TRIPLET'S💞 💔THE STRUGGLE💔 Dasunan Allah mai Rahma mai jin kai tsira da Amin sukara tabbata ga manzon mu manzon Rahma Annabi Muhammad SAW farkon ƙaga karshen aika, Allah ina mai godiya daka bani iko da dama na kammala book 1 na littafin nan Alhadulillah Alhadulillah, ya Allah ka bani ikon kammala littafin gaba ɗaya lafiya, ya Allah kasa sakon da nake son isarwa ya isa in da nake son isarwa, ya Allah ka yafe mana kura kuran mu Amin 🤲 Yanzu wasan zai fara muje zuwha, please masu taya ni sharing yanzu kam ya isa haka dan mun gama Free wannan paid ne, nagode da tayani sharing na free da mukayi Allah ya bar zumunci!!!. Duk wanda ya karatamin book na bai biyani hakkina ba na bar mutun da Allah shi zai saka min!!!. Ya Ubangiji bamu da wayo bamu da dabara mun miƙa wuya a gareka ya Allah ka kawowa kasan 🇳🇬 mu zaman lafiya, babu wani mahaluki da ya isa ya bawa kasar 🇳🇬 mu zaman lafiya sai kai ya Ubangijin, dan karfi ikon ka ya Allah dan isar ka da izzan ka ya Allah ka bamu zaman lafiya da kwantatciyar hankali, Allah ka karemu da kariyar ka, Allah ka bawa duk wasarasa lafiya na gida dana asibiti lafiya, Allah ka buɗawa duk wani mai neman halak ɗin sa hanyar samun sa hagun sa da daman sa gaban sa da bayan sa, ya Allah ka bamu arziki mai albarka mai amfani O Allah, guide me along with those whom You have guided, pardon me along with those whom You have pardoned, be an ally to me along with those whom You are an ally to and bless for me that which You have bestowed. Protect me from the evil You have decreed for verily You decree and none can decree over You. For surety, he whom You show allegiance to is never abased and he whom You take as an enemy is never honoured and mighty. O our Lord, Blessed and Exalted are You. # BOOK 2📚📙✍️ 💔💔Episode 1-2💔💔 Kukan mai Tsananin Lucky, Winston, Copper, wato karnukan Michael, sosai suke haushi suna ɗaga murya wadda sai da ya bawa kowa dake cikin gidan mamaki, Romeo yana can part nasa yana aiki yayin da dad kuma ya fita ya je dan ya bawa Pasto agajin gaggawa karya mutu, Kukan su Copper ba karamin razana su Tga sukayi ba dan basu taɓa jin su suna irin wannan kuka mai sauti haka ba, Tga da kan sa ya shiga cikin ɗakin nasu yayi, yayi amma sunki yin shiru, ya rasa me matsalar su, ya rasa ya zai yi da su dan shi ba wani damuwa da kare yayi ba bare yasan halayen su. Romeo yana aiki a laptop amma zuciyar sa na bugawa da karfi sanna kukan da su Copper suke ya dame sa, dan har ga Allah basu taɓa kuka haka ba, banza yayi dasu dan bai kawo komai a rasan saba, ya zaci Michael ne ya musu laifi, bugun zuciyar nasa ma ya dangan ta da James, ci-gaba yayi da aikin sa yana ciza laɓɓan sa. Da gudun gaske Brady ya shigo cikin ɗaki, kai tsaye jikin Romeo ya nufa yana ta tattaɓa shi da bakin sa yana jan shi alamar yazo ya gani, ganin Brady a haka yasa Romeo ya san ba lafiya ba, dan Brady ma baya shiga harkan kowa har su Copper baya shiga karkan su, haka Romeo ya koya masa, idan kaga Brady yayi wani yunkuri a kan abu tofa abun abun dubawa ne. Miƙewa Romeo yayi yabi bayan Brady suka nufi waje dan yaje yaga menene ke faruwa. Tsaye cirko cirko ya isko su Tga a tsakar gidan sunyi shiru kawai sun zabawa kofar ɗakin su lucky ido, ganin Romeo yasa suka ja baya duk suka sha jinin jikin su, suka nitsu tsit. Kai tsaye cikin ɗakin su lucky Romeo ya nufa, yana shiga suka fara tsalle suna kama jikin sa suna daka haushi mai bala'i sauti, kasan cewar Romeo ya musu farin sani, dan yanzu a kalla su lucky sun kai 12 years tare dasu, tun suna jarirai Michael ya sayo su, su huɗu Brady shine babba sai Lucky sai Copper da Winston, kasan cewar Brady yafi girma kuma yafi kyau yasa Romeo ya ɗauke shi ya dawo nashi ya barwa Michael su copper, to karnukan basa kuka haka kawai sai da dalili mai karfi ya san halin su sosai. A sukwane Romeo ya juyo ya dubi su Tga "Where is Michael?" Yar waige waige suka farayi alamar suna neman Michael ɗin, sai lokacin suka tuna da Michael ɗin, da sauri Romeo ya fito daga cikin ɗakin, lucky na kokarin bin sa yayi saurin rufe kofar yana faɗin "I said whare is Michael? What happened to him?" Lokaci guda tsoro ya bayyana a kan fuskar kowa dake wajen, dan sunji Romeo yace me ya faru da Michael, ina kuma yake, dama kuma tun da sukaji yadda su copper ke wannan daka haushi mai razana kwakwalwar suka san ba lafiya ba, sai dai basu yi tunani wani abune ya faru da Michael ba. Romeo ya san su Copper ba zasu yi kuka haka kawai ba, dan karnuka daban suke da ɗan adam suna da kaifin gani mai nisa, idon su na ganin abun da ɗan adam baya gani. Da sauri Romeo ya koma cikin gida, part ɗin Michael ya nufa dan ya duba shi, ko da yaje part ɗin Michael Michael ɗin baya nan, part nasa ya koma ya ɗauki wayar sa ya kira layin Michael, tana ta ringing amma bai ɗauka ba. Ɗauko laptop nasa yayi ya shigar da number Michael ɗin dan yabi diddigin ina Michael ɗin yake Yana shigar da number ta nuna masa wayar Michael na *Medstar Washington hospital center* kara zaro dara daran blue eyes nasa yayi har sai da suka kara kyalli sosai, shi dai yasan yanzun nan ba jimawa Michael na gidan nan har ya mare sa, to me ya kai sa hospital kuma. A sukwane ya ajiye laptop ɗin ya ɗauki wayar sa ya fice daga bedroom ɗin. Yana fitowa ya bawa sojojin sa umarni a kan su tashi motoncin zuwa *Medstar Washington hospital center* ji kake dip, dip, dip, jibga jibgan sojojin nan na gudu suka haye saman bayan motoncin su, shi kuma Romeo farar motar sa kirar *Bugatti La voiture* ya shiga Kamar ɗazun jerawa sukayi cikin dankara dankaran motoncin su sukayi layi a jere suka bar gidan, sai mamakin meke faruwa su Tga suke suna son sanin abun dake faruwa amma ba halin tambayar Romeo domin babu dama ba mai karfin zuciyar tinkarar sa dan yadda sukaga wannan fusataccen fuskar nasa abun ba'a magana. Suna isa asibitin jibga jibgan sojojin nan suka diddiro kasa daga bayan motoncin su, a guje suka je suka kewaye gaba ɗaya asibitin ga hannun su riƙe da manya manyan makamai masu numfashi wadda kusan kare dangi za'a kira jibga jibgan makaman nasu. cikin sauri lion ya fito ya nufi cikin hospital ɗin jinga jibgan sojoji 6 suka take masa baya, sai furzar da iska mai bala'i zafi yake daga bakin sa, yana wani huci. Duk wanda ya hango lion daga nesa a cikin asibitin tofa a sukwane yake canza hanya yabi wani wajen saboda tsoro ga fuskokin wayan nan fusatattun sojijin nan masu razanar da mai rai Kai tsaye office ɗin babban dr suka wuce, duk wani hallitar dake cikin asibitin nan wanda yaga shigowar motoncin su lion sai da ya razana kowa ya nitsu ya ɓoye kan sa a ɗakin sa, ji kake tsit duk girman asibitin kowa ya nitsu suna tsoron ruwan wuta. Kai tsaye ɗakin da Michael ke kwance dr yayiwa su lion jagora, yana kwance saman gado bawan Allah fuskar nan tasa tayi wani fayau da ita, har wani yellow yayi, fuskar nasa ta kunbura sosai, ga jinin sa na malala kamar fanfo har kasan gadon da yake kwance a kai, kallo ɗaya zaka masa ka san babu rai a jikin sa. Gaban gadon Romeo yaje ya tsaya yana kallon fuskar Michael ɗin, ganin abun yake kamar a mafarki kamar ba gaskiya bane, lokaci guda idon lion ta rikiɗe tayi jawur kamar jini, har wani mimmiƙewa zara zaran eyelashes nasa suke saboda tashin hankali da ya shiga, zuciyar sa dukan uku uku take ji yake kamar ya fasa ihu ko zai samu sauki a ransa, gaba ɗaya jijiyoyin dake jikin sa sai da suka mimmiƙe, jikin sa har wani tsuma yake saboda ɓacin rai da tashin hankali, lokaci guda ya sauya kamar ba shi ba, wasu zara zaran jijiyoyi ne suka bayyana a wuyar sa, ga wani zufan wahala dake karyo masa a gefe da gefen kunnen sa, zuciyar na tafasa kamar an ɗaurata saman wuta mai bala'i ci da zafi. Cikin kankanin lokaci labarin mutuwar Micheal ta karaɗe ko ina a birnin Washington DC lungu da sako, ba karamin girgiza Washington DC tayi ba Ba iya lion ne kawai ya girgiza ba, ba gaba ɗaya birnin Washington DC sai da ta girgiza da mutuwar ɗaya daga cikin family William jacop, cikin family ma, ɗaya daga cikin Triplets tashin hankali, lungu da sako ko ina sai da ya girgiza saboda sakon mutuwar Michael ya kewaye ko ina cikin kankanin lokaci yan jarida da gidan Tv suka baza zancen, duk wani harka a cikin birnin sai da ya dakata cak, komai ya tsaya cak, duk kasuwanni an rufe su, shugaban kasa da kan sa ya fito yayi magana a kan a dakatar da komai a cikin kasan, saboda The general of the army yayi rashin Triplets nasa ɗaya, duk wasu makaratu a ranar sai da aka rufe su, duk yadda Washington DC keda girma ga harka ranar tsit kake ji, zaka iya kwanciya a kan titin ka jima mota bata zo ta wuce ba bare ma ta bugeka saboda komai da aka dakatar, Umarni Romeo ya bada da a kashe duk wani Tv dake gidan su kuma Tga ya karɓa wayar dake hannun daddy dan karya samu labari, shima zai iya mutuwa idan naji labarin kai tsaye dole sai a hankali za'a faɗa masa, haka kuwa akayi duk wani Tv dasu laptops dake cikin gidan William jacop sai da aka kashe su, Tga ne yaje ya karɓi wayar hannun daddy cikin dabara ba tare da daddy ya kawo wani zargi a ran saba, sosai Tga yayi kuka kamar ransa zai fita, Jay da John kam basu samu labari ba tukun nan, Tga ne kawai ya sani shima dan yaje ya karɓa wayar dad kuma ya kashe su Tv dake gidan yasa Romeo ya sanar masa. Romeo ya kasa bari ayi wa Michael sutura ya zauna ya zuba masa ido, ga idon nasa yau abun tsoro saboda riƙiɗewa da sukayi, ya kasa wani kataɓus Manya manyan ministoci da yan majalisu governors duk sun hallara a cikin asibitin amma babu wanda ya samu damar shiga wajen da su Romeo suke, asibiti ya cika makil har bakin titin waje motoci ne na manya manyan masu faɗa a ji a kasar tare da security su. Shugaban kasa tare da wani ɗan jarida ɗaya wadda ya kasan ce kanin sa ne suka samu daman shiga wajen su Romeo nan ma sai da Romeo ya bada izinin a barsu su shigo. Ɗan jaridan da ya shigo tare da sugaban kasa ne ya tinkari in da Romeo ke zaune da camera a hannun sa, a tunanin sa tun da tare suka zo da shugaban kasa ba wani abu, Romeo ya duker da kan sa kasa, dan bai son ɗago idon sa, in ya ɗago ido mai ƙaramin zuciya ya gansa zai iya mutuwa, bai ankara ba yaji alamar ɗaukan hoto, kafin ya ɗago kai yaji murya ɗan jaridan yana cewa "Sir ko zaka iya gaya mana wani irin hali ka tsinci kanka lokacin da kaga ɗan uwan ka kwance cikin jinin nan?" Tashin hankali shugaban kasa yana ganin katoɓarar da ɗan jaridan sa yayi sai ya ja baya kaɗan, yana tausayawa ɗan jaridan yasan duk da cewa ɗan jaridan kanin sane na jini tofa lion ba zai raga masa ba, kuma kafin su zo sai da ya ja kunnen kanin nasa a kan karya kuskura yayiwa lion wata tambaya ya ɗauki hoto kawai tun da daman hoto yace zai je ya ɗauka. Shugaban kasa yayi nisa cikin tunanin da yake bai ankara ba sai ganin kanin sa yayi a saman iska yana reto yana kokarin faɗuwa kasa ga cameran sa can gefe ta ragargaje, abun mamaki kuma abun da ya kullewa shugaban kasa kai shine ga dai Romeo yana zaune kamar yadda yake bai motsa ba, kenan to waye ya daki kanin sa har yayi sama haka, wannan tambaya ce da bashi da amsar ta Abun da ya faru lokacin da ɗan jaridan yayiwa Romeo tambayar, Romeo ya ɗago kai da ido kawai ya kalli wayan nan jibga jibgan sojojin sune suka lillisa ɗan jaridan suka masa pata pata suka ragargaje cameran. Allah sarki ɗan jarida kanin shugaban kasa, shi yazo samun hoton gawan Michael tun da ba wani gidan jarida dake da hoton gawar, dan ba wanda ya samu damar shiga wajen, labarin mutuwar ne kawai jama'a keji amma basu samu daman ganin hoton gawar ba, ko hoton shi Romeo. Jina jina sojojin nan suka yiwa ɗan jaridan nan, wannan ma dan sun yiwa shugaban kasa kara ne yasa basu kashe ɗan jaridan ba, lion kuwa ya kasa fita daga cikin hospital ɗin, tamkar shine wanda ya mutu ba Michael ba ko motsin kirki ya kasa yi, banda zazzafan huci da yake fitarwa ba abun da zakaji yana fita daga wajen shi, yayi mutuwar zaune, time to time yana sauke nauyayyar ajiyar zuciya. Jiki ba kwari shugaban kasa yazo ya dafa kafa ɗun lion tare da zama kusa da shi ya ɗan rungumo shi cikin muryan rarrashi yace "My lion please and please kayi hakuri, nasan dole akoi zafi muma mukaji zafi bare kai, amma ka daure kamar yadda na sanka da dauriya kayi hakuri ka bari ayiwa Michael sutura dan ba abun da yake buƙata sama da wannan a yanzu. Kamar wadda alluran sojan sa ya tashi haka ya juyo a fusace ya damki wuyar shugaban kasa, yana zaro ido cikin tsawa yace "No uncle, no Michael bai mutu ba, ka daina dangan ta shi da gawa, kuma babu in da za'a kai shi" tashin hankali president matsayin kakan su yake, dan kani ne ga kakan su jacop amma yau Romeo ya shake masa wuya kamar zai kashe shi dan kawai yace aje ayiwa Michael sutura Sai zaro ido waje shugaban kasa yake yana jin kamar zai mutu, daman yasan za'ayi haka mawuyacin abune Romeo ya yarda yana ji yana gani a saka Michael cikin rami shiyasa ma ya hana kowa zuwa ɗakin, dan bai son su kawo masa maganar, duk wanda yayi gigin kawo masa maganar saka Michael a kabari zai iya kashe sa. Sai da Romeo yaga president na faman sumewa sannan ya sakar masa wuyar sa, cikin tsawa yace da "get out uncle" kasan cewar shugaban kasa yasan halin jikan nasa sai ya miƙe ya fice daga ɗakin hannun sa riƙe da wuyar sa dan yasha shaƙa. Kifa kan sa Romeo yayi a saman fuska Michael yana jin zuciyar sa na tafasa tamkar zata fasa kirjin sa ta fito waje, saboda dakiyar zuciya irin na Romeo baiyi hawaye ba, ya daure dan shi cewa yake hawaye faɗuwar namiji ne, amma fa daga ta ciki yayi hawayen a zuci ya shiga tashin hankali da bai taɓa shiga ba. To masu karatu muje mu leƙo Akil sannan mu dawo, sai muga ko ya zata kaya, ya za'a karƙe da Romeo wajen bari ayiwa Michael sutura. 💞💞KADUNA STATE NIGERIA💞💞 Sai bugawa Akil kofa mum take amma yaki sauraron ta, dan baya duniyar mutane, ya shiga Umaisha sai aiki yake, sai kuka take tana zagin sa tana dukan sa amma yaki kyale ta, ya dage sai ya mai data cikakkiyar mace. Jin da gaske far ma Umaisha Akil yayi yasa Hajiya Umaiya komawa palo ta sake kiran Abba a waya ta sanar da shi wlh Akil yayiwa yar mutane fyaɗe kuma a cikin gida a cikin ɗakin sa, tashin hankali, Hajiya Umaiya ta tsorata sosai har Imran sai da ta kira a waya, ta sanar da shi, duk tabi ta ruɗe ga Akil baya jin kira. A wannan hali Aafia ta shigo cikin gidan da gudun ta tana neman Umaisha, nan Hajiya ke Tambayar ta wace ce ita daga ina take, wace yarinya Akil ya ɗauko, tsabar rashin zumunci itama Aafia bata san Hajiya ba, cike da rashin kunya tace "Ke ni ban sani ba kanwata kawai nazo ɗauka" da farko Hajiya kamar zata mare ta sai kuma taga rashin dacewar hakan domin koma me Akil ya ja musu. A takaice dai Akil bai kyale Umaisha ba har sai da ya mai da ita cikakkiyar mace, sai dai fa taci wuya kamar ba zakayi rai ba da kyar da kyar take numfashin, kuma ta zubar da jini sosai, yayin da shima ɗin ya sha wahala sosai sama sama yake numfashi yayi aiki wajen nan over, felling iya felling hankali ya kwanta wani daddaɗan barcine ya kwashe sa, ita kuwa Umaisha sai nishi take, yanzu babu bakin yin ihun ma ta kwanta shiru kawai tana jin raɗaɗin azaba a jikin ta. Barcin 10mins yayi kamar wadda aka tsikara ya tashi da sauri yana kallon ɓarnan da yayi ga Umaisha kamar ba zatayi rai ba, da sauri ya miƙe ya wuce toilet ya haɗa mata ruwa mai zafi ya fito ya ɗauke ta cak kamar yar baby suka wuce toilet. Sai nishi take tana masa kukan wahala kasa kasa, sosai ya gasa mata jiki sannan ya mata wanka ya fito da ita ɗaure da towel ya shinfiɗe ta saman sofa, sannan ya cire bed sheet ɗin nasa da yayi baca baca da jini ya ajiye a gefe ya ɗauko wani ya shinfiɗa sannan ya dawo da Umaisha saman gadon ya kwantar da ita ya wuce ya koma toilet dan yayi wanka. A ɓangaren Hajiya da Aafia kuwa, Hajiya bata sake tankawa Aafia ba ta yi shiru kawai ita ma Aafia shiru tayi tana jira taga ta in da Umaisha zata fito, dan a nata tunanin dole ne Akil ya kyale Umaisha ai ta koma gida tun da ba matar sa bace ba a ɗaura auren ba tukun nan, bata san shi kam Akil tuni ya ɗaurawa kan sa auren ba har ma ya raya Sunnah abun sa, sai dai jiran sakamako wato baby kenan. A wanna hali Abba ya dawo ya same su, hankali tashe Abba yace "ina Akil ɗin yake muje" da sauri Hajiya tayi gaba Abba ya bi bayan ta, Aafia ma bata bari an barta a baya ba tabi bayan su da saurin ta. Kofar bedroom nasa suka tsaya suna bubbuga wa da karfi, lokacin yana kokarin saka kayan sa ya fito daga wanka, wani nishaɗi da farinciki na musamman yake ji yau, Umaisha kuma barcin wahala ne ya ɗauke ta Jin bugun kofan yasa ya zura jallabiya kawai ya nufi kofar yaje ya buɗe, yana buɗewa su Abba suna cusa kai cikin ɗakin Hajiya tana faɗin "Yar waye kaje ka ɗauko?" Shafa kan sa yayi kafin yace "Matata ce" Mata Abba ya furta da karfi, eh Akil yace, tashin hankali Akil manya naka ba irin nasu bane Wucewa Abba yayi ciki dan yaga wace ce Akil ya ɗauko, bayan sa Hajiya da Aafia suka bi dan suje suma su gani, shikuwa oga Akil yana tsaye a bakin kofa, wai yaji kunya su Abba zasu je sugan masa mata kwance Allah ma yasa ya lulluɓeta da bargo, kai jama'a Akil manyan kasa oho Allah wai kunya yaji hmmm Kallo ɗaya Abba yayiwa fuskar Umaisha yace "Kai Akil amma wannan ai kamar yar gidan Zahraddeen ce ko? Dan ga kamanin Deen sosai fuskar ta" ɗan sunkuyar da kai Akil yayi yana ɗan shafa kan nasa irin kunyar nan yace "Eh Abba ita ce matata ce ai, naje na ɗauko tane" salati Abba yasa kafin yace "Matar ka waye ya aura maka ita? Ko dai kana da wani uban bayan nine?" To fa, ita kuwa Aafia saman gadon ta haura tana kuka tana jijjiga Umaisha, ganin Aafia na kokarin yaye bargon daya rufe Umaisha da shi ne yasa ya daka mata tsawa wadda yasa ta ja da baya daga kusa da Umaisha Hajiya Umaiya ce ta jawo Aafia tana faɗin "Ya isa kiyi shiru" Abba kam ya rasa bakin magana wai yau Akil ne da hankalin sa da ilimin sa ya yayiwa yarinya fyaɗe, fyaɗen ma ya rasa wadda zai yiwa sai yar kanin sa, kuma fyaɗen ma har gida ya kawo ta gaban kowa yadda zasu gani da idon su bawai suji labari ba, lallai Akil ya cika ɗan duniya mai lasisi Duk dakin sunyi shiru anrasa mai bakin magana, shi dai Akil ko ajikin sa, soma yake su fice masa daga ɗaki ya samu dama ya sawa matar sa kaya, yau ga ɗan duniya. Da kyar Abba yace "Yanzu Akil da hankalin ka zaka yiwa yar mutane fyaɗe?" "Abba fyaɗe kuma? A'a ni ba fyaɗe na mata ba dan matata ce ai" a kule Abba yace "Matar ka uban waye ya aura maka ita?" Akil zai yi magana Hajiya Umaiya tace "A'a Alhaji ni kada ka sake yi masa tsawa, dan kawai yayiwa wata yar talakawa fyaɗe shine zaka fara wani ɗaga masa murya, ni bana so, idan iyayen ta sunji ba zasu iya yafewa ba, sai su faɗa min nawane kuɗin budurcin yar nasu sai na biya, kai wannan yar ma da gani ba budurwa bace ka duba bed sheet da suka kwanta mana babu wani alama da zai nuna cewa budurwa aka yiwa fyaɗe a nan" to fah gaba da gaban ta, su Aafia suna ganin su hamshaƙan masu kuɗi ne to ga Hajiya Umaiya ta kira su da talakawa Kasan cewar shi Akil yana son Umaisha da gaske sai bai ji daɗin abun da Hajiya tace ba ran sa ya sosu sosai, rai a ɓace yace "Haba Ammie bai kamata kice wa matata haka ba, nifa da gaske nake son ta ba wasa ba, kuma bayan ita ba wata mace da nake so, babu wadda kuma zan so" zaro ido waje Ammie tayi a kule tace "Wace ce matar taka? Ba dai jinin Abban kaba sai dai wasu ƴaƴan manya shuwagabanni ko sarakuna, amma wannan yarin ba dai ina raye ne zata zama matar kaba" tirkashi, shi dai Abba bawan Allah shiru yayi ya zuba kusu ido kawai yana kallon ikon god Turo baki Akil yayi yace "Ni ita nake so kuma ita ce zaɓi na, sannan ita ba kamar yadda kike tunani bace tana da hankali ba namijin daya taɓa taɓa ta sai ni" yana kai karshen maganar ya fice daga ɗakin da sauri dan ma kar Ammie ta masa baki a kan Umaisha ko wani abu dan yasan halin Ammie sarai yadda bata son family Abba ko kaɗan ɗin nan ba abun da bazata iya faɗa ba in dai a kan sune Sakin Aafia Hajiya tayi ta bi bayan Akil dan ita bazata taɓa yarda da ya auri Umaisha ba, Allah sarki Abba yana tsaye shiru ya zubawa sarautar Allah ido, ita kuma Aafia sai kuka take. Ko da Ammie ta fita bata ga Akil ba dan ɓuya yayi baya son su sake maganar Umaisha da ita, sama yayi kasa yayi wallahu a'alam bata gan shi ba, shima Abba jiki ba kwari ya fito ya wuce bedroom nasa dan ya rasa bakin magana abun yafi karfin sa. Yana shiga bedroom nasa ya isko Akil kwance saman gadon sa ya ɗaura hannu a saman fuskar sa kamar mai tunani, Ammie kuma tana can tana neman shi a cikin gida Kusa da shi Abba yazo ya zauna a gefen gadon cikin nitsuwa yace "Haba Akil me yasa zaka yiwa yar ɗan uwana haka?" Miƙewa zaune Akil yayi cikin nitsuwa shima ya fara magana "Kayi hakuri Abba na, amma magana ta gaskiya shine Umaisha mata tace, da igiyar aurena uku a kan ta" juyowa da kyau Abba yayi suna fuskantar juna cike da murna yace "Yaushe hakan ya faru?" Yar murmushi Akil yayi kafin yace "Tun kafin na koma school, naji ba zan iya tafiya ba tare da an mana aure ba, dan ina ganin kamar idan na tafi bappa zai aura mata wani, shine bayan naje munyi sallama da ita, na wuce wajen Bappa na rokesa daya aura min ita kafin na tafi, da farko bappa yaki yarda sai da yaya Imran da yaya Irfan suka sa baki sannan ya yarda na bashi sadaki, a masallaci bayan sallar la'asar aka ɗaura mana aure, daman abun da yasa ban sanar daku ba, na bari sai na dawo ne in ɗauko ta in kawo muku ita, to ina shigo kasar nan kuma na wuce school nasu dan naje na ganta na ɗauko ta na kawo muku ita ku ganta, shine ta ɓata min rai har hakan ta faru tsakanin mu" kallon gefen ido Abba ya masa irin hararar wasan nan ya masa kafin yace "A'a ba dai ta ɓata maka rai ba, dama can da muguntan ka kadawo" ɓuye fuska Akil yayi a jikin Abba yana dariya kasa kasa, cakulkuli Abba ya shiga yi masa yana faɗin "A'a baka isa ba ai sai ka buɗe fuska muga juna ido da ido zai fi, dan rashin kunya ka kwaso zafin ka kazo tsakiyar rana ka sauke a kan ƴata gidan nan duka suna jin ka bakaji kunya ba sai yanzu zaka wani ɓoye fuska to wlh baka isa ba maza ɓuɗe muyi ido biyu" a shagwaɓe Akil yace "Kai Abba ka bari mana ni wlh kunyar ka nake ji" "Eyee kunyata ba, ai dole kaji kunya ta irin wannan ɗanyen aiki daka yiwa ƴata to Allah dai yasa ina da rabon jika" kara ɓoye fuska Akil yayi yana dariya yana jin farinciki Jin motsin Ammie na zuwa ne yawa dukan su suka yi shiru Abba ya ɗan matsa gefe yayin da shi kuma Akil ya diro kasa daga saman gadon ya nufi hanyar fita A bakin kofa sukayi karo da Ammie da sauri ya wuce ta ya koma bedroom nasa, kafin ma ta ɓuɗe baki tayi wani magana ya wuce ta, girgiza kai tayi tace "Zamu haɗu ne" ta kai karshen maganar tare da wucewa cikin bedroom ɗin Abba. Akil kuwa yana shiga ya samu Aafia zaune kusa da Umaisha tana hawaye, kusa da ita yazo ya zauna yana faɗin "Kiyi shiru ki dai na kuka ki tashi kije ɗakin Akila ki kwanta ki huta kafin Akila ta dawo school sai kuyi hira zan kira bappa a waya na faɗa masa kina nan" banza tayi da shi ta ci-gaba da kukan tana mai jin kamar ta shaƙe shi dan haushin ya raba kanwar ta da budurcin ta a banza ba auren ta yayi ba, kuma ga maman sa tana cewa ba zai auri Umaisha ba shikenan ya cuci rayuwar Umaisha a tunanin Aafia kenan. Ganin taki tashi ta tafine yasa ya miƙe ya riƙo hannun ta ya miƙar da ita, tana kokarin kwace hannun ta a fusace ya ɗaga hannu kamar zai mare ta sai kuma ya dakata, da ɗan karfi yace "Karki fara wuce mu tafi!" ganin ya haɗe rai sosai ne yasa ta hakura tabi bayan sa suka tafi ya kai ta ɗakin Akila ya dawo ya ɗauki jallabiyar sa ya sanyawa Umaisha ya wurzawa kofar ɗakin su key ya dawo ya kwanta kusa da ita yana mai jin matikar farinciki da annashuwa har cikin ransa. Ita kuma Aafia kwanciya tayi saman gadon Akila tana kallon sama tana hawayen bakin ciki, har barci ɓarawo ya ɗauke ta Ammie kuwa bala'i ta tsayar wa Abba wai dole yasa Akil ya dai na zancen auren Umaisha dan ba zata taɓa yarda ƴaƴan ta su aurin ƴaƴan talakawa kamar family sa ba, ayya Abba da yake tariga ta shanyesa yana son yan uwan sa amma babu halin nuna musu soyayya, sai kawai ya shiga bawa Ammie hakuri yana ce mata dole Akil ya bar zancen auren Umaisha, ba zai aure taɓa, ya nemi wata, sai daɗi Ammie take ji, bata san Umaisha kam already matar Akil bace. Wannan kenan mu leƙa Daular mutuwa mu ga meke faruwa sai mu dawo 👹👹DAULAR MUTUWA👹👹 Gudu Rimsha take sosai kamar zata tashi sama Kausar na biye da ita a baya, kasan cewar cikin ramin akoi hanyoyin da dama sai suka kauce hanyar da suka bi da farko suka kama wata hanyar daban saboda tashin hankali da ruɗu, su kuma su barbushi sunyi gudu mai nisa a wajen basu haɗu da su Rimsha ba, suma su Rimsha ɗin sunyi gudu sosai har suka kasa ci-gaba da gudu basu ga daular mutuwa ba ya ɓace musu, zama sukayi kasa a wajen suna numfashi sama sama kamar ba zasu yi rai ba bayin Allah. Suna zaune a wajen tun suna ganin haske kaɗan kaɗan har suka fara ganin duhu alamar dare kenan, kasan cewar wajen a karkashin kasa yake ba zaka iya wani banban tashi da yamma ba, danma akoi wasu wurare dake da huji kamar Windows a wajen hakan yasa ake ɗan samun haske kaɗan a wajen, ga yinwa ga kishin ruwa ga gajiya duk abun ya haɗe musu, banda sunan Allah ba abun da suke ambata a zuciyoyin su. A takaice dai kwana sukayi zaune a wajen, basu samu ganin Ayla ba, suma kuma su Barbushi basu samu damar ganin su Rimsha ɗin ba saboda addua'o'i da suke samu ta ɓangarori daban-daban, dan ko Jehan ta dukufa sosai kwana biyun nan tana yiwa Rimsha addu'a dan kwana biyun tana yawan mafarkin Rimsha ɗin shiyasa ta dukufa da yi mata addu'a sosai, a ɓangaren gwaggo ma haka ne ta dukufa sosai wajen yi ma Rimsha addu'a dan dukkan su kwana biyun nan suna mummuna mafarki a kan Rimsha ɗin, ta gefen guda kuma ga malaman da mum ta bawa kuɗi suyiwa Rimsha saukan Al Qur'ani mai girma suma yau suka gama saukan Al Qur'ani shine ma dalilin da yasa Allah ya bawa su Rimsha damar kuɓuta daga daular mutuwa, sannan ga baba da Mustapha suma ba'a barsu a baya ba sosai suke wa su Rimsha addu'a a zuciyar su, hakan yasa su Barbushi basu samu daman ganin su ba. Washegari ganin Kausar na kokarin mutuwa ne saboda yinwa da kishin ruwa yasa Rimsha tayi ta maza ta miƙe, Allah sarki itama yinwan take ji amma da ɗan sauran karfin ta tafi Kausar kwari, haka ta tattara karfin ta dukka ta goya Kausar a bayan ta tana jan kafarta a hankali hankali, dan duk kafar nata ya faffashe tun jinin ta na zuba har ya bushe wajen ya dai na zuba, tafiya take kamar zata faɗi kasa dan Kausar ta mata nauyi amma haka ta daure ta cije tana hawaye ta nufi hanyar da sukabi suka zo, ma'ana suka koma in da suka fara tafiya da farko. Rimsha tayi tafiya mai ɗan nisa da Kausar a goye a bayan ta kafin su iso wata kofar dafaffiyar karfe, da kyar ta iya sauke kausar ta zaunar da ita a kasa, ta sa hannun ta ta kwance ruwan tsafin da duna ya bata wadda ta kulle sa a jikin igiyar rigan ta dan karya faɗi kasa, kamar yadda ya faɗa mata haka ta zuba ruwan kaɗan a jikin kofar sai ga kofar ta buɗe nan take wani haske ya kaure musu ido, lokacin rana ya ɗago tsakiyar duniya, da sauri suka rintse idon su dan sun jima basu ga haske irin haka ba Sun ɗan jima a haka kafin Rimsha ta buɗe dara daran sleeping eyes nata da sukayi ja sosai, duk sun faɗa kamar ba wayan nan kyawawan idon nata masu kama da audiga dan haske ba, banda zara zaran eyelashes nata dake ɗan taimaka musu wajen fito da su da bazaka taɓa gane su ba saboda wahala da azaba da ta sha A hankali ta fara bin wajen da kallo, bata ganin komai sai bishiyoyi masu cikar ganye, juyowa tayi tasa hannu zata ɗago Kausar ta goyata, Kausar tayi sauri dakatar da ita ta hanyar yunkurawa da kan ta ta miƙe, rungume juna sukayi dan su tallafawa juna suka fara jan kafafun su da kyar da kyar zawa wajen wurin Sai kuma me, kungurmin daji ne sosai a wajen wadda baka gane gabas baka gane yamma, ga dogayen bishiyoyi masu abun tsoro, lokaci guda tsoro ya dira musu a ransu, tunani suka fara yi gara musu cikin daular mutuwa da wan nan wajen, domin koba komai cikin daular mutuwa akoi mutane nan kuma fa, sai karan tsuntsaye kuma da alama ba za'a rasa yamun dawa a wajen ba, macizai kam ma guarantee ne sai an same su ba adadi a wajen. Shin nan ɗin ma wace kasa ce? Wani gari ne? Tashin hankali Masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu TRIPLET'S💞 # BOOK 2📚📙✍️ 💔💔Episode 3💔💔 💔RIMSHA💔 A hankali suka fara kutsawa cikin dajin nan suna tafiya suna tangal tangal kamar zasu faɗi kasa, saboda wahalar da suka sha, duk sunyi wani iri dasu, sun koɗe futu futu, kamar ba su ba, kamar wayan da aka tono su daga rami, ko aka kwato su daga bakin kura, har wani duhun wahala sukayi, gashi sun manne junan su sosai saboda tsoro. A wannan lokaci da suka fito sun samu damar kiran sunan Allah a baki, gaba ɗaya dark black curly hair Rimsha ya cukurkuɗe kamar bashi ne wannan kyakkyawan bakin gashi mai shekin ba, mai tashin kamshi, yanzu ya dawo duk dattin, kuran daular mutuwa ya buɗe shi, sai warin datti suke saboda wanka ma da ruwa kawai suke ba sabulu, bare kuma mayukan gyaran jiki, ita kam Kausar daman ba gashin gare taba, abunku da kan yarbawa basu da gashi sosai aguiguye kan nata yake, sai dai itama fa ba laifi tana da kyan ta daidai gwargwado. Sunyi tafiya mai ɗan nisa kafin su iso wani katon rafi mai cike da ruwa, Allah sarki bayin Allah daman kishin ruwa suke ji kamar zasu mutu, suna ganin ruwan sukayi saurin isa wajen, suka kafa bakin su kamar shanu suka fara shan ruwan, basu damu ruwan da datti ko babu ba, su dai burin su kawai su sha ruwa. Sosai suka sha ruwan sai da sukaji cikin su na musu barazanar fashe wa sannan suka dakata. Sai kuma me cikin sune ya fara murɗa musu, saboda yinwa da ya musu yawa, gashi sun zo sun ɗirka ruwa ciki empty ba abinci. Kwanciya sukayi a bakin yafin cikin ciyayi dake wajen, suna murkusoso suna juyin azaban ciwon ciki, dukan su babu mai tallafa ma wani, saboda dukan su suna neman tallafi a wannan yana yi, kowannen su ta kan sa yake. Almost 30mins suna haka kafin su sami ciwon ya ɗan lafa musu. A hankali Rimsha ta miƙe zaune tana kallon Kausar, sai kuma hawaye suka fara bin kuncin ta, lokacin da ta kalli Kausar Ayla ce ta faɗo mata a ran ta shiyasa take kuka. Kausar bata lura da kukan da Rimsha ɗin keyi ba saboda ita bata gama dawowa cikin hayyacin taba. Sun ɗauki lokacin mai ɗan tsawo a wajen kafin su lallaɓa su tashi su ci-gaba da tafiya, basu san in da suka dosa ba tafiya kawai suke suna fatan Allah ya fitar da su daga wannan bala'i bakin dajin lafiya kar wani naman dawa ko wani abun ya kama su. Ita dai Kausar bata tsorata da dajin sosai ba, kasan cewar ita bayarbiya ce, kuma asalin kasar yarbawa mafiyawancin gida jen su a cikin ɗan daji daji suke, sai dai ba mai girman wannan ba, ita kuwa Rimsha rainon madara da Ice cream su chocolate bata san wannan wahala ba, gata daman da tsoron bala'i Jehan ta fita jarunta sosai. A takaice dai sunyi tafiya har rana ta kusa faɗuwa amma basu ga alamar karshen wannan daji ba, daga karshe da suka gaji, kasan wata itaciyar mangoro mai girman gaske suka samu suka zauna a wajen suna sauke numfashi. Duk sunyi tsuru tsuru dasu gwanin ban tausayi, ji suke gara musu daular mutuwa da wannan azaba da suke ciki a yanzu, ba abinci, ba motsin ɗan Adam, sai kukan wasu halittu wanda basu san menene ba ne, a daular mutuwa kuma ana basu abinci sau ɗaya a rana kuma suna ganin mutane saɓanin nan. Suna zaune a wajen har barcin wahala da gajiya ya kama su, zaune manne da junan su sukayi barci bayin Allah, sun sha wahala, ga ba abinci, babu wajen kwana, ba wani motsin ɗan adam a wannan daji, abun ya haɗu ya cakuɗe musu. To su Rimsha sai dai muce asuba ta gari, bari mu koma Washington DC mu gani ko zamu dace. 💞💞 WASHINGTON DC💞💞 Ya kasa motsawa daga wajen, sannan ya kasa cire fuskar sa daga kan fuskar Michael, dan ji yake kamar idan ya raba fuskar sa dana Michael zuciyar sa zata iya fasa kirjin sa ta fito waje, yaki bari ayiwa Michael sutura dan har zuchiyar sa bai yarda da cewa Michael ya mutu ba. Duk dakiya da taurin zuciya irin na soja, sai da wayan nan jibga jibgan sojojin suka ji zuciyar su ta raunata, sai da sukaji mugun tausayin ogan su ya kama su, har wani fuskar tausayi sukayin yau. A hankali hankali kunnen sa ta fara jiyo masa wani abun da ji yake tamkar gizone kawai kunnen sa ke masa, kara nitsuwa yayi dan ya tabbatar wa da kan sa shin abun da yake ji da gaske ne ko dai karya ne. Tabbas gaskiyane sautin bugun zuciyar Michael ne ke fita a hankali hankali. A sukwane ya raba fuskar sa dana Michael ɗin, ya mai da kan sa sai tin kirjin Michael dan ya tabbatar da abun da yake ji, kasa kunnen sa yayi sai tin wajen bugun zuciyar Michael. A sukwane ya ɗago yana faɗin "Call doctors for me!!" Yayi maganar da karfin gaske Ji kake dap dap wayan nan jibga jibgan sojojin sun fita da gudun gaske dan suje su kira likita, _shi kuma hannu yasa ya tallaɓo kan Micheal ya ɗan ɗago shi dan ya samu damar yin numfashi da kyau, dan kan sa yayi kasa sosai daman. Kusan gaba ɗaya manya manyan likitocin dake cikin asibitin ne suka biyo bayan sojojin nan, da gudun gaske suka shigo cikin room ɗin. Har likitoci nan suna rige rigen saka hannu, su karɓi Michael daka hannun Romeo, dan ko ba a faɗa musu ba sun san kiran da Romeo ya musu kenan. Cikin kankanin lokaci suka dukufa aiki a kan Micheal babu kama hannun yaro, gefe guda Romeo ya koma ya tsaya yana shafa kyakkyawa dark black curly hair sa, yana cizan lallausan laɓɓan sa, tare da furzar da iska mai zafi daga bakin sa, a zuciyar sa yana yiwa ɗan uwan sa addu'ar Allah ya tashi kafaɗun sa. Abun ka da kwararrun likitoci, ga kuma kayan aiki na zamani masu inganci, sannan ga kuɗi, dan in baka da kuɗi ko da kayan aiki ba mai kula ka. Cikin ƙanƙanin lokaci suka bawa Michael taimako sosai, ɗaya daga cikin taimakon da suka bashi shine sunyi kokarin wajen gyare wajen da yake bleeding, daman wajen kan sane ta baya kunnen sa ya fashe, sai kuma gefen cikin sa nan ma yaji ciwo sosai, wajen na bleeding. Ba karamin daɗi sojojin nan suka ji ba, dan ko ba komai hankalin ogan su zai kwanta, idan hankalin ogan su ya kwanta, suma hankalin su zai kwanta su samu nitsuwa, sai dai abun da basu sani ba shine, ogan su fa hankalin sa ba zai kwanta ba, dan ko ya gama da case ɗin Michael akoi James a site. Daddy kuma yana can gida yana fama da kokarin ceto rayuwar pastor, Tga John Jay duk suna gida hankalin su a matukar tashe, dan Tga ya sanar da su John abun da ya faru da Michael, sau biyu John yana suma, suna zuba masa ruwa yana farfaɗowa, kafin ya samu kan shi, saboda John yafi su Jay shakuwa da Michael, dan tare suke tsula tsiyar su a School, kuma mafi yawancin lokuta tare suke fita suje wajaje daban daban, irin su party da sauran su, shiyasa John yafi su Jay shiga tashin hankali, kuma duk wannan suma da yake yana farfaɗo dan bai yardan wa zuciyar sa Michael ya mutu bane, idan ya yardan wa zuciyar sa, kila mutuwa zai yi ma gaba ɗaya, dan son da yakewa Michael ba sone na wasa ba. Good 3 hours doctors suka ɗauka a kan Micheal suna bashi kulawa yadda ya dace. Sai da suka tabbatar sun masa duk wani abun da ya dace, sun tabbata ya fita daga haɗari, sannan suka nemi iznin komawa office nasu daga wajen Romeo, Romeo ya basu izinin komawa kam sai dai yace likitoci uku su tsaya kusa da Michael su lura da shi sosai, kar su kuskura su fita daga room ɗin, hakan kuwa akayi, likitoci uku ne suka tsaya a kan Micheal sauran kuma suka koma bakin aikin su, kowannen su ya koma cikin office na sa. Romeo bai bar hospital ɗin nan ba sai wajen 11 na dare, sannan ya wuce gida, amma kafin ta tafi sai da ya sanar da likitocin a kan gobe za'a mai da Michael gida wasu daga cikin likitocin su bisu gida suje suyi jinyar sa a can, dan su daman family William jacop basa zuwa asibiti, asibitin da kan ta take zuwa ta same su, ma'ana likitocin suke zuwa gida suyi jinyar su, yanzun ma Romeo bai san lokacin da aka kawo Michael hospital bane da ba zai yarda ba, sai dai ya ɗauko likitoci azo gida a kula da shi, yanzu kuma ba halin su ɗauki Michael a yau ne, saboda na'urori da aka dasa mashi, da sauran kayan aiki, dole dai su hakura sai gobe zasu samu daman ɗaukan nashi zuwa gida. Jibga jibgan sojoji 30 Romeo ya sanya su tsaya a hospital ɗin, dan kula da Michael. Cikin ɗakin da Michael jibga jibgan sojoji 6 ne aciki dan bashi kyakkyawan tsaro, ga kuma kwararrun likitoci uku a zaune kusa da shi, abun ku da masu hannu da shuni, abun ba'a magana sai dai muce Masha Allah. Bakin kofar ɗakin kuma sojoji huɗu ne, sauran sojojin kuma suka kewaye asibiti gaba ɗaya. Ko da Romeo ya koma gida, zaune su Tga suke gaba ɗayan su a palon kasa, bai bi ta kan kowa ba ya wuce da sauri ya nufi sama, saboda jinin Michael dake jikin rigan sa, baya son dad yaga jinin, za'a samu matsala idan ya gani. Dad na tambayar sa ina Michael, amma bai kula dad ba, saboda bai son tsayawa har dad yaga jinin, yanzu sai ya birkice musu, shima dad ganin Romeo bai tsaya ya bashi amsa ba, sai yayi tunanin ba lafiya, dan haka sai ya miƙe da sauri ya bi bayan Romeo. Koda ya shigo bedroom na Romeo, Romeo baya ciki, sai dai saukan ruwa dad yaji daga toilet, alamar wanka Romeo yake yi kenan, zama dad yayi a gefen gado yana jiran fitowar sa, dan yaga cikin kwayar idon sa ko zai ga wani abun. Romeo na fitowa kallo ɗaya yayiwa dad, ya kawar da kan sa yana faɗin "My dad what are you doing here?" Tun da daddy yaji Romeo na tambayar sa me yakeyi a nan, sai yaji wani irin dan bai taɓa masa makamanciyar tambayar nan ba, daga nan yasan ba lafiya ba, a gefen shima Romeo duk sai yaji wani iri, bai san lokacin da yayiwa daddy wannan tambayar ba, ganin dad ya sa shi ya shiga ruɗune dan yasan halin dad sarai, zai tsare sane da tambayoyi, shiyasa tun bai fara yi masa tambayoyin ba shi yayi saurin tambayar me dad yake yi a nan. Kamar wani mara gaskiya da sauri ya wuce dressing room nasa, yau ko shafa mai ɗin ma ba zai yi ba tun da dad na ɗakin, daddy kuwa ya zuba masa ido yana kallon sa yana mamakin me ya firgitar masa da lion nasa lokaci guda ne haka, duk yayi wani iri da shi, abun da dad bai taɓa ganin makamancin haka a tattare da lion ɗin ba sai yau. Dad na zaune har lion ya gama shiri cikin kayan barci masu kyau da tsada, ya dawo cikin bedroom ɗin sai tashin fitinannen kamshi yake, sai wani ɓoye fuskar sa yake bai son suyi ido huɗu da dad, dan yasan dad akoi kaifin basira, duk da matsalar da yake da shi, yana da basirar gane abu da kallo ɗaya, suna haɗa ido zai gane lion na cikin damuwa. "What is wrong with you my lion?" Dad ya jefo masa tambaya Tamkar saukan aradu haka yaji tambayar dad Juyowa yayi ya kalli dad kallo ɗaya, sannan ya kau da kan sa gefe, a nitse yace "Nothing My dad, have you noticed any change from me?" _miƙewa dad yayi yazo kusa da shi yana faɗin "tell me the truth my lion, what is wrong with you? I knew there is something wrong with you, because I have seen some changes on your face" Ji yake kamar ya fasa ihu, saboda tsananin tashin hankali da yake ciki, tambayoyin dad suna sawa yaji tamkar ana caka masa mashi a zuciyar sa, abubuwa sun haɗe masa, bai san in da James yake ba, ga kuma Michael kwance a gadon asibiti rai a hannun Allah, tsananin ciwon da jikin sa ke masa ma kawai ya ishe shi, ba sai ya samu kari ba, ko ina na jikin sa ciwo yake masa, sakamakon ciwon da Michael ke ciki da kuma ɓatar James. Jin yayi shiru ne yasa dad yace "why are you hiding something to me, I'm i not your Father?" Rungume daddy yayi yana ɓoye fuskar, dan saboda dara daran idon sa har sun canza launi, bai son daddy ya gani, "My lion please t... Bai bari dad ya kai karshen maganar ba yayi saurin rufe masa baki yana faɗin "Babu wani abun da na ɓoye maka My dad, just kawai I'm feeling headache ne" kokarin raba jikin su dad ya fara yi, dan ya samu damar ganin cikin kwayar idon lion, amma ina lion yaki yarda da hakan, dan ya rungume dad sosai, yau ga ikon Allah. Da dai dad yaga lion bai da niyar sakin sa, sai yace "Sorry muje na baka drugs" "No dad ba sai ka bani ba, I I'll take it by myself" yayi maganar with full confidence, ta yadda dad zai yarda eh da gaske babu komai ɗin. "Where is Michael and James, since morning banga James ba, Michael kuma tun ɗazun da yayiwa pastor wannan abun, ban sake jin motsin shi ba" har wani dum dum kirjin Romeo ya bada bugu, shi damuwan sa ɗaya, idan daddy ya san halin da James da Michael suke ciki, mawuyacin abune su ɗauke sa da rai a daren nan, zuciyar sa zata iya bugawa, dan Triplets na sa, sune duniyar sa, sune rayuwar sa, gashi ba isshesshen lafiya ke gare shi ba, ga tsufa, yana da saurin rikicewa a kan abu, abu kaɗan yake birkita shi. "James baya nan, ya tafi Spain, Michael kuma yana white house" Romeo ya bawa dad amsa yana raba jikin su, "Me James yaje yi Europe? Kuma why bai faɗa min ba?" Wucewa Romeo yayi, ya haye saman bed nasa yana faɗin "Ni na aiki James Spain akoi abun da zai karɓo min a can" shiru dad ya ɗan yi, kafin yace "Okey let me call his number" "No dad, no need ka kira shi, saboda yana tsaka da min aiki, idan ka kira shi za'a iya samun matsala" yayi maganar yana kokarin jawo wayar sa da system nasa, to dad yace masa tare da matsowa kusa da shi ya manna masa kiss a goshi, shima lion ɗin juyowa yayi, ya mannawa dad kiss a kumatu, daga nan sukayi sallama dad ya nufi hanyar fita daga bedroom ɗin, zuba masa dara daran blue eyes nasa lion yayi yana kallon sa cike da so da kauna. Har ya kai bakin kofa zai fita, sai kuma ya dakata tare da juyowa, a sukwane lion ya kawar da kallon sa gefe, dan kar dad ya zargi wani abu "Ya kamata ka dai na cin abinci tsakiyar dare, yanzu ka sauko kaci abinci, dan naga yinwa a tattare da kai" cewar daddy, yayi maganar yana tsare lion da ido "No dad, I'm not feeling hungry know, i can't eat food, amma kace Tga ya kawo min maltina" kamar dad zai sake yin magana, sai kuma ya fasa, dan ya lura lion ya fara ɗaure fuska sosai, saboda bai son yawan magana, surutu sa shi ciwon kai yake, wucewa kawai dad yayi, ya fice daga part ɗin ya koma palon kasa, ya sanar da Tga sakon lion, daman Tga kamar jira yake, ya matsu yaji halin da ake ciki game da mutuwar Michael, dan haka sai ya miƙe da sauri ya nufi sama, dan akoi drinks kala kala shaƙe da katuwar freezer a palon lion, A ɓangaren lion kuwa, dad na fita ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya, tare da jawo system nasa ya fara bincike a kan ɓatar James, tunani yake, ko dai ya shirya ya tafi Spain ɗin yaje yayi bincike da kyau a can ne, dan gaba ɗaya binciken online ɗin nan bata masa yadda yake buƙata. Baki ɗauke da excuse Tga ya shigo cikin bedroom ɗin, hannun sa ɗauke da plate mai ɗauke da maltina mai sanyi da kyakkyawan glass cup, mai kyau da tsada. Saman bedside drawer ya ɗaura plate ɗin, sanna ya zauna gefen lion yana faɗin "Good evening sir" shiru Romeo ya ɗan yi, kamar ba zai amsa ba, almost 3mins, sannan ya ɗago ya dubi Tga, kallo ɗaya ya kawar da kan sa gefe, gently in a cool voice yace "what is wrong with you uncle T?" Kamar jira Tga yake a masa magana, cike da damuwa yace "lion what about Michael?" Yayi maganar hawayen na kokarin zubowa daga idon sa, Allah sarki yana son jin ya su lion sukayi da gawar Michael, dan lion ya hana su zuwa asibitin, yace su zauna a gida, dan kar daddy yayi zargi wani abu. "calm down micheal is not death he's alive" Duk rashin murmushi irin na Tga, yau bai san lokacin da ya saki cool murmushi ba, har hakwaran sa suka bayyana, ga kuma ido cike da kwalla, ga murmushi. Saboda daɗi bai san lokacin daya rungume Romeo yana ta murmushi kamar bakin sa ba zai rufuba. Gyaran murya Romeo ya masa, wadda ya sanya shi raba jikin sa dana Romeo da sauri, da hannu Romeo ya masa nuni da hanyar fita daga ɗakin ba tare da yayi magana ba,Tga bai wani damu ba, dan ya lura aiki Romeo yake, ba dan aiki yake ba, ba zai ce ya fita masa a ɗaki ba, dan wani lokaci a ɗakin suke wuni, shi murnan Michael na raye ma ya wanke masa komai dake zuciyar sa, cikin sauri ya miƙe ya fice daga ɗakin, dan yaje ya sanar da su John Michael na raye, dama kuma shi John tun da yaji labarin mutuwar Micheal ɗin, bayan ya gama suman sa, sai ya dawo yana ta musu sambatu Michael bai mutu ba, Michael bai mutu ba. Tga na fita Romeo ya ci-gaba da aikin dake gaban sa, dan neman mafita a kan case ɗin James. Sai ƙarfe huɗu na dare sannan ya kwanta, ya samu barcin wahala ta ɗauke sa, zuciyar sa cike da tunani kala kala a kan yan uwansa. To kafin lion ya farka bari mu leƙo Jehan ɗin gwaggo mu gani me take ciki ne. 💞💞KATSINA STATE NIGERIA💞💞 Super restaurant Tun karfe 7 Jehan taje wajen aiki, kamar kullun wajen serving abinci ta wuce abun ta, suna tsaƙa da aiki, sukaji diran motoncin a cikin restaurant ɗin, ko a jikin ta, ta ci-gaba da aikin da take dan daman ba ta shiga harkan kowa, kuma ko menene zai shigo cikin restaurant ɗin in dai ba ya biyo ta kan aikin taba, to bata kula shi. Tana faman sakawa wasu costumers abinci, ɗaya daga cikin ma'aikatan wajen tazo wajen ta tana faɗin "Jehan oga Ibraheem yace ki bar duk abun da kike, ki kaiwa su yarima abinci, yau har da dr Nawid suka zo" tana magana tana washe baki. Ko kallon in da take Jehan ba tayi ba, bare ta sa ran zata mata magana, dama kuma kowa ya san da wannan hali na Jehan, na rashin tanka magana idan aka mata, wucewa ma'aikaciyar tayi ta koma bakin nata aiki. Shi kuma Ibraheem duk lokacin da manyan baki suka zo, yafi son ya aika Jehan, dan tafi kowa kyau a wajen, sai dai kuma tafi kowa miskilanci, da shariya, gashi idan tana wani aiki kasa ta wani tofa ba zata kula kaba bare kuma kasa ran zata maka wannan aikin da kace, haka take, yanzun ma haka ne, su yarima suna can suna jiran abinci Jehan na aikin gaban ta, taki ta kula su. Tsab ta gama shiryawa costumers ɗin farko da suka riga zuwa abinci saman trey, sannan ta ɗauka ta fito wajen, daidai lokacin ɗaya daga cikin bodyguard na yarima yake yiwa Ibraheem faɗa a kan ya zai bar yarima zaune ba su kawo masa abinci ba, Jehan kam ko a jikin ta tazo zata wuce su, tsawa Ibraheem ya daka mata, "Ke Jehan ina abincin dana ce ki shiryawa yarima?" irin wannan abun da ake cewa burgagi shine Ibraheem yayi, dan yaga idon su yarima, ya daka mata tsawar amma zuciyar sa na dukan uku uku saboda tsoron amsar da Jehan zata bashi, dan yasan ba karamin aikin ta bane ta tsinka shi cikin jama'a. Sai dai kuma yayi sa'a ko kallon in da yake ba tayi ba tare yasa ran zata tanka mashi, tayi wucewar ta, ta nufi wasu ma'aurata biyu dake zaune saman table ɗin cin abincin suna jiran ta. A fusace bodyguard da yake yiwa Ibraheem magana ya daka mata tsawa, "Ke ba da ke ake magana bane?!!" Kamar da ita ce sukayi magana ba Jehan ba, tayi wuce warta kamar kurma, daman ita Jehan maganar nata ma zuwa zuwa ne, idan ta ga dama in ka mata magana zata amsa, idan kuma bata ga dama ba, sai ka shekara kana magana bata san kana yi ba. Ganin ta raina musu wayo ne yasa bodyguard ɗin yin sauri yasha gaban ta, tare da yin patali da trey ɗin abincin dake hannun ta yana faɗin "Ke akoi sa'ar ki a nan ne, hattara yar talakawa, idan ba haka ba ki kare rayuwar ki a prison!!" Kallon trey abinci tayi, yadda ya faɗi kasa, abincin dukka ya tarwatse a kasa, plate ɗin ɗaya yayi gefen can ɗaya yayi gefen nan, Dawo da kallon ta tayi kan bodyguard ɗin, sai wani ɗaure fuska yake, shi adole ya ɓata rai. Ta rasa me ma zata cewa wannan mummunar mutumi, yau bata jin yin magana, haka ta tashi cikin wani irin yanayi mara daɗi, saboda ɓatar Rimsha ya dawo mata sabo ne a yan kwana kin nan, yau sosai ta tashi da tunanin yar uwar ta, jikin ta duk a mace yake, bata son hayaniya "Amma kai jahili ne ko" ta faɗa cikin harshen Hausa, a zahirin gaskiya bata san menene ma'anar jahili ba, a bakin amaryan baban Sadiq take ji word ɗin, amarya na yawan zagin baban Sadiq da wannan kalmar, tun daga nan Jehan ta riƙe, a cewar ta koma me kalma ce mara daɗi, shiyasa ta faɗa wa wannan bodyguard ɗin, dan tana son yaji babu daɗi, saboda ya bata haushi. Aikuwa hakan ce ta faru, ya fusata iya fusata, ya ɗaga hannu zai mareta, cak aka riƙe hannun sa ta baya, cikin sauri ya juyo dan ganin wanene. Ganin Nawid ne yasa ya ɗan ja da baya yana faɗin "sorry sir" kallon Jehan kawai Nawid yake, ita kuma kallo ɗaya ta masa, taja guntun tsaki tare da kawar da kan ta gefe guda. Nawid na kokarin yin magana, muryan ta ta katse shi tana faɗin "Ka tsugunna ka kwashe abincin nan duka, sannan ka bani kuɗin abinci" rai a ɓace bodyguard ɗin yace "Ke baki da hankali ko? Waye yace miki idan yarima yazo nan waje, ana barin sa aje a bawa wasu talakawa abinci? To bari kiji, idan yarima yazo nan kowa dake nan fita waje yake har sai yarima ya gama abun da yake ya fita tukun nan" _kallon tsab tayiwa bodyguard ɗin, sai wani huci yake shi a dole ran sa ya ɓaci. "Au hakane tsarin ku? To idan ma haka ne, ni ba haka nawa tsarin yake ba, ni mutun ce mai adalci, banga wani ɗan adam da zai shigo cikin restaurant nan na tsallake wayan da suka riga shi, na kai mashi abinci ba, babu wannan mutumin aduniya, ni adilace bana zalunci, kuma ai bani kaɗai ce ma'aikaciya a wajen ba akoi wasu me yasa sai ni? Ku nemi wata ma'aikaciyar ta kai muku abincin ba dai ni Jehan ba" Nawid na kokarin yin magana a karo na biyu muryan yarima ya katse shi cewa "Ku kawo min yarinyar nan gaba na" ko a jikin ta, ta juya ta nufi hanyar komawa in da suke girki, tana faɗin "Zanje na haɗa musu wani abincin kafin na dawo ka kwashe wanda ka zubar kuma ka ajiye min kuɗi na" tayi maganar with her full confidence, babu alamar tsoro ko ɗari, Shi dai Nawid kallon ta kawai yake dan ba karamin burge shi tayi ba, yana son mace irin ta mai izza da dakiya, mara tsoro. Tazo zata wuce su Yarima sauran bodyguard na shi dake wajen suka sha gaban ta, suna masu bata umarnin a kan ta wuce ta tafi gaban yarima ta zube gwiwowin ta a kasa da kan ta, idan ba haka ba su ɗauke ta da kan su, su kai ta gaban shi, ganin da gaske zasu iya ɗaga ta yasa ta wuce da kafar ta, ta karisa gaban yarima. Yana hakimce saman kujera, sai wani shan kamshi yake, yana wani basarwa. Tsayuwa tayi a gaban sa, tare da kawar da kallon ta gefe, tsawa bodyguard ɗin suka daga kama, a kan ta tsugunna, dan ba'a yiwa yarima haka. Shi kam Ibraheem yasha jinin jikin sa, dan yasan halin yarima Al ameen bashi da mutunci ko kaɗan, ɗane ga kanin sarkin yanzu, kasan cewar sarki bashi da ɗa namiji, hakan yasa ake cewa ɗan kanin sa yarima, wannan restaurant ɗin ma mallakin family sune, na kanwar sarki wato gwaggon yarima kenan, amma restaurant ɗin yana hannun babban ɗan tane. Duk lokacin da Nawid yazo Katsina a restaurant ɗin yake sauƙa, ya kwana a ɗaki ɗaya daga cikin ɗakunan Hotel ɗin, bai cika son kwana a gidan sarki ba. Duk sauran ma'aikatan dake wajen sai da suka tsorata, dan sun san yarima bashi da imani, karamin aikin sa ne yanzu yasaka Jehan frog jump daga nan har gidan su da kafa. Jehan na tsaye taki tsugunnawa yayin da shikuma yarima izzar sa ke ta daɗa motsawa. Karisowa wajen Nawid yayi yana faɗin "Al Ameen ka kyale ta ta tafi" ya kai karshen maganar tare da zama a ɗaya daga cikin gujerun wajen. Sosai Jehan ta tsorata, ji take kamar fitsari zai zuba mata a wando, ga wayan nan bodyguard ɗin masu fuska abun tsoro, har kerman tsoro jikin ta ya fara yi. "Kneel down!!" Yarima ya furta yana wani shan kamshi, shiru tayi tana tunanin, tayi kneel down ɗin ne ko kar tayi, idan tayi shikenan mutuncin ta ya zube a idon su Ibraheem, idan kuma taki yi, wannan mugun mutumi zai iya saka wayan nan munanan bodyguard ɗin su mata mugun duka, yanzu me mafita, ta tambayi kan ta, duk ta tsorata, yau duk wani izzan ta ya sauka, saboda bataga alaman wawanci a tattare dasu yarima ba, daman duk wayan da take wa tsiwa, dan tasan jahilai ne, babu ilimin boko, ba na islamiya, shiyasa take rai na musu hankali, su kuma su yarima, gogewa na duniya ne a tattare da su, wayayyun guy's ne, na bugawa a jarida, ga kuɗi ga mulki, ga ilimi da isa, ga izza da isgilanci. Ibraheem da sauran ma'aikatan dake wajen sun yi shiru sun zuba musu ido, suna son suga, shin Jehan zatayi wannan kneel down ɗin kuwa? Koyaya. Runtse ido Jehan tayi tana mai jin zafin rashin daddyn ta, yau da daddyn ta na nan, akoi wanda ya isa ya zo kusa da ita ne a cikin su, ji take kamar ta saka ihu ko zata samu sassauci a zuciyar ta. Tsawa Yarima ya dakawa bodyguard ɗin, a kan su ladabtar da ita, su sakata kneel down ɗin dole, a sukwane ta waro idon ta waje, jin yarima yace bodyguard su ladabtar da ita, bodyguard ɗin kuwa, cikin bin umarnin yarima suka fara kokarin riƙota, ban da sunan Allah babu abun da take kira a zuciyar ta, dan ta sawa ranta ba za tayi kneel down ba, dan kar mutuncin ta ya zube a idon su Ibraheem. Bodyguards ɗin suna ƙoƙarin kamata Nawid ya daka musu tsawa "Kai kuna da hankali kuwa?!! Al Ameen meke damun kane? Mace ce fa, Ke jeki abun ki, koma bakin aikin ki, ki shiryo mana abinci da zamu ci yanzu" cak bodyguard ɗin suka tsaya suka fasa kamata, yarima na kokarin yin magana muryan Jehan ta katse su "Ni ba zan kawo muku abinci ba har sai na kaiwa wayan can da suka riga ku zuwa" tashin hankali. Murmushi Nawid yayi yace "To jeki kai musu, idan kin dawo sai ki haɗa mana namu, ai kina da gaskiya, hakan shine adalci" Yarima zai yi magana Nawid ya dakatar da shi ta hanyar cewa "Bana son na ji komai daga gareka, ke jeki abun ki" da sauri Jehan ta wuce ta bar wajen, shi kuma yarima rai a matukar ɓace ya miƙe ya bar wajen, yana cika yana batsewa, yau yayan sa Nawid ya tsinkashi a cikin jama'a, a kan yar talakawa kazama, a cewar sa. Shi kuwa Nawid sai murmushi yake, bakin sa yaki rufuwa, yana ta bin Jehan da kallo, duk in da ta wuce sai ya bita da ido. Har ta gama serving wayan can da suka riga, sannan ta shirya nasu Nawid ɗin ta ɗauko, ta kawo musu, Nan ta tarar Yarima ya tafi, ko a jikin ta, ta ajiyewa Nawid ta koma bakin aikin ta, shima Nawid ɗin bai wani damu da tafiyar da yarima yayi ba, dan ya san halin yarima fin haka ma zai aikata. Cikin kwanciyar hankali yaci abincin sa tsab, sannan ya miƙe bayan ya gama, ya nufi wajen Ibraheem, yaje ya karɓi key ɗin ɗaki ɗaya, ya wuce ya nufi ɗakin, yana jin zuciyar sa na masa daɗi ganin Jehan da yayi, bai san taba, bai taɓa ganin taba sai yau, amma da kallo ɗaya, ya kamu da matsanancin son ta, niko nace tab kana da babban aiki in dai Jehan ce, dan bata san soyayya ba bashi kuma a gaban ta, Tunanin Jehan cike fal ransa, ya karisa room number 14, ya buɗe ya shiga, yana mai sauke ajiyar zuciya. A ɓangaren Jehan kuwa, ko a jikin ta, dan bata ma san yana yi ba, ita ko kallon fuskar su da kyau ma bata yi ba, zata iya sake haɗuwa da yarima a hanya ma ta kasa gane shi, dan bata kalli fuskar sa ba, ɗan gara Nawid da yake ya taimake ta, shi ta kalle shi sau ɗaya. Lallai akoi aiki, to mu dai je zuwa, bari mu koma wajen su Rimsha muga wani hali suke ciki Karku manta idan Allah ya kai mu ranar Jumma'a da rai da lafiya, zan ɗauki hutu na ɗan wani lokaci, dan in ɗan huta in samu kwakwalwata tayi fresh, in ji daɗin zubo muku zafafan page's masu tashin kai, ina godiya sosai da sosai Allah ya bar zumunci 🥰 Masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu . 💞💞TRIPLET'S💞💞 # BOOK 2📚📙✍️ 💔💔Episode 4💔💔 💔RIMSHA💔 Lallai akoi aiki, to mu dai je zuwa, bari mu koma wajen su Rimsha muga wani hali da suke ciki. Kwance suke bayin Allah kasan wannan itaciyar mangoron, duk da suna barci hannun su rike cikin na juna, sun kan kan me junan su sosai, kamar wani yace zai raba su. Hasken rana daya ɗago ne ya haske musu idanuwan su, wadda hakan yayi sanadiyar farkawan su daga barcin wahala daya ɗauke su, a hankali suka waro jajayen idanuwan su waje lokaci guda, jikkunan su gaba ɗaya ciwo yake musu, tsananin yinwa da kishin ruwa ne ya tattaru ya musu yawa, plat tummyn su nan ya kara yin plat sosai saboda azaban yiwan, fuskokin su gaba ɗaya ya canza launi, sun zama abun tausayi, sunyi wiki wiki da su, gasu futu futu da datti, idan ka gansu ba zaka taɓa gane su ɗin bane. A hankali Rimsha ta yunkura ta miƙe zaune tana faɗin "Good morning Kausar" miƙewa zaune ita ma Kausar tayi tana faɗin "Meesha yinwa nake ji, ba zan iya ci-gaba da tafiya ba muddin banci abinci ba" Rimsha na kokarin yin magana idon ta ya sauƙa a kan mangoririn (Mangos) da suka faffaɗu kasa daga saman bishiyan dasu wajen, kallon Kausar tayi a nitse tace "Kausar ga abinci nan Allah ya bamu, dama Allah ba azzalumin bawan sa bane sai dai bawa ya zalunci kan sa, yanzu mu ɗebi mangoririn nan muje mu wanko su, musha mu koshi, sai mu sha ruwa, mu ɗauro alwala muzo mu fara biyan bashin sallolin dake kan mu" shiru Kausar ta ɗan yi kafin tace "Meesha dame kike tunani zamu yi sallah? Bayan dukan mu babu mai ɗankwali bare hijabi" yunkurawa Rimsha tayi ta miƙe ta fara zaɓan mangoron da ya mata tana faɗin "Ba zani bane a jikin ki? Idan mu kayi alwala sai ki bani zanin ki na rufa nayi Sallah, idan na idar ni kuma sai na baki rigana ki saka, tun da ina da wando da best a ciki, idan kin saka rigana sai ki yafa zanin kiyi Sallah" murmushi ne ya bayyana a kan fuskar Kausar, dan jin sun samu hanyar da zasu yi Sallah su kaiwa Allah kukan su, daman tasan rashin Sallah da basa yi ne, yasa abun ya haɗu ya musu yawa, dan basu samun dama su kaiwa Ubangijin mu kukan su. Tayi shiru tana tunani, bata san lokacin da Rismha taje ta wanko musu mangoron a wajen wani rami da ruwa ke taruwa a wajen ta dawo ba, sai ji tayi Rimsha ta ɗaura mata mangoro a saman hannun ta, tana faɗin "Kici da wuri muyi Sallah mu ci-gaba da tafiya dan mu samu mu bar dajin nan" godiya mai yawa Kausar tayiwa Rimsha tare da yi mata addu'ar fatan Alkhari da fatan nasara. A takaice dai haka suka ci wannan mangaron sannan sukaje sukayi alwala sukazo sukayi kamar yadda Rimsha tace na musayan kayan su, sukayi Sallah, sannan suka ɗebi wasu mangoririn a hannun su, suka ci-gaba da tafiya, yanzu sun samu karfin jikin su, har hira suke suna tafiya. Nan Kausar ke bawa Rimsha labarin yadda su Barbushi suka sato ta har suka kawota Daular mutuwa. "Ni dai sunana Kausar, bayarbiya ce ni yar jahar kwara state, munje kaduna wajen yan uwan mama ta ce, kasan cewar ita ba bayarbiya bace, ba haushiya ce, daga zuwa ziyara na fito ganin gari shikenan suka sace ni" sosai Rimsha ta jajan ta mata tare da yi mata fatan Allah yasa suna da rabon sake ganin yan uwan su, Amin Kausar ta amsa da shi sannan tace "Ke fa? Ya akayi suka kawo ki Daular mutuwa" Rimsha mace ce mai sirri duk da kananan shekarun da wuya ka samu tana yiwa wani ɗan adam hiran a kan rayuwar ta, dan haka sai tace da kausar "Ni yar Katsina ce, daga can suka sace ni na fito sayan ashana" Kausar ta nuna rashin jin daɗi ta, ta kuma yiwa Rimsha addu'a ita ma sosai, Amin Rimsha ta amsa da shi, suka ci-gaba da tafiya suna hiran gwanin ban tausayi da kuma burgewa. Basu gane lokacin, kawai da sukaga rana ya ɗaga sosai, sai suka tsaya sukayi sallar azahar a kasan wata katuwar bishiya kanya, kasan cewar lokacin damuna ne, dajin akoi ruwa sosai ta ko'ina, ko baka ga rafi ba, zaka samu rami da ruwa, shiyasa basa wahalan wajen samu ruwa, haka zalika yanzu basa wahalar abinci, saboda lokacin damuna ne akoi ƴaƴan itace sosai, irin su gwaiva, mangoro, kashu, lemu, da sauran su, duk in suka ji yinwa, sai su tsaya ci tsinki ƴaƴan itace su ci sai sun koshi, Kausar itace ke hawa musu bishiya, Rimsha kam bata iya ba, kuma ita Rimsha akoi ta da tsoron bala'i, bazata iya hawa itacen ba, sai taga kamar zata faɗo kasa, itakuwa Kausar yar yarbawa, hayewa take kamar ɗan biri tayi ta tsinko musu ƴaƴan itace tana jefowa kasa Rimsha na ɗauka, sun zama kamar wasu ƴaƴan daji, har wani fresh suka fara yi ɗan wunin yau da suka samu ƴaƴan itace suna taci suna shan zuwa. Idan sun koshi sai su ci-gaba da tafiya, har yanzu kuma basu fara jiyo kamshin wani garin a kusa ba, hakan kuma bai wani ɗaga musu hankali ba, dan sun ɗan samu sakewa da dajin, mafi yawancin lokaci Rimsha na yawan tunani a kan su gwaggo, haka zalika tana yawan tunani a kan GAR, mutumin da tafi so fiye da komai a duniya idan aka cire iyayen ta da Jehan da gwaggo, wani lokaci idan suka zauna a kasa wata bishiya, har zana fuskar sa da face mask take a kasa, dan ta kware wajen iya zane, idan kausar ta tambaye ta wanene wannan, sai tace wani ne wanda yake burge ta, kuma take kaunar sa, a hankali hankali har kausar ta fara iya zana fuskar GAR ita ma, saboda yadda Rimsha ke zana shi ko wani lokaci idan suka zauna. Haka zalika idan suka zauna Rimsha bata da wani magana sai maganar GAR yana burgeta, tayi kewar ganin fuskar sa, bata damu da rayuwar ta kamar yadda ta damu da missed na fuskar GAR ba, tun Kausar na mamaki har ta dai na, ta dawo biye mata suna yi kawai, dan idan kana son kaga Rimsha na magana tana dariya to kayi mata maganar GAR yanzu zata amsaka da dariya a fuskar ta. Allah sarki baiwar Allah, tana dakon soyayyan mutumin da bai san taba bai taɓa ganin taba, bai san hanyar African ba sai dai ya gani a Media, amma ita tun tana yar shekara 9 take kaunar ganin labarai a kan sa, a hankali har son sa ya shige ta, so ma mai bala'i tsanani, wadda bata damu da rayuwar ta kamar yadda ta damu da shi ba, wannan shine gaibu, ko ace soyayya da aljani ko soyayya da duhu dan duk ɗaya ne, soyayya da abun da baka ganin sa, akoi matsala, akoi cakwakiya. To mu leƙo wajen su Aafia mu gani me suke aikatawa ne. 💞💞KADUNA 💞💞 Sai karfe 6 na yamma Aafia ta farka daga barcin da ya ɗauke ta, cikin sauri ta miƙe zaune tare da dirowa kasa daga saman gadon. A sukawane tayo waje, A palon kasa ta isko Akila, Abba, da Ammie, ba tare da ta gaishe da ko ɗaya daga cikin su ba, tace "Ina Umaisha?" Akila ce tace "Aunty Aafia barka da tashi" kallon sama da kasa tayiwa Akila kafin tace "Ina Umaisha nace?" Akila zata yi magana Ammie ta rigata da cewa "Ke mara kunya, ki kiyaye ni ko na tashi na miki ɗan banzan duka, zoki wuce ki bargidan nan ma kafin na tashi" Abba yana son yin magana amma ba hali, dan yana tsoron Hajiya Umaiya, bata da mutunci, haka yayi shiru yana bin Aafia da ido, _Guntun tsaki Aafia taja kafin tace "Ni daman idan ba kaddara ba, me zai kawo ni gidan nan, ku faɗa min ina yar uwata, shine kawai a gaba na, banson wani abu kuma" miƙewa Ammie tayi da niyar ta dake ta, sai sukaji muryan Akil a bayan su yana faɗin "Ke baki da hankali ko? Idan baki shiga cikin hankalin ki ba, sai na karya ki kafin ki koma, wuce mu tafi na mai daki gida, motar naki ki bar shi a nan driver zai dawo miki da shi" tasan halin Akil sarai yanzu zai iya karya tan da gaske, dan haka ba musu tabi bayan sa, tana turo baki. Allah sarki Akila baiwar Allah mai kaunar yan uwan ta, taso su fahimci Juna da Aafia amma abun bai samu ba, Aafia akoi ta da ji da kai, da nuna isa da izza. Kai tsaye gida Akil ya kai ta da motar sa, kuma da kan sa ya tuka, sai dai ko da suka je gate ɗin gidan, shi bai shiga ba, a kofar gida ya sauƙe ta, ya juya kan motar sa zuwa gida. Cikin gida ta wuce tana rakuɓe rakuɓe, tana addu'ar Allah yasa daddyn Jelly baya palo, dan idan ya kalle ta da kayan jikin tan nan akoi matsala ba kaɗan ba. Tayi Sa'a kuwa daddy baya palon, cikin sauri ta wuce ta haye sama ta nufi bedroom nasu.Tana shiga ta cire kayan jikin ta ta faɗa toilet dan yin wanka. Bayan tayi wanka ta fito, ta shirya cikin atamfa riga da skit kayan sun kama ta sosai, ta ɗauki after dress ta ɗaura saman kayan nata, ta fito palon kasa hannun ta riƙe da maganin da Rufee ta bata, dan ta zubawa Aunty a abinci, taci cikin jikin ta ya zube. Shiru palon kasan babu kowa, ga kuma abinci saman table an geresu, sauri sauri ta nufi table ɗin, kulan miya ta buɗe ta zuba maganin a ciki tare da gauraya miyar sannan ta rufe, tana tunanin anya idan su Abbi suka ci maganain nan ba zai musu illa ba kuwa, gashi kuma bata da wata hanya da zata sa Aunty taci maganain nan dole dai sai dai ta zuba a kulan miyar gaba ɗaya, shiyasa ta zuba, kuma ta dawo tana danasani kar su Abbi suci maganin ya zamo musu illah. Tayi nisa cikin tunanin da take, sai ji tayi Aunty nace mata "Aafia lafiya?" Yar firgigit tayi irin na marasa gaskiya. Ganin Aunty ne yasa taja dogon tsaki tare da wuce wa, ta bar wajen, ta koma saman sofa ta zauna, Aunty kuwa baiwar Allah bata kawo komai a ran taba, tayi tunanin ma ko yinwa Aafia take ji ne yasa tazo wajen table ɗin, shiyasa ma ta tambaye ta ko lafiya. Dai dai lokacin daddyn Jelly ya shigo palon shirye cikin wata dakakkiyar shadda fara tas ɗinkin full jompa, yayi kyau sosai, ɗan zaman sa a gidan har ya fara murmurewa. Har kasa Aunty ta tsuguna ta gaishe shi, da fara'a ya amsa tare da ce mata "Zan fita kila yaya ya rigani dawowa, idan ya dawo ki sanar da shi na fita, ganin gari shine abun da ya shigo dani part naku" cikin girmamawa Aunty ta amsa masa da to, ita kuwa Aafia ko ajikin ta kamar bata gan shi ba, sai faman tura baki take, wucewa yayi ya fice daga palon, dan tun da suka nuna masa basa son shi a gidan ya daina shiga harkan su, idan sun masa magana fine ya amsa, idan kuma basu masa magana ba shima baya kula su, dan baya son raini ko kaɗan, ko part nasu bai cika shigowa ba, sai dai idan Abbi yana nan, sai ya shigo palo suyi hira, Abbi na fita shima zai fice ya koma part na shi, wato ɓangaren Irfan kenan. Bayan daddy ya fitane Aunty ta duɓi Aafia tace "Aafia me yasa zaku rinƙa yiwa kanin mahaifin ku haka? Babu kyau abun da kuke yi fa, ya kamata ku gyara kuyiwa kan ku faɗa domin baku san me gobe zata haifar ba, kuma kuna sane da tashin hankali da bawan Allah nan yake ciki, kamata yayi ku jashi a jiki dan ku ɗebe masa kewar rashin Jalila a tattare da shi, sannan kuma shima fa a matsayin mahaifi yake a gare ku ida.... Bata kai karshen maganar ba Aafia ta daga mata tsawa "Ke dallah kima mutane shiru, ina ruwan ki da rayuwar mu? Ba dai kanin mahaifin mu bane? Ai ba kanin tsohon ki bane, to dan haka ki shiga hankalin ki, ina buga miki last warning da babban murya, idan kika sake shiga harkana, wlh sai na miki illa, wawuya kawai yar datti!!" rai a matukar ɓace Aunty tace "Ke Aafia ina son ki shiga hankalin ki, ya issheki haka nan, ya isheki cin mutunci na a gidan nan in kyaleki, na gaji, wlh idan kika sake faɗa min wata maganar banza idan ranki yayi dubu sai na ɓata miki shi" Miƙewa tsaye Aafia tayi tana faɗin "Eyee a lallai yar talakawa kin sha jar miya, har ni kike wa last warning kenan, to wlh baki isa ba, in dai ni Aafia na haifu sai kin bar gidan nan yau!!" guntun tsaki Aunty taja kafin tace "To sai me? Dan na bar gidan ku sai me? Mutuwa zan yi ne dan na bargidan, ko kuma a'a aljanna ce ba zan samu ba idan na bar gidan, ai wlh da zaman wannan gidan naku gara mutun ya tabbata a gidan uban sa, yan iskan yara mara sa hankali, marasa tarbiyya, ku daga gani wlh uwarku ba hausa fulani bace , dan wanna bakin halin naku bayyi kala da na mu ba, amma ni ina mai baku shawara wlh kubi duniya a sannu, idan ba haka ba, watara na sai kunyi nadamar zuwan ta, ku mata ne, baku san ina aure zai kai ku ba" Rai a matukar ɓace Aafia ta nufi Aunty da niyar ta mare ta, cak Aunty ta riƙe hannun ta, yau fa hakurin mai hakuri ya kare, daman ance mai hakuri bai iya fushi ba, to wanna ma hake ne Wanke ta da wawan mari Aunty tayi a fuska, tare da daka mata tsawa "Dan baki da hankali sai kiyi yunkurin saka hannun ki a jikin mahaifiyar ki, matar baban ki?!!" tashin hankali Aunty fa ta fusata. Kokarin kwace hannun ta Aafia take daga riƙon da Aunty ta mata dan ta rama marin ta da aunty tayi, tureta aunty tayi ta faɗa sama sofa, sanna ta wuce da sauri ta haye sama abun ta, dan bata son tsayawa tayi faɗa da Aafia, yin hakan zubar da kai ne, sai dai kuma Aafia tana da burin hakan ko dan ta daki Aunty a ciki. Da gudu Aafia ta miƙe tabi aunty sama, sai dai kafin ta iso Aunty ta shige bedroom nata tare da murzawa kofar ta key, haushi kamar Aafia ta fasa ihu, kafa tasa ta shuri kofar da karfi sannan tace "Zaki fito ai, wlh sai kin yabawa aya zaƙin ta a gidan nan" hayewa saman gadon ta aunty tayi abun ta, ta kwanta tana mai jin bakin cikin abun da yake faruwa a gidan nan, Aafia ta kureta, ta kai ta bango, taso suyi zaman lafiya amma abun ya faskara, ba yadda za tayi dole ta fito ta karɓawa kan ta yanci kawai dan ta samu zaman lafiya kuma ta samawa ɗan da zata haifa ko ƴa yancin kan su a gidan baban su. Aafi kuwa palo ta koma tana ta surfa ruwan bala'i a kan aunty zata fito ta same ta, ba zata kyale taɓa. A ɓangaren Umaisha kuma, da zazzaɓi mai zafi ta tashi tare da kuka, lokacin ana kiraye kirayen sallar mangariba, Akil baya nan, ya tafi kai Aafia gida bai kai ga dawowa ba, ya wuce masallaci daga nan. Jin kukan Umaisha yasa Akila ta tashi ta nufi part ɗin Akil, lokacin Ammie ta bar palon ta koma bedroom nata, shi kuma Abba ya wuce masallaci. Tana shiga bedroom ɗin ta haye saman gadon kusa da Umaisha tana faɗin "Umaisha lafiya? Me ya same ki kike kuka? Ko dai yaya Akil ya miki wani abu ne? Ko kina son komawa gida ne?" Kuka kawai Umaisha keyi, bata samu damar samun bakin magana ba "Dan Allah akila kiyi shiru kinji? Tun ɗazun fa nake ta murna ina jiran ki tashi daga barci muyi hira, tun da na dawo school yaya Akil ya sanar min ya ɗauko ki, kuma ke yanzu matar sace, sai murna nake tayi, ina fatan ki tashi daga barci muyi hira, amma shi ne kuma zaki tashi kina kuka? Dan Allah ki dai na kuka ki faɗa min, idan ma yaya Akil ne ya miki wani abun to yanzu zan kira yaya Imran a waya na faɗa masa, kuma zai rama miƙi, dan yaya Imran yana da adalci" nan ma Umaisha bata kula taba, ci-gaba da kukan ta tayi kawai, ita ka ɗai tasan me take ji a jikin ta, ganin haka yasa Akila ta sauƙo daga gadon, ta fice daga ɗakin da sauri, ta nufi bedroom ɗin Ammie. Zaune bakin gado ta samu Ammie, da sauri ta tafi ta faɗa jikin ta tana faɗin "Ammie dan Allah kizo ki lallaɓa Umaisha tayi shiru, sai kuka take taki yin shiru, ban sane me ya same taba" guntun tsaki Ammie taja kafin tace "Kije kice mata, ta tashi ta tafi gidan su tun kafin nazo na same ta a wajen" zaro ido Akila tayi tare da turo baki tace "Haba Ammie yaya Akil fa yace matar sa ce, to ya za'ayi kuma ta tafi gida?" "Waye yace miki matar sace? Ba matar sa bace, shi ba ajin irin wayan nan yaran bane, ki tashi kije ki ce mata ta wuce ta tafi gida tun kafin nazo na karya ta, dan haushin suma nake ji gaba ɗaya" Kukan shagwaɓa Akila tasawa Ammie, tana ɗan bubbuga kafar ta a jikin gadon tana faɗin "Haba Ammie, to ai ko ba matar yaya Akil bane yar uwar mu ce, kinga kuwa zata iya zama a gidan nan" Jin Akila tace yar uwan suce yasa Hajiya ta miƙe a fusace ta fito ta nufi part ɗin Akil. Da sauri Akila ta miƙe tabi bayan ta Kamar yadda Akila ta bar Umaisha haka Ammie ta shigo ta same ta, tsawa ta daka mata "Ke tashi ki wuce gidan uban ki, ban son munafurcin banza" shiru Umaisha tayi bata amsa mata ba, kukan ta kawai take. A fusace Ammie ta haye saman gadon tare da yaye bargon da Umaisha ke lulluɓe, ta riƙon ta, ta miƙar da ita tsaye tana faɗin "To wuce a kai kaya ma sauki" kasa tsayuwa Umaisha tayi, Ammie na sake ta, ta zube a kan gadon tare da kara sautin kukan nata, daidai lokacin Akila ta shigo ɗakin, kamar zatayi kuka tace "Ammie dan Allah kiyi hakuri ki barta kinji?" Ammie bata kula taba, sai ma kara mikar da Umaisha tayi, ta jata, sai kokarin faɗuwa kasa Umaisha take saboda jikin ta ba kwari, kuma ba zata iya taka kafar ta ba, saboda azaban da take ji, sai kukan wahala take abun gwanin ban tausayi. Kai tsaye waje Ammie ta nufa da ita, tana jan ta kamar wata rago, sai kuka Akila take tana addu'ar Allah ya kawo yaya Akil ko Abba. Ammie tana zuwa bakin kofar Palo, ta tura Umaisha waje tana faɗin "Kar na sake ganin kafar ki a gidan nan" tana turata ta tafi sai saman kirjin Akil ta faɗa, yanzu ya dawo daga masallaci yana kokarin shigowa kenan Umaisha na kokarin sulalewa kasa daga kirjin nasa, yayi saurin riƙota yana kallon Ammie dake tsaye a bakin kofa tana kallon sa Kasa tsayuwa Umaisha tayi dan kafar ta babu kwari, sai kerma jikin ta keyi, dawo da kallon sa kan fuskar Umaisha ɗin yayi, kasa kasa yace "I'm so so sorry" ya kai karshen maganar tare da ɗaukan ta cak, ya juya ya bar wajen, ya nufi motar sa da ita ba tare da yace da Ammie ko uppan ba, dan baya son jan magana da ita a kan Umaisha, yasan halinta sarai zata iya yi masa baki a kan hakan, ta raba shi da Umaisha, shiyasa baya son maganar Umaisha ta haɗa su juyawa ita ma Ammie tayi ta koma cikin Palo, tana jan guntun tsaki, a tunanin ta Akil zai mai da Umaisha gida ne. Ita kuma Akila tana ɗakin Akil tana kukan ta. Kai tsaye asibiti Akil ya wuce da Umaisha dan yaji jikin ta da zafi sosai, yan gwaje gwaje aka mata, sannan aka basu bagunguna, ya ɗauko ta suka dawo gida. A palo ya samu Ammie da Akila suna zaune, Abba bai dawo ba, bai yiwa kowa magana ba, ya wuce ya nufi ɗakin sa, "Akil kazo ka ci abinci" cewar Ammie, a takaice yace "Bana ci, na ƙoshi" yayi maganar ba tare da ya tsaya daga tafiyar da yake ba, "Ka fitar da yarinyar nan daga gidan nan nace ko?" Ammie ta sake yi masa magana, shiru yayi bai tanka ba, ya wuce bedroom nasa. Saman gado ya kwantar da Umaisha, wadda take fitar da numfashi da kyar saboda wahala, bargo yaja ya rufa mata sanna ya fice ya dawo palon Kusa da Ammie ya zauna yana faɗin "Ammie me yasa yanzu baki son farinciki nane ne? Me na miki? So kike na mutu ne eh Ammie na?" Zaro ido tayi kafin tace "Haba Akil kasan me kake faɗe kuwa? Nice bana son ka? Idan ni bana son farincikin ka waye kake tunanin zai so farincikin ka?" Kallon Akila dake zaune tayi shiru tana tunani, tasha kuka ta koshi, dan ita a tunanin ta Ammie ta kori Umaisha ɗin ce "Heartbeat tashi kije ɗaki bari muyi magana" Akil ya faɗa yana tsare Akila da ido, tun bai kai karshen maganar ba ta miƙe ta wuce bedroom nasa wajen Umaisha, dan bata da burin da ya wuce ta gan ta tare da yan uwan ta. Dawo da kallon sa yayi kan Ammie cikin nitsuwa yace "Ammie na faɗa miki ina son matata, kuma ita ce farinciki na, me yasa baki son hakan? Me ta miƙi? Na san bai wuce kice abun da ya faru tsakanin ku da baban ta, da kuma su bappa Husaini bane, to ita me nata a ciki, kinga ai ita bata san komai ba, kuma da wuya ma idan ta san labarin abun da ya faru kafin a haife mu, dan Allah Ammie ina son kiyi min wannan alfarma, ki yafe wa family'n Abbana komai ya wuce kinji ko?" Ya kai karshen maganar tare da riƙo hannun ta yana kallon cikin idon ta "Akil, Akil, Akil, sau nawa na kira sunan ka?" Shiru yayi yana kallon ta "Ba zaka bani amsa ba, nace sau nawa na kira sunan ka?" "Sau uku kika kirani Ammie" ya bata amsa, "To wlh ka fita ido na, karka sake min maganar su Hussaini a gidan nan, ita kuma yarinyar tun da kace ita kake so, kaje kai kasani da ita can, in dai family'n Abban kane da kan ka ma zaka guje su ba sai wani yace ka barsu ba" murmushi yayi kafin yace "Shikenan Ammie in dai kin yarda na zauna da ita shikenan ba damuwa ai" kawar da zancen tayi da cewa "To ka tashi ka ɗauko abinci ka kaci" to kawai ya amsa da shi tare da miƙewa ya nufi saman table ya ɗauki abinci kula ɗaya da plate ɗaya tare da spoon shima ɗaya, ya wuce bedroom na sa, binshi da kallo Ammie tayi, kasa kasa tace "Ba zan taɓa bari ka zauna da yarinyar nan ba, dan bana son ta, kuma bana kaunar iyayen ta, dole ka rabu da ita" Da sallama ɗauke a bakin sa ya shiga cikin bedroom na sa, Akila na zaune saman gado tana rarrashin Umaisha dake ta faman kuka har lokacin. "Heartbeat ɗauko min Yoghurt a Palo" turo baki Akila tayi kafin tace "Yaya Akil ba haka zaka ce ba, kace Heartbeat tashi ki fita min a ɗaki" murmushin yayi kafin yace "Ni na isa in ce ki fita min a ɗaki ne? Yoghurt fa kawai nace ki ɗauko min" "Yaya Akil yaushe ka fara shan Yoghurt ban sani ba? Kai da ko tea da madara baka sha saboda karni shine yau zakace na ɗauko maka Yoghurt, na sani ba wani Yoghurt kawai korata kake yi" ɗaga mata gera ɗaya yayi yana faɗin "To tun da kin gane me kika tsaya yi ware da wuri" dariya tayi tana faɗin "Ba damuwa yaya Imran ya kusa dawowa ai, idan ya dawo ba zan sake zuwa nan ba, kuma shi nasan ko ya auri Aunty jelly ba zai koreni a ɗakin saba" "oho dai tashi ki tafi" yayi maganar yana kokarin hawa saman gadon, bayan ya ajiye musu abincin su saman table dake cikin ɗakin, Da sauri Akila ta diro kasa daga saman gadon tana faɗin "Aunty Umaisha Amarya sai da safe, yaya Akil mun ɓata da kai" shiru ya mata, dan bai son biye mata, so yake ta fita ta basu waje. Tana fita ya sanya hannun sa ya tallaɓo Umaisha yana faɗin "Sorry tashi kici abinci kisha magani" cikin kuka tace "Na koshi" girgiza kai yayi yana faɗin "a'a ban yarda ba ki tashi kici" ba dan taso ba, haka ya miƙar da ita zaune ya rinƙa ɗura mata abinci tana ci dan dole Bayan ta gama ya bata ruwa ta sha, sannan ya mai da ita ya kwanta, ya sauƙo ya wuce toilet dan yayi wanka yazo ya gabatar da sallar issha da bai samu yayi ba, sakamakon kai ta asibiti da yayi. Bayan yayi Sallah ne ya haye gadon kusa da ita ya kwanta, yana faɗin "I'm sorry kinji?" Shiru ta masa ba tayi magana ba na ɗan lokacin kafin tace "Ka mai dani gida kada Abbi ya neme ni" juyo da kallon sa yayi kan fuskar ta "Already na kira bappa a waya na sanar masa da nazo na ɗauke ki daga school kina tare dani" mamaki ne ya kamata tace "Abbi na fa wanda ya haifeni" ya gane me take yiwa mamaki, wato ya za'ayi Abbi ya yerda ya ɗauke ta su tafi su kwana, bayan ba aure sukayi ba, shine abun ya kulle mata kai "Eh Abbin maki fa, bakin san cewa ke matata bace ko?" Shiru ta zuba masa ido tana kallon sa "To ki rufe idon ki ya isa haka kallon nawa, karki haifa mana baby mai kama dani, zai fi kyau ki haifi mai kama dake, kiyi barci da safe zamuyi magana" ya kai karshen maganar tare da sanya hannun sa ya rufe mata ido, mamaki ya hana ta magana ta kwanta shiru, da haka barci ya ɗauke ta. Shima shiru y kwanta har barci ya ɗauke sa. Ammi kuma tana can palo tanan saka yadda za tayi da Akil dan ya rabu da Umaisha, Akila kuwa tana fita ɗakin Akil nata ɗakin ta wuce dan taje ta kira daddyn Jelly dasu Abbi, yayan Imran, haka take, kafin tayi barci sai ta kira kowa daga cikin yan uwan ta, har da Abla sun sha hira sannan take barci. Muleƙo Washington DC mu dawo Yau ban haɗa muku page biyu bane, sakamakon bana jin daɗin jikina, shiyasa ban samu damar yi muku editing 2 page ba, amma In Sha Allah gobe zan biya Karku manta idan Allah ya kai mu ranar Jumma'a da rai da lafiya, zan ɗauki hutu na ɗan wani lokaci, dan in ɗan huta in samu kwakwalwata tayi fresh, in ji daɗin zubo muku zafafan page's masu tashin kai, ina godiya sosai da sosai Allah ya bar zumunci 🥰 Masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu . 💞💞TRIPLET'S💞💞 # BOOK 2📚📙✍️ 💔💔Episode 5-6💔💔 💔RIMSHA💔 💞💞Washington DC💞💞 09:30am A hankali yake sako kafar sa a saman benen yana tafiya kafar baya son taka kasa, jikin sa gaba ɗaya a mace, sai wani cizan lallausan laɓɓan sa yake, jikin sa na sanye da Ripped Jeans black color, da white Round neck t-shirt, kayan sun masa kyau sosai da sosai, kamar dan shi akayi su, kyawawan fararen kafafunsa na sanye cikin Hermes Birkenstock sandal fari tas kalar rigan sa, ya ɗaure wannan kyakkyawan dark black curly hair nasa a bayan, ya bar wanna ɗan guntu a gaban goshin sa, sai tashin fitinannen daddaɗar kamshi yake, kamar anyi ɓarin turare. Palon kasa shiru babu kowa kasan cewar already sun riga sun breakfast kowa ya kama harkan gaban sa, masu barci sun koma barci, masu fita sun fice yawon party da sauran su, dan basu da aiki da ya wuce wannan. Jiki na kerman tsoro bodyguard dake cikin palon suka fara ɗaga masa gaisuwa ta hanyar ɗaga hannayen su, suna sara masa, ko kallon in da suke bai yi ba, ya sa kai ya fice daga palon. Already an jera motocin da zasu fita, shi kawai suke jira. Yana fitowa jibga jibgan sojojin sa suka fara sara masa, wucewa yayi kai tsaye ya nufi motar sa kirar Bugatti La voiture, da sauri wani jibgegen soja yazo ya buɗe masa motar, ya shiga ya zauna. A guje sauran sojojin suka haye saman bayan nasu motoncin. A jere motocin suka tashi, suka fice daga gidan, tare da sakin jiniya, tamkar yaki zasu tafi. Kai tsaye white house suka nufa. Kun dai san yadda white house yake ba sai na tsaya dogon bayani ba, ko ta ina sojoji ne kewaye a cikin gidan, hannayen su riƙe da manya manyan bindigu masu rai da lafiya, ga yan sanda ma ba'a barsu a baya ba, suna tsai tsaiye. His excellency mr president yana cikin fadan shugaban kasa, kai tsaye wajen sa Romeo ya nufa yana taku irin na manyan jarumai sadaukan yaki, duk in da ya wuce sai sojojin wajen sun sara masa, jibga jibgan sojojin sa huɗu ne suka take masa baya har zuwa bakin kofar shiga cikin fadan, a daidai wajen suka dakata, shi kuma ya shige ciki. Fadan shugaban ƙasa waje ne mai girman gaske, duniya ne guda, cikin fadan ɓangarori ne daban daban, sannan akoi ofisoshin da dama a ciki, kaɗan daga ciki, akoi office ɗin shi kan shi His excellency mr president, sai office na vice president, sai na secretary sa, da dai sauran su, sannan akoi manya manyan kujeru masu rai da lafiya, launin ja set nasu daban, haka zalika launin blue suma set nasu daban, akoi abubuwa da dama wadda faɗen su da baki ba zai yiwu ba, sai dai ku kawata su a ran ku, a takaice dai fadan shugaban ƙasa ya haɗu iya haɗu, domin tsayawa zayyana muku yadda cikin fadan yake zamu jima bamu gama ba, dan fadan dunaya ce guda. Kusa da His excellency lion ya wuce yaje ya zauna, kallon sa cike da so da kauna His excellency yayi yace "My dear what is happening, naga kamar ranka a ɓace?" Ba sai na faɗa muku ba, kun dai san da turanci suke magana. _Shiru lion yayi na yan sakanni kafin yace "kasan komai uncle ba sai na sake faɗa maka ba, Ina son a matsayin ka na president kayi magana da president na Spain, ina son a bincika min bayan James ya sauƙa daga jirgi ina ya nufa, shin ya hau wani jirgin ne ko kuma ya shiga cikin kasar ne, idan ya shiga cikin kasar wani gari yaje, uncle ina da ayyuka dayawa, ba zan iya zuwa Spain yanzu ba, kuma ina da tabbacin duk in da James yake yana cikin damuwa da tashin hankali, na kasa samun nitsuwa, ina jin har cikin zuciya ta, James na neman taimako na, a halin da nake ciki yanzu, ba zan iya fita daga Washington DC ba, saboda matsawa ta zai iya sanya mu rasa jigo na rayuwar mu, wato daddy, a situation ɗin da daddy yake yanzu, yin nisa da shi babban haɗari ne, da gara idan Michael yana da lafiya ma, zai iya ɗebe masa wasu matsaloli da kuma damuwa na rashin mu ni da James, amma ace babu ko ɗaya daga cikin mu, abune mai wuya a gare shi ya iya zama, jiya nayi tunanin zanje Spain da kai na, zuwa wayen gari na sake wani tunanin kuma, hakan ba mai yiwuwa bane, jiya ne kaɗai daddy bai ga James ba, ya damu sosai, yau da safe tun karfe 6 yazo bedroom na, wai sai na kira masa James a waya dan yayi mafarkin sa, da kyar na lallaɓa shi ya hakura, idan aka ci-gaba a haka, tofa akoi babban matsala, ka sani kuma ba sai na sake maimai ta maka ba" shiru His excellency ya ɗan yi kafin yace "Yes you are right, but kana ganin wani abune ya faru da James?" "No uncle i don't know, ban sani ba, kuma bani da amsa a kan hakan, sai dai ina ji a jikina hakan ne" shafa dark black curly hair sa His excellency yayi yana faɗin "I really like William family so much" ya kai karshen maganar tare da mannawa lion kiss a kumatu "Same here uncle we like you" ya faɗa shima yana mannawa kakan nasa kiss a goshi, murmushi His excellency yayi kafin yace "My lion zanyi yadda kake so, fata na dai James yana cikin koshin lafiya, sanna kuma ka kula da William da Michael sosai, yanzu nauyin su na kan ka, kada ka bari William ya san abun da ya samu Michael, idan hakan ya faru zamu iya rasa shi, ba tare da mun shirya ba" miƙewa Romeo yayi yana faɗin "Maybe in dawo yau maybe kuma sai gobe, duk yadda kayi da president ɗin Spain zan kira ka zuwa dare" ya kai karshen maganar tare da wucewa, ya nufi hanyar fita daga fadan, sai fatan Alkhari His excellency ke masa, a zuciyar sa yake amsa fatan alkharin da kakan nasa ke masa. Yana fitowa sojojin da suka take masa baya zuwa bakin kofar fadan, suna tsaye a wajen, yana fita suka bi bayan sa zuwa wajen mota. Kamar yadda suka zo, haka jerin gwanon motocin suka tashi, suka bar white house, suka nufi *Madstar Washington hospital center*. Alhamdulila ba laifi jikin Michael ya fara kyau, saboda kwararun likitoci da suka tsaya, tsayin daka wajen ganin sun bashi kulawa, ga kuma kayan aiki masu kyau, inganci, da kargo. Sun cire masa kayan jikin sa, sun sanya masa kayan asibiti na majinyata. Kusa da shi lion yazo ya tsaya yana kallon yadda fuskar sa ta sauya kamar ba Michael Triplets ɗin sa ba, ko motsi baya yi, da alama har yanzu bai san in da kan shi yake ba. Romeo ya ɗauki tsawon lokaci yana kallon sa kafin ya juyo yana kokarin fita daga ɗakin idon sa ya sauka kan diamond watch nasu na Triplets na Michael, ɗaure saman wani kyakkyawan plate irin na ajiye zobe abun hanu na majinyata, da likitocin suka cire masa ne, sai suka ajiye a wajen, hannu Romeo ya kai ya ɗauki watch ɗin, ya nufi hanyar fita daga ɗakin, yana yiwa Michael addu'ar samun lafiya. Gida lion ya koma bayan ya bar hospital, dan baya son yin nisa da dad, kasan cewar ba Michael kuma ba James, idan shima yayi nisa da shi za'a iya samun matsala. Babu kowa a palon kasa, sai daddaɗar kamshi air freshener da sanyin Ac dake tashi, ko'ina a palon a gyare yake tsab, kamar sabbin kaya aka zuba, wucewa yayi ya haura sama, kai tsaye bedroom ɗin dad ya nufa. Daddy na kwance saman gado, yana kallon News a jikin makeken Tv plasma dake manne a bango a cikin ɗakin, kusa da shi Romeo yaje ya zauna yana faɗin "Good afternoon dad" murmushi dad yayi kafin yace "My lion how are you doing?" Shiru Romeo yayi bai amsa ba, dan shi ba hira yazo yi da dad ba, kawai yazo su zauna ne dan kar ya fara sa masa rigiman ya kira masa James ko Michael, dan dad idan ya fara rigiman shi kamar ƙaramin yaro haka yake zama saboda tsufa, sannan kuma ga ciwo dake damun sa. Ganin Romeo yayi shiru ya zubawa Tv ido kamar mai kallo ne, amma kuma a zahirin gaskiya ba kallon yake ba, kawai dai yayi zubawa Tv dara daran idon sa ne, wani tunani daban yake yi "My lion wai up till now Michael bai dawo bane? Ko dai ya tare wajen His excellency ne" ba tare da ya kalli dad ba yace "in the evening zai dawo" "What about James?" Nan ma ba tare da ya kalli dad ba yace "Sai bayan two weeks ko three zai dawo" zaro ido dad yayi ya miƙe zaune yana faɗin "What? Wai me yaje yi a Spain ɗin ne daman?" Sai lokacin Romeo ya juyo da kallon sa kan dad "Ba wani aiki ne mai wuya ba" ya bawa dad amsa, dad na komarin sake yin magana yayi saurin cewa "No dad, please stop asking me these silly silly questions, don't worry they will come back soon" shiru dad yayi ba wai dan yaso hakan ba, sai dan kawai lion ya zauna tare da shi, yasan cewa idan ya cika yiwa lion tambayoyi da magana, yana sanya shi yin magana to zai tashi ta fice ne, kuma dad ba zai so hakan ba, dan Romeo baya zuwa ya zauna tare da shi haka, idan kaga Romeo yazo wajen dad to fa sai dai in drugs na shi zai bashi, haka kawai ba zaka taɓa ganin sa a wajen dad ba, yauma da dalilin zuwan nasa, bai son dad yazo yayi ta takura mashi a kan ina James ina Michael shiyasa yazo rufe wa dad baki. Sun jima suna zaune shiru sun tsare Tv da ido, dad yana kallo da gaske, shi kuma Romeo yana duniyar tunani. A gefe guda kuma, Musharraf ya kara samun lafiya sosai da sosai, sai dai ɗan kwana biyu da James baya nan, ya shiga damuwa sosai, saboda babu mai yi masa alwala, sai dai shi ya lallaɓa ya rarrafo yaje ya ɗauki ruwa yazo yayi alwalan da kan shi, haka zalika babu mai ɗaura shi saman kujera ya kai shi toilet, abun ya fara damun sa sosai, babu wanda zai iya tinkara ya sanar wa damuwan sa, dan shi gani yake duk yan gidan danja ne, babu mai saukin kai a cikin su. To bari dai mu leƙo My Rimsha kuma muga wani wai na take toyawa. 💔💔RIMSHA💔💔 Makale Kausar take saman bishiyar gwaiva tana tsinko musu, ita kuwa Rimsha tana tsaye a kasa sai aukin cewa "Kausar ga wani nunanne ta can" bata san ya wuyar hawa bishiya yake ba, ci kawai ta sani, sai bakin iya magana, dan yanzu Rimsha ta kware wajen iya magana zaman ta da Ayla da Kausar, dan Ayla yarinyar akoi ta da surutu, amma mafiyawancin surutun nata mai amfani ne, ita kuwa Kausar akoi murya, kunsan dai yadda yarbawa suke, idan suna magana sai ka rantse da Allah faɗa suke, gata bata da jumiriyar yinwa, kundai san halin yarbawa da bala'i cin abinci basa wasa da ciki, shiyasa koda suka fito daular mutuwa ta kasa tafiya, sai da Rimsha ta goyata, saboda bata iya jurewa yinwa ko kaɗan, idan kuma taci ta koshi, tofa akoi iya magana, gata da karfi kamar doki, dan ko a gaɓɓai tafi su Rimsha, kuma tafi su ƙiba sosai, wahalar daular mutuwa ya mai da ta siriri ya, amma Kausar mace ce mai ƙiba, sak yarbawan haka take. Tana makale saman bishiya tana ta faman gabzan gwaiva, daɗi da santi ya ɗebe ta sai surutu take hankalin kwance "Meesha yau baki zana masoyin mu GAR ba" Kausar ta faɗa daga saman bishiya tana dariya, murmushi Rimsha tayi har sai da dimple nata ya lotsa, wani daɗi taji ya ziyarci cikin farfajiyar zuciyar ta, Kausar ta taɓo mata in da yake mata kai-kayi, ita ka ɗai sai murmushi take, tana cin gwaiva tace "Ke dai bari Kausar am, ina nan zuwa in zana shi, yanzu har jikin bishiya zan rinƙa bi ina zana shi, dan wannan daji tasan da zaman mu" dariya Kausar tayi kafin tace "Kai Meesha ina da shawara" cikin sauri Rimsha tace "Shawarar me? Faɗi ina jin ki" gefowa Rimsha gwaiva tayi kafin tace "Me zai hana mu tara kuɗi muje wajen wannan mutumi mu gan shi ido da ido" Rimsha bata san lokacin da dariya ya kubce mata ba, har da faɗuwa kasa, zuba mata ido Kausar tayi tana kallon ta da mamaki, bata taɓa kallon Rimsha na irin wannan dariya ba, sai dai murmushi kawai, amma yau Rimsha ce saboda dariya har da faɗuwa kasa Da dai Kausar taga Rimsha fa bata da niyar dakatawa daga dariyar da take, sai tace "Haba Meesha menene kuma abun dariya?" Har wani dafe ciki Rimsha take saboda dariya, ga hawayen dariya nan wani na bin wani a kumatun ta, Kausar kuwa dataga Rimsha taki kulata sai ta saka kuka tana faɗin "Wlh idan baki dai na dariyar nan ba mun ɓata, haba dan Allah mahaukaciya kika mai danine?" Sai da Rimsha taga Kausar ta ɓata rai da gaske tana kuka, sai ta dakata da dariyar nata, ta ɗago ta dubi kausar, murya ɗauke da dariya tace "Sorry Aunty yar lukuta, ai ke ɗin ce santin gwaiva ya ɗebeki sai faman sakin layi kike da zance, ke kwata kwata kin manta aina muke" A kule Kausar tace "sai dai sama da yar lukuta ba yar lukuta ba" guntse dariya Rimsha tayi dan tasan in tayi dariyar nan, bazasu wanye lafiya da Kausar ba, kuma tana sane da gangan ta kira ta da yar lukuta, tasan ba abun da Kausar ta tsana biyun wannan suna Aunty yar lukuta, baba da Mustapha suka sa mata sunan, suma dan ba yadda zatayi da sune yasa take amsa wannan suna idan sun gaya mata. "Me ya baki dariya to?" Kausar ta tambaya tana kara haurawa saman bishiyar da kyau, dan ta hango wani gwaiva nunanne a can sama, sake kwashewa da dariya Rimsha tayi dan Kausar ta tuna mata da abun da ya saka ta dariya ɗazun Saboda haushin dariyar da Rimsha take, tsinko gwaiva ɗanye Kausar tayi ta sai ta tsakiyar kan Rimsha ta kwala mata, ihu Rimsha tasa tayi baya tana faɗin "muguwa Aunty yar lukuta" sake tsinko ɗanyen gwaiva Kausar tayi ta jefo mata, a sukwane ta matsa a wajen tana faɗin "kin dai yi na farko kinci riba, amma ba zaki kara ki ci riba ba" harara Kausar ta wurga mata tana faɗin "Allah idan baki faɗa min abun da yasa kike min dariya ba, sai na sauko kasa na fasa ciro gwaivan, sai dai mu wuni da yinwa" Fuska ɗauke da murmushi Rimsha ta fara magana "Ai kece da abun dariya Kausar, idan ban da ke, muda muke wannan kungurmin daji, wadda bamu san ina muka nufa ba, wai kike maganan mu tara kuɗi mu tafi America, mu zabiya uwar yawo, to amma uban waye zai bamu kuɗi a dajin nan? Kuma ma dakike wannan magana an faɗa miki GAR mutun ne kamar kowa? A'a GAR ba mutun ne kamar kowa ba, manyan shuwagabannin ma kafin su samu ganin sa sai sun shirya, shifa ba iya soja bane kawai, jikane ga shigaban kasa mai mulki yanzu, bayan haka, shi ba irin sojan da kike tunani bane, the general of the army fa aka ce miki, hmmm Kausar baki da lafiya, wai mu tara kuɗi mu tafi wajen sa, to ki bari muci mu koshi mu samu muga iyayen mu da yan uwan mu tukun nan, kafin muyi tunanin tsiyar da zamu zuba gaba, amma yanzu mu bamu da wani bakin magana, daga kikaji zaƙin gwaiva kawai ki fara sakin zance, kefa daman haka kike, da kinci kin koshi kin gane kanki shikenan kuma, sai ki saki layi kita zuba kamar kanya, zance mara kan gado.....bata karisa maganar ba Kausar ta faɗo kasa dim daga saman bishiyar nan, tana ihu kamar makoshin ta zai yage, a sukwane Rimsha tayi kan ta tana faɗin "Kausar lafiya? Me ya faru?" Ina Kausar bata saurare taba, ta hau cire kayan jikin ta, tana yasar wa a kasa, tana yi tana ihu _Sosai Rimsha ta ruɗe tana faɗin "Kausar menene?" Ayya Rimsha akoi tausayi, har ta fara yi mata hawaye tun bata ji me ya faɗo da Kausar ɗin ba. Tsab Kausar ta cire kayan jikin ta, ta zubar a kasa, sai sosa jiki take tana ihu, Allah sarki gaba ɗaya fatan bayan ta, yayi ruɗu ruɗu da cizon wayan nan mayun (ant) cinnakun ko ince kwarkwasa, ga cizon nasu da bala'i zafi, sai ya ɗauki sati wajen na maka zogi, gashi kuwa sun cijeta sosai da sosai, ruɗu ruɗu cizon nasu ya fito a bayan ta, sai kuka take tana sosa wajen, wani wajen ma idan ta sosa shi jini yake. Riƙe hannayen ta Rimsha tayi tana faɗin "Kiyi hakuri Kausar, ki dai na sosawa kinji? Kinga idan kika sosa wajen yana yin jini" rungume Rimsha tayi tana mutsu mutsu, saboda azaban zafin da yake mata "Meesha dan Allah ki barni na sosa kinji? Wlh zafi yake min, ga kuma bala'i kai-kayi" tayi maganar dakyar saboda kukan da take, rungume ta Rismha ma tayi tana ɗan shafa mata bayan nata a hankali tana faɗin "A'a Kausar kiyi hakuri ki daure kinji" kankame Rimsha tayi tana jin zogin har cikin ranta, yarinya abun tausayi, wayan nan mugayen abu duk sun kunbure mata baya. Sun jima tsaye a wajen Rimsha na shafa mata bayan nata tana mata addu'a tana tofa mata, da kyar suka samu raɗaɗin ya lafa. Sakin Kausar ɗin Rimsha tayi ta nufi riga da zanin Kausar da ta cire yake jefe, ta ɗauko ta karkaɗe mata su sosai, sannan ta dawo ta riƙo hannun ta tana faɗin "Kiyi hakuri kinji" shiru kausar tayi ta kasa magana saboda azaba, hannun juna suka riƙe suka ɗan matsa daga wajen bishiyar. Can ɗan gefe suka tsaya, Rismha ta sanya mata rigan ta, sai dai bata ja mata zip ba, saboda bayan nata ya samu iska, haka ta ɗaura mata zanin ta, tana ta yi mata sannu, daman Kausar akoi ta da saurin kuka, kuma idan tayi kukan duk sai idon ta yayi luhu luhu kamar panke. Haka suka daure suka ci-gaba da tafiya suna hira, In da sukayi kuskure wajen tafiyar nasu, tun da suka miƙi hanya ɗaya wato yamma basu ɗauki wani kwana ba, tafiya kawai suke a miƙe abun su, kuma suna sa ran ganin gari tab lallai, yau tsawon kwana uku suna wannan tafiya, amma ko alamar gari basu gani ba, sai ma kara nutsawa suke cikin daji mai girma da faɗin da basu iya ganin karshen sa, basu san ina suka nufa ba, shin ta gabas suke tafiya ne ko ta yamma, basu san ta ka mammen a wani kasa ma suke ba, su dai kawai tafiya suke suna burin fita cikin wannan bakin dajin, Allah ma ya tsare suna addu'a sosai, tun da suka fara tafiya basu haɗu da wani mugun abuba, haka idan sun tashi yin Sallah basu san gabas ba, kawai in da sukaga ya dace tanan suke kallo a matsayin gabas suyi Sallah. Maraice ya fara shiga, irin bayan la'asar ɗin nan, rana yayi sanyi, tafiya suke suna hira da dariya, ita dai Kausar daurewa kawai take, tana biyewa Rimsha suna hira, amma harga Allah tana jin zafin jikin ta sosai, ga bayan nata sai kaya ɓaro ɓaro cizon cinnakun yake. kasan wani katon bishiyar ɓaure mai cike da koren ganyen damuna, a nan suka zauna Kausar na tsokanan Rimsha wai har ta fara yin fresh, dajin nan ya karɓe su, ko dai suyi zaman sune kawai, sun zama yan daji, hararar wasa Rimsha tayi mata tare da ɗaukan wani ɗan karamin sanda, ta ɓare ɓawon jikin sa tas, sannan ta ta fara zanen fuskar GAR a jikin wannan bishiyar ɓauren, kasan cewar lokacin damuna ne, jikin bishiyar akoi taushi sosai, hakan ya bata daman zana katon fuskar GAR, zanen kuma ya fita sosai, kamar ka kira shi ya amsa, yayin da Rimsha ke zana shi ta wannan ɓangare ita kuma kausar tana zana shi ta ɗayan ɓangaren. Sas suka zane jikin bishiyar nan da fuskar lion masoyin Rimsha, su dukkan su sai murmushi suke kamar wasu taɓɓaɓu, ita dai Kausar ba laifin ta bane, Rimsha ta koya mata, ance zama da maɗaukin kanwa shike kawo farin kai, ita kuma Rimsha laifin zuchiyar tane. Har ta kai ta kawo, duk in da suka zauna karkashin wata bishiya, sai sun zana fuskar GAR a jikin wannan bishiyar kamar ba lafiya ba, wani lokaci ma ba zama zasu yi a kasan bishiyar ba, kawai zanen suke yi su wuce idan bishiyar ta musu kyau. Sai da suka ga yamma na daɗa yi sosai sannan suka miƙe suna murmushi kamar ba lafiya ba, suka ci-gaba da tafiya suna hira. Sunzo zasu wuce wata bishiyar kashu, Kausar ta tsaya tana tsinko kashu dake ta kasa kasan bishiyar, kasan cewar bishiyar tana da manyan rassa da sukayi kasa, ita kuwa Rimsha ta tsaya daga gefe tana bin dajin da kallo, dan bata jin yinwa, kuma ita bata cika cin abinci sosai ba, sai su wuni sau ɗaya zataci fruits, sai aukin shan ruwa. Kamar a mafarki Rimsha ta hango wani yaro, wadda ba zai wuci shekara biyu ba, yana zaune kusa da wata bishiya, da sauri ta karisa wajen tana mamaki Ɗaga kan ta tayi tana kallon yadda garin yayi, yamma yayi, to me ya kawo wannan yaron kuma nan? Ta tambayi kan ta, bata gama tunanin da take ba, taga wani zabgegen maciji mai kan faranti yana tunkaro yaron, a sukwane ta ɗauke yaron tana faɗin "Kausar ki bar ɗaukan kashu ɗin nan mu gudu maciji" Jin maciji yasa kausar tayi watsi da kashun dake hannun ta suka fara gudu. Sanadiyar wannan maciji, da wanann yaro, yasa suka canza akalar hanyar da suke tafiya a kanta da suka juya suka gudu ta gefe, saboda tashin hankali da razana da suka shiga. Sunyi gudu sosai, kamar ba zasu tsaya ba, sai sukaji daga can bayan su da karfi ana faɗin "Dare dare (kutsaya kutsaya)" ba musu suka tsaya, tare da juyowa suna haki kamar numfashi su zai ɗauƙe Wasu mutane su biyu mace da namiji, suka kariso wajen su da gudu, suna haki suma suna jan numfashi. Hannu matar tasa ta karɓi yaron ta dake hannun Rimsha tana faɗin "Nagode baiwar Allah" murmushi Rimsha tayi tace "Ba komai" Kausar sai faman haki take, saboda tafi Rimsha ƙiba sosai, da kyar ta iya buɗe baki tace "Ina macijin yake? Kun kashe shine?" mutumin da sukazo da matar ne yace "Eh na kashe shi" sai lokacin Rimsha ta samu damar sauke nauyayyar ajiyar zuciya saboda jin an kashe macijin, amma har lokacin kirjin ta na dukan uku uku, ta tsorata sosai da dajin, bata taɓa tunanin akoi irin wayan nan mugayen dabbobin a dajin ba. Juyawa iyayen yaron sukayi zasu tafi, Kausar tayi saurin ce musu "Dan Allah ku taimake mu, ku faɗa mana hanyar da zamu bi mu fita daga wannan bakin dajin" mutumin ne yace "Me ya kawo ku dajin daman? Ni na ɗauka ai ku yan kauyen dake gaban nan ne" cikin sauri Rimsha tace "A'a muba yan can bane, mu yan Katsina ne" mata da mijin har suna haɗa baki wajen cewa Katsina kuma? Eh Kausar ta basu amsa, girgiza kai sukayi kafin suce "Katsina na can bayan ku, kun baro shi, nan kuna kusa da Ilorin ne, baku da nisa sosai da ilorin" zaro ido Rimsha tayi zatayi magana Kausar tayi saurin cewa "Ta ina zamu bi dan Allah mu je cikin Ilorin, dan shine garin mu" da hannu mutumin ya musu nuni da hanya, sannan suka wuce shida matar sa suka barsu tsaye sunyi cirko cirko. Kallon Rimsha kausar tayi tace "Rimsha muje ko?" "Ina zamu je?" Rimsha ta tambaya kamar zatayi kuka "Gidan mu, bana faɗa miki ni yar ilorin bace" girgiza kai Rimsha ta farayi tana faɗin "A'a Kausar ni gida zan koma" riƙota Kausar tayi tana faɗin "ta ina zaki koma gidan? Ke da baki san hanya ba, kiyi hakuri idan mukaje gidan mu, sai asaki a mota ki koma gida" kwacewa daga riƙon da Kausar ta mata tayi, ta juya ta nufi hanyar da suka bi suka zo dan ta koma, tun da ance mata Katsina na baya sun baro shi. Karku manta idan Allah ya kai mu ranar Jumma'a da rai da lafiya, zan ɗauki hutu na ɗan wani lokaci, dan in ɗan huta in samu kwakwalwata tayi fresh, in ji daɗin zubo muku zafafan page's masu tashin kai, ina godiya sosai da sosai Allah ya bar zumunci 🥰 Masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu . 