru ba'a amsa mata ba,yasa ta wuce ciki izuwa bedroom ɗinshi,tana ƙoƙarin shiga,tajiyo maganganunsu shi da Omar,kasa kunne tayi tana sauraronsu,   "Yanzu ya zamuyi?duk mun jefa kanmu cikin haɗari,idan har Abba yasan cewa ƙaryane ba kidnapping ɗin su Junaid akayi ba daga ranar zai ƙullace mu aranshi,kuma girmanmu zai faɗi agaban ƙannenmu ne,nayi regretting wlh,"Omar ne yayi maganar,a yayin da yake zaune gefen gadon,   "Omar,nima ina danasanin yin hakan,na shiga damuwa sosai,bansan ya zamu yi ba,remain just one week and some days,daddy tare dasu fawan jiranmu kawai suke yi mu kawo masu Junaid"yayi maganar ne yayin da yake tsaye gaban mirror yana gyara jikinshi dake sanye da Bathrobe,ga danshi danshin ruwa da alama bai jima da fitowa wanka ba,   Kowanne fuskarshi akwai tarin damuwa,abun ya tsaya masu aransu,   Jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,   "Assalamu alaikum,"jin muryarta yasa suka tsagaita da yin firartasu,    "Who's there"Sgr ne yayi tambayar   "Sehrish ce,breakfast ne na kawo maka"   Murmushi Omar ya fara saki,yana kallonshi,harara Sgr ya ɗan wurga mashi,   Miƙewa Omar din yayi"kar na takura maka,bari na baka wuri,idan Mun haɗu zamuyi magana,"bai tanka mashi ba,Ya nufi hanyar fita daga ɗakin,   Sehrish na ganinshi tayi saurin gaisar dashi"Ina kwana ya Omar,"   Fuskarshi ɗauka da fara'a ya amsa mata"Lafiya lou,ina fata kema haka".    "Ina lafiya,"daga haka ya matsa mata hanya ta wuce ciki,Shi kuma ya fuce daga ɗakin, A hankali take tafiya ta cikin mirror yake ƙare mata kallo,A saman table ta ajiye mashi tray ɗin,sannan ta ɗan juya tare da kallon bayanshi,gaisar dashi tayi"Gm ya Rafayet,ka tashi lafiya,"shiru bai amsa mata ba,kamar bashi bane ya gama magana yanzu tare da Omar, Juyawa tayi saɗaf saɗaf zata bar bedroom ɗin nashi,   "Where are u going?kin kammala aikin ki ne?"    "A'a,naga kamar kana shiri ne,Zan jira a falo,idan ka kammala zan shigo daga ciki in yi aikin,"   A wani slow ya juyo tare da kallonta,adai dai lokacin itama ta waiwayo shi,    Har sai da gabanta ya faɗi lokacin da idanuwansu suka haɗu cikin na juna,   Da hannu yayi mata alamar ta dawo,kamar wadda aka zarewa laka,haka ta dawo daga ciki duk tasha jinin jikinta,ƙoƙarin gyara Mashi bedroom ɗin ta shiga yi,kamar daga sama taji ya cire mata mayafin jikinta,da sauri ta juya tana kallonshi    "Taya zaki ji daɗin yi mun aiki da wannan abun a jikinki"?   Shiru tayi batace komai ba,Sae ƴan kame kame takeyi,    Jefa mata shi yayi asaman bayanta,"ki san inda zaki ajiye shi,"   Ruƙo mayafin tayi tare da ɗaure ɗamararta dashi kamar yadda ta saba yi,mayar da hankalinta tayi wurin gyara mashi gadon,   Cike da tsantsan sha'awarta yake bin jikinta da kallo,bai ta6a sanin kyawun launin ja ba sai da yayi arba da rigar jikin Sehrish wadda ta kasance Red colour,ga shi hannu ɗaya gareta,Soft skin ɗin bayanta mai matukar jan hankali sai fisgarshi takeyi izuwa gare ta, Tana cikin gyaran taji motsinshi a bayanta,A firgice ta juya karaf suka haɗa idanu,Zazzare mashi kyawawan idanuwanta ta shiga yi,farare ƙyal dasu masu ɗauke da kwayar ido brown colour,ja da bayan da take ƙoƙarin yi ne yasa ta kusa faɗawa saman gadonshi saboda ta ƙure mashi,da sauri ya cafko Waist ɗinta da hannu ɗaya ya janyota izuwa jikinshi,gaba ɗaya yayi hugging ɗinta so tightly,ta ko'ina ƙamshin turarenta neman yi mashi illa yake yi yana ƙoƙarin Zautar dashi,natsuwa Sehrish tayi yayin da kanta ke kwance luff asaman faffaɗan ƙirjinshi,wannan daddaɗan ƙamshin turaren nashi ne ke dakar hancinta,Gaba ɗaya jikinta ya mace,   Moving hands ɗinshi yayi tun daga kan Ass ɗinta ya tarboshi,ya jinjina girman hips ɗinta,slowly yayi sama da hannun zuwa cikin sumar kanta,sosai ya shiga murza gashin da yatsun hannunshi,tamkar yana yi mata susa haka ta dinga ji,ga wani irin daɗi mara misaltuwa,almost 5 mins ya rabata da jikinshi,Yayin da idanuwansu ke kallon cikin na juna kamar masu jin bacci,dawo da hannun nashi yayi saman Hips ɗinta tare da pulling ɗinta ya haɗe gabansu sosai,Ji yake tamkar kawai ya aiwatar da abunda zuciyarshi ke raya mashi,but this is not the right time da yake son wannan abun ya kasance, "Meyasa baki gaishe ni ba"?da wata irin kasalalliyar murya yayi maganar,    Muryarta na kerma tace"wlh na gaishe da kai,tunda na shigo,"    "Haka ake gaisuwa?"?   Abun nashi ya fara ɗaure mata kai,    Cigaba da magana yayi"Ni ba haka nake son ana gaishe dani ba,a kowani lokaci idan kika zo part ɗina,lemme teach u.."moving face ɗinshi yayi izuwa gefen fuskarta,Ya manna mata kiss,side by side na fuskarta,slowly ya dawo da sweet lips ɗinshi saman nata soft lips ɗin ya haɗesu wuri guda,kissing ɗinta ya fara yi,da niyyar ya koyar da ita yadda yake son ta dinga gaisar dashi,Boss man ɗin sai gashi ya fara Hawa kan Network,sosai ya matseta ajikinshi,A susuce ya shiga sucking lips ɗinta,Mayar mashi da martani ta shiga yi hakan yasa shi ƙara zaucewa,gaba daya ya sabeta izuwa saman gadonshi ya kwantar da ita,yabi kayansa ya turmushe,Zage zip ɗin rigarta ya fara yi,ƙankame hannunshi tayi saboda bata kaiga fita hayyacinta ba,kuma ta jiyo motsin mutun a falo,a rude yake faɗin"feed me pls,i really need it,"hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,ya zauce gashi wani yana tunkaro ɗakin,    Girgiza mashi kai ta shiga yi tana faɗin"Akwai mutun a falo,bazan iya ba,"    "I don't care,just feed me,ƙoƙarin sabule mata rigar jikinta yake yi,don ya samu yasha ko ya kore kishin ruwan da yake ji,don maƙoshin shi a bushe yake,    "Rafayet"!muryar Abbansu ce ta karaɗe kunnuwansu,jiki na rawa Sehrish ta janye jikinta daga nashi,A hanzarce ta diro daga saman gadon ta faɗa bayan labule ta 6oye,tana faman sauke ajiyar zuciya,   Kasa amsa mashi kiran nashi yayi numfashin shi na fita da wani irin huci huci,yayi Uban goho asaman gadon,Sumar kanshi duk ta rufe mashi fuskarshi,   Shigowa cikin bedroom ɗin Abba yayi,yana kallonshi cike da mamaki yace"Rafayet baka da lafiya ne"?   Daƙyar ya iya motsa lips ɗinshi"Am ok,"   Ƙarasa shiga cikin ɗakin Abbansu yayi tare da samun wuri ya zauna daga gefen gadon yana ƙare mashi kallo,Yaƙi yadda ya ɗago da kanshi,gudun kada Abbansu ya gano shi,Don kallo guda zai yi mashi ya shaida cewa wani abu ke faruwa,ga janbakin sehrish daya 6ata mashi chest ɗinshi,    "Rafayet,inason magana da kai game da Junaid,na kasa cin abinci ko isasshen bacci bana samu,Raina yana bani cewa kamar bazai dawo ba,idan har akwai abunda kuke 6oye mun kaida Omar dan Allah ku sanar dani,Don in fidda rai da dawowarshi,"   Gyara bathrobe ɗin jikinshi yayi,ya ɗaure igiyoyin jikinta,sai da ya fara daidaita natsuwarshi sannan ya miƙe daga zaune ya zuro da ƙafafunshi ƙasa,kallon juna su kayi shi da Abbansu,hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,Ganin hawaye asaman fuskar Abbansu,   "Daddy,don Allah kadaina zubar da hawayenka,before end of this month,in sha Allah daddy,zan sanar dakai komai,"   "Har yaushe ne zaku cigaba da samun ran dawowarshi?Idan mutuwa yayi ku sanar dani mana,na fara zargin hakan acikin raina,da ace kidnapping ɗin Junaid akayi dagaske,Even one day bazaku bari yayi ba,batare da kun dawo dashi cikin gidan nan ba,Amma almost 3 Weeks Junaid baya a gidan nan?kullum ƙara samana ran dawowarshi kuke yi"miƙewa yayi daga tsaye jikinshi na kerma ya soma tafiya daƙyar yake iya tafiya,har sai da yakai bakin ƙopar sannan ya dakata da yin maganar ya juyo tare da kallonshi har lokacin bai motsa ba daga zaunen da yake,    Cikin sanyin murya ya Ambaci sunanshi"RAFAYET" "Na'am Abba,"ya furta hakan yayin da yake kallonshi,jikinshi ya gama yin sanyi,   "In cigaba da sa ran dawowarshi ne?ko in fidda rai,"shiru Sgr yayi batare daya tanka mashi ba,Nazarin maganar shi ya shiga yi,muddin yace mashi ya fidda rai,to tabbas zai fahimci cewa Junaid ya mutu ne,   Muryarshi tamkar zai fashe da kuka yace"Am really sorry Abba,dan Allah ka bani time,zan baka amsar tambayarka,Amma ba yanzu ba,akwai wani investigation da nakeyi,Zan sanar dakai komai,"   Gyaɗa kanshi yayi tare da kama hanya ya fita daga cikin ɗakin,Yana juyo muryarshi yana fadin"Zan cigaba dasa rai,"   Sun jefa kansu cikin tsaka mai wuya,kifa kanshi yayi A saman mattress ɗin,   Sehrish dake la6e abayan curtains ɗin sai faman shessheƙar kuka takeyi,tausayinsu ne ya kamata,ta jima tana kuka abayan labulen kafin ta fito tana tafiya izuwa gefen da Sgr yake a kwance,   Tsayawa tayi tana kallonshi,yatsun hannunshi sae kerma sukeyi kamar wanda sanyi ya kama,   A hankali ta furta sunanshi"Ya Rafayet,"   "Pls,Just Leave am not in the mood,"da gudun gaske Sehrish ta kama hanyar fita ɗakin tana kuka,bata ji zafin maganarshi ba, Yinin ranar ko abinci Sgr baici ba,Yadda takai mashi kayan abinci haka ta kwaso su,bai ta6a koda Coffee ba, After 5 days,bayan kwana biyar,wanda yayi dai dai da sati uku da kwana Biyu da rasuwar baby Junaid!!!!!saura kwana 5 ya rage masu su bayyanar da Junaid,komai ya gama hargitse masu babu wani sauran kwanciyar hankali da suke dashi, Wuraren ƙarfe 9 na dare,Suna kwance a ɗakinsu,har lokacin Atare suke kwana da Oummansu,Har ɗaki aka ware mata haɗaɗɗen bedroom amma tace ita tafi son ta kwana tare da ƴa'ƴanta,Su uku ne saman gadon suna bacci,Oummansu tare dasu Hosana da Jahad,Sae faman sharar bacci suke yi,   Sehrish kuwa sam ta gaza runtsawa,ta sanya damuwa sosai aranta,ta ɗaurawa kanta nauyin alhakin Ƙaryar dasu Ya Omar su kayi ma Abbansu,   Tana zaune saman sallaya bata jima da kammala yin nafilfilin dare ba,hannayenta ta ɗaga saman tana addu'a,yayin da hawaye ke shararowa akan fuskarta,kusan minti 30 Sehrish bata dakata da yin addu'ar ba,sai da tayi mai isarta aƙarshe ta fashe da matsanancin kuka,da sauri ta sanya tafin hannayenta saman fuskarta ta toshe bakinta gudun kada sautin kukanta ya tashi su Oummansu, A saman dardumar ta kwanta,tana ci gaba da yin kukan,taso ace zata iya taimaka masu sai dai babu halin yin hakan,tafi damuwa da Sgr don tun ranar da Abbansu ya ƙara tunasar dashi akan Junaid,ita shaidace bai ƙara cin abinci ba,Sai dai lemu da yake sha,babu bacci a idanuwanshi,kullum babu lafiya ajikinshi,duk yabi ya hargitse, A cikin wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita,     _Sae da suka kammala hoton sannan ta lura da zoben diamond ɗin dake hannunshi,sae faman ƙyalli yake yi_ _Waro ido waje tayi alamar mamaki tace"wow junaid wannan fa,waya siya maka shi_   _Mommy azeema ce ta bani shi,dama ɗazu na sanar dake cewa zan nuna maki gift din da takawo mun,to itace wannan_   _Ya ƙarasa maganar yana nuna mata zoben da Wrist watch din_   _Junaid sunyi kyau wlh,musamman daya kasance kaine ka sanyasu_    _Thank u reesh,sunyi mun kyau amman idan ke kika sanyasu sae sun fi yi maki kyau,bari na ciro maki su ki sanya,nafison su kasance a hannunki_   _cikin sauri tace mashi"no junaid that's impossible,Auntynku azeema ce ta baka shi,muddin ta neme shi a hannunka bata ganshi ba zata nemi jin ba'asin inda ka kai su,kuma ma in banda abun ka junaid wannan ae irin naku ne!kamar diamond ne fa,nida ko zoben azurfa ban ta6a sanyawa a hannu ba,balle diamond_ A firgice Sehrish ta farka daga baccin da ya dauketa,mafarkin da tayi yayi matukar ɗaure mata kai,Zurfin tunani ta shiga lokacin guda ta gane wannan zoben da Junaid ya ta6a nuna mata Shi ne tagani a ɗakin Aunty azmee kamanninsu ɗaya Sak!tabbas kuwa shi ne na Diamond wanda Aunty azeema ta siya mashi mai harafin *j* Wata irin zufa ce ta shiga gangaro mata agafe da gefen fuskarta,tunani ta soma yi mai yakai zoben Junaid a dakin Aunty azmee?Yakai mata ajiya ne,?sam bata kawo komai aranta ba,Amma tunawa da tayi cewa junaid duk inda zaije zoben nan na ahannunshi wannan yasa ta fara kokonton wani abu,Zumbur ta miƙe daga saman sallayar ta nufi saman gadonsu, Lalla6awa tayi ta haye saman gadon,saitin wurin da Jahad take a kwance,hannu tasa tana ɗan bubbugata yayin da take ambaton sunanta a Hankali don kada ta tashi Oummansu,   "Jahad!jahad!"can cikin bacci jahad tajiyo muryarta,dakyar ta iya buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,ganin Sehrish yasa ta dan mike daga zaune"lafiya rishi?dama baki yi bacci ba?"   "Jahad duk ba wannan ba,wata tambayace nakeso nayi maki,A ranar da kuka fita tare da Junaid shan ice cream shin kin kula akwai agogon diamond da ring a hannunshi ko babu"?   'Meyasa kikayi mun wannan tambayar Sehrish!So kike ki tayarmun da hankalina?Kinsan fa banaso ana tunamun mutuwar Junaid,"tayi maganar hawaye na zuba akan fuskarta   Arude Sehrish tace"dan Allah ki sassauta muryarki Jahad,bana so kowa yaji,nasan baki so amma dan Allah ki yi hakuri ki amsa mun tambayata,"   Shiru Jahad ta ɗan yi da alama ta shiga zurfin tunani,kusan minti 5 kafin tace"Kamar naso naga zoben a hannunshi,Amma bazan iya tunawa ba gaskiya"   "Ko hoto baku ɗauka tare dashi ba"?   Rai aɗan 6ace Jahad tace"haba Sehrish sai kace wata ƴar jarida,irin waɗannan tambayoyi haka?   "Nidai ki amsa mun tambayata,"a kule tayi maganar,   Ganin ranta ya 6aci yasa Jahad cewa"Am Sorry,munyi hoto da junaid,hada ma videos muka ɗauka,Amma wayar bata a hannuna,Tana a wurin Ya Omar....."tunkan takai ƙarshen maganar Sehrish ta fuce daga cikin ɗakin a fujajen💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋 𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤ 𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠 *🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥* Abun ya ɗaurewa Jahad kai,irin wannan tambayoyi haka,Anya ba aljanu bane suka shige ta ba, Babu kowa a babban falon,ko tsoro bata ji haka ta nufi Upstairs,gudu gudu sauri sauri take tattaka staircases ɗin,kaitsaye ta wuce bedroom ɗin Marshal Omar,sallama tayi jin anyi shiru ba'a amsa mata ba,Yasa ta fada cikin falon nashi,babu kowa a falon,da sauri ta nufi bedroom ɗinshi,a bakin kopar ta tsaya tare da Leƙawa cikin ɗakin nashi,A kwance ta same shi yana ta bacci,Ajiyar zuciya ta sauke,Cikin sanɗa ta shiga cikin ɗakin nashi,saɗaf saɗaf ta nufi side drawer dinshi dake a righ hand na gadon,Zuƙunnawa tayi agaban drawer chest din,Ta sanya hannu tana bubbuɗesu a hankali,tare da bincikawa ko zata ga wayar jahad,babu ita aciki,a hasale ta miƙe ta nufi wardrobe din kayan shi,gaba daya duk ta hargitsa kayan amma bata ga wayar ba,tsayawa tayi a tsanake ta shirya mashi kayanshi yadda suke,Bayan ta kammala jiki asanyaye ta nufi hanyar fita daga ɗakin dakatawa ta yi da yin tafiyar,Waiwayowa tayi tana kallon cikon ɗakin,tunani take yi kamar akwai wurin da bata duba ba,can ta tuna da Drawer ɗin dake ɗauke da mirror,da sauri ta juya izuwa gaban mirror ɗin,Janyo gida na farko tayi lokaci guda ta sauke ajiyar zuciya,ganin Wayar Jahad ajiye aciki, Saukowa downstairs tayi,a main palour ɗin ta zauna saman Sofa tare da kunna wayar don akashe take,Allah yaso babu password a wayar, Direct ta shiga Gallery ɗin wayar,videos ta gani tare da hotunan dasu Jahad sukayi tare da juna,A hanzarce ta shiga kunna videos ɗin ta ƙura ido tana kallonsu,   Cikin motar Junaid shi da Jahad suka ɗauki video ɗin da take kallo,da hannu ɗaya yake ɗaukarsu video,yayin da dayan hannu ya rungumo jahad ajikinshi yana dariya,yana fadin"With My Juliet,My wife to be in sha Allah" Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu rass!rass!a zabure ta miƙe tsaye tana kallon yatsun hannun Junaid dake sanye da diamond ring ɗinsa,ya Aza hannu saman sumar kan jahad Sosai Zoben ya fito mai ɗauke da harafin *J* sai ƙyalli yake yi Abun yayi matukar ɗaure mata kai,a rude tace"Kai!junaid ya fita da zoben shi aranar!Ya akai zoben kuma ya koma ɗakin Aunty azmee?Taya akai hakan ta faru?Ta yaya zoben shi ya koma ɗakin Aunty azmee..?" tuni zufa ta wanke mata fuskarta,Still bata kawo komai aranta ba, Jiki na rawa ta nufi bedroom ɗinsu,asaman side drawer ta ɗauki wayarta da ta ajiye,kafin ta ajiye wayar Jahad asaman drawer ɗin, Gaban mirror ta koma ta zauna saman kujera,Layin Aunty Azeema ta kira,Cikin sa'a wayar ta soma Ringing,'natsuwa tayi tana jiran ta amsa kiran nata,jikinta sae kerma yakeyi,Allah Allah take yi acikin ranta ta samu Aunty azeema ta ɗaga kiran, Almost 15 missed Calls hajiya Azeema bata ɗaga kiran ba,A ƙarshe dole ta haƙura da kiran nata,ba don taso ba,saboda akwai wani muhimman abu da take so ta tambayeta kuma a wurinta ne kaɗai zata iya samun amsoshin tambayoyin da take dasu, Ajiye wayar tayi gaban mirror ɗin,Kafin ta miƙe tsaye tare da kai idanuwanta ta kalli wall clock ƙarfe 2 na dare, Dafe kanta tayi saboda matsanancin ciwon kan da ya farmata lokaci guda,a sakamakon tunanin da take ta yi,Zuciyarta tayi nauyi sosai,ga kokwanton da take yi,ga fargabar da take ji,Abubuwa dak sun tarar mata, Don bala'e a zaune ta kwana,batare da ta runtsa ba,sai wuraren sallar asuba bacci ya ɗauketa can cikin kunnanta taji ana ambaton Sunanta sehrish sehrish,a firgice ta farka,idanuwanta a zare, Oummansu ta gani atsaye tana kallonta"Sehrish A zaune kika kwana?meyasa baki tafi ɗakin Auntyn taku ba"? Muryarta da alamun bacci bai isheta ba tace"Oumma,bansan bacci ya ɗauke ni ba,"    "Ki tashi kiyi sallah,Anata kira"ta ƙarasa maganar tare da wuce wa cikin toilet, Miƙewa tayi dakyar take iya ɗaga ƙafarta saboda baccin da take ji,zuwa ta fara yi ta hau saman gadonsu ta tayar dasu Hosana suka farka tukunna ta sauko,bayan kowa yayi al'wala,Abu ta shimfiɗa masu Sallaya suka kabbara Sallah,a tsanake suke yin sallar,Bayan sun kammala sallar ne sun zauna kowa ya ɗaga hannunshi suna addu'a,Sehrish ta ɗan yi gyaran murya tare da cewa"Oumma,Jahad Hosana,dan Allah ku tayani da addu'a,Akan abunda nake yi," "Kada ki damu indai addu'a ce kin samu rishi,"acewar Oummansu,hosana tace"A nawa"?   Harara Sehrish ta wurga mata batare da ta tanka mata ba, Suna cikin yin addu'ar nan,Wayar Sehrish dake ajiye gaban mirror ta soma ruri,A zabure ta miƙe tare da nufar wayarta,    "Kira kuma tunda Asuba?Wanene ke kiranki"?tsayawa tayi cak jin abunda oummansu tace,juyawa ta ɗan yi tare da kallonta,ɗan murmushi ta sakar mata"ummm dama Ina tunani ko Aunty Azeema ce ke kira ne"   "Okey,ki amsa kiran"da sauri Sehrish ta ƙarasa gaban dressing mirror ta dauki wayar tare da duba screen ɗin,Wani irin farin ciki ne ya lullu6eta ganin kiran Aunty Azeema, Juyawa ta ɗan yi kamar mara gaskiya ta saci kallon Oummansu dake zaune saman darduma,Hosana harta fara hammar bacci sai cewa takeyi"Wai Oumma addu'ar bata isa haka ba?Dan allah mu koma mu kwanta,murmushi abu tayi tare da kallonta, "kije ki kwanta mana,Wani ya ruƙe maki ƙafafunki,ibadarma baki iya yi da abinci ne duk mun yawanshi sai kin tada shi....."jahad ce tayi maganar tana harararta,   Ganin hankalinsu ya koma kan Hosana yasa ta lalla6a ta fuce daga cikin ɗakin,Gudu gudu sauri sauri take tafiya,kaitsaye ta nufi hanyar nan da zata sadaka da wajen gidan,fitowa tayi ta nufi garden don batason kowa yaji ta, A gefen wata bishiya ta tsaya,tare da duba Screen ɗin wayar missed call har 3 Aunty azeema tayi mata,Danna mata kira Sehrish tayi cikin sa'a Auny Azeema ta ɗaga kiran, A hanzarce Sehrish ta kara wayar a kunnanta,tun kafin tayi magana Aunty Azeema tace"Sehrish lafiya kuwa?kin tashi hankalina,kawai ina farkawa yin sallar asuba sai naga missed calls ɗinki" Muryar ta har shaƙewa takeyi saboda tsabar saurin tayi magana"Aunty azeema,babu abunda ke faruwa,lafiya lou nake,Dan Allah wasu tambayoyi ne nakeso nayi maki,Wani Assignment ne aka bamu a school," "Okey,Allah yasa nasani" "Aunty azeema,Malamar da ta bamu assignment ɗin tana buƙatar muyi bincike akan wani accident daya faru ne,Sai mu sanar da ita amsar da muka samo," Natsuwa hajiya Azeema tayi tana sauraronta,   "Saurayi ne da budurwa,suka shirya zuwa shan ice cream,to akan hanyar zuwansu,sai suka dakata agefen titi,ita budurwar ta tsallaka titin zata siya musu ice cream,ta bar saurayinta acikin motar,kwatsam sai ga wata truck ƙatuwa tabi ta kan motarsu,nan take kuma sai wuta ta kama ci da motar,kafin ƴan kwana kwana su ƙaraso wurin,Wutar taci ta cinye,ba'a samu komai ba daga sassan jikin saurayin, Katseta Aunty azeema tayi"ita malamar taku me takeso ku gano mata ne," "Bari na kai maki ƙarshen labarin,shi saurayin ya zama toka,sai ƙarahunan motar aka samu,to abun mamaki kawai sai kuma ga Zobenshi na Diamond an tsince shi a hannun wani dattijo,zoben bai yi komai ba,sai ƙyalli yake yi kamar sabo,to shine take son kowa yayi nazarin labarin ya fada mata abunda yake hasashe" Abun mamaki tana kai ƙarshen labarin sai taji Aunty azeema na dariya,bubbuga ƙafa Sehrish tayi kamar tana agabanta"Wayyo Allah mommy azeema,meyasa kike dariya,dan Allah ki taimaka ki bani amsar tambayata," Tsagaitawa tayi da yin dariyar,sannan tace"Abun mamaki abun Al'ajabi,kawai sai aka tsinci zoben diamond ɗin saurayin a hannun wani,bayan shi mamallakin Zoben ya ƙone ƙurmus,Gaskiya Sehrish ta baku Assignment me wuya,Amma fa ni abunda nake tunani,in har babban Diamond ne kamar irin wanda na ta6a siya ma Junaid,nasan kin ta6a ganinshi a hannunshi mai harafin J,"   Muryarta har kerma takeyi wurin amsa mata"eh naganshi ahannunshi" "Yawwa,so kin ga kalar wannan Diamond ɗin,In har wuta ta ta6a shi baiyin komai,Sai dai akwai wani abunda yake yi idan wutar ta haura mintuna tana ci ajikinshi,Stone ɗin jikinshi zaiyi duhu sosai,kuma ba hakan yana nufin ya mutu bane,Lafiyarshi ƙalau Amma fa wannan duhun da dutsen jikinshi yayi,A nigeria basu da chemical ɗin da zasu gogeshi,Sae dai anan dubai Companyn da nake siyayyar Diamonds ɗin a wurinsu ne kaɗai zasu iya goge wannan baƙin ya dawo yana ƙyalli" "Amma Aunty Azeema me kike tunani game da Zoben da aka tsinta hannun wani dattijon?Wanda kuma ba'a gabanshi hatsarin ya faru ba,kuma shi saurayin da zoben ya shiga cikin motar Har ya haɗu da hatsarin"ta ƙarasa maganar tana jiran amsarta,don a ƙagare take, Shiru Aunty azeema ta ɗanyi na wani lokaci da alama nazarin wani abu takeyi,   "Naji kinyi shiru mommy," Sai lokacin ta ɗaura da maganarta"Gaskiya abu biyu ne nake tunani,Shi wannan dattijon suspect ne,Amma kuma in har dagaske shi matashin da zoben ya shiga cikin motar,dole abu biyu ne zai kasance!Kodai Shi saurayin ne yayi wurgi da zoben ya faɗo daga cikin motar ko kuma mamallakin Zoben Yana raye!!Yayi escape daga cikin motar shiyasa har aka samu Zobenshi kuma lafiyarshi ƙalau zoben babu alamun wuta ta ta6a shi,kinga kuwa Shima mai zoben bai mutu ba a hasashe na kenan,   Gaban sehrish ne yayi wani irin mugun bugu,Hankalinta yayi matuƙar tashi,idanuwanta azazzare,jikinta har kerma yakeyi, .."amma Aunty azeema,meyasa kike tunanin cewa mamallakin Zoben yana raye,"   "Wlh sehrish ni ko a school ban ta6a cin karo da question mai sarƙaƙiya ba irin wannan tambayar da kikayi mun,Gaskiya nidai nafi kyautata Zaton Shi Mamallakin Zoben ya ku6uta daga cikin motar,Ai kince ita budurwar ta tsallaka titi ne,taje siya masu ice cream. Katse mata hanzarinta sehrish tayi"Amma fa Aunty,ita budurwar koda ta tsallaka titi,Shi saurayin sai da ya kira sunanta,ta juya har yana ɗaga mata hannu ta cikin motar,"   "Kinsan tazarar minti nawa ita budurwar ta ɗauka lokacin da mai ice cream ɗin yake zuba mata ice cream ɗin?   