💞💞TRIPLET'S💞💞 💔💔Episode 6💔💔 💔💔RIMSHA💔💔 Kallon Rimsha kausar tayi tace "Rimsha muje ko?" "Ina zamu je?" Rimsha ta tambaya kamar zatayi kuka "Gidan mu, bana faɗa miki ni yar ilorin bace" girgiza kai Rimsha ta farayi tana faɗin "A'a Kausar ni gida zan koma" riƙota Kausar tayi tana faɗin "ta ina zaki koma gidan? Ke da baki san hanya ba, kiyi hakuri idan mukaje gidan mu, sai asaki a mota ki koma gida" kwacewa daga riƙon da Kausar ta mata tayi, ta juya ta nufi hanyar da suka bi suka zo dan ta koma, tun da ance mata Katsina na baya sun baro shi. Ganin Rimsha ta juya zata koma cikin wannan bakin wahala ne wato cikin dajin, hakan yasa Kausar tace "Meesha kin manta da wannan macijin da muka gani ko? To wlh akoi dubun sa a gaba, Allah ne ya tsare bamu haɗu da su a baya ba sai yanzu" a guje Rimsha ta juyo, tazo ta rungumi Kausar tana zare dara daran sleeping eyes nata, da suka shawuya sukayi ja. Kankame ta Kausar tayi tace "Muje ko? Nasan mun kusa isa gida" shiru Rimsha tayi ba tayi magana ba, sai dai ta saki Kausar suka ci-gaba da tafiya tare. Wannan hanyar da mutumin ya nuna musu, nan sukabi suka ci-gaba da tafiya, suna yar hirar su, amma dukkan su, zuciyar su sai dukan uku uku take saboda tsoron macijin da suka gani. Gari ya fara duhun mangariba, basuyi wani tafiya mai nisa ba, suka hango wani kauye, da sauri suka karasa kauyen, kauye ne sosai, dan ko wuta basu da shi, irin kauyen yarbawan nan wadda suke ɗan yin sa a cikin daji, wanda bazaka wuce samun gida 10 zuwa 15 a wajen ba, mafiyawanci ma family ɗaya zaka samu a wajen. Babu wanda ya kula su, kowa harkan gaban sa kawai yake, tsuru tsuru suka tsaya, ga mutane sun rasa waza su tunkara suyiwa magana, saboda fuskar kowa dake cikin wannan kauye a ɗaure basuga alamar wasa ba. Suna tsaye har wani matashin bayarbe yazo wucewa, cikin sauri Kausar ta masa magana da yarbanci "Sannun ka bawan Allah" kallon tsab ya mata, kafin ya dawo da kallon sa kan Rimsha, itama ya kare mata kallo, wasu putu putu yan datti da su, kamar wayan da aka kwato su daga bakin kura saboda squeezing da kayan jikin su yayi, wucewa yayi zai bar wajen ba tare da yayi musu magana ba Da sauri Kausar ta riƙo hannun sa tana faɗin "Please borda ka taimake mu" jin da gaske Kausar keyin yarbanci yasa ya dakata, dan da farko ganin Rimsha yasa ya gane ba yarbawa bane shiyasa ya wuce bai yi musu magana ba, amma yanzu da Kausar ta masa yaren yarbanci da kyau sai ya dakata yace "Me kuke so in muku?" Nauyayyar ajiyar zuciya Kausar ta sauke kafin tace "Mu baƙi ne, cikin Ilorin zamuje dare ya mana dan Allah wajen kwana muke nema" "Yarbawa ne ku?" Matashin ya tambaya, da sauri kausar tace masa eh ita bayarbiya ce, nuni ya musu da gidan sarkin kauyen nasu yace suje can, shine yake da alhakin bawa duk wani baƙo wajen kwana, godiya Kausar ta musu sannan suka wuce, shima saurayin ya wuce. In da saurayin nan ya nuna musu, nan suka nufa. Gidane mai ɗan girman, bukkoki ne a cikin gidan, kamar kubbakar fulani, kun san dai yadda kauyen yarbawa yake ba sai na faɗa muku ba, ko da baku taɓa zuwa kasan yarbawa ba, to nasan kuna gani a Tv ko kunaji a labari. Daidai zasu shiga cikin gidan sarkin kauyen wadda matashin ya nuna musu kenan, daga ɗan nesa suka hango wata yarinya tana zuwa, kallon juna sukayi kamar a mafarki har suna haɗa baki wajen cewa Ayla, da gudu suka tafi suka rungumeta, itama ganin su yasa ta taho da gudu, suka jungumi juna, tare da sakin kuka gaba ɗayan su, kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Sun ɗauki tsawon lokaci suna kuka rungume da juna, kafin su raba jikin su, suna kallon juna, Allah sarki Ayla, duk ta rame, ta dawo kamar kashi da rai, duk fuskar ta ya rame sosai, sai ido zaka gani, kasusuwa wuyar tannan kamar mutun ya sanya sabulu ya ajiye a wajen saboda rama, tayi duhu sosai, alamar tasha wahala sosai. Cikin kuka Rimsha tace "Ayla ina kika ɓace kika barmu? Mun juya bamu gan ki ba, mun koma baya nan ma bamu samu ganin kiba, ina kika bi?" Hannu Ayla tasa tana gogewa Rimsha hawaye tace "Zan faɗa muku, amma ba yanzu ba, sai mun nitsu" to kawai suka iya ce mata, sannan ta riƙo hannun Rimsha tana faɗin "muje gidan sarki" a tare suka jera zuwa cikin gidan. Sunyi Sa'a kuwa sarkin kauyen yana da kirki, duk da cewa krista ne, amma yana da kirki, in da ya bawa Ayla masauki, nan ya bawa su Rimsha, wato ɗakin su ɗaya. Sosai sukaji daɗi, ruwa suka fara ɗeba sukayi wanka, sannan sukayi alwala, yau sunyi wanka da sabulu, sau uku suna wanka, suyi su sake, sai daɗi suke ji, kamar wayan da suka koma cikin iyayen su, sai da sukaji jikin su ya ɗan sake musu sannan suka dakata da wanka suka fito, Ayla ta basu kayan da matar sarki ta bata, suka karɓa suka saka, suka tada Sallah. Kafin su fara Sallah sai da suka tambayi Ayla inane gaɓar, bata sani ba ita ma tace musu, kawai nuna musu in da take kallo take sallah tayi, suma suka kalli wajen sukayi Sallah Sai bayan sunyi Sallah har issha, sun zauna ne, matar sarkin mutuniyar kirki, ta kawo musu abinci, tuwon teɓa da miyar ganye. Tana ajiye musu Abincin Kausar ta jawo kwanon, ta fara loma hannu baka hannu kwarya, yayin da Ayla ke taya ta, kamar wayan da basu taɓa ganin abinci ba. Sosai Kausar da Ayla suka, take tuwun nan, ita kam Rimsha tun da ta ɗanɗana, sau ɗaya, ta cire hannu, tace bazata iya ciba, daman kuma Kausar tasan za'ayi hakan, dan ba kowa wani bahaushe ne zai iya cin abincin yarbawa tashi ɗaya ba. Haka Rimsha ta hakura ta sha ruwa, ita kuwa Ayla yau kwanan ta biyu a gidan ta ɗan saba da cin abincin nasu, kuma ita daman can ba yar masu kuɗi bace, yar malam Shehu ne bata zaɓen abinci, duk wanda ta samu ci kawai take, ta godewa Allah. Yau su Rimsha suna cikin farinciki zasu kwana cikin mutane kuma ba'a daular mutuwa ba, yau zasu yi barci mai daɗi. To muje mu leƙo su Aafia kafin nan mu dawo kila su Ayla sun gama take abinci tas. Zaune suke gaba ɗayan su saman table ɗin cin abincin dare, daddyn Jelly, Abbi, Aunty, sai kuma Aafia dake ta faman wurgawa Aunty harara. Palon yayi shiru baka iya jiyo sautin komai, sai sautin karan chokula da suke cin abinci da shi. "Abbi wan can Akil ɗin yazo ya ɗauki Umaisha a School" cewar Aafia, ba tare da Abbi ya kalleta taba yace "Ba yayan ki bane? Me yasa zaki kira shi Akil kai tsaye?" Shiru ta ɗan yi kafin tace "Sorry Abbi, yaya Akil yazo ta ɗauki Umaisha" jinjina kai Abbi yayi kafin yace "Eh ya sanar dani" da mamaki Aafia tace "Abbi ya sanar da kai fa kace? Gidan su fa ya kai ta, kuma ɗakin sa, wai matar sa ce" "Eh mana ai bai yi karya ba, matar sace" "Matar sa kuma Abbi? Yaushe ta zama matar sa?" Jinjina mata kai Abbi yayi yana faɗin "Daga lokacin dana aura masa ita mana" Shiru tayi da kanta ya ƙulle, tana bukatar a mata karin baya ni. Ta buɗe baki zata sake magana, Abbi ya miƙe da sauri ya nufi bedroom na sa, yana dafe ciki, yana faɗin wash Allah, zaro ido Aafia tayi tana addu'ar Allah yasa ba wani mugun abu maganin nan da sukaci ya aikata wa Abbi ba, daman ita taki cin abinci, indomie ta girka ma kan ta. Bata ankara ba sai taga daddyn Jelly ma ya miƙe da sauri ya fice daga palon yana dafe ciki, Aunty kuwa ta miƙe tana tana kokarin bin bayan Abbi, jiri ya ɗebeta ta zube kasa a wajen, tare da dafe cikin ta tana murkusoso tana juyi a wajen tare da zafafan hawaye, da karfi karfi take ambato sunan Allah tana kara riƙe cikin nata, kan kace me jini ya fara zuba, yana bin kafafun ta, ganin haka yasa Aafia ta tsorata sosai, kar aunty ta mutu fa, da gudu ta miƙe ta nufi bedroom na Abbi tana ta kwala masa kira. Bawan Allah shi kuma yana can bayi yana fama da zawo, kamar zai mutu, saboda maganin ya kwance musu ciki, shida daddyn Jelly shejiya Aafia ko loma ɗaya ita taƙi ɗan ɗana abincin, tabar su Abbi da wahala ga Aunty rai a hannun Allah Karku manta idan Allah ya kai mu ranar Jumma'a da rai da lafiya, zan ɗauki hutu na ɗan wani lokaci, dan in ɗan huta in samu kwakwalwata tayi fresh, in ji daɗin zubo muku zafafan page's masu tashin kai, ina godiya sosai da sosai Allah ya bar zumunci 🥰 Masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu . 💞💞TRIPLET'S💞💞 💔💔Episode 7-8💔💔 Bawan Allah shi kuma yana can bayi yana fama da zawo, kamar zai mutu, saboda maganin ya kwance musu ciki, shida daddyn Jelly shejiya Aafia ko loma ɗaya ita taƙi ɗan ɗana abincin, tabar su Abbi da wahala ga Aunty rai a hannun Allah. Ko da ta shiga bedroom ɗin Abbi yana toilet, ta tsorata sosai kada Aunty ta mutu. Da gudu ta fito ta nufi part ɗin Irfan wajen daddyn Jelly, shi ma yana toilet, dawowa palon tayi ta zube kasa kan gwiwowin ta kusa da Aunty tana taɓa ta tare da kiran sunan ta, "Halima!!Halima!!" amma ina saboda azaba Aunty ta sume a wajen, kuka sosai Aafia ta farayi, tana jijjigata, ita har ga Allah batayi hakan dan ta kashe Aunty ba, kuma har cikin ranta take nadamar aikata hakan, sai dai kuma Rufee ba zata saka ta aiki ta kiyi bane, shine matsalar, ba zata iya cewa Rufee a'a ba, amma a kasan zuciyar tana son Aunty. Ganin wannan kuka da take bashi da wani amfani yasa, ta miƙe tsaye, ta nufi ɗakin yar aikin da Abbi ya kawo, ta kirata akan tazo ta taimaka mata susa Aunty a mota su wuce asibiti kafin Abbi ya fito. Yar aikin yarinyar kirki ce, haka tazo tasa iya karfin ta, Aafia ta dage, da kyar suka ɗaga Aunty zaune, kun san dai idan mutun ya suma, ba karamin nauyi yake karawa ba, saboda jikin sa duk ya saki, Sun yi nasarar miƙar da Aunty zaune, amma ba su iya ɗaga ta sama ba, wannan miƙar da ita zaunen ma da sukayi, sai haki suke kamar wayan da suka tiki uban gudu suka koshi. Sun kasa miƙar da Aunty tsaye, kuka Aafia tasa mai sauti tana faɗin "Mun shiga uku!" Itama yarinyar ta tsorata sosai da sosai, dan koda Aunty ta suma, jinin jikin ta bai dai na zuba ba, tana bleeding sosai. Tsabar ruɗu da shiga tashin hankali yasa Aafia ta fara jan Aunty a kasa, suka nufi wajen, yar aikin ma ta bi bayan su. Bayan sun fito wajen palon ne, ta bar Aunty kwance a kasa ta koma cikin ɗaki, ta ɗauko wayar ta, sannan ta wuce ɗakin Abbi ta ɗauki key ɗin motar sa, dan nata motar yana gidan su Akil, duk wannan abun dake faruwa, Abbi da daddyn Jelly suna toilet suna faman cetan kan su suma, dan sun kasa ko fita waje, da sun miƙe zasu kuma komawa, Aafia ta musu tsiya ba kaɗan ba. A ɓangaren Aafia kuwa, tana fitowa, ta wuce wajen motar Abbi, ta shiga ta kunna motar, ta jawo shi zuwa wajen da Aunty ke kwance, sannan ta fito ba tare da ta kashe motar ba, ta buɗe gidan baya, suka haɗu tare da yar aikin, da kyar suka tura Aunty cikin motar, sai wani uban nishi suke kamar wayan da suka ɗaga tayar trailer. Suna shigar da ita Aafia ta rufe motar ta shige gidan gaba, da gudun gaske taja motar, mai gadi dake tsaye tun ɗazun yana kallon su ba halin yazo ya taimaka musu, dan bai shafi aikin saba, tun Aafia bata kariso wajen ba, ya wangale mata gate ɗin gidan, da gudu ta fice, ta nufi asibiti. Abbi da daddy suna can, suna ta kan su, bayin Allah, Aafia tajaza musu wahala. A ɓangaren Umaisha kuma, bata farka daga nauyayyar barcin daya ɗauke ta tun bayan sallar asuba ba, sai karfe 9 na safe, shima ba ita ta farka dan kan ta ba, Ammie tazo ta tashe ta, lokacin Akil baya nan ya fita, Akila kuma ta tafi school. Wani gigitacen tsawa Ammie ta daka mata wadda ya sanya ta jin duk wani barci da take ji ya gudu "Ke zaki tashi ne ko sai na sa kafa na hanɓare ki sai kin faɗi kasa!!" Da kyar Umaisha ta iya miƙewa zaune, dan har yanzu jikin ta ba wani kwarin kirki Zubawa Ammie dake tsaye a kan ta ido tayi, sai wani turɓune fuska Ammie take, tana mata kallon kankanci Cikin tsawa Ammie ta fara magana cike da bada umarni, da nuna izza da kuɗi "Ina son ki buɗe kunnan ki da kyau ki saurare ni, daga yau tun karfe 6 zaki rinƙa tashi ki mana shara da wanke-wanke, sai gyaran ɗaki, shima ki mana shi tsab, da ɗaki na dana, Abban Akil, har dana su Akila, idan kin gama ki wanke toilets duka, sannan kiyi mopping na ko'ina, shi dai girki, Allah ya taimake ki bama son naki kina jina?!!" Gyaɗa mata kai Umaisha tayi alamar eh, kun dai san yadda gidan Hajiya Umaiya yake basai na sake faɗa muku ba, kuma kun san dai yadda ita kan ta Hajiya Umaiyar take, da kazan ta, datti ta ko'ina, babu gyaran gida babu na jiki, duk wasu yan aiki idan aka kawo mata, sai sun gudu saboda masifar ta, ga saurin hannun dukan ƴaƴan mutane, ga bakar zuciya kamar kafuran farko, bata da mutunci ko kaɗan, ga yiwa talaka kallon kaskanci, bugu da kari ga makirci, makirace ajin farko. Tsawa ta kuma dakawa Umaisha "zaki tashi ne ko dai sai na kwasheki da wawan mari?!" A hankali Umaisha ta zuro kafafun ta kasa, ta miƙe a nitse, da kyar da kyar take ɗaga kafar nata, saboda har ga Allah zafi wajen yake mata, haka ta nufi hanyar fita daga ɗakin, tana jiyo Ammie tana ta ruwan bala'i, wai Akil ba zai zauna da yar talakawa ba. Tofa wannan shine gaba da gaban ta, muje zuwa Shi kuma Akil bawan Allah yana can super market yana mata sayyan kaya, shi saboda tsabar kishin sama, bai yarda suje super market da ita ba, gara ya tafi shi kaɗai yaje ya sayo mata kayan ya kawo mata, idan ma colors ɗin da ya sayo mata ya mata fine, idan kuma bai mata ba, nan ma ita ta jiyo, shi dai ya sayo kuma dole tasa masa ya gani, duk abun da ya masa kyau kawai yake ɗauka, ba ruwan shi da zai burgeta ko ba zai burgeta ba, in dai shi zai burge shi. Yau Umaisha taga ta kan ta, dan ko bata iya aikin komai ba, wannan dalilin yasa ake cewa, duk abun da kayiwa wani sai an maka, lokacin da suka sako Aunty a gaba, suka rinƙa takurawa matar nan baji ba gani, bata isa tayi wani motsin kirki ba ita da gidan mijin ta, Allah sarki ita kuma kullun nasihar da take musu, ku mata ne baku san in da aure zai kai ku ba, ku bi a hankali, amma duk basu ji suka sa kafa sukayi fatali da duk wani shawara da nasiha da take musu, sukayi kunnan uwar shegu, to yau dai ga gari ya wayan wa Umaisha, kuma da garin ya tashi wayan mata, sai ya wayan mata a gidan Hajiya Umaiya, wadda bakin ta kaɗai idan aka bar mutun da shi, ya isa ya sashi yayi ta rama har ya mutu, ina ga ankai kan sauran aikin kuma, ai sai dai muce Allah ya kyauta. Palo Umaisha ta fara gyarawa tana yi tana tuna yadda taga Aunty na aiki a gida, gashi gaban ta na mata zafi sosai, da kyar take iya ɗaga kafar ta, har wani zufan wahala take haɗawa. Da kyar ta iya gyara palon, amma ta ɗauki wajen 1 your a palo kawai, kuma iya shara da shirya pillows na kishin kawai, ba'a kai ga mopping ba, sannan ta wuce cikin kitchen, gaba ɗaya kitchen ɗin sai warin rubaɓen abinci da su fruits da sauran abubuwa yake, haka ta daure, ta zage ta fara aiki babu kama hannun yaro, tanayi tana kuka, ita kuma Ammie ta wuce sama abun ta, ta samu sabuwar yar aiki, sai kuma abun da hali yayi. Tana kitchen Akil ya dawo bata sani ba, bedroom na su ya wuce hannun sa riƙe da wani katon trolley yana ja, dan shi saboda kishin sa bai yarda mai gadi ko mai bawa flowers ruwa ko driver su taya shi ɗaukan kayan matar sa zuwa cikin gida ba, a'a da kan sa ya jido komai zuwa cikin bedroom na su. Yasha mamakin ganin Umaisha bata ɗakin, shi da yayi tsammanin zaizo ya same ta kwance, dan bata jin daɗi, sai kuma yazo yaga bata nan. Bayan ya gama shigo da kayan, toilet ya fara leƙawa, wayam ba ta ciki, hakan yasa ya fito waje dan ya duba ta. Lokacin da ya fito palo, lokacin ita ma Ammie ta fito daga bedroom nata, ta sauƙo ƙasa "Ammie where is my wife" ya faɗa yana ɗan waige waige kamar mai neman wani abu, Murmushi makirci Ammie tayi kafin tace "Ashe yarinyar nan yar albarka ce Akil am, ni ban sani ba, na dage ka rabu da ita, ashe yar halak ce, tun ɗazun ta fito ta fara shara da mopping, nayi nayi ta bari amma taki, tace ita kam tana son taga tana yimin aiki, dan a matsayin uwa ta ɗauke ni, tana cikin Kitchen tana faman gyarawa", murmushi shima yayi kafin yace "Ai daman Ammie na faɗa miki, zaki so ta In Sha Allah dan tana da hankali" kara faɗaɗa murmushi ta Ammie tayi tanan faɗin "Ai tunima na kamu da son ta, yarinya yar albarka haka, ina hana ta aikin nan, yarinyar nan tace sai dai na kyale ta tamin, nace ta bari bata da lafiya, amma taki tace zatayi, har da kuka ta samin, kamar yadda kaga Akila ke yimin ita ma haka ta min, baiwar Allah a uwa ta ɗauke ni" shima kara faɗaɗa murmushin sa yayi yace "To yanzu dai ta bari tazo taci abinci tasha magana, sannan tazo ta ci-gaba" shiru Ammie ta ɗan yi kafin tace "Eh hakan ya kamata" wucewa yayi ya nufi kitchen ɗin ba tare da ya sake magana ba, harara Ammie ta bishi da shi, a zuciyar ta tana faɗin "Sai ka koreta da kan ka, In Sha Allah, ko kuma ita da kan ta, ta gudu" Umaisha na aikin wanke-wanke tana kuka, kusa da ita yazo ya tsaya, tare da rungumota ta baya yana faɗin "Ke kika jawa kan ki, kin san baki da lafiya me na cewa lallai sai kin yi aiki? To gashi yanzu kina yi kina kuka, nasan kuma dole daman kiyi Kuka, saboda ba koshin lafiya gare ki ba, yanzu dai ajiye aikin muje na baki abinci, kici ki sha magani ki ɗan huta, sai ki dawo ki ci-gaba da aikin" ajiye soson wanke-wanken dake hannun ta tayi, tare da kunna pampo ta wanke hannun ta, sannan ta juyo ta rungume sa da kyau tana kara faɗaɗa kukan da take A ɗan ruɗe yace "Lafiya? Me kuma ya saki kuka?" Yayi maganar yana ɗago haɓar ta, cikin kuka tace "Yaya Akil dan Allah ka mai dani gida kaji?" Hannu yasa yana goge mata hawayen dake zubowa yana faɗin "Ya isa haka, kiyi shiru, zan kai ki gida amma ba yanzu ba, kiyi hakuri sai bayan sati biyu kinji ko?" Gyaɗa masa kai kawai tayi bawan dan ta gaji da rokan sa ba, a'a sai dan bakin ta ya mata nauyi, ta sha wahala, tun da Akil yayi dis virgin ɗin ta take cikin wahala da azaba, ta gala bai ta sosai, tasha wahala. Hannun ta ya riƙo yana faɗin "Muje ko?" Da kyar ta iya ɗaga kafa ɗaya, tana kara sautin kukan nata, ganin haka yasa ya ɗauke ta cak ya fice daga kitchen ɗin. "Akil me ya faru? Lafiya ka ɗauko ta haka?" Cewar Ammie tayi maganar cike da nuna damuwa na makirci, "Ammie kafar ta ke yi mata ciwo" ya faɗa yana haurawa sama, bin sa da kallo takaicin Ammie tayi har ya shige part ɗin sa. Saman sofa ya zaunar da Umaisha yana faɗin "Sorry my wife" sai jan hanci take, alamar tasha kuka har ta koshi. Abinci ya ɗauko mata, da kan shi ya zauna kusa da ita, ya fara bata a baki, tana ci tana kallon cikin idon sa, lokaci guda taji mugun son shi na shigar ta, "Ke wai me yasa kike yawan kallon fuska nane?" Ya tambaya yana kallon ta shima, shiru tayi ba tayi magana ba, dan bata da amsar da zata bashi "Ba za kiyi magana ba?" Nan ma shiru tayi, kuma ba ta daina kallon nashi ba, "Ki dai na kallo na, kada ki haifa min baby mai kama dani, dan ni mai kama dake nake so" nan ma shiru ta masa, still har lokacin ko kyafta idon ta ba tayi ba, ta tsare sa kawai tana kallon sa, duk abubuwan da yake faɗa ma, basa shiga kunnan ta, tana can duniyar tunanin son da take masa, da kuma yadda za tayi ta bar wannan gida, dan zaman ta da Ammie ba zai yiwu ba. Hannu yasa ya rufe mata ido yana faɗin "Zan rinƙa saka nikaf kada ki kwashe min kyau na, da wanan irin kallon naki" murmushin cikin kuka tayi har sai da ta sanya shi sauke nauyayyar ajiyar zuciya, uhm soyayya daɗi. Sosai ya ɗura mata abincin nan, sai da ya tabbatar ta koshi, sanann ya ɗauko maganin ta ya bata, bayan ta sha, ya ɗauke ta zuwa toilet, da kan sa ya mata wanka, yana yi yana tsokanar ta, har suka gama suka fito, ya buɗe trolley da ya sayo mata kaya, ya ciro mata wani dogon riga mara nauyi, ya bata ta karɓa ta sanya. Bayan ta gama shiri, yace ta hau gado ta kwanta, ba musu ta haye gado ta kwanta tana jin matikar kaunar mijin nata har cikin ranta, shi ba mugu bane kamar yadda take tunani, idan ka fahimce shi zaka ji daɗin zama da shi, shi raini ne baya so, kuma yana son a nuna masa shine a sama da mutun, yana son abashi kulawa, kuma a nuna masa ya isa da mutun, baya son a masa jayayya da maganar sa idan yayi, ya fison da yace abu ace masa to, kuma baya son ya kawo abu ya baka kace masa color ko wani abu bai yi maka ba, a takaice dai shi ka nuna masa shine boss, idan kayi haka zaku zauna lafiya, zai maka abun da ma baka taɓa tunani ba na alkhari da kyautatawa. Har ta fara barci sai taga yana kokarin fita, zubur ta miƙe zaune tare da saka masa kuka tana faɗin "Yaya Akil dan Allah karka fita" juyowa yayi yana kallon ta da mamaki, ganin da gaske take masa kuka har da hawaye yasa ya dawo kusa da ita ya zauna tare da ɗan rungumota kaɗan yana faɗin "My wife me yasa kike kuka?" Kankame shi tayi tare da kara faɗaɗa kukan nata, dan tasan yana fita Ammie zata zo ta saka ta aiki, kuma jikin ta na mata ciwo "My wife kiyi magana mana, me yasa kike kuka?" Cikin kuka tace "Yaya Akil dan Allah kada ka fita, ka zauna kaji?" Mamaki ne ya kara kama shi, hannu yasa ya ɗago haɓarta yace "Wajen bappa zanje fa, yaya Imran ya aike ni, yace lallai naje gidan ku na duba masa ina bappa Maik ya kai Jelly, dan kullun idan suka kira shi, sai yace musu ko tana barci ko ta tafi shopping da Aafia, shine yaya Imran yace naje na duba masa, dan ya shiga damuwa sosai yana ji a jikin sa kamar ba lafiya ba, akoi abun da bappa Maik da kuma Abbin ku suke ɓoye masa, ki bari naje na dawo, ba zan jima ba kinji?" kara kankame shi da kyau tayi tana cusa kan ta a kirjin sa, cikin kuka tace "Ni dai a'a wlh ban yarda ba, sai dai mu tafi tare, ko kuma ka zauna babu in da zaka je" lokacin guda yaji wani bakin ciki ya ziyarci zuciyar sa, ba komai ne ya hassasa hakan ba, face cewa da tayi ya zauna babu in da zashi, a nashi ganin ta raina shi umarnin ma take bashi, dan haka sai ya daka mata tsawa "Ni zaki gayawa abun da zan yi? Wato umarni ma kike bani, na zauna babu in da zanje, to baki isa ba, ke mata tace a karkashi na kike nine zan baki umarnin ba kece zaki bani ba, I am the boss here" ya kai karshen maganar tare da kwace jikin sa daga riƙon da ta masa, ya miƙe ya fice daga bedroom ɗin yana wani hucin ɓacin rai, yau Umaisha ta raina shi. Oh Akil manya, wannan ma bashi ne babba a gidan ba, idan da shine Imran kam, ai da shikenan an shigesu, mutun sai bala'i son girma, Umaisha aiki na gaban ki, babba kuwa. Masu karatu mukoma wajen First lady wato Rimsha, Meesha, Siha, first lady, duka sunan tane, ɗaya tamkar da dubu in ji daddy ta, bari mu leƙo ta mu dawo. Ayla da Kausar tas suka take abincin nan, Kausar kam har da lashe kwano da harshen ta, tas tayi wa kwanon kamar an sanya ruwa an wanke kwanon miƙewa tayi hannun ta riƙe da kwanon tuwo dana miyar duka bayan ta gama lashewa "Ina zaki je Kausar?" Cewar Rimsha, kumbura kumatu tayi tana ɗan jujjuya ido tace "Zanje in ce su kara min abincin mana" salati Ayla tasa tana tafa hannu, Rimsha kam ta rasa bakin magana dan Kausar tafi karfin ta, daman haka Kausar take, a daular mutuwa ne take kamar malama, tab lallai daman idan kuna cikin wahala da kunci baka taɓa gane halin mutun, sai kun samu freedom ko yaya ne. Suna tsaka da tunani, basu san lokacin da Kausar tayi wuce wan taba, basu fargaba sai ganin Kausar sukayi da wani kula a hannun ta, zama tayi a in da ta tashi, ta bude kulan abun ta ta fara cin abincin "Ke Kausar waya baki wannan abincin?" Cewar Rimsha, turo baki tayi tace "Gani mana nayi na ɗauka" salati Ayla tasa tana faɗin "Wlh abincin yaron sarki ne, kuma bashi da mutunci mashayin giya ne lamba ɗaya, shekaran jiya dana zo gidan nan, wlh ya kusa yimin fyaɗe dan yasha ya bugu, da kyar maman sa ta kwace ni a hannun sa" ina ai su Ayla zancen su kawai suke ita kausar bata tare da su, loma kawai take kaiwa baki abun ta, hannu baka hannu kwarya, har wani lumshe ido take, saboda daɗin miyar matar sarki, hannu Ayla tasa ta janye kulan abincin daga gabar Kausar, ta rufe tana faɗin "Ke so kike a koremu daga gidan nan ko? To wlh ki dawo cikin hankalin ki, kin samu sun bamu abincin da masauki ba zamuyi taka tsantsan dan mu samu mu rabu da su lafiya ba" turo baki Kausar tayi kafin tace "Ori dafun" kallon Rimsha Ayla tayi, sannan ta dawo da kallon ta kan Kausar tace "Ke kika san shi" murmushi Rimsha tayi kafin tace "Ita ta san me kuma Ayla" "Ita ta san shi Ori dafun ɗin mana" dariya Rimsha tayi kafin tace "Kai amma fa idan baka jin yare akoi abu, dan a mahaukaci kake ɗaukan mai yin wannan yaren" miƙewa Ayla tayi, ta wuce kitchen na matar sarki taje ta mai da kulan abincin ta dawo ta zauna. "Ayla dan Allah kiji mana ba gaskiya na faɗa ba, nace mu tara kuɗi mu tafi wajen GAR ɗin Meesha, dan yadda take bamu labari kinga ai mai kuɗi ne, idan mukaje zamu samu kuɗi, amma meesha tana min dariya" ita ma Ayla dariya ta kwashe da shi tana tafa hannu kallon sama da kasa a cikin duhu Kausar tawa Ayla kafin tace "Ke ma a mahaukaciya kika ɗauke ni kenan?" Girgiza kai Ayla tayi kafin ta tsagaita dariyar tace "Haba Our Aunty yar lukuta, ni na isa in ɗauke ki a mahaukaciya? A'a bamu isa ba ai, kawai abun ne abun dariya, ke daga kinji cikin ki ya ɗauka yayi nauyi shikenan baki da wani case sai ki hau zuba zance mara kan gado, yanzu da kike wannan magana ma, uban wa zai bamu kuɗi, mu samu mu samu kuɗin mota mu koma wajen iyayen mu ma, tukun nan mana, kafin mu fara tunanin zuwa wani waje" shiru Kausar tayi bata sake yi musu magana ba dan gani take su duka basu hangi abun da take hango musu na kuɗin da zasu samu idan sukaje wajen GAR ba, amma ita dai koma ne tasawa ranta, sai taje wajen GAR. "Ayla ya akayi kika fita daga daukar mutuwa?" Cewar Rimsha, Ayla za tayi magana, wani matashi ya shigo da irin Mp manyan nan, kiɗa na tashi na wakan yarbawa, ana wakar omomo maryamo ashokine lule ashokine lule. Kamar wadda aka tsikara haka Kausar ta miƙe ta fara dikar rawa, irin nasu na yarbawa tana biye wakar, abun ku da yarba, shima matashin ajiye mp yayi suka shiga tika rawa tare da Kausar, yau Rimsha taga ikon Allah daman haka Kausar take, tirkashi, ita kam Ayla kwana biyu da tayi a nan ta saba ganin fiye da haka ma, mace da namiji suna rawa suna rungume juna haɗuwar titi rabuwar gate. Sai wani kasa suke suna sama, Kausar da matashin nan, kamar wasu zabbi, kan kace me matar sarki ta fito daga nata ɗakin, tana karkaɗa jiki kamar kaza na karkaɗa fuka fukin ta, abun ma dariya ya bawa Ayla, yadda yau kuma matar sarki ta fito da wani sabon salon rawa na daban Rimsha da Ayla sun shagala da kallon wannan chasun na su matar sarki, basu ankara ba sai ganin Kausar sukayi ta riƙo hannun Ayla tana faɗin "Taso ki taka mana" ba musu Ayla ta tashi dan wani lokaci idan matar sarki tana rawa, tana riƙo hannun ta suyi tare, a kwana biyun da tayi tare da su, shiyasa yanzu ta fara sabawa da rawan nasu. Jawo Rimsha ma Kausar tayi suka riƙe hannu suna biyewa Kausar tana ta wani jijjiga su, ita kam Rimsha duk ta in da Kausar ta ja ta, bin ta kawai take kamar wani igiya, babu wani action ba komai, zololo zololo take bin ta dan bata saba ba. Sun ɗauki 45 mins suna chashewa kafin nan, su zube kasa a wajen suna mai da numfashi, matar sarki kam bata yi rawa sosai ba, bata fi 20mins ba ta tafi ta basu wajen. Bayan sun zauna ne, matashin ya kashe kiɗan yana kallon su a cikin duhu, duk da cewa akoi hasken wata, amma ba sosai ba "Alay yaushe mukayi baki?" Cewar matashin, yayi maganan da broken English, Ayla zatayi magana Kausar ta rigata cikin harshen yarbanci tace "Sunan ta Ayla ba Alay ba" murmushi tayo yayi kafin yace "Ba zan iya faɗa hakan ba, shiyasa nake ce mata Alay" shiru Kausar ta ɗan yi kafin tace "Okey boder daga nan zuwa ilorin akoi nisa?" Yayi mamakin jin yadda Kausar ke yarbarnci reras, dan haka sai ya kunna wutar mp sa mai bala'i haske dan yaga fuskar ta da kyau. Sai dai kunna wutar da yayi ta ja mashi matsala, domin kuwa yana haske su, yaji duk duniya ya samu mata, tun da idon sa ya sauƙa a kan Rimsha shikenan, sai dai kuma ko da ya haska mata wutar a ido, tsawa ta daka masa da karfi wadda sai da gaba ɗayan su suka tsorata. Da sauri Ayla ta dafa ta tana faɗin "Rimsha lafiya?" Ture hannun Ayla tayi, cikin tsawa tace "Kada ku sake haska min haske a ido" Kausar ta tsorata sosai domin wanna ba muryan Rimsha bane kwata kwata, cikin sauri Kausar tayi baya, yayin da shima matashin ya kashe hasken mp nasa yana faɗin Sorry, shi da yake bai san kalar muryan Rimsha ba, sai yayi tunanin ko dai haka muryan ta yake, su kuma su Ayla already sun san yadda voice nata yake, shiyasa suka tsorata dan sunji wannan murya da tayi magana da shi yanzu dai ba muryan ta bane. Tirkashi meyake shirin faruwa kenan, anya Rimshan gaske ce a wajen, idan ba Rimshan gaske bace, ina ta gasken take, meke faruwa da wayan nan yan matan ne? ya akayi Ayla ta riga su zuwa kauyen nan? Ya akayi ta kuɓuta daga hannun su Barbushi? Hmmm akoi cakwakiya mu dai je zuwa dan muga yadda zata kaya, tsakanin wayan nan yan mata. 💞💞TRIPLET'S💞💞 💔💔Episode 7-8💔💔 Ɗan baya kaɗan itama Ayla tayi dan ta tsorata jin yadda muryan Rimsha ta sauya lokaci guda, kallo juna suke cikin duhu, tayo kuma da bai san meke faruwa ba, sai ya washe baki yace "Alay wayan nan bakin naki da alama suna da faɗa" shiru Ayla ta masa, dan tsoron magana ma take, kada tayi wani magana kuma ya zama faɗa tsakanin ta da Rimsha. Kausar ce tace "Boder baka bani amsa taba?" "Amsar me fa?" Ya tambaya yana kokarin tashi daga wajen "Amsar daga nan zuwa ilorin akoi nisa" hanyar fita daga gidan ya nufa yana faɗin "Babu nisa, daga nan zuwa cikin lasoju naira 200 ne daga lasoju zuwa eyankorin shima 200 ne daga eyankorin zuwa cikin Ilorin wato gari alimi 150 ne kuɗin transport kinga kuwa ai ba nisa" cikin sauri tace "A'a mu ba cikin Ilorin bama zamu shiga, a eyankorin zamu tsaya, a nan gidan mu yake" dai dai zai fita gidan yace "Naira 400 zai kai ki can ai" sosai Kausar taji daɗi, sun kusa isa gidan su. Ita kuwa Ayla tunani take sosai a kan Rimsha menene ya sauyawa Rimsha muryan ta cikin kankanin lokaci haka, matsowa Kausar tayi ta dafa Rimsha tana faɗin "Meesha kin ji mun kusa isa gida ko?" A hankali kasa kasa Rimsha tace "Ke dai kin kusa isa gida, ni kam da saura na sosai" jin Rimsha tayi magana da normal muryan ta ne yasa Ayla matsowa kusa da ita tana faɗin "Meesha muje mu kwanta ko? Dare nayi sosai" suna kokarin miƙewa babban ɗan sarkin ya shigo cikin gidan yana wani tafiya yana bonshin wando na faɗu wa ya riƙe gefe. Kai tsaye kitchen ya nufa yaje ya ɗauko abincin sa wanda Kausar ta ɗauka ta fara ci. A inda tayo ya tashi a nan shima olohunwa wato ɗan sarkin yaje ya zauna tare da buɗe kulan abincin, ya zurma hannu ciki ya fara kai loma, babu ko wanke hannu. Sosai Ayla tayi godiya ga Ubangiji da Allah yasa olohunwa ban gane cewa Kausar taci masa abinci ba. Lallaɓawa sukayi suka miƙe suka nufi wani ɗaki wanda ya kasan ce shine ma saukin su. Babu komai a cikin ɗakin sai tabarman mai ɗan girma, da pillow guda ɗaya, sai godiya ga Allah suke, dan hakan ma ba karamin daɗi suka ji ba, domin a daular mutuwa ko taburman ma basu samu ba. Addu'ar barci sukayi tare da kwanciya suka saka Rimsha a tsakiyar su, kasan cewar ita ce karama, dan a shekaru dukan su Ayla zata girme musu, dan ita zatayi 15 years, ita kuma Kausar 14 to 15, Rimsha ce karama mai 13 years, sai dai duk cikin su babau wacce ta fara period har yanzu, amma dukan su, sun fara kirgan dangi, Ayla kam ma har ta fara zama yan mata. "Ayla baki faɗa mana ya akayi kika bar daular mutuwa ba" cewar Rimsha, shiru Ayla bata amsa musu ba, sake mai-mai ta tambayar Rimsha tayi, nan ma shiru Ayla bata amsa ba, hannu Rimsha tasa ta ɗan bubbuga Ayla tana faɗin "Me haka Ayla? Ki bani amsa na mana, sai magana nake, amma kinyi banza dani" shiru Ayla ba tayi magana ba, haurar da hannun ta sama Rimsha tayi tana laluɓar fuskar Ayla dan taji idon ta arufe ne ko abuɗe ne, dai-dai cikin Ayla taji wani abu kamar dutse gashi da girma kulu lu, a sukwane ta miƙe zaune tana faɗin "Ayla me a cikin ki?" Shiru Ayla ba tayi magana ba, gashi ɗakin da duhu, cike da tsoro Rimsha tace "Kausar ki taɓa cikin Ayala kiji wani abu kamar dutse" ita ma Kausar ɗin shiru batayi magana ba, hannu Rimsha ta sake kaiwa saman cikin Ayla, sai taji wayam babu komai, wannan dutsen ya ɓace, jijjiga Ayla ta fara yi da karfi tana kiran sunan ta "Ayla!! Ayla!! Ayla" cike da ruɗu da tashin hankali, dan a tunanin ta Ayla mutuwa tayi, tun da yanzu suka kwanta ba jimawa, amma ace Ayla tayi shiru kamar wadda ta mutu. Ta kai 5mins tana jijjiga Ayla da karfi tana kuka, ga kuma Kausar ita ma kwance bata jin su, kuma bata motsi, ganin sunki tashi ne yasa ta miƙe da gudu zatayi waje, kamar a mafarki taji Ayla na cewa "Rimsha ya naji kamar kina magana?" Tashin hankali "What!!? Rimsha ta faɗa a tsorace, miƙewa zaune Ayla tayi za tayi magana, matar sarki ta shigo ɗakin hannun ta riƙe da ɗan ƙaramin fitilla irin mai amfani da battery remote ɗin nan, tazo ta ajiyewa Ayla a in da ta saba ajiye mata tana faɗin "Ya ke kuma kike tsaye" tayi maganar cikin harshen yarbanci, kasan cewar ita Rimsha bata jin yarbanci sai tayi shiru bata amsa ba, kamar a mafarki Kausar da Rimsha ke ta kira tun ɗazun tace cikin harshen yarbanci "Meesha bata jin yarbanci" shafa kan Rismha matar sarkin tayi tace "Fine girl" sannan ta wuce ta fice daga ɗakin. Dawowa Rimsha tayi ta zauna kusa da Ayla tayi shiru tana mamaki, me yasa duk lokacin da ta tambayi Ayla ya akayi ta fita daular mutuwa sai wani abun ya gipta, kuma da alama Ayla bata son sanar da su ta yadda ta fito daga daular mutuwan, dan da farko da suka tambaye ta, tace musu sai sun huta, na biyu kuma tayo yazo, yanzu kuma gashi ta sake tambayar ta daga ita Ayla ɗin har Kausar duk sunyi kamar sun suma, basa jin komai, anya ba wani abu kuwa. To masu karatu me kuke tunani game da Ayla, Kausar, da kuma Rimsha? Mu haɗu a comments section. A takaice dai a wannan dare Ayla bata samu damar sanar da su ya akayi ta fita daga daular mutuwa ba, haka zalika ita kuma Rimsha bata dai na tunanin yadda akayi Ayla ta fito daga daular mutuwa ba kuma ya akayi ta kasa faɗa musu ta yadda ta fito. Kasa barci Rimsha tayi tana tunani, su kuwa Kausar da Ayla tuni sunyi barcin su abun su, sai can tsakiya dare sannan barci ɓarawo ya ɗauki Rimsha tunani cike fal ranta. A ɓangaren Jelly kuwa, yau gidan babu kowa, Hajiya ta tafi super market yi musu shopping, Nawid yana Katsina gidan kakanni sa, shi kuma Abbo bai dawo ba, ita ka ɗai ce zaune a palon Hajiya, tayi zaman yan bori, ta baje abun ta, kafa ɗaya can ɗaya nan, tayi ɗai-ɗai, ta tasa abubuwa a gaban ta, irin su chocolate, Ice cream, yogurt, soyayyen naman kaza, sweet da sauran su, Gaba ɗaya ta damalmale wannan ɗan bakin nata da ice cream, har gemun ta, duk sai da ya samu ice cream sai taunan naman kaza take, ga wani cinyar kaza a hannun ta, tana ci tana kaɗa kai tare da lumshe idanun ta irin santi na ɗeban ta. Jikin ta na sanye da wandon jeans pink color da yar riga mai karamin hannu white color, ta sanya turban cap pink mai shegen kyau a kan ta. Da sallama Abbo ya shigo palon, bata san ma ya shigo ba, dan da alama sai an mata weji, idan ba haka ba zata iya kwacewa, nama yayi daɗi baji ba gani, shi kuwa wani sanyi yaji ya ziyarci zuciyar sa, lokacin da ya ɗaura idon sa a kan ta, kasan cewar yasan Hajiya bata nan, hakan yasa ya kariso cikin palon da sauri Kusa da ita ya zauna, a kasa kenan, har lokacin Jelly bata san da shigowar saba, hannu yasa ya ɗauki nama ɗaya zai kai bakin sa, cikin sauri ta riƙo hannun sa, ba tare da ta kalle shi ba, tana ta faman kaɗa kai alamar santi idon ta a lumshe tace "Ajiye shi" yar murmushi yayi kafin yace "Baby nine fa" "Kai waye? Nace ka ajiye shi kawai" ta faɗa, har lokacin bata buɗe ido ta kalle shi ba, "Abbon kine fa" sai lokacin ta buɗe ta kalle shi, sakin hannun nasa tayi tana faɗin "Cemin zakayi old man" zaro ido yayi yace "Daga ina yau kuma kika jiyo old man?" Roban wani Ice cream ɗin ta ɗauko ta buɗe ta fara dumbutsan ice cream ɗin da hannu tana kaiwa bakin ta, har gemun ta duka yana shafa, cike da santi tana kaɗa kai tace "A Tv naji, wai idan mutun ya tsufa old man ake ce masa, dan haka daga yau sunan ka kenan" murmushi yayi ya sanya hannun sa yana shafo wuyar ta, yana faɗin "Idan dai kece zaki cemin old man ɗin ina so ai" a sukwane ta miƙe tsaye tana faɗin "Kwarto jama'a Kwarto" zabura shima yayi ya miƙe tsaye yana faɗin "Ina kwarton yake?!!" Da hannu ta nuna shi tana faɗin "Ga ka nan, wayyo Kwarto" tsawa ya daka mata ganin tana kokarin tara masa jama'a "Ke waye yace miki ni Kwarto ne? Tukun nan ma aina kika ji sunan Kwarto?" Turo baki tayi kafin tace "A Tv naji mana, nagani wata mata da wani mutun yazo zai taɓa ta shine tayi ihu tace kwarto ne, mai neman mata, shine jama'a suka kama shi suka masa duka, kai ma yanzu kazo zaka taɓa ni dan haka kai kwarto ne, wayyo jama'a kwarto nima kuzo ku taimake ni ku kama shi ku masa ɗan iskan duka!!" Da karfi tayi ihu, ganin da gaske take, kuma yasan halin ta, idan duniyar nan duka zai bata, bazata taɓa yin shiru ba sai lokacin da taga dama, dan haka sai ya kwasa a guje yayi cikin bedroom na shi ya banko kofa, yana mai dana sanin barin ta da suke tana kallo, yarinya sai kaifin ƙwaƙwalwan bala'i, kome ta gani a Tv ta riƙe a kwakwalwan ta, amma kuma idan aikin arziki ake koya mata bata ɗaukan komai. Duk da ya gudu Jelly bata dai'na ihun kwarto kwarto ba, har su maman Afnan suka shigo ihu kwarto take, sai tambayar ta ina kwarton yake suke, amma Jelly taki kula su, dan Hajiya tace kada tayiwa kowa na gidan magana, shiyasa bata kula suba, ihun ta kawai take tana bubbuga kafa a kasa tana yarfe hannu. Da dai sukaga Jelly fa kamar ta haukace sai suka kama kan su, dan daman suna zargin Jelly da taɓin hankali, to yau dai sun tabbatar, sai tsaki maman Afnan take jelly ta ɓata mata rai, yarinya ita kaɗai a ɗaki ta kama ihun kwarto kamar ba lafiya ba a cewar su. Ita kuwa Jelly sai da tayi ihun kwarton ta mai isar ta sannan ta koma ta zauna ta ci-gaba da ɗure ɗuren abubuwan da take, idan ka ganta sai ka rantse da Allah ba itace tayi wannan ihu yanzu ba. 30mins da faruwar Abun Hajiya Turai ta dawo cikin gidan daga shopping, har lokacin Jelly na wajen da take zaune tana baje abun ta, shi kuma Abbo yana bedroom na sa kwance saman gado yana tunanin yadda zai yi, dan son Jelly na neman yi masa illa, ta ɗayan gefen zuciyar sa kuma, yana dana sanin fara yunkurin taɓa Jelly da yayi, dan yasan halin ta sai ta faɗa wa hajiya. Haka kuwa akayi, Hajiya na shigowa ta miƙe ta nufeta da gudu, tana faɗin "Ummi kwarto ya taɓa Ni" jin haka yasa Abbo miƙewa a razane, ya diro kasa daga saman gadon nasa, yazo bakin kofar bedroom ɗin ya laɓe, ya kasa kunne yana jiran yaji me Hajiya zata ce. "Waye kuma kwarto baby?" Hajiya ta tambaya tana ajiye niƙi niƙin kayan dake hannun ta, "Abbo mana, shine yazo yana taɓa min wuya" zaro ido Hajiya tayi, cikin sauri tace "Wani Abbo kuma?" "Abbon Nawid mana" Jelly ta faɗa tana turo baki "Abbon ya dawo ne?" Cewar Hajiya, eh Jelly ta bata amsa, miƙewa Hajiya tayi ta nufi bedroom ɗin Abbo tana faɗin "Ina zuwa ki jirani" Nima na tattara kayana nace ina zuwa bari naje na gaida Josephine a New York sai na dawo, bye sai mun haɗu gobe. Karku manta idan Allah ya kai mu ranar Jumma'a da rai da lafiya, zan ɗauki hutu na ɗan wani lokaci, dan in ɗan huta in samu kwakwalwata tayi fresh, in ji daɗin zubo muku zafafan page's masu tashin kai, ina godiya sosai da sosai Allah ya bar zumunci 🥰 Masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu . 💞💞TRIPLET'S💞💞 💔💔Episode 9-10💔💔 "Waye kuma kwarto baby?" Hajiya ta tambaya tana ajiye niƙi niƙin kayan dake hannun ta, "Abbo mana, shine yazo yana taɓa min wuya" zaro ido Hajiya tayi, cikin sauri tace "Wani Abbo kuma?" "Abbon Nawid mana" Jelly ta faɗa tana turo baki "Abbon ya dawo ne?" Cewar Hajiya, eh Jelly ta bata amsa, miƙewa Hajiya tayi ta nufi bedroom ɗin Abbo tana faɗin "Ina zuwa ki jirani" Abbo na jin Hajiya ta nufo bedroom na sa, sai yayi sauri ya haye saman gadon sa, ya kwanta tare da lumshe ido kamar mai yin barci, har da wani yin mumfashi irin na mai barci za Da sallama ɗauke a bakinta Hajiya ta shigo cikin bedroom ɗin, shiru Abbo yayi bai amsa mata ba, kamar mai barci, saman gadon ta haye ta zauna tana faɗin "Abbon Nawid har kayi barci ne?" Shiru ya mata bai yi magana ba, ganin haka yasa tayi tunanin ko barci yake, dan haka sai ta sauƙa ƙasa, ta fito daga cikin bedroom ɗin. Tana dawowa palo ta tarar da Jelly ta mata aika-aika, ta zazzage mata duk wayan nan niki-nikin kayan da ta shigo da su a jaka, ta haɗe su waje guda, sai faman bubbuɗe kwalayen take, tana fitar da duk wasu abubuwa dake ciki. "Baby me yasa baki ji ne?" Hajiya ta faɗa a raunane, dan jikin ta duk a mace, ta gaji sosai, kasan cewar tana da kiba da tayi tafiya kaɗan take gajiya. Saman sofa tazo ta zauna tana faɗin "Tattara komai da kika fitar ki mai da shi" turo baki Jelly tayi tana faɗin "Ni Ummi ban iya ba" kwanciya Hajiya tayi tana faɗin "Wash Allah na gaji" ci-gaba da watsa kayan Jelly tayi abun ta, tana neman abubuwan ci kawai taci, shiru Hajiya tayi bata sake tanka mata ba, dan a gajiye take, ba zata iya rigimar jelly yanzu ba. Tsab Jelly ta fitar da komai daga cikin kwalin sa, na ledoji ma ba'a bar su a baya ba, sai da ta yaje duk ledojin ta fito da abubuwan dake ciki, wayan da ake ci duk ta tara a gaban ta, irin su chocolate, sweet, popcorn, chips da sauran kayan kwaɗayi da maƙulashe da Hajiya ta sayo mata. Yage ledar popcorn tayi, ta fara dumbuza tana kai wa bakin ta, Hajiya kuwa tana kwance idon ta a lumshe, saboda gajiya, bata san aikin da Jelly ke yi ba. Bayan ta gama da popcorn ta ɗauko wani leda mai ɗauke da chin-chin a cikin sa, yage shi shi ma tayi, ta fara cin chin-chin ɗin. Kaɗan taci wannan chin-chin ɗin ta ajiye sauran tana faɗin "Ba daɗi kamar an wanke kan wancan matar, maman Afnan take kowa, kan ta a gwaguye ba gashi, sai masifa kamar sheɗaniya" Hajiya na jin ta, amma ba ta tanka ta ba. Haka Jelly ta rinƙa cin abin da zata iya ci, wanda ta ji ba daɗi kuma haka zata bar shi, a watse a wajen, ta yage ledar. Suna cikin wannan hali Nawid ya shigo bakin sa ɗauke da sallama, waro ido Hajiya tayi tana kallon sa, hannun sa riƙe da yar karamar trolley ɗin sa mai kyau, ya dawo daga Katsina. Saman kujerar kusa da Ummi ya.zo ya zauna yana ta faman washe baki, murmushi baki har kunne, Jelly kam kamar bata san da shigowar sa ba. "Nawid lafiya kake wannan murmushi haka? Ko dai kakan ka ya maka wani kyautan ne?" Ummi ta tambaya tana tsare shi da ido, baki har kunne saboda murmushi yace "Ummi na samu mata ne wlh, shiyasa nake cikin farin ciki, shiyasa ma ki kaga na dawo da wuri dan na sanar dake, farinciki ya hana ni na cika satin da nace zan yi, dole na zo na sanar dake" zaro ido Ummi tayi kafin tace "Mata kuma? Ai na ka sami matar?" Kara faɗaɗa murmushin sa yayi tare da ɗan duƙar da kai ƙasa yace "Ummi a Katsina take, tana aiki a restaurant ɗin gwaggo Auta" kara zaro ido Ummi ta yi kafin ta miƙe zaune tace "Lallai Nawid, ita kuma baby fa?" Zaro ido shi ma Nawid yayi yace "Ummi baby kuma?" "Kwarai da gaske baby fa" Ummi ta ba shi amsa with her full confidence Tashin sense lokaci guda yaji duniya ta tsaya masa cak, har wani yanan duhu yake gani na gilmawa a idon sa, nan take yaji duniya na masa wani irin juyi, kan sa na sara masa, da karfi karfi, kamar zai rabe biyu, zancen zuci ya fara yi, "ko na rasa mata a duniya ba zan auri baby ba, yarinya bata da hankali, bata da kan gado ko kaɗan, kamar ni dr Nawid a ce wannan mahaucikayar ce matata, kai ina hakan ba zai yi wu ba, yarinyar da bata san kan ta ba, ita da kan ta, sannan ace ni in aure ta, muyi zaman mata da miji da mahaukaciya" wani irin zufar ne ya fara gan garo masa daga gefe da gefen kunnen sa, kasa ya duƙar da kan sa yana tunanin abun yi "Nawid menene naga ka canza lokacin guda haka?" Cewar Ummi, furzar da iska mai zafi yayi daga bakin sa, kafin yace "Ummi ni a kanwa na ɗauki baby, ko kaɗan babu son ta a rai na, dan Allah Ummi kiyi hakuri, kada ki sanya na auri ta, wlh idan na aure ta, na san zan cutar da ita ne, dan bana son ta" salati Ummi tasa tana tafa hannu, har ta kai karshen salatin "Nawid yanzu ni kake cewa baka son baby? To tun da baka son baby zaɓi na, ni ma bana son wanda ka kawo kake son aura, har zan ce maka ga zaɓi na kace baka so lallai ka girma" zamowa ƙasa daga saman sofar Nawid yayi ya zube gwiwowin sa a kasa, cikin raunanniyar murya cike da tashin hankali yace "Ki yi hakuri Ummi, ba wai bana son baby ba ne, ina son baby amma a matsayin kanwa, dan Allah Ummi ki fahince Ni, ki so zaɓi na, ki bari na aure ta, wlh tana da kirki sosai" Oho Allah ko yaushe Nawid ya zauna da Jehan har yasan tana da kirki, kai jama'a hmmm maza mutanen mu😹. Ummi za tayi magana Jelly dake zaune tana faman cinye sauran naman ta na ɗazun tace "Yaya Nawid kar ka damu, ni ma bana son ka ai, tun da baka so na, Ni ma haka ne" guntun tsaki Ummi taje kafin tace "Ke baby ta shi ki kwashe kayan cimar ki, ki wuce ɗakin ki" ba musu ta tashi ta tattare kayan ciman ta, da wanda ta fara ci ta ajiye da kuma wanda ma bata samu daman ci ba, duk ta kwashe ta wuce ɗakin ta tana turo baki. Dawo da kallon ta, kan Nawid Ummi tayi "Nawid idan dai har kana son auran wancan, tofa sai ka fara auran baby, zan sanar da Abbon ka, nan da 3 weeks masu zuwa a ɗaura muku aure a wuce wajen, idan yaso daga baya sai ka auri wan can, amma fa ka sani ba zaka kawo min wadda zata takurawa baby ba tom" kasa kasa yace "To shikenan Ummi Nagode" sannan ya miƙe ya ja trolley sa zuwa bedroom na sa murna ya koma ciki, yana tafiya yana tunanin hanyar da zai bi ya gujewa auren baby, "ko dai na ɗauke ta naje can wani gari na jefar da ita ne?" Ya tambayi kan sa, ɗayan ɓangaren na zuciyar sa ne yace masa "Da kuwa hakan zai fi, dan idan ba haka kayi ba Ummi ba zata fasa aura maka wannan mahaukaciyar kwailar yarinyar ba" tunani kala-kala yake cikin ransa har ya karisa cikin bedroom ɗin nasa. A ɓangaren Abbo kuwa daga cikin bedroom nasa yana jiyo duk yadda Ummi tayi da Nawid, shi ma tunani yake ta yadda zai ɓullo wa lamarin, ji yake kamar yabi dare ya ɗauki baby ya kai ta gidan shi na Abuja ya ajiye ta a can, sai ya rinƙa biyan bukatar sa da ita, tun da daman a nan bai isa yayi hakan ba, saboda Hajiya, ga shi kuma yana bala'i son ya ga ya keɓe da baby, yana son kasan cewar tare da ita a ɗaki ɗaya. Shi ma tunani cike fal ransa yana tuna yadda zai sa mu mafita. A ɓangaren Ummi kuwa tunanin bikin Nawid da baby kawai take, dan har ga Allah Ummi tana bala'i kaunar Jelly. Wayar ta ta ɗauƙo daga cikin jakarta, ta danna kira, sannan ta kara wayar a kunnan ta. Jim kaɗan a ka ɗa ga kiran "Hello Hajiya Batula ya kike?" Daga ɗayan ɓangaren Hajiya Batula tace "Lafiya lou Hajiya Turai ya su Nawid?" "Nawid yana nan lafiya yanzu ma kiran na shi ne ai" cikin sauri Hajiya Batula tace "Kiran nashi ne kuma? Kaddai ki ce min auren sa ne ya tashi" kyakkyawan murmushi ne ya bayyana a kan fuskar Hajiya Turai, tana murmushi tana faɗin "Eh wlh auren sa ne ya tashi, ina Abla?" "Abla tana school, lallai abu namu maganin a kwaɓe mu, ki ce na kamo hanya kawai" kara faɗa ɗa murmushi ta Ummi tayi kafin tace "Sosai ma kuwa kamo hanya kam mai kyau ma, da wuri kai" "Yaushe ne bikin?" Shiru kaɗan Ummi tayi kafin tace "Eh nan da sati uku haka" "wow lallai dole nan da sati biyu nayiwa Kaduna diran mikiya" ɗan tsagai ta murmushi ta Ummi ta yi sannan tace "Gaskiya kam abun da yasa ma kenan na kira ki, saboda matar tasa, ki taimaka tun ana sauran sati biyu biki kizo ki fara gyara min ita" shiru Hajiya Batula ta ɗan yi kafin tace "Gaskiya tun ana saura sati biyu kam ba zai yi wu ba, sai dai saura sati ɗayan dai, saboda saura sati biyu biki ina da manyan baki, kuma kinga Abla ma zata dawo hutu daga school, zan yi kokari dai ana sauran sati ɗaya biki nazo, ranan tun safe zan biyo jirgi, kuma ai tsakanin Maiduguri da Kaduna tafiyar ba yawa, jirgin safe zan biyo, ina dirowa mu fara aiki" ɗan canza fuska Ummi tayi alamar bata ji daɗin maganar Hajiya Batulan ba, amma ba yadda ta iya dole ta hakura ta bi yadda Hajiya Batulan tace, dan Hajiya Batula ta kware wajen gyara mata, kuma babban aminiyar tace tun na yaran ta. Ba dan taso ba, ta amsa wa Hajiya Batula da to Allah ya kai mu, sannan suka yi sallama, ta mai da wayar ta ajiye, ta koma ta kwanta, ta ci-gaba da tunanin tana kawata yadda bikin zai kasance a ran ta. To masu karatu mu leƙo Rimsha mu gani me take aikatawa. Tun karfe 6 na safe su ka farka su ka shirya, a tare suka je suka yi wa matar sarki sallama, sannan suka je wajen sarki a ɗakin sa shi ma, suka yi masa sallama, sarki da matar sa basu ji daɗin tafiyar da su Rimsha za su yi ba, dan har ga Allah tun da suka gan su, suka ji kaunar yaran har cikin ran su ya ka ma su, to amma ba yadda za su yi, tun da ba ƴaƴan su bane, dole su kyale su su koma wajen iyayen su, dubu biyu sarki ya basu, sai godiya suke zuba masa, baki har kunne saboda murmushi jin daɗin sun samu kuɗin mota, Rimsha ce ta kulle kuɗin a igiyar rigar ta kusa da in da ta ƙulle goran da duna ya bata cike da murna suka fito tsakar gida, matar sarki ma ba'a barta a baya ba, ta basu kyautan 500, sosai suka ji daɗi sai murna suke, suka yi sallama, su Rimsha suka nufi waje matar sarki da sarki suka koma cikin ɗakunan su Su Rimsh sun fito zasu tafi kenan suka ci karo da olohunwa yana ƙoƙarin shigowa cikin gidan, hannun sa riƙe da buta, alamar bayan gari yaje yayi. Murya kamar na yan shaye-shaye yace "Wow beautiful girl" yayi maganar yana kallon Rimsha, shiru su dukan su suka yi, ba su yi masa magana ba, hannu olohunwa ya kai zai shafi fuskar Rimsha, cak hannun sa ta maƙale ya sanƙare kamar itace, ihu ya fara yi yana kokarin jaye hannun sa baya, amma ina ya kasa, su ma ihu suka yi suka bazama cikin gari da gudu, dan sun tsorata da ihun olohunwa A guje sarki da matar sa suka fito, olohunwa yana tsaye a wajen ya kasa motsawa, ga hannun nasa sai kumbura yake ya sankare waje guda, su kuwa su Rimsha tsorata da ihun da olohunwa yayi ne yasa su bazama cikin gari suna gudu kamar marasa hankali, a tunanin su, wani abun mugunta zai musu. Sosai suke gudu basu san in da suka nufa ba, sarki kuma sai faman kokarin janye olohunwa a wajen yake, amma abun yaci tira ko motsa olohunwa sun kasa yi, to kun san halin yarabawa da tsoro ire-iren wayan nan abubuwa, ihu matar sarki ta kurma tana neman a kawo mu su ɗauki. Kan kace me gidan sarki ya cika da jama'a maƙil, sai hayaniya ke tashi kamar gidan biki, sai kokarin ture olohunwa suke daga wajen amma sun kasa, kamar bishiyar da a ka dasa shekara da shekaru haka ya zama a wajen, gashi sai ihu yake ya ka sa magana saboda azaban zogi da hannun sa ke masa, hannun ya kumbura sosai har ya fara fitar da wani irin farin ruwa mai warin bala'i, alamar hannun ya ruɓe. Su kuwa su Rimsha bayin Allah basu san meke faruwa ba, sai zunduma gudu suke wai kar olohunwa ya kama su, dan Ayla ta faɗa musu olohunwa fyaɗe yake yiwa mata shiyasa ma suka tsorata sosai da shi. Sun yi gudu sosai, har sai da suka dai na ganin alamar wannan kauye gaba ɗaya, sannan suka tsaya wajen wani bishiyar lemon tsami suna mai da numfashi, suna haki. Almost 10mins suna tsaye, sannan suka zauna, a kasan bishiyar, da yake akoi ganyen damuna sosai a jikin bishiyar, sai suka sa mu inuwa, wajen akoi sanyi sosai gwanin daɗin zama, haka suka baje Ayla ta duɓi Rimsha tace "Allah ya cece mu, ba dan haka ba olohunwa fyaɗe zai mana, ɗan iska ne sosai, ga shi da bala'i shaye-shaye" da kyar Rimsha ta iya cewa "Gaskiya kam, amma kuma basu da mutunci in dai haka ne" ita dai Kausar ta kasa magana saboda ta fi su shan wahala, dan ta fi su ƙiba shiyasa ta fi su jin jiki. Sun yi shiru su na zaune, bishiyar na kaɗa musu iska mai sanyin daɗi, har wani lumshe ido suke kamar ma su jin barci Kaɗan-kaɗan daga can nesa suka fara jiyo hayaniyar mutane, suna nufo in da suke, kasa kunne suka yi suna sauraro su ji, wannan hayaniya ta mecece. Basu fargaba sai ganin gungun jama'ar kauyen su ka yi sun nufo su, hannayen su riƙe da sanduna wasu kuma suna riƙe da wuƙaƙe, zuba musu ido su Ayla suka yi, sun kasa tashi ma bare su yi yunkurin guduwa, dan su a nasu tunanin ma basu yi laifin komai ba, sun ɗauka wasu can daban yan kauyen suka biyo. Sun zuba ido suna ganin ikon Allah, har yan kauyen suka iso wajen da suke. Su na zawa ba su yi wata-wata ba suka fara sauƙe musu sandunan hannayen su a jikin su, sosai Ayla da Kausar ke ihu ita kam Rimsha tana zaune shiru, alamar bata san ma meke faruwa ba, ga shi kuma su yan ƙauyen a nasu ganin ido suna duka har da Rimsha, sai dai kuma abun da ba su sani ba sandunan nasu baya taɓa jikin Rimsha Sosai yan ƙauyen ke dukan Kausar da Ayla, ita kuma Rimsha ga shi dai a zahiri suna sauƙe mata sandan a jikin ta, amma a ɓaɗini ba haka bane, domin ko kaɗan bata ji alamar saukan sanda a jikin ta ba, tana dai ganin jama'ar ƙauyen suna ɗaga sanduna kamar zasu buga mata, sai kuma taga sandar ya ɓace, ga shi sai magana take musu, amma basa jin komai da take faɗa, duka kawai suke kai mu su, a yaren yarabanci suna ce mu su mayu ne, su suka kashe olohunwa Kausar da Ayla sun daku jikin su duk ya farfashe sai jini yake, bayin Allah, ita ma Rimsha a idon yan ƙauyen jikin ta ya fashe yana jini, amma kuma ba hakan bane. Sai da yan ƙauyen nan suka ga kamar su Kausar sun mutu basa numfashin, sannan suka kyalesu suka wuce suka bar su a wajen kwance cikin jini. Suna tafiya wani haske ya fita daga jikin Rimsha ya tashi sama, ya bi bayan yan ƙauyen, wannan hasken na fita Rimsha ta dawo cikin hayyacin ta, ta tsorata sosai lokacin da idon ta ya sauƙa kan su Kausar, cike da tashin hankali ta fara girgiza su, tana kiran sunaye su. Sosai take kuka ta na kiran su, amma ina ko motsi ba sa yi, kamar sun mutu, juyawa gabas da yamma kudu da arewa Rimsha tayi babu kowa a wajen, kara sautin kukan nata tayi baiwar Allah, sai jan hanci take, hawaye bibbiyu a fuskar ta, banda sunan Allah ba abun da take kira. "Sannun ki baiwar Allah" taji wani zazzakar murya irin nata sak ta bayan ta, a razane Rimsha ta juya, wata kyakkyawar yarinya ce, yar matashiyar budurwa, wadda ba zata wuce Rimsha ɗin a shekaru ba. Cikin sauri Rimsha ta miƙe tsaye ta kari sa wajen yarinyar tana kuka kamar ranta zai fita, da kyar ta iya cewa "Dan Allah ki taimake ni, yan uwana zasu mutu, suna zubar da jini" tayi maganar cikin ruɗu da kiɗi ma haɗi da tashin hankali mai tsanani. Sanya fararen hannayen ta yarinyar tayi, ta goge wa Rimsha hawayen fuskar ta, a nitse tace "Ki yi shiru, abun da nazo yi kenan, taimakon ku" ta kai karshen maganar tare da wucewa wajen da su Ayla ke kwance. A gaban su ta tsugunna tare da ciro wani magani daga jakar da take rataye da shi a jikin ta, cikin sauri Rimsha ta ƙariso wajen ita ma, tana hawaye ta tsugunna kusa da yarinyar tana kallon yadda yarinyar ke shafawa su Ayla maganin hannun ta. "Ki yi shiru Rimsha, ki dai'na kuka kin ji?" Cewar yarinyar, zaro ido Rimsha tayi murya na kerman tsoro tace "Waye ya faɗa miki sunana" cool murmushi yarinyar ta saki, har sai da dimple nata irin na Rimsha ya lotsa, haka zalika murmushi nata yayi sanadiyar bayyanar kyawawan fararen hakwaran ta, har wani haske ke fitowa daga tsakanin hakwaran nata, yarinyar kyakkyawar yarinya ce ajin farko, jikin ta sumul babu ko alamar tabo a jikin, fara ce tas kamar farin turawa ko in ce yan Korea, hancin nan nata ɗan siriri kamar pencil, tana da manya-manyan ido kyawawa, sai dai abun mamaki idan nata sak na Rimsha babu abun da ya ra ba, ita ma sleeping eyes gare ta, haka zalika bakin ta sak na Rimsha babu abun da ya raba. Babu abun da ya fi jan hankalin Rimsha a fuskar yarinyar nan face gashin gerar ta da kuma yanayin shape na fuskar nata, babu abun da ya raba shi da na Rimsha ɗin, sosai Rimsha tayi mamaki ganin wannan halitta mai kama da ita, gashi kuma a tsawo ma ba zata wuci Rimsha ɗin ba, haka a shekaru, a takaice dai banbancin wannan yarinya da Rimsha hasken fata, ita Rimsha fatar ta chocolate color ne, yarinyar kuma fara ce tas, kuma jikin yarinyar bai yi yana yi da jikin ɗan Adam ba, dan baka iya ganin joint na jikin ta, sannan kuma babu tabo ko kaɗan a jikin ta sumul take. Zuba mata ido Rimsha tayi tana kallon ta, har ta kammala aikin shafawa su Ayla maganain da ta taho da shi, sannan ta miƙe tana faɗin "Nan da minti biyar za su tashi, kuma za su tashi lafiya lou ba tare da wani ciwo ba" ta kai karshen maganar tare da juyawa zata bar wajen, cikin sauri Rimsha tace "mun gode mai taimako" Wannan cool murmushi nata irin na Rimsha ta saki, har sai da dimple na ta irin na Rimsha ya bayyana a nitse tace "Ba sunana mai taimako ba, sunana Malika" tana kai karshen maganar ta wuce da sauri ta bar wajen, dawo da kallon ta kan su Ayla Rimsha tayi tana faɗin "Allah nagode maka, Malika kema mun gode miki" Kamar yadda Malika ta faɗa haka su Ayla su ka tashi lafiya Lou, sun yi sumut da su, sai yar waige-waige su ke kamar ma su neman wani abun "Ayla sannun ko, Kausar kema sannu" Cewar Rimsha tayi maganar tana kallon su miƙewa zaune suka yi, suna zare ido kamar ma su neman wani abun, matsowa Rismha tayi ta riƙo hannun Ayla tana faɗin "Ayla akoi in da yake miki ciwo ne?" Girgiza kai Ayla tayi kafin tace "A'a babu" riƙo hannun Kausar ma Rimsha tayi ta tambaye ta, ko akoi in da ya ke yi mata ciwo, ita ma a'a tace, miƙewa Rimsha ta yi tana faɗin "To ku tashi muje ko?" a tare suka miƙe Ayla da Kausar suna jin kamar sun yi mafarkin an mu su duka, abun ya zama musu tamkar a mafarki, ita ma kuma Rimsha bata sanar da su cewa a zahiri ne ba a mafarki ba, sai ta kyale su kawai suka ci-gaba da tafiya. Sun yi tafiya mai nisa kafin su isko wani karamin titi, lokacin karfe goma na safe zai yi. Sun jima tsaye a bakin wannan ɗan karamin titi kafin su samu wani mota wanda ya ɗauko katako, irin wayan nan taxi ɗin ne, masu kirar mota 206 Cikin sauri Kausar ta daka tar da motar, dan sun gaji da tsayuwa a bakin titi bayin Allah, da farko kamar mai motar ba zai daka ta ba, amma ganin yanmata tsaye a wajen wannan daji yasa ya tsaya, cikin sauri Kausar ta karisa wajen nasa, su kuma Ayla da Rimsha suna tsaye. Da harshen yarabanci Kausar ta yiwa mai motar magana, a kan ya taimaka ya kai su eyankorin, hakuri ya bata kasan cewar babu filin da zai ɗauke su su dukan su a motar nasa, cikin sauri Kausar tace masa, "Baba zamu zauna a gaba" dawo da kallon sa yayi wajen da Kausar ke nuna masa zasu zauna yace "Ku uku a gaban mota kuma kan kujera ɗaya" da sauri ta gyaɗa masa kai tana faɗin "Eh baba zamu zauna, dan Allah ka taimaka mana, idan ka wuce ba mu san ya za mu yi ba" jinjina kai yayi kafin yace "To shikenan ku shigo mu tafi" da sauri ta juya ta kwalawa su Rimsha kira, da yar gudun su, suka kariso wajen. Ayla ce ta fara shiga sai Kausar, suka ɗaura Rimsha a saman cinyar su, saboda ita ce karama kuma bata da nauyi, dan yar siriri ya ce, sai kallon su mai motar yake kamar zai yi masu magana, sai kuma ya fasa ya kunna motar kawai suka bar wajen. Sai satar kallon Rimsha yake ta cikin mirror taxi ɗin nasa, shi dai tun da yake bai taɓa kallon yarinya mai bala'i kyan Rimsha ba, musamman ma idan ta ɗan motsa ɗan karamin bakin ta, dimple nata ya lotsa, subhanallah idan mutun yayi wasa kyan Rimsha sai ya sa shi ya saki kan motar sa, duk da wuyar da ta sha na Daular Mutuwa ga kuma tafiyar da suka yi a dajin nan, duk da haka, ba wani canji a fuskar ta sai ɗan rama kaɗan da tayi, amma kyan ta na nan. Shiru suka yi ba wan da yayi wa ɗan uwan sa magana, har suka isa eyankorin junction, a nan mai motar ya sauke su, kwance kuɗin dage ɗaure a igiyar rigar ta Rimsha tayi suka bawa mai mota, kin karɓa yayi yace suje dan Allah ya kawo su, sai murna suke, suka masa godiya tare da tsallaka titi suka nufi hanyar ogele, suna tafiya suna hira kaɗan kaɗan, jikin su duk ciwo yake musu. Gaban wani ɗan ma ɗai-ɗai cin gida suka tsaya, gida ne na mai kuɗi dai-dai gwargwado, gaba ɗaya gidan rufi ɗaya ne, kun dai san yadda ginin yarabawa yake, basu cika yin fencing na gida ba, haka suke barin sa, basu da sirri komai a wangale ake yin sa, a waje suke girki wanke-wanke, wanki da sauran su. Kausar ce ta sanya hannun ta ta fara knocking na kofar palon, dan na gaya muku dama ba fencing gidan, rufin ɗaku na ne kawai. Daga cikin ɗakin wata murya tace "Tani? Nbowa (waye ne? Ina zuwa)" shiru Kausar tayi tana tunanin yadda zata ga maman ta. Sun kai 3mins tsaye a wajen kafin nan wata mata wadda da ka ganta kaga bahaushiya, kuma kaman ta ɗaya da Kausar, ita ce tazo ta buɗe kofar tana faɗin "Kilode (menene)" Ihu ta kurma lokacin da idon ta ya sauka kan fuskar Kausar, rungume ta Kausar tayi, ita ma matar ta rungume Kausar tana faɗin "oh oluwa" kun san dai yadda shaukin soyayya tsakanin uwa da ƴa yake, musamman a ce sun jima basu haɗu ba, abun ba'a cewa komai, dukan su hawaye suke sun rungume juna, sai ihu iya Kausara take tana kiran oluwa oluwa, kan kace me makota sun tattaro cincirindon dan suzo su ji lafiya iya Kausara ke ihu haka. Ganin Kausar yasa suma suka fara na su ihun murnan, su Rimsha sun tsorata sosai da jin yadda suke ihu, basu san yarabawa bane, yarabawa idan suna magana cikin kwanciyar hankali ma sai ka ɗauka faɗa ake, saboda Allah ya zuba musu murya mai sauti, har sama idan suna magana, ina ga kuma abun murna ya samu, ai shikenan kuma sai dai wanda bai saba ji ba ya toshe kunne Gaba ɗaya sun cike anguwar da ihun Kausara ta dawo Kausara ta dawo, wannan ya ja Kausar ta nan wannan ya ja ta ta can, farinciki a wajen su ba'a magana, babu wanda ya kula da Rimsha da Ayla, Allah sarki bayin Allah sai bin su kawai suke da ido, sun ga abun da yafi karfin su. Almost 20mins ana wannan ihun murna na dawowan Kausara kafin iya Kausara ta jata zuwa cikin gida tana faɗin suje tayi wanka taci abinci sannan tazo ta basu labarin ina ta ɓata, suma makotan kowa ya wuce gidan sa, suka bar su Rimsha tsaye sun rasa madafa, sai zare ido suke gwanin ban tausayi. Har sun shige cikin gida, Kausar ta fito da gudu tana faɗin "Iya friends ɗina" bin ta da ido iya Kausara tayi tana kallon ta, har ta fito wajen palon. In da ta bar su Rimsha tsaye wajen ta fito ta same su, sun kasa ko motsawa Allah sarki, tunanin nasu iyayen kawai suke, ita Rimsha tana tunanin ita ma idan ta koma gida kila haka su Jehan za su yi mata, ita kam Ayla ƙoƙarin ɓoye hawayen dake ƙoƙarin zubo mata take, dan ganin Kausar cikin yan uwan ta, ya jefa ta cikin tashin hankali, dan ita ba ma ta da yan uwan bata da kowa sai maman ta kawai. Suna tsaye sunyi jugum jugum babu wanda ya kula su, Kausar tazo ta jawo hannayen su tana faɗin "Kuzo muje?" Bin ta su kayi zalalau-zalalau zuwa cikin gida, duk jikin su a mace, ji suke kamar su yi ta kuka kada su dakata "Kausar su waye wayan nan?" Iya Kausar ta tambaya cikin harshen Hausa "Iya friends ɗina ne tare muka zo ai" kallon tsab iya Kausar ta musu kafin tace "Ban gane tare kuka zo ba? Ina za su je?" Saman sofa dake cikin palon Kausar ta zauna tana faɗin "Iya nan mana suka zo, basu da kowa ne shiyasa" tsawa iya Kausar ta daka mata "Dan basu da kowa, sai ki kwaso su ki kawo ma na su? Tukun nan ma daga ina kuke?" Cikin sauri Kausar tace "Daga Daular Mutuwa muka fito" Har wani bonsin iya Kausar tayi jin an ambaci sunan Mutuwa, dafe kirji tayi tana zare ido tace "oloni Kausara Mutuwa kuma?" Gyaɗa mata kai Kausar tayi tana faɗin "Eh iya Daular Mutuwa" "kaiii Kausara ki dai na kiran Mutuwar nan, wannan suna mai sanya tashin hankali haka, tukun nan ma ai na kuka samu wannan suna?" Tana magana tana zare ido ta dafe kirji "iya gaskiya na faɗa miki daga Daular Mutuwa muka fito, Daular da ba'a shiga a fito a raye, mu Allah ne ya tsare muna da sauran kwana" hannu biyu duka iya Kausar ta ɗaura a kan ta, ta kara zaro idon nan waje, nan take ta birkice musu kamar wadda notir ɗin kan ta ya kwance, cikin sauri ta dawo kusa da Kausar ta zauna, kun san dai yadda yarabawa suke idan suka tsorata "Yanzu Kausar Mutuwa ma har da Daula yake da shi? Na shiga uku ni jummai, Kausara anya kinji me kika faɗa kuwa?" Gyaɗa mata kai Kausar tayi, sannan ta fara bata labari cikin Daular Mutuwa da yadda suke yanka mutane, a zabure iya Kausar ta miƙe da karfi tace "Kai kakai kakai Kausara bari bani wannan labari, bar shi kada ni ki kashe ni, ke basu kashe ki a Daular Mutuwa ba ni kuma zaki kashe ni a nan da labari, ni wlh bana son ji, ya isa haka, bayin Allah sannun ku eyeee wannan bala'i haka, gaskiya na tausaya mu ku" tana magana tana zare ido kamar idon ta zai faɗi kasa, dariya Kausar tayi tace "Iya wannan fa baki ji ko kwata daga cikin labarin abun da muka gani a Daular Mutuwa ba, har da masu canza ido fa" ihu iya Kausara ta kurma tana faɗin "oloni Kausara zan wurgaki waje idan baki dai na kiran wannan bala'i ba, ki dai na kira mun Mutuwa tsirarar ta a nan" abun ma dariya yaso bawa Rimsha da Ayla, ganin yadda iya Kausar ta birkice musu lokaci guda, daga jin sunan Daular Mutuwa, wanna da ita aka kai Daular Mutuwa tsoro da fargaba ne za su kashe ta, mata sai bala'i tsoro, ji yadda take zare ido, tana bahaushiya amma zaman ta da yarabawa yasa ta dawo sak su, ta koyi ɗabi'un su da komai nasu, idan ba kaga fuskar ta na hausawa ba, bazata taɓa cewa bahaushiya bace, duk wani attitude nata na yoroba ne yanzu. Iya Kausar kam daga jin zancen Daular Mutuwa sai ta nitsu tayi hankali har da yiwa su Rimsha sannu. "Iya ina boder Jami'u?" Cewar Kausar "Baki tambayi dadyn ki ba, kina tambayar boder Jami'u ko?" Dariya Kausar tayi kafin tace "Ai zan manbaye shi ina suke?" Tayi maganar tana miƙe wa ta nufi wani ɗaki mai kama da kitchen "Daddy'n yana Lagos, Jami'u kuma yana cikin Ilorin" iya Kausar ta bata amsa, already Kausar ta shige cikin Kitchen abun ta. Tukunyar abinci ɗungurungum na shi ta ɗauko , ta dawo palon ta yi zaman yan bori a kasan carpet, ba wanke hannu ba komai ta fara dumbulan abincin tana kai loma bakinta, "Kausar ba zaki kira friends na ki su zo ku ci bane?" Cewar iya, kallon su Kausar tayi, duk sun yi tsuru-tsuru da su, kamar wasu marayu, kamar biri yana jin matsanancin yinwa, haka suka yi da fuskokin su "Ayla kuzo kuci abinci mana" ta faɗa tana tura abinci a baki, jolof rice ne ya ji kayan haɗi sai kamshi yake, dan ba karya yarabawa sun kware wajen iya girki Haushi yasa Rimsha tace bazata ci ba, dan a ganin ta Kausar ta wulakanta su ne, ga shi tana jin matsananciyar yunwa saboda jiya ma bata iya cin abincin da matar sarki ta ba su ba, amma ba zata ci abincin nan dake gaban Kausar ba, dan Kausar ta raina su, kuma har ga Allah ita Rimsha bata ɗaukan wannan wulakanci, karku manta duk da Rimsha take shiru-shiru mai sauƙin kai, jinin Nawazudden ne ke gudu a jikin ta, kanwar DPO Jehan ce, family Nawazudden basa ɗauran raini da wulakanci ko kaɗan Ita ma Ayla ganin Kausar taƙi cin abincin yasa ita ma tace ta ƙoshi, Kausar ko a jikin ta dan sun ce sun ƙoshi, ta ci-gaba da ɗura abincin ta kawai, dan ita bata da burin da ya wuce taci ta ƙoshi, bata wasa da abinci, sannan ko wani irin wulakanci zaka mata, ka mata in dai zaka ba ta abinci to zata ɗauka Ita ma iya Kausar ba ta wani damu ba, dan su Rimsha sun ƙi cin abinci, haka suna ji suna gani, suna jin matsanancin yunwa haka Kausar taci abincin nan iya cin ta ta mai da sauran kitchen bayan ta ƙoshi, sai wani ƙugi cikin su yake, musamman idan suka shaƙi kamshin abincin sai ka ji cikin su na kulululu saboda bala'i yunwa, Allah sarki bayin Allah. Bayan Kausar ta mai da sauran abincin Kitchen ne ta dawo tace su tashi su je ɗakin ta su ɗan huta, ba musu suka ta shi, tayi gaba suka bi bayan ta Ɗaki ne mai ɗan girma, dan ginin yarabawa suna yin sa da girma ɗakunan su, ƙaramin gado ne guda ɗaya a ciki, sai yar drawer saka kaya shikenan. Saman gadon Kausar ta haye tana faɗin "Yau zan yi barci mai daɗi Alhadulillah" gefen gadon Ayla da Rimsha suka zauna suna bin ɗakin da kallo. To masu karatu sai Allah ya sa da mu bayan na dawo hutu, ku ci-gaba da yiwa Rimshan daddy addu'a, dan har yanzu da sauran ta, bata fita ukubar rayuwa ba, baiwar Allah 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode 11-12🌹🌹 Ɗaki ne mai ɗan girma, don ginin Yarabawa suna yin sa da girma ɗakunansu, ƙaramin gado ne guda ɗaya a ciki, sai 'yar drawer saka kaya shi ke nan. Saman gadon Kausar ta haye tana faɗin, "Yau zan yi barci mai daɗi Alhadulillah!" Gefen gadon Ayla da Rimsha suka zauna suna bin ɗakin da kallo. "Kausar ina ne toilet naku? Ina son in je in yi wanka." Cewar Rimsha. Miƙewa zaune a tsakiyar gadon Kausar ta yi tana turɓune fuska ta ce, "Idan kin fita falo ta wannan hanya da na bi na je na ɗauko abinci, to ta nan za ki bi toilet na wajen." Miƙewa Rimsha ta yi tana faɗin "Ayla bari na je na yi wanka." Ayla kam ta kasa magana baiwar Allah saboda tsananin yunwa da take ji, haka ta zuba wa Rimsha waɗannan idanun nata da suƙa ƙanƙance saboda wahala tana kallon ta har ta fice daga ɗakin, shiru suka yi daga ita har Kausar ɗin, kowa da abin da yake tunani. 💞💞After some minutes💞💞 Ɗaure da towel nasu da ta ɗauko a toilet ɗin Rimsha ta shigo cikin ɗakin Kausar, yadda ta fita ta bar su haka ta dawo ta same su, tana shigowa Ayla ta miƙe tana faɗin, "Ni ma bari na je na yi wankan ina zuwa." To, kawai Rimsha ta amsa mata da shi, sannan ta zauna a gefan gadon tana kokarin mayar da kayan dattin ta da ta cire kafin ta yi wanka, duk bala'i datti ya canza wa kayan launi, ba za ka taɓa gane cewa wannan pink blouse gown ɗin nata mai bala'i kyau da ta fita da shi gida ba ne, saboda tsananin dattin da ya yi, ya zama launin kasa, har wani maiƙo-maiƙon datti jikin rigan yake. "Meesha kada ki saka kayan dattin nan kin ji? Ki tashi ki duba kayan da kike so a cikin drawer kayana ki saka." Cewar Kausar, da kamar Rimsha za ta ƙi, sai kuma ta tuna kayan nata warin datti yake sosai, don haka sai ta hakura ta miƙe ta nufi drawer kayan Kausar. Mafi yawancin kayan dake cikin drawer wandunan Jeans ne da T-shirt, sai gown na kanti da na materials, atamfofi ƴan kwaranni ne a ciki, duk wanda ya san Yarabawa ya san su da sanya ƙananan kaya, daga yaransu har manya, kai har tsofaffi, ba su damu da atamfa ko leshi ba, idan ka gan su da atamfa ko leshi to biki za su je, ko Walima ko dai wani shagali, amma ban da haka za ka ga jibgegiyar mata ga tsawo ga ƙiba, sai ka gan ta da wandon Jeans ya matse ta kamar cinyoyin ta za su fasa wandon su fito waje, kana ganin komai na daga halittarta, a haka suke yawo a cikin gari, a haka suke rayuwarsu ba ruwansu, ba ruwan kowa da kowa, sai wanda ka shigo da shi cikin rayuwarka. Da kyar Rimsha ta laluɓa ta fito da wata doguwar riga mai faɗi kaɗan, ita ta sanya a jikinta, duk da Kausar ta fi su jiki, rigar ta zauna wa Rimsha sosai a jikin ta, saboda Allah ya mata wata irin halitta wanda Hausawa ke cewa karuwan jiki, komai ta sa zama yake a jikinta ɗas kamar don ita aka yi shi. After some hours💞💞 Sun gama shirin su tsab, har ita ma Kausar ta yi wanka, ta sha wandon jeans da T-shirt, kayan sun matse ta sosai, sai wani washe baki take, ta ci ta ƙoshi ta bar su Rimsha da jin bala'in yunwa. Suna zaune a falo, yayin da ita kuma Iya tana cikin kicin tana ƙoƙarin girka abincin rana. Kamar wadda aka tsikara Kausar ta miƙe tana faɗin, "Ku zo mu je ku ga garin Yarabawa yau kam, tunda Allah ya kawo ku." Da farko Rimsha ta ce, a'a ita ba za ta je ba, sai da Ayla ta sa baki sannan ta hakura ta miƙe suka fito a tare, sai wani murmushi Kausar take kamar ba lafiya ba. Miƙar hanya suka yi zuwa Eyankorin Junction, sai surutu Kausar ke zuba musu, ban da um da uhm ba abin da suke bin ta da shi, saboda yunwa suke ji, ba bakin yin magana sosai, gara ita ta ci ta ƙoshi. Duk wanda suka wuce in ma mace ko namiji sai ya kara waigawa ya kalli Rimsha, ga shi yanayin yadda take ta fi kama da mai jin barci saboda kasalar da yunwa ta sauke mata, sannan kuma ta sanya takalman Kausar mai ɗan tudu kaɗan a kafarta, hakan yasa take jan kafa a hankali. Jama'a sai tambayar Kausar suke yaushe ta dawo, ina kuma ta samo yar Indiya, wasu ta ba su amsa wasu kuma ta share su Sun zo za su wace wasu gidaje da ke jere kamar tagwayen gida, komai na ginin iri ɗaya, wata yarinya dake zaune a tsakanin gidajen tana wasan ƙasa ne ta ce "Kausar iya Ganiyu ta fara zane, masu kyau." Ƴar yarinya ba za ta wuce shekara bakwai ba, cikin sauri Kausar ta ce, "Da gaske kike Waliya?" Gyaɗa mata kai yarinyar ta yi tana duƙe tana wasan kasarta. Cikin sauri Kausar ta juya tana faɗin, "Meesha ku zo mu je Iya Ganiyu ta yi mana zane." Girgiza kai Rimsha ta yi tana faɗin "Ni Kausar ba na son yawon nan mu koma gida." Ƴar dariya Kausar ta yi kafin ta ce, "Kada ki damu idan mun je wajenta, ta mana zane sai mu dawo gida." Shiru Rimsha ta yi ba ta sake yin magana ba, wucewa gaba Kausar ta yi suka bi bayanta, kamar raƙumi da akala, duk in da Kausar ta yi haka suke daurewa ga yunwa suna jan ƙafa su bi bayanta, ita kuwa Kausar har wani taku take ta ci ta ƙoshi abinta. Kafin su kai gidan iya Ganiyu suka iso ko wani shagon kanti. "Kausar bari na sayi drinks a nan shagon kin ji?" Cewar Rimsha ta yi magana tana fito da wannan ₦2,500 ɗin da sarki da matarsa suka ba su. Kausar ko a jikinta, wai an yakushi kakkausa ta ce, "Ki saya mana Meesha, duk abin da kike so ki saya." Miƙa wa Ayla dubu ɗaya Rimsha ta yi tana faɗin, "Ayla ke ce babba ki riƙe wannan, ni da Kausar kuma sai mu raba ragowar ₦1,500 ɗin." Cikin sauri Kausar ta ce, "A'a ni ba na so, ni da na dawo gida, na bar muku tunda ni na iso gida." Kallon Ayla Rimsha ta yi, abin gwanin ban tausayi, murya a raunane saboda yunwa ta ce, "To shi ke nan Ayla ga ɗari biyar ɗin nan, ki haɗa ni kuma zan riƙe 1k Kausar mun gode." Girgiza kai Ayla ta yi tana faɗin "Ai yanzu tsakanin mu babu zancen raba kuɗi, ki bar kuɗin duka a wajenki, ki riƙe mana, idan buƙatar su ta taso sai mu yi amfani da su." To, kawai Rimsha ta ce tare da karɓar kuɗin ta haɗa, sannan ta shige cikin shagon bakinta ɗauke da sallama. Sai kallon ta mai shagon yake, da Yarabanci ya ce da Kausar "Kausar ina kika samu wannan ƴar Indiyar?" Kallon banza Kausar ta masa ta ce, "Sadudin amma kamar na ce kada ka sake yi mini magana kafin mu yi tafiya da Iya ko?" Shi ma kallon sama da kasan ya mata kafin ya wuce ya je ya ɗauko wa Rimsha Coca Colar gora biyu, masu sanyi daga fridge ɗinsa, sannan ya haɗo mata da biscuits guda biyu, kamar yadda ta buƙata. Karɓa Rimsha ta yi tare da miƙa masa 1k da ke ɗayan hannunta, karɓa shi ma ya yi ya ɗauko canjin 400 ya miƙa mata, ta karɓa ta fito, ta zo ta miƙa wa Ayla Coca Colar guda ɗaya da biscuit ɗaya, ita Kausar ta ce ba ta buƙata, karɓa Ayla ta yi, suka wuce suna hira "Ku sha lemon mana Meesha." Cewar Kausar, kallon ta Rimsha ta yi kafin ta ce "A'a ya za a yi mu ci abu muna tafiya a kan hanya?" Dariya Kausar ta yi tana faɗin, "Meesha nan fa ƙasar Yarabawa kuke, ba cikin Hausawa ba ne, mu a nan babu ruwanmu da kowa, ko a tsakiyar titi kika ji za ki iya cin abin da kike so za ki ci, ba ruwan wani da ke, ke ba ki ga wancan gidan da muka wuce in da Waliya ke zaune tana wasan nan ba ne? Ba ki ga a waje suke girkinsu ba ne? Ku Hausawa ku ne kuka san wani abu wai sai an shiga gida ake wasu abubuwa, mu ba ruwanmu da hakan, a nan kowa yana da ƴancin ya yi abin da yake so." Shiru suka yi dukansu, don daga Rimsha har Ayla babu wanda zai iya cin abinci a kan hanya, don ba su saba ba, ita ma Kausar ɗin da ta ga ba su da ra'ayi cin abu a kan hanya, sai ba ta takura musu ba, don ta san Hausawa ne su, ta sha zuwa garuruwansu ta san yadda suke rayuwar daban da ta Yarabawa, su Hausawa suna siririnta abubuwansu da dama, amma su Yarabawa babu ruwansu, abin da suka yi ra'ayi za su yi kuma ko a ina ne a cikin garinsu. Da sallama suka shiga wani gida, wanda ba za a iya ce masa gida kai tsaye ba, sai dai a ce ɗaki, domin babu katanga gidan, ɗaki ɗaya ne a wajen kamar shago, sai wani waje daga ɗan nesa da ɗakin wanda aka kewaye da bulo, ba gini aka yi ba, an ɗaura bulon ne ɗaya kan ɗaya, kuma ba har sama ba, iya rabi aka yi shi kawai, kana tsaye daga ɗan nesa ma kana iya hango abin dake cikin wajen, murhun girki ne da gingima-gingiman tukane da sauran kwanuka, da alama shi ne kicin na masu gidan. Ganin ba kowa a wajen yasa Kausar ta sake kwaɗa sallama, wata mace ce mai ƙiba ta fito daga cikin ɗakin wadda da ka gan ta ka ga asalin Bayerabiya. Cikin harshen Yarabanci ta yi musu sannun da zuwa, sai murmushi take saboda ta san Kausar, da fara'a ita ma Kausar ta amsa mata tare da gaishe ta. Bayan sun gama gaisawa ne Kausar ta sanar da ita abin da ya kawo su. To matar ta ce tare da wuce wa ta koma cikin ɗaki, su kuma suna tsaye, Rimsha da Ayla sai faman bin garin da kallo suke, ita kuma Kausar sai wani murmushi take kamar ba lafiya ba. Jim kaɗan matar ta fito hannunta riƙe da wata baƙar gora mai ɗauke da wani baƙin ruwa kamar tawada, ɗayan hannun kuma ɗauke yake da wata ƙatuwar kujera. Ajiye kujerar ta yi a ta gefe da bakin kofar ɗakin nata, sannan ta zauna tana faɗin me za ta zana musu, Rimsha ta ce ita kam ba ta so, ganin Rimsha ta ce ba ta so, ya sa ita ma Ayla ta ce ba ta so, kuma da ma ita Ayla ba ta sa a ranta za ta yi wani zane ba, da ma dai ta ce idan Rimsha ta yi, ita ma za ta ce a mata, idan kuma Rimsha ba ta yi ba, to ita ma ba za ta yi ba. Kausar kam cike da zumuɗi ta miƙa hannunta ta bayan hannun ta ce a zana mata sunan boda Jamiyu, kama hannun nata matar ta yi ta fara zana mata da wani abu mai kama da fensir. Duk wanda ya san asalin Yarabawa ya san mafi yawancinsu da irin wannan zane, na zana sunan miji a jikinsu da wannan abu kamar tattoo ɗin amma ba tattoo bane. Su Rimsha sun zuba ido suna ganin yadda matar take zana wa Kausar sunan boda Jamiyu a hannunta, lokaci guda Rimsha ta ji sha'awar abin har cikin ranta, cikin sauri ta ce "Kausar ki ce ni ma ina so a zana mini." Murmushi irin na mai jin matsanancin yunwa Ayla ta yi kafin ta ce, "Me za a zana miki to? Kin ga dai ita Kausar boda Jamiyu ta ce kuma daga gani wannan boda Jamiyu shi ne mijin da za ta aura, don tun da muka zo nan ba ta da wata magana sai boda Jamiyu, ko dai ke ma boda Jamiyun za a zana miki ne? Ko kuma sunan ki Rimsha? Don na san dai ba ki da saurayi." Cool murmushi Rimsha ta saki, wanda sai da ya sanya kyawawan haƙwaranta bayyana, sannan wannan kyakkyawan dimple ɗin nata ya lotsa gwanin ban sha'awa, a nutse ta ce, "Yanzu Ayla sai ki rasa waye za ki ce a zana mini sai boda Jamiyu? So kike Kausar ta sumar da ni ne yadda take ji da wannan boda Jamiyu, ni har na ƙosa ya dawo na gan shi, in ga waye wannan Kausar ta dame mu da zancensa." Ƴar dariyar yunwa Ayla ta yi kafin ta ce, "To ai na ga ke ba ki da saurayi ne, to ko dai sunanki za a zana miƙi ne?" Shiru Rimsha ta yi tana ta murmushi ita kaɗai, kamar ba lafiya ba, ba ta sake ce da Ayla ko uffan ba, shiru ita ma Ayla ta yi, suka zuba wa Kausar da matar ido kawai suna kallon zane. Duk hirar da suke yi Kausar na jin su sai dai bata tanka su ba. Bayan an gama yi mata zanen, Rimsha ta miƙe ta je gaban matar ta tsugunna tana faɗin "Kausar kin faɗa mata ne?" gyaɗa kai Kausar ta yi alamar e. "A ina za a zana miƙi? Kuma me za a zana miƙi?" Cewar matar, ta yi maganar cikin harshen Yarabanci, juyowa Rimsha ta yi tana kallon Kausar tana jiran Kausar ta fassara mata, fassara mata abin da matar ta ce Kausar ta yi, wani haɗaɗɗen murmushin Rimsha ta sake saki a karo na biyu, sai kallon ta su Kausar suke Ayla kam mamaki irin murmushi da Rimsha take ya hana ta yin magana Miƙa wa Ayla Coca Colar da biscuit dake hannun ta Rimsha ta yi, bayan Ayla ta karɓa, sai ta sanya hannunta, ta cire mayafin kanta, ta ɗan zuge zip ɗin rigarta, ƙasa kaɗan, ta zamo da hannayen rigar nata zuwa kafaɗar ta, su Ayla dai sun zuba ido suna ganin ikon Allah, suna jira suga me Rimsha za ta yi ne wai. Bayan ta gama zamo da hannun rigar ta zuwa kafaɗar ta sai ta matsowa da matar kirjinta, ta ce a rubuta mata "The General Of The Army Romeo'', Tashin hankali babbar magana, kallon-kallon su Ayla suka fara yi wa junansu ita da Kausar, tunani suke anya Rimsha ba ta samu matsala a ƙwaƙwalwarta ba kuwa? Ta rasa sunan da za ta ce a zana mata sai sunan wannan kafurin Bature da bai san da zamanta a duniya ba, kuma ma ta rasa a ina za a zana mata wannan suna sai a kirji, kai lallai ya tabbata Rimsha ba ta da hankali. Suna can suna zancen zuci su ba su sani ba Iya Ganiyu ta gama zana wa Rimsha rubutun nan a kirjinta, da kananan rubutu, saboda tsawon sunan. Su Ayla ba su ankara ba sai jin muryan Rimsha suka yi tana faɗin "A kasan The General Of The Army kuma a rubuta mini, GAR." Tana magana tana kara sauƙe wuyan rigar nata zuwa saman breast nata, tashin hankali da ba a saka maka rana, Rimsha fa da gasken-gaske take, babu wasa a lamarin nata ko kaɗan, haka kuwa matar nan ta rubuta mata sunan Romeo kamar yadda ta buƙata, ga shi ruwa baya wanke abin, idan aka zana maka, tofa ya zauna ke nan, idan kana son gogewa sai an maka aiki a wajen, yau ga ikon Allah. "Ayla me za a zana miƙi?" Cewar Rimsha, girgiza kai Ayla baiwar Allah ta yi tana faɗin, "Ni jikar mutumin da ban san shi ba, ku rufa mini asiri, ni ba na so, to waye ma nake da shi da har zan zana sunansa a jikina? Sai dai idan sunanki ke da Kausar za a zana mini." Zaro dara-daran idanu Rimsha ta yi ta ce, "Ba mu gane ba? Kamar yaya sunana ni da Kausar? Ki yi mana bayani." Murya a raunane Ayla ta ce "Da kuke gani na ɗin nan, mamata kawai na sani a duniya, ita ma ban san asalin sunanta ba, don tun da na girma take cikin ciwo har na bar wajenta, babana ko alamar mai kama da shi ban taɓa sani ba, sunansa kawai nake ji, a takaice ma ƴan unguwarmu ce mini suke ba ni da baba wai shegiya ce ni." Ta kai karshen maganar tare ta miƙewa tana kokarin goge hawayen da ke zubo mata, Allah Sarki! Cikin sauri Rimsha sarkin tausayi ta miƙe ta nufe ta tana faɗin, "Ki yi hakuri Ayla, ki yi wa baba addu'a Allah ya jikan sa kawai." Rungume Rimsha ta yi ta saki kukan da ta jima tana ɓoyewa, "Don Allah Ayla ki daina kuka kin ji ko, addu'a kawai za ki yi wa baba Allah ya jikan shi da rahma." Cikin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro Ayla ta ce, "Meesha waye ya ce miki babana ya rasu ne?" Hawaye ita ma Rimsha ta fara yi tana faɗin, "To idan bai rasu ba yana ina? Me yasa ba ki san shi ba?" Matsowa ita ma Kausar ta yi ta rungumo Ayla tana ɗan bubbuga bayanta alamar rarrashi, ita dai iya Ganiyu kallon su kawai take, da yake ba ta jin me suke faɗa sai ta bi su da ido kawai, don wannan al'adar Yarabawa ce, in dai ba kai ka kira su cikin magana ba, tofa ko kana yi ba za su saka maka baki ba, musamman ma idan ba da yarensu kake yi ba sai su yi banza da kai. "Rimsha babana yana nan da ransa, bai mutu ba, amma jama'ar unguwarmu suna ce mini ni shegiya ce, na tambayi mamana ina babana ta ce mini yana nan kuma ba ƙaramin mutun ba ne, babba ne a kasar nan, babba mai faɗa a ji ma kuwa. Sai dai kuma ban taɓa ganin shi ba, ban taɓa sanin inda yake ba, jama'a shegiya suke kira na, mun rayu cikin takaici da ukubar rayuwa, na yi fama da mamana ta faɗa mini me yasa ta rabu da babana, amma ta ki faɗa mini, ta ce babana yana da kuɗi sosai amma kuma ni da ita mun rayu cikin talauci babu cin yau bare na gobe, babu makaranta, wahala kan wahala, wani lokaci ma sai na ji gwara mutuwa da wannan rayuwata" Ta kai karshen maganar tare da sakin kuka mai sauti. Ganin sosai Ayla take kuka ne yasa iya Ganiyu ta miƙe ta fara rarrashin ta, duk da cewa ba ta san a kan me suke magana ba, ta lura yaran da suna cikin damuwa. Da kyar suka samu Ayla ta yi shiru, tare da taimakawar Iya Ganiyu, bayan Ayla ta yi shiru ne Kausar ta tambayi Iya Ganiyu nawa ne kuɗinta na zane, don su biya ta su koma gida. Kin faɗa musu kuɗin ta yi, ta ce su je ta yafe musu, godiya sosai suka mata sannan suka wuce, Kausar ce ta ɗauka musu Coca Colarsu, don Ayla ta yasar da shi lokaci da take kuka. Ko da suka koma gida a falo suka samu Iya Kausar tana zaune tana kallon Yoruba Film. Zama suka yi kusa da ita, da kyar su Rimsha suka iya shan Coca Colan da biscuit ɗin, sai shasshekar kuka tare da ajiyar zuciya Ayla take. Matsowa kusa da su Iya ta yi ta ɗan shafa kan Ayla ta ce "Me ya same ki kayi kuka?" Kausar ce ta yi maza ta cafe zancen ta fara ba wa Iya labarin abin da ya faru, sosai Iya ta tausaya mata, sannan ta tambaye su yadda aka yi suka bar gidan iyayensu, Rimsha ce ta fara gaya mata cewar ta fito sayan ashana ne ƴan Daular Mutuwa suka ɗauke ta, sosai Iya ta tausaya mata tare da ba ta hakuri. "Ke kuma Ayla ba ki faɗa mana ya aka yi kika bar wajen mamanki ba?" Cewar Iya, ɗaukar last biscuit da ya rage a cikin ledar Ayla ta yi, ta kai bakinta sannan ta ce "Tun da na taso na girma na yi wayo, mamana take cikin rashin lafiya, ba ta iya fita ko tsakar gida, ni nake zuwa na yi bara na samu mana abinci na kawo na bata ta ci a baki, idan za ta je banɗaki ni nake taimaka mata ta je, ba ta iya miƙewa da kanta, sai an taimaka mata, gidan da muke haya kuma, mu kaɗai ne a cikin gidan, babu kowa, ba zan taɓa manta wata ranar Laraba ba shekara uku cikin na huɗu da suka wuce, ranar jikin mamana ya tsananta, na dawo daga wajen bara na same ta tana wani irin numfashi kamar za ta mutu, sai kuka take, na ji tsoron kada ta mutu ta bar ni, sai na fito da gudu don na je na nemo wanda zai taimaka ya duba mini ita, a baya kafin na fara bara, duk inda na je neman taimako sai suce sai na basu kaina kafin su taimaka mini, mamana kuma ta tsawatar mini a kan hakan, ta ce ko mutuwa za ta yi kada na yarda na sayar da mutuncina, shi yasa na daina neman taimakon kowa a layinmu, sai dai na je wajen masu barar bakin kasuwa na zauna na yi bara. To wannan ranar Laraba na fito a gigice kamar mahaukaciya ina neman wanda zai taimaka wa mamana ya duba mini me ke damun ta, na je wajen mutane da dama amma ba su kula ni ba, don suna tunanin kuɗi nake so, na yi tafiya mai ɗan nisa ina neman taimako, har na bar layinmu. A gaba da layinmu na ci karo da wani mai ƙatuwar mota yana tsaye, ban yi wata-wata ba na karasa wajensa, har kasa na duƙa a gabansa ina haɗa shi da Allah da ya taimake ni ya zo ya duba mini me ke damun mamana, bai musa mini ba, ya ce na shiga mota mu je ya gan ta, na ruɗe na kiɗime ba na ganin komai sai mamana, hakan yasa na shiga motar, don mu je ya taimaka wa mamana, ashe ɗan Daular Mutuwa ne, shi ke nan tun da na shiga motar ban kara sanin inda nake ba, sai buɗe ido na yi na gan ni cikin Daular Mutuwa, na sha wahala fiye da tunanin mai tunani, shekarata kusan huɗu a can, babu kalar azabar da ban gani ba, ba irin tashin hankalin da ban gani ba, a gaban ido na ake kwakwalewa yara ido, a yanke wa mata nono da gaban su, baba da kuke ganin nan, shekaran sa zai kai talatin a Daular Mutuwa, su Mustapha kuma a gabana aka kawo su, ba zan iya misalta muku wahalar rayuwa da na sha ba, don ya wuce misali, sannan har yau da nake yi muku magana ban sake jin ɗuriyar wani da na sani ba, ban sani ba mamana tana raye ko ta mutu, duka ban sani ba!" Ta kai karshen maganar tare da kara sautin kukan da take. Duk falon ba wanda bai yi wa Ayla kuka ba, musamman Rimsha ta fi kowa kuka a cikinsu, sai jan hanci Iya take. Haɗuwa suka yi, suna hawaye suna rarrashin Ayla, da kyar suka samu ta yi shiru, hakuri iya ta ba ta tare da yi musu alkawarin baban Kausar na dawowa za ta karɓa musu kuɗi a wajensa, ta je da kanta ta sanya su a mota su koma wajen iyayensu, sosai suka ji daɗi tare da zuba mata ruwan godiya. After some minutes👌 Falon ya yi shiru, miƙewa Iya ta yi ta nufi kitchen, da sauri Rimsha ta miƙe ta bi bayanta tana faɗin, "Ina son in koyi girki Iya." Miƙe kafafu Kausar ta yi ta gyara ta kwanta saman sofa tana faɗin, "Ba sai ki koya ba, ni me ruwana, abin da na sani dai shi ne a girka a ba ni na ci kawai na sani, ni ce ƴar auta a gidan nan, kuma ni kaɗai ce mace dole ba zan yi aikin komai ba, sai dai su boda Wasiu." Ita dai Ayla shiru ta yi tana son koyon girki ita ma, amma ba yau ba, don yau ta tuna da rayuwarta ta baya, duk jikinta a mace ba za ta iya ko motsa jikinta sosai ba. Ita kam Rismha zagewa ta yi Iya na nuna mata yadda ake girki tana koya, don tun asalinta da ma tana da sha'awar koyon girki, shi yasa ko lokacin da suke gida tare da daddy tana yawan shiga kitchen wajen masu aiki ta tsaya tana ganin yadda suke aiki, saɓanin Jehan da ko hanyar kitchen ba ta bi bare ma ta shiga, ko abu take buƙata a Kitchen sai dai ta sanya masu aiki su ɗauko mata. Kwanciya ita ma Ayla ta yi saman sofa ta rintse ido tana jin kanta na sara mata a hankali saboda kukan da ta sha, da haka har barci ya ɗauke ta. Ita kuma Kausar ta ɗaura kafa ɗaya kan ɗaya daga kwance, ta kafe TV da idon tana kallo, Rimsha na Kitchen abinta tana koyon aiki tare da Iya. Ni kuma na tattara kaya na, na wuce Kd don na je na ga wani hali Aunty take ciki? 💞💞KADUNA💞💞 Cike da tsananin tashin hankali Aafia ta figi mota zuwa asibiti, gudu take shararawa a kan titin nan kamar ba gobe, ga shi kuma dare ne, don lokaci karfe takwas da rabi za ta yi Allah ya tsare, Allah ya kai su asibiti lafiya ba tare da wata matsala ba, tana shiga kuma ta yi sa'a likitoci suka karɓi Aunty hannu bibbiyu, suka shiga da ita A&E (Accident and Emergency) ke nan, sai kai komo Aafia take a bakin kofar, tana ta faman share zufar wahala da ke ta karyo mata ta gefe da gefen kunnenta, sai haki take kamar wadda ta ci uban gudu ta ƙoshi, gabaɗaya ta rasa sukuninta, ta yi da-na-sani har ta gaji. A can gida kuma, Abbi da daddy su ma suna can cikin bedroom nasu, ransu na musu barazanar fita daga jikkunansu, sai fafutuka wajen neman ceton rayukan nasu suke, lokacin guda suka zazzage suka yi wata uwar rama kamar wadanda suka jima cikin ciwo, da ma shi Daddy Jelly akwai shi da dara-daran ido kamar na Jellynsa, ramar da suka yi ya sanya idanun nasa kara fitowa sosai abin gwanin ban tausayi. A takaice dai daddy da Abbi zaune suka kwana, sun daina iya tafiya da kafafunsu, karfinsu duk ya kare, tun suna iya shiga bandaki da kafarsu, har suka dawo shiga da rarrafe, daga karshen a kasa wajen bakin gadajensu suka zube kan gwiwowinsu, suka kwantar da kansu a jikin gadon barcin wahala ya ɗauke su, ba su san abin da ke faruwa a cikin gida ba. Ita ma Aafia kusan a tsaye ta kwana, don ba su ba ta damar ganin Aunty ba, ita kuma ba ta dawo gida ba, a kujerar da ke bakin kofar wajen ta zauna, idan ta jima ta jima sai ta tashi ta fara zarya a wajen tana tunanin ya su Abbi suke? Idan ta gaji da zaryar sai ta koma ta zauna, haka har dare ya tsala, a zaune saman kujerar wajen barcin wahala ya ɗauke ta. A ɓangaren Umaisha kuma, kuka take sosai lokacin da Akil ya fita, bai kula ta ba yana jiyo kukan nata, amma yayi buris saboda ta raina shi sai wani cika yake yana batsewa, fuuu ya fice kamar wata guguwa. Ya je ya shiga motarsa da niyyar ya tafi, sai kuma ya kasa kunna motar, a zahirin gaskiya har cikin dodon kunnensa, yake jiyo sautin kukan nata, ya kasa kunna motar tasa, har cikin ransa yake jin zafin kukan da take, sai dai kuma idan ya tuna cewa ta raina shi, sai ya ji ba zai iya komawa ya rarrashe ta ba, kuma ya kasa tafiya, don yana ji a jikinsa ba zai iya tafiya ya bar ta tana kukan nan ba, zuciyarsa ba zacta juri hakan ba. Shiru ya yi ya kasa gaba ya kasa baya, ya jingina kansa da jikin kofar motar yana tunanin ya zai yi? Daga karshe dai ya yanke shawarar komawa don ya kasa tafiya, buɗe motar ya yi ya fito ya koma cikin gida. Yadda ya bar ta tana zaune tana kuka, haka ya dawo ya same ta, kusa da ita ya zauna tare da ɗan rungumo ta a jikinsa yana faɗin "Is okey!" Kankame sa ta yi ta ci gaba da kukanta, hannu yasa ya ɗago haɓarta yana kallon cikin idonta, "Ya isa haka kukan nan kin ji?" Shigewa cikin kirjinsa da kyau ta yi ta lafe tana sauke ajiyar zuciya, ta daina kukan nata, shiru suka yi yana ɗan shafa bayanta a hankali, ya jingina kansa da jikin kayin gadon yana sauke numfashin a hankali, yana jin matukar son ta na kara ratsawa har cikin kwakwalwar kansa. A ɓangaren Jelly kuwa, sosai Nawid ya ke tunanin yadda zai yi da ita, don a zahirin gaskiya ba zai iya auren Jelly ba, kwata-kwata babu son ta ko kaɗan a ran shi, Jehan yake so, ita kaɗai, bai taɓa jin son wata mace a ransa ba sai Jehan, yana ji a jikinsa cewa, ba zai iya rayuwa da ko wace mace ba bayan ita, har ƴar rama ya yi saboda tunanin mafita. Gefen shi kuma Abbo tunanin yadda zai ɓullo wa lamarin Jelly yake, don a gaskiya ba zai iya haƙura da ita ba, yana bala'i son ta bai san ya zai yi da rayuwarsa ba. Kamar kullun suna zaune saman table ɗin cin abinci, suna cin abinci dare, Nawid, Ummi, Jelly da kuma Abbo, Ummi sai faman cin abincinta take cikin kwanciyar hankali, tana farin ciki Nawid nata ɗa ɗaya tilo zai yi aure, kuma zai auri yarinyar da take bala'i so bayan shi, wato baby. Ita kuma Jelly tana zaune tana ta yagar cinyar kaza hankalinta kwance, ba ta san me duniya take ciki ba, ba ta san abin da ake shirya mata ba, kun san dai Jelly da masifar kaunar nama, idan tana cin naman nan ba ta ji ba kuma ta gani, gabaɗaya barin duniyar mutane take, ko magana kake mata, ba ta amsawa matukar tana gaban nama. Hmm su Jelly manya. "Abbon Nawid da ma ina son mu yi magana a kan auren baby da Nawid." Wani irin dum-dum gaban Nawid ya ba da duka, shi kansa Abbo dukan uku-uku jirginsa ya yi, har wani irin duhu ya gani ya gilma masa ta gaban idonsa, lokaci guda ya rasa nutsuwarsa, sai wani ƴan kame-kame ya fara yi kamar wani marar gaskiya "Abbon Nawid lafiya na ga yanayinka ya canza cikin kankanin lokaci haka?" Cewar Ummi, ta yi maganar cikin kwanciyar hankali, shi ma Nawid ba karamin mamakin ganin Abbonsa ya shiga yanayi marar kyau ya yi ba. Da kyar Abbo ya iya sai ta nutsuwarsa ya ce, "Ina fa lafiya, ai ba lafiya, dole ki ga damuwa a tattare da ni." Zaro ido Ummi ta yi yayin da shi ma Nawid ya bude kunnuwansa yana jiran ya ji me Abbo zai ce? Sai addu'a yake Allah Ya sa Abbo ya ce, wannan haɗin da za a masa shi da jelly, ba ba ya so, bai yarda ba. Cike da tashin hankali Ummi ta ce "Abbon Nawid ka mini bayani mene ne matsalar?" Ta yi maganar tana kara zaro ido cike da tashin hankali, dogon numfashi Abbo ya ja tare da sauƙewa a hankali kafin ya ce, "Ba na son wannan haɗi na Nawid da wannan yarinya baby?" Wani sanyi Nawid ya ji ya ratsa masa daga tafin kafar sa har izuwa tsakiyar kansa, wani murmushi siririn ne ya bayyana a fuskarsa. A ɓangaren Ummi kuwa ƙara zaro ido waje ta yi ta ce, "Abbo mene ne ya sa ba ka son haɗin?" A takaice ya ce, "Saboda tsintaciyar mage ce, ba mu san asalinta ba." _Ni ma na tattare kayana na yi nan wannan dirama ba a nan ba._ Sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode 13-14🌹🌹 A ɓangaren Ummi kuwa ƙara zaro ido waje ta yi ta ce "Abbo mene ne ya sa ba ka son haɗin?" A takaice ya ce "Saboda tsintaciyar mage ce, ba mu san asalinta ba." Ayya Jelly baiwar Allah tana can duniyar kaza ba ta tare da su, ba ta san wainar da ake toyawa ba. "A'a Abbon Nawid kada mu yi haka da kai, idan muka ce don ba ta da asali ba za mu ba ta ɗanmu ba, to waye kake tun nin zai aure ta? Mu da muka san komai ma mun ki yarda, to waye kake tunani zai so ta, kuma ma ai yanzu mun zama mu ne asalinta iyayenta komai nata." Ɗaure fuska sosai Abbo ya yi kamar da gaske yana son hana Nawid ne don baby ba ta da asali, alhalin kuma kansa yake gyarawa hanya, yana son ya rushe maganar Nawid ne don ya gina tasa, wannan ita ce cakwakiya. "Ummin Nawid na gama magana, ɗana yaro ne mai asali, don haka ba zai auri wadda ba ta da asali ba." Ya kai karshen maganar tare da cire hannunsa daga abincin ya miƙe ya bar wajen, cike da ɓacin rai a zahiri, amma cikin ransa kuma farinciki kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha. Sosai Ummi ta ji babu daɗi, kuma ta kudure a ranta sai Nawid ya auri Jelly don ita ce zaɓinta, ba ta son Nawid da kowace mace fa ce Jelly, ko me zai faru sai dai ya faru, ɓera ya ɓarar da garin kyanwa. Nawid, Jelly zai aura. Rai a matukar ɓace ita ma ta miƙe ta nufi bedroom nata, yau ranta ya ɓaci sosai ba za ta je wajen Abbo ɗin ba, kwanciya ta yi a ɗakinta. Shi ma Nawid ganin iyayen nasa sun tafi ya sa ya miƙe ya nufi ɗakinsa, ransa fes sai wani murmushi yake saki, Abbonsa ya rushe maganar aurensa da mahaukaciya a cewarsa. Ita kuwa Jelly sai faman cin naman kaza take, kwatakwata ma ba ta san me suke tattaunawa a kanta ba, tana dai jin zancen nasu sama sama haka yana bi ta gefen kunnenta. Sai da ta cinye kaza guda tas, ko kaɗan ba ta rage ba, kamar wata mai aljanun cin nama. Bayan ta kammala sai ta miƙe ta wuce bedroom nata tana lashe baki kamar wata tsohuwar mayya. Tana shiga ta haye saman gadonta tana sauke ajiyar zuciya, yau ko kayan barci ba ta samu sawa ba, don da ma Ummi ke saka mata kayan barci yau kuma ran Ummi a ɓace yake. Abbo da Ummi ransu a ɓace barci ya yi awon gaba da su, Nawid kuwa farinciki cike fal ransa ya yi barci. A gefen ita ma Jelly da yake ba ta san me aka kulla ba, sai ta yi barcinta cikin kwanciyar hankali. A ɓangaren Umaisha kuma, bayan sun ɗan yi shiru na yan mintuna ne, Umaisha ta katse musu shirun da cewa, "Yaya Akil don Allah gobe ka ɗauko Aunty Afi ta zo ta mana kwana biyu ka ji?" Shafa kanta ya yi kafin ya ce "To, na ji kuma zan je na ɗauko ta." Wani daɗi Umaisha ta ji ya rufe ta, da ƙarfi ta matse shi a jikinta, tana murna. "Za ki ɓalla ni ko?" Ya tambaya yana tsare ta da ido, dariya cikin hawaye ta yi tana faɗin, "Kai yaya Akil ni na isa na ɓalla ka ne?" Shiru ya mata don shi ma ba mai son yawan Magana ba ne. Haka suka yi shiru, ta yi luf a jikinsa har barci ya ɗauke ta, shi kuma sai faman kallon fuskarta yake yi. Mu koma wajen Rimsha. Bayan sun gama girki ita da Iya, ta fito ta shige cikin bandaki ta sake yin wanka abinta, don Rimsha akwai ta da bala'i son tsafta sosai, ba ta son datti ko kaɗan. Bayan ta yi wanka ta sake shiryawa cikin wata doguwar riga ta Kausar, ta fito falo, nan ta samu Kausar da Ayla suna cin abinci, amma kowa kwanonsa daban, ma'ana daban-daban Iya ta saka musu abincin. Kusa da su ta zo ta zauna, Ayla ce ta jawo wani kwano da ke rufe a gefen su ta miƙa mata tana faɗin, "Ga naki abincin." Karɓa ta yi ta fara ci tana jin daɗi yau ta iya yadda ake yin miyar Steew da shinkafa. Suna tsaka da cin abincin ruwan sama mai karfin gaske ya ɓarke, babu hadari babu komai suka ji zubar ruwa kamar da bakin kwarya, mamaki ne ya kama Ayla. Cike da mamaki ta ce, "Da ma wai har yanzu lokacin damina muke ne?" Kausar na fama da kokarin gutsirar ganda ta ce, "E mana, ni ma dai abin ya ba ni mamaki, rabon da na ga ruwan sama yau wajen sati biyu kenan? Tun da muka shiga Daular Mutuwa, kuma da muka fito ma ba a yi ruwa ba har muka iso nan." Juyawa Ayla ta yi tana kokarin yi wa Rimsha magana, sai suka ga, Rimsha ta a jiye kwanon abinci ta miƙe da gudu ta yi waje. Cikin sauri Ayla ta ajiye cokalin hannunta, ta miƙe ta bi bayanta, don a tunaninta wani abin ne Rimsha ta ji a waje, shi ne ta je leƙowa. Rimsha na fitowa ta shige cikin ruwan saman nan, tana dariya tana juyi a ciki kamar kifi, mamaki ya hana Ayla magana, ta tsaya kawai daga bakin kofa ta zuba wa Rimsha ido. Ita kam Kausar da ma idan tana cin abinci ba ta taɓa yarda wani abu ya tayar da ita, ba ta tashi har sai ta kai aya a cin abincin da take, sai ta ga karshen kwano take samun nutsuwa, don haka yanzu ma ba ta taso ba, tana zaune tana cin abincinta kawai. Wani nishaɗi Rimsha ke ji yana ratsata, sai juyi take cikin ruwan saman nan tana dariya, ga ruwan zuba yake sosai kamar da bakin kwarya, ga shi babu iska. Tun tana karama take bala'i son ruwa, ko lokacin da suke gida tare da daddy in dai ba cikin dare aka yi ruwan sama ba, in da rana ne sai ta shiga, tun daddy na hana ta har ya hakura ya dai'na. "Rimsha kina son ruwan sanyin nan ya saki mura ko?" Daga bayanta ta ji wannan zazzakar murya mai kama da tata, a sukwane ta juya, Malika ce ke tsaye ita ma cikin ruwan tana ta murmushi dimple nata irin na Rimsha na lotsawa. Yar dariya Rimsha ta yi kafin ta ce "Malika me kika zo yi a nan? Ko dai ke ma yar nan garin ce?" Matsowa kusa da ita Malika ta yi tana ta murmushi ta ce, "A'a ni ba yar nan ba ce, na zo wucewa ne na gan ki kina wasa cikin ruwa na ce bari na zo mu gaisa" Kara faɗaɗa murmushi Rimsha ta yi tana faɗin "Gaskiya kina da kirki sosai, ina godiya." "Duk kirki na ai ban kai ki ba Rimsha" Cewar Malika, shiru Rimsha ta yi tana tunanin wani kirki ita kuma ta yi da har Malika take ce wa tana da kirki. "Rimsha ki fita a cikin ruwan nan fa, kada mura ta kama ki". Cewar Malika, ta yi maganar tana kara matsowa kusa da ita, "Malika to ai ke ma kin shiga cikin ruwan, ke ma ki fita kada mura ta kama ki". Jan dogon hanchinta Malika ta yi, kafin ta ce, "Ni kam mura ba za ta kama ni ba, don asalina ma a ruwa nake rayuwa, ke dai ki fita". Rimsha za ta yi magana Ayla dake tsaye a bakin kofa ta cikin falo tana ganin ta ta ce, "Rimsha kan ki ɗaya kuwa?" Juyowa Rimsha ta yi ta kalle ta tana faɗin, "Ban gane kai na ɗaya ba, me na yi kuma?" Ta yi maganar tana zaro dara-daran idanunta alamar mamaki, "Da wa kike magana to?" Cewar Ayla. A sukawane Rimsha ta sake dawo da kallon ta kan Malika dake tsaye ta goya hannu a kirjinta sai murmushi take tana kallon su, juyawa ta yi ta sake kallon Ayla. A ɗan tsorace ta ce, "Ayla ban gane da wa nake magana ba? Ni da Malika ce mana". Ɗan sako kai waje Ayla ta yi ta leƙo da kyau ko za ta ga wani ko wata da ke magana da Rimsha, amma sai ta ga wayam ba kowa. A kule ta ce "Wace ce kuma Malika? A ina kuma take? Don ni ban ga kowa a nan ba." Zaro ido sosai Rimsha ta yi ta ɗan ja baya daga kusa da Malika, ta matsa tana faɗin, "Ga ta nan ki gan ta." Zaro ido Ayla ta yi da nufin ya yi tozali da wacce ake nuna mata din amma babu abin da ta gani. "Ki daina wahalar mini da kanki Rimsha Ayla ba za ta gan ni ba". Cewar Malika, juyo da kallon ta kan Malika ta yi, kirjinta sai dukan uku-uku yake, ta tsorata sosai, taya za a yi a ce ita tana kallon Malika, amma Ayla ba ta kallon ta. "Me yasa kike tunani Rimsha?" Malika ce ta katse mata tunanin da take da tambayar ta. Yar firgita ta yi kafin ta ce, "Dole zan yi tunani mana Malika." Tsare ta da ido irin nata Malika ta yi tana faɗin "To tunanin me kike yi?" Ayla dai ta ga ikon Allah, don ba ta ganin Malika sai dai ta ga Rimsha nata surutu ita kaɗai kuma abin mamaki ba ta iya jiyo me Rimsha ke faɗa, sai dai bakinta kawai take gani yana motsawa. Babban magana wannan shine ruɗani! "Malika me yasa Ayla ba ta ganin ki?". Cewar Rimsha, ta yi maganar a matukar tsorace, "Kina son ta gan ni ne?" Malika ta tambaya tana sanya hannunta a saman tsakiyar kan Rimsha, don ta tare mata ruwan saman dake dukan tsakiyar maɗigarta, don ruwan zuba yake sosai kamar da bakin kwarya. "Eh mana Malika yana da kyau ai kowa ma ya gan ki, bai kamata ki ɓuya ba sa ganin ki ba, ai sai su yi tunanin da aljana nake magana." girgiza kai Malika ta yi tana faɗin "Yaro, yaro ne, amma dai ke yarinya ce mai zuciyar manya, ki ce Ayla ta kalli cikin ɗaki". Kananun shekarun Rimsha ya hana ta gane in da Malika ta dosa, don haka sai ta juya ta ce, "Ayla ki kalli cikin ɗaki." Ayla kuma ta yi zaton wani abu Rimsha ke nuna mata a cikin ɗakin don haka sai ta juya, ta kai kallonta cikin ɗakin, kafin ta juyo Malika ta bayyana yadda kowa zai iya ganin ta Ayla ganin babu komai a cikin ɗakin yasa ta juyo tana faɗin, "Rimsha me zan gani a cikin ɗakin? Don na juya ban ga komai... Ba ta ƙarasa maganar ba idon ta ya sauka a kan Malika, a zabure ta ce, "Wace wanna mai bala'in kama da ke ɗin kuma Rimsha?" Juyowa Rimsha ta yi tana kallon Ayla kafin ta yi magana, Ayla ta yanke jiki ta faɗi kasa sumammiya, a sukwane ta dawo da kallon ta kan Malika, sai ta ga wayam babu Malika a wajen, Malika ta tafi, cike da tsoro ta fara waigawa ko za ta ga Malika, amma babu ita babu alamarta, da gudu ta kwasa ta bar cikin ruwan ta nufi wajen Ayla, in da take kwance magashiyan a kasa. Kanta ta yi ta fara jijjiga ta tana kiran sunanta, hakan ya yi sanadiyar jawo hankalin Iya da kuma Kausar. Da sauri suka karaso wajen a tare, iya tana faɗin "Lafiya Rimsha?" Ganin Ayla kwance magashiyan a kasa yasa Iya ta yi kanta tana kiran sunanta. Ruwan saman dake zuba daga jikin Rimsha shi ya zubar wa Ayla a fuskarta zuwa wuya. Hakan yasa ta farfaɗo daga suman da ta yi. Har suna haɗa baki wajen cewa "Ayla lafiya?" Shiru ta ɗan yi kafin ta ce, "Babu komai." Don ta mance komai, a zahirin gaskiya abin da ya sanya ta suma shi ne ta ga lokacin da Malika ta ɓace, kuma kafin ta ɓace sai da ta ɗora hannunta a kan Rimsha dana sakin cool murmushi sannan ta ɓace, lokacin ita kuma Rimsha tana kallon Ayla ɗin abin ya faru. Wannan shi yasa Ayla ta suma, da ta farfaɗo kuma ta kasa faɗa musu me ta gani yasa har ta suma. Haka ta miƙe sai tambayar ta suke amma ta ce ba ta sani ba, ita ba ta san komai ba, haka suka kyale ta, Iya da Kausar suka koma cikin gida tare da Ayla, ita kuma Rimsha tsayuwa ta yi a wajen tana tunanin ina Malika ta tafi lokacin guda haka, ko alamarta babu, sannan me ya sanya Ayla suma? Sosai ta shiga duniyar tunanin sai dai kuma babu wata amsa da ta samu. A hankali ta sako kafarta ba ta daddara ba ta sake komawa cikin ruwan saman ta ci gaba da wankanta, don ita da ruwan sama ba a raba su. Sai juyi take, wannan bakin gashin nan nata rabi ya kwanto mata a fuskarta rabi kuma ya kwata har gadon bayanta, sai sheki yake gwanin ban sha'awa. Ruwan saman ya kai awa ɗaya yana zuba kamar da bakin kwarya, haka Rimsha ta tsaya a cikin ruwan tana wanka har sai da ruwan ya ɗauke. Ba yadda Ayla da Iya ba su yi da ita a kan ta fita cikin ruwan ba, amma taki, har sai da ruwa ya ɗauke sannan ta koma cikin falo, sai ɗigar ruwa take. Tana shiga falo ta wuce ɗakin Kausar wanda yanzu ya zama ɗakinsu. Canza kaya ta yi zuwa riga T-shirt da wani wandon palazo jeans na Kausar, ta yi kyau sosai, don wankan da ta yi a cikin ruwan nan ba karamin fita ta yi ba, har wani sheƙi fatarta take sosai ta yi kyau kamar ita ta yi kanta. Sai bayan da ta gama shiri ne, ta dawo falo ta ɗauki abincinta, ta ci gaba da ci, tana yi tana murmushi tana shafa kirjinta wajen zanen sunan GAR kamar ba lafiya ba. Bayan sun kammala cin abincin ne suka zauna shiru kowa da abin da yake tunani. Can kamar wadda aka tsikara Rimsha ta miƙe tana faɗin, "Kausar bari na tambayo Iya ko tana da waya, in saka lambar mamana ko sister na in ƙira in ji ko tana shiga." To, kawai Kausar ta ce mata, wucewa Rimsha ta yi zuwa bedroom na Iya. A bakin kofa ta tsaya ta yi sallama, daga cikin ɗakin Iya ta amsa tare da ba ta izinin shigowa. Ciki Rimsha ta shiga tana faɗin "Sannu da hutawa Iya" da fara'a Iya ta amsa mata tana daga kwance saman gadon ta. Daga ɗan gefe ta tsaya cikin girmamawa ta ce "Iya dan Allah idan kina da waya ki taimaka min da ita zan saka number mamana ko sister na ne na gwada kira." Ba tare da Iya ta sake yin wata magana ba, ta ciro babban wayarta kirar Tecno ta miƙa mata, cikin sauri Rimsha ta karɓa wayar, jikinta har wani kerma yake wajen karɓan wayar. Cike da zumuɗi ta fara gwada number mum. Sai da kirjin ta ya ba da wani dum-dum lokacin da kunnuwan ta suka ji layin mum a kashe. Sake gwadawa ta yi, nan ma a kashe, kamar za ta yi kuka ta sanya number Jehan, shi ma a rufe, nata number ta sa ta gwada ƙira, shi ma a kashe, turo ɗan bakin nan nata tayi kafin ta gwada number daddynta duk da ta san tasa wayar a kashe take, saboda tun kafin ta bar gida, numbersa ba ta shiga. Kamar a mafarki ta ji number daddy ta shiga, cikin sauri ta ciro wayar daga kunnanta don ta gani shin da gaske numbersa ta sanya da kyau, ko kuma akwai in da ta yi kuskure. Tabbas da gaske ne babu wani kuskure number daddy ne. Sai dai wayar ta yi ringing har ta katse ba a ɗaga ba, Iya dai tana daga kwance ta zuba mata ido. Sake kira na biyu tayi, nan ma ba'a ɗaga ba, sai a karo na uku ne, aka ɗaga. Cike da zumuɗi ta ce, "Hello daddy." Wani murya ta ji wanda da alama Hausa bai ishi mai wannan murya ba, "Hello waye ne?" Mai wannan murya ya tambaya, sake ciro wayar daga kunnenta ta yi don ta sake tabbatarwa da kanta number daddy ne. Tabbas numbersa ne, sake mai da wayar kunnenta ta yi ta ce "Ina wuni?" Bai amsa gaisuwar ba sai cewa ya yi "Waye ne wai?" A ƙule ta ce "Kai ba musulmi ba ne?" Shi ma da alama ya ji haushin maganar nata, da ɗan karfi ya ce "Ban sani ba, ki kira ni kuma kina neman gaya min magana!" Ɗaure fuska ta yi ƙamar tana gaban shi ta ce "Ka bawa mai wayar wayarsa, ina son yin magana da shi" "Ke wai waye ke ne tukun nan ma?" Kamar za ta masa da faɗa, sai kuma ta tuna cewa daddynta take nema, dan haka sai ta ce "Dan Allah ka bawa mai wayar wayarsa, ni yarsa ce, magana na ke son na yi da shi ka taimaka" "Ke ni bani da wata ƴa, wannan waya kuma wayanane, dan haka kada ki sake kira" ranta ya ɓaci sosai, cike da jin haushi ta ce "Kai malam idan baka bawa mai waya wayar sa ba, wlh sai na saka an ɗaure ka dan kaga ina bin ka a hankali ko?" tofa ba karya jinin dake gudu a jikin Jehan shike gudu a jikin Rimsha, kada ku manta da hakan. Jin ta ce za ta saka a ɗaure sa sai ya yi kasa da murya ya ce "Ni ban san mai wayar nan ba, wata ɗaya da ya wuce ne, na tsinci wayar kusa da wani gawa, na dawo daga gona zan koma gida lokacin, dan Allah ki rufamin asiri wlh ban san komai ba, wasu ne suka kashe shi". Saboda tsabar shiga tashin hankali ya ta kasa tsayuwa a kan kafafun ta, zubewa ƙasa ta yi, ta zauna zaman dirshan, nan take hawaye masu bala'i zafi suka fara zarya a kan kuma tunta, cikin sauri Iya ta sauƙo kasa daga saman gadon, ganin Rimsha na hawaye ta tada mata da hankali. "Bawan Allah a wani gari ka ke?" Rimsha ta faɗa cikin kuka, "A nan agadas nake" sakin wayar Rimsha ta yi, wayar ya faɗi kasa, kuka ta sa mai tsuma zuciyar mai sauraro, yanzu da man da gaske ne daddyna ya rasu, ta tambayi kanta, tambayar da ba ta da amsar shi. Sosai Iya ta rinƙa bata baki tana bata hakuri tare sa tuna mata da yarda da kaddara. Rimsha tasha kuka har ta koshi, da kyar iya ta iya samo kan ta, har tayi shiru. Bayan tayi shiru ne ta miƙe jiki ba kwari ta koma ɗakin Kausar dan kanta dake mata barazanar fashewa saboda tsananin ciwo tana son ta kwanta ta huta. Kausar da Ayla suna falo ba su san meke faruwa ba. Tana shiga ɗakin Kausar ta haye gado ta kwanta tana mai da numfashi tare da jan hanci. Tunanin irin rayuwar da suka yi da daddyn su ta fara yi, tana yi wasu siraran hawaye na biyo ta gefen idon ta zuwa kunnen ta. Allah sarki rayuwa kenan, yau gare ka gobe ga ɗan uwanka. To masu karatu mu leƙo Washington DC wata kila kafin mu dawo Rimsha ta yi shiru. 💞💞Washington DC💞💞 Romeo Zaune yake saman katafaren lallausan bed nasa, jikinsa na sanye da farin short da farar singlet, hakan ya bayyanar da kyakkyawar kakkarfar surar jikinsa, irin na jarumai sadaukan yaki. Ya ɗaure dark black curly hairsa a bayansa ya bar wannan guntu na gaban goshinsa mai kara fito da kyansa. Ya zubawa system da ke gaban sa wayan nan dara daran blue eyes ɗin nasa, ya yi shiru ya dukufa aiki yake yi sosai a nutse, sai faman cizan lallausan red lips nasa yake, har wani ja sosai lips ɗin nasa ke karawa saboda ciza wa da yake yi. "What CIA?!" Ya furta da ɗan karfi, kara zaro dara daran idon nasa ya yi, har sai da suka kara haske saboda zaro su da ya yi, kara cizan lips ɗin nasa ya yi da karfi, alamar abun da yake gani a cikin system ɗin ya ɗan ɗaga ma shi hankali, kuma ya bashi mamaki. Wayarsa dake gefen sa ne ya fara ruri yana neman ɗauki. Sai da wayar ya kusa katsewa, sannan slowly ya mai da idon sa izuwa kan wayar, Dr Tyrion, shi ne sunan da ya bayyana a kan screen ɗin wayar, shiru ya ɗan yi bai ɗauka kiran ba, har wayar ta katse. Kira na biyu ne ya sake shigowa, alamar Dr fa a matse yake, shiru lion ya yi kamar mai tunani. Kiran na gab da yanke wa ne, ya sa hannun sa a nitse ya ɗauki wayar tare da yin picking call ɗin, tun bai yi magana ba ya jiyo sautin kukan Michael ta cikin wayar, katse kiran ya yi ba tare da ya yi magana ba, ya miƙe cikin sauri ba tare da ya kashe system nasa ba, ya nufi toilet. A nutse ya yi wanka, sannan ya fito ya tsaya a gaban mirror, kamar yadda ya saba haka ya tsaya ya rinƙa shafe dark black curly hair nan nasa da mayukansa masu kyau da tsada. Bayan ya gama da kai ne, ya shafe soft skin nasa da wadannan mayukan nasa masu bala'in kamshi da tsada tare da feshe jikinsa da wannan haɗaɗiyar perfume ɗin nan nasa mai bala'i fitinannen kamshi, sannan ya wuce dressing room nasa, sai tashin daddaɗar fitinannen kamshin yake. Bayan wasu yan mintoci ya fito sanye da wandon jeans fari tas, da Turtle High T-shirt, kasancewar rigar ta kama shi sosai ta bi jikinsa, hakan ya bayyanar da kakkarfar surar jikinsa, damtsen hannun nan nasa kamar za su fashe saboda karfe da yake ɗagawa, ga breast nasa ɓul-ɓul, sai tashin kamshin yake, ya ɗauki wayarsa ya fito ya bar system nasa. Kodayaushe motoncinsa a shirye suke, duk lokacin da ya fito don su tafi wani waje, to tafiya kawai za su yi, yanzu ma yana fitowa kawai buɗe masa kofar motarsa wani jibgegen Baturen soja ya yi, fari ƙal da shi. Duka sojojin Romeo farare ne kal, masu kirar cikakkun mazaje, kallo ɗaya zaka musu, kasan sun shirya shiga fillin daga a ko wani lokaci, fuskokin suma kawai abun tsoro ne, ganin fuskarsu takan sa hantar manyan maza ya kaɗa, amma a haka, suna mutuwar tsoron fusataccen fuskar Romeo wato lion, duk da cewa kullun a kame suke suna nutse, idan suka gan shi ya fito, har wani damke kakin jikin su suke yi saboda kamewa da suke kara yi idan suka gan shi. A jere motoncin nasu suka tashi suka miki titin zuwa bakin babban gate, jibga jibgan jaruman security da ke bakin gate ɗin ne, suka wangale musu katafaren gate ɗin gidan, amma kafin su isa babban gate sai da gate na biyu ya yi checking na motocin da wannan na'uran, sannan ya kira numbobin motocin gaba ɗaya ya shigar cikin babban na'uran Romeo dake ɗakin bincike dan already na'urorin a haɗe suke da juna tura sako kawai suke. Da gudun gaske suka danna hancin motocin waje tare da sakin jiniya tamkar wayan da za su tafi filin yaƙi, kai tsaye hospital suka nufa. Duk wasu abin hawa dake kan hanya, tun jerin motoncin su Romeo bai iso wajen su ba, suke basu hanya dan jin jiniyar sun san jerin motoncin The General of the Army ne. Suna shiga asibitin suna wuce parking space, kasancewar asibitin yana da girma sosai ya ɗauke gabaɗaya motoncinsu. Suna parking a guje jibga-jibgan sojojin nan suka diro kasa daga saman bayan motoncinsu, ɗaya daga cikin sune ya buɗe kofar motar lion suka tsaya a bakin kofar motar suna jiran fitowar sa. Yana sako kafar sa ɗaya waje, a sukawane suka ɗaga hannayen su dake sanye cikin black hand gloves su ka sara masa, ba su sauƙe hannayen su ba, har sai da ya fito ya nufi cikin hospital ɗin. Sai ya wuce su sannan suke sauke hannayen nasu. Sojoji shida madaka karti ne suka take masa baya zuwa ciki. Kai tsaye ɗakin da Michael ke kwance wato ɗaki na musamman ya nufa. Tun daga nesa yake ji yo kukan Michael, da ma kuma ya san za a yi hakan, dan ya san halin Michael da ragon ta. Kwance Michael yake saman bed nasa, na majinyata sai kuka yake, hawaye sharaɓa sharaɓa a fuskarsa kamar ƙaramin yaro, ga shi idon nasa a runtse. Gaban gadon lion ya je ya tsaya tare da riƙo hannun Michael ɗin, Michael jin an kama hannun sane yasa ya yi saurin waro brown eyes nasa. Ganin Romeo ne yasa ya kara sautin kukan nasa, yana ƙara kankame hannun Romeo, kallon jinin da aka kara masa Romeo ya yi kafin ya dawo da kallon sa kan fuskar Michael ɗin. Gently in a cool voice ya ce "Michael whapped? Why are you crying?" Yun kurin tashi Michael ya yi, cikin sauri Romeo ya mai da shi yana girgiza masa kai alamar kada ya yi yunkurin tashi, kara sautin kukan sa ya yi. Shafa lallausan dark brown hair sa Romeo ya fara yi alamar rarrashi, cikin kuka da shagwaɓaɓɓiyar murya ya ce "My lion zafi nake ji, jiki na ciwo yake min, ji nake kamar zan mutu, wayyo ka taimake ni". Ikon Allah shi da ya je zai kashe kansa, an ceto rayuwarsa da kyar amma yake kukan zai mutu zafi yake ji, a taimake sa, lallai Michael tabbas ba laifin ka bane, laifin kwakwalwar kane da take nuna maka komai daidai ne. Gently cike da kaunar Triplets nasa lion ya ce "Is okey My Tiger zai dai na yi maka zafi ka ji, ka yi shiru, just for a while minutes zafin zai tafi." Kuka sosai Michael yake yi kamar ba namiji ba, har da wani shassheka tare da jan hanci. Romeo baya son ganin kukan nasa dan haka sai ya juyo ya ce da Dr Tyrion ya yi masa alluran barci. Jin lion ya ce a masa allura yasa ya kara sautin kukan nasa, dama kuma already kun san halin sa da rashin son allura. Da kyar ya yarda aka ma shi allura, nan ma sai da lion ya karɓi alluran da kansa ya masa. Bayan an kammala komai, Michael ya yi barci ne, Dr T wato Dr Tyrion ya dubi lion fuska ɗauke da murmushi ya fara magana, "Congratulations Sir." Zuba masa dara-daran kyawawan idanunnan nasa ya yi ba tare da ya yi magana ba. Ci gaba da magana Dr ya yi "Abin da muƙa ɗauki tsawon shekaru muna fafutuka a kan shi, yau mun yi nasaran samun bakin zaren matsalar." Still Romeo bai yi magana ba, ya dai tsare Dr da ido yana jiran ya ji karshen maganar kawai. "Yau mun yi nasaran samun bakin zaren matsalar Michael, kuma muna sa ran nan da yan kwana ki zuwa watanni zai iya samun sauƙi kwakwalwan sa za ta koma daidai, zai daina yin abubuwa kamar yaro, zai zama cikakken mutun, kuma duka hakan ta farune sakamon buguwa da kansa ya yi a sanadiyar accident da ya sa mu, amma fa a yan kwana kin nan sai kun kara hakuri da shi, dan zai birkice mu ku fiye da a baya, amma daga nan zamu yi nasara". Jin abin lion ya ke tamkar a mafarki, dan sun kwashe shekaru suna neman wa Michael magani, sun je hospital kala-kala, amma ba su yi nasara ba, dan ko wani likita cewa yake a haka a ka haife shi, dan haka babu wani magani, sun tambayi daddy sun lokacin da suka yi wayo, menene asalin abun da ya faru da Michael daddy ya ki faɗa musu sai dai ya ce musu shima bai sani ba. To yau Allah ya yi Michael zai samu sauki, farinciki ya hana lion magana,. Kasan cewar shi baka taɓa gane farincikin sa ko bakin cikin sa, hakan yasa ba wanda ya gane cewa lion ya yi farinciki da samun saukin Michael. Yau saboda murna lion ya jima sosai a hospital ɗin kafin ya koma gida. Yana zuwa gida, ya isko daddy a falo, nan fa daddy ya tsayar da shi, tare da sa masa kuka a kan ya har yanzu Michael bai dawo daga white house ba, kuma yana kiran layin James baya shiga. Da kyar lion ya samu ya lallaɓa daddy tare da yi masa alkawarin gobe Michael zai dawo, da kyar daddy ya yarda sannan ya wuce bedroom nasa. Kai tsaye bedroom na James lion ya wuce, dan ya je ya yi wasu binciken na shi. Ya jima a ɗakin James yana yan bincike-binciken shi, kafin nan ya fito ya koma part nasa. A gaban mirrorsa ya tsaya yana kallon fusataccen fuskarsa, sosai ya zubawa kansa ido kamar mai son gano wani abun, a hankali ya kai hannun sa yana shafa kyakkyawan fuskar sa, tunani yake sosai a kan James, tabbas James na bukatar taimako. Kamar wanda a ka tsikara ya ciro wayar sa daga aljihun sa tare da fitowa da sauri ya shige ɗakin binciken sa. Ɗaki ne mai girman gaske, kasan ɗaki wani irin tiles ne mai kamar glass kana iya ganin fuskar ka jikin tiles ɗin, ga shi tsab tiles ɗin yake kamar kafa bai taɓa takawa ba. Bangon jikin ɗakin ta gabas, ma'ana ta wajen mahangar garin, glass ne a wajen maimakon gini kana tsaye daga cikin kana hangen cikin birnin Washington DC. Gaba ɗaya cikin ɗakin kewaye yake da haɗaɗɗun drawers masu kyau, wanda a ka ɗaura Manya-manyan na'urorin da kuma manya-manyan desktop computer a kansu, wadanda da ka gan su ka san ba aikin wasa ake da su ba, ga kuma wasu haɗaɗun chairs masu kyau da tsada, a kalla chairs ɗin nan za su kai 20 a cikin ɗakin, dan gaban kowani na'ura ko kuma desktop computer akoi wannan kyakkyawan chair ɗin a wajen. Komai na dakin a share a gyare tsaf kamar sababbin kaya a ka zuba, su kan su computers ɗin ba za ka taɓa cewa hannu ya taɓa taɓa su ba, saboda hasken da suke da shi ba datti ko kaɗan, wani daddaɗar kamshin tare da sanyin AC ke tashi a ɗakin wadda zai baka tabbacin mamallakin ɗakin nan mutunne mai mugun bala'i tsabta tare da son kamshi, dan komai nasa wani hadaɗɗe. Kamshi yake yi. Um Masha Allah lion na mu duniyar tsabta da kamshi, kai dai in dai kamshi da tsabta ne to kai ne number 1 amma kar aje ta ɓangaren tausayi da horar da masu laifi dan a komai kai number 1 ne ba'a magana!!. Saman wani haɗaɗen chair lion ya zauna, da kaga chair ka san na musamman ne, kamar yadda mamallakin ta yake na musamman, ɗaya tamkar da billion. Zama ya yi yana fuskantar wani makekiyar desktop computer mai bala'i kyau da tsada, mai girma sosai. Kunna computer ya yi, ya sanya hannun sa a kan screen ɗinta ya fara aiki. Number James ya shiga cikin computer dan ya binciko a daidai ina aka soke layin James, kuma bayan an soke layin ya aka yi da ita. Sosai ya nutsa cikin bincike ba ji ba gani, aiki yake tukuru babu kama hannun yaro. Duk da daddaɗar sanyin AC dake tashi a ɗakin, hakan bai hana zufa karyo masa daga gefe da gefen kunnensa ba, lokaci guda ya birkice kamar ba shi ba. Zaro idon nan nasa ya yi yana kallon cikin computer, kamar wanda alluran sojansa ta motsa, nan take idon nan nasa suka canza launi zuwa ja, wasu siraran jijiyo ne suka bayyana daga goshinsa har zuwa wuyansa, sai huci yake fitarwa. Ya jima a haka kafin nan ya furzar da iska mai bala'in zafi daga bakinsa tare da jan dogon numfashi ya sauƙe a hankali. Ci gaba da bincikensa ya yi na tsawon lokaci, duk yanayinsa ya canza, kamar ba shi ba, ya fito a asalin lion ɗinsa, duk wanda ya yi gigin tinkarar shi a yanzu za a iya ce masa mai kararren kwana, don halin da yake ciki a yanzu tsaf zai iya hallaka duk wanda ya tinkare shi, ganin shi a yanayin da yake ciki yanzu zai iya sanya mutun ya mutu ba tare da shiri ba. Dakatawa ya yi da binciken nasa, ya miƙe a zafafe ya nufi bangrensa. Yana shiga bedroom nasa ya wuce toilet. Ruwa mai bala'in sanyi ya zuba wa kansa, don ya samu sauƙi, ya samu zuciyarsa ta ɗan sauka, ya huce, saboda ba ya son ya yi aiki cikin fishi da ɓacin rai, shi yasa ya yi hakan. Bayan ya zuba ruwa ya fito ne, ya wuce dressing room ya shirya cikin pajama launin fara, sannan ya dawo saman lallausan gadonsa ya kwanta, ya jawo system nasa zai kunna hasken screen ɗin, sai kuma ya fasa, saboda har lokacin zuciyarsa na masa zafi, ba ya son yin aiki cikin ɓacin rai, don haka sai ya mayar da system ɗin saman bedside drawer ya kwanta tare da lumshe dara-daran idonsa yana tunanin James har barci ya yi awon gaba da shi. After some day's, a yanzu Musharraf ya samu lafiya sosai, don yana iya taka kafarsa a hankali ya fito falon kasa, haka zalika shi ma, Michael ya samu sauƙin ciwokan da ya ji a sanadiyar hatsarin da ya yi, sai dai matsalar kwakwalwarsa ce, har yanzu da saura. _Ni ma na tattare kayana na yi nan wannan dirama ba a nan ba._ Sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode 15-16🌹🌹 After some day's, a yanzu Musharraf ya samu lafiya sosai, don yana iya taka kafarsa a hankali ya fito falon kasa, haka zalika shi ma Michael, ya samu sauƙin ciwukan da ya ji a sanadiyar accident ɗin da ya yi, sai dai matsalar kwakwalwarsa ce, har yanzu da saura ba ta warke ba. Yau tun safe sosai helicopters ke shawagi a sararin samaniya, daga cikin Washington DC zuwa wajenta, kamar masu duba wani abin. Tun da daddy ya ji shawaginsu ya yi yawa ya san Romeo zai bar kasar ke nan, don da ma in dai ba fitar sirri zai yi ba kafin ya fita kasar sai an tashi helicopters sun yi ta kewaye cikin Washington DC, don tabbatar da tsaro, sai sun duba ko'ina. Idan sun tabbatar normal sannan private jet ɗin Romeo ya ɗaga, amma kafin ya ɗaga sai manya-manyan jiragen sojoji na kota-kwana biyu sun yi gaba, sannan nasa jet ɗin ya bi bayansu, sai wasu jiragen biyu su saka jet ɗinsa a tsakiya sai jirgin yaki ɗaya a bayan jet ɗin, don tabbatar da sun ba wa The General Of The Army kuma jika ga His excellency tsaro mai kyau, don ran Romeo daidai yake da ran zaratan sojoji 100 a cewarsu, don za a tara sojoji 100 ba za su iya aikin da shi kaɗai yake yi ba, kasancewar shi ba komai yake saka wa karfin dantse ba, akwai shi da aiki da kwakwalwa kamar agogo, manyan kasashe na duniya idan abin ya shige musu duhu sai sun nemi taimako daga wajensa, sannan kuma His Excellency yana bala'in kaunar sa fiye da tunanin mai tunani, duk cikin jikokinsa ya fi son lion, daga shi sai Michael yana matukar son su sosai. Ran Romeo babban abu ne mai matukar mahimmanci ba ga iya USA ba, har wajenta. Matukar Romeo zai fita Washington DC to fa sai an bincike ko'ina, har kasar da zai je, kafin ya dira cikin kasar sai helicopters sun tashi a cikin kasar ma, sun duba ko'ina da kyau. Cikin taku irin na jaruman maza masu jini a jika, ya fito daga ɓangarensa, jikinsa na sanye da blue jeans mai bala'in kyau, sai Round neck T-shirt black color mai ratsin blue, a saman kayan nasa ya ɗora wannan jacket ɗin nasu, wato Puffer Jacket, ita ma black color, kalar rigarsa, kyawawan fararen kafafunsa na sanye da Hermes Birkenstock sandal, hannayensa na sanye cikin hand gloves baka, yayin da fuskarsa ke sanye da face mask baki, ya ɗaure dark black curly hair sa nan a baya, ya bar na gaban goshin kamar kullun. A yau fusatacciyar fuskar nan tasa ta fi ta koyaushe razana mai rai, domin yau fuskar tasa a ɗaure take tamau kamar wani hadari, har wani siraran jijiyo ne suka bayyana masa a goshinsa saboda ɗaure fuska sosai da ya yi, girarsa sun haɗe waje guda, saboda ɗaure fuska da ya yi, da ma gashin girar nasa ya kusa haɗewa saboda yawa, shi yasa da ya ɗaure fuska sai girar tasa ta haɗe, kwarjininsa ya kara bayyana sosai, tamkar wani zakin da ya yi shekara babu abinci, kallo ɗaya za ka masa ka san yau a fusace ya ke ainun. Yana sako kafarsa ta saman benen zai sauƙo kasa, shi ma Musharraf yana sako tasa kafar zai hauro, bawan Allah bai san da cewa idan lion na saman staircase to ba wanda ya isa ya hau ba, har sai ya sauka, shi bai ma san waye lion ɗin ba, sunansa kawai yake ji. Ga shi yau ran lion a matukar ɓace yake, don shi kaɗai ma sai wani huci yake, kamar ba lafiya ba, yana tafiya yana wani bubbuɗe kirjinsa, da ma kuma ga kirjin nasa a bubbuɗe. A daidai tsakiyar staircase ɗin suka yi karo da Musharraf yana ɗan jan kafar sa a hankali yana ɗingisawa. Wani mahaukacin mari lion ya sauƙe wa Musharraf a fuskarsa, wadda ya sanya shi yanke jiki ya zube kasa sumamme, kasancewar bene ne, hakan yasa ya gangara a sume ya sauka kasa, tsallakawa ta kansa lion ya yi, ya nufi hanyar fita daga cikin falon, don ma yana sauri ne shi yasa ya yi wa Musharraf mari ɗaya ya wuce. "My lion where are you going?" Cewar daddy da ya fito daga ɗakin magungunansa da yake kasan benen, a hankali lion ya juyo da kallon sa kan daddy. Ganin fusatacciyar fuskarsa ba karamin razana daddy ya yi ba, ya sha jinin jikinsa don ya san halin ɗan nasa, kun san halin daddy da saurin birkicewa nan take ya ruɗe ya fara haɗa wa lion words yana in-ina. "My lion what is going on? What is happening? What is wrong with you?". Sai jero tambaya yake yi yana haɗe words, kuma ya yi maganar cike da tashin hankali. Furzar da iska mai matikar zafi daga bakinsa lion ya yi, da kyar ya iya buɗe ɗan karamin bakinsa ya ce, "Zan je Spain ne dad, I need your prayer." Yana kai karshen maganar bai tsaya ya jira amsar da dad zai ba shi ba ya fice da sauri, don ba abin da zai hana shi dira cikin Spain yau, kuma bai son ganin tashin hankali da dad zai shiga, don ya san ba karamin tashin hankali zai shiga ba, ya san halinsa sarai, musamman ma Michael ba ya nan James ba ya nan, halin da zai shiga ba zai yi kyan gani ba, kuma ba tafiyar sirri zai yi ba ya zama dole daddy ya sani, ko bai faɗa masa ba, dole zai sani ko don jiragen dake shawagi a sama, shi yasa ma bai ɓoye masa ba, ya sanar da shi ga in da zai je kawai. Yana fita daga falon ya nufi jerin gwanon motocinsa dake jere kamar kullun suna jiran tafiya kawai. Gidan nasu yau ya cika da zaratan sojoji sosai ta ko'ina, saboda sun san da tafiyar tasa, gabaɗaya sun jeru layi kamar wadanda za su tafi fareti, tun daga farkon kofar falon har zuwa, babban gate na gidan, Jibga-jibgan zaratan sojoji ne. Tun da ya fito suke ta faman ɗaga hannu suna sara masa tare da buga kafafunsu ɗaya a kasa. Ko kallon in da suke bai yi ba, ya wuce ya nufi motoncin nasu, yau saɓanin kullun ne, don an kara yawan motoncin nasu, saboda kowa ya san da tafiyar tasa, don karin tsaro zuwa airport, shi yasa aka karo manya-manyan motocin sojoji masu numfashi. Motarsa da ya saba shiga nan wannan Baturen ya buɗe masa kofar motar, ya shiga ya zauna. Yana zama Tga ya fito hannunsa riƙe da system da wayar lion, shi ma Tga yau sanye yake cikin kaki. Zuwa ya yi, ya miƙa wa lion system ɗin sannan ya ɗaga hannu ɗaya ya sara masa, karɓar system da wayar kawai lion ya yi ba tare da ya kalli Tga ɗin ba. Runtse dara-daran idanunsa ya yi, har cikin ransa yake jiyo sautin kukan Brady, don yasa su Tga sun kulle Brady a ɗaki, saboda ba zai tafi da shi ba, kun san Turawa yadda suke da dabbobinsu, lion ya fi jin zafin rabuwa da Brady a kan su Tga, har ga Allah yana jin ciwon kukan da Brady ke yi, shi ma kuma Brady sai haushi yake dakawa da karfi, don Romeo ya ji shi ya dawo ya ɗauke shi, amma ina Romeo na jin shi, sai dai ba zai yiwu ya tafi da shi ba ne kawai. Zuba masa ido sojan da zai tuka motarsa ya yi wato direbansa na yanzu tun da ya tura Tyrone gadon asibiti, da ma Tyrone shi ne asalin direbnsa, Tga kuma na hannun damarsa, kuma uncle nasa, ɗan autansu daddy. To har yanzu Tyrone na asibiti tun dukan da ya masa a kan watch. Yau tun daga cikin gida suka saki jiniya mai tashin kai, tamkar fillin daga za su tafi, jiniyar yau ma ta daban suka saki, wadda da ka ji ka san manya-manyan jiga-jigan kasar ne za su fita. Da gudun gaske motoncin suka tashi, don sun saka alamar danja a gaban motoncinsu, duk da cewa ko ba su saka alamar danja ba ma, babu wani abin hawa da ke hawa titin da suke kai har sai sun wuce, to amma yau da yake za su yi gudun wuce ka'ida sai suka sanya alamar danja don bin doka, kada su zama suna matsayin masu doka kuma suna karya doka da kansu. Tun kafin su iso bakin gate security sun wangale musu katafaren gate ɗin gidan, a guje suka danna hancin motocinsu waje. Ko'ina jiniya ta kareɗe cikin unguwar, da ma tuni jama'a sun san da tafiyar tasa don sun gani a labarai sai dai babu wanda ya san abin da zai kai shi Spain, sannan ba kowa ma ya san ina zai je ba, kawai dai sun san The General of The Army zai fita cikin Washington DC yau. Tsabar gudun da suke shararawa a kan titin nan, gudu na wuce ka'ida, hakan yasa suka isa *Dulles International Airport* cikin ƙankanin lokaci. Ko'ina a cikin airport ɗin cike yake makil da manya-manyan sojoji da kuma jiga-jigan masu faɗa a ji a faɗin kasar, ga kuma manya-manyan gidajen TV wato ƴan jarida ta ko'ina, da ƴansanda ma ba a bar su a baya ba. Idan na ce zan tsaya zayyana muku jama'ar da suka halarci wannan airport ɗin to sai mu kwana mu wuni ba mu gama ba, kawai ku kwatanta a ranku, don fa waje airport ya cika iya cika, saboda lion bai yarda da su zo yi masa rakiya daga gida ba. Idan ba ku manta ba kun san family William Jacop gabaɗayansu ba sa yarda da mutane, ba wai kuma dan tsoro ko wani abu ba, haka suke ba sa son bako kuma ba sa yarda da mutun, kila suna da nasu dalilin na yin haka ba mu sani ba, shi yasa jama'a suka zo yi masa sallama a airport. Suna danna hancin motocin su cikin airport ɗin, jerin gwanon motocin His Excellency Mr President ya danno hanci cikin airport ɗin, shi ma ya zo yi wa jikansa sallama. Kusan a tare lion da His Excellency suka fito daga cikin motocinsu, dukansu manya-manyan jiga-jigan sojojin ne suka take musu baya. Rungume lion His Excellency ya zo ya yi, yayin da shi ma lion ya sanya hannayensa duka biyu ya rungumo kakan nasa sosai. Sai hotuna ƴan jarida ke ɗaukar su, don ba halin su matso kusa da su, ga shi kuma suna son jin me zai kai lion Spain, suna son tambayar shi amma ba dama, don ko lion shi kaɗai ya fito babu ɗan jarida mai karfin gwiwar iya tinkarar sa, ya ce zai masa tambayoyi, ballantana yau ga jiga-jigan dubban sojoji ta ko'ina, ai ko kusa ma ba su kawo a ransu za su samu damar ganin shi da ido ba ma, don ba tafiyar yara yake ba, taku yake irin na jaruman sadaukan yaki, da ya fito daga motarsa kafin su farga ya shige cikin jet ɗinsa. Amma Allah ya taimake su sun sa mu damar ganin shi albarkacin His Excellency, don ya tsaya su yi sallama. Kiss His extcellency ya manna masa a kumatu tare da ɗan raba jikinsu yana masa fatan alkhari. Saboda face mask dake fuskarsa yasa bai sa mu damar yi wa His Excellency kiss ba, don ba zai cire face mask ɗin nan a gaban ƴan jarida ba, hakan yasa ya wuce ya nufi cikin jet nasa His Excellency na ɗaga masa hannu tare da fatan alheri. Gabaɗaya sojojin dake wajen suka ɗaga manya-manyan bindigun su sama, suka saki harbi, ji kake ratatata ruwan wuta. Wucewa yayi ya shiga cikin jet na sa, jibga-jibgan sojojin shida ne suka take masa baya zuwa cikin jet ɗin, su ka tsaitsaya a kansa, riƙe da manya-manyan jiga-jigan bindigogi masu numfashi, masu kai sako direct in da aka aika su. Zama yayi saman wani haɗaɗen sofa wadda da ka gan shi kasan na musamman ne, duk da cewa gaba ɗaya, luntsuma-luntsumar sofar dake cikin jet ɗin, sofa ne masu numfashi wanda idan ka gansu, kai kace a fadan shugaban ƙasa kake, saboda haɗuwar su, ga su da laushi sosai, ko wani sofa akoi wani kyakkyawan glass table a gaban shi, wanda za a ɗaura maka drinks ko wani abin. Kasan cewar mamallakin Jet ɗin sarkin son kamshi ne hakan yasa cikin Jet ɗin ke tashin wani fitinannen daddaɗar kamshi turare mai kwantar da hankalin mai shaƙa, ga kuma daddaɗar sanyin Ac dake tashi, abun gwanin burgewa, Jet ɗin nan ya haɗu iya haɗuwa, dan haɗuwar sa ma ba zai faɗu a baki ba, ɗauke yake da tambarin sunan Romeo kamar haka *The General of the Army Romeo, da manyan baki*. Jingina kai ya yi da jikin sofar da yake zaune, ya lumshe dara-daran kyakkyawan idon sa, ya yin da jibga jibgan sojojin sa ke ta faman kallon gefe-gefen sa dan bashi tsaro, amma basu isa su kalle shi direct ba dan bai son yawan kallo, sai dai su kalli gefe-gefe da shi, dan su tabbatar ba wani motsi ko wani na'uran nesa dake ɗaukan shi, don yanzu daga nesa za'a iya dasa maka na'ura ta ɗauko ka duk halin da kake ciki, har makiya su iya farmakar ka, sai dai a na iya gane na'uran a jikin mutum idan a ka dasa maka, hakan yasa suke yawan kallon in da yake, don su tabbatar ogan su yana kalau yana cikin tsaro. Manyan jiragen sojoji biyu ne suka fara tashi kamar da mintuna goma sannan jet ɗin lion ya tashi, sai wasu manya-manyan jiragen biyu saka tashi, suka saka jet ɗin a tsakiyarsu, sai na yaki ɗaya a baya. Haka suka nufi Spain. A ɓangaren daddy kuwa, Romeo na fita, ya zauna saman sofa yana dafe kirjinsa da ke masa bala'i ciwo kamar zai fashe. Already da ma lion ya san hakan za ta faru shi yasa ya ce da Tga ya zauna a gida kada ya bi shi, ya kula da daddy kawai, time to time su rinƙa yi masa alluran barci zuwa gobe zai dawo, shi ma kuma Michael gobe za'a dawo da shi gida, dan ya samu sauƙi ba laifi. Sai faman dafe kirji daddy yake, a wannan halin Tga ya dawo cikin falon ya same shi, bayan ya kaiwa Romeo system da wayar ke nan. Cikin sauri ya kariso cikin palon yana faɗin "What happened daddy?" Shiru daddy ya yi ya kasa magana saboda zafin da kirjinsa ke yi masa, dan a tunanin sa yaki lion zai tafi, shiyasa ya shiga damuwa, ga shi kuma lion ya ce Spain zai tafi, kuma daddy yasan da cewa James na can, tsoro yake kar dai wani abin ne ya faru a can Spain ɗin, dan yadda ya ga fuskar lion yau ba'a magana, abin sai dai mu ce Alhadulillah. Ganin daddy ya ki yin magana yana ta faman dafe kirjinsa ne yasa Tga ya ɗauke sa cak kamar ƙaramin yaro, kai tsaye word room ya wuce da shi. Yazo zai haura saman benen ne yaci karo da Musharraf sume a kasa yana kwance magashian. Mamaki Tga ya yi na me ya kawo Musharraf nan, har ya suma haka. Ransa cike da tunani ya wuce word room ɗauke da daddy. Bayan ya kai daddy ya masa alluran hutu ne, ya dawo ya ɗauki Musharraf dan ya mai da shi word room, amma kuma ya yi hakan ne dan James da Romeo ba wai dan yana son Musharraf ba, kawai don dai ya san akwai camera a palon ne, kome ya yi James ko Romeo za su gani, shi yasa ya yi hakan, ba dan haka ba, kun dai san Tga baya kaunar Musharraf ko kaɗan. Word room ya mai da Musharraf ya kwantar da shi saman bed nasa, ya fito ya nufi nashi bangaren don ya je ya yi wanka ya canza kakin jikinsa. To mu leƙo Nigeria kafin mu dawo wata kila lion ɗin mu ya isa Spain sai mu bi shi muga ne ya je yi a can Ilorin, Kwara State💞💞 Sai misalin karfe 6 na yamma Rimsha ta farka daga barcin wahala da ya ɗauke ta, jikin ta duk zafi yake mata, kamar an mata duka da itace haka ta ke ji. Meƙewa zaune a tsakiyar gadon ta yi tare da zuro kafafunta kasan gadon, wanka da tayi a ruwan saman nan ya ja mata ciwon kai sosai, ga shi tazo ta sha kuka rasuwar daddynta, abin sai ya haɗu ya mata yawa. Da kyar ta iya miƙewa ta nufi drawer kayan Kausar. Mayafi ta ɗauko tare da ɗaukan 1k daga cikin ragowar canjin da ya rage. Falo ta fito, babu kowa, Kausar da Ayla ba sa nan, tasha mamakin ina kuma suka je, da kamar za ta wuce ta fita, sai kuma ta fasa ta juyo ta dawo ta nufi wajen Iya. Kamar yadda ta bar Iya ɗazun haka ta dawo ta same ta tana kwance saman gado. Sallama ta mata, daga kwance Iya ta amsa sannan tare da mata izinin shigowa. Shiga cikin ta yi, wajen da ta tsaya ɗazun a nan ta tsaya yanzu ma. A nutse ta ce "Iya ina Kausar da Ayla." "Sun tafi tallar kifi." Iya ta ba ta amsa, mamaki ne ya kama ta, tallar kifi kuma ta faɗa a ranta, ita dai a nata tunanin sai talakawa ne kawai ke yin talla, amma me yasa su Kausar, za su je talla bayan su suna da rufin asiri, bata san yarabawa da neman kuɗi bane, basa zaman banza, fita suke su nemi halak ɗinsu, matansu da mazansu, basa wasa da neman kuɗi. Kamar za ta sake yiwa Iya wata maganar, amma sai ta fasa ta fito ta nufi waje. Kai tsaye shagon Sadudin ta nufa, dan yanzu ta san hanya zuwa shagon nasa. Makilin da brush na goge baki ta saya, brush guda biyu ta saya, makilin kuma guda ɗaya. Ta ba shi 1k ya bata canjin 400, har ta karɓi canjin za ta tafi sai kuma ta sake ba shi canjin ta ce ya bata cardboard paper and pencil, Allah ya sa yana da shi, ya karɓi kuɗin ya ɗauko ya bata tare da canjin 180, color na zane ta sake saya da ragowar canjin. Bayan ta gama sayyan zata wuce Sadudin ya fara tambayar ta daga ina take, ya suke da Kausar, tana jin abin da ya ce, dan da broken English ya yi magana, saboda ya san ba bayarabiya bace. Saboda tsiya irin na Rimsha sai ta nuna masa ita bata jin English ma kwata-kwata, shi kuma ya dage sai ya ji gulma, sai ya fara yi mata yar kurma-kurma da hannu, nan ma ta ce masa bata gane komai ba. Saboda gulma irin na shi har da fitowa waje daga cikin shagon yana mata kwatancen ta in da arewa yake ya na faɗi daga can take. Hannu ta ɗaga sama ta ce masa daga duniyar wata take, nan fa ya gane raina masa wayo tayi ashe tana jin sa, ta bar shi sai yin yar kurma-kurma yake kamar mahaukaci ya zage sai kwatance yake. Kafin ya gama tunanin da yake Rimsha ta sa kai ta wuce abinta, ciza laɓɓa ya yi alamar bai ji daɗi ba, yaso ya ji daga ina take, ya so ta saki jiki da shi, amma ina bai samu dama ba, dan ita ma Rimsha ba kanwar lasa ba ce, ta iya tsiya, amma sai idan ka taɓota take tsiyar nata. A nutse take tafiya har ta isa gida. Da sallama ɗauke a bakinta ta shiga cikin palon, wani matashi ta yi arba da shi zaune cikin palon saman sofa yana cin abinci, kamannin sa ɗaya da Kausar, sai dai shi baki ne Kausar kuma tana da ɗan haske. Cikin girmamawa ta gai da shi cikin harshen turanci dan tasan da wuya idan baya jin turanci, fuskarsa ɗauke da fara'a ya amsa tare da tambayar ta wa take nema, dan a tunaninsa Rimsha yar garin ce, tazo neman Kausar ce ko Iya, shiru ta masa ta rasa amsar da zata ba shi. Ganin ta yi shiru ne yasa ya ce "Wajen Kausar ki ka zo ne?" Ya yi maganar cikin harshen Hausa dan ya lura kamar Rimsha bahaushiya ce ba bayarabiya ba ce, cikin sauri ta gyaɗa masa kai alamar eh wajen Kausar ta zo. Girgiza kai ya yi yana faɗin "Eyya sorry ba ki san Kausar ta ɓata da su ka je Kd da Iya ba ko?" Shiru Rimsha ta masa, ta rasa ta ya zata masa baya ni, tunani take ko dai ta ce masa, ita ma yanzu yar gidan ce. Ci-gaba da cin abincin sa ya yi tun da ya ga taki yi masa magana, ita ma shiru ta tsaya, tana son wucewa cikin ɗakin Kausar ta je ta jiye mu su brush nasu ita da Ayla, sannan ta fara aikin zanen fuskar GAR, amma kuma tana tsoron wuce wa kada wannan matashin ya yi tunanin ko wani abu ta zo ɗauka musu. Ta jima tsaye a wajen kafin Iya ta fito daga cikin ɗakin ta tana faɗin "Wasiu idan ka gama cin abinci ka sayo mana kifi da ɓomo, dan zan ɗaura abincin dare" ta yi maganar cikin harshen yarabanci. Da alamar shi ma Wasiu irin Kausar ne fagen cin abinci, dan ga shi nan Iya tana masa magana bai tanka ba, sai kai loma kawai take hannu baka hannu kwarya. Wani nauyayyar ajiyar zuciya Rimsha ta sauƙe lokacin da Iya ta shigo palon kamar wadda aka tsare a prison yanzu kuma anzo fitar da ita, haka ta ji a ranta. "Rimsha me ya tsai da ke a nan?". Cewar Iya, kasa da kai Rimsha ta yi tana ɗan satar kallon bodar Wasiu. Ganin haka ya sa Iya ta gane me Rimsha take yi wa kame-kame. "To wuce ciki abinki, wannan yayanku ne, yayan Kausar na biyu ne." sai lokacin ya da kata da cin abincin, ya dawo da kallonsa kan Rimsha. "Iya daga ina kuma ku ka samo wannan yarinya mai bala'i kyau haka?" Yar dariya Iya ta yi kafin ta ce "Tare suka zo da Kausar" a zabure ya miƙe tsaye yana faɗin "Me ki ke ce Iya? Kausar fa, to ina Kausar ɗin ta ke? Yau she ta dawo? Ai na a ka gane ta?" Ya yi maganar yana zaro ido waje. "Oh sorry ban faɗa ma ka Kausar ta dawo ba ko?". Cewar Iya. Jin sun kamo wani topic na hira ne yasa Rimsha ta lallaɓa ta wuce da Sauri abinta ta shige ɗakin Kausar tana sauƙe ajiyar zuciya, ta baro su nan suna zance. Tana shiga ta ajiye brush da makilin ɗin da ta sayo musu ita da Ayla, a saman ɗan karamin drawer dake ɗakin, sannan ta haye saman gado, tare da shinfiɗe cardboard paper ta ɗauki pencil ta fara zanen fuskar GAR kamar yadda ta saba. Kasan cewar ta kware a zanen na shi ne yasa ta yin saurin gamawa, dan in da sabo ta saba, yanzu yanzu zata zana shi, kuma ya fita ras, kamar ki kira shi ya amsa. Yau zanen sa da ta yi ma, na daban ne da kullun, dan yau ta zana shi a babba da face mask, sai kuma ta zana wani karamin hoton na shi, a kasan babban, shi kuma wannan karamin ba bu face mask ta zana shi, duk da cewa bata taɓa ganin shi ido da ido ba, ma'ana bata taɓa ganin asalin fuskarsa babu face mask ba, tana iya kawata yadda kyansa zai kasance a zahiri, sai ta zana shi ita yana yin yadda fahimtar kyansa da ta yi. "Rimsha rubutun mene wannan a kirjin ki?" Kamar daga sama ta ji muryan Malika, ko a ce muryarta, don ba abin da ya raba muryarta da ta Malika. Cikin sauri ta ɗago kai tana kallon Malika. Tsaye take a bakin kofar shigowa ɗakin, ta goya hannu a kirji tana murmushi, kamar kullun dogon riga ne har kasa purple color a jikinta, ta yafa mayafin rigar a kanta. Murmushi ita ma Rimsha ta yi tana faɗin "Ina ki ke tafi ɗazun?". Karisowa cikin ɗakin Malika ta yi tare da zama kusa da ita tana kallon zanen sunan GAR dake kirjin Rimsha. "Baki faɗa min zane me a kirjin ki ba". Cewar Malika ta yi maganar tana kai hannun ta saman kirjin Rimsha. Kasan cewar Rimsha ta fara kirgan dangin sai abin ya bata kunya ta ɗan ja baya bata bari Malika ta taɓa mata kirji ba, kuma azahirin gaskiya tun da tayi zanen sunan Romeo take rufe wa bata son kowa ya gani yanzu ma da Malika ta gani, bata sani ba, ta duƙa tana zane ne wuyar rigarta ya ɗan zazzago rubutun ya bayyana. Kara faɗaɗa murmushita Malika ta yi kafin ta ce "Rimsha ki na da kamala da kamewa, ina miki fatan ki kasan ce haka har karshen rayuwarki, ki zama mai tsare mutuncin kan ki dan mutunci madara ne idan ya zube ba zata taɓa kwasuwa ba, naji daɗin yadda kika janye jikin ki baya, amma ina son ki sani ni ba zan taɓa cutar da ke ba, sai dai ma nayi iya kan bakin kokari na wajen ganin na taya ki tsare mutuncin ki". Ajiyar zuciya Rimsha ta sauƙe sannan ta ce "Ina godiya sosai Malika, amma dai kina ba ni tsoro da kuma mamaki" "Mamakin me Nake baki Rimsha?" Cewar Malika tayi maganar tana ɗan zaro ido. "Me yasa wani lokaci mutane basa kallon ki sai ni kaɗai? Sannan kuma me yasa da Ayla ta gan ki ta suma? Ya aka yi kika shigo gidan nan yanzu? Me yasa idan muna magana da ke ba wanda yake ji me muke faɗe?". Zuba mata ido Malika ta yi, har sai da ta kammala jero tambayoyin nata, sannan ta saki haɗaɗɗen murmushi tana faɗin "Rimsha ki na da abin dariya, to amma kina da gaskiya dole zaki ji tsoro dan baki saba ba, ni ba mutun ba ce kamar yadda kika ɗauka, ni aljana ce" a zabure Rimsha ta ja baya tare da miƙa wa tsaye tana zaro dara daran sleeping eyes nata, "Menene Rimsha? Kada ki ji tsoro na mana". Runtse ido Rimsha tayi tare da kurma wani razananiyar ihu, wadda ya sanya Malika ɓace wa ba shiri. Da gudu Iya da boda Wasiyu suka shigo cikin ɗakin Iya tana faɗin "Rimsha lafiya ki ke kurma ihu haka?". Idon ta a Runtse saboda tsoro ta kasa magana kuma ta kasa buɗe ido, dan tana ganin idan ta buɗe idon ta mutuwa za ta yi, Malika aljana za ta kashe ta. Da kyar Iya ta samu ta lallaɓata tayi shiru tare da komawa ta zauna tana tunanin ita kuma daga ina ta samo aljanna, ganin ta yi shiru yasa su Iya suka koma palo. Shiru ta zaune a wajen tana tunani har su Kausar suka dawo ƙarfe 6:30pm daidai su ka shigo cikin gidan daga tallan kifi. Da sauri Rimsha ta miƙe ta rungumo Ayla tana son faɗa mata cewa Malika aljana ce, sai kuma ta kasa, ga dai maganar a bakin ta, amma ta kasa faɗe. Haka ta hakura suka yi alwala dan lokacin sallar mangariba ya yi. Sai bayan sun yi sallah mangariba da issha ne suka zauna a palo suna hira. Miƙe wa Rimsha ta yi ta shiga kitchen wajen Iya, dan taya ta girki. Yau tuwon semo da miyar Egusi Iya da Rimsha suka yi. Sai karfe 9 na dare suka kammala girkin suka dawo palo suka baje, suka fara cin abinci, suna ci suna hira, ita kuma Kausar tana ci tana haɗa zufa, don ba ta magana kam sai dai kai loma. Suna tsaka da cin abincin ne boda Jami'u da boda Kabiru suka dawo. Da gudu Kausar ta tashi ta nufe su, tana ta washe baki. Tsalle tayi ta haye jikin boda Jami'u, ɗaga ta ya yi sama kamar yar baby, duk wannan kiba na Kausar bai hana shi ya iya ɗaga ta ba, dan Jami'u irin mazan nan masu tsawo da ƙiba, ga shi da kiran karfi. Ihu ne ya kaure a gidan, na karti wato boda Jamiyu da boda Kabiru, don ba su san kanwarsu kuma yar autarsu ta dawo ba. Shi boda Jamiyu ɗa ne ga yayan baban Kausar kuma shi yake son Kausar ɗin ma'ana saurayinta ke nan. Ihu suke kamar ba lafiya ba, wai a haka murna suke nunawa, miƙewa Iya ta yi ta fara taya su. Bayin Allah Rimsha da Ayla suna ganin ikon Allah iya ganin idonsu a kasar Yarabawa, wani lokaci ma har tunani suke anya Iya ba ta samu matsala a ƙwaƙwalwarta ba kuwa mata ce wani lokaci bata da setti ko kaɗan. Haka suka yi ta ihun nuna murnarsu na wani lokaci kafin nan su tsagaita, Jami'u ya sauƙe Kausar kasa daga jikin sa, sai dariya suke. Daga Jami'u har Kabiru sun yi shocked da ganin su Rimsha, sai kallon Rimsha suke, dan akwai wutar nepa, haske ya karaɗe palon gabaɗaya hakan ya sa suka samu daman ganin Ayla da Rimsha sosai. Jami'u ya kasa hakuri har sai da ya tambayi daga ina Rimsha take, nan fa Kausar ta fara basu labarin irin wahalar da suka sha tun shigar su daular Mutuwa har fitowar su. Sosai su Jami'u suka tausaya musu. Hannu ya kai zai shafi kan Rimsha, cikin sauri ta ɗan ja baya, yar dariya ya yi kafin ya ce "As from today you are my sister, so kada ki damu, na san halin ku Hausawa baku son a rinƙa taɓaku sai ku rinƙa avoiding na mutane, kamar ba ku da gaskiya." cikin harshen Turanci ya yi maganar. Shiru Rimsha ta masa, dan ita gaba ɗaya ma haushi suka bata, jibi yadda yake wani rungume Kausar dan iskanci kuma yasan akwai aure a tsakanin su. A ɓangaren Ayla ma ba karamin haushin abin ta ji ba, wasu karti da su ba kyan gani, ga shi dukansu sun wani saka gajeren wando zuwa guiwa da riga mai karamin hannu. Shi kam Kabiru sai kallon Rimsha yake ya kasa dai'na wa, haka shi ma Jamiyu, sai dai shi Jamiyu satar kallon ta yake dan kada Iya ko Kausar su gane yana kallon nata. Yanzu su ma a nan gidan za su kwana, Rimsha da Ayla suka yi wa kansu tambayar a tare a cikin zuciyoyinsu kamar abin haɗin baki, sai dai kuma ba su da amsar tambayar tasu. Haka suka zauna a palon tare da su Jami'u, Rimsha kamar za ta yi kuka dan haushin zama da karti, haka ita ma Ayla. Ita kuwa Kausar sai faman wage hakwara take tana dariya kamar wata yar fari, sai murna take, ta wani zauna kusa da Jami'u suna kallon Yoruba film, ita kuma Iya ta ɓige da barci kwance saman sofa. Sai misalin 11 na dare sannan su Jami'u suka wuce ɗakin su, wanda ya kasance kusa da ɗakin Iya ne, duk dai cikin rufi ɗaya. Tsoro sosai Rimsha ta ji lokacin da taga cewa a nan gidan su Jami'u za su kwana, ga shi ta lura da irin kallon ta da suka rinƙa yi mata. Haka cike da tsoro suma suka wuce na su ɗakin, bayan Kausar ta tashi Iya daga barci, Iya ce ta kulle kofar falon da key da kuma sakata, sannan ta wuce ɗakinta ita ma. Rimsha dai ta tsorata sosai, gani take kamar za su zo su kama ta, shiyasa da suka shiga ɗaki ta riga su hayewa gado, ta tafi can karshen gado ta kwanta ta manne da bango, Ayla ce ta kwanta kusa da ita, sai Kausar a karshen gadon To Rimsha mu Sarkin tsoro sai dai mu ce Allah ya tsare, na yi nan sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu. Sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode17-18🌹 Haka cike da tsoro su ma suka wuce nasu ɗakin, bayan Kausar ta tashi Iya daga barci, Iya ce ta kulle kofar falon da key da kuma sakata, sannan ta wuce ɗakinta ita ma. Rimsha dai ta tsorata sosai, gani take kamar za su zo su kama ta, shi yasa da suka shiga ɗaki ta riga su hayewa gado, ta tafi can karshen gadon ta kwanta ta manne da bango, Ayla ce ta kwanta kusa da ita, sai Kausar a karshen gadon. Suna kwanciya ba jimawa Kausar da Ayla suka yi barci, ita kuma Rimsha ta jima idonta a rintse amma ba ta yi barci ba har sai da dare ya tsala sosai tana ta tunani rayuwa, baiwar Allah har kusan asuba, sannan barci ya yi awon gaba da ita. Asuba ta gari. 💞💞Spain💞💞 Helicopters guda shida aka tasa tun kafin lion ya iso, sai kewaye cikin *Madrid* wato babban birnin Spain suke. *Madrid* shi ne baban birnin Spain, birni ne mai girman gaske wanda a kalla Population nasu ya kai 3.3 million, birnin ya tsaru iya tsaruwa, ga dogayen gine-gine Turawan masu kyau da kawatuwa, ta ko'ina tsaf-tsaf, suna da wuraren shakatawa da yawon buɗe ido, ga wajen wasanni kala-kala, shimfiɗaɗɗun tituna masu kyau wadda suka ratsa ta cikin unguwanni lungu da saƙo, ga kuma manya-manyan gumakai na manyan shuwagabannin da suka suɗe, an yi guma kan su a tsakiyar garin, suna da manya-manyan teku wato koguna, masu ɗauke da ruwa mai kyau da karawa garin kyau, sannan akoi gumakan da irin na mace a keken doki, ko namiji ya ɗaga igwa zai sake wuta. Tsayawa zayyana muku yadda Madrid take ba zai yiwu ba, dan sai ya cinye mana wannan page ɗin ba mu kammala ba. Karfe 12 na rana daidai, The General of the Army jet ya yi landing a *Madrid-Barajas International Airport,* har lokacin da suka yi landing helicopters suna sama suna shawagi, dan tabbatar da tsaro, kuma ba za su sauko ba yau a sama za su wuni har sai lion ya bar kasar. Airport ɗin cike take makil da dubban sojojin Spain, dan tuni sun san da zuwan lion, sun karɓi umarnin daga sama, a kan su tarbo shi daga airport su tabbatar sun kai shi masauki lafiya, hakan kuma ya samo asali ne sakamakon His Excellency mr President kakan su lion ya kira President na Spain ya sanar da shi zuwan jikan nasa, hakan yasa a ka kara tsananta tsaro sosai, ko'ina a cikin birnin sojoji ke yawo, duk ta in da ka juya sai ka ga sojoji, a kan titi ne, lunguna da sakon birnin ne, ta ko'ina. Ko da jiragen suka sauka lion bai fito daga cikin jet ɗinsa ba, yana zaune tamkar bai san sun sauƙa ba. Kasancewar sojojin Spain ba su san halinsa ba, labarinsa kawai suke ji, hakan sai ya dame su, rashin fitowar na shi ya dame su sosai, gani suke kamar ba lafiya ba, suna son tinkarar jet ɗin nasa dan su duba ko lafiya, amma babu dama domin jibga-jibgan sojojin Washington DC wato sojojin lion da suka zo a sauran jiragen sun kewaye jet ɗin, hannayen su riƙe da manya-manyan bindigu, hakan ya sa sojojin Spain ba su yi gigin tinkarar jet ɗin ba, dan sojojin Usa ba wasa ba, ba su da wasa a kan aikinsu, manya-manyan kasashen duniya tsoron su suke ji, saboda idan suka tinkari abu tofa basa juya baya komai wuya komai daɗi har sai sun cin ma abin da suke so, basu da imani ko kaɗan. Wasu dankara-dankaran motonci masu numfashi His excellency president ɗin Spain ya turo su ɗauki lion. Motocin sojoji guda 6 sababbi gagal, sai kyalli suke, sai kuma wata dankareriyar mota wadda da ka gani ka san na musamman aka tanadawa lion, motar ta haɗu sosai kirar Bugatti cantodieci fara tas sai kyalli motar take kamar yanzu a ka ɓallota gal-gal. Good 40mins lion ya ɗauka zaune cikin Jet ɗinsa ya jingina kai da jikin sofa da yake zaune, dara daran idon sa a lumtse sai faman furzar da iska mai zafi yake daga bakinsa. Sojojinsa dake tsaye a kansa, sai faman satar kallon sa suke, dan su kansu burge su ogan nasu yake, Allah ya masa wani irin sihirtaccen kyau, ga bala'i kwarjinin da farin jini masifa, duk in da zai shiga, za su so shi sosai amma kuma za su ji tsoron sa kamar su mutu, dan fusataccen fuskar sa ma kawai abun tsoro ne. Yar kara wayarsa dake gefen sa ya yi, alamar shigowar sako, sai da ya ɗauki 5mins sannan slowly ya waro idanuwansa tare da ɗaukar wayar da system nasa ya miƙe tsaye. Cikin sauri sojojinsa dake tsaye a kansa, suka ɗaga hannu suka sara masa. Wucewa ya yi ya nufi waje. Yana sako kafarsa wajen jet ɗin, sojojinsa da ke kewaye da jet ɗin suka ɗaga manya-manyan bindigun hannunsu suka fara sakin wuta a sama, gaba ɗaya karan harbi ya kewaye ko ina, nan take masu ɗaukan shi a hoto suka fara ɗaukan shi. Wucewa ya yi ya nufi wayan nan dankara-dankaran motonci da His Excellency ya turo, yana taku cike da izza da cikan gwarzon ɗa namiji. Su dai sojojin Spain sun zama yan kallo, dan abin ya fi karfinsu duk yadda suke tunanin lion ashe ya wuce nan ba su sani ba, haka zalika yadda suke tunanin sojojin USA sun wuce nan. Ji kake dip-dip-dip a guje direbansa na yanzu ya nufi motar da a ka tana da domin shi , jikin sa har kerma yake wajen buɗe kofar motar, dan lion ya kusa isowa wajen, idan kuma ya iso bai buɗe masa kofar motar ba to akwai matsala, shiyasa jikinsa sai ɓari yake wajen buɗe kofar. Cikin zafin nama yake taku irin na jaruman maza har ya isa wajen motar, bai wani tsaya ɓata lokaci ba ya shige cikin motar kawai, yana shiga driver sa ya ɗaga hannu ya sara masa sannan ya rufe kofar motar, gaba ɗaya sojojin dake wajen har sojin Spain sai da suka ɗaga hannu suka sara masa, sannan sojojin sa suka nufi motoncin da a ka tana da musu, a guje suka haye saman bayan motoncin. Cikin zafin nama driver sa ya shiga gidan gaba na motar. Kamar yadda suka saba a Washington DC, a nan ma haka suka yi a jere suka tashi motoncin suka bar Airport ɗin da gudun gaske, tun kafin su fita Airport suka saki jiniya. Motoncin suna fita sojojin Spain suka yi saurin shiga nasu motoncin suka rufa musu baya. Kai tsaye gidan His Excellency suka wuce, dan shi Romeo baya son kama hotel, ya fi son zaman gida, idan ka gan shi a hotel to dole ce ta sanya. Kun san dai yadda gidan Turawa yake, mu samman gidan President kun san yadda gine-gine yake, ba sai mun tsaya nan ba. Gaba ɗaya gidan His Excellency President ɗin Spain a cike yake da sojojin Spain da yan sanda, ga kuma manya-manyan baki masu faɗa a ji a kasar, duk sun hallara a gidan, dan tarban jika ga His Excellency Mr President of USA. A tunaninsu lion mutun ne mai sauƙin kai, labarinsa kawai suke ji ba su taɓa zama da shi ko ganin shi ba. Yau sun ga asalin kalar halinsa, dan kuwa yana fitowa daga cikin motoncin nan ya wuce cikin gida, duk wayan nan manya-manyan baki dake tsaye a wajen domin shi bai kula kowa ba, ko kallo ma ba su isshe shi ba ya sa kai ya wuce abinsa. Babbar magana. Sun sha mamaki wasu daga cikinsu kuma sun ji haushi sosai, a ganinsu lion ya wulakanta su ya musu cin mutunci. Tuni Lion ya san in da a ka tana da masa, domin sai da ya yi bincike a wajen kafin ya zo, sai da ya sauƙe sojojinsa sama da guda 15 wadda suka riga shi zuwa, suka zo suka bincike wajen tsaf, shi ya sa yana fita mota ya wuce wajen. Jama'ar da suka zo domin shi, cike da jin haushin abin da ya musu suka koma cikin fadan His Excellency. Nan su ka shaida masa abin da lion ya mu su, hakuri His Excellency ya ba su tare da faɗa mu su haka halin lion yake, baya da yawan magana kuma baya son hayaniya, yanzu ma idan suka takura masa da hayaniya tofa barin gidan zai yi, idan kuma ya bar gidan nan, za su samu matsala da His Excellency mr President na USA, zai ce sun yi wa jikansa wulakanci, ba zai taɓa yi musu uzuri ba. Dole ba dan sun so ba, haka suka ja bakin su suka yi shiru dan kar su yi wani magana ya zamo musu matsala, dan sun san halin His Excellency Mr President of USA a kan family sa, kuma sun jin halin yaran William Jacop, suna ji a News, yanzu a kan haka lion zai iya sawa su rasa mukamansu ko rayuwar su ma baki ɗaya, dan sun san halin gwamnatin USA ba wasa. A ɓangaren lion kuwa, yana shiga part na musamman da a ka ware domin shi, sai ya kara ɗaure fuska sosai da sosai, ya fito daga wajen, a cewar sa wajen yayi datti kuma abubuwan ciki sun masa local. A zahirin gaskiya ba laifi komai dake cikin wajen sabbi ne kal-kal a ledansu a ka fito da su, sannan an zuba komai da ɗan adam zai buƙata, kuma an share wajen sosai da sosai, shi ɗin ne dai ba'a iya masa, baka taɓa gane gabansa bare bayansa, yana da bala'i tsabta, ko datti kaɗan ya gani a waje to sai ya haɗe wajen gaba ɗaya ya ce akwai kazanta ba zai zauna ba, yanzu ma abin da ya faru kenan, kura kaɗan ya gani wajen mirror shikenan ya ce wajen akwai datti, sannan kuma bayan haka furnitures da ke wajen ba su masa ba. Yana fita sojojin sa suka take masa baya, kai tsaye motoncin da suka kawo shi ya nufa. Da gudu wani soja ya zo ya buɗe masa motar gidan baya, ya shiga ya zauna. Cikin zafin nama sojojinsa suka haye saman bayan nasu motoncin, kusan a tare suka yi wa motoncin key. Jin tashin motoncin ya sanya His Excellency fitowa daga fadarsa. A hanzarce ya iso wajen yana tambayar lion ko lafiya, ina zai je. Shiru lion ya yi na yan mintoci kafin ya sanar da shi wajen da suka tana da masa bai masa ba, sosai His excellency ya ji ba daɗi tare da yiwa lion alkawarin yanzu za'a canza komai zuwa yadda yake buƙata ya fito ya koma cikin fadar shugaban kasar ya zauna. Shiru ya yi na ɗan lokacin, kafin ya ba wa sojojinsa umarni a kan su tashi motonci su tafi, dan shi idan ya yi magana baya canzawa komai zai faru, sai dai ya faru, kai ko tunani ya yi a zuciyarsa zai aiwatar da wani abin to fa ba zai canza wannan tunani ba kome za'ayi. _Kai jama'a wannan iri hali na Romeo ba mai iya shi sai daddynsu shi ya san halin kayansa, wai ta ko'ina ba sauƙi, gaskiya Lion ba dama._ His Excellency bai ji daɗi ba, domin ya san kakansu lion ba zai fahimce shi ba, kuma ba zai masa uzuri ba, zai ce da gangan ya wulakanta masa jika, sosai ya shiga duniyar tunanin ya zai yi da His Excellency, ya zai yi His Excellency ya yarda cewa shi bai wulakanta Lion ba, zancen zuci ya fara "To ma ni na isa in wulakanta Lion ne, mutumin da muke neman taimakonsa idan abubuwa sun fi gaban tunaninmu, dole a matsayinmu na tsofaffi sai mun nemi agajin sabon jini, dan zaren ba kalar yadin ba ne, kwakwalwar ma ba ɗaya ba kuma ko da gwaji ma ba za'a gwada ba, ni yanzu ya zan yi?" Haka ya tsaya sai zancen zuci yake, shi kuma Lion ya wuce ya bar gidan. Yana fita su ka nufi *Westin Palace Madrid Hotel*, a karon farko da Lion ya fara sauƙa a hotel idan ya je wata kasar, ba ya son zaman hotel amma ya zamar masa dole ne ba yadda zai yi. Katafaren Hotel ne mai girman gaske, wanda yake tsakiyar teku, a cikin ruwa Hotel ɗin yake, amma yana da shinfiɗaɗiyar hanya da zata fito da kai kamar gada haka, sannan Hotel ɗin yana da tsaro sosai, kasan cewar yana tsakiyar ruwa mai ɗauke da manya-manyan halittu irin su shak da sauran su. Duk da tsaron da wannan Hotel ɗin yake da shi, sai da jama'ar cikin ta su ka san da Lion ya shiga cikinta, saboda dubbanin sojoji da su ka kewayeta, ta ko'ina, hannayensu riƙe da manya-manyan bindigu masu aiki ba saɓa saiti. A zahirin gaskiya ba kowa ke iya kama wannan hotel ɗin ba, domin hotel ne na manya-manyan mutane, duk kuma wanda ya sauƙa a hotel ɗin ya kwana, yana barin hotel ɗin masu hotel ɗin za su kwashe komai kama daga gadaje da sauransu, duk za su kwashe su zuba sabbi. Ɗakin da Lion ya kama ba a magana ɗakin ya kawatu iya kawatuwa ya haɗu sosai, kana zaune daga cikin ɗakin kana kallon daga mahangar glass da ke a matsayin bangon gefe guda, zaka rinƙa kallon yadda ruwa ke juyi yana gudana ga wasu kananan kifaye suna tsalle saman ruwa, suna sake komawa, tekun na da girman sosai, girma da ba ka iya ganin karshensa, abin gwanin ban sha'awa ga masoya, shi kuwa Lion da bai san mene ne soyayya ba, ba shi da wani shauƙi, ko kallon wajen ma bai yi ba bare ya burge shi. Driver sa ne ya kawo masa trolley sa ya ajiye masa a wajen da suka tanada dan ajiye trolley sannna ya fice daga ɗakin Wanka ya fara yi, sannan ya shirya cikin kananan kaya, wando three quarter da riga marar nauyi duka farare tas, ya yi kyau sosai da sosai kamar shi ya yi kansa, dan shi a ko da yaushe shine ya ke yiwa kaya kyau ba kaya ke masa kyau ba, ya saki dark black curly hair nan nasa ba tare da ya ɗaure ba, sai tashin fitinannen kamshi ya ke, ya haye saman lallausan bed na Hotel ɗin tare da ɗaukan system da wayarsa ya fara aiki, yayin da jibga-jibgan sojojin ke zagaye da ɗakin nasa riƙe da manyan bindigu, dan tabbatar da tsaro. _Wai Romeo wannan aiki haka ai sai kai ɗin mu bari mu koma Nigeria watakila kafin mu dawo abubuwa sun setu a nan._ 💞💞Nigeria 💞💞 💞💞GIDAN ABBI💞💞 Sai washegari Abbi ya iya gane kansa, a nan ne kuma yake tambayar ina Aunty da Aafia? Mai aikin da ya kawo ke sanar masa da suna asibiti, ya sha ruwan mamaki sosai jin hakan, dan haka sai ya koma bedroom nasa, ya yi wanka ya shirya ya fito dan zuwa hospital ɗin, ya yin da shi kuma daddy Jelly har lokacin yana can bedroom nasa yana barcin wahala bawan Allah, ya fi Abbi jin jiki sosai da yake daman ba koshin lafiya ke gare shi ba. Lokacin da Abbi ya isa asibiti da motar Irfan, dan already daman ya san asibitin da suke zuwa, shiyasa ya wuce kai tsaye. Ya kuwa isa a kan gaba domin ya isa lokacin da Dr ke cewa Aafia yana son ganin wani na Aunty ko baban ta ko kuma babban yayan ta, ko mijinta, dan haka Abbi na zuwa ya ce ga shi nan. Wucewa office Dr ya yi ya ce Abbi ya biyo shi. Haka kuwa a kayi, da suka shiga office sosai Dr ya masa bayanin abortion ɗin da Aunty ta yi ya haifar mata da matsala sosai a mahaifarta, domin ta yi shine ba bisa ka ida ba, so yanzu sai an mata aiki, kuma ko anyi aikin ma ba lallai ta sake iya ɗaukan wani ciki ba. Tashin hankali a zabure Abbi ya miƙe tsaye bakinsa na maimaita kalmar abortion, lokaci guda zufa ya fara wanke masa fuska, sabon murɗawan ciwo cikinsa ya fara yi masa, kunnuwansa sun ki yarda da jin cewa Aunty ce da kanta ta yi abortion ji yake kamar a mafarki, ya kasa gaba ya kasa baya, komai ya tsaya masa cak, tunani yake "Yanzu da ma Halima za ta iya kashe min jinina? Da ma Halima ba ta kaunar kyautar cikin da Allah ya ba mu? Da ma Halima ba ta so na? Da ma duk ilimin addini Halima na banza ne? Kullun idan muka zauna wannan nasiha mai ratsa jiki da take mini ashe duka ta karya ce? Why Halima? Me ya sa za ki zama Musa a baki, Fir'auna a zuci? Me yasa za ki cutar da ni? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun". Dafe kansa da ke masa barazanar tarwatsewa ya yi, yana ganin yadda cikin office ɗin Dr ke juya masa kamar fanka. Bawan Allah da ma ba ƙoshin lafiya gare shi ba Aafia ta tagayyara shi ta gama da rayuwarsa. Dr na kokarin magana sai kawai ya ga Abbi ya zube kasa sumamme, a sukwane Dr ya yi kansa yana faɗin innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Ganin ya sume ya sa ya fito da sauri ya kira nurses suka zo suka ɗauki Abbi a saman bed na marasa lafiya, suka wuce da shi ɗakin da Aunty ke kwance. Ba karamin tashin hankali Aafia ta shiga ba ganin Abbinta a sume, ta tsorata sosai tana son jin me ya sumar da shi. Cikin sauri ta ciro wayar ta ta fara kiran layin Irfan tana yi tana kuka hawaye bibbiyu. Bugu ɗaya Irfan ya ɗauki kiran, a ruɗe ta ke magana "Hello yaya Irfan, Abbi ya suma Aunty ma haka ita kam kamar ta mutu ban san ya zan yi ba" daga ɗayan ɓangaren Irfan ya ce "Aafia ki nitsu ki faɗa min meke faruwa!" Muryarta sai kerma yake tana ta faman haɗe words ta kasa nitsuwa ta ce "Yaya Irfan jiya ne muna cin abinci da daddare sai Abbi da Bappa Maik su ka tashi zuwa bedroom nasu, palon ya rage daga ni sai Aunty, ita ma daga baya ta miƙe zata tafi sai ta faɗi kasa jini ya fara zuba mata, shine na gudu ne je zan faɗa wa Abbi sai naga yana toilet shi ne na ɗauko ta muka zo asibiti, sai yau shi kuma Abbi yazo dr ya kira shi dan su yi magana yana zuwa wajen Dr ya suma shima" dafe kai Irfan ya yi dan Aafia ta sake sa shi a duhu, ban da shine shine ba abin da take ta labka masa, ta ruɗe sosai. "Ina bappa Maik ɗin?". Cikin sauri ta ce, "Abbi shi kaɗai ya zo banda Bappa Maik." Shiru Irfan ya ɗan yi kafin ya ce, "Tom ina zuwa." Bai jira amsarta ba ya katse kiran. Zarya ta fara yi a wajen tana kuka, duk wannan abin da ya faru bai sanya Aafia ta yi dana sanin zuba musu magani a abincin da ta yi ba, dan aikin ba nata bane na Rufee ce, sai dai ta ji babu daɗin ganin su a halin da suke ciki. Sai safa da marwa take a wajen har Akil ya zo hospital ɗin ba tare da sanin taba, sai ji ta yi yana faɗin "Yaya Irfan ya kirani a waya a kan bappa yana hospital, ina yake? Me kuma yake damun shi?" A zabure ta ɗago kai dan ba ta san lokacin da ya zo ba, maganarsa kawai ta ji. Cikin ruɗu da tashin hankali shi ma ta fara ba shi labarin abin da ya faru, jikin ta har wani ɓari yake, da alama ta tsorata sosai. Da yake shi Akil ɗan baiwa ne akwai kwakwalwa sai ya gane me take nufi, dan haka sai ya ce ina ne office ɗin dr, ba musu ta nuna mi shi, wucewa ya yi ya bar ta nan tsaye. Ya yin da ita kuma Umaisha ke can tana gwagwarmaya da Ammie, dan Akil na fita Ammie ta zo ta tasata a gaba suka wuce kitchen dan ta je ta karisa aikin da ta fara. Tana aiki tana kuka hawaye sharɓa-sharɓa, ga shi tana aikin Ammie na aiko mata da zagi yar matsiyata da sauransu, abin ba ƙaramin ciwo ya ke mata a zuciyarta ba. Haka ta jure ta kammala aikin kitchen nan tas, amma fa tasha bakar wahala ba kaɗan ba, dan ita kanta har wani baki ta yi na wuya, sai haɗa bakin zufar kuran kitchen da ya hau jikin ta take, kasan cewar ba'a wani amfani da kitchen ɗin sai dai a ajiye ragowar abinci ko fruits, hakan yasa kitchen ɗin ya yi bala'i kura over. Baiwar Allah haka ta gyare ko ina tsab sannan ta fito. A tunaninta ta gama zata wuce ɗakinsu, nan fa Ammie ta ce bata san wannan ba, tasata a gaba ta kuma yi zuwa bedroom na ta, sannan ta nuna mata bedroom ɗin Abba a kan idan ta gama nata ta haɗa dana Abba ta gyare tsab. Kuka Umaisha ta kara saki mai ban tausayi lokacin da idon ta ya sauka a kan cikin bedroom ɗin, tamkar ba ɗan adam ke kwana a ciki ba, sai warin datti yake, ga saman mirror da sauran drawers ɗin duk kura ya baɗe su, shi mirror ma baka iya ganin komai saboda kura ya lulluɓe shi, mamaki da al'ajabi ya hana Umaisha motsawa, dan ita bata taɓa kallon bedroom na mutun mai rai da lafiya da datti haka ba. Jikin ta har kerma yake saboda gajiya da kuma rashin lafiya da take ciki. Tana jan kafa taje ta fara tikar aikin gyaran bedroom ɗin. Shi kuma Akil yana zuwa wajen dr. Dr ya masa bayanin abin da ke faruwa, shiru ya yi yana tunanin anya kuwa Aunty za ta iya abortion da kan ta, duk da cewa sau ɗaya ya taɓa kallon ta ya ga ala'mar kamala da mutunci a tattare da ita. Ganin tunanin ba wani mafita ne yasa ya miƙe ya nemi izinin ganin Abbi, ya yi sa a dr ya ba shi izini, wucewa ya yi zuwa ɗakin da Abbi ke kwance. Har wani hasken wahala Abbi ya kara bawan Allah ya haɗu da jarabawa, yar cikinsa yau ta jefa shi cikin wahala da tashin hankali mai tsanani. Kusa da shi Akil ya zauna ya zuba masa ido yana mai jin kaunar bappan nasa kuma surukin sa har cikin ransa. Ita kuwa Aafia tana tsaye a waje, ta yi kuka har ta gode Allah. Bayan wasu kwanaki. A ɓangaren Abbi ya samu sauki sai dai ita Aunty Aafia ta ja mata bala'i domin kuwa har yanzu tana sume bata san in da kan ta yake ba, Allah ne kaɗai yasan wani irin magani Rufee ta baiwa Aafia ta zuba mu su a abinci, ta cuce su ta gama da su. Abbi ya biya kuɗi ayiwa Aunty aiki sai dai kuma ya juya mata baya, domin sai ya fi kwana biyu bai zo asibitin ba, ya ce baya son ganin fuskarta tun da har zata iya zubar masa da cikinsa. A ɓangaren Imran da Irfan kuma sun dawo dawowar da ba'a yi zato ba, dan dukkansu suna zargin gida babu lafiya, shiyasa suka dawo. Sun shiga tsananin tashin hankali jin abubuwan da suka rinƙa faruwa, musamman Imran kowa yasan yadda Imran ke bala'i kaunar Jelly tun tana da shekara biyu a duniya, ya shiga tashin hankali mara misaltuwa lokacin da ya ji zancen ɓatar ta, sosai ya dukufa neman ta a cikin garin Kano, dukkan su ba wanda ya kawo a ransa cewa Jelly na Kaduna a Kano suke yawon neman ta. Ita kuwa Aafia bata samu damar haɗuwa da Alhajin da Rufee ke son haɗa su ba, domin kuwa ranar da za su gama Exam Irfan ne ya kai ta school kuma da kan shi ya je ya ɗauko ta bayan sun gama, tun daga ranar kuma bata kara fita ba, dan ko shopping take son zuwa shi ke kai ta, dan baya son fitar ta ita kaɗai, daman shi haka yake in dai yana gida to basa fita, hakan yasa ba su haɗu da alhajin ba, Rufee bata ji daɗin hakan ba, ba haka ta so ba, sai dai ta kudiri niyar sai ta haɗasu idan suka dawo hutu. Tofa Rufee lallai a gaisheki, mu dai munyi gaba. A ɓangaren Umaisha kuma ba ƙaramin azabtuwa take wajen Ammie ba, ga shi kuma yanzu Akil baya zama a gida sosai, yau suna Kano gobe suna Kaduna dan neman Jelly, har wani mugun rama Umaisha ta yi, wadda da kallo ɗaya zaka mata kasan ba lafiya ba, sai dai Akil baya cikin kwanciyar hankali da zai gane hakan, kuma kullun ya tambaye ta meke damunta sai ta ce masa bata da lafiya ne, tana ba shi wannan amsa ne saboda tsoron Ammie, dan Ammie ta ce idan ta kuskura ta faɗa wa Akil abin da take mata to sai ta kashe ta. Shi kuma baya kawo wani tunani a ransa, dan a tunaninsa Ammie na bala'i son ta yanzu, sai dai ya manta duk wanda ya ce bai sonka da safe da daddare ya dawo ya ce yana son ka to karya yake wani abin dai naka yake so. A ɓangaren Rimsha kuwa yanzu ta zama yar Yarabawa, ta fara sabo da su, har yarensu ta fara ji, sai dai har yanzu mugun tsoron su boda Jami'u take, saboda dukkansu basu da burin da ya wuce su gan su kusa da ita, yanzu har Ayla ta fara gane abin dake faruwa. A ɓangaren Malika kuwa tun ranar da Rimsha ta mata ihu ta tsorata ta ɓace bata sake zuwa ba. Idan muka koma Washington DC kuma. An dawo da Michael gida dan ya samu sauƙi ba laifi, saboda aikin kwararun likitoci da ya samu, da kuma kyakkyawar kulawa, sai dai ciwukan nasa ba su gama bushewa ba, akwai ɗan saura, amma ba laifi. Shi ma Musharraf ya sa mi sauki sosai. Yau ta kama Wednesday kwana biyu kenan da tafiyar lion gaba ɗaya William Jacop Family suna zaune a dining room suna cin abincin rana, banda James da kuma Lion dan su har yanzu shiru ba bu wani News a kansu dukkansu. Wadannan jibga-jibgan bodyguard ɗin nasu ne ke tsaye a kansu suna zuba musu duk wani abin da za su buƙata. Cike da murna Jay ya dubi uncle herry wato daddynsu ya ce "Dad I have a wonderful surprise for you" yar murmushi uncle Herry ya yi kafin ya ce, "Really? Which kind surprise is this? That make my son happy." Kara wash baki Jay ya yi kafin ya ce, "Close your eyes daddy." Ba musu uncle Herry ya rufe ido. Miƙewa Jay ya yi ya isa bakin kofar shigowa palon ya sanya hannu ya daddanna pin na jikin kofar, zuba masa ido suka yi gaba ɗayansu suna jiran su ga wai mene ne wannan surprise ɗin. Michael da ke zaune kusa da dad ya langwaɓar da kai a kafarɗar daddy ya zubawa uncle Tga wayan nan shanyayun brown eyes ɗin nasa, yanzu sabon shagwaɓa Michael ya fito da shi, dama kuma Dr Tyrion ya ce sai sun kara hakuri da shi a yan kwanakin nan, abu kaɗan idan ka masa sai ya sa kuka, kuka kuma har da hawaye kamar ƙaramin yaro, bawan Allah. Buɗe kofar palon Jay ya yi, wata kyakkyawar matashiyar baturiya ce tsaye a bakin kofar tana goye da baby ta gabanta a irin abin goyon babyn nan, Jay sai murmushi yake yi dan yasan lion da James basa nan shi kuma Michael bai da lafiya, dama sune matsalar gidan a cewar sa. Iso ya yi wa yarinyar yana ta faman washe baki. Zubur Tga ya miƙe tsaye a zafafe, ba Tga kawai ba harta bodyguard dake tsaye a wajen sai da suka razana, dan yau sawon shekara 8 kenan suna aiki a gidan William jacop ba su taɓa kallon wata mace bayan mum ɗin su ba a gidan, yau rana tsaka rana ta farko mace a gidan William jacop bayan Josephine mum ɗin su kenan, a zahirin gaskiya har ta security dake bakin gate sun tsorata sosai da ganin mace a gidan, duk wani soja dake gidan sai da ya kallin yarinyar ya sake kallon ta domin kallon gawa suke mata, dan kuwa ko da sunan wasa basu taɓa gani mace a gidan ba, ba dan Jay shi da kan shi ya ɗauko ta a motarsa ba da ba za su bari ta shiga gidan ba. "Jay me nake gani? Who is she?!!" Tga ya faɗa cikin tsawa wadda ya sa sai da yarinyar ta tsorata. Jin maganar da Tga ya yi ne ya sanya Michael da John ɗagowa a tare, shi kuma uncle Herry sai murna yake dan ba shi da burin da ya wuce daman ƴaƴansa su samu mata, ya tsufa yana son ganin jikokinsa, daddy ma ya ji daɗi sosai, dan shi ma yana son su yi aure amma dan ya san basa son ko maganar mace hakan yasa bai taɓa gigin kawo musu zancen ba ko da wasa. Washe baki Jay ya yi yana faɗin "she's my girlfriend uncle ita nake son aura" da sauri Michael ya kai kallonsa kan babyn dake hannun ta yana son tantancewa shin ita ce uwar babyn ko kuma dai aro shi ta yi. "What girlfriend? are you mad jay? Are you heard what you said?" Tsuru tsuru da ido Jay ya yi dan bai taɓa tunanin su uncle Tga za su yi rejecting na budurwansa ba, a iya tunanin sa Triplets ne kawai basa son mata, suma saboda mum ɗin su ne yasa, kuma dan ya ga basa nan ya sa ya ce bari ya yi amfani da wannan dama ya gabatar da matar da yake son aura ga iyayensa, bai taɓa tunanin su ma basa son mata ba, shi kuma gaskiya yana son yin aure ya ga ji da zama haka. Tashin hankali. "Jay are you out of your sense?" Cewar John, ya yi maganar yana satar kallon Michael da ya yi shiru kamar wani wawa yana bin su da ido kawai, ita kan ta yarinyar ta tsorata sosai, tazo da murnanta zata zama ɗaya daga cikin family William jacop, sai kuma ga shi suna kokarin yin rejecting nata, abin ya taɓa mata zuciya sosai, dan burinta kenan ta shigo gidan, ko zata samu damar ganin lion, dan a zahirin gaskiya ba Jay take so ba, saboda lion take soyayya da Jay. Tirkashi wannan shine chakwakiya lallai yarinya kin ɗebo da zafi, kin ɗebo ruwan dafa kanki. Tga na kokarin sake yin magana uncle Herry ya dakatar da shi ta hanyar cewa "is okay general bana son sake jin wani magana a nan, Jay come in with her, i really like her, i excepted her to be your wife". Cikin sauri daddy ya ce "Yes this is true, I'm with you herry, Jay come in, our new daughter you are welcome to William jacop family". Yau sun samu zakunan gidan ba su nan suna cin karensu babu babbaka, su uncle Herry harda magana da bada umarnin, shi kuma daddy yana magana yana satar kallon Michael, still Michael bin su kawai yake da wayan nan shanyayun idon nasa, mai kama da mai jin barci, Bawan Allah bai ce komai ba, kamar ba Tiger'n daddy ba. "This baby is for who?" John ne ya jefawa Jay tambaya. Kallon babyn da kyau Jay ya yi kafin ya ce "are we not looking alike? Is my son mana" kara zaro ido waje Michael ya yi duk da cewa su turawa yin hakan a wajen su ba wani abu bane, wani lokaci ma sai sun haifi ƴaƴa uku da mace sannan suke aure a tsakanin su, amma abin da ban mamaki ba su taɓa tunanin haka daga wajen Jay ba, domin su mutane marasa yarda da mutun kuma suna kula da lafiyar su sosai, shine yaushe ma Jay yake fita da har ya je ya aikata hakan bai gaya mu su ba, bayan kuma basa ɓoyewa juna komai, abin ba karamin mamaki ya ba su ba, Jay da baby, babyn ma ba karami ba zai kai 1 year tab. Wani cool murmushi yarinyar ta saki lokacin da ta ji amsar da daddy da uncle Herry su ka bada na sun yi accepted na ta a matsayin surukuwa, ta riga Jay wucewa gaba tana ta murmushi ta nufi su dad. "Don't come here!!" wani gigitatchiyar tsawa Micheal ya daka mata wadda ya sanya ta juyawa a guje ta koma ta rungumi Jay, su kansu su daddy sun tsorata ainun da jin tsawar da Michael ya daka mata, abin da ya bawa Michael haushi wato Jay ya daɗe tare da yarinyar har ma da baby a tsakaninsu. Uncle Herry ne ya yi ta maza ya ce "Why my tiger? Why zaka ce karta zo nan?" "Shut up uncle!!" Tsawa ya dakawa uncle Herry, a fusace ya ce da yarinyar "get out!!" sanin cewa lion da James basa nan yasa Jay ya yi kokarin tirjewa Michael a kan yarinyar ba zata bar gidan ba ya yi duk abin da zai yi. Lallai yau a ke yin ta. Da yar dugu Michael ya haura sama, harara Jay ya bi shi da shi yana shafa kan budurwar tasa, a zuciyarsa yana faɗin "Ba ka da abin da za ka yi, sai dai hakuri, ba ka da aiki sai bawa mutane umarni bayan shi ba wani abin da ka iya". A fili kuma kasa-kasa ya ce "Sorry Jennifer" ya kai karshen maganar tare da raba jikinsu ya riƙo hannunta su ka karisa wajensu daddy. Daddy kam har jikinsa ya fara kerma, saboda baya son tashin hankali ko kaɗan dama daga jiya zuwa yau yana cikin rashin lafiya sosai, saboda rashin James da kuma lion. Saman chairs Jay da budurwarsa suka zauna, suma su daddy komawa suka yi suka zauna, sai tunanin Michael dad yake yi. Suna zama Michael ya fito da gudu hannunsa riƙe da pistol gun ɗin Romeo, sai ta su ya yi yana faɗin, Jennifer ta fita gidan nan ko ya harbeta ya harbe banza. A tunanin Jay Michael bai iya harbi ba dan haka sai ya ce ya harbeta ɗin su gani. Ai kuwa Michael bai yi kasa a gwiwa ba ya ɗana kunamar bindigar ya harbi Jennifer a hannunta, Allah ma yasa Jay ya yi saurin janyota jikinsa ta kauce bullet ɗin ya same ta a hannu ba dan haka ba kanta Michael ya yi niyar harba. A zafafe gaba ɗayansu suka miƙe ya yin da gaba ɗaya bodyguard dake wajen suka duka kasa gudun kar bullet ya taɓa su, ihu sosai Jennifer ta ke kamar makoshinta zai fashe saboda bala'i a zabar da take ji, ga jinin ta ya fara malala kamar famfo. Kara sai ta Jay da bindigar Michael ya yi zai harbe shi, cikin sauri Jay ya zube kasa bullet ɗin ta fita ta samu bango, ji kake dam. Kamar wanda baya a cikin hayyacinsa haka Michael ya zama, duk ya ruɗa jama'ar dake palon kuma dukkansu sun san halin Michael sun san matsalar da yake da shi, komai daidai kwakwalwarsa ke faɗa masa. Gudun cetan rayukansu suka fara, shi kuma yana binsu da gun a hannusa, yana kokarin harbinsu, sai ihu suke, Tga da yake soja ma ya gudu, dan yasan idan mutum irin Michael ya riƙe makami tofa zaman lafiyar ka shine ka gudu ka ceci ranka, idan ba haka ba, ka tsaya kace zaka nuna masa karfin dantse tofa zai maka illane kawai a banza saboda komai daidai kwakwalwarsa ke faɗa masa. Kewaye palon suka fara yi Michael ya hana su haurawa sama. Ba su ankara ba sai suka ji karar wani harbin dum, Michael ya harbi uncle Herry. Ihu suka fara yi, John kam har da cire wando ya yi wurgi da shi gefe dan wandon tana hana shi gudu, irin wandon yan gayun nan ne wanda suke sakin sa yana faɗuwa rabin bayansu a waje, to idan yana gudu sai dai ya rike wandon idan ba haka ba faɗuwa za ta yi, shine ma kawai ya cire ya yi wurgi da ita gefe guda dan ya sami damar fecewa da kyau. Gaba ɗaya palo ya hargitse Michael ya birkice mu su da gaske, ya koma mayinwacin Tiger, kokarin harbinsu kawai yake su kuma suna kokarin cetan rayukan nasu. Kamar a mafarki suka ji wannan daddaɗar fitinannen kamshi perfume ɗin, cak suka tsaya da ga su har Michael ɗin, a razane suka ɗago kai suna yan waige-waige ta ina za su ga mai wannan kamshi, dan sun san mutun ɗaya ne mai wannan perfume ɗin, shiyasa ko barci suke idan suka ji kamshin sun san waye a wajen. Tsaye yake saman bene can bakin kofar ɗakinsa ya goya hannayensa a saman faffaɗar kirjinsa, harbin gun da Michael ya yi ne ya fito da shi, jikinsa na sanye da bathrobe milk color zuwa gwuiwar sa, zara-zaran dogayen kyawawan kafafunan nasa a wajen, ga wasu dark black gashi mai bala'i kyau da tsantsi kwance a kafafun nasa har izuwa idon sahu na kafar. Ya saki dark black curly hair sannan yau bai ɗaure ba da gani kasan wani aikin yake mai muhimmanci, fuskar nan tasa kamar kullun a ɗaure tamau kamar hadari, idon nan nasa yau sun sauya launi sun rikiɗe izuwa ja, ga shi sun rage girma alamar barci bai isshe shi ba, ko kuma wani abin ya taɓa shi. Dukkan su sun yi mutuwar tsaye sun sha jinin jikinsu, duk wata halitta mai rai a palon sai da hantar cikin ta ya kaɗa. Tuni jikinsu Tga ya fara kerma dan ko a mafarki ba su taɓa zaton lion ya dawo yana cikin gidan ba, Michael ne kawai ya sani ko daddy bai sani ba saboda shigowar daren jiya ya yi kuma dawowar sirri ya yi dan wani aikin nasa da ya saka a gaba, yanzu ma da Michael ya je ɗakinsa ya ɗauko gun yana cikin dressing room nasa yana shiryawa bayan ya yi wanka kenan. Fitsari a wando Jay ya saki dan ya san yau kashinsa ya bushe, ya kawo mace a gida lion na nan kuma macen ma har da babyn sa, bayan yasan cewa lion ya hana su yin hakan, dan tun basu kai haka ba tun ba su wuce 24 years ba lokacin ma lion bai wuce matakin general ba a wajen aiki, ton tsanar mum ɗin su bai yi mu su yawa haka ba, lion ya ce duk mai son yin aure ya nemi mata ya yi aurensa amma zai bar gidan nan za'a saya masa wani gida, duk rintse duk wuya kada su nemi mace ba tare da aure ba amma shi Jay ya yi hakan a tunaninsa da wawtarsa lion ba zai sani ba, shi a nashi lissafin idan ya kawota gida kowa ya ganta tunda lion baya nan, sai ya wuce da ita church a ɗaura mu su aure, dama ya jima yana dakon ranar da lion zai fita wata ƙasa sai ya gabatar da Jennifer ga su uncle, sai dai kash rana ta kwaɓe masa. Tsuru-tsuru dukkan su suka yi, ya yin da Jennifer ta suma a wajen haka zalika shima uncle Herry ya sume. Duk da cewa Jay ya yi fitsari a tsaye bai daina matse cinyoyinsa ba kamar ba lafiya ba, jikinsa sai kerma yake tamkar wanda ya haɗu da zaki, ko da yake a cewarsu gara su haɗu da zakin a tsakiyar dokar dajin da ba komai sai mugayen namun dawa da su haɗu da Romeo sun yi laifi, domin zaki cinyewar lokaci guda zai yi mu su, shi kuma Romeo sai ya azabtar da su, ya basu wahalar da sai sun gwammaci mutuwa. Yau sun shiga tashin hankali ainun Zama dad ya yi saman sofa dan ba zai iya ci-gaba da tsayuwar ba, zai iya faɗuwa kasa, jikinsa sai kerma ya ke yi. Allah sarki baya son tashin hankali ko kaɗan Kuka Michael ya sa tare da sakin gun ɗin ta faɗi kasa, shi ma kuma zama ya yi a kasan yana kuka kamar ƙaramin yaro. Tga John duk zube gwiwowinsu a kasa suka yi jikin na ta ɓari, ga shi sun san lion baya son kalmar sorry ko kaɗan idan ma suka yi gigin ce masa sorry wlh tsab zai iya harbesu da gun su mutu, zaman lafiyar su shine su zube gwiwowinsu a kasa kawai su jira hukuncin da zai yanke mu su. Sannan kuma sun ɓata masa rai domin kuwa ga alama nan a kan fuskar sa. Lalai yau kuna tsaka mai wuya, ni na yi nan, ba zan iya ganin kilishi da tsiren da za'a yi da ku ba yau🤣🤣🤣 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode17-18🌹 Haka cike da tsoro su ma suka wuce nasu ɗakin, bayan Kausar ta tashi Iya daga barci, Iya ce ta kulle kofar falon da key da kuma sakata, sannan ta wuce ɗakinta ita ma. Rimsha dai ta tsorata sosai, gani take kamar za su zo su kama ta, shi yasa da suka shiga ɗaki ta riga su hayewa gado, ta tafi can karshen gadon ta kwanta ta manne da bango, Ayla ce ta kwanta kusa da ita, sai Kausar a karshen gadon. Suna kwanciya ba jimawa Kausar da Ayla suka yi barci, ita kuma Rimsha ta jima idonta a rintse amma ba ta yi barci ba har sai da dare ya tsala sosai tana ta tunani rayuwa, baiwar Allah har kusan asuba, sannan barci ya yi awon gaba da ita. Asuba ta gari. 💞💞Spain💞💞 Helicopters guda shida aka tasa tun kafin lion ya iso, sai kewaye cikin *Madrid* wato babban birnin Spain suke. *Madrid* shi ne baban birnin Spain, birni ne mai girman gaske wanda a kalla Population nasu ya kai 3.3 million, birnin ya tsaru iya tsaruwa, ga dogayen gine-gine Turawan masu kyau da kawatuwa, ta ko'ina tsaf-tsaf, suna da wuraren shakatawa da yawon buɗe ido, ga wajen wasanni kala-kala, shimfiɗaɗɗun tituna masu kyau wadda suka ratsa ta cikin unguwanni lungu da saƙo, ga kuma manya-manyan gumakai na manyan shuwagabannin da suka suɗe, an yi guma kan su a tsakiyar garin, suna da manya-manyan teku wato koguna, masu ɗauke da ruwa mai kyau da karawa garin kyau, sannan akoi gumakan da irin na mace a keken doki, ko namiji ya ɗaga igwa zai sake wuta. Tsayawa zayyana muku yadda Madrid take ba zai yiwu ba, dan sai ya cinye mana wannan page ɗin ba mu kammala ba. Karfe 12 na rana daidai, The General of the Army jet ya yi landing a *Madrid-Barajas International Airport,* har lokacin da suka yi landing helicopters suna sama suna shawagi, dan tabbatar da tsaro, kuma ba za su sauko ba yau a sama za su wuni har sai lion ya bar kasar. Airport ɗin cike take makil da dubban sojojin Spain, dan tuni sun san da zuwan lion, sun karɓi umarnin daga sama, a kan su tarbo shi daga airport su tabbatar sun kai shi masauki lafiya, hakan kuma ya samo asali ne sakamakon His Excellency mr President kakan su lion ya kira President na Spain ya sanar da shi zuwan jikan nasa, hakan yasa a ka kara tsananta tsaro sosai, ko'ina a cikin birnin sojoji ke yawo, duk ta in da ka juya sai ka ga sojoji, a kan titi ne, lunguna da sakon birnin ne, ta ko'ina. Ko da jiragen suka sauka lion bai fito daga cikin jet ɗinsa ba, yana zaune tamkar bai san sun sauƙa ba. Kasancewar sojojin Spain ba su san halinsa ba, labarinsa kawai suke ji, hakan sai ya dame su, rashin fitowar na shi ya dame su sosai, gani suke kamar ba lafiya ba, suna son tinkarar jet ɗin nasa dan su duba ko lafiya, amma babu dama domin jibga-jibgan sojojin Washington DC wato sojojin lion da suka zo a sauran jiragen sun kewaye jet ɗin, hannayen su riƙe da manya-manyan bindigu, hakan ya sa sojojin Spain ba su yi gigin tinkarar jet ɗin ba, dan sojojin Usa ba wasa ba, ba su da wasa a kan aikinsu, manya-manyan kasashen duniya tsoron su suke ji, saboda idan suka tinkari abu tofa basa juya baya komai wuya komai daɗi har sai sun cin ma abin da suke so, basu da imani ko kaɗan. Wasu dankara-dankaran motonci masu numfashi His excellency president ɗin Spain ya turo su ɗauki lion. Motocin sojoji guda 6 sababbi gagal, sai kyalli suke, sai kuma wata dankareriyar mota wadda da ka gani ka san na musamman aka tanadawa lion, motar ta haɗu sosai kirar Bugatti cantodieci fara tas sai kyalli motar take kamar yanzu a ka ɓallota gal-gal. Good 40mins lion ya ɗauka zaune cikin Jet ɗinsa ya jingina kai da jikin sofa da yake zaune, dara daran idon sa a lumtse sai faman furzar da iska mai zafi yake daga bakinsa. Sojojinsa dake tsaye a kansa, sai faman satar kallon sa suke, dan su kansu burge su ogan nasu yake, Allah ya masa wani irin sihirtaccen kyau, ga bala'i kwarjinin da farin jini masifa, duk in da zai shiga, za su so shi sosai amma kuma za su ji tsoron sa kamar su mutu, dan fusataccen fuskar sa ma kawai abun tsoro ne. Yar kara wayarsa dake gefen sa ya yi, alamar shigowar sako, sai da ya ɗauki 5mins sannan slowly ya waro idanuwansa tare da ɗaukar wayar da system nasa ya miƙe tsaye. Cikin sauri sojojinsa dake tsaye a kansa, suka ɗaga hannu suka sara masa. Wucewa ya yi ya nufi waje. Yana sako kafarsa wajen jet ɗin, sojojinsa da ke kewaye da jet ɗin suka ɗaga manya-manyan bindigun hannunsu suka fara sakin wuta a sama, gaba ɗaya karan harbi ya kewaye ko ina, nan take masu ɗaukan shi a hoto suka fara ɗaukan shi. Wucewa ya yi ya nufi wayan nan dankara-dankaran motonci da His Excellency ya turo, yana taku cike da izza da cikan gwarzon ɗa namiji. Su dai sojojin Spain sun zama yan kallo, dan abin ya fi karfinsu duk yadda suke tunanin lion ashe ya wuce nan ba su sani ba, haka zalika yadda suke tunanin sojojin USA sun wuce nan. Ji kake dip-dip-dip a guje direbansa na yanzu ya nufi motar da a ka tana da domin shi , jikin sa har kerma yake wajen buɗe kofar motar, dan lion ya kusa isowa wajen, idan kuma ya iso bai buɗe masa kofar motar ba to akwai matsala, shiyasa jikinsa sai ɓari yake wajen buɗe kofar. Cikin zafin nama yake taku irin na jaruman maza har ya isa wajen motar, bai wani tsaya ɓata lokaci ba ya shige cikin motar kawai, yana shiga driver sa ya ɗaga hannu ya sara masa sannan ya rufe kofar motar, gaba ɗaya sojojin dake wajen har sojin Spain sai da suka ɗaga hannu suka sara masa, sannan sojojin sa suka nufi motoncin da a ka tana da musu, a guje suka haye saman bayan motoncin. Cikin zafin nama driver sa ya shiga gidan gaba na motar. Kamar yadda suka saba a Washington DC, a nan ma haka suka yi a jere suka tashi motoncin suka bar Airport ɗin da gudun gaske, tun kafin su fita Airport suka saki jiniya. Motoncin suna fita sojojin Spain suka yi saurin shiga nasu motoncin suka rufa musu baya. Kai tsaye gidan His Excellency suka wuce, dan shi Romeo baya son kama hotel, ya fi son zaman gida, idan ka gan shi a hotel to dole ce ta sanya. Kun san dai yadda gidan Turawa yake, mu samman gidan President kun san yadda gine-gine yake, ba sai mun tsaya nan ba. Gaba ɗaya gidan His Excellency President ɗin Spain a cike yake da sojojin Spain da yan sanda, ga kuma manya-manyan baki masu faɗa a ji a kasar, duk sun hallara a gidan, dan tarban jika ga His Excellency Mr President of USA. A tunaninsu lion mutun ne mai sauƙin kai, labarinsa kawai suke ji ba su taɓa zama da shi ko ganin shi ba. Yau sun ga asalin kalar halinsa, dan kuwa yana fitowa daga cikin motoncin nan ya wuce cikin gida, duk wayan nan manya-manyan baki dake tsaye a wajen domin shi bai kula kowa ba, ko kallo ma ba su isshe shi ba ya sa kai ya wuce abinsa. Babbar magana. Sun sha mamaki wasu daga cikinsu kuma sun ji haushi sosai, a ganinsu lion ya wulakanta su ya musu cin mutunci. Tuni Lion ya san in da a ka tana da masa, domin sai da ya yi bincike a wajen kafin ya zo, sai da ya sauƙe sojojinsa sama da guda 15 wadda suka riga shi zuwa, suka zo suka bincike wajen tsaf, shi ya sa yana fita mota ya wuce wajen. Jama'ar da suka zo domin shi, cike da jin haushin abin da ya musu suka koma cikin fadan His Excellency. Nan su ka shaida masa abin da lion ya mu su, hakuri His Excellency ya ba su tare da faɗa mu su haka halin lion yake, baya da yawan magana kuma baya son hayaniya, yanzu ma idan suka takura masa da hayaniya tofa barin gidan zai yi, idan kuma ya bar gidan nan, za su samu matsala da His Excellency mr President na USA, zai ce sun yi wa jikansa wulakanci, ba zai taɓa yi musu uzuri ba. Dole ba dan sun so ba, haka suka ja bakin su suka yi shiru dan kar su yi wani magana ya zamo musu matsala, dan sun san halin His Excellency Mr President of USA a kan family sa, kuma sun jin halin yaran William Jacop, suna ji a News, yanzu a kan haka lion zai iya sawa su rasa mukamansu ko rayuwar su ma baki ɗaya, dan sun san halin gwamnatin USA ba wasa. A ɓangaren lion kuwa, yana shiga part na musamman da a ka ware domin shi, sai ya kara ɗaure fuska sosai da sosai, ya fito daga wajen, a cewar sa wajen yayi datti kuma abubuwan ciki sun masa local. A zahirin gaskiya ba laifi komai dake cikin wajen sabbi ne kal-kal a ledansu a ka fito da su, sannan an zuba komai da ɗan adam zai buƙata, kuma an share wajen sosai da sosai, shi ɗin ne dai ba'a iya masa, baka taɓa gane gabansa bare bayansa, yana da bala'i tsabta, ko datti kaɗan ya gani a waje to sai ya haɗe wajen gaba ɗaya ya ce akwai kazanta ba zai zauna ba, yanzu ma abin da ya faru kenan, kura kaɗan ya gani wajen mirror shikenan ya ce wajen akwai datti, sannan kuma bayan haka furnitures da ke wajen ba su masa ba. Yana fita sojojin sa suka take masa baya, kai tsaye motoncin da suka kawo shi ya nufa. Da gudu wani soja ya zo ya buɗe masa motar gidan baya, ya shiga ya zauna. Cikin zafin nama sojojinsa suka haye saman bayan nasu motoncin, kusan a tare suka yi wa motoncin key. Jin tashin motoncin ya sanya His Excellency fitowa daga fadarsa. A hanzarce ya iso wajen yana tambayar lion ko lafiya, ina zai je. Shiru lion ya yi na yan mintoci kafin ya sanar da shi wajen da suka tana da masa bai masa ba, sosai His excellency ya ji ba daɗi tare da yiwa lion alkawarin yanzu za'a canza komai zuwa yadda yake buƙata ya fito ya koma cikin fadar shugaban kasar ya zauna. Shiru ya yi na ɗan lokacin, kafin ya ba wa sojojinsa umarni a kan su tashi motonci su tafi, dan shi idan ya yi magana baya canzawa komai zai faru, sai dai ya faru, kai ko tunani ya yi a zuciyarsa zai aiwatar da wani abin to fa ba zai canza wannan tunani ba kome za'ayi. _Kai jama'a wannan iri hali na Romeo ba mai iya shi sai daddynsu shi ya san halin kayansa, wai ta ko'ina ba sauƙi, gaskiya Lion ba dama._ His Excellency bai ji daɗi ba, domin ya san kakansu lion ba zai fahimce shi ba, kuma ba zai masa uzuri ba, zai ce da gangan ya wulakanta masa jika, sosai ya shiga duniyar tunanin ya zai yi da His Excellency, ya zai yi His Excellency ya yarda cewa shi bai wulakanta Lion ba, zancen zuci ya fara "To ma ni na isa in wulakanta Lion ne, mutumin da muke neman taimakonsa idan abubuwa sun fi gaban tunaninmu, dole a matsayinmu na tsofaffi sai mun nemi agajin sabon jini, dan zaren ba kalar yadin ba ne, kwakwalwar ma ba ɗaya ba kuma ko da gwaji ma ba za'a gwada ba, ni yanzu ya zan yi?" Haka ya tsaya sai zancen zuci yake, shi kuma Lion ya wuce ya bar gidan. Yana fita su ka nufi *Westin Palace Madrid Hotel*, a karon farko da Lion ya fara sauƙa a hotel idan ya je wata kasar, ba ya son zaman hotel amma ya zamar masa dole ne ba yadda zai yi. Katafaren Hotel ne mai girman gaske, wanda yake tsakiyar teku, a cikin ruwa Hotel ɗin yake, amma yana da shinfiɗaɗiyar hanya da zata fito da kai kamar gada haka, sannan Hotel ɗin yana da tsaro sosai, kasan cewar yana tsakiyar ruwa mai ɗauke da manya-manyan halittu irin su shak da sauran su. Duk da tsaron da wannan Hotel ɗin yake da shi, sai da jama'ar cikin ta su ka san da Lion ya shiga cikinta, saboda dubbanin sojoji da su ka kewayeta, ta ko'ina, hannayensu riƙe da manya-manyan bindigu masu aiki ba saɓa saiti. A zahirin gaskiya ba kowa ke iya kama wannan hotel ɗin ba, domin hotel ne na manya-manyan mutane, duk kuma wanda ya sauƙa a hotel ɗin ya kwana, yana barin hotel ɗin masu hotel ɗin za su kwashe komai kama daga gadaje da sauransu, duk za su kwashe su zuba sabbi. Ɗakin da Lion ya kama ba a magana ɗakin ya kawatu iya kawatuwa ya haɗu sosai, kana zaune daga cikin ɗakin kana kallon daga mahangar glass da ke a matsayin bangon gefe guda, zaka rinƙa kallon yadda ruwa ke juyi yana gudana ga wasu kananan kifaye suna tsalle saman ruwa, suna sake komawa, tekun na da girman sosai, girma da ba ka iya ganin karshensa, abin gwanin ban sha'awa ga masoya, shi kuwa Lion da bai san mene ne soyayya ba, ba shi da wani shauƙi, ko kallon wajen ma bai yi ba bare ya burge shi. Driver sa ne ya kawo masa trolley sa ya ajiye masa a wajen da suka tanada dan ajiye trolley sannna ya fice daga ɗakin Wanka ya fara yi, sannan ya shirya cikin kananan kaya, wando three quarter da riga marar nauyi duka farare tas, ya yi kyau sosai da sosai kamar shi ya yi kansa, dan shi a ko da yaushe shine ya ke yiwa kaya kyau ba kaya ke masa kyau ba, ya saki dark black curly hair nan nasa ba tare da ya ɗaure ba, sai tashin fitinannen kamshi ya ke, ya haye saman lallausan bed na Hotel ɗin tare da ɗaukan system da wayarsa ya fara aiki, yayin da jibga-jibgan sojojin ke zagaye da ɗakin nasa riƙe da manyan bindigu, dan tabbatar da tsaro. _Wai Romeo wannan aiki haka ai sai kai ɗin mu bari mu koma Nigeria watakila kafin mu dawo abubuwa sun setu a nan._ 💞💞Nigeria 💞💞 💞💞GIDAN ABBI💞💞 Sai washegari Abbi ya iya gane kansa, a nan ne kuma yake tambayar ina Aunty da Aafia? Mai aikin da ya kawo ke sanar masa da suna asibiti, ya sha ruwan mamaki sosai jin hakan, dan haka sai ya koma bedroom nasa, ya yi wanka ya shirya ya fito dan zuwa hospital ɗin, ya yin da shi kuma daddy Jelly har lokacin yana can bedroom nasa yana barcin wahala bawan Allah, ya fi Abbi jin jiki sosai da yake daman ba koshin lafiya ke gare shi ba. Lokacin da Abbi ya isa asibiti da motar Irfan, dan already daman ya san asibitin da suke zuwa, shiyasa ya wuce kai tsaye. Ya kuwa isa a kan gaba domin ya isa lokacin da Dr ke cewa Aafia yana son ganin wani na Aunty ko baban ta ko kuma babban yayan ta, ko mijinta, dan haka Abbi na zuwa ya ce ga shi nan. Wucewa office Dr ya yi ya ce Abbi ya biyo shi. Haka kuwa a kayi, da suka shiga office sosai Dr ya masa bayanin abortion ɗin da Aunty ta yi ya haifar mata da matsala sosai a mahaifarta, domin ta yi shine ba bisa ka ida ba, so yanzu sai an mata aiki, kuma ko anyi aikin ma ba lallai ta sake iya ɗaukan wani ciki ba. Tashin hankali a zabure Abbi ya miƙe tsaye bakinsa na maimaita kalmar abortion, lokaci guda zufa ya fara wanke masa fuska, sabon murɗawan ciwo cikinsa ya fara yi masa, kunnuwansa sun ki yarda da jin cewa Aunty ce da kanta ta yi abortion ji yake kamar a mafarki, ya kasa gaba ya kasa baya, komai ya tsaya masa cak, tunani yake "Yanzu da ma Halima za ta iya kashe min jinina? Da ma Halima ba ta kaunar kyautar cikin da Allah ya ba mu? Da ma Halima ba ta so na? Da ma duk ilimin addini Halima na banza ne? Kullun idan muka zauna wannan nasiha mai ratsa jiki da take mini ashe duka ta karya ce? Why Halima? Me ya sa za ki zama Musa a baki, Fir'auna a zuci? Me yasa za ki cutar da ni? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun". Dafe kansa da ke masa barazanar tarwatsewa ya yi, yana ganin yadda cikin office ɗin Dr ke juya masa kamar fanka. Bawan Allah da ma ba ƙoshin lafiya gare shi ba Aafia ta tagayyara shi ta gama da rayuwarsa. Dr na kokarin magana sai kawai ya ga Abbi ya zube kasa sumamme, a sukwane Dr ya yi kansa yana faɗin innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Ganin ya sume ya sa ya fito da sauri ya kira nurses suka zo suka ɗauki Abbi a saman bed na marasa lafiya, suka wuce da shi ɗakin da Aunty ke kwance. Ba karamin tashin hankali Aafia ta shiga ba ganin Abbinta a sume, ta tsorata sosai tana son jin me ya sumar da shi. Cikin sauri ta ciro wayar ta ta fara kiran layin Irfan tana yi tana kuka hawaye bibbiyu. Bugu ɗaya Irfan ya ɗauki kiran, a ruɗe ta ke magana "Hello yaya Irfan, Abbi ya suma Aunty ma haka ita kam kamar ta mutu ban san ya zan yi ba" daga ɗayan ɓangaren Irfan ya ce "Aafia ki nitsu ki faɗa min meke faruwa!" Muryarta sai kerma yake tana ta faman haɗe words ta kasa nitsuwa ta ce "Yaya Irfan jiya ne muna cin abinci da daddare sai Abbi da Bappa Maik su ka tashi zuwa bedroom nasu, palon ya rage daga ni sai Aunty, ita ma daga baya ta miƙe zata tafi sai ta faɗi kasa jini ya fara zuba mata, shine na gudu ne je zan faɗa wa Abbi sai naga yana toilet shi ne na ɗauko ta muka zo asibiti, sai yau shi kuma Abbi yazo dr ya kira shi dan su yi magana yana zuwa wajen Dr ya suma shima" dafe kai Irfan ya yi dan Aafia ta sake sa shi a duhu, ban da shine shine ba abin da take ta labka masa, ta ruɗe sosai. "Ina bappa Maik ɗin?". Cikin sauri ta ce, "Abbi shi kaɗai ya zo banda Bappa Maik." Shiru Irfan ya ɗan yi kafin ya ce, "Tom ina zuwa." Bai jira amsarta ba ya katse kiran. Zarya ta fara yi a wajen tana kuka, duk wannan abin da ya faru bai sanya Aafia ta yi dana sanin zuba musu magani a abincin da ta yi ba, dan aikin ba nata bane na Rufee ce, sai dai ta ji babu daɗin ganin su a halin da suke ciki. Sai safa da marwa take a wajen har Akil ya zo hospital ɗin ba tare da sanin taba, sai ji ta yi yana faɗin "Yaya Irfan ya kirani a waya a kan bappa yana hospital, ina yake? Me kuma yake damun shi?" A zabure ta ɗago kai dan ba ta san lokacin da ya zo ba, maganarsa kawai ta ji. Cikin ruɗu da tashin hankali shi ma ta fara ba shi labarin abin da ya faru, jikin ta har wani ɓari yake, da alama ta tsorata sosai. Da yake shi Akil ɗan baiwa ne akwai kwakwalwa sai ya gane me take nufi, dan haka sai ya ce ina ne office ɗin dr, ba musu ta nuna mi shi, wucewa ya yi ya bar ta nan tsaye. Ya yin da ita kuma Umaisha ke can tana gwagwarmaya da Ammie, dan Akil na fita Ammie ta zo ta tasata a gaba suka wuce kitchen dan ta je ta karisa aikin da ta fara. Tana aiki tana kuka hawaye sharɓa-sharɓa, ga shi tana aikin Ammie na aiko mata da zagi yar matsiyata da sauransu, abin ba ƙaramin ciwo ya ke mata a zuciyarta ba. Haka ta jure ta kammala aikin kitchen nan tas, amma fa tasha bakar wahala ba kaɗan ba, dan ita kanta har wani baki ta yi na wuya, sai haɗa bakin zufar kuran kitchen da ya hau jikin ta take, kasan cewar ba'a wani amfani da kitchen ɗin sai dai a ajiye ragowar abinci ko fruits, hakan yasa kitchen ɗin ya yi bala'i kura over. Baiwar Allah haka ta gyare ko ina tsab sannan ta fito. A tunaninta ta gama zata wuce ɗakinsu, nan fa Ammie ta ce bata san wannan ba, tasata a gaba ta kuma yi zuwa bedroom na ta, sannan ta nuna mata bedroom ɗin Abba a kan idan ta gama nata ta haɗa dana Abba ta gyare tsab. Kuka Umaisha ta kara saki mai ban tausayi lokacin da idon ta ya sauka a kan cikin bedroom ɗin, tamkar ba ɗan adam ke kwana a ciki ba, sai warin datti yake, ga saman mirror da sauran drawers ɗin duk kura ya baɗe su, shi mirror ma baka iya ganin komai saboda kura ya lulluɓe shi, mamaki da al'ajabi ya hana Umaisha motsawa, dan ita bata taɓa kallon bedroom na mutun mai rai da lafiya da datti haka ba. Jikin ta har kerma yake saboda gajiya da kuma rashin lafiya da take ciki. Tana jan kafa taje ta fara tikar aikin gyaran bedroom ɗin. Shi kuma Akil yana zuwa wajen dr. Dr ya masa bayanin abin da ke faruwa, shiru ya yi yana tunanin anya kuwa Aunty za ta iya abortion da kan ta, duk da cewa sau ɗaya ya taɓa kallon ta ya ga ala'mar kamala da mutunci a tattare da ita. Ganin tunanin ba wani mafita ne yasa ya miƙe ya nemi izinin ganin Abbi, ya yi sa a dr ya ba shi izini, wucewa ya yi zuwa ɗakin da Abbi ke kwance. Har wani hasken wahala Abbi ya kara bawan Allah ya haɗu da jarabawa, yar cikinsa yau ta jefa shi cikin wahala da tashin hankali mai tsanani. Kusa da shi Akil ya zauna ya zuba masa ido yana mai jin kaunar bappan nasa kuma surukin sa har cikin ransa. Ita kuwa Aafia tana tsaye a waje, ta yi kuka har ta gode Allah. Bayan wasu kwanaki. A ɓangaren Abbi ya samu sauki sai dai ita Aunty Aafia ta ja mata bala'i domin kuwa har yanzu tana sume bata san in da kan ta yake ba, Allah ne kaɗai yasan wani irin magani Rufee ta baiwa Aafia ta zuba mu su a abinci, ta cuce su ta gama da su. Abbi ya biya kuɗi ayiwa Aunty aiki sai dai kuma ya juya mata baya, domin sai ya fi kwana biyu bai zo asibitin ba, ya ce baya son ganin fuskarta tun da har zata iya zubar masa da cikinsa. A ɓangaren Imran da Irfan kuma sun dawo dawowar da ba'a yi zato ba, dan dukkansu suna zargin gida babu lafiya, shiyasa suka dawo. Sun shiga tsananin tashin hankali jin abubuwan da suka rinƙa faruwa, musamman Imran kowa yasan yadda Imran ke bala'i kaunar Jelly tun tana da shekara biyu a duniya, ya shiga tashin hankali mara misaltuwa lokacin da ya ji zancen ɓatar ta, sosai ya dukufa neman ta a cikin garin Kano, dukkan su ba wanda ya kawo a ransa cewa Jelly na Kaduna a Kano suke yawon neman ta. Ita kuwa Aafia bata samu damar haɗuwa da Alhajin da Rufee ke son haɗa su ba, domin kuwa ranar da za su gama Exam Irfan ne ya kai ta school kuma da kan shi ya je ya ɗauko ta bayan sun gama, tun daga ranar kuma bata kara fita ba, dan ko shopping take son zuwa shi ke kai ta, dan baya son fitar ta ita kaɗai, daman shi haka yake in dai yana gida to basa fita, hakan yasa ba su haɗu da alhajin ba, Rufee bata ji daɗin hakan ba, ba haka ta so ba, sai dai ta kudiri niyar sai ta haɗasu idan suka dawo hutu. Tofa Rufee lallai a gaisheki, mu dai munyi gaba. A ɓangaren Umaisha kuma ba ƙaramin azabtuwa take wajen Ammie ba, ga shi kuma yanzu Akil baya zama a gida sosai, yau suna Kano gobe suna Kaduna dan neman Jelly, har wani mugun rama Umaisha ta yi, wadda da kallo ɗaya zaka mata kasan ba lafiya ba, sai dai Akil baya cikin kwanciyar hankali da zai gane hakan, kuma kullun ya tambaye ta meke damunta sai ta ce masa bata da lafiya ne, tana ba shi wannan amsa ne saboda tsoron Ammie, dan Ammie ta ce idan ta kuskura ta faɗa wa Akil abin da take mata to sai ta kashe ta. Shi kuma baya kawo wani tunani a ransa, dan a tunaninsa Ammie na bala'i son ta yanzu, sai dai ya manta duk wanda ya ce bai sonka da safe da daddare ya dawo ya ce yana son ka to karya yake wani abin dai naka yake so. A ɓangaren Rimsha kuwa yanzu ta zama yar Yarabawa, ta fara sabo da su, har yarensu ta fara ji, sai dai har yanzu mugun tsoron su boda Jami'u take, saboda dukkansu basu da burin da ya wuce su gan su kusa da ita, yanzu har Ayla ta fara gane abin dake faruwa. A ɓangaren Malika kuwa tun ranar da Rimsha ta mata ihu ta tsorata ta ɓace bata sake zuwa ba. Idan muka koma Washington DC kuma. An dawo da Michael gida dan ya samu sauƙi ba laifi, saboda aikin kwararun likitoci da ya samu, da kuma kyakkyawar kulawa, sai dai ciwukan nasa ba su gama bushewa ba, akwai ɗan saura, amma ba laifi. Shi ma Musharraf ya sa mi sauki sosai. Yau ta kama Wednesday kwana biyu kenan da tafiyar lion gaba ɗaya William Jacop Family suna zaune a dining room suna cin abincin rana, banda James da kuma Lion dan su har yanzu shiru ba bu wani News a kansu dukkansu. Wadannan jibga-jibgan bodyguard ɗin nasu ne ke tsaye a kansu suna zuba musu duk wani abin da za su buƙata. Cike da murna Jay ya dubi uncle herry wato daddynsu ya ce "Dad I have a wonderful surprise for you" yar murmushi uncle Herry ya yi kafin ya ce, "Really? Which kind surprise is this? That make my son happy." Kara wash baki Jay ya yi kafin ya ce, "Close your eyes daddy." Ba musu uncle Herry ya rufe ido. Miƙewa Jay ya yi ya isa bakin kofar shigowa palon ya sanya hannu ya daddanna pin na jikin kofar, zuba masa ido suka yi gaba ɗayansu suna jiran su ga wai mene ne wannan surprise ɗin. Michael da ke zaune kusa da dad ya langwaɓar da kai a kafarɗar daddy ya zubawa uncle Tga wayan nan shanyayun brown eyes ɗin nasa, yanzu sabon shagwaɓa Michael ya fito da shi, dama kuma Dr Tyrion ya ce sai sun kara hakuri da shi a yan kwanakin nan, abu kaɗan idan ka masa sai ya sa kuka, kuka kuma har da hawaye kamar ƙaramin yaro, bawan Allah. Buɗe kofar palon Jay ya yi, wata kyakkyawar matashiyar baturiya ce tsaye a bakin kofar tana goye da baby ta gabanta a irin abin goyon babyn nan, Jay sai murmushi yake yi dan yasan lion da James basa nan shi kuma Michael bai da lafiya, dama sune matsalar gidan a cewar sa. Iso ya yi wa yarinyar yana ta faman washe baki. Zubur Tga ya miƙe tsaye a zafafe, ba Tga kawai ba harta bodyguard dake tsaye a wajen sai da suka razana, dan yau sawon shekara 8 kenan suna aiki a gidan William jacop ba su taɓa kallon wata mace bayan mum ɗin su ba a gidan, yau rana tsaka rana ta farko mace a gidan William jacop bayan Josephine mum ɗin su kenan, a zahirin gaskiya har ta security dake bakin gate sun tsorata sosai da ganin mace a gidan, duk wani soja dake gidan sai da ya kallin yarinyar ya sake kallon ta domin kallon gawa suke mata, dan kuwa ko da sunan wasa basu taɓa gani mace a gidan ba, ba dan Jay shi da kan shi ya ɗauko ta a motarsa ba da ba za su bari ta shiga gidan ba. "Jay me nake gani? Who is she?!!" Tga ya faɗa cikin tsawa wadda ya sa sai da yarinyar ta tsorata. Jin maganar da Tga ya yi ne ya sanya Michael da John ɗagowa a tare, shi kuma uncle Herry sai murna yake dan ba shi da burin da ya wuce daman ƴaƴansa su samu mata, ya tsufa yana son ganin jikokinsa, daddy ma ya ji daɗi sosai, dan shi ma yana son su yi aure amma dan ya san basa son ko maganar mace hakan yasa bai taɓa gigin kawo musu zancen ba ko da wasa. Washe baki Jay ya yi yana faɗin "she's my girlfriend uncle ita nake son aura" da sauri Michael ya kai kallonsa kan babyn dake hannun ta yana son tantancewa shin ita ce uwar babyn ko kuma dai aro shi ta yi. "What girlfriend? are you mad jay? Are you heard what you said?" Tsuru tsuru da ido Jay ya yi dan bai taɓa tunanin su uncle Tga za su yi rejecting na budurwansa ba, a iya tunanin sa Triplets ne kawai basa son mata, suma saboda mum ɗin su ne yasa, kuma dan ya ga basa nan ya sa ya ce bari ya yi amfani da wannan dama ya gabatar da matar da yake son aura ga iyayensa, bai taɓa tunanin su ma basa son mata ba, shi kuma gaskiya yana son yin aure ya ga ji da zama haka. Tashin hankali. "Jay are you out of your sense?" Cewar John, ya yi maganar yana satar kallon Michael da ya yi shiru kamar wani wawa yana bin su da ido kawai, ita kan ta yarinyar ta tsorata sosai, tazo da murnanta zata zama ɗaya daga cikin family William jacop, sai kuma ga shi suna kokarin yin rejecting nata, abin ya taɓa mata zuciya sosai, dan burinta kenan ta shigo gidan, ko zata samu damar ganin lion, dan a zahirin gaskiya ba Jay take so ba, saboda lion take soyayya da Jay. Tirkashi wannan shine chakwakiya lallai yarinya kin ɗebo da zafi, kin ɗebo ruwan dafa kanki. Tga na kokarin sake yin magana uncle Herry ya dakatar da shi ta hanyar cewa "is okay general bana son sake jin wani magana a nan, Jay come in with her, i really like her, i excepted her to be your wife". Cikin sauri daddy ya ce "Yes this is true, I'm with you herry, Jay come in, our new daughter you are welcome to William jacop family". Yau sun samu zakunan gidan ba su nan suna cin karensu babu babbaka, su uncle Herry harda magana da bada umarnin, shi kuma daddy yana magana yana satar kallon Michael, still Michael bin su kawai yake da wayan nan shanyayun idon nasa, mai kama da mai jin barci, Bawan Allah bai ce komai ba, kamar ba Tiger'n daddy ba. "This baby is for who?" John ne ya jefawa Jay tambaya. Kallon babyn da kyau Jay ya yi kafin ya ce "are we not looking alike? Is my son mana" kara zaro ido waje Michael ya yi duk da cewa su turawa yin hakan a wajen su ba wani abu bane, wani lokaci ma sai sun haifi ƴaƴa uku da mace sannan suke aure a tsakanin su, amma abin da ban mamaki ba su taɓa tunanin haka daga wajen Jay ba, domin su mutane marasa yarda da mutun kuma suna kula da lafiyar su sosai, shine yaushe ma Jay yake fita da har ya je ya aikata hakan bai gaya mu su ba, bayan kuma basa ɓoyewa juna komai, abin ba karamin mamaki ya ba su ba, Jay da baby, babyn ma ba karami ba zai kai 1 year tab. Wani cool murmushi yarinyar ta saki lokacin da ta ji amsar da daddy da uncle Herry su ka bada na sun yi accepted na ta a matsayin surukuwa, ta riga Jay wucewa gaba tana ta murmushi ta nufi su dad. "Don't come here!!" wani gigitatchiyar tsawa Micheal ya daka mata wadda ya sanya ta juyawa a guje ta koma ta rungumi Jay, su kansu su daddy sun tsorata ainun da jin tsawar da Michael ya daka mata, abin da ya bawa Michael haushi wato Jay ya daɗe tare da yarinyar har ma da baby a tsakaninsu. Uncle Herry ne ya yi ta maza ya ce "Why my tiger? Why zaka ce karta zo nan?" "Shut up uncle!!" Tsawa ya dakawa uncle Herry, a fusace ya ce da yarinyar "get out!!" sanin cewa lion da James basa nan yasa Jay ya yi kokarin tirjewa Michael a kan yarinyar ba zata bar gidan ba ya yi duk abin da zai yi. Lallai yau a ke yin ta. Da yar dugu Michael ya haura sama, harara Jay ya bi shi da shi yana shafa kan budurwar tasa, a zuciyarsa yana faɗin "Ba ka da abin da za ka yi, sai dai hakuri, ba ka da aiki sai bawa mutane umarni bayan shi ba wani abin da ka iya". A fili kuma kasa-kasa ya ce "Sorry Jennifer" ya kai karshen maganar tare da raba jikinsu ya riƙo hannunta su ka karisa wajensu daddy. Daddy kam har jikinsa ya fara kerma, saboda baya son tashin hankali ko kaɗan dama daga jiya zuwa yau yana cikin rashin lafiya sosai, saboda rashin James da kuma lion. Saman chairs Jay da budurwarsa suka zauna, suma su daddy komawa suka yi suka zauna, sai tunanin Michael dad yake yi. Suna zama Michael ya fito da gudu hannunsa riƙe da pistol gun ɗin Romeo, sai ta su ya yi yana faɗin, Jennifer ta fita gidan nan ko ya harbeta ya harbe banza. A tunanin Jay Michael bai iya harbi ba dan haka sai ya ce ya harbeta ɗin su gani. Ai kuwa Michael bai yi kasa a gwiwa ba ya ɗana kunamar bindigar ya harbi Jennifer a hannunta, Allah ma yasa Jay ya yi saurin janyota jikinsa ta kauce bullet ɗin ya same ta a hannu ba dan haka ba kanta Michael ya yi niyar harba. A zafafe gaba ɗayansu suka miƙe ya yin da gaba ɗaya bodyguard dake wajen suka duka kasa gudun kar bullet ya taɓa su, ihu sosai Jennifer ta ke kamar makoshinta zai fashe saboda bala'i a zabar da take ji, ga jinin ta ya fara malala kamar famfo. Kara sai ta Jay da bindigar Michael ya yi zai harbe shi, cikin sauri Jay ya zube kasa bullet ɗin ta fita ta samu bango, ji kake dam. Kamar wanda baya a cikin hayyacinsa haka Michael ya zama, duk ya ruɗa jama'ar dake palon kuma dukkansu sun san halin Michael sun san matsalar da yake da shi, komai daidai kwakwalwarsa ke faɗa masa. Gudun cetan rayukansu suka fara, shi kuma yana binsu da gun a hannusa, yana kokarin harbinsu, sai ihu suke, Tga da yake soja ma ya gudu, dan yasan idan mutum irin Michael ya riƙe makami tofa zaman lafiyar ka shine ka gudu ka ceci ranka, idan ba haka ba, ka tsaya kace zaka nuna masa karfin dantse tofa zai maka illane kawai a banza saboda komai daidai kwakwalwarsa ke faɗa masa. Kewaye palon suka fara yi Michael ya hana su haurawa sama. Ba su ankara ba sai suka ji karar wani harbin dum, Michael ya harbi uncle Herry. Ihu suka fara yi, John kam har da cire wando ya yi wurgi da shi gefe dan wandon tana hana shi gudu, irin wandon yan gayun nan ne wanda suke sakin sa yana faɗuwa rabin bayansu a waje, to idan yana gudu sai dai ya rike wandon idan ba haka ba faɗuwa za ta yi, shine ma kawai ya cire ya yi wurgi da ita gefe guda dan ya sami damar fecewa da kyau. Gaba ɗaya palo ya hargitse Michael ya birkice mu su da gaske, ya koma mayinwacin Tiger, kokarin harbinsu kawai yake su kuma suna kokarin cetan rayukan nasu. Kamar a mafarki suka ji wannan daddaɗar fitinannen kamshi perfume ɗin, cak suka tsaya da ga su har Michael ɗin, a razane suka ɗago kai suna yan waige-waige ta ina za su ga mai wannan kamshi, dan sun san mutun ɗaya ne mai wannan perfume ɗin, shiyasa ko barci suke idan suka ji kamshin sun san waye a wajen. Tsaye yake saman bene can bakin kofar ɗakinsa ya goya hannayensa a saman faffaɗar kirjinsa, harbin gun da Michael ya yi ne ya fito da shi, jikinsa na sanye da bathrobe milk color zuwa gwuiwar sa, zara-zaran dogayen kyawawan kafafunan nasa a wajen, ga wasu dark black gashi mai bala'i kyau da tsantsi kwance a kafafun nasa har izuwa idon sahu na kafar. Ya saki dark black curly hair sannan yau bai ɗaure ba da gani kasan wani aikin yake mai muhimmanci, fuskar nan tasa kamar kullun a ɗaure tamau kamar hadari, idon nan nasa yau sun sauya launi sun rikiɗe izuwa ja, ga shi sun rage girma alamar barci bai isshe shi ba, ko kuma wani abin ya taɓa shi. Dukkan su sun yi mutuwar tsaye sun sha jinin jikinsu, duk wata halitta mai rai a palon sai da hantar cikin ta ya kaɗa. Tuni jikinsu Tga ya fara kerma dan ko a mafarki ba su taɓa zaton lion ya dawo yana cikin gidan ba, Michael ne kawai ya sani ko daddy bai sani ba saboda shigowar daren jiya ya yi kuma dawowar sirri ya yi dan wani aikin nasa da ya saka a gaba, yanzu ma da Michael ya je ɗakinsa ya ɗauko gun yana cikin dressing room nasa yana shiryawa bayan ya yi wanka kenan. Fitsari a wando Jay ya saki dan ya san yau kashinsa ya bushe, ya kawo mace a gida lion na nan kuma macen ma har da babyn sa, bayan yasan cewa lion ya hana su yin hakan, dan tun basu kai haka ba tun ba su wuce 24 years ba lokacin ma lion bai wuce matakin general ba a wajen aiki, ton tsanar mum ɗin su bai yi mu su yawa haka ba, lion ya ce duk mai son yin aure ya nemi mata ya yi aurensa amma zai bar gidan nan za'a saya masa wani gida, duk rintse duk wuya kada su nemi mace ba tare da aure ba amma shi Jay ya yi hakan a tunaninsa da wawtarsa lion ba zai sani ba, shi a nashi lissafin idan ya kawota gida kowa ya ganta tunda lion baya nan, sai ya wuce da ita church a ɗaura mu su aure, dama ya jima yana dakon ranar da lion zai fita wata ƙasa sai ya gabatar da Jennifer ga su uncle, sai dai kash rana ta kwaɓe masa. Tsuru-tsuru dukkan su suka yi, ya yin da Jennifer ta suma a wajen haka zalika shima uncle Herry ya sume. Duk da cewa Jay ya yi fitsari a tsaye bai daina matse cinyoyinsa ba kamar ba lafiya ba, jikinsa sai kerma yake tamkar wanda ya haɗu da zaki, ko da yake a cewarsu gara su haɗu da zakin a tsakiyar dokar dajin da ba komai sai mugayen namun dawa da su haɗu da Romeo sun yi laifi, domin zaki cinyewar lokaci guda zai yi mu su, shi kuma Romeo sai ya azabtar da su, ya basu wahalar da sai sun gwammaci mutuwa. Yau sun shiga tashin hankali ainun Zama dad ya yi saman sofa dan ba zai iya ci-gaba da tsayuwar ba, zai iya faɗuwa kasa, jikinsa sai kerma ya ke yi. Allah sarki baya son tashin hankali ko kaɗan Kuka Michael ya sa tare da sakin gun ɗin ta faɗi kasa, shi ma kuma zama ya yi a kasan yana kuka kamar ƙaramin yaro. Tga John duk zube gwiwowinsu a kasa suka yi jikin na ta ɓari, ga shi sun san lion baya son kalmar sorry ko kaɗan idan ma suka yi gigin ce masa sorry wlh tsab zai iya harbesu da gun su mutu, zaman lafiyar su shine su zube gwiwowinsu a kasa kawai su jira hukuncin da zai yanke mu su. Sannan kuma sun ɓata masa rai domin kuwa ga alama nan a kan fuskar sa. Lalai yau kuna tsaka mai wuya, ni na yi nan, ba zan iya ganin kilishi da tsiren da za'a yi da ku ba yau🤣🤣🤣 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode 19-20🌹 Kuka Michael ya sa tare da sakin gun ɗin ta faɗi kasa, shi ma kuma zama ya yi a kasan yana kuka kamar ƙaramin yaro. Tga John duk zube gwiwowinsu a kasa suka yi jikin na ta ɓari, ga shi sun san lion baya son kalmar sorry ko kaɗan idan ma suka yi gigin ce masa sorry wlh tsab zai iya harbesu da gun su mutu, zaman lafiyar su shine su zube gwiwowinsu a kasa kawai su jira hukuncin da zai yanke mu su. Sannan kuma sun ɓata masa rai domin kuwa ga alama nan a kan fuskar sa. Lalai yau kuna tsaka mai wuya, Bodyguard dake palon gaba ɗaya miƙewa suma suka yi suka zube gwiwowinsu a kasa, ala'mar sun shiga tashin hankali da kuma bala'i yau. Tsit palon ya yi tamkar babu wata halitta mai rai a cikinta, numfashi ma a hankali suke saki Shi kam Jay mutuwar tsaye ya yi ai, gaba ɗaya baya tare da mutane, da alama suman tsaye ya yi, Jennifer da uncle Herry da suka sha harbin bindiga a hannayensu suna sume hannayen nasu na malalar da jini. Lion ya jima tsaye a wajen yana kallonsu ba tare da ya ce upan ko ya yi wani motsi ba, shi kuwa Michael yana aikin kuka da hawaye da yawu. After some minutes, a hankali lion ya sako kafarsa ya fara taka benen ya sauƙo cikin palon. Bayan ya sauƙo ne ya nufi hanyar fita daga palon, har ya kai bakin kofa sannan ya ce su biyo shi, ya kuma ce da Michael da ya ta shi ya ɗauko masa puffer Jacket a ɗakinsa saboda bala'i sanyi da a ke yi a waje, a cikin kam ba'a sanyi saboda na'urorin ɗumama ɗaki da suke amfani da su. Jin haka yasa Michael ya miƙe cikin sauri ya haye sama dan ya ɗauko jacket ɗin, su kuma su Tga cikin zafin nama suka miƙe suka bi bayan lion. Har sun kai bakin kofa sai ku ma suka ga ba Jay, da sauri suka juya, Jay na tsaye ya kasa motsawa saboda bala'i tashin hankali da yake ciki, ji yake tamkar ya murɗe wuyarsa kawai ya kashe kansa ya huta da punishment da lion zai ba shi. Cikin Sauri Tga ya dawo ya janyo shi suka nufi waje dan sun san lion baya jira sai dai a jira shi. Suna fita shi kuma daddy ya aiki bodyguard daya kawo masa first A box dan ya fara bawa Jennifer da uncle Herry taimakon gaggawa. Haka kuwa a kayi ɗaya daga cikin bodyguard ne ya kawo masa A box ɗin ya karɓa ya fara aiki. Sai godiya bodyguards ɗin suke na lion bai kula da su ba, ya kyalesu bai bi ta kansu ba Shi kuma Michael cikin zafin nama ya ɗaukowa lion puffer Jacket ɗin ya kai masa wajen horarwan sa. Waje ne da lion ya ware na azabtar da masu laifi a gidan, duk wani nau'i na kayan azabtar da ɗan adam akwai shi a wannan waje, kama daga ruwan kankara, sai wani ruwa mai kalar green color mai kauri kamar gantsa kuka, ruwan yana da kauri sosai ga wari, sannan akwai na'urori kala-kala irin na yankewa mutun yatsa, gabansa, hannu, kafa, da sauransu, ga wasu manya-manyan kunamu da wasu kwari da a ka tana da cikin wasu glasses mai kama da show glass, cikin kwarin nan har da wasu halittu da ke da cizon bala'i, idan suka cijeka sai kafi wata kana fama da jinya, wannan wajen duniya ne wajen kayan horar wa, akwai abubuwa da dama wadda ba za su kirgu lokaci guda ba. A cikin wajen akwai zaratan sojoji masu lafiya da jini a jika, wadda da ka kallesu bakaga alamar imani a tattare da su ba, fuskokin nan nasu babu annuri ko kaɗan, ga su jibga-jibga da tsawo da ƙiba dukka, ga cikar halitta, sun samu horo mai kyau. Gaban wannan green ɗin ruwan Romeo ya je ya tsaya, da sauri Michael ya ɗaura masa puffer Jacket ɗin nasa, a kafaɗar sa, zura hannayensa ya yi ya sanya jacket ɗin da kyau a jikinsa. Shiru suka tsaya suna kallon ruwan shi da Michael, ruwan yana da tsawo sosai, amma bai da wani faɗi sosai. Tun kafin lion ya ce su shiga cikin ruwa suka yi sauri suka faɗa, Tga, Jay, da kuma John, shi kuwa Michel da shi ya haddasa komai yana tsaye kusa da Romeo har da wani kwanto da kai ya yi a saman bayan Romeo, yana turo baki irin na shagwaɓa. Saboda son kai irin na Romeo sai bai yi yunkurin hukunta Michael ba, sai ma kara jan sa a jiki ya yi a cewar sa ai Michael bai da lafiya dan haka sai dai a lallaɓa shi ba dai a hukunta shi. Kai Romeo wannan son kai ne, bawani bai da lafiya ya harbi uncle Herry da Jennifer da bindiga fa, ba shi da lafiya amma ya iya harbi ai😭 Su Tga kuwa suna shiga cikin ruwan, wasu zaratan sojoji guda biyu suka ɗauko wasu zabga-zabgan bulalu wanda ganin su da ido ma kawai ya isa ya saka mutun fitsari a wando, ga shi fuskokin sojojin nan babu alamar annuri ko kaɗan bare mutun ya sa ran zasu tausaya masa. Cikin Ruwan da su tga suka shiga nan wayan nan sojojin suka shiga, amfanin su a nan shine, su Tga za su nitsa cikin ruwan tundaga farkon ta har kashe, za su yi tafiya a cikin kasan ruwan zuwa bakin gaba, idan suka ɗago kai wayan nan sojojin zasu zabge kan nasu da bulala, a dokar ruwan idan an shiga ba'a ɗago kai dan shakan numfashin sai an kai karshe. Haka suka fara iyo cikin wanan kakkauran ruwan, wadda aka zuba masa abubuwa kala-kala, ga shi ba daman shan ruwan kuma ba daman numfashin. Idan suka yi iyo kaɗan sai su ɗan ɗago dan su shaki numfashin, suna ɗagowa wayan nan jibga-jibgan sojojin masu kama da samudawa zasu zabga musu wayan nan zabga-zabgan bulalu dake hannunsu, sai dai ka ji shaw, ga shi ba halin yin kuka ga azaba, amma haka suke ɗan ɗagowa su shaki numfashi saboda kar su mutu, gara musu su ɗago su karɓi wannan bulala a kan rashin numfashi ya kashe su. Lion na tsaye ta goya hannayensa a saman faffaɗar kirjinsa yana kallon su, fusataccen fuskar nan tasa kamar hari tamau take, Michael kuma sai wani kara langwaɓe masa yake a baya. Wahala iya wahala su Tga sun sha, ɗan gara ma Tga da yake ya ɗan saba dan ya yi training aikin soja, amma Jay da John ba'a maganar irin azaban da suka sha sun azabtu over. (Hmmm Romeo ba baya ba wajen bada horo, idan ka bari ku ka yi arba kayi laifi ta bakin sojojin nasa gara ka kashe kanka da kanka a kan hukuncin sa, dan hukuncin sa ya fi haɗarin mota muni, musamman ma yanzu da yake cikin zafin kai yana aiki suka takura masa da hayaniya, ga kuma Jay ya kawo musu mace, macen ma har da yaro, tashin hankali lallai akwai show!) Da kyar suka iya kai bakin gaɓar ruwan, duk sun ji ga ta, da kyar suke iya numfashi. Suna kai bakin kaɓa suka ɗago kai cikin sauri dan su samu damar yin numfashi. Sojojin dake zane sune suka fara fita daga cikin ruwan kafin su ma su miƙe zaune amma sun kasa fita saboda tsami da gwiwowinsu suka mu su dan rarrafe suka rinƙa yi. Gyaran murya lion ya musu, cikin sauri suka tattara duk sauran karfin da ya rage musu su ka miƙe tsaye, sai tangal-tangal suke gwanin ban tausayi, ga shi kuma ba su isa su ce ba za su iya tafiya ba saboda sun san sauran. Wucewa lion ya yi zuwa wajen ruwan kankara. Da kyar suke jan kafa suka fito daga cikin ruwan suka bi bayan shi. jay yana ji kamar ya murɗe wuyarsa kawai ya mutu, amma kuma idan ya tuna in ya mutu shikenan zai rabu da yaronsa sai ya fasa dan yana bala'i son yaron nasa. Wajen ruwan kankaran nan Romeo ya tsaye tare da goya hannunsa a saman faffaɗar kirjinsa yana kara ɗaure fuska. Ba zaka taɓa cewa akwai kankara a wajen ba, saboda kamar swimming pool a kayi wajen sai dai wannan ya fi pool tsawo kuma bai kai pool faɗi ba, sannan an fure saman wajen da tiles ba zaka taɓa cewa akwai ruwa ko maka mancinsa a cikin wajen ba. An yi kofa biyu ma su design na cycle ɗaya a farkon wajen ɗaya a karshen wajen, ala'mar kofar shiga da fita ne, idan ka shiga ta nan sai ka fita ta can, ga cikin wajen ta sama kankarane kasan kuma normal ruwa, da kallo ɗaya zaka yi wa wajen kasan tsara shi a kayi, an tsara shine ya kasan ce hakan, da alama wani abin suke sakawa ruwan yake mugun sanyi haka, har ya zama kankara ta sama, kasa kuma normal ruwa, ta yadda idan ka shiga ba zaka iya ɗagowa sama ba, saboda kankaran. Ba tare da lion ya ce musu su shiga ba suka yi saurin fara shiga dan already sun san da wayan nan kalar mugunta na Romeo kuma sun san idan suka kuskura suka bari ya musu magana sai ransu ya yi mugun ɓaci, sai na lahira ya fi su jin daɗi, shiyasa suka yi saurin shigewa. Kasancewar Tga yana da training ɗin sojoji hakan yasa ya yi saurin iyo a cikin ruwan ya fito ta ɗayan kofar, sai dai kuma sanyin cikin ruwan mai bala'i mugun kama kashi ne, dan kuwa yana fitowa ya zube kasa yana riƙe da kafafunsa al'amar suna masa zogi. John da Jay kuwa sai da suka ɗauki minti 5 kafin su iya fitowa. Idon nan nasu ya kaɗa ya yi jawur kamar jini, harta fuskarsu sai da ta yi ja sosai alamar sun wahala iya wahala, kuma daman kun san farar fata bata jure wuya, sun sha ruwa sun koshi, dan ga cikinsu nan kamar zai fashe. A tunanin su tun da sun jigata lion zai kyalesu sai su kaga akasin haka, domin kuwa suna fitowa lion ya wuce ya nufi wasu tanki masu kama da drom na manja. An jera su layi a wajen ɗaya da ruwa ɗaya ba ruwa haka a ka jere tankunan a wajen, suna da yawa a kalla za su kai kwara 20 haka suka tafi layi har karshe. Kuka sosai John ke yi, kuma da ka ji kukan kasa na gabalaita da a zaba ne, duk wanda ya gansu a halin da suke ciki sai ya zubar mu su da kwalla, wannan ma a haka lion ya mu su da sauƙi. Tashin hankali to idan ba da sauki ya mu su ba kuma sai yaya kenan? Ina ga sai mutuwa kawai, Jinjina mai girma lion, wannan dole a baka jinjina wai.🤔 Shi kuwa Michael sai wani kara lafewa yake a jikin lion, shi ma lion ɗin yana biye masa, dan yana son a yan kwanakin nan Michael ya samu farinciki over saboda ciwon nasa. Duk in da lion ya je sai Michael ya bi shi ya kwantar da kansa a saman bayan lion ɗin yana turo baki yana yamutse fuska. Lion na isa wajen wadannan tankuna zaratan sojojin biyar suka karaso wajen da gudun gaske, haka zalika suma su Tga jan kafafunsu suka yi zuwa wajen dan gara musu su lallaɓa su kai kansu idan su ka bari lion ya ce a ɗaukosu ba zai mu su da kyauba. Cikin siririyar murya lion ya ce, "Uncle T, you and John go and rest." Cike da murna suka zube kasa a wajen suna mayar da numfashi da kyar da kyar. Shi kuma Jay sojojin da su ka zo wajen suka damko shi suka tsayar da shi gaban ɗaya daga cikin tankunan da ke wajen suka ɗauko ɗan cokali suka miƙa masa sanna suka umarce shi da ya ɗaga kafarsa ɗaya ya ɗora saman ɗayan, ma'ana ya tsaya da kafa ɗaya ke nan. Haka sai layi yake ya tsaya da kafa ɗaya suka miƙa masa wannan cokalin tare da ba shi umarni a kan ya rinƙa ɗebar ruwan wannan tanki mai ruwan yana zubawa a cikin mara ruwa har ya kwashe ruwan gabaɗaya kuma da wannan cokalin, sannan kuma ko da ya kusa gamawa idan ya kuskura kafarsa ɗayan da ya ɗagan nan ta taka kasa to za a sako lissafi daga farko. Tashin hankali lallai Lion ka kware yanzu na san dalilin da ya sa sojojinka ke kashe kansu idan har aka ce kai za ka musu hukunci, yanzu na gano dalilin da ya sa tsawarka kawai takan sa zuciyar mutun ta buga ya mutu, irin wannan azabtarwa haka wannan ma dan yan gida ne, to da na waje ne kuma sai yaya? A haka kuma dan ba wani laifi mai girma suka aikata ba, wayyo Jay soyayya ba ta maka adalci ba ga shi kana cikin ha ula'i😭😭 Haka Jay ya fara wannan aikin bakar wahala. Yana farawa Romeo ya sa kai ya wuce cikin gida, ya bar shi da wayan nan sojoji marasa imani wadda basa taɓa saɓa umarnin sa ko kaɗan, ina da tabbacin ko daddy lion ya kawo ya ce su hukunta shi tofa babu makawa sai sun hukunta shi, dan ba su da imani ko kaɗan da sun karɓi umarni shikenan kuma, aiki ba kama hannun yaro, ko shekara za su yi a tsaye sai sun kammala aikin da ya umurce su, ba su da wasa ko kaɗan. Lion na wucewa cikin sauri Michael ya bi bayansa, John da Tga kuma suna zaune a wajen suna hutawa tukunnan. Dad na kokarin ceto rayuwarsu Jennifer da uncle Herry, a wanna hali lion ya same shi, wucewa ya yi ya haura sama ba tare da ya ce da daddy upan ba, kamar ma bai san da zaman dad a wajen ba. Haka shi ma Michael ya zo ya wuce bai tanka dad ba, ya bi bayan Romeo. Romeo na shiga bedroom nasa bai fi da 3mins ba sai ga jibga-jibgan sojoji su shida sun shigo palon, daidai lokacin yaron Jennifer ya tashi ya fara kuka, ɗaukan yaron dad ya yi yana rarrashin sa. Wayan nan sojoji da suka shigo kuma zuwa suka yi suka ɗauki Jennifer da uncle Herry suka fice da su daga palon suka nufi babban hospital, shi kuma dad ya ɗauki yaron su ka koma sama dan ya je ya ba shi madara ko zai dai na kuka. A ɓangaren lion kuwa yana shiga bedroom nasa ya ɗauki hand gloves ya sanya tare da cire jacket ɗin jikinsa ya fito ya nufi wani ɗan siririn hanya dake tsakanin part nasa dana James. Michael bai ga fitar sa ba ya yi tunanin ko toilet ya shiga, shiyasa da ya shigo ɗakin ya hanye saman gado ya kwanta. Wani waje mai kyau da ɗan girma lion ya shiga, wajen gaba ɗaya ɗaure yake da buhun masge, rai a matukar ɓace ya fara chaskale da buhu ɗaya, da karfi-karfi yake kai wa buhun nan duka da hannunsa, yana yi yana kara ɗaure fusataccen fuskar nan tasa, yadda yake kai wa buhun naushi yasa damtsen hannun sa suka kara kunbura har wasu jijiyo green suka bayyana a damatsan hannun nasa, gaba ɗaya jikinsa ya fara haɗa zufar, sai cizan lallausan red lips nasa yake da karfi-karfi. Lokacin guda ko me ya tuna ya kara ɗaure fuska sosai tare da damke lips nasa na kasa da karfi gaske, a fusace ya dunkule hannun sa ya kai wa buhun naushi da karfin gaske har sai da buhun ta fashe duk karfin da take da shi. Kai da gani kasan yau lion na cikin damuwa, sai Allah kaɗai ya san meke damun shi. Damke buhun ya yi da hannayensa ya kifa goshinsa a saman buhun yana sauke numfashi tare da furzar da iska mai bala'i zafi daga bakinsa. Ya ɗan ɗauki tsawon lokaci a haka kafin nan ya saki wani nauyayyar numfashi tare da sakin buhun masgen ya juya ya nufi waje, kai daga ganin yadda lion ke tafiya a yau kasan baya cikin kwanciyar hankali, yau wani irin tafiya yake yana kara bubbuɗe faffaɗar kirjinsa duk da cewa daman kirjin nasa a buɗe take, amma yana kara buɗe wa, alamar baya cikin kwanciyar hankali. Yana shiga bedroom nasa ya wuce balcony. Zubur Michael ya miƙe zaune yana mamakin wai daman lion baya ɗakin ne, cikin sauri ya diro kasa daga saman gadon ya nufi balcony ɗin dan ya ga me lion ya ke yi. Cikin ɗan karamin pool dake wajen Michael ya isko lion kwance a ciki, gaba ɗaya jikinsa na cikin ruwa, daga kansa zuwa wuyarsa ne kawai a waje, ya lumshe dara-daran idon nan nasa ya ɗaga kai sama kamar mai tunanin wani abin, zara-zaran dogayen eyelashes nasa nan sun jiƙe da ruwa, da alama ya wanke fuskar tasa. Bakin pool ɗin Michael ya zo ya zauna yana faɗin "My lion ina son shan Ice cream" ya yi maganar a shagwaɓe, shiru lion ya yi bai tanka shi ba, amma har cikin ransa ya yi mamakin wai yau Michael ne zai sha ice cream, su da ko tea basa sha da sugar, ɗan garama James amma Michael kwata-kwata baya son zaki a rayuwarsa. Ganin lion bai tanka shi bane yasa ya fara kukan shagwaɓa yana turo baki. Banza da shi lion ya yi kamar bai san da zamansa a wajen ba. Tsawon minti goma suna haka sannan Michael ya miƙe ya zai nufi hanyar komawa cikin ɗakin. "come here Michael". A nitse lion ya yi maganar. Komawa Michael ya yi ya zauna yana faɗin "My lion na ce maka zan sha Ice cream amma ki min shiru". Slowly ya waro dara-daran blue eyes na sa da suka kara kirma sosai saboda yar rama da fuskarsa ta yi alamar baya samun isasshen barci. Sosai Michael ya tsorata da ganin yadda idon Lion ɗin nasa ya zama, zaro dara-daran brown eyes nasa ya yi yana faɗin "My Lion what happened to your eyes? What is wrong with you? And where is James?" Ya jero masa tambayoyi ne yana kara zaro ido waje. "Which kind of ice cream you want?" Shine abin da lion ya faɗa a maimakon ya amsa masa tambayoyin da ya masa. Make kafaɗa Michael ya yi kaman karamin yaro yana girgiza kai ya ce "No need of ice cream again, please my lion amsa me what is wrong with you?" Slowly ya mai da idon sa ya lumshe ba tare da ya sake cewa Michael ko uppan ba. Kwafa Michael ya yi yana kallon kyakkyawar fuskar Lion da yanzu ya ƙara haske da kuma kyau, sai sheki fuskar nasa yake yi kamar fatar jariri, ga gashin sa sun bazun masa har saman fuskar tasa, ba karamin burgesu Lion yake yi ba, duk da suke Triplets basa kama da shi, sai dai kama ta jini, amma duk ya fi su kyau, dan shi da dad yake kama, har kwayar idonsa na dad ya ɗauko tsawo da komai duka na dad ne, sai dai yafi dad ɗin ma kyau sosai. Ganin ya jima a zaune Lion bai ce masa komai bane yasa ya kai hannunsa ya ja dogon hancin lion yana faɗin "Wake up and answer me" shiru Lion ya masa kamar baya jin shi. Hakan yasa Michael ya miƙe ya bar wajen yana turo baki. Lion ya jima sosai a wajen kafin ya fito ya ɗauki towel ɗaya daga cikin towels dake jere a wajen, ya ɗaura a jikinsa sannan ya nufi cikin ɗaki jikinsa na ɗigar da ruwa. Lokacin da ya koma bedroom nasa Micheal ya yi barci, kallo ɗaya Lion ya masa ya kauda kai tare da wucewa dressing room nasa. Jim kaɗan ya fito sanye da wando jeans three quarter fari tas da kuma riga mai ƙaramin hannu mara nauyi launin sky blue mai haske. Gaban mirror ya zo ya tsaya ya fara shefe-shafen lotion nasa masu bala'i kamshi da kyau da tsada. Bayan ya kammala ya wuce ya zauna saman chair dake gaban wani kyakkyawan table a cikin ɗakin, tare da fito da wasu chemicals ya fara haɗawa, yana yi yana tunani. Ya yin da shi kuma Jay yake halin kakani kaye, yana tsakanin mutuwa da rayuwa, ga shi kuma da alama lion ya mance da shi, kuma koda Jay ya kammala matikar Lion bai bada umarni sojojin su kyale shi ba, to fa ba za su kyale shi ba, ko da ya gama transferring na ruwan a ɗayan drom ɗin sake sa shi za su yi ya sake transferring na ruwan zuwa drom da ya kwashe da farko, ga shi kuma drom ɗin a kalla zata kai 200lt ma'ana jarkan ruwa takwas kenan. (Tashin hankali to kai fa Jay sai dai mu ce Allah ya kwace ka kawai, amma in ba haka ba kana cikin gararin rayuwa, ka ga ta kan ka yau idan halinka ne gobe ma ka sake. Su kuwa su Tga bayan sun gama hutawarsu, da su ka samu kafarsu ya ɗan yi kwari sai su ka miƙe su ka wuce cikin gida. Tga na shiga bedroom na sa wanka ya yi ya haye gado sai barcin wahala, shi kam John ko wankan ma bai yi ba dan wahala da ya sha saboda bai yi training na soja ba shiyasa ya wahala sosai Tga ya fi sa kwari. Bajewa ya yi a saman bed nasa ya hau barcin azaba. Su kuma uncle Herry da Jennifer an wuce da su hospital, kuma hakan ya faru ne sakamakon umarnin da Lion ya ba wa sojojin nasa a kan su wuce da su asibiti. Daddy kuma yana can ɗakinsa yana fama da renon yaron Jay. Wanna fa shine cakwakiya. To mu dai bari mu leƙo Rimsha yar amanar mu mu dawo 💞💞Nigeria💞💞 Rimsha! Zaune take a wani irin waje wadda kamar ba a duniyar mutane ya ke ba, wajen cike yake da furanni masu kyau da kamshi, abin mamaki kuma kamshin wajen sak irin kamshin jikin Lion ne, wajen ya kasance a bakin wani katon teku ne mai matukar girma da baka iya ganin karshensa, saboda girma, daga ɗan jefenta wani irin haɗaɗen ɗakin da Turawa suke a cikin daji ne, mai kama da bukka, duk da a cikin dajine, ɗakin yaji komai da ake bukata kamar ɗakin wata sarauniya, an kawata shi sosai da sosai. Yana yin iskar da dogayen bishiyoyin wajen ke kaɗawa abin gwanin ban sha'awa da ɗaukar hankali, idan iska ta kaɗa sai ruwan tekun nan ya taho da gudu har zuwa bakin gaba kusa da in da take zaune, idan ruwan ya koma sai kaga wasu kananan kifaye suna tsalle abin ba'a cewa komai ya kayatar ba kaɗan ba. Sanye take da wando guntu zuwa santala-santalan kyawawan cinyoyin ta dake ta sheki ga laushi kamar fatar jariri, daga ta sama kuma tana sanye da riga zuwa cibiyarta, iya tula-tulan ta kawai ya rufe, ga su a tsaitsaye damdam da su Masha Allah, duk wanda ya ganta sai ya kyatsa domin ta cika ta haɗu ta ko ina, komai ya zauna daidai, kamar ba Rimsha ba. Daddaɗar iskar dake kaɗawa sai kaɗa mata dark black curly hair ta yake, gashin na bazuwa yana rufe mata fuska, sai cizan Pink lips nata take, tare da lumshe dara-daran sleeping eyes nata kamar mai jin barci, hakan yasa zara-zaran dogayen eyelashes nata suka kara bayyana kamar wadda ta yi kari dana kanti, ta yi shiru tana sauraran kukan tsuntsyen dake tashi daga dogayen bishiyoyi dake gefe-gefen tekun. A hankali ya tako zuwa in da take zaune, shima jikinsa na sanye da short fara tas daga ta samansa kuma ba bu riga, faffaɗar kirjin nan nasa a waje ga wasu kyawawan bakin gashi mai bala'i tsantsi kwance a saman kirjin nasa, breast nasan nan bul'bul gwanin burgewa. A zahirin gaskiya bayyanar asalin surar jikinsa ba karamin haukata mai kallo zata yi ba, domin akwai wasu sirrika a tattare da shi wadda duk wanda ya gan shi to dole ya faɗa da mahaukacin son shi, sai dai kuma bayyanar asalin halittar tasa ta kara masa bala'i kwarjini wadda babu wanda zai iya tinkararsa ya masa wani magana, ko kallonsa cikin ido ba zaka iya yi ba, saboda baiwar kwarjini da Allah ya masa ga kuma yanayin kirar jikin nasa na manya jarumai sadaukan yaki, damatsan hannun nan nasa kawai ya isa ya firgitar da mai rai, shiyasa mutane ke razana da kallonsa. Shima kamar ita bai ɗaure gashin kansa ba haka iskan ke kaɗa masa gashin nasa zuwa fuskarsa, abin ba'a cewa komai sai wanda ya gani, domin baki ba zai iya fasalta yadda kawatuwansu ya kasanceba. Ta bayanta ya duƙa tare zuro kyakkyawan hannunsa ta saman shafaffen flat tummynta. Dogon numfashi ta ja tare da sauƙewa a hankali lokacin da ta ji saukan hannun nasa a saman cikinta. Slowly ya matso da ɗan karamin bakinsa daidai saitin kunnenta, kasa kasa da wata iriyar murya mai kama da mai mayen barci a hankali ya motsa laɓɓansa ya ce "Ke ma kin yi missed ɗi na ne?" Ya kai karshen maganar tare da sanya ɗayan hannunsa ya fara tattare mata gashin kanta dake rufe mata kyakkyawar fuskar ta saboda iska dake kaɗawa. "Dole zan yi missing naka mana, ka fa san kai ɗin na daban ne a duniya" yana kokarin ɗaure mata gashin nata ne ya matso da ɗan bakinsa sai tin lallausan wuyarta ya manna mata kiss a wajen, gently ya ce "My Rimsha you are special" lokacin da ta ji saukar lausasan laɓɓansa a saman wuyarta wani irin ɗauke wuta ta yi, na yan mintoci kafin ta saki cool murmushi wadda ya sanya dimple nata lotsawa, yatsansa ɗaya ya sanya cikin dimple ɗin nata tare da sakin gashin kanta dan yaki ɗauruwa ya yi tsantsi sosai, a hankali ya kwanto da kansa saman kafaɗar ta yana sauke numfashi a hankali, yana shakan daddaɗar kamshin dake fita daga gashin kanta, sai faman lumshe ido yake kamar mai jin barci. Numfashi sa dake sauka mata a saman kirjinta a hankali-hankali ba karamin kara gefata cikin yanayi yake ba, yana kara gigitata sosai, shima kuma kamshinta da yake shaƙa ba ƙaramin gigitashi tare da ingiza zuciyarsa take ba. Ta yi nisa cikin tunanin wadda sai Allah kaɗai yasan tunanin da take. A hankali ta jiyo hannunsa yana shafa mata shafaffen cikinta, sai ajiyar zuciya take sauƙewa a hankali. Uhmm abin nema ya samu🤣 Cikin salo da kwarewa ya juyo da ita suna fuskantar juna tare da matso da ɗan karamin bakinsa saitin tata yana kokarin kissing nata, ba karamin razanata kyansa ya yi ba, yau yazo mata ba face mask, ta tsorata da kyansa musamman kwayar idonsa da suke ta kwalli sabo zarosu da ya yi, kunsan blue eyes da kyalli. Tsoratar da tayi da ganin kyansa ne yasa ta saki ihu wadda ya yi sanadiyar farkawar ta daga nauyayyar barcin daya ɗauke ta tun bayan sallar asuba. A zahirin gaskiya ko a mafarki kwarjinin Lion ya tsoratata bata da kwarin gwiwa iya kallon cikin idonsa ko da a mafarkin ne. Tirƙashi babban magana, yau a ke yin ta🤔 A zafafe ta miƙe zaune a tsakiyar gadon Kausar, sai zufa take haɗawa saboda mafarkin Lion da ta yi, addu'a ta yi sosai, dan neman tsari daga wajen Allah, kullun tana yawan mafarkinsa sosai, amma bata taɓa yin irin na yau ba, kullun sai dai ta yi mafarkinsa yana zaune gefenta suna ɗan hira kuma da face mask, bai taɓa taɓa ta ba ko da sunan wasa sai mafarkin yau, abin ya bata tsoro da kuma mamaki, duk ta firgice ta yi wiki-waki da ita, dark black curly hair tan nan ya watse ya bazun mata har ta gaban fuskar ta, da kyar take iya jan numfashi. Idan ta tuna yadda taga fuskarsa a mafarki yadda ya juyo da ita suka haɗa ido da wayan nan dara-daran kyawawan blue eyes ɗin nasa, sai ta haɗiyi wani wahalallen yawo mai wuyar wucewa. Tana kokarin sauƙa daga saman gadon ne ta ji jikinta a jike, dubawa da zata yi ashe fitsari ta yi a wando, tashin hankali ganin kyakyawar fuskar Lion a mafarki ya saka Rimsha fitsarin kwance (Niko nace to Rimsha dama ba za ki iya ba kika fara, kallon fuskar Lion a cikin mafarki ma kawai ya saki fitsari a wando, to ina ga kuma a zahiri? Ga shi kuma Kausar ta ce ku tara kuɗi ku je wajen sa, Babbar magana, hmmm anayi muna jin daɗi🤣🤣🤣 amma dai i pity you my Meesha 🥺) kara tsorata ta yi cikin sauri ta diro kasa daga gadon ta nufi wajen kayan Kausar, wani dogon riga ta ɗauka ta fito ta shige toilet. A gurguje ta watsa ruwa, daga cikin toilet ɗin ta sanya kayan Kausar ta fito falo, nan ta isko su Ayla har sun ci abincin safe sun zauna suna kallo. Zama ta yi sama sofa kusa da Ayla ta ɗauko remote ta canza tasha zuwa news dan taga meke faruwa a duniya, ta ko yi Sa'a tana shiga News dara-daran sleeping eyes nata suka mata arba da hotunan Lion a Airport zai tafi Spain lokacin, sai tattaunawa manya-manyan gidan Tv suke yi a kan hakan, kara tsorata da shi tayi dan yadda taga fuskar sa a Airport ɗin lokacin yana sallama da His excellency, dama kuma kun san ranar ya fita cikin ɓacin rai a fusace, runtse ido ta yi, alamar bata son kallon fusataccen fuskar sa, Sai dai kuma me tana runtse ido a sukwane ta buɗe domin kuwa tana runtse idon fuskar sa ta gani yana kokarin yi mata kiss lokacin a mafarki. Ihu ta saki tare da miƙe wa tsaye, daidai lokacin gidan Tv suka ɗaura wani shot video sa in da yake magana da president ɗin Spain lokacin da zai bar gidan ya koma hotel, kun san lokacin a fusace ya yi maganar, ganin haka yasa Rimsha ta watsa a guje zuwa cikin bedroom na su tana dafe kanta dake mata barazanar tarwatsewa saboda ciwo, ga shi Lion na neman haukatata, ko in ce tana neman haukata kanta, domin Lion kam bai ma san tana yi ba, bai san da zamanta a duniya ba ma. Tashin hankali wanna shine Babbar cakwakiya. Da sauri su Ayla suka bi bayanta. Saman gado kusa da in da ta yi fitsari suka iskota, ta dafe kanta tana hawaye, baiwar Allah idan ta rufe ido ba abinda take kallo fa ce fuskar lion yana ƙoƙarin yi mata kiss, ga shi bala'i tsoron ganin fuskar tasa take, kwarjininsa yana haukatata, idan kuma ta buɗe ido fusataccen fuskarsa da ta gani a Tv yanzu take gani, Allah sarki ta ko ina ba sauki, duk ta ruɗe ta zama kamar zararriya abin tausayi, lokaci guda ta canza ta rasa ina zata sanya rayuwar ta ta ji daɗi, ta rasa nitsuwar ta. Wanna abu yana azabtar da ita, a zahirin gaskiya ko daga nesa idan taga fuskarsa cikin face mask sai gabanta ya faɗi kuma a haka zuciyarta ta kamu da bala'i kaunar shi, a yan wanna kananun shekarun nata, zuciya baki wa Rimsha adalci ba ko kaɗan. Sosai take hawaye ta rasa madafa, kuma a haka ma a cikin farinciki Lion ya mata magana a cikin mafarkin tata, wanna da a ce tsawa ya mata ai ina ga Rimsha sai mutuwa. Kusa da ita Ayla tazo ta zauna tana faɗin "Rimsha lafiya ki ke kuka?" Shiru ta kasa magana, haka ita ma Kausar tazo ta tambaye ta, nan ma shiru bata amsa su ba, sai kuka kawai take baiwar Allah. (Why Lion zaka yi mana haka, ai ya kamata a ce da akwai amana, ko kwarjinin ka zai firgita kowa bai kamata ka bari ya firgita mana Rimshan mu ba, dan ta ɗebi tsawon shekaru da dama tana dakon sonka🥺.) Su Ayla sun jima zaune suna ta rarrashinta, kafin su samu ta daina kuka amma taki yin magana, saboda bata san me zata ce musu ba. Sun shafe 1 hour a haka kafin Rimsha ta iya samu abin ya sake ta, ta miƙe zaune. Kasa kasa kamar mai raɗa ta ce "Ina Iya kausar?" "Iya ta fita unguwa" Kausar ta bata amsa, matsowa Ayala ta yi ta rungumeta tana faɗin "Rimsha dan Allah ki faɗa mini me ya sanya ki kuka?" Kakalo murmushi dole ta yi tana faɗin "Ayla a yanzu ba ni da wanda ta fi ku, dan haka zan faɗa miki amma ba yanzu ba" shiru Ayla ta yi kamar mai nazarin wani abin, ita kuma Kausar wucewa tayi ta nufi waje tana faɗin "Bari na je gidansu waliya ina zuwa, Iya ta ce na karɓo mata abin ɗebar ruwanta da suka ara" to kawai su Ayla suka bita da shi, juyawa ta yi ta fice daga ɗakin. Kausar na fita Rimsha ta Matso kusa da Ayla sosai tare da riƙo hannunta ta fara bata labarin abin da ke faruwa da ita a kan Lion, daga karshe ta rufe da cewa "Bana son Kausar ta sani ne saboda banson matsala" kasa kasa Ayla ta ce "Matsalar me kuma Rimsha?" Kara kasa da murya Rimsha ta yi kafin ta ce "Ke dai Ayla ki riƙe amana amma ita Kausar ba ta da amana ita da Iya akwai abin da suke shirya mana, shiyasa yanzu na ja baya da su, jiya na shiga ɗakin Iya na samesu suna magana kasa kasa suna gani na suka yi shiru kuma tun kafin na shigo na ji suna magana, sannna kuma ki yi taka tsantsan da wayan nan boda Jami'u wlh yan iskane dan dana fita yin alwala da asuba na haɗu da ɗaya daga cikinsu ban gane wanene bane ya yi kokarin taɓa min kirji na kauce na gudu na dawo ɗaki" a hankali Ayla ta ce "Haka ne kam nima ɗazun sai da ɗayan bansan sunan shi ba sai da ya taɓa min kirji, kin san munrigaki ta shi barci, kuma Iya ta fita ta bar mu da su, ina ga da gangan ya aiki Kausar shagon wajen nan, tana fita ya kama mini breast na, shi kuma ɗayan lokacin yana wanka, ɗayan kuma yana ɗakin su, dana ja da baya zan ta shi ya yi saurin riƙeni ya ce idan nayi wani magana sai ya yanka ni, shine na yi shiru, ya ci gaba da taɓani, yana cikin taɓa ni Kausar ta dawo sai ya yi saurin ya sake ni" ta kai karshen maganar tana hawaye, goge mata hawayen nata Rimsha ta yi a kule ta ce "Wlh kada ki sake bari ya taɓa ki, idan ya sake yin gigin hakan ki masa ihu, ba gara mu bar musu gidansu ba da su taɓa mana mutuncin mu, ko yatsana ba wanda zan bari ya taɓa, banzaye wayan da basu san ciwon kansu ba kazamai kawai" ta kai karshen maganar cikin fishi, dan har ga Allah abin da suka wa Ayla ya ɓata mata rai dan tana barci ne da bazata bari hakan ta faru ba, Allah sarki Iya ita ma bata nan ne da ba zata yarda da Jami'u ya taɓa ko ɗaya daga cikinsu ba, kuma har ga Allah Iya bata san halin Jami'u kenan ba shi yasa, bai taɓa nuna musu hakan a filli ba, kullum a mutumin kirki Iya ta ɗauke shi shiyasa ma ta yarda da neman auren Kausar da yake yi, bata san ɗan iskane mai lasisi ba, ga bin mata ga shaye-shaye. Tirƙashi su Rimsha kuna cikin tsaka mai wuya, ba abin da zamu ce sai dai Allah ya shiga lamarin ku. Duk wannan magana da Ayla da Rimsha keyi kaf a kunnen Kausar suka yi shi, domin kuwa ba wani gidan su waliya da ta tafi tana fita ta laɓe musu a bakin kofa tana sauraren su, daman kuma da gangan ta ce musu Iya ta aiketa, dan ta lura Rimsha bata son yin magana a gaban tane, shiyasa ta musu hakan, dan su tattauna. To meke shirin faruwa ne? Mu je dai zuwa. Bayan ta gama sauraren tattaunawan nasu ne, ta lallaɓa ta fice daga falon ta nufi waje tana riƙe da haɓa tana girgiza kai, a zuciyar ta tana faɗin "Ku zauna a gidan mu, muyi mu ku komai, ci, sha, sutura, amma ku rasa waye zaku yi wa sharri sai yayana kuma mijin da zan aura, wlh ba zata sakuba". Tana ta zancen zuci har ta isa gidan su Waliya Su kuwa ba su kawo cewa Kausar zata musu laɓe ba dan hakan yasa suka saki jiki wajen yin hirar su, a hakan ma kasa kasa suka yi dan kada wani ya ji yo su, suna gudun matsala. Allah sarki bayin Allah, Allah dai ya fitar da ku daga cikin wannan ukubar rayuwa. Bari mu leƙo Daular mutuwa mu dawo To masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu, Much kauna 🥰 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode 20-21🌹 Su kuwa ba su kawo cewa Kausar zata musu laɓe ba dan hakan yasa suka saki jiki wajen yin hirar su, a hakan ma kasa kasa suka yi dan kada wani ya jiyosu. Allah sarki bayin Allah Allah dai ya fitar da ku daga cikin wannan ukubar rayuwa. Bari mu leƙo Daular mutuwa mu dawo. ☠️☠️Ɗaular Mutuwa☠️☠️ Guguwa ne mai karfin gaske ta kewaye ko ina, wani masifaffen duhune ya lulluɓe gidan gaba ɗaya, daga cikin guguwar wasu sautika ne ke tashi kala-kala na muryoyin sheɗanun aljanu daban-daban, masu magana da yaren da ɗan adam baya ji, idan ba kana da karfin imani ba baka iya zama a wajen, gaba ɗaya gidan ansawa yake yana bada wani irin amo mai sautin gaske, gaba ɗaya wayan da ke cikin gidan, kowa ya yi ta kan shi, ma'ana sun shige cikin ɗakunan su. Wannan nasifaffen guguwa ya jima yana yi kafin haske ya karaɗe gidan, amma ita guguwar bata dakataba. Gingima-gingiman jiga-jigan matsafane suka fara fitowa ta sassa daban-daban daga cikin gidan, munin halittar su ma kawai ya isa ya sa ɗan Adam suma. Gaba ɗaya matsafa dake gidan sai da suka fito yau, sun jeru layi a cikin part ɗin su Baba da Mustapha, duk girma irin na part ɗin nan sai da suka cika shi tab da yawansu, dan suna da yawa sosai ba wasa ba, munanane gaba ɗayan su, basu da kyan gani ko kaɗan, tsayawa zayyana muku bala'i munin su ma ba zai yi wu ba, domin zai cinyemin ɗan fillin dake gareni, dan haka ku ayyana su a ranku kawai, suna da kattin kai da katon hancin ga idon nan nasu jawur kamar jini, kamar kuma zai faɗo kasa saboda girma. Sun tsaitsaya kamar wasu gumaka, numfashinsu kamar na saniya, sai dai a cikin su babu duna, baya wajen. Ko ina suka kai shi oho. Daga ta bayan su wani sauti mai bala'i karfi ya fara fitowa, ji kake dip-dip-dip, ƙasa na amsawa, wannan sauti kuma ba komai bane face sautin takun Queen oga kwata-kwata kenan. Wannan sauti ya ɗan jima yana yi, alamar daga nesa take kenan, sautin na kara matsowa alamar tana tunkaro wajen. Lokacin da ta iso wajen, sautin ya kara karfin amon da yake yi ne sosai, gaban su tazo ta tsaya. Kai-kai-kai, ya subhanallah, Queen mummuna ce ajin farko, tana da tsawo sosai ga kuma ƙiba, da kallo ɗaya zaka mata ka san ƙabilar Ebo ce, gaba ɗaya Daular Mutuwa mallakin kabilar Ebo ne. Queen tana da katon hanci kamar tukunya, ga hancin nata a baje a kumatunta, alamar ta kara girma shi da tsafinta, haka zalika bakinta wargajeje gari guda, sannan tana da manya-manyan hakwara guda biyu ta gaban hakwaranta na sama, wayan nan hakwaran nata guda biyu, suna da tsini kamar kifiya, sannan suna da tsawo wadda ko ta rufe baki su basa shiga cikin bakin nata saboda tsawon su, wayan nan hakwara nata masu kama da na zamisa tsab za su iya tsinke jijiya mafi karfi na jikin ɗan Adam, shiyasa ita bata yanka mutun da wuka wayan nan mayun hakwaran nata take damke makogoron mutun ta ɓalle shi ta tsinke jijiyoyin shike nan mutun ya mutu, sannan daga tsakiyar goshinta akwai wani tsagu wadda yazo mata har gemunta, ya yi kamar ya raba kanta gida biyu, ga kan nata ba'a magana girman shi ba zai faɗu a baki ba. (Tashin hankali ke Queen naki bala'i ya wuci tunanin mai tunani😳) Fitowar ta sai da ya sanya gaba ɗaya Daular Mutuwa ya girgiza, gaba ɗaya yan adam dake gidan sai da suka suma, baba da Mustapha ne kawai ba su suma ba, amma sun tsorata ainun suma, saboda munin Queen ba kowa zai iya ganin ta bai sume ba, idon nan nata gula-gula jawur da su kamar jini kamar zasu faɗo kasa, gashin kanta kuwa ba'a magana, idan ka gan shi kai ka ce jijiyoyin bishiyoyi ne, a tsaitsaye suke kamar ba lafiya, ga su da bala'i datti kamar me, tsayawa zayyana muku munin Queen zai cinye mana ɗan sauran filin dake gare mu, ku ayyana muninta a ran ku. Ko da ta tsaya a gaban su, jijjiga jikinta ta yi da karfi kamar wata giwa, sannan ta waje wannan mummunar wagegen bakin nan nata wadda hayaki ke fitowa daga cikinsa, kamar an hura wuta a cikin nata. Da karfin gaske ta kurma wani mahaukacin ihu wadda bala'i sautin sa sai da ya sanya dakarun nata da kansu suka toshe kunnuwan su, ihun nata kuma ya karawa guguwan dake tashi karfin gudu, haka zalika muryoyin dake fitowa ta cikin guguwar suma sun kara sautin muryoyin nasu. Good 2mins ta ɗauka tana kurma wannan balaƴaƴƴen ihun, kafin ta tsagaita, ta sake girgiza jikinta, gaba ɗaya dakarun nata tsugunnawa kasa suka yi a gabanta alamar girmamawa. Cikin yaren su na matsafa ne ta basu Umarni a kan duk in da su Rimsha suke, su tabbatar sun nemo su cikin kankanin lokaci sun dawo da su sun mata ferfesun su, idan ba haka ba ransu zai yi mummunar ɓaci, domin dole ne su Rimsha su karɓi hukunci saboda sun karya mata record na gidan ta, ba'a shiga a fito da rai, su sun shiga sun fito, abin da ba'a taɓa yi ba wai ɗan adam ya shiga kuma ya fito a raye, ina sai a kan su Rimsha. Sosai dakarun nata suka rinƙa bata hakuri tare da yi mata alkawarin ko ina su Rimsha suke sai sun dawo da su cikin gidan nan, yanzu za su fita gari, su shiga cikin al'umma, za su saje da su su nemo su. Wucewa kawai Queen ta yi bata sake yin wata magana ba, tana taku kasa na ansawa, haka ta wuce cikin fadarta, dakarun dake tsaron fadarta ne suka rufa mata baya. Da haka taro ya watse, dakaru goma ne suka shirya suka rikiɗe zuwa siffar kyawawan matasan samari sannan suka wuce izuwa cikin gari, cikin jama'a dan neman su Rimsha. Su kuma sauran kowa ya koma bakin aikinsa. A cikin Daular Mutuwa dakaru basa amfani da kaya irin namu na mutane, saboda ba zai shigesu ba, wani irin tamfol suke using mai matikar karfi da tauri kamar fatar shanu, kuma basa ɗinka shi kamar yadda mutane ke yi, no ɗaɗɗaura tampol ɗin kawai suke a jikin su, sannan gaba ɗaya Daular Mutuwa iya maza ne kawai matsafar dake ciki, Queen ita kaɗai ce mace, kuma mai jagorantar su, Asali gidan na kakantane chigozie, shi ya wallafa Daular tun shekaru 40 baya, dukkansu kuma kabilar Ebo ne, sai dai basa magana da yaren Ebo a gidan, da wani yare nasu na matsafa suke amfani, sannan kuma basa da yawan magana, duk gidan duna ne kawai mai magana da mutane, su Barbushi sai dai yanka da shan jini, manya-manyan gidan matsafa daga sassa daban-daban a faɗin kasa da wajen ta suna zuwa wajen Queen domin sayan wasu sassa na jikin ɗan adam domin yin tsafinsu, shiyasa idan suka kasa shan jinin mutum sai su ajiye shi zuwa lokacin da wasu gidan matsafar zasu bukaci wani sassa daga jikinsa, sai su yanka shi su sayar, amma sai dai duk wani gidan tsafi dake son sassar jikin mutun, akwai wani waje na daban da suke haɗuwa dan yin taron, ba a cikin Daular Mutuwa wajen yake ba, yana daga gefe. Baba da Mustapha bayin Allah, suna zaune shiru a cikin ɗakin, a cikin zuciyoyinsu suna yi wa su Rimsha addu'ar Allah yasa kada Queen ta yi nasarar gane in da suke, Allah yasa sun tsira kenan, shi baba haka kawai yake jin matukar kaunar Rimsha a cikin ransa, baya son ganin ta cikin wahala, gara masa shi ya mutu da wani abin ya same ta. Allah sarki baba bai san cewa Rimsha jikarsa bace. (Wayyo duna ko ya suka yi da shi oho, muje dai zuwa mu gani kila gaba mu sani, bari mu leƙo lion mu gani.) 💓💓Washington DC💓💓 Wunin yau zumbur Jay yana wannan aiki, ya jigata, duk wanda ya gan shi sai ya matsa masa kwalla, ga shi kuma da alama Lion ya mance da shi. (To fa Babbar magana.) Sai can gari ya fara sanyi irin bayan la'asar kenan, His Excellency yazo gidan dan yi wa jikansa sannu da dawowa, a palon kasa ya zauna, masu ba shi tsaro kuma daga wajen sojojin bakin gate suka tsaya, dan tsarin Lion ne babu wani jami'in doka da ya isa ya shigo mu su cikin gida, har sai ya samu izinin Lion. Daga His Excellency sai daddy a palo suna hira, lion yana ɗaki, ya ji zuwan kakan nasa amma sai ya yi kamar bai ji ba, yana kwance saman lallausan bed nasa kusa da Michael, ya lulluɓe jikinsa daga kafa zawa kirjinsa da wata shegiyar duv mai bala'i laushi kamar jikin mage, ga bala'i kyau da tsada, launin fari tas kamar yanzu a ka fitar da shi daga ledansa. Kallon daddy His Excellency ya yi kasa kasa ya ce "William ya kamata Lion ya yi aure gaskiya, akwai wata Jesy jika ce ga babban abokina kuma tana bala'i son shi, dan kowa yasan da haka a gidansu why not ba zaka masa magana a kanta ba? Yarinyar tazo ya ganta, idan ta mishi to sai mu san abin yi" (Tofa kai Lion ita budurwar ita zata zo ka ganta ba kai zaka je ba, a lallai mulkinka ya ka, wai wannan isa haka🤔) Dogon numfashi dad ya ja tare da sauƙewa a hankali, ya zaro ido, sannan ya yi kasa sosai da murya kafin ya ce "Uncle ai naga ka fi kusa da shi why kai ba zaka masa maganar ba? Ni ba zan iya tinkarar Lion da wannan maganar ba, ba zan iya ba, zan iya masa magana a kan abubuwa da dama, ba zai damu ba, amma magana a kan aure, kai ina bani da wannan kwarin gwiwa, amma kai ka gwada kila idan kai ka mishi ba zai ɗauki wani action mara kyau a kan hakan ba" cikin sauri His Excellency ya ce "Ni kuma William? a'a ka rufamin asiri, kai dai zaka masa magana tunda ɗanka ne, zai fi sauraren maganar ka ai" "Ɗa nane kuma mafi soyuwa a gareni uncle, amma ai ya fi kusanci da kai, ya fi sakin jiki da kai" har wani zufa His Excellency ya fara haɗawa saboda ance ya tinkari Romeo da maganar aure, muryan sa na rawa ya ce "No William i can't gaskiya, idan ba zaka iya yi masa magana ba to ina ga sai dai a bar zancen kawai" daddy zai yi magana su ka ji takun tafiya daga bayansu ta saman bene, ko ba su juya ba sun san shi kaɗai ne mai irin wannan taku a gidan, Lion namu 1 in billion. Tsit suka yi kamar ba su suke magana yanzun nan ba, kusa da His Excellency ya zo ya zauna, daman ya fito ne zai je ya karawa Jay wani punishment ɗin, Shiru ya yi na yan mintoci, ya yin da suma suka yi shiru, sun kasa kunne suna sauraron su ji me zai ce, sun kuma tsare shi da ido. Ya jima a haka kafin gently da wannan sexy voice ɗin nasa, kasa kasa a nutse ya ce "uncle yaushe kazo?" Shafa kansa His Excellency ya yi yana sauke nauyayyar ajiyar zuciya kamar wanda ya aikata wani abin rashin gaskiya, har sai da lion ya kalle shi. "Yanzu ba jimawa nazo, nazo maka barka da dawowa ne, My Michael ya kirani a waya ya faɗa mini kayi dawor sirri" ɗan kwanto da kansa Lion ya yi saman kafaɗar His Excellency bai sake cewa komai ba, sai faman lumshe ido ya ke. Ba karamin mamaki daddy ya yi ba, dama Lion har kwanciya a jikin His Excellency ya ke yi ne, amma shi ko da sunan wasa bai taɓa kwanciya a jikin sa ba, Allah sarki daddy har wasu hawaye takaici ne ke kokarin zubo masa a idon sa, cikin hanzari ya mai da hawayen nasa dan kada su gani, har ga Allah yana mutuwar kaunar Triplets nasa, kuma duniyar sa, yana bala'i son ya gansu kusa da shi, sai dai su kuma dukkansu ba wanda yake yawan manne masa, hasalima idan sun zo wajensa to wani abin suka zo yi, haka kawai basa zuwa in da yake. "Where is my Michael?" His Excellency ya tambaya yana kara tsurawa Lion ido, shiru ya yi wa His Excellency kamar ba shi a wajen, da alama dai bai da niyar amsawa, sanin halinsa yasa basu wani da mu ba, sun ma yi mamaki da yazo ya zauna da su haka. After some minutes ya miƙe ba tare da ya sake yi musu magana ba ya fice daga palon zuwa wajen Jay. Kallon daddy His Excellency ya yi kafin ya ce "To William ni zan tafi, idan ka samu lokaci please ka yi wa Lion maganar auren ka ji....?" Tun His Excellency bai gama rufe baki ba dad ya ce "No uncle never" shiru His Excellency ya ɗan yi yana tunanin waye ya kamata su samu wanda zai iya tinkarar Lion da maganar, zuba masa ido dad ya yi yana kallon sa. His Excellency ya jima yana tunani amma ba wani mafita domin babu wanda zai iya tinkarar Lion da wannan magana, ba mai kwarin gwiwar yin hakan. Haka suka hakura, His Excellency ya wuce ya nufi waje, ya je ya shiga motoncinsu suka koma white house. Shi kuma Lion lokacin da ya isa wajen horar war tasa, nan ya isko Jay yana suma sojoji na zuba masa ruwa, idan ya farfaɗo sojijin nan ba imani bare tausayi haka za su sake miƙa masa spoon ya ci gaba, idan ya ga ji sai ya sake sumewa, babu imani ko kaɗan a tattare da su, Jay ya wahala iya wahala abin ba'a magana. Umarni Lion ya ba wa sojojin a kan su ɗauke shi zuwa wajen mai kamar katifa yana da ɗan girma launin gree color, ruwa na feshi a wajen kamar tiyo ya fashe. Haka suka ɗauke shi suka kai shi, ruwa ya rinƙa fesuwa a jikinsa yana wanke masa jiki. Sai da ya wankesa tsab sannan Lion ya ce su kai shi wajen wani ɗaki mai ɗumin gaske, bayan sun kai shi ne suka fito suka bar shi a ciki. Massage Lion ya yi wa Tga a kan yazo idan Jay ya ɗan sha ɗumi ya ɗaukesa ya ɗauresa a tsakiyar gidan kan shi na kallon rana, zuwa rana ta karisa faɗuwa, dan lokacin bai wuci irin 4:20 nan bane, idan rana ta faɗi sai a mai da shi ɗaki zuwa gobe ya dasa. (Tab Jay ka shiga uku, gobe kuma ka dasa, kai kam ina ga sanadiyyar ajalinka kenan🤣) Tun Lion bai bar wajen ba Tga ya kariso wajen dan cika aikin ɗansa kuma ogansa, wucewa Lion ya yi zuwa cikin gida. Yana shiga bedroom nasa ya tarar sarkin rigima wato Michael ya ta shi daga barci, sai faman turɓune fuska yake yi yana turo ɗan bakin nan kamar wanda yaga wani abin ƙyamar. Kallo ɗaya Lion ya yi masa ya kawar da kallonsa gefe tare da zama gefensa yana ajiye wayarsa saman bedside drawer. A bayan sa Micheal ya kwanto da kansa yana turo baki, shiru Lion ya masa tamkar bai san da shi ba,. "My blood please where is James?" Wani irin yanayi mara daɗi Romeo ya ji lokacin da Michael ya jefa masa wannan tambayar. (Allah sarki Michael duk da cewa ba shi da lafiya yana kewar ɗan uwansa, jini ba wasa ba, ya damu sosai a kan rashin ganin James, da abin yake kwana yake tashi a ransa.) Juyowa Romeo ya yi suna fuskantar juna, kallon tsab ya yi mi shi kafin ya ce "Ni ne James mana baka gane ni bane?" Zaro brown eyes nasa ya yi da kyau yana kallon cikin idon Lion, yana son tantance gaskiya, shiru ya yi yana kallon fuska biyu a fuskar Lion ɗin, kwakwalwarsa ta kasa tantance masa waye ne a gaban sa, turo baki ya yi a shagwaɓe ya ce "No Lion ba James ba ne kai ne" ɗaure fuska sosai Lion ya yi "Ni ne James mana" ya faɗa yana zarewa mishi wayan nan dara-daran idanun nasa, dama bai zaro su bama yaya, da girmansu sosai, bare kuma ya kara zarosu, ai sai su saka mutun fitsari a wando. Dafe kai Michael ya yi yana kallon yadda idon Lion ke canza kala daga Blue eyes zuwa Ash eyes irin na James, bayan haka, idanunsa na nuna masa fuskoki biyu a fuska ɗaya, yana ganin Lion kuma yana ganin James, duk kuma a fuskar Lion, dafe kansa da karfi ya yi ya fara kuka yana sambatu yana juyi a tsakiyar gadon kamar ba lafiya ba, zuba masa ido Lion ya yi yana kallon yadda yake juyawa, abin gwanin ban tausayi, Bawan Allah Lion ya kara birkita masa kwakwalwa, dama yaya lafiyar kura bare kuma ta yi zawo. Sosai yake kuka yana sambatu, kansa na bala'i sara masa kamar zai fashe, a take wani zufa ya fara karyo masa, wasu jijiyoyi ne suka bayyana masa a gaban goshin sa, da ka gansu kasan wahala ne ya bayyanar da su, gaba ɗaya tsikar jikinsa sai tashi yake, harta gashin jikinsa sai mimmiƙewa suke. Ya jima yana juyi a wajen dafe da kai, kafin nan ya kurma ihu tare da sakin jikinsa ya zube saman gadon sumamme. Nauyayyar ajiyar zuciya Lion ya sauƙe tare da miƙewa ya ɗauko last injection da za'a masa ya dawo ya zauna tare da haɗa injection ɗin ya masa a hannunsa. Kasa kasa ya ce "Ya zama dole na ƙure kwakwalwar kan nan ko zamu samu sauƙi" Bayan ya gama ya tattare fankon injection ɗin ya mayar in da ya dace, sannan ya dawo ya zauna ya zubawa Michael ɗin ido yana kallonsa cike da kauna da kuma tausaya masa a halin da yake ciki. Ya jima sosai yana karewa Michael kallo kafin ya sauƙo daga bed ɗin tare da shiga dressing room nasa. Gaban wani makeken drawer kayan sa ya tsaya, a hankali ya sanya hannu kamar zai buɗe drawer, yana kai hannunsa kusa da drawer sai ta kuɗe kanta da kanta. Kayane kala-kala masu bala'i kyau da tsada shaƙe a ciki, a shirya suke set-set, kai ka ce shangon sai da kayane a wajen, daga gefe kuma ga wa su dankara-dankaran suit masu bala'i kyau, kai da ganin su kasan an zuba dollars wajen sayan su, dollars ta yi kuka a cikin dressing room nan, abin ba'a magana, suit ɗin makale suke a abin makale kaya an jera su da kyau, sai dai ga dukkan alamu ba a taɓa sanya ko guda ɗaya ba, ba a amfani da su kwata-kwata, alama ta nuna gaba ɗaya kayan cikin wannan drawer ba a taɓa amfani da su ba, kasan cewar manya-manyan drawer kaya huɗu ne a room ɗin, Lion sarkin son kwalliya ne da gayu, shiyasa yawan kayan sawansa, su agogo, takalma, da sauransu ba za su faɗu a baki ba, dan ya fi karfin tunanin mai tunani. Wajen wayan nan suit ɗin ya kai hannun sa ya Matsar da da su gefe guda tare da danna wani ɗan madanni dake jikin bangon wajen sai ga hoton hannun mutun ya bayyana kamar computer yana magana, alamar ya sanya hannunsa, buɗe yatsun hannunsa ya yi ya ɗaura a wajen, nan take na'uran ta yi magana tare da yin yar kara, sannan wata yar karamar kofa kamar Window ta buɗe a wajen, ba zaka taɓa cewa akwai kofa ko makamancin shi a nan wajen ba. Alama ta nuna ma ajiyar sirri ce. Abubuwa da dama ne a cikin wajen, kama daga muhimman takardu keys, da wasu yan akwatina kanana masu bala'i kyau. Wata takarda ya ɗauko tare da rufe wajen ya fito daga dressing room ɗin, gefen bed na sa ya zauna yana duba takardan. Ya jima yana kallon takardun wanda a kayi rubutu da wani yare na daban, domin ba da English aka yi rubutun ba. After some minutes ya buɗe bedside drawer sa ya fito da diamond watch nasu gaba ɗaya ukun. (To fa tambayar a nan shine James bai tafi da watch na shi ba kenan? Ko dai a Spain Lion ya samo watch ɗin?) Zubawa watch's ɗin ido ya yi yana kare musu kallo, alamar yana tunanin wani abin. A nan ma ya ɗan jima kafin nan ya mai da watch biyu cikin drawer, ya ɗaura nasa a hannunsa, ya miƙe yana kokarin karanta menene a jikin wannan takarta. Tun Triplets ba su fi shekara biyar a duniya ba Lion yake tare da wannan takarda, lokacin yana yaro bai damu da sanin me a cikin taɓa, amma yanzu bincike ya biyo ta kanta da dole ya san menene a rubuce a jikin ta. Asalin takardan ya sameta ne a ɗakin mummy'n su, tun kafin su koma sabon gidan su na biyu, wata rana yana wasa a cikin ɗakin ne ya tsinci wata yar akwati karama a kasan gadon mummynsu, ko da ya buɗe wannan yar akwati takarda guda biyu ya samu a ciki masu ɗauke da wani irin rubutu, sai kuma wani ɗan siririn sarka wadda yana da tabbacin na Josephine ne wato mum ɗin su, domin tana yawan saka irin sarka, duk wani hoton ta da zai gani da irin sarkan yake ganinta, sarka uku ya samu a cikin akwatin, abin da ya ba shi mamaki yadda aka yi rubutun takardan ya kasa gane wani yarene, sannan abin mamaki na biyu duk lokacin da ya yi yunkurin bincikar abin da aka rubuta sai wani abin ya gifta ya hana shi, to yanzu yana son sanin gaskiya a kan ciwon Michael ne, hakan yasa yake bincikar kayan mum da daddyn su na baya ko zai sami wani abin, domin a binciken da ya yi a kan matsalar Micheal ya gano akwai sanadin ciwon nasa, shi ba Dr ba ne amma kwakwalwarsa ta fi tasu aiki, yana taɓa aikin likita sama-sama, kasan cewar shi a nitse yake komai hakan yasa ya fi Daddy'n sa da yake babban likita ma iya binciken lafiya mutane, dan kwakwalwar ma ba ɗaya ba. Yanzu haka abin da yasa ya firgita Michael a binciken da ya yi ya gane cewa kwakwalwar Michael tana bukatar a rinƙa kureta sosai, a rinƙa sanya masa tsoro da razana, idan abin ya yi yawa kwakwalwar tasa zata birkice sosai daga nan kuma zata ɗauki matsaya guda. To fah Yana da yakinin cewa tabbas wannan rubutu dake jikin takardan tana da alaka da su, kuma tana da alaka da ciwon Michael, tunani ya fara yi, ko dai ya je ya sa mum dole ta karanta masa rubutunne, dan dai wannan rubutu tata ce. Ɗayan ɓangaren na zuciyarsa ce ta ce masa "Ka manta irin abin da ta muku? Idan har ka kusan ce ta hakan yana nufi ka duƙa kenan? Ka karya maganar ka? Kenan fa ka faɗi idan har ka yi hakan" karo na farko ya ja dogon tsaki, dan shi ba abin da ya tsana a rayuwarsa irin a ce yau ga shi ya nemi wani abu daga wajen wani, baya son wannan ko kaɗan, bai taɓa ba, kuma ba zai taɓa ba, duk abin da yake so, da karfin yake kwata, idan kuɗin sa bai saya masa ba tofa mukaminsa da izzar sa zai karɓa masa, ya fi karfin ya nemi alfarma ko kuma ya nemi shawara, kai shi fa ko irin tambayar mutun wani abu ko hanya ko wani waje, baya yi, a cewarsa ya fi karfin hakan. Baya kula kowa, abubuwa uku da ya kamata ku sani a tattare da shi, shi kansa ma bai yarda wani ɗan adam ya ce masa sorry ba, ya haramta hakan, baya son kalmar a rayuwarsa kwata-kwata idan ka yi gigin gaya masa haka, to wlh zai iya hallaka ka, abu na biyu, a cewarsa babu wani ɗan adam da ya isa ya cewa sorry, ya fi karfin bada hakuri ga koma waye, idan ya maka laifi to ya zamar maka dole ka yafe masa, idan kaki kace zaka yi wata magana, ko a siyasa kake, yana iya sanyaka ka yi dana sanin zuwarka duniya, abu na uku, baya taɓa neman wani abu wajen wani, a cewar sa ya fi karfin yin hakan, komai da izza da isa yake karɓa. Sosai ya zubawa rubutun nan wayan nan dara-daran idon nasa, yana kokarin gane menene aka rubuta a wajen, yana daf da fahimtar wani abu daga cikin rubun ne kamar a mafarki ya ji kukan baby daga palon kasa, ga shi yaron da karfin yake tsala kukan nasa. Ɗaure fuska ya yi sosai dan shi baya son yara ko kaɗan a rayuwar sa (Oh ni Allah shi komai baya so, baya son a masa laifi a ba shi hakuri haka zalika suma yara baya son su, lalai akwai cakwakiya) Dogon tsaki ya ja tare da sanya takardan a drawer bedside, sannan ya fito ya sauƙa palon kasa. Daddy na riƙe da yaron Jay sai ihu yaron yake yana jin yinwa, ya kuma ki ya sha madara. Tga da John suna zaune saman sofa suna latse-latse a wayarsu, sun sha barcin wahala sun ko shi, shi kuma daddy sai zarya yake a palon ya ɗaura yaron a kafaɗarsa yana ɗan bubbuga masa baya, alamar ya yi shiru. Daddy Bawan Allah ya iya reno sosai, ko da yake shi ya yi renon yan ukunsa ai, ba kuma wanda ya taya shi. "Who is this?!!!" Wata gigitatchiyar tsawa Lion ya daga musu, yana tsaye daga saman bene. A ɗari su Tga suka ɗago kansu tare da miƙewa tsaye suna bin Lion da kallo, shiru Lion ya yi bai sake magana ba, ya zuba musu ido yana sauraron amsa kawai. Tga ne ya yi ta maza, ya amsa masa da cewa "Yaron Jay ne, shi ne wadda Michael ya harbi mamansa da gun kace su Major su kai ta asibiti...." Tga bai karisa maganar ba Lion ya sake daka musu tsawa a karo na biyu "Ni na ce su kai ta hospital? Suna da hankali kuwa? Uncle Herry kawai na ce su kai hospital ita kuma na ce su fitar min da ita daga gidan nan" . Tashin hankali Tsuru-tsuru da ido suka yi, dama kuma Tga ya yi mamaki da ya ji cewa Romeo ne ya ce a kai Jennifer asibiti, abin ya ba su mamaki, ashema shi cewa ya yi a je a jefar masa da ita, tab lallai kuwa. Shiru suka yi, har shi kansa daddy ya kasa magana, dan shima kai Jennifer asibiti da a kayi ya ba shi mamaki. "General take this boy out from this house" zaro ido daddy ya yi, me Lion ke nufi kenan? Yana nufin a je a jefar da yaron ko me. Yaro kuwa sai tsala kuka yake yana jin yinwa, shi kuma Romeo yana gama magana ya wuce ya koma part nasa, duk cikin su babu wanda ya yi gigin rokarsa ko ya nemawa yaron alfarma dan sun san Lion idan ya yi magana babu wanda ya isa ya sa shi ya canza, shi kaifi ɗaya ne, kamar dutse yake baya tankwaruwa. Wucewa Tga ya yi, ya karɓi yaron daga hannun daddy ya fice daga palon, daddy kamar zai yi kuka, dan yana son yaron sosai, yana son jika, ga ƴaƴan nasa kuma babu tunanin auren a lamarinsu, duk cikin su ma ba wanda yake da lokacin magana da na miji ma ballantana kuma mace. (Allah sarki daddy haka zaka ci gaba da hakuri, domin koma me suka yi kai ne mai laifi tun da kai ka renesu a kan hakan, kai ka ki yarda ka yafewa mum ɗin su tazo ta basu kulawa, da ita ta renesu ai da lamarinsu ya zo maka da sauƙi, amma renon namiji, ai a mazan zasu taso, uwa uba kuma ba addini hmmm abin ba'a magana) Zama daddy ya yi saman kujera yana tunanin ya Jay zai ji a ransa, irin wannan abin ɗa guda. Shi kuma John ɗan ba ruwana ko a jikinsa, dan shi ko kashe yaron ma a kayi ba abin da zai ji, saboda shi sammakal ne, komai daidai ne irin Michael. Tga kuma yana fita palon ya wuce wajen da ya ɗaure Jay, Allah sarki Jay idan ka gan shi sai ka rantse da Allah baya numfashin ya mutu, saboda yadda numfashin nasa yake fita a hankali-hankali dan wahala, duk wannan hukunci da Lion ya masa, su Tga ba su ga laifin Lion ba, domin a wannan gaɓar a kan gaskiya yake hukunta Jay, dan bai shiga hakkinsu ba, ya ce musu idan suna son mace to su yi aure, kada su kusanci mace ba tare da aure ba, amma Jay ya yi fatali da maganar, dole ya karɓi hukunci. Kusa da shi Tga yazo ya tsaya, Allah sarki jin kukan yaronsa yasa ya ɗan waro wahalallun idanun sa, da suka ji uban jiki, "Jay ina ne family House na su Jennifer?" Ciki ciki Jay ya ke magana, ba ka jin komai sai iska dake fitowa daga bakinsa, matso da kunnensa Tga ya yi daf da bakin Jay ɗin, da kyar ya iya samun damar jin abin da jay ke faɗa na kwatancen in da gidan su Jennifer ya ke. Wucewa ya yi zuwa parking space bayan ya gama jin kwatancen Jay, motarsa ya je ya shiga da yaron, kai tsaye ya hau titin zuwa babban gate. Ko da ya isa gate na farko sai da ya tsaya wannan na'ura tayi scanning na motarsa tsab sannan ta buɗe masa kofa ya fita izuwa babban gate da zata sada shi da wajen. Kai tsaye gidan su Jennifer ya wuce, ya je ya kai musu yaron, yana miƙa musu ya fice, sai tambayar sa suke, ina Jennifer, shiru ya musu bai kula su ba ya wuce abinsa dan ba shi da amasar da zai ba su. Lion kuma yana komawa part nasa ya kwanta saman bed nasa ya mance ma da wata takarda da yake bincika, ransa ya ɓaci, a kan me zasu kai Jennifer asibiti, ya zama dole ya musu hukunci mai tsanani, dan nan gaba su rinƙa tsayawa suna sauraron abin da yake basu umarnin a kai da kyau. To bari mu koma Nigeria dan muga wani lamari ne ke gudana 💓💓KATSINA STATE 💓💓 Bayan tafiyar Yarima shima Nawid ya wuce ɗakin ɗaya da ya sauka a cikin Hotel ɗin. Da shigarsa ɗakin bai yi minti 20 ba ya kira Ibraheem a waya a kan ya turo masa Jehan yana da aiki da zai bata, cikin hanzari Ibraheem ya yi maza ya isar mata da saƙon Nawid, da farko ta ce ba zata je ba, amma daga baya da ta tuna cewa Nawid ya mata rana yau, ya ceceta daga hannun yarima, sai ta hakura ta nufi ɗakin nasa. Jehan mutunce wadda bata manta alkhari komai kankantarsa, in dai ka taɓa mata wlh ba zata taɓa mancewa da kai ba, ko da ka mata sharri daga bayan wannan Alkhari, to zata rinƙa ganin kane da wannan Alkharin, haka zalika bata manta sharrin idan ka mata, komai Alkharin da za ka mata bayan wannan sharri tofa in dai sharrin ka fara yi mata shi zata riƙe. A bakin kofar ɗakin nasa ta tsaya ta kwankwatsa masa, kamar jiranta yake yi dama, cikin sauri ya buɗe kofar. Fuskar sa ɗauke da kayatatcen murmushi ya ce "Sannu ki" ɗaure fuska sosai ta yi kamar wadda aka aikowa da mutuwa, wani irin faɗuwar gaba Nawid ya ji lokacin da ya ga yadda ta ɗaure fuskar tata. "An ce kana nema na lafiya?" Shine abin da ta ce masa, wani wahalallen yawu ya haɗiye kafin ya ce "To malama da farko dai sunana Nawid kuma Ni..." Bata bari ya kai karshen maganar ba ta ɗaga masa hannu alamar bata son jin maganar tasa, shiru ya yi ya zuba mata ido. A yatsene ta ce "An ce kana nema na me kake buƙata, oder me zaka bada?" Ta yi maganar a nitse cikin kwanciyar hankali, da kallo ɗaya zaka mata kasan izza ya samu mazauni a tattare da ita, gata kuma kaifi ɗaya ce, bata magana ta sauya ko me za a yi mata, idan tana magana ɗai ɗai take yin shi, kuma a nitse take, ba ta haɗa ɗaya da ɗaya. Kakalo murmushin dole ya yi, dan harga Allah bai ji daɗin yadda ta tarbe shi ba, duk da cewa izzarta yasa ya kamu da son ta, amma da ta yi masa shi, bai ji daɗi ba. "Malama ki bari mana na faɗa miki sunana tukunnan ko?" Kawar da kanta gefe ta yi kafin ta ce "Sunan ka baya cikin jadawalin tsarin aikina, so please ina ganin girmanka, ka kama kanka, just tell me what you want direct kawai dan ina da abin yi" Ta yi maganar tata cikin harshen turanci, dan har yanzu hausa bai zauna a bakin ta ba, Sosai ya yi mamakin jin yadda take rero turancin nan kamar dan bakin ta a ka yi yaren. Wow ya furta a ransa, a fili kuma daurewa ya yi ya ce "To shikenan tun da baki bukatar jin sunana bari na gaya miki me yasa na kiraki" kara ɗaure fuska ta yi ba tare da ta yi magana ba, kuma bata kalli in da yake ba. "A gaskiya malama ba zan ɓoye miki na cuci kai na ba, ke ɗin kyakyawa ce ajin farko, kuma na kamu da matukar kaunar ki da kallo farko" ko aji kin ta, bata yi wani alama da zai nuna cewa ta ji wani abu ko wani mamaki da jin zancen sa ba. "Malam ba mu sayar da kyau da kuma Kauna a wannan restaurant ɗin nan, daga shinkafa da miyar steew, sai jolof da su tuwon semo, pepper chicken, pizza, burger, shawarma, da dai sauran kananan kayan cima, amma gaba ɗaya cikin jadawalin girke-girken mu babu me ma kace sunan abin cin? Yauwa kyau da kuma Kauna ko? To su dai babu su". Tofa, Babbar magana me Jehan ke nufi kenan?🤔 Mutuwar tsaye Nawid ya yi tare da kara zaro idonsa yana kallon ta da kyau. "A iya sani na ko yan kauye sun san menene so da kuma Kauna, sun san menene kyau, in fact sun san menene aure, amma yarinya santaleliya kamar Jehan gata kalar wayayyu yan gayu, ga iya zuba turanci, amma ta ce ba ta san soyayya ba, anya ba raina min wayo ta yi ba kuwa?" Sai zancen zuci yake. Zazzakar muryar ta ne ta katse masa zancen zuci nasa da cewa "In kawo maka shinkafa irin ta ɗazun ne? Ko dai na yi tafiya ta?" Kara mamaki ya yi sosai "Wai shin da gaske Jehan ta ke yi ba ta san menene soyayya ba ne?" Ya sake tambayar kansa da kansa, tambayar kuma da ba shi da amsarta, domin Jehan ita kaɗai keda amsar, kuma bai ga ala'mar fuskar da zai samu damar tambayarta ba. Ya yi nisa cikin tunani, sai ganinta ya yi ta sa kai zata wuce ta bar wajen, cikin sauri ya fito daga ɗakin, ya sha gaban ta yana faɗin "Haba Malama, ya isa haka zolayar mana please" karo na farko da ta ɗaura idon ta cikin na shi, taɓe baki ta yi, alamar mamaki ma ya bata, "let me pass" shine abin da ta ce masa, Kin matsa mata ya yi, sai ma kara matsowa kusa da ita da ya yi, ya kara kashe murya kasa kasa, irin salon jan hankalin nan ya ce "Haba Malama, ni nasan ba halinki bane saboda ba ki yi kalar wulakanta mutane ba, sannan kuma daga ganinki kin san me nake nufi, kuma kin fahimci ina na dosa, wlh ba son wasa na ke miki ba, har ga Allah nake son ki, kuma aurenki zan yi, ba da wasa nazo ba" tamkar da dutse yake magana haka Jehan ta masa shiru kamar bata a wajen, sai surutu yake zubawa ko uppan bata sake ce mi shi ba, kuma idan baku mance ba Jehan bata da yawan magana bata shiga harkar kowa. Sun jima tsaye a wajen, bata sake magana ba. Da ta ga ji da jin surutan shi sai ta ce "Malam ina son wucewa" mamaki ne ya kama shi kenan yanzu duk wayan nan kalaman soyayya da ya zuba mata bata san su bane ko menene. A zahirin gaskiya Jehan bata gane kalamansa ba, ta dai san soyayya da kaunar bayan haka duk kalaman da ya mata ba abin da ta fahimta, domin da hausa ya yi su, ita kuma kunsan ba jin hausa sosai take ba,. Bawan Allah ya zage sai zuba kalamai yake yi ashe duk a banza ya yi su. Kuma sanin soyayya da Jehan ta yi bawai ta san yadda ake yi bane, a'a kawai dai sunan ta sani, dan ita bata kallon finafinai ma bare a ce zata kalli soyayya a wajen, bugu da kari bata da kawaye ko makamancin su, ba wani abin da ta sani game da soyayya bayan sunan shi soyayya. Ganin Nawid ya yi mutuwar tsaye yana tunani ne yasa ta raɓa gefensa zata wuce, cikin sauri ya riƙo hannunta yana faɗin "Haba malama kada ki min haka, wlh soyayyarki zata iya yi mini illar ki tausaya min, sosai kika mamaye zuciyata, ta ko ina, har ina ji a jikina ba zan iya rayuwa ba sai da ke, kada ki ce ba zaki karɓeni ba..." Ji kake tass ta wake masa fuska da wani gigitacen mari ba tare da ya gama kalameta da yake yi ba, a fusace ta kwace hannun ta daga riƙon da ya mata, rai a matukar ɓace ta bar wajen ta bare da ta yi magana ba. Shiru ya dafe kumatunsa, ya kasa yi mata magana, kuma ya kasa dakatar da ita har ta tafi, ko kaɗan bai ji zafin marin da ta masa ba, sai ma son ta da ya karu masa sosai a zuciyar. (Umm giyar soyayya ba🤣) A gaskiya zuciyarsa ma kara yaba mata yake yi ta yi namijin kokarin, hakan kuma ya kara burgeshi, yanzu ya dace ya kara ɗaura ɗamarar neman aurenta, a cewar sa, domin ita ce matar aure, mace mai kare mutumcin kanta wadda ko hannunta bata yarda wani namijin ya taɓa ba. Sosai Nawid ya sa a ransa dole ya nemi auren Jehan kuma ya zama masa dole ya nemi soyayyarta, ita ta dace da rayuwarsa. (Tirkashi aikuwa ka haɗa hanya da wahala) Jiki ba kwari, tunani cike fal a ransa, ya wuce ya koma cikin ɗakinsa. Yana shiga ya tsaya a gaban mirror ɗakin tare da shafo in da ta maresa da hannunsa ya mannawa hannun nasa kiss, har da wani lumshe ido, shi a dole izzar Jehan da kuma kamewarta sun tafi da imaninsa. Shi ga shi ɗan soyayya. ( Soyayya manya.) Ya ɗan jima tsaye a wajen, kafin ya fara haɗa kayansa dan ya koma Kaduna ya sanar da Ummi abin da ke ransa. Ita kuma Jehan tana koma, kai tsaye cikin office ɗin Ibraheem ta nufa, yana ganin ta tun daga nesa ya zuba mata ido yana jiran ya ji wani bala'i zata sauƙe masa kuma. (Ibraheem na cikin gararin da bala'i Jehan🤣 bawan Allah) "Ibraheem!! Ibraheem!! Ibraheem!! Sau nawa na kira sunan ka?" Shine abin da Jehan ta faɗa lokacin da ta iso wajen, shiru ya zuba mata ido yana kallon ta. Rai a matukar ɓace ta ce "Na ce ka kiramin ogan ka a waya ya zo nan ina son yin magana da shi" "Ki yi hakuri zai zo ranar Jumma'a sai ku yi magana" Ibraheem na gama kai karshen maganar ta wuce ta koma bakin aiki ta, tana tunanin idan ogan su ya zo, ya zama mata dole ta faɗa masa, ba ɗakin kato da zata sake zuwa, domin ita ba yar iska ba ce. Shi dai Ibraheem ido kawai ya bita da shi, dan yanzu shi burinsa ya lallaɓata ta samu ta yi aiki ta biya shi kuɗin sa, shiyasa baya wani biye mata, dan in ta ce ba za ta yi aikin ba, waye zai biya shi kuɗin sa, dan dai yasan gidan su Jehan ba ta in da za'a fitar da dubu ɗari biyar, kuma ko ƙararta ya kai ba ta in da za su iya biyan kuɗin, sai dai ma shi ya sake kashe wa su kuɗaɗen wajen biyan yan sanda da sauransu.. Tofa Jehan yau ake yin ta, ni na haɗa kayana nayi gaba sai mun haɗu da ku a gidan su Aafia gobe idan mai dukka ya kai mu 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode 23-24🌹 GIDAN ABBI💖 A yau a ka dawo da Aunty gida, ba laifi jikin nata ya ɗan yi kyau, amma bata iya tafiya saboda aiki da a ka mata, ba ta iya miƙewa tsaye sosai kamar yadda kowa zai miƙa, dan ma ita ta matsa zata dawo gida shiyasa Irfan ya karɓa mata sallama, baiwar Allah ta damu ne sosai a kan me ya sanya Abbi baya zuwa asibiti sosai, kuma a zahirin gaskiya ba'a faɗa mata me ya faru da ita ba, ba wanda ya gaya mata, ko mamanta da tazo ta yi jinyar ta, ita ma bata san meke damun yar tata ba. Sosai abin ke damun Aunty a ranta, me ta yi wa Abbi ya ke shareta haka. Kusan komai Irfan ya ɗauki nauyin Aunty, ko wani abin take so shi ake kira, ko shi ko kuma Akil ko Imran, Abbi kam ko sun kira shi baya ɗaukar wayar, idan ya kirasu sau ɗaya da safe to sai kuma gobe da safe, Aunty ta yi kuka sosai sannan ta faɗa wa mamanta cewa tana ganin kamar Abbi na fushi da ita, sosai mamanta ta mata faɗa tare da shawari masu kyau a kan ta rinƙa yi wa mijinta uzuri wata kila wani aikin ne ya sha masa kai, hakan yasa Aunty ta matsa kawai su dawo gida, Allah sarki bata san me zata zo ta tarar a gidan ba. A motar Irfan suka dawo, kuma shi ya ɗauko su, ita da mamanta, ita kam Aafia tun da taga Aunty ta farfaɗo ba ta mutu ba shikenan sai ta kama shabgar gabanta abin ta, ta koma ruwa, ta je suna kulla wani abin ita da Rufee. Ko da su Aunty suka shiga cikin gida Abbi baya nan, haka shima daddy'n Jelly baya nan yana part nasu, a palo suka ba je. Ganin sai zufa Aunty ke haɗawa ne ya sanya Irfan kunna musu Ac sanna ya wuce part na shi, shi da Imran, dan suna tare ko ina za su shiga. Allah sarki Imran bawan Allah ya rame sosai sai manya-manyan idanun nan nasa irin na Jelly nan suka kara firfitowa saboda rama, gaba ɗaya fuskar sa ta sauya kamar ba shi ba. Karfe biyu na rana daidai, motar Aafia ya danno hanci cikin gidan, har lokacin Aunty suna falo sai dai su Irfan sun fita basu a gidan, sun sake komawa neman Jelly, bayin Allah, kullun suna zarya tsakanin Kano da Kaduna. Kusan a tare Aafia ita da Rufee su ka fito daga cikin motar, sai wani yauƙi da rangwaɗa Rufee ke yi, ta ci uwar kwalliya kamar wata aljana, ta labka wani uban eyeliner a ido, ga wani purple color jambaki da ta damɓara a bakinta, ko kyan gani babu, kamar mutun ya yi amai. Sanye take da wasu shegun riga da wando sun matseta sosai, wandon jeans ne da kuma riga top ta ɗaura wani jacket mai ɗan girma a saman kayan, wadda yazo mata iya cinyarta, ta zuba attachment a kanta, kamar wata yar kafurai. Sai wani taunan chewing gum take yi tana baza baki. "Aafia anya Auntyn kun nan ta dawo kuwa? Kada na yi zuwan banza ne" ta faɗa tana hura chewing gum da ta ke ci, Aafia tana kokarin rufe kofar motar ta ce "Eh ta dawo mana, kafin ma su baro asibitin yaya Irfan ya ƙirani, ba kin ji ma lokacin da yake cemin na baro gidanku na wuce na same su a gida za su dawo da Aunty ba" Wani nauyayyar ajiyar zuciya Rufee ta sauke, irin ta ji daɗin nan, kai da ganin Rufee kasan ba zuwar Allah da annabi ta yi ba, akwai wata manufa da ya kawo ta, ba duba jikin Aunty tazo ba, ko daga yanayin shigarta zai tabbatar maka da cewa ba dubiya ta zo ba, akwai dai wani abin. Jerawa suka yi zuwa cikin falo. Aafia ce ta kwaɗa sallama, Aunty na kwance saman sofa idon ta cike tab da kwalla abin tausayi, ita kuma maman Aunty ta shiga kitchen dan yi musu girki. Wani mummunar faɗuwar gaba Aunty ta ji lokacin da idon ta ya sauƙa kan Rufee, kasan cewar mace ita mai addini hakan yasa ta yi saurin karato addu'ar neman tsari daga wani mugun abu ko iska ko ɗan adam ko dai abokin gaba. اللَّهُمَّ مُنْزِلَ الْكِتَابِ، سَرِيْعَ الْحِسَابِ، اهْزِمِ الأحْزَابَ، اللَّهُمَّ اهْزِمْهُمْ وَ زَلْزِلْهُمْ Tana karanta addu'ar ta ji zuciyarta ta samu kwanciyar hankali. Saman sofa Aafia ta zauna tana faɗin "Rufee kizo ki zauna, wannan ita ce Halimar sai ku gaisa, ki yi sauri mu wuce ɗaki dan na ga ji ina son in yi wanka" Wani shu'umin murmushi Rufee ta yi wadda ya sanya Aunty tantama a kan ta. Kusa da Aafia tazo ta zauna tana faɗin "Ke Aafia ba ki da kunya yanzu matar Abbin ne kike kiran sunan ta kai tsaye haka? Gaskiya baki kyauta ba" Mamaki ya hana Aafia magana, tunani ta fara yi "ko dai basaja Rufee ke yi wa Aunty ne, amma in ba haka ba ai ita ce ta ce mu rinƙa kiran Aunty da sunan ta Halima, shine kuma yau dan a gaban Aunty ne zata wani ce min bani da kunya, lallai Rufee anyi yar duniya" Aafia tana can duniyar tunanin makirci irin na Rufee, ita kuma Rufee ta zamo kasa daga saman kujera, ta zube gwiwowinta a kasa ta ce "Mummy ina wuni? Ya jiki?" Tashin hankali zaro ido waje Aafia ta yi, tamkar idanun nata za su faɗi kasa, ta fara tsorata da lamarin Rufee, har da zubewa kasa tana gaishe da Aunty anya kuwa. Aunty kuwa tun da ta karanta addu'ar nan sai ta ji karfin gwiwa, kuma ta ji bata shakkan komai, dan haka sai ta ce da Rufee "Lafiya lou Alhadulillah, jiki kuma da sauƙi" Shiru Rufee ta yi ta kasa magana kuma ta kasa mikewa ta koma saman sofar, kamar wadda ta yi sumar zaune, da alama dai Akwai wani abin da ta shirya wa Aunty ne, Allah kuma bai nufa zai kama ta ba, shine ya sanya jikinta ya mutu. Ta ɗan jima a wajen ta kasa tashi, har sai da Aafia ta taɓa tare da kiran sunan ta, sannan ne ta ɗan firgita ta miƙe ta koma saman sofa ta zauna. "Rufee ba zama za ki yi ba, mu wuce ɗaki kawai, dan na je na yi wanka" Aafia bata gama Rufee baki ba, suka ji shigowar motar Abbi cikin gidan. Da murna Aafia ta miƙe tana faɗin "Ga Abbi nan ya dawo ki tsaya ku gaisa sai mu wuce" Wani kululun bakin ciki ne ya tokarewa Aunty maƙoshi, har ga Allah bata son Abbi ya kalli Rufee, tana ki shin mijinta sosai, to amma ba yadda ta iya, bata isa ta yi wa Aafia wata magana ba, ga shi kuma ba lafiya ke gareta ba, yanzu idan ta yi wata magana suna iya samun matsala da Aafia, hakan ya sa ta ɗaure, ta danne, ta cije, har wa su siraran hawaye ya fara bin gefe da gefen idonta, kasan cewar tana kwance ne hakan yasa hawayen ke gangarawa ta kunnanta. Ita kuwa Rufee lokacin da ta ji abin da Aafia ta ce, sai ta ji wani mugun sanyi ya dira mata a zuciyar ta, har da wani sauƙe nauyayyar ajiyar zuciya, sai wani kara fari da ido ta ke yi. Suna wannan hali Abbi ta shigo bakin sa ɗauke da sallama, duk da cewa ya rame saboda damuwa, hakan bai hana shi yin kyau ba, ya sha dakakkiyar shaddasa sky blue, ɗin kin ya masa kyau sosai. Tun da Rufee ta ɗaura idon ta a kan shi take ta haɗiyar yawu, kamar wata mayya, cikin sauri ta zura hannun ta a cikin jakarta, cikin dabara ta lakuto wani abu kamar mai, ta shammaci su Aafia ta shafa a idanuwanta. Abbi na karisowa cikin falon Rufee ta yi saurin karisawa in da yake, ta sanya hannu ta karɓi jakar computer dake hannunsa, tana faɗin "Sannu da dawowa Abbi" Galala Aafia ta wangale baki tana kallon ikon Allah, Aunty kuwa, tsabar shiga tashin hankali bata san lokacin da ta miƙa zaune ba. Shi kuwa Abbi yana kokarin janye jakar computer sa kada Rufee ta karɓa, a nan ne aka yi rashin sa'a idanunsa suka sauƙa a cikin tata. Wani irin zirr ya ji a jikinsa kamar wadda aka yi wa allura, lokaci guda ya ji wani irin yanayi, ji yake duk duniya ita kaɗai yake so. Ya kasa ɗauke idonsa daga kallonta, har ta karɓi jakar nasa tana faɗin "Abbi ina ne ɗakin ka na kai maka jakar" tana magana tana kara fari da ido. Da hannu ya nuna mata sama, ya kasa magana, kallonta kawai yake, yana jin tamkar ya riƙota, zuciyarsa na azalzalansa da so da kuma kaunar ta, lokaci guda Abbi ya zama kamar wawa kawai binta da ido ya ke yi. Aunty da Aafia yau sun ga duniyanci, sun ga abin da ya fi karfinsu, dukkansu an rasa mai bakin magana, sun yi mutuwar tsaye, ba abin da Aafia ke kallon fa ce yadda Rufee ke ta faman yi wa Abbi rakwarkwasa, da karairaya, Abbi ya sake baki kamar wawa yana bin ta da ido, har wani fari take masa da ido, abin ma gwanin ban haushi, ba kyan gani. Ita kuma Aunty yadda Abbi ke bin Rufee da ido kawai take gani, ji take tamkar ta haɗiyi zuciya ta mutu dan haushi, Allah sarki. Wucewa ta yi tana wani yauƙi ta nufi sama, hannunta riƙe da jakar, shima Abbi wucewa ya yi, ya bi bayanta, ko kallon in da Aunty da Aafia suke bai yi ba. Tsabar bakin ciki Aunty bata san lokacin da ta ce "Ke dan uban ki zoki wuce ki bar gidan nan" Tamkar ba da ita ake ba ta wuce abinta ta haye sama, shima Abbi bai kula Aunty ba, Aafia kam babu bakin magana. Sai bayan Abbi da Rufee sun haye sama ne Aunty ta dawo da kallonta kan Aafia. "Kin cuceni Aafia, kin cuci rayuwata, ki rasa wa zaki kawo mini gidan nan sai wancan tsinanniya, mai kama da yan kwalta ɗin, Allah ya isa tsakanina da ke Aafia, Allah ya isa mini" tana magana tana hawaye, ga shi ba damar ta tashi. A wulakance Aafia ta ce "Ke Halima wlh ki iya bakin ki, idan ba haka ba, sai na tattaka ki a nan wajen banza kawai" Aunty za ta yi magana mamanta ta shigo falon bakin ta ɗauke da sallama. Wucewa Aafia ta yi ta haura sama ta barsu a nan. Tana kokarin shiga bedroom nata Rufee ta fito daga bedroom na Abbi, sai wani washe baki take yi. Aafia na son yi mata magana amma ta kasa, har ga Allah abin da Rufee ta yi sam bai yi wa Aafia daɗi ba, ta ji haushin hakan, sai dai ba zata iya ce mata komai ba, already Rufee ta riga ta kai sunan su wajen Malam, ba wanda zai iya mata gardama ko ya ja da maganar ta acikinsu. "Ke Aafia me ki ke wani kallona haka, kamar na ce ina son Abbin ki? Ni fa kawai jakarsa na agaza mi shi da shi, na kai mi shi ɗakinsa, ko na yi laifi yin hakan? Kuma ai nafa ita Halima bata iya kula da miji bane, shiyasa nake nuna mata example". Girgiza kai Aafia ta yi, kamar wata wawiya, a sanyaye ta ce "A'a baki yi laifi ba, mu je ɗakina bari na yi wanka" girgiza kai ita ma Rufee ta yi kafin ta ce "A'a zan wuce sai mun haɗu kawai" (Shegiya kin gama aikin da ya kawo ta, dole kice zaki wuce ai) Tana kai karshen maganar bata jira amsar Aafia ba ta wuce ta nufi kasa, rai a ɓace Aafia ta wuce cikin bedroom nata. A ɓangaren Aunty kuwa, Aafia na wucewa, mamanta ta ce "Sadiya me ya haɗa ki da yar taki? Na ji kamar kuna magana mara daɗi wa junan ku" Goge hawayen fuskar ta Aunty ta yi, dan kada mamanta ta gani, saboda kullun tana mata nasiha a kan hakuri da fawwalawa Allah komai. "Babu komai Inna kawai naga ta dawo ranta a ɓace ne shine nake tambayar ta". Wucewa Inna tayi ta nufi wani ɗaki dake kusa da Kitchen tana faɗin "To dai ki rinƙa yi mata a hankali dan kin san yarinya ce, ku zauna lafiya da juna". Kasa amsawa Aunty ta yi saboda azaban bakin ciki da ta ke cikin zuciyarta. A wannan hali Rufee ta sauƙo ta sameta, a tsakiyar falon ta tsaya, ta fara bin Aunty da kallon banza daga sama har kasa. A wulakance ta ce "ƴan kwanaki suka rage miki" tana kai karshen maganar ta wuce ta nufi hanyar fita daga falon. Tana fita daidai lokacin daddy'n Jelly ya fito daga part ɗin Irfan, ya nufo cikin gida, zai zo ya yi wa Aunty ya jiki, dan ya ji Abbi ya dawo, kuma dama idan ba dole ba, baya shigowa part ɗin nasu sai Abbi na nan. Mutuwar tsaye Rufee ta yi tana kallonsa, ga shi kuma yau shigar kananan kaya ya yi, yar ramar da ya yi ma kyau ta kara masa, daddy'n Jelly ba baya wajen kyau, da shi Jelly ke kama, ga golden eyes nasan nan ba'a magana gasu manya-manya kamar ball, ya fi Abbi kyau nesa ba kusa ba, kuma shi idan ka ganshi zaka ce matashi ne, domin kuwa bai da wani shekaru sosai, kuma yana da karamin jiki, auren wuri ya yi, shiyasa ya haifi Jelly. Rufee ta kasa motsawa har ya zo ya wuce ta, da yake shima ba mai shiga harkar mutane ba ne, sai bai ce mata ko sannu ba ya shiga cikin falo. A sukwane ta juya ta bi shi da kallo har ya kurewa ganin ta. Afili ta furta "No ya zama dole na kunce aikin da na yi wa Abbi ya dawo kan wanna saurayin, kai kaga kyau iya kyau, tab dole naje wajen malam gobe". (Tofa ke Rufee ruwan ido ne zai kashe ki, ke kowa kina so anya kanki ɗaya kuwa?) Ta ɗan jima tsaye a wajen tana tunanin ya zata ɓullowa lamarin, kafin ta sa kai ta fice daga gidan, ta fita bakin titin ta tari abin hawa zuwa gida, da waje bata zo da motar ta ba. Shi kuwa daddy'n Jelly ko a jikinsa, ya je ya gaishe da Aunty ya fito ya koma part nasu. Allah sarki Aunty ji take kamar zata mutu, Abbi ya dawo bai kula ta ba, ko sannu bai ce mata, kamar bai ganta ba, ga shi kuma ya kara mata wani bakin cikin na yarda da Rufee da ya yi ta karɓar masa jaka. (To Aunty sai dai muce Allah ya fitar da ke, mu dai bari mo leƙo Jelly muga wani hali take ciki) 💖GIDAN ABBO💖 Zaune Nawid ya ke saman sofa a falo, ya yi shiru yana tunanin yadda zai ɓullo wa abin da ke faruwa, domin har cikin ransa yana zargin Abbonsa. Ya yi nisa cikin tunani Jelly ta watso a guje tana ihu, a sukwane ya miƙe zai gudu dan ta tsorata shi, har wani kaɗawa hantar cikinsa ya yi, dan har ga Allah bai san zata zo ba, wani sufa ya yi ta saman sofa zai yi waje, kamar wani jikan chinawa haka ya yi, bawan Allah. Ganin ya da ka tsufa ta saman sofa zai yi waje ne yasa Jelly ta ce "Kai yaya Nawid ashe kai ma ɗan China ne, ashe ka iya firewa". Cak ya tsaya, a fusace ya juyo dan har ga Allah bai san ita ɗin ba ce. "Ke ni kam anya ke mutun ce kuwa?" Ya tambaya yana kare mata kallo. Sanye take da riga da wando, wandon jeans da riga mai dogon hannun, rigar tata kamar bargo haka jikinsa yake da laushi, saboda sanyin da ake yi, sannan rigar a iya kugunta ya tsaya, kayan sun zauna a jikin ta, gata kuma dama da shape sosai, ga shi an fara zama yan mata, komai na daɗa bayyana Masha Allah, kanta babu ɗan kwali, ta saki wannan bakin gashin fulanin nata, ya sha gyara wajen Ummi sai sheki yake yi. Cikin sauri ya kawar da kansa daga kallonta domin har cikin zuciyarsa ya ji wani yanayi, ganin ta ba dressing mai kyau duk surar jikinta a bayyane ya sanya zuciyarsa wani mummunar tunani a kanta, cikin sauri ya kori sheɗan ya koma ya zauna tare da ɗaure fuska sosai ya ce "Me ya fito da ke da gudu haka? Ina kuma Ummi?" Turo ba ki ta yi, kafin a shagwaɓe ta ce "Ummi ba ta nan, ta shiga cikin gida" "To baki bani amsa ba, me ya fito da ke daga cikin ɗaki da gudu haka, har ma da ihu". Yar dariya ta yi kafin ta fara bashi labari "Ina zaune ina kallo ne sai naga wata yarinya tana gudu tana ihu wasu maza na binta, suka shiga cikin wani falo, a cikin wani gida, suna shiga falon sai yarinyar ta ɗauko wuka ta fara nuna musu tana faɗin...." Bata karisa maganar ba ta wuce saman table in da aka ajiye wata yar karamar wuƙa cikin kayan fruits. Yana zaune yana kallonta, da gudu ta yi kansa da wukar tana faɗin "Idan ka matso kusa da ni sai na yanke ka" tana magana tana gyadawa da karfi. Ganin da gaske wannan zata iya buga masa wukar nan, ta jimi shi ciwo ne ya sanya ya miƙe yana faɗin "Ke baki da hankali ko?" Turo baki ta yi kafin ta nufi saman table ta mai da wukar tana faɗin "To ai zan nuna maka yadda matar ta yi ne, wai ma yaya Nawid kai komai na yi, ban maka ba, komai na yi sai ka zageni" "Dole na zage ki, yanzu na ce ki nuna mini yadda matar ta yi ne?" Ya yi maganar yana kokarin gyara zaman shi. "Dama ai ba kai zan nunawa ba, gwada kaya na nake yi ko zan iya nima, kai ne nan ka tsayar da Ni kana tambayata me yasa na fito ina ihu, to abin da na fito gwadawa kenan". Haushi ma ya hana shi yin magana, dan in ya ce zai biye mata tsab zai karya ta koma ya sumar da ita gaba ɗaya, yarinya kamar sheɗan ya mata fitsari a kai, cewarsa. Ganin ya mata shiru ne yasa ta juya zata wuce cikin ɗaki, bata kai ga karisa juyawa ba idon ta ya sauƙa kan wani ɗan karamin kwaro dake tafiya a kan ƙafarsa, irin karon nan ne dake bin sanyi. Da karfi Jelly ta ɗaga kafarta ta sauke masa a kan nasa, har wani kara ya bada, Nawid bai san lokacin da ya saki ihu ba, domin bai lura da lokacin da ta ɗaga kafar tata ba, hankalinsa na kan wayarsa dan ya ce baya son sake ganin ta a irin dressing da taken nan, shiyasa ya ɗauke kansa daga kallonta. Jin ya yi ihu yasa ta ce "Yaya Nawid kai fa Allah kamar mace kake, kai rago ne, yanzu kashe kwaron ka ke yi wa kuka? Allah sai na maka irin ta Ram Charan yake ko waye, wannan dai na cikin Tv nan, sai kana barci na ɗebo ruwa yana tafasa a wuta na zuba maka, yadda Ram ya yi wa abokinsa a Tv bayan sun ɓata". A fusace Nawid ya miƙe zai wanka mata mari Abbo da ya shigo tun ɗazun kyan Jelly da dressing tata sun ja hankalin sa ya kasa magana, kuma ya kasa karisowa cikin falon, ya tsaya kawai ya zubawa Jelly ido, sai da ya ga Nawid zai mare ta sannan ya ce "Kada ka kuskura ka taɓa ta, baka ganin yarinya ce kuma bata da lafiya". Sosai Nawid ya kara yin mamaki "wai ba jiya Abbo ya ce yarinyar nan tsintaciyar mage bace, baya son ta baya kaunar ta, me kuma yasa ya dawo bayan fage yana kareta" Nawid ne ya tambayi kansa a cikin zuciyarsa. Wucewa Jelly ta yi tana turo baki tana kunkuni ciki-ciki, ta shige ɗaki abinta, shima Abbo zuwa ya yi ya wuce zuwa na shi ɗakin. Nawid kam ya kasa magana tunani kawai yake a kan Abbo, sannan ga in da Jelly ta dakesa ya masa zafi sosai, dan da iya karfinta ta take masa kafar nasa. Yana zaune a wajen Har Abbo ya sake fitowa, dama Abu yazo ɗauka. Ko sannu bai ce da Nawid ba, ya sa kai ya fice abinsa. Yana fita ba jimawa Ummi na shigowa bakinta ɗauke da sallama, ka sa amsa mata sallamar Nawid ya yi. Bata wani damu ba tazo ta zauna kusa da shi tana faɗin "Baka fita zuwa asibiti bane Nawid?" Da kyar Nawid ya iya ce mata "E Ummi ban fita ba". "Lafiya Nawid na ganka cikin wani yana yi?" Ta tambaya tana kare masa kallo. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Ummi dan Allah ki fahince ni ba wai zan miki gyarane dan kin gaza ko wani abu makamancin hakan ba, na san ke mace ce mai hankali, ilimi, addini, da kuma hakuri, to amma a wannan fannin kin kaza, bana ganin laifin ki saboda baki taɓa haihuwar ƴa mace ba, sannan kuma kema ke kaɗai ce mace a wajen kaka, baki taso kinga yadda ake kula da ƴaƴa mata ba, wannan dalili yasa ni bana ganin laifin ki". Zuba masa ido Ummi ta yi tana kallon cikin kwayar idanuwansa masu ɗauke da damuwa turun. Ci gaba da magana ya yi "Ummi dan Allah ina so idan zaki fita anguwa, koma ina ne ki fita tare da baby, kada ki barta ita kaɗai a cikin gidan nan, yin hakan babban haɗari ne, wlh ko jiya a asibiti sai da na yi wa yarinya yar shekara 3 ɗinki saboda fyaɗen da wani azzalumi ya mata, kuma kinga gidan ba mu kaɗai bane ga su Sadiq suna nan, ba wai ina zarginsu ko wani abu bane, a'a kawai dai kula ce, ka kula da kayan ka, ya fi kazo kana cikiya, kuskure kaɗan za ka yi a tarbiyar ƴa mace ya zama mata babban illa, kuma zai iya zama sanadiyyar tarwatsewar rayuwar ta gaba ɗaya, sannan Ummi dan Allah wasu dressing ɗin baby ta dai na yin su, kinga yanzu ta fara zama cikakkiyar mace, koda a gida ne ta daina saka su, saboda bamu san wani irin bako za mu yi ba, kuma idan kika duba mai son abinka ya fika dubara". Sosai Ummi ta ji nasihar Nawid har cikin ranta, dama bata taɓa kawo hakan a ranta ba, kuma dama haka ne wani abin sai an nusassheka ka ke iya gane hakan, ta yi kukan zuci a kan abin da ya faru da yarinyar da Nawid ya yi wa ɗinki jiya, ta kuma kudiri niyyar kula da Jelly sosai fiye da a baya, ta wani ɓangaren kuma ta ji daɗi sosai, domin a tunanin ta Nawid ya fara son Jelly shi ya sa ya fara kishinta. "Nawid na san ba iya wannan ne abin dake damunka ba, ka faɗa mini gaskiya me kake ɓoye min" Ummi ce ta sake jefo masa tambaya tana tsare shi da ido. Dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali, sannan ya fara magana "E Ummi ba shikaɗai ke damu na ba, akwai wani matsala dake cin min tuwo a kwarya, ke mahaifiya tace, bani da kamar ki, ba zan iya ɓoye miki komai ba" Cikin sauri ta ce "Menene wannan kuma? ina jinka faɗa mini" Juyowa ya yi suna fuskantar juna sosai, ya riƙo hannayenta cike da kaunar ta ya fara magana "Ummi ki yi hakuri da abin da zan faɗa, amma ya zama dole na gaya miƙi, wata kila ke kina da hanyar iya maganin abin" tsare shi da ido kawai ta yi tana kallon sa, tana jiran ta ji me zai faɗa. "Ummi ina zargin Abbo kamar yana da wata manufa a han baby" zaro ido sosai Ummi ta yi, har haɗe words ta ke wajen cewa "Wani irin manufa kuma Nawid?". "Ummi yanzu idan a ka ce miki Abbo yana son baby ya za ki yi?" Dariya sosai Ummi ta yi, kafin ta ce "Nawid har yanzu kai yarone" "Yaro kuma Ummi?" Gyaɗa masa kai ta yi, tana faɗin "E mana Nawid banda kai yaro ne tayaya Abbonka zai so baby? To ma idan ya sota ya yi yaya da ita? Kada fa ka manta Abbonka matansa huɗu, bayan gidan nan akwai nasu Zainab ka sani, ina hakan ma ba zai yiwu ba". Shiru Nawid ya ɗan yi kafin ya ce "Amma Ummi ai abin da Abbo yake a kan babay ne abin ya yi wa sosai". Miƙewa tsaye ta yi tana faɗin "A'a ba wani yawa, kawai ɗoukin soyayyar yaya mata ne ke ɗibarsa, kada ka manta bamu da ƴa mace fa, kawai kaunar ta ya ke yi, dan haka ka dai na kawo tunani mara kyau a zuciyar ka, ka yi mana fatan alkhari kawai" ta kai karshen maganar tare da nufar ɗakinta tana faɗin ina babyn ma take, tazo na shiryata mai kunshi zata zo ta yi mata. Shidai Nawid ya kasa magana tunani yake a zuciyar sa "Lallai Ummi kin yi nisa, yanzu in banda ke da abin ki, Abbo yana da mata huɗu, ƴaƴan sa mata sun kai shida dukka bai yi ɗouki a kansu ba sai kan baby tsintaciyar mage, anya Ummi ba amiki wani abin ba kuwa?". Sai zan cen zuci yake yi bawan Allah, abin ma yaso ya wuce tunaninsa. (Nan na barosu na haɗa kaya na zuwa, wajen Jehan) 💗💗Super restaurant💗💗 Sai karfe 6 na yamma Jehan ta baro restaurant, sai sauri take ta nufi bakin titi dan tarar abin hawa zuwa asibiti, daga bayanta ta ji murya ana faɗin "Sannunki yan mata" kin juyawa ta yi, ta ci gaba da tafiyarta kawai, dan ba komai take kulawa ba. Cikin sauri ya sha gaban ta, matashine wadda ba zai fi shekara 23 ba. Kallon sama da kasa ta masa, kafin a wulakance ta ce "Lafiya ka tare min hanya?" Yar murmushi ya yi tare da fito da wayarsa kirar Tecno camon 11 yana faɗin "Wlh yan mata kin yi mini ne, idan ba damuwa ki zuba mini shaɗatar ki a nan" ya yi maganar yana miƙo mata wayarsa. Tsabar bakin ciki ta ɗan jima kafin ta ce "Sai ka rasa uban waye yake koyawa yaran nan wasu abubuwan, zaka wuce ka je ka yi firsari ka je ka kwanta dare ya yi ne ko sai na ɗauki bulala na zane maka jiki? Yara kanana sai wani iya shege, yanzu ni ce zan baka number ta, lallai yaron nan" Da turanci ta yi maganar. Kasan cewar yana jin turanci hakan yasa ya gane me take nufi, ya sha ruwan mamaki, cikin sauri ya fara bin jikinsa da kallo, ya tsurawa gaban sa ido yana son gane me Jehan ta gani ta ce masa yaro. Wucewa ta yi abinta, ta bar shi a nan tsaye yana yan dube dube a jikinsa. Mashin mai taya biyu ta tara ta hau zuwa asibiti, kamar kullun yauma ta sayowa su gwaggo abinci a restaurant nasu, dama kullun idan zata dawo zata sai takeaway guda uku, Sadiq ɗaya, gwaggo ɗaya, sai maman Sadiq ɗaya, ita bata wani damu da cin abincin dare sosai ba, Sadiq yana sayo mata maltina ta sha ta yi barci abinta. Kamar kullun tana isa asibiti Sadiq yana isowa, a tare suka jera zuwa cikin asibitin, sai murna Jehan take, an ce gobe mum zata farfaɗo. Allah sarki gwaggo ta rame sosai kamar ba ita ba, kusa da ita Jehan ta zauna, tana kallon fuskar mum ɗinta. Mum kamar ba mai jinya ba ta yi ƙiba sosai, saboda karin ruwa da jini da aka mata. Gaishe da gwaggo Jehan da Sadiq suka yi, sannan suka tambayi jikin mum, da fara'a gwaggo ta amsa, Jehan zata sake yin magana wata hamshakiyar Hajiya wadda da ka ganta kasan nera ta zauna mata, tasha kwalliya da sarkan gold, ta zuba abin hannu shima na gold, ga wani dankareren lace da ta sanya a jikinta abin ba'a cewa koma. Kariso wajen na su ta yi, tana faɗin "Hajiya Aisha wayan nan kuma su waye ne?" Ta yi maganar tana nuna Jehan da Sadiq, Nan gwaggo ta gaya mata ƴaƴan ta ne. Murmushi Haniyar ta yi tana faɗin "Kai amma suna da kyau sosai wlh" shiru gwaggo ta yi bata sake magana ba, su Jehan da Sadiq ba wanda ta tanka matar a cikin su, shi Sadiq dama ɗan abi yarima ne a sha kiɗa, duk abin da Jehan ta yi, shi yake yi shima, to da ya ga Jehan bata kulla matar ba, shine shima ya ki kulata. Cikin gwababɓen fulatanci Jehan ta tambayi gwaggo wace ce wannan Hajiya, nan gwaggo ta gaya mata, kanwar Hajiyar ce a ka kwantar a ɗakin kusa da su tana jinya, yau Hajiyar tazo daga Abuja duba jikin kanwar tata. Shiru Jehan ta yi bata sake cewa komai ba, gaba ɗayan su shiru suka yi kowa da abin da yake tunani Yau sun jima sosai a asibiti, sai wajen karfe 10:20 sannan suka sallami gwaggo Jehan ta bata abincin ta suka wuce zuwa gida, sun bar gwaggo tare da wannan Hajiya suna hira. Yau kasan cewar sun yi dare ko da suka fita bakin titi basu sami abin hawa ba, hakan yasa suka fara ta fiya da kafa, suna yi suna hira, har suka ci karfin tafiyar ba tare da sun sani ba. Basu ankaraba sai sukaga har sun kusa isowa anguwarsu, hakan yasa suka ce bari su karisa da kafa kawai. Sun ci gaba da tafiya suna hira, sun zo daidai hanyar da zata shigo da su anguwarsu wasu jibga-jibgan mutane masu bakin kaya da kuma bakin marks a fuskar su, suka tare su. Daga Jehan har Sadiq sai da suka kusa sakin fitsari a wandon su, nan take jikinsu ya fara kerma, ga shi wayan nan mutane za su kai su goma, ga shi baka iya gane ko ala'mar kamannin su, saboda dare ne sosai akwai duhu, kuma koda ma ba dare bane, sun rufe ko'ina a cikin su, ba zaka gane su wanene bane. Ɗaya daga cikin su ne ya matso kusa da Jehan ya fara magana kasa kasa "Ke ina wayar da kika yi recorded na oga Farooq? Ki bamu wayar ko kuma mu kasheki a nan, kuma mun kashe banza" Wani wahalallen yawu ta haɗiye, nan take zufa ya fara karyo mata, ina amafanin karyar da ta yi, ta tambayi kanta. Tana kokarin yin magana, suka ji jiniyar motar yan sanda sun zo wucewa, a guje wayan nan mutane suka bar wajen, ita kuma Jehan da sauri ta juya ta nufi hanyar komawa asibiti, tana sauri tana tunani a ranta ta ja wa kanta bala'i, a tunanin ta komai ya wuce, ta tseratar da Hanan, sai ga shi ita kuma ta jefa kanta cikin bala'i. Da sauri Sadiq ya bi bayanta, har suna haɗawa da gudu, Sadiq ya ce "Jehan me kuma zai mai damu asibiti? Tun da sun tafi mu wuce gida mana" girgiza kai ta yi tana faɗin "A'a Sadiq ba zancen komawa gida, tun da ka ga sun tare mu a nan to tabbas sun san gidan mune, Farooq ya gaya musu in da gidan mu yake, shi ya sa suka zo suka tsaya a bakin unguwar mu, yanzu dole asibiti zamu koma, zan je in sanar da su gwaggo meke faruwa" tana magana tana kwaɓawa da turanci. Haka suka sake takawa da kafa har zuwa asibiti, dan ba abin hawa, kasan cewar kauye ne da wuri suke shiga. Yadda suka bar gwaggo da Hajiya haka suka dawo suka same su, cike da tashin hankali Jehan ta sanar da gwaggo abin da ta aikata, na karyar da ta yi wa Farooq na tayi recorded na muryan sa yana yiwa Hanan maganganun banza, ga kuma abin da karyan ta zamar mata. Sosai gwaggo ta shiga tashin hankali ta kuma yi mata faɗa sosai, a kan ba yanzu ba ko gaba ta guji yi wa mutun karyar abin da ta san bata aikata ba, ga shi yanzu ta ja musu bala'i. Sun shiga tashin hankali sun rasa mafita, idan suka ce Jehan ta koma gida, to tabbas wayan nan mutane za su iya bin dare su mata yankar rago, domin Farooq ba shi da mutunci ko kaɗan, zamanta a asabiti kuma ba zai yi wu ba, hakan ya sa suka fara neman mafita ta hanyar shawara. A nan ne wanann Hajiya ta ce musu idan ba damuwa zata tafi da Jehan zuwa gidan ta, daga nan zata sama mata aiki a gidan masu kuɗi, ko wani wata za'a rinƙa biyan ta dubu ɗari, idan anyi mata salary Hajiyar zata rinƙa turowa su gwaggo. Babu tunani babu komai gwaggo ta miƙawa Hajiyar nan Jehan domin ita burinta kawai Jehan ta tsira da ranta, bata son wani abin ya sameta, rubuta musu number wayarta Hajiyar ta yi tare da address ɗinta na Abuja da kuma gidan iyayenta dake nan Katsina. Gwaggo ce ta karɓa takardar sannan suka yi wa Haniyar godiya, gwaggo ta ce Sadiq ya koma gida da safe Hajiya zata wuce da Jehan Abuja, kwata-kwata sun manta da zancen aikin Jehan, sun kuma mance da Ibraheem na bin su bashin kuɗi. (Toh fah, haka za ku yi wa Ibraheem, shi yana can yana kokarin yadda zai lallaɓa Jehan ta samu ta yi aiki ta biya shi hakkinsa, lallai akwai cakwakiya) Haka Sadiq cike da tsoro ya koma gida yana ta tunanin Jehan, ya yi sa'a daya bi hanyar mutanen basa nan, sun gudu, saboda yan sanda dake zagaye a wajen dan maka yan shaye-shaye, ita kuma Jehan a asibiti ta kwana a kan gobe za su wuce Abuja da Hajiya ta kai ta gidan aiki. Sai dai bata ji daɗin rabuwa da su gwaggo ba, amma bata da mafita dole ta bi Hajiya. To bari dai mu leƙo Washington DC mu dawo 💓💓Washington DC💓💓 Zaune suke gaba ɗayan su a palon kasa, ban da Lion da kuma James da baya nan, sai uncle herry dake asibiti shima baya nan, Jay ma yana wajen punishment nasa, dan yau tun safe ya dasa daga in da ya tsaya. Dukkansu kowa za abin da yake yi, Tga da John sun kafa kai a kan wayoyinsu suna latsawa, shi kuma daddy yana kallon News a makeken Tv su, while shi kuma Michael yana buga game a system. Dukkan su kayan shan iska ne a jikin su, barim ma Tga shi ko riga ma bai saka ba, daga shi sai gajeren wando, ya bar wayan nan dama daman damtsen hannun nasa a wajen, ga sarkan kros daya sanya a wuyarsa, sai sharholiyar su suke banda Jay. Cikin nitsuwa Musharraf ya sauƙo daga sama izuwa cikin palon. Sannu ya musu sannan ya wuce zai zauna saman sofa. Dukkan su ba wanda ya amsa sannun na shi. Tsawa Tga ya daga masa wadda ya sanya gaba ɗayansu ɗagowa "What brought you here?!!" Kallon Musharraf Michael ya yi sanna ya dawo da kallon sa kan Tga da yake ta wani cika yana batsewa, Allah Sarki Musharraf har jikin sa ya fara kerma, kasa zama ya yi saman sofar, ya tsaya yana kallon su. A fusace Tga ya ce "Ba da kai nake magana bane?!" Shiru Musharraf ya yi dan ba shi da amsar da zai ba su, miƙewa Tga ya yi yana wani huci ya ɗaga hannu zai mare shi, cikin sauri Michael ya miƙe ya riƙe hannun nasa yana faɗin "No uncle me ya maka?" Kwace hannunsa Tga ya yi ya nuna Musharraf yana faɗin "Kada na sake ganin kafarka a palon nan, a word room zaka rinƙa zama". Jikin sa har kerma yake yi ya wuce zai koma sama, Michael ya ce "Come back uncle" tsayawa Musharraf ya yi ba tare da ya juyo ya dawo ba. Karisawa wajensa Michael ya yi yana faɗin "Uncle T wannan fa uncle ɗin James ne, kuma duk abin da James yake so nima ina son shi, dan haka ya zama dole uncle ɗin James ya rinƙa zama a duk in da yake so a gidan nan, duk in da James zai iya shiga a cikin gidan nan, nima zan shiga kuma shima uncle ɗin James zai shiga, ba kuma wanda ya isa ya hana shi, saboda James" Tga zai yi magana sai ya tuna Akwai camera a palon yanzu haka Lion na kallonsu, kuma sun san shi Lion idan ya fito bayan Triplets nasa yake bi, koda kuwa basu da gaskiya, sanin hakan yasa ya yi shiru bai ce da Michael komai ba, amma ya kudiri niyar azabtar da Musharraf ta kowani hanya, sai ya bashi wahalar da sai ya gwammaci mutuwa, dan shi baya son ganin wani a cikin gidansu, ga shi kuma Musharraf ya sanya hanun zama da su na tsawon shekaru huɗu, sanan babban abin haushi shine James da Michael suna son shi, idan kuma suna son shi tofa shima Lion zai so shi. (Toh fa Tga a hakan ma bai san Musharraf Musulmi bane, idan ya sani kuma sai yaya?🤔) Riƙo hannun Musharraf Michael ya yi suka koma saman sofar da yake zaune, suka zauna, cike da nuna kulawa ya ce "Uncle ɗin James ka san yadda ake buga game? Ka iya?" Gyaɗa masa kai Musharraf ya yi yana faɗin "E na iya sosai dan muna bugawa a gida" A zahirin gaskiya Musharraf bai iya buga Game ba kawai saboda ya lura da cewa Michael yana son su buga tare ne yasa ya ce ya iya, dan ya sanya Michael farinciki. Miƙa masa part ɗaya Michael ya yi yana faɗin "To karɓa mu buga, amma dama kuna da gida ne?" Nan ma gyaɗa masa kai Musharraf ya yi yana faɗin "E muna da shi" kara musu power game ɗin Michael ya yi sannan ya ce "Kuna da gida kuma kazo zaka zauna a nan? Ko da yake ra'ayin kane, yanzu dai nine mai mutane masu bakin kaya kai kuma blue za mu ga waye zai yi winning" to kawai Musharraf ya ce masa sannan suka fara buga game ɗin. Tun daga farkon farawar su Michael ya fara tikar dariya, dan ba abin da Musharraf ya iya. Zuba musu ido daddy ya yi yana kallonsu da mamaki, shi kuwa Tga ji yake kamar ya shake Musharraf ya kashe shi, John kuwa ɗan ba ruwana, ko a jikin sa, shi ko kashe kansu za su yi ma can ta matse musu. LION Zaune yake saman bed nasa, ya zubawa system dake gabansa ido yana bincike sosai a kan James, dan yanzu ya kara tsananta binciken nasa, dan ya samo wani information akan James ya bar kasar Spain last week ta jirgin ruwa ya nufi cikin London. Makeken Tv dake manne a bango cikin bedroom ɗin nasa ne ta fara ɗauko masa hayaniyar su Tga a palo lokacin da Tga ke cewa Musharraf ya bar palon, shiru ya yi na ɗan lokacin kafin ya dakata da aikin da yake y, sannan ya kashe system ɗin dan ya samu abin da yake nema, juyowa ya yi ya zubawa Tv ido. Wani sanyi ya ji har cikin ransa lokacin da yaga yadda Michael ke dariya saboda Musharraf, tun da suka taso suka girma suka yi wayo james ne kawai mai ɗan murmushi a cikin su, kwata-kwata Michael bai taɓa dariya ba, shi kam Lion dama ai ba'a magana kowa yasan magana ma ba wani yin ta yake yi ba bare wani abu wai murmushi. Sosai ya ji daɗi, yau Musharraf ya saka Tiger dariya, zubawa Michael wayan nan dara-daran blue eyes ɗin nasa kawai ya yi yana kallon su, shi kuma Michael sai tikar dariya yake yi saboda yana winning na Musharraf. Da zarar ya ci kwallo ɗaya sai ya kwashe da dariya yana faɗin "Uncle ɗin James na fika iya wa" Allah sarki Michael ɗan ba ruwa na, kowa nashi ne matikar Triplets nasa na son mutum, ba shi da wata matsala. Ba Lion ne kaɗai ya yi farincikin ganin dariyar Michael ba, har da daddy da John, hakan yasa suka matso dan su karawa abin armashi saboda kada Michael ya dai na dariya, dan ya yi kyau sosai, shi kuma Tga bakin ciki ne yasa ya miƙe ya bar palon. Da zarar Michael ya ci kwallo ɗaya sai John da daddy su tafa hannu suna faɗin "Tiger ya yi winning" hakan ba karamin daɗi yake sanya Michael ya ji ba, sai kara bada himma yake yi dan ya yi ta cinye Musharraf, shi kan shi Musharraf ya ji daɗin yadda Michael yake farinciki, ko dan saboda halakcin da James ya masa ya zama dole ya rinƙa sanya Michael farinciki. Da wasa ta yi wasa Michael ya ga ya ci har kwallo 10 Musharraf bai ci ko ɗaya ba, har da juyowa ya yi ya mannawa Musharraf kiss a kumatu yana faɗin "Uncle ɗin James kullun da kai zan rinƙa buga game saboda in rinƙa yin winning ɗin ka" wani farinciki Musharraf ya ji, sai dariya suke gaba dayan su palon, shi kuma Lion ya zubawa Tv ido yana kallon Michael. (Ni kuma haɗa kaya na nayi na bar gidan sai mun haɗe da ku gobe idan mai dukka ya kai mu) 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode 25-26🌹 💖RIMSHA💖 Yau ta kama ranar Laraba, a yau a ke cin kasuwar Eyankorin market, tun safe Kausar ta takura musu a kan su shirya su je kasuwa, da farko Rimsha ta ki yarda, sai da iya ta ce mata "Rimsha ki shirya ku je, dan ki kalli kasuwar mu, kin dai ga baban Kausar ranar litinin zai dawo, kuma yana dawowa zan karɓa mu ku kuɗin mota ku koma gida, to ki je ki ga yanda kasuwar mu yake" to kawai Rimsha ta amsa da shi, sannan suka yi wanka suka shirya. Sai wani murna Kausar ta ke yi kamar ba lafiya ba, Rimsha dai kullun doguwar riga take sanyawa, dan bata son fita da kananan kayan nan na Kausar, ga shi Kausar bata da Hijabi babba, sai yan kanana zuwa kirji, ita kuma bata son hakan. Haka ita ma Ayla doguwar riga ta sanya, ita kuma Kausar riga da skit. Jerawa suka yi suka fito daga gidan, Rimsha da Ayla sun sanya hijabi, ita kuma Kausar ta sanya hula kawai ta rufe gashin kanta. Duk in da suka wuce sai an kalli Rimsha an sake, masu gajen hakuri har magana suke yi mata, amma bata kula kowa, ba wanda ta tanka a cikinsu. Daidai za su shiga kasuwa Rimsha ta hango wata yar matashiyar budurwa ta yi wani irin banzan dressing abin ba'a magana, ba kyan gani, zuba mata ido Rimsha ta yi, har kan bakin nononta ana iya gani, saboda bata sanya breziya ba, ga shi rigar ya matseta sosai da sosai, wandon kuma ya fito mata da zanen shatin gabanta gaba ɗaya, abin ma kunya ya bawa Rimsha, cikin sauri ta sanya hannunta a kirjinta, dan ta ji ko akwai in da ya bayyana a waje. Rimsha akwai tattalin kirgan dangin nan nata, bata son su sha iska ko kaɗan, da zarar ta ji wuyar rigarta ya zamo, a sukwane ta ke yin maza ta janye ta mai da, akwai ranar da ta watsawa Iya miya mai zafi a kan hakan, suna cikin yin girki a kitchen, Iya na zaune a gefen murhun tana tsinka ganyen ugun, ita kuma Rimsha tana juya kayan miyar dake kanwuta yana soyuwa, ta ɗebo kayan biyar a ludayi sai ta fasa yake yi, tana son gane ya soyune ko bai soyu ba, dan ba wani kwarewa ta yi da aikin ba, hakan yasa take bin abin dalla dalla. Tana riƙe da miyar cikin ludayi sai tafasa yake, kasan cewar tana duke hakan yasa wuyar rigarta ya ɗan zazzago, a sukwane ta yi wurgi da ludayin ta kama wuyar rigar tata, bata ma san a fuskar iya ta wurga ludayin ba, har sai da ta ji ihun Iya hakan yasa ta farga ta fara bata hakuri. Kasan cewar Iya ta san abin dake faruwa, tasan halin Rimsha, ita da wannan kirgan dangin tata, sai bata damu ba. "Rimsha me ki ke kallo? Mu tafi mana, ga can Kausar ta tafi ta barmu" Cewar Ayla. Ajiyar zuciya Rimsha ta sauƙe tana faɗin "Ga abin da nake kallo can Ayla, kina ganinta kamar tsirara, ai wannan dama cire kayar kawai ta yi, ta tafi a haka sai a san ta cika tantiriyar yar iska". Yar dariya Ayla ta yi, sannan ta jawo hannunta tana faɗin "Ke dai ba ruwan ki, wuce mu tafi, idan kuma duka kike son sha tom zaki samu, ke kowa ne sai kin masa wa'azi, to wlh ni a yadda na ji labari, yarabawa da kike gani ba kananan masu ilimin addini ba ne, sune fa suka kawo saka nikaf a Nigeria, dan haka ba ruwan ki, komai ki kalle shi da ido, idan ya miki munin kallo to ki rufe ido, alshekiya, dan ke ba al Sheikh za'a ce ba" Shiru Rismha ta yi bata sake magana ba har suka shige cikin kasuwa. Sai dai kuma menen? ko da suka duba ba su ga Kausar ba, tsuru-tsuru suka yi da ido sun rasa ina za su nufa. Sai haɗa zufa suke yi kasan cewar sun tsaya a rana, sai yi musu magana jama'a suke yi a kan su baro rana su dawo inuwa, amma ina basan jin me jama'a ke faɗe, saboda ba wani iya yarabanci sosai suka yi ba. Sun jima tsaye a wajen, dan sun fi awa guda, sun ga ji bayin Allah, suna kuma tsoron komawa gida ba tare da Kausar ba, ita kuwa Kausar da gangan ta shige wani masallaci kusa da wajen, ta laɓe, tana leƙo su ta window, tana ganin yadda suke haɗa zufa a wannan uban ranar, kuma tasan ba za su koma gida su barta bane shiyasa ta yi mu su hakan, kuma dama ta kudiri niyar basu wahala har sai sun gwammaci dama basu zo gidan su ba. Bayin Allah sai magana jama'a suke musu a kan suzo su zauna, idan ma wata suke jira, ga wajen zama a inuwa, amma saboda basa jin yaren sosai sun ki kula kowa, har jama'a suka ga ji suka kyale su, kuma Ayla daman ta san haka zata faru, dan tasan koda ma da English jama'a suka yi musu magana, mawuyacin abu ne Rimsha ta yarda ta shiga cikin shagon mutun, ko kuma runfarsa ta zauna, ba zata taba yarda ba kome zai faru, dan Rimsha tana kula da jikinta da mutuncinta fiye da tunanin mai tunani, kuma bata son shiga harkar kowa, haka zalika bata son rainin hankali da wulakanci, shi ya sa bata kula kowa. Sai wajen awa ɗaya da rabi, sai da taga sun kusa zubewa kasa sannan ta fito, tana dariya, ba su ce mata komai ba, hakuri ta ba su, ta ce musu ai tana can wata kawar ta ce ta tsayar da ita, binta da ido kawai suka yi, ba su ce ko uppan ba. Wucewa gaba ta yi tana faɗin "Muje wajen takardun koyar girki, Rimsha ke ki gani, dan nasan kece mai son iya girki. Da farko Rimsha ta ce bazata sake zuwa ko ina ba, idan ba gida ba, amma da ta ji takardar koyar girki sai ta daure kamar zata faɗi ta bi bayan Kausar. Wajen wani shagon sai da takardun koyar girki suka je, sosai Rimsha ta ji daɗi, ta kuma yi sa'a takardar ba tsada sosai 200 Naira ne ko wani guda ɗaya, wananna ragowar 500 ɗin wadda ya rage musu Shikenan, ta ɗauko ta miƙa masa ta ce Abata takardu guda biyu, kala daban-daban, karɓa ya yi, ya ce su zaba. Masu kyau kala biyu Rimsha ta zaɓa sannan ya basu canjin Naira 100, suka wuce zuwa gida, sai neman su da magana Kausar take yi, idan sunki kulata, sai ta fara yi musu habaici, suna jin ta, kuma sun san da su take yi, amma basu nuna wani damuwa ba. Bayan sun koma gida, bai fi da minti 40 ba Kausar ta sake sako su a gaba a kan lallai sai sun ta shi sun rakar wani gida. Kamar za su yi kuka haka suka hakura suka tashi, dama ita Rimsha bata cire hijabin jikinta ba, suna dawowa ta zauna ta fara karanta takardar girki abinta. Kausar ta riga su fita, sannan suka bi bayanta. Sai tafiya suke yi, Kausar na wani babbuɗe jiki kamar wata niga. Wani gida mai ƙaramin gate ta shiga da su, su dai duk in da ta yi nan suke yi. Tun da suka shiga gidan Kausar ta fara baya baya, basu ankara ba suka ji ihun wasu mahaukatan karnuka, juyawar da za su yi dan su yi wa Kausar magana, sai su ka ga ba Kausar ta ware, kafin su yi wani yunkuri wayan nan mayun karnuka sun fito daga cikin wani lungu a cikin gidan. A guje suma suka juya, Rismha ta fi Ayla iya gudu. Suna fita gidan karnukan suka dakata daga cikin gida, su kuma saboda sun tsorata sai gani suke yi kamar karnukan suna binsu, hakan yasa suka rinƙa tikar gudu, Ayla ta faɗi, ta buga bakin ta saman wani dutse, sai jini ya fara zuba, amma haka ta miƙe dan a tunaninta, karnukan suna binta. Ko da suka koma gida Kausar bata Nan. A palo suka sami iya, tana ganin sun shigo a guje ta miƙe tsaye tana faɗin Lafiya Rimsha me yasa ku gudu haka. Ka sa magana suka yi, suka zube gwiwowinsu a kasa, suna hawaye, ga Ayla baki ya kunbura sai jini yake zubarwa. Ganin Jinin yasa Iya ta kariso wajen su, a ruɗe ta rungumesu tana faɗin "Ina kuka je? Me ya same ki Ayla" har lokacin ba su iya buɗe baki sun yi magana ba, sai haki suke yi suna mai da numfashi. Miƙewa iya ta yi taje ta ɗauko musu ruwa mai sanyi roba ɗaya, ta dawo ta miƙa musu, har suna rige-rigen wajen sanya hannu su karɓa. Ganin Ayla tafi shan wahala ya sa Rimsha ta hakura Ayla ta fara shan ruwan, sai dai bata kai ga gama sha ba, gaba ɗaya ruwan ya ɓaci da jini, haka Rimsha ta hakura da ruwan sanyin ta sha na rijiya, dama ruwan guda ɗaya ya rage a fridge ɗin, Iya bata ji daɗin hakan ba, ita ma Ayla bata ji daɗi ba. Sai da suka huta, sannan iya ta ɗan gasawa Ayla bakinta da ruwan zafi, ya kumbura suntum, Allah sarki sai fuskar tata ya koma kamar ruɓaɓen alale. Bayan Iya ta gama gasa mata bakin ne teka tambayar ina suka je, Rismha ce ta bata labarin sun je wani gida ne, kare ya biyo su, ta ɓoye mata cewa a kan Kausar ce ta kai su ta gudo ta baro su. Sosai Iya ta musu sannu, sannan ta gaya musu kada su sake zuwa gidan, domin gidan wani pastor ne, kuma kabilar Ebo ne, sannan ko da ya ɗaure karnukansa ma, kada su sake zuwa dan ɗan iska ne yana lalata mata. Sosai suka ji tsoro tare da yiwa Iya alkawarin ba zasu sake zuwa ba. "Ina Kausar?" Iya ce ta tambaye su tana ƙoƙarin miƙewa. Cikin sauri suka fara kallon juna, Ayla kam bata iya yin magana sosai saboda bakin nata ya kunbura sosai. "Iya ba mu ganta ba" Rimsha ta bata amsa, Iya na ƙoƙarin shiga Kitchen ta ce "Wannan yarinya, wata kila tana gidan su Waliya ce, to shikenan ni bari na ɗaura mana girki" cikin sauri Rimsha ta miƙe ta bi bayan Iya zuwa kitchen dan taya ta Aiki. Ayla na zaune a wajen har Kausar ta dawo, tana shigowa cikin palon ko sallama babu, idon ta ya sauƙa a kan Ayla, wani mahaukacin dariya ta kwanshe da shi tana faɗin "Ayla me a bakin ki haka kamar an hura balo-balo" ta kai karshen maganar tare da sake kwashewa da dariyar shakiyanci, har da rike ciki. Binta da ido kawai Ayla ta yi tana tunanin yadda yan uwanta maza ke kokarin lalata musu rayuwa, ita shine ma babban abin da ya fi ɗaga mata hankali, shine ma abin da ya fi jefa ta cikin tashin hankali, duk abin da Kausar zata yi musu, mai sauƙi ne a kan wadda Jami'u ke kokarin yi musu. Kausar sai da ta yi dariyar ta mai isar ta sannan ta wuce zuwa cikin dakinta, a ranta tana faɗin "Allah yasa ita kuma Rimsha karyewa ta yi" sai dai ta manta cewa, ita Rimsha duk rintsi duk wuya bata manta askar, haka duk rintsi duk yuwa bata fita gida ba tare da ta yi addu'a ba, dan haka duk in da zata je tana karkashin kulawar Mala'ikun Allah ta'ala. After some hours💖 Iya da Rimsha sun kammala girki, yau sun girka, semo da miyar ɗanyen kuɓewa, yanzu Rimsha ta kware a iya tuka tuwon semo, kuma yanzu ta iya girki kusan kala bakwai kenan. Da yarabanci Iya ta ce mata ta fito musu da abincin Palo, yanzu tana gane yaren duk da ba sosai ba, sama sama haka take ganewa, idan aka yi mai ɗan tsawo, kamar yadda ɗazun a kasuwa, jama'a suka rinƙa ce musu su fita a rana suzo su zauna a inuwa, ta dai ji suzo su zauna, amma bata gane su fita a rana ba domin bata san sunan rana da yaren ba, hakan yasa ta yi banza da su, kuma dama ko da ta ji me suka ce ma, ba zata taɓa shiga cikin shagon su ko rumfarsu ta zauna ba. Bayan ta kawo abincin palo ne ta koma ɗaki ta cire kayan cikin ta, ta ɗaura towel ɗin Kausar ta wuce toilet dan yin wanka. Lokacin da ta yi wanka ta fito Kausar na zaune a ɗakin, sannu ta ce mata sannan ta wuce wajen drawer kayan ta, kamar ba Kausar a cikin ɗakin haka ta yi banza da ita bata amsa sannun ba. Dogon riga Rimsha ta ɗauko, tana kokarin sakawa a jikinta, Kausar ta yi saurin cewa "A'a Meesha kayan nan nake son sakawa yau" cikin sauri Rimsha ta juyo tana kallonta, kawar da kai Kausar ta yi kamar ba ita ba. Mamaki Rimsha ta ke yi, domin farkon zuwansu ko da Kausar ta yi niyar saka kaya, idan Rimsha ta ɗauki kayan, hakura Kausar ta ke yi, amma yau shine zata ce kayan take son sakawa lallai. Mayar mata da kayar Rimsha ta yi, ta ɗauko wani zata saka, nan ma Kausar ta ce "Kai Rimsha ki nayar da wannan saboda bana son a saka shi yau, kinga last week kin saka, kuma idan kika cika saka kaya mutuwa yake yi" wasu zafafan hawaye Rimsha ta ji sun cika mata ido. Haka ta hakura ta mayar da kayan, sau huɗu tana ɗauko kaya Kausar tana cewa ba zata saka ba, daga karshe ma cewa ta yi "Ni fa Rimsha jikin ki na kashe min kaya, da alama ke renon miyar kuka da tuwon dawa ce, idan ba haka ba, da kin saka kaya sai ya koɗe kamar ba lafiya ba, to ni gaskiya na ga ji, ba zan iya ba" Hawayen da Rimsha ke kokarin ɓoyewa ne suka zubo mata, wani na bin wani, dogon tsaki Kausar ta ja, tare da miƙe wa ta nufi waje tana habaici "An zo an zauna mana a gida, a ci a sha a saka sutura amma sai a laɓe a cikin ɗaki ana zagin yan gida, kai butulu kam bai yi ba, a canza hali ko za'a ji daɗin rayuwa". Ta kai karshen maganar tare da ficewa daga cikin ɗakin. Zubewa kasa a wajen Rimsha ta yi tare da dafe kanta tana kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Iya na falo tana ta jiran ta, ganin ta jima bata fito bane yasa ta ce "Kausar ki kira Rimsha tazo kuci abinci". Toro baki ta yi tare da miƙe wa ta koma cikin ɗakin. Rimsha tana duke a kasa kan gwiwowinta tana shan kukan ta, a haka Kausar ta iskota, wani daɗi ta ji ta saka Rimsha kuka, ta fara kuntata musu. Ta ɗauki yan mintoci tana kallon Rimsha kafin ta ce "Ki ta shi ki ɗauki wando da riga ki saka ba dan halinki ba, sai dan na lura kina son ɓoye abin, baki so a gani, amma daga yau ni zan rinƙa baki kayan da zaki saka" ta kai karshen maganar tare da bushewa da dariya, cikin sauri ta sanya hannu ta toshe bakinta, kada Iya ta jiyo dariyar tata. Miƙewa Rismha ta yi, tazo ta raɓa gefenta ta wuce tana goge hawaye. "Kizo ki saka kayan mana, ko haka zaki fita?" Banza da ita Rimsha ta yi, bata kula ta ba (Ni ko nace baki san jinin Nawazudden da bala'i zuciya bane, zuciya da izza a cikin jinin su yake kawai dan dai Rimsha tun tana karama mum ɗin ta ta koya mata hakuri ne, da Jehan ne ai baki isa ba, ke da gidan ku Jehan zata mai daki baiwa, jinjina Jehan Nawazudden yau ga ranarki) Tsohon kayanta da ta cire suka mai da tsumma shi ta ɗauka ta sanya a jikinta, ta fito palo. "Subhanallah Rimsha yau kuma wannan dattin kika saka a jikin ki, ke da kike da tsabta baki son datti ko kaɗan?". Cewar Iya, kakalo murmushi Rimsha ta yi tare da zama kusa da Ayla tana faɗin "E iya yau ina son tuna gida ne shiyasa" "To na ji, amma me ya saki kuka?" Cikin sauri ta ce "Ba komai Iya ni ban yi kuka ba" da yake iya bata son matsa musu sosai, ta san halin su yanzu kila akan gida ta yi kuka, sai ta kyaleta, tare da miƙa musu abincin su. Karɓa suka yi suka faraci kenan Kausar ta fito tana wakar habaice habaicen ta. Cike da ɓacin rai Rimsha ta cire hannunta daga cikin abincin, ta miƙe ta nufi Kitchen ta wanko hannun tata, sannan ta dawo ta zauna. "Rimsha lafiya? Me yake damun kine?" Cewar Iya, ita dai Ayla ta san matsalar dan haka sai ta yi shiru, kuma da yake ita bata kai Rimsha zuciya ba, sai ta ci gaba da cin abincin ta. "Iya ba wani abin da ke damuna, kawai dai na ƙoshi da abincin ne" Wani sanyi Kausar ta ji a ranta, ta jawo abincin Rimsha tana faɗin "To tun da ta ƙoshi ni bari na haɗa". Tsawa Iya ta daka mata a kan ta ajiye abincin, ba musu ta ajiye tana turo baki, a zuciyarta tana tunanin ta yadda zata cusawa iya tsanar su Rimsha. Ita kuma Iya miƙewa ta yi, ta dawo kusa da Rimsha ta zauna ta hau lallashin ta, dan ta lura Rimsha tana da bala'i zuciya, ga zurfin ciki, ko zaka kwana kana tambayarta meke damunta, idan ba ta yi niyya ba bazata faɗa ba, sai dai ka gaji ka yi shiru. Da kyar ta iya shawo kan Rismha ta hakura, hakan ma sai da ta haɗa ta da Allah da annabi, sanan ta yarda. Sai godiya Ayla take yi ga Allah daya sanya Rimsha ta hakura, dan tasan halin ta, idan ta yi fushi da abinci, to ko kashe ta yinwa zai yi, ba zata ci wannan abincin ba, a hakan ma tana duba abin da annabi ya ce na latatba kada ku yi fushi, ba dan haka ba, Rimsha da ta jima da hallaka kanta da zuciya. Iya tana zaune tana kallonsu har sai da Rismha ta ci abincin nan tas, sannan ta ce da Kausar ta ɗaukowa Rismha kaya, Rimsha na kokarin cewa bata so, Iya ta yi sauri ɗaga mata hannu tana faɗin "In dai kika ce baki so, to baki ɗauke ni a matsayin uwa ba kenan" shiru Rimsha ta yi bata sake yin magana ba. Ita kuma Kausar ta miƙe ta nufi ɗakin nata tana turo baki tana faɗin "Ke ma Iya da son kalen dangi, yaushe kika taɓa ganin wani daban ya ɗauki wata a matsayin uwa, tab to idan ba ki sani ba ma, har zagin ki ake yi" "Ni dai kaya na ce ki ɗauko mini ba surutu ba". Wucewa ta yi sai cika take tana batsewa, ita a dole an bata mata rai. Kasan cewar tasan Rimsha bata son kananan kaya dan mugunta sai ta ɗauko mata, Rimsha kamar zata yi kuka ganin kayan da a ka ɗauko mata, ga shi kuma bata son yiwa Iya gardama ko dan saboda alkhari da ta musu. Jinin Nawazudden basa manta Alkhari komai kankantarsa, haka suke, haka iyayen su suka koya musu. Iya da kan ta ta sanya mata wandon. Sai bayan ta sanya mata wandon ne tazo zata zuke zip ɗin rigar, a zafafe Rimsha ta damki wuyar rigar, kada Iya ta cire mata kaya a gaban su Kausar, ga shi ba wani vest ne ta sanya a ciki ba. Abinma dariya ya bawa Ayla da Iya, sai murmushi suke yi. "Rimsha dukkan mu fa mata ne kuma yan uwanki ne, me abin ɓoye ɓoye?". Cewar iya, girgiza kai Rimsha ta yi tana faɗin "A'a Iya mum ɗina ta faɗa mini idan yara suna kanana kana cire musu kayansu a gaban juna, hakan yana sanyawa yarana sha'awar lesbian, idan kuma mazane luɗu, haka zalika idan yan matan suna cire kaya a gaban juna shima yana sanya musu sha'awar lesbian, kuskure ne ka cire kayan ka a gaban koma waye, ko mahaifiyar ka, idan ba wata lalura ba kada ka cire kaya a gabanta, kuma ko a addinance ma yin hakan haramun ne, ganin tsiraicin ɗan uwan ka Allah ya haramta, ai ba'a banza Ubangiji ya haramta ba, saboda tsiraici yana sanya sha'awa in ma mace ko namiji, to yanzu an mai da abin kamar wasa, sai kaga yan mata da girmansu suna wanka tare su biyu a toilet ɗaya, sheɗan kuma yana daga gefe yana kallonsu, kuma hakan ya samo asaline daga laifin uwa, ita take cire musu kaya a idon juna tun suna yara, kuma idan zata yi musu wanka tana kai su cikin banɗa ki tare ta yiwa ɗaya wanka ɗayar na tsaye tana kallonta, bata damuwa saboda za ta yi tunanin ai dukkan su mata ne, ko kuma dukkansu maza ne, bata san babban kuskure take yi ba, a kwai wani hadisi da na karanta, in da annabi (SAW) yake tsawatar wa da nana Faɗima a kan yiwa Al Hassan da Al Hussaini wanka a tare, so cire tsiraici koma a gaban waye kuskure ne, dan yana sanya sha'awa ko ba ka yi niyar yin abu ba, shaiɗan zai buga maka ganga ka yi ba tare da ka sani ba, kuma Mum ta ce wani karin kuskuren ma da iyaye suke yi, sai su bar ƴara mata da maza suna kallon irin Indian Film ɗin nan, ana kiss ana runguma dukka a gaban su, kuma suna ganin mace da namiji keyin hakan, ai dole suma su ɗauki hanya". Zuba mata ido kawai suka yi har ta kammala sannan Iya ta ce "Kina da gaskiya Rimsha, mu iyaye bamu damuwa ba, muna yin hakan, mu na ɗaukan kamar yara ne shiyasa muke haɗa su a toilet mu yi musu wanka, kuma idan misali a ce yara uku ne, sai ki ga mun yi wa biyu wanka mun baro su a ɗaki muna yiwa ɗayan wanka, kawai dan son jiki, muna bin sauki muna ɓata yaranmu da kanmu, wani lokaci kuma zaki gani idan kika gama yiwa ɗayar na karshen wanka kika fito zaki samu su biyun nan ɗaya na wasa da gaban ɗaya, idan maza kenan, a tunanin mu yara ne, so kawai ya ɗauki abin kamar abin wasa ne, shiyasa bamu wani mai da hankali a kan hakan, amma tabbas yanzu da kuka faɗa na gane yin hakan babban kuskure ne, shike ruguza al'umma, sai kaga ka dage ka bawa yar ka tarbiya, sai ka rasa ta ina ka samu tangarɗa idan ta lalace, ashe baka sani ba tun farko kake lalata farkon ginin, wani lokaci ma ƴaƴan namu mace ce da na miji ne, amma haka muke haɗe su muna musu wanka a tare, saboda shegen son jiki, ba zamu hakura mu fara yi wa daya, mu gama mu shirya shi tsab sai mu zo nu yiwa ɗayar ba, wani sain kuma sai ki ga uwa tana cire kayanta a gaban yaro, a tunaninta yaro ne bai san komai ba, duk wayan nan kuskure ne, ko kasa ɗan ka matashi ya yi wa kanwarsa mace wanka, Allah dai yasa mu ji mu gyara, amma Rimsha kin bani mamaki waye ya koya miki wannan dukka abin" Yar murmushi ta yi har sai da dimple nata ya lotsa, "Mum ɗina ne ta koya mini, kuma ai na karanta su Fiqhu da sauransu, na san abubuwa da dama, kuma mum tana karamin haske har shima dad, sannan ni ina da yawan tambaya idan na ga abu, kalmar lesbian ma ni a wani kittafi na karanta shine naji kalmar ta mini wani irin, sai na je na tambayi mum, shine tamin bayani dalla dalla, har na gane nima nake yi wa mutane" Leƙo fuskar ta Iya ta yi tana faɗin "Eyee da mum tana gaya miki ya kika ji sarkin kunya" rufe ido tayi da hannunta tana dariya kasa kasa. "Kai gaskiya ba zan yarda ba, Rimsha dole mu yi sauri mu miki aure dan ke ai kin gama sanin komai". Cewar Iya, cikin sauri Rimsha ta ce "Kai Aure kuma Iya?" Gyaɗa mata kai iya ta yi tana faɗin "Sosai aure kuwa, ai kin gama sanin komai ne, dole mu kai ki daga ciki" wucewa Rimsha ta yi ta shiga cikin ɗakin Kausar hannun ta riƙe da rigar tata. Bata son tsayawa magana da Iya, dan kada Iya ta bawa zancen auren karfi, dan ita bata da wani buri da ya wuce ta je ta ga mum ɗin ta da Jehan ɗin ta, kuma ita bata son aure. (Tofa Rimshan mu ma bata son aure, a'a lallai banga laifin Jehan ba) Tana shiga ɗaki ta sanya rigar sannan ta yi zaman ta saman gadon Kausar tana tunanin GAR, ba abin da yake mata yawo a ƙwaƙwalwar ta fa ce yadda ya matso zai yi kissing nata, a hankali ta kai hannunta saman lallausan laɓaɓɓan ta, mai kama da fure, ta shafo lips ɗin nata tana murmushi ita kaɗai, daga bisani kuma sai ta maida hannun tata saman kirjinta tana shafa sunan Lion, lokaci guda wani tunani ya faɗo mata, idan ta koma gida Mum taga wannan zane fa, ya zata yi, ta sani ko Jehan ce ta ga wannan zane ba zata taɓa barinta ta zauna lafita ba bare kuma mum. Miƙewa tsaye ta yi a zabure, tana tunani tare da danasanin me ya kaita ta zana sunan wanda ba Musulmi ba a girjinta, bayan ba musulmi bama bai san da zaman ta a duniya ba, sunan Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya kamata ta rubuta ko sunan dad da mum ɗin ta, wai shin me ya shiga kanta ne, har ta aikata hakan. Sai tunani take yi, tunanin da ba shi da amfani, domin suna dai ya riga da ya zanu ba gogewa, ba ta tashi sanin kuskure ta aikata ba, sai yau da ta tuna da littattafan musulunci. (Lalai Rimsha kin shahara, to ni dai na kwashe kaya na, na wuce gidan Abba) 💖💖GIDAN ABBA💖💖 Yau tun safe su Akil suka wuce kano shi da Imran da Irfan, kamar yadda suka yi sammakon safe zuwa garin Kano, haka ita ma Hajiya Umaiya ta dakawa Umaisha sammako da uban kayan wanki. Umaisha ta sha mamaki, ta ce ga engine wanki za ta yi amfani da shi, amma Ammie ta hana ta, ta ce ai tasan da washing machine ɗin, ta ce ta mata wanki da hannunta, har ga Allah Umaisha bata iya wanki ba, bata taɓa yin wanki ba, ko kananan kayan ta irin su pant breziya ba ita take wanke wa ba, mai aiki ke wanke mata, haka suka taso, ba abin da suka iya, kayan sawan su akwai mai wanke musu namiji ne. Tun karfe shida na safe take wankin uban kayan Ammie, tana yi tana kuka har karfe 1 na rana, abin haushin ma shine jijjiƙa kayan kawai ta yi, ta kara musu datti, ba abin da ya fita, hakan kuma ba ƙaramin haushi ya bawa Ammie ba, cikin zafin nama ta hauta da faɗa da masifa, ta ko'ina ɗura mata zagi ta ke yi ba sassauci, sai da tayi zagin mai isarta, sannan ta sa ta a kan ta sake faro wankin daga farko, sai ta wanke kayan sun fita fes idan tana son zaman lafiya, ga shi bala'i yinwa take ji, kuma Akila ta kai mata takeaway ɗaya ɗakinsu kafin ta wuce school, amma Ammie ta ki barinta ta je ta ci abinci, ga kukan yinwa ga na wahala, ta yi har ta ga ji. A wannan hali su Aafia suka tarar da ita, Aafia tare da Rufee da Anisa ne suka zo, Irfan ne ya sa driver ya kawo su, tun kafin su wuce kano, dan Akil ya gaya masa yana son Aafia ta je ta taya Umaisha kwana tun da kwana za su yi a Kano, kuma daman Umaisha ta matsa masa a kan ya ɗauko mata Aafia. Sai dai da driver ya ɗauko ta ne, sai ta ce ya biya su je su ɗauki Rufee da Anisa, idan yamma ya yi sai ya mayar da Rufee da Anisa gida, Irfan ya hana Aafia tuki yanzu duk in da zata je kai ta a ke yi a ɗauko ta. Ganin Umaisha na wanki a tsakar gida, da ruwan famfo duk ta rame, hakan yasa Aafia banko wani uban ashar wadda baki ba zai iya faɗin shi ba. "Kutumar uban can, ke Umaisha wani dakikin bagidajen ya saki wannan ɗan iskan aikin?!!" Kasa magana Umaisha ta yi, ta kuma kasa miƙewa ta je wajen su, sai kara sautin kukan ta da ta yi. Aafia da Anisa har suna rige-rigen karisowa wajen ta, ita kuma Rufee sai bin gidan take da kallo, taga tamɓatsetsen gidan da ya ci uban nasu Aafia a komai da komai, ta saki baki galala kawai tana kallo. (Kai Rufee akwai son duniya) A tare Aafia da Anisa suka ɗago Umaisha, duk ta rame ta ba kyan gani. "Ba kuka zaki yi ba Umaisha, ki faɗa mana waye yake baki wahala haka?" Cewar Anisa. Cikin kuka da kyar ta iya buɗe baki ta ce "Ammie yaya Akil ne, ita ce wlh kullun take azabtar da ni, Aunty Afi dan Allah ki mai dani gida, idan ba haka ba, zan iya mutuwa a nan". Wani sabon ashar ɗin Aafia ta sake wulwulowa, tare da jawo hannun Umaisha suka nufi cikin gida, tana faɗin "Ke mara mutuncin mata ina kike?". Ummi na zaune saman sofa, palonta sai kamshi yake zubawa Umaisha ta gyare ko ina tsab, ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya tana kallon Tv ta bar baiwar ta Umaisha a waje tana tikar aiki. Jin hayaniyar su Aafia ya sa ta juyo tana kallon kofar shigowa, ganin su yasa ta ja tsaki tare da mai da kallonta kan Tv. Gabanta Aafia tazo ta tsaya rike da hannun Umaisha tana faɗin "Ke dai wlh anyi azzaluma muguwa, annamimiya, yanzu uban me Umaisha ta miki ki ke azabtar da ita haka?" Anisa ce ta karɓi zancen da cewa "Baiwa ce ita da zaki saka ta wancan uwar aikin? To wlh muna baki last warning idan kika sake saka ta aiki sai kin yabawa aya zakin ta, ai ba baiwa aka kawo miki ba". Miƙewa Ammie ta yi tare da riƙo wuyar rigar Aafia ta dalla mara maruka masu kyau guda biyu, sannan ta ce "Ke wlh da alama sai na koya miki tarbiya, to shi bappan naku ma me a ido na bare uban ku bare kuma ku? To wlh tun wuri ku fita mini a gida tun ban muku dukan mutuwa ba, banza ye marasa tarbiyya". Sanin su Akil basa nan ya sanya Aafia ta yi kokarin ja da Ammie, sake riƙota Ammie ta yi zata dake ta, daidai lokacin Rufee ta shigo, cikin sauri ta tarewa Aafia tare da riƙo wuyar rigar Ammie tana faɗin "Ke tsohuwar kilaki, ashawo, ki kama kanki wlh, idan ba haka ba zamu nuna miki mun fiki zama tantiran ƴan bariki, yanzu sai mu miki dukan kawo wuƙa a cikin gidan nan, muga uban da zai karɓe ki, muguwa azzaluma, kin tasa karamar yarinya a gaba sai zaluntar ta kike yi, idan kin kai shegiya, ai manyan yan duniya zaki samu irin mu sai mu buga game ɗin, ba karamar yarinya kamar Umaisha ba, wadda kin kusa jika da ita, dan da ga gani ke old woman ce sosai". Idan kaga Rufee yadda take tarewa Aafia faɗa sai ka yi zaton da gaske tsakani da Allah take yi, amma azahirin gaskiya ba haka bane, kawai dan taga Ammie ta mata kama da matar gidan ne hakan yasa ta zage take cin mutuncin Ammie sosai, dan a cewarta gidan ya mata, ta samu wajen zama. (Tof fa, lallai Rufee ai in dai gidan Abba ne, Bismillah zoki zauna, duk wanda ya ci tuwo da gidan Abba wlh miya ya sha, bake yar son duniya ba Bismillah to) Dun wani baki na Ammie yau sai da Rufee ta kashe mata shi, tatas ta mata, har sai da Aafia ta tsorata ta fara ce mata ta yi shiru, tana tsoron kada Ammie ta gaya wa su yayan Akil su ci ubanta. Amma ina Rufee ta ki yin shiru, tsab ta wanke Ammie, wankin babban bargo. Idan kaga yadda yau Ammie ta yi shiru ta nitsu sai ta baka tausayi, gaba da gaban ta, yau ta haɗu da jiga-jigan yan bariki, wayanda suka fita gogewa a fannin iskanci da iya shege, wato Rufee da Anisa, dan Anisa ma ba baya ba wajen baki da iya faɗa, sai dai ita tsakani da Allah take tare da su Aafia, ba da wata manufa ba, kuma ita bata bin maza, cikakkiyar budurwa ce, amma ta iya faɗa. Sai da suka tabbatar sun rufe bakin Ammie sannan suka wuce part ɗin Akil, Umaisha ta musu jagora. Kwafa Ammie ta yi, a ranta tana faɗin "Kun jawo wa yar uwarku bala'in da sai ta gwammaci mutuwa" Toh fa, su Aafia suna tunanin sun kashe wuta, basu san kara hura wutar suka yi ba. (To mu dai koma Washington DC kafin mu dawo wata kila abubuwa sun ɗan gwaru a nan) 💖💖Washington DC💖💖 After some day's👌 A yanzu Tyrone ya samu sauki kuma ya dawo bakin aiki gadan-gadan. Zaune suke a palon kasa, Michael ya tada kai da cinyar Uncle ɗin James wato Musharraf, yanzu Michael ya samu sauki sosai, sai dai ba gaba ɗaya ba, amma an samu cigaba sosai da sosai, yanzu yana iya tantance daidai da ba daidai ba, kuma ya fara koyan karatu da wasu abubuwan, sai dai shagwaɓar nan tasa tana nan. Yanzu ma sai zubawa Uncle ɗin James shagwaɓa ya ke yi, Musharraf na biye masa, a yan kwanakin da suka yi, sun saba sosai, sun shakuda Michael fiye da yadda suka shaku da James, duk da cewa lokacin da James yake nan Musharraf baya iya tafiya, hakan yasa basa wasu wasannin tare, yanzu kuma yana iya tafiya, James baya nan, sai Michael ya maye masa gurbin James ɗin, idan kana son ku yi faɗa da Michael to ka taɓa masa uncle ɗin James ɗin sa, nan fa zai gwada maka shi Triplets ɗin The General of The Army ne, tuni zai ɗauko gun ya saita maka hanya, dan ma dai Lion ya tattare pistol dake cikin ɗakinsa dukka ya canza musu wajen zama saboda Michael, amma gaba ɗaya sojoji da bodyguards dake gidan, har wani girmama Musharraf suke yi, har sara masa suke yi idan zai wuce, kuma duk saboda Michael ɗan lalele. Lion Tga Tyrone, tsaye suke gaban wani makeken desktop computer dake cikin ɗakin binciken su. Tga da Tyrone sanye suke da Army trousers da kuma Army t-shirt, while shi kuma oga Lion yana sanye da irin wandunan nan masu aljihu dayawa a jikinsu, har ta gefen gwiwar su akwai aljihu, da kuma kyawawan ijiyoyi masu kama da igiyar boot, daga ta sama kuma yana sanye da farar t-shirt mara nauyi yar shara-shara, ya saki kyakkyawar gashin kansa, bai ɗaure ba, wannan guntu gashin na gaban goshin nasa yana nan, yar ramar da ya yi tasa idanuwansa sun kara girma. Tsaye suke sun zubawa computer ido, Lion nata faman hargitsa dark black curly hair sa, alamar zuciyar sa na masa zafi, sai cizan red lips nasa yake yi. Sun jima tsaye suna kallon yadda computer ke tariyo musu bayanan da suke bincike a kai. Tga ne ya ce "Amma Lion wai wannan binciken na waye ne haka?" Shiru Lion ya yi na tsawo mintoci. Har su Tga sun cire rai da zai yi magana, sai kuma suka ji sexy voice nasa yana faɗin "James ya yi kuskure, ya jefa kansa a in da mawuyacin abune ya fita, ko kuma ya rayu". A sukwane Tga da Tyrone suka zaro ido suna kallon Lion, a tare kuma suka mai da kallon su kan desktop computer ɗin, dan su kara ganin abin da suke gani shin da gaske ne ko dai gizo idon su ke musu. Sun jima sosai dukkansu a tsaye, sun yi mutuwar tsaye, dan sun kasa yarda da abin, sai wani gwalo idanuwan su suke kara yi ko zasu samu damar ganin akasin result da suke gani a system ɗin, amma ina wannan result da suka gani da farko shine dai a wajen. Ganin haka yasa Tga ya ce "Amma Lion ba last month kasa su Tyrone sun tarwatsa kungiyar *I .D .A. E .S. A* ɗin nan ba?". Dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali, sannan ya fara magana a nutse. "James ya sa na yi bincike a kan su, saboda na samu wasu abubuwa na tambarin kungiyar nasu a ɗakin sa, *I .D .A. E. S .A* sunan kasashen da suke da reshe a can ne, shine suka sanya a matsayin sunan kunguyar su". Cikin sauri Tga ya ce "Wace kasa da wace kasa kenan?" Ɗaukan wani ɗan karamin game Lion ya yi, irin wannan game ɗin da a ke haɗa shi da hannu, fara jujjuya game ɗin ya yi, yana kokarin haɗawa, zuba masa ido suka yi, sun ƙagu su ji amsar da zai bada, ga shi shi kuma idan ka masa magana sai ya ɗauki tsawon lokaci kafin ya amsa ka. Haka suka yi ta dakon jiran amsar shi, har sun fara fidda rai, sai can suka ji zazzakar muryarsa ya fara magana, ya kuma lumshe dara daran idanuwansa. "*I .D. A. E. S. A* Yana nufin I. India D. Dubai S. Spain, sune kasashen da na yi bincike na gano su jiya zuwa yau, so sauran ban san ina bane" cikin sauri Tga ya ce "Amma Lion why not nu duba kasashen da suka fara da wayan nan harufan A.E.A". Nan ma Lion ya jima kafin ya ce mu su "Ba iya sunan kasashe bane a wajen, har da sunan garuruwa, ina kyautata zaton saura ukun nan sunan garuruwa ne, ko kuma sunan wajajen da suke haɗuwa". Shiru Tga ya yi yana tunani ko zai gano wani abin, amma sai dai ba abin da ya iya gane wa, dan bai isa ya haɗa kwakwalwarsa da ta Lion ba, a shirmen sa wai zai gwada tunano sunan garuruwa dake cikin Spain India da kuma Dubai, sai ya ga fa aikin ba ƙaramin aiki ba ne, ba zai yiwu ya iya gane ko gari goma ba, aikin na manya ne, ya jinjina wa Lion da ya iya gane wayan nan ukun ma daga daren jiya zuwa yau, kuma ba'a faɗa masa sunan kasashe bane, kawai saboda ya saba aikinne, sai ya lura da yadda a ka rubuta sunan, bai yi kama da sunan jimillan abu guda ɗaya ba, kuma basu yi kamanceceniya da abu biyu zuwa uku ba, aikin akwai rikita ƙwaƙwalwa, ya za'a yi Lion ya iya gane garuruwan da suka fara da A.E.A a cikin duniyar nan tab, ai garuran da suka fara da haka suna dayawa, taya zai iya ganewa, har ya zaƙulo garin da ya kasance eh shine suke nema, aiki ja. Dukkan su sun ɗauki tsawon lokaci a haka suna kallon computer, ba wanda ya iya yiwa Lion wata magana. Sai can Tga ya ce "Amma Lion ya a kayi ba su saka sunan dabar su na nan ba?" Shiru ya yi na tsawon minti 10 kafin gently ya ce "Already manyan cikinsu mazauna nan ne, kuma nan shine maɓoyarsu, ba zasu taɓa saka sunan maɓoyarsu ba, ina da tabbacin akwai su sosai a nan, ina buƙatar kama James da kai na, ina son isa gare shi tun kafin CIA su rigani". Kara zaro ido waje Tyrone. Tga suka yi a tare, cikin sauri har yana haɗe words Tga ya ce "Lion kana nufin CIA na neman James ne? To me ya musu?" Shiru Lion ya yi bai sake yin magana ba, dan shi ba mai buɗe sirrinsa ga kowa bane, ko da Tga yake uncle ɗin sa kuma na hannun damar sa, baya yarda ya buɗe masa sirrinsa, sai dai idan ya gama bincike ya basu umarnin a kan su tafi aiki kawai. Har zaman nasu ya kare kowa ya watse Lion bai sake cewa komai ba, ba haka Tga ya so ba, yaso jin da wani kungiya da wanne James ya ke yi wa aiki, sai dai ba hali, dan bai isa ya tambayi Lion ba, kuma ko bincike zai yi, ba wani abin da zai gane, dan binciken Lion na daban ne, kwakwalwar ba ɗaya ba. Sai dai fa Tga ya shiga matsanancin tashin hankali fiye da misali, domin zuciyar sa ba zata iya jurar rashin James ba, kuma yasan a wannan hali tabbas Lion ya kama shi, to da kansa zai harbe shi. (BABBAR MAGANA, TOH FA YAU A KE YIN TA) Shima Lion ɗakin sa ya koma ya shige toilet dan ya zubawa kansa ruwan sanyi, ko zai samu sauƙin raɗaɗin da zuciyar sa ke yi masa, har wani jiri yake gani, Bawan Allah tun jiya bai ci komai ba, ba abin da ya saka a cikinsa sai ruwa, ya dukufa bincike yana son gane in da James yake nan da lokacin kalilan. Ni kuma tattara kayana na yi na tafi, sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu, much kauna my fans yan amana!!.🥰 💞💞TRIPLET'S💞💞 🌹🌹Episode 27-28🌹 Shima Lion ɗakin sa ya koma ya shige toilet dan ya zubawa kansa ruwan sanyi, ko zai samu sauƙin raɗaɗin da zuciyar sa ke yi masa, har wani jiri yake gani, Bawan Allah tun jiya bai ci komai ba, ba abin da ya saka a cikinsa sai ruwa, ya dukufa bincike yana son gane in da James yake nan da lokacin kalilan. Shi kuwa Michael yana can yana aikin shagwaɓa, ganin ba mai kula shi sosai a palon sai Musharraf ne, hanan yasa ya ce "John maltina nake son sha" a sukwane John ya ɗago ya kallesa, yau iskancin Michael ta kansa ya biyo, kuma idan Michael ya ce kai yake son ka kawo masa abu, tofa ba wani bodyguard da ta isa ya ɗauko masa, dan ba zai karɓa ba. Haka ba yadda ya iya ya ajiye wayarsa tare da miƙewa tsaye ya nufi wajen tampatsa-tampatsan fridge dake cool room basu. Jim kaɗan ya dawo hannunsa ɗauke da maltina mai sanyi tare da glass cup mai bala'i kyau. Miƙa wa Michael ɗin yazo ya yi, kin karɓa Michael ya yi, ya wani make kafaɗa kamar yaro. Zuba masa ido John ya yi yana jiran ya ji wani iskanci kuma zai masa. Ya jima a tsaye Michael ya ki yin magana, da dai ya ga da gaske Michael ba shi da niyar yin magana, sai ya ce "Please Michael take it now" girgiza kai Michael ya yi yana faɗin "No i can't" zaro ido John ya yi yana faɗin "Why?" "Saboda baka buɗe mini ba" John haushi kamar zai kashe shi, haka ya duƙa a wajen ya ajiye glass cup ɗin a kasa, sannan ya buɗe bakin robar maltinan ya zuba cikin cup ɗin, ya ɗago tare da miƙa masa yana faɗin "Okey ga shi nan to" sake make kafaɗa Michael ya yi, alamar baya so. "Yanzu kuma me matsalar?" John ya tambaya yana kokarin ajiye cup ɗin a kasa, "Who ask you to put it for me inside the cup? Ni ba a cikin cup na ke buƙata ba" mamaki ya hana John magana, dan shi dai yasan gaba ɗaya yan gidan nan ba shan abu da bakin roba suke yi ba, ko ruwa sai bodyguard sun zuba musu a cup suke sha, wato yau da sabon iskanci Michael ya ke ji da shi. John yana duƙe ya kasa miƙe wa, ganin haka yasa Michael ya saka musu kuka, daidai lokacin Tga da Tyrone suka sauƙo daga sama. Har suna rige-rigen wajen haɗa baki, suna faɗin "Who touch our Heartbeat?" Cikin sauri John ya miƙe tare da tattare maltinan ya nufi cikin Kitchen, dan yasan Tga yanzu zai iya yi masa dukan mutuwa a kan Micheal. Shi kuwa Michael ganin Tga yasa ya kara karfin kukan nasa, cikin sauri Tga ya kariso wajen yana tambayar me ya sa me shi. Cikin kukan shagwaɓa ya ce "Uncle Please where is My James? Where is my blood? I missed him, i want to see his face, na ga ji". Jin Michael ya yi zancen James ya sanya daddy juyowa yana faɗin "Michael James yana nan lafiya jiya munyi waya da shi ya cemin soon zai dawo" a sukwane Michael ya miƙe daga jikin Musharraf zuwa jikin daddy yana tambayar daddy a kan da wani number james ya kira shi. Nan daddy ya sanar masa a kan cewa da number wasu ma'aikatan da suka tafi tare ya kira shi. Shi kuwa Tga ya san ba wani James da ya kira daddy Lion ne ya shirya wa daddy hakan, dan ya lura daddy na kokarin kashe kansa, a kan tunanin James shiyasa suka yi masa muryan James a waya, ko raɗaɗin zai ragu masa. Haka daddy da Tga suka rinƙa bawa Michael baki a kan ya hakura James ya kusa dawowa, da kyar Michael ya yarda. Yana yin da Michael ya shiga ya sanya Tga ya kara jin ba zai iya aminta da rashin James ba, ya zamar musu dole su dukufa wajen neman shi, idan ba haka ba, Michael zai kara birkice musu fiye da a baya. After some hours 👌 Misalin karfe biyu na dare, duniya dukka sun yi shiru, Lion shi kaɗai zaune a palo saman table, ga kuma bodyguard suna tsaye a kansa dan zuba masa abinda zai buƙata, wayan nan bodyguard ɗin yadda kasan wayan da suke shan wani abin, kwata-kwata basa jin barci, da zarar lokacin cin abinci ya yi to fa suna wajen table tsaitsaye, suna zuba abinci, haka zali ko kwana za su yi a tsaya za su yi, matukar Lion bai zo ya ci abincin dare ba, ba su isa su je su kwanta ba, domin shine last ɗin cin abinci a gidan, haka suke hakuri su jirashi har sai ya zo ya ci, sannan suke shiga dakunan su, su kwanta, duk kuma ranar da ba zai ci abinci ba, to Michael ne zai zo ya sallame su, su wuce ɗakin su, su kwanta. Suna nan tsaye sai karfe uku na dare sannan Lion ya miƙe ya nufi sama ba tare da ya ci komai ba, domin ya kasa cin abinci, tunanin James ya saka shi a gaba, ya sanya aikin a cikin ransa, kwakwalwar ban da tunani ba abin da yake yi, ya zafafa da yawa, domin yana son isa ga James tun kafin a riga shi, ga kuma tarin wasu aiyuka dake gabansa, ciki har da bincike a kan menene asalin damuwar Michael, me ya hassasa masa ciwon, sai dai ya fi kwallafa rai a kan binciken James. Haka ya wuce part nasa, bakin sa har wani ɗaci yake yi mi shi, saboda wunin yau bai ci komai ba, sai uban yawan yin brush da yake yi tana kara mi shi yinwa. Wanka ya sake yi ya shirya cikin kayan barci, riga da dogon wando, launin sky blue, sai kamshi yake zubawa ya haye saman lallausan katafaren bed nasa. Bawan Allah a maimakon ya yi barci ya huta wa ransa, sai ya jawo system da wayarsa ya fara bincike, duk idanuwansa sun yi jawur alamar barci da yinwa, amma ya hana kan shi saboda James, yana jin raɗaɗi a zuciyarsa wadda ba zai iya barci ba. Yana kewar ɗan uwansa, sune duniyar sa, sune farincikin sa, ba shi da abin da yake gani ya ji daɗi sai su, bai san me yasa har ga Allah baya son daddyn sa ba, kuma yana kokarin sakawa zuciyar sa son daddyn nasu, amma abin yaci tira, dannewa kawai yake yi yake kula da daddy yadda ya kamata domin ya sauƙe nauyin da ya rataya masa a kansa, amma bashi da farincikin da ya fi Triplets, shiyasa baya iya hukunta su, dan da alama sune rauninsa. A zahirin gaskiya Lion ya fi son Tga a kan daddy, yana iyaka bakin kokarinsa ya cusawa kanshi son daddy, amma ya kasa, bai san me dalili ba. (Ni kuwa nace ai Lion shi son abu ba'a cusawa zuciya, ita ke zaɓar abin da zata so) Rashin barcin da bai yi ba, yin hakan kuma ba karamin nasara ya samu ba, domin ya kara faɗaɗa bincikensa, a in da ya gano ba soke number James a kayi ba, sun yi amfani da kimiya ne wajen ɓoye number ta yadda duk wanda zai kira za'a sanar masa an soke number, sai dai ko da ya gane number tana nan, ba zai iya bin diddigin ta ba, saboda tana karkashin tsaro sosai, wadda dole sai ya nitsu ya musu kutse cikin tsaron su kafin ya iya samun damar laluɓo in da location na number take, kuma number bata kasance wa a kunne ko da yaushe. Kamar yadda Bawan Allah nan ya ga rana haka ya ga dare, kun san barci idan baka samun yin shi, har wani rama yake saka ka, to shima haka ne, har wani rama yake yi, domin tun da James ya ɓace yake ta fafutuka, baya wani cin abinci sai ruwa, ga shi ba barci. Misalin karfe 8 na safe, cikin hanzari Tga ya faɗo ɗakin Michael, sai sharara barci Michael yake abin sa, ya yi ɗai ɗai da kafafu ya baje sosai bisa lallausan bed nasa, ya wani rungumo pillow a kirjin sa, ga brown hair sannan duk ya bazu masa a fuskarsa, gwanin birgewa, yana sanye da kayan barci irin na jikin Lion wato riga da wando, sai dai kowa da kalar tasa. Cikin zafin nama Tga ya haye gadon yana faɗin "Hey wake up, saura minti goma Lion ya fito" a razane Michael ya farka jin Lion ya kusa fitowa, zama ya yi tsakiyar gadon yana goge idanuwansa da suke cike da barci, ganin haka ya sanya Tga ɗaukan sa cak suka yi waje. Abin da ya faru shine, tun da Michael ya fara samun sauki Lion yana ba shi horo na musamman, domin ya samu kwari, duk da cewa yana da shi a baya, amma a gaskiya na baya ba nasa bane, kwakwalwar tasa ke saka masa power a kan abu, ita ke sanya shi ya yi abu da karfin da zaka yi tunanin cewa karfin shine, amma ba nashi bane, yanzu da ciwon nasa ya fara warkewa, sauki na samuwa, sai duk wannan zafin nasa ya tafi, ya dawo real shagwaɓaɓɓe, ba shi da karfin komai, hakan yasa Lion ke bashi horo. Saboda aiki da suka sha kan Lion, sai ya wakilta Tga a kan ya rinƙa saka Michael a gaba tun karfe 6 na safe zuwa takwas, ya rinƙa kula da shi yana yin training yadda ya kamata, har sai shi Lion ɗin ya fito, karfe takwas daidai zai rinƙa fitowa, sai ya duba me Michael ɗin ya yi. Rana ta farko da Michael ya fara, kuka ya rinƙa yi ya ce shi ba zai iya ba, gara masa ɗaga wayan nan kananan karafuna da yake yi a baya shi da James, Lion ya ce ba zai yi wuba, ai wancan karon wasa ne, yanzu ne na gaske, dan haka dole ya yi, ya sha kuka ranar, har dare ya kasa tafiya da kafafunsa tsabar shagwaɓa wai ba zai iya takawa da kafafunsa ba, dan ya yi training na rana ɗaya, wunin ranar duk in da zai je Tga ke kai shi, haka da daddare ya zo ya baje lallausan bed ɗin Lion, yana masa kukan shagwaɓa wai kafarsa zafi. Haka Lion ya ajiye aikin da yake yi, ya haɗa masa wani inji mai kama da robot ya rinƙa yi masa tausa. Duk da haka washe gari Lion bai kyale shi ba, sai da ya yi training, sai kuka yake yi, to wannan kukan da yake yi ne ya sanya Tga ba zai iya jurewa ba, sai ya kyale shi yana ta barcin sa, har sai karfe takwas ta kusa, idan sun daidaici Lion ya kusa fitowa, sai Tga yazo ya tashe shi, su je wajen training ɗin, suna yin sa'a sau biyun da suka yi haka dukka Lion baya zuwa wajen yana fitane saboda aikin dake gaban sa, yau shine rana ta uku. Tga na fita da Michael suka samu daddy a palon kasa, sai zarya yake yi, yana jiransu, da yake bakin su ɗaya dukkansu. Kai tsaye wajen gym nasu suka wuce, a cikin gym ɗin akwai wata ɗaki, wadda yan koyo ke farawa daga can. Kasan ɗakin wata iriyar katifar nan ne, wadda idan ka yi tsalle a kan ta zata kara wurgaka sama, kamar balo balo, kananan injuna ne a cikin ɗakin na yan koyon gym, amfanin wannan katifa shine, idan yan koyo sun faɗi kasa, zata tare musu jin ciwo, sai dai katifar tana karkashin wata na'ura wadda ana iya kunnata, idan kuma a ka kunna ta, zata rinƙa juyawa kamar fanka tana ɗaga mutun sama yana dawowa cikinta. Su kuma injunan dake wajen already a dashe suke, an dasa su ne daga kasa kafin a ɗaura wannan katifar, shiyasa ko katifar tana juyawa su ba za su motsa ba, sai dai ita ta yi ta juyowa, dan an musu kofa a jikinta yadda zata juya ba tare da sun hanata ba, kai daga ganin wajen nan kasan tsara shi a kayi, tsari ma na musamman. Saman wani inji mai kama da keke Tga ya ɗaura Michael, saboda sabo da suka yi wajen canja saitin Injin, cikin kankanin lokaci Tga ya canza saitin zuwa tun awa biyu da suka wuce Michael ke amfani da mashin ɗin, shi kuma daddy dan ya karawa karyar tasu armashi har da wani ɗauko bottle water, ya hau sakawa Michael ruwa a faska, kamar zufar gaske. Michael ma yanzu ya maye gurbin James a zama ɗan basaja, har da wani haki, da numfashi sama sama. (Kai jama'a gidan daddy gidan comedy, ba kalar mutanen da ba bu) A wannan hali John ya isko su. "Ina ka tsaya John?" Tga ne ya jefo masa tambaya. Wucewa ya yi kamar abin haɗin baki, ya fara gyarawa Michael kafarsa yana faɗin "Naje word room duba jikin Jay ne, shine ya tsayar da ni, sai kuka yake yi uncle". Guntun tsaki Tga ya ja, kafin ya ce "To angaya masa punishment ɗin Lion wasa ne, ya gode ma, da ya samu Lion yana tsaka da aiki, abubuwa sun sha masa kai, da ai ba a iya jinya zai tsaya ba, wata kila sai kabari, ɗan rainin wayo, lallai ma ya samu punishment mai sauki, tun da yau kwana uku da gama bashi horo har ya samu bakin kuka, ni lokacin da Lion ya bani punishment na wani laifi da na taba yi masa a baya a wajen aiki, hmmm sati biyu ban san in da kaina yake ba, duk tunanina na mutu ashe ina raye, shi ai Jay ya ma yi murna, tun da jinyar kwana uku kawai ya yi har ya samu bakin kuka". Cikin sauri Michael ya ce "Yes Uncle T naga Lion ya mishi da sauki, kwata-kwata horo kala huɗu ya ba shi, kuma Jay bai wani suma sosai ba, bai fi suma biyar ya yi ba fa, kuma da aka kai shi word room iya wuni ɗaya daddy ya ɗauka kafin ya samu ya ceto rayuwar sa". Dangware masa kai Tga ya yi yana faɗin "Close your mouth hai, ba kai ma ka kara musu zafi kan zafi ba, ai kai punishment da ka yi wa Jay ya fi zama masa tabo a zuciya fiye da wahalar da Lion ya ba shi". Turo baki Michael ya yi a shagwaɓe ya ce "Me kuma na yi?" Hararar wasa Tga ya watsa masa kafin ya ce "Ka harbe masa beb ɗin sa mana, ga shi kuma Lion ya ce ajefar da babyn boy ɗin sa da suka haifa" kasan cewar yanzu Michael ya san daidai da ba daidai ba, sai zaro ido yana faɗin "Uncle like how a jefar da baby kuma? Me babyn ya yi?". Tga zai yi magana suka ji dakun tafiya, wadda duk gidan shi kaɗai ke irin wannan tafiya. A zafafe kowa ya kama matsayar sa, dukkan su suka nitsu, Michael ya fara aikin training ɗin sa, ga ruwan da daddy ya zuba masa kamar zufar gaske. Gaskiya daga daddy har ƴaƴan sa Michael da James duk sun iya basaja over wai, ko da yake gado ba ka ranbani ba, a wajen sa suka koyi basaja. Lion na shigowa wajen da kallo ɗaya ya musu ya san basu da gaskiya kwata-kwata, sai wani yan kame-kame suke yi, shi kuma Michael har da wani nishi, irin na wanda ya sha wahala sosai ɗin nan. A nitse Lion ya tako izuwa cikin ɗakin, jikinsa na sanye da Ripped Jeans blue color, ta sama kuma yana sanye da Turtle high, ya yi wa kayan kyau kamar me, shike yiwa kaya kyau, ba kaya ke masa kyau ba, sai tashin wannan fitinannen kamshi perfume ɗin nasa yake mai bala'i daɗin kamshi, yau dai ya ɗaure ga shin kansa a bayan wuyar sa, while shi kuma guntu na gaban goshin sa yana nan. Tsare su ya yi da ido yana kallon rashin gaskiya karara a bayyane a fuskar su. "Who changed this setting?" Ya yi maganar yana nuna saitin na lokacin da aka shiga ɗakin, domin shima kofar ɗakin yana da ma ajiyar bayan yaushe aka shiga, yaushe kuma a ka fita, to shima Tga ya canza, sai dai garin sauri ya je ya saka karfe 6 na dare a maimakon na safe. Tsuru-tsuru suka yi da ido, sun kasa magana. Kallon daddy Lion ya yi, cikin sauri daddy ya girgiza masa kai ala'mar shi bai san komai ba a kan hakan, shiru ya ɗan yi kafin ya maido da kallonsa kan Tga, tun bai yi magana ba Tga ya yi sauri cewa "Tun karfe 6 ya fara" Kai daga jin yadda Tga ya yi maganar kasan a tsorace ya yi ta, kuma karya ya labka, kallon machine ɗin Lion ya yi, already Tga ya kara mata gudu wadda yake nuna tun awa biyu da suka wuce a ke amfani da ita, shi kuma Michael munafiki sai wani hakin karya yake yana mai da numfashi da kyar da kyar kamar da gaske. Yan basaja. "Daddy shiga ciki" shine abin da Lion ya ce, tun da John ya ji haka sai ya yi sauri ya riga daddy miƙewa zai bar wajen, da ido kawai Lion ya gan shi ba tare da ya masa magana ba, a ɗari ya koma ya zauna, nan take jikinsa ya fara kerma, sun taro match, Na dama Tga ya fara yi na karya da ya yi, sun biyewa Michael suna goya masa baya, bayan kuma sun san in dai Lion ya zo wajen tofa sai ya gane su, sai dai sun sa a ransu zasu jure duk wani hukunci amma ba zasu iya ganin Michael cikin wannan ukubar wahala ba, dan bai saba ba, kwata-kwata ma yaushe ya tashi daga ciwo Romeo zai ɗaura masa wata azabar. Shi kuma daddy tuni ya tashi ya wuce cikin gida abin sa, har da saurinsa bayan kuma shi ya hassa komai, shi yake goya wa Michael baya suna zuba tsiyar su, ga shi kuma yau sun zo sun yi wa Lion karyar da sun san dole zai gane su. (Oh su Tga har da chanza saitin machine ɗin, a tunaninsu sun tsira🤣) Duba time a jikin diamond watch ɗin hannunsa Lion ya yi, sannan ya ɗago ya kalli Micheal. Wucewa ya yi ba tare da ya ce musu komai ba, ya je ya kunna na'ura dake saman wajen kusa da camera, sannan ya koma bakin kofar wajen ta waje ya tsaya kamar mai jiran wani abin. Minti biyu da kunna na'uran gaba ɗaya saman katifar da suke ya fara juyi kamar fanka, sai sama suke suna kasa, Michael daga shi har machine ɗin nasa juyi suke, dan har da mashunan Lion yasa su rinƙa juyawa, dan su Tga su sha wuya, Tga da John sai gwara kansu suke waje guda, ba halin su tsaya, ba zama su iya kama jikin su ba, sai yadda wajen ya yi da su kawai, shima Michael zubewa kasa ya yi daga saman machine ɗin, ya yi joined na su, idan kafitar tayi sama da su sai ta dawo da su, su gwara kai da juna, wani lokaci kuma ɗaya ya faɗo kan ɗaya, rufe musu kofar Romeo ya yi ya tafi ya kwalesu. Lallai kuna tsaka mai wuya. Duk bakin Tga ya fashe ya fara jini, saboda buguwa da katon kai ɗin John da ya rinƙa yi, ga shi ba za su iya ta shi bama, bare su kashe na'uran, kuma idan suka yi hakan ma, Romeo zai gansu ta camerar dake wajen, idan ya gansu kuma sun shiga uku, dan sai sun karɓi hukunci mai tsanani sosai, wannan ma iya hukuncin karya da suka masa ne, ba'a zo kan hukuncin karawa Machine ɗin Michael gudu da suka yi ba. (Tofa kuma kuna ruwa, ni dai bari na je Nigeria na dawo🛫) 💖💖GIDAN ABBA💖💖 Yau wuni su Rufee suka yi wa Umaisha, sai murna take yau ɗaya ta samu farincikin da tun da ta yi aure, idan ba Akil yana nan ba, bata zamun hakan, a gaskiya Akil yana nuna mata kulawa sosai da sosai, dan yana son ta, soyayya mai tsanani, tun bata kai komai ba, yake son ta, hakan zai tabbatar maka ba wani abu na jikinta yake bukata ba, ita ɗin dai yake so, dan tun ba nono a kirjinta ya fara sonta, shiyasa yake nuna mata soyayya fiye da nunanin mai tunani, sai dai ɓatar Jelly ya jefa su cikin wahala, hakan yasa yanzu bata samun lokacin sa, kuma bata ganin laifin sa ko kaɗan, dan idan ya dawo yana biyan duk wayan nan lokutan da ya ɗauka ba tare da ita ba, yana faranta mata ya sa ta mance da a baya ya hanata wasu lokuta nashi, shiyasa bata damuwa, ga shi yanzu ya koya mata wani azababben son shi, wadda ba zata iya rabuwa da shi ba, Akil ya kware a iya soyayya fiye da tunanin mai tunanin. Sai karfe 7 na dare driver ya zo ya ɗauki su Rufee zuwa gida, amma kafin ta tafi, sai da ta sace wa Akil danƙara-danƙaran watchs nasa masu bala'i tsada guda uku, duk su Aafia ba su sani ba, bayan nan ta ga wasu kuɗaɗe cikin drawer mirror, wadda Akil ɗin yake ajiye wa, idan Umaisha ko Akila za su bukaci wani abin idan baya nan, sai suyi amfani da su. Sai dai basu taɓa taɓa ko naira a cikin kuɗin ba, domin ba su bukatar komai, akwai duk wani abin da za su bukata a gidan, sannan ita Akila idan zata je school Ammie da Abba suna bata kuɗi, kuɗi kashewa har yawa yake yi mata, sai dai ta yi ta bawa kawayen ta a school. Tas Rufee ta kwashe kuɗin ba tare da sanin su Aafia ba, sannan kuma har da wani cewa Aafia gobe zata dawo su wuni, sai Akil ya dawo ya mai da su gida, to kawai Aafia ta ce mata, Anisa kam ta ce ba zata dawo gobe ba, dan ba za'a barta a gida ba, ta fita yau ta fita gobe ba mum ɗin ta ba zata yarda ba. Wannan sai Rufee uwar sallamammu, kamar an sallamata wa duniya, sai taje waje ta kwana ma ba mai wani damuwa, in dai zata kai musu kuɗin dafa abincin da za su ci ai Shikenan, bata da wata matsala kuma. Da suka zo tafiya manya-manyan kwalaben turaruka wadda Akila ta sayo mata a shopping, guda huɗu Umaisha ta bawa su Rufee, ita biyu Anisa biyu, bayan haka ta ce bari ta ɗebo musu kuɗi ko za su sayi wani abin a hanya, cikin sauri Rufee ta dakatar da ita, dan ta san idan ta kyale ta, ta je wajen drawer, zata ga ba kuɗin ta kwashe su, asirin ta zai iya tonuwa, shiyasa tayi saurin hana ta. Haka suka wuce ita da Anisa driver ya mai da su gida. Misalin karfe 8 na dare bayan sun yi sallar issha Aafia ta ce da Umaisha su je palo su ɗan huta su yi kallo, ta ga ji da zama a cikin ɗakin, nan fa Umaisha ta sanar mata ai Ammie ta hana ta zama a palo, tsaki Aafia ta ja sannan ta riƙo hannunta suka fice daga ɗakin zuwa Palo. A nan suka isko Ammie da Abba sai Akila, suna zaune suna hira, zama Aafia ta yi tun ba'a bata izinin zama ba, cike da kulawa ta ce "Bappa ina wuni?" Da fara'ar sa ya amsa mata da lafiya sannan ya tambayi ya Abbi da Irfan, suna lafiya ta ba shi amsa, haka suka zauna shiru har zuwa lokacin da mai kawo musu abinci daga restaurant ya kawo musu. (Ku dai aiki ya ganku kullun sayan abinci tab🤔) Cikin kwanciyar hankali suka ci abincin su, Umaisha ta samu sake yau, har da hira da dariya tare da Akila, sai karfe 9 da rabi, sannan kowa ya wuce ɗakin sa. Misalin karfe 12 na dare, Aafia da Umaisha suna cikin barci, kamar a mafarki Aafia ta ji ana ta kwala mata kira a palo, abin mamakin kuma muryan Irfan take ji, ita kuma Umaisha bata jin komai, sai zuba barcin ta take yi cikin kwanciyar hankali. Miƙewa Aafia ta yi, idon ta duk barci, a hankali ta zuro kafafun ta kasa daga saman gadon, ta laluɓa a cikin duhu ta fito wajen dan ta je palo taga wake kiranta. Tana isa palo taga duhu ba haske, lallaɓa ta yi zata koma sama, sai ta ji muryan Irfan yana faɗin "Ki kunna mana haske" nauyayyar ajiyar zuciya ta sauƙe, dan da farko ta tsorata sosai, ta ɗauka wani abin ne. "To yaya Irfan" ta ba shi amsa. Da kyar ta iya karisawa wajen switch na palon, tana kunna wutar idon ta ya mata arba da abin da kwakwalwar ta ba zai iya ɗauka ba, ihu ta saki tare da watsawa a guje zata haura sama, sai dai kuma ina, kamar wadda a ka sakawa mayen karfe, haka suka jawota. Wani karin haske game da dodannin nan, in dai kana cikin gidan Abba idan suka zo matikar baka da riƙo da addini sai sun haɗa da kai sun zane ka, Akila baiwar Allah akwai riƙo da addini shiyasa basu taɓa zaneta ba, haka ita ma Umaisha ta fi Aafia riƙo da addini ga askar, shiyasa kome zai faru a gidan su basa ji, Imran da Akil kam dama ba'a magana, wayan nan ai malamaine, kuma dodannin basu iya shiga ɗakin da akwai Alkur'ani mai girma, wannan dalili yasa suka jawo Aafia da dabara, domin part ɗin Akil dai Akwai Alkur'ani mai girma, haka ita ma Akila tana da Alkur'ani mai girma, amma Ammie da Abba ba su da Alkur'ani a ɗakunan su. Dodannin uku ne suka rike Aafia, wani mummunar katon dodo, ya fito da wani zabgegen kafurin bulala ya hau zabga mata a baya, ga shi sun bankare masa ita gwanin daɗin duka. Sai ihun azaba take yi amma babu mai jin ta bare kuma ya kawo mata ɗauki. Edited Suna rike da ita, ta ga Abba da Ammie ma sun fito kamar wayan da a ka kira, kuma dama haka ne, mafiya yawan lokuta dodannin nan suke kiran su Ammie palo, ko su saka su jin yinwan dare dan su fito palo, saboda sun fi jin daɗin azabtar da mutane a palon, dan akwai balance, akwai fili, suyi ta wujijjiga mutun yadda suke so, suna wurgi da shi sama da kasa. (Yau Aafia jarabar gidan Abba dake ya afka, sai dai mu ce sorryyyyy, kinzo a kan gaɓa🤣) A guje Abba da Ammie suka juya za su koma sama, Aafia na gani dodanin nan suka riƙo su, suma a ka ɗaura su a kan hanyar karɓan, wannan zabgegen kafurin bulalan. Aafia tana ihu tana ganin yadda Ammie ke ihu amma ba mai jinsu, sai fashe musu baya mugun azzalumin mummunar dodan nan yake yi, Abba kam ba'a magana ya azabtu matuka, kuma shi suka fi duka, Bawan Allah, har wani gwalalo idanuwansa waje yake yi. Good 10mins wannan baki mummunan azzalumin dodan ya ɗauka yana zane musu jiki, kafin nan ya yi wa dodannin da suka riƙe su magana da ido a kan su sauke su, ba musu suka sauke su. Dukkan su uku har Aafia ba wanda ya iya zama da mazauninsa, domin a daidai wajen ya fi yawan zabga musu bulalan. Sai numfashin suke sama sama, dukkan su, a kasa suka kwanta suna hawaye, kwanciyar ma ruf da ciki suka yi. Yau sun ma yi Sa'a iya bulala kawai dodannin suka musu suka bace, sai dai kuma ko da suka ɓace raɗaɗin azaban zafin da suke ji na bulalan, ya jima bai sake su ba, sai wajajen asuba, sannan raɗaɗin ya sake su, yana sakin su kuma suka mance komai suka hau barcin azaba. Sai karfe 7 na safe Akila ta fito zata je part ɗin Akil dan ta duba Umaisha, Akila Akwai amana, in dai Akil baya gari, to da sassafe zata je ta gaishe da Umaisha, ta tambaye ta ko tana bukatar wani abin, idan ta ce mata bata bukatar komai sai ta wuce ta je ta yi shirin zuwa school. Ganin su Ammie kwance rashe-rashe a palo, hakan yasa Akila mamaki sosai, daidai lokacin ita ma Umaisha ta fito dan duba Aafia. Cirko-cirko suka tsaya ita da Akila domin abin ya basu mamaki, ba kaɗan ba, sun rasa ta ina za su fara. Akila ce ta yi ta maza ta fara kiran sunan Ammie, ta ɗan jima tana kiran sunan kafin Ammie ta farka a firgice tana faɗin "Dan Allah ku bari bana so" . "Ammie suwa ye za su bari?" Cewar Akila. Sai lokacin da ta ji muryar Akila sannan ta dawo hayyacinta, miƙewa tsaye ta yi tana faɗin "Akila kin dawo school ne?" Kallon mamaki Akila ke yi mata, wani school Ammie ke nufi kenan, ta tambayi kanta. Bata kai ga yin magana ba Ammie ta sanya hannu tana ɗan bubbuga Abba tana kiran sunansa, a zafafe shima ya miƙe bayin Allah sun mance komai. Haka suka wuce part na su, Akila sai mamaki ta ke yi, abin gwanin ban tausayi, gwanin kuma a dasa masa ayar tambaya, dan dai ba lafiya ba. Umaisha ce ta tashi Aafia, a mai makon ta tashi kamar yarda kowa ke ta shi daga barci, sai ta tashi da banko ashar, wa iya zubillah, Aafia ta iya zagi sosai. "Aunty Afi lafiya ki ka zo nan ki ka kwanta?" Umaisha ce ta tambaya tana tsare ta da ido. Ina ai Aafia ta mance komai, dan haka sai ta miƙe ta wuce part na su kawai. Kallon kallon Akila da Umaisha suka yi wa junan su, lokacin guda, alamar tambaya ya ɗarsun musu a ransu dukkan su, sai dai babu mai basu amsa. Sun ɗan jima tsaye a wajen ba wanda ya ce da ɗan uwansa uppan, sai daga bisani suka gaisa sannan suka wuce part ɗin Umaisha a tare, sai al'ajabin abin suke yi. Nima sai al'ajabin abin na ke yi, amma haka na kwashe kayana zuwa kasar yarabawa 💖RIMSHA💖 Yau tun safe ta tashi da matsananin zazzaɓi da ciwon kai mai bala'i zafi, hakan kuma ya samo asaline sakamakon kukan da ta sha tsakar daren jiya, lokacin da duniya gaba ɗaya suke barci, alokacin ita kuma baiwar Allah ta cusa kan ta cikin cinyoyinta tana ta rera kuka. Ayla da Kausar ba wanda ya ji kukan nata, domin yau ba a kan gadon Kausar ta kwana ba, ta ki yarda ta kwanta a gadon, ta zuciya, a kasa ta bakin kofa ta kwanta. Haka da asuba ma ta sake shan kukanta son ranta, shi kuma kukan asuban da ta yi, ta samo asaline, saboda ta fita yin alwala, boda Jami'u ya fito shima, shine ya zo zai taɓa ta, zata gudu ya damko gashin kanta, dama ita Rimsha bata da wani wajen kamawa a jikinta, sai gashin kanta, kowa ya ta shi kamata, gashin kanta yake riƙowa, saboda tsawon gashin. Data kware baki zata masa ihune ya yi maza ya sake ta, shine ta dawo ɗaki taci kukanta, tana mai kara jin zafin rashin daddynta a raye. Misalin karfe takwas na safe, Kausar da Ayla sun ci abinci, amma ita Rimsha tana ɗaki saboda zazzaɓi, ko miƙewa bata iya yi, Iya da kanta ta kawo mata abincin ɗaki sannan ta lallaɓata a kan ta ci. Kaɗan ta tsakuri abincin ta barshi, ba yadda iya ta iya, haka ta kyaleta. Ita kuwa Kausar sai murna take yi, yau za su je biki a kasar anguwar su can, sai shiri take yi, ba ta bi ta kan Rimsha ba. Iya ta yi ta yi a kan Rimsha ta yi hakuri ta tashi ta yi wanka su tafi, amma ina Rimsha ta ki, ta ce ba zata iya zuwa ba, domin sosai take jin zazzaɓin, ga jikin nata kamar wuta saboda zafi, Iya ta ce zata taho mata da magani. Ayla ma ta ce tun da Rimsha ba zata je bikin ba, ita ma ba zata je ba, Iya ce ta tasa ta gaba ta ce a'a ita tun da tana da lafita ta shirya su je. Ba yadda Ayla ta iya haka ta shirya suka tafi bikin nan, suka bar Rimsha ita kaɗai, baiwar Allah sai nishi take yi, ga numfashi ta dake ta fita da wani irin sauti kamar mai minsharin barci, sannan numfashi tata ma, zafi ne da shi kamar me. A haka har barci ya yi awon gaba da ita. Can cikin barci ta ji ana ƙoƙarin zame mata wandon dake jikinta, a zabure ta farka tare da buɗe idonta, mai ɗauke da ciwo karara. Karaf sai cikin idon boda Jami'u,. idanunta suka sauƙa, ga shi idon nasa sun yi jawur kamar jini, dama ga shi ɗan baki. Ihu ta saki, sai dai ihun nata ba sauti saboda matsananin zazzaɓin da take ji, da kyar ma take iya buɗe bakinta, tattara iya karfin ta tayi zata miƙe, da hannu ɗaya ya mai da ta ya danneta da karfi. Sai ihu take yi, amma ba wanda zai iya jin ta saboda ihun tata ba sauti. Zame hannunsa da ya danne ta ya yi yana kokarin cire mata wando, wani irin karfin ta ji ya zo mata, da iya karfin ta na karshe ta ture shi ya faɗi saman gadon kan shi a kasa, saboda tsawon gadon ya kare ta wajen. A zafafe ta miƙe ta nufi hanyar fita daga ɗakin, sai dai bata kai ga fita ba, ta ji ya danko gashin kanta. Ita dai Rimsha bata da wajen kamawa a jikinta sai gashin kanta, saboda suna ganin shi har baya, yana da daɗin kamawa, koda gudu take yi, za'ayi saurin riƙota ta gashin nata. Janyota ta ya yi da gashin nata, wani wahalallen ihu ta saki, domin har ga Allah ji ta yi kamar zai tunɓuke mata gashin tata, saboda da iya karfin sa ya ja gashin. Jan ta ya yi har zuwa saman gadon, ya kwantar da ita sannan ya sauka ya nufi wajen drawer kayan Kausar, dama gaba ɗaya kofofin gidan basa rufuwa, jam lock nasu ya ɓaci kuma ba su da key. Kofar palo ne kawai ke da sakata, shima an saka mishi sakatane, saboda shine na fita waje, da su Iya suka tafi, Rimsha bata rufe kofar ba, saboda bata ma san yadda ake rufewa ba. Ganin ya tafi wajen drawer kayan Kausar ne yasa ta sake tattara iya sauran karfinta, ta miƙe ta diro kasa, ta nufi palo, yana ganin ta amma bai wani damuba, sai bincike yake yi cikin kayan Kausar. Ita kuwa tana fita Palo ta nufi kofar fita, sai kuma me? Ashe azzalumin ya rufe kofar, dama ashe yana laɓe a cikin gidan tun da ya ji su iya za su ta fi biki, ita Rimsha ta ce ba zata je ba, shikenan sai ya laɓe yaki fita wajen aiki, har sai da suka tafi ya fito ya rufe kofar palon. Cike da tashin hankali ta fara ƙoƙarin cire sakatar, bata iya ba, kuma bata taɓa ganin irin sakatar ba sai da tazo gidan. Sai jan sakatar baya take yi, tana yi tana kukan a kawo mata ɗauki. Bata ankara ba, ta ji ya riƙo hannun ta, ya fisgota da karfi, ya ja ta zuwa cikin ɗakin, tun tana kokarin ihu ko za'a kawo mata ɗauki, tana tirjewa, har ta hakura dan yanzu muryar ta ma ya dai na fita ya dashe. Saman gadon Kausar ya kwantar da ita, tana kokarin miƙewa, ta ki yarda ta kwanta, kafarsa ɗaya ya sanya ya take kafafunta dukka biyu, da karfi, sannan ya damki hannunta ɗaya, ya dauko wani gyalen Kausar ya ɗaure hannun nata da jikin kafar gado, shi kuma ɗayan hannun nata ya ɗaure a jikin window. Bayan ya gama ɗaure hannu sai ya cire kafarsa a saman nata da ya take, kamar jira take yi ya cire, ta fara wuncila kafafun nata sama, alamar bata so, tana haɗa shi da girman Allah ya rabu da ita, ya kyaleta, amma ina babu imani ko kaɗan a ransa. Daukar wani zanin Kausar ya yi ya ɗaure kafar ta ɗaya a jikin wannan window kusa da gadon, in da ya ɗaure hannun nata, sai dai ya ɗaure hannu ta a farkon window shi kuma kafarta a karshen window, sannan bai matse kafar nata da window ba, dan window ya ɗan yi sama, sai ya saki igiyar wato gyalen, ya ɗan yi musu balance, shi kuma ɗayar kafarta, a jikin kafar gadon ya ja igiyar zanin ya ɗaure a wajen, ɗaiɗai ya yi da ita kamar ana gasa kaza. Ta yi kuka har hawayen ta suka dai na fita, sauka ya yi ya fita zuwa na shi ɗakin. Yana fita ta fara kokarin tsinke ɗaurin da ya yi mata, amma ina ta kasa, dan gyale dai yana da kaurin da ba za ta iya tsinke shi ba. A haka ya dawo cikkin ɗakin ya sameta, hannun sa rike da almakashi, zaro sleeping eyes nata ta yi wadda yanzu suka rine saboda kuka, da kyar da kyar ta ke iya maga, muryar ta baya fita, ga zafin zazzaɓi, amma a haka take ta haɗa shi da Allah ba gajiyawa. Ganin tana takura masa da, Uhm, uhm ɗin dake fita da ga bakin ta ne, ya sanya ya ɗauko wani rigar Kausar ya cusa mata a cikin bakinta, sai girgiza kai ta koma yi, abin gwanin ban tausayi, duk wanda ya ganta sai ya mata ruwan hawaye. Sanya almakashin nan ya yi, ya fara yanka mata wandon jikinta, daga kafar wandon ya fara har zuwa ƙugunta, ta gefe kenan. Bayan ya yanke wannan gefen ya dawo ta ɗayar gefen ma. (Kai wannan Jami'u anya akwai Allah a kamarinka kuwa? Anya kai Musulmi ne? Marainiyar Allah ta'ala? Sai haɗaka da Allah take yi, amma kaki bari, Kai jama'a duniya ina zaki damu) To ni dai ba zan iya wannan abin ba dan haka na haɗa kayana sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu 💞💞TRIPLET'S💞💞 E29-30 Sanya almakashin nan ya yi, ya fara yanka mata wandon jikinta, daga kafar wandon ya fara har zuwa ƙugunta, ta gefe kenan. Bayan ya yanke wannan gefen ya dawo ta ɗayar gefen ma. Runtse idanuwanta ta yi a cikin zuciyarta take faɗin "Ya Allah, kai kace mu nemi taimako ka a lokacin da muke bukata, matikar munyi yakini da kai kuma mun yarda kai ne zaka iya biya mana bukatar mu, ya Allah ina tawassuli da sunayenka tsarkaka guda 99 ya Allah ka kawo mini ɗauki, kada ka bari wannan mugun ya lalata mini rayuwa, ya Allah alfarma girman zatinka da izzar ka, albarkacin girmanka ya Allah ka sauko mini da ni'imar ka a gareni, na kareni daga wannan azzalumi, kaine arrahmanu ya Allah, mai rahma a kan bayinsa, mun saida, kuma na miƙa wuya agareka, babu wanda ya isa ya yi wa bawa abin da baka tsara masa ba, ba kuma wanda ya isa ya hana bawa abin da ka tsara masa, babu abin da ya isa ya yi motsi a dukka faɗin sammai da kassa ba tare da izinin ka ba, ya Allah ka taimake ni, wasbunallahu waniimal wakil, daga karshe ta rufe addu'ar tata da salatin Annabi salatin ibrahimiyya Shi kuma boda Jami'u almakashin yasa yana, ya fara yanka ɗayan gefen wandon nata. Yana tsaka da yanka wa kawai ya yanke jiki ya faɗi a gefen ta, ita kuma dama ta runtse ido tana hawaye. Jin ya faɗi kusa da ita ya sanya ta waro idanuwanta da sauri, dan a tunaninta ya gama yanke mata kayan ne zai fara lalata mata rayuwa. Rinannun idanuwanta ne suka mata arba da Ayla tsaye riƙe da katon katako a hannu ta, sai haki take yi, tana mai da numfashi. Cikin sauri Rimsha ta yi kokarin yunkurawa ta tashi, ta mance a ɗaure take, ba zata iya tashi ba, kuka ta saka da wannan dashashiyar muryar tata, ga kuma rigar Kausar a bakinta, ita ma Ayla kukan ta saka tare da yin wurgi da katakon ta haye saman gadon ta rungumo Rimsha tare da cire mata tsummar rigar Kausar ɗin dake bakin ta, suka ci gaba da hawayen a tare. Abin da ya faru shine, lokacin da Rimsha ke jan sakatar kofar ta kasa buɗe wa, to da ya zo ya fisgo hannunta, wannan jan ta da ya yi, dama hannun ta ɗayar na kan sakatan, yana jan ta, ta janyo sakatar ya fita, sai dai dukkansu basu lura da cewa sakatar ta fita ba. Ayla kuma bayan sun je gidan, ta kasa samun nitsuwa, ta kasa zama waje guda, sai tunanin jikin Rimsha take yi, har kuka ta rinƙa yi a ɓuye. Su iya suna can suna cin uwar sabada, an sake musu kiɗa, sai tikar rawa suke, shine ita ta lallaɓa ta saci hanya ta bar gidan bikin, ta kamo hanyar gida dan tazo ta duba jikin Rimsha ko zata samu nitsuwa, baiwar Allah ta kasa samun sukunin. Kasan cewar bata san hanya ba, sau uku tana ɓata hanya sai ta sake komawa baya, da kyar ta Iya gane hanyar. Lokacin da ta shigo gidan Allah yasa bata yi magana ba, kawai ta nufi ɗakin Kausar, tun da ga ɗan bakin-bakin kofar ɗakin take jiyo nishin Rimsha hakan yasa ta karisa da sauri. Turus ta tsaya a bakin kofa ganin abin da ke faruwa, lokacin ya gama ɗaureta yana kokarin yanka mata wando, ga shi ya toshe mata baki. Ganin haka yasa Ayla ta ja da baya a hankali, zuciyar na tafasa kamar zai fashe ya fito waje, har ta fara hawaye, addu'a take yi Allah yasa bai lalatawa Rimsha rayuwarta ba. Kitchen ta fara shiga, bata samu madaki ba, sai ta fito waje, da farko katon dutse ta ɗauke, sai ta ji bai yi ba, hakan yasa ta jefar, ta fara yan dube-dube, can ta hango katako, shine ta ɗauko cikin sauri ta koma cikin gida. Ta shiga ɗakin a hankali-hankali take tafiya, Allah ma yasa Rimsha ta runtse idanunta a lokacin, shi kuma hankalin shi ya yi nisa yana tunanin yadda zai fara shigar Rimsha. Tana isowa wajen ta ɗaga katakon da iya karfinta na karshen ta buga masa a kai, shine ya yanke jiki ya faɗi sumamme ne ko matatce ne wallahu a'alam, wannan shine abin da ya faru. Sosai suke kuka. Sai da suka yi mai isar su, sannan Rimsha ta ce "Ayla kwanceni" Ayla bata iya jin me Rimsha ke faɗe saboda maganar nata baya fita sosai, sai da ta matso da kunnenta sai tin ɗan bakin Rimsha ɗin, sannan ta iya jiyo me take faɗa. Cikin sauri ta sanya hannu tana kokarin kwancewa amma ina abin yaci tura, ba ɗaurin wasa ya yi mata ba. Ganin ba zai kwancu ta daɗi bane ya sanya ta ɗauko wannan almakashi da ya fara yanka wa Rimsha wando, ta fara yanka kayan Kausar ɗin dukka tana zubarwa. Bayan ta kammala, Rimsha ta miƙe ta rungumeta da kyau tana zuba mata godiya. Itama Ayla godiya ta rinƙa yi mata, domin a cewar ta kome zata yi wa Rimsha ba zata iya biyan ta ba, domin Rimsha ita ce silar fitarsu Daular Mutuwa, shekara uku Ayla tana Daular Mutuwa, har ta cire ranta da fita sai ga shi Rimsha ta tazo ta zamo musu silar fita, hakan ya sa take kula da Rimsha sosai. Da kyar Rimsha ta iya dirowa kasa daga saman gadon sannan ta miƙe tsaye, sai layi take yi kamar zata faɗi, wajen drawer kayan Kausar ta nufa, dogon riga ta ɗauka ta sanya, sannan ta ɗauki wani dogon wandon jeans ta cire na jikinta daya yanka ta jefar ta sanya wannan, sai binta da ido Ayla take yi. bayan ta gama saka kayan nata, ta shirya tsab, ta fito da wannan paper da ta yi zanen Romeo a jiki, sannan ta ɗauki takardun girkin da ta saya jiya a kasuwa, ita dai Ayla sai binta da ido kawai take yi. Sai da ta gama haɗa komai nata, bata bar ko abu guda ɗaya ba, sannan ta riko hannun Ayla tana faɗin muje Ayla. "Rimsha ina kuma zamu je? Waye muka sani a nan?" Rimsha kamar zata yi kuka, sai layi take yi, ga zafin zazzaɓi, kanta kamar zai fashe mata saboda ciwon da yake yi mata. Da kyar ta iya fara magana "Ayla kina son ne mu cigaba da zama a nan gidan? Kina son ne mu zauna su lalata mana rayuwa, ko ma su kashe mu baki ɗaya?". Girgiza kai Ayla ta fara yi tana faɗin "A'a Rimsha bana so su lalata mana rayuwa, to amma abin da zaki duba a nan shine, waye muka sani a nan? Idan mun bar gidan nan ina muka nufa? Dawa muka san zamu haɗu? Gara wayan nan da already mun san halin su, mun san abin da suke nufi da mu, idan muka barnan bamu san da suwaye zamu sake haɗuwa ba, wata kila ma wayan da zamu haɗu da su sunfi wayan nan munin hali, dan haka Rimsha ina son ki tsaya ki yi tunani kin ji?". Hawaye sosai Rimsha ta ke yi, "Ayla ya zama dole mu bar gidan nan, koma da su waye zamu sake haɗu, dole mu tafi, kada ki manta Ayla, muna Sallah sau biyar a rana, har ma mu kara da nafila, irin su walaha, shafa'i da witiri da sallar dare, sannan kada ki manta muna azumin litinin da Alhamis, muna askar da rokar Allah ya kare mu a ko yaushe, a kuma duk in da muke, In Sha Allah, Ubangijin ba zai taɓa barin rayuwar mu ta wulakanta ba, kada ki manta Allah da kansa ya yi alkawarin tallafawa duk wanda ya riƙe Sallah biyar a rana, yana yin su yadda ya dace kuma a kan lokacin su, ki sa a ranki Ayla Allah na tare da mu, kuma bayin Allah masu taimako basa karewa a duniyar nan, ki yarda dani mu bar gidan nan, kuma idan zamu fita, mu fita da yakinin Allah ya taimake mu ba wani ba, da izinin Allah zai kawo mana ɗauki" Ta kai karshen maganar tare da fara tafiya tana tangal-tangal. "Rimsha a hakan zamu tafi? Kina tafiya kamar zaki faɗi kasa" "Ayla kiyi wa Allah kizo mu tafi, idan kuma zaki zauna a nan ne to Bismillah, kada ki duba dan bana iya tafiya da kyau, niyar mu na tseratar da mutuncin mu shi zaki duba" Tana magana tana tafiya, ganin hakan yasa Ayla ta yi saurin karisawa wajen ta, ta ɗan riƙota dan ta taimaka mata, shi kuma boda Jami'u ya ji bugun katako, ko motsi baya yi, haka zalika baya numfashi, da alama cikin kansa ne ya sha bugun da babu jini ko kaɗan, sai kumburi da kan nasa ya yi kamar anhura balo-balo. Wajen gidan gaba ɗaya suka fito, sai da suka tsaya na yan mintocin da ba su fi biyar ba, sannan suka fara tafiya ta Eyankorin junction. Sunyi Sa'a babu kowa, har kofar gidan su waliya ba mutane. Da kyar Rimsha ta iya kai bakin junction ɗin, daga nan suka miki gabas suka ci-gaba da tafiya. Sun yi tafiya mai nisa har suka sauƙa daga bakin titin suka fara ratsa lunguna. Daidai wani kangon gida, Ayla ta zube kasa, saboda azababben ciwon mara da ya ziyarce ta lokaci guda. Hankali tashe Rimsha ta yi kanta tana kiran sunan ta, sai murkusoso take ta riƙe cikinta, nan take ta fara hawaye, wani na bin wani. "Ayla dan Allah ki yi mini magana, ki faɗa mini meke damun ki, na shiga uku na, Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Ayla dan Allah ki ta shi". Ina Ayla ko magana ta kasa yi, sai kuka kawai yake yi, Rismha na ƙoƙarin sake yin magana, idanunta suka mata arba da jini a jikin rigar Ayla, da yake doguwar rigar da ta sanya mai haske ne, sky blue ne. Ihu Rimsha ta saki, lokacin guda ta ji karfi yazo mata, dan a tunanin ta wani abinne ya sami Ayla, tabbas ta karanta mace na yin haila, sai dai bata san ya hailar take zuwa ma mace ba. Da sauri ta miƙe ta bazama neman wanda zaizo ya duba mata meke damun Ayla, ko kaɗan Rimsha ba ta yi dana sanin barin gidan su Kausar ba, sai dai ita Ayla ta yi dana sanin yin hakan ɗin, domin a cewar ta, da tana gidan su Kausar ko ba komai za'a kawo mata ɗauki. Ta hanyar da suka bi zuwa wajen, nan Rimsha ta bi, sai kuka take yi tana addu'a Allah ya dafa musu. Tana kokarin fita lungun dan ta nemo mai duba mata Ayla, gaba ɗaya ta birkice, jiri take gani, saboda yinwa da kuma ciwo, bata gani sosai, saboda karfin hali da tausayi irin tata, hakan yasa ta rinƙa ɗaga kafa da iya karfinta kawai tana takawa, bata san inda take sauke kafar tata ba, domin bata iya ganin gaban ta. Bata ankaraba ta ji ta yi karo da mutun, baya ta yi zata faɗi, cikin sauri ya riƙe hannun ta yana kallon kyakkyawar fuskar ta wanda ya birkice a yanzu. "Lafiya baiwar Allah? Ina zaki je kike sauri hakan nan? Me ya same ki kike kuka?" Cikin harshen Hausa ya yi mata magana. Jin an mata magana da Hausa yasa ta yi saurin waro idanuwanta waje. Wani matashine, irin matasan fulanin nan, masu zuwa karatu ko dai wani abin, daga ganin sa, ɗan arewa ne, ba bayarabe bane, yana da tsabta jikinsa fes fes, ɗan gayu, ya ci gayunsa, daga gani kasan akwai naira a tattare da shi, hannusa ɗaya na riƙe da wani leda da a ka rubuta Item 7 a jiki, ledar tana da girma, sai tashin kamshin yake yi, kai daga gani kasan ba ɗan datti bane, a shekaru ba zai wuce 27 years ba, yana da kyau daidai gwargwado, kunsan jinin Hausa fulani da kyau ba'a magana. Ganin shi yasa Rimsha ta kara fashewa da kuka, sakin hannunta ya yi yana faɗin "Lafiya ko dai baki jin Hausa ne? To bari na miki yarabanci ko fulatanci sai ki zaɓi yaren da kike ji ki bani amsa" haka ya maimaita tambayar da ya yi mata da farko, da yaren yarabanci da kuma fulatanci, ko zai samu ta amsa masa yare ɗaya. Ciki ciki ta amsa masa da taimako take nema, sai dai bai iya jin taba saboda muryarta baya fita kuma ga shi tana kuka. Ganin ta ki yi masa magane ya sa, ya sanya kansa zai wuce ta, cikin sauri ta riƙo rigarsa, tare da sanya hannu ta shake wuyarta tana kokarin kakalo magana da karfi. Ganin haka yasa ya fahinci tana yi masa magana, amma baya ji ne, wata kila kurma ce ko bebiya, hakan yasa ya fara yi mata yar kurma-kurma, ita ma yar kurma-kurma kawai ta dawo yi masa, tun da magana yaki fitowa. Da hannu ta nuna masa in da Ayla take, cikin sauri ya riƙo hannunta suka karisa wajen, gaba ɗaya jikin Ayla ya ɓaci da jini, saboda juyawa da ta rinƙa yi. Shiru matashin nan ya tsaya, ya rasa ta ina zai fara taimaka musu, shi bai san komai game da period ba, ita Rimsha ta san yadda mai haila ya kamata ta kasan ce idan tana yi, ta karanta, sai dai kuma bata san ya mace ke fara yin hailar ba, ta san dai ance ya mace zata yi jini duk wata. (Tofa yau ake yinta) Miƙawa Rimsha ledar hannun sa ya yi, ya ce musu yana zuwa, karɓar ledar Rimsha ta yi tare da tsugunnawa kusa da Ayla tana hawaye. Suna wajen har matashin nan ya dawo tare da wata bayarabiya, da kallo ɗaya ta yi wa Ayla ta gane matsalar, sai ta ce da saurayin ya saya mata always bari ta taimaka wa yarinyar suje gida ta wanke jiginta, ina ne gidan su?. Kallon Rimsha ya yi, dan shima bai san gidan su ba, girgiza masa kai Rimsha ta yi, alamar ba su da gida. Matsowa kusa da ita sosai ya yi ya ce "Kanwata kwata-kwata baki iya magana ne? Ko kaɗan ba zaki iya ba? Na zaci bebiyace ke ai ba kurma gaba ɗaya ba". Cikin sauri ta ce masa "A'a ina iya magana" jin maganar ta na fita a hankali-hankali ne ya sanya ya matso da kunnensa kusa da ɗan bakinta dan ya ji me take faɗe, nan ta sanar masa tama magana. Cikin sauri ya ɗago ido ya kalle fuskar ta, yadda ya ji zazzakar muryarta, ba karamin daɗi ya masa ba. "Wow beautiful girl and sexy voice" ya furta a zuciyarsa. Sake jefa mata tambayar ina gidan su yake ya yi, sannan ya mai da kunnansa kusa da bakinta. Nan ta gaya masa su yan Katsina ne, basu da gida a nan. Ɗago ido ya yi yana kallonsu dukkan su biyu, lokacin guda ya ji yana son taimaka musu, dan haka sai ya ce da matar nan white house zata kai su, cikin sauri matar ta kalle shi. Da yaren yarabanci ta ce "Haba Ahmad me yasa zaka lalata wa yarannan yaruwarsu? White House fa? Bai kamata ka ɗauki yara kanana kamar wayan nan ka kai su hotel ba". Zaro idanuwansa waje ya yi, dan shi kwata-kwata bai kawo hakan a ransa ba, shi ba mazinaci bane, kawai sauƙa ya yi a white house ya kama ɗaki, dan ba shi da yan uwa a nan, amma bayan haka ba wani abin da yake yi a hotel, yana son taimaka musu sai dai ba shi da kowa, ya zamar masa dole ne ya kai su masaukinsa, in dai zai taimaka musu. Da yarabanci shi ma ya ce mata "Iya kin san halina, yau shekara uku kenan ina zuwa garin nan, duk da baki san daga in da nake ba, amma ai ke da kanki kina yabon halina, bani da wani shagon da nake sayan kaya, sai shagonki, ke da bakin ki kike cewa Allah ya yi wa iyayena albarka, sun bani tarbiya, to ina son ki sani, ni ba mutumin banza bane, wayen nan da kike gani kanne nane, ba wai wasu bare bane". Cikin sauri Iya ta fara bin fuskokin su Rimsha da kallo sannan ta kalli Ahmad ɗin, kasan cewar Hausa fulani duk in da suka shiga kamannin jini baya ɓata ɓuya, sai Iya ta ga kamanin Ayla da wannan matashin. Yar murmushi ta yi sannan ta ce "Ahmad na yarda, ga wannan mara lafiyar kamannin ku ɗaya sosai da ita, mu je to ka yi mana jagora zuwa room ɗin naka, amma gaskiya wannan tafiku kyau sosai, ita ta yi kama da indiyawa, kila da babanku ta ke kama". Ta kai karshen maganar tana kallon Rismha. Shi dai Ahmad burinsa kawai ta taimaka ta kai masa su ɗakin shi, dan yana son yaje wajen wani abokinsa ɗan school na su. Haka matar nan ta saɓi Ayla a kafarɗar ta, kasan cewar kakkarfar mace ce, kun san yadda matan yarabawa suke ba sai an tsaya ɓata lokaci wajen zayyana muku yadda suke ba. Allah sarki tana da kirki matar, bata ji kyamar jinin jikin Ayla ba, haka ta ɗauke ta suka tafi izuwa white house. White House wani tampatsetsen hotel ne mai girma, wadda yake ɗan gaba da su kaɗan, dan haka ba su yi wani tafiya mai nisa ba suka isa wajen. Ahmad ya musu jagora har zuwa Room na shi. Bayan sun shiga ɗakin, banɗaki Iya ta wuce da Ayla, ita kuma Rimsha zama ta yi saman bedside drawer tana ta bin ɗakin da kallo, rabonta da ganin ɗaki mai kyan wannan tun gidan su na Abuja, shiru ta yi tana jin yadda sanyin Ac ke ratsa mata jikinta, nan take ta fara rawar sanyi, dama already da zazzaɓinta a jikinta. Ganin haka yasa Ahmad ya kashe Ac sannan ya ce mata yana zuwa bari ya sayo abin da Iya ta ce ya sayo wato always, da kyar Rimsha ta gyaɗa masa kai, duk ta takure taki sakin jikinta. Har ya kai bakin kofa zai fita, sai kuma ya juyo ya ce da ita, "Ki hau gadon ki kwanta mana? Kada ki damu yar uwarki zata samu lafiya" girgiza masa kai ta yi alamar bata son hawa gadon. Shiru ya mata bai sake magana ba, dan bai son takura musu. Ya juya zai fita muryan Iya ta katse shi da cewa "Ahmad har da pant zaka sayo mata" sai lokacin ya gane me ke damun Ayla, shi kan shi kunya abin ya bashi, satar kallon Rimsha ya yi, ita ma ta sunkuyar da kai tana satar kallon shi dan ta ji iya ta ce pant, duk sai kunya ya kamata. Ganin hakan yasa ya wuce da sauri ya fice daga ɗakin. Yana fita Rimsha ta sauƙe nauyayyar ajiyar zuciya sannan ta ajiye masa ledarsa da ya bata ajiya awaje. Ta yi shiru tana tunanin rayuwa, daga wannan sai wannan kullun cikin jarabawa suke. Iya baiwar Allah, da kanta ta yi wa Ayla wanka, sannan ta ɗauki towel dake cikin toilet ɗin ta naɗota a ciki suka fito waje, Alhadulillah yanzu ciwon cikin Ayla ɗin ya ɗan ragu, yanzu kaɗan kaɗan take jin ciwon nata. Kusa da Rimsha tazo ta zauna, suka takure waje guda, yar dariya Iya ta yi kafin ta ce "Me yasa kuke takure jikin ku wajen guda? Ku da ɗakin yayan ku? Ko dan kun ganni ni bakuwa ce? Tom ku saki jikin ku, ni da yayan ku mun jima muna tare, kullun yazo garin nan a shagona yake sayayya, sai dai ban taɓa sani daga ina yake zuwa bane, ban san gidan da yake sauƙa ba sai yau". Cikin harshen yarabanci ta yi maganar, kasan cewar ba wani jin yaren suke yi sosai ba, sai basu gane zancen nata ba, dan haka sai basu kulata ba. Gefen gadon tazo ta zauna suna jiran Ahmad. A haka ya dawo ya same su, bakin sa ɗauke da sallama ya shigo cikin ɗakin, bakar ledar hannun sa ya miƙawa iya sannan ya fita wajen. Riƙo hannun Ayla iya ta yi, suka koma cikin toilet ta nuna mata yadda ake amfani da komai, sannan ta fito ta musu sallama ta fice waje. A waje ta isko Ahmad yana tsaye daga sama yana kallon garin da yadda yake. "Ahmad it seems like wayan nan ba yan uwan ka bane" cikin sauri ya juyo yana faɗin "Like how Iya?" Yar murmushi ta yi kafin ta ce "The way na ga suna kame jikin su, basu saki jiki da ɗakin naka bane, sai wani ɓoɓɓoye kansu suke cikin jikin juna, kamar basu yarda da ɗakin ba". Girgiza kai ya yi yana faɗin "No Iya kawai dan basu taɓa zuwa hotel bane shiyasa, amma yan uwana ne, kuma ai kema baki taba ganin na zo da su ba ko?" Gyaɗa masa kai ta yi alamar ne "To kin gani basu taɓa zuwa hotel bane, shiyasa suke tsoro, yanzu ma akwai dalilin da ya sanya na zo da su garin nan, amma idan ba haka ba, basa fita kullun suna gida". Shiru Iya ta ɗan yi kafin ta ce masa to shikenan ita ta wuce, godiya ya mata sannan ya ciro 10k ya bata, ta karɓa ta yi masa godiya, sai mamakin irin karyar daya zuba yake yi, shi ba ma'aboci karya bane, ya sha mamakin ya akayi ya zuba karya son ranshi yau, ya ma akayi ya iya tsara karyar haka. Ya ɗan jima tsaye a wajen kafin ya koma cikin ɗakin, zaune ya same su saman drawer ɗaya sun takure jikinsu waje guda. Kallo ɗaya ya yi musu ya kawar da kansa gefe saboda Ayla bata da kaya a jikinta, towel kawai ta ɗaura, rigar tata duk ya ɓaci da jini. Kasa magana ya yi sai ma juyawa ya yi ya fice daga ɗakin yana tunanin kyan Rimsha. Kasa gaba ɗaya ya sauƙa, har ya sauka sai kuma ya sake haurowa sama ya koma cikin ɗakin, a gefen gadonsa ya ɗauko key ɗin mota mai bala'i kyau, sannan ya fito. Kai tsaye wata dankareriyar mota ya nufa kirar *McLaren solus GT.