Girgiza kai sehrish tayi kamar tana agabanta haka take gani"A'a bansani ba gaskiya,"   "Idan har aka samu tazara koda na minti biyar ne,ita budurwar ta kawar da idonta daga kanshi,ta mayar da hankalinta wurin mai siyar da ice cream din,A wannan interval ɗin zai iya yiyuwa Ya ku6uta daga cikin motar,ko kuma an ɗaukeshi,Ni daga jin wannan labarin ma wlh duk shiri ne aka tsara don a caza maku brain ɗinku,kin sani sai surutu nakeyi ko breakfast banyi ba,"ta ƙarasa maganar da zolaya,   Dariya Sehrish tayi tare da cewa"Am sorry Auntyna,thank u so much Aunty Azeemana,Kin taimake ni sosai,Yanzu na samu amsar da nakeso,"   "Kada ki damu Daughter,duk lokacin da wani abu ya shige maki,ki sanar dani kawai a shirye nake dana baki shawara"   Murmushi sehrish ta saki,har sunyi sallama zata kashe wayar da sauri hajiya azeema ta dakatar da ita "Wait!kince saurayin ya zama toka ko"?   "Hakane,"ta amsa mata, "Taya za'ace ko ƙashin jikinshi ba'a samu ba?wutar tayi more than one hour ne tana ci?ba kince an kira motar kwana kwana ba,"    "A'a banda masaniya akan wannan amma zan tambaya,"   "Okey,akwai wani incident daya ta6a faruwa, makamancin labarin da kika bani,almost 30 mins wutar naci A motarsu,ba'a kashe wutar ba,saboda babu wasu a kusa,Ko daga baya da mutane suka zo aka kashe wutar an samu wasu konannun 6angarori na jikinsu,duk da zai iya faruwa dagaske ae yasha faruwa ma,mutun ya ƙone ƙurmus sai tokarshi,ko indiyawa ma ai suke ƙona gawarsu su kuma ƙulle tokar in zasuyi jana'iza Amman kinga ai wutan tana daukar lokaci tana kona gawar,Amma nidai gaskiya a labarinki Ban yadda cewa Wannan mamallakin Zoben ya mutu ba!!Amsar da zaki ba malamar ku kenan!Ki sanar da ita duk wani bayani da nayi maki,Nasan zata baki mark sosai," Jiki asanyaye sehrish tace"in sha Allah Aunty azeema,Zan rubuta duk wani bayani da kika yi mun nagode sosai," Daga haka su kayi sallama,kamar jira takeyi ta katse kiran,jiki a mace ta zauna gefen bishir,Ta gaza yadda da abubuwan da kunnuwanta suka jiye mata,Dama kuma it will be very hard farat ɗaya ta fara suspecting ɗin Azmee,Bakomai yafi tsaya mata arai ba,fa ce waɗannan tambayoyin masu matuƙar wuyar amsuwa Junaid yana raye ko ya mutu?taya akai zoben Junaid yaje ɗakin Aunty Azmee?kodai zoben aljani ne yana da fiffike harya tashi sama ya fito daga cikin motar da fika fikinshi yazo ɗakin Aunty azmee?Sai lokacin ta soma tunanin wai ma wacece Aunty azmeen nan?tunda suke atare da ita,bata ta6a bata labarin danginta ba,kwata kwata bataso a tambayeta dangane da danginta,Sannan kuma tunda take da Aunty Azmee bata ta6a cewa zata je gano gida ba,Uwa uba kuma Aunty azmee bata ta6a gajiyawa dayi masu aiki ba,A ƙalla idan zata lissafa shekarun Junaid da akace ta shayar dashi tun yana jinjiri,Azmee tayi more than 20 years a gidan, Zurfin tunani ta shiga yi,maganganun ya sayyadi ne suka shiga dawo mata acikin kanta,inda yake cewa kaf family dinsu a tafin hannunsu suke,Duk wani motsi nasu akan idanuwansu suke,Kenan Suna da ɗan leƙen asiri acikin gidan?Dolen doliya akwai wanda ke shirya wata maƙarƙashiya acikin gidan,Tunawa tayi da wannan malamin makarantar nasu Ya Mu'allim da ya ta6a bata ruwan addu'a ta sha saboda yawan bacci da take a aji,lokacinne kuma ta Manta dasu Hosana kwata kwata,Tabbas Akwai abunda akayi mata,still Sehrish bata fara zargin kowa ba kuma har lokacin bata sanyawa ranta cewa Aunty Azmee tana da sa hannu a Mutuwar Junaid ba,Tama fi zargin Haroon don yasha sanar da ita cewa Zai kashe farin cikin gidan,Duk da tana doubting akan kalamanshi,Saboda shi ɗan giya ne yawancin kalamansu suna faɗi ne ba don su aiwatar ba,koba don haka ba,tana ji aranta cewa Haroon bazai iya kashe junaid ba, Sehrish bata bar wurin bishiyar nan ba,Har sai da ƙarfe 10 ta buga,kamar wadda tasha ƙwaya haka take tafiya,Ga wani matsanancin ciwon kai da ya rufar mata,Ta caza ƙwaƙwalwarta sosai, Lokacin da ta shigo cikin gidan,ta ƙopar da ta fita,kaitsaye bedroom ɗinsu ta wuce,Tura ƙopar ɗakin tayi ta shiga,Oummansu ta samu zaune gefen gado tana shan Coffee, Jin motsin shigowar sehrish ne yasa ta ɗago da idonta tana kallonta,   "Ina kika je ne?har muka kammala yin breakfast baki dawo gida ba,"   Daƙyar ta iya buɗe baki tace"na shiga garden ne shan iska,"gudun karta ƙara tambayarta yasa tayi saurin cewa"Oumma,Coffee kike sha"   "Azmee ce ta kawo mun shi yanzun nan,"   Murmushin yaƙe sehrish ta dan saki tare da samun wuri gefen oummansu ta zauna,   "Ba zaki ci abinci bane"?cike da kulawa tayi mata maganar,   "A'a,na ƙoshi bana jin yunwa sai zuwa anjima zanci,"    Miƙa mata cup ɗin hannunta tayi"kar6i kisha,"batayi mata musu ba tasa hannu ta kar6i Cup din takai bakinta tana sha,kur6a uku tayi ta dakata da shan Coffee ɗin tare da kallon Oummansu,   Ganin tana kallonta yasa tace"Lafiya,kike kallona?"   Murmushi sehrish ta dan yi "babu komai oumma,kawai inaso na tambayeki wani abu ne,"   "Ina sauraronki" "Amm oumma,jiya naga kin ɗan razana da kika ga Azmee,kinsanta ne?   "Kamar nasanta amma bazan iya tunawa ba,"    "Dan Allah Oumma kiyi ƙoƙari ki tuna,"   "Shikenan,idan na tuna zan sanar dake,"   Ba ƙaramin daɗi taji ba,Miƙewa tayi da sauri ta nufi toilet,Shaf shaf tayi wanka,lokacin da ta fito bata samu Oumman tasu da ta batari a azaune ba,babu kowa a ɗakin, Tunani ta shiga yi ko Sgr Yana acikin gidan?tanaso taje ta duba lafiyarshi amma tana fargabar a wani hali zata same shi,dan kwanakin nan sam baya buƙatar kowa atare dashi, Wani haɗaɗɗen lace ta ɗauko Ash colour sai ƙyalli yakeyi,riga da skirt ne,Sanya kayan tayi a jikinta,sunyi mata cuf cuf sun bi shape ɗin jikinta,Ɗinkin ya fito da ita sosai,kashe ɗaurin kallabi tayi,bayan ta ɗaure gashin kanta da ribbom,Gaban mirror ta koma ta zauna ta fara yin make up,murza wanccan shafa wancan manna wancan,kamar Aljana haka ta koma tayi kyau Over, Wayarta ta ɗauka,ranta ne ya bata cewar ta tura mashi text message,may be ya bata amsa,   _Hi,Gm Ya Rafayet ina fata ka tashi cikin ƙoshin lafiya,bansani ba ko yau kana buƙatar wani abu in kawo maka_   Almost 5 mins da tura mashi saƙon saiga reply ya maido mata"I need coffee,"   Murmushi ta saki kamar bata da damuwa acikin ranta,Ajiye wayar tayi agaban mirror ɗin,ta fito daga cikin ɗakin,kaitsaye ta nufi kitchen,A babban falo ta samu mutanen gidan suna fira abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,ga Oummansu ga Alex gasu fawan ga kuma su Jahad,tare da Abusufyan,"mutun uku ne kaɗai basu Hallara ba,Sgr Omar da Abbansu junaid, Basu jiyo takun takalminta ba,saɗaf saɗaf ta shiga kitchen,har sai da gabanta ya faɗi lokacin da ta ga azmee a cikin kitchen ɗin,Batayi tsammanin akwai mutun aciki ba,   "Kin tsorata ni,"Azmee ce tayi maganar,A yayin da take tsaye gaban sink tana wanke kwanukan da sukayi amfani dasu,   Murmushin yaƙe sehrish ta sakar mata   'Afuwan Aunty azmee,nikaina saida na tsorata dana gan ki,Banyi tunanin akwae mutun ba,Shiyasa banyi sallama ba,"   "Irin wannan kyau haka Sehrish?lace ɗin nan ba ƙaramin kyau yayi maki ba,"tayi maganar fuskarta ɗauke da murmushi,    Murmushi sehrish ta kuma saki"babban yaya zan kaiwa coffee,'   "Allah sarki,kwana biyu na lura yana cikin matsananciyar damuwa shi da Omar,musamman Abba Allah ya kawo masu mafita,Allah ya bayyanar da Junaid,"damuwace ƙarara akan fuskar azmee da tayi maganar,   "Nima na damu akan rashin Junaid aunty azmee,kowa ya shiga damuwa sosai,bawan Allah,junaid da baison komai ba sai kyautatawa,Amma dan rashin imani da tausayi aka samu wasu mugayen suka ɗauke shi,in sha Allah Nan bada jimawa ba asirinsu zai tonu,Sai sun gane kuskurensu,kuma sai sunyi danasanin abunda suka aikata"da biyu sehrish tayi maganar,don taga react ɗin da Azmee zatayi,   "Am naji kince zaki kaiwa Sgr coffee ko?Yakamata ki hanzarta kai mashi,idan kin dawo inaso muyi gurasa atare,nasan mutanan gidan nan zasu ji daɗi sosai idan akayi gurasa,Don An jima ba'ayi masu ita ba kuma suna so,"   Cike da mamaki sehrish ke kallonta,Maimakon ta bata amsa kan maganar da tayi mata,amma sai gashi ta Canza magana,    "Shikenan Aunty Azmee,Bari na kaimashi," After some minutes ta fito hannunta ruƙe da Cofeen, Sai da ta fara tsayawa ta gaisar da mutanen falon kowa nata yabon wankanta,kafin ta wuce upstairs, Lokacin da ta shiga bedroom ɗinshi,a kwance ta same shi saman katafaren gadonshi kamar mai yin bacci alhalin nan kuwa idonshi biyu yadai lumshe idanuwanshi ne, Ƙarasa shiga ciki tayi ta ajiye mashi cup din asaman table,Sannan anatse ta ambaci sunanshi"Ya Rafayet,ina kwana," Banza yayi bai amsa mata ba,tunani ta shiga yi kodai bacci yake yi ne?   "Babban yaya,"ta ƙara kiran sunanshi nan ma yayi mata shiru,sai da ya mula yasha iska kafin ya ɗan buɗe idanuwanshi tare da kallon wurin da take a tsaye,duƙar da kanta ƙasa tayi tana wasa da yatsun hannunta,    Da wannan sexy voice ɗin tashi ya furta"Au is that how i taught u to greet me"   gabanta ne ya ɗan faɗi tunawa da irin gaisuwar da yakeso ta dinga yi mashi,tabɗijancan,wani irin kunyarshi take ji,   "Am waiting within 3 mins"ya ƙarasa maganar tare da mayar da idanuwanshi ya rufesu, Da sauri ta cire takalmanta kafin ta hau saman gadon,Sai da taje saitin inda yake kwance sannan ta tsaya tana tunanin taya Zata fara,ga lokaci na tafiya,don ma Allah Yasa ya rufe blue eyes ɗinshi,     daidai lokacin da minti uku suka cika Cuf,a hanzarce ta ɗan ranƙwafa gefen fuskarshi,lips ɗinta na kerma ta manna mashi kiss,har sai da taji ajiyar zuciyarshi alamar yayi receiving ɗinshi,other side ɗinma ta Manna mashi kiss,Saura na baki,   Zuba ma Sexy lips ɗinshi ido tayi tana kallonsu gwanin ban sha'awa yadda kasan na jinjiri haka suke,saboda kyau da softnesss dinsu,   Ganin yana ƙoƙarin buɗe idanuwanshi ne yasa tayi saurin hada mouth ɗinsu wuri ɗaya,sam bai ta6a tsammanin zata iya yi mashi kiss ba,sosai take shan lips ɗinshi tun daga kan lower lip dinshi zuwa upper,baisan lokacin da ya ƙara ƙankameta ba ajikinshi,hannayenshi gaba ɗaya suna asaman Ass ɗinta,yayin da ita kuma hands ɗinta ke tallabe cikin sumar kanshi,gaba daya suka harɗe wuri guda kamar tip da tyre,da niyyar gaisuwa tayi mashi hakan kamar yarda ya umarce ta sai gashi ta zarce da sarrafashi,ƙaramar yarinya na neman Zautar dashi,sai da yayi dagaske sannan ya samu yayi control ɗin kanshi,a lokacin harya zuge zip ɗin rigarta,kwantar da fuskarshi ya yi asaman boobs ɗinta,hancinshi na gogarsu haka la66ansa,tana jin saukar numfashinshi dake fita da zafi zafi,jurewa kawai yake yi,Shi kaɗai yasan halin da yake shiga a duk time din da ya kasance tare da ita,   Zagayo da hannunta tayi ta cikin sumar kanshi tana shafa mashi ita,nan fa ya ƙara narkewa a jikinta kamar jinjiri ajikin Babarsa,    Bakomai ya faɗo mata aranta ba fa ce abunda Aunty azeema ta sanar da ita,Wato ta ɗaukeshi kamar jinjirin da aka bata rainonshi,komai ta koya mashi zai ɗauka ne harya fara kwatanta yi mata,    Moving lips ɗinta tayi izuwa saitin kunnashi,Calmly ta furta sunanshi"Ya rafayet,"    Ƙasa ƙasa taji ya amsa mata"yeah,"   "Have you ever been in love"?ita kanta batasan ta furta mashi hakan ba,    "I don't know anything about love,I only know how to hold a gun" Sam batayi expecting ɗin zai bata amsa ba,   Murmushi tayi sosai,kafin ta kuma cewa"Coffee ɗinka fa?Zai huce,"    "I don't need it now,Am just enjoying being with u"daƙyar yake yin maganar saboda yanayin da yake jin kanshi,sehrish tsantsar farin ciki ne ya lullu6eta,kalamanshi sun ƙayatar da ita,   Wasa wasa bacci yayi awon gaba dashi,dama kwanakin nan bai samu ya runtsa ba,Reesh da babynta,saura babyn baby mai zuwa, Dayake itama bata samu enough sleep ba adaren jiya,sai gashi ta fara jin baccin, Wayar Sgr dake ajiye saman side drawer ce ta soma ringing,firgit ta farka,tare da miƙa hannunta tana lalubar wayar,don batason tayi moving din da zaisa ya farka, Daƙyar ta samu yatsun hannunta suka ruƙo wayar,janyota tayi izuwa saitin fuskarta,Wani kalar suna ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,Can dai na yarensu na sojoji, Picking Call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta,   Wata kakkausar murya ce ta soma ji acikin kunnanta,   "Sir!kana magana da sergeant Lee ɗaya daga cikin sojojin da ka sanya Su tsare maka grave ɗin younger brother ɗinka Junaid,"   Har saida gaban sehrish ya faɗi rass gashi ta kasa sanar dashi cewa ba Sgr ɗin bane,    "Since yesterday night naso na kira wayarka bansamu halin yin hakan ba!abunda ke faruwa shi ne yau almost 1 week kenan,akwai wani matashin saurayi dake yawan yin zarya a titin nan,kullum yana zuwa ne cikin motarshi ƙirar Venza Ash colour,mun sanya mashi ido sosai,gaskiya Sir we are suspecting him,Zaryarshi tayi yawa,kuma bai tashi zuwa sai wuraren 10 na dare,kuma idan yazo wurin ƙabarin sai yayi parking ɗin motarshi ya fito daga ciki,Yayi ta zagaye wurin da grave ɗin yake,kamar yana neman wani abu......"   Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,batasan lokacin da tayi rejecting kiran ba,jikinta har kerma yake yi,mayar da wayar tayi saman drawer ɗin ta ajiyeta, Lalla6awa tayi da sauri ta zame jikinta daga nashi,gyara zip ɗin rigarta tayi,kafin ta sauko daga saman gadon,Zuciyarta sai faman harbawa takeyi,tayi danasanin picking call ɗin,da bataji wannan tashin hankalin ba acikin kunnanta, Fitowa falonshi tayi asaman sofa ta zauna jikinta nata kerma,tsananin tsoro ne ya kamata,tunani ta shiga yi wanene Yake yin zarya a wurin ƙabarin junaid?me yake kai shi?me yake nema a wurin!tuni kanta ya fara yi mata ciwo,dama akwai ciwon kan ya ɗan lafa ne, Hawaye ne suka soma saukowa akan fuskarta,lamarin ya fara rikitar da ita,daga wannan sai wannan?wai duk waye ke shirya wannan Maƙarƙashiyar ne"? Miƙewa tayi bayan ta share hawayenta,fitowa tayi daga cikin part ɗinsa ta sauko downstairs kitchen ta koma,A bakin ƙopar shiga kitchen ɗin ta tsaya tare da goya hannayenta akan ƙirjinta tana kallon Azmee dake gasa Gurasa a frying pan,   Gaba ɗaya hankalinta bai atare da ita,   "Sehrish,"Azmee ce ta ambaci sunanta a firgice takai idanuwanta kan Azmeen,    "Tun ɗazu nake ta jiranki baki zo ba,har na fara gasa gurasar,ko zaki taimaka ki yanka mun vegetables din da zanyi amfani dasu?ga kuma ƙuli da za'a daka,"   Tunda ta soma magana sehrish tayi kasaƙe tana kallonta,batare da tace uffan ba,abubuwa dak sun cunkushe mata kwalwarta,ta fara rasa tunaninta,ji take kamar ta tambayeta ya akai Zoben Junaid yaje ɗakinta amma ta kasa yin hakan,    Dafa kafaɗunta Azmee tayi tare da ɗan girgiza jikinta"Wai baki ji ina magana bane"?   Da sauri tace"Amm ummm yanka kuli ko zanyi"   Dariya azmee tayi sosai jin abunda tace,    "Kin ta6a ganin inda aka yanka ƙuli ne?Nifa Cabbage dasu tumatur nace ki yanka mun,Shi kulin daka shi za'ayi,already akwai shi,wai ko baki da lafiya ne?naji jikinki da zafi"tayi maganar tare da sanya hannunta agefen wuyan Sehrish,    "Banajin daɗi Aunty azmee,ina buƙatar addu'arki,"tana magana kamar ta fashe da kuka,    Janyota azmee tayi tare da rungumeta ajikinta,   "Allah ya baki lafiya ƙanwata,in dai addu'ace zan cigaba da tayaki,kema kuma ki dage da yin addu'a akan Allah ya yaye maki abunda ke damunki"    Lamo sehrish tayi ajikin azmee har yanzu bata fara zarginta ba,kuma bata kawo komai aranta ba,Tana jinta tamkar mahaifiyarta,Saboda irin kulawar da take bata,    "Aunty azmee na gode sosai,Allah ya barmu tare" ."Ameen ameen,"ta ƙarasa maganar tare da ɗago sehrish daga jikinta,    "Kije ki kwanta kawai kina buƙatar hutu ni zan ƙarasa yin gurasar"    Girgiza kai Sehrish tayi"A'a ae da sauƙi ciwon,Inaso na tayaki aikin,Ae ba wani abu bane me wahala,"   Batare da 6ata lokaci ba,Sehrish ta fiddo kayan da zasu yi amfani dasu,Cabbage ne tare da tomotoes,Albasa da sauransu, Suna cikin yin aikin Sehrish ta soma ƙoƙarin bugun cikinta,   "Aunty azmee,jiya da kika ga Oummanmu naga kin ɗan razana haka kamar kinsanta,"    "Kallon sani nake yi mata,Amma gaskiya bansanta ba,Zai iya yiwuwa sunyi kama da wata wadda na ta6a sani ne,"    "Okey,amma tunda nake dake Aunty azmee,baki ta6a bani labarin danginki ba,Gashi na kwaɗaitu da son jin Labarinki,inaso wata rana idan kin tashi kai musu ziyara mu tafi tare,"   Shuru Azmee ta ɗan yi har lokacin tana tsaye agaban gas tana gasa gurasar,almost 15 mins bata ce komai ba,har sai da Sehrish ta ambaci sunanta"Aunty azmee,kin yi shiru,"   Murmushi azmee tayi irin na gefen fuskar nan,   "Sehrish tunda nake dake baki ta6a tambayar dangina ba sai yau,shiyasa ban ta6a baki labari ba nima,ina da wani hali ni,in har mutun bai tambayeni abu ba,to kuwa bazai ta6a ji ba abakina,Amma yanzu tunda kin tambaye ni,idan muka samu Free time zan baki tarihin rayuwata,"   Daga haka suka mayar da hankalinsu akan aikin da suke yi,Bayan sun kammala yin gurasar a saman faffaɗan tray Suka jejjerata,uban ƙuli suka barbaza asamanta,sannan suka shanana mai asaman kulin,ko ina yaji,daga sama kuma sukayi mata ado da kayan lambun da sehrish ta yanka, Fita azmee tayi daga kitchen ɗin tabar Sehrish kamar yadda sukayi ita zata raba masu gurasar,Ba ƙaramin daɗin gurasar nan suka ji ba,musamman matasan gidan har rububi suka dinga yi,kowa sai da ya yaba daɗin da tayi, Wurarren ƙarfe biyu na rana,bayan ta kammala sallar azhar ta koma kitchen ta shirya ma Sgr tashi gurasar,A saman wani ƙayataccen plate mai faɗi,batasan ko yana ra'ayinta ba,ita dai kawai tayi niyar kai mashi ne, Tana ƙoƙarin shiga falonshi suka ci karo da juna,ƙiris ya rage plate ɗin hannunta ya 6are da sauri ya tallabo mata shi,tun daga ƙasa ta soma kallonshi,T shirt ce a jikinshi Blue ta fito da hasken shi sosai,Sai trouser ɗinsa black colour,da alama sauri yake yi ya fita, Zuba ma juna ido sukayi batare da ƙyaftawa ba, "Ina yini,ka tashi lafiya"? Lumshe mata eyes ɗinshi yayi alamar yana lafiya batare daya furta mata ba, ..."menene wannan"yayi tambayar yana nuna plate ɗin hannunta, "Gurasa ce,kai na kawo mawa," Yatsina fuskarshi ya ɗan yi,tare da cewa"Sauri nake yi zan fita,"jiki asanyaye ta juya zata koma da ita, "zonan"ya kirata,da sauri ta juya tana kallonshi, "Someone called my line,Ke kika ɗaga"? Zuru tayi mashi da idanuwa gudun kada yayi mata faɗa, ..a ɗan hasale yace"Am asking u!" A tsorace ta ɗaga mashi kai alamar eh' "Its okey,juyawa yayi tare da komawa ciki" Bin bayanshi tayi asaman Sofa ya zauna,Ta ajiye mashi gurasar saman table,cire mashi murfin da ta rufe plate ɗin tayi,    💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Saman Sofa ya zauna,Sehrish ta ƙaraso ta ajiye mashi plate ɗin saman table ɗin gabanshi,hannu tasa ta cire murfin da ta rufe gurasar dashi,ɗan ɗagowa tayi tare da satar kallonshi samun shi tayi ya jingina bayanshi a jikin kujerar,idanuwanshi a lumshe suke,gyaran Murya ta ɗan yi mashi"Ya rafayet,"slowly ya buɗe idanuwanshi akanta,nuna mashi gurasar tayi alamar yaci, Muryarshi a kasalance yace"who asked u to pick the call?" gabanta ne ya fadi calmly tace"dama naga baka dade da yin bacci ba,don kar kiran ya tashe ka yasa na dauka don in fadi ma mai kiran bacci kake,to kuma sai naji banjin abunda ake cewa shine nai rejecting kiran,amman kayi hkr"ta karasa kanta a kasa,still yayi yana cigaba da kallonta can taji yace"Ni zanci da kaina?" dagowa tayi suka hada ido, saurin kawar da idanuwanta tayi saboda kunyarshi da take ji,musamman inta tuna abunda tayi mashi asaman shimfiɗarshi, Daƙyar ta iya buɗe baki tace"zan iya baka idan kana so," Nuna mata gefenshi yayi ta zagayo ta zauna,ƙamshin turarenshi har cikin kanta,A yangance tasa hannu ta nannaɗo gurasar,tana ƙoƙarin kaiwa bakinshi idanuwansu suka haɗu wuri guda,kasa janye idanuwanshi yayi daga kallonta,wasu abubuwa sun ɗan fara ɗaure mashi kanshi,Ta canza mashi sosai ba kamar daba time ɗin da ko haɗa ido bata iyayi dashi amma yanzu takan ɗan kalleshi harma su haɗa ido,kuma jikinta ya daina wannan rawar da yake yi duk in tazo part ɗinshi,hakan na nufin ta rage jin tsoronshi?ko meyasa?ko dan saboda romancing ɗin da yake yi mata ne? Ganin ta kasa tura mashi gurasar abaki yasa ya ruƙo hannunta tare da matso dashi saitin bakinshi ya tura gurasar ya ɗan 6alla yana Ci,yayin da idanuwanshi ke kallon fuskarta,ita kuwa tuni ta kawar da idanuwanta daga kallonshi da take yi,sai dai satar kallon mouth ɗinsa da take yi,yadda yake chewing ɗin gurasar,soft lips ɗinsa na motsi ba ƙaramin fisgarta yake yi ba,sun 6ata mintuna a wurin nan,har sai da ya kammala ci sannan Sehrish ta miƙe ta nufi fridge,Coke ta ɗauko mashi mai sanyi ya kora da shi,bayan ya kammala sha Ya nufi bedroom ɗinshi,bin bayanshi tayi don ta gyara mashi ɗakin,A tsaye ta same shi ya kara waya a kunnanshi yana magana,   Shiga ciki tayi da sallama abakinta,kaitsaye ta fara gyara mashi bed ɗinshi,tana jin moving ɗinshi lokacin daya kammala yin wayar ya faɗa toilet,jim kaɗan ya fito yana gyara wrist watch ɗin hannunshi"Am leaving"Shi ne abunda taji yace,juyowa ta ɗan yi tare da kallonshi"when are u coming back"?daƙyar ta samu ta iya tambayarshi,tana ƙoƙarin yin practice ɗin abunda Azeema ta koya mata,   Shi kanshi ya jinjina tambayar da tayi mashi,hakanan kawai dai yace"Zan kai 12 na dare,"   Gyaɗa kai tayi tare da mayar da hankalinta kan Gadon da take gyarawa,tun kafin ma ya fita harta fara Missing ɗinshi,ga wani abu da ke yi mata yawo a kanta,Tana so ta sanar dashi about Junaid's ring da ta gani a cikin drawer ɗin Azmee amma ta kasa faɗa mashi,saboda bata ƙarasa investigation ɗinta ba,Amma taci alwashin muddin ta gano dasa hannun Azmee dumu dumu saita gaya mashi ne,' tana cikin wannan zancen zucin unexpected taji yayi hugging ɗinta ta baya,gaba ɗaya ya saukar mata da kasala,hannayenshi ya zagayo ta saman stomach ɗinta,A hankali yake rubbing tsinin Hancinshi asaman fatar wuyanta,lumshe idanuwanshi yayi tamkar maijin bacci,bakomai yake yi mashi yawo acikin kanshi ba,fa ce zancen Marshal Na little Junaid,Still yana deciding din lokacin da ya dace ya aiwatar da hakan duk da yanzu baya cikin kwanciyar hankalinshi,wata irin kasala ce ta kama kowannansu ya jima ahaka kafin ya saketa,da sauri ya fuce daga Bedroom ɗin yana jiyo voice ɗinta tana yi mashi adawo Lafiya, Fitarshi ke da wuya,Sehrish ta zauna gefen gadonshi tana tunanin ta yadda zata iya taimaka masu,remain 4 days Yanzu acikin waɗannan kwanakin Yakamata Su gano Abu biyu waɗanda suka kashe Junaid,ko kuma shi junaid ɗin if he'a still alive,Kamar yarda Aunty azeema take hasashe,abubuwa da yawa sun shige mata kanta,akwai buƙatar zuwanta ɗakin azmee domin ƙara yin bincike,Sai dai tana tsoran Azmee ta kamata, Miƙewa tayi taci gaba da gyaran ɗakin,bedroom ta fara gyarawa,kafin ta shiga toilet ɗinshi nan ma ta gyara,dawowa palourn tayi tana Aiki tana sambatu kamar wata zautacciya, Wuraren ƙarfe 4 na yamma,Amrish na kwance tana bacci saman katafaren gadonta,daga ita sai gajeran wando black colour,sai half vest wadda bata rufe cibinta ba,juyi ta soma yi alamun zata farka daga baccin,lokaci guda ta ware manyan idanuwanta tana kallon ceiling,ranta yayi matuƙar 6aci lokacin da ta tuna dalilin yin baccin nata,sam batasan ya ɗauketa ba,kuma tana zargin cewa maganin bacci aka bata,dama kwanakin nan duk in Mommynta zatayi baki saita ɗura mata ƙwayar da zata sata bacci,Yawanci acikin abunsha take sanya mata,miƙewa tayi daƙyar saboda kasalar da take ji,Saukowa tayi daga saman gadon tana miƙa tare da yin Hamma,toilet ta nufa zata shiga sai kuma ta fasa,Fitowa tayi daga cikin ɗakinsu ta nufi bedroom ɗin Mommynta,hannu tasa zata ruƙo handle ɗin ƙopar ɗakin don ta buɗe,Surutun da tajiyo daga cikin ɗakin yasa ta dakata,tare da kasa kunnanta tana sauraranta,   "Wlh bazan ta6a ƙyalesu ba,Zasu yi galaba akanmu ne,ai kawai ku kashe shi,ku kashe shi kawai,ko ku cire mashi idanuwanshi,Uban kowa ya rasa,idan har ba zaku iya ɗaukar mataki ba,to ni zan ɗauka dakai na,"da alama waya take yi,yadda kasan yar daba,   Hankali amatuƙar tashe,ta toshe bakinta da hannunta,gudun kada ta saki ihu,jikinta sai kerma yake yi,lalla6awa Amrish tayi cikin sanɗa ta koma bedroom ɗinta,agefen gado ta zauna,Yayin da zuciyarta ke ta bugawa,Dama ta jima tana zargin Momynta,   "Amma mommy bata da Imani,sai cewa takeyi akashe akashe,kamar wata zararra,wlh nima bazan ƙyaleki ba mommy ki yi kisan kai ina gani,Zan cigaba da samaki ido ne batare da kinsani ba,kuma Allah muddin nagano cewa kashe ƴa'ƴan mutane kikeyi da kaina zan kaiki ƙara wurin hukuma su garƙameki,"tana magana tana cizon le6enta, Turo ƙopar ɗakin nata akayi,da sauri ta baje saman gadon tana baccin ƙarya hada minshari,mommy ce ta shigo hannunta ruƙe da wayarta, Zuba ma Amrish ido tayi tana kallonta,kafin ta Kanga wayar a kunnanta   "Har yanzu Bata farka daga baccin ba,Ni na bata maganin bacci,Wlh ta cika sa ido,ga bin ƙwaƙƙwafin tsiya,Har sa'insa take yi dani shiyasa nake bata maganin bacci"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar tana sauraron wanda suke yin wayar dashi, "Ae ni na kwace wayar hannunta,Shiyasa ko ka kira bazaka same ta ba,idan ba haka ba zata iya zame mun matsala,"   Kasa kunne Amrish tayi tana sauraronta,Aranta tace"Asirinki ya tonu mommy,yau naji da kunne na,wato ke kike bani maganin bacci ina sha,ko wa take faɗama cewa ina bacci hmmmm,ta ƙarasa zancen zucin tare da jan dogon numfashi irin na wanda yayi nisa a baccin nan,   "Okey,Bazan barta da yunwa ba,Yanzu zan tashe ta taci abinci,Ae bazan ƙara wasa da lafiyarta ba,duk da bata da hankali,"   Sallama sukayi da mutumin da take yin wayar dashi,zama tayi daga gefen gadon,a tsanake ta soma kiran sunanta   "Amrish!Amrish!"kusan sau biyar tana ambaton sunanta,hada bubbuga ƙafarta,A hankali Amrish ta ɗan buɗe idanuwanta,muryarta a kasalance ta furta"Mommy,lafiya kike ƙwala mun kira"?   "Tun ɗazu kike bacci,Ko sallah bakiyi ba halan?Ga la'asar ma na ƙoƙarin yi,ki tashi ga Abincinki can a dining kije ki ci," miƙewa tayi daga zaune,tana yin hamma kafin ta wuce cikin toilet,koda zata rufo ƙopar saida ta ƙara leƙen Mommynta,kafin ta datse ƙopar, *AMANI* Zaune suke acikin falon gidan,Hayaam Da Abra na zaune saman 3 seater,Yayin da Amani ke zaune saman 2 seater,hayaam ce ta soma magana"Aunty Amani,mun yanke shawarar zamu koma gida gobe,bai kamata mu cigaba da zama anan ba muna ɗaura maku nauyinmu,kinyi mana abunda bazamu ta6a mantawa ba,"ta ƙarasa maganar yayin da idanuwanta ke acike tab da kwalla, Ajiyar zuciya amani ta sauke tare da cewa"Shikenan,gaskiya yakamata ku koma kam kodan Saboda Mammy da Abra ta baro kwance tana jinya,Bamusan a wani hali take ciki ba ayanzu,'   "Aunty laila fa'?Abra ce tayi tambayar,   Hayaam tace"Ina ruwanmu da ita?tana raye kota mutu matsalarta ce,bata da amfani acikin rayuwarmu,"   "Kada ki ce haka hayaam,itafa ƴar uwarkuce,duk da bata kyauta maku ba amma bai kamata kuyi watsi da ita ba,Yanzu dae bamu san awani hali take ciki ba,Amma mujira mu gani,indai Laila ce nasan zata dawo ne,sannan ina ƙara gargaɗinku akan irin rayuwar da kuka ɗaurawa kanku,musamman ke Abra,kinga dai irin abunda ya faru da hayaam kema kuma in baki kiyaye ba,zaki jefa rayuwarki cikin hatsari ne,mazan da kuke mu'amala dasu ɗaya daga cikinsu bazai iya aurenku ba,Idan ma ya aureku to bazai darajaku ba,sannan kullum zaku kasance cikin zargin juna,so wannan rayuwar ba mai 6ullewa bace,kuma ku mika dukkan al'amuranku wurin Allah,duk abunda yake rabonka ne kana zaune zai same ka,in ku ka ga baku samu abunda kuke so ba,to Allah bai kaddaro rabon ku bane...."sosai Amani tashiga yi masu nasiha jikinsu duk yayi sanyi,hada kuka, Suna cikin tattaunawar nan,Amal ta faɗo cikin falon,hannunta ruƙe da wayar Amani,ƙarasowa tayi wurin da amanin take a zaune ta miƙa mata wayar"Yaya Abbas ne ya kira," Harararta Amani tayi"Dama wayata tana a hannunki,"?sunnar dakai ƙasa tayi tana dariya,   "tare da Amal zamu tafi gobe'?acewar abra,tayi maganar tana kallon Amal ɗin    Wani irin kallo Amal tayi mata,hada cizon la66a,dariya Amani tayi tare da cewa"Ba zaki bisu ba,kinga yanzu komai ya dai daita,ki amince kawai ki koma cikin ƴan uwanki da zama,   A shagwa6e Amal ta bubbuga ƙafarta tare da ruqe qugunta"Nifa wlh bazan bisu ba,idan kin gaji da zamana ne a gidanki,nan bada jimawa ba,Yaya Jahan zai ɗauke ni," Gaba daya suka zuba mata ido suna kallonta cike da mamaki a fuskokinsu,banda Amani dama ita tasan tsakaninta da Jahan,   Murmushi Amani ta saki tare da cewa"Nima wasa nake maki,Ae Amal ta gama zaman maiduguri in ba dai zuwa kai ziyara ba,daga Abuja sai ƙasar waje ko ba haka ba?'cike da zolaya tayi mata maganar, Murmushi Amal tasaki,tare da juyawa da gudu tabar falon tana dariya Tashin sense,jikinsu Abra ba ƙaramim sanyi yayi ba,duk irin burin da suke dashi na zama surukan Alexandra ya tashi abanza,Sai gashi Yarinyar da suka raina,Suke wulaƙantawa ita ke da rabon auran jinin Alexandra,Abun ba ƙaramin ta6a masu zuciya yayi ba,sunyi danasanin rayuwarsu,zuba masu ido Amani tayi tana kallonsu ganin yadda kowa tasha jinin jikinta, *General Ishaq* Fitowarshi kenan daga cikin toilet,Jikinshi sanye da jallabiya,tun yana acikin toilet yaji ringing ɗin wayarshi,ƙarasawa yayi tare da kai hannu ya ɗauki wayar,New number ce aka kirashi da ita,Bin kiran yayi kiran na shiga aka ɗaga wayar"Assalama Aleekum"muryar wani inyamurin mutunce,   "Wa'alaikum salam,ko zan iya sanin dawa nake magana"? On the other hand mutumin yace"Yalla6ai dama wani bawan Allah ne keson magana dakai,Shine yace in taimaka in kira mashi layinka,"   "To bashi wayar,"tsayawa yayi yana jiran jin muryar mutumin da akace yana son magana dashi,   Abun mamaki sai yaji kukan Laila Acikin wayar,ya cika kunnanshi,cikin shessheƙar kuka ta wanda ya galabaita ya jigata sosai ta soma magana"Abban hafsat ni ce laila,dan Allah akawo mun ɗauki,ina cikin mawuyacin hali,"   Murmush Ishaq ya ɗanyi tare da cewa"Bangane wake magana ba?kodai wrong number ne aka kira"?   Jin haka yasa ta ƙara sautin kukan nata"Ishaq kada kayi mun haka,Wlh ina cikin masifa,gani nan a Enugu yashe gefen bishiya,sai an bani sadaqa sannan nake samun abunda nake sawa acikina,Wlh Ishaq na tuba nabi Allah,Akawo mun agaji ƙafata ta lalace ta ru6e...."tana magana tana kuka,   Handsfree ya sanya don yaji daɗin sauraronta,Sai da takai ƙarshen maganarta sannan yace"the number you're trying to call is switch off,pls try again Later"yana kai ƙarshen maganar,yayi rejecting kiran yana dariya,ko kaɗan baiji tausayin kukanta ba,Don tafita aranshi kwata kwata,Yayi mamakin jin wai tana a Enugu ko ubanme yakaita enugu?ta6e le6enshi yayi tare da faɗin"I don't care Allah ya raka taki gona,nasamu na rabu da jangwamgwam,"   Ƙarar shigowar message yaji,da sauri ya duba screen din wayar ya soma karanta saƙon   _Ishaq ka taimaka ka ceci rayuwata,wlh ina cikin masifa,naga tashin hankalin da banta6a gani ba Ishaq,wayar ma aronta nayi a hannun wani inyamuri,kayi taimakon musulunci ishaq karka duba halina,dan Allah zakayi,ataimaka a dauko ni daga Enugu ko maiduguri ne a mayar dani in mutu acan_   Guntun tsoki ishaq yaja,tare da yin deleting ɗin saƙon,a karshe ma blacklist ya tura number,yadda ko an kira baza a same shi,"   Murmushi ya saki lokacin daya tuna da hajjaju,macen da yake burin aure,duk da taƙi amince mashi amma kullum saita kirashi ta tambayi lafiyarshi,Wannan ya tabbatar mashi da cewar tana sonshi,tunda ta damu dashi,sannu a hankali Zai samu yayi Wuff da ita ya kawota Cikin gidan shi, *Boss Bature* Yinin Ranar Sehrish da Ciwon kai Tayi shi saboda tsabar tunane tunanen da take yi,ta kasa tsaye ta kasa zaune,Har magani tasha amma kan yaƙi lafawa kamar ana kunna wuta acikin ƙoƙan kan nata,abun ya ɗaure mata kai yadda Azmee ta share zancen bata Labarinta,Har lokaci suka samu amma bata tada zancen ba,kuma ko tayi yunƙurin zata tuna mata sai tayi saurin Canza zancen,hakan ne yasa Sehrish ta fara accusing ɗinta,Ta sanya mata ido sosai duk wani motsinta akan idanuwan sehrish take yinsu, Wuraren ƙarfe 9;30 na dare,gidan yayi tsit da alama wasu daga cikinsu sunyi bacci,Oummansu kaɗai ta rage a ɗakinsu,Zaune saman sallaya tana tasbihi,Yayin da su sehrish ke kwance saman gadon,hosana da jahad sunyi Bacci banda Sehrish wadda idonta biyu,ta kasa runtsawa,jira take yi Oummansu ta kammala Sallar ta dawo saman gadon ita kuma ta koma ɗakin Azmee, Tana cikin Jan cazbahar nan wani abu ya faɗo mata aranta,abunda ta jima tana ƙoƙarin tunanawa,a hanzarce ta miƙe jiki na rawa ta tunkari gefen da sehrish take kwance saman gadon,Hannu tasa tana ɗan bubbuga kafaɗarta"Rishi!rishi!ko kinyi bacci ne,"yatsina fuskarta ta ɗan yi daƙyar ta iya huɗe idanuwanta,   "Tambayar da kika yi mun game da wannan Auntyn taku Azmee,Na tuna inda nasanta.."tunkan takai ƙarshen Maganar,jiki na rawa Sehrish ta tashi daga zaune tana kallonta"Oumma a ina kika Santa?   "Zan faɗa maki Sehrish amma fa karki kuskura ki sanar da ita cewa nasanta,tunda bansan da wata manufa take zaune acikin gidan nan ba,"   "Bazam faɗamata ba Oumma" Jinjina kai abu ta ɗanyi"Wannan matar da kike gani,Lokacin da na haifeku babu wanda yazo yi mun wankan jego,Sai daga baya Ya sayyadi yazo da ita amatsayin ƴar uwarshi da zata yi mun wankan jego...."   Jin wannan maganar yasa hankalin Sehrish yayi mugun tashi,Saboda tsabar kiɗima gaba ɗaya idanuwanta suka firfito waje,Hannu tasa ta daki ƙirjinta"Ƴar uwar Ya sayyadi!"ta ambaci hakan a tsorace   Abu ta lura da Yanayin da Sehrish ta shiga,bata dakata da yin maganar ba taci gaba da cewa"Wlh Sehrish matarcan da kike gani,Ba ƙaramar shu'uma bace!abun tsoroce ita,Dalilin dayasa nace maki haka,Lokacin da sayyadi yazo mun da ita don tayi mun wankan jego,Kamar kurma haka ta koma,duk in naso na bugi cikinta don ta sanar dani wani abu game da danginsu,Sae taƙi tanka mun,Nasan dai ta bani kyakkyawar kulawa a lokacin amma gaskiya ba abun yarda bace,saboda nayi mamaki dana ganta acikin gidan nan,Kuma sai surutu take yi kamar ba ita ba,Sa6anin a yadda nasanta lokacin da tazo gidanmu ko uffan bata cewa,daga um sai um um shine abunda ke fitowa daga bakinta," Hannu sehrish tasa tare da dafe kanta dake jujjuya mata,a hankali tashiga furta"Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un!Amma Azmee ta gama damu!indai abunda nake zargi ya tabbata to tabbas Azmee Itace Ƴar leƙen asirinsu dake fitar da surrukan gidan nan......" Cike da mamaki abu ke sauraron kalamanta sae da takai ƙarshen maganarta Sannan tace"Meyasa kika ce haka?Dama kina zarginta ne?Amma naga kamar kuna zaman lafiya da ita,' Hawaye na kwaranyowa akan furkarta ta shiga faɗin"Oumma,muna cikin tashin hankali in har ya kasance AZMEE itace take shirya maƙarƙashiya acikin gidan nan...."dafa kafadarta abu tayi"ki sanar dani abunda yasa kike zarginta inaso inji,ko Zan iya taimaka maku"   Duk da tana cikin mawuyacin hali na firgici,haka ta zauna ta kwashe dukkan abunda ke wakana acikin gidan ta sanarwa Oummansu,abun mamaki tana kai ƙarshen maganar sai taga Abu na murmushi gami da girgiza kanta,   "Oumma ko kin gano wani abu akanta ne?naga kina murmushi,"   "Akwai wani abu da nakeso na sanar dake sehrish!Shi ɗan adam ba abun yadda bane,Bakomai zaisa kiyi kokwanto akan azmee ba fa ce Yardar da kukayi da ita,Ta ko'ina azmee ta gama daku,Ta siye zuciyoyinku ta hanyar kyautatawar da take yi maku,Shi mutun maison ɗaukar fansa,Zai iya yin 6adda kama ya shiga jikin maƙiyansa har na tsawon shekaru Yana yi masu bauta batare da gajiyawa ba,yayin da yake shirya masu maƙarkashiya batare da sun ankare ba,Har sai ranar da ya tarwatsa su gaba daya tukunna zai bayyana kanshi,Yanzu kinga gaba ɗaya ta gama sanin surrukanku......"dakatawa abu tayi da yin maganar,Ta jinjinawa azmee sosai,ta iya shirya tuggu   "Gaskiya sehrish dole kiyi taka tsantsan,don wlh in har ya kasance zargin da muke yi ya zama gaskiya,To fa Azmee ba ƙaramar shu'uma bace,Kuma zata iya kashe duk wanda yayi gigin tona mata asiri,a yadda ta faro shirinta tsawon lokaci yanzu bazata bari wani Ya fallasa ta ba,"   "Amma Oumma,nibansan ya zanyi ba,abubuwa sunyi mun yawa akaina,"tayi maganar damuwa ƙarara a kan fuskarta,   Dafa kafaɗarta abu tayi"Ni dai shawarar da zan baki shi ne,Ki samu wani babba ki sanar dashi komai dangane da ita....."   A ruɗe sehrish tace"Wazai yarda dani Oumma!idan har na faɗi cewa Azmee ƴar uwar sayyadi ce,kuma ina zarginta da mutuwar Junaid"   "Tabbas kuwa babu wanda zai yarda dake a halin yanzu,a ƙarshe ma reshe zai iya juyewa da mujiya,Zata iya ɗaura maki laifin kinsan fa shi mugun mutun hatsari ne shi,balle su da suke da tsafi,duk da dai mu mun dogara da Allah ne,babu ja da baya Allah shi zai bamu kariya,"   "Yanzu ya zanyi!inaso naci gaba da bincike akanta,Saboda inaso na tambayeta dangane da zoben Junaid dake a wurinta me yakai shi cikin kayanta,"   "Nace maki karki kuskura ki ce zaki nuna cewa kinsan wani abu game da ita,in ba haka ba zatayi maki mummunar illane,Nidai shawarar da zan baki A yanzu ki damƙa binciken nan a hannun ɗaya daga cikin mutanen gidan nan,Zaifi ma ki sanar da Daddynku,Zan ma yi mashi magana,nasan zai yarda dani sosai' Shikenan Oumma,Yanzu zan iya zuwa ɗakinta in kwanta"?   "Me zai hana amma dai ina ƙara jan kunnanki akanta,karki kuskura ki tsananta bincike akanta,Don zata ganoki ne,"gyaɗa kai Sehrish tayi tare da saukowa daga saman gadon ta nufi hanyar fita daga ɗakin,ruƙo handle ɗin ƙopar tayi,bayan ta fita taja ƙopar ta rufe,gyara kwanciya Oummansu tayi saman gadon,ita kanta abun ya razanar da ita,Ta yadda akai har ƴar uwar sayyadi ke aiki acikin gidan,daƙyar bacci yayi awon gaba da ita, Tafiya sehrish takeyi kamar wadda aka zarewa lakar jikinta,komai ya tsaya mata Cak,don abun ya girmi tunaninta,a ƙopar ɗakin Azmee ta tsaya gabanta na faɗuwa a hankali ta furta"La'ila ha illa anta subhaka inni kuntu minazzalimin,tana kai ƙarshen addu'ar ta tura ƙopar ta shiga daga ciki,abun mamaki bata samu kowa ba acikin ɗakin,Ranta ne ya bata cewar kodai ta shiga toilet ne, A wauta irin na Sehrish,maimakon tabi abunda Oummansu ta sanar da ita,Sai ta soma tunanin Yin bincike acikin ɗakin don a qagare take da ta gano gaskiyar wacece AZMEE, Agaban bedside drawer ɗinta ta zuƙunna jikinta na kerma,ta shiga bubbuɗe drawer chest ɗin,Yawanci duk tarkace ne na magunguna sai ƴan ƙulle ƙulle kamar na maganin Zafi,gida na ƙarshe ta bincika anan ne taga abun daya ɗaure mata kai,Ƙura ido tayi tana kallon Galleliyar wayar dake ajiye a wurin,Ƙirar i phone 13pro Batasan lokacin da ta furta"Ya Allah!dama Aunty Azmee tana da waya?Amma meyasa ban ta6a ganin wayarta a hannunta ba,"ta ƙarasa maganar tare da zura hannunta ta ɗauki wayar,ta kunna power ɗinta,Nan take haske ya kawo,Gabanta ne ya faɗi Ganin Hoton dake ajikin Wallpaper ɗinta,bakowa bane face Fuskar HAROON,da ƴar ƙuruciyarshi,nan fa tashiga ruɗanin abun al'ajabin da take gani,Menene Alaƙarta da haroon da har ta ɗaura hotonshi a fuskar wayarta?dama ta jima tana zargin haroon ba mutumin kirki bane,kodai hadashi atare suke shirya maƙarƙashiyarsune? Tana cikin wannan wasi wasin,kira ya shigo cikin wayar da baƙuwar lamba,kwata kwata babu sautin ringing an sanya wayar silent,Yadda ko an kira baza'aji ƙararta ba, Sehrish da karanbani sai ta ɗaga kiran tare da kara wayar a kunnanta, Shiru tayi tana jiran jin wanene zaiyi Magana, Cikin harshen fulatanci taji ana magana,gashi ita bata iya yaren ba,Tunani ta shiga yi dama azmee bafullatana ce?dama ta ta6a ganin Zanen kalangu a gefen fuskarta,   Tana cikin wannan zancen zucin tajiyo takun tafiyar mutun yana tunkaro ɗakin,Ba shakka Azmee ce,A tsananin tsorace Sehrish ta katse kiran,gashi wayar akwai password,babu yarda za'ae ta goge kiran da akayin,dole idan aka shiga Call log agane cewa An ɗaga kiran da akayi, A matukar firgice Sehrish ta tura wayar acikin drawer ɗin,Duk tabi ta ruɗe ta rasa inda zata dosa,A ƙarshe ta faɗa toilet ta rufe,tana faman sauke ajiyar zuciya,jijiyoyin wuyanta duk sun fito saboda tsabar tsoro,Tayi danasanin ɗaga kiran wayar Azmee da tayi, A hankali Azmee ta turo ƙopar ɗakin ta shigo,Jikinta sanye da baƙaƙen kaya,Jallabiya ce tare da mayafinta,kamar wadda taje anguwa,zama tayi daga gefen gadon,tare da kai Hannu jikin drawer ɗin ta ɗauko wayarta,dannata ta shiga yi,kafin ta danna call, Sehrish dake la6e acikin toilet ɗin da alama mutumin da ya kira Sehrish ta ɗaga shi Azmee ta kira,Addu'a sehrish tashiga yi hannunta na kerma ido ya raina fata,tuni zufa ta wanke mata fuskarta,Ga fitsari daya matse,ta kasa tsugunnawa tayi futsarin gudun kada azmee taji ƙarar fitarshi,   Ba ƙaramin haushi Sehrish taji ba lokacin da Azmee ta soma Magana Cikin harshen fulatanci,taso ace da yaren hausa tayi maganar don ta samu taji abunda zata ce,yanzu ta ƙara ƙarfafa zarginta akan Azmee, *Boss Bature* Around 10pm Jami'an da Sgr ya sanya su tsare grave ɗin Junaid,sunyi 6adda kama yadda kasan ba Sojoji ba,kowannansu na sanye da Kaya namu na hausawa,riga da wando na yadi,ɗaya daga cikinsu yana zaune saman dogon benci yayin da ɗayan ke zuƙunne agaban bencin gefenshi kayan Shoe shiner ne,Yana goge ma na saman bencin Takalminshi,dayake akwai hasken street light,Bakomai suke jira ba fa ce wannan mai zuwa yana yin zarya a ƙabarin nasa,bisa Command ɗin da Sgr ya basu nasu sanya ido akanshi idan ya ƙaraso,Su sanar dashi yana so yaga ko wanene,Suna zaman jiran zuwanshi,Aikuwa cikin sa'a ƙarfe goma na bugawa,kamar yadda ya saba zuwa,Sai motar nan ƙirar Venza ta shararo da gudu izuwa titin,tunkan ya ƙaraso ɗaya daga cikin sojojin wanda ke zaune saman Bencin yace"Gashi nan!yakamata mu sanar da Sgr,tun kafin ya kufce mana"   Wanda ke goge mashi takalmin yace"sai munyi taka tsantsan if not zai gudu ne," Koda ya ƙaraso wurin ƙabarin slowly yayi parking ɗin Motar a gefen titin batare daya fito ba, A hankali Sergeant ɗinnan dake zaune saman bencin ya ɗauko wayarshi tamkar yana dannata,message ya turawa Sgr,bayan ya kammala tura saƙon Ya mayar da wayar cikin trouser ɗinshi, Buɗe murfin motar yayi tare da saukowa daga cikinta,kamar yadda ya saba zuwa haka yau ma yazo,Ya sanya face mask a fuskarshi yayin da idanuwanshi ke sanye da glass baƙi,Jikinshi na sanye da Crazy jeans tare da T-Shirt purple,tafiya ya soma yi har izuwa gefen bishiyar nan inda aka kewaye ƙabarin Junaid,tsayawa yayi kamar mai neman wani abu,hada ruƙe qugu,kusan minti 5 kafin ya soma zagaye bishiyar yana jinjina kanshi, Miƙewa ɗaya daga cikin Sojojin nan yayi,A hankali ya nufe shi batare daya ankara ba,koda matashin nan Ya lura da cewa wani na tunkaroshi,Aikuwa da gudun gaske yabar wurin bishiyar,Sojojin nan suka bishi a guje,duk yabi ya rude ko motarshi bai tsaya ɗauka ba,a rikice ya faɗa saman titin yana gudun ceton rai kamar zai tashi sama,da gudu suma suka bi bayanshi don karya kufce masu,yana gudu yana waiwayen bayanshi,Unfortunately Yana ƙoƙarin karya kwana,Adai dai Lokacin Motarsu Sgr ta shawo kwanar,Kwatsam ya faɗama motarsu ta bugeshi sosai,ya saki wata irin razananniyar ƙara tare da zamewa ya faɗi wanwar ƙasa,Ƙarasowa Sojojin suka yi suna faman sauke ajiyar zuciya,Ta kwana gidan sauƙi, Fitowa Sgr yayi daga cikin motar,Armstrong ma ya fito,Atare sojojin suka sara mashi,Kafin ɗaya daga cikinsu ya nuna saurayin dake a kwance ƙasa yana bullayi"Sir,Wannan shi ne wannan matashin dake zarya a ƙabarin ƙaninka,rashin gaskiya yasa yana ganinmu ya zabura zai gudu", Zuba mashi ido Sgr yayi yana bin shi da kallon ƙurulla,tun kafin ma Ya cire mashi face mask ɗin fuskarshi,Ya shaida shi,zuƙunnawa yayi saman guiwarshi ɗaya,tare da kai hannu Ya zame face mask ɗin saurayin tare da cire glass ɗin fuskarshi Yayi throwing dinshi saman titin,runtse idanuwanshi yayi jikinshi sae kerma yake yi, A hankali Ya furta sunanshi"HAROON" kamar bashi ba,Ya rame,yayi baƙi,jin muryar Sgr yasa haroon ware manyan idanuwanshi masu kama dana mujiya,koda yayi tozali Da Sgr a hargitse Ya tashi daga zaune yana kallonshi yayin da yake faman zazzare ido,wata irin zufa ce ta soma tsastsafo mashi agefen fuskarshi,.    "Dama kaine"?cike da mamaki Sgr yayi tambayar,   Shiru Haroon yayi bai tanka mashi ba,   "Me kake yi a wurin grave ɗin Junaid"   Daƙyar ya iya furta"ƙabarin junaid kuma?yayi maganar tamkar baisan akan me suke magana ba,   ɗagowa Sgr yayi tare da kallon sojojin dake tsaye suna ta faman haki"Zaku iya komawa bakin aikinku,"juyawa su kayi da sauri suka bar wurin,   "U will explain it don ubanka,I have been suspecting you for a while,Zuba maka ido nayi kawai inga ƙarshen gudun ruwanka,abunda ka aikata ne yasa ka gaza samun natsuwa acikin ranka That's why kazo kana zarya akan ƙabarinsa"? Waro ido haroon yayi amatuƙar tsorace Yayi yunƙurin miƙewa ya gudu,damƙar ƙafarshi Sgr yayi hakan yasa ya gaza motsawa,   "Amstrong,ɗaukarmun shi ka sanyamun shi acikin mota," Gadan gadan Amstrong ya tunkareshi,Yadda kasan ƙaramin Yaro haka ya ca6eshi asaman kafaɗarshi,Ya turashi cikin motar Sgr,Front seat suka shiga,Sgr da Amstrong Tada Motar yayi da gudun gaske ya fisgeta, "Wai ina zaku kaini ne?Motata fa?kun barta a wurin"shiru su kayi mashi babu wanda ya tanka mashi,   "Wlh kada kuce zaku ta6ani,Rafayet ku sauke ni in kama gabana!Ni bansan akan me kuke magana ba"Sai faman sambatu yake yi,zufa duk ta wanke jikinshi"   Har Lokacin basu tanka mashi ba,ƙoƙarin buɗe motar yayi donya buɗe,amma yaji ƙopar adatse ta ko'ina babu hanyar da zai gudu, Da gudun gaske motarsu ta shigo cikin gidan A lokacin Sehrish na la6e cikin toilet ɗin Azmee,Har cikin kunnanta tajiyo sautin Shigowar Motar Sgr,kamar ta fasa ihu haka take ji ga Azmee taƙi yin bacci bare ta lalla6a ta gudu,Sae dannar wayarta take yi,Yadda kasan tasan da zaman wani acikin ɗakin, Window ta hango acikin toilet ɗin,Da gudu ta nufe ta,so take ta leƙa window ɗin don taga idan shi ne ya dawo dagaske,net ne ajikin tagar,kuma tagar tayi nesa,Tsawon sehrish bazai kai ta leƙa tagar ba,Lalla6awa tayi cikin sanɗa ta ɗauko bokiti,Ta kifa shi ajikin bangon,Sannan ta daddage ta haye saman bokitin cike da tsoran karya fashe bokitin, Ƙura idanuwanta tayi tana leƙan wajen gidan daƙyar take hangen wurin da motar Sgr take,fitowa yayi daga cikin motar tare da zagayawa ya Shaƙo wuyan rigar haroon ya wurgo shi waje,gaba ɗaya ya kife ƙasa a susuce,Gabanta ne ya faɗi rass!lokacin da taga Ya damƙo rigar haroon,Tabbas ranta na bata cewar Sun kamoshi ne a matsayin me laifi!tsoranta kada Sgr yayi kuskuren raunata shi,wata'ƙil Sunji kalamanshi ne dayake cewa zai kashe Farin cikin mutanen gidan Shiyasa suke tuhumarshi,kamar ta bur6a tagar ta fito haka take ji, Ɗaukarshi Sgr yayi asaman kafadarshi Ya wuce dashi cikin gidan Amstrong na biye da bayanshi,ɗakin horon nan nasu Ya shiga tare dashi,ɗakinda idan aka rufe ƙoparshi ko ihun mutun ba'aji, Sauke shi yayi yana tangal tangal Zai faɗi ƙasa,Nuna mashi ɗaya daga cikin kujeru biyu dake kallon juna yace"Ave a seat,magana nakeso nayi dakai,"   "Nifa bansan komai ba!meyasa ka shigo dani wurin nan"? Wani irin kallo da Sgr ya wurga mashi yasa shi lalla6awa ya zauna,jikinshi nata kerma,kai cike da iskanci ga shegen tsoro Zama Sgr yayi suna fuskantar juna yayin da Amstrong ke atsaye yana kallonsu,   Sai faman mazurai haroon keyi,irin na marasa gaskiyar nan,   "Meyasa ka aikata hakan"?girgixa kai ya shiga"Ni wlh ban aikata komai ba,Nifa bansan komai ba,bansan akan me kake magana ba"   Tsabar takaici ne yasa sgr ware yatsunshi Biyar ya kwasa mashi mari asaman fuskarshi,nan take le6enshi ya fashe,hannu yasa ya dafe kuncinshi saboda zafin daya ji, "Ka faɗamun meyasa ka kashe junaid"?     "Rafayet ba zaka ta6a jin komai ba,a abakina"Duk da halin da yake ciki hakan baihana shi gaya magana ba, ..rai amatuƙar 6ace,Sgr Ya damƙi kwalar rigashi da iya ƙarfinshi na ƙarshe ya daddaɗao da haroon a zafafe ya tunkari faskeken Madubin dake a aɗakin,Gaba ɗaya ya rotsa kanshi acikin glass ɗin,Wata irin gigitacciyar ƙara Haroon ya fasa yana fadin"Nashiga uku!Rafayet ka kashe ni!Na bani Na Lalace!!!.."kafin Haroon yayi wani yunƙurin kwace kanshi tuni Sgr ya ƙara Tarwatsa kanshi Acikin glass ɗin madubin,Nan take jini Ya soma tsastsafowa Asaman kanshi,Ya hada mashi Jini da Majina,Fitsari ya saki a wando ya shiga zubowa Zirrrrr yana kawarara Yaji bala'e,   Naushin cikinshi sgr ya shiga yi gaba ɗaya,Duk In ya naushe shi sai Jini ya fito ta bakinshi,Ganin yana ƙoƙarin kashe shi yasa Amstrong Yin saurin dakatar dashi Ta hanyar ruƙo damtsen hannunshi"Allah ya huci zuci zuciyarka,Bai kamata ya mutu a yanzu ba,Still bamu samu bayanan da muke son samu a wurinshi ba," Ranshi amatuƙar 6ace yake magana"Kabarni in kashe wannan mugun mutumin Mara imani da tausayi!In har ban kashe shi ba,bazan samu kwanciyar hankali ba,Bazan cigaba da jure ganinshi yana yawo araye ba,   Haroon dai tuni ya fita hayyacinshi sai faman ambaton Innallahi wa'inna ilaihirraji'un yake yi acikin bakinsa kamar wani musulmin ƙwarai,Jini duk ya wanke mashi fuskarsh,   Daƙyar Amstrong ya samu ya shawo kanshi,Ya haƙura da zancen kashe haroon,Zuƙunnawa yayi agabanshi Yana kallonshi,Idanuwanshi tuni sun jima da juyewa,Yayi bleeding sosai,   "Sir!ya rasa jini sosai,Yakamata Abashi Emergency treatment,don ya dawo cikin Hayyacinshi,idan yaso sai mu tuhu me shi daga Baya,    Hannu Sgr yasa tare da kinkimar haroon ya wuce dashi medical Room ɗinsu,Ba don yaso ba haka ya shiga duba shi,Uban bandage ne akan goshinshi,duk ya cire mashi pieces na gilashin daya Sossoke shi,biji biji yake kallonsu Zama daga gefen gadon Sgr yayi,yana kallonshi cike da jin tsanarshi acikin zuciyarshi,   "Najima Ina samaka ido haroon,ban ta6a ɗaukar mataki akanka ba,saboda ina zargin cewa Ba yin kanka bane,Akwai wanda ke take maka baya kana aikata hakan!   "Nazo nigeria ne saboda in ƙarfafa bincikena akanka,kafin na yanke maka hukunci,Na sanya maka ido sosai duk wani motsinka acikin garin nan ko ince acikin ƙasar nan a idona kake yinshi!!" Haroon dai sai binshi da idanuwayake yi,sunyi jawur dasu ga raɗaɗin ciwon da yake ji,ga wani nishi da yake saki don ba ƙaramin jiki yaji ba,   "Tun lokacin da ka sanyawa yarinyar can ido,Ka takura mata akan cewa ta amince ka kusanceta ko kuma Ka tona mata Asiri,Anyi haka ko ba'ayi ba"   Waro ido waje haroon yayi Yana kallonshi,hankalinshi a matuƙar tashe,   Cigaba da magana Sgr yayi"A kwai ranar dana sanya ta kawo mun injection inyiwa kaina,Saboda bata iya karanta hand writting ɗina,Sai kayi mata wayau da nufin zaka taimaketa,Shi ne ka bata allurar Maye ta kawomun,bisa rashin sani har nayiwa kaina"!   Wani irin wahalallan Yawu haroon ya haɗiya,abun yayi mugu mugun ɗauke Mashi kai!Taya akai duk yasan da wannan?mutun sai kace Aljani   Cigaba da magana sgr yayi"Bayan wannan,Kayi masu Twins barazana akan su baka 80million ko ka fallasa porn video wanda ka ɗauka a hotel room ɗinsu yayin da suke aikata Homo!Anyi haka ko ba'ayi ba'?   Tashin Hankali,kasa buɗe baki Haroon yayi sai faman wurga idanuwa yake yi,   "Kullum kalamanka sune zaka kashe farin cikin gidan na,kayi niyar kashe junaid sai kuma ka fasa saboda ƙaunar da yake nuna maka,Har so kayi ka shiga Jikinshi donka cutar dashi Amma ka gaza yin hakan saboda sonshi da kakeyi,Daga baya kuma Sai wani abu ya faru tsakaninka da Marshal Omar sakamakon marin da kayiwa Reesh,Shi da Uncle suka kwasa maka mari a lokaci ɗaya,bayan haka kuma Omar yayi maka bugun tsiya,wannan yasa ka dawo da wannan mummunan ƙudirin naka na son kashe Junaid....."tunkan yakai ƙarshen maganar Haroon daya gama razana yace"Duk ya akai kasan da wannan?kuma meyasa tun lokacin baka hukuntani ba?bayan kasancewa Ni maƙiyinku,Na tsaneku bana son farin cikinku,banda burin daya wuce inga na tarwatsa farin Cikinku,Kuma nayi nasara akanku tunda har na Kashe junaid,Ko yau nafaɗi na mutu na gama daku, A fusace Amstrong ya zabura zai ɗauke shi daga saman gadon don ya rugurguzashi dasauri Sgr ya dakatar dashi"Ka barni dashi,Na ishe shi,"   "Bansan wanene yake tunzuraka ba haroon,Amma inaji araina cewa Sanyaka akeyi kana yi,Laifin me muka aikata maka?da har muka cancanci hakan a wurinka?me junaid ya aikata maka da har kayi silar mutuwarshi?duk irin halarcin da akayi maka acikin gidan karasa dame zaka saka mana sai wannan?Da wani ido kake tunanin Abbanmu zai kalleka?Ya ta6a banbantamu dakai ne"?   "Banbanci kuma na yaushe?babu mai sona acikin gidan nan,ba ku damu dani ba,bakusan halin da nake ciki ba,kowa kuna nuna mashi so da ƙauna acikin gidan nan,Ni kaɗaine kuka ware kamar wani bare,"yana magana yana kuka   "Nikaina bada son raina nayi silar mutuwar junaid ba,ɗacin raɗaɗin ƙuncin da kuke cusa munne yasa har nasa aka bi takanshi da mota,Yanzu bana jin tsoran kowa yaji cewa Na kashe junaid,Saboda nima so nake na mutu,tun ranar dana kashe Junaid na gaza samun kwanciyar hankali,duk wani mugun abu da nake aikatawa na daina duk don saboda shi,haƙƙinshi kaɗai ma bazai barni inyi rayuwa cikin salama ba,Duk ni najawa kaina wannan masifar da nake ciki........"sosai ya fashe da matsanancin kuka,gaba daya basu yarda da kalamanshi ba,Yana yin magana tamkar wanda yayi danasani,   "Ka fadamun wanene yake baka Command kana aikata hakan?idan har ka faɗamun zan ƙyaleka kayi tafiyarka,"   Girgiza kai Haroon ya shiga yi yayin da hawaye ke kwaranyowa daga cikin idanuwanshi"Wlh bazan iya faɗa maka ba!bazan iyaba,da ace zan iya dana fada maka,Amma bazan iya ba,"   Jinjina kai Sgr yayi tare da miƙewa tsaye yana kallonshi"its okey,tunda baza ka faɗamun ba,Amstrong ɗaukarshi ka mayar dashi ɗakin horon nan,".    Fashewa haroon yayi da matsanancin kukan Yana ƙoƙarin dakatar da Amstrong akan karya ɗaukeshi,abun ba ƙaramin ɗaure masu kai Yayi ba,   "Leave him,"Ya ambaci hakan tare da dakatar da amstrong daga ɗaukarshi,"   Allura Sgr ya ɗauko,Aikuwa a firgice haroon ya shiga girgiza mashi Kai yana fadin"kada ka kashe ni dan Allah,kabarni da raina,inason Na nemi yafiya a wurin Abba kafin nabar duniya...."   "Kasan daɗin ranka meyasa shi junaid ka kashe shi baka bari ya gana da iyayenshi ba?Haroon Rayuwarka bata da amfani"Turmushe shi Amstrong yayi,Sgr ya Caka mashi allurar a wuyanshi,lokaci guda jikinshi ya saki gaba ɗaya,Lokaci guda idanuwanshi suka kakkafe,daga bisani ya sanƙare babu numfashi, Tashin Hankali!Haroon Zai rayu Koya mutu?Ya sehrish ƙare acikin toilet ɗin Azmee ga futsari ya matse ta,Junaid Yana raye Koya Mutu?Am confused *Ga duk maison Abban sojoji ya tuntu6i Layina whatsapp message kawai banda call 08103884440* 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋 𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤ 𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠 *🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥* Not edited .Anan suka barshi saman gadon batare da sun kawar dashi ba, Har zasu fita daga ɗakin sgr ya kalli Amstrong"Wayarshi nakeso ka ɗauko mun,Nasan dole akwai wasu mahimman bayanai da yake ajiyewa acikinta," Juyawa Amstrong yayi tare da nufar Haroon dake kwance magashiyan saman gadon,Hannu yasa cikin aljihun wandonshi Ya lalubo wayarshi tare da key ɗin Motarshi,dawowa yayi ya mika mashi su duka,hannu Yasa ya kar6esu daga hannun Amstrong, Bayan sun fito daga ɗakin,Sgr Yayi Locking ɗin ƙopar,Sallama su kayi da Amstrong ya wuce upstairs part ɗinshi, Gaba ɗaya ƙyanƙyamin jikinshi ya ke ji,blood ɗin Haroon daya fallasar mashi duk ya 6ata Shirt ɗin jikinshi,quickly yake taka staircases ɗin harya haura Sama,Lokacin daya ƙarasa Cikin Falonshi,yayi expecting ɗin zai sameta aciki,yaji daɗin ganin yadda ta gyara ko'ina gwanin ban sha'awa,kullum furniture ɗin ɗakin kamar sabbi suke komawa duk in suka sha gyara, A hanzarce ya wuce cikin bedroom ɗinshi, Ya zancen sehrish da take ƙumshe cikin toilet ɗin Azmee,Ta shiga matsanancin tashin hankali,ba laifi bane idan ta shiga toilet ɗin Azmee,matsalar da aka samu shine Wayar da tayi picking,in Azmee ta ganta zata gane cewa itace ta ɗaukar mata waya, Jiki na rawa ta sauko daga saman bucket ɗin,Tasa hannu ta ɗago shi cikin sanɗa ta mayar dashi inda ta ɗauko shi,komawa tayi bakin ƙopar toilet ɗin ta tsaya,Duk tabi ta tsorata,fitsarin da take ta faman matsewa ne ya kufce mata nan take ya shiga fitowa Ziiir ta tsakankanin cinyoyinta,Runtse idanuwanta tayi sosai Cikin zuciyarta tana ambaton"Allahumma Ajirni filmasibati aklifni khairan minha' Tana cikin wannan yanayin Kwatsam Ba zato ba tsammani tajiyo Muryar Azmee daga cikin ɗakin tana cewa"Sehrish idan kin gama la6e la6en naki,ki fito kizo ki kwanta dare nayi,"   Gabanta ne taji yayi wani irin mugun bugu,Zuciyarta tamkar zata 6allo daga ƙirjinta,Idanuwanta sun Zazzaro waje kamar ƙwayar idon zata faɗo ƙasa   Jin tayi shiru yasa Azmee ta ƙara ɗaga muryarta"ke fa nake Jira!" Wani irin wahalallan Yawu ta haɗiya abakinta,Tashin Sense,kenan duk wannan la6e la6n da take yi Azmee tasan da zamanta acikin Toilet ɗinta How that Can be possible?Bayan batasan Lokacin da ta shiga cikinshi ba,Wannan ya ƙara firgitar da ita,   "Ko saina Shigo cikin toilet ɗin nan"?   Muryarta na kerma tace"A'a gani nan zuwa,"   Tayi maganar tare da nufar tap ta kunna ruwa ya shiga kwararowa,Ɗebo ruwan tayi ta yayyafa shi a jikinta sosai Ta wanke fitsarin,' Gabanta na faɗuwa ta nufo ƙopar,Yatsun hanunta na kerma ta buɗe ƙopar ta fito, A bakin ƙopar toilet ɗin ta tsaya,kamar an dasa mata Aya,Idanuwanta na kallon ƙasa, Juyowa Azmee tayi tare da kallonta,Sam babu wani sauyi akan fuskarta,Sai ma cewa tayi"Ya akai naga wandon jikinki a jiƙe"?   La66anta na rawa tace"Fitsari ne ya matse ni,ina ƙoƙarin nayi shi ne ya zubo mun,Amma na wanke shi,"   "Eyya,duk kin bi kin jiƙa jikinki,Sanyi zai iya kamaki,bari na ɗauko maki kaya ki sanya,"   Da sauri Sehrish ta dakatar da ita"A'a aunty Azmee,Zan koma ɗakin mu ne," "Why"?tayi tambayar da ɗan mamaki akan fuskarta,   "Ba'anan kike kwana ba"? "Eh,Zan dawo akwai abunda zanyi acan"tana magana jikinta na kerma,   Gyaɗa kai Azmee tayi"its Okey,Sai kin dawo,".   Da sauri da sauri sehrish ta lalla6a ta nufi ƙopar fita daga ɗakin Harta ruƙo handle ɗin ƙopar zata buɗe,muryar azmee da katse mata hanzarinta"Take care of ur self"shi ne abunda taji tace mata,Ai ko waiwayonta bata yi ba,gudu gudu sauri sauri ta fito daga ɗakin Azmee,A haukace Ta faɗa bedroom ɗinsu,tana shiga ta fara jin ƙaiƙayi ajikinta,Hannu tasa tana sosa wuyanta,Abu kamar wasa bayanta ya ɗauka,cinyoyinta duk suka ɗauka ko'ina na jikinta,da gudun gaske ta faɗa cikin toilet,After some minutes ta fito ɗaure da towel,Ƙaiƙayin ya rage amma akwaishi kamar lafawa yayi,wadrobe taje ta buɗe tare da ɗauko Ƴar rigar bacci shara shara rigar haka take,Zura ta tayi ajikinta,har lokacin tana sosa jikinta,Burinta taje part ɗin Sgr don tasan Zai jirane ta kawo mashi coffee,turaren nan nata ta fesa ko mai bata tsaya shafawa,duk jikinta ba daɗi, Slipper ta zura a kafarta,quickly ta nufi ƙopar ɗakin ta buɗe,Ta yafa mayafi akanta,Kitchen ta shiga shaf shaf within mins ta fito hannunta ɗauke da Cup of coffeee hada Fuits ta haɗo mashi,Don ya jima bai shasu ba, Gadan gadan ta nufi cikin babban falon,tun tana tafiya ta soma jin wani irin kuka kuka Kamar na namun dawa,hakanan ta dake don bata kawo aranta ba,lokacin da ta ƙarasa Part ɗinshi,ta shiga falon da sallama bata same shi aciki ba,Bedroom dinshi ta shiga,Tana aza ƙafarta karaf idanuwanta suka sauka Akan Sgr wanda ke zaune Tsakiyar gadon jikinshi sanye da Sleeping dress ɗinshi,Yana daddana Laptop ɗinshi gaba daya ya mayar da hankalinshi akanta,gabanta ne ya faɗi Rass Lokacin da idanuwata suka fara nuna mata danƙara danƙaran kunamai A kewaye dashi suna ƙoƙarin Harbinshi, Waro ido tayi waje tare da Sakin tray din dake hannunta,Ta fasa wata irin razananniyar ƙara wadda ta firgitar dashi,A hanzarce ya ɗago yana kallonta,Ta toshe kunnuwanta jikinta sae kerma yake yi,A ruɗe ta dinga nuna shimfiɗarshi tana fadin"Ya Rafayet Majici!kunama!zasu ɗalle ka gasu nan gasu nan Ya rafayet ka tashi....."Gaba daya gizan tsoranta sun tashi,To Fa, Abun yayi matuƙar ɗaure mashi,Shi dai baiga komai ba,A wurinda yake zaune,Janye laptop ɗin yayi saman mattress ɗin,Gently ya sauko daga saman gadon ya tunkareta,Fashewa ta sake yi da uwar ƙara kamar maƙoshinta zai 6allo waje,Macijan nan ta gani tare da kunaman sun sauko daga saman gadon sun biyo Sgr suna ƙoƙarin sarin Kafarshi,   Muryarta na kerma ta shiga fadin"Ka janye ƙafarka ya rafayet!gasu nan wlh gasu nan wurin ƙafarka zasu sare ka,Zasu cinye maka ƙafafunka....."   Ƙarasawa yayi tare da ruƙo ƙafaɗunta,girgiza ta yayi"Hey!what's wrong with u?A ɗan tsawace yayi maganar,aikuwa nan take ta sume mashi Asaman wide chest dinshi ta faɗa,hannunshi yasa sosai yayi hunging ɗinta,Still abun ya bashi mamaki ya kuma ɗaure Mashi kai,wurga idanuwanshi yayi ƙasa saman tiles ɗin ɗakin mai kama da glass,Kayan marmarin da ta kawo mashi ne yashe a ƙasa sun tarwatse hatta cup ɗin Ya fashe,sigh yayi tare da mayar da idanuwanshi Kan sehrish dake sume a ƙirjinshi,bin fuskarta yayi da kallo,jiƙe take sharkaf da hawaye,la66anta duk sun bushe,tafin hannunshi ya sanya a saman kanta ya ɗan shafa sumar kwantacciyar sumarta,mayafinta tuni ya jima da sulalewa ƙasa,ɗaukarta Yayi gaba ɗaya saman kafaɗarshi Ya juya da ita izuwa wurin Katafaren gadonshi,Ya Kwantar da ita,kafin ya miƙa hannu ya dauke laptop ɗinshi Ya wuce da ita Palour don bai kammala aikinshi ba, Almost 30 mins Yana zaune saman Sofa Yayin da yake daddana laptop ɗinshi,after Ya kammal aikin,Ya rufe ta,anan ya barta ya nufi fridge ya dauko Bottle water mai sanyi,walking slowly ya shiga bedroom ɗin, Saman gadon Ya haye har izuwa saitin inda take akwance,emotionally yake kallon kyakkyawar fuskarta,expcially soft brownish lips ɗinta,tausasan gaske masu matuƙar fisgarshi,cire murfin bottle din yayi,ya tarfa ruwan a hannunshi,Ya yayyafa mata nan take ta soma sauke nauyayiyar Ajiyar zuciya,Ajiye robar yayi Saman side drawer ɗinshi,Still yayi yana kallonta,Yadda numfashinta ke fita duk in taja shi sai ƙirjinta yayi sama,da alama ta zarce da yin bacci ne, Saukowa Yayi daga saman gadon sai da ya fara tsince Fruit ɗin da ta zubar mashi a ƙasa tare da cup ɗin data fasa duka ya tattarasu W cikin ƙaramin tray ɗin data zubo su, Ya kaisu palour,saman table ya ajiye plate ɗin,bayan ya ɗauki Laptop ɗinsa daya bari,bedoom ya koma bayan ya ajiye laptop ɗin,Ya ƙarasa wurin switch Ya kashe Hasken dakin,Nan take furniture ɗin suka fara haskaka ɗakin Komawa yayi saman gadon Ya haye,tare da janyota zuwa ƙirjinshi,sosai yayi tighting ɗinta,yadda xaiji daɗin jin breath ɗinta,kamar ƴar jinjira haka sehrish ta koma a ƙirjinshi,zafin daya ji ajikinta ne ya tabbatar mashi da cewa Babu Lafiya atattare da ita, *Boss Bature* *AMRISH* Sam ta kasa runtsawa sakamakon tattaunawar da taji Mommynta nayi na ɗazu da rana,Abun ya tsaya mata aranta,yayi matuƙar tayar mata da hankalinta,Kalmar akashe shi kawai take tariyowa acikin kanta,Shin wanene Mommynta ke bada Umarnin a kashe shi!!idan ma laifi yayi mata meyasa bazata haɗa shi da hukuma ba su ɗauki mataki akanshi,'Sai faman Juyi take yi asaman gadonta Sam ta gaza runtsawa,ƙwaƙwalwarta a cunkushe take Dirar Motar da taji acikin gidansu ne yasa ta miƙe zaune,tana mai mamakin jin shigowar mota acikin gidan Adai dai irin wannan Lokacin,halan mommy ce ta fita,dama ta saba fitar dare,ta ambaci hakan acikin Ranta,Saukowa tayi daga saman gadon cikin sanɗa ta nufi hanyar fita daga ɗakinta,hannu tasa zata buɗe ƙopar taji an datseta,da ƙarfi ta dinga jan ƙopar amma ko motsi wannan batayi ba,hakan ya tabbatar mata da cewar,Mommynsu ce ta rufe ta da mukulli, Ranta yayi mugun 6aci,kamar ta aza hannu akai ta fashe da kuka haka take ji,safa da marwa ta shiga yi acikin ɗakin,Can ta tuna da window ɗin ɗakin,Jiki na rawa ta ƙarasa gaban window ɗin,hannu tasa ta zuge glass ɗin a hankali don kada aji ƙarar buɗe ƙopar,Sai dai kash, bata iya hangen meke waakana acan down stairs,Motsin mutane ta dinga ji suna shigowa cikin gidan,Sosai ta kwallafa rai akan son ganin Su wanene ke shigowa Cikin gidan a irin wannan lokacin,tsabar haushin da taji kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu,ba don taso ba haka ta baro jikin window ɗin Ta koma Cikin ɗakin,Zuciyarta sae faman tafarfasa takeyi, *RishRaf* Wuraren ƙarfe 2 na dare,sunyi nisa acikin baccinsu,wannan ƙaiƙayin na jikinta ya fara takura mata,soshe soshe ta dinga yi tana karkarce fatar jikinta,A ƙarshe da raɗaɗin ya addabeta A zabure ta farka tare da miƙewa Zaune saman gadon nashi, Har cikin kunnanshi sautin kukan sehrish ke kaimashi,A hankali ya ɗan buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci yana kallonta,lokaci guda ya miƙe zaune,Ya tasata gaba'meya yake damunki ne"yayi maganar muryarshi a kasalance, Cikin shesheƙar kuka tace"ƙaiƙayi nake ji ajikina,ko'ina,"Ta takure kanta ajikin head board din gadon   Moving yayi izuwa kusa da ita,sosai ya shiga jikinta,da niyar ya taimaka mata,Wurin sosa jikin nata kota samu relief,Zura hannyenshi yayi acikin rigar jikinta,nan take taji tsigar jikinta ta fara tashi,slowly ya fara shafa fatar laps ɗinta mai sul6in gaske,after ward ya gangara da hannunshi in between laps ɗinnata yana sosai mata wurin,Wani irin shock taji agigice ta ƙanƙameshi,gyara mata zama yayi ajikinshi,Ya buɗe ƙafafunta sukayi rouding waist ɗinshi,shessheƙar kukan da take yi ne ya fara disturbing ɗinshi,hakan yasa shi zura harshenshi cikin bakinta,Ya soma bata hot kissing a tsanake,ɗuff kake ji babu wannan kuka kukan da take yi,a wani irin yanayi mara misaltuwa yake shafa jikinta da sunan susa,natsuwa tayi tana recieving saƙonnin da Sgr ke aika mata a kowani sashe na jikinta,yayin da ita kuma hannuwanta ke acikin sumar kanshi,lokaci guda numfashin kowannansu ya canza,Yayin da bugun zuciyoyinsu ya ƙarfafa,moving yayi da hannayenshi waɗanda ke acikin rigarta ya zagayo dasu ta bayanta yana shasshafa bayanta,after 15 mins Ya cire tongue dinshi daga cikin bakinta,Haɗa tsinin hancinsu yayi guri guda,yayin da suka fara kallon junansu,idanuwan kowannan su ke lumshewa,ga yanayin ƙyallin hasken ɗakin da yake ƙara ƙayatar da abun, Motsi taga yanayi da pink lips ɗinsa,da alama so yake ya furta wani abu amma ya kasa,    yunƙurawa yayi tare da ita,suka faɗa saman lallausar mattress ɗin,kasa jurewa yayi nipple Ɗinta sai gogar mashi lips ɗinshi yake yi ta cikin rigarta,gaba ɗaya ya fara hawa kan Network,Cafka yakai ma nipple din da teeth dinsa har saida ta ɗanji zafi ta runtse idanuwanta sosai,tana cizon la66anta,tamkar jinjiri haka ya shiga sucking ɗinta tunkafin ya zame rigar,A ƙarshe ya ƙarasa zameta gaba daya har zuwa waist ɗinta sosai ya shiga jikinta,almost 20 mins kafin wani lokaci bacci yayi Awon gaba dasu,ƙankame da juna,yadda kasan Anta da Jini, Wuraren Sallar asuba,Marshal na kwance saman gadonshi bai kaiga farkawa ba,Abbansu Ya faɗo cikin ɗakin a hargitse daga shi sai ƴar singlet da gajeran wando fari,bawan Allah duk ya rikice,tsufanshi ya fara bayyana sosai,hannunshi na ruƙe da wayarshi,   Hawa saman gadon yayi yana bubbuga ƙafar Marshal tare da kwaɗa mashi kira"Omar!Omar!Omar?" Can cikin kunnanshi ya dinga jin kiran Sunanshi da Abbansu ke yi,ba arziki ya farka,tunkan ya mike zaune yake kallon abbansu biji biji,kafin idanuwan nashi su washe, "Abba lafiya"?yayi maganar muryarshi da kasala,   Hawaye ya gani a kan fuskar abbansu,ya kasa buɗe baki yayi magana,sai dai wayarshi da yake miƙa mashi,   Gaban marshal na faduwa yasa hannu ya kar6i wayar tare da kallon screen ɗin,Text message ne Aka turo da new number,wani irin jagwalgwalon rubutu ne acikin saƙon,   "Abba bangane me aka rubuta a saƙon nan ba?wanene ya tura maka shi,wasu haruffa ne aka rubutasu ta yadda mutun bazai iya karanta abunda aka sanya ba,   Cikin shesshekar kuka kamar ƙaramon yaro yace"Omar!nima bansan wanene ya tura mun saƙon nan ba,Amma inaji araina cewa JUNAID ne ya turo mun shi,Saboda yana buƙatar taimakona,'   Shiru Omar yayi yana kallonshi,baisan ta yadda zai fahimtar dashi cewa Wannan sakon ba daga junaid bane,Taya wanda ya mutu zai turo saƙo?rashin sani ne yasa shi tunanin cewa Ɗanshi ne yayi mashi saƙon   Lallashinshi ya soma yi"Abba dan Allah kayi haƙuri,babu abunda zai samu junaid ɗinka,wannan saƙon bana junaid bane wani ne can daban,zai iyayiyuwa ma cikin ƴa'ƴan Abokanan ka ne aka samu wani ya dauki wayar mahaifinshi ya tura maka wannan jagwalgwalon,   Daƙyar ya ƙarasa maganar,jikinshi yayi mugun sanyi,Ya fara jin tsoran halin da suka jefa mahaifinsu,Duk ya rame yayi duhu,idanuwanshi sun faɗa,   "Omar dan Allah ku dawomun da junaid,wlh bazan iya rayuwa batare dashi ba,na saba dashi tun yana jinjirinshi kullum a jikina yake kwana,abinci tare muke ci,Duk inda zaije ƙafata ƙafarshi,na saba dashi sosai,nafi son shi fiye da komai na rayuwata,dan Allah na roƙe ku,ku dawomun da junaid,"   Tuni idanuwan marshal sun cicciko da ƙwalla,ji yake tamkar ya sanar dashi ainin abunda ya faru junaid,Don ya fidda rai da dawowarshi,Sai dai kash bazai iya ba,yana fargabar halin da Abban nasu zai shiga,Ya zama abun tausayi kamar ƙaramin yaro,haka ya tasa omar gaba yana yi mashi kuka,daƙyar ya samu ya shawo kanshi,harya samu ya Lafa da yin kukan yana faman sauke ajiyar zuciya   "Abba lokacin sallah yayi,ka tashi mu tafi masallaci,daga nan sai muyi mashi addu'a,in sha Allah junaid zai kasance cikin ƙoshin lafiya,"   Jikinshi na kerma ya sauko daga saman gadon yana tafiya ƙafafunshi.na hardewa kamar zai faɗi kasa,da sauri Omar ya sauko daga saman gadon yabi bayanshi,Don yayi mashi jagora ixuwa Bedroom ɗinshi, Bayan ya raka abbansu ɗakinshi,Ya dawo bedroom dinshi da niyar yin Alwala,Toilet ya shiga after some minutes ya fito yana gyara agogonshi dake sanye a wuyan hannunshi,ƙarasawa yayi gefen gadonshi,ya ɗauki phone ɗinsa dake ajiye saman bedside drawer dinshi, ƙarar shigowar message yaji ta cikin wayarshi,da Sauri yakai idanuwanshi kan screen ɗin wayar,buɗe message ɗin yayi don yaga menene,abun mamaki irin saƙon da aka turo ma abbansu ne,Wato wannan jagwalgwalon rubutun na haruffa da aka cakuɗesu,abun ya ɗaure mashi kai,amma bai kawo komai aranshi ba,fitowa yayi daga cikin ɗakin Ya nufi downstairs,tun akan benen ya dannawa Sgr kira, Da ƙarfi kiran Ya shiga cikin wayar sgr dake ajiye gaban mirror ɗinshi, Sehrish ce ta fara farkawa tana mutsu mutsun bude idanuwanta,zame jikinta tayi daga nashi,miƙewa tayi daga zaune tana faman sauke ajiyar zuciya yayin da take gyara zaman rigar jikinta,sai da ta samu natuwa sosai Sannan ta sanya hannunta Akan damtsen hannunshi,tana dan bubbuga shi a hankali  Cikin sanyin murya ta soma ambaton sunanshi"Ya rafayet!Babban yaya"har cikin kanshi