* Launin baki, sai kyalli motar ke yi, ciki ya shiga ya kunna motar ya ja ya fice daga hotel ɗin. Yana fita kai tsaye cikin Ilorin ya nufa. Su Rimsha kuwa, dukkan su sai kugi cikinsu ke yi musu, yinwa suke ji sosai, Rimsha ga zazzaɓi Ayla kuma ciwon mara. Suna zaune a wajen, har bayan awa ɗaya basu tashi ba, haka ba wanda ya yi wa ɗan uwansa magana, haka Ahmad ya dawo ya same su, hannun sa riƙe da manya-manyan ledoji guda biyu, irin ledojin shopping ɗin nan. Da sallama ɗauke a bakinsa ya shigo cikin ɗakin, Ayla ce ta amsa masa sallamar tasa, haka kawai Ahmad yake jin tamkar yana da wata alaka da su, shiyasa ya zage yake taimaka musu, yana jin kwanciyar hankali tarayyar sa da su. Kusa da su ya ajiye ledojin sannan ya juya ya nufi waje yana faɗin "Kayan sawa ne a ciki, ku shirya ina zuwa". Ayla ce ta miƙe bayan fitarsa ta buɗe ledojin, kayane masu kyau da tsada, abayas ne da hijabai. Abaya ɗaya ta zara ta sanya a jikinta, ita ma Rimsha daga baya Miƙewa ta yi ta shige toilet, wanka ta yi sannan ta fito. Itama abaya ɗaya ta ɗauko ta shirya cikin shi, ba karamin kyau ya mata ba, kayan sun karɓi jikinta sosai, ga shi Abayan launin sky blue ne, abin ba'a cewa komai. Yafa mayafin abayar ta yi a kanta, sannan suka kwashe kayan da suka cire, suka zuba cikin ledar suka koma mazauninsu suka zauna. Kasa kasa Ayla ta ce "Rumsha kin san me?" Girgiza kai Rimsha ta yi alamar bata sani ba. "Wai haila na fara yi". Zaro ido Rimsha ta yi tana faɗin "Waye ya ce miki haila ce?" Kara kasa da murya Ayla ta yi, sannan ta ce "Ba kin ce mensuration shine haila ba?" Gyaɗa mata kai Rimsha ta yi alamar eh. "To matar nan da tana mini wanka, shine take gaya mini da yarabanci, da na ce mata bana jin yarabanci, sai ta faɗa mini da turanci wai mensuration na fara yi sai na fara kula da kaina sosai". Zaro ido sosai Rimsha ta yi tana tunanin dama haka haila take da bala'i zafi kamar mutun zai mutu, to ita kam gaskiya bata son hailar nan, ga shi kuma mum ta ce mata wata mace sati take yi, wata kuma kwana huɗu, kenan kullun idan jinin zai zuba sai an yi ciwo kamar a mutu, wayyo ta shiga uku. Ganin sai zazzare ido take yi yasa Ayla ta dafa ta tana faɗin "Rimsha lafiya? Me yake damun ki?" Kara zazzaro sleeping eyes nata da suka fara washewa zuwa asalin kalarsu wato farare tas ta yi, yanzu muryar ta ma ya fara komawa normal. Kasa kasa ta ce "Ayla wlh ni kam bana son hailar nan, ki taya ni da addu'a Allah yasa kada na yi, kuma na ji mum ta ce ko wace mace tana yi, wlh ni kam bana so". Ayla ta rasa me zata ce mata, dan ita dama ba wani ilimi ke gareta a kan haila ba, tana dai da ilimin Alkur'ani mai girma wadda mamanta ta koya mata, sai kuma addua'o'i da ba'a rasa ba, amma bata wani karanci littattafan musulunci ba. Rimsha zata sake yin magana, Ahmad ya shigo, bakin sa ɗauke da sallama, har suna haɗa baki wajem amsa masa, tun da ya shigo ya kasa kawar da kallonsa da ka kan Rimsha. Saman bakin gado ya zauna tare da jawo ledar da ya bawa Rimsha ta riƙe masa ɗazun a waje. Buɗe ledar ya yi ya fito da takeaway guda ɗaya sai shawarma shima ɗaya da coca colar ɗaya, da ruwan shabram. "Ku sauƙo ku ci abinci kun ji? Dama abinci naje na sayo zan ci sai Allah ya haɗa mu, to ku sauƙa ku ci ni zan sayo wani". Har suna haɗa baki wajen cewa sun koshi. (Oh ka ji yara da gulma yanzu suka gama kukan yinwa fa🤔) "A'a banyarda da kun koshiba, ku sauƙo ku ci, ina son ku saki jikin ku, ku sani Allah ne ya haɗa ni da ku, domin ni tun da nake zuwa garin nan ban taɓa fita ba tare da motata ba, ban taɓa hawa taxi ba sai yau, kuma sai yanzu na gane dalilin da ya sanya, Allah ya sa naji sha'awar fita ba tare da motata ba, dan na haɗu da kune shiyasa, kuma karin abin mamaki, wlh lungun nan da na biyo ban taɓa bi ba, kawai dai daga wajen balcony ɗaki nan ina hangen hanyar ne, shiyasa yau dana hau taxi ya sauƙe ni a bakin wancan titi sai ya biyo lungun dan na iso da wuri, kuma kunga a bakin hotel ɗin nan akwai titi, amma nace mai taxi ya sauke ni a can, to dan haka ku saki jiki ku ci abinci ku koshi sai ku gaya mini me ya kawo ku wannan gari". Ya kai karshen maganar yana tura musu abincin kusa da su. Shiru suka yi ba wanda ya iya magana a cikin su, ita Rimsha tsoro take ji kada ya yi musu wani abin, dan kullun mum ɗin ta tana gaya mata a duniyar yanzu ɗan Adam ba abin yarda bane, ita kuma Ayla ganin Rimsha ta ki ci ne yasa bata ci ba, Rimsha ta kasance kamar madubin Ayla haka suke. Sai lallaɓa su Ahmad ya ke yi, har da basu labarin abin dariya, duk dan suci abinci. Da kyar ya samu suka sauƙo kasa suka buɗe abincin, jolof rice ne da kirjin dankwaleliyar kaza, ga shi abincin ya ji kayan haɗa su green beans carrot da sauransu, sai kamshi ke tashi. Shiru suka yi saboda spoon ɗaya ne a wajen, waye zai ɗauki spoon ɗin a cikin su. Shi kuma Ahmad ya mance da cewa spoon ɗaya ne a cikin abinci, sai ce musu yake yi su ci mana, su kuma sun kasa gaya masa spoon kwara ɗaya ne, kuma suna kunyar tsunduma hannunsu a cikin abinci. Cikin zolaya ya ɗauki spoon ɗin yana faɗin "Bari to na baku a baki wata kila zaku ci" ya kai karshen maganar yana miƙawa Rimsha spoon ɗin, karɓa ta yi sannan ya mai da hannun sa cikin ledar da niyar ya ɗaukowa Ayla spoon ɗin ita ma, sai ya ji wayan, ya mance abincin mutun ɗaya ya saya. Ɗan shafa kansa ya yi yana murmushi, a hankali ya ce "Sorry bari na duba wajen masu saida abinci a hotel ɗin na karɓo muku wani spoon ɗin, dan ni duk abincin da nake sayowa jefar da takeaway ɗin nake yi idan na gama, kuma bana sayen abincin hotel ɗin nan dan ba shi da daɗi ko kaɗan". Satar kallon sa Rimsha ta yi ta kasar ido, a ranta tana faɗin "Ko akwai wanda ya tambaye shi abincin hotel ɗin da daɗi ne ko babu, sai shegen surutu". Muƙewa ya yi ya fito dan ya je ya karɓa musu spoon. Yana fita Ayla ta dumbuza shinkafar ta danna a bakinta, ta cika baki taf, dariya Rimsha ta kwanshe da shi tana faɗin "Allah yasa akwai camera a cikin ɗakin nan, idan ya dawo ya ga kalar abin da kika yi". Baki cike da abinci Ayla ta ce "Ba sai ya gani ba, hauka nake zan tsaya har sai ya kawo spoon, kin san yinwar da nake ji kuwa? Ni spoon ɗin ma sun mun kanana ne". Kara faɗaɗa murmushita ta Rimsha ta yi tana faɗin "Eye lallai Ayla yanzu na gasgata zancen Kausar da take cewa muna cinye musu abincin gida, ashe dai ke ce mai cinyewa". Yago fatar saman namar kirjin Ayla ta yi ta sunkuma a bakin ta tana faɗin "Ai da kika ce masa mun koshi da abincin nan, ji nayi kamar na shake ki dan haushi, ashe shima ɗan Albarka ne, ya yi kyan kai da ya matsa sai munci". Banda dari ba abinda Rimsha take yi, bayin Allah sun samu natsuwa yanzu kam. Jin alamar motsin shi yasa Ayla ta yi maza ta goge bakin ta da bayan hannun ta, ta sunkuyar da kanta kasa tana ɓoye fuska, bata gama tauna abincin ba ta haɗiye ji kake gwat, ita dai Rimsha ta kasa daina murmushi, dariyar ma da kyar ta tsagaita shi. Ahmad na shigowa bai san lokacin da spoon ɗin hannun sa ta suɓuce ta faɗi kasa ba, saboda bala'i kyau da ya gani, Rimsha na murmushi ga dimple na lotsawa, ga open teeth wow Masha Allah ya faɗa a ranshi. (Niko nace dan ma bakaga lokacin da take cikin jin daɗi tana tare da daddy bane, yanzu ai duk ta rame ta kara duhu saboda wuya, ba ta samun lotion masu kyau da kayan kyaran jiki, fatar ta ya fara canzawa) Sai da Rimsha ta ɗago sleeping eyes nata ta kalle shi sannan ya farga, cikin sauri ya duka ya ɗauki spoon ɗin ya kariso cikin ɗakin. Tun bai zauna ba yake faɗin "Zan iya sanin me ya sanya wannan tauraruwar gimbiyar wannan murmushi mai kayatarwa haka?". Jin haka yasa Rimsha ta yi saurin kame kanta, ta dakatar da murmushi da take yi. A ɗan ruɗe ya ce "Haba gimbiya menene abin ɓata rai kuma? To shikenan ki yi hakuri yanzu dai ku ci abinci kun ji? Ni bari na je wajen wani abokina, sai karfe huɗu idan nayi sallar la'asar zan dawo, idan na dawo sai ku faɗa mini me ya kawo ku nan, kada ku fita ko'ina fa, dan kunga nan hotel ne akwai mutane kala-kala na banza dana kirki, dan haka ku kula" yana kai karshen maganar ya miƙa wa Ayla spoon ɗin sannan ya ɗauki key ɗin motarsa ya fice daga ɗakin ya ja musu kofat ya rufe, amma bai sa key ba. Yana fita suka fara ɗura abinci, hannu baka hannu kwarya, Ayla kam tana ci tana korawa da coca colar, ita kuma Rimsha ruwar shabram dake wajen take korawa da shi. Tas suka cinye abinci har da lashe takeaway ɗin, kamar basu koshi ba, a ɓangaren nama kuwa har da kashin suka taune abinsu. Bayan sun gama a tare suka tattare wajen, sannan suka kwanta a kasa, sun ki yarda su kwanta a gadon, sai ajiyar zuciya suke sauƙewa. Yar hiran duniya suka fara yi, tun Ayla na amsawa kasa-kasa har barci ya ɗauke ta, ita kuwa Rimsha ta jima kaɗan kafin ita ma barci ɓarawo ya ɗauke ta. (Ni kuma na kwashe kayana zuwa wajen James) 💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖 Wani irin gida ne wadda da ka ganshi kasan maɓoya ne ko na yan ta'adda ko kuma na matsafa, dan gidan bana tunanin a saman kasa yake, na fi tunanin a cikin kasa yake, sannan ginin gidan an yi masa wani irin tsari wadda ya fita daban da gidan zaman mutane, ba sai na tsaya zayyana muku yadda maɓoyan yan ta'adda yake ba, kun san dai yadda suke yin abinsu. Wani katon mutumi ne ya fito daga wata ɗaki hannun sa riƙe da bokiti mai ɗauke da ruwa sanyi, gaba ɗaya jikin mutumin nan a rufe, ya sanya long coat zuwa gwiwarsa da wando dogo na jeans, launin baki, daga ta ciki riga mai godon hannu ne launin baki, kafarsa na sanye da irin takalmar waterproof ɗin nan shima baki, ya sanya hand gloves baki, fuskar sa akwai mask shima baki, a takaice dai baka iya ganin komai na daga jikinsa, ga shi kuma yana da tsawo da kuma ƙiba ba kaɗan ba. Kai tsaye wani ɗaki mai girman gaske ya shiga, ɗaki ne mai filli wadda babu komai a cikin ta, sai wani bawan Allah da suka ɗaure a saman chair a tsakiyar ɗakin, daga gefe kuma wasu mutane masu dressing irin na wannan mutumin ne ke ta faman aiki a desktop computer dake gaban su, da alama wani binciken suke yi, ɗakin akwai manya-manyan Windows na glasai a cikin shi, wadda akalla Windows nan za su kai goma, duk kuma Windows ɗin a buɗe suke. A tsakiyar ɗakin ya ajiye bukitin hannunsa sannan ya karisa wajen wayan nan mutane masu dressing irin na shi wadda baka iya ganin komai na su. Cikin harshen turanci ya ce musu "Kun samu damar kutse cikin wayar? Kun iya gane wani kungiya ne suka turo shi?" Girgiza masa kai suka yi, cikin harshen turanci suma suka ce "No sir ba mu samu komai ba, da alama wayar nan tasa komai nata a datse yake, duk yadda akayi babbar kungiya masu amfani da kimiya yake yi wa aiki, domin ba zaka iya shiga komai a cikin wayar nan tasa ba, idan ma muka matsa sai mun shiga, wayar kashe kanta da kanta take yi, idan muka sake kunnata kuma sai ta ɗauki tsawon awa tana bamu hawala kafin mu samu ta buɗu" Wani hucu wannan mutumi ya fara tare da juyawa ya koma wajen bokitin da ya ajiye, ɗaukar bokitin ya yi ya nufi wajen da suka ɗaure James, da karfi ya kwara masa ruwan cikin bukitin, daga kansa har zuwa kasansa, wani dogon numfashi James ya ja tare da sauƙewa a hankali, da kyar ya iya ɗago kansa, duk sun fasa masa fuska, sun masa dukan mutuwa, a takaice James bai san in da kansa yake ba, dan dukar da suka yi mashi ya fita hayyacinsa. Damko dark brown curly hairsa wannan mutumin ya yi yana faɗin "Zaka sanar mana waye ya turoka ka kashe mu ne ko dai sai mu mun kashe ka?" Kada ku manta da turanci suke yin maganar. Banda numfashi wahala mai sauti da James ke fitarwa ba abinda za ka ji yana ta shi a wajen, baya iya magana, bakin sa duk ciwoka, wani ciwon ma har ya fara bushewa, alamar sun kwana biyu da jimasa ciwon, wajen idanuwansa nan duk sun kunbura, da alama ma kunburin yasa baya iya buɗe idanuwansa, ba zaka taɓa cewa James bane saboda gaba ɗaya fuskarsa ta canza, har jikinsa ya kumbura ba iya fuska kawai ba. Duk kuma wannan duka da suke yi masa, James bai taɓa gigin buɗe bakinsa ya yi magana ba, in fact ko muryarsa ba su taɓa ji ba, dan yaki basu haɗin kai, ya amsa musu magana. Dun kule hannu wannan katon mutumin ya yi ya kai mashi duka a fuska daidai saitin dogon hancinsa. Wannan naushi da ya kai mashi hakan ya yi daidai da farkawar Romeo da kuma Michael daga barci. A razane Romeo ya miƙe zaune a tsakiyar bed nasa, duk da sanyin Ac dake cikin ɗakin shi zufa yake haɗawa, gaba ɗaya idanuwansa sun sauya zuwa ja sosai, alamar barci yake ji, amma bai isa ya kwanta ba, da ya kwanta zai rinƙa jin azaban zafi a jikinsa tamkar shi ake mawa azaba ba james ba, gaba ɗaya dark black curly hairsa ya watse, ya bazu masa har saman kyakkyawar fuskarsa, bin ɗakin nasa ya yi da kallo, ya rasa meke yi masa daɗi a duniyar nan, a takaice Lion ya fi James shiga tashin hankali da azabtuwa na zuciya. A wannan hali Michael ya shigo ɗakin ya same shi, dama shi Micheal barcin wahala ya yi bawan Allah, ya sha gwarel da su Tga na rufe su a ɗaki da Lion ya yi, ya kuma sha kuka, da kyar ya samu ya yi barci bayan Lion ya buɗe su kenan. Saman gadon ya hau yana hawaye ya ce "Lion please and please tell me where is James, ina ɗan uwana yake? Duk lokacin da na tuna shi ina jin zuciyata tana bugawa da karfi, zafi zuciyata take yi mini tamkar zata fashe ta fito waje, Lion zan iya mutuwa in dai James bai dawo ba, jikina na mini ciwo kamar ana dukana da wani karfe haka". Yana magana yana hawaye. Gwanin ban tausayi Dafe kai Lion ya yi dan shima kan sa sara masa yake yi, kuma duk abin da Michael ya faɗa yana ji a jikinsa, hakan shima yake ji, ya kara tabbatarwa kansa James baya lafiya, domin tun suna yara haka suke, idan ɗaya bai da lafiya a cikinsu, to tamkar dukkansu ne basu da lafiya. Sosai Michael ya kara sautin kukan nasa ganin Lion ya ki kula shi, jin kukan Michael na kara masa azaba a cikin zuciyarsa dan haka sai ya ce "Get out Michael". Zaro idanuwansa waje Michael ya yi yana mamaki, cak ya tsaya da kukan nasa, dan yasan Lion bai taɓa ce masa ya fita masa a ɗaki ba sai yau. Sanin halin Lion baya magana biyu, yasa ya sauƙo daga gadon tare da cigaba da hawayen da yake yi ya fice daga ɗakin, shi kan shi Lion ji yake kamar ya yi hawayen ko zai samu sauƙin abinda yake ji a ransa, shi zafin ma ya masa yawa, ga daddy a gefe, ga Michael sannan ga bala'i da suke ciki na rashin sanin ina James yake, abubuwan sun taru masa, amma idan ka gan shi bazaka taɓa gane hakan ba, dan shi already dama a hakan yake, fuska a ɗaure kullun, ba'a gane murna bare bakin cikinsa. A hankali ya mai da bayansa ya jingina da gikin kayin gadon yana tunanin menene A.E.A ke nufi, idan ya gane su zai iya gane in da James yake, sannan yana bukatar kutse cikin tsaron da a ka sanyawa wayar James, me yasa wayar ta kasance haka, wannan ma abin tambaya ce. Ba wanda ya isa ya yi kutse cikin wayar James har ya yi bincike sai wanda ya kasan ce makura wajen basira da sanin kimiya na hanyar sadarwa. Haka shima wayar Lion take, ba zaka iya bin diddgin wayar ba, haka ba zaka iya datsar layin sa ba, sai dai wayar James, an ɓoye layin ne a karkashin wata tsaro na musamman, kuma a wannan tafiya da ya yi ne hakan ta faru. Maganar gaskiya kuma mutanen da suka kama shi ne suka ɓoye layin nasa a karkashin tsaro domin kada a bibiyi in da suke, saboda basa son kashe wayar suna son yin bincike a kanta, kuma sun san idan basu kasheta ba za'a iya bin diddigin su har a kama su, wannan dalilin yasa suka saka mata matakan tsaro ta yadda ba za a iya bin diddigin su ba Ya jima a haka sannan ya jawo system nasa ya fara bincike a kan menene A.E.A a cewar sa idan ya gano ma'anar su sai ya fara kutse cikin wayar James dan sanin a wani location ɗaya yake. (Toh fa aiki ya ganku, sai mun haɗu da ku a gidan Abbo gobe idan mai dukka ya kai mu) 💞💞TRIPLET'S💞💞 E31-32 Ya jima a haka sannan ya jawo system nasa ya fara bincike a kan menene A.E.A a cewar sa idan ya gano ma'anar su sai ya fara kutse cikin wayar James dan sanin a wani location ɗaya yake. A ɓangaren Michael kuwa, yana fita part nasa ya koma. Yana shiga ya isko Musharraf yana Sallah saman Chinese carpet dake gaban katafaren bed nasa, saman gado ya haye ya ɗan kishingiɗa yana hawaye yana kallon yadda Musharraf ke sallah. Allah sarki Michael saboda son da yake yi wa Musharraf ya sa ya ce Musharraf ya baro word room ya dawo part nasa su zauna tare, kuma duk hakan ya samo asaline saboda son da James yake yi wa Musharraf ɗin. Sai hawaye yake yi har Musharraf ya idar da sallah, hannu sama ya ɗaga ya jima yana addu'a sai kallonsa Michael ke yi, har ya dai na zubar da hawayen da yake yi ba tare da ya sani ba, ganin Musharraf na ibada yana sanya shi samun nitsuwa da kuma farinciki. Bayan ya kammala addu'ar ne, ya miƙe ta hawo saman gadon yana faɗin "Michael what is wrong with you? Why are you crying?" Ya kai karshen maganar yana zama kusa da Michael ɗin, amma kafin ya hau gadon sai da ya yi bismillahi. Shiru Michael ya ɗan yi mashi kafin ya ce "Uncle ɗin James me yasa idan zaka zauna kake yawan faɗin wannan kalmar da ka faɗa yanzu". Murmushi Musharraf ya yi yana faɗin "Wai bismillahi kake nufi?" Gyaɗa masa kai ya yi alamar e. Shafa kansa Musharraf ɗin ya fara yi yana faɗin "Ina koran sheɗan ne" miƙe wa daga kishingiɗar da ya yi ya yi, ya zubawa Musharraf brown eyes ɗin nan nasa, na ɗan lokacin kafin ya ce "Waye shi shaiɗan ɗin?" "Sheɗan makiyi ne ga duk wani ɗan adam, baya son mutane, ya kuma yi alkawarin sai ya kai mutane dayawa wuta, sai wanda Allah ya tsarene kawai ba zai je wuta ba" Musharraf ya ba shi amsa. Shiru ya yi yana maimaita kalmar wuta, Allah, sheɗan da kuma makiyi. Ganin ya yi shiru ne yasa Musharraf ya ce "Kai ma idan zaka zauna karinƙa faɗin bismillahi, dan ka kori shaiɗan daga kusa da kai, kuma ba iya shaiɗan kawai bismillahi ke kora ba, yana sanya Mala'ikun su kasance kusa da kai, sannan kuma idan aka maka wani sharri a wajen, Allah zai kareka ta sanadiyar wannan bismillar da ka yi". Cikin sauri ya ce "To zan rinƙa yi". Wani daɗi Musharraf ya ji ya ziyarce shi lokaci guda. "Baka faɗa mini me ya same ka kake kuka ba?" Tambayar Musharraf ta fama masa ciwon dake damun shi, nan take ya fara hawaye, "Subhanallah a'a Michael idan har baka son faɗa mini abin da ke damun kane ne ba sai ka sake yin kuka ba ka ji? Ka yi shiru ni na fasa ji ma" kwantar da kansa saman cinyar Musharraf ɗin ya yi, cikin kuka ya fara gaya masa halin da yake ci dan gane da James. Sosai shima Musharraf ya ji wani irin kuna a zuciyarsa domin har ga Allah yana matuƙar kaunar James, cigaba da shafa kan Micheal ɗin ya yi yana karanto addua'o'i yana tofa masa, shiru Michael ya yi yana jin zuciyarsa tana masa sanyi, har cikin ransa yake jin sauƙi. Dama kuma tun da Musharraf ya dawo part nasa yau kwana biyu kenan, kullun sai ya karanto masa addu'a ya tofa ya shafa masa a jikinsa, haka idan ya yi barci sai ya masa addu'ar barci kafin nan ya bar ɗakin zuwa ɗayar ɗakin na kusa dana Michael ɗin, da yake bedroom uku ne a part ɗin, shiyasa Musharraf ke kwana a daya, amma fa barci ne kawai ke raba shi da Michael, domin kuwa ko da rana a ɗakin Michael yake zama, saboda yana son jan shi a jiki sosai. Ya jima yana tofa masa addu'a kafin nan ya ce "In Sha Allah zan yi wa James azumi gobe, da izinin Allah zai dawo cikin koshin lafiya, kuma yau ma ba zan yi barci ba zan kwana ina yin Sallah ina rokan masa Allah daya tsaresa a duk in da yake". Allah sarki Michael ya samu nitsuwa sanadiyyar addua'o'i da yake samu daga wajen shi, a nitse ya ce "Uncle ɗin James idan kayi azumin James zai dawo?" Gyaɗa masa kai Musharraf ya yi yana faɗin "Da izinin Allah zai dawo lafiya". Juyo da kallonsa kan fuskar Musharraf ɗin ya yi kafin ya ce "Uncle ɗin James ni ma zan yi azumin domin muyi dayawa don James ya dawo da wuri" kara faɗaɗa murmushinsa ya yi yana faɗin "To shikenan bari na gaya maka yadda ake yi, idan muka ci abinci da asuba ba zamu sake ci ba har sai rana ta faɗi..." Bai kai karshen maganar ba Michael ya katse shi da cewa "I already knew it through James friend, yana da wani aboki musulmi, a school ɗaya muke amma shi kamar ɗan Dubai ne ko Saudia ne na manta, kuma ai pastor a church ma ya gaya mana yadda akeyin azumi, so kaga na san yadda ake yi, kullun wannan friend ɗin James ɗin yana yin azumin Monday and Thursday". "Tom shikenan My Michael Allah ya kai mu da asuba sai mu yi sahur ko?". Gyara kwanciyarsa ya yi yana faɗin "Tom me zaka ci da asuba ɗin sai na gayawa masu dafa abinci dan su tashi a kan time su dafa maka da wuri". Cikin sauri ya ce "A'a ni ruwan tea ma is okey for me, sai dai idan kai ne zaka ci wani abin" girgiza kai ya yi ala'mar shima baya son komai. Shiru suka ɗan yi Musharraf sai tofa masa addu'ar Allah ya bashi lafiyar ƙwaƙwalwarsa yake yi, "Uncle ɗin James do you know what?" Lokacin Musharraf yana karanta addu'a bai kai karshe ba, hakan yasa ya girgiza masa kai kawai alamar a'a. "Sometimes if am with you I feel like am with james". Hannu Musharraf ya sanya yana ɗan jan dogon hancinsa a hankali ba tare da ya yi magana ba, har sai da ya kai karshen addu'ar da yake karantowa a zuciyarsa, ya tofa masa sannan ya ce "Saboda ina son James ɗin sosai ne shiyasa wani lokaci nake maka kamar shine, kuma kaga James ya kasance tare da ni sosai mun saba shiyasa" "Yes Uncle, idan na ganka sai in ji kamar James nake kallo, saboda mafiyawancin kuna tare lokacin da yake nan". Cike da tsoron abin da zai biyo baya, dan ya san wani lokaci Michael birkitacce ne, ya ce "Michael why are you not calling your mum on phone?" Abin mamakin da bai taɓa tunani ba, ya yi tunani Michael zai ɗauki zafi sosai, dan James ya gaya masa kada ya kuskura ya yi maganar mum ɗin su ga kowa a cikin gidan idan ba haka ba, to zasu kashe shi, amma ya ga akasin haka, dan kuwa Michael ce masa ya yi "Because i don't have her phone number that is why I'm not calling her". Zaro ido Musharraf ya yi dan bai yi tsammanin haka ba. Kenan ƙwaƙwalwar Michael na baya ne bata son mum ko yaya? Kada ku manta yanzu ya fara sakun sauƙi yana kuma iya rabe daidai da ba daidai ba. "To ka karɓi number nata mana, sai ka kirata ku gaisa zata ji daɗi sosai" ya yi maganar yana tsare shi da ido, turo ɗan bakin ya yi kafin a shagwaɓe ya ce "To kana da number ne ka bani?" Girgiza kai ya yi alamar a'a bashi da shi. idan banda Michael da meman magana ta ina Musharraf zai samu number mum ɗin su, shi da yake bako. "In je in tambayi Lion number?" Cikin sauri Musharraf ya ce "A'a kada ka masa maganar". Musharraf ya san cewa idan Michael ya yi wa Romeo wannan magana to za'a samu matsala, domin kuwa yasan Lion sai ya tambayi shi waye ya masa zancen mum, shi kuma Michael baya ɓoye abu, bai iya karya ba, sai dai idan saka masa magana a baki kayi, amma da kan shi kam baya karya, idan kuma ya faɗa cewa ga wanda ya yi masa zancen mum tofa yasan dole Lion ya hukunta shi, dan ya lura tabbas Lion bayason mum ɗin su, da gaske yake yi, shi ma James baya son ta, amma yana kokarin dannewa ne kawai ya kula ta, shi kuma Michael ƙwaƙwalwarsa ta baya ce bata son ta, na yanzu kuma babu tsanar kowa a cikinta, sai zallar soyayyar wayenda suke tare da shi, kowa na gidan Michael na son shi, har da daddy yake nunawa soyayyar da bai taɓa tunanin zai samu irin shi daga ɗaya daga cikin triplets nasa ba, amma sai ga shi Micheal yana nuna masa, hakan kuma ya faru ne yan kwana biyu da suka wuce, saboda addua'o'i da Musharraf ke yawan tofawa ƙwaƙwalwar tasa, hakan yasa Michael ya canza sosai da sosai, sai dai har yanzu ragwanta da shagwaɓa yana nan bai tafi ba. Haka suka yi ta hira Musharraf na shafa lallausan brown hair ɗin Michael ɗin, har barci ya ɗauki ke shi kwance ya tada kai da cinyar Musharraf, ganin ya yi barci yasa ya cigaba da tofa masa addua'o'i yana mai jin kaunar Michael James har Lion da ya dake shi, duk yana jin kaunar su a ransa, domin a cewar sa dukkan su sun yi mashi rana, kuma duk cikin su Lion ma ya fi yi mashi rana, domin idan bai taimaka ya bashi gurbin zama a gidan ba, su James ba su isa su zaunar da shi ba, bai isa ya zauna har ya saba da su ba, kai idan Lion baya son shi ma, ko duba jikinsa James ba zai yi ba, domin kuwa da tun farkon zuwan shi Lion zai ce ayi waje da shi, kuma ya zama dole a fitar da shi, ko da James baya so, ya zamar masa dole ya bi abinda Lion yake so. Musharraf ya jima a haka yana ta faman karantawa Michael Addu'a har shima barci ya ɗauke shi yana daga zaune, ya jingina jikinsa, da jikin bangon kayin gadon. Duk wannan hirar da suka yi, basu san da camera a ɗakin ba, domin Lion ya sakawa duk wani dake gidan ido, dan yaga me suke yi, tun bayan abin da ya faru da James, sai dai ba kasafai yake samun time na duba cameras ɗin ba, sai irin tsakiyar dare bayan ya kammala aikin da yake yi, sai ya ɗan bincika ya ga me suka aikata yau, amma fa wani lokaci ya kan yi kwana biyu bai bincika ba, saboda yanzu ba sai an gaya muku ba, kun sa abubuwa sun masa yawa. (To bari mu koma Nigeria dan jin wani hali suke ciki) 💖💖GIDAN ABBO💖 Zaune Jelly take a tsakiyar palon Ummi, ta baza kayan cimanta a gaba, ciki harda nama, wato soyayyen kaza, ya ji kayan kamshi da kayan haɗi, sai tashin kamshi yake yi, kun san dai jelly akwai amana tsakaninta da kaza tom. Sai faman yagar cinyar kazar nan take yi, ga su hollandia da Yoghurt a gefenta, Ummi ta kira mai kunshi ta tsara mata kunshi sosai da sosai, ya fito zane mai kyau, ya yi maroon color, sai ɗaukan ido yake yi, idan ba ku mance ba Jelly farace tas, hakan yasa jan kunshin ya yi mata bala'i kyau, sannan kuma an zana mata baki a saman kafarta, ta samar jan kunshin, haka su ma hannayen ta an zana bakin kunshi, zannen manya-manyan flowers masu kyau, abin ba'a cewa komai, Jelly ta yi kyau sosai. Sanye take da doguwar riga na kanti, daga samar rigar ya kamata, daga daidai kugunta zuwa kasa kuma ya yi wani bala'i buɗe wa sosai kamar umbrella, Ummi ta wanke mata gashin kannan nata, ta busar mata da hand dryer, sannan ta ɗaure mata shi a tsakiyar kanta, bayan ta shafe mata shi da mayuka masu kyau da kanshi da tsada, sai kyalli gashin nata yake yi. Haka zalika Ummi da kanta ta yi mata simple make up a fuskar ta, yau dai Jelly ta fito a asalin Jellyn daddynta, tayi kyau sosai. Tun daga bakin kofar palon ya tsaya ya zuba mata ido yana kallonta, ya kasa ɗauke idanuwansa daga kanta, kuma ya kasa karisowa cikin palon, sai famar yagar nama take yi abinta, bata ma san da wani na kallonta ba. Ya jima tsaye a wajen yana kallon duk abin da take yi, wani lokaci idan namar ya yi mata tauri ta kasa gutsira, sai ta turo ɗan bakin nan tana kunkuni ita kaɗai, abin ba karamin burgeshi yake yi ba. Ya shagala da kallon ta kamar a mafarki ya ji an ce "Nawid lafiya kake yi wa baby irin wannan kallo haka?" Yar firgita ya yi ya maido da kallonsa kan Ummi dake tsaye hannunta riƙe da robar ice cream, kwata-kwata bai ma ga shigowar ta ba, ya shagala da kallon Jelly. Ɗan sunkuyar da kansa kasa ya yi yana ɗan murmushi yana sosa kai. Sosai Ummi ta ji daɗi, dan a nata ganin Nawid ya fara son baby. Karisowa cikin palon ya yi, sai wani yan kame-kame yake yi, kawar da kallon ta daga kansa Ummi ta yi tana faɗin "Baby ga Ice cream ɗin" Cikin sauri ya ce "Haba Ummi ashe kace kike goyawa baby baya tana wannan ciye ciyen da take yi". Hararar wasa ta wurga masa sannan ta ce "Ina ruwan ka to? Cikin ka ta ke kaiwa ne?" Girgiza kai ya yi yana faɗin "A'a My Ummu, uwa ta gari, ni ba ruwana ta ci iya cinta, idan ma bai isheta ba, ni sai na karo mata wasu cimar". Nauyayyar ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tana godiya ga Allah da ya sa Nawid ya fara sauƙowa a kan lamarin baby. Duk wannan abin da ke faruwa Jelly bata san komai ba, ita dai tana duniyar nama, kwata-kwata bata jin me suke faɗe, in fact bata ma san da su a palon ba. (Tashin hankali a lallai Jelly kin shahara, wai🤔) Sai miƙa mata ice cream ɗin Ummi ke yi tana magana, amma ina Jelly bata ma san da tsayuwar ta a wajen ba. Nawid ne yazo ya karɓi Ice cream ɗin yana faɗin "Ke dai Ummi bani nan, bari na zauna na jirata, wata kila idan ta kammala cin namar ta karɓa Ice cream ɗin". Ba musu Ummi ta miƙa masa robar sannan ta wuce cikin bedroom nata. Zama ya yi kusa da ita yana kallon asalin kyau babu miss, sai tashin kamshin take yi abinta. Yana zaune ya zuba mata ido har ta gama cin namar tas, sannan ta ɗago kai tana kallon shi. "Yaya Nawid kai ma ka zama ɗan iska ne?" Zaro ido ya yi da mamaki yake kallon ta, ɗan iska kuma, ya maimai ta kalmar a zuciyarsa. Ganin ya mata shiru yasa ta sanya hannunta zata karɓi Ice cream ɗinta dake hannunsa, wani irin shock ya ji lokacin da hannunta ya taɓa shi, lokacin guda ya ji wani irin yana yi mai wuyar misaltuwa a gare shi, zuba mata ido ya yi ya kasa ɗauke wa, yadda take shan Ice ɗin kawai yake kallo, yadda lips nata ke motsawa ba karamin jefashi cikin yanayi take yi ba. "Yaya Nawid baka amsa mini ba? Kai ma ka zama ɗan iska ne?" Da kyar ya iya saita nitsuwarsa murya kasa kasa, cike da annashuwa ya ce "Baby me nayi kuma na zama ɗan iska?". "Kana kallon mata mana, ai san duk mai kallon mata ɗan iska bane? Shiyasa ranar ai nacewa wannan Abbon kwarto". Zaro idanuwansa waje ya yi, a ɗan razane ya ce "Me Abbo kuma ya yi da kika ce masa kwarto". Nan fa ta shiga bashi labarin abin da ya haɗa ta da Abbo ranar, tana yi tana shan Ice cream ɗinta, yana sanyaya mata zuciya, har wani lumshe ido take yi abinta, daga karshen ta rufe masa da cewa "Dana gayawa Ummi Abbo ya yi mini kwartanci sai ta ce wai na dai na ce masa kwarto babana nane, kuma ni na gani a Tv duk mai taɓa mata kwarto ne, mai kallon mata kuma ɗan iska". Mutuwar zaune Nawid ya yi ya kasa tantance a wani matsayi zai ajiye Abbo, wannan wace irinyar lalacewa ne, ace yarinya kusan jijarka tana ce maka kwarto, kuma duk kai kaja, kawai ka samu yarinya ka fara shafa mata wuya, wa iya zubillah. Ya jima shiru kafin ya ce "Baby kada ki sake ce masa kwarto kin ji ko?" Gyaɗa masa kai ta yi alamar e. "Yauwa My baby, baban ki ne kamar yadda Ummi ta gaya miƙi" shiru ta masa sai shan Ice cream nata take yi, dan ita in dai tana cin abinda ranta ke so, to idan ba ya zama dole ba, bata magana. Shiru suka zauna har ta kammala shan Ice cream ɗin duka, sannan ya ce "Baby gyara na yi miki hoto kin ji ko? Ƙunshin nan ya miki kyau sosai zan miki hoto na ajiye tarihi" to ta amsa masa da shi, sannan ta gyara zama ya fara ɗaukar ta hoto. A wannan hali Abbo ya shigo ya same su, cikin fushi ya ce "Kai Nawid me kuma ya haɗa ka da baby haka? Me ya zaunar da kai kusa da ita" miƙewa tsaye Nawid ya yi yana mamakin karfin hali irin na Abbonsa, kuma dama ya san haka zata iya faruwa, tabbas yana jin wani abu a zuciyarsa game da baby, amma bai ɗauka soyayya bace, ya fara kula tane dama dan ya nisanta Abbonsa da ita, tun da ya yi kokarin fargar da Umminsa amma taki ganewa, shiyasa ya biyo ta wannan hanya domin ya nuna yana son baby ko Abbo'nsa zan ji kunya ya daina wani tunani a kanta, idan ma yana yi, amma shi zance na gaskiya Jehan yake so ba baby ba. Tsawa Abbo ya sake daka masa "Ba da kai nake magana bane Nawid?" Sunkuyar da kai kasa Nawid ya yi yana ɗan sosai kai, kasa kasa cikin girmamawa ya ce "Abbo ka manta Ummi ta ce ita zan aura ne?". A fusace Abbo ya ce "A'a ai na gaya maka ba zaka auri tsintaciyar mage ba, mai asali zaka nemo mana, bamu son mara asali a cikin zuriar mu". (Toh fa, lallai Abbo) Ɗago kai Nawid ya yi yana kallon Abbonsa, mamaki karara ya bayyana a kan fuskarsa, tunani ya fara yi anya Abbo nan shine babansa kuwa. Muryan Jelly ne ya katse masa tunanin sa da cewa "Yaya Nawid ka gama hoton ne in tafi ɗaki?" Kakalo murmushi ya yi tare da sakin fuskarsa sosai, ya miƙa mata hannusa yana faɗi "Riƙe hannuna muyi selfie" yana magana yana satar kallon Abbo. Cikin sauri Jelly ta riƙe hannunsa, matso da ita jikinsa kaɗan ya yi tare da ɗaga wayarsa sama yana faɗin "Oya yi murmushi....." Bai gama rufe baki ba Abbo ya daga musu tsawa "Ke baby wuce ki tafi ɗaki, kai kuma Nawid daga yau idan ka sake bari na ganka da rana a gidan nan sai ranka ya ɓaci!!!" Turo baki Jelly ta yi a shagwaɓe ta ce "Ni dai ba zan tafi ko ina ba har sai yaya Nawid ya gama yi miki hoton da ya ce". Sanin halin Jelly da kafiya ya sa Nawid ya bi umarnin Abbo ya sa kai ya wuce, dan yasan Jelly ce kawai maganinsa. Ai kuwa bai kai tsakiyar palon ba Jelly ta zube kasa tana mirgina kafafu a kasa tana ihu kamar ba lafiya ba. Da yar gudu Ummi ta fito daga cikin bedroom nata, shi kuma Nawid cak ya tsaya a cikin zuciyarsa yana faɗin "Ai beby dolle ma na rinƙa kulaki dan kece kawai maganin Abbo" Ganin Ummi ta fito yasa Abbo yasa kai ya wuce ya nufi nashi bedroom ɗin. "Nawid lafiya me kayi wa baby?" Cikin sauri ya ce "A'a Ummi ni ba ruwana ita da Abbo ne fa, shi ya hana na ɗauke ta hoto shine take ihu". Girgiza kai Ummi ta yi tana faɗin "A kan me to zai hana a ɗauke ta hoto kuma?" Buɗe hannaye Nawid ya yi yana faɗin "Ni ma dai ban sani ba, amma ki tambaye shi" wucewa ta yi ta bi bayan Abbo ba tare da ta sake yin magana ba. Tana tafiya Nawid ya dawo kusa da Jelly da sauri, a zuciyarsa yana tunanin ta yadda zai ja ta a jikinsa sosai har su saba, su zama kamar masoyan gaske, dan Abbo ya goge duk wani kudiri dake ransa a kanta. "Ki yi shiru kinji babyn yaya Nawid? Yanzu ta shi mu yi hoton, kuma anjima da daddare zaki rakani shopping, daga nan sai muje gidan kallo mu kalli film" wani ihun murna ta saki, dan Jelly ba baya ba wajen kallon film, akwai ta da son kallon bala'i, tun ma tana da lafiyar ta haka take. Nan take ta fara murmushi kamar ba ita ce mai kuka yanzun nan ba. Sai dariya take yi Nawid ya ɗauke su hoto kala-kala sannan ya wuce ɗakin sa yana sake waigowa ya kalleta, ita ma sai kallon shi take yi, yau yaya Nawid ya yi abin kai a cewar ta. Har ya shige part nasa kallon shi take yi, shima kuma har ya shige juyowa yake yi yana sake kallon ta, yadda kasan masoya na bankwana da junansu. Sai da ya kurewa ganin ta sannan ta wuce ɗakin ta ita ma, ba tare da ta tattare kayan cimar da ta ci ba, a nan ta barsu watse. Tana shiga bedroom nata ta haye gado ta kwanta ta yi shiru kamar mai tunani. A ɓangaren Ummi kuwa, tana shiga bedroom na Abbo ta same shi yana kokarin rage kayan jikinsa zai shiga wanka. "Abbon Nawid a kan me zaka hana Nawid ya yi wa baby hoto?" Shiru ya ɗan yi yana tunanin ta yadda zai kubce mata. Tsawon minti ɗaya sannan ya ce "Saboda idan ya ɗauke ta hoto zai iya ɗaurawa a media har yan uwanta su gani su zo su rabamu da ita". Yar murmushi Ummi ta yi, da da farko ta shigo ranta a matukar ɓace har zuciyar ta fara raya mata anya zancen Nawid da ya gaya mata a kan Abbo na da wata manufa a kan Babby anya ba gaskiya bace kuwa, amma yanzu jin abin da ya ce yasa ta yi watsi da wannan tunani da ta fara yi ta saki fuska tare da karisawa kusa da shi tana faɗin "Gaskiya ne kuma, to shikenan yanzu bari na koma bedroom na, dan ina shiryawa baby pants ɗin ta, da sauran kananan kayan ta ne a cikin drawer kayana" "Me ya mai da kayan baby kuma bedroom naki?" Ya yi maganar yana nufa hanyar toilet. Nufa hanyar fita ta yi ita ma tana faɗin "A'a ba na sawan ta bane, sabbin dana saya mata jiya ne, wayan da take amfani da su already suna ɗakinta" ta kai karshen maganar tare da ficewa daga ɗakin, shi kuma ya shiga cikin toilet ransa fes ya yi Ummi wayo. (Nima raina fes na kwashe kayana zuwa wajen su Rimsha) 💖RIMSHA💖 Sai misalin karfe uku na yamma suka farka daga barcin nishaɗi da ya kwashe su, Rimsha ce ta fara farkawa, sannan ta tashi Ayla. A gurguje suka yi alwala suka fito, kowace ta ɗauki hijabi guda daga cikin hijaban da Ahmad ya kawo musu, can saman kyakkyawar trolley ɗin sa suka hango daddumar. Rimsha ce ta ɗauko musu, suka shimfiɗa suka gabatar da sallar azahar, sannan suka zauna saman daddumar. Sai bayan sun zauna ne, Rimsha take cewa, "Ayla na manta mai haila fa bata Sallah, kuma bata azumi sai bayan ta gaba" zaro ido Ayla ta yi, cike da mamaki ta ce "Dama Akwai lokacin da musulmi ba zai yi sallah bane?" E Rimsha ta bata amsa sannan ta shiga yi mata bayani yadda mai haila ya kamata ta kasan ce, sosai Ayla ta gamsu, ta kuma cire hijabin, ta mai da cikin leda tare da komawa saman bedside drawer ta zauna. Ita kuwa Rimsha tana zaune a wajen tana askar har a ka kira sallar la'asar, mikewa ta yi ta gabatar da sallah sannan ta koma ta zauna tana karatun Alkur'ani mai girma a fili, kasan cewar tana da hadda a kai sai bata nemi Alkur'ani mai girma ba ta fara karatu da kai kawai. Sai misalin karfe 4:30 Ahmad ya dawo, bawan Allah hannunsa ɗauke da niki nikin leda mai ɗauke da kayan fruits a ciki. Sannu da dawowa suka yi masa, sannan suka ɗaga masa gaisuwa, da fara'a ya amsa Ayla ta miƙe ta shiga bayi. Su Ayla manya ba'a saba ba, duk lokacin da jinin ya ɓata always ɗin ko kaɗan ne sai ta canza, sai jibga always ɗin take yi cikin shadda tana korawa da ruwa, mani ma kaɗan ya ɓaci amma haka zata cire, daga tashin su barci zuwa yanzu always huɗu ya canza. (Tab babbar magana) Yanzu ma canza always ta yi ta dawo ɗakin, zaune ta isko Ahmad da Rimsha, ita Rimsha ta tashi daga kan dadduma ta koma saman drawer, shi kuma yana zaune bakin gado. Kusa da Rimsha Ayla tazo zata zauna, cikin sauri ya ce "A'a sister zo ki zauna a nan kin ji? Drawer ya yi muku kaɗan ai, ku dai na takure kanku, ku saki jiki, ni yayan kune" ya kai karshen maganar yana nuna mata gefen gadon a kan tazo ta zauna. Girgiza kai ta yi tana faɗin "A'a yaya wajen bai yi kaɗan ba, ai bamu da ƙiba, zai ishe mu" cikin sauri ya kara waro idon sa yana kallon ta, a fili ya furta "Allah mai halitta, ya sunan ki?" "Sunana Ayla" ta bashi amsa tana kokarin zama. Miƙewa tsaye ya yi dan ya lura in dai har zai zauna a bakin gadon tofa su ba zasu taɓa yarda su zauna ba, yara kanana da kamun kai sosai haka, ya faɗa a ransa yana nufar wajen da Rimsha ta mayar da daddumar sa ta ajiye. Ɗaukowa ya yi ya shinfiɗa ɗan nesa da su ya zauna yana faɗin "To ku koma bakin gadon ku zauna dan ku daina takura kan ku". Saboda ganin girmansa basa son yi masa musu yasa Ayla ta zauna a bakin gadon, ita kam Rismha ta makale drawer nan gam taki sakinsa. "Ayla kin san me?" Ahmad ya tambaya yana ciro wayarsa daga aljihun wandon sa. Girgiza masa kai ta yi tana faɗin "a'a ban sani ba" "Wlh Ayla muryar ki sak na daddyn mu, bayan haka kina kama da shi sosai, abin ya bani mamaki" yar murmushi ta yi tama rasa me zata ce masa, dan ita ba wani iya magana da namiji ta yi ba, tun da ma ta taso bata taɓa zama da wani namiji kamar yadda suka zauna yanzu suna hira ba, sai baba na Daular Mutuwa da kuma duna, suma ba keɓewa haka suke yi ba, kuma hirar su bata wuce na cikin Daular Mutuwar ɗin. Ganin ta yi shiru ne yasa ya ce "Ina son ku bani labarin me ya kawo ku garin nan, dan in san ta ina zan taimaka muku". Ayla ce ta fara bashi labarinta tun ranar da aka sace ta zuwa yau, sosai idon Ahmad ya cika da kwalla, duk dakiya irin na ɗa namiji sai da zuciyar Ahmad ta zubar wa da Ayla hawaye. "Allah sarki yanzu mama da baba suna can suna haukar neman ki" Ahmad ya faɗa yana kokarin ɓoye hawayen dake ƙoƙarin zubo masa. Allah sarki bai ma san Ayla kam bata da baban ba, maman nata ma bata da tabbacin tana raye ko ta mutu, Ayla bata ba shi labarin asalin taba, abin da yasa bata yi hakan ba kuma, saboda Rimsha ta mata faɗa ranar da ta gayawa su Iya asalin wace ce ita, Rimsha ta mata faɗa sosai a kan ta koyi ɓoye sirrinta, ba kowa bane daga haɗu zata gaya mishi ita wace ce, dan ba kowa ne zai riƙe ka tsakani da Allah ba, shiyasa yanzu bata gayawa Ahmad asalin tarihinta ba, ta dai ce masa aikan ta mamanta ta yi, ta fito kenan yan Daular Mutuwa suka sace ta. Sun ɗan jima suna jimamin labarin da Ayla ta bada, kafin nan Ahmad ya ɗago ya kalli Rimsha "Ke kuma fa Queen of beauty? Ya akayi kika bar gida?" Haka ita ma ta datsi labarinta daga wajen da taje sayo ashana aka sace ta, daga nan ta bashi story har zuwa yau, bata ɓoye masa abin da ya sanya suka baro gidan su kausar ba, ta gaya mishi komai, dan tasan idan bata gaya mishi ba ma, zai tambayi me yasa suka baro gidan su Kausar ɗin, shiyasa ta gaya mishin kawai. Sosai ya tausaya musu, kuma ya ji kunan rai sosai, na fyaɗe da Jami'u ya yi yunkurin yiwa Rimsha, abin ya ɓata masa rai sosai. Shiru suka ɗan yi na ɗan lokaci sannan Ahmad ya ce "Ni ma ba ɗan nan bane, a Abuja iyaye na suke, karatu na ke yi a nan, ko in ce na kammala akwai abin da nazo gyarawa a nan ne, zan ɗauki sawon sati biyu kafin na kowa Abuja, amma ku ba zan ajiye ku a nan har tsawon wannan lokacin ba, gara ku koma gida dan nasan iyayen ku suna tsaka mai wuya, to gara ku koma ko zasu samu kwanciyar hankali, nima dai dole ce ta kawo ni nan, domin ba a nan kasar ma na yi karatu na ba, kawai wani course ne ya burgeni shine na nema, da farko Ahmadu Bello university na zaɓa daga baya na fasa na ce bari na zo University of Ilorin, ashe rabon na taimakawa rayuwar ku ne, ina matikar farinciki da hakan, yanzu ku gaya min yaushe kuke son komawa gida? Kuma da me kuke son komawa jirgi ko mota?". Bayin Allah har suna haɗa baki wajen cewa "Yau muke son komawa, kuma ko da me aka mai damu mun gode". Murmushi ya yi yana kallon yadda Rimsha ta yi maganar cike da zumuɗi har kamar zata tashi daga mazauninta dan murna. "Queen of beauty ai yanzu yamma ta yi, sai dai zuwa gobe da safe, zan yi waya da daddyna ya nema muku alfarma ku samu jirgin safe". Kamar abin haɗin baki, a tare suka zamo kasa daga mazaunin su, suka zube gwiwowinsu a kasa, suna hawaye suka fara zuba masa godiya. Fuskarsa ɗauke da murmushin tsantsan farinciki ya ce "Ya isa haka kukan, ina jin ku tamkar yan uwana ne ku, musamman Ayla yadda ta yi kama da daddyna ji nake yi kamar kanwata Anisa, ba dan na san cewa Anisa na wajen mum ɗin ta ba wlh da na riƙe Ayla nace Anisa ce, dan sun yi kama sosai, ita ma Anisa da daddy take kama, bari ma ku ga hotonta, amma dai Anisa zata fiki shekaru dan yanzu haka tana 200 level a school, kin ga kuwa zata girme miƙi" ya kai karshen maganar tare da fito da hoton Anisa a wayar hannunsa, sannan ya miƙa musu wayar. Karɓar wayar suka yi suna kallon matashiyar budurwa dake jikin hoton, tabbas kamaninta ɗaya da Ayla, ba abin da ya raba su, sai dai ita cikakkiyar budurwa ce ba yarinya kamar Ayla ba ce, zata iya kai 21 years. Rimsha ce ta ɗago kai tana faɗin "Allah ta yi kama da Ayla sosai" "Ni kuma fa Queen of beauty? ban yi kama da ita ba ne" ya yi maganar yana tsare ta da ido. Kawar da kallonta daga kanshi ta yi tare da sunkuyar da kai kasa ta ce "Gaskiya muryan kane ya yi iri ɗaya dana Ayla, amma baku kama Sosai, ta fi kama da Aunty Anisa" murmushi ya yi, a zuciyarsa yana faɗin "tabbas Rimsha ta yi gaskiya shi kan shi lokacin da ya fara jin muryar Ayla da tasa muryar ta masa kama, sai daga baya daya saurara sosai sai ya ji tafi kama dana daddynsu. Miƙa masa wayarsa Ayla ta yi, karɓa ya yi ya ajiye a gefensa yana faɗin "To yanzu idan kuka koma gida, idan na dawo Abuja ina son ganin ku a ina kenan zan ganku?" Cikin sauri Rimsha ta ce masa "Ni ai Katsina nake ba Abuja ba, ita kuma Ayla Kaduna take" Zaro ido ya yi kafin ya ce "Kai to kenan ku da kanku ma idan kuka rabu baku da tabbacin zaku sake haɗu ko ba zaku sake haɗuwa ba, tun da baku san in da gidan juna yake ba, kuma bama gari ɗaya kuke ba". Jin wannan magana tasa ta sanya gaba ɗayan su idanuwansu suka cika da ruwan hawaye, jikinsu ya yi muguwar sanyi, ɗagowa Rimsha ta yi tana kallon Ayla, a yayin da ita ma Ayla kallonta take yi, abin gwanin ban tausayi, kenan yanzu idan suka bar nan sun rabu kenan? A tare suka gefawa kansu wannan tambayar. Ganin haka yasa Ahmad ya yi murmushi sannan ya ce "Ai ko dan ma wannan zumunci naku ya ɗore dole na saya muku waya, domin ku rinƙa kiran juna kuna gaisawa, sannan nima idan zan zo wajen ku na kira ku a waya ku bani address, kuma idan ɗaya na son zuwa wajen ɗaya kunga zaku yi ta waya kuna yiwa juna kwatance har ku samu ganawa". Tsabar murna ji suka yi kamar su miƙe su rungume shi saboda daɗi, shi kuma abu uku ne yasa ya yi musu wannan babbar taimako, na farko saboda Allah, na biyu saboda ya kamu da matsanancin son Rimsha lokaci guda, na uku kuma yana jin Ayla tamkar kanwarsa, tamkar yar uwarsa ta jini, wannan dalili ya sa ya tsaya musu. After some hours👌 Bayan sun yi sallar mangariba. Da sallama Ahmad ya shigo cikin ɗakin, ya dawo daga masallaci. Cike da kulawa ya ce "Ku shirya muje cikin gari mu sayi abinci daga nan sai na saya muku waya, sannan kuma daddy ya gaya mini jirgin Kaduna zaku hau, Queen of beauty, idan kin sauƙa a Kaduna zaki iya zuwa park ki shiga motar Katsina?" Shiru ta yi tana tunani ita da bata san ko ina ba, shima Katsinar tun da suka koma sau ɗaya ta fita, sai kuma ranar da aka sace ta shine rana ta biyu. Ganin ta yi shiru yasa ya ce "To idan kuka sauƙa a airport zamu yi magana, zan kira ki a waya sai na gaya miki in da zaki je, sai ki tari mashin zuwa wajen, idan kin je wajen sai mu sake yin waya, daga nan zan gaya miki in da motocin Katsina suke, idan kin je wajen sai ki haɗa ni da driver a waya zamu yi magana da shi, dan nasan wannan shirun da kika yi ya tabbatar baki san ko'ina ba a Kaduna, bayan haka kuma dama nasan da wuya ki san wani wajen tun da ba garin ku bane". Sunkuyar da kai kasa kawai ta yi ba tare da ta yi magana ba. "Queen of beauty kuma Queen of kunya, to dai yanzu ku shirya mu je mu dawo da wuri dan kuzo ku yi barci da wuri, saboda jirgin karfe 7 zaku hau". Yana kai karshen maganar ya juya ya fice daga ɗakin, dan ya basu damar shiryawa a nutse. Hijabi kawai suka ɗaura saman Abayar jikin su, sannan suka sanya takalmar Kausar da suka zo da shi, domin a kayan da ya sayo musu babu takalmi. Har sun kai bakin kofar ɗakin zasu fita, sai Rimsha ta dawo da sauri ta ɗauki perfume na shi dake saman drawer mirror ta fesa, dariya Ayla ta yi, kasa kasa ta ce "Ɓarauniya, to dai shi turare ba'a satarsa". Wucewa wajen switch na ɗakin ta yi, ta kashe wutar tana faɗin "Anyi ɗin idan mutun shima yana da ra'ayi ba sai ya yi satar ba". Sai faman guntse dariya Ayla take yi ta ce "Allah yasa ma turaren makale mata ne, ki makale masa ki ce ba zaki koma ba". A kule Rimsha ta ce "Bakar muguwa, to dai nariga ki na ce Allah, kuma ta Allah ba ta mutun ba!" tuntsurewa da dariya Ayla ta yi, daman dariyar ya ciwota sosai, wato ita dai Rimsha duk wani zance da zai kawo mata zancen kada ta koma gida bata son shi ko da wasa. Haka suka fito waje sai faman guntse dariya Ayla ke yi, ita kuma Rimsha ta sha kunu ta murtuke kamar hadari fuskar nan ta zama, dama Rimsha ba baya ba wajen iya tsare gida, idan aka ɓata mata rai. Tsaye suka same shi yana kallon gari ya juya musu baya. Sallama suka mashi, juyowa ya yi yana kallonsu da yake hotel ɗin akwai wuta, an tada gen, hakan ya bashi damar kallonsu sosai, Rimsha Queen of beauty tamkar ka sace ta ka gudu da ita saboda kyau, hijabin ya mata kyau sai dai bai karisa kai har kasa ba. Sai murmushi yake yi ya ce "Muje ko?" Ya yi maganar yana nuna musu hanya, gaba suka yi ya bi bayan su, yana kallon yadda suke tafiya a nutse ɗaiɗai abin su, ba hayaniya ba hargaga kamar yan matan kauye, a nutse suke. Wani azababben son Rimsha ne ke kara ninkuwa masa a zuciyarsa, sai wani murmushi yake yi shi kaɗai, kamar ba lafiya ba. Ya kasa daina kallon su har suka isa wajen mota, abin mamaki sai yaga dukkansu sun shiga gidan baya, ɗan ɗaure fuska ya yi kafin ya ce "Ni driver ku ne? Ku fito ku dawo gaba". Ba dan sun so ba suka fito suka dawo gidan gaba, sannan shima ya shiga ya tada motar suka bar wajen. Challenge suka fara nufa, wato kasuwar wayoyi. Wayoyine iri daban-daban a wajen, gasu nan a zube kamar kyauta ake rabawa. Wani katafaren shago suka shiga, kun san yarabawa da son kyawawan mata, duk in da Rimsha ta wuce sai sun kalleta sun sake kallonta, da yake ko ina a wajen akwai hasken wuta sosai, saboda business ɗin su. Wani irin bakin ciki Ahmad ya ji, haushi ya kama shi yadda suke ta kallon Rimsha, ji ya yi dama bai zo da su ba, kuma yanzu in da suka yi parking na motar su akwai ɗan nisa, ga shi yana son su yi sauri dan su koma su yi sallar isha, haka ya hakura ya danne suka shiga cikin shagon. Wayoyi yasa aka kawo musu kala, huɗu ya ce su saɓi dai ɗaya, duk ka kuma Samsung ne masu tsada, A72 ne da A 12 sai A10 guda biyu. Kallon su ya yi ya ce "Ku zaɓi wanda kuke so a ciki" Mai shagon duk da baya jin Hausa ya fahinci zaɓi Ahmad ya basu ai kuwa ya yi maza ta cap ke da cewa "Wannan kyakkyawar yarinyar da A72 ta dace" ya yi maganar cikin harshen turanci ba yarabanci ba, ai kuwa Ahmad ya zo har wuya, cikin ɓacin rai ya ce ba za su sayi wayar a nan shagon ba sun fasa, sosai mai shagon ya rinƙa ba shi hakuri, amma ina ya murje idanuwansa ya ce ba za su saya ba. Haka suka wuce zuwa wani shagon, a nan ya sai musu A12 guda biyu iri ɗaya har color ma ɗaya, sannan suka fito, ya saya musu sim card, sai ya wuce da su wani katon super market dake gaba da challenge ɗin kaɗan. Ko da suka je wannan super market ɗin kuwa, saboda karfin hali irin na Ahmad har da cewa su zauna a mota su jira shi, dan tsabar kishi, haka suka zauna ya rufe su tare da kunna musu Ac, ya wuce ya je ya yi sayayyar da zai yi ya dawo suka wuce Item 7, a nan suka sayi abinci suka dawo gida. Lokacin da suka dawo karfe 9:10. A hanzarce Rimsha ta yi alwala ta gaba tar da sallar isha, shi kuma Ahmad suna dawowa da ya rako su ɗaki ya juya ya fice, ita kuma Ayla saman drawer ta zauna tana kallon Rimsha. Bayan ta idar da sallah ne, suka jawo ledar abin cin da ya basu kafin ya fita da nashi, sosai suka ci abincin, sannan suka haɗa da fruits da ya sawo ɗazun kafin su fita, dama kafin ya fita ɗakin sai da ya ce musu su sha fruits ɗin su ya sayawa. Bayan sun gama, sun tattare komai tsab, sai suka yi kwanciyar su a kasa wajen da suka kwanta ɗazun. Can kuma kamar wayan da a ka tsikara, haka suka ta shi suka kunna kallon a Tv dake ɗakin, suka kama tashar zee wold. Sai karfe 10 daidai Ahmad ya dawo hannunsa ɗauke da kananan trolley guda biyu, kusa da nashi trolley ya ajiye sannan ya zauna saman dadduma suka ɗan yi hira kaɗan, zuwa karfe 10:30 ya ta shi ya sanya musu wayoyin su a charji bayan ya sanya musu sim card da ya sai musu, saboda suna sauri gobe zasu tafi hakan yasa ya saya musu sim mai register amma ya ce musu idan suka koma su yi register wani sim ɗin da kan su. To suka amsa mashi da shi, sannan ya musu sallama ya ce su rufe kofar da key ta ciki su kwanta su yi barci da asuba zai zo ya tashe su. Ba karamin daɗi suka ji ba, dama suna ta tunanin ya za su yi su kwana da shi ɗaki ɗaya, ashe dai yana da hankali sosai. Yana fita Ayla ta haye gado ta baje kafafu tana faɗin ",Yau dai ba gadon Kausar zamu kwana ba". Ita kuma Rismha wuce wa ta yi ta rufe musu kofar ɗakin da key sannan ta shiga toilet dan yin wanka. Bayan ta yi wanka ta fito ta shirya cikin ɗayar abayar da ta rage a ledar da ya kawo musu ɗazun, bayan ta gama ta haye gado tana faɗin "Ayla ki je ki yi wanka mana". Ina Ayla barcin gajiya ya ɗauke ta baiwar Allah, yau dai sun kwana cikin farinciki, ita ma Rismha tana kwanciya ba jimawa barci ya yi awon gaba da ita. Amma kafin ta yi barci sai da ta ɗan yi tunani a kan ya za'ayi su hau jirgi ba passport ba komai, ko dai private jet ne, ko kuma sai da safe idan sun je zai musu passport ɗin. Da wannan tunani a ranta ta yi barci. (Uh su Rimsha yau ana busy kuma ana murnan komawa gida, ba'ayi tunanin masoyi GAR ba🤣 an samu freedom) Asuba ta gari Nima kuma na haɗa kayana zuwa gidan Abba, sai mun haɗu gobe dan jin yadda zata kaya a gidan Abba. Na barku lafiya da yar dan mai duka. 💖💖TRIPLET'S💖💖 E33-34 💖💖GIDAN ABBA💖💖 Yau ma kamar jiya Umaisha ta yi wuni mai cike da annashuwa da farinciki, sakamakon Rufee ta sake dawowa, tun karfe 7 na safe ta dawowa gidan, yau ko shara Umaisha ba ta yi bare kuma a kai ga su gyaran ɗakin Abba da Ammie. Ita kuwa Ammie kwata-kwata bata shiga harkar Umaisha ba, kamar bata nan a gidan ita ma, ta yi shiru a ɗakin ta, saboda tana tsoron bala'i Rufee. (Toh fa wannan shine gaba ma da gaban ta) Su Imran kuwa, wannan zuwa Kano da suka yi, sun sallami su Zuwaira masu aikin gidan su Jelly, Imran ya ce musu idan komai ya daidai ta zai zo har kauye da kansa ya ɗauko su, sannan ya ɗauki dollyn Jelly dan su dawo da ita Kaduna, da suka ta shi tafiya, sun rufe ko'ina na gidan, duk wani kayan wuta dake jone a sucket sun cire shi, daga karshema Akil ya kashe wutar gidan gaba ɗaya suka wuce suka kama hanyar Kaduna rai a ɓace domin har wa yau ba su yi nasara ba, amma sun bar baba mai gadi a gidan basu sallame shi ba, sun ce ya cigaba da kula da gidan. Shi kuma baban Muneer yana yawan zuwa neman daddyn Jelly sai dai Allah bai taɓa haɗa shi da su Imran ba, ba'a kwana biyu bai zo gidan ba, sai dai su Zuwaira su ce mashi daddyn Jelly ya yi tafiya, ya ci alwashin nan da wata ɗaya in har daddyn jelly bai bayyana ba, to zai saki wannan video wa duniya, a cewar sa daddyn Jelly ai ɓuya ya yi, domin Company sa na aiki, bai san cewa Imran da Irfar ke tafiyar da company yanzu ba, kuma yana zuwa har company ya tambayi Engineer Muhammad Imam shin ko Maik ya dawo, kullum amsa ɗaya yake ba shi shine a'a bai dawo ba, duk kuma mafiyawancin lokutan da baban Muneer ke zuwa, su Irfan sun bar company, kuma a zahirin gaskiya daddy'n Jelly bai gayawa kowa abin da ke tsakanin shi da baban Muneer ba, a cewar sa idan ya yi hakan ya tonawa kan shi da kan shi asiri ne, shiyasa ya rufe maganar kawai, ya yi wa su Imran karya. Sai Misalin karfe 6 na yamma su Akil suka shigo gida, gaba ɗaya a gajiye suke, sai wani ɗaure fuska Akil yake yi, to da yake shi Akil part na shi a cikin nasu Ammie yake, shi kuma Imran daga waje harabar gidar part nasa yake ta gefe, bai haɗu da nasu ba, hakan yasa suka rabu da Imran a harabar gidan, Imran ya wuce part nasa hannunsa riƙe da dollyn Jelly, duk ta rame, saboda bata cin abinci sai su Zuwaira sun mata ɗure. Shi kuma Akil ya nufi cikin gida. Yana shigowa babban palon su, ita kuma Ammie tana saukowa daga sama. Sauri sauri ya yi mata sannu da gida zai wuce part nasa, dan a gajiye yake sosai. "Ina kuke yawan zuwa ne Akil?" Ammie ce ta jefa masa wannan tambayar, wadda ya ji ta tamkar saukar aradu, domin kuwa idan har ya gaya mata cewa gidan bappansu suke zuwa neman yar uwarsu ta gefen Abba, to ba makawa tsine masa zata yi, ga shi shi kuma bai iya karya ba, shiya lokacin da ya auri Umaisha ya fito karara ya gaya musu gaskiya, bai ma san ta ina zai fara yin karyar ba, to idan ma zai yi karyan me zai faɗa mata. Ganin ya yi shiru ne yasa ta ce "Akil lafiya kake kuwa?" Yar firgita ya yi ya ɗago yana kallonta "Ammie na ga ji sosai ne, daga Kano fa nake, dan Allah ki bari naje na huta kin ji? Idan ba haka ba zan iya faɗuwa". Jin haka yasa ta ce to ya wuce part na sa da wuri ya je ya huta, kuma a gaskiya ita bata ma san asalin garin da yan uwan Abba suke ba, bata san suna Kano ba, a iya nan Kaduna ta sani, shiyasa bata yi wani tunani ba ta ce ya wuce part na shi, da ta sani ko tana zargin yan uwan Abba na Kano to ba faɗuwa Akil zai yi ba ko mutuwa zai yi sai ya gaya mata gidan uban da ya je, idan kuma ya gaya mata, ta ji cewa wajen yan uwan Abba ya je, to ba makawa tsine mashi zata yi, kamar yadda ya faɗa. Da sallama ɗauke a bakinsa ya shigo part ɗin, gaba ɗayan su suna palonsa, Akila, Rufee, Aafia, Umaisha, kasan cewar 24 hours akwai wuta a gidan su, hakan yasa gaba ɗaya ko'ina haske ya gauraye cikin palon. Akila da Umaisha ne suka ta shi a tare suka nufe shi suna faɗin "sannu da dawowa yaya Akila". Wani haɗiyar yawu Rufee ta yi, a ranta ta furta "dama nan ne gidan gayen nan? Sorry Umaisha dole na ari mijinki na yan kwanaki" (Tofa rashin sani ya fi dare duhu, in dai Akil ne bismillahi) Cikin rawar kafa ta miƙe tsaye tana faɗin "Sannunka da dawowa mijinmu" galala Aafia ta saki baki tana kallonta. Da yake shima Akil ɗan air ne ko kallon in da take bai yi ba, ya rungumo Akila ta gefe Umaisha ta gefe yana faɗin "Na yi missed na ku my pleasures". Lafewa suka yi a gefe da gefen kirjinsa suna fuskantar juna, sai murmushi suke yi kamar dukkan su matan sane. Cike da zolaya ya ce "Heartbeat ke daga nan na sallame ki, ki zauna a nan da su Aafia, ke kuma my baby mu je ki yi mini wanka ki mini tausa dan na gaji sosai". Turo baki Akila ta yi, ta turɓune fuska a shagwaɓe ta ce "Wlh yaya Akil kana cimin fuska, kana saka Aunty Umaisha tana rena ni, kuma na fita shekaru, haka ranar ma har da ce mini ta yi wai mijinta ya kusa dawowa na wuce ɗaki na, wannan cin fuska Allah ya yi mini yawa" ta kai karshen maganar tana raba jikinta da na shi, ita a dole ta yi fushi. Cikin sauri ya jawota ta dawo jikin nasa, cikin sigar rarrashi ya ce "Haba my heartbeat wasa nake yi miki ai, ke ai kin san tawa ce, ban isa ba, amma yanzu dai ki zauna a nan ina zuwa" ya kai karshen maganar yana jan hancinta, Turo baki ta kuma yi kamar zata saki kuka, ita dai Aafia bin su kawai take yi da ido, abin gwanin ban sha'awa, sai fatan Alkhari da fatan kasancewa cikin farinciki na har abada take yi musu, saɓanin Rufee da take kallon su take ayyana wa a zuciyar ta, wannan farinciki da ita ya kamata Akil ya rinƙa yi, duk wannan tarairaya da soyayya ita ya kamata ya yi wa ba Umaisha ba. Umaisha kuwa tana lafe a kirjin mijinta ta fito da ɗan harshenta waje tana yiwa Akila gwalo, a kule Akila ta ɗaga hannu zata make bakin nata, cikin sauri Akil ya tare hannun nata yana faɗin "So kike yi ki fasa mini baki na ko? To baki isa ba, ai gara ki buge nawa ba nata ba, dan idan kika buge nata sai na fita jin zafi da ɓacin rai" (Akwai wanda ya gane zancen Akil kuwa?🤔) "Kai yaya Akil yanzu wlh ka dawo mai son kai sosai" "Wai ku ba zaku kyaleni naje nayi wanka na huta ba, sai na faɗin muku a nan ne? Ku dama idan kuka haɗu kuka sani a tsakiya Allah ne kawai ke kwatata". Raba jikinsu Umaisha ta yi tare da riƙo hannunsa tana faɗin "Muje hai yaya Akil, muje na maka wanka bar heartbeat ɗin nan bata da aikin yi sai dai ta zo ta dame mu" ta kai karshen maganar tana yi wa Akila gwalo, kwafa Akila ta yi tana faɗin "Wlh ba zan bari ki ba, kin ɗauki bashi, kuma sai na rama, nice ma bani da aiki ya ba? Ba komai". Shi dai murmushi kawai yake yi, yana matukar kaunar Akila dan tana son duk wani abin da yake so, kuma tana goya masa baya sannan ta taya shi kula da wannan abin, idan baya nan sosai take kula da Umaisha, ko motsi Umaisha ta yi sai ta tambaye ta me take so, sai dai idan ta tafi school ne, sannan suna sharing secret tare da Umaisha, suna kuma rufawa juna asiri, yanzu ma duk abin da Ammie ke yi wa Umaisha Akila tana sane, sai dai abin da yasa bata gayawa Akil ba, tana tsoron idan ta faɗa Ammie zata iya saka shi ya saki Umaisha, shiyasa ta yi shiru, amma fa tana nan tana kulla ta yadda za'a yi Akil ya canzawa Umaisha gida, dan kullun sai ta yi mata kukan abin da Ammie ke yi mata, sannan kuma in dai tana nan Ammie tasa Umaisha aiki to tare suke yin wannan aikin, shiyasa yanzu ta iya wanke-wanke da ɗan aikace-aikace gida. Wucewa cikin ɗaki Akil da Umaisha suka yi, ita kuma Akila ta dubi su Aafia ta ce "Kuzo mu je ɗaki na mu zauna, idan yaya Akil ya fito zai mayar da ku gida..." A hanzarce Rufee ta tari numfashi ta da cewa "A'a ki dai bari mu zauna a nan ɗin tun da mu bakin Umaisha ne" da yake Akila bata kawo komai a ranta ba, sai ta biye musu kawai suka zauna a wajen. Shi kuma Akil su na shiga ɗaki ya jawo matarsa ya runguma yana faɗin "Nayi kewar ki my baby", ya kai karshen maganar yana sumbatar goshinta. Hannayenta ta kai saman botir na rigarsa ta wuya ta fara ɓalle wa tana faɗin "Ai nima na yi kewar ka yaya Akil". Cire hannayen nata ya yi ya kankame ta a jikinsa sosai, a nitse ya haɗe bakin su ya fara bata hot kiss, ba ɓata lokaci ita ma ta fara mayar masa da martani, nan take suka birkicewa juna, hannun sa ya zura cikin rigarta ya fara bata sako na musamman. Sun jima a haka har sai da karfin su ya kare, Umaisha na kokarin faɗuwa mashi kasa, sannan ya yi saurin sakin ta, idanuwansa duk sun sauya launi, har wani duhu-duhu yake gani. Da kyar ya iya sai ta nitsuwarsa ya wuce toilet dan yin wanka. Ita kuma ta kasa binshi ta cire masa kayan, a bakin gado ta zauna tana sauƙe ajiyar zuciya dan dama in da sabo ta zaba Akil ya kware wajen iya soyayya, yanzu zai sata ta mance duk wani damuwa da take ciki komai girmar damuwar, hakan yasa da ya dawo gida duk wata matsalar ta, ta kau kenan, sai zallar farinciki. Tana zaune a wajen ta kasa motsawa har ya fito wanka ɗaure da towel a kugunsa. "My baby this time fa kin yi kewata sosai kema na ga alama" ɓoye fuska ta yi tana murmushi, domin kuwa ya faɗi gaskiya ta yi kewar shi sosai da sosai. Yau dai komai shi ya yi wa kansa, har kayan sawa shiya ciro wa kansa dan ya lura babyn tasa ta karɓi wuta sosai har lokacin bata dawo normal ba. Jallabiya ya sanya a jikinsa sai tashin kamshi yake yi, ya shinfiɗa dadduma ya gabatar da sallar mangariba, ita kuma Umaisha miƙewa ta yi da kyar ta fito wajen su Aafia, ta ce suje ɗakin Akila su yi sallah a tare, ko kuma su shiga ɗayar ɗakin kusa da nasu, Rufee ce ta ce lallai su shiga ɗakin kusa da nasu, a nan za su yi sallah, A'afia ta lura Rufee bata son barin part ɗin ne tun da ta kalli Akil ya dawo, Allah dai yasa ba wani abin take shiryawa ba. A ɗayar ɗakin suka yi sallah a tare gaba ɗayan su har Umaishan, sai dai ita Rufee bata yi sallar ba, ta ce musu wai tana period, Aafia tasan karya Rufee keyi domin kuwa kullun haka take ce musu a school wai tana period, har suka gane karya take yi, a zahirin gaskiya kuma wani lokaci bokanta ke hanata yin sallar gaba ɗaya, wani zubin ya ce mata iya sallar mangariba kawai ya halakta mata da tayi, wani lokaci kuma sai ya ce kwata-kwata ma kada tayi. Bayan sun idar da sallah ne suka fito palo suka zauna suna hira. Cikin dabara Umaisha ta zame jikinta ta gudu wajen mijinta abinta, dan tana kewar shi sosai, ashe Rufee na ankare da ita, tana ganin tafiyarta, sai wani ciza laɓɓa take yi alamar tana kishi da Umaisha, kuma tana jin haushi. Umaisha kuwa tana shiga cikin ɗakin ta isko shi yana miƙe a saman bed nasu. Cikin sauri ta tafi ta faɗa jikinsa tana murmushi, shiru ya yi mata kamar bai san da zuwanta ba. A shagwaɓe ta ce "Yaya Akil meyafaru?" Shiru ya yi kamar ba shi a wajen, ganin haka yasa ta kama lips nasa na kasa ta fara tsotsa kamar sweet. Kwace lips nasa ya yi yana lumshe idanunsa alamar ya ji daɗin hakan, sai dai kuma fushi yake yi da ita, kasa ta yi da murya cikin girmamawa ta ce "Kayi hakuri" a kule ya ce "Ba zan yi ba, ai baki damu da ni bane, har da zaki tafi ki barni a ɗakin nan tun jiya fa rabon mu da juna..." Bata bari ya karisa maganar ba ta yi maza ta cabke lips nasa tana mashi wasa da hannun ta a saman babban sashe. Jin wannan salon yasa ya mance da fushi ya kara jawota jikinsa suka lula duniyar sama jannati. Su Aafia kuwa sai hira suke yi a palo, amma ita Rufee kunnanta da hankalinta duk yana jikin kofar bedroom ɗin su Akil, tana mutuwar son taga meke faruwa a cikin ɗakin, burinta kawai ta ga me suke yi a cikin. Kiraye kirayen sallar isha ne ya dawo dasu daga duniyar sama jannati da suka lula, da kyar ya iya saita kan shi tare da kamewa, sannan ya miƙe zaune duk idanuwansa sun rine tamkar ba shi ba, ita ma Umaisha duk ta birkice masa, sai wani lumshe idanu take yi. "Ta shi kiyi wanka kizo ki yi sallar isha sai ki shiya ki saka nikaf zamu fita restaurant" ya yi maganar da murya kamar mai raɗa. Ɗan zaro idanuwanta ta yi murya a dashe ta ce "Yaya Akil wanka kuma?" Gyaɗa mata kai kawai ya iya yi, dan ya kasa magana. "To ai yaya Akil naga ba mu yi komai ba, in dai yi alwala idan na yi sallah in zamu kwanta barci sai na yi wankar" girgiza kai ya yi yana kokarin sauƙa daga gadon ya ce "Wanka za ki yi saboda ai kin more" shiru ta yi tana tunanin kalmar ta more, "to me na more yake nufi? Shifa yaya Akil ɗin nan haka yake sai ya rinƙa gayawa mutun magana ta sigar da ba zai gane ba" ta faɗa a cikin ranta. Tana kwance ta kasa ta shi har sai da ya yi wanka tare da ɗauro alwala ya fito tana kwance. Bakin gadon ya zo ya tsaya tare da miƙa mata hannunsa a kan ta kama ta miƙe, da kyar ta iya miƙa masa hannun nata, a hankali ya miƙar da ita, ta sauƙo kasa ta nufi toilet. Kafin ta fito ya gabatar da sallar sa yana zaune saman dadduma. Ita ma shiryawa ta yi ta zo ta yi sallar. Bayan ta idar ne yake tsokanar ta a kan yau ta hana shi yin Sallah a masallaci, domin kafin ya yi wanka an idar da sallah. Kwanto da kanta a saman kafaɗarsa ta yi tana zuba masa shagwaɓa, a hankali ya kai hannunsa yana shafar kumatunta yana zuba mata addua'o'i tare da sanya mata Albarka. Sun kwashe good 10mins a haka kafin nan su miƙe ya ɗauki laptop nasa da wayarsa, ya ce ta same shi a cikin mota idan ta gama shiryawa, kwata-kwata ya mance da su Aafia dake palo. Yana fitowa Rufee ta miƙe tana faɗin "Angon mu ai tun ɗazun nake jiran fitowar ka domin in maka godiya, tsayawa ya yi yana kallon Akila dake ta famar turɓune fuska, ita a dole tana fushi da shi. "Heartbeat fushi kike yi da yaya Akil naki?" Ya yi maganar cikin sigar rarrashi. Akila bata kai ga yin magana ba, Rufee ta rigata da cewa "Angon mu a gaskiya muna godiya sosai, domin Umaisha ta gaya mana yadda kake bata kulawa sosai, ta ce mana ka iya soyayya da kula da mace, ka iya tarairaya, sannan ka kware a kan gado" A sukwane ya ɗago kai yana kallon ta, ba iya shi kaɗai ba har da Akila da Aafia sai da suka girgiza da jin zancen da Rufee ke yi, duniyar tunani Aafia ta faɗa na yaushe Umaisha ta basu wannan labari, ita da iya hirar school kawai suka yi da ita, amma shine Rufee zata yi mata wannan sharrin wajen Akil, lallai Rufee ta iya makirci. Ita kan ta Akila sai famar karyata zancen zuciyar ta keyi, duk da tana zuwa school bata wuni da su ba, amma dai ta yi wa Umaisha farin sani, ta san cewa ko A'afia ita kaɗai Umaisha ba zata gaya mata sirrin aurenta ba, domin kuwa ko ita da suke tare dare da rana Umaisha bata taɓa gaya mata abin da ke tsakanin ta da Akil, sai ita Rufee ce zata gaya wa, lallai wannan magana ta Rufee abin dubawa ne. Ita kuwa Rufee ganin Akil ya ɗago yana kallonta, abin nema ya samu dama attention nasa take bukata, dan haka sai ta ci gaba da cewa "Gaskiya Umaisha ta more sosai, dan yadda ta bamu labarin ka, na yi mata murna ba kaɗan ba, amma fa kayi hakuri, na buge mata baki domin abin da ta yi bai dace ba, shiyasa na mata faɗa sosai, na ce kada ta sake faɗin sirrin mijinta ga wata, Allah ma yasa mu ta gayawa ba wasu a waje ba, shiyasa nayi saurin taka mata birki, fatan ba zaka ji babu daɗi ba dan na yi mata faɗa ta rinƙa rufe maka sirrin ka? Kasan irin ku wayan da suka kware wajen iya soyayyar nan basa son a yiwa matansu faɗa". Tana magana tana nufarsa "Kawo laptop ɗin na kai maka in da zaka zauna" ta faɗa dai dai lokacin da ta fariso wajen da yake tsaye yana kare mata kallo, hannu tasa zata karɓi laptop ɗin, daidai lokacin Umaisha ta fito cikin shiga Abaya baka da hijabi har kasa brown color sai plat shoe shima brown colo, tana riƙe da jakarta baka da bakin nikaf a hannunta Ganin Rufee na ƙoƙarin karɓar laptop dake hannun Akil yasa Umaisha ta kariso da sauri, tana kokarin yin magana. Bata kai ga buɗe baki ba ta ga saukar wani mahaukacin mari Akil ya sauƙe wa Rufee, ji kake yi dif kamar an ɗauke wuta haka Rufee ta ji, gaba ɗaya duniya ya tsaya mata cak, har wani taurari ta gani sun gilma mata ta cikin idanunta. Sai da ta ɗauki 1mins sannan ta samu damar fara hawaye, wani uwar tsawa ya daga mata "Who are you?!!" Ƙasa ta zube a kan gwiwowin ta tana hawaye. Rai a matukar ɓace ya dawo da kallonsa kan A'afia, cikin tsawa ya ce "Wace kazama ce wannan? Kuma me ya kawota cikin gidannan?" murya na rawa Aafia ta ce "Kayi hakuri yaya Akil kawar mu ce ta school..." Ai bata kai karshen maganar ba ya tako zuwa in da take tare da ajiye laptop da wayar dake hannunsa ya hau dukan ta, haɗa hannayen ta dukka biyu ya yi ya riƙe da hannun sa ɗaya, ya ɗaga ɗayan hannun nasa ya fara bata maruka. Hakan ma bai masa ba, sai da ya dakawa Umaisha tsawa a kan ta ɗauko masa belt nasa a ɗaki, da sauri ta wuce ɗaki dan ta ɗauko mashi, mamaki Akila take yi na me Aafia kuma ta mashi da yake dukanta haka. Umaisha na kawo belt ya karɓa ya hau dukan ta. Da farko ta daure ba zata yi kuka ba, amma da ta ji duka mai kyau sai ga shi ta fara ihu, Rufee na ƙoƙarin guduwa ta bar palon ya yi saurin kwashe kafafunta da nashi kafar, haka ta zube ƙasa kamar kayan wanki. Ya haɗe su su biyun dukka ya musu dukan kawo wuka, sai kuka Akila da Umaisha suke yi sun rungumi juna, ga shi sun san idan ransa ya ɓaci ba mai iya tinkararsa sai Abba, ko Ammie tsoron shi take yi wani zubin, dan idan mutun ya je ma, zai iya haɗa wa da shi. Sai da Akila taga da gaske idanuwansa sun rufe zai iya illata su Aafia akan laifin da basu san menene ba, hakan yasa Akila ta fita da gudu zuwa ɗakin Abba, dan tasan shi kaɗai ne zai iya dakatar da Akil. Cikin mintuna da basu fi biyu ba, sai ga Akila da Abba sun dawo ɗakin, su Aafia kuwa sun daku iya dakuwa, a kan laifin da bai gaya musu ko laifin menene ba. Da kyar Abba ya iya dakatar da shi, sai huci yake yana haɗa zufa. "Akil me yafaru? Me suka yi maka haka?" Shiru ya yi yana haki ya kasa magana. "Akila kawo masa ruwa mai sanyi a fridge" da sauri Akila ta wuce tana tafiya tana waigowa domin bata taɓa ganin ɗan uwan nata cikin fushi haka ba. Saman sofa ya zauna yana runtse idanuwansa kamar zai saka ihu yake ji, zuciyar sa har wani harbawa take yi da karfi karfi. Akila na kawo ruwa Abba ya karɓa ya buɗe ya miƙa masa, ba musu ya karɓa ya fara sha, domin ya fi bukatar ruwar sama da komai a yanzu. "Aafia me kuka yi wa yayan naku?" Abba ne ya tambaya yana dawo da kallonsa kan su. Sai kuka suke da kyar da kyar, sun kasa magana, Akil duk ya fashe musu jikin su, domin mahaukacin duka ya musu, wadda idan ana irin shi ko ina ake sauƙewa mutun bulala shine mahaukacin duka. Sun jima a haka sun kasa magana, ita kam Rufee ma kwanciya ta yi plat a kasa domin ta samu ta rinƙa kwakwalo numfashin ɗan numfashi da ya rage mata yake fita da kyar. Kamar daga sama suka ji muryan sa cikin tsawa yana faɗin "Aafia ki gaya mini gaskiya, idan kika kuskura kika yimini karya, na yi bincike na gane abin da kika gaya mini karya ce wlh da hannuna zan kashe ki!!!". Ihu Akila ta kurma jin abin da Akil yake faɗe shi kansa Abba ba shiri ya ja baya kaɗan dan ya samu damar ganin shin da gaske Akil ɗin ne ko ba shi ba, ita kan ta Umaisha da take matarsa sai da ta kara waro idanuwanta dan ta tabbatar shin shi ɗin ne ko dai an yi mata canjin shi. "A'afia kin taɓa sanin namiji a rayuwar ki?!!" Jin tambayar suka yi tamkar saukar aradu, domin babu wanda ya san dalilin da ya sanya ya yi musu wannan ɗan iskan duka haka. Girgiza kai ta fara yi ta kasa magana, wata uwar tsawa ya daka mata wadda ya sanya ta buɗe baki ba shiri "Zaki buɗe baki ki yi mini magana ne ko sai na taka wuyarki a nan?!!!". Jikinta sai kerma yake yi, hannunta ya kasa tsayawa waje guda, da kyar ta iya buɗe baki murya na rawa ta ce "A'a ban ta ɓa ba" Abba ne ya ce "Akila ke da Umaisha ku wuce ɗaki" cikin sauri ya dakatar da su "No Abba ka kyalesu a nan, gara su ga komai da idanuwansu domin duk wanda ta yi gigin kamanta abin da Wannan tsinanniya ta yi to tabbas ni da kai na zan yankata, zuciyata ba zata iya jurar ganin ɗaya daga cikin nawa ya aikata zina ba" ya kai karshen maganar yana nuna Rufee. Abba dai kansa ya kullu, su ma su Akila kan su ya ɗaure, suna bukatar sanin mekefaruwa a nan wajen. "Akil ka gaya mana wai me yake faruwa ne" Abba ne ya tambaya yana kara tsaresa da ido. Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Akwai wata rana dana je Abuja, na sauƙa a hotel, ina kwance cikin ɗaki na naji ana knocking, na gaji sosai amma haka na daure na ta shi naje ya buɗe kofarnan, ina buɗewa idanuwana suka yi mini arba da wannan shaiɗaniyar yarinya, tana cikin maye, ta sha giya ta bugu ta fita hayyacin ta, sai layi take yi, ina kokarin yi mata magana sai wani matashin a ɗakin kusa da ni ya fito yazo ya ja hannunta yana faɗin "Baby sai da nace miki kada ki sha kayan nan yau zan mai daki gidanku, amma kin zo kin ɗebi kaya, kayar ma dayawa, ga shi sun bugar dake sosai, yanzu a haka zaki koma gida? Zama ki iya shiga gidan kuwa? Koda na sauke ki a kofar gida? Na san mama basu da matsala dan kin koma a buge Matsalar dai shine ki iya karisawa cikin gidar, ga shi nan da ɗaki na ma kin kasa ganewa kinzo kina buga wa mutun kofa" ya kai karshen maganar tare da jan hannunta ya rungumeta yana bani hakuri suka shiga ɗakin su dake kusa da nawa, tana buge lokacin shiyasa bata iya gane fuskata ba, shine yanzu ta zo har tana yi wa matata sharri" Wani irin sanyi Akila ta ji lokacin da Akil ya ce sharri Rufee ta yi wa Umaisha, Allah sarki ya san halin matarsa farin sani, ya san abin da zata yi da wanda ba zata yi ba, kuma ba wanda ya isa ya zo ya ce masa matarsa ta yi kaza ya ɗauka, yana da dogon nazari da tunan a kan abu, ba da kai yake yin abuba, baya karɓar jita jita, sai dai idan ya ji da kunnensa ya kuma gani da idonsa (To da Akil ba mai tunani bane da mekuke tunanin zai ɗauki Umaisha?) Jin abin da Akil ya ce ya sa Abba a fusace ya ce "Ka taka ta har sai ta gaya maka gaskiya, domin abokin ɓarawo ɓarawo ne, dole sai hali ya zo ɗaya ake abota, wannan mummunar abin a family'n mu, a'a wlh ba zata sakuba, ka mata duk abin da zaka yi mata har sai ta faɗi tsakaninta da Allah" yana kai karshen maganar ya wuce ransa a matukar ɓace. Har ya kai kofar fita sai kuma ya juyo ya ce "Ka je ka sanar da Deen ina daka masa warning a kan kula da yarannan, hauka yake yi ne ace kawayen ƴaƴansa ire-iren wayan nan, aikin me yake yi da ba zai bincika dawa suke tare ba? Kullun ranar Wednesday sai na shirya naje makarantar su Akila ba tare da sanin ta ba, haka kawai zan je in zauna a office na detector, dan naga suwa ye kawayen ta da sukawaye take tare, duk wanda na gansu tare sai na yi bincike a kan yanayin tarbiyar gidan su, amma daga kai har Imran ba wanda ya san da hakan bare kuma ita Akilar, dan haka ka ce da Deen na ce ya shiga hankalinsa ya dawo cikin hayyacinsa da kyau, ya san abin da yake yi, neman kuɗi ba hauka bace, dan nasan yanzu bai wuce ya ce yana fita baya zama ba, to idan ma haka ne ka ce ina ba shi umarni da ya auro musu wata uwar da zata kula da su tun da wancan ta watsar da su". "Abba ai bappa yana da mata ya yi aure" "ya yi aure?" Abba ya furta da mamaki a kan fuskarsa. "E Abba ya yi aure" shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Me matar tasa take yi da bazata kula da yaran nan ba? Yanzu ma ai Aafia ita kaɗai ta rage, me yasa ba zata kula da ita ba? Ko dan ba ita ta haifeta ba ne?" shiru Akil ya yi dan ba shi da amsa. Sai da ya ji Abba ya fara faɗa sosai yana zagin Aunty sai ya ce "Abba kayi hakuri, matar da bappa ya aura yarinya ce sa'ar su Aafia ɗin, kaga kuwa ba zai yiwu ta basu kulawa kamar babbar mace ba, domin za su rinƙa ganin ai kan su ɗaya da ita, dan haka ni zan yi magana da bappa zan ɗauki Aafia ta dawo nan domin na bata tarbiya da ta rasa a baya, amma kafin nan sai na yi bincike dan na tabbatar da gaskiyar abin da ta gaya mini" Albarka Abba ya sanya masa sannan ya wuce ya fice daga ɗakin. Dawo da kallonsa kan Rufee ya yi cikin tsawa ya ce "Idan kika sake yi wa Aafia magana sai na take wuyarki kowa ya huta, ba ke babu yar uwata, ke ma Aafia ki buɗe kunnanki da kyau ki saurare ni, zan canza miki makaranta zuwa school ɗin su Akila, amma kafin nan zaki cigaba da zuwa school zuwa next week mu samu transfer later, wlh idan ki ka kuskura kika bari na samu labarin kin sake yiwa wannan shegiyar magana sai na lahira ya fiki jin daɗi, yau a gidan nan zaki kwana gobe da safe ki shirya ki wuce school tun da naga kun buɗe, idan kun tashi ki wuce gida zan zo na yi magana da Bappa, ke kuma kafin na shiga ɗaki na fito, ki tashi ki bar gidan nan idan ba haka ba kika bari na fito to zan tattaka miki wuya!!" yana kai karshen maganar yana nuna Rufee da hannu. Da kyar ta iya miƙewa ta ɗauki jakarta dake saman sofa ta fice daga palon bakinta sai jini yake yi, shi kuma Akil ya koma cikin bedroom nasu dan ya canza kayan jikinsa, dan duk ya nannaɗe wajen dukansu. Yana shiga ɗaki Akila ta lallaɓa Aafia suka wuce ɗakinta, ita kam Umaisha ta kasa motsawa daga in da take tsaye, abin duniya sun taru mata, mamaki take yi daman haka halin Rufee yake, tun da jimawa take ta ce wa Aafia ta fita harkar Rufee amma taki yarda to ai yau ga shi ta ji asalin wace ce Rufee, har Abuja take zuwa bin maza, wa iya zubillah. Tana tsaye tana tunani har Akil ya fito ya same ta, bata ji fitowarsa ba, sai jin hannunsa ta yi ya shafa mata fuska yana janyota jikinsa. "My baby tunanin me kike yi? Kada fa ki je ki saka wa kanki tunani ki jamin rashin morewa yau". Da yake ya saba yi mata magana a dunkule ba wani gane wa take yi ba, sai tayi murmushi kawai ta ce "Me haɗin tunanina da jin daɗin ka kuma?". Matso da bakinsa ya yi daidai sai tin kunnenta kamar wani na part ɗin zai ji su, kasa-kasa ya ce "Idan kina cikin damuwa ruwan daɗi ba zai zo ba" rufe fuska ta yi tana murmushi, shima murmushin kawai yake yi. Bawan Allah yana matikar son Umaisha duk ɓacin ran da ya shiga yana ganin fuskarta yake shiga cikin farinciki. Rungume a kirjinsa take suka fita daga palon bayan ya ɗauki wayarsa da laptop da ya ajiye, haka suka wuce zuwa cikin motar sa, sai bayan sun shiga motar da kan shi ya ɗaura mata nikaf ɗin a fuskarta sannan ya tada motar suka bar gidan zuwa restaurant. (Gaskiya aiki ya ganku, kullun sayan abinci, kai Umaisha a dage a koyi girki, idan ba haka ba irin su Rufee suna nan a duniya masu kwace maza🤣🤣 ni dai na haɗa kaya na zuwa gidan daddy gidan comedy wato Washington DC dan muji ya ake ciki) 💖💖 Washington DC💖💖 Misalin karfe 4:30 na asuba Musharraf ya tashi ya nufi kitchen a palon kasa kenan, da kansa ya haɗa tea mai kauri sannan ya dawo part ɗin su. Saman dining table dake palon part ɗin, ya ɗaura tea ɗin nasa, sannan ya wuce bedroom na Michael. Yana baje a saman bed nasa, ya rungume pillow a kirjinsa, sannan ya sanya wani pillow a tsakanin kafafunsa, kyakkyawar fuskar nan tasa sai kyalli take yi, tamkar wadda ya shafa baby oil, soft skin ɗin nan nasa kamar bai taɓa taka kasa ba, kyakkyawar brown curly hair sannan ya bazu masa har saman idonsa, da yake shi yana rage tsawon gashin nasa, baya barinta ta kai na lion da James tsawo, ya ce takura masa yake yi, shiyasa yake yankewa ya bari iya goshinsa, ta baya kuma iya bayar wuyarsa. Ɗakinsa sai ta shin daddaɗar kamshin air freshener irin na ɗakin Lion ta ke yi, shi kan shi tashin haɗaɗen kamshin perfume nasa yake yi, yana sanye da dogon wando da riga mai dogon hannu na barci, kayan suna da laushi kuma basu da nauyi, yan shara-shara ne, launin Ash color. Barcinsa yake yi cikin kwanciyar hankali, yana sauƙe numfashin nan nasa a hankali-hankali. Musharraf ya ɗan jima yana karemasa kallo, hutu iya hutu suna da shi, dukkansu Triplets suna da bala'i farin jini ga shegen shiga rai kamar me, duk da cewa basu kula kowa, sannan da James da Lion sun fi Michael kwarjini, shi ma James Lion ya fishi sosai, shi Lion abin da ya sanya wasu ma suke tsoron haɗa ido da shi, idanun nasa sun kasance tamkar ya sanya musu kwalli, ga shi dai kwayar idon nasa blue ne, sannan farin ciki kuma farine tas, amma kasar idanun nasa tamkar ya zana musu kwalli, wajen baƙi ne, sai kuma ya haɗe da dark black zara-zaran eyelashes nasa masu tsawon gaske, hakan ba karamin karawa idanuwansa kwarjini suke yi ba, akwai wasu sirrika na musamman a tattare da idanunsa, wadda sai wanda ya iya kallon cikin idanun nasa zai gane hakan, sai dai har yau ba'a samu mai karfin zuciyar iya kallon cikin kwayar idanun nasa ba, sai dai gefe-gefe. Shi kuma James design na idanuwansa ɗaya ne da Lion, sai dai na Lion ya fi nashi girma, sannan nasa bai yi kamar an sanya kwalli ba, normal ida ne nasa, shi kuma Michael ba in da design na idanuwansa suka baro na uncle T da ya rena. A hankali Musharraf ya haye saman bed ɗin, fuskar sa ya fara shafawa yana kiran sunan sa a hankali-hankali "Michael, wake up" ina ai Michael baya duniyar mutane yana can hanyar Englan. Sai da Musharraf ya masa kira uku sannan ya ɗan motsa, a kunne Musharraf ya raɗa masa ya tashi lokacin sahur ya yi, kamar zai yi kuka ya turo baki tare da tuɓune fuska, cikin magagin barci ya ce "Please uncle leave me alone". Ba yadda Musharraf bai yi ba, amma ya ki tashi, haka ya hakura ya kyalesa ya wuce ya nufi waje. Tea ɗin sa ya ɗauka ya sha sannan ya koma ɗakin sa dan ya je ya yi alwala ya yi sallar raƙatainil fajir dan asuba ta kusa. Da safe kamar kullun misalin karfe 6 Tga ya zo ya tashi Michael, dan tun da suka sha punishment suka dai na goyawa Michael baya, da wuri suke tashin sa ya je ya fara gym nasa. Yana turo baki yana yi har sai Romeo ya fito, yanzu ya fara sabawa da gym ɗin. Bayan ya gama gym ɗin ya yi wanka ne ya wuce wajen Musharraf. Kwance ya isko sa samar gadonsa yana askar da kansa ba tare da littafi ba. Kusa da shi yazo ya zauna yana faɗin "Uncle ɗin James barka da hutawa". Miƙewa zaune a tsakiyar gadon ya yi yana kallonsa "Michael me yasa na yi ta tashinka kayi sahur ka ki ta shi?" Nisawa ya yi ya ce "Uncle ai ba dole sai anyi abin da ka ce ɗin ba ake iya ɗaukan azumi, na sani ai saboda pastor ya gaya mana". Murmushi Musharraf ya yi yana faɗin "Eh ba dole sai an yi sahur ba, amma yana da kyau ne ayi ɗin" Jinjina kai ya yi kafin ya ce "To shikenan ni haka zan yi babu sahur ɗin, amma ina da tambaya?" Tattara hankalinsa waje ɗaya ya yi ya zuba masa ido yana faɗin "Ina jin ka mece ce tambayar taka?" "Idan ina azumi zan iya shiga toilet? Sannan zan iya yin wanka?" Gyaɗa masa kai Musharraf ya yi sannan ya shiga rabe masa abin da aka halaktawa mai azumi da kuma wanda aka haramta masa. Sosai ya gamsu ya kuma yi alkawarin zai kiyaye. Haka suka cigaba da hirarsu har zuwa karfe 11 a nan wajen barci ya yi awon gaba da Michael, yana yin barci Musharraf ya fara tofa masa addua'o'i kamar yadda ya saba. 💖After some hours 👌 Misalin karfe biyu na rana Michael ya fara yi wa Musharraf kuka da hawaye a kan yinwa yake ji, shi gaskiya ba zai iya wannan azumi ba, idan Musharraf ya ce masa to ya karya ya ci abinci, sai kuma ya sake saka wani sabon kukan yana faɗin, idan ya karya azumin ai shikenan basu yi dayawa ba James ba zai dawo ba, abin har mamaki yake bawa Musharraf kuma ya fara tsorata kada Romeo ya ji halin da Michael yake ciki, ga shi kuma shi Micheal baya karya, a na tambayar shi, zai faɗa cewa Musharraf ya sanya shi yin azumi, dan su roƙi Allah James ya dawo gida da wuri, idan su Tga suka ji wannan maganar za su gane cewa Musharraf musulmi ne, kuma yana neman musuluntar da Michael, daga nan kuma ya shiga uku a hannunsu, ga shi zaman shekara huɗu zai yi da su, ba halin ya ce zai bar gidan, ba zai yi wu ba, zama da su ya zama dole, kuma ukuba ya zama dole ya karɓa, ko yana so ko baya so, dolema ya so domin punishment ɗin Tga yana maka kuma kana dariya, ba halin ka ɗaure fuska. Bawan Allah duk ya kiɗime ya shiga tashin hankali, cike da ruɗu ya rinƙa rokar Michael a kan ya karya azumin dan Allah, har da yi mashi alkawarin zai haɗa masa tea da kansa, amma ina Michael ya murje ido ya ce ba zai karya ba, kuma yaki dai na yin kukan ƴunwa. (Babbar magana Musharraf kana tsaka mai wuya, kai sarkin shisshigi ba) Da kyar Musharraf ya samu Michael ya sake yin barci, sai rokon Allah yake yi Allah yasa kada Michael ya tashi sai mangariba, idan ba haka ba, yana tsaka mai wuya. Bawan Allah ya kasa zaune ya kasa tsaye, sai zarya yake yi a cikin ɗakin, ga yunwar azumi, da zarar ya ga Michael ya yi motsi zai yi maza ya je ya duba ya gani ko ya tashi ne. Sai Misalin karfe 4 daidai Michael ya farka, ya farka kuma da sabon kukan ƴunwa, yau ɗaya har ya rame, sai kwala-kwalan brown eyes zaka gani, sai rarrashin shi Musharraf yake yi amma ya ki yin shiru. A wannan hali Tga ya zo ya same su, bedroom ɗin Michael ya fara shiga baya nan, ya zo zai fice sai ya ji magana a ɗayar ɗakin shine ya shigo. Cikin tsawa ya ce "Michael what brought this man in to your part...?!!" Bai gama rufe baki ba, idanuwansa suka sauƙa kan hawayen dake fuskar Michael ɗin, a zafafe ya kariso wajen yana faɗin "What happened Michael?" Shiru Michael bai yi magana ba, sai kukansa yake yi. Wani wawan damka Tga ya yi wa wuyar Musharraf, har sai da Musharraf ya ji kamshin lahira, wani irin mahaukacin tsawa ya daka masa "Me ka yi wa Michael yake kuka?!!" Musharraf ya kasa magana dan ba damkar wasa Tga ya yi wa wuyarsa ba, sai zaro idanuwansa waje yake yi. A fusace Tga ya ɗaga hannu zai wanka masa mari, cikin sauri Michael ya shiga tsakaninsu marin ta sauƙa a kan fuskarsa, ji kake yi tas, ihu Michael ya saki mai ɗan sauti, domin ƴunwar da yake ji, tasa sautin sa bata fita sosai. A sukwane Tga ya saki Musharraf ya fara shafa kumatun Michael ɗin yana bashi hakuri, kuka kawai Michael yake yi ya kasa magana. Tga ya yi ya yi amma ina Michael ya ki yi masa magana kukan sa kawai yake yi, daga karshe Musharraf ne ya yi karanbani muryar sa na rawa ya ce "Kayi hakuri ka ji Michael?" Juyawa ya yi ya kwantar da kansa saman cinyar Musharraf ɗin yana faɗin "Uncle ɗin James my stomach am feeling hungry over". "Okey tashi muje na baka abinci" cewar Tga. Dawo da kallonsa kan Tga ɗin ya yi "Uncle T I can't eat anything now" "Why?" Tga ya tambaya yana zaro ido Michael zai yi magana kira ya shigo wayar Tga dake aljihunasa, kin ɗaukar wayar ya yi dan a cewarsa koma waye ke kiran shi yanzu dole ya hakura domin shawo kan matsalar Micheal ta fi masa komai a yanzu. "Uncle T pic your call mana". Ya yi maganar cikin kuka, girgiza kai ya yi yana faɗin "No Michael ina son in ji me damuwar ka first tukun nan, kafin na ji na wasu kuma". "To uncle idan Lion ko kuma James ne suka kira ka fa?" Jin haka yasa ya ciro wayar a sukwane, ai kuwa Lion shine sunan da ya bayyana a kan screen ɗin wayar, a zafafe ya juya ya fice daga ɗakin har yana haɗawa da ɗan gudu, dan yasan Lion baya kiran layin kowa haka kawai sai da kwakkwaran dalili mai karfi, bare kuma yanzu da suke fama da case ɗin James ai dole ma su kasance tare. Yana shiga part ɗin Lion ya isko shi tsaye yana fuskantar balcony ɗakin nasa a cikin bedroom nasa kenan. Sanye yake da kayan sanyi yau, saboda sanyin yau ya yi yawa over, ya yi wa kayan kyau sosai, dan shi, shi yake yi wa kaya kyau ba kaya ke masa kyau ba, ya zura hannayensa a cikin aljihun wandon, a yayin da ya sanya hular rigar a kansa, kayan suna da laushi sosai, jikinsu kamar jikin mage, kun san Lion da son kalar farin abu, to wannan ɗin ma hakan ne, fari ne tas kamar yanzu ya cirosu daga ledarsu. Excuse Tga ya masa sannan ya tsaya daga ɗan bayan sa yana shakar daddaɗar kamshin perfume nasa dake tashi a jikinsa. Sun kwashi tsawon 10mins a haka kafin nan Lion ya fara magana ba tare da ya juyo ba. "General na karawa wayar James tsaro saboda bana son mutanen da suka kama shi su iya shiga cikin wayar nan, a yanzu sun kama shi ne saboda ya kashe musu mutane a takaice dai alakarsu na ta'addanci ne, idan kuma suka iya shiga cikin wayarsa suka yi bincike za su gane cewa ɗan uwana ne, daga nan za su masa hukumci biyu, bana son hakan ta faru saboda ina bukatar James a raye, da kai na nake son yi masa hukunci, gudun ire-iren wannan abin yasa nake sanya wa wayoyin gaba ɗaya yan gidan nan tsaro, ta yadda ba wanda zai iya bincikar wayoyin naku, zan yi tafi next week ka kasan ce cikin shiri a ko wani lokaci zan iya kiranka ka buɗe mini wayar James, kafin na tafi zan tabbatar na kutsa cikin nasu tsaron da suka sanya wa wayar, yanzu ku tashi kungiyar su dake India yau ɗin nan, na gama komai" yana kai karshen maganar ya juyo ya nufi hanyar shiga cikin balcony ɗin. Mamaki ne ya kama Tga, tunani yake yi ashe Lion ne yake rufe musu wayoyinsu ta yadda babu wanda zai iya bincikar wayar, lallai ma to a yaushe ya aikata hakan oho, yanzu ga shi ya rufe wayar James ba mai iya bincike a cikin wayar, su kuma wayan da suka kama shi sun ɓuye layin daga hanyar sadarwa ma gaba ɗaya, dan kada a gane location ɗin da suke a kama su. (Lallai akwai cakwakiya, ni dai na haɗa kayana zuwa wajen su Rimsha wato kasar Yarabawa) 💖💖Ilorin State💖💖 Kamar yarda Ahmad ya yi alkawari haka ya zo da asuba ya tashe su, Already ita Rimsha ta tashi tana zaune kan dadduma bayan ta ɗauro alwala, ta kwana tana sallah tana yi wa Allah godiya daya sanya zata koma gida. Bayan sun yi komai, sun shirya cikin abaya da hijabi, sun kuma ɗauki kayan su, har da takardun girkin Rimsha ba abinda ta bari, shi kuma ya ɗauki trolley guda biyun da ya kawo, ya sanya a bayar motarsa. Misalin karfe shida ya fita da su a motarsa zuwa airport. Suna isa airport ya yi musu passport da yake yana da goyon baya, ya samu alfarma sai aka yi musu komai cikin sauri, wayannan kananan trolley da ya shigo da su da daddare, su ya fitar daga bayan motarsa ya bawa ko wacce ɗaya. Har hawaye suka yi masa wajen nuna matukar godiyarsu a gare shi, murmushin kawai yake yi musu, amma shima a cikin zuciyarsa ba daɗi yake ji ba, domin ji yake yi tamkar zai rabu da wani sashe na rayuwar sa, kamar sun yi shikaru a tare. Sai da ya shigar da number wayarsa a wayoyinsu, sannan ya ɗauki number ko wacce ya tura musu kati daga Account ɗin sa, bayan ya gama ya basu wayoyinsu ya ce suyi saving numbersa da kansu, sai murna suke yi za su koma gida. Zama suka yi a ɗaki na musamman da aka basu suna jiran lokaci ya cika, dan an ɗaga tashin jirgin sai karfe 8 daidai, haɗaɗen abinci yasa aka kawo musu dan yin breakfast. Da farko sun ki cin abinci saboda tsabar murnar za su koma gida, ko yinwa basu ji, sai da ya matsa musu ya nuna ya ɓata rai sannan suka ci, fried rice ne ya ji kayan kamshi da kayan haɗi, sai ta shin kamshi yake yi. Kaɗan suka ci abincin sannan Ayla ta sha coca colar da aka kawo musu, ita kuma Rimsha ta sha ruwa kawai. Bayan sun kammala ne ya tsare Rimsha da ido yana kallon ta, sai faman sunkuyar da kanta kasa take yi tana wani ɗaure fuska, dan bata son kallon nan da yake yi mata, tun jiya da ta fahimci hakan bata sake yin murmushi a gaban shi ba. "Queen of beauty idan kika koma wajen mama zaki tuna ni kuwa?" Ya jefa mata tambayar yana mai do da kallonsa kan dogayen yatsun hannunta masu ɗauke da kyawawan kumba (farce) farare tas. "E zan tuna ka" wani nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe sannan ya ce "Amma idan ba damuwa ina son ki bani wannan sarka da na gani a wuyarki jiya, dan Allah ina son in samu wani abu da ya kasance daga wajen ki yake, dan na riƙe a waje na na rinƙa tunaki da shi". Wani dum-dum ta ji gabanta ya bada bugu, domin kuwa idan ba mutuwa ba bazata iya yarda wani abu ya rabata da wayan nan sarkokin ba, guda biyu ne a wuyarta, yan sirara, ɗaya na zinarin da gwaggo ta bata ɗayar kuma mum ɗinta ta bata, ba zata iya rabuwa da ko kwaya ɗaya ba. Ganin ta yi shiru ya sa ya fara rokarta da Allah, hawaye ta fara yi, yau ga wanda ya ceci rayuwarsu, kuma zai haɗa su da iyayensu, ya musu babban taimako arayuwa, yau yana bukatar wani abin a gare ta da ya kasance ba zata iya rabuwa da shi ba, innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Murya kasa-kasa ta ce "Yaya Ahmad ka zabi duk wani abin da kake so a tattare da ni, zan baka amma banda wayan nan sarkan". Dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali "Kome nake so kin yi alkawarin zaki bani?" Gyaɗa masa kai ta yi tana faɗin "E matukar bai saɓawa Allah ba". Ita dai Ayla ido kawai take binsu da shi. Murmushi ya yi kafin ya ce "Ki yi mini alkawarin zaki kaunace ni, ki yi mini alkawarin zaki bani soyayyar ki, kiyi mini alkawarin idan kin koma gida zaki sanar da su mamaki ina son ki, kiyi mini alkawarin ba zaki kula ko wani ɗa namiji ba, kada kuma kice mini a'a domin kece kika ce kin yi alkawarin na zaɓi ko me nake so zaki bani, to wannan shine abin da nake so". (Babbar magana) Kasan cewar batasan illar yin hakan ba, bata ma san menene soyayyar da yake magana a kai ba, kuma batun kula maza dama ba ta kula kowa, kananun shekarunta ya sata ta yi wani kuskuren da ba zai yi mata kyan gani ba gaba, haka ta buɗe baki ta ce masa "Na yi maka alkawari hakan" (Tashin hankali) Bata san wanene Ahmad ba, bata san daga ina yake ba, bata san shin mutune ko aljaniba, bata san cewa idan ya kasance aljani bata isa ta warware wannan alkawarin ba, bata san cewa ko mum ɗinta ta ji abin da ya faru ba makawa sai ta bawa Ahmad aurenta ba, a kananun shekarunta bata san duk wannan kuskure ta aikata ba, ita kan ta Ayla dake zaune tana kallonsu babu abin da ta sani game da hakan. A haka har lokacin tashin su ya yi, suka wuce ya raka su suka shiga cikin jirgi, yana ɗaga musu hannu har suka tashi, suna tashi ya canza mata sunan da ya sanya a number ta, daga Queen of beauty zuwa My wife. (Yau akeyin ta, *TRIPLETS* yanzu zai fara ɗaukan zafi, ku gyara zama dan jin yadda wasan zai kaya, yanzu muka fara ɗan kutsa kai cikin labarin. Ma'assalam, na barku lafiya sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu a airport na Kaduna) 💖💖TRIPLET'S💖💖 35-36 💖💖RIMSHA💖💖 Tun da suka shiga jirgi waya suke yi da Ahmad, domin jirginsu na tashi ba jimawa bayan ya koma gida ya kirata a waya, haka ta ɗauka sai surutu yake zuba mata, ban da E da a'a ba wani abin da take ce masa, da yake ya san halin ta ɗan zaman da suka yin nan, sai bai wani damu ba, ya cagaba da janta da hira har Allah yasa jirginsu ya sauka a airport lafiya. Suna sauƙa ya gaya mata in da zata tari mashin tace a kai ta, to kawai ta amsa mashi da shi, sannan ya bata daman sararawa wajen katse kiran. Bayan sun sauƙo suka rungumi juna da Ayla suna kuka amma haka kowacce ta ɗauki trolley ta, za su tafi sai suka ji magana daga bayan su. Cikin sauri suka juya ɗaya ne daga cikin ma'aikatan dake wajen, sannu ya musu suka amsa sannan ya ciwo kuɗi daga aljihunsa, ya kirga naira dubu ashirin-ashirin ya basu, kin karɓa suka yi saboda basu san shi ba, hakuri ya basu sannan ya kira Ahmad a waya ya haɗa su da shi. Rimsha ce ta karɓi wayar suka gaisa, Ahmad ya ce mata ta karɓi kuɗin mancewa ya yi bai basu ba, amma tun jiya ya ciro kuɗin a kan zai basu sai da suka zo tafiya ya manta, shiyasa ya kira waya airport ɗin domin a basu. Jin haka yasa suka karɓa suka yi godiya sannan suka sha kukan rabuwa da juna suka tafi. Ita Ayla ta hau mashin zuwa gida, ita kuma Rimsha zuwa tasha, Ayla taso Rimsha tazo su je gidan su, ko da a tsaitsaye ne Rimsha ta ga gidan su, amma ina Rimsha taki yarda burinta kawai ita ma ta isa ga nata iyayen, hakan yasa Ayla ta hakura suka yi bankwana. Lokacin da Rimsha ta je tashar kawo sai da ta tambayi ina ne wajen motar Katsina, wani bawan Allah ya nuna mata. Ganin yadda ake ta kallonta ya yi mata yawa ne yasa ya sayi face mask da ake saidawa a wajen, ta saya ta sanya a fuskarta. Lokacin da taje wajen motocin Katsina, ta yi Sa'a mutun biyu ya rage ake jira, Ahmad ya kirata a waya, shine take gaya masa saura mutun biyu mota ya cika, sai ya umarce ta da ta bawa driver wayar, ba musu ta nemi driver ta ba shi wayar. Nan suka yi magana da Ahmad ya ce da driver a tashi motar yanzun nan zuwa Katsina, ya kama mata kujeran gaba dukka ita kaɗai, ma'ana zai biya kuɗin mutun biyu dukka, to driver ya ce, sannan Ahmad ya rufe da cewa ya turo mashi account number sa bari ya sanya mata kuɗin motar, to ya ce sannan suka yi sallama. Miƙa mata wayarta driver ya yi ya ce ta rubuta Account number sa, yana karanto mata tana sanyawa, abin mamaki shine sunan GAR Rimsha ta sanya a matsayin password na wayarta, haka ta rubuta account number ta turawa Ahmad sannan driver ya buɗe mata gidan gaba na motar ta shiga ta zauna, ba ɓata lokaci a ka loda kaya, passengers suka shiga. Bai fi minti ashirin ba da zuwanta motan su ya tashi zuwa Katsina, lokacin da motan su zai tashi Ahmad ya kirata, suka fara hira. Haka zalika lokacin da motarsu ya tashi bai fi da minti biyarba, Ayla ta shigo park ɗin da sauri tana neman Rimsha tana kuka. Wani bawan Allah ne ya gaya mata motar Katsina ta tashi bai fi minti biyar da suka wuce ba. Zama tayi saman wani dakali a wajen ta kifa kanta da gwiwowinta ta ci kukanta mai isarta, ga kuma trolley ta a gefenta, kuka ta yi har na tsawon minti goma, sannan ta ɗago ta goge hawayen ta, ta fito da wayarta tana kokarin kiran Rimsha, sai taga ashe sun mance basu karɓi number juna ba. Tana hawaye ta kira layin Ahmad dan ya tura mata number Rimsha ɗin, shima Ahmad ɗin da kyar ta iya kiranshi, dan ba wani sanin kan waya ta yi ba, yanzu ma Rimsha ce ta koya mata wasu abubuwa kaɗan a cikin jirgi kafin su sauƙo. Lokacin da ta kira Ahmad yana waya da Rimsha kiran bata shiga user busy yake nuna mata, ta gwada yafi sau goma, daga karshe dai ta hakura ta miƙe sai kallonta jama'a ke yi, haka ta ja trolleynta ta fita daga park ɗin. Tana tafiya tana hawaye har ta hau kan titi ba tare da ta sani ba. Ji kake wani irin kara mai sauti ya tashi, wata mota ce da ta yi kokarin taka wani irin mahaukacin burki dan kada ta taka Ayla, amma duk kokarin da mai motarnan ya yi wajen taka birki, sai da motar ta ɗan bugeta kaɗan, Allah ya tsare ba wani ciwon da ta ji, faɗuwa dai ta yi kasa ta ɗan buga kanta da jikin bambam motar, trolley ta da wayarta suka faɗi kasa, ɗan gefe da ita. Kan kace me jama'a sun taru a wajen, mai motar ne ya fito cikin sauri yana faɗin "Ya subhanallah" daddyn Jelly ne da kuma Irfan, sune a cikin motar, daddy'n Jelly ke tuka motar, suna tafiya suna hira, amma hankalinsa yana kan tunanin in da jellyn sa take, bai ankara ba sai ganin Ayla suka yi a gaban su za su taka ta, Allah ya tsare daddy'n Jelly tsohon hannune a jan mota, ya yi kokari wajen taka birki. Sannu suka yi mata ta ɗan bugu, ta kasa yi musu magana, saboda wani jirijiri da take gani. Irfan ne ya fara tsugunawa a gaban ta yana faɗin "Kina cikin hayyacin kuwa?" Kasa magana ta yi, sai ido kawai da take binsu da shi, ga idanun nata cike da kwalla. Ɗagowa Irfan ya yi ya kalli daddyn Jelly "Bappa Maik ina ganin mu kai ta asibiti, da alama ta ɗan bugu, dan bata cikin hayyacin ta" cikin sauri daddyn Jelly ya ce tom ya ɗauko ta. Kamar yar baby haka Irfan ya ɗauke ta, daddyn Jelly ya buɗe masa gidan baya na motar ya sanya ta, sannan ya dawo ya ɗauka mata trolley ta, sai dai babu wayar har an samu masu dogon hannu sun yi gaba da shi, da yake su Irfan basu san da zancen wayarta ba, sai basu wani damu da duba wayar ba, suka tashi motar suka bar wajen. "Suna tafiya a hanya ne Irfan ya sake jarraba yi mata magana "Sannuki, ya sunan ki?". Da kyar ta iya buɗe baki saboda sara mata da kanta yake yi "Sunana Ayla". Ruwan faro dake gabansu ya ɗauka ya miƙa mata yana mata sannu. Ba musu ta karɓa ta sha, ba su kai ga isa asibiti ba, ta warware ta fara magana sosai. Koda suka je asibitin ma, lafiya lou da a ka dubata, ba wata matsala, sai dai yan magunguna da ba'a rasa ba, aka rubuta mata, Irfan ya sawo mata. Bayan sun koma cikin mota ne, daddy'n Jelly ya ke tambayar ta ina ne gidansu su mai da ita gida su bawa iyayenta hakuri. Jin wannan tambayar tasu bata san lokacin da ta fashe da kuka ba, juyowa suka yi a tare suna kallonta. Irfan ne ya fara tambayar ta lafiya take kuka, kasa magana ta yi, yana kokarin sake tambayar ta, daddyn Jelly ya dakatar da shi, ta hanyar ɗaga mashi hannu, shiru ya yi yana kallon yadda take kukan. Shiru suka yi suna kallonta, basu yi mata magana ba, kuma basu tada motar sun ta fi ba, tsawon minti talatin sannan fa, daddyn Jelly ya fara rarrashinta yana faɗin "Ya isa haka, kinga ai mun barki kin yi kukan ko, to yanzu ki huce haka, zuciyar taki ta ɗan sauka ki gaya mana me yake faruwa?". Sai da ta kara minti goma sannan ta iya buɗe baki ta gaya musu cewa, ita bata da kowa, kallon juna suka yi sannan suka dawo da kallonsu kan kayan da yake jikinta, gata tsabtsab, ga kaya mai tsada a jikinta, kuma ta ce bata da iyaye to fa, shi kam Irfan har da kallon trolley ta dake gefenta. Sake tambayar ta daddyn Jelly ya yi a kan ta natsu ta gaya musu ina ne gidan su. Ba wani ɓoye ɓoye ta basu labarin tun ranar da aka sace ta har zuwa yau da ta koma gida, bata ga mamanta ba, gidan ma an rushe shi ana sake yin wani ginin, ta tambayi mutane da dama a unguwar amma sai su ce mata su ma basu san in da maman nata ta yi ba, wasu suce ta haukace wasu suce ta mutu. Daddy'n jelly sarkin saurin kuka, tun da ta fara bada labari yake yi mata ruwan hawaye, har ta kammala. Domin su tabbatar da zancen ta sai suka wuce anguwar ta su, ai kuwa sun gani da idanuwansu, har gidan su Ayla da aka rushe sai da ta kai su suka gani da idonsu, sannan sun tambayi mutanen layi, abin da ta gaya musu na yadda yan unguwa ke faɗe, haka suka sake ji da kunnansu. Jin haka yasa daddyn Jelly ya fara tunanin ko dai ita ma Jellyn sa abin da ya faru da ita kenan, tuna haka yasa ya ce "Zaki iya sanin inane hanyar Daular Mutuwa take?" Girgiza masa kai ta yi ala'mar a'a. Kamar zai sake yin kuka haka ya tashi mota suka wuce zuwa gida tare da Ayla ɗin, sosai daddy'n Jelly bawan Allah ya shiga matsanancin tashin hankali, addu'a yake yi Allah yasa dai ba abin da ya faru da Jelly'n sa ba kenan, Allah yasa ba su kai ta can ba kenan. Ko da suka koma gida, a babban palon gidan suka zauna, domin yau suke shirin kaura zuwa sabon gidan da Abbi ya saya, sai shirye-shirye maman Aunty take yi, dan ita Aunty har yanzu bata wani iya tafiya sosai. Wayar da ya sake saya daddy'n jelly ya ciro daga aljihunsa tare da fito da hoton jelly wadda ya tura daga wayar Imran, ya nunawa Ayla hoton yana tambayar ta ko taga wannan a Daular Mutuwa, karɓar wayar ta yi tana kallon, kyakkyawar hoton Jelly, tana sanye da guntun wandon jeans iya gwiwarta, da kuma yar riga mai ƙaramin hannu launin pink color, ya rungume dollyn ta a kirjinta, sai murmushi take yi, ta saki gashin nan nata, ta yi kyau sosai. Girgiza masa kai Ayla ta yi tana faɗin "A'a gaskiya ba'a kawo wannan Daular Mutuwa ba" wani nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon Aunty dake ta faman kallonsu tana zaune. "Halima ga kanwa nan mun kawo miki, ba sai na faɗa ba nasan zaki riƙe ta da amana, dan Allah ki ɗauke ta tamkar yar uwa, zamu yi bincike a kan ina iyayenta suke amma sai mun gama da case ɗin Jelly". Da fara'a Aunty ta amsa da to, har cikin ranta kuma tana kaunar Ayla, da hannu ta mata nuni da ta zo, ba musu ta miƙe ta koma kusa da ita ta zauna, "Ya ya ne sunan ki?" Aunty ta tambaya tana kallon Irfan da yake ta fama da latsa waya. "Sunana Ayla" maimaita sunan Aunty ta yi tare da faɗin suna mai daɗi. "Irfan ina Aafia ne?" Sai lokacin ya ɗago ya kalli Aunty, dan baya shiga harkar ta ko kaɗan, idan kunga suna magana to wani abin ne take bukata, saboda yanzu Abbi kam sai addu'a ya dai na ko kallon in da take, ba kuma ita kaɗai ya juyawa baya ba, har da su Irfan ɗin, daddy'n Jelly da kowa da kowa, basu kawo cewa asiri aka yi masa ba, no sun bar abin ne a kan dan sun kafe masa a kan cewa Aunty ba zata aikata abin da yake tunanin nan ba, amma a zahirin gaskiya ba haka bane, asirin da Rufee ta yi masa ne ya sanya shi ya watsar da kowa da komai, sai tunanin Rufee kawai yake yi, ko ya fita company ma baya wani abu banda tunanin Rufee, ina take? Yaushe zai sake ganinta?, Aikin kenan kullun, shiyasa yanzu Irfan da daddy'n Jelly ke kula da Aunty, daddyn Jelly yana zama da ita yana bata hakuri ya yi ta tausanta, shi kuma Irfan da ta bukaci wani abin shi yake biya mata bukata, ya sawo ya kawo mata, iya shine kawai ke haɗa su, bacin haka baya shiga harkar ta, dan bai son reni, ya girmeta kusan da shekaru biyar zuwa shidda. "A'afia tana gidan bappa babba, amma zata dawo" ya bata amsa tare da miƙewa, shima daddy'n jelly miƙewa ya yi suka nufi waje suna kara gayawa Aunty da ta shirya anjuma zasu wuce sabon gidan. To ta bisu da shi, sannan ta kira mai aikinsu da Abbi ya kawo, a kan yazo ta shiga da Ayla ɗakin su Aafia ta je ta yi wanka ta huta, kafin a kawo mata abinci. Cikin hanzari mai aikin ta zo ta mata jagora suka tafi zuwa bedroom na A'afia. Sai da suka shiga Ayla ta ɗan zauna ta huta, sannan ta fara tunanin ina wayarta bari ta sake kiran yaya Ahmad dan ya taimaka ya tura mata layin Rimsha ta kirata ta gaya mata mamanta ta rasu, amma ina bata ga wayar ba. Cikin sauri ta buɗe trolley ta fara dubawa, wasu tsadaddun kaya ne a cikin trolley, dukka kuma dogayen riguna ne masu kyau, sai hijabai da kuma mayuka da turaruka, sai wani haɗaɗen plat shoe guda ɗaya, sosai ta wargaza kayar amma bata ga wayar ba. Kuka ta sa mara sauti mai tsuma zuciyar mai sauraro, hanya ɗaya da take da shi na yin magana da Rimsha, shikenan shima ya salwanta, idan ta tuna hakan sai ta ji zuciyarta tamkar zai fashe ya fito waje. Allah sarki wannan baiwar Allah akwai ciwo sosai a tattare da Rayuwar ta. Mai aikin da ta mata jagora tana nuna mata ta fice daga ɗaki, dan haka bata samu damar ganin kukan da take yi ba, saman gadon su A'afia ta kwanta, tana hawaye har barci ɓarawo ya yi awon gaba da ita, ga kayanta a watse, ko wankar bata sami damar ta yi ba, haka ta yi barci. A ɓangaren Rimsha kuwa. Sai wuraren karfe 2:30 suka isa Katsina. Suna isa ba ɓata lokaci ta tari abin hawa ta ce ya kaita unguwar farin yaro, domin kunnuwanta sun kasa mance mata da sunan unguwar, tun ranar da suka zo Katsina, ta kasa mance wa. Ana kaita ta sallami mai mashin, sannan ta sanya wayarta a silent ta nufi cikin anguwarsu tana jan trolleyn ta, dan a bakin daidai wajen da aka tare Jehan ranar, a nan mai mashin ya sauƙeta, duk da cewa bata san anguwar sosai ba, amma tana iya kar bakin kokarin ta wajen tuna hanya. Kasan cewar akwai face mask a fiskar ta hakan yasa jama'a wajen suke mata kallon wata ma'aikaciya, ga kuma kyakkyawar trolley a hannunta, abin ya kayatar, tana cikin hijabi har kasa. Tun daga nesa ta hango gidan su, saboda tsabar murna ji tayi tamkar ta zura a kuje ta karisa gidan, wani farinciki na musamman ne ya dira mata a ranta, duk da tana cikin face mask amma bakinta yaki rufuwa saboda murmushi da take yi, tsantsar farincike ne a tattare da ita yau. A hanzarce ta karisa wajen, turus ta tsaya ganin katon kwaɗo a jikin kofar, an rufe gidan, sakin trolley ɗin hannunta ta yi ta fara bubbuga kofar tana hawaye, tana surutai kamar haka ",Mummy, gwaggo, Jehan, ina kuka je? Ina kuka tafi kuka barni?". Abin gwanin ban tausayi Yusuf ne ya hangota daga in da yake tsaye a kofar gidansu, a tunaninsa wata ce can daban, sai ya kariso wajen yana tambayar ta waye take nema. A razane ta juya murya na rawa ta gaya masa, ga wayan da take nema, girgiza kai ya yi yana faɗin "Eyya ki yi hakuri ai sun barnan". Zaro dara-daran sleeping eyes nata ta yi har tana haɗe words wajen ce masa "Ina suka koma dan Allah, ka gaya mini, ni yarsuce". Cikin sauri ya ce "Ke ce Rimsha wace ta ɓata?" A hanzarce ta gyaɗa masa kai alamar E ita ce. "Allah sarki ai su mum sun sha wahala wajen neman ki, har suka godewa Allah, yanzu dai muje na kai ki wajen mamana ki zauna har yaya Sadiq ya dawo daga wajen aiki, wata kila shi yasan in da suka tafi, amma ni dai ban sani ba, domin shekaranjiya, yaya Sadiq da ya dawo da daddare yake ce mini ai su mummy sun bar nan, wlh bakina kuma ya mini nauyin na tambaye shi ina suka tafi". Sosai Rimsha ke kuka tana tunanin ina su mummy suka tafi. Jiki a mace ta bi bayan Yusuf, ya ɗauka mata trolley ta suka wuce gidansu. Sai kallonta yan unguwa suke yi. Ko da suka shiga gidan, sai kallonta Amarya da su Hanan suke yi. Kai tsaye ɗakin mamansa ya wuce da ita, kwance suka iskota saman yar katifarta. Sallama Yusuf ya yi mata sannan suka shige ciki, da kallo ɗaya maman Sadiq ta yi wa Rimsha ta gane yar mummy ce, domin idan baku mance ba, ita Rimsha babu in da ta bar mum a kamanni, ita kuma Jehan daddy ta ɗauko. Tarbar mutunci maman Sadiq ta yi mata sannan ta bata ruwa cikin sakin fuska. Rimsha ta kasa shan komai, abu biyu take bukata, na farko ta ji ina su mum suke, na biyu kuma ta je a wanke mata kannan nata ya yi datti sosai, tun ranar da ta wanke a gidan su Kausar bata sake samun dama ta wanke ba. Saboda tsabar ƙaguwa, ta kasa hakuri har sai da ta ce "Mama dan Allah ina su mummyna suke?" Cike da tausayinta ta ce "Kiyi hakuri yar nan su mummynki sun bar nan shekaranjiya, bayan an tafi da Jehan kenan". Kara zaro idanuwanta waje ta yi, cike da matsanancin tashin hankali mara misaltuwa ta ce "Mama ina suka koma?" Ajiyar zuciya maman Sadiq ta sauke kafin ta fara magana "E gaskiya dalilai biyu ya sanya suka bar nan, na farko an tafi da Jehan mummynku tana a halin rashin lafiya, to a ranar da aka tafi da Jehan ɗin a ranar mymmyn ku ta farfaɗo, kuma anyi sa'a ta farfaɗo cikin koshin lafiyarta, jin cewa antafi da Jehan sai ta ce ba zata yarda ba, baki nan ga mahaifinku baya nan, sannan Jehan yar ɗaya ɗayan ma a ce an tafi da ita, gaskiya ba zai yiwu ba, ya zama dole Jehan ta dawo, shine suka nemi aron waya suka kira number da matar ta basu bata shiga, suka je ɗakin jinyar da matar take jinyar yar uwarta, a nan ake gaya musu cewa, ai ba yar uwarta bace, ashe wai kanwar kawarta ce ke jinya tazo duba ta, da suka tambayi kawar a ina za su ga matar, sai ta ce musu ita ma bata sani ba, domin a online suka haɗu, address ɗin da ta rubuta musu ma, ashe address ɗin gidan su wannan kawar tata ce, shine fa hankalin su mum ya yi muguwar tashi ko in ce miki hankalin mu ya tashi, muna tsaka da Wannan tashin hankali kuma bayan na dawo gida na baro su a asibiti dan ba'a sallamosu ba, da daddare wasu mutane suka shigo gidan nan, hannunsu riƙe da bindiga wai suna neman Jehan da iyayenta, ba su kira sunan Jehan ɗin kai tsaye ba, amma kwatancen da suka yi ya tabbatar da Jehan ɗin suke nema, da kyar muka sha a gidan nan, dan sunce sai mun gaya musu ko kuma su kashe mu, ga shi mu kuma ba zamu iya gaya musu cewa mummy na asibiti ba, hakan yasa Sadiq ya ce musu ai su mummy sun gudu ne sun tafi Kano, shine muka samu muka tsira, washegari da asuba Sadiq ya je asibiti ya sanar da su mummy abin da ya faru da mu, shine fa daga asibitin basu dawo nan ba, gari na yin haske ba su ma jira sallama ba, suka bar Katsina, mu dai sun ce mana neman Jehan za su je yi". Tun da maman Sadiq ta fara magana Rimsha ke hawaye har ta kai karshen maganar, ta kasa yin shiru, tunani kawai take yi me Jehan ta yi suke nemanta, ko dai mutanen da suka kashe mata daddyn tane suka biyosu har nan. Tana tsaka da wannan tunani bata kai karshen ba ta yanke jiki ta sulale kasa sumammiya. (Nima kuma na tattare kayana zuwa Washington DC dan naje naga yaya baby Michael ya yi buɗa baki, sai mun dawo🛫🛬) Misalin karfe 5 na yamma, gaba ɗayan su zaune suke a palon kasa, ban da Lion and James su ba su nan, sai Michael da Musharraf, suma suna part nasu, Uncle Herry yana zaune ga hannunsa duk bandeji, yau aka dawo da shi gida ba jima, daddy zai cigaba da ba shi kulawa, ita kuma Jennifer yan uwanta sun ɗauke ta, uncle T yana zaune yana fama da laptop, da alama wani aiki mai muhimmanci yake yi, John yana rike da wayarsa yana kallo, Jay kuma dama kunsan yana word room yana fama da jinya, daddy kuma yana kishingiɗe yana kallo. Da kyar da kyar Michael ke sako kafarsa a benen yana saukowa palon kasa, dukkan su sun zuba masa ido, ban da John da ya kafe waya da ido, har daddy sai da ya miƙe zaune suna kallon yadda Michael ke wani irin layi kamar wadda yake cikin maye. Bai bi da kan kowa ba, ya wuce saman sofa, ya yi bismillahi a bayyane zai zauna, daddy da Uncle T ne suka daka masa tsawa a tare suna tambayar me ya ce, ko kallon in da suke bai yi ba, bare ma su saka ran zai basu amsa, ya yi zaman sa kusa da John, yana jin cikin sa na mashi ƙugin yunwa. "Michael na ji kamar kayi wani yare ne da zaka zauna yanzu" Tga ne ya tambaya, daddy kuma shiru ya yi yana maimaita kalmar bismillahi a zuciyarsa, domin shi ya ji abin da Michael ɗin ya ce. "Uncle T please leave me, i don't want to talk now". Kallon daddy uncle T ya yi yaga alamar daddy fa ya lula duniyar tunani ne. Michael kuwa yana kokarin kwanciya karaf idanuwansa suka sauka kan John, mamaki ne ya bayyana a kan fuskar sa, a zuciyarsa ya ce. "Wai nikam me John yake yi da waya ne, kullun ba shi da aiki sai latsar waya, sai ya yi shiru a waje, ba zaka taɓa jin motsin sa ba, tamkar baya nan". Yana zancen zuci yana karewa John kallo, kara zaro idanuwansa waje ya yi ganin yadda John yake wani mammatse jikinsa. Cikin dabara ya kai hannunsa ya fusge wayar John ɗin, ya kawota sai tin fuskar sa dan ya ga me John ke kallo. Shiru ya yi sumar zaune, gaba ɗaya palon kallon shi suke yi, suna so suji akan me ya kwace wayar John, amma ina ya kasa motsi, basu ankaraba kawai sai ganin wayar John ɗin suka yi ya faɗi kasa, alamar Michael ya sume musu awajen. A sukwane Tga ya ajiye laptop ɗin sa, ya taso da sauri ya zo ya taɓa shi yana faɗin "Michael are you okey?" Yana taɓa shi Micheal na sake masa jiki ka faɗo jikinsa. Jijjiga shi Tga ya fara yi sosai, tuni su daddy ma suka yo kansa, shi ma John ɗaukar wayar tasa ya yi ya yi kan Micheal ɗin, sai kiran sunan shi suke yi amma ina, sai da daddy ya ce a bashi ruwa domin Michael suma ya yi. Kwantar da shi Tga ya yi ya damko wuyar John yana tambayar sa menene a wayar tasa da ta sanya Michael suma, John ya ji shaƙa da kyar ya iya miƙa masa wayar a kan ya duba ya gani, dan shima bai sani ba. Tga na karɓar wayar John ya wuce da wuri ya je ya kawowa daddy ruwa dan a yayyafawa Michael. Yana kawo ruwa daddy ya karɓa ya buɗe tare da tarfo ruwar a hannun sa, Tga na kokarin duba wayar John, bai san lokacin da daddy ya zubawa Michael ruwa ba, sai dai ganin Michael suka yi ya tashi da sauri ya diro kasa daga saman sofar, yana haki kamar wadda ya yi gudu. Zuba masa ido suka yi har shi Tga ɗin, ya dakata da duba wayar ya koma kallon Michael, abin da ya basu mamaki shine, Michael na saukowa daga saman sofa sai ya fara ƙoƙarin cire wandon sa. Abin da ya faru abin da ya gani a cikin wayar John ta sanya shi suma, film ɗin batsa John ke kallo wato bf, tun da yake a rayuwarsa bai san da wannan ba, shi kwata-kwata ma bai taba lura me a cikin wandonsa ba. Bawan Allah bai san komai ba saboda ciwon nan nasa, amma yau sai ga shi ya ga abu muraran ga mace ga namiji tsirara, shine ya diro kasa dan ya cire wandonsa ya duba shin shima abin da ya gani a video a tattare da namijin nan shine a wandonsa ne ko yaya. Yau su daddy sun ga iko god, domin kuwa Michael dai ya ga abin da ya kwance masa lissafin ƙwaƙwalwarsa, cikin sauri Tga ya riƙe hannunsa yana faɗin "Michael what is wrong with you ne?". Kunsan Turawa basu da kunya ko kaɗan, a nan tsakar palo gaban kowa Michael ke son cire wandonsa dan ya duba. "Uncle T I want check something inside my trouser". "What is This that you want to check". Shiru ya ɗan yi kafin ya nunawa uncle T abin da ya gani da hannunsa, yana yi yana magana bawan Allah ya ce abin kato ne kamar hannusa. Kallon daddy uncle T ya yi dan ya gane me Michael yake son dubawa, shima daddy ya gane. Allah sarki ciwon Michael bata yi masa adalci ba, domin ko abin da yake cikin wandonsa bata bari ya iya samun damar sanin menene ba, bare kuma har aje ga sauran abubuwa, ashe ba abanza shi Micheal ya fi kowa ganin mace a matsayin katon gardi ba, duk da cewa dukkan su gidan kusan haka ne, idan ban da Jay ba wani mai wani tunani a kan mace, barema Lion da James sun fi kowa yi wa mace kallon namiji, sai dai su da lafiyarsu suke yi mata kallon da ita da namiji duk ɗaya ne, kuma bata da wani amfani, tsaɓanin shi kuma Michael na shi ya haɗu da ciwo, su ko dan saboda aikin da suke yi ma ba za su so ganin mace a kusa da su ba, James yana ta'addancin ina yake da lokacin mace, shi kuma Lion a yanzu dai baya wani aiki a matsayinsa na babba, sai dai ya sanya yara su yi aiki, amma ba shi da wani feeling a kan mace, kuma hakan ya samo asaline saboda tun baya lokacin da yake aiki sosai irin horon da ya yi wa kansa kenan, a lokacin ya tsani mum ɗin su over, lokacin zuciyar yaranta, hakan yasa ya tsani mata gaba ɗaya, yanzu kuma daya girma sosai ya mallaki hankalin kansa, ya rage tsanar da ya yi wa mum ɗin, saboda a cewarsa bashi da lokacin ta yanzu, to amma saura mata kuma yariga ya faro gininsa babu su a tsarinsa, sai ginin nasa ta tafi a kan hakan kawai, har wa yau, bai taɓa ɗaga ido ya kalli wata mace ba, saboda shi tun asalinsa in da yake tafiya nan kawai yake kallo, baya kalle kalle haka zalika baya son a kalle shi. (Mu koma cikin labarin mu) Sai kokarin cire wandon Michael yake yi, da kyar Tga ya dakatar da shi, amma shi ya dage sai fa ya ga me a wandorsa shi ma, tun da yau yaga zahiri, a saman wuya Tga ya ɗauke shi yana ƙoƙarin fara kewaye palon da shi dan ya lallaɓashi, kamar daga sama suka ji daddaɗar kamshin perfume nan, wadda mutun ɗaya ke amfani da shi. Cikin sauri Tga ya sauƙe Michael gaba ɗayan su suka natsu, ban da daddy duk kan su sun kasa ɗaga ido su kalli saman benen, domin ganin fuskarsa a wani yanayin gara maka ka kalli fuskar Tiger a tsakiyar dokar daji, kuma dama ba ko wani lokaci suke iya kallonsa idan sun ji kamshin perfume nasa ba, domin idan ka sake ka kalleshi ka bari kuka haɗa ido tofa kai kam ka shiryawa hukunci, dan kwata-kwata baya son kallo a rayuwarsa. Sai wani nuku-nuku suke yi, suna son sanin shin su yake kallo ne ko kuma dai ya aka ciki, shi John ya fi kowa shiga tashin hankali da ruɗu. Michael zama ya yi yana turo baki, ɗan wannan hirar da ya yi a palo, tasa ya rage jin yunwa. Lion ya jima tsaye yana kallonsu yana tunanin irin hukuncin da ta dace da su, bf kuma a gidan nan, abin ya ɓata mashi rai, yana kwance a saman bed nasa a ɗaki ya ga abin da suke yi a cikin Tv, amma hakan kuma da suka yi ya ɗan sa ya fahimci wani abin dangane da ciwon Michael, ya lura kamar sarrafa Michael ake yi, wasu abubuwa ba yin kansa bane, saboda yanzu zaka iya ganin Michael tamkar cikakken mutum anjima ka ganshi kamar a birkice, yau da Michael ya ce bai san asalin me a wandonsa ba, kuma bayan yana wanka abin ya ɗan bawa Lion mamaki, ya kuma kara darsa ayar tambaya a kan Micheal ɗin sosai. Sun kwashe 10mins a haka kafin ya ce da Tga ya hukunta John yadda ya kamata, shi kuma Michael yazo su wuce ɗaki. Cikin sauri Michael ya miƙe ya bi bayan sa, shi kuma Tga da yanzu ya gane me Michael ya kalla a wayar John sai ya fara da fasa wayar sannan ya ɗauki John a kafaɗar sa suka fice waje. Yin hakan da John ya yi a wajen Turawa ba laifin bane, amma su a tsarin gidan su, laifi ne, domin ko Lion baya nan, Tga sai ya hukunta John, saboda su basa son ire-iren waɗan nan abubuwa, kuma Lion bai shiga hakkin kowa ba, ya ce duk mai son aure ya yi magana ayi mashi, kuma yana yin pastor ko in ce yana yin church da suke bi, basu yarda da ganin ire-iren su Bf ba, domin a Kristen ɗin ma, ko wani church da abin da suka fi bawa karfi, to su church nasu bai yarda da yin hakan ba, domin sun san biyawa kai bukata babbar illace ga lafiya, hakan yasa suka tsawata, bayan kuma an tsawatar a church daddy ma ya kara tsawatar musu a gida, da yake sun rena daddy shine shi John ya aikata. Lion kuwa suna shiga bedroom nasa Micheal ya yi maza ya haye bed, domin yanzu ya fara mancewa da zancen yunwa da yake ji. Dama Lion yana da aiki a gabansa, dan haka sai ya ɗauko laptop nasa, ya zauna a saman bed ɗin kusa da Michael, bayan ya kunna laptop ɗin ya gama komai ne ya ɗauko ɗaya daga cikin watch nasu na Triplets, A hankali ya zaro memory's ɗin, ya ciri guda ɗaya ya sanya cikin system ɗin, videos sosai ya fara cin karo da su, kan vedio na farko ya fara dannawa ya yi Play, Michael na kwance a gefensa kamar a mafarki ya ji muryan James a cikin video yana faɗin "Idan ka je lahira ka sanar da su Roshan ni na kashe su" a sukwane Michael ya miƙe zaune yana kallon system ɗin, ya yin da shima Romeo ya kafe video da idanuwansa, James ne ke tsaye a gaban camera daya kunna da kansa, ya na riƙe da gashin wani dattijon Bature, wadda da ka gan shi ka san mutumin kirkine dan ya yi shigar mutunci, kuma da alama yana da mukami a gomnatance, sannan kuma ya tsufa dan zai kai 50 to 55 years haka, sai hawaye mutumin nan yake yi, ga shi ba halin ya yi magana domin James ya ɗaure masa bakin sa, sai dai hawayen sa kawai zaka gani, abin tausayi. Babu tausayi babu imani da iya karfinsa James ya sanya wukar dake hannunsa mai bala'in kaifi ya yanka wuyar mutumin nan, sai jini ya fara feshi kamar fanfo. Ihu Michael ya kurma yana faɗin "No this is not my blood, wannan ba shi bane wani ne mai kama da James" Romeo kuwa ko a jikinsa dan kisan da ya fi wannan muni ma ya saba gani, shi ba ma James yake kallo ba wani tambari hoto dake bayan su yake kallo, yana son gane wace kungiya ce, ihu da Michael yake yi kamar zararre ne ya sanya shi juyawa ya daka mashi tsawa a kan ya yi mashi shiru, yana takura mashi yana aiki. Tsabar tsorata da tsawar ta sanya Michael sumewa a wajen. Bayan James ya yanka mutumin sai ya ɗauko fake face na sa ya sanya sannan ya wuce ya kashe cameran. Video na biyu lion na sake yin playing, a nan ma dai James ɗin ne ke zaune a sansanin su na yan ta'adda, sai dai a wannan video da fake face a fuskar sa, yana zaune suna haɗa boma bomai, wasu gunguma gumguman yan ta'adda ne a cike a wajen, mai ɗaukar su video yana bin su ɗaya bayan ɗaya yana basu hannu suna dunkule nasu su bugi na juna. Ko da yazo kan James ko kallon in da yake James bai yi ba, sai faman haɗa bom nasa kawai yake yi, ga tarin wayoyin lantarki a gabansa, idan ka kalli James a wajen, ya saje da su, barema da ya sanya wannan fuskar robar tasa, ba zaka taɓa cewa shi ɗin bane, ya shige cikinsu sun saje da juna, sai famar aiki yake yi, ba dan Lion ya kalli video na farko, ya kalli yadda James ya sanya fake face ɗin ba, da shima ba zai gane fuskarsa ba, sai dai ya gane shi da jikinsa. Karewa mutanen wajen kallon Lion ya yi, suna nan kamar wasu yan yinwa, ya faɗa a ransa, kuma haka ne, a kaidar ta'addancin akwai kuɗi amma ba damar su iya zama suci kuɗin nasu, kullun suna cikin fargabar za'a kawo musu hari dan ɗaukar fansa, kullun tunanin yadda zasu farmaki waje kaza suke yi, dan su zama don a kasa, abincin kirkima basu iya zama su ci. Fita daga video lion ya yi ya sake shiga wani, nan kuma James da kansa yake ɗaurawa kananan yara bom a jikinsu, yaran da basu fi 15 years ba, runtse ido Lion ya yi ya fita daga wannan video, gaba ɗaya ya zare Memory ya ajiye ya ɗauki ɗayar ya sanya, bayai ne a kan ta'addancin, da kuma kungiyoyin da James ya kai wa hari ya taɓa su, ya kashe musu mutane, jerin kungiyoyin Lion ya zubawa ido yana kallon, manya-manyan kungiya uku James ya kaiwa hari ya kuma kashe wasu daga cikinsu, kuma dukka mai gidansa ya sanya shi wannan aiki, shiru Lion ya yi yana tunanin dole a cikin wayan nan kungiya ukun ne ɗaya suka kama James dan ɗaukar fansa, to su waye? Bashi da isashen lokacin da zai yi bincike a kan ko wace kungiya, hakan yasa ya yi watsi da su gaba ɗaya ya cire memory ma gaba ɗaya ya zube su cikin drawer, dan ba abin da za su kara masa sai zafin kai, dama idan baku manta ba, shi Lion baya karɓar taimakon kowa, aiki da ƙwaƙwalwarsa kawai yake yi, dan hakan yasa ya yi watsi da wayan can, a cewarsa faɗuwa ce ya karɓi taimakon wani, dan haka sai ya cigaba da aikin da nasa ƙwaƙwalwar kawai ba tare da ya dubi wani taimako daga wani wajen ba. Michael kuwa ba shine ya farfaɗo ba sai karfe 7 nan ma Lion ya fito palon kasa ne ya cikaro da Tga a Palo, sai ya bashi umarnin a kan yazo ya zubawa Michael ruwa. Yana farfaɗowa, da sunan James a bakinsa ya farfaɗo, sosai Tga ya rinƙa rarrashin shi yana lallaɓa shi, da kyar ya hakura ya miƙe ya nufi part nasa. Nan ya isko Musharraf yana buɗa baki, zama ya yi a kusa da shi yana faɗin "Uncle ɗin James lokacin cin abinci ya ne?" Gyaɗa masa kai Musharraf ya yi sannan ya ce "Tun ɗazun na fita na nemeka a palo ban ganka ba, shine na haɗo tea da kayan fruits nace bari nazo na yi buɗa baki na". Miƙewa ya yi ya nufi hanyar fita yana faɗin "Kazo muje palon kasa mu ci abinci mai kyau". Kasan cewar Musharraf yana son Michael sosai kuma bayan son ya ja baya da shi, hakan yasa ya amsa da to kuma ya miƙe ya bi bayan shi. Abin mamaki yau zaune a saman dining table suka isko Lion, abin da ba su taɓa gani ba, Lion da cin abinci karfe 7 basu taɓa gani ba, har su kansu bodyguards ɗin sun sha ruwan mamaki, domin wani lokaci abincin dare sai karfe uku yake ci, wani lokaci ma haka yake kwana bai ci komai ba, barema yan kwanakin nan kwata-kwata baya wani cin abinci. Musharraf bai taɓa zama a saman dining table nasu ba sai yau, ganin Lion ya sa ya sha jinin jikinsa, ji ya yi tamkar ya koma ɗaki, amma ba hali, domin sun riga sun fito idan ya koma Michael ba zai ji daɗi ba. Kusa da Lion Michael ya zauna yana faɗin "Good evening Lion" tamkar babu shi a wajen, haka Romeo ya kasan ce, ko kallonsu bai yi ba, fruits kawai yake sha, cikin class da kwantatciyar hankali. "Uncle ɗin James me zaka ci?" Cewar Michael, ɗan satar kallon Romeo ya yi, yana son cewa zai ci komai amma banda namar da Allah ya haramta idan suna ci, shi baya ci, amma kuma yana tsoron faɗin hakan, dan James ya ce masa kada ya yarda ya bari su gane cewa shi musulmi ne. "Uncle ɗin James why kayi shiru talk now?". Musharraf ya rasa me zai ce, yana tsoron ya ce a bashi komai, azo a zuba masa abin da Allah ya haramata ya ci ba tare da ya sani ba, sannan yana tsoron ya ce kada a saka masa abin da Allah ya haramta ya jawo baban yaki a gidan. Ganin haka yasa Michael ya ce da bodyguard ɗin su haɗa masa tea kawai, Lion na jin duk abin da suke yi, sai dai ba su isheshi kallo ba ne, dan kallonsu ma ɓata masa ido za su yi. Bayan bodyguards sun haɗawa Musharraf sun miƙa mashi, shi kuma Michael ya fara ɗura fruits yana shan ruwa mai sanyi. Ya ji yunwa sosai bawan Allah. Bai wani ci sosai ba ya fara kwarara amai a wajen kamar menene, cikin sauri bodyguards biyu daga cikinsu suka yo kansa, shi kuma Lion zame hannunsa ya yi daga kan fruits da yake sha, ɗaya daga cikin bodyguard ya miƙa masa tissue, ya karɓa ya goge ɗan bakinsa tare da hannunsa, sannan ya juyawa su Michael baya tare da ɗaukar wayarsa dake gefensa ya fara latsawa. Cikin yan mintuna kalilan sai ga Tga, kusa da Lion ya zo yana faɗin ga shi nan, da hannu Lion ya yi masa nuni da Michael ba tare da ya yi magana ba, sannan ya miƙe ya bar wajen. Da sauri Tga ya ƙarisa wajen Michael ɗin yana tambayar bodyguards ɗin lafiya me ya sami shi, cikin girmamawa suka ce suma basu sani ba, Musharraf yana son zuwa ga Michael amma yana tsoro, da farko saboda Lion na wajen yasa bai karisa wajen Michael ɗin ba, lokacin da Lion ya tafi kuma Tga ya zo, hakan yasa ya hakura kawai yana ganin Tga ya saɓi Michael suka wuce sama. Kai tsaye toilet ya kai shi, sannan ya fito ya kyaleshi, da kyar ya iya yin wanka saboda ya galabaita sosai, yinwa ya ke ji over, ga shi ya zo ya sha ruwa mai sanyi da fruits shiyasa ya yi amai. Ɗaure da towel a kugunsa ya fito bayan ya yi wanka, pajama kawai ya sanya a jikinsa, ya lallaɓa ya fito palon kasa. Bai ga Musharraf ba, kuma bai damu ba, dan yasan ya tafi ɗakin sa ne, saman table ɗin ya sake komawa, domin yunwa yake ji, already bodyguard ɗin sun gyara ko'ina fes, sun goge amai ɗin sai tashin kamshi wajen yake yi. Zama ya yi tare da basu umarnin su haɗa masa coffee mai zafi, cikin hanzari suka haɗa masa, yau ba shan salo da class, tun da ya kafa ɗan bakinsa a cup ɗin bai sauƙe ba har sai da ya shanye tas, wani daɗi ya ji, lokacin da ya ji cikinsa ta yi ɗumi. Miƙewa ya yi dan ya kasa iya sake cin komai. Yana kokarin hawa saman bene suka haɗu da Tga yana sauƙowa, nan fa Tga ya ce ya wuce su tafi word room a duba lafiyarsa. Tirjewa ya yi ya ce shi lafiyarsa lou dan haka babu in da zai je, ba yadda Tga ya iya haka ya hakura ba dan yaso ba, sai dan baya son su yi jayayya, dan ya san Triplets gaba ɗayansu ba mai magana ya sauya, ɗan gara shi Micheal ɗin ma, idan abu ya zo da matsala yana iya sauya magana, amma Lion da James ko uban matsalane basu taɓa sauya magana sai dai ayi wace za'a yi, sai dai a mutu. Wucewa Part nasa ya yi, kai tsaye bedroom ɗin Musharraf ya shiga. Sallah ya isko Musharraf yake yi, saman gado ya haye yana kallonsa. Bayan ya idar ya yi addu'a ne ya ce "Michael sannu ko" dogon numfashi Michael ya ja tare da saukewa a hankali. "Uncle ɗin James gobe zan saka John ya karo maka wasu kayan sawa, dan na lura wayan da James ya saya maka basu da yawa sosai" murmushi Musharraf ya yi yana zuba mashi godiya. Saukowa kasa Micheal ya yi, ya zo ya zauna suna fuskantar juna, a nutse ya ce "Uncle ɗin James, idan kana yin wannan abin da ka yi yanzu yana burgeni sosai, ko zaka koya mini ne?" Cikin sauri Musharraf ya ce mashi "Sallah kake nufi?" Gyaɗa kai ya yi yana faɗin "Wannan abin da na shigo na sameka kana yi yanzu". Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Michael ba'a yin Sallah sai idan mutun ya kasan ce musulmi ne, azumin ma da kaga na barka ka yi saboda nasan kuma kuna yin shi ne, a addinin ku ya halakta, amma shi Sallah wanda ya musulta ya karɓi Kalmar shahada ne kawai yake yin shi". Shiru ya ɗan yi kamar mai tunani, can kuma sai ya ce "To shi me ma kace? Idan za'a shigeshi kuɗi za'a bayar ne ko me?" girgiza kai Musharraf ya yi alamar a'a, sannan ya ɗora da cewa "Musulunci ba'a shigar shi da kuɗi, kyauta ne". "To ko ma da kuɗin ne ni ka shigar da ni ina so, kuma ina da kuɗi a account na sai na sanya a ciro maka, idan ma yanzu kake so sai na je ɗakin Lion na ɗebo maka, dan shi yana ajiye kuɗi sosai a ɗakin shi". Tsabar daɗi Musharraf bai san lokacin da ya riƙe hannayensa ba, cike da farinciki ya ce "A'a Michael kyauta ake shiga musulunci, kuma yanzu zan saka ka, amma fa sai ka mini alkawarin ba zaka taɓa gayawa kowa ba, kuma ka yi mini alkawarin duk abin da na koya maka zaka ɗauka kuma zaka rinƙa amfani da shi, sannan ba zaka gayawa kowa ba". Cikin sauri Michael ya amsa da ya yi alkawari zan rinƙa rike komai da za'a koya mashi, sannan kuma ba zai taɓa gayawa kowa a gidan ba, kuma zai rinƙa yin duk wani abin da Musharraf ɗin ya ce masa ya yi. Daɗi a wajen Musharraf ba'a magana, duk da cewa dama yasan Michael ba zai yi wuyar karɓar addinin musulunci ba, saboda a halin da yake ciki yanzu ƙwaƙwalwar sa babu komai na kin wata addini a cikinta, sai ma son mutane dake cikinta. Babu tunanin me zai je ya zo, babu tunanin abin da zai iya fuskanta, ya mance gidan William jacop yake, a tunaninsa Michael zai iya riƙe sirrin, cikin sauri ya yanke hukuncin bawa Michael kalmar shahada, shi kuma Michael cike da murna ya karɓa ya maimaita, sau uku yana maimaita wa, ya ce kalmar ta mashi daɗi over. (Babbar magana, yau ake yin ta, shin kuna tunanin Michael zai iya rufe wannan sirrin? Kuna tunanin Michael zai iya addinin musulunci? Zai iya Sallah sau biyar a rana? Ya batun tashi sallar asuba? Zai iya kuwa? Zai iya azumi? Sannan zai iya yin basaja, a cikin gida ya nuna musu shi Kristar ne a wajen Musharraf kuma musulmi? Kada ku mance Michael baya karya, bai iya ba kuma bai taɓa yi ba, in fact bai ma san yadda akayi ba, ya ya kuke ganin wannan cakwakiya zata kasance? Yau ake yin ta, ni dai sai dai na ce Allah ya jiƙanka Musharraf) Farinciki yasa Musharraf ya ringume shi yana hawayen murna, shi Micheal bai ɗauka wani abin arziki ya yi ba, sai bai wani damu ba, mamakin farincikin da Musharraf yake yi ma ya yi. "Michael daga yau na canza maka suna zuwa Aryan" turo ɗan bakinsa ya yi ya ce "Ni uncle ɗin James bana son Aryan, ba bu daɗi sunan, why zaka canza mini suna ma tukunnan?" Fuska ɗauke da murmushi Musharraf ya ce "Ai dole na canza maka suna, domin sunan ka ba na musulmai bane, kai kuma musulmi ne yanzu" jinjina kai ya yi yana faɗin "Okey tom ka nemo wani suna banda Aryan kam, dan Aryan babu daɗi" shiru Musharraf ya ɗan yi, na yan mintoci kafin ya ce "Yauwa to Asif ya yi maka?" Gyaɗa masa kai ya yi alamar E ya yi mashi. Yau farinciki a wajen Musharraf ba'a magana, shi kuma Michael mamakin ganin Musharraf a hakan ya jefashi cikin tunani. Suna zaune a wajen har lokacin sallar isha ya yi, a tare suka shiga toilet suka ɗauro alwala, Musharraf ya nuna masa yadda ake yi. Bayan sun fito, Musharraf ya yi kokarin nuna masa yadda zai yi sallah, nan fa ya ce aa ai yasan yadda ake yi, abin da dai ake karantawa ne bai sani ba, amma yana kallon friend ɗin James yana Sallah, bayan haka kuma a school nasu akwai musulmai da suke sallah yana gani. Musharraf bai da mu ya ce to ya kwatanta masa ya gani, haka kuwa ya kwantanta, kaɗan ba yawa Musharraf ya ci gyaranshi sanann ya yi musu jagora ya tada Sallah in da ya ce duk yadda ya yi shima Michael ɗin haka zai yi, ba sai ya karanta komai ba tun da bai iya ba. Sun yi Sa'a har suka idar da sallah ba wanda ya shigo cikin ɗakin, bayan sun idar da sallah ne, Musharraf ya zauna ya fara koya masa wasu abubuwa daya kamata ya fara iyawa (To fa me kuke tunanin makomar Musharraf idan har zakunan gidan suka gane ya musuluntar da Michael wato Asif a yanzu? Hmmmm a kwai dai chakwakiya, ni dai na haɗa kaya na domin na je na gani ya Rimsha take, ta farfaɗo ne ko yaya) 💖💖NIGERIA 🛬💖💖 💖💖KATSINA STATE💖💖 Cike da tashin hankali maman Sadiq ta zuba mata ruwa, bakin ta ɗauke da kalmar shahada tare da salatin annabi ta farfaɗo. Baiwar Allah zuciyarta tamkar zai buga ya faso kirjinta ya fito waje. Hakuri maman Sadiq ta yi ta bata, haka ta hakura ya zata yi, a halin da take ciki yanzu mutuwa shine abinda kawai ta fi buƙata, a cewarta ta ga ji da wannan bakar rayuwa mai cike da bakinciki. After some hours👌 Bayan ta ɗan warware, har wanka ta yi, sannan ta nemi Yusuf da ya rakata wajen da ake wanke kai, gashinta ya yi datti sosai zata wanke. Nan Yusuf ya sanar da ita sai sun shiga cikin gari sannan za su samu shagon wankin kai. Buɗe trolleynta ta yi ta sanya wayarta a ciki sannan ta ɗauki hijabinta har kasa tare da face mask ɗin ta suka tafi bayan sun sallami maman Sadiq kenan. Ahmad ya kira wayarta dan ya ji ko ta isa lafiya, amma ina shiru bata ɗauka ba, ya mata miss call ya kai goma, ta sanya wayar a silent bata ji ba, ya shiga damuwa sosai, sai tunani yake kadda ace wani abin ne ya sameta a hanya, ya yi kokarin kiran layin Ayla, amma a kashe, daga karshe dai ya hakura zuwa dare ya ce sai ya sake gwadawa. Ita kuma Rimsha kuɗin mashi ta biya musu zuwa cikin gari. Da suka je, a cikin kuɗin da Ahmad ya basu 20k ɗin nan, a ciki ta zari 2k ta biya aka wanke mata, dark black curly hair ta, ba karamin kyau ta yi ba, daga nan suka wuce wajen gyaran kafa, bata yi wani tunani ba kawai ta hau kashe kuɗin hannunta a wajen gyara, har da wani cewa a mata kunshi, ai kuwa kunshi mai kyau suka mata suka karɓi 3k, ta yi kyau kam iya kyau kamar ka saceta ka gudu da ita. Rimsha tana bala'i son gyaran jiki da sauransu, tana da bala'i tsabta, ko nawane zata iya kashewa a kan gyaran jiki, haka ita ma Jehan akwai ta da bala'i tsabta, sai dai Rimsha ta fita. Bayan an mata komai ta fito tsab, sai ta ce da Yusuf su tafi, shi kuma duk in da ta je yana biye da ita, haka kawai ta burge shi, saboda tafi jehan saukin kai da girmama mutane, domin kuwa ita tun farkoma yaya ta kira shi, saɓanin Jehan da take ce musu dirty boys. Kamar yadda suka zo haka suka koma a kan mashin, sai dai kowa da na shi mashin ɗin, naira 7500 Rimsha ta kashe, wankin kai da gyaranshi 2k, wankin kafa da yanke kumba (farce) shi kuma 1500, kunshi 3k sai kuɗin mashin zuwa su biyu 500 komawa ma 500 saboda kowa da mashin nashi. Suna komawa gida suka isko maman Sadiq a kitchen tana ta faman hura wuta, ɗaki Rimsha ta shiga ta cire hijabinta tare da yafa gyalen abayar jikinta ta fito ta kama wa maman Sadiq aiki, ta fara share tsakar gidan. Sai mamaki maman Sadiq take yi, sai tambayar kanta take yi ya akayi Rimsha ta iya aiki Jehan bata iya ba, kuma Jehan ce babba, sai dai babu mai bata wannan amsa, haka ta share zance ta ce da Rimsha ta koma ɗaki ta zauna, kada ta damu zata yi aiki, kin yarda Rimsha ta ya, ba yadda maman Sadiq ta iya haka ta kyaleta ta kama mata aikin. (Nikuma na tattare kayana sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu a gidan Abba, wato wajen yaya Akil🙃 amma dai kawai cakwakiya, yanzu muka fara shiga cikin ainahin labarin, sai ku gyara zama Ma'assalam✍️🥱) Kafin na tafi bari na yi muku tambaya, wace ce Hajiyar da ta ɗauki Jehan? Ina kuma ta kai ta? Me yasa ta ba su address na karya? Me hakan yake nufi? Ina su mum suka tafi? Ya makomar Rimsha? Ina jiran amsa. 💖💖TRIPLET'S💖💖 37-38 💖💖GIDAN ABBA💖💖 Aafia suna shiga ɗaki, Akila ta ce mata tana zuwa bari ta ɗebo ruwan zafi ta haɗa mata tea, ai kuwa Akila na fita Aafia ta tashi cikin sauri ta lallaɓo zuwa palon su Akil, kamar wata ɓarauniya haka take tafiya. Tana shiga ta ɗauki wayarta dake saman sofa cikin sauri ta fice. Tana komawa ɗakin Akila ta fara neman layin Rufee. Ai kuwa kamar jiran kiran Rufee take yi, bugu ɗaya ta ɗaga, murya kasa kasa A'afia ta ce "Kiyi hakuri Rufee, gobe zamu haɗu a school kin ji?" Daga ɗayan ɓangaren Rufee ta ce "Ba komai kada ki damu, yanzu dai abin da nake so da ke ki turomin hoton wannan da ya bugemun nan idan kina da shi" to A'afia ta amsa da shi, sannan suka yi sallama, cikin sauri A'afia ta shiga WhatsApp ta tura mata duka wasu hotonan Akil da take da su a wayar. Bayan ta kammala ta ajiye wayar ta kwanta tana tunanin yadda za'ayi ta iya zama a wannan gida tare da Akil, dan ta san takura mata zai yi, saboda ya fi yaya Irfan tsanani, ya fi su Imran duka tsanani, gara Imran sau dubu a kanshi, shine karami amma idan ranshi ya ɓaci, Imran da yake babba ma lallaɓashi yake yi, yana da bala'i zuciya sosai. A wannan yanayin Akila ta dawo ta sameta, saman bedside drawer ta ajiye cup ɗin kakkauran tea din da ta haɗa mata, sannan ta ce "Aunty Aafia ki ta shi ki sha kin ji ko?" Tamkar da gunki Akila take yi, Aafia ta ki kula ta, ko sannu bata ce da ita ba. Allah sarki Akila baiwar Allah, ta yi tunanin ko dai A'afia bata ji me ta ce da kyau ba ne, sai ta sake maimaita maganar. Tsawa A'afia ta daka mata wadda ya sanyata wucewa ta fice daga ɗakin. Kallon banza Aafia ta bita da shi, har ta kurewa ganinta, sannan ta ja dogon tsaki tare da runtse ido, a cikin zuciyarta tana jan wa Akil Allah ya isa na dukan da ya yi mata. After some hours👌 Bayan sun ci Abinci dare sun kammala komai sun kwanta, Aafia tana tsaka da barci ta ji wani bala'i yunwa ya addabawa rayuwarta, cikinta sai kugi yake yi mata, har wani irin murɗa mata yake yi, ba shiri ta tashi zaune a tsakiyar gadon, wutar ɗakin a kashe ko ina duhu, hakan yasa ta laluɓi wayarta dake saman bedside drawer, ta kunna hasken. A hankali ta zuro kafafunta kasa tare da sauƙowa gaba ɗaya daga saman gadon, sannan ta nufi palo. Ko da ta je palo ba kowa, kai tsaye wajen switch ta nufa ta kunna wutar, nan take haske ya gauraye palon baki ɗaya. Saman table ta nufa, abin mamaki abinci ne a jere kala-kala a saman table ɗin, jolof rice, white rice and beans with steew, ga su indomie ne, gasassun kaji, ga soyayyu a gefe, abinci dai kala-kala, kuma dukka anyi serving nasu a cikin plate, sai ta shin kamshi suke zubawa kamar me, Saboda tsabar yunwa dake cinta, cikin hanzari ta zauna tare da ɗaukar spoon, cikin natsuwa ta fara cin jolof rice, wani irin ɗanɗano na musamman ta ji a bakinta, lokacin da ta kai abincin, ɗanɗano ne wadda bata taɓa jin mai daɗi irin shi ba, har wani lumshe idanuwanta take yi, abincin ya yi daɗi over. Cikin natsu take cin abinci, tana tsaka da ci ta kware ta fara tari, kamar daga sama wani kyakkyawar hannu ya ɗauko wani kyakkyawar glass cup mai ɗauke da ruwan sanyi dake wajen, ya miƙa mata, sai faman tari take yi, ganin an miƙo mata ruwa yasa ta karɓa cikin sauri ta kafa a bakinta ta fara sha. Shi kanshi ruwan wani irin ɗanɗano ne mai zaki ga daɗi, tas ta shanye ba tare da ta sani ba. Bayan ta shanye, sai ta ci-gaba da cin abincinta cikin kwanciyar hankali. Da zarar bakinta ya ɓaci za'a sanya tissue a goge mata, kwata-kwata bata yi tunanin waye mai mata hakan ba, bata ma san ana yi mata ba. A ɓangaren su Ammie kuwa, tana tsaka da barci ta ji ana taɓa ta, cikin tsiwa ta ce "Kai Abba Akila ba zaka daina tashin mutun daga barci bako? Wlh kada ka sake yi mini haka, ni bana son jarabar tsiya..." Bata kai ga rufe bakinta ba a ka sake taɓata, hannunta ta kai ido a rufe ta bude hannun wanda yake taɓa tan, a tunaninta Abba ne. Can kuma aka sake taɓa ta, dogon tsaki ta ja, ta miƙe zaune a tsakiyar gadon tare da fara surfa masifa tsakiyar dare, dan lokacin karfe 2 na dare zai yi. Abba ne a tsaye a kanta ta gani, amma a nata ganin ne Abba a zahirin gaskiya kuma ba Abba bane, domin Abba baya ɗakin ma kwata-kwata sai Allah kaɗai yasan ina ya tafi. "Abba Akila wai meyasa baka da imani ne wani lokacin? Yanzu ba zaka barni na kwanta na hutawa rai na ba?..." Bata kaiga rufe bakinta ba, ya ɗauketa da wani mahaukacin mari mai razanar da kwakwalwar duk wanda a ka yi wa shi. Ji take yi dif komai ya tsaya mata cak, har wani bala'i duhu ta gani ya gilma mata ta cikin idanuwanta. Ihu ta kurma tare da miƙewa ta damko kwalar rigar Abba da idanuwanta ke nuna mata. "Har ni zaka mara? To wlh baka isa ba". Ta kai karshen maganar tare da ɗaga hannu zata wanke masa fuska da mari, abin mamaki ko da ta kai mashi marin, sai ta mari iska, bata ji komai ba, sake kai masa wani marin ta yi, shima sai ta ji iska ta mara. Sau uku tana gwada marin, amma ina ko sau ɗaya bata sami damar taɓa fuskar ba, nan fa ta fara tsorata, jikinta ya fara kerma, cikin sauri ta saki wuyar rigar mutumin tana ja da baya-baya. Ina bai bari ta yi nisa ba, ya damko wuyarta, nan fa ya fara yar carafke da ita a cikin ɗakin, kamar ba mutum ya riƙe ba, haka ya rinƙa wurgi da ita yana sake caf kota, sannan ga wasu siraran bulalu guda uku, wadda suke zane mata jikinta idan ya ɗaga ta sama, sai ihu take yi, amma babu wanda ya kawo mata agajin. A ɓangaren ita kuma A'afia, sai cin abincinta take yi. Abin mamaki shine bayan ta koshi ta tashi zata ta fi, kamar daga sama taga wasu mutane su biyu masu kamanni irin na Abba sun bayya a kujerun gefe-gefen ta, ma'ana sun sanyata a tsakiya, tsabar tsorata yasa ta kurma ihu, tana kokarin guduwa, suka yi maza suka danneta suka fara bata abincin nan a baki. Ji take yi cikinta na mata barazanar fashewa saboda ƙoshi, amma sun ki kyaleta sai da suka ɗura mata abinci na wuce misali, sai ihu take yi ba wanda ya iya kawo mata agaji dan ba mai iya jinta. Sabo tsabar rashin mutunci irin na dodannin nan sai bayan sun kammala ɗura mata abincin nan son ransu, sannan suka fito mata da ainahin suffar abincin da taci dan ta gani. Kai kai kai wai iya zubillah, wasu irin manya-manyan tsutsotsi ne sai yawo suke cikin plate ɗin, sauran plate ɗin kuma akwai mai ɗanyen nama, akwai nai hanjin mutun ba'a wanke ba, shi kan shi ruwan da ta sha kakkauran jinine mai kaurin gaske. Ai daga wannan lokaci Aafia bata sake motsi ba, nan take numfashi ta ya ɗauke ta sume a wajen, tana suma suka ɓace abin su, kamar yadda suka ɓace kuma haka duk wani abu na su ya ɓace. A ɓangaren Hajiya Umaiya kuwa, yau Abba ne ya mata duka ita kaɗai, sai ihu take yi tana tambayarsa shin me ta yi masa, amma ina bai yi magana ba, domin ba asalin Abba bane, sai Allah kaɗai yasan in da asalin Abba suka kai shi, lilis suka yi wa Ammie kafin su ɓace su barta da azaba. Sai bayan awa biyu da tafiyarsu sannan ta samu azaban ya sake ta, ta samu ta yi barci, amma fa Abba bai dawo ba har barci ya yi awon gaba da ita. A ɓangaren gidan Abbi kuwa. Sun yi kaura lafiya, sun koma tsantsararren gidan su mai bala'in kyau da girma, hawa biyu ne, ya tsaru iya tsaruwa, Irfan ya kashe kuɗi wajen zuba musu tsan tsararrun furnitures masu bala'i kyau da tsada, kai kace gidan wani gwamna ne saboda haɗuwa. Ansha walima da sadakar abinci, su Imran duk sun haɗu a part ɗin Irfan, sai murna ake yi. Misalin karfe uku Aunty ta ce Ayla ta ɗauki abinci ta kai wa su yaya Irfan part ɗin su, domin yau cikin gidan a cike yake da yan Walima, kuma yaya Irfan ya ce yanzu ya kamata su dai na cin abinci a Palo gaba ɗayan su, su za su rinƙa ci a part nasu saboda yanzu Abbi baya zama da su, kada wata matsala ta sake faruwa, Aunty ta amince da hakan kuma ta ji daɗi. Ayla ta yi wankanta fes, ta shirya cikin ɗaya daga cikin dogayen rigunanta, ta fito tas kamar ba ita ba, amma babu wani abin da ta fi yawan tunawa kamar Rimsha, ai na za su sake haɗuwa, shikenan sun rabu, idan ta tuna hakan sai ta yi kuka. Jiki ta gaba ɗaya a mace ta ɗauko katon kular abincin, mai aikinsu kuma ta biyota da kular miya da kuma basket na su kayan latus da su plates and spoons. Zaune daddyn Jelly yake a palon Irfan yana latse-latse a wayarsa, ya yin da shi kuma Irfan yake cikin toilet a bedroom nasa yana wanka, lokacin da ta shigo kuma, a lokacin Imran ya fito ya zo ya zauna a sofar kusa da daddy. Gabansu ta zo ta ajiye abincin, ta yi musu sannu tare da gaisuwa, ta miƙe zata tafi abin mamaki daddyn Jelly da bai ɗago ya kalleta ba tun da ta shigo amma da ta miƙe zata tafi kamar daga sama ta ji yana cewa "Me ya sanya ki kuka kuma? Ba na ce kada ki sake yin kuka ba?" Cikin sauri ta juyo da kallonta kanshi, tabbas bai ɗago ya kalli fuskar ta ba, tun da ta shigo kanshi na kan wayarsa, to tayaya ya kalli fuskarta? Kuma tun da ta shigo kanta a kasa yake. Ganin ta yi shiru yasa ya ajiye wayar tasa ya ɗago tare da yi wa yar aikin nasu umarnin a kan ta tafi, ita kuma Ayla ta zo nan, ya kai karshen maganar nasa yana nuna wa Ayla gefensa a kan tazo ta zauna. Zuwa ta yi ta tsugunna a gaban shi tana faɗin gata nan, ita kuma mai Aiki ta wuce ta tafi abinta. "Bappa ina kuka samo wannan yarinya kuma?" Imran ne ya tambaya yana kare mata kallo. "Zan baka labari amma ba yanzu ba" to kawai ya amsa da shi. Kallon tsab daddyn Jelly ya yi mata sannan ya ce "Me ya saki kuka? Na san dole ki kasance da damuwa a ranki, saboda iyaye ba wasa ba, amma ai nace kada ki sake kuka, kuma nace zan nemo miki iyayen naki, ko ba haka muka yi ba?" Cikin girmamawa ta gyaɗa masa kai alamar E haka suka ka yi. Daddy Jelly ya kware wajen iya rarrashi, domin Jellyn sa duniya ce wajen iya kuka, sai ya ɗauki minti talatin yana lalllaɓa Jelly yana bata hakuri, har sai ta hakura, to yanzu kuma ya gama da Jelly ga Ayla. Hannu yasa ya ɗago haɓarta yana kallon fuskar ta "Daga yau ki yi mini alkawari in dai zaki yi hawaye to sai dai ya kasance na farincikin haɗuwarki da iyayenki" Kuka ta sa mashi domin ba zata iya dai'na yiwa Rimsha kuka ba, dole idan ta tuna Rimsha ta yi kuka. Subhanallah daddy Jelly ya faɗa tare da miƙewa ya mikar da ita tsaye, bayan ta miƙe sai ya koma ya zauna tare da janyota ta zauna kusa da shi, shi dai Imran sai kallonsu yake yi yana mamakin yadda daddyn Jelly ya kware wajen kula da yara, ko da yake dama dole ya iya, kada ku mance shi kaɗan shi ya reni Jelly sa har ta girma. Ɗan rungumota kaɗan ya yi a jikinsa sannan ya fara goge mata hawaye, kamar dai yadda yake yi wa Jellynsa haka ya yi mata, da kayar ta yi shiru, bayan ta yi shiru ne sai ta yi kokarin barin jikinsa, bai hana tana ba, domin shi matsayin jini ɗaya yake kallonta, ganin ta yake tamkar jelly barema da Jellyn nasa bata nan yanzu, bawan Allah yaso ya ja su Aafia a jiki dan su ɗebe masa kewa, amma sun ki yarda, shine yanzu yake jan Ayla a jiki ko kewa zai ragu masa. "Kada ki damu, ki ɗauke yi tamkar yayanki ko daddyn ki, duk yadda kika ɗauka, yanzu dai kada ki sake yin kuka" Ayla ta kasa gaya mashi cewar kukan rabuwa da Rimsha take yi, domin a yanzu Rimsha ita ce duniyarta, saboda mamanta ta rasu ga shi ita bata san waye babanta ba. Sai da daddyn Jelly ya tabbatar ya sanya Ayla murmushi sannan ya mata izinin tafiya, ran ta ya ɗan yi fes kaɗan, amma ba zata iya dai'na tunanin Rimsha ba. Bayan tafiyar tane Imran ya ce "Bappa wlh yarinyar nan tana mini kama da Ustadz" "waye kuma Ustadz Imran?" "Bappa ka manta Ustadz da muka taɓa zuwa da shi Kano, A,A Salahuddeen, wannan babban abokina ɗin nan, yanzu ma ya je gyara wani abin dan gane da makarantar sane, amma idan ya dawo zan kawo maka shi kaga ni, wlh muryan sune ma ya fi kama da na juna". Shiru daddyn Jelly ya yi kafin ya ce "Kamannin ne kila kawai, domin a labarin da ta bamu ba ta da ɗan uwa AA Salahuddeen" "No bappa dama nima bance ɗan uwanta bane, AA Salahuddeen me zai haɗa shi da wannan yarinyar? Kai bappa AA Salahuddeen fa nace maka, ina ai ba su ma haɗu ba, kawai dai kamar murya ce data fuskar, ita ma ta fuskar ai ba sosai ba ce, muryar dai ta fi sosai, bacin haka ai yan uwan A.A Salahuddeen ma kwata-kwata ba wanda yake kasar nan, shima bai jima da dawowa ba, kai bappa in takaice maka zance duk yan uwan sa babu wadda yake ɗaga ido ma ya kalli mutun da daraja, sai shi kaɗai, shine ya fita zakka a cikinsu, yana son mutane, ga shi da taimako, kuma dukkansu yaran Salahuddeen mazauna Englan ne basu zama a nan Naija". Shiru daddy jelly ya ɗan yi kafin ya ce "Yanzu dai Imran yaushe za ku koma Kano?" Shiru ya ɗan yi kamar mai tunani, can kuma sai ya ce "E to jibi zamu je Katsina ni da Dr dan ya takura mini a kan nazo na ga matar da zai aura, wai yar Katsina ce, idan muka dawo washegari sai mu wuce Kano ba" "wani Dr kuma?" Daddy ya tambaya Miƙewa ya yi yana faɗin "Wani abokina ne wadda muka yi primary tare da shi, shine ya takura mini ya samu mata a Katsina nazo na ganta" Fatan alkhari daddyn Jelly ya yi musu sannan Imran ya wuce ya koma cikin bedroom nasu dan ya duba shin Irfan ya gama wanka ne ko ya ya. Shi kuma daddyn jelly kishingiɗa ya yi yana tunanin rayuwa. To mu koma Katsina dan jin ya ake ciki. 💖💖KATSINA💖💖 After 1 day👌 Abubuwa sun faru a cikin wannan kwana ɗayar, ciki hadda bayan Sadiq ya dawo da yamma daga gareji, ya sanar da Rismha su mummy sun ce za su je neman Jehan ne, idan sun ganta kuma za su wuce Maiduguri su nemi yan uwan mum ɗin, Rimsha ta sha kuka har kamar ranta zai fita, yanzu shikenan ta rabu da su mummy kenan, idan ta tuna hakan sai ta sake sakin wani sabon kuka. Da kyar Sadiq ya lallaɓata ta yi shiru, amma bata iya samun barcin dare ba har sai can tsakiyar dare barcin ɓarawo ya yi awon gaba da ita. Washegari tun karfe 7 na safe Ibraheem ya yi musu dirar mikiya a kofar gidansu, domin yau kwanan Jehan huɗu kenan bata je restaurant ba, kuma babu wani bayani, shine ya biyo sahu. Sallama ya yi a kofar gidan, lokacin Rimsha na sharar tsakar gida. Baiwar Allah tun da ta yi sallar asuba bata koma barci ba, ta tattara wanke-wanke ta yi yanzu tana shara, kamar dai yadda take yi a gidan su Kausar. Jin sallama yasa ta ajiye tsintsiyar ta fito dan taga waye ne, sallama ita ma ta yi masa sannan ta gaishe shi, sai kallonta yake yi, abun ku da jini sai ya yi mata kallon kama da Jehan "Ke ina Jehan take?". Daidai lokacin Sadiq ya fito daga ɗakin su dake cikin zauren, dan shima ya ji sallamar. "Rimsha me kike yi a nan?" Sadiq ne ya tambaya. Cikin girmamawa ta gaishe shi, da fara'a ya amsa sannan ya miƙa wa Ibraheem hannu suka gaisa. "Rimsha ki shiga ciki mana?" Girgiza kai ta yi tana faɗin "A'a yaya Sadiq na ji yana tambayar ina Jehan ne, to ina son in ji me ya kawo shi wajen Jehan" Kallon Sadiq Ibraheem ya yi ya fara magana rai a matukar ɓace "Sadiq ina Jehan? Me yasa kwana biyu bata zuwa aiki? Kasan dai yarjejeniyar dake a tsakanin mu ko? To ni gaskiya ma na fara gajiya da wulakancin Jehan, ba zan iya ba, na taimaka mata na rufa mata asiri, amma ni kuma tana kokarin ta tona mini nawa asirin akan menene? Me yasa take yi mini hakan? Wlh ku ja mata kunne, idan ba haka ba, to ni gaskiya ta biya ni kuɗi na a dunkule". Tun da ya fara magana Sadiq da Rimsha suka tsare shi da ido, har sai da ya kai aya sannan Sadiq ya ce "To Ibraheem ni dai ba abin da zan ce maka sai dai na ce Allah ya baka hakuri, domin kuwa Jehan da iyayenta basu nan, sun bar Katsina saboda wata jarabawa da ta hau kan su....". Kun san Katsinawa da iya zagi, tun Sadiq bai kai karshen maganar ba Ibraheem ya banka wani uban ashar mai tashin kan mai sauraro. Nan fa ya fara ruwan bala'i, wai Jehan bata isa ba, dan ubanta sai ta biya shi kuɗin sa. Ganin yana kokarin ya tara musu jama'a ne yasa Rimsha ta yi saurin cewa "Ka yi hakuri zamu biya kuɗin yanzu dai ka yi shiru". Dawo da kallonsa kan ta ya yi from head to toe yake kallonta, jikinta na sanye da wannan hijabin nata har kasan, ita kuma kallon Sadiq ta yi ta ce "Yaya Sadiq me ya faru? Me ya haɗa Jehan da mutumin nan har ta karɓa masa kuɗin sa? Kuma naira nawa ne ma kuɗin nasa?" Ba tare da ɓata lokaci ba Sadiq ya shiga bata labarin abin da ya faru sama-sama dai haka, shiru ta yi tana tunain ko dai ta cire sarkar wuyarta nan ne ta ba shi, domin sarkar da gwaggo ta bata, za tafi kuɗin sa da yake ikirari tsada, to amma idan ta bashi sarkar bata da tabbacin zata sake haɗuwa da su gwaggo domin suma sun cire rai da ita kwata-kwata, sun hakura da ita. Ganin ta yi shiru ne yasa Sadiq ya ce "Rimsha lafiya kuwa?" Yar firgita ta yi sannan ta ce "Lafiya yaya Sadiq, idan ba damuwa ni zan karisa aikin da Jehan ɗin ta fara, domin na biya bashin, ni bana bukatar ma ya rinƙa zarar wani abu daga cikin kuɗin kamar yadda suka tsara da Jehan, kai tsaye kawai ya ɗauki albashi na ɗin gaba ɗaya har sai kuɗin shi sun kare". Cikin sauri ya ce ",Ai ni yanzu kuɗi na sun karu, daga 500k ya koma 700k, domin ammini wulakanci". Ɗaure fuska sosai Rimsha ta yi, rai a matukar ɓace ta ce "Da cewa ka yi na yi aiki na kara maka saboda Allah to zan kara maka, amma kuɗin riba kuɗin ruwa baka isa ba wlh, ni Rimsha ba zan yi wannan saɓon Allah ba, wato ka bada bashi kuma ka kara kuɗin ruwa, to ba ka isa ba, ina maka aiki na daidai kuɗin ka zan bar restaurant ɗin". Ta kai karshen maganar tare da wucewa cikin gida abinta, Jinjina kai dukkansu suka yi daga Ibraheem ɗin har Sadiq ɗin, a fili Sadiq ya ce "Jini ba karya ba, jini ba ruwa ba, kai tab ɗi jam". A ɓangaren shima Ibraheem abin da yake tunani kenan a cikin zuciyarsa, jini ba karya ba kuma ba ruwa ba, dole a sami ɗabiun Jehan ko ma yayane a tattare da Rimsha, ga kuma zahiri sun gani da idonsu, ita ma Rimsha bata takuwa. Sun jima tsaye shiru kafin nan Ibraheem ya katse musu shirun da cewa "Ka ce ta shirya mu wuce aiki yanzun nan, domin Jehan ta ɓata kwanaki huɗu bata zuwa aiki, dan haka dole ta fara aiki daga yau" Sadiq ya yi kokarin rokar shi a kan ya bari sai gobe, amma ina ya ce shi ba zai yarda ba dole tazo su tafi, haka Sadiq ya hakura ya kirata a kan ta zo su tafi, ba musu ta shirya suka wuce da Ibraheem, ya goyata a bayan mashin nasa, Sadiq ya ce mata da yamma zai zo ya ɗauke ta. A ɓangaren Ahmad kuwa, tun da Rimsha ta jefa wayar nan nata a cikin trolleynta bata sake bi ta kan wayar ba, ya kira har ya gaji, ya shiga damuwa sosai, ya rasa meke yi masa daɗi bawan Allah, har ya fara tunanin zuwa Katsina dan ya duba ko lafiya take. (Ni kuwa nace in dai Rimsha ce baka ga komai ba ma🤣) To Rimsha dai ta isa restaurant lafiya kuma ta fara aikin da Jehan ta fara ta bari, kasan cewar ita Rimsha baa san fuskar ta media sosai ba, sai ba wanda ya gane ta, kuma ga zahiri ma kun gani, ita Jehan lokacin da take tare da wayarta, kullun zaku ga waya a hannunta, sannan kuma tana yawan hawa media, amma ita kuma Rimsha kun dai gani tun da ta sanya wayar cikin trolley bata sake bi ta kanshi ba, so ita bata wani damu da media sosai ba. Ma'aikatan wajen daga mazan su har matansu sai da Rimsha ta burgesu, sai kallonta suke yi, ga shi tana da girmama mutane, sai dai fa ita ma bata murmushi bare dari, fuskar nan nata a ɗaure tamau, taki sake musu fuska, dan bata son a kawo mata shirmen banza a lamuranta, sai ɗaure fuska take yi, amma tana aiki lafiya lou tare da su, sannan tana basu girma, shi kanshi Ibraheem ya fi jin daɗin aiki da ita fiye da Jehan, domin ita idan ya saka ta yin abu, bata yi mashi musu, tana yi, tsabanin Jehan da sai ta ga dama, ko kuma idan aiki ya saɓawa dokar da ta sawa kanta tofa ba zata yi shi ba. (Tofa wannan shine reshe ya juye da mujiya, ga Rimsha a restaurant, ko me zai faru?🤔 Mu dai je zuwa) Idan muka koma ɓangaren gidan Abbo kuwa. Lafiya lou Nawid ya fita shopping nasa shi da jelly, daga nan suka je suka yi kallo, ya sai mata Ice cream kala-kala tare da chocolate dayawa kamar yarda ya faɗa. Bayan sun dawo gida, da misalin karfe huɗu na yamma washegari kenan, gaba ɗaya gidan shiru babu kowa, Ummi tana bedroom nata tana barci. Sanye da wando da riga Jelly ta fito daga bedroom nata, sai dai ta ɗaura wani irin riga mai kama da after dress a kan kayan nata, amma shi wannan bai kai mata har kasa ba, iya gwiwarta ya tsaya mata, kanta babu ɗankwali, ta saki wannan stubborn hair nata. Gaban Tv ta je ta tsaya tana ganin wani India film da suka sanya, ganin Film ɗin ya yi mata kyau ne yasa ta koma saman sofa ta zauna. Tana tsaka da kallo ta ga ansanya wakar kutchi kutchi hotaye, haba ai a ɗari Jelly ta miƙe ta fara tikar rawa, kamar wata yar tsana haka Jelly ke rawa tana juyi, sai ka rantse da Allah babu kashi a jikinta, har wani karairaya take yi tana lankwasa kugunta. (Kai jama'a ashe ba iya baiwar cin kaza ke gareta ba, har da baiwar rawa🤣) Har wani wurgi da hannu sama take yi tana yin wani abu kamar yadda maciji ke juyawa, dama gata ba kiba yar siririya, sai abin ya bata abin da ake bukata. Yafi minti biyar yana tsaye yana kallonta, tun lokacin da ta fara rawar ya shigo cikin gidan, bata ji shigowar shi ba, kuma bata gan shi ba, sakamakon ta kure Volume na Tv, dan a cewar ta idan Tv na kara sosai wakar ta fi daɗi. Sai wani kallonta yake, duk ta yadda ta juya haka shima yake juya idanuwansa yana binta da kallo, har sai da aka gama wakar sannan ta zube saman sofa tana dariya tana mai da numfashi, har lokacin bata lura da shi a wajen ba. Shi kuma ganin ta gama rawar ne yasa ya shigo cikin palon hannunsa ɗaya riƙe da jakar computer ɗayar kuma ya ratayo coat nasa, daya cire ya bar na cikin. Cike da murna ta tashi tana faɗin "Yaya Nawid baka dawo da wuriba da ka kalli rawana". Wani irin farinciki yake ciki kamar wadda akayi wa albishir da gidan aljanna, Jelly ta tafi da imaninsa yau, lokacin da take rawarnan, kamar yarda take rawa haka zuciyarsa ke kaɗawa a kanta, yanzu duk wani shirme da zata yi masa, burge shi take yi, komai nata kyau yake yi mashi. Miƙa mata jakar hannunsa ya yi yana faɗin "Ga shi rike mini wannan dan a gajiye na dawo" to ta ce tare da karɓar jakar. Saman sofa mai zaman mutun 3 ya zauna yana sauke numfashi a hankali. "Baby jeki kawo mini ruwan sha". Ajiye mashi jakar ta yi da sauri ta juya zuwa wajen fridge. Kallo ya bita da shi, yana mai jin wani abin da ba zai iya misaltawa ba a zuciyarsa. Ruwan faro mai sanyi sosai ta ɗauko masa, sannan ya ɗauko glass cup kamar yadda taga Ummi na yi wa Abbo. Bayan ta kawo mashi, sai ya ce ta zuba mashi ruwan, to ta ce sannan ta sanya karfinta tana kokarin buɗe robar ruwan, amma ina ta kasa, ɗan kishingiɗa ya yi tare da karɓar robar ruwan ya buɗe mata sannan ya miƙa mata a kan ta zuba mashi a cup, ai kuwa yana miƙa mata ta karɓa ta fara zuba mashi daga tsakiyar kanshi har zuwa jikinshi. A sukwane ya tashi ba shiri, ita kuma ganin ya ta shi, sai ta ce "Yaya Nawid ko dai ruwan bai maka yadda kake so bane?" sanyin ruwan yasa ya ji tamkar ya kifa mata mari, amma ina zuciyarsa ba zata iya barin shi ya mare ta ba, daurewa ya yi ya ce "Haba baby meyasa zaki zuba mini ruwa mai bala'in sanyi haka?" Turo ɗan bakin nan nata ta yi, cikin shagwaɓa ta ce "Kai yaya Nawid, ka manta ne?, Kai fa ka ce na zuba maka ruwan". Dafe kansa ya yi yana faɗin "Kash baby nifa a cup na ce ki zuba ki bani na sha, ba a jikina na ce ki zuba mini ba..." Cikin sauri ta katse shi da cewa "A'a yaya Nawid wlh karya kake yi, ni baka ce na zuba maka a cup ba, cewa ka yi in zuba maka ruwan, shine ni kuma na zuba maka, amma shine zaka zaje ni" ta kai karshen maganar tare da sakin kuka ta nufi hanyar ɗakin Ummi. Cikin sauri ya yi maza ya riƙo hannunta yana faɗin "To ki yi hakuri kin ji ko? Na ji nine nayi laifi yanzu ɗauko wani ruwan ki zuba mini a cup ki bani na nasha kishi nake ji" To kawai ta amsa mashi da shi, sannan ta wuce ta ɗauko wani ruwan. Shi kuwa ɓalle botir ɗin rigar jikin nasa ya yi, ya cire ya ɗaura saman sofa, ya zauna daga shi sai farar singlet. Ya yi Sa'a yanzu da ta kawo ruwan ya buɗe mata a cikin cup ta zuba mashi, sannan ta miƙa mashi, karɓa ya yi ya kafa a bakinsa, wani sanyi ya ji tana ratsa mashi zuciyarsa a lokacin da sanyayyar ruwannan ke ratsa maƙogwaransa. Tas ya shanye ruwan tare da miƙa mata cup ɗin, karɓa ta yi ta mai da mazauninsu, sannan ta dawo ta zauna kusa da shi. "Baby sai yaushe zaki koyi girki ne?" Ya tambaya yana kallonta, Cikin nuna ko in kula, ba tare da kalli in da yake ba ta ce "Sai ka auro wannan matar taka da kace kake so, ranar auren ni zan yi muku girki". Mamakine ya kama shi, dama ta ji abin da suka ce shi da Ummi ne? Lokacin da suka yi maganar tana cin kaza fa, kenan tana sane da abin da yake faruwa kawai magana ne bata yi? Lallai kam yarinyar nan akwai kwakwalwa sai dai iskanci ya cika mata ƙwaƙwalwar tata over. Sai tunani yake yi ita kuma hankalin ta na kan kallon da yake gaban ta. A wannan hali Abbo ya dawo ya samesu, wani irin kululun bakin ciki ya ji lokacin da ya kallesu a haka, ga Nawid ya cire riga daga shi sai singlet, ita kuma Jelly ta zauna kusa da shi tana kallo, ga fuskokinsu dukkansu ɗauke da annuri na farinciki, alamar zaman su a inuwa ɗaya ya yi bala'in yi musu daɗi, sannan shi Nawid sai kallon Jelly yake yi yana murmushi, ita kuma tana kallon film. Ganin Abbo yasa Nawid ya ce "Amma baby ai nace ina son ki ko?" Hankalinta na a kan kallo ta ce "E ka ce wa Ummi dai ka yarda zaka aureni amma zaka haɗa ni da wancan". Murmushi ya yi sannan ya ce "To dai na ji yanzu ki faɗa mini kina sona? Dan dai ni kin san ina son ki ko? Baki ga jiya a baki na baki ice cream bane?" Sai lokacin ta juyo da kallonta kanshi, fuska ɗauke da murmushi ta ce "Zaka sake saya mini Ice cream irin na juya ɗin ne?" Gyaɗa mata kai ya yi yana faɗin "Dayawa ma kuwa, amma yanzu dai ki faɗa mini kina so na?" Ita ma gyaɗa masa kai ta yi tana dariya ta ce "E mana ina Sonka". Abbo ji yake yi kamar ya shake Nawid saboda bakin ciki, rai a makutar ɓace ya wuce cikin bedroom nasa, shi kuma Nawid ya ci-gaba da jan Jelly da hira, domin ya ja raayinta ta rinƙa sakin jiki da shi, ta bashi haɗin kai a kan abin da yake son yi na takurawa Abbo har sai ya dai na yin duk wani tunani da yake yi a kan ta. (Ni kuma na kwanshe kayana zuwa Washington DC) 💖💖Washington DC💖💖 Musharraf and Asif wato Michael Sun yi Sa'a har suka idar da sallah ba wanda ya shigo cikin ɗakin, bayan sun idar da sallah ne, Musharraf ya zauna ya fara koya masa wasu abubuwa daya kamata ya fara iyawa. Abin mamaki ƙwaƙwalwar Michael da take da matsala a baya, amma yanzu duk wani abin da Musharraf ya gaya masa sau ɗaya yana haddacewa, hatta kalmar shahada da aka bashi da farko ya haddace, abin ya bawa Musharraf mamaki. Yau dai cikin farinciki suka kwanta, kuma a tare suka yi barci ɗaki ɗaya, da Asuba Musharraf ya yi kokarin tashin shi domin su yi sallah amma ina yaki tashi, da Musharraf ya matsa mashi ma, sai ya ce cikin magagin barci idan Musharraf ya sake tashin shi sai ya harbe shi da gun idan ya tashi. Haka Musharraf ya hakura ya kyale shi, amma wani hanzari ba gudu ba, gaba ɗaya daren jiya tun da karfe 2 ta cika Musharraf bai sake iyayin barcin ba, daya fara barci zai yi mummunar mafarki a kan Micheal da ya musulta, daya fara barci zai ga wata mata sanye da fareren kaya komai nata fari tas sai dai jini na zuba daga idanuwanta hannunta riƙe da katuwar wuka mai kaifi ta zo zata caka mashi, tana kuka a kan me zai cuce su, haka zai farka a birkice yana addua'o'i, wani lokaci kuma sai ya fara barci, sai ya kalli wata bakar mata, baka kirin kamar zunubi, tana rike da wuƙa, yana ji yana gani zata yankawa Michael wuya jini ya yi ta zuba. Haka har asuba bai samu barci ba. Hakan yasa yake tunain tabbas akwai wani abu a gidan nan nasu, ba lafiya ba, kuma shima ya dasa ayar tambaya a kan Micheal, kuma ya zamar masa dole ya kula da lafiyar Michael ɗin ta hanyar yi masa addua'o'i da sauransu tun da shi ya sanya shi ya musulta, komai ya faru da shi to shima yana da sa hannu. (To fa me kuke tunain zai iya kasancewa a gidan William jacop? Me kuke tunanin ya jawo hakan? Me kuke tunanin ya samu Michael? Waye kuke tunanin ya ke aikata hakan? Me yasa sai Michael kawai? Ko dai sauran dan basu musulunta bane?) Bayan ya yi sallar asuba sosai ya ɗaga hannu ya rinƙa zubawa Allah kirari yana rokonsa da ya kare Michael a duk in da yake. Bayan ya kammala ya dawo saman gadon ya dukufa wajen tofawa Michael ɗin addu'a domin abubuwan da ya gani a mafarki dan gane da Michael ɗin ba abubuwan wasa bane, sannan abin akwai rikitarwa da ɗaure kai. After some hours👌 A ɓangaren Lion kuwa. Tsaye suke a cikin ɗakin binciken su, yau daga shi sai Short da singlet, kakkarfar kuma kyakkyawar suran jikin nasa a bayyana, hakan yasa kwarjininsa ta kara bayyana sosai, soft skin nan nasa ba'a magana, yana kwance luf tamkar ka taɓa jini ya zuba, sai wani kyalli yake yi, ga bala'in laushi kamar bai taɓa fita waje ba, kamar fatar jariri, ya saki dark black curly hair nan nasa wadda ya zuba masa har bayan wuya, kyau iya kyau ba'a magana. Daga gefensa Tyrone ne da Tga a tsaye kusa da shi, sun zubawa system dake gabansu idanuwa, suna ta kallon irin kisan da James yake yi, aiki suke yi sosai ba bu kama hannun yaro, domin Lion zai yi tafiya next week saboda ya samu abin da yake nema dan gane da binciken da yake yi a kan A.E.A shiyasa ya tarasu a ɗakin bincike suna duba wasu gunjiyoyin dake kewaye da A.E.A. Tyrone ne ya ɗago kai cikin girmamawa murya kasa kasa a nutse yadda kasan wanda yake gaban mahaifinsa, wani ma ko mahaifinsa ba zai yi wa irin wannan biyayya ba, muryarsa har sarkewa take yi ya ce "Sir meyasa zaka tafi next week, why ba zaka bari sai nan da 3 weeks ɗin kamar yadda suka rubuta nan da 3 weeks za su yi gangami a wajen ba, kaga a lokacin zaka iya bamu umarni mu yi musu dirar mikiya mu kashe kowa mu ɗauko James". Shiru Lion ya yi yana mamakin ma ya akayi mutun mai ƙaramin kwakwalwa irin Tyrone ya zama lieutenant General kwakwalwarsa sam bata da kaifin gudu na hangen nesa, ya zama dole ya rinƙa kara musu hangen nesa idan ba haka ba wata rana za su yi shirme. Ya jima shiru bai yi magana ba, sai da ya kwashi good 15 mins san nan ya ce "Saboda C.I.A" Kallon Tga Tyrone ya yi, yana son karin haske amma yana tsoron sake yin wata tambayar saboda ya san Lion baya son yawan surutu, idan ka cika saka shi magana sai ya jefaka ta window kowa ya huta. Sarai Lion ya san suna sun karin haske, kuma yasan tambayar da za su yi mashi, hakan ya sa ya ce "Idan har C.I.A suka riga mu isa ga James to fa zasu har be shi ne lokaci guda ya mutu, ni kuma ba haka nake so ba, ina bukatar wasu amsoshin daga wajen shi kafin na hukunta shi". Tga ne ya yi karfin hali cewq "To why not ba zamu tafi tare ba? Please Lion ka taimaka ka bari mu bika, ina bukatar kama James da hannuna". Wucewa Lion ya yi ba tare da ya sake yi musu magana ba, dama kuma sun san hakan domin baya magana biyu. Shi dai Tyrone mutuwar tsaye ya yi yana zancen zuci "lallai James ya cika tantirin ɗan ta'adda, irin wannan kisa da yake yi kamar ba mutane yake kashe wa ba, shi kawai da sun ba shi aiki sai ya karɓa, baya duba waye zai kashe, kai anyama James jinin Romeo ne kuwa? Domin Romeo da Michael dai ba haka suke ba, sannan Romeo da yake The General of the Army ma ba ya yin irin kisan rashin imanin da James ke yi ba. Wucewa Tga ya yi ya bi bayan Lion dan yau ko dukan shi Lion zai yi sai dai ya duke shi, amma sai ya roƙe shi akan su tafi tare. Zaune saman bed ya isko shi ya yi shiru kamar mai tunanin wani abin. Gefen shi Tga ya zo ya zauna, shiru suka yi na tsawon mintuna ashirin. Sannan Tga ya ce "Lion ka bari ku tafi tare mana, ina son kama James da hannuna". Shiru Lion ya yi mashi kamar ba shi a wajen, zuba mashi ido Tga ya yi yana jiran amsa, tsawon mituna biyar sannan in a cool voice a nutse ya fara magana "Ba tare za mu tafi ba, amma dai ku zaku tarwatsa sansanin, sai dai ina son kasan wani abu ɗaya, James ba zai kamun maka ba, domin ya wuce yadda kake tunani, zata iya yiwu wa ku iya tarwatsa wayan da suka kama shi, amma fa ka sani daga lokacin da ku ka kuɓutar da shi daga hannunsu tofa kai kuma ba zaka iya kama shi ka dawo da shi gida ba". Zaro ido Tga ya yi yana mamakin kalaman Romeo, cike da tsoro ya sake tambayarsa "Me yasa ba zan iya kama shi ba?". Nan ma dai shiru na ƴan mintoci Lion ya yi kafin ya ce "Bawai ba zaka iya kama shi ba ne, kunema zaku yaki kungiyar amma dai ina son ka sani James ya fi General training mai karfi, sannan ya fi General ƙwaƙwalwa saboda jinane shi, ba bu wata hukuma da zata iya kama shi cikin sauƙi, mutane biyu ne training na su yake gaba da James a yanzu, na farko The general of the army, ajiye muƙamina a gefe, na biyu Ni da kai na, bayan ni ba mai iya kama James cikin sauki". Kasa magana Tga ya yi domin Lion ya ɗaure mashi kai dayawa, shi dai ya san koda James yana kashe mutane shi da yake matsayin uncle nasa ba zai kashe shi ba, amma me yasa James ba zai kamun musu ba? Shine abin da ya tsaya mashi a rai. Miƙewa Lion ya yi ya nufi Balcony yana faɗin "General kada ka rikita kanta dayawa, James ba zai kamun muku cikin sauki yadda ka ke tunanin nan ba, domin kuwa kungiya daban daban ne suke neman shi ruwa a jallo, sannan ni ma yanzu idan na fita kasar nan bawai kai tsaye kama James zan je yi ba, no bam ma tabbatar a wani waje takamaimai yake ba, saina natsu". Ya kai karshen maganar tare da shigewa cikin balcony ɗin ya shige cikin karamar pool nasa dake wajen, ya lumar da jikinsa gaba ɗaya a cikin ruwan, ya bar iya kai kawai a wajen, sannan ya lumshe idanuwansa kamar mai yin barci. Shi kuma Tga tashi ya yi, jiki ba kwari zuciya cike fal da tunani ya wuce ya koma wajen Tyrone dan su ci-gaba da aikin da ya sanya su. Shi kuma John yana word room dan ya ci kwakwa wajen Tga, ba karamin horashi ya yi ba, hakan yasa daddy yake bashi kulawa a word room. Shikuma Michael sai karfe takwas bayan ya gama gym ya dawo ne ya gabatar da sallar asuban shi, Musharraf na zaune yana kula da shi yadda yake Sallah har ya idar, sannan Musharraf ya gaya masa ba'a tsallake lokacin yin Sallah, da lokacin ya yi to dole ne ayi, dan haka ya koyi tashi da asuba, kasan cewar yana son abin sai ya ce da Musharraf ya yi masa alwarin zai rinƙa tashi da asuba, sosai Musharraf ya ji daɗi, kuma yasan wannan nasara da yake samu akan Michael ba komai bane face addu'ar da yake yawan yi ne Allah yake ɗaura shi a kan Micheal ɗin. Daga jiya da daddare da Michael ya karɓi musulunci zuwa yanzu, har wani haske fuskarsa ta kara, sai kyalli yake yi, har gashin kansa sai da ta san ya shiga addini kai tsarki, domin gashin nasa har wani kwanciya ta karayi tana wani curly kamar me, idanuwansa duk sun sauya, wasu sihirtattun kyau suka kara yi, idan ka gan shi kai kace ba shi ba ne, ya kara wani sihirtaccen kyau sosai abin shi, lokaci guda haiba ta bayyana a tattare da shi, ga kwarjini na addinin musulunci ya bayyana, ya ƙara natsuwa, ga shi ƙwaƙwalwar tasa tana ta kara buɗuwa saboda karatun Alkur'ani mai girma da suka yi da Musharraf jiya da daddare, Suratul Fadiha Musharraf ya koya masa jiya, bawan Allah da yake babu wata hayaniya a ƙwaƙwalwar tasa, har ya haddace surar, yanzu ba shi da damuwar komai, ya dai na fita Palo ma, yau tun safe suna tare da Musharraf ya dage a kan sai Musharraf ya kara koya masa wata surar, haka suka wuni yana koyar nasi da falaki, sai farinciki yake yi abinsa bawan Allah....... Nima sai farinciki nake yi na tattara kayana na wuce sai mun haɗu gobe a sabon gidan Abbi idan Allah ya kai mu da rai da lafiya 💖💖TRIPLET'S💖💖 39-49 💖After 2days👌💖 (Bari mu fara da restaurant kafin mu yi wani wajen kuma) Acikin yan kwanaki biyun nan Rimsha ta saba sosai da aikin restaurant ɗin, dama kun san ta da son koyar girki, dan haka sai ta tare wajen girkin hotel ɗin, saɓanin Jehan da ko leƙa wajen bata yi, sai dai idan ta zo ɗaban abinci zata kai wa masu saya. A yanzu Rimsha fa ta iya abinci sosai, kuma akalla zai kala girki kala 15 ta iya, bata da kiwuyar aiki, haka zalika bata jin nauyin jikinta, sake jiki take yi ta murji aikin ta, idan ta koma gida ta yi wanka ta yi ta barcin ga ji ya, sannan a yan kwana biyun nan kafin ta tafi restaurant ɗin sai ta yi wa maman Sadiq shara da wanke-wanke sannan ta tafi. Yau ma kamar kullun da sassafe ta tashi ta yi wanke-wanke da shara, sannan ta yi wanka, ta shirya, ta ɗauko wayarta, tun da ta zo sai yau ta ɗauki wayar, kokarin kunnawa ta yi amma ina battery ya kare wayar ta mutu ba charji, turo ɗan bakin nan nata tayi sannan ta yi wa mamam Sadiq sallama ta wuce sauri sauri domin Sadiq yana tsaye a waje yana jiranta. Tare suka jera zuwa bakin titi, a yanzu saura mata 4k a cikin 20k da Ahmad ya bata, gaba ɗaya ta kashe kuɗin a sayawa maman Sadiq irin su omon wanke-wanke da sabulun wanki da wanka, bata damuwa idan ta zo zata yi abu idan taga babu sai ta ciro kuɗi ta saya, harta tsintsiya ita ta saya musu guda uku, Yusuf mai rakata sayowa, dan shine babban abokinta. Karfe 8 daidai ta shiga restaurant ɗin nasu, kai tsaye wajen girki ta nufa, masu shara har sun yi sun goge koina, wajen ya yi fes, Rismha akwai goshi kamar me, tana shigowa suka fara samun baki, har Ibraheem ya campa abun, kullun cewa yake yi idan Rimsha bata zo ba basu samun ciniki, amma idan ta zo kuma, tana shigowa restaurant ɗin yake fara cika da jama'a, amma fa wa su ba abinci suke zuwa saya ba, kallonta suke zuwa yi sai su ɓige da sayar abinci, idan ta kawo musu abinci sai suyi ta rokarta akan ta basu number wayarta, amma ko kula su bata yi, suna yi mata kallon babba saboda tana da tsawo kuma tana zuba hijabi har kasa, a cikin hijabi sai ka yi mata kallon babba, amma idan ta fito yar firitu zaka ganta. Bata taɓa kula kowa ba, fuskar nan nata kullun a ɗaure kamar hadari. Sanya wayar ta ta yi a charji kusa da Ibraheem sannan ta fara karɓar oder kowa tana kawo masa abin da yake buƙata, ita da Faiz suke wannan aiki, shi kan shi Faiz ɗin daurewa kawai yake yi yana aiki tare da ita, amma magana ta gaskiya ya gama faɗawa da ita, haka zalika shima Ibraheem ya faɗa da ita sosai daurewa kawai yake yi saboda bata ba shi fuska ba. Bayan ta kammala kaiwa duk wayan da suka zo a lokacin abincin ne, sai ta koma saman wani kujera da suke zama idan sun kammala aiki, shiru ta yi tana tunanun rayuwa, tunanin ina zata sake ganin su mum ɗin ta kawai take yi, tunanin Ayla ne ya faɗo mata a ranta, cikin sauri ta miƙe ta nufi wajen Ibraheem. Tana zuwa ta ciro wayarta daga charji ta shiga neman layin Ayla, abin haushi gaba ɗaya wayar number Ahmad ne kawai a ciki, shiru ta yi tana tunanin a ina zata samu number Ayla. Tana tsaka da tunani wayar tata ta fara ringing, kallon screen ɗin ta yi, Yaya Ahmad shine sunan da ya bayyana a kan screen ɗin wayar. Picking call ɗin ta yi tare da kara wayar a kunanta. Daga ta cikin wayar ta ji wani nauyayyar ajiyar zuciya da ya sauƙe, muryarsa can kasa-kasa ya ce "Hello Queen of beauty" dogon numfashi ta ja tare da sauƙewa a hankali. "Yaya Ahmad baka da lafiya ne?" Nisawa ya yi sannan ya ce "Bani da lafiya my princess" zaro dara-daran sleeping eyes nata ta yi tare da marairace murya cike da tausayi ta ce "Allah sarki sannu ka ji? Allah ya baka lafiya, ka ga ma ko sallama ban yi ba bare mu gaisa, saboda yadda na ji muryar ka" "Allah sarki Queen of beauty ai kece silar rashin lafiyar tawa". Zaro idanuwanta waje ta yi, tana ƙokarin yin magana Ibraheem ya ce mata ga baƙi fa sun zo tun minti biyar da suke wuce, kuma sune masu wannan restaurant ɗin, jin haka yasa ta sallami Ahmad a kan anjuma zata kirashi, bata jira amsar shi ba ta katse kiran, sauri sauri ta nufi bakin dan tambayar me suke buƙata. Sallama ta yi musu, Dr Nawid ne da Imran, Imran ne ya amsa mata sallamar nata shi kuma Dr Nawid cewa ya yi "Ina Jehan? Ki je ki ce ta kawo mana abinci". Tana kokarin yin magana muryar Imran ya katse ta da cewa "Rimsha Nawazudden right?" Ya yi maganar yana zaro idanuwansa waje. Dawo da kallonta kan shi ta yi, zaro idanunsa waje ya yi sosai yana kare mata kallo, tabbas ita ce, abin da kawai yake faɗi a zuciyarsa, ita kuma kokarin gane wanene shi ai na kuma ya santa kawai take yi, shi kuma Nawid ya zuba mu su ido yana kallon ikon Allah. Sake maimaita mata tambayar Imran ya yi "Rimsha Nawazudden ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar E. A zabure ya miƙe tsaye yana binta da kallo, ganin ya miƙe tsaye ne yasa Nawid ya ce "Imran lafiya? Ai na kasan ta? Wace ce kuma ita ɗin?" Dawo da kallonsa kan Nawid ɗin ya yi, sannan ya fara magana "Nawid baka san Nawazudden ba? Ɗan takarar shugaban kasa wadda ya yi ɓatar lokaci guda shida familynsa, daga baya aka kawo gawarsa ya yi haɗari ya mutu?". A zabure shima Nawid ɗin ya miƙe suna kallonta, ganin yadda take jujjuya idanuwanta ne yasa suka kai kallonsu wajen, gaba ɗaya jama'ar dake restaurant ɗin ne suka zuba musu ido suna kallon su. Ganin hakan yasa Imran ya koma ya zauna yana faɗin "Ranki ya daɗe dan Allah ki zauna mu yi magana". Ba musu ta zauna domin ta jima tana addu'ar Allah yasa ta haɗu da wanda ta sani, mai kuma mutunci. Shima Nawid komawa ya yi ya zauna yana faɗin "Yanzu kai Imran kana da tabbacin wannan yar Nawazudden ce?" Gyaɗa mashi kai Imran ya yi kafin ya ce "Har cikin gidan su na taɓa zuwa sau uku, a nan ne ma na santa, dan ita bata wani yin media sosai, account nata ma bata da wani abu da take posting da ya wuce abubuwan addini da tunatarwa, su kawai take posting, shiyasa ma kai baka santa ba, amma ni har cikin gidan su naje sau uku shiyasa na santa". Ita dai Rimsha kasa kawai ta yi da kai tana jiran ta ji da me ya zo shi kuma. "Rimsha ina iyayen ki, ina His Excellency? Ina su mummy? Ina Jehan? Ina following nata a Instagram, lolacin da kuka yi ɓatar lokaci gudan nan, na je har gidan ku, amma gidan a rufe da kwaɗo na yi wa Jehan magana a Instagram amma shiru ba amsa, na nemeku shiru ban same ku ba, ni dai nasan kuna nan da ranku ake ta ce wa wai kun mutu a lokacin" ya kai karshen maganar kamar zai yi kuka. Kasa ta yi da kanta, wasu siraran hawayene suka fara bin kuncinta, ganim haka ya sa Imran ya ce "Ya isa yanzu ta shi muje ki kai ni wajen su Madam". Murya can kasa kasa ta ce "Ni kaɗai na rage, su mum sun ɓata ban san in da suke ba, ban san ina suka je ba, nima shekaran jiya na dawo, ina dawowa na samu wannan aiki wadda ya zama mini dole na yi shi, shine na fara yi" ta kai karshen maganar tana kokarin sakin kuka mai sauti. Cikin sauri Imran ya miƙe ya riƙo hannunta suka fice daga wajen ɗin zuwa wajen motarsa. Gidan gaba ya buɗe mata ta shiga ta zauna, shi ma ya shiga ɗayar gefen ya zauna yana kallon ta, shi kuma Nawid ya nufi wajen Ibraheem domin tambayar ina Jehan. "Rimsha ki natsu ki gaya mini menene yake faruwa kin ji? Ni yayan kine, kin sani, ina zuwa har cikin gidan ku, dan haka ki gaya mini ina His Excellency ina su Madam?". Kasa ta yi da kanta tana hawaye haka ta fara ba shi labari tun daga ranar da aka ɗauki daddynsu har zuwa yau, duk dauriya irin nasa sai da ya matse mata kwalla, ko ɓatar Jelly bai yi kuka ba amma jarabawar da Rimsha ta haɗu da shi ya taɓa mashi zuciya, ya sanya shi hawaye. Jugum-jugum suka, zauna ba wanda ya iya ce da ɗan uwansa kala, har sai da Nawid ya zo wajen sannan suka dawo cikin hayyacin su, a ruɗe Nawid ya ce "Rimsha Ibraheem ya ce mini ke kanwar Jehan ce, dan Allah a ina take? A ina zan sameta?". Ɗagowa ta yi ta kalli Imran a yayin da shima ita yake kallo, girgiza mata kai ya yi alamar ta ce bata sani ba, haka kuwa ta yi masa, kuka ne kawai Nawid bai yi ba, sannan ya kuduri niyyar nemanta koma a ina take. "Dr ka shiga mota mu wuce gida, kada mu ɓata lokaci". Jin abin da Imran ɗin ya ce na Nawid ya shiga mota su tafi, sai ta juya tana kokarin buɗe kofar motar zata fita, Cikin sauri Imran ya riƙo hannunta yana faɗin "Ina kuma zaki je?" Cikin halin nuna ko in kula ta ce "Wajen aiki na zan koma" girgiza kai ya yi yana faɗin ",Haba muna raye a duniyar nan family Nawazudden su yi rayuwar kunci, kai ina a baya ma da kikaga hakan ta faru bamu san in da za mu same ku bane, yanzu kuma gaki na ganki kuma kice zaki tafi, a'a haba ai ke daga nan sai Kaduna, idan duk wani abin da zan mallaka zai kare a kan family Nawazudden to ba zan taɓa danasani ba, daddynku ya taimakemu a rayuwa, ba zan iya kwatanta miki irin taimakon da ya yi mana ba, yau duk wani kuɗin da Abbana yake tin kaho da shi to Allah ne ya bashi kuma sanadin daddyn ku, dan haka yau rana ta yi da zan ramawa His Excellency abubuwan da ya yi mini, nasan ban isa na biya shi dukka ba, amma In Sha Allah zan yi kokari wajen ganin na baki kulawa, kuma na san cewa His Excellency ya fi son ki sama da komai nasa, yanzu dai abubuwa masu mahimmanci guda uku zan fara yi, na farko zan tafi da ke gidan mu, na biyu zan fara neman family ki ina suke, na uku kuma ki zaɓi duk makarantar da kike so a duk kasar da kike so, sai in kai ki karatu can". Kasa ta yi da kanta tana jin wasu zafafan hawaye na kokarin bin kuncinta, amma haka ta daure ta mai da hawayen nan ta ɗago kanta sama ta fara magana kamar haka "Daddyna ina alfahari da kai, ina mai farincikin kasan cewar ka mutumin kirki, yau ga shi an wayi gari baka duniyar, amma saboda kirkin ka duk in da muka shiga sai an taimakemu, ba wanda za mu zauna da shi kuma mu yi kuka babu, kowa son mu yake yi, saboda kai daddy, saboda kirkin ka da alkharin ka ga mutane, gaskiya zama mutumin kirkima wani babban baiwa ce a duniya da lahira, ko kai baiwar bata taimake ka ba zata taimaki family ka, saboda gaskiyar ka aka kashe ka, aka raba mu da kai, amma ga shi muna cin albarkaci gaskiya da kuma amanar ka, har na koma ga Allah ba zan dai'na yi maka addu'a ba daddy na" ta kai karshen maganar tare da sakin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, matsowa kusa da ita ya yi, ya ɗan riƙo kafaɗun ta yana ɗan jijjigata alamar rarrashi, a nitse ya ce "Ki yi shiru Rimsha ki dai'na kuka kin ji ko? Yanzu dai ki gaya mini kasar da kike son zuwa karatun sai na fara shirye-shiryen tafiyarki" kuka ya ci karfinta ta kasa magana. Ganin haka yasa Nawid ya ce "prof ka barta ta huta tukunnan, ka kyaleta zuwa gobe ko anjima sai ayi zancen school". Dawo da kallonsa kan Nawid ɗin ya yi yana faɗin "Dr ba zaka gane bane amma ba danu wa yanzu dai ka shiga muje gida, idan munje sai mu karisa magana a can". To Nawid ya amsa da shi sannan ya shiga gidan baya, ya bar Rimsha a gidan gaban. Har Imran ya tada mota cikin sauri ta ce "Ba zai yi wu in biku ba, saboda kaga aiki nake yi, sai na gama biyawa Jehan kuɗin da ta karɓa tukunnan". Abin ma dariya ya bawa Imran, cikin zola lace "Ashe first lady ta girma". Sanya kyawawan hannayenta ta yi ta rufe fuskarta tana turo ɗan baki, zuba mata ido Imran ya yi na ɗan lokacin kafin ya ce "Ke dai ba in da kika baro Madam a kamanni," ya kai karshen maganar yana mai do da kallonsa kan Nawid dake gidan baya yana fama da latsa waya. "Dr fita dan Allah ka karɓi account number Ibraheem ɗin nan ka sanya masa 1m mu samu mu tafi da wuri, kasan First lady mu daman akwai ta da gaskiya da amana kamar His Excellency, idan ba ku biya wannan kuɗin ba ba zata taɓa barinmu mu bar nan ba". Ita dai shiru ta yi tana binsu da kallo ta kasan ido. Tuna cewa 1 million Imran ya ce a bawa Ibraheem sai ta ce "Kuɗin shi 500k ne ba 1m ba" fuska ɗauke da murmushi ya ce "E na sani amma shima dole yaci albarkacin ya taimaki family Nawazudden, ni abin da ma ya fi bani mamaki ya akayi basu iya gane Jehan ba? Ya akayi ta yi aiki a nan kuma manyan mutane suna zuwa nima ina zuwa kuma bamu taɓa haɗuwa ba?". Nawid ne ya cafki zancen da cewa "Ai yanzu da na san asalin wace ce Jehan sai na gane a baya da fake face take amfani, nima na yi mamaki da kuka ce Jehan Nawazudden ce ta yi aiki a nan, wlh ba dan daga wajen yar uwarta na ji zancen ba, da ba zan taɓa yarda ba, domin ni ba asalin fuskar ta na gani ba, da asalin fuskarta ce ai da tuni na gane ta na ɗauketa in je in haɗa ta da baby uwar dirama, amma kasan abin da ya ke bani mamaki kuwa?" Girgiza masa kai Imran ya yi alamar a'a bai sani ba "Jehan Nawazudden tun tana primary 6 lokacin da ta fara media lokacin na kamu da son ta, kasan ita ko ka mata dm bata reply, naso yarinyar nan kamar hauka, amma bani da hanyar da zan iya ganinta, hakan yasa na danne na hakura ina dakon so, sai ga shi yau an wayi gari na haɗu da ita a wani irin yanayi da ba zamu ina gane juna ba, kai wannan abu ya mini ciwo sosai, ba zan taɓa mantawa da shi ba". Yar dariya Imran ya yi yana faɗin "Baka sanar da ni bane ai ni dana kai ka har cikin gidan su, His Excellency yana da kirki sosai, yana kuma kaunata fiye da tunaninka, ni bana zama a palon baki ma idan naje, kai tsaye palon gidan nake shigewa kamar ɗan gida, lokacin da na koma school ne abubuwa suka ja baya, amma duk yaran sa ba wanda bai san ni ba, kuma kamar yadda kaga Jehan a Media bata yi wa mutane magana, to haka take ko a gida ma, bata yi wa mutane magana sam, idan naje ga mai yi mini magana nan first lady, daga ita sai Aunty Aisha da Madam, ita kuma wannan mage sarkin son jiki ce, kulkun tana jikin daddynta, ko ba haka akayi ba?" Ya kai karshen maganar yana dariya yana leƙo fuskarta. Murmushi ta yi har sai da dimple nata ya lotsa, tabbas ta gane Imran amma sai dai lokacin da yake zuwa gidansu tana karama bata kai haka ba. Fita daga motar Nawid ya yi zuwa cikin restaurant ɗin, kamar yadda Imran ya ce haka ya yi, ya karɓe Account number Ibraheem ya sanya mashi kuɗin, sannan ya juya zai ta fi, cikin sauri Ibraheem ya miƙa mashi wayar Rimsha yana faɗin "ga phone ɗin ta" karɓa Nawid ya yi, sai zuba godiya Ibraheem yake yi, da haka suka yi sallama. Lokacin da ya dawo mota ya same su, Rimsha ta ɗan saki jiki suna hira da Imran, domin tun abaya ta sanshi, kuma ko ba'a faɗa mata ba tasan mutumin kirki ne, domin daddynta baya alaka da mutanen banza, duk wanda ka gani tare da daddy to yana da kirki sosai, ba mutunne wanda za'a yar ba, ba zata taɓa manta lokacin da Jehan take cewa bata son ganin Imran ba, a lokacin ya zo gidan su, daddyn su ya ce In Sha Allah in dai yana da rai sai ya aura mata Imran tun da ta raina shi, ranar wuni kuka Jehan tayi wai an kaskantar da ita, ko da wasa daddy yake yi bai yi mata adalciba, ya haɗa ta da bawansu. (Kai Jehan duniya, ka ji wai bawan su🤔) Kallonta Imran ya yi yana faɗin "First lady zamu iya tafiya?". Cikin girmamawa ta ce "Yaya Imran tun da ka ganni a nan ai kasan dole akwai wayan da nake karkashin kulawar su ko? Amma shine zaka ce mutafi ban sallame su ba?" "Afuwan our first lady yi mana jagora zuwa gidan su mu zuba musu godiya". Shiru ta ɗan yi tana tunani ko zata iya gane hanyar, dan kwana biyun da ta yi, Sadiq ne yake kawo ta kuma da yamma ya dawo ya ɗauke ta, sai dai ta gaya musu sunan anguwar kawai idan sun kai nan zata iya gane gida, haka yasa ta juya ta sanar da shi sunan anguwar, kallon Nawid ya yi alamar ko ya san anguwar, dan shi ba garinsu bane. Gyaɗa masa kai Nawid ya yi alamar ya sani, ba ɓata lokaci ya tashi motar, Nawid na nuna musu hanya suka nufi gidan su Sadiq. Kamar Kullun zaune suka isko Yusuf a kofar gida yana aikin nashi, wato sa wa mutanen da suka zo wucewa ido, ita kuma Hanan tana aikin tuyar awararta, Sadiq na gare ji bawan Allah. Kusan a tare Rimsha da su Imran suka fito, sai kallon su Yusuf yake yi. Tun daga ɗan ne sa Rimsha ta ce "Yaya Yusuf ya kake zaune a ranan nan?" Washe baki ya yi dan a tunaninsa Rimsha ba zata kula shi ba, dan ta zo da masu mota, Allah sarki bai san cewa ita Rimsha ba bakuwar arziki bace, a cikinta ta taso dumu-dumu. Ba tare da ɓata lokaci ba ta yi musu sallama ta fito, mayafi maman Sadiq ta ɗauka ta rakota har wajen motar, gaisawa suka yi da Imran cikin mutunci da girmama juna, sannan ya zuba mata godiya sosai da sosai suka yi sallama, ya ciro 200k ya bata yana kara yi mata godiya. Da farko taki karɓa, amma daga baya daya matsa mata sai ta karɓa ta yi mashi godiya, ita kuma Rimsha ragowar 4k da ya rage a hannunta ta ɗauko ta bawa Yusuf dan shine abokinta. Ɗan kwana biyun nan da tayi sun yi sabo sosai, dan Yusuf ma yana da hankali. Da haka suka yi sallama, Rimsha ta shiga mota kamar zata yi kuka, Imran ya buɗe gidan baya ya sanya mata trolley ta sannan ya shiga mazaunin driver ya ja motar suka kama hanyar Kaduna, Dr Nawid sai fama da latsar waya yake yi. (Nima kuma na haɗa kayana na nufi wajen Jehan yar amana) 💖ABUJA💖 Kata faren gida ne mai girman, wadda da kaga gidin kasan arziki ya zauna wa mamallakan wannan gidan. Hawa ɗaya ne, zaka iya saka gidan a jerin gidan manyan masu kuɗi na faɗin Nigeria. A kofar wannan gidan motar Hajiya da ta ɗauko Jehan ta tsaya tare da danna horn. Horn ɗaya mai gadi ya wangale mata gate ɗin gidan, cikin kwarewa ta danna hancin motar cikin gidan, kallon gidan nan Jehan take yi tana tunanin anya gidan nan ba wani abu kuwa, ace irin wannan haɗaɗen gida kuma azo ayi shi a keɓaɓen waje kamar haka? Dole a dasa mashi ayar tambaya, Jehan akwai kwakwalwa da kaifin basira abin ba'a magana. Tana tsaka da tunani ta tsinkayo muryar Hajiyar tana faɗin "Jehan mu je ko?" Kallonta Jehan ta yi kafin ta fito daga cikin motar, zuciyarta sai ayyana mata abubuwa da dama dangane da wannan gida take yi, domin wannan gida bai yi kama da gidan masu gaskiya ba, ya fi kama da gidan marasa gaskiya, ita kanta Hajiyar bata yi kalar masu gaskiya ba. Jehan bata karasa shi ruɗani da tantama a kan wannan gida ba har sai da suka shiga cikin palon gidan, a irin kallon da take yi wa wannan Hajiyar bata yi kala da mace mai aure ba, to waye ya bata wannan gida? Sannan me yasa za'a yi wannan gida a wajen keɓaɓe haka?. Suna shiga wani ɗan karamin yaro da bai wuci shekara biyar ba, kamaninsa ɗaya da Hajiyar nan, ya taso da gudu ya yi wajen Hajiyar yana faɗin "oyo mummy". Rungume shi ta yi a jikinta, ita ma tana faɗin "Oyoyo ɗan lele na". Mamakine ya sake kama Jehan, kenan Hajiyar nan ta yi tafiya daga nan Abuja har zuwa Katsina ta bar wannan yaron shi kaɗai a cikin gidan ne? Dan da alama ba wani motsi mutun a cikin gidan, wannan yaron shi kaɗai ne a ciki, sai mai gadi dake bakin gate. A karo na biyu ta lula duniyar tunani sai tsinkayo muryar Hajiyar ta yi tana faɗin "Jehan ga waje ki zauna mana, ki saki jikin ki fa, zuwa dare zan kai ki wajen aikin kin ji?". Ba musu ta zauna saman luntsumemen sofar dake wajen, har yanzu zuciyarta bai dai na mamakin dukiyar da aka narka wa gidan nan ba, ta dai zuba ido ta ga me zai faru. Saman sofa ita ma Hajiyar ta zauna tana sauƙe numfashin a hankali hankali, shi kuma ɗan lele da gudu ya nufi cikin ɗaki ya ɗauko cake ya fito yana faɗin "Mummy i want to play with this cake". "Go ahead mana my ɗan lele" ta faɗa tana ƙoƙarin fito da wayarya daga cikin jakarta. Kusa da Jehan ɗan lele ya zo ya zauna, tare da fara ɗaban cake ɗin yana shafa mata a fuska, kamar ta ce mashi ya yi mata hakan. "Ɗan lele me yasa kake ɓata mata fuska da jikinta haka? Ka bari mana, baka ga bakuwa bace?" turo baki ya yi yana faɗin "A'a mummy ni ina son ɓata mata ko ina a jikinta ne". Murmushi Hajiya ta yi tana faɗin "To ɗan lele na, amma da ka barta ai". Wani mugun kallo Jehan tabi Hajiya da shi, a ranta taka maimaita abin da Hajiyar ta faɗa, wato ɗan lele ya ci gaba da ɓata mata jiki, su ga su ƴaƴan masu kuɗi, komai suka yi daidai ne, basa laifi. Tana tsaka da tunani, ɗan lele ya ɗebo cake yana kokarin cusa mata a cikin hancinta. Wani gigitatcen mari ta sakar mashi, wadda ya sanya shi tafiya ta baya baya, ya buga kai da jikin table, da karfi ya fasa ihu mai raza kwakwalwar mai sauraro, ita kuma Jehan miƙe wa tsaye ta yi, rai a matukar ɓace ta ce "It seems like you have not been morally train in this house, and I will give you instantly, be get prepare" (Toh fa ɗan lele ga maganin ka nan ta zo gidan, sai ka shirya.🤣) A zafafe Hajiya ta miƙe cikin tsawa ta fara magana, da karfi-karfi "Akan me zaki mare shi Jehan? Dan ya saka miki cake a jiki? Baki ganin yaro ne shi?!!". Ko kallon in da take Jehan ba ta yi ba, shi kuma ɗan lele sai kuka yake yi yana birgima a kasa, irin dai sangartattun yaran nan. Komawa Jehan ta yi ta zauna saman sofa tana ɗaure fuska, domin a cewar ta bata da lokacin ɓata bakinta wajen bawa Hajiyar nan amsa. Da kamar Hajiyar zata sake yin magana, amma kome ta tuna sai ta fasa ta ɗauki wayarta da jakarta tare da ɗan lele suka wuce sama bene. Kallon banza Jehan ta bisu da shi kafin ta dawo da hankalinta kan binciken da tunanin a kan gidan. Hajiya kuwa tana shiga cikin ɗauki ta rarrashi ɗan lele, bayan ya yi shiru ne sai ta ɗauki wayarta ta danna kira. Jim kaɗan a kayi picking call ɗin, kamar tana gaban wadda take waya da shi, cikin girmamawa har tana wani yin kasa da kai ta fara magana "Allah ya taimake ki ranki ya daɗe, yau fa Allah ya yi zan cafki kuɗi yadda ya kamata" shiru ta ɗan yi da alama tana sauraron abin da ake faɗe a ɗayar ɓangaren ne, ma'ana tana sauraron abin da wadda ta kira ɗin take faɗe. Bayan wasu yan sakannin da ba su 30 ba, sai ta cigaba da cewa "Wlh ranki ya daɗe yarinya ce bata san komai ba, kuma idan kin ganta ko ke sai kin ruɗe kyakkywa ce, amma fa nasan idan kika ganta zaki iya gane yar wace ce, yarinyar Nawazudden ce, kin san sun yi haɗarin mota ya rasu, to ashe familynsa suna Katsina dana je duba kanwar kawata ɗin nan da abin ya sha kan taaaaaa, to a nan naga Jehan". Shiru ta sake yi tana sauraron abin da ake faɗe a ɗayar ɓangaren bayan ta kai aya. Bayan ɗan lokaci kamar minti ɗaya sai ta ce "E da farko da fake face take yawo, nima ban gane taba, sai da na ce zan ɗauketa shine iyayen nata suka gaya mini gaskiya, sai na ce to ta cire fake face ɗin dan yanzu mutane ai sun fara mantawa da ita, wasu ma sun mance da ita, dama kin san Jehan akwai kyau iya kyau, wlh zaki samu kuɗi bana wasa ba" dakatawa ta yi dan jin me wacan ɗin zata ce. Bayan ta gama ji sai ta ce "To shikenan kamar dai yadda aka saba, shabiyun dare na cika daidai zan kawo ta, amma fa kin san bata san komai ba kada ki bari su zinariya su taɓata har sai kin dawo, sai ki ɗaurata a kan hanya da kanki". Shirun minti biyu ta sake yi kafin ta kwanshe da dariya ta ce "Gaskiya na ji daɗi, amma da an kara mini wani abu a saman 1 million ɗin, kin ga fa budurwace". Dif ta ji an katse kiran ma'ana kenan ciniki ya faɗa Millon ɗaya aka sayi Jehan. (Toh fa babbar magana🤔) Bayan ta kammala wayar ta ajiye ta miƙe ta sauƙo Palo, yadda ta bar Jehan ɗin haka ta dawo ta sameta, shi kuma ɗan lele dama tun lokacin da ta fara waya ya fice abin shi. Da kanta ta kawowa Jehan lafiyayyen abinci har da ruwan sha, har cikin zuciyarta Jehan tana tantama a kan wannan matar, amma da yake tana jin yunwa sai ta sauƙo ta ci abincin, bayan ta kammala Hajiyar ta nuna mata ɗaki akan ta shiga ta kwanta ta huta zuwa dare sai suje wajen aikin. Ba musu ta wuce zuwa ɗakin, ita ma Hajiya ta wuce ta koma sama abinta, ranta fes yau ta kawo mai tsoka an bata 1 million. After some hours 👌 Karfe 12 na dare daidai motar wannan Hajiya ya fito daga gidan ta ya miƙi wani hanya, kai daga ganin irin wannan fita kasan babu gaskiya ko kaɗan a cikinta, ita kan ta Jehan sai mamaki take yi, anya ba wani abin a kasa kuwa? Kamar wasu munafukai, fita tsakiyar dare, kai ba'a kulla gaskiya a wannan lamarin ba kwata-kwata. Sun yi tafiya mai ɗan nisa kafin su iso wani sihir tatcen gida cikin gidan. (Tofa gida kuma cikin gida?🤔) Da farko idan ka shigo gidan zaka yi tunanin normal gida ne kaman ko wani gida, sai dai ba hakan bane, ginin gaba anyi shine kamar normal gidan mutane, while daga baya kuma ta ciki aka yi wani irin tsantsarerren gida wadda kusan rabin shi a cikin kasa yake, hakan yasa ba zaka sami damar ganin wannan ginin daga ta waje ba, sannan ta bayan wannan ginin sirrin akwai wani gini shima mai kama da gidan mutane, a takaice dai gini a kayi kamar normal wadda ya kewaye wannan ginin sirrin dan kada a gane me yake ciki, idan har ba shigo da kai akayi ba, ba zaka taɓa tunanin cewa akwai wannan gini a wajen ba. Horn ɗaya Hajiyar nan ta yi masu ganin wajen suka wangale mata tampatsetsen gate ɗin gidan. Kutsa hancin motarta ta yi zuwa cikin gidan, a parking space nasu ta yi parking sannan ta fito tare da faɗin Jehan ta fito su tafi. Ba musu Jehan ta fito suka kama wani ɗan hanya a wajen suka fara tafiya, ginin farko akwai wutar lantarki a wajen, haske ko ina, amma da suka ratsa cikin gidan zuwa gini na biyu sai taga wutar ginin na biyu daban dana farko, wuyar wajen green ne da kuma blue ba su da haske sosai, sannan ginin dake kewaye da wannan suna da tsawo sun kare wannan ta yadda ba wanda zai iya ganin wannan daga ta wajen. 🏬*A company of quality Prostitutes*🏬 Shine abin da Jehan tagani an rubuta a kofar shiga wajen, mamaki ne ya kara bayyana a kan fuskar ta, amma ta kasa yin magana domin bata ma san me zata ce ba. Wani kafataren palo suka fara cin karo da shi, palon ya ji komai da ake buƙata, sai dai an yi wa palon tsari irin na office ne, idan ka ga palon zaka yi tunanin office ne, amma fa ya haɗu sosai da sosai, saman sofa suka zauna, daga gefe a cikin palon, wani kyakkyawar table ne mai ɗan girma sai kuma office chair a wajen, da alama dai wajen manager company ne. Wani katon hoton ne ke manne a jikin bangon kusa da table ɗin ta sama, hoto ne wadda ko ba a faɗa maka ba kasan cewa wannan hoton mamallakin wajen ne, irin hamshaƙan matan nan ne, wadda Naira ta zauna musu, farace tas amma kana gani kasan farin bilicin ne, ga hancin nan nata kamar me a bage a kumatun nata, ga kofofin hancin nata a buɗe kana hango har canciki, amma a haka ta zo ta damɓara hujin hanci ta kuma saka wani katon yan kunne, abin ba kyan gani ita a dole ta yi kwalliya, a dake take saman wani haɗaɗɗen kujera irin na gidan sarautar nan, tana hakimce ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya, kai daga ganin wannan matar kasan ba sauƙi, dan ga shi a hoton ma fuskarta babu alamar annuri ko kaɗan, inaga kuma anzo zahiriyya? Ta ci uban make up a fuskarta, ga eyelashes da ta tabka a ido kamar bindin kaza, duk da wannan kwalliya da ta sha, hakan bai hana ka ganin muninta a filliba, mummuna ce sosai, daga gani wannan kabilace ba hausa fulani ba ce. Ta shagala da kallon wannan hoton tana mamaki sai sinkayar Muryar hajiya ta yi tana faɗin "Jehan ta shi ku je ko" cikin sauri ta dawo da kallonta kan Hajiya, sai ta ga wata matace ke tsaye a kan su, ta shiga duniyar tunani kwata-kwata bata ga shigowar matar bama. Matar irin Hamshaƙan tantiran yan duniyar nan ne, ta wani ci uban make up ga eyelashes ita ma a idonta kamar bindin zakara, ta ci matsu riga t-shirt da wando guntu zuwa gwiwarta, kayan sun matseta over, idanunta a buɗe garau suke, babu alamar kunya bare tsoron Allah, kai daga gani kasan bariki ya yi musu katutu, da alamama bariki ta kusa yayesu ma, amma kuma a shekaru ba zata wuci 35 years ba. Ba musu Jehan ta miƙe ta bita, domin dama ta ƙagu ta shiga cikin gidan nan dan ta ga me suke aikatawa a cikin shi, sannan kuma aikin me zata yi. Suna shigewa cikin gida Hajiyar nan ta tashi ta fita zuwa wajen motarta, ta shiga ta bar gidan baki ɗaya ta koma gidanta. Ita kuma wadda ta tafi da Jehan, bayan sun shiga cikin gidan, ɗakuna ne a gere a gere, a rufi ɗaya kamar hostel na student, ko wani ɗaki da number a jikin shi. Daidai tsakiyar wajen suka tsaya matar ta ce "Shekarun ki nawa?". "16 to 17 Jehan ta bata amsa. Wucewa gaba matar ta yi ba tare da ta sake yin magana ba, bin bayarta Jehan ta yi har suka je wajen wani ɗaki da aka sanya number 17 a kofar ɗakin, da hannun matar ta nuna mata ɗakin a kan ta shiga, ba musu ta buɗe kofar ɗakin ta shiga bakinta ɗauke da sallama. Ɗaki ne kamar ko wani ɗaki, sai dai kuma gadaje huɗu ne a cikin ɗakin, shiru ta yi tana kallon yan matan dake kwance a saman gadaje biyu daga ciki gadajen. Shiru ta tsaya ta kasa gaba ta kasa baya, kawai kallon ɗakin take yi. Kamar daga sama ta ji an taɓata ta bayan ta ana faɗin "Barka da zuwa gidan farinciki". Cikin sauri ta juyo da yake wutar ɗakin nasu green color ne baka iya ganin fuskar mutun da kyau, sai Jehan bata sami damar gane wace ce ta yi mata magana ba. Hannunta yarinyar ta ja zuwa saman ɗaya daga cikin bed ɗin ɗakin, sannan ta miƙe ta canza musu wutar ɗakin zuwa blue light dan su samu damar ganin juna. Bayan ta kunna ta dawo ta zauna kusa da ita tana faɗin "Garama ki saki jikin ki domin ba bu wani abin da kamewa zata yi miki a nan". Ita dai ido kawai ta ke binsu da shi. Hannu yarinyar ta sanya tana bubbuga yan mata biyu dake saman nasu gadon tana kiran sunayen su, da yake gadon nasu kusa da kusa yake da juna. "Aisha Adiva ku ta shi ga bakuwa mun yi" miƙa Aisha ta yi kafin ta miƙe zaune tana faɗin "Sabuwar jini ce ko tsohuwa?" Duka yarinyar da ta tashe sun ta kai mata tana faɗin "Ke dai wlh Allah ya shiryeki" daidai lokacin wadda aka kira da Adiva ta farka daga barci tare da miƙewa zaune a tsakiyar gadon. Duk da blue light da yake a cikin ɗakin bai hana Jehan gane furkar wadda ta miƙe yanzu ba, cikin sauri da ɗan karfi ta furta "Adiva me kike yi a nan? Ina daddy?" Ita ma Adiva ta gane Jehan, waro idanuwanta waje ta yi tana faɗin "Jehan ai ke zan tambaya me kike yi a nan? Ina kuma daddyna yake?". Tofa zuba musu ido A'isha da Maryam suka yi. Matsowa Adiva ta yi ta riƙe hannayen Jehan ɗin ta fara hawaye tana faɗin "Jehan dan Allah ki gaya mini ina daddy na yake? Tun da ya fita bai dawo ba" kankameta Jehan ta yi kafin ta ce "Adiva ki ajiye zancen su daddy yanzu, zamu yi shi daga baya, ni abin da nake son sani me wannan gida yake nufi? Ku yi mini bayani, ni a farkon shigowata naga ansanya A company of quality Prostitutes ina bukatar karin bayani a kan shi!". Shekewa da dariya Aisha ta yi, zuba mata idanu suka yi suna kallonta, sai da ta yi mai isarta sannan ta ce "Ni zan gaya miki gidan menene wannan" kasa kunne Jehan ta yi tare da tattara hankalinta izuwa ga A'isha'n dan ta ji gidan menene. Nan fa Aisha ta fara basu bayani kamar haka. "Company of quality Prostitutes gida ne da Hajiya kankana ke shigo da mata kala-kala kamar yadda aka shigo da ke, idan nace mata kala-kala ina nufin ko wace iriyar mace da wuya idan ba zaki sameta a nan ba, kama daga matan aure, zawara, yan mata, yara, manyan, tsofafi, ke harma da mahaukata" zaro idanu waje Jehan ta yi tana maimaika kalmar mahaukata kuma. Dafata Aisha ta yi tana faɗin "Ki natsu zan warware maki komai a hankali, dan ni kaɗai ce a cikin ɗakin nan zan iya gaya maki asalin gidar hajiyar daɗi ko kuma hajiya kankama duk wanda kika kira dai dai ne, wayan nan da kike gani, Adiva da Maryam shekaran jiya aka kawo su, ni kuma na kai shekara ɗaya a nan, tun ina ɗakin yan 16 years, har aka dawo da ni nan wajen, so na san komai dan haka ku saurareni kawai. Hajiyar daɗi da kuke jin nan, hamshakiya ce, tana da kafa a wajaje da dama, sana'ar tane wannan harkar da kuke gani, bari na fara muku daga kan matan aure, akwai matar aure a harkar nan nata sosai, domin wasu alazawan sun fi son matan aure, saboda wani dalili nasu na kansu, mafiya yawancin matan auren da suke shiga wannan harka, yawancinsu mazansu ba mazauna bane, wasu kuma mazan su basu basu kuɗin kashe bukatun yadda ya kamata ne, wasu kuma mazansu basu biya musu bukatun su ne, shiyasa Hajiyar daɗi take janyosu a jiki ta rinƙa kashe musu kuɗi tana gyarasu sai ta rinƙa gaɗasu da manyan alazawan ana harka, amma fa kashe mu raba suke yi, ba karamin kuɗi hajiyar daɗi take samu a harkar ba...." Jehan sarkin hanzari ta kasa tsayawa ayi mata bayani ta katse Aisha da cewa "Ya za'ayi matan aure su zauna a cikin wannan gida? To auren nasu fa ina suke kai shi? Ina suke kai mijin nasu da za su zo su zauna a nan?" Hararar ta Aisha ta yi sannan ta ci-gaba da cewa "Ke na lura yar gaggawa ce, to yana da kyau ki koyi hakuri da juri dan zai taimaka miki, idan kika yi hakuri dukka wayan nan bayanai zan miki su, su matan aure da kike gani, Hajiya bata ajiye su a nan gidan, suna gidan mazajensu, idan mijinsu baya nan, ya yi tafiya suna kiran hajiya su gaya mata suna free, ita kuma hajiya da wani alhajin mai bukatar matar aure ya zo, zata tambaye shi irin macen da yake so, idan ya gaya mata sai ta kira irin wannan mace a waya, ke idan ma bata da irin wannan macen wlh kwana ɗaya ya yi yawa zata samo, idan ta fita taga matar aure mai irin wannan kalar haka zata bita ta fara yi mata ruwan kuɗi har ta jawo raayinta daga nan ta ɗaura ta akan hanya, sannan idan mijin mace ya kasance ba mai tafiye-tafiye bane, akwai dabarar da Hajiya take shiryawa mace idan wani alhajin na bukatarta, sai ta shirya mata karyar da zata yi wa mijinta ta fito, idan an gama komai sai ta koma gida, sannan misali yanzu idan mijin mace ya yi tafiya wani alhajin na bukatarta, tofa ba'a zuwa ɗaukarta sai cikin dare, ko kuma ita ta fito da kanta tazo wani wajen sai Hajiya ta tura a ɗaukota, yar sirri ake yin abin saboda yan kuɗaɗe kin gane ai? Kin gane na matan aure mu shiga ɓangaren yan lesbian ne ko dai kina da karin wasu tambayoyin?". Shiru Jehan ta yi tana tunanin tabbas ta taɓa jin irin wannan case ɗin na matan aure suna zina, to amma a ina ne ta manta, yanzu ace dan mijinki baya baki kuɗi sai ki shiga saɓon Allah, sannan kuma ita Hajiyar daɗi ba zata taimaka wa mace ba sai in zata mureta ita ma?, Ai da kama ta ya yi tun da tana da kuɗi sai ta bawa matan jari ta ce su je su kama sana'a su fita har kar kuɗin mazajen nasu tun da basa basu, amma sai ta rinƙa ɗora mata a harkar banza wannan bala'i da me ya yi kama, ya zama dole na san abin yi dan gane da wannan gida, dole mu san yadda zamu rushe shi koma ta wace hanya ce. Tayi nisa cikin tunanin da take yi Aisha ta katse mata tunani da cewa "Su kuma yan lesbian da kike gani, hajiya tana da mataimaka a online wayan da suke samo mata yara kanana, sai ta ja su a jiki tayi kamar karamar yarinya, ta ce ai tana son su da kawa ne, sai sun saki jiki, sai ta fara basu kuɗi a hankali-hankali har ta koya musu lesbian, kuma tana yin hakan ne saboda akwai manyan Hajiyoyin wayan da mazan su basa zama suna bukatar morewa ta lesbian, shine sai suce wa hajiya ta nemo musu yara yan shekara 15 zuwa 20 haka, shine aikin su Zinariya ta online suke nemo yara irin su facebook da sauransu, sai hajiya ta zubawa yaran kuɗi ta koya musu lesbian ta video a cikin wayarsu, idan suka iya sai ta haɗa su da wayan can Hajiyoyin, dukka kuma wannan abin ta waya ake yin shi, amma akwai yan lesbian da hajiya ke ɗaukowa na zahiri, ba na online ba, sannan akwai wayan da hajiya ke sayan su, kamar irin yaranda suka gudo daga gidan iyayen su idan za'a yi musu auren dole, ko kuma wayan da iyayen sun suka mutu suka gudo saboda wahalar matar baban su, ko kuma wayan da suke zuwa neman aikin yi, ko dai wayan da mahaifiyar su ta fita gida ta barsu da wahalar matan baba, idan sun gaji su gudo, kamar dai ni kin ganni gudowa na yi saboda za'a auramini ɗan kanin babana kuma bana son shi, ina shigowa Abuja wata mata ta ɗauke ni, na yi kwana uku a gidan ta sannan ta kawo ni nan ta sayarwa Hajiya, shine hajiya ta koya mini lesbian dan farkon zuwana wata hamshakiyar Hajiya ce ta ce tana son yin lesbian da ni, shiyasa hajiya ta koya mini, amma dai tana haɗa ni da mazan ma, sai dai ni bana son mazan nan nafi son mata, sunfi daɗi, kin ga Adiva tun da aka kawo su sun ki yarda da ni yarannan, har ita ma Maryam sun ki yarda, amma ban damu ba nasan dan Hajiya bata nan ne time da aka kawo su amma tana dawowa zata saita su a kan hanya, sai na cigaba da kwasan daɗi, ajiye zancen nan duk a gefe mu koma kan bayanin mu, dan ina son ki fahimci komai dan gane da gidan Company of quality Prostitutes". Jehan ta ji abin da ya goge mata hadda yau, har wani bugawa ƙwaƙwalwar ta ya yi, wannan masifa da me ta yi kama innalillahi wa inna ilaihir rajiun, kwata-kwata Aisha 17 years take da shi, amma Hajiya ta lalata mata rayuwa. Ita kuwa ci-gaba da maganarta ta yi, ko a jikinta. "Akwai manyan masu kuɗi dake zuwa har cikin gidan nan, idan sun zo suna bukatar mace, kamar idan suna son mace yar shekara sha bakwai kamar mu, to hajiya zata zo ta tsara mana kwalliya dan su zaɓi wadda suke so, sannan Hajiya tana kai mata aikatau a kasashen ketare, wadda idan ta kai ki zata yanka miki kuɗin da zaki biya ta, kamar dai a nan ɗin ma, kin ga ni 500k ta saye ni, a lokacin ina yar kauye, idan ta saye ki 500k misali ke kuma sai kin kawo mata 5 million zuwa 10 haka idan ta kai ki aiki kasar ketare, zata biya miki jirgi da komai amma zata yanka miki makudan kuɗi shi zaki biya, idan ba haka ba ta kama iyayen ki ko kuma kanwarki idan kina da ita, wayan da take kaiwa aikatau kasar waje su sai ta san iyayensu kafin ta ɗaukesu, amma mu bata bukatar hakan, kuma jama'a da aikin kai mutane aikatau suka santa, basu san wannan harka tamun ba, da kuna shigowa ba kinga wani gida a farko ba? To shine gidan ta da kowa ya sani kuma sana'ar kai aikatau aka san tana yi a cikin gidan, ba'a san gidan nan da muke cikin ba, yauwa kada na mance akwai ma maza da suke neman maza suma akwai nasu part ɗin ɗan gaba da namu, dan kin san akwai manyan masu kuɗi dake bukatar maza yan uwansu yara dan holewa, shiyasa ma wasu zakiga basu kula matan su domin suna samun maza suna holewa, shiyasa sai kiga matan ma sun faɗa neman mazan da zasu ɗebe musu kewa, abin dai duka fifty by fifty ne....." Bata kai karshen maganar ba aka buɗo kofar ɗakin. Zinariya ce ta shigo tana faɗin "Surutun me nake jiyowa daga wannan ɗakin?" Shiru suka yi, ba wadda ta yi magana. "To koma me kada na sake jin bakin wata a ɗakin nan, ku kwanta ku yi bar ci" tana kai karshen maganar ta fice tare da rufo musu kofar. Kasa kasa Aisha ta ce "Mu kwanta zuwa gobe zan karisa gaya maki me da me ake yi a cikin wannan gidan, amma fa akwai abubuwa fiye da tunanin ki" ta kai karshen maganar tare da kwanciya ta ja blanket ta rufe jikinta. Adiva da Jehan kam sun yi sumar zaune domin abin ya wuci tunaninsu. Da kyar Adiva ta iya jan Jehan suka haye gadon Adiva suka kwanta, ita dai Jehan ta kasa barci sai tunanin take yi a kan yadda maza basa iya kula da matan su har su faɗa irin wanann abin, sannan suma maza da suke bin maza yan uwansu basa biyawa matan su buƙata har matan su faɗa irin hannun hajiyar daɗi, wannan bala'i da me ya yi kama, Hajiyar daɗi ta koyawa yara kanana lesbian a online sannan idan ta gama ta barsu ba kullun take basu abin biyar buƙata ba, dole suma su fita domin neman wasu na kusa da sun dan biyar bukatarsu, shiyasa wannan ta koyawa wannan wannan ta koyawa wannan har abin ya yi yawa, ya yaɗu sosai, wannan bala'i dayawa take Allah ka tsinewa mutane irin Hajiyar daɗi. Sai kusan asuba Jehan ta samu barci ya yi awon gaba da ita (*Ni kuma na kwashe kayana zuwa gidan Abbi, wata kila kafin na dawo Jehan ta farka, amma me kuke tunani zai faru a gidan hajiyar daɗi? Jehan zata yarda ta zauna kuwa? Duk da ance Hajiyar daɗin ta wata irin siga take jan ra'ayin mutane, kuna ganin ra'ayin Jehan zai jawu kuwa? Tofa a wani part za'a sanya mana Jehan ɗin mu?