yake jin muryarta,daƙyar ya iya ware blue eyes ɗinshi akan fuskarta,   Calmly tace"time ɗin salla yayi," Lumshe idanuwanshi ya ɗanyi,sam baccin bai ishe shi ba,sai da ya ƙara mintina kafin ya daure ya miƙe tare da saukowa daga saman gadon,Ya nufi wayarshi dake ta ringing, Hannu yakai tare da daukar wayar,ya karata a kunnanshi tare da yin sallama On the other hand Marshal Omar yace"Ka sauko down zamu tafi masallaci,"   "Okey,"ya amsa mashi tare da yin rejecting ɗin kiran,Yana ƙoƙarin mayar da wayar ya ajiye,idanuwanshi suka sauka akan message ɗin da aka turo mashi,kuma ta layinshi wanda ba kowa yasan shi dashi ba,Special ne Sai kana da mahimmanci a wurinshi sannan yake yin saving ɗin numbarka  a layin,   Dangwala yatsanshi yayi akan Screen ɗin wayar,nan take saƙon ya sauko kasa ya buɗe,ƙura ido Sgr yayi yana kallon jagwalgwalon ruhutun da aka turo mashi,da baƙuwar number,ya ɗanyi mamakin ganin saƙon da aka turo mashi,tunani ya shiga yi kowanene da wannan shiriritar? Calling ɗin numbar yayi,nan take aka sanar dashi cewa Wayar a kashe take,Sae lokacin ya lura da lokacin da aka tura mashi sakon wuraren ƙarfe 3 na dare,bana yanzu bane, Mayar da wayar yayi saman mirror ya ajiyeta,A hankali ya ɗan waiga tare da kallon sehrish,tuni ta jima da komawa bacci A zaune, Toilet ya shiga,bayan ƴan mintuna ya fito tare da nufar closet ɗinshi,shiryawa yayi cikin jallabiya brown colour,gaban mirror ya koma ya feshe jikinshi da turare,tana cikin bacci taji an manna mata kiss a gefen fuskarta,da sauri ta buɗe idanuwanta don taga wanene,bata ga kowa ba,Amma ranta yana bata cewar Sgr ne Yayi mata Kiss ɗin, Fitarshi ke da wuya,ta fara jin faɗuwar gaba,wani irin tsoro ne ya lullu6eta,motsi ta soma ji tamkar wani abu zai fito daga cikin toilet dinshi,Wani irin gurnani gurnani,da gudun gaske ta sauko daga saman gadonshi,a sukwane ta fito daga part ɗinshi ta sauko downstairs, alokacin har sun tafi masallaci,Tana ƙoƙarin giftawa ta falon muryar abusufyan ta katse mata hanzarinta   "Daughter ina zuwa"?da sauri ta juya tare da kallonshi,yana a tsaye jikinshi sanye da jallabiya,fuskarshi na ɗauke da murmushi,Ajiyar zuciya ta sauke tare da ƙarasawa da niyar ta rungumoshi,nan take ya 6ace 6aat babu shi,   Tashin hankali,Watsawa tayi a guje ta nufi bedroom ɗinsu,tana ƙarasawa jikin ƙopar ta sanya hannayenta duka biyun ta tura ƙopar ta shige,A lokacin Har sun Kammala sallarsu,Suna zaune saman darduma suna addu'a,   Gaba daya suka ɗago suna kallonta,sae faman zazzare idanuwanta take yi,   "Meya faru ne"?Oummansu ce tayi mata tambayar,ganin yadda ta faɗo dakin a fujajen babu shiri,   Ƙarawa tayi wurinsu,gaba daya ta zube saman ƙafafunta,agaban oummansu, Kallo ɗaya abu tayi mata,ta gane cewa akwai matsala,   Hannu tasa ta janyota izuwa jikinta ta ɗan rungumeta,   "Serish baki lafiya ne"?Jahad ce tayi tambayar,tana kallon sehrish ɗin dake manne jikin oummansu   "Bana jin daɗin jikina ne,"muryarta ƙasa kasa tayi maganar,   "Meya ke damunki ne"?ta kuma tambayarta,   "Nikaina bansani ba,kawai bana jin daɗi" Cike da tausayawa jahad take yi mata ya jiki,   Hosana kuwa batasan ma wainar da ake toyawa ba,tana daga zaune gefen jahad tana gyangyaɗin bacci,dama daƙyar aka tashe ta don tayi sallah,   Addu'o'i oummansu ta shiga yi tana tottofa mata asaman kanta,  Dakatawa tayi da yin addu'ar,ta juya tare da kallon jahad dake a gefenta"Jahad hosana ku koma saman gado,"ta faɗi hakan ne don tasamu damar tambayar sehrish, "To oumma," ta miƙe tare da ruko hannun hosana taja ta zuwa saman gadon,   Ɗago da sehrish tayi daga jikinta, "Faɗamun me yake damunki"?   "Oumma na tabka kuskure,kin hanani na ƙara yin bincike akanta amma naqi ji," Cike da takaici abu tace"Hmmm ta kama ki ko"?   ɗaga mata kai tayi alamar eh,daganan ta bata labarin abunda ya faru jiya a dakin Azmee,amma bata sanar da ita zuwanta Ɗakin Sgr ba,Don har yanzu batasan meke tsakaninta dashi ba,   Rufe ta da faɗa abu tayi"meyasa bakin jin magana sehrish?kunnan ƙashi ko?Wannan matar da kike gani tafi ƙarfinki,Shiyasa nace ki damƙa binciken da kike yi a hannun wani,In ba haka ba zaki jama kanki ne"   "Oumma nima bazan ƙara ba"ta faɗi hakan ne kawai ba don ta haƙura da bincikenta ba,Don tayi alƙawarin saita fallasa Azmee,Koda kuwa Zata Rasa Ranta ne, "Tashi kije kiyi alwala"acewar oummansu, Jiki asanyaye ta miƙe ta nufi cikin toilet ɗin,Bada jimawa ba ta fito tana faman yarfa hannunta,hijab ta ɗauko cikin wardrobe ta zura ajikinta,Sannan ta dawo saman dardumar ta kabbara salla, Till Monday in sha Allah, Ayi hkr da wannan,daƙyar na samu nayi shi,bana jin daɗi sai a slow, *Ga duk mai buƙatar littafin Abban sojoji yayi mun magana kai tsaye ta layina,Amma fa whatsapp kawai banda kira,08103884440*   💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋 𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤ 𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠 *🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥* Cikin natsuwa ta kammala sallar,zama tayi saman dardumar ta ɗaga hannayenta sama tana addu'a,kafin ta ƙarasa yin addu'ar Abu ta miƙe daga kan dardumar,saman gadon ta koma daga gefe ta zauna tana jan casbaha, Tana cikin yin Addu'ar ta tunano da wannan malamin nasu na makarantar Boko Ya Mu'allim,tabbas suna buƙatar taimakon malamai domin magance waɗannan miyagun mutanan,Shafa addu'ar tayi kafin ta miƙe tare da ɗaukar sallayar ta nannaɗe ta,Cire hijab ɗin jikinta tayi ta mayar dasu a wardrobe, Komawa tayi gefen oummansu ta zauna, "Oumma"ta ambaci sunanta, "Na'am?ba zaki koma bacci bane"?   "Zan koma,dama wata shawara nake nema a wurinki,me zai hana mu haɗa da malamai?su tayamu da addu'a,"   Jinjina kai Oummansu ta ɗan yi"Kinyi tunani mai kyau,yakamata mu sanya manyan malamai aciki,domin kawar da waɗannan Azzaluman mutanan da suka addabi rayuwarmu,mu ma kuma mu dage da addu'a,Allah dai ya kawo mana ƙarshensu kowa ya huta,"   "Ameen Oumma," Ta ambaci hakan tare da gyara kwanciyarta saman gadon ta kwanta,cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba da ita,dama jiya bata samu isasshen bacci ba," A 6angaren su Amrish kuwa,mommynta bata buɗe mata ƙopar ɗakinta ba,har sai wuraren ƙarfe takwas na safe,tana cikin taji mutsu mutsun za'a buɗe mata ƙopar,dama jiranta take yi,Saukowa tayi daga saman gadon ta tsaya ruƙe da qugunta tana jira a buɗe ƙopar, Turo ƙopar Mommynta tayi hannunta ruƙe da key ɗin ɗakin,ganin Amrish tsaye a bakin ƙopar yasa ta ɗaure fuskarta"Lafiya kika wani ruƙe qugu kamar zaki dake ni"   "Mommy yanzu abunda kika yi mun kin kyauta!kamar wata dabba dabbar ma akuya haka kika rufe ni a ɗaki batare da kinyi tunanin wani abu zai iya faruwa dani ba?meyasa Mommy?wai laifin me na aikata maki ne"?ƙarasa maganar tayi yayin da idanuwanta suka cicciko da ƙwalla,   Ta6e baki mommyn tayi dama ba imani ta cika ba,   "Rashin jinki ne yasa nake rufe ki a ɗaki,kin cika bin ƙwaƙƙwafin tsiya shegen sa ido,ga taurin kai,Ban isa na faɗa maki abu ki yi ba,da ace kina respecting ɗina as ur mother,da mun zauna lafiya,"   "Shikenan Mommy in har wannan ne dalilin dayasa kike yi mun haka,Wlh zan daina......"   Katse mata hanzarinta tayi"Zaki daina!ko kin daina,ban fahimceki ba"? Da sauri Amrish tace"Na daina,"   Jinjina kai Hajiya Sarat tayi"shikenan,Kin ga yanzu zamuyi zaman Lafiya dake,faɗamun me kikeso na kawo maki ki ci"?   Yatsina fuska Amrish tayi still bata yarda da mommynta ba,   "Duk abunda kikeso Mommy shi nake so,Yanzu dae dan Allah mommy wayata nakeso ki bani!pls mommy nayi missing ɗinta sosai,school friends ɗina duk nayi kewarsu,ina so nayi chatting dasu,"aɗan shagwa6e ta ƙarasa maganar,   "Amrish!ni kaina bansan inda na jefa wayarki ba acikin gidan nan,Ranar kin 6ata mun raine,shiyasa Na ɗauketa,but in kinaso Zamu fita shopping atare daga nan saiki za6i wayar da kikeso,"   Daƙyar Amrish ta ƙaƙaro murmushi akan fuskarta,   "Shikenan mommy,Yanzu bari na shiga ciki nayi brush,"   "Idan kin kammala brush din,Ki jira ni a dining,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta sauko Downstairs,"   Komawa cikin ɗakin Amrish tayi,tsayawa ta ɗanyi ruƙe da qugu aranta tana faɗin"Matar nan bata da gaskiya,ko su waye suka shigo daren jiya?daga gani ba abun arziƙi suka aikata ba shiyasa suka garƙame ni acikin ɗakin kamar wani ɗan kuikuyo,"   Ƙwafa tayi tare da nufar toilet,ta shiga ciki,   After ta kammala,har wanka ta ɗanyi ta zura jeans da farar vest ajikinta,Saukowa downstairs tayi atsanake take tafiya,hannunta acikin aljihun wandonta irin nigogin nan, Tana cikin tafiyar nan kwatsam taji ta taka wani abu a ƙafarta,da sauri ta ɗan ɗaga ƙafarta tare da kai idanuwanta kan abun,Wrist watch ce da alama yarda ta akayi a ƙasa,Zuƙunnawa tayi agaban agogon sai faman ƙyalli take yi da alama ta Diamond ce, Hannu tasa ta ɗauki agogon tana jujjuyata,Aranta tana ayyana farashin agogon,Daga gani ba ƙaramin diamond bane,Don tunda ake siya mata Diamond ba'a ta6a siya mata mai ƙyalli kalar wannan ba,Agogon ta haɗu sosai,Tayi mata kyau,   Murmushi ta saki tare cewa"Yanzu haka cikin baƙin jiya ne da suka shigo cikin gidan nan da daddare aka samu wani ya yarda ita ƙasa wanda baisan muhimmancin kuɗinshi ba,Ko kuma wanda bada guminshi aka siya agogon ba," Jin takun takalmin Mommynta Yasa tayi saurin,zura agogon acikin aljihun jeans ɗin jikinta "Wlh bazan bari mommy taga wannan danƙareriyar agogon ba,Don ta burgeni da ita Zanyi Hotunan Birthday ɗina,Inyaso daga baya sai a mayarwa mai agogon kayanshi,"   Ta ƙarasa zancen zucin tare da miƙewa ta wuce dining,Kujera taja ta zauna tana jiran ƙarasowar breakfast ɗinta,   Shigowa area ɗin Hajiya Sarat tayi hannunta ruƙe da faffaɗan tray mai ɗauke da kayan kalacinsu,Saman table ɗin ta ajiye tray ɗin,   Murmushi Amrish ta saki tare da yi mata sannu"   "Yawwa Daughter,"ta amsa mata a yayin da take ɗaukar plate,warmer ta buɗe mai ɗauke da Chips ta soma zuba mata,bayan ta gama ta haɗa mata da kakkauran Tea,tare da slide bread wanda aka jerashi da wainar kwai," Nan fa suka hau cin abincin atare suna fira,abunda basu ta6a yi ba ita da amrish, Wuraren ƙarfe 9,Sehrish ta farka daga bacci tana ta faman yin hamma wata irin matsiyaciyar Yunwa ce ta addabe ta,Saukowa tayi daga saman gadon babu kowa a ɗakin,duk sun fita yin breakfast,ita kaɗai ta rage, Toilet ta shiga,shaf shaf tayi wanka after some minutes ta fito ɗaure da towel,gaban mirror ta zauna tana shafa mayukan jikinta,sai da ta kammala mulke ko'ina,Sannan ta ɗauki powder zata shafa,Kamar ance ta ɗago ta kalli mirror,kwatsam ba zato ba tsammani taga madubin ya koma mata tamkar tv,manya manyan bishiyoyi ta gani acikin daji ga wasu gwaggon burai gandara gandara masu uban gashi ajikinsu,Sae miƙo mata hannu suke yi ta cikin madubin suna kiran Sunanta"Sehrish kizo,Sehrish kizo"shi ne abunda suke faɗi Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,Idanuwanta suka firfito waje tamkar ƙwayar idonta zata faɗo ƙasa sai kuma taga madubin ya koma lafiya lau,jikinta na kerma ta miƙe ta bar gaban madubin,Da sauri da sauri ta buɗe wadrobe ta ɗauko jallabiya ta zura ajikinta,Mayafin ma a hannu ta ruƙe shi,ko takalmi bata sanya a ƙafarta ba,Gudu gudu sauri sauri ta fito daga cikin ɗakin, Lokacin da ta ƙaraso dining area din gaba ɗaya ta samu kowa zaune suna cin breakfast ɗinsu,tun daga kan Daddynsu Abusufyan,Oummansu da kuma su Hosana da Jahad,Ga Abba kuma tare da Mommynsu Alex,sai su twins da fawan kanal yousouf dasu Jabeer,Ganin Azmee tayi atsaye tana yin serving ɗinsu,Nan fa ta ƙara shan jinin jikinta, Jiki asanyaye ta ƙarasa dining ɗin,hankalin kowa ya dawo kanta, Fuskarta ɗauke da murmushi ta soma gaisar dasu"Abba ina kwana" "Lafiya lou ƴan matan Abusufyan"murmushi ta ɗan saki tare da kallon Mommy"ina kwana mommy an tashi lafiya,   "Lapiya lou Daughter," Komawa tayi kan Daddynsu"Ina kwana daddy kun tashi lafiya," Fuskarshi ɗauke da murmushi Ya amsa mata"lafiya lou daughter,An sha bacci ko"?   Dariya sehrish ta ɗan yi tare da kallon Oummansu ta gaisar da ita,Sai da tabi kowa ta gaisar dashi,tana ƙoƙarin zama Abusufyan yace'baki ga Aunty Azmee bane?naga kamar baki gaisar da ita ba,"   Jimm ta ɗanyi kafin ta wurga eye balls ɗinta kan fuskar Azmee dake tsaye,murmushi ta samu akan fuskarta, Ba don taso ba hakanan ta daure ta gaisar da ita"ina kwana Aunty Azmee," "Lafiya lou Sehrish,Yanzun nan nake shirin zuwa na taso ki sai gashi ma kin fito"   Baki asake Abu da sehrish ke kallonta,Ta ƙware wurin iya kisisina da munafurci,   Banza sehrish tayi,batare da ta tanka mata ba,   Zagayowa Azmee tayi wurinta tare da kai hannu ta ɗauki plate,Warmer ta buɗe mai ɗauke da farfesun Ƴan cikin shanu,Ta zuba ma Sehrish ta tura mata shi agabanta,   Zuƙunnawa tayi daidai saitin kunnan sehrish cikin raɗa tace"Nasan zaki ji daɗin shan farfesun nan,"   Tana kai ƙarshen maganar ta miƙe daga tsaye,kallon Oummansu tayi da ido tayi mata alamar ta kwantar da hankalinta, Ajiyar zuciya ta ɗan sauke tare da zura yatsun hannunta cikin plate ɗin,A tsanake ta soma shan farfesun ba ƙaramin daɗi yayi mata ba, Sai da ta nutsa cikin shan farfesun ta dinga jin motsin wani abu a hannunta,duk in takai hannu zata ɗebo ƴan cikin sai taji suna kufce mata daga hannunta kamar abu mai rai,hakan yasa takai idanuwanta cikin plate ɗin,Tsutsotsi ta gani suna yawo acikin plate ɗin manya manya,A wani irin firgice Sehrish tayi wurgi da plate ɗin ta fasa Uwar ƙara,Nan take ta shiga kwarara Amai, Gaba ɗaya hankalin Kowannansu Ya tashi haiƙam,Mikewa tsaye su kayi suna kallonta,kowa na tambayar Lafiya,Da ƙarfi take ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Wayyo Allah na,Na bani na lalace Daddy,Oumma ku taimake ni,Naci tsutsotsi acikin cikina, Tana magana amai na zuba daga bakinta,duk ya 6ata gaban rigarta jaga jaga,duk tabi ta gigice ta rikice,Watsa wa tayi da gudun gaske tana kuka ta nufi bedroom ɗinsu,A guje Suka bi bayanta Toilet ta faɗa cikin fitar hayyaci ta nufi basin,Cigaba da kwarara aman tayi har saida takai ga babu abunda ke fitowa bakinta sai ɗigon jini ta ƙarar da koma da taci ko ruwa babu a cikinta,   Soso ta ɗauko tare da detergent ta zazzaga shi abakinta,Adai dai lokacin suka ƙaraso ƙopar toilet ɗin,sunyi ƙoƙarin su tura ƙopar amma ƙopar ta datse sakamakon Bugata da sehrish tayi bayan ta shiga,Ƙwanƙwasa ƙopar suka shiga yi kowa na ambaton sunanta,   'Sehrish!kizo ki buɗe mana ƙopa,kada ki Lahanta kanki fa,"muryar Oummansu ce keyi mata magana,tamkar zata fashe da kuka Abusufyan ma murya na kerma yace"Wai baza ki buɗe mana ƙopa ba?meyake damunki ne?Dan Allah Daughter ki fito kiyi mana bayani," Kwata kwata Sehrish bata jinsu domin kuwa ta jima da makancewa,Ta fita hayyacinta,abunda ta gani a plate ɗinta keta dawo mata cikin kanta,   Tura soson tayi abakinta,Ta dinga gurzar bakin,har saida Le6enta suka faffashe jini ya soma zuba ta ko'ina abakinta,daga waje suka dinga jin Azababben kukan da Sehrish ke yi,na tashin hankali,   Da gudun gaske Abusufyan yabar ɗakin kaitsaye ya nufi upstairs don ya sanar da Sgr,Suzo su 6alle ƙopar kada ta kashe kanta, Lokacin da ya shiga Part dinshi ko sallama babu,faɗawa kawai yayi gudu gudu sauri sauri ya shiga bedroom ɗinshi,Sai faman haki yake yi,A kwance ya sameshi yana bacci jikinshi sanye da jallabiya,   Tun kafin ma Ya ƙarasa wurin gadon ya shiga ƙwala mashi kira"Rafayet!Rafayet!!"   Farkawa Sgr yayi lokaci guda ya wurga idanuwanshi masu ɗauke da bacci kan Abusufyan dake ta kwala mashi kira,   "Uncle lafiya"? "Ina fa lafiya!Ga sehrish can zata kashe kanta acikin toilet,bamu san meke damunta ba,sai ihu take tana kuka,Munyi munyi mu buɗe ƙopar ta datse ta,"   Tunkafin Ma Abusufyan yakai ƙarshen maganarshi,Sgr ya sauko daga saman gadon,da wani irin sauri ya fito daga part ɗin,gudu gudu sauri sauri Ya nufi bedroom ɗinsu,Abusufyan kuwa bai baro Upstairs ɗin ba sai da ya wuce ɗakin Omar ya taso shi daga baccin don abun kowa ta shafa, Lokacin da Sgr ya ƙaraso ɗakin abun ya tashi hankalinshi sosai,Tunda ya shigo corridor ɗin ɗakin Ya fara jin sautin kukan da sehrish keyi,Tamkar ana zare ranta daga jikinta,   A sukwane ya faɗa cikin ɗakin,Ganinshi yasa suka matsa mashi daga wurin ƙopar,A zafafe ya daddage ya bangaji ƙopar da ƙafaɗarshi,Nan take ƙopar ta buɗe,Faɗawa cikin toilet ɗin yayi a lokacin Harta yanke jiki ta faɗi ƙasa,jinin da ya gani jaga jaga ajikin basin ɗin ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba,inda take kwance kasa ga soso nan a gefenta ga kuma ledar detergent ɗin da ta fasa,Bakinta yayi jaga jaga da jini fatar le6enta ta munana duk rauni,   Jikinshi Yayi mugun sanyi,yaso ace tun lokacin da ta fara haukan suka sanar dashi,slowly ya zuƙunna agabanta,tare da kai hannu ya tallabo kanta,da hannu ɗaya,Ɗayan hannun kuma zura shi yayi cikin bakinta Ya buɗe shi,runtse idanuwanshi yayi yayin da zuciyarshi ke ta faman tafarfasa,harshenta gaba ɗaya ya faffashe,detergent ɗin yayi mata illa sosai,duk ya sale fatar harshen nata,Yaji raɗaɗin abun har cikin zuciyarshi,miƙewa yayi azafafe ya juya yana kallonsu dayake duk sun shigo cikin toilet ɗin,Oummansu sai kuka takeyi,Haka su Jahad da Hosana ma,   "Tun yaushe ta fara wannan abun?meyasa ba'a sanar dashi ba!"a ruɗe yayi maganar   "Rafayet yanzu duk ba lokacin wannan bane dan Allah ka taimaka,kada mu rasata,"Abbansu Yayi maganar fuskarshi duk a hargitse Juyawa yayi tare da sanya duka hannayenshi ya ɗaukota tare da ɗaurata saman kafadarshi,Ya fuce da ita daga ɗakin,A hanzarce Ya haura da ita Upstairs part ɗinshi,A saman gadonshi ya kwantar da ita,da sauri ya kuma saukowa down bayan ya ɗauki key Ya nufi medical Room ɗinsu,da kanshi Ya shiga duba Sehrish koda ta farfaɗo tana koke koke Allurar bacci yayi mata, kowa ya shiga damuwa,abincin ma duk sun ƙoshi dashi,A ƙarshe saman Sofa kowa ya zauna cike da jimamin halin da Sehrish ta shiga,Abun ya ta6a masu zuciyarsu sosai, Har lokacin abu bata daina kuka ba,Haka Jahad da Hosana ma   "Dan Allah ku kwantar da hankalinku,In sha Allah Sehrish zata samu lafiya,"acewar Kanal yousouf,   "Kusan kashe kanta tayi fa,Omo ta zuba abakinta ta wanke da soso,Ni bansan meke damunta ba,Sae faman ambaton tsutsa takeyi ni banga komai ba a plate ɗin abincinta,"Abusufyan ne yayi maganar idanunshi cike tab da kwalla, "Dole akwai wani abun dake damunta,ni tsorona ma kada ta Zauce" Abba da Mommy sai kwantar musu da hankali suke yi,   Hannun Abu sae kerma ya ke yi,acan ƙasan zuciyarta kuwa,tunanin yarda zata fallasa Azmee take yi don tasan cewa itace Silar Halin da Sehrish ke ciki,tayi jinkiri ne saboda bata jima da zuwa gidan ba,ba lallai bane su yarda da maganarta ba, Miƙewa Tayi tare da kama hanyar zuwa kitchen,tana shiga ta samu Azmee tana gyara kitchen ɗin,hankalinta kwance, "Meyasa kika yi mata haka"?ɗagowa Azmee tayi tare da kallon abu dake tsaye,lokaci guda ta saki murmushin gefen fuska tare da cewa"Bangane akan me kike magana ba"   "Amma baki da Imani!munafuka mai fuska biyu,kina son ki cutar da ita ne saboda kina tsoran karta tona maki asiri,shiyasa kike ƙoƙarin kashe mun ita"tana magana hawaye na zuba akan fuskarta,,   Girgiza kai azmee tayi"ko kusa ni bani da alaƙa da Abunda ya faru da Sehrish!kada kiyi mun ƙazafi,Ni bazan iya cutar da Sehrish ba,Saboda ina jinta tamkar ƴar cikina....." Tunkan takai ƙarshen maganar a fusace abu tace"karki kuskura ki ƙara kwatanta sehrish da ƴar cikinki!mushirika kawai,muguwa kuma azzaluma!Makira!Ni bana jin tsoronki,Da Allah na dogara ba da wani tsubbace tsubbace ba irin naku,waɗanda suka jahilcewa addininsu,har yaushe ne zaku gane gaskiya ku daina aikata irin wannan mummunan zunubin da kuke aikatawa ne?Kuna ɗaukar kanku tamkar wasu shaggu saboda kawai kuna taƙama da tsafin da kuke dashi,In banda ma daƙiƙanci da jakkanci da jahilci irin naku,Kun manta cewa Allah shi ya halicce ku kuma a kowani lokaci zai iya ɗaukar ranku,Kuma zaku koma gareshi sannan ku gir6i abunda kuka shuka,akwai ranar da wannan sihirin da kuke taƙama dashi bazai ta6a amfanarku ba!tunda baku isa ko mutuwa ku hana kanku ba....." Tunkan ta ƙarasa Maganar Azmee ta daka mata tsawa har sai da abu ta girgiza"Ya isa haka!ke baki isa ki ce zakiyi mun wa'azi ba!Idan ilimin addini kike taƙama dashi,ko ƙafata baki kama ba!ke kinsani basai na faɗa maki ba,Idan da naso tun lokacin dana zo gidanki yi maki wankan jego da tun lokacin Na murƙushe ki ke da ƴa'ƴan naki,Amma banyi hakan ba don baki acikin ainihin abun hari na,Idan har kika cika zaƙewa Wlh Zaki rasa Rayuwarki ne!Zanyi silar da zaki bar duniyar nan ne!   "Raina ba ahannunki yake ba!A hannun Allah yake,Idan har kinga na mutu to lokacina ne yayi,kuma koda ace Na mutu ta silarki,inaso ki sani kema wata rana zaki zo inda nake ne,kuma zaki yi bayani ne,banza kawai,ina ilimin da kike taƙama dashi ne?ai dake da dabba duk ɗaya kuke dan wlh ƙwara dabba dake Azmee,ita haka Allah ya halicce ta,Amma ke fa?mutunce wadda ta sani ta take sanin,ko yau kika faɗi kika mutu kinsan makomarki,babu ruwan Allah da ilimin da kike dashi,in har bakiyi aiki dashi ba,Toh ya tashi abanza don azabar da za'ayi maki ranar gobe ƙiyama tafi azabar da za'ayiwa kafiri,"   Lokaci guda Azmee ta juye tamkar ba ita ba,ta fito da ainihin suffarta ta mugaye marasa Imani,Idanuwanta sunyi jawur dasu wani kalar huci ke fita daga bakinta da hancinta,Kalaman Abu sun ƙona mata rai,Kamar ta shaƙo wuyanta haka take ji,   "Ki fita ki bani wuri Zainab!tunkafin Nayi maki Illa"   A harzuƙe abu tace"kiyi duk abunda kika ga dama Azmee,Wlh bazan ta6a karaya ba,koda kuwa zan rasa rayuwata saina tona maki asiri mushirika kawai,"abu nakai ƙarshen maganar,taja dogon tsoki ta juya a fusace tabar kitchen ɗin, Komawa Azmee tayi saman ɗaya daga cikin kujerun dining na kitchen ɗin ta zauna,maganganun abu ta shiga tariyowa acikin kanta,tunda take a rayuwarta Wani ɗan adam bai ta6a fuskantarta ba,Ido cikin ido ya gaya mata baƙaƙen maganganu ba,in ba abu ba,Itace ta farko kuma ta ƙarshe don taci alwashin duk wanda yayi yunƙurin exposing ɗinta saita Kashe shi har LAHIRA, Runtse idanuwanta tayi lokaci guda ta shiga tunanin Sehrish,sam bataso hakan ta faru da ita ba,ta ƙetare Iyakarta ne shiyasa Ta jefa ta a halin da take ciki, Da sallama Omar ya shiga part din nashi,A lokacin Sgr yana ta Zarya acikin bedroom ɗin,lokaci bayan lokaci yakan juya ya kalli Sehrish dake kwance tana bacci,Ba ƙaramin jiki taji ba,don ma Allah Yasa ta samu emergency treatment a wurinshi,Da ba'a son me zai biyo baya ba, Sam baiji sallamar da Omar yayi mashi ba,har saida ya Ambaci sunanshi"Rafayet"tukunna ya juyo tare da kallonshi,   Ƙarasawa wurinshi Omar yayi tare da dafa kafadarshi,   "Ya jikin nata"? "tana samun sauƙi,nayi mata allurar bacci ne,in ba haka ba bazata daina firgitar da take yi ba,"   Ajiyar Zuciya Omar ya sauke tare da cewa"Allah ya bata lafiya,amma meke damunta ne? "I don't even know,jira nake ta farka,Don in tambayeta,nasan zata faɗamun meke damunta,me take gani ne da yake razanar da ita,"   "Haka ya dace,ƴan uwanta na son ganinta,Zasu iya shigowa yanzu?"Omar yayi tambayar yana kallonshi,   Girgiza mashi kai yayi alamar a'a,sannan yace"sai dai zuwa anjima idan taji sauƙi,"   Omar yace"Okey,"harya juya zai fita ya kuma juyowa,   "Ya maganar Haroon"? Sgr yace"Still bai farfaɗo ba,Nasan zuwa anjima zai tashi,"   Gyaɗa kai Omar yayi tare da juyawa ya fuce daga ɗakin,'   Wuraren Sallar Azhar gaba ɗaya suka tafi masallaci,Ya rage saura matan Acikin gidan, Abu sam ta kasa samun natsuwa,gashi batasan ina aka kwantar da Sehrish ɗinba balle taje dubata,basu jima da kammala sallar Azhar ba,Abu ta mike tare da kallon Jahad"Inaso naga sehrish,gashi bansan inda aka kwantar da ita ba,   Jahad tace"Tana a ɗakin Ya rafayet,nima inason na ganta,"ta ƙarasa maganar tare da miƙewa,hosana ma ta miƙe"Nima zanje ganin rishi ɗin," Kowannansu sanye da hijabi,Atare suka nufi upstairs,Da sallama suka shiga falon babu kowa,kaitsaye suka wuce bedroom ɗinshi,daga ciki suka shiga,gwanin ban tausayi haka suka tsaya cirko cirko abakin gadon suna kallonta,Tana bacci tana firgita,Numfashinta na fita daƙyar daƙyar, Zama Oummansu Tayi daga gefen gadon Yayin da su Jahad ke atsaye,idanuwansu cike tab da kwalla,   "Oumma wai meke damun rishi ne?duk tabi ta furgice ta fita hayyacinta," Hosana ce tayi maganar cikin shessheƙar kuka,   Abu tace"ku tayata da Addu'a in sha Allah zata samu sauƙi ne,"   Jahad tace"wlh dama ciwon ya dawo jikina,ita ta huta,Saboda taji jiki ba kaɗan ba,"    Hannu abu tasa tare da shafa fuskar Sehrish,aikuwa kamar jira take yi taji an ta6ata nan ta fara sambatu da muryarta da bata fita sosae saboda ciwon cikin bakinta tana faɗin"ku kira mun shi,dan Allah ku kira shi,Ya mu'allim nake son gani,"lokaci guda kuma tadaina sambatun   Kallon juna sukayi cike da mamaki,har suna haɗa baki wurin cewa"Ya mu'allim kuma?Wanene Shi"? "Jiya tayi mun magana akanshi,Wai wani malaminsu ne Ya mu'allim,Ta sanar dani cewa Ya ta6a taimakonta,ko kunsanshi ne"?Tayi tambayar tana kallonsu jahad,   "Ni ko sunan ma banta6a ji ba,"acewar hosana,   Jahad tace"bazamu iya sanin malamin da take magana akai ba,tunda ba wurinmu ɗaya ba,"   Addu'a suka shiga yi suna tattofa mata ajikinta,basu bar ɗakin ba sai wuraren sallar La'asar,Suka tafi banda hosana,tana zaune gefenta,ta kasa ta tsare sai rishi ɗinsu ta farka, Bayan sallar La'asar,Abusufyan tare da Abba Suka shigo cikin ɗakin,a bakin gadon suka tsaya suna kallonta,A lokacin hosana ta fita daga ɗakin "Banji daɗi abunda ya faru ba,Allah Ya bata lafiya,"cike da jimami Abba yayi maganar, Abusufyan yace"tabbas akwai abunda ke damunta,tana faɗin abunda mu bamu gani ba,kuma a sanadin hakan ta kusa lahanta kanta,In har bamuyi kokarin gano abunda ke damunta ba,za'a iya samun matsala,"yana kai ƙarshen maganar Abba yace"in sha Allah hakan ma bazata faru ba,Yanzu dai ita muke jira ta farka sai muji daga bakinta,Tayi mana bayanin abunda ke damunta," Sunjima suna tattaunawa,Anan su kanal Yousouf da sauran matasan gidan suka same su,Kowa ya shigo ɗakin sai ya yi ma Abusufyan ya jikin Sehrish,daga bisani bayan Sgr Ya dawo ne suka ɗan basu wuri,Ya jima yana jiran farkawar Sehrish Amma babu alamun baccin nata zai ƙare, Wuraren karfe 8 na dare,Sgr da Omar suka nufi Medical room ɗinsu Wurin Haroon,Lokacin da suka shiga a kwance suka same shi yana ta faman Jan numfashi,Idanuwanshi sunyi jawur dasu jikinshi sai kerma yake yi, Tsayawa Sgr yayi tare da goya hannayenshi saman ƙirjinshi,Omar kuma wuri ya samu gefen gadon Ya zauna yayin da idanuwanshi ke akan Haroon    "Ya jikin naka"? Ba ƙaramin mamaki yayi ba,jin Omar yayi mashi ya jiki,yayi tsammanin da bugu zasu fara tambayarshi,   Daƙyar ya iya buɗe baki Yace"babu sauƙi,Naji jiki sosai,Rafayet baiyi mun da sauƙi ba jiyan nan,dan Allah Ya Omar ka taimaka mun nasan kafi shi sauƙin kai,wlh ni babu ruwana kashe Junaid da nayi ma kuskure ne,Sharrin shaiɗanne,In fact ni bayin kaina bane....."a fusace Sgr Ya daka mashi tsawa"Idan ka kuskura ka sake ambaton shaiɗan a wurin nan saina Canza maka kamanni,akwai wani shaiɗanin daya wuce kaine"?   Shiru yayi batare daya kuma cewa komai ba,Don bazai manta da lugudan wahalan daya shaba Adaren jiya, A tsanake Omar ya soma magana"amsa ɗaya kawai nakeso a wurinka!Wanene yake baka Umarni?   "Wlh bazan Iya faɗa maku ba,Ae ko ban sanar daku ba,in har rafayet zai iya sanin duk wani abu da nake aikatawa,Sanin wanda ke bani Umarni bazai gagare shi ba,Yasan Komai" Haushi kamar ya shaqe shi haka yake ji,daƙyar ma yake magana saboda raɗaɗin ciwon da yake ji,Ga Yunwar da yake ji,ba don Omar ya hanashi Dukanshi ba,da ba abunda zai hana ya karairaya ƙasusuwan Jikinshi,ya tsani haroon kamar mutuwarshi,   "Rafayet baisan komai ba,kai nakeso ka sanar dani!Haroon ka amsa mun tambayata,kai da Uban wanene kuke aika aika acikin gidan nan?" Shiru haroon yayi,A hasale Sgr ya ɗaga Hannu zai mauje mashi kai,Omar yayi saurin ruƙoshi,"just leave him,Idan bai amsa mana ba,Wayar shi zata bamu amsa,"   Basu bar ɗakin ba sai da suka ɗaure haroon jikin gadon sosai,Suka rufe bakinshi,Yarda baza aji Sambatun shi ba" Datse ƙopar ɗakin Sgr Yayi,Sun jima suna tattaunawa da Omar kafin Ya wuce upstairs,Omar kuma ya nufi sashen su Abbansu, Lokacin daya shiga bedroom ɗin,Still Sehrish bata farka ba,toilet Ya shiga,After some minutes ya fito sanye da bathrobe da alama wanka yayi,gaban mirror ɗinshi Ya tsaya yana kallon kanshi ta mirror,Abubuwa dayawa suna yi mashi yawo akanshi,yanzu baida burin daya wuce ya kawo ƙarshen maƙiyansu cikin kwanakin nan,da zarar ya gama dasu Zai fara tunanin komawa U.S, Yana cikin zancen zucin nan,Ya fara Jin numfashin Sehrish dake fita da ƙarfi da ƙarfi,Da sauri Ya koma gefen gadon Ya zauna yana kallonta,A hankali ta soma ƙoƙarin buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,biji biji ta fara ganinshi,har sai da ta sanya hannunta saman fuskarta tana mutsustsuka idanuwan tukunna ta samu damar ganin shi da kyau,kwata kwata Jikinta babu ƙwari daƙyar ta samu ta miƙe zaune,Ciwo na yini ɗaya amma duk ta rame,idanuwanta duk sun faɗa,lips dinta sun dan kumbura,jikinta sai kerma yake Yi, "How was ur body"?yayi tambayar Yana kallon Clavicle ɗinta, Shuru bata bashi amsa ba,Sai dai zuba mashi ido da tayi tana kallonshi,Sake maimaita mata yayi"Ya jikin naki,"nan ma shiru bata bashi amsa ba,Cike da mamaki yace"Baki ji ina magana ba"   Tunawa da ciwon bakinta ne yasa shi yin shiru,don yasan bazata iya magana ba sai a hankali,   "If u can't talk to me,zaki iya yi mun alama ta yarda zan fahimci abunda ke damunki," Lumshe idanuwanta tayi tare da buɗesu a hankali   "Are u hungry"?. Da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a,ba don taso ba,ita kaɗai tasan halin da take ciki,Ga matsiyaciyar yunwa tana ji amma fargabar abunda zata ƙara gani acikin abincinta take ji,   Moving yayi kusa da ita,tare da sanya tafin hannunshi ya ruƙo kanta,A saman ƙirjinshi ya kwantar da ita,nan take taji natsuwa ta zo mata,hawaye ne suka soma zarya akan fuskarta,taso ace zata iya buɗe baki ta sanar dashi ainihin abunda ke damunta amma ta kasa,harshenta Ya raunata sosai,magana ma wuya take yi mata, Shafa sumar kanta ya soma yi har izuwa tsakiyar bayanta,sosai ta manne mashi tana shaƙar kamshin jikinshi,   "I really worried about it,pls Tell me what scared you?meyasa kike firgita"?   Yayi maganar tare da mayar da hannunshi saitin zuciyarta dake ta bugawa da ƙarfi da ƙarfi,tunda ya aza hannun kuma sai heartbeat ɗin nata ya dai daita,   Ƙanƙameshi tayi sosai,tana ji aranta kamar bazata rayu ba,tun da ta fara wannan ƴan gane ganen na tashin hankali,   Waist ɗinta Ya ruƙo tare da Janyeta daga jikinshi,Miƙa hannunshi yayi gaban drawer chest,Ya curo biro tare da jotter,   Miƙa mata yayi tasa hannu biyu ta kar6a   "Ki rubutamun duk wani abu dake damunki anan,"   Hannunta na kerma ta buɗe empty page ta soma rubutu,bayan ta kammala ta miƙa mashi jotter ɗin   Hannu yasa ya kar6a yana karantawa _Oumma tasan komai,Ka tambayeta zata faɗa maka abunda ke damuna_ Wannan shi ne abunda Sehrish ta rubuta mashi, ɗagowa yayi tare da kallonta suka haɗa ido,hannu ya zura cikin front pocket ɗinsa Ya zaro wayarshi,Nan take ya kira Fawan ya sanar dashi cewa Ya kira Mashi Oummansu, Miƙewa Yayi ya nufi cikin ɗakin,sai gashi ya dawo sanye da sleeping dress ɗinshi riga da wando Maroon colour,Gefen gadon Ya koma ya zauna yana jiran zuwan Abu, Kusan 15 mins,Abu tayi sallama a ƙopar ɗakin,   "Assalamu alaikum," "Wa'alaikum salam,"ya amsa mata tare da bata izinin shiga daga ciki, Tana sanye da hijab ajikinta,Tunkan ta ƙarasa Sgr ya mike tare da janyo mata chair ɗin dake gaban dressing mirror ɗinshi ya ajiye mata ita,Tunda ta shigo ɗakin idonta ke akan Sehrish,Ba ƙaramin daɗi taji ba da sehrish ta farka,da alama jikin nata da sauki duk da akwai sauran ciwo atattare da ita,   "Ya jikin naki"?tayi tambayar bayan ta zauna,shiru Sehrish bata ce uffan ba,Hakan yasa ta ɗan tashi hankalinta,   "Kada ki damu,ba zata iya magana a yanzu ba,saboda raunin dake abakinta,   Ajiyar zuciya abu ta sauke kafin tace"Allah ya baki lafiya," "Ameen"ya amsa mata amadadin Sehrish ɗin,don ita sai dai ta ɗaga kai, gaisar da ita Sgr yayi cikin girmamawa,ta amsa mashi fuskarta asake, "Inaso ki faɗamun meke damunta ne"? Buɗe baki abu tayi zata yi magana kenan taji anshaƙe mata maƙoshinta,runtse idanuwanta tayi tana ambaton Sunan Allah acikin Zuciyarta, "Be calm and answer me pls"Ya faɗi hakan ne don Ya lura tamkar bata a cikin natsuwarta,Sehrish kuwa hankalinta ya tashi ganin Oummansu ta kasa buɗe baki tayi magana,tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla, Wasu addu'oi abu ta shiga jerowa acikin bakinta,da ƙarfi da ƙarfi,bata daina ba har sai da Maƙoshinta Ya buɗe,nan take zufa ta wanke mata fuskarta,miƙewa Sgr yayi cikin sauri ya shiga palour,within secs ya dawo hannunshi ɗauke da bottle water,zama yayi tare da cire murfin ya miƙa ma Abu,hannu biyu tasa ta kar6a,kusan rabin ruwan ta shanye,janye robar tayi daga bakinta,har lokacin tana cigaba da karanto addu'o'in neman tsari a wurin ubangiji don ta gane cewa so ake a hanata magana,gashi ita kuma gwana ce wurin yin ibada, da kuma yin azkhar da sauransu,zaiyi wuya sihiri ya kama irinsu wani lokacin sai dai suci wahala, Lokacin da taji zata iya magana,da sauri ta soma bayyana mashi halin da sehrish ke ciki"tun jiya da ta shiga ɗakin Azmee bata ƙara samun natsuwa ba,ta sanar dani cewa tana ƴan gane gane,wasu abubuwa nayi mata gizau,kamar ɗazu da safe lokacin da muke cin abinci,Sehrish ta dinga sambatu tana faɗin tsutsotsi ne acikin plate ɗinta,har tayi wurgi da plate ɗin ta watsa da gudu ta shiga ɗaki,wannan ne silar data rikice ta shige toilet tana wanke bakinta da Omo da soso,kamar yarda ka gani....." Dakatawa ta ɗan yi da yin maganar tana faman sauke ajiyar zuciya,Sehrish sai murmushi take yi farin ciki kamar ta miƙe ta rungume Oummansu, Shiru Sgr yayi yana kallonta yayin da yake nazarin wani abu acikin brain dinshi,bakomai ya faɗo mashi arai ba face daren jiya da Sehrish tazo ɗakinshi ta tsorata harta yi wurgi da plate ɗin hannunta,tana fadin Ya rafayet maciji kunama zasu harbeka,anan ya gane cewa Bayan ta fito daga ɗakin Azmee ne ta shigo ɗakinshi, Jinjina kanshi ya ɗan yi tare da cewa"Kina Zargin Azmee"? Da sauri abu ta ɗaga mashi kai Alamar eh, "Meyasa kike zarginta"? "Saboda na santa,lokacin dana haifi su Sehrish,Itace Ƴar uwar sayyadi wadda tazo yi mun wankan jego," Tunkan takai ƙarshen maganar Sgr yace"Kenan ita ƴar uwar shi ce?", Jinjina mashi kai tayi alamar eh,murmushin takaici Sgr ya saki, Yana ƙoƙarin buɗe baki ya kuma tambayarta,Yaji Sehrish ta ruƙo hannunshi,da sauri yakai idonshi wurinta, Da hannu ta dinga yi mashi Alamar ya miƙo mata jotter dinnan zata yi rubutu, Hannu yasa ya dauki jotter ɗin tare da mika mata,dama biron na hannunta, Zane yaga tana yi maimakon rubutu bayan ta kammala ta mika mashi jotter ɗin, Hannu yasa ya kar6a tare da kallon abunda ta zana,Zobe ne ta zana,bai gane me take nufi ba, "Zan iya ganin me ta rubuta?"abu ce tayi tambayar, Miƙa mata jotter din Yayi tasa hannu ta kar6a,koda abu taga zanen sai ta tuna da binciken da Sehrish ke yi dangane da Junaid,dayake ta bata labarin mutuwarshi,baiwar Allah tana so tayi mashi maganar Junaid ɗin ta kasa,Gashi ita kuma abun ta manta bata sanar dashi ba, "Kin gane me take nufi"? Jinjina kai abu tayi kafin ta ɗaura da bayani"Ta sanar dani komai daya faru dangane da mutuwar ƙaninku Junaid!"tunda sgr yaji ta ambaci junaid,hankalinshi gaba ɗaya ya koma kanta, "Akwai wata rana da ta shiga ɗakin Azmee,zatayi sallah tana ƙoƙarin ɗauko hijabi acikin wardrobe ɗin ita azmeen,Sai ga zoben ƙaninku na Diamond ya faɗo daga cikin wardrobe ɗin,A binciken da sehrish tayi ta gano cewa tare da zoben nan Shi Yaron ya fita aranar da al'amarin ya faru kuma abun mamaki Zoben nan nashi baiyi komai ba!babu alamar wuta taci shi!" Gaban Sgr ne ya faɗi rasss!ya ware idanuwanshi gaba ɗayansu,Abun ba ƙaramin girgiza shi Yayi ba,jikinshi har kerma yake yi,aruɗe yace"Taya akai Ita reesh ɗin tasan cewa tare da zoben Ya fita aranar'? "Ta hanyar hotunan da suka ɗauka tare da Junaid a wayar Jahad," A hanzarce Sgr ya ɗauki wayarshi tare da dannawa Fawan kira,tana fara ringing ya ɗaga kiran, "Fawan Am sorry na takura ka ko"? On ther hand fawan yace"A'a babban Yaya,baka takuramin ba," "Idan kana kusa,pls inaso ka kira mun Jahad,ka sanar da ita cewa tazo mun tare da wayarta da kuma wayar Sehrish ina buƙatar ganinsu," "Toh babban Yaya"yana kai ƙarshen maganar ya ajiye wayar,zuciyarshi sai faman tafarfasa take yi,ita kanta daurewa kawai takeyi saboda maƙoshinta da ake ƙoƙarin shaƙewa ta dage sai ta faɗi gaskiya,koda kuwa Rai zaiyi halinsa, Bayan wasu mintuna,Jahad ta faɗo ɗakin da sallama a bakinta,jikinta sanye da dogon hijabi,yayin da hannunta ke ruƙe da wayarta da kuma wayar sehrish, Atare suka amsa mata sallamar,shiga cikin ɗakin tayi,gaba daya idanuwanta na akan Sehrish zaune tana ta murmushi,wani irin farin ciki ne ya lullu6e Jahad, "Sehrish Ya jikin naki?na damu sosai akan halin da kika shiga" "Jahad Rishi bazata iya magana ba a yanzu,ki tayata da addu'a,"acewar Oummansu, Jikin Jahad ba ƙaramin sanyi yayi ba,miƙa mashi wayoyin tayi,Yasa hannu ya kar6a,danna wayar Jahad ya shiga yi,direct ya shiga Gallery ɗinta, ɗagowa yayi tare da kallon Jahad"Ina hotunan da kukayi keda junaid aranar da kuka fita shan ice cream"? "Suna acikin Gallery ɗina,daga ka shiga zaka gansu," "I did not see anything,ko kin gogesu ne"? Gaban abu ne ya faɗi rass,Ita kanta Sehrish saida hankalinta ya tashi, Jahad tace"Wlh ya rafayet ban gogesu ba suna acikin wayata,ko yanzu haka kafin nazo nan hotunan nake kallo" Miƙa mata wayar yayi"nuna mun su," Bayan Jahad ta kar6i wayar,ta shiga neman pictures ɗin gaba ɗaya an goge mata su har vedios din daga cikin wayarta, Tamkar zata fashe da kuka,"Ya rafayet wlh an goge munsu,bansan ya akai ba," "Wani ya amsa wayarki ne"? Girgiza kai tayi"a'a,duk yinin yau wayata tana a hannu na," Mayar da idanuwanshi yayi kan abu"taya zan gane cewa,Junaid ya fita da zoben a hannunshi?ina yin amfani da shaida ne,kafin na yanke hukunci," Gaba ɗaya sunyi shiru,jikin kowa yayi la'asar musamman Sehrish domin kuwa harta fara zubar da kwalla,Azmee tayi masu tsiya suna ƙoƙarin fallasa ta ita kuma ta hana hakan,Shi kuma Sgr bai yarda da sihiri ba,koda zasu fada mashi cewa tana amfani da sihiri zaiyi wuya ya yarda, Hannu Sehrish tasa tare da ta6o shi,juyawa Sgr yayi yana kallonta,Nuna mashi wayarta tayi da yatsanta alamar tana buƙatarta, Miƙa mata wayar yayi,tasa hannu ta kar6a, Tana kunna Power din wayar ta kawo haske,Sai ga text message Ya shigo ta layin AMRISH! Yaushe rabon da ta samu layin Amrish harta manta,kullum in ta kira kashe take samun wayar,Yanzu haka da ta kar6i wayar Amrish take so Ta tura ma saƙo akan ta nemo mata number Ya mu'allim ɗinsu, Shiga message ɗin tayi,ta ƙura ido tana kallon jagwalgwalon Rubutun da aka turo mata,Na haruffan da aka cakuɗesu,abun ya ɗaure mata kai!Nikaina Boss Ya ɗaure mun kai! Duk maison Karanta Littafin Abban sojoji Yayi mun magana ta Layina amma whatsapp kawai banda kira 08103884440     💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋 𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤ 𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠 *🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥* Ta jima tana kallon haruffan nan bata fahimci me aka rubuta a saƙon ba,layin Amrish ta kira nan take aka sanar da ita cewa wayar a kashe take!sam bata so haka ba,ɗagowa tayi tare da kallon Sgr dake magana da Oummansu,   "Nagode sosai da bayanin da kika bani,duk da ban samu evidence ɗin da nake buƙata ba,but i wll try my best wurin ganin nayi investigation akanta,Zaku iya tafiya,"cikin girmamawa Yayi mata maganar,miƙewa Abu tayi"mun gode sosai Allah Ya taimaka,Ya baku sa'a..."sosai ta shiga yi masu Addu'a yana amsa mata da Ameen,"   Ruƙo hannun Jahad tayi atare suka fuce daga ɗakin,Sae da suka fito palour sannan Oumma tace"Jahad ya akai ba'a ga hotunan a wayarki ba?ko kin gogesu ne batare da kin sani ba"?   "Wlh Oumma ban gogesu ba,Nikaina abun ya ɗaure mun kai,"   Jinjina kai Abu tayi"bakomai akwai Allah,Amma Sehrish ɗin fa?Anan zata kwana?ba ɗakin shi bane"?dama abun ya tsaya mata aranta shiyasa ta tambayeta,   "Bedroom dinshi ne Oumma,kada ki damu mu tafi kawae," Bayan fitarsu ɗakin,Sgr ya mayar da hankalinshi kan Sehrish,har lokacin hannunta ruƙe da wayarta yayin da idanunta ke kallon Screen ɗin wayar, "What are u looking at"jin muryarshi yasa ta ɗago da kyawawan idanuwanta tana kallon fuskarshi, "If u need something pls lemme know"cike da kulawa yayi maganar,miƙewa tsaye yayi sai da ya fara ɗaukar Laptop ɗinshi sannan ya fita palour,Ji take kamar ta dakatar dashi,Saboda tsoran da take ji, Yatsun hannunta na kerma Ta shiga danna wayar call log ta shiga ta kara dannawa Amrish kira,Nan take aka kara sanar da ita cewa Layin akashe yake,tamkar ta fasa ihu haka taji,runtse idanuwanta tayi tare da ɗan buɗesu kadan,yanke shawarar zuwa whatsapp group ɗinsu tayi Na Classmates ɗinta,Akwai kuma Na general wanda kowa ke aciki students ɗin da kuma malamansu ne aciki,A Group ɗin teachers kaɗaine zasu Iya tura saƙo banda students,tana fatan Allah yasa Ya Mu'allim yana acikin group ɗin,profile ta shiga daga ƙasa wurin da List ɗin Malaman dake group ɗin suke ta fara duba sunayensu tundaga kan Admins,Gasu nan sunayen birjik amma bata ga Numbar Ya mu'allim ba,Sai dai wasu numbobi da aka rubuta sunansu da harshen Larabci,shiru tayi tana tunanin kowanne ne aciki nashi,A ƙarshe dae duka numbobin masu ɗauke da rubutun Larabci ta turama Saƙon,bayan ta kammala rubuta saƙon ta ajiye wayar a saman bedside drawer, Wuraren ƙarfe 2:30 na dare Lokacin masu bacci sunyi nisa a baccinsu,kamar yarda suka saba kwanciya a saman gadonsu su ukku,Hosana na a tsakiyarsu Abu na a ta 6angaren hannun dama inda yake fuskantar ƙopa,Jahad nata Can 6angaren hannun hagu,kwatsam Suna cikin Baccin nan,Abu ta soma jin wani irin gurnani gurnani asaman Gadonsu,a hankali ta buɗe idanuwanta tana ƙoƙarin ganin menene,har sai da gabanta ya faɗi rass,Wata Mummunar mage ce baƙa wulik mai Uban gashi ajikinta Hakoranta dogaye irin na Vam pires,Kafin abu tayi wani Yunƙuri Magen nan ta daddage ta kai Mata suka ta dira akan wuyan Abu,wasu Manyan ƙumbuna ta fiddo a hannunta tana ƙoƙarin Caccaka ma Abu akan fuskarta,A firgice Abu ta damƙi wuyan magen,Kokawa ta 6arke a tsakaninsu,duk yarda baƙar magen nan taso ta cutar da abu amma abun ya faskara,Domin kuwa Allah yaba Abu sa'a tunda ta damƙi wuyan magen nan ta dinga Jibgarta batare da jin shakkun wani abu ba,A jikin side drawer abu ta dinga buga kan magen nan bugu bana wasa ba,Har sai da magen ta fara kuka tana faman ambaton Miyau miyau,A faɗace Abu tace"Zaki ci ubanki ne,Baki ga komai ba,Nasan cewa ke ce Azmee,kika zo mun da suffar mage don ki kashe ni,Saboda kinga Asirinki na shirin Tonuwa ko? Tunda abu ta ambaci hakan sai Magen nan ta bace 6aaat babu ita tamkar bata ta6a bayyana ba,ajiyar Zuciya abu ta sauke tana mai godiya ga Allah,daya bata nasara Akan Azmeee, Saukowa tayi daga saman gadon,ba ƙaramin daɗi taji ba dasu Hosana basu farka ba,duk wannan badaƙalar da akayi suna ta shan baccinsu, Toilet ta shiga,Bayan wasu mintuna ta fito ɗaure da alwala,Hijabi ta ɗauko tare da darduma ta shimfiɗa ta kabbara Sallah A 6angaren Sehrish kuwa kasa samun natsuwa tayi acikin ɗakin,har sai da Sgr ya shigo sannan hankalinta Ya kwanta,ruwa tace mashi zata sha don💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋 𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤ 𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠 paid book *🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥* Not edited👌 Lokacin da suka sauko downstairs,gaba ɗaya kowa Ya hallara akan dining suna Yin break fast,ƙarasawa Su kayi Bayan sun gaishe da kowannansu,Kowa saiyi Mata Ya jiki Yake yi,Taji daɗin yarda Suka nuna damuwa akanta,kusa da oummansu ta xauna,Jahad ma ta zauna a gefenta,a dai dai Lokacin Azmee ta dawo hannun ɗauke da wasu kayan abincin data ɗauko a kitchen,A saman table ɗin Ta ajiye tray ɗin,Atare Sehrish da Abu suka ɗago ido suna kallonta,fuskarta ta kumbura idanuwanta sunyi jawur kamar wadda tasha kuka,a gefen fuskarta hada gurjewa,fatar wurin ta tattare,Abu batayi mamaki ba,don kuwa ta gane cewa Itace ɗin tazo mata da suffar mage a daren jiya,Ga alamu nan Sun nuna, Zagayawa tayi wurinsu Sehrish,plate biyu ta ɗauko ta zuzzuba masu abinci,tare da tura masu agabansu,Jahad ta hauci,Sehrish kuwa ƙin cin abincin tayi,Miƙewa Tayi daga saman chair ɗin,   "Ina zaki je"?omamnsu ce tayi magana ganin ta miƙe,   Daƙyar ta iya cewa"Kitchen zanje,"ta ƙarasa maganar tare da kama hanyar zuwa kitchen don ta shirya mashi breakfast ɗinshi,tun da ta fara jin sauƙin jikin nata, Shaf shaf Ta shirya mashi asaman ƙayataccen tray,Ta wurinsu ta gifta cikin main palour,Upstairs Ta haye lokacin data ƙarasa part ɗin nashi tana ƙoƙarin Shiga,tajiyo muryoyinsu suna magana Shi da Omar,   "The same fa irin message ɗin da aka turomin Ni da Abba,da farko da abba ya nuna mun saƙon nayi tsammanin ɗaya daga Cikin friends ɗinshi ne,Aka samu wani Yaron Ya ɗauki wayar mahaifinshi Ya rubuta jagwalgwalon,Amma daga baya dana ga saƙon sai abun Ya tsaya mun araina,kuma sai gashi kaima An tura maka,to wai wanene da wannan aikin"?Yayi tambar yana kallon Sgr,dake a gefenshi,   "Am confused Omar,Nagaza fahimtar me aka rubuta ajikin message ɗin nan,abu 2 nake hasashe akan saƙon nan,kodai ƙaramin Yaro ne Ya rubutoshi,ko kuma wanda baya acikin hayyacinsa,Amma abunda yafi ɗaure mun kai shi ne,Taya akai wanda ya turo saƙon Ya samu special line ɗina,Wanda bakowa ne yasanni dashi ba,"ya kai ƙarshen maganar yayin da idanuwanshi ke akan Omar, Kafin Omar yace wani abu,Sehrish Ta katsesu da sallama,Atare suka ɗago suna kallonta,    Ƙarasawa tayi gaban table ɗin dake agabansu,ta sauke trayn asaman shi, kafin ta ɗan ɗago tare da kallon Marshal Omar,murmushi ta samu akan fuskarshi,   'Ina kwana Ya omar,ka tashi lafiya,"   "Lafiya Lou Sister,Ya jikin naki"?   "Da sauki ya omar,"_ "Allah ya ƙara maki lafiya," "Ameen ngde,"ta amsa mashi, Cike da Zolaya ya nuna kayan abincin data ajiye masu"Nawa ne ko nashi"?   Duƙar dakai ta ɗanyi tana murmushi "Naku ne,na kawo maku," "Kinsan da zuwana part ɗinshi ne,"?   "A'a,"tayi maganar tare da satar kallon Sgr,Ya tsareta da blue eyes ɗinshi,duk saita shiga kame kanta,    "Ya akai naga ka tsareta da ido?faɗamun menene sirrin kallon nan"yayi maganar yana ɗage mashi gira,da sauri Sehrish Ta juya ta kama hanyar fita ɗakin,   "Kallon Ya isa haka,Its better ka kame kanka malam,saura ƴan satittika,Ka sakar mashi Ƴar shi,Ka koma U.s wurin Eva nasan har yanzu tana jiranka," Ɗaure fuska Sgr yayi"Omar bana son wannan joke ɗin,idan kaga nabar ƙasar nan,ƙafata ƙafarta,zan tafi tare da ita u.s don taci gaba da yi mun aiki acan,"   Harararshi Omar yayi"Sannu ko?masu aikin dake garemu a U.s fa,Sallamarsu zaka yi ne"?   "Aikinta daban nasu daban," "Kana nufin aikin gyara shimfiɗa"?dariya ce ta kufce ma omar,hakan ba ƙaramin hasala shi yayi ba,   Ganin ya 6ata rai yasa shi cewa"Shikenan nadaina,yanzu dae bari nayi serving ɗinmu ko?nasan kana jin Yunwa,"   Yayi maganar tare da kai hannu yana buɗe warmer,   Sehrish kuwa Bayan fitarta daga part ɗinshi,jiki asanyaye take tafiya,maganar da taji su Ya omar nayi akan saƙon nan ya tsaya mata aranta,Taya akai aka tura masu message iri ɗaya,Amma ita saƙon nata bada new number bane,ta layin Amrish ne,kuma a iya saninta Amrish bata da Number ɗinsu Ya omar,balle ace itace ke tura masu saƙon dagangan,to kodai ta yarda wayarta ne?wani yaron ya tsinta Yake tura masu saƙo,Can kuma ta tuna abunda Sgr yace da Special line ɗinshi aka tura mashi saƙon,Wanda ba kowa ne keda shi ba, Ƙarasa Zancen zucin tayi a lokacin data sauko palour,bata koma dining ɗinba ta wuce bedroom ɗinsu tana zarya acikin ɗakin nasu, *Amrish* lokacin data juya izuwa cikin gidan A sukwane ta faɗa falon,da gudu ta nufi wani Corridor,Gidan Yana da girma sosai,tana da tabbacin cewa anan downstairs Suka rufe shi,haka ta dinga bin ɗakunan dake a gidan kaf tana bincikasu,Tasha wahala sosai,Ga uban gumi data haɗa,fuskarta sai naso take yi,A ƙarshe data gaji ta shiga ƙwala mashi kira ko Allah zaisa Yaji kiran nata Ya amsa mata,   "Junaid!Junaid"tamkar maƙoshinta zai 6allo waje saboda yarda take 6are baki wurin kiran sunanshi, A galabaice Amrish tayi ruku'e hannunta dafe da guiwowinta,Sae faman haki take yi,runtse idanuwanta tayi gam,yayin da take tariyo ɗakunan data bincika a ƙalla sun kai ɗaki takwas masu zaman banza wanda ba'a amfani dasu,zurfin tunani ta shiga,nan take wani abu ya faɗo mata aranta,Acan backyards ɗin gidan Akwai wani munafukin ɗaki,Wanda tun tana yarinya hajiya Sarat ta hanata shiga ɗakin,ko wurin ɗakin taje saita tsawatar mata,tunda take ita dai bata ta6a gani an buɗe ɗakin nan ba,Akan idanuwanta,Kamar an daina amfani dashi amma akwai wasu surruka da aka 6oye acikinsa,Shiyasa aka hanata zuwa, Cike da ƙwarin guiwa Amrish Ta miƙe,ta juya tare da kutsawa Can ciki,Ta ƙopar baya ta fita,tsayawa Tayi tana kallon Girman ginin,A hankali ta aza idonta kan ƙopar ɗakin dake fuskantar backyard din,Wani ƙaton ƙwaɗo ta gani an garƙame ɗakin dashi,Wanda duk bala'enta bazata iya cire wannan makullin ba,tsabar baƙin ciki kamar ta haɗiyi zuciya a wurin nan,Gashi window ɗin ɗakin sunyi nesa can sama,matsawa tayi jikin ƙopar ta kanga kunnanta,hannu tasa tana ɗan kwankwasa ƙopar ko zata ji motsinshi,Amma shiru babu wani alamun akwai mutun,cike da takaici ta juya zata bar wurin kenan idonta ya hango mata ɗigon Jini a ƙasan wurin,har sai da ta dafe saitin zuciyarta saboda faɗuwar gaban da taji,wannan Yasa ta ƙara yarda cewa Akwai mutun a cikin ɗakin,tabbas Sun shiga dashi cikin ɗakin,da gudun gaske ta koma cikin gidan,akwai wani ɗaki dake jingine da wannan ɗakin dake a backyard ɗin Amma shi yana fuskartar Cikin gidan,ranta na bata cewar Zata Samu window ɗin ɗakin ta cikin ɗakin dake acikin gidan,cike da sa rai Amrish ta faɗo cikin gidan,gudu gudu sauri sauri Ta shiga ɗakin,kamar Store ne na ajiyar buhun hunan kayan abinci da jarkokin Mai,A jikin ƙopar store ɗin ta samu Key ɗin ɗakin,hannunta na kerma ta murza key ɗin ɗakin,kafin ta hankaɗe ƙopar ta shiga,Gabanta sai faɗuwa yake yi tsoranta kada Mommynta ta dawo,dan Wlh har kashe ta zata iyayi,Dama tasha faɗa mata cewa ita bata damuba don ta rasa ba,ba ɗigon Imani azuciyarta,Kamar arniya hake take, Ajiyar zuciya ta sauke Lokacin data hango Window mai girman gaske Duk da akwai net ajikinta,Amma batayi nisa ba,in har ta taka wani abu zata Iya hangen abunda ke wakana acan ɗakin bayan gidan,Ga uban duhun da ke cikin ɗakin,Bazata Iya hango abunda ke aciki ba,da gudun gaske ta juya tabar store ɗin,kitchen ta nufa Ta ɗauko wuƙa lafiyayya,Kafin ta ƙarasa saman hannun kujera inda ta ajiye wayar junaid ta ɗauketa,dama ita waya koda security torch ligh na kawoka,Don haka ta kunna fitilar wayar,Ta nufi store ɗin a hanzarce,Rufe ƙopar tayi bayan ta shiga,gaban waɗannan jerin Jarkokin man ta nufa,da yake Allah yayi mata ƙarfi,ɗaukar jarkar Tayi tajata izuwa gaban window ɗin,Sannan Ta hau saman jarkar,Iya idanuwanta ne suka kai Wurin net ɗin tagar, Wuƙar hannunta ta sanya,ta dinga caccakata jikin Ragar,nan take wurin ya lomatse,Gagara wuƙar ta shiga yi tana Yanka Ragar,har sai da ta cire Rabinta,Tukunna Ta saki wuƙar kasa,Haska wayar tayi tana leƙen ɗakin,Saboda tsabar duhun ɗakin fitilar wayar tayi mashi kaɗan,Amma a haka tadinga ƙura ido tana kallon abubuwan dake cikin ɗakin,Wato wasu tsofaffin makamaine aka ajiyesu acikin ɗakin,ga wasu tuluna kamar na ruwa,A jikin bangon ɗakin Ƙwaryoyi ne aka ratayasu,Samansu an rufesu da faifai,ta kasa ganinshi,har sai da ta fidda rai,tana ƙoƙarin janye wayar ta bar wurin,kawai ta hango ƙurar dake danƙare a ƙasan ɗakin tana motsi,nan take gabanta Ya faɗi Rass,lokaci guda ta gane cewa mutunne kwance ƙasan ɗakin,yayi buɗu buɗu da ƙura,nan take zuciyarta ta karaya batasan Lokacin da ta fashe da kuka ba,Don tana ji aranta cewa Shi ne,Batasan taya zata Iya taimakonshi ba,tunda alamun sun nuna cewa babu ƙwari a jikinshi,balle ya iya takowa wurin Window ɗin Ya biyo ta ciki,tunda tagar tana da girma, Tana cikin wannan Yanayin,Hawaye shaba shaba akan fuskarta,karaf kunnuwanta Suka jiyo mata dirar Mota a cikin gidan,Zo kaga tashin hankali,A firgice ta duro daga saman jarkar,saboda tsabar ruɗi anan tabar wayar Junaid ƙasa, ta rarumi wuqar data wurgar,ta ruƙota a hannunta Da gudu ta rufe ɗakin,Ta nufi kitchen,ƙiris Ya rage ta shiga kitchen ɗin,Muryar Hajiya sarat ta katse mata hanzarinta   "AMRISH"!a gigice Amrish Ta juya tana kallonta,Material ne ajikinta,Ta kashe ɗaurin kallabin nan na rashin mutunci,hannunta ruƙe da hand bag ɗinta,   Wani irin fitsari ne ya matsi amrish,Sai faman haɗiyar yawu take yi,idanuwan nan wuri wuri dasu na mara gaskiya,   "Naga kamar bakiyi farin ciki da dawowata ba ko"?   Shiru bata amsa mata ba, "Ko har yanzu fushin kike yi dani ne"?nan ma shiru Amrish bata Amsa mata ba   Sai lokacin Hajiya sarat ta lura da wuqar dake hannunta,cike da mamaki tace"Ke!me kikeyi da wuqa a hannunki?Ya akai naga hawaye sharkaf akan fuskarki?wai meke faruwa ne"?   Ajiyar Zuciya Amrish ta sauke,Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Albasa nake yankawa a kitchen,ina girka abinci ne,saboda Yunwa nake ji,"ta ƙarasa maganar tana shafa cikinta, Dariya Saratu Tayi"Manya Na girki,kinga yarda kika canza kamanni?Sai kace bada Gass kike girki ba?Yo wanna ae koda murhu kike girki baza ki yi irin wannan galabaitar ba,Fuskarki ta ca6e sosai kamar ma hada kwalliya kikayi ga janbaki nan dama dama har akan kumatunki"Tana magana tana dariya,   Murmushin yaƙe Amrish tayi tareda sanya hannu tana goge zufar goshinta,Ba ƙaramin daɗi taji ba,Ganin bata Ganota ba,   "Nasan ban kyauta maki ba,Nayi maki alƙawarin zamu fita shopping,Banji daɗi ba daughter,Wani emergency call ne aka yi mun Shiyasa na fita batare dana sanar maki ba,"   "Kada ki damu mommy,Ni yanzu ma ta cikina nake yi,bari na shiga na ƙarasa Yanka Albasar,"   "Okey,Zan shiga ciki na ɗan watsa ruwa,inaso na kwanta na huta,don wlh na gaji,Amma idan na tashi,Zuwa anjima kaɗan sai mu fita Shopping ɗin"   "Toh mommy,A huta Lafiya,"daga haka ta shiga kitchen ɗin,Hajiya Sarat kuwa Upstairs ta wuce, Ajiyar zuciya Amrish ta sauke,A dole ta ɗauko albasa ta shiga yayyankata,can kuma ta ajiye yankar albasar,ta soma zarya acikin kitchen ɗin tana tunanin Ta yadda za'ae Ta taimaki Junaid Ya koma wurin Iyayenshi,In ba haka ba kashe shi zasu yi,in ma basu kashe shi ba,Wannan daƙyar zai kai labari, Tunanin kiran Sehrish Tayi a waya,Domin kuwa Ta haddace numberta,Babbar matsalar shi ne Babu wayar da zata Kirata,Wayar Junaid akwai security,duk ta gaza samun natsuwa,a ƙarshe ta ajiye yankar Albasar,ta fito daga kitchen ɗin ta nufi upstairs,A bakin ƙopar ɗakin mommy ta tsaya,tura ƙopar ɗakin tayi a hankali ta leƙa,bata same ta aciki ba,amma taji saukar ruwa alamar wanka Take yi, Jiki na rawa ta shiga cikin ɗakin cike da fargabar karta kamata,handbag ɗinta ta buɗe anan ta samu wayoyinta guda biyu,ƙaramar nokia da kuma Infinix,duka ta haɗa wayoyin,Sannan ta ɗauki key ɗin ɗakin data gani saman side drawer,fitowa tayi daga cikin ɗakin,Ta garƙame Hajiya Saratu da mukulli,gudu gudu sauri sauri ta sauko downstairs,tana ƙoƙarin kunna ƙaramar wayar kenan,Infinix ɗin hannunta ta soma ringing,ƙura ido tayi tana kallon Sunan daya bayyana akan screen ɗin wayar,Daddyn Amrish,   Maimaita sunan Tayi"daddyn Amrish!"da mamaki akan fuskarta, "Dama amrish nada uba,"ta tambayi kanta sai kace ba ita bace Amrish ɗinba   Picking call ɗin tayi tare da kara wayar akan kunnanta,    "Kina jina saratu,Wlh karki kuskura kibar yaron nan araye,Don na lura Yaya bazata ta6a bari A ɗauki fansa akanshi ba,Abunda nakeso dake shine,ki ƙwaƙule mashi idanuwanshi nasan zaki iya,Sannan ki binne mun shi da ranshi in bai mutu ba,"   Wata irin zufa ce ta wanke mata fuskarta,Lokaci guda tsananin tsoro ya bayyana akan fuskarta,mutumin bai jira amsarta ba,Yaci gaba da magana duk a tunaninshi da Saratun Yake magana,   "Banaso Ya wuce Yau araye,Kawai ki aiwatar da abunda nace maki,"a gigice Amrish tayi rejecting ɗin kiran,don bazata juri bata lokaci ba wurin sauraron munanan kalaman mutun daya kira wayar,Amma fa tajima tana nanata sunan da Mommynta tayi mashi saving a wayarta,wai daddyn Amrish,A rasa wa za'a sanya ma suna daddyn Amrish sai wannan Mugun,me kashe ƴa'ƴan mutane, Dogon tsoki Taja,taso ace zata Iya buɗe infinix ɗin don tayi bincike akan wayar,Sae dai kash akwai security ajikin wayar,ƙaramar wayarce kaɗai babu security ajikinta,Call log ta shiga tare da dialling number ɗin Sehrish ta danna mata kira,Sai faman tsuma take yi,don ta qagara Sehrish ta ɗaga kiran ta sanar da ita cewa Yayanta na a gidansu,Suzo su dauke shi, Almost 3 times Kiran nashiga,amma Sehrish bata ɗaga ba,sakamakon Wayarta dake a silent,tana cikin aljihun doguwar rigar Jikinta,   A ruɗe amrish ta shiga faɗin"Nashiga Uku!Sehrish dan Allah ki ɗaga kiran!Ya zanyi in bata ɗaga ba,Yanzu idan suka kashe shi fa,Wayyo Allah na,"tana cikin wannan zullumin, A can ɗakin Hajiya saratu kuwa,tana fitowa daga toilet,daga ita sai towel ɗaure a chest ɗinta,kaitsaye ta nufi handbag ɗinta donta ɗauki wayarta,tana zura hannu taji wayamm babu wayoyinta,Zazzage kayan cikin jakar tayi nan ma wayaam babu su dagaske dai an ɗauke mata wayoyinta,da farko tayi tunanin cewa ko a wurin meeting ɗin da taje ne aka dauke mata waya,Amma daga baya kuma sae ta tuna cewa tayi waya acikin mota lokacin da take shigowa cikin gidan,kodai Amrish ce ta ɗauke su!Nan take gabanta Ya faɗi rass,Sae lokacin ta tuna da wayar Junaid data bari asaman gadon,itama wayar babu ita,tun lokacin da tashigo ɗakin tayi noticing ɗin hakan amma bata kawo komai aranta ba,saboda ranta ya bata cewa ko ba anan ta ajiye wayar tashi ba, A hargitse ta nufi ƙopar da dukkan ƙarfinta tasa hannu ta tura ƙopar,aikuwa taji an rufeta da mukulli,bubbuga ƙopar tashiga yi tana ƙwala mata kira   "Amrish!Amrish!wlh karki kuskura kice zakiyi mun bincike acikin wayata!kizo ki buɗe ƙopa tunkafin in buɗeta dakaina," Ƴan hanjin cikinta ne suka kaɗa lokacin da tajiyo Muryar Mommynta,.    Tabbas in bata yi hanzarin kawar da junaid daga cikin ba,su duka biyun zasu iya rasa ransu,   Duk da halin da take ciki hakan bai hanata mayar ma mommynta martani ba,.    "Wlh bazan buɗe ba mommy,Allah ya kamaki,Yau saina tona maki asiri,"   Kamar ƴar dambe haka Hajiya saratu ta dinga bubbuga ƙopar,   "Amrish wlh idan har kika kuskura kika tona mun asiri,Saina kashe shi acikin gidan nan,"ita duk a tunaninta Amrish a iya binciken wayarta ta tsaya batasan cewa ta gano inda suka 6oye shi ba,   Ganin taƙi zuwa ta buɗe mata ƙopa yasa ta nufi cikin ɗakin tana neman ɗayan key ɗin ɗakin,Gaba ɗaya ta hargitsa ko'ina,   Amrish kuwa yatsun hannunta na kerma Ta shiga ƙoƙarun rubuta ma Sehrish saƙo,Bayan ta tura mata text message ɗin,ta jefar da wayoyin saman Sofa,dabara ce ta fado mata,In har ta shiga ta cikin tagar dakin nan data cire ragarta,Zata Iya ƙoƙarin ku6utar dashi, Da gudun gaske ta koma Store ɗin nan,Ta janyo jarkar man zuwa saitin tagar,ta haye samanta,hannuwanta ta sanya da dukka ƙarfinta ta ƙarasa yayyaga ragar jikin tagar,dama ta tsufa sosai daga taja saita kece,gaba ɗaya ta yakice ta,saukowa tayi daga saman jarkar ta dauko wayarshi da tayi wurgi da ita a ƙasa ɗakin,ta kunna torchlight ɗinta,Sannan ta koma saman jarkar,Da ƙarfin gaske ta kutsa kanta Cikin tagar,ba ƙaramar wahala tasha ba,Saboda girman jikinta don ma Allah yasa Tagar tana da girma,tana jin sauran ragar dake agefe da gefen tagar tana kartar jikinta amma haka ta jure,gaba ɗaya ta rubza cikin ɗakin,ta faɗo ƙasa timmm cikin ƙurar nan,duk ta 6ata mata fuska,A galabaice ta ɗago tare da sanya hannunta,Tana kakka6e ƙurar dake akan fuskarta,ɗago da wayar hannunta tayi tana haska ɗakin,Ga tsoro ga furgici,miƙewa tayi tana haska ƙasan ɗakin har Allah yasa ta gano inda yake kwance,numfashinshi na fita sama sama,zubewa tayi saman guiwowinta,Ta sanya dukkan hannayenta tare da ɗago dashi,yayi buɗu buɗu dashi,ƙurar duk ta rufe fuskarshi,har cikin hancinshi,baka iya ganin komai daga fatar jikinshi,fashewa amrish tayi da matsanancin kuka,kamar ranta zai fita,ya raunata sosai,Alamun sun nuna cewa yana akan hanyar gangara,daƙyar zai iya rayuwa,rungumeshi tayi ajikinta yayin da zuciyarta ke bugawa,Tunawa da Mommynta yasa Ta yunƙura tare da ɗaukarshi asaman kafaɗarta,Yayin da hannunta ke ruƙe da wayarshi,miƙewar da zatayi kenan hasken fitilar hannunta ya hasko mata Wayarta dake dadda6e da ƙura,bata bi ta kanta ba,don a halin yanzu tafi buƙatar Rayuwar Junaid,Ita dai koda gawarshi ce takai masu su ganshi,dole ta tagar ta fara turashi kamar tsumma haka ya faɗo ƙasan ɗakin,ita ma ta biyo ta window ɗin, a hanzarce ta ɗauke shi,saman kafadarta ta kama hanya,fitowa tayi daga cikin ɗakin ɗauke dashi,Ƙura duk ta buɗesu,musamman shi,kamar dodo haka ya koma,ya rame ya shanye ya bushe Ya ƙanjame bawan Allah Adai dai Lokacin Hajiya saratu ta samu ɗayan mukullin ɗakin dake a cikin drawer chest,jinjina kai tayi tana huci tamkar zakanya haka ta Nufi bakin ƙopar,Ta murza key ɗin......... *Masu buƙatar karanta Abban Sojoji har zuwa Takun ƙarshe yayi mun magana Ta Layina whatsapp kawai 08103884440* *Ayi hakuri da wannan* ⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐? *_MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI_* *DOMIN. DAWO DA MARTABAN NONONKI* Shin ko kinsan nono yanada matukar muhimmanci a wajan mai gida ,? Shin ko kinsan babu abunda namiji yafiso yafi daukar hankalinahi kamar cikar k'irji , ? To nono shine babban Martaban mace a wajan mijinta , don babu namijin da zaiso mace mai yakunannen nono kamar silifas ,wannan yasa Nazo maku da sahihi kuma ingantaccen maganin nono Wanda bashida wata matsala hadin gargajiya ne , acikin lokaci kalilan zakisha mamakin yadda nononki zai ciko sosai Wanda wannan cikowar ita zata bashi damar da zai tashi sosai ta yadda kema zaki Shiga cikin jerin mata masu aji agaban mazajensu ........kedai hanzarta ki nemi mmn Yusuf mai kayan mata yar mutan sokoto zaki samu ingantattun kayan mata masu tafiyar da hankalin maigida.......don neman Karin bayani 07069711327 ......💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋 𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤ 𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠 *🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥* Har ta kusa Fita palourn ta tuna da wayar Mommyn nan Nokia,Sehrish zata iya kira Kuma in har tabar wayar za'a samu matsala,Juyawa tayi ɗauke dashi ta koma saman Sofa ɗin ta ɗauki nokia ɗin ga wayar Junaid duka ta haɗasu Sae faman nishi takeyi,tana ƙoƙarin kama Hanya ta fuce,Hajiya Sarat ta bude Ƙopar A fujajan ta fito,waro ido waje Amrish tayi a wani irin Firgice ta watsa da gudu tamkar ba mutun ta ɗauko a kafaɗarta ba,Lokacin Da Hajiya Sarat ta ankare da Junaid dake sa6e a kafaɗar Amrish,Wani irin kukan Kura tayi da dukkan ƙarfinta ta watso a guje irin gudun nan na fitar hayyaci,Cikin Rashin sa'a tana Sanya ƙafarta saman benen,Tamkar an ja ƙafarta gaba ɗaya ta burkice,a jirkice ta sulalo daga saman benen,kanta yayi Mugun buguwa,Qugunta kuwa sae dai muce Allah ya kyauta, Amrish kuwa tsabar tsoro ko waiwaye batayi ba,lokacin data faɗo entry hall na gidan,Da gudu ta nufi gate,A lokacin baba mai gadi yana yin alwalar sallar Azhar da aka fara kira,Koda yayi arba da Su Amrish Baiyi tsammanin mutane bane,Wurgi yayi da butar hannunshi ya watsa da gudu zai shige ɗan ɗakinshi Ya ɗauko sandar shi,   Daƙyar Amrish ta iya buɗe baki tace"Baba Mai gadi ni ce,Dan Allah kataimake ni,Ka tsaida mana Taxi mu kaishi asibiti kada ya mutu,"dakatawa baba mai gadi Yayi a sukwane ya juyo yana kallonta,Sae lokacin Ya gane ta,kuma ya gane yaron nan ne na jiya ta ɗauko,ganin zai 6ata mata lokaci yasa ta fashe da kuka tana faɗin"Baba mai gadi kashe mu zatayi,In har bamu bar gidan nan ba,"   A hanzarce Baba mai gadi ya buɗe mata ƙopa suka fita,har zai tsaya ya tuna cewa Shine yaba Amrish Labarin Yaron,kenan shima Yana cikin hatsari,aikuwa da gudu ya bi bayan Amrish suka miƙi hanya suna neman Abun hawa,A ƙarshe daya ga ta jigata shi ya kar6i Junaid ya ɗaura shi a kafaɗarshi,Babban tashin hankalin tunda suka fito Unguwar babu kowa wayaam dama haka unguwannin ƴan gayun nan suke,Da ace irin geto ne da tuni jama'a sun agaza masu,ɗaiɗaikun mutanan dake wucewa duk wanda yayi arba dasu Amrish saiya watsa da gudu kamar sunga Aljanu,saboda ƙurar da ta 6ata masu jiki, Da iya ƙarfinta Na ƙarshe ta daddage ta miƙe,ɗago kan da zatayi keda Wuya haƙorinta ɗaya ya 6allo jaga jaga da jini,qugunta ya ruƙe sosai,wani irin azababben raɗaɗi,daƙyar ta samu ta fara jan jiki a galabaice ta nufi wayarta dake ajiye saman sofa,jikinta sai tsuma yake yi,daƙyar ta iya cire password ɗin wayar,Call log ta shiga ta kira wani layi da akayi mashi saving da ƙare kukanka,Daƙyar take magana saboda ciwon bakinta,   "Duk yarda za'ae karku bari yarinyar nan tabar cikin unguwar nan,Nasan zaiyi wuya su samu abun hawa,da ita da yaron Gawarsu kawai nakeso ku kawo mun...."tana magana tana goge zufar goshinta,ga wani irin huci dake fita abakinta,.    "Akwai ƙaramar nokia ɗita a hannunta,Zan tura maku Lambar wayar kuyi tracking ɗinta,"ta ƙarasa maganar tare da yin rejecting ɗin kiran,Gaba ɗaya Amrish ta ɗaure mata kai,saboda ta ɗauketa Shashasha,A irin rainon da tayi ma Amrish irin sangartattun nan ne,bata da wayau haka,Sai gashi yau ta bata mamaki,wai har tasan ma inda suka 6oye shi,koya akai duk tasan wannan? Lokacin da Su Amrish suka haura saman titi,suna neman abun hawa,duk mai motar da suka tsaida sai yaƙi tsayawa,Baiwar Allah duk tabi ta ruɗe gashi sam taƙi tunanin yarda nokia ɗin Hajiya sarat data ɗauko,kuma ta hanyar bin diddigin layinne kaɗai za'a san Location ɗin da suke, Suna cikin wannan tsayuwar,wata danƙareriyar mota ta shawo kwana da gudu,bata tsaya a ko'ina ba sai agabansu Amrish,mutuwar tsaye tayi lokacin,shi kanshi baba maigadi ya firgita da ganin motar,Jim kaɗan mamallakin Motar ya fito jikinshi sanye da fararen kaya hatta takalmanshi,Facemask ɗin fuskarshi Ya hana Amrish ta gane shi, Yayi mamakin ganinsu cikin wannan halin,bai tsaya tambayarsu Lafiya ba Kawai ya buɗe masu bayan motar,badon ta yarda dashi ba hakanan dai kawai suka shiga cikin Motar tunda ba yarda zasu yi,a back seat na motar ta shiga baba mai gadi ya jinginar da junaid a tsakiya kafin shima ya shiga,Mai motar ya fusgi motar da gudu,a dai dai Lokacin motoci guda uku masu blank tunted ƙirar Range rover suka bi bayan motar shi,da wani irin mahaukacin gudu mutumin ke tuƙa motarshi,yarda kasan filin ƴar tseral haka motocin nan suke gudu asaman titi, Amrish sai kuka takeyi tunda take a rayuwarta bata ta6a ganin tashin hankali ba irin na ranar,ba komai ya ƙara tsoratar da ita ba fa ce Harbin bindiga da taji a bayan motarsu,Ya salam!gashi hanyar da suka biyo babu ƴan sanda balle su samu taimako, Ɗaya daga cikin Ƴan ta'addan da suka biyosu wanda ya buɗe murfin motar ya miƙe a tsaye hannunshi ruƙe da irin wannan bingidar mai fitar da bullet kamar bomb,kwakkwaran Saiti Yayi ma Motarsu,Yana sakin Bullet ɗin mai girman gaske nan take Ya hau saman motarsu Ya fashe gaba ɗaya Wuta ta kama ci a bayan boot ɗin Motar,Hakan yasa motar ta dakata da tafiya,ganin sun ci nasara akansu yasa suka tsayar da motocinsu,Suka diddiro daga cikinta kusan Su takwas ne,Ƙirar jikinsu gwanin ban tsoro,babu ɗigon imani akan fuskarsu,kowanne hannunshi ruƙe da manyan makamai, Suna ƙarasowa gaban motar,ɗaya daga cikin samudawan nan ya damƙi murfin motar ya 6alleshi,hannu yakai tare da damƙo rigar mutumin dake acikin motar ya wurgoshi waje,basu tashi ankara ba,Sae da Mai tuƙin motar ya fito yana faman ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'una,Leƙa cikin motar sukayi Wayaam basu ga Amrish da yaron ba,Ashe Ba motarsu bace,Sunyi mistake Saboda mai wannan motar da suka kama iri ɗaya ce da motar da suka bi su Amrish, Da sauri Suka koma cikin motocinsu,A guje suka ja motar,Sunbar bayin Allah da aikin neman taimakon kashe masu wutar motarsu,don ma Allah yasa babu wanda ya raunata acikinsu, A 6angaren Su Amrish kuwa,mutumin dake tuƙa motarsu ne ya umarce ta data jefar da wayoyin hannunta gaba ɗayansu,nan take ta zuge glass ɗin motar ta wurgar dasu waje,Bayan ta jefar dasu sai ya Canza hanya da wani irin gudu yabar titin,Su kuma waɗannan miyagun da suka fara yin tracking ɗin Layin wayar Hajiya sarat na ƙaramar nokia ɗin da aka basu,Ta hanyar laptop ɗin dake a hannun wani kwararre acikinsu,Sae location ɗin ya dinga nuna masu hanyar da Amrish ta jefar da wayoyin,Nan fa suka miƙi hanyar cike da sa ran zasu kamasu,Lokacin da motarsu ƙare kukanka ta ƙarasa inda Location ɗin Ya basu,Sai suka tsayar da motocinsu,A zafafe suka fito suna waige waigen neman inda suka ajiye motarsu,Sai da suka gama shan wahalar nemansu a Area ɗin wurin abun takaici sai ga wayoyin sun tsinta yashe a ƙasa,Rai a matuƙar 6ace suka hanzarta komawa cikin motocinsu batare da sun ɗauki wayoyin ba,Nan fa suka ruɗe saboda hanyoyi ne guda uku,Ta hannun dama da kuma ta hannun hagu,Ga kuma wadda ta mike straight,To fa sun ruɗe a wannan lokacin,Basu san ta wace hanya su Amrish suka bi ba,A ƙarshe kawai suka raba motocinsu dama guda uku ne ɗaya tabi straight,ɗaya tabi Left ɗayar kuma tabi Right,Don sunsan Dole a ɗaya daga cikin hanyoyin suka bi, *Boss Bature* Wuraren ƙarfe 2 na rana, Wayar Ishaq ta soma ringing,A lokacin dawowarshi kenan daga wurin aiki,Buɗe mashi mota sergeant Yayi Ya fito daga cikin motar hannunshi ruƙe da wayarshi,picking call ɗin Yayi tare da kara wayar a kunnanshi, Fuskarshi ɗauke da murmushi ya soma magana"Mutanan Damaturu,Sai yau ake jinku"? On the other hand Hafsat tace"Wlh Daddy fushi nake dakai,you forgot about me,"   "Nima ae fushi nake dake,tunda na baro damaturu kin ƙara kirana ne?Ko irin Morning message ɗin nan babu ko,Yanzu da ace ban kiraki ba da shikenan bazaki neme ni ba,"ya ɗanyi maganar yana ɗaure fuska kamar tana agabanshi,    "Shikenan na ɗauki laifin,Am so sorry,Amma daddy meyasa ka canza Layinka?in na kira wancen Mtn ɗin bana samun shi"   "Kinga yanzu na dawo daga wurin aiki,Agajiye nake,bari na ɗan samu natsuwa I will call u later," A ɗan shagwa6e tace"dan Allah Daddy,idan ka huta kada ka manta ka kirani akwai maganar da nakeso nayi dakai,"   "Toh,"ya amsa tare da kashe kiran Ya nufi cikin gidan aranshi yana faɗin"yanzu haka saboda Mommynta ne yasa ta kira ni,lokacin daya shiga gidan ya yi mamakin yarda aka gyara mashi ko'ina fess,murmushi ya dinga saki don ya san cewa aikin hajjaju ne,wani irin ƙamshi ke tashi acikin palourn, Ga lafiyayyen abinci An jera mashi asaman dining,Dama da wata matsiyaciyar yunwa ya dawo,A hanzarce ya haura upstairs ya shige Bedroom ɗinshi,Bayan ya rage kayan jikinshi ya faɗa cikin toilet,Within mins Ya fito Ya kimtsa kanshi cikin jallabiya,Saukowa Downstairs Yayi kaitsaye ya nufi dining ya zauna,Da kanshi Yayi serving ɗin abincin ya zauna yana ci yana murmushi kamar wani zautacce,Sai da ya kammala cin abinci,tukunna ya koma saman Sofa ya zauna tare da aza ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya, Wayarshi ya ɗauko ya lalubo Layin Hafsat ya danna mata kira,Kamar jira takeyi ta ɗaga kiran,   "Daughter ina sauraronki!maganar menene kikeson Yi dani"? "Daddy dan Allah ka taimaka,Nasan zaiyi wuya ka fahimceni,wlh Mommy tana cikin mawuyacin hali,Ta zama abun tausayi,ta kira ni da wani layi jiya tana kuka tana rokona cewa inyi maka magana ka yafe mata,Ta gane kuskurenta,Rayuwarta ta wulakanta Daddy a gefen bishiya take kwana zaune ba bacci,dare da rana a wurin nan take Yini......." Tunkan Hafsat takai ƙarshen Maganarta,Ishaq ya katse ta"ke yanzu kin yarda da maganarta?Kodai kun haɗa baki ne da ita?   Da sauri hafsat tace"Wlh daddy da gaske take,Ae nasa ta ɗauko mun video ɗinta,Wayarma fa aronta takeyi don ta kiramu,Zan tura maka video ɗin ta whatsapp yanzu,zaka shaida abunda nake faɗa maka,"   Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"its okey,Am waiting for the video,"yana kai ƙarshen maganar ya katse kiran,Kafin Ya kunna wifi ɗinshi ya shiga whatsapp,Messages ne suka fara shigowa cikin wayar,can sai ga saƙon hafsat ya shigo, Chat ɗinsu Ya shiga,Anan ya samu video ɗin data tura mashi,yatsanshi yasa ya ɗan ta6a video ɗin nan take Ya soma loading,ƙura ido Ishaq yayi akan Screen ɗin wayar yana kallon video ɗin,    Bai ta6a tunanin zaiga laila a irin wannan ƙasƙantacciyar rayuwarba,a gefen bishiya take zaune,gefenta kwanon bara ne,ƙafarta ɗaya ta lalace babu kyan gani wani irin ruwa ke fita acikinta,Sae kuka takeyi tana magana   "Don Allah Ishaq ka taimaki rayuwata,ba don halina ba,dan Allah da manzonsa zakayi,Nasan nina jefa kaina cikin wannan halin,Ku kalli irin wurin da nake rayuwa,kowa ƙyamar taimakona yake yi,babu mai son zuwa wurina saboda warin da nake yi,"_   Saboda tsabar tashin hankali,Da sauri Ishaq ya kashe video ɗin tare da yin wurgi da wayar saman sofa ɗin, Jingina bayanshi Yayi ajikin kujerar,tabbas Yaji tausayinta amma abunda ya ɗaure mashi kai shine taya akai taje Enugu!Uban me yakaita?don a iya saninshi bata da wata alaƙa da garin,Ya jima a haka kafin Ya ɗauki wayar Ya sake kiran Hafsat,   Tana ɗaga kiran Yace"Naga video ɗin,wlh hafsat ba don zuciyar musulunci ba,babu abunda zaisa na taimaki Laila!ke bari in faɗa maki zan taimaketa ne kawai Saboda Allah!Taci albarkacinki hafsat!Zansa a ɗaukota akaita asibiti,Inyaso ko ƙafarce su cireta A maidata maiduguri,Amma ni bazan sake rayuwa da laila ba,"   Fashewa hafsat Tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,daƙyar ta samu ta tsagaita da yin kukan tace"Nagode sosai Daddy,koma miye laifinta ne,ita taja ma kanta,naji daɗi sosai Daddy Am really proud of u,"   "Yaushe zaki dawo gida!kinsan cewa hutun aikin da kika ɗauka ya qare ko"?   "Eh daddy,Ina nan ina shirin dawowa amma yanzu gidan bazaiyi mun daɗi ba,nafison na zauna a wurinsu Abba,tunda ga ƴan uwana acikin gidan inyaso sai ka nema mun transfer na dawo aiki a Abuja,"   "Idan kika koma Abuja,ni kuma fa?nikaɗai akeso inyi ta zama a kaduna "?   A ɗan shagwa6e hafsat tace"idan zaka ƙara aure,Sai in dawo nan," Murmushi ya saki anzo dai dai inda yafi so,   "Calm down ur mind,just ki dawo gida kawai,Cikin ƴan kwanakin nan Nima zanyi aure,"   Yana jiyo sautin dariyarta,alamar taji daɗin maganarshi,sun jima suna waya kafin suka Yi sallama, *Boss Bature* *AMANI* Tana kwance saman gadonta,Amal ta faɗo cikin ɗakin Hannunta ruƙe da wayarta,hawa saman gadon tayi har zuwa inda Amani ke kwance tana sharar bacci,Hannu tasa tana bubbuga ƙafarta,   "Aunty Amani!ki tashi ana kira," Daƙyar ta iya buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,sun ɗanyi jawur dasu,rai a6ace ta kalleta"Bana hanaki tashi na daga bacci ba in aka kira ni"?   Sunnar dakai Amal tayi"Am sorry,dama Aunty hayaam ce ta kira tana kuka......"hankali aɗan tashe Amani ta yunƙura tare da mikewa zaune tana faɗin"kuka kuma!Allah yasa lafiya,"ta ƙarasa maganar tare da kar6ar wayarta da Amal ke miƙo mata,   Call log ta shiga,Anan taga kiran da hayaam tayi mata,   Calling ɗin layin tayi,bayan Hayaam ta ɗaga kiran Amani ta kara wayar a kunnanta,tun kafin tayi sallama taji shessheƙar kukan Hayaam   "Subhanallahi!wai meke faruwa ne?hayaam ki buɗe baki kiyi magana mana,"a ɗan ruɗe tayi maganar,     "Kodai Wani ya rasu ne"? Sai lokacin Hayaam ta soma magana"Aunty amani muna cikin masifa!munga rayuwa,rayuwarmu ta wulaƙanta a idon jama'a......"anan hayaam ta kwashe dukkan abunda Ya faru bayan komawarsu maiduguri ta sanar da ita,   Saukowa Amani tayi daga saman gadon tana ambaton"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,.    "Allah yajiƙan Mammy,Allah ya gafarta mata zunubbanta,Amma banji daɗin irin mutuwar da tayi ba,ƙaddara ta riga fata,da kunsani tun farko baku barota ba,   Cikin shessheƙar kuka hayaam taci gaba da magana,   "Munaji muna gani,zama gidanmu ya gagaremu,Mutane sun ɗaura mana karan tsana,Yanzu haka a gidan Malam limam muke,matanshi sun tsanemu,suyi ta tseguminmu suna zaginmu,Abinci basu bamu sai in liman yana acikin gidan,Abra ma sai addu'a domin kuwa ta fara samun ta6in hankali,sai sambatu takeyi tana faɗin duk ita taja,Itace tayi silar mutuwar Mammy...."kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da ya cuyota,   Daƙyar Amani ta lallasheta"kuyi haƙuri ku rungumi ƙaddara,in sha Allah komai zai wuce,Yanzu nidai zanyi ƙoƙari wurin ganin na taimaka maku,Ko gidan ne a gyara maku shi,kafin Allah ya kawo maku mazajen aure,don kuwa yin auren shikaɗaine rufin asirinku,in ba haka ba mutane bazasu daina tsangwamarku ba,"   (Wlh matsalar mutananmu kenan,idan mutun Ya aikata zunubi arayuwarshi yazo ya yi nadama ya shiryu,Sai su dinga tseguminshi suna ƙyamatarshi,Shi kanshi Allah daya halicce mu yana son bayinsa waɗanda suka Tuba daga aikata zunubi,Amma wasu mutanan da ruƙo,shiyasa wasu ko sun shiryun daga baya sai su koma ruwa saboda mutane,Wannan babban kuskure ne saboda mutane ka koma kana aikata barna,Makomarka zaka duba,In zaka tuba dan Allah zakayi,Dan kuma kanka,ba don mutun ba,a karshe ina mai jan hankalinmu da mu kiyaye harshenmu don zai iya jefamu a halaka,aduk lokacin da wata mummunar kaddara ta fada ma wani muyi Addu'a mu nemi tsarin Allah kada mu rinka zundenshi don muma bamu fi karfin Allah ya jarabemu ba,Allah ubangiji ya rabamu da mummunan kaddara yasa mufi karfin zukatanmu,Amin ) Sosai Hayaam ta shiga yi mata godiya,kafin daga bisani Su kayi sallama, *Boss Bature* Wuraren ƙarfe 6 na marece,Sehrish na kwance saman gadonsu abun duniya ya isheta,duk ta shiga damuwa saboda rashin samun kwakkwarar hujjar da zasu kama Azmee,tana cikin wannan zancen zucin taji an banko kopar ɗakin,A firgice takai idanuwanta kan mai shigowa,Jahad ce ta faɗo ɗakin fuskarta sharkaf da hawaye,a ruɗe Sehrish ta shiga tambayarta Lafiya,   "Bakisan meke faruwa ba,Ga Abba can ya yanke jiki ya faɗi rai hannun Allah,"jin wannan maganar yasa Sehrish ta sauko daga saman gadon jikinta na kerma ta nufi hanyar fita ɗakin,atare da jahad suka fita, Abunda ya faru,Alex na zaune gefen gado tana jiran fitowarshi daga toilet,tun da ya shiga shiru bai fito ba,tun tana sa ran fitowarshi harta fara tunanin ko lafiya kusan Awa ɗaya da rabi yana acikin toilet ɗin nan,Miƙewa tayi ta nufi toilet ɗin tasa hannu ta kwankwasa ƙopar"Abban Junaid!"ta kira sunanshi da ƙarfi,Shiru bai amsa mata ba,a ƙarshe dai ta yanke shawarar shiga ciki,tana tura ƙopa ta same shi kwance saman tiles,idanuwanshi sun jirkice,jikinshi sai kerma yake yi,Fasa ƙara Mommy tayi anan ta zube tana jijjigashi,Ganin cewa dagaske fa baya acikin hayyacinshi yasa ta miƙe da gudu ta fito daga ɗakin tana kuka, A lokacin Abusufyan da abu suna zaune a main palour tare dasu Hosana da Jahad,Tun daga kan yarda ta faɗo falon Yasa su miƙewa suna tambayar lafiya,Kasa buɗe baki tayi sai dai nuna masu hanyar bedroom ɗinshi da tayi duk tabi ta ruɗe,da gudun gaske Abusufyan ya nufi ɗakin tare da abu,suna shiga ciki dama ƙopar toilet ɗin abuɗe Mommy tabarta,nan suka sameshi cikin mawuyacin hali,sunyi matuƙar girgiza,Cuccuboshi Abusufyan yayi ya fito dashi daga cikin toilet ɗin,Ya janyoshi zuwa saman gadon ya kwantar dashi,jiki na rawa Ya curo wayarshi saboda ruɗu daƙyar ya iya lalubo Layin Sgr ya danna mashi Kira,Sai daya bi kowannansu Ya sanar dashi halin da Mahaifinsu ke ciki, A lokacin dasu Sehrish suka faɗo falon Ya yi dai dai da shigowar Omar da Sgr,da gudun gaske suka shigo kaitsaye suka nufi bedroom ɗin Abbansu,wucewarsu keda wuya Kanal yousouf ya faɗo falon da gudu shima Ya wuce part ɗin,gaba ɗaya sai da matasan gidan suka hallara a ɗakin,wasu tuni sun fara zubar da hawaye,tsoransu kada su rasa mahaifinsu a wannan halin da suke ciki,sae faman ambaton innalillahi wa'inna ilaihirraji'un suke yi, Fawan dasu twins kuwa tuni sun fara kuka kamar wasu ƙananun yara,   "Addu'a zakuyi mashi ba kuka ba,in sha Allah zai samu lafiya,"acewar Abusufyan shi kanshi dauriya kawai yake yi,don kada suga rauninshi,hakan zai ƙara tayar masu da hankali,    yanke shawarar kaishi Asibiti suka yi,Sgr ne ya ɗauke shi asaman kafaɗarshi,Sauran suka bi bayanshi,   Suna fitowa entry hall ɗin gidan,da gudun gaske armstrong ya buɗe mashi mota ya kwantar da Abbansu aciki,Sannan ya bude mashi front seat ya zauna,Jan motar yayi da gudun gaske motar Marshal tabi bayansu,Motocinsu Kanal yousouf suka rufa masu baya,hada Oummansu Sehrish aka tafi asibitin a motar fawan ta zauna tare da Jahad da Hosana,Mommynsu Junaid kuwa tana a motarsu Abusufyan sai lallashinta Yake yi,duk ta shiga damuwa alokacin motocinsu suka fita daga babban gate ɗin gidan,mutun uku aka bari a gidan Aunty Azmee dake kumshe a ɗakinta,Sae Haroon dake kulle a medical room dinsu, Sehrish bata samu tabisu ba,daga komawa ta ɗauko mayafinta sai dai tajiyo tashin motocinsu,kamar tayi hauka lokacin da ta fito waje bata samu motar ɗaya daga cikinsu ba,anan ta zuƙunna gaban ƙopar palourn tana kuka,ga tsoron shiga gidan da takeyi, Da wata irin jiniya motocinsu suka hau saman titi a jere,Lokacin da suka ƙaraso Katafaren Asibitin Sgr,Sai suka tsaida jiniyar,a hanzarce bayan sunyi parking ɗin motocin nasu,Sgr ya fito Ya ɗauki Abbansu,sauran ma suka fito gaba ɗaya suka wuce cikin asibitin,Zo kaga taron nurses da likitoci,Ai tunda suka ji isowar Sgr kuma suka ji cewa Mahaifinshi ne baida lafiya,nan fa sukayi dandazo domin duba lafiyarshi, A wani katafaren ɗaki suka kwantar dashi,kusan likitoci shida ne akanshi daga cikinsu hada Doctor Emran, Sgr baisamu shiga ba,saboda a halin da yake ciki a yanzu bazai iya duba Abbansu ba,yana cikin matsananciyar damuwa saboda yasan dalilin ciwon Abban nasu,dama yace su fara ƙirgen kwanakin mutuwarshi,in har basu dawo mashi da yaronshi ba, A saman waiting seat suka zazzauna suna jiran tsammani,Omar da Sgr suna a tsaye,Kowa ka kalli fuskarshi gwanin ban tausayi,   "I can't forgive my self,idan har Daddy ya mutu silar 6oye mashi mutuwar Junaid da mu kayi,"Ya ƙarasa maganar yayin da idanuwanshi suka cicciko tab da hawaye,   Ruƙo hannunshi Omar yayi"bakai kaɗai ba Rafayet,nima bazan yafewa kaina ba,in har muka rasa shi,wlh i ave regretted already,Da mun sani tunfarko mun sanar dashi gaskiya kawae tunda dama gudun hakan yasa muka 6oye mashi,"gaba ɗaya duk sun sha jinin jikinsu, "Dan Allah kukan ya isa haka,twins,fawan da irfan,in na sake jin shessheƙar kukan wani acikinku wlh zaku koma gida ne,"kanal yousouf ne keyi masu faɗa,.    "Sai kace ba musulmai ba!maimakon ku tayashi da addu'a amma kun dage sai kuka kukeyi,"ya ƙarasa maganar tare da jan guntun tsoki,idanuwanshi cike tab da kwalla,   Abu kuwa sai faman lallashin Mommy takeyi,ganin yadda take ta shar6ar kuka,   Abusufyan ne yace"don Allah Aunty kidaina,kina ƙara tayar masu da hankalinsu,keda yakamata ace kina lallashinsu,"hannu tasa tana share hawayen fuskarta,juriyarce bazata iya ba,ita kaɗai tasan yarda take ji acikin zuciyarta, Fitowa Doctor emran yayi daga cikin ɗakin da aka kwantar da Abbansu,Aikuwa da sauri suka tunkareshi,kowa yana tambayar ya jikin nashi,   "Ku kwantar da hankalinku,Yana samun sauƙi,Addu'ar ku kawai yake buƙata,"yakai ƙarshen maganar tare da aza idanuwanshi kansu Sgr da Marshal"ina son ganinku a office,"   Tunda suka ji haka sai jikinsu ya ƙara yin lakwas,gaba Dr emran Yayi suka bi bayanshi,har izuwa Office ɗinshi,Wuri ya samu ya zauna,kafin suma suka zauna suna fuskantarshi,   A tsanake ya soma yi masu bayani"nasan kunsan meke damun mahaifinku,damuwa ce akan rashin Junaid,Yanzu haka dana baro ɗakin,Sambatu yake yi yana ambaton sunan shi,"dakatawa ya ɗan yi da bayani yana kallonsu,jikinsu sai tsuma Yake yi,   "Jinin shi ne ya hau sosae,Ga kuma Ciwon zuciya dake barazanar kamashi..."   Tunkan emran yakai ƙarshen maganar,Omar ya dafe kai jikinshi na kerma,jikinsu Ya gama mutuwa,   "Yanzu ya zamuyi kenan?menene solution"?Sgr ne yayi tambayar,   "Akwai matsala fa,saboda ya ƙwallafa ranshi akan son yaron,Idan har ba ganinshi Yayi ba,tofa sai dai abishi da addu'a,"   "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"miƙewa Sgr yayi da sauri ya fice daga Office ɗin,gaba ɗaya sun rasa inda zasu tsoma ransu suji daɗi, Miƙewa Sehrish tayi daga zuƙunnan da take abakin ƙopar palourn,Hannu ta zura acikin aljihun rigarta,ta curo wayarta don ta kira Jahad taji Ya jikin Abban nasu,   Tana kunna wayar,ta shiga Call log anan ta samu missed calls da baƙuwar number,har kusan sau 10 aka kira,Batasan number ɗin wanene ba,Har jaraba kiran Layin tayi wayar nata ringing ba'a ɗaga ba,   Bayan kiran ya katse ne,ta lura da message ɗin da aka turo mata,Da sauri ta buɗe saƙon ta soma karanta shi kamar haka, __Sehrish na kira layinki baki ɗaga ba,Amrish ce inason magana dake game da ɗan uwan nan naki,dan Allah idan kinga saƙon nan ki kira ni_   Abun ya ɗaure mata kai,tunani ta shiga yi wani ɗan uwanta ne Amrish ke magana akai,sake kiran Layin tayi wayar ta dinga ringing amma ba'a ɗaga ba,   Katse kiran tayi,tana ƙoƙarin juyawa ta koma cikin gidan kira ya shigo layinta da baƙuwar number,da sauri ta ɗaga kiran tare da kara wayar a kunnanta,tunkafin tayi sallama muryar Amrish ta katse mata hanzarinta,   "Sehrish kina ina ne!ina ta kiran Layin wayarki amma baki ɗaga ba,magana ce akan Junaid na tura maki Address ta message,kibar komai kikeyi kizo ki same mu"tana kai ƙarshen maganar ta katse kiran,   Wani irin faɗuwar gaba Sehrish taji,Abun ya matukar ɗaure mata kai,musamman data ambaci sunan Junaid,   Hannunta na kerma ta shiga duba message ɗin da aka turo mata,kwatancen inda zata same su ne, Tarasa ya zatayi,ita dai ba mota gareta ba,gashi babu wanda ya rage acikin gidan balle ya kaita,kama hanya tayi ta miƙi titin da zai sadaka da babban gate ɗin gidan,Sae faman zumbula sauri take yi,Sai da tasha wahalar zuwa babban gate ɗin,Sojojin dake tsaron gidan suka hanata fita,kamar ta fashe da kuka, A dole ta shiga kiran layin matasan gidan,Duk wanda ta kira bai ɗagawa,har Abusufyan ta kira shima bai ɗaga kiran ba,   Sai da ƙyar ta samu Hosana ta ɗaga kiranta,da sauri ta kara wayar a kunnanta,   "Hosana Ya jikin Abban"?   "Nima bansani ba,Sun shiga dashi ciki,"   "Dan Allah idan akwai wani kusa ki bashi wayar,"   "To"ta amsa mata,jim kaɗan taji muryar Kanal yousouf,   Sai da ta fara tambayarshi jikin Abban nasu,Ya sanar da ita cewa da sauki,tukunna tace"Gani nan zan fito gida an hanani,dan Allah ka taimaka kasa su barni na fita,nima asibitin zanzo," "Ki basu wayar,"Cire wayar tayi daga kunnanta ta miƙa ma ɗaya daga cikin sojojin,ya kar6a su kayi magana dashi sannan ya miƙa mata wayar,"Zaki iya tafiya,amma yace kada abarki ki fita ke kaɗai,don haka wani daga cikinmu zai ɗaukeki a mota ku fita,"   Ba ƙaramin daɗi taji ba,dama ƙarfin hali ne kawai,ko kuɗin abun hawa bata dashi, Anan ta tsaya,wani sergeant ya ɗauko mota ta buɗe ta shiga ciki ya tashi motar,saida suka hau saman titi sannan yace"Madam ina zuwa"?   Karanto mashi Address ɗin wurin tayi kamar yadda Amrish ta rubuto mata a saƙon, Wani private hospital ne suka shiga,sojan ya fito ya buɗe mata ƙopa ta fito daga ciki,a bakin ƙopar shiga ciki ta samu Amrish a tsaye hannunta ruƙe da waya,wani irin farin ciki ne ya lullu6e Sehrish da gudun gaske ta nufeta,rungume juna sukayi nan take Amrish ta fashe da kuka,   Ɗago da ita Sehrish tayi tana tambayarta lafiya,   "Amrish dama kina nan?layinki kona kira bana samu,meya sameki ne?me kike yi a asibitin nan ne"?   Cikin shessheƙar kuka Amrish tace"mu shiga daga ciki ki gane ma idanuwanki,"   Ta ƙarasa maganar tare da janyo hannun Sehrish suka shiga asibitin,A A&E aka kwantar dashi,a bakin ƙopar ɗakin Sukayi kici6us da Ya Mu'allim malamin da take ta nema,   Cike da mamaki ta ambaci sunanshi"Ya mu'allim,"fuskarshi da alamun damuwa atare da ita,Ya amsa mata"Na'am,kina ta nemana ko"? Jinjina mashi kai tayi alamar eh   "Naga saƙon da kika turomin,idan muka samu natsuwa zamuyi magana,Yanzu dai ga ɗan uwanki can kije ki duba jikinshi,"   Gabanta ne ya faɗi rasss!,kawar da idanuwanta tayi daga kallon fuskar Ya mu'allim ta mayar da idanuwanta kan ƙopar ɗakin,mutun ta hango kwance an sanya mashi oxygen a hancinshi,yayin da hannunshi ke sanye da robar ƙarin jini,zuciyarta na harbawa a haka ta nufi cikin ɗakin,lokacin data ƙarasa gaban gadon tayi arba da fuskar Junaid,Sai ta yanke jiki ta faɗi a sume....... Shigowa Cikin ɗakin Ya mu'allim yayi tare da Amrish,ruwan dake ajiye saman drawer din dake gefen gadon Ya ɗauka,Ya cire murfin ya tarfa ruwan a tafin hannunshi Ya watsa mata akan fuskarta,Nan take ta farfaɗo tana faman Sauke ajiyar zuciya,Yayin da take ambaton Sunan Junaid abakinta,Miƙawa tayi agaban gadon ta zube saman guiwowinta,kamar a mafarki haka take ganin Junaid,bazata Iya jurewa ba,fashewa tayi da matsanancin kuka yayin da take kallonshi,Dama sai da ranta ya bata cewa Junaid bai mutu ba,Yana araye,Ashe dagaske ne,tasha kuka ta gode ma Allah,Cikin shessheƙar kuka ta soma magana tana kallon Ya mu'alim da amrish dake a tsaye, "Taya akai junaid daya mutu ya dawo?a ina kuka same shi,A iya saninmu junaid yayi hatsarin mota Ya ƙone ƙurmus"   Jin wannan maganar yasa Ya mu'allim da Amrish suka kalli Junaid,har suna haɗa baki wurin cewa"Junaid Yayi hatsarin mota'?   Jinjina kai Sehrish tayi"Babbar motace tabi takan Motarsu,Wuta ta kamaci,ba'a samu komai daga sassan jikinshi ba,wannan Shi ne abunda muka sani a game dashi....."tana kuka ta Zayyana masu Komai daya faru har 6oye mutuwar junaid dasu Marshal Su kayi,Da kuma Halin da abbansu ke ciki na rashinsa,.    Amrish tasha kuka hada majina,Shi kanshi Ya mu'allim jurewa kawai yake yi,rashin imanin Yayi yawa   "In sha Allah komai Yazo ƙarshe,duk wanda keda sa hannu a wurin cutar da family ɗinku,Zai gane kuskurenshi,don wannan karan da shirina nazo,"Babu wasa a fuskarshi yayi maganar,   "Dan Allah ku faɗamun ya akai kuka samu junaid"?tayi maganar yayin da take share hawayen fuskarta,   Anan Amrish ta kwashe dukkan abunda Ya faru daga farko har ƙarshe Miƙewa Sehrish tayi tana kuka,Ta rungume amrish tana Yi mata godiya,bawan Allah ashe shine Yake tura mana saƙo da layinki,muka kasa gane wanene,da yake ni ina da numberki,Shiyasa saƙon Ya bayyana da sunanki,nayi tunanin ko kin yada wayarki ne,Ashe junaid ne ya ɗauketa,Bawan Allah,wlh da ace zan iya mayar da ciwonshi jikina da nayi hakan,junaid bai ta6a shan wahala rayuwarba,Sae wannan karan da ƙaddara ta rutsa shi....."   "Mu gode ma Allah junaid yana raye,duk yarda suka so su cutar dashi,basu ci nasara akanshi ba,domin kuwa junaid kainuwa ne dashen Allah,badai mutun ba,lokacin da muka kawo shi asibitin nan,jinin jikinshi Yayi ƙanƙanta,cikin sa'a likita ya gwada jinina,kuma aka dace yayi dai dai da nashi,gashi nan ana ƙara mashi,Amma yana bukatar jini sosai," *ƙarin Bayani* Abunda ya faru lokacin da Sehrish ta tura saƙonnin nan cike da saran Ya mu'allim zai gani,malaman da ta tura ma saƙon daga ciki akwai numbar Ya mu'alim,Yaga Saƙonta saƙonta sai kuma Aka kirashi a waya ana sanar dashi cewa ɗalibarsa na nemanshi,Sauran malaman data tura ma sakone suka sanar dashi,An turo masu saƙo ana nemanshi,Wannan dalilin ne yasa Ya mu'alimm Ya shirya zuwa gidan,tun lokacin baya ya ta6a zuwa gidan security guards ɗin gidan suka hanashi wuce wa,baisamu shiga ba a wannan lokacin,Sai yau daya samu saƙonnin nemanshi da sehrish keyi,Shi ne ya yanke shawarar Ya fara zuwa gidansu Amrish don tayi mashi jagora zuwa gidansu sehrish ɗin su tafi atare,Da yake ya ta6a zuwa gidansu Amrish lokacin da tayi jinya,kuma cikin sa'a ya zo adaidai lokacin da suke buƙatar taimako,Kunji yarda akai Allah ya hadasu dashi Har ya ɗauke su, Saboda halin da Abban junaid ke ciki,Ya mu'allim Ya basu shawarar su ɗauki junaid su koma dashi Can Sgr hospital ɗin,Don A haɗashi da mahaifinshi in yaso sai acigaba da jinyarshi acan asibitin,Sai da suka tsaya Jinin ya ƙare sannan Likita ya sallamesu,Suka ɗauke shi a back seat ɗin motar Ya mu'alim Aka shigar da junaid,Sehrish ta shiga ta ruƙoshi ajikinta,bawan Allah ya zama tamkar lagwanin filita jikin sae kerma Yake yi sam baya acikin hayyacinshi,Mazaunin driver Ya mu'allim Ya shiga,Amrish ta zauna gefenshi,Ya tashi motar,a tsanake yake driving ɗinsu,Amrish sae faman zabga murmushi take yi,burinta Ya cika,junaid zai koma wurin ƴan uwanshi,Sehrish kuwa ba'a magana,Bakinta yaƙi rufuwa,Kamar wadda akayi ma Albishir da gidan Aljanna,Tsabar farin ciki ne kawai,Ta ƙankame junaid ajikinta kamar ta mayar dashi cikin cikinta,Saboda tsabar ƙaunar da take yi ma ɗan uwanta,A ranta tana ayyana irin farin cikin dasu Babban Yaya zasu yi idan suka ga junaid bai mutu ba, Slowly motarsu ta ƙaraso cikin katafaren asibitin SGR................ *dakwai yiyuwar littafin Abban Sojoji yakai farkon march,Ba kamar yarda nace ba ƙarshen February,Amma idan kuna son ayi maku after 3 years,kuyi mun magana,sai mu katse shi,ra'ayinku nakeson ji,littafin yazo ƙarshe masu tunanin zai kai azumi,Aniyarku tabi ku😂* *masu son karanta Littafin Abban Sojoji su tuntu6i layina,Message za'a tura mun ta whatsapp banda phone call*