🤔 Nayi nan sai kun zo*) 💖💖GIDAN ABBI💖💖 Aunty and Ayla, zaune suke a katafaren palon kasan na sabon gidan da suka koma, sai hira suke yi abinsu, Ayla na bata labarin abubuwan da suka rinƙa yi ita da Rimsha, sai murmushi Aunty take yi, idan ta ji wani labarin kuma sai idanuwanta sun kawo ruwa. Sun nutsa cikin hirarsu, suna yi ne cike da girmama juna da kuma kaunar juna. Kamar daga sama su ka ga faɗowar mutun cikin palon, ba karamin tsorata suka yi ba, babu ko sallama ta shigo musu cikin palon, wani irin taku take irin na kasaitattun matan nan, babbar mace ce, jikinta na sanye da wani dankareren lace mai bala'i kyau da tsada launin pink color, hannunta da wuyarta dukka shake suke da kayan ado na gold, wato sarka da abin hannu, sai ta shin wani fitinannen kamshi turaren humra take yi, ɗinkin doguwar riga aka yi mata, irin ɗinkin manyan Hajiyoyin nan, ta yafo wani ɗan iskan karamin mayafi a kafaɗarta, ɗayar hannunta na riƙe da jaka irin suwaga bag ɗin nan mai bala'i kyau, while ɗayar hannun nata na riƙe da wayarta kirar Iphone 14, sai wani taunar chewing gum take yi, kafar ta na sanye cikin plat shoe dukka Pink color, ta sha make up kamar kamar yarinya, alhalin babbar mace ce ba karama ba, tana da matsakaicin jiki haka zalika tana da matsakaicin tsawo, farace amma ba tas sosai ba, da ka ganta kaga jinin kanuri wato barebari, tana da kyau daidai gwargwado. A tsakiyar palon tazo ta tsaya tana karewa ko'ina na cikin palon kallo, mamakin irin dukiyar da aka narka wa palon nan take yi, tamkar bata san da su Aunty a palon ba, sai wani ɗage hanci sama take yi. "Malama lafiya kika shigo mini gida babu ko sallama?" Cewar Aunty. Yadda kasan kurma haka wannan Hajiyar ta kasance, ba wadda ta kalla a cikinsu, bare ma har su saka ran zata amsa musu. Ganin haka yasa Aunty ta ɗan tsorata saboda duniyar yanzu ba abin yarda bace, jikinta har ya fara kerma, da sauri ta ɗauki wayarta ta fara kiran layin Irfan, bai ɗauki wayar ba, hakan yasa ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya domin ta samu natsuwa, saboda ta san su Irfan ɗin suna nan kenan, domin dama haka yake yi mata, in dai ta kira shi yana gida to baya ɗaukar kiran, sai dai ya baro part nasa ya zo ya ji da kunnansa kiran me take yi mashi. Ai kuwa hakan ne ta faru, ba'a fi minti biyu da kiran da ta yi mashi ba, sai ga shi nan ya shigo bakinsa ɗauke da sallama. Cak ya tsaya ya kasa karisowa cikin palon, zubawa Hajiyar nan ido kawai ya yi yana kallon ta, ganin abin yake yi tamkar mafarki yake yi, ita kuwa Hajiyar har lokacin bata ɗago ido ta kalli mutun ɗaya daga cikin su ba, palon kawai take bi da kallo. Sun jima a haka ba wanda ya yi wa ɗan uwa magana har sai da daddyn Jelly ya shigo cikin palon bakinsa ɗauke da sallama, ya zo duba Ayla ce dan tun safe yau ban sake ganin taba. "Lafiya Irfan ka tsaya a nan baka shiga ciki ba?" Yar firgita ya yi kafin ya buɗe baki yana kokarin yin magana kenan wannan Hajiyar ta riga shi da cewa "Ba dole ya tsaya a wajen ya kasa magana ba Maik, ai kasan ya ga dodanniya ne a cikin palon shiya sanya". Sai lokacin daddy Jelly ya kai kallonsa kanta, haka zalika sai lokacin ya san da ita a cikin palon, ɗaure fuska sosai ya yi rai a matukar ɓace ya ce "E ba shakka dole mana, ashe dodanniyar ya gani da gaske, a'a Irfan banga laifinka ba dole ka kasa shiga daga ciki, ke Hadizatu wlh idan akwai abin da ya fi dodanniya annoba to kece!!". Ya yi maganar yana kare mata kallon. Jin abin da ya faɗa yasa ta bushe da wani irin dariyar shakiyanci, zuba mata ido kawai suka yi suna kallonta, sai da ta yi kai isarta sannan ta tsagaita tana kare musu kallo, "Wato kai AbdulMalik har yanzu baka chanza ba, to point of correction ba Hadizatu sunana ba Khadijat, ka rinƙa kara T a gaba saboda sunan ya fita sosai". Saboda tsabar bakin ciki, daddyn jelly ji ya yi kamar ya je ya shaƙeta ta mutu kowa ya huta bala'i kawai. "Yaya Maik wace ce wannan ɗin?" Aunty ce ta tambaya tana kare mata kallon. Satar kallon Irfan ya yi kafin ya ce "Hajizatu kenan mahaifiyar su Aafia tsohuwar matar yaya Deen..." Bata bari ya karisa ba ta ce "Kai kai kai haba Maik ya za ka ce mini tsohuwar matar Deen? To idan ma haka kake tunani tun wuri ka canza domin ni na wuci tsohuwa, ko ka mance bai sake ni bane? To idan ka mance na tuna maka, kuma nan da sati mai zuwa zan dawo ɗakin mijina, domin wannan gida gidan Khadijat ne, da ni ya dace" (Babbar magana,😯 ɗan sanda yaga gawar soja!!) Wani dukan uku uku Aunty ta ji gabanta ya yi, da kyar ta iya haɗiyar wani wahalallen yawu mai wuyar wucewa, nan take zufa ya fara tsastsafo mata daga gefe da gefen kunnen ta, wani irin jiri ta fara gani tare da wasu taurari masu haske suna gilma mata ta gaban idanun ta, ta kasa sake yin magana, ta yi mutuwar zaune. Daddyn Jelly, Irfan, Ayla duk sun lura da halin da ta shiga lokacin guda, dama kuma sun san za'a yi hakan, domin ko da da Aafia kawai ka zauna ta ishela bala'i ta wannan duniya, ballantana uwarta gaba ɗaya, Hadizatu bala'i, Hadizatu gobara daga kogi kasheki sai dai lillahi, da Irfan da Umaisha duk basu son halinta ko kaɗan, duk da cewa ita Umaisha tana karama ummun tasu ta bar gidan, amma duk da haka ta san bala'i Ommun tasu, lokacin da ta bar gidan ba karamin daɗi su ka ji ba, bawai dan ba su son taba, sai dan abubuwan da take yi wa Abbi, a lokacin ba shi da kuɗi, idan ya zo fita bai bata kuɗin cefeneba ko kuma ya bata kaɗan, wuyar rigarsa take kamawa ta cima shi mutunci fes, kuma haka zata yi girki ta hana shi, wani lokaci Umaisha ke ba shi abincinta, sai dai ko ta bashi baya ci, hakan yasa ya dai'na tunanin cin abinci a gida, daddyn Jelly yasan komai da yake faruwa a lokacin, dan lokacin shima yana Kaduna bai koma Kano ba, daga baya ya koma Kanon. Wani lokaci ma har kusan faɗa suke yi da Hadizatu, bata da mutunci ko kaɗan. Jugum-jugum suka yi dukkansu suna kallon ta, daddyn Jelly ya ce "Irfan zaka iya tafiya" ba musu Irfan ya wuce part nasa dan dama kamar a kan kaya yake tsaye, yana jin zafin ya ga ana ciwa mahaifiyarsu mutunci, amma koma me ita ta ja ma kanta. Irfan na tafi daddy ya ce "Wlh Hajizatu, ki zo ki wuce ki fita daga gidan nan ko kuma in taka wuyarki, kuma bari kiji ko mafarki kika yi kin dawo gidan nan a matsayin matar yaya Deen, to idan kin farka kiyi sadaka, wlh baki isa ina raye ki dawo ki sake kuntatawa rayuwar ɗan uwana ba, Allah ya rufa mashi asiri ya huta da bala'in ki shine yanzu zaki ɗebo jiki ko? Dan kinga yanzu ya yi arziki, to wlh baki isa ba, dama tun farko akasi aka samu wajen haɗa jini dake, da kuma mukaddari daga Allah, to yanzu tun da Allah ya yi mun raba gari ki yi maza ki kama kanki, ko yaya Deen bai sake ki ba ni na sake ki saki uku a madadin shi" ya kai karshen maganar yana yiwa Ayla alama da hannu a kan ta tashi ta shiga ɗaki. Ba musu ta miƙe ta haye sama. Takowa Ommu ta yi, irin takun nan na nuna isa, har gaban shi ta zo ta tsaya, from head to toe ta kare masa kallo sannan ta ce.......✍️ Sai mun haɗu ranar Monday idan mai dukka ya kai mu dan mu ji me Ommu za ta ce wa daddy... 💖💖TRIPLET'S💖💖 E41-42 Takowa Ommu ta yi, irin takun nan na nuna isa, har gaban shi ta zo ta tsaya, from head to toe ta kare masa kallo sannan ta ce "Kayi kaɗan Maik, kuma ka kwana da shiri kamar yadda na gaya maka, next week ina nan dawowa, domin wannan gidan gidan Khadijat ce" ta kai karshen maganar tare da fice daga cikin palon fuuu kamar kumfa. Dawo da kallonsa kan Aunty da ta yi mutuwar zaune ya yi "Ki yi hakuri Sadiya, kuma kada ki ɗauki zancen nan nata kin ji?". Gyaɗa mashi kai kawai ta yi alamar ta ji, amma cikin zuciyarta ita kaɗai ta san me take ji. Karisowa cikin palon ya yi, ya zauna saman sofa yana faɗin "A kira mini babyn daddy mu ɗan yi hira". Murmushi Aunty ta yi tana faɗin "Yaya Maik ko dai za mu aura maka ita ne? Dan ka fita daga cikin wannan gwabrancin na shekara da shekarun, Wlh tana da hankali sosai". Dariya ma abin ya bashi, abu kamar wasan yara, cikin raha da wasa ya ce "To ai dama aurentan zan yi, kinga idan Allah ya yi muka gane Jelly sai na haɗa su na riƙe su sanya mini hawan jini da ciwon zuciya na mutu da wuri ku huta". Yar dariya Aunty ta yi kafin ta ce "Kai yaya Maik yanzu me jalila take yi maka da za ta iya sanya maka hawan jini? Sannan ita ma Ayla banga wata matsalar a tattare da ita ba" "Ke dama ta ina zaki ga matsalarsu, ai ina rokar Allah ya sanya a gane Jelly, zan baki ita na kwana biyu, ina ga ko kwana ɗaya ma ba zata yi ba, zaki dawo mini da aba ta" kara faɗa murmushinta tayi tana kwalawa mai aikinta kira. Da sauri yarinyar ta zo tana faɗin gata nan, umarni ta bata a kan ta kira mata Ayla, to ta amsa da shi, sannan ta tashi ta haye sama. "Yaya Maik ni fa ba zan taɓa gajiya da Jelly ba, ni ban ma san me ta ke aikatawa da kake cewa babu mai iya ta ba sai kai ba, ban taɓa zama da ita ba, amma ina ji a jikina tana da kirki da hankali sosai" jinjina kai ya yi irin alamar abarkaza cikin gashin ta, sannan ya ce "Ai ni yanzu ma ina tausayawa duk wayanda Jelly ke hannunsu, addu'a nake yi Allah ya dawo mini da abata lafiya" Amin ta amsa da shi, sannan ita ma ta kara mashi da nata addu'ar. Tun daga Ayla ta sako kafarta a sama benen daddyn Jelly ya tsareta da wayannan dara-daran idanun nasa irin na Jellynsa, sai kallonsu Aunty take yi tana murmushi. Kusa da shi ta zo ta zauna dan yanzu sun saba, gaishe shi ta fara yi sannan ta tambaye shi batun school, dan ya ce Irfan ya sanya ta makaranta, tana son yin karatu sosai. Sai kallonta yake yi ya ce "Sarkin son karatu ba, to yaya Irfan ɗin naki ya gama komai, saura mu jira narar Monday kawai ta yi" kayatatcen murmushi ne ya bayyana a kan fuskarta, sannan ta sanya hannu ta rufe fuskarta. "To jeki ki shirya mu je shopping a sayi wasu abubuwan buƙata na school dana gida". Da sauri ta miƙe tana faɗin "to daddy". Binta da ido ya yi har ta kurewa ganinsa, sannan ya dawo da kallonsa kan Aunty dake ta kallonsu tana murmushi. "Kina bukatar wani abin ne idan muka je shopping ɗin Sadiya?" Ya tambaya yana ƙoƙarin miƙewa. Cikin sauri ta ce "Yaya Maik zauna mu yi magana", ba musu ya koma ya zauna yana kallon Tv dake magana kasa kasa, dan shi dama idan ba dole bama baya son shigowa part ɗin Abbi, sai dan ya zamar mashi dole, haka idan ya shigo ko ɗaga ido baya yi ya kalli Aunty har sai idan bisa kuskure, ko zai kalli wani abin, kallonsa ya faɗa kanta. "Yaya Maik wlh Allah kana son Ayla, me yasa kake ɓoye mana?" Wani irin murmushi ya yi wadda take fita da ɗan sauti kamar dariya. "Yanzu Sadiya ni na ce maki ina son Ayla? Me yasa kike haɗa ni da yar cikina ne? Kawai wlh tausayin ta nake da kuma kaunarta kamar yadda nake son Jelly, sannan kuma tana da hankali sosai, ga son karatu shiyasa nake jin ta a rai na, kuma nake son ganin ta kusa da ni tana farinciki, daɗin daɗawa kuma, ita marainiya ce a halin yanzu". Ita ma Aunty kara faɗaɗa murmushinta ta yi ta ce "Yaya Maik wlh ba iya kaunar uba da ƴa kake yi wa Ayla ba, wlh kana son ta, so na soyayyar miji da mata, kai ne dai ba zaka yarda ba, amma tun jiya na fahimci hakan". "Sadiya baki son zaman lafiya na lura" ya kai karshen maganar yana miƙewa, "Yaya Maik cewa fa na yi ka zauna muyi magana, to ai bamu kammala maganar ba, ina kuma zaka je?". Ba musu ya koma ya zauna yana faɗin "To maganar taki ce na lura kwata-kwata bana tsayawa a saurara bane, saboda zancen naki bai ɗauki hanyar da hankali zai kama ba". Aunty zata yi magana Ayla ta sauƙo kasa, jikinta na sanye da hijabinta har kasa, wadda Ahmad ya saya mata, zuba mashi ido Aunty ta yi tana kallon yadda yake kallon Ayla, a cikin zuciyarta tana faɗin "Wlh yaya Maik ko kana so ko baka so ka kamu da son yarinyar nan, garama ka yi sauri ka auri abarka tun kafin arigaka, gamu da matasa a gida, suma kuma suna zuwa da abokan su, kana yin sake wani zanyi wuff da wannan santaleliyar yarinyar, ka dawo kana gwara kai da bango kana dana sani". Kusa da shi Ayla ta sake dawowa ta zauna tana faɗin "Daddy na gama shi" ɗan ɗaure fuska ya yi kafin ya ce "Waye ya ce maki ki sanya perfume a jikin ki?" Kasa ta yi da kanta, cikin girmamawa ta ce "Kayi hakuri daddy". Kara ɗaure fuska ya yi ya ce "A'a ba zan hakura ɗin ba, koma ki canza kayan kisa wasu wadda ba perfume sai ki zo mu tafi". To ta amsa mashi da shi sannan ta miƙe ta koma sama, Aunty dai tana ganin ikon Allah kishi karara daddyn Jelly yake nunawa a fili amma sai ya ce ba son Ayla yake yi ba tausayinta yake yi, ina aka taɓa yin hakan?. Shiru suka zauna har Ayla ta canza kaya ta dawo. Miƙewa ya yi, ya yi gaba ta bi bayansa tana yi wa Aunty sallama. Fatan alkhari aunty ta yi musu a bayyane, daga ta ciki kuma ta yi musu fatan Allah yasa kafin su dawo sun kullu soyayya, dan tana bala'in son daddyn Jelly ya auri Ayla, ta san idan ya aureta zata samu farinciki fiye da tunanin mai tunani, mutumin kirkine sosai daddy, ga son mutane, sannan ya iya aikin komai na gida, yana da kula da yan uwansa ma bare kuma matansa, ga riƙo da addini, ya san darajar mace, ta ko'ina ya haɗa, idan Ayla ta same shi zata fita daga wannan kukan maraicin nata da take yi. Haka Aunty ta zauna tana ta tunane tunane. Su Ayla kuma sun wuce shopping. Ni kuma na tattara kayana na wuce izuwa Washington DC dan jin wace waina ake toyawa. 💖💖Washington DC💖💖 Misalin karfe 8 na dare, Musharraf na kwance saman bed nasa, shi kaɗai a ɗakin, shi kuma Michael ya fita palon kasa. Kamar a mafarki ya rinƙa jiyo motsi kamar na mutun, idan ya tashi ya duba kuma, sai ya ga wayam ba bu komai, wani lokaci ma inuwar abu yake gani kamar mutun kamar wata halittar da ban, ta bakin kofa, amma idan ya tashi zai duba sai inuwar ta ɓace, abin har ya fara bashi ɗan tsoro-tsoro, tunani ya fara yi a kan mafarke mafarken Michael da ya rinƙa yi daren jiya, abin ya fara ɗaure mashi kai, shin meke faruwa acikin wannan gidan ne? Ya faɗa a cikin zuciyarsa. Kamar a mafarki ya ji an kara masa karfin gudun Ac ɗakin, cikin sauri ya miƙe yana kallon yadda Ac ke gudu, ɗaukar remote ya yi ya rage gudun. Yana ragewa tun bai ajiye remote ɗin ba Ac ta sake kure gudun da kanta, a sukawane ya zaro idanuwansa waje yana kallon samar. Da karfi-karfi Ac ke futa har kamar zata tarwatsa kanta, banda sunan Allah ba bu abin da yake iya faɗi a cikin zuciyarsa, ya tsorata sosai, wutar ɗakin ne ya fara rawa ya kawo ya ɗauke kamar spark na wutar nepa, bai ankaraba ya ga samar ɗakin nasa yana ƙoƙarin faɗo mashi a kansa, runtse idanuwansa ya yi yana ihu tare da furta sunan Allah a cikin ihun nasa, ya aza hannun bisa kayinsa yana jiran faɗowar ɗakin kawai a kansa. Tsawon minti ɗaya ya ji shiru, ba wani abin da ya faɗo mashi, cikin sanɗa da dabara ya yi kokarin buɗe idanuwansa. Ai kuwa yana buɗe wa ya yi arba da wata iriyar halitta mai bala'in munin gaske, yar karama kamar mage, ga idanunta kamar na mutun, sake runtse idanunsa ya yi ya kurma wata razananiyar ihu da karfi!! Wadda da ka jita kasan ba ta lafiya bace. Yana tsaka da ihun sai ya ji an taɓa shi, a zabure ya buɗe idanuwansa, a zuciyarsa yana ayyana yanzu kuma dame zai yi arba. Tga ne tsaye a kansa, ga su John a gefe. Wata uwar tsawa Tga ya daka mashi wadda ta sanya shi haɗiyar wata bakar wahalalliyar yawu mai wuyar wuce maƙogoro, "Why are you shouting for us here?". Tsuru-tsuru ya yi da idanu ya kasa ko motsi bare kuma magana. Ganin ya ki magana ya sa ran Tga ya kara hasala sosai, wato Musharraf ya raina shi, cikin fushi ya ɗaga hannu zai mare shi, da sauri Michael da ya shigo yanzu ya yi maza ya riƙe hannun nasa yana faɗin "Sorry uncle T, uncle ɗin James whapped kake ihu haka?". Bin ɗakin da kallo Musharraf ya yi, komai ya koma yadda yake, wannan halittar ma ta ɓace, ga kuma Ac ya koma normal gudun da yake yi, cikin sauri ya kai kallonsa saman ɗakin dan ya ga shin shima saman ya komane ko dai ya faɗo, gaba ɗayan su da suke ɗakin suma ɗaga ido sama suka yi dan suga me yake kallon. Sakin hannun Tga Michael ya yi, ya koma kusa da uncle ɗin James, ya zauna yana faɗin "Uncle lafiya me yake faruwa ne?" Kasa magana Musharraf ya yi, dan bai san me zai ce musu ya gani ba, wannan wace iriyar musifa ce ya faɗa a zuciyarsa. Wucewa Tga ya yi rai a matukar ɓace ya nufi hanyar fita daga ɗakin yana faɗin "Zan turo sojoji su ɗauki mutumin nan zuwa gidan mahaukata". A zabure Michael ya miƙe tsaye, "Uncle T uncle ɗin James ba haukaci bane, dan haka ba bu wanda zai fita da shi daga gidan nan, ai ni a gani nama ya fi ku hankali.....". Kai daga jin yadda Michael ya yi maganar kasan a matukar tsorace yake, sai wani haɗe words yake yi. A sukawane Tga ya juyo jin yadda Michael ɗin ke ta faman haɗe masa words ɗin kamar ba lafiya ba "Michael are you okey kuwa?" Gyaɗa musu kai ya yi alamar yana lafiya, shi ma John kallon tuhuma yake bin Michael ɗin da shi, domin sun ga canji sosai a tattare da shi, sannan yanzu baya shiga cikinsu suyi hira, baya zama a palo, kuma ga yawan fita da yake yi, saɓanin da a baya da baya fita, daga school sai white house, kuma babban abin da ya kara basu mamaki kuma ya ɗaure musu kai shine, na farko da ka taɓa Musharraf gara shi ka yi masa dukan tsiya, na biyu kuma jiya da kansa ya samu Lion da maganar zai koma school, abu na uku idan yana magana kamar pastor su, a cewar su, dan pastor kawai suke yi wa ganin yana magana kamar malami, to yanzu haka Michael yake yi musu magana, cike da ilimi, babu shirme kuma babu shagwaɓa sosai, duk da cewa shagwaɓar ta bishi, amma dai ya ragu sosai, yanzu idan kaga yana yin shagwaɓar ma sai idan yana bukatar wani abin daga wajen su, shine sai ya yi ta musu magana cikin shagwaɓa dan su bashi, sannan yanzu ga bala'i kaunar yan uwansa da yake yi, idan sun yi abin da ba daidai ba sai ya zauna yana ce musu hakan da suka yi babu kyau su tuba, abaya suna ɗauka cewa karatun pastor ne ya fara shiga kanshi, sai daga jiya zuwa yau sai suka fahimci ilimin Michael ya wuci na pastor, hakan yasa suka fara zargin shi, ga shi kuma idan sun tambaye shi waye ya koya mashi hakan, sai ya ce musu kawai a bakinsa ya ji ta zo masa, daga sama take zuwa. (Dama ilimi na zuwa daga sama ne? Gaskiya Michael ka iya rainin hankali) Amma fa duk wannan abin da Michael yake yi, Musharraf ya yi nasarar rufe bakinsa ne ta hanyar addu'a da kyakkyawar niya, hakan yasa Allah ya taimake shi ya rufe mashi bakin Michael ɗin, baya iya gayawa su Tga ga mai koya mashi abubuwa, a yan kwanaki biyun nan ya iya abubuwa sosai dan gane da addinin musulunci, ga ƙwaƙwalwar tasa sai kara buɗuwa take yi, da angaya mashi abu zai haddace, hakan ma yasa ya ce zai koma school ya ci-gaba da karatu. "Michael you are not okey!!" Tga ya faɗa tare da dawowa cikin ɗakin, "Uncle T like how am not okey? I didn't understand" ya kai karshen maganar tare da komawa ya zauna. Zuba musu ido Tga ya yi shi da Musharraf ɗin, yana yi musu kallon tuhuma tare da rashin yarda da su. "Where are you coming from?" Ya yi tambayar yana kallon Musharraf. Cikin sauri Michael ya ce "he is from england" ɗaure fuska sosai Tga ya yi alamar babu wasa a tattare da shi, cike da izza da bada umarni na uncle da yaronsa ya fara magana. "Michael i don't want to hear your mouth again, hey man i said where are you coming from?". "I'm from England". Musharraf ya ba shi amsa daidai da abin da Michael ɗin ya faɗa, sai dai ya yi maganar a cikin wani irin yana yi na matsananciyar tsoro da fargaba, gabansa sai faɗuwa yake yi, dan ya san basu da imani da tausayi ko kaɗan, idan suka san shi musulmi ne ba karamin azabtar da rayuwarsa za su yi ba. Furzar da iska mai zafi Tga ya yi daga bakinsa kafin ya ce "impossible!!" Satar kallon Michael Musharraf ɗin ya yi, daidai lokacin da ya miƙe yana faɗin "Uncle T please mana ka kyale shi ka ji? Shi ba mugu bane, kuma ba shida komai a ziciyarsa sai alkhari". Wucewa Tga ya yi ya fice daga ɗakin ba tare da ya sake yin magana ba, hakan da ya yi kuma ba karamin jefasu cikin ruɗani ya yi ba, musamman shi Michael dan yasan uncle T ɗin nasa da bakar zuciya kamar me, yasan ba zai yi wu ya kyale Musharraf haka kawai ba, wannan shirun da ya yi dole akwai abin da ya ayyana a ransa. Wucewa shima John ya yi ya bi bayan Tga, shi kuma Michael zama ya yi gefen Musharraf yana bashi hakuri, akan kada ya damu, haka yan uwansa suke, basu son baƙo ko kaɗan, amma kada ya damu ya kyalesu suyi su gama, ba komai Musharraf ya ce masa, shi ba ma su Tga ne a gaban sa ba, babban abin da yake damunsa shin wanene ke razanar da shi? Wanene zai iya kasancewa matsafi a cikin family William jacop? Domin wannan abin da suke yi tsafice, to waye ne zai yi hakan? Me yasa suka takurawa Michael shi kaɗai? Ko dan sauran basa magana ne? Me yasa tun ranar da ya musuluntar da Michael abubuwa suke ta faruwa da shi marasa kyau? Sannan meyasa kullun mace ce ke aiwatar da hakan? Hakan na nufin zancen James gaskiya ne, mum ɗin su tana da alaƙa da magicians? Ko kuma ita ke yin tsafin da kanta? To me yasa take tsafin akan ƴaƴanta na cikinta? Sannan kuma tana ikirarin tana bala'in kaunar su? Ko dai a nata haukan hakan yana nufin tana basu kariya ne?. Wayan nan tunanin su suka cikawa Musharraf ƙwaƙwalwar kansa, wadda kuma ko kusa ko alama bashi da amsoshin su. Idan muka koma ɓangaren Lion kuwa. 💖Bayan wasu ƴan awanni.💖 Ruwan sama ne ke zuba kamar da bakin kwarya, ga shi ruwan zuba yake yi babu iska ba tsawa, kawai shaaaa yake zuba. Tsaye yake a balcony bedroom nasa, yana kallon yadda ruwan saman nan ke zuba Kamar da bakin kwarya, kasan cewar wutar dake a wajen blue light ne, ga kuma wajen ya yi duhun hadari, da kuma duhun dare, sai abin ya kara kyau da kawatuwa, hasken wutar yadda take haska shi abin ba'a magana, ta saje da kwayar idanuwansa da suka kara haske a yanzu saboda dare. Sanye yake da bathrobe fara kal a jikinsa, rigar bata karisa isa mashi gwiwarsa ba, ya ɗaure dark black curly hair san nan a bayan wuyarsa, ya bar na gaban goshin, yau fuskarsa har wani kyalli take yi, ya kara kyau sosai, da alama yau yana cikin farinciki, daya ke shi baka gane farincikin da bakin cikin shi, saboda kullun fuska a ɗaure, hakan yasa ba wanda ya iya fahimtar yana cikin farincikin, fari kuma kyakkyawar hannunsa riƙe take da wani kyakkyawar cup mai ɗauke da hot coffe sai tiriri yake yi. Bai cika shan coffee sosai ba, a cewar Triplets nasa wato James da Michael idan kaga Lion na shan coffee to yana cikin farinciki kenan, shi daga abincin da yake ci suke iya gane cewa yana cikin farinciki ko bakin ciki, haka zalika daga abin cin da yake ci suke iya gane bashi da lafiya ko yana da lafiya, wani irin murɗaɗen mutun ne wadda duk duniya ba wanda yake iya gane gaban sa bare bayan sa, ba zaka taɓa gane ina ya dosa ba, kullun a siffa ɗaya yake, komai abin farincikin da ya same shi, fuskar nan tamkar hadari take ako da yaushe. A hankali yake kai cup ɗin sai tin ɗan bakinsa yana kurɓar coffee ɗin, kai daga ganin yadda yake yau kasan yana cikin yanayi na musamman. (Amma me kuke tunanin ya sanya shi shiga cikin yanayin nan? Bayan kuma James baya nan? To ko dai ya yi nasarar gano ainahin in da aka kai James ɗin ne? Kun san dai kwana biyu da suka wuce ya ce ya gano ma'anar A.E.A ko? Sannan ya ce James yana ɗaya daga cikin A.E.A to ko dai mun samu damar sanin asalin takamaimai location ɗin ne? Muje dai zuwa?) Tun da Tga ya shigo cikin ɗakin ya tsaya daga ɗan nesa ya zuba mashi ido yana kallon yadda yake kallon zubar ruwan saman nan, yasan ba haka kawai ba akwai dai wata a kasa, sai dai matsalar ko ya tambaya ba zai samu amsa ba. Ya jima tsaye a wajen har ya ga ji, da alama shi kuma Lion zai iya kara tsayuwar awa biyar a wajen ma bai gaji ba, ganin haka ya sa ya kariso wajen yana faɗin "Well-done sir". Kamar ba mutun a wajen, ko motsi bai yi ba bare ka yi tunanin ya ji shigowar Tga ɗin, haka zalika bai amsa sannun ba. Gefen sa Tga ya tsaya yana faɗin "Lion gaskiya ina zargin wannan mutumi da James ya kawo gidan nan, so ina son yin bincike akan shi ka bani dama!!". Cikin natsuwa ya sake kai cup ɗin saitin ɗan bakinsa ya kurɓi coffee ɗin, yau jin duniyar yake yi tana mashi mugun daɗi, sai dai ko alamar hakan babu akan fuskar tasa. "Lion sai magana ta biyu da ta kawo ni, akan yarancan da su Tyrone suka kama, masu yi wa kananan yara fyaɗe nan, wani hukunci zan yi musu?". Good 30mins ya ɗauka har lokacin bai karisa shan coffee ɗin ba, kuma bai yi magana ba, daya sha iya yadda ya ishe shi, sai ya riƙe cup ɗin kawai ya dakata da sha yana kallon ruwan sama, Tga kuma sai satar kallon shi yake yi, dan yau ya kara kyau sosai, har wani kyalli soft skin nasa take yi. "Wayan da su Tyrone suka kama ka musu kachiya part two is okey, shi kuma mutunmin zan yi bincike akan shi, but not now, saboda saura kwana uku in yi tafiya so i don't have enough time da zan yi bincike akan shi, sai na dawo kawai" ya yi maganar gently kuma in a cool voice nasa, idan kaga yadda yake maganar ba zaka taɓa cewa yana motsa laɓɓansa ba, saboda cike da class yake maganar, a hankali yake fitar da ko wace words ta yadda lips nasa basu wani motsawa sosai. Ba irin Maganar su Tga ɗin yake yi ba, cike da salo na jan hankali mai kallonsa da class maganar take fita. (Lion Masha Allah komai ya haɗa🥰) Tga ya kasa tafiya duk da cewa an bashi amsar abin da ya zo nema, ya tsaya sai satar kallon Lion ɗin yake yi, saboda kyan da ya yi mashi, shi kuma Lion sai kallon ruwa yake yi a cikin zuciyarsa yana tunanin ya kamata kafin ya yi tafiyar nan ya binciki Michael, mum nasu, da kuma John and Jay, domin idan ya yi tafiyar nan zai ɗan ɗauki lokacin kaɗan bai dawo ba, zai iya kai 1 week ko 2, so gara ya duba wani hali suke ciki kafin ya tafi. Sun jima tsaye a haka, da Tga ya gaji sai ya yi mashi sallama ya wuce dan ba zai iya jure tsayuwar nan ba, domin training ɗin General ba ɗaya bane da The General of The Army, ko da gwajima ba haɗi, basu haɗa hanya ba, abin da Lion zai yi ko rabin shi ba za su iya ba. Sai da ruwan samar nan ta ɗauke sannan ya ajiye cup dake hannunsa saman glass table dake a wajen ya dawo cikin ɗakinsa. A gaban Mirror ya tsaya yana kallon fusataccen fuskarsa, a hankali ya kai hannunsa yana shafa lallausan dark black curly gashin dake kwance a gefen lallausan kumatunsa, shi kansa fuskarsa burge shi take yi, kyau fuskarsa take yi mashi. Slowly ya dawo da kallonsa saman kyakkyawar wuyarsa, kallon kashin da ya bayyana masa a wuyar tasa yake yi, wadda take nuna alamar ya rame, rashin James ya sanya shi rama. Ya jima a haka, can kuma ko me ya tuna a zafafe ya juya zuwa cikin dressing nasa. Jimkaɗan ya fito hannunsa ɗauke da wannan akwatin na mum ɗin su, a gefen bed nasa ya zauna tare da buɗe wa, wannan sarkar ya fitar kallonsu yake yi, haka kawai ya ji yana son saka sarkar a wuyarsa. Ɗaya daga cikin sarkar tana da design of heart a jikinta, kuma heart ɗin tana da ɗan girma kaɗan, saura biyun kuma akwai design of heart ɗin sai dai su rabi rabin heart ɗin ne ba full heart kamar ta farkon ba, zubawa sarkar idanu ya yi na ɗan lokacin. Can kuma sai ya ɗauki kayin sarkar guda biyu masu rabi rabin heart ɗin ya yi kokarin haɗesu su fita full heart, amma sai suka ki zama alamar ba nasu bane, ɗaya ma ya fi ɗaya girma, ajiye su ya yi ya miƙe zuwa dressing room ɗin. Jim kaɗan ya fito riƙe da wani hoto, a in da ya tashi a nan ya koma ya zauna, zubawa hoton ido ya yi yana kallon sarkar dake wuyar Josephine ɗin lokacin bata kai haka shekaruba. Tabbas wannan sarka mai full heart ɗin shine a wuyarta, shiru ya yi yana tunanin ina ragowar gefe da gefen heart ɗin can kuma suke. Lokacin guda wani tunani ya faɗo mashi a zuciyarsa, a nutse ya ajiye hoton ya ɗauko wannan sarka na wuyar Josephine wadda ta sanya musu cikin akwatin yanzu, cikin hikima da dabara ya raba heart ɗin biyu, da yake kana iya raba su, shiyasa sauran suke rabi rabi, abin da yasa kuma bai taɓa damuwa ya nemi ina rabin su yake ba kenan, dan yana tunanin wata ƙila a hargitsi ne suka rabe suka faɗi, shiyasa bai nema ba, amma yana son nemansu domin ya haɗesu su yi full heart ya bawa su Michael su sanya a wuyarsu, sai dai bai sami lokacin yin hakan ba. Bayan ya rabe heart ɗin sai ya yi kokarin gwadawa ko zai iya rufe ɗaya daga cikin masu rabi rabin nan, amma ina ko wanne da nashi, ba mai rufe na ɗan uwa, hakan yasa ya mai da jikin wanda ya ciro kawai, sai ya ɗauki babban cikin ya ɗaura a wuyarsa, da yake su basu damuba maza suna saka sarka sosai, su kuma biyun sai ya ɗauke su ya mai da guda ɗaya cikin akwai tin, ɗayar kuma ya ajiye saman bedside drawer da niyar idan Michael ya zo ya bashi ya sanya a wuyarsa, duk da basu son mahaifiyar tasu, suna kokarin ganin basu mance da ita ba, kuma yanzu shi Lion ya fara jin wani abu a zuciyarsa dan gane da ita, a yan kwanakin nan kullun zuciyarsa na yawan gaya mashi cewa daddy ne bai yi mata adalci ba, sai dai aikin da yake yi a kan James ya hana shi binciko gaskiya lamari akan faɗar daddy da mummy ɗin. (Tofa a ganin ku waye mai laifi a cikin su kenan?) Sosai sarkar ta yi mashi bala'i kyau, dama kuma already akwai wani ɗan siririn sarka a wuyarsa, mai bala'i kyau da tsada, sai ya haɗe su. Bayan ya sanya sai ya tattare komai harda hoton mum ɗin tasu ya maida ma'ajiyar su, sannan ya dawo ya haye bed ya kwanta tare da jan wannan bargon nasa mai bala'i laushi ya rufe jikinsa zuwa wuyarsa, ga sarkar Michael kuma ya ajiye mashi a saman bedside drawer duk time da shigo sai ya ba shi. Yan da ya lume a lallausan bed ɗin nan nasa abin ba'a magana, ga black curly hair nan nasa ya zubo mashi har fuskarsa, sai wani lumshe idanuwansa yake yi kamar mai jin barci, ga yanayin garin gwanin burgewa saboda ruwan saman da akayi, iskan mai sanyin daɗi na kaɗawa, iskar yanayin garin tafi ta Ac daɗi. Ya ɗan jima cikin wannan yana yi mai daɗin kafin nan ya lumshe idanuwansa gaba ɗaya alamar barci ya zo kenan. To Lion asuba ta gari. A ɓangaren Michael da Musharraf kuwa a tare suka yi sallar isha, sannan suka kwanta suna hira, a nan ne fa Michael ke sanar da Musharraf ya kamata su je masallaci gobe, tun da ya ce mashi yin sallar Jumma'a a cikin masallaci yana da falala mai girmar duniya da abinda ke cikinta, to ya kamata gobe su je sallar Jumma'a a masallaci, ba karamin daɗi Musharraf ya ji ba, har wani murmushi na musamman yake yi, dama shi ya jima yana son tambayar ina masallaci yake, to da yake bai san waye zai tambaya ba sai ya yi shiru, amma yanzu tun da ga shi Micheal ya ce akwai masallaci sai su koma yin sallah a can, dama sallah a nan gida suna yin shi ne cikin tsoro da fargabar kada wani ya zo ya gansu, sai sun kulle kofar da key suke samun damar yin Sallah, to yanzu tun da akwai masallaci, sai suka tsara cewa za su rinƙa yin sallar asuba a gida, azahar kuma su fita zuwa masallaci, idan sun yi azahar ba za su dawo ba, sai an yi la'asar sai su dawo bayan sun yi, daga nan ba za su sake fita ba sai lokacin sallar mangariba idan suka fita shima sai sun yi isha za su dawo, sosai Michael ya ji daɗi kuma ya ce shi da kansa zai rinƙa jan su a motarsa suna zuwa masallacin. (Amma kuna ganin yadda Lion ya sa musu tsaro yanzu zai iya barin Michael ya fita ba tare da sojoji ba?🤔) Wannan shawara suka yanke kafin su yi sallama da juna, Michael ya wuce bedroom nasa, shi kuma Musharraf ya yi addu'ar barci sannan ya kwanta. Shi kuma Michael da ya shiga ɗakin sa, wanka ya yi ya shirya cikin kayan barcinsa masu kyau da tsada, sannan ya haye saman bed nasa ya yi addu'ar barci dan yanzu ya iya har da addu'ar shiga toilet dana fita gida, da sauransu, bayan ya yi sai ya kwanta ya ja blanket zuwa kirjinsa, ba jimawa barci ya yi awon gaba da shi. A ɓangaren Tga kuwa, da tunanin yadda zai ɓullo wa Musharraf ya yi barci, ya ci alwashin idan Lion ya tafi sai ya binciki wanene Musharraf, dan ba zai iya hakurin jiran har Lion ya dawo sannan ya yi bincike a kan shi ba, dan haka ya kuduri niyyar azabtar da Musharraf ɗin sosai idan Lion ya tafi. (To fa ni kuma na haɗa kayana na zuwa Nigeria dan na gano yan hanyar Kaduna, shin sun isa ne ko kaka, na yi nan sai kunzo.) 💖IMRAN💖 Sai misalin karfe 2 na rana su Imran suka shiga Kaduna, kai tsaye gidan su Nawid suka fara zuwa dan su sauƙe shi, saboda da motar Imran suka je. Bayan sun isa gidan sun yi parking Nawid ya ce sai dai ya zo su shiga cikin gida, Imran ya ce "A'a Dr kasan dai ba dan dole ba da ba zan shigo da kai har cikin gida ba ko? Kasan dai bana zuwa gidan nan sai dole, dan haka kawai ka gaishe mini da Ummi". Guntun tsaki Dr Nawid ya ja kafin yace "Kai ai yanzu Abbo ya raba mana part Ni kai na ina fin wata wlh ban saka maman su Afnan a idanuna ba, dan haka yanzu sai ka dawo zuwa kamar da" girgiza kai Imran ya yi sannan ya ce "A'a ni ba zan shiga ba gaskiya, saboda bana son matsala, kai dai ka gaishemini da Ummi kawai" yana kai karshen maganar ya tashi motar suka bar gidan, ita kuma Rimsha sai barci take yi abinta, ta kwantar da kanta jikin lallausar kujerar motar ga sanyin Ac na ratsata. Wucewa cikin gida Nawid ya yi, zaune ya isko Jelly saman sofa a Palon Ummi tana kallon wani Korean Film. Tsayuwa ya yi daga bakin kofa ya ɗan zuba mata idanu yana kallonta, bata lura da shi ba, hankalinta ya yi nisa a kallon da take yi, har wani abu take yi, idan ta kallin suna faɗa suna firewa sai ta yi kamar zata fire ita ma, idan sun yi wurgi da mutun zai faɗo kasa, har wani sa hannu take yi kamar zata tare shi ya faɗo hannunta. Ba karamin birge Dr ta yi ba, ta tafi da imaninsa, ga shi dressing nata yau ba'a magana ta yi kyau sosai cikin Pakistan riga da wando, sai dai a maimakon ta sanya gyalen a kanta sai ta ɗaura shi a saman hannun sofa ta bar kai ba ɗan kwali. Ya ɗan jima yana tsaye yana kallonta kafin nan ya shigo daga ciki bakinsa ɗauke da sallama, kamar bata a palon bata amsa sallamar ba sakamakon ta yi nisa ta lula duniyar kallo. Gefenta ya zo ya zauna daidai lokacin da Ummi ta fito daga cikin ɗakinta, tana faɗin "Baby kizo ki shirya mu tafi, ko kuma in tafi in barki". Ganin Nawid a wajen yasa ta ce "Yaushe ka dawo Nawid?" Ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Yanzun nan na dawo, dan Allah Ummi ina Abbo? Ina son yin magana da shi" "Abbonka yana nan, yana part ɗin su Afnan sai ka bari sai ya fito ko kuma ka kirashi a waya, bana son ka je can, dan dai kasan sauran, idan kaje ba zaku wanye lafiya da su ba". Guntun tsaki ya ja irin yana cike da haushin su Afnan ɗin, a yatse ne ya ce "No zan jira shi sai ya dawo part ɗin nan, amma ina zaku je na ji kina cewa baby ta zo ku tafi". Murmushin ne ya bayyana a kan fuskarta ta ce "Wajen Aunty Hajizatu zan je mana" ɗan kishingiɗa ya yi yana faɗin "Yaushe Aunty Khadija kuma ta dawo?" "Kwana uku da suka wuce ta shigo kasar, tun da ta shigo take kirana wai nazo muje gidan mijinta, to ban samu zuwa ba sai yanzu nake son in je in ji me kuma zata je yi a gidan tsohon mijin nata". Jinjina kai ya yi yana faɗin "Hmm adawo lafiya, amma dai Ummi dan Allah kada ki biyewa Aunty Khadija duk da take yarki ki" Harara ta wurga mashi kafin ta sa kai ta wuce wajen Jelly take ta zuba kallonta kamar bata a cikin palon. Hannunta ta kama ta mikar da ita tana faɗin "Wuce mu je ko na tafi na barki". Ba dan ta so ba ta miƙe suka wuce cikin ɗaki. Shima Nawid ya miƙe ya wuce bedroom nasa. A ɓangaren Imran kuwa, kai tsaye gidan su ya nufa. Ya na yin parking ya fito ya buɗe kofar gefen da Rimsha take a ciki, cikin natsuwa ya sanya hannu ya ɗauke ta cak, domin shi har yanzu kallon yarinya karama yake yi mata, jin an ɗauketa yasa ta farka a razane, ganin ta buɗe idanunta ya sa ya ce "Kin tashi lafiya?" Ya yi maganar ba tare da ya sauƙeta ba, kuma bai daina tafiya ba, kokarin zamewa daga jikin nasa ta yi ba tare da ta yi mashi magana ba, ganin haka yasa ya sauƙeta yana faɗin "Sorry bana son tashin kine shiyasa" shiru bata yi masa magana ba, domin kanta wani mugun ciwo yake yi mata, har wani jiri take gani saboda barci bai ishe ta ba. Da hannu ya yi mata nuni da kofar palon, kusan a tare suka shiga, zaune suka isko Ammie saman sofa, bakinsu ɗauke da sallama suka shigo ciki. Juyo da kallonta Ammie ta yi izuwa kansu, a zabure ta miƙe tsaye tana kallon Rimsha, gaba ɗaya tsikar jikinta sai ta shi yake yi, kamar wadda taga wani mugun abin tsoro, jikinta har kerma yake yi, tana haɗe words cikin tsawa ta ce "Wace ce ke?!" Zaro ido Imran ya yi yana mamakin yadda Ammie ta ɗaga murya haka. "Koma wace ce ke ki fita daga cikin palon nan yanzun nan, bana son ganinki" sosai Rimsha ta tsorata, shi kanshi Imran ya tsorata juyowa ya yi yana kallon Rimsha ko zai ga wani abin a tattare da ita wadda ya sanya Ammie ta ce bata son ganin ta, amma ina bai ga komai ba sai ma kyakkyawar, ga kyawawan dara-daran sleeping eyes nata masu ɗauke da barci. Tsawa Ammie ta kuma daka musu "Imran idan baka fitar da yarinyarnan daga palon nan ba, wlh zan tsine maka albarka, nace maka bana son ganin fuskarta ko?!!" Tashin hankali juyawa ya yi ya riƙo hannun ta suka fice daga palon. Suna fita Ammie ta zube saman sofa tama mai da numfashi sama sama, alamar fuskar Rimsha ya tsorata kuma ya ɗaga mata hankali sosai. Shi kuma Imran yana fita palon kai tsaye part nasa ya wuce hannunsa riƙe da nata, wasu siraran hawayene suka fara bin kuncinta, ba tare da Imran ya lura da hakan ba. Suna shiga part nasa ya ce "Kada ki damu a nan zaki zauna, kada ki je cikin gida, kada ki fita ko kofar palon nan, kiyi zaman ki a nan, heartbeat ɗin mu Akila zata rinƙa zuwa kuna hira, wancan ɗakin shine naki, ni kuma ga nawa ɗayar, kada ki sa komai a ranki, duk abin da kike so ki tambaye ni kai tsaye kin ji ko?" Ya kai karshen maganar yana dawo da kallonsa kan fuskarta. "Subhanallah Rimsha kukan me kuma kike yi haka?" Ya yi maganar yana goge mata hawayen nata, kasa magana ta yi sai ajiyar zuciya kawai da take sauƙewa, sai rarrashinta yake yi har ta yi shiru, sannan ya kai ta har ɗakin nata ya fito domin ya ɗauko mata trolley ta. Ɗaki ne mai bala'in kyau kamar dai ɗakin ta time da daddynta yake raye, ɗakin ya yi kyau sosai, ga katafaren bed 6 by 7 an shinfiɗa masa bed sheet na alfarma mai kyau launin pink da white color, abin ba'a magana, sai kamshi ke ta shi a ɗakin. Kai tsaye toilet ta nufa dan yin wanka ta ɗauro alwaya ta gabatar da sallar azahar. Lokacin da Imra y kawo mata trolleynta tana cikin toilet ajiye mata kawai ya yi, sannan ya wuce nashi ɗakin dan ya je ya yi wanka shima ya yi sallah. Bayan yan wasu awanni. Shirye take tsab cikin doguwar riga ɗaya daga cikin wanda Ahmad ya saya mata, ta yafa mayafin rigar a kanta, tayi kyau sosai kamar ka sace ta ka je ka ajiye ta kayi ta kallonta dan kyau, sai dai kallo ɗaya zaka yi mata kasan bata cikin walwala da farinciki. Palon ta fito ta ɗan kara gyara shi fes, sannan ta nufi wani wajen da take zaton shine Kitchen na part ɗin. Ai kuwa Kitchen ne, ko ina a gyare tsab, sai dai da alama ba'a amfani da Kitchen ɗin sosai, ana kwana biyu ba'ayi amfani da shi ba, ciki ta shiga ta fara yan dube-duben ta, akwai komai da mace zata buƙata a cikin Kitchen ɗin, irin su pot, spoon, plate, cup, da kuma ingredient na miya, da sauransu, sai dai babu kayan abinciki a cikin kitchen ɗin, hakan yasa ta nufi wani ɗan karamin kofa dake cikin Kitchen ɗin wadda take zaton store ne. Tana shiga ciki ta yi arba da kayan abinci kala-kala, wani daɗi ta ji, cikin sauri ta fito ta ɗauki pot mai kyau daga cikin sets da suke jere cikin drawer kitchen ɗin, a wanke yake tsab, amma sai da ta sake wankewa, sannan ta ɗaura ruwa a saman gas, farar shinkafa ta dafa, sai kuma ta rasa da me zata yi miya, domin bata ga kayan miya irin su Tomatoes a cikin Kitchen ɗin ba, yan dube-dube ta fata yi ko zata ga kayan miyar, can ta hango wani katon freezer daga gefe, cikin sauri ta karisa wajen ta buɗe, ai kuwa shake yake da kayan miya nama kifi da sauran su, shiru ta yi tana tunanin kenan yaya Imran yana yin girki da kanshi ne? Ko kuma dai yana da mata ta yi tafiya ne?. Ganin babu wani abin da tunani zai tsinana mata, sai ta ɗebi iya adadin kayan miyar da take buƙata, tazo ta wanke su tas ta ajiye a gefe, sai ta koma ta ɗebo nama kamar an sata, haka tazo ta wanke namar ta gyara shi fes tare da yi mashi haɗi da kayan kanshi da sauransu ta ɗaura saman wuta, bayan ta ɗaura sai ta ɗauki kayan miya ta zuba a blender ta fata markaɗe. Bayan ta gama nama ya dahu ta soya shi ta kwashe, sai ta zuba kayan miya ta fara soyashi shima. Haka ta haɗa miyar nan ya ji kayan kamshi da nama, sai tashin kamshi yake yi, ta gama komai ta wanke duk wani abin da ta ɓata sannan ta zuba abincin a cikin kuloli masu kyau, ta jera a saman tray ta ɗauka da niyar fitarwa palo, juyawar da zata yi suka yi ido huɗu da shi, yana tsaye ya goya hannu a kirji, yana sanye da jallabi ash color, ya zuba mata ido kallonta kawai yake yi. Wani irin tsorata ta yi saura kaɗan ta saki tray ɗin abincin ya faɗi kasa. "Asarar abincin zaki yi mini ko? Baki son yau naci girkin first lady kenan?" Ya kai karshen maganar tare da karisowa cikin Kitchen ɗin ya karɓa mata abincin yana faɗin "Waye ya koya miki girki haka? Nafi 30mins ina tsaye ina kallonki, karar blender da kika kunna ta fito da ni". Ya yi maganar yana fita Palo. Bayansa ta bi tana faɗin "A gidan su Kausar na koyi girki, sannan kuma ina da takardar girkin ina koya". Saman table ya ɗaura tray sannan ya ce "Gaskiya ne ga shi kamshin abincin duk ya addabawa cikina yasa sai yunwa nake ji, amma fa wannan shine first and kuma last kada ki sake yin girki, domin ba yar aiki na ɗauko ki ba, ki bari zamu rinƙa fita mu sawo, wannan kayan da kika gani a kitchen ɗin ma ina ajiyewa ne saboda abokaina, akwai wasu daga cikinsu basu cin abincin restaurant sai dai su girka da kansu, to saboda su nake ajiyewa". Turo ɗan bakin nan nata ta yi tana faɗin "To nima ai ina daga cikin mutanen da basu cin abincin restaurant, ni ba zan iya ba gaskiya, dan Allah ka bari zan rinƙa yin girkin da kai na". Baya son ɓata mata rai dan haka sai ya amsa mata da to Shikenan, daman kun san ta da son iya girki, sai murna take yi, shi kuma ya ce zai ɗauketa su je shopping anjuma da daddare ya saya mata kayan sawa da su man shafawa da duk wani abin bukata sannan ya saya mata littatafan koyan girki masu kyau. Saboda tsabar murna ji tayi tamkar ta ringume shi, sai zuba mashi godiya take yi. Yau dai Imran zai ci abincin da ba na restaurant ba, ɗaukar plate ta yi ta fara serving nasa. Zuba nata ido ya yi yana kallon ta, sai da ta shake masa plate ɗin tap da abinci, yana ta ce mata ya isa amma taki bari sai da ta cika plate ɗin, sannan ta tura mashi gabansa tare da miƙo mashi spoon, karɓa ya yi yana zuba mata Albarka, ba ɓata lokaci ya fara cin abinci dan dama yunwa yake ji, wani irin daɗi ya ji lokacin da ya kai abin cin bakin sa, ɗanɗano na musamman ya ji, nan take ya fara santi, ɗaukar wani plate ta yi ta zuba nata abincin ɗan kaɗan tana ƙoƙarin zuba miya, nan fa ya ce bata isa ba, karɓar serving spoon ɗin ya yi ya cika mata plate ɗin shima kamar yadda ta mashi, sannan ya bata dama ta zuba miya ta ɗauka ta wuce bedroom nata. Subhanallah wani shegen daɗi ya ji lokacin da ya kai tsokar namar cikin miyar bakinsa, wow ya furta afili Rimsha ta iya girki, ga hannunta da zaƙi, haka ya buɗe cikinsa ya fara ci, yau ba abincin restaurant bane, bai san lokacin da ya cinye abincin nan tas ba, cikinsa kamar zai fashe saboda koshi, bai taɓa yin lodin abinci irin na yau ba. A wannan hali Akila ta shigo ta same shi, dawowarta daga school kenan, tasha ruwan mamaki ganin yadda yake ta santin abincin, ta kasa hakuri har sai da ta tambaye shi. Daɗi ya hana shi yin magana, da hannu kawai ya nuna mata kular abincin, buɗe kular ta yi, wani daddaɗar kamshin steew ɗin ne ya daki hancinta, cikin sauri ta ɗago ta ce "Yaya Imran wannan abincin wani restaurant ne?" Girgiza mata mai ya yi sannan ya shiga bata labari. Ai kuwa da murnarta ta miƙe tana faɗin "Kai yaya kace na samu kanwa kuma mai koya mini girki, bari naje wajen ta" bata jira amsar shi ba ta wuce zuwa ɗakin da Rimsha take a ciki, . Akila baiwar Allah bata da matsalar komai, tana bala'i son mutane sosai. Da fara'a sosai ɗauke a kan fuskarta ta shiga cikin ɗakin. Rimsha na cin abinci, domin lokacin da ta shigo ɗakin ajiye abincin ta yi sai da ta yi wanka ta shirya cikin wata doguwar rigar sannan ta ɗauki abincin ta fara ci, shiyasa Akila ta iskota bata kammala cin abincin ba. Murmushi ɗauke a kan fuskarta ta ce "Sannunki da zuwa" ɗago kai Rimsha ta yi tana kallonta, lokacin guda ta sakar mata cool murmushi har sai da hakwaranta suka bayyana, a ruɗe Akila ta ce "Wow dimple, open teeth, dogon hanci, karamin baki, kyakkyawar gashin gerar, sleeping eyes da nake mutuwar so, kyau iya kyau duk sun haɗu waje guda, ya ilahi ya lillihi ka bani yarinya mai kama da wannan baiwar taka, kyau iya kyau". Dariya abinma ya bawa Rismha, zuba mata ido Akila ta yi tana kallon yadda take dariyar abin ba'a magana gwanin birgewa. "Gaskiya kina da kyau sosai" Akila ta sake faɗa tana karisowa wajen da take zaune, saman mirror chair, miƙewa Rimsha ta yi dan ta bata wajen zama tana faɗin "Kece Akila ko?" Da sauri Akila ta gyaɗa mata kai ala'mar sannan ta ce "Yaya Imran ya baki Labarina ko?" "E ya bani labarinki ai ya ce mini ke ce bugun Zuciyar su gaba ɗaya gidan" kara faɗaɗa murmushinta Akila ta yi sannan ta karɓi plate ɗin abincin ta ce "Mu koma tsakiyar ɗakin saman carpet muci abincin a tare" to Rimsha ta amsa mata da shi, sannan suka koma saman carpet ɗin suka fara cin abincin a tare da spoon ɗaya, wannan ta ci ta bawa wannan kamar sun jima a tare haka suka yi sabon lokaci guda. A ɓangaren Aafia kuwa, tun da ta suma a wajen bata farka ba sai washe gari da safe da Umaisha ta zo ta tashe ta, lokacin already ta mance komai kuma lokacin da dodannin suka ɓace ta farfaɗo daga sumar sai dai kuma barci ya ɗauke ta shiyasa bata tashi ba. Wanka ta je ta yi ta shirya zuwa school, bata zo da motar ta ba kuma Akil baya nan hakan yasa ta hau abin hawa zuwa school ko breakfast bata tsaya ta yi ba domin burinta kawai su haɗu da Rufee. Karfe 8 daidai ta shiga cikin school, kai tsaye wajen da suka saba zama ta nufa, ai kuwa a nan ta isko Rufee tana zaune ta dukar da kanta kasa. Kusa da ita ta je ta zauna tana faɗin "Good morning Rufee, where is Anisa?" Ɗago kai ta yi bakinta a kunbure saboda dukan da Akil ya yi mata jiya, ganin bakin nata a kunbure yasa Aafia ta fara bata hakuri domin ta san menene sila. B komai Rufee ta ce mata sannan ta ɗaura da cewa "Aafia ina son ki rakani wani wajen idan ba damuwa" to Aafia ta amsa mata da shi sannan suka miƙe a tare suka nufi motar Rufee ɗin. Rufeen ta ja su suka bar school ɗin. "Ina zamu je Rufee?" Aafia ta tambaya tana ƙoƙarin sanya wayarta a silent. "Wani waje zaki raka ni, ke dai ki zuba ido ba zamu jima ba" "A'a Rufee bana son yin nisa da school dan kin ga yaya Akil ya ce zai yi bincike kuma ga yaya Irfar yana gari, ina tsoron su zo school ba su same ni ba" ta yi maganar cikin raunanniyar murya. "Kai A'afia kin cika tsoro wlh, to ba wani jimawa za mu yi ba, minti 40 ya yi zamu dawo" Allah ya dawo da mu lafiya shine abin da Aafia ta faɗa kawai, daga nan bata sake yin magana ba. Sun yi tafiya mai nisa ya yin da suka sauƙa daga kan titi suka keta ta cikin daji, Aafia ta fara tsorata domin bata taɓa wuce school, shopping, kasuwa, sai kuma gidan su Imran, iya in da take zuwa kenan, amma yau ga shi har cikin daji suka shiga, hakuri ta yi ta jure ta zuba ido tana kallon yadda Rufee ke keta cikin dajin da motarta. Wajen wasu guntayen bishiyoyi masu cikar ganye ta tsaida motar, sannan ta ce Aafia ya jirata tana zuwa, to A'afia ta ce mata amma zuciyarta tsorone a cike a cikin shi fal, kijinta har kerma yake yi, dan bata taɓa zuwa makamancin waje irin wannan ba, ita kuma Rufee fita ta yi daga motar ta kama hanya. Cikin dajin ta kuma ketawa da kafarta, tun A'afia na iya ganinta, har ta kurewa ganinta. Wajen malaminta ta je, nan ta sanar mashi da cewa tana son ya kwance aikin da ya yi wa Abbi ya mai da shi kan daddyn Jelly, sannan ta bashi hoton Akil ta ce tana son a haukata mata shi, ya shiga duniya kowa ya huta, to bokan nata ya ce sannan ya karɓi hoton ya gaya mata kuɗin da zata biya, buɗe jakarta ta yi ta zube mashi kuɗin sannan ta masa sallama ta dawo wajen A'afia. "Rufee me kika yi a cikin wannan daji haka?" A'afia ta tambaya fuskarta ɗauke da mamaki ga tsoro kamar zata yi fitsari a wando, shiru Rufee ta yi mata bata tanka ta ba ta kunna mota suka kama hanya. Suna tsaka da sharara gudu suka ga an tare hanyar da wasu duwatsu, wani irin mahaukacin burki Rufee ta ja, domin basu san da wayan nan duwatsu ba, dan a lokacin da suke zuwa babu su a hanyar, kuma yanzu ma basu lura da su ba har sai da suka iso wajen, saura kaɗan ma su bi ta kai, Allah dai ya tsare suka gani. Suna taka birki Rufee ta buɗe kofar motar zata fito kenan, wasu mutane suka fito daga cikin dajin hannayensu ruƙe da bindigu, ihu Rufee ta fara kurmawa ita kuma A'afia ta fara salatin annabi kawai. Cikin tsawa ɗaya daga cikin mutanen ya ce su fito daga cikin motar. Gaba ɗaya mutanen sun rufe fuskokinsu da irin rawanin buzayen nan, baka iya ganin fuskokinsu sai dai idanuwansu da hujin hanci da baki. Ba musu suka fito jikinsu sai kerma yake yi, Rufee kuwa wage baki ta yi tana kurma ihu ko wani zai kawo musu ɗauki, ba imani bare tausayi ɗaya daga cikin bandit ɗin nan ya sanya bindiga ya harbeta a tafin kafarta suna faɗin "Idan baki yi mana shiru ba, sai mun harɓe ki a in da zaki mutu" Wani irin azaba take ji amma haka ta sanya hannu ta toshe bakinta tana hawaye. Tasasu a gaba suka yi suka shige cikin daji da su, wani irin bakin azaba Rufee take ji, ga shi kuma sun ce sai dai ta taka kafar nata idan ba haka ba su fasata da bindiga, haka ba yadda ta iya ta fara taka kafarta suka bar wajen, suka bar motar a buɗe wayoyinsu da komai yana a ciki. Cikin wannan azabar suka rinƙa taka kafafunsu a cikin wannan ƙungurmin dajin, banda sunan Allah ba abin da A'afia take kira, ita kuma Rufee kuka kawai take yi, azaba ya yi mata yawa, ga wahalar tafiya ga azabar sun fasa mata kafa ɗaya, sai jini yake zuna kamar me. Sun yi tafiya mai nisan gaske, har suka wuce wani katon dutse kafin su iso wani waje kamar cam haka wajen yake, an yi ɗakuna da irin manya-manyan tampol ɗin nan. Gaba ɗaya wajen kewaye yake da manya-manyan maza madaka kanti suna riƙe da bindiga suna tsaitsaye, da alama gadin wajen suke yi. Suna isa wajen ɗaya daga cikin bandit da suka taho da su Rufeen ya ce "Kai Habu ku shigar da wayan nan ciki zuwa anjima idan su garba sun dawo, sai mu haɗa su mu ga yau mutane nawa muka kama" Wadda aka kira da Habun ne ya kariso wajen hannunsa riƙe da bindiga ya sanya irin rawanin buzayen nan shi ma ya rufe kai zuwa fiskarsa, baka iya ganin komai na daga fuskarsa sai ido, jikinsa na sanye da kaki na sojoji, a shekaru ba zai wuci 22 years ba. Tasa su ya yi agaba zuwa cikin ɗaya daga cikin ɗakunan tampol dake wajen. Rufee dai ya sha azaba iya azaba, ga shi ba halin ta yi wata magana za su harbeta suka ce, ita kuma A'afia tunanin ta ɗaya shine idan su yaya Irfan suka je school ba su same ta ba me zata ce musu, ba ta yi tunanin cewa matsalar da take a ciki yanzu ya ci uban wanda take hangowa ba, a'a ita tunanin hukuncin yaya Irfan take yi, domin ita bata san kidnaping ba, labari kawai take ji, bata san yadda ake yi ba. Habu na kai su bakin kofar ɗakin ya ce su shiga sannan ya juya ya bar wajen, jikin su a mace suka ja kafafunsu zuwa cikin ɗakin. Mata ne za su kai mata 30 a cikin wannan ɗan ɗakin, gaba ɗaya matan dake a wajen suna ƙoɗe alamar sunci bakar wahala, duk sun yi futu-futu da su, mafiyawancinsu akwai busasshen hawaye a kan fuskarsu alamar sun sha kuka, wasu kuma iyayene da yaransu kanana, wasu yan mata wasu kuma sun manyanta, abin gwanin ban tausayi, duk wata zuciya mai imani idan taga wayan mata sai ta zubar mu su da kwalla, saboda yana yin da ke a kan fuskokinsu ma kawai ya isa ya karyarwa da ɗan adam zuciyarsa, ya sanya shi kuka, ko makiyinka ba zaka yi mashi fatar kasancewa a waje irin wannan ba. Babu wadda ta kula su kowacce daga cikin matan nan tana fama da kanta, tsuru-tsuru su A'afia suka tsaya sun kasa gaba sun kasa baya, ga kuma Rufee kafarta na mata ruwan bala'in azaba. Wata wace ce wadda take zaune daga ta bakin kofa ta miƙe kafafu yarta wadda ba zata fi shekara 14 ba ta tada kai da cinyoyinta ita kaɗai ta iya ce da su A'afia su shigo su zauna, ba musu suka je kusa da ita suka zauna a takure, dan dama sun ga ji, A'afia da ta zo zama sai da ta kakkaɓe wajen tas sannan ta zauna, ita kam Rufee zaman yan bori ta yi tare da ciki hannunta daga bakinta ta fara kuka kasa-kasa dan kada su ji. "Sannunku da zuwa" matar ta sake yi masu magana, Aafia ce ta iya amsa mata ita kam Rufee ba'a magana da kyar ma take iya fidda numfashi. "Da kin dai na wahalar da kanki kina zubar da hawayen ki a banza ma da ya fi maki, idan baki daina ba hawayen ne za su kare a banza" Cewar matar ta kuma yi maganar tana kallon Rufee. A'afia ce ta yi karfin halin cewa "To saboda me zata daina kuka? Baki son su ji kukan nata har a sami wani mai tausayi ya tausaya ya taimaka matane?" "Taimako a lallai ke yarinya ce sosai" matar ta bata amsa ta kuma ci-gaba da cewa "Ai tun da ba su ji tausayinku wajen ɗauko ku su kawo ku nan ba, to fa duk abin da za su yi muku ba za su taɓa jin tausayin ku ko kaɗan ba, babu zancen imani a nan wajen, kawai ku yi addu'ar Allah ya kuɓutar da ku, amma a halin da muke a ciki yanzu ma ko an kawo kuɗin fansa suna karɓa sai su ki sakin mutun ya koma gida, mafiyawanci haka suke yi, mu samman idan suna son mace, wlh aurenta suke yi wata zubin suce da yan uwanta yaransu sun kasheta da basa nan wata zubin kuma idan suna son mace taki yarda tofa suna kashetan da gaske kuma su karɓi kuɗin fansa ba yadda aka iya da su, ba mai iya tinkararsu, sun fi karfin kowa ne nake ga a kasar nan, ku dai tun da kuka shigo nan sai ku kama addu'a a cikin zuciyoyin ku domin ko sallah ma basa bari bawa ya yi bare kuma har ya samu damar kai kukan sa ga Ubangiji, amma duk da haka ku dage da addu'a cikin zuciyoyinku dan Allah ya kuɓutar da ku, a yanzu kuɗi baya kuɓutar da mutun daga hannunsu". "Amma su ɗin su waye ne a kasar nan har da suke aikata hakan ba mai kama su ayi musu hukunci?" A'afia ta tambaya tana kallon yarinyar dake kwance kan cinyar matar "Ya naga yarinyar nan kamar bata da lafiya?" Ta sake cefawa matar tambaya. Nisawa matar ta yi kafin ta ce "Su ake cewa masu garkuwa da mutane wato kidnapas, yarinya kuma e bata da lafiya, zazzaɓi take yi, amma sun bamu magani ai ta ji sauki". Shiru A'afia ta ɗan yi tana jujjuya kalaman matar, sun bata magani kenan suna da asibiti ne a nan wajen? Ta tambayi kan ta a cikin zuciyarta, kidnapas dama haka suke? Ta sake tambayar kanta. Sake ɗagowa ta yi ta kalli matar sanna ta ce.......... Dole na dasa aya a nan na don na so ba sai dan page ɗin ya cika da yawa, mu haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu 💖TRIPLET'S💖💖 Episode 43-44 This page dedicated👇 *Aisha baita Jiddah, Ruky Aunty, N Hidan, Hafiza ayuba* Shiru A'afia ta ɗan yi tana jujjuya kalaman matar, sun bata magani kenan suna da asibiti ne a nan wajen? Ta tambayi kan ta a cikin zuciyarta, kidnapers dama haka suke? Ta sake tambayar kanta. Sake ɗagowa ta yi ta kalli matar sanna ta ce "To suna da likitoci a nan ne da za su bata magani?" Girgiza mata kai matar ta yi sannan ta ce "Ni dai tun da nake nan wajen yau tsawon wata uku ban taɓa ganin wani likita ba, sai dai idan suka ga baki da lafiya sosai sai kiga sun kawo maki magani, ban san daga ina suke samo maganin ba" "Wata uku!" A'afia ta maimai a fili tana zare ido, gyaɗa mata kai matar ta yi tana faɗin "E wata na uku a hannunsu, kuma sun karɓi kuɗin fansa daga wajen yan uwana har sau biyu amma sun ki su sake ni na koma gida" Zaro ido sosai A'afia ta yi domin bata taɓa tunanin hakan ba, ita a nata zaton idan suka kama mutun suna bashi kulawa saboda za su samu kuɗi, kuma tana tunanin da zarar an basu kuɗin fansa suke sakar mutun ya koma gida, bata taɓa zaton wajen nasu haka yake ba. Jugum jugum su ka zauna abin gwanin ban tausayi. Can kuma Aafia ta sake cewa "To amma ke meyasa basu barki kin koma gida ba tun da sun karɓi kuɗin fansa?" Wani dogon numfashi matar ta ja tare da sauƙewa a hankali sannan ta ce "E wannan ne ban san ni ba, abin da dai na sani shine da suka buƙaci kuɗin fansa sai suka ce mace ce zata kawo musu kuma macen ma babban ƴata mai shekara 17 shine yan uwana suka ki yarda suka ce mace ba zata zo wajen ba, sai aka bawa yayana kuɗin ya kawo, basu musa ba sai da yayana ya zo ya kawo musu kuɗin a in da suka yi da shi zai zo, bayan sun karɓi kuɗin sai suka sa bindiga suka harbe shi, wai dan saboda sun ce mace suke son ta kawo kuɗin yan uwana sun bujirewa umarnin su, haka yan uwana suka sake ba su hakuri suka rinƙa rokansu a kan su yi hakuri su sako ni, nan suka sake cewa sai an basu million biyu kuma kanina suke son ya kawo kuɗin, a cikin kannena ɗin ma sai suka zaɓi jarumin gidan mu, mai faɗa da kuma zafin rai, ni na rasa waye yake gaya musu family ka idan suka kamaka, sai kiga kusan komai naka sun sani, to da kanina ya kawo kuɗin sai suka yi ƙoƙarin jan ra'ayinsa a harkar dama haka suke yi, shiyasa suka yi yawa a cikin al'umma, idan sun ga namiji lafiyayyen mai karfin zuciya mara tsoro sai suyi ƙoƙarin jan ra'ayinsa, idan ya ki sai su yi mashi yankar rago, su yi video su turawa duniya amma ba za su taɓa faɗin abin da ya sanya suka yanka shi ba, sai dai suce ba'a kawo kuɗin fansan shi ba, abin da ya faru da kanina kenan, ya ce musu shi ba zai iya wannan harkarba, wlh a saman dutsen da suka karɓi kuɗin a nan suka ɗaure shi suka yi mashi yankar rago, sai bayan sun dawo suna magana na samu labari daga maganar da suke yi da ogan nasu, sannan dan su huce haushi suka zo suka ɗauki yarinyar nan suka tafi da ita shekaranta 14 a duniya amma haka shaiɗanunan suka lalata mata rayuwarta, na yi na yi su kashe ni na huta da wannan bakin ciki amma sun ki kula ni, kuma tun daga lokacin da suka yi wa wannan yarinyar aika-aikan nan ba su sake bi ta kai na ba, ni yanzu bani da wata bukatar da ta wuce su kashe ni, na yi kuka har hawayena sun kafe, yanzu zuciyata ta kekashe bana tsoro ko shakkar komai" Ta kai karshen maganar tana shafa kan yar tata dage kwance saman cinyarta gwanin ban tausayi. Sosai A'afia take zubar da kwalla yau ta ji abin da ya fi karfinta, wannan rashin imani har ina, su sace mutane bayan haka kuma su rinƙa lalata musu rayuwa sannan suna kashe masu yan uwa, wannan bala'i dame ta yi kama, idan ba Allah maɗaukakin sarki ba ba wanda ya isa ya fitar da bawa daga cikin irin wannan bakin zalincin. Dafata matar ta yi tana faɗin "Ki daina kuka domin kada hawayen ki su kare, abin kuka yana gaba, domin baki ga komai ba, tun kina da sauran hawaye har ma su ƙafe, ni yanzu addu'ar da nake yi maku Allah yasa kada su lallata maku rayuwarku, domin da wuya yanzu su ɗauko mace ba tare da sun kwana da ita ba su mai da ta, ɗazun da asuba ma naga sun kawo wasu mata sun zuba su cikin wancan ɗakin, an jima kaɗan za su zo su fitar da mu tsakar wajen cikin ciyayin can dan su azabtar da mu da rana, haka suke yi, idan rana ya yi sai su fitar da mu rana, idan yamma ya yi su dawo da mu, to idan sun fitar da mu sun haɗe mu waje guda ne sai kiga suna zaɓar mace da ta yi musu suna sanyawa yaransu na kasansu suna shigar musu da matan ɗaki, ina rokan Allah ya tsare ku yasa kada su lalata maku rayuwar ku, mu kam sun gama da mu saura su karisa mu kawai mu huta, ni na rasa ma me ya sanya basu kashe ni ba". Banda kuka ba abinda A'afia take yi, ita kuma Rufee tuni ta sulale kasa ta kwanta kamar bata numfashi sai dai hawaye kawai zaka gani yana bin kuncinta. (Toh fa su Aafia kuna cikin garari, na barku lafiya na tafi izuwa wajen Rimsha, kada ku manta part na Aafia True life story ne!) A ɓangaren Rimsha kuwa, tare suka ci abincin ita da Akila, su na ci suna hira gwanin ban sha'awa, bayan sun kammala ne suka fito Palo, zaune suka isko Imran saman sofa, ya tattare komai na kwanikan abincin da ya ci, har da goge wajen ya yi bawan Allah. Saman sofa mai zaman mutun 3 suka zauna Akila tana faɗin "Yaya Imran Aunty Aafia bata dawo ba fa, kuma yaya Akil ya ce idan ta je school ta dawo, to tun jiya bata dawo ba". Ba tare da kalle su ba ya ce "To bata da ra'ayin zama a nan ɗin ne shiyasa, sai ku kyaleta ta zauna in da take so, ko ana dole ne?" Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a ba'a dole. Shiru sukayi ba wanda ya sake magana, wayar Imran dake saman bed nasa a cikin bedroom nasa ne ta fara ruri tana neman agaji, da sauri Akila ta miƙe dan ta ɗauko mashi wayar, ɗagowa ya yi ya kalli Rimsha cike da kulawa ya ce "First lady gaskiya kin iya girki sosai kuma ina godiya, wlh na ji daɗi fiye da tunanin ki". Kasa ta yi da kanta tana murza yan yatsun hannunta, bata ce da shi komai ba, a haka akila ta dawo ta same su, hannunta ruƙe da wayarsa, miƙa mashi ta zo ta yi sannan ta koma saman sofar da ta tashi ta zauna tana murmushi. Picking call ɗin ya yi tare da kara wayar a kunnansa yana faɗin "Hello Dr ya akayi ne?" Daga ɗaya ɓangaren Nawid ya ce "Wlh na mance ne ban bawa Rismha wayarta ba ga shi sai kiran layin nata ake yi zan bawa driver ya kawo muku". To Imran ya amsa mashi da shi sannan suka yi sallama ya dawo da kallon sa kanta "First lady dama kina da waya har yanzu ne?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar E sannan ta ɗaura cewa "E wannan da nace maka ya taimaka mana a Ilorin shine ya saya mani wayar" yana ƙoƙarin sake yin wata maganar wayar tasa ta sake fara ruri, mai do da kallonsa kan wayar ya yi AA Salahuddeen shine sunan da ya bayyana akan screen ɗin. Picking ya yi tare da karawa a kunnansa ya ce "Hello AA" daga ɗayan ɓangaren Ahmad ya ce "Prof ina cikin matsananciyar damuwa da tashin hankali wadda yake yi wa rayuwata barazana". Zaro idanu Imran ya yi yana faɗin "A'A me ya yi zafi haka? Haba bana boss kada mu yi haka, tukun nan ma menene sila faɗi in ji, ba dai yarinyar da ka bani labarin nan bace?". Tamkar Imran na a gaban shi haka ya yi ya gyaɗa kai yana faɗin "Wlh Prof ita ce, kwana biyu ina kiranta bata ɗaga waya, sai yau da safe, shima muna magana ta katse ko gaisuwar kirki bamu yi ba, na sake kiranta sau ba adadi, amma bata ɗauka ba, ni narasa ina zan saka rayuwata, duniyar gaba ɗaya bata yi mani daɗi". Jinjija kai Imran ya yi kafin ya ce "A'A na tausaya maka, amma ina son ka sani halin da ni nake ciki ko rabin shi baka shiga ba, matata shekara 15 muna tare ina kula da ita rana ɗaya na nemeta na rasa, ta ɓata, duk duniya idan ka cire iyayena ba wadda nake so biyunta, idan na tuna hakan jin zuciyata nake tamkar zata fashe ta fito waje, gara ma kai kana iya kiran wayar tata, ɗauka ne sai time to time take yi, ni kuma fa? In da take ma ban sani ba, bana jin Muryarta bana gani ba, bansan ai na zan ganta ba ya ilahi ya lillihi". Ya kai karshen maganar kamar zai yi kuka. Zuba mashi ido Akila da Rimsha suka yi suna kallon shi gwanin ban tausayi. "Yanzu Prof wani shawara zaka bani?" Shiru ya ɗan yi yana sauƙe ajiyar zuciya kafin ya ce "Shawarata a nan shine ka rabu da soyayya da gaibu, ka kama dahir, yanzu yaushe zaka shigo Kd? Idan ka shigo sai mu tsaida matsaya ko?" Jinjina kai Ahmad ya yi sannan ya ce "Toh shikenan zan shigo next week" to Imran ya amsa da shi, sannan suka yi sallama, ya miƙe zai wuce bedroom nasa dan AA ya fama mashi ciwon dake a cikin zuciyarsa, sallamar da akayi a bakin kofar shigowa ce ta dakatar da shi, amsawa ya yi tare da bada izinin shigowa dan ya san mai wannan sallamar, baba mai gadi ne. Karisowa ciki mai gadin ya yi tare da dukawa kasa suka gaisa sannan ya miƙa mashi wayar Rimsha yana faɗin "Ga shi nan wai na baka in ji driver su Dr" karɓa Imran ya yi tare da yi mashi sannu ya juya ya miƙa wa Rimsha wayar sannan ya wuce ya nufi bedroom nasa yana faɗin "Akila zan ɗan kwanta zuwa la'asar domin kaina yana yi mani ciwo sosai" bai jira amsar su ba ya wuce ciki, shi kuma baba mai gadi ya miƙe ya koma bakin gate, su kuma suka miƙe suka wuce cikin ɗakin da ya kasance mallakin Rimsha a yanzu. Saman gado suka kwanta Akila tana faɗin "Bari naga wayar taki". Lokaci guda suka yi sabo kamar sun jima a tare, saboda Akila akwai shiga rai ita ma sannan ga shi bata da mugunta tana son mutane sosai ga fara'a Masha Allah. Miƙa mata wayar Rimsha ta yi, ta karɓa tare da kunna wutar screen ɗin, miss call ɗin Ahmad guda 20 ta gani, cikin sauri ta miƙa wa Rimsha wayarta tana faɗin "Ga shi nan yaya Ahmad naga ansa ya kira ki miss call har 20" karɓar wayar ta yi, kamar dama jira yake yi, tana karɓa sai ga kiran shi ya shigo, picking ta yi tare da kara wayar a kunnanta. "Hello yaya Ahmad" nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Why my Queen why zaki azabtar da zuciya ta haka? So kike yi na mutu ko?" Cikin sauri ta girgiza kai tana faɗin "A'a yaya Ahmad bana so ka mutu" "To baki so na mutu me yasa kika ki ɗaukar wayata?" Ɗan satar kallon Akila da ta tsare ta da ido ta yi tana faɗin "Kayi hakuri wayar ne bata kusa da ni, ina wuni? Ya karfin jiki?" Shiru ya ɗan yi mata, can kuma sai ya fara magana "Lafiya lou Alhadulillah, amma dan Allah kada ki sake yin nisa da wayar nan, idan ba haka ba zuciyata zata iya fashewa" gyaɗa mashi kai ta yi kamar tana gaban shi, nan fa ya shiga zuba mata surutu tana bin shi da eh da kuma a'a, har ta ga ji shi kuma da alama yanzu ma ya fara. Ganin haka yasa Akila ta karɓe wayar, ta kara a kunnenta tana faɗin "Yaya Ahmad amarya tana jin barci, ta gaji da magana ka rage mata maganar da zata yi maka anguma mana". Ta yi maganar cikin raha da wasa. Ita kuwa Rimsha kamar wadda aka raba da ƙaya, Akila na karɓar wayar ta miƙe ta kwanta abinta, sosai Ahmad da Akila suka rinƙa zuba hira ta ce mashi ita sister Rimsha ce uwa ɗaya uba ɗaya, rashin sani ya fi dare duhu ai kuwa ya yarda har da cewa ta bawa mama waya su gaisa, nan fa ta sake shirga mashi wata karyar wai mama bata nan, ai kuwa nan ma yarda ya yi ya ci-gaba da bata labarin yadda suka haɗu da Rimsha da sauran tarihin rayuwarsa. Rimsha kam bata ma san lokacin da suka gama waya ba, sai dai ɗagowa Akila ta yi bayan ta gama wayar sai ta tarar ta yi barci, ajiye wayar ta yi saman bedside drawer ita ma ta kwanta a jefenta ba jimawa barci ya yi awon gaba da ita, dama a gajiye ta dawo daga school. A ɓangaren Jehan kuwa. Ba wanda ya tashe su domin su yi sallar asuba, da yake ita ta saba tashi, time na cika ta farka, bayan ta yi alwala ta zo ta fara ƙoƙarin tashin su A'isha, amma ina sun ki tashi, cewa ma suka yi ba za su yi sallar ba, Adiva ce kawai ta tashi suka yi Sallah tare da Jehan ɗin, sai dai fa dukkansu biyu ba wadda ta san ina ne ainahin gabas a cikin ɗakin, kawai sun fuskanci in da suke ganin ya fi yi musu kama da Gabas ne suka gabatar da sallar su. Bayan sun idar suka zauna suna askar har gari ya yi haske, still har lokacin ba wanda ya shigo ɗakin da nufin zai tashe su ko wani abu makamancin hakan, abin ya bawa Jehan mamaki, kenan su a gidan nan ma ba ruwan su da kayi sallah da karka yi duk ubansu ɗaya kenan, Allah ka tsare mu ka barmu da imanin mu, Jehan ta faɗa a cikin zuciyarta. Sai Misalin karfe 8 Aisha da Maryam suka farka daga barci, wanka suka yi sannan suka fito suka shirya cikin kayan su mai bala'i kyau, riga da wando, ita ma Jehan wanka ta yi Adiva ta bata kaya, amma taki sakawa domin kayar gaba ɗaya ba na hankali a cikinta, duk kayan yan iska ne, kayanta da ta tuɓe shi ta ɗauka ta maida jikinta, ko wacce ta gyara gadonta. Zama suka yi Jehan ta ce "Aisha ina jinki dan Allah ki ci-gaba da gaya mani menene tarihin wannan gida? Da kuma abubuwan da suke aikatawa a cikinta" gyara zama Aisha ta yi sannan ta fata magana tana dariya. "Jehan sarkin sauri, ai da kin natsuma zaki ji komai, amma tun da kin matsa bari mu ci-gaba, akan Maganar yan lesbian, kin ga wannan part ɗin na maki bayani yadda ya kamata sai dai in kina son karin haske a kai" Cikin sauri Jehan ta ce "Ni ina son ki gaya mani ainahin abin da yake saka matan aure zuwa irin gidan nan na Hajiyar daɗi ne?". Guntun tsaki Aisha ta ja sannan ta fara magana kamar haka "Na gaya maki wasu matan auren wlh basu da raayi a kan ire-iren wayan nan abubuwa Hajiyar daɗi ke shiga jikinsu da sunan kawance, sai ta yi ta sakar masu kuɗi, sai sun saba sannan ta jawo ra'ayin su a hankali, idan ke mai kwaɗayin abin duniya ne to sai ki tsinci kanki a ciki dumu dumu, wani lokaci ma baki sani lokacin da zaki faɗa cikin harkar, saboda daɗin duniya, kafin ki farga sai kigan ki kin rufta ko in ce Hajiya ta ruftaki, wa su kuma su da kansu suke neman Hajiya da ta samo musu maza irin ƴan yara shekara 23 zuwa 25 haka, manyan mata fa, sai ki ga sun maƙalewa yara sa'annin ƴaƴan cikin su, irin Hajiyoyin nan ne da mazan su basa zama a gida, irin matan manyan nan, kin gane ai?" Gyaɗa mata kai Jehan ta yi alamar ta gane. Ci-gaba da magana A'isha ta yi "Wa su matan kuma talaucine ya yi musu yawa, mazansu basu kula da su, basu basu ci da sha a wadace, ga kuma yara sannan ba su sauƙe musu sauran buƙatu da kuma hakkin da ya rataya masu akansu, haka za su sa kafa su fita su bar gida da yunwa ga yara, kinsan uwa kuma ba zata iya jure ganin ƴaƴanta suna kukan yunwa ba, sai kiga ta fita neman taimako, to kin dai san yadda taimakon kasar ta mu ta kasance yanzu, chuɗa ni in chuɗa ka ne, ban gishiri in baka Manda, dayawan mutane basu taimako saboda Allah, sai dai idan za su mori wani abin daga wajen ka suma, kamar wata mata da Zinariya ta zo tana gayawa Hajiya last week, ina jinsu ta ce wlh matar mace ce kyakkyawar gaske ga diri iya diri sai dai talauci ya yi musu katutu, yarta bata da lafiya ta kaita asibiti amma likitoci sun ki su kula yarinyar nan, yarinya kamar zata mutu, amma ba likitan ko Norse ɗin da ta kulasu, wai dan ba su yanki kati ba, kuma ko Naira biyar basu da shi, hakan yasa ta fita goye da yar ta mai shan nono da kuma ɗayar yarta yar shekara 10 dan su je neman taimako, Mahaifin ƴaran nata yana nan yana tura ruwa a kura, to yanzu kin san ruwa a kura ba kowa ke saya ba, yana iya bakin kokarinsa wajen ganin ya basu abin da za su ci, haka matar ta fita neman taimako, ta sha wahala har ta ga ji bata samu komai ba, saboda rayuwar ta yanzu sai a hankali kowa ta kai ta kai yake yi yana neman abin da zai sanya a cikinsa, haka taje wajen wani mutumi ya ce sai ta bashi kanta, da farko taki yarda daga baya da bata da mafita sai ta dawo wajensa ta yarda ta bashi kanta, ta sauƙe yarta na goye ta bawa karamar akan ta riƙe mata suka shiga cikin ɗakin mutumin, bayan ya gama biyan bukatarsa ya ɗauki Naira 500 ya bata ya ce idan tana son karin wani gobe ma ta dawo ya sake biyan bukatarsa ya bata wani 500 ɗin, idan kuma zata bashi wannan yar tata mai shekara 10 ita ma ya kwanta da ita, to zai ba su 1000, ƙinyarda ta yi ta ce ya bar mata yarta ta karɓi 500 tana kuka suka dawo asibiti......" Jehan ta kasa bari Aisha ta dire zance ta tari numfashi ta da cewa "Iskancin banza dana wofi, bata zuwa ta nemi aikatau ne, sai ta bada kanta, to ba gara yarinyar ta mutuba akan abin da ta aikata, wlh ba duniya ce ta lalace ba zuƙatan mutanen duniyar ne ta mutu murus, ga aiki kala-kala Allah ya yi yawa da su a cikin al'umma, amma ta kasa zaɓar abu guda ta kama dan rufa wa kanta da ƴaƴanta asiri, wlh ban ga laifin mutumin nan ba, laifinta na gani akan me zata bada kanta? Na san cewa azamanin yanzu dama ba komai da komai namiji zai iya ɗauke wa mace ba, shiyasa dama abin da ya fi tun farko kada ki yi zaman banza ki kama sana'a, da ya kasance lokacin bikinki an zuba maki kaya a ɗaki gara abaki kuɗin ki fara sana'a, idan Allah ya sanya mashi albarka kyasayi abin buƙata, dama rayuwar yanzu waye yake ta kayan ɗaki, ku koyawa yara Sa'a a gida shine babban abin riƙewa, da shi za su riƙe miji har ku juya shi, domin idan kina da sana'a har dangin miji ba wanda zai yi gigin kawo maki raini, shima miji zaki ga har wani tarairayar ki yake yi, amma kunzo kun saki jiki an zuba muku kayan kallo idan kuka kafe Tv da ido bakwa tashi kuyi sallah a kan lokaci, ta ina za ku ga daidai? Ni bance maza basu laifi ba, amma mafi yawan laifin na mata ne, ko in ce na iyaye ba zaku binciki sana'ar mutun ba yana samu sosai ko yaya, zai iya riƙe yarinyar ku da abin da zata haifa ne ko yaya, yana da zuciyar nema ne ko zuciyar amace take, amma ku kuna saurin ku aurar da ita ku huta, to wlh in dai haka ne ba zaku taɓa hutawa ba a rayuwar nan, wahala wani na tafiya wani na zuwa, sai ki ga namiji bai da sana'ar arziki amma matansa biyu ko uku, sai ki rasa me iyayen matan suka gani suka aura mashi matar, wani fa ko mace ɗaya da take gidansa ya kasa riƙewa, amma za ki ga wai ya je neman wani auren, kuma sai iyaye su ɗauki yar su bashi, ko da ba abinci a gidan shi, ya je ya buɗe wa yarinya hanyar zina ya kasa riƙeta, ya sake su a gari suna nema suna ciyar da kansu, duk ba ga shi nan ina gani ba, kuma mummy tana bani labari ita da gwaggo wlh idan...." Bata kai karshen maganar ba Adiva ta rufe mata baki (*Kada ku mance duk wannan surutu da Jehan ta yi, cikin harshen turanci ta yi shi, sannan abu na gaba kada ku mance, duk abin da za ku gani na rubuta dan gane da gidan Hajiyar daɗi ko abin da za su faɗa a cikinta True life story ne, da gaske ne sai dai akwai abubuwan da na kara a ciki dan ya kawata abun ciki kuma har da shi kanshi gidan Haniyar, amma dai duk wani abin da za ku ji ku gani dangane da gidan gaskiya ce ta faru ne*.) "Jehan ke dai ba zaki bari mu gama jin labarin gidan nan ba ko?" Cewar Adiva guntun tsaki Jehan ta ja kafin ta ce "Allah Adiva abin ne ya ɓata mani rai talauci hauka ce". Dariya A'isha ta yi sannan ta ci-gaba da cewa "Ni dai bari na baki iya labarin da ya sawwaƙa, ina ganin dai yanzu mu rufe babin matan auren nan ko..." Tun bata kai ƙarshe ba Adiva ta ce "A'a kada ki rufe ki cigaba da gaya mana". Jinjina kai Aisha ta yi sannan ta cigaba da cewa "To matan auren dai abubuwa wajen kala huɗu ke kawo su nan, kun ji uku na farko Hajiyar daɗi ke janyo ra'ayin su da kuɗi, na biyu kuma mazansu basu kula da su, na uku kuma talauci, to abu na huɗun kuma wadda shine na karshe ni a iya nawa sanin da yake kawo matan aure cikin wannan harkar, shine masu auren namijin da baya son su, ko kuma mai biye-biyen mata, hakan yakan sa baya kula su baya biya musu buƙatar aure, idan sun ga ji sai su faɗo wajen Hajiyar daɗi neman mafita, wa su kuma kwaɗayin abin duniya, wayan nan sune ke kawo matan aure cikin wannan harkar, amma ni anawa ganin babbar matsalar shine mace ta zauna ba sana'a wato talauci, dan mafiyawancin wayan da Hajiya ke kawo wa nan zaki tarar talauci ya yi masu katutu, idan ka basu kyautar naira ɗari sai su ji tamkar ɗubu ɗari ka basu, saboda ba su samu, wata ma sai ta fi wata guda bata riƙe naira hansin nata na kanta ba, hakan shiyafi yawan kawo su cikin wannan harkar, da za'a samu su kama sana'a abubuwa za su yi sauƙi sosai, yanzu dai mu rufe babin matan aure mu shiga babin maza. Akwai maza a nan masu naman maza, wato yan luɗu, su kuma suna farowa ne daga wasu manya dake lalata su, misali kin ga akwai irin matsafa ko masu zuwa wajen boka, da boka zai ce masu sai sun yi luwaɗi da karamin yaro sannan za su sami biyan buƙatar da suka je nema, wani lokaci ma wani maganin boka ke basu akan su zuba wa karamin yaro a duburansa, to daga haka wasu mazan ke faro luɗu, idan wayan nan sun koya musu sun kuma tafi sun kyalesu basu samun biyan buƙata suna kashe kishin da suka saba da shi, to fa shine suma sai su shiga neman yara suna lallata su, da haka abin yake yawai ta, akwai maza je ma da suke da mata amma ba su son matan sai dai maza yan uwansu shine sai su bar mace tana gantale basu biya mata buƙata, saboda su sun samu sun biya nasu, wata macen sai ta fi shekara ba tare da sun kwanta da mijijta ba, kinga kuwa tunda ba dutse ke da akwai a kirjinta ba, dole ta fita neman mafita, to kin ji na maza kuma shine Hajiyar daɗi take tara su a nan dan saboda business ɗin ta ya kara karfi..." Katse ta Jehan ta yi da cewa "To mutanen ba su iya gudu su bar gidan ne?". Shiru A'isha ta ɗan yi kafin ta ce "E ni dai ban taɓa jin ance ga wata ta gudu ba, ke gidan nan fa da kin shigo za ki ji baki son fita, wlh da kin yi ido biyu da Hajiya zaki ji ke fa ko mutuwa ba zaki so ta raba ki da gidan nan ba, kuma kin san gidan ne akwai daɗi, idan kin bawa hajiya goyon baya wlh har shopping zata rinƙa sanyawa ana ɗaukan ki kuje a sai miki mayukan gyaran jiki da kaya masu kyau dan saboda ki fito da kyau yadda masu kuɗi za su yi rububinki, babu abin da Hajiya bata saya mana, ni kam ai na sha zuwa shopping tare da ita ma, sau ba adadi, amma idan kika ki bata haɗin kai zaki sha wahala, ni sau ɗaya ma na taba ganin wadda taki yarda ta bawa Hajiya haɗin kai, amma daga baya yarinyar nan tafi kowa zaƙewa a cikin gidar nan, tana nan yanzu ma haka, sai dai yanzu tauraronta ya dishashe bata kawo wuta sosai, ba kowani Alhaji bane idan ya zo zai kwasheta.." Shiru Jehan ta yi tana tunanin ta yadda zata bar gidan, dan wlh ba zata zauna ba. "Amma A'isha idan Alhaji ya ɗauke ki fita kuke yi ne? Ko dai a cikin gidan nan ake gama yin komai?" Yar dariya A'isha ta yi kafin ta ce "Kai Jehan tunanin me kike yi da kika yi mani wannan tambayar?" Girgiza kai Jehan ta yi alamar ba wani tunanin da take yi. "Akwai alhajin da zai ce fita za ku yi kuje ku yi kwana biyu, akwai kuma wanda zai ce a nan zai biya bukatarsa ya wuce" ajiyar zuciya Jehan ta sauƙe sannan ta ce "Amma Hajiya bata tsoron idan an fita da yarinya ta gudu?" girgiza kai Aisha ta yi tana faɗin "Ai hakan ma ba zai yi wu ba, kin manta na gaya maki duk wadda ta shigo gidan nan ba zata so fita ba? Saboda daɗin shi, sannan kuma ba haka kawai Hajiya take barin wani ya fita da yarinya ba, a'a sai idan ya ajiye maya makudan kuɗi da zata yanka mashi, idan ya dawo da yarinyar kamar yadda ya ɗauke ta, to sai ya karɓi kuɗinsa, idan kuma yarinyar ta sulala ta gudu, shikenan wayannan kuɗin sun zama na Hajiya a madadin yarinyar" "Amma Aisha su alazawan basu tada bala'i aba su kuɗin su?". Wani irin dariyar shakiyanci Aisha ta yi kafin ta ce "Lallai Jehan baki san waye Hajiyar daɗi ba, ke dai kiyi fatar Allah yasa zuciyarta ta soki kema kuma ki sota, amma wlh ni banga wanda ya isa ya nunawa hajiya yatsaba, ke kinga yadda take zarewa manyan mutane ido kuwa? Amma fa kawata Afnan na ɗakin gaban mun nan ta ce mani wai abin da yasa Hajiya take zare musu ido su ji tsoron ta wai magani take yi masu, amma fa ni baruwa na ban sani ba" Ta kai karshen maganar tana girgiza kai tare da yarfe hannu alamar ba ruwanta. Shiru Jehan ta yi tana tunain yadda za'a yi ta bar gidan ita da Adiva. A wannan hali Zinariya ta shigo cikin ɗakin ta same su, tana sanye da wata arniyar wandon jeans gundu zuwa cinya da yar karamar riga, kamar dai jiya ta ci uban make up kamar me, "Ke Aisha ku fita kuje kitchen ku karɓi abincin ku, sannan idan kun gama ci Aisha ki same ni a office na" tana kai karshen maganar ta wuce ta fita. Miƙewa Aisha ta yi tana faɗin "Kuzo mu je mu karɓi abinci" "Abinci kuma?" Jehan ta maimaita, gyaɗa mata kai A'isha ta yi alamar e, "Waye mai sayan abincin?" "Kuɗin da muke samowa wajen alazawa mana, da shi Hajiya take bamu abinci mai rai da lafiya sau uku wata sain ma sau huɗu ga mayukan gyaran jiki, turarukan, da kayan sawa, ga su ice cream da su chocolate, shiyasa nace maki zaki ji daɗin zaman gidan nan komai akwai wlh, sai dai muce Alhadulillah, ban da kema da abinki idan Hajiya bata gyara mu ba, ta yaya zamu fito tsab har agan mu ace ana yi da mu". Zubawa Aisha ido kawai Jehan da Adiva suka yi, ba shakka bariki ya zauna wa Aisha sosai, ta kware a duniyanci ba'a magana, wannan da ba dan sun tabbatar sheɗan shi kaɗai ne bai da yan uwa kanne da yayyuba, da sai su ce tabbas Aisha kanwar shaɗan ce, yarinya kamar shaiɗan ya mata fitsari a kai, wai badon ana gyara su ba ta ya za'a gansu a buƙace su, innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Duk wannan zance Jehan ke yin shi a cikin zuciyarta. Suna zaune a wajen har Aisha ta dawo hannun ta riƙe da plate na abinci sai tiriri yake yi, lafiyayyiyar jolof rice ce, ta ji kayan kamshi da kayan haɗi, ga kwai a gefe guda sai kayan ganye su cucumber and cabbage da sauransu, saman carpet ɗin dake a cikin ɗakin ta zauna tare da ɗaukan spoon ta fara ci, su dai ido kawai suka zuba mata. Ita ma Maryam da ta ga su Jehan ba su da niyar tashi sai ta tashi abinta ta nufi waje dan zuwa kitchen ɗin karɓar nata abincin. Suna zaune shiru, ita kuma A'isha tana ta kai loma bakinta. Zinariya ce ta sake turo kofar ta shigo cikin dakin, kai tsaye wajen Jehan ta nufa, ba tare da ta yi musu magana ba ta riƙo hannun Jehan suka fice waje. Kai tsaye wani ɗaki ta kai ta, a nan ta zaunar da ita saman wani luntsumemen sofar mai bala'i taushi, bayan ta zaunar da ita sai ta koma saman table chair dake a cikin ɗakin ta zauna tana faɗin "Ki saki jikinki Hajiya ce ta ce kada a baki abincin da ake bawa yan gida, ta ce a rinƙa baki abinci na musamman har sai ta dawo, dan haka yar gold zata shigo maki da abinci yanzu". "Me yasa ba za'a haɗa mu a bamu abinci iri ɗaya ba?" Cikin sauri Zinariya ta waro ido tana kallon ta, mamakine ya bayyana karara a kan fuskarta anya yarinyar nan kanta ɗaya kuwa? Har ki samu an yanta ki shine zaki yi wata magana, lallai wannan da zafin ki kika zo, amma zama ki yi sanyi ne, duk wannan zancen zuci Zinariya take yi. Ganin ta yi shiru yasa Jehan ta ce "Duk abin da zan ci, shi Adiva zata ci, domin yar uwata ce ta jini, idan kuma ba za ku bata abin da za ku bani ba, to nima bana buƙata" ta kai karshen maganar tare da miƙewa zata bar wajen. Tsawa Zinariya ta daka mata wadda ya sanya ta dakatawa ba tare da ta shirya ba. "Koma ki zauna!!" shine abin da Zinariya ta ce. Shiru ta tsaya tana tunanin ta koma ko kada ta koma. A wannan hali wata yar figaggiyar mata ta shigo wadda kuma da alama ita ce yar gold ɗin, domin kuwa ga shi ta yi kalar gold ɗin, fuska golden color kafa bakinkirin kamar zunubi, ta ci bleachin ta ƙoshi, har wani ɗayewa fatar kumatunta ya yi, tsabar ta shafa mai ɗin ya mata yawa, har wani ɗanye-ɗanye fatar fuskarta ta yi, kana iya ganin jan namar ciki, tana sanye da wani kafurin doguwar riga wadda ya matseta sosai, ga bayan nata a shafe kamar anyi pilastar dakali da siminti, ba ta da shape ko kaɗan, amma ba laifi kyakkyawa ce jinin hausa fulani, sai dai tana nan kamar bulala saboda sirranta, abin ba'a magana. Hannunta ruƙe da ƙatuwar tray mai ɗauke da abinci mai ji da lafiya, fried rice ne ya ji su green beans carrot da sauransu, sai kamshi yake tashi, daga gefe kuma wani karamin plate ne mai ɗauke da haɗin salat, ga gasashen rabin kaza a gefe, sai hollandia ɗaya da ruwan swam water. A gaban Jehan ɗin ta zo ta ajiye tana faɗin "Ya na ganta a tsaye?" Fuska a ɗaure Zinariya ta ce "Rabu da yar nema wai dole abincin da muka bata shi za mu bawa yarinyar nan da Hajiya ta turota shekaran jiya, wai yar uwarta ce dole ta re za su ci". Zaro wayan nan shegun idanun nata yar gold ta yi, ga idanun nata saboda tsabar shaye-shaye sun sauya launi zuwa kalar fuskarta, wato golden color, dama kuma idanun nata ba farare bane, sannan gasu a tsaye a bushe kar. Tsawa ta dakawa Jenan "Ke wuce ki zauna ki ci abinci ko kuma na kira madaka katti su ɗura maki abincin nan tas!!". Kare mata kallo Jehan ta yi tsab, fuska a yatsune ta ce "Idan kuma bani da niyar ci, na ce na ƙoshi fa? Akwai dole ne?" Wani irin bakin ciki yar gold ta ji, ranta a matukar ɓace ta wankewa Jehan fuskarta da mari. Cikin sauri ta dafe kuncin nata, idanuwanta suka ciko da kwalla yau shine karo na farko da aka taɓa marin wannan kyakkyawar face ɗin nata, ga shi marin ya shigeta sosai, tunani ta fara yi shin ta rama ne ko dai ta hakura sai ta gama sanin yadda gidan yake. "Uban me kike kallo da kika tsareni da ido? Ko zaki rama marin ne? Idan rashin kunya kike ji da ita to gidan ta kika zo, ki wuce ki zauna ki fara cin abinci nan, idan ba haka ba mu yi maki dukan kawo wuƙa". Ba tare da ta yi magana ba ta nufi hanyar fita daga cikin ɗakin. Damƙo rigarta yar gold ta yi ta janyota baya har sai da ta faɗi kasa, a fusace ta miƙe ta damki wuyar yar gold, domin ta kure hakurinta, ta ɓata mata rai sosai. Zinariya na ganin haka ta yi maza ta taso suka haɗu suka fara naɗawa Jehan ɗan iskan duka domin su sauƙe mata wannan ji da kan nata, sosai Jehan ta yi ƙoƙarin kare kanta dan kada su ji mata ciwo, amma da yake su biyu ne, sai suka yi mata ɗan iskan dukar kawo wuƙa. Tun tana iya kuka mai ɗan sauti har kukan nata ya dai'na fita, sai da suka ga sun raunatata, sannan suka kyaleta suna mai da numfashi, Zinariya ta koma mazauninta ta zauna, ita kuma yar gold cike da izza da bada umarni ta ce "Ki yi maza ki tashi ki ci abincin nan ko kuma na kara maki wani dukan wadda sai kin kasa motsi, har mu zaki buɗewa ido? To tun kafin kizo duniya mukenan, iyayen ki ne mu a iskanci da rashin kunya, in dai a gaban mu kike to ba a ma haifeki ba a rashin kunya!!". Ita dai Zinariya sai haki take yi kamar wadda ta yi tseren gudu, ba karya sun jibji Jehan iya san ransu, sun gwada mata karfin shekaru da iya bariki. "Wai ba zaki tashi ba ina magana!!" Yar gold ce ta sake magana, ko gezau Jehan ba ta yi ba, kamar bata a cikin ɗakin, tana kwance rashe-rashe a kasa tana hawaye tare da fitar da kuka mara sauti sosai. Ganin taki tashi yasa Yar gold ta kariso wajen ta sanya hannu ta ɗagota ta zaunar da ita tare da turo mata tray ɗin abincin a gabanta, kin ci ta yi kamar ma bata ga abincin ba. Abin ba karamin fusata yar gold ya yi ba, cikin fushi ta ɗaga hannu zata mareta, sai lokacin Zinariya ta sanya baki ta hanyar dakatar da ita, domin ta lura Jehan mace ce mai taurin kai ga kafiyar bala'i, idan suka biye mata to za su ji mata babban ciwo wadda idan hakan kuma ta faru to fa ba makawa sai sun biya Hajiya kuɗin da ta sayeta. Miƙewa ta yi ta kariso wajen a ya yin da take sallamar Yar gold, gaban Jehan ta zo ta tsugunna tana faɗin "Shawarar da zan baki a nan shine idan zaki sauƙe wannan rashin kunya da wani jiji da kai to garama ki sauƙe tun wuri, idan ba haka ba, zaki ci bakar wahalane kawai a banza, domin duk wanda kika gani a gidan nan idanuwansa a buɗe yake, kowa shegen kanshi ne, so is better for you da ki natsu ki bi mu sau da kafa, domin ki zauna lafiya, yanzu ki ɗauki abincin nan ki ci!". Tamkar babu Jehan a wajen haka ta yi shiru ta kyaleta, domin ta riga ya kafe a kan ba zata ci abincin ba. Ba yadda Zinariya bata yi ba, amma Jehan ta ki ta ci abincin nan, haka ta hakura ta kyaketa ta ce ta koma ɗakin su. Jikinta har kerma yake yi saboda dukan da suka yi mata, haka ta miƙe zuwa ɗakin nasu, tana shiga Adiva ta taso da sauri ta riƙe ta tana faɗin "Jehan lafiya? Me yafaru naga bakin ki a fashe?". Shiru ta yi masu ba magana, zama suka yi saman katifar gadon nasu, Aisha da Maryam dake cin abinci ma suka taso suka zo wajen. Aisha ce ta ce "Sun dake ki ko?" Gyaɗa masu kai Jehan ta yi alamar e. Jinjina kai Aisha ta yi kafin ta ci-gaba da cewa "Ai in dai kina son zama lafiya da su, to fa sai dai ki yi hakuri ki zauna a yadda suke son ki kasance". Kuka Adiva ta fara yi tana faɗin "Jehan dan Allah ki gaya mani ina daddyna, na gaji da wannan bakar wahala, wlh tun da ya fita ya ce zai je gidan ku na jira shi, shikenan bai sake dawowa ba". Ita ma Jehan ɗin wani sabon kuka ta fara yi ba tare da ta yi magana ba. Wai shin wace ce Adiva, Adiva ya ce ɗaya tilo ga uncle Shitu wato abokin daddyn su Jehan, uncle Shitu yana bala'i son Adiva sosai da sosai ita kaɗai Allah ya bashi, sosai abaya suna samun ciki kafin Adiva, wasu cikin zubewa suke yi, wasu kuma ana haifa yaranne basa zama suna mutuwa, Adiva ce kawai Allah ya bar musu, suna bala'i sonta. Sai da Jehan ta yi kukar rashin mahaifi sosai yau, sannan ta goge hawayen da yake akan fuskar, sai hakuri su Aisha suke bata amma bata kula su ba, sai da ta yi mai isarta tukun nan ta yi shiru dan kan ta, kallon Adiva ta yi cike da kwarin gwiwa da kulawa ta ce "Adiva da daddyna da daddyn ki dukka Allah ya yi musu rasuwa, dan haka yanzu mu za mu yi faɗa domin rayuwarmu, dole ne mu san abinyi, su daddy ba za su iya zuwa in da muke ba bare su taimake mu, mu zamu tai maki kan mu da kan mu, yanzu ina son ki gaya mani ina mummy ki?". Sosai Adiva take kukan jin daddynta ya rasu, sun shaku sosai da shi, uncle Shitu ya bata kulawa fiye da tunanin mai tunani, rayuwar farinciki tun ranar da tasan wace ce ita, tun ranar da ta iya tantance mutun da dabba, yau rana tsaka ta yi wani irin rabuwa mai muni tsakaninta da iyayen ta, wannan wace iriyar rayuwace. Rungume ta Jehan ta yi ta fara bata hakuri, tana bata hakurin ita ma tana hawaye, domin yau ta yi kukan rashin daddunta sosai, da ace daddynta yana nan da wayan nan shaiɗanun ba su isa sun dake ta ba. Sai basu hakuri su Aisha suke yi, amma ina sun ki yin shiru, su kaɗai suka san raɗaɗin dake a cikin zuƙatansu, su kaɗai suka san azabar da suke ji, bayin Allah duk wanda ya gansu a haka sai ya matse musu kwallah. Sun kwashi mintuna 20 suna shan kukansu, sai da suka ji zuciyoyinsu sun musu sanyi sannan suka raba jiki dana juna, Jehan ta miƙe ta nufi toilet dan zuba ruwa, idan ba haka ba, zata iya sumewa a wajen. Bayan ta fito Adiva ma ta shiga ta zuba ruwa. After some hours da basu wuci biyu ba. Zaune suke a saman gadon Adiva, dan Jehan ta ce ba zata rabu da yar Uwarta ba, haka ita ma Adiva ɗin. "Adiva ina mummynki?" Jehan ta tambaya tana tsareta da ido, kamar za ta yi kuka ta ce "Mummy ban ganta ba" "Kamar ya ya baki ganta ba? Ina ta je?!" "E naje school na dawo naga gida ba bu kowa sai masu aiki, dana tambayi baba mai gadi ya ce mum ta fita, na jirata har dare bata dawo ba, washe gari masu aiki suka yi girki na yi wanka na shirya zuwa school, na je na dawo ban ga mum ba, bata dawo ba, na tambayi mai gadi ya ce E bata dawo ba, haka har sati ɗaya ban sake ganin mummy ba, na kira layinta bata shiga, shine tun daga lokacin ban sake saka ta a ido na ba, ina cikin wannan hali wa su mutane suka zo wai banki na bin daddy kuɗi kuma lokacin biya ya yi dan haka mu fita a gidan za su yi gwanjon gidan, ni bansan in da zan ga kowa na yan uwan daddy ko mummy ba, kinga daddy shi ɗan Niger ne, mummy kuma ni ban sani ba, to alokacin ban wani damu ba domin ina tunanin kuna gida, haka na haɗa kayana abubuwan da nake buƙata tare da wayata na ce driver ya kai ni gidanku, haka ya ɗauke ni a mota muka nufi gidan ku, tun a bakin babban gate na ku ya sauƙe ni na juya kan motar domin har da motar a cikin gwanjon da za'a yi, na sha kuka lokacin da na je naga gidan ku a rufe, ba bu kowa, nan ne hankalina ya yi mugun tashi, zama na yi a kofar gate ɗin ku ina ta kuka, ban kawo komai a zuciyata na ɓatar daddyna ba, na yi tunanin ko sun yi tafiya da daddynku ne, tun da kunga suna yin hakan wani lokacin, da na zo naga gidan ku a rufe hakan yasa na kara gasgata cewa E tafiya kuka yi, na shiga tashin hankali domin bansan in da zan je in kwana ba, ina zaune a wajen har yamma, da dai naga dare ya fara yi sai na tashi na koma bakin hanya na tari abin hawa dan na koma gida, ina komawa na tarrar an sanyawa gidan mu kwaɗo an rufe shi, nasha kuka sosai shine na zauna a bakin gate ɗin, tun da bani da in da zan je, a nan wata mata ta zo ta same ni, shine ta ce na zo muje gidanta ga gidan nata a can, ita makwanciyar mu ce, ba musu na bita domin ina jin yunwa kuma na gaji. Da muka je gidan matar ta riƙe ni da amana, sai dai kuma mijinta ɗan iska ne, sai cikin dare yake lallaɓawa ya shiga ɗaki na, yana mini baraza idan ban yarda da shi ba sai ya yanka ni...." Cikin sauri Jehan ta katse ta da cewa "Kuma kika yarda?". Girgiza mata kai ta yi ta ci-gaba da cewa "A'a Allah yana tsareni Allah yana taimakona, ina tserewa duk wani tarko nashi, toilet nake gudu na shiga, ba halin ya buga kofar matar zata ji, sai dai ya hakura ya tafi, daga baya na dawo rufe kofana da key idan dare ya yi, amma dai nasha wahala ba kaɗan ba, lokacin da Hajiyar ta gane cewa mijinta yana nemana, sai ta bani laifi ta koreni daga gidanta, haka na bar gidan na fita kan hanya ba ni da mafaka, ranar na sha kuka, kuma duk in na kira layin daddy bata shiga haka ita ma mummy layinta baya shiga, na sha wuyar tafiya a ranar, ga uban trolley da nake ja, to a hanya na haɗu da wata Hajiya ta kawo ni gidan nan" ta Kai karshen maganar tana goge hawayen da yake zubo mata akan fuskarta. "Yanzu ina wayar taki?" Cikin sauri ta miƙe ta buɗe trolley ɗinta ta ɗauko wayar tare da dawo ta zauna ta miƙawa Jehan ɗin. "Dama kin zo da kayan sawar ki ne ɗazun kika bani kaya marasa hankali?" Girgiza kai ta yi kafin ta ce "An hana ni yin amfani da sune a gidan nan, iya kayan da Hajiya ta saya maki su kawai zaki sanya, shiyasa ban baki ba" guntun tsaki Jehan ta ja tare da miƙewa ta wuce izuwa wajen trolleyn, doguwar riga abaya pink color ta fitar tare da mayafinsa, ta ɗauka ta wuce toilet. Jim kaɗan ta fito sanye da kayan a jikinta, da yake ta ɗan fi Adiva tsawo, sai rigar bata kai mata har kasa ba Kallonta Aisha ta yi ta bushe da dariya tana faɗin "Amma Jenan kin kai yar duniya, wato tun da an hana amfani da su, ke kin yi kena, wato dai ayi uban da za'ayi, wlh ina jiye maki ni dai". Bata bi ta kansu ba ta koma ta zauna tare da ɗaukar wayar Adiva ta fara gwada layin daddyn Adiva wato uncle Shitu, layin akashe kamar kullun haka ma na mum ɗinta shima baya shiga, shiru ta ɗan yi kafin ta saka nata layin ta gwada shima shiru, mum ɗin su shiru, har na daddyn su shima shiru a kashe, a fili ta furta "Wannan wace irinyar bala'i ce, kowa layin a kashe sai ka ce abin haɗin baki" Ta kai karshen maganar tare da ajiye wayar ta kwanta tana jin cikinta yana mata bala'i kugin yunwa, kuma ta rantse wannan abincin dai da suka bata ba zata ci shi ba matukar ba tare da Adiva za su ci ba. Suma kwanciya suka yi suka fara hira, ita dai bata saka masu baki ba, ita ma Adiva da ido kawai take binsu, Aisha da Maryam ke ta zuba kamar kanya (To fah Jehan kina tsaka mai wuya ni dai na haɗa kayana zuwa wajen Rimsha dan muga ya suka je shopping) Karfe 8 daidai na dare, bayan sun yi sallar isha, sun ci abincin da Rimsha da Akila suka girka, Imran ya ɗauke su zuwa shopping ita da Akila da Umaisha, da farko Akil ya ce Umaisha ba zata je ba, sai daga baya da Imran ya ɓata rai shine fa ya hakura ya ce ta sanya nikaf su tafi. Sosai Akila da Umaisha suka ɗebi kaya son ransu, ita kuma Rimsha sai nuƙu-nuƙu take yi, domin kunyar ɗibar kayar take ji, da Akila ta lura da hakan ne sai ta fara ɗebar mata, har da su chocolate suka ɗeba, kayan sawa sosai, da suka zo layin breziya Akila da tsiya sai ta juya tana kallon Rimsha ta gani ko dai ta ɗaukar mata ne ko bata fara ba. Ganin haka yasa Rimsha ta kama kanta ta bar wajen, Imran na zaune daga ɗan nesa da su, yana kallon su yana murmushi, abin gwanin ban sha'awa. Ganin Rimsha ta gudu yasa Akila ta kwasan mata breziyar dozin biyu ƴan madaidaita, bayan ta ɗauka ne sai ta nufi wajen ta, nan ta same ta wajen kayan barci. "Au a nan kika fi kauri kenan? Tom ni dai na fin son a rinƙa yi wa yaya Ahmad ciko" ko sannu Rimsha bata ce mata ba, dan bata ma gane me take nufi ba, sai dariya Umaisha take yi musu. Daga nan suka wuce wajen always, kallon Rimsha Akila ta yi ta ce "Kin fara ne na ɗibar maki?". Duka Umaisha ta kai mata a baya tana faɗin "Me ta fara? Ke Akila kin lalace wlh, sai na gayawa yaya Akil ayi maza ayi maki aure kada ki wuce gona da iri". Turo baki Akila ta yi tana faɗin "Wai ke Aunty Umaisha na kasa da ke ne? Ni da kanwata nake magana, ba dole na tambayeta ta fara bane ko bata fara ba, ko so kike naje na kwaso mata abu kuma azo bata fara ba". Ita dai Rimsha ta rasa gane me ta fara, kwata-kwata ba ta fahinci akan me suke magana ba, domin hankalinta bai kai kan Always ɗin ba, yana kan lotion da shower gel dake kusa da wajen, so bata lura da always ɗin ba. "Ke idan zaki ɗauka mata gara ma ki ɗauka mata, domin dai kin san dole zata fara, baki ga ma har kirjinta ya fara cika bane? To kirji ya cika kuma ai dole a fara". Sake baki Imran ya yi yana kallonsu yana salati a cikin zuciyarsa, wai yaushe Akila da Umaisha suka iskance haka ne bai sani ba? Lokaci guda tunanin Jelly ya faɗo mashi a ransa, in dai Rimsha ta fara period to ba shakka Jellynsa ma ta fara, domin a irin ganin da yake yi wa Rimsha jelly zata fita shekaru, kuma haka ne Jelly ta girmi Rimsha, nan fa ya fara tunanin tare da addu'ar Allah yasa bata fara ba, Allah yasa a hannunsa zata fara, Allah ya bayyana mashi ita, lokaci guda mood nasa ta sauya, har ja idanuwansa suka yi, damuwa karara ya bayyana mashi a kan fuskarsa. Su kuwa su Akila sai tsula tsiyarsu suke, basu yi tunanin yana ganin su kuma yana jinsu ba. Da suka gama da always sai suka wuce wajen pant, a nan ma sai da suka yi tsiya son ransu, har da wani cewa Rimsha ta fi su mazaunai dan haka ta juyo su gwadata karsu ɗauki pant karami wadda ba zai isheta ba, tun Rimsha na nokewa bata biye masu, har ta fara biye masu, suna yi suna dariya, abin gwanin ban sha'awa. Sai da suka gama kwasan duk abin da za su buƙata, sannan sa ka wuce wajen biya, keken ya cika tab da kaya, dogayen riguna kam ba'a magana, sun kwashesu iya son ransu. Haka aka yi wa Imran bill ya biya, ma'aikatan wajen suka shirya musu kayan a bayan mota, daga nan suka wuce gida. Suna zuwa ya wuce bedroom nasa, su kuma a ɗakin Rimsha suka baje kayan saman gado, suka shiga rabawa kowa tana ɗaukar nata, suna yi suna hira. Ba su suka rabu ba sai da Akil ya kira Umaisha a waya, sannan ta yi masu sallama ta kwashi kayanta ta wuce, ita kuma Akila sai da ta taya Rimsha suka jere kayan a cikin wall-drof sannan ta yi mata sallama tare da kwasan nata kayan ta wuce zuwa cikin gida, bata so rabuwa da Rimsha ba, ta so su kwana tare amma ba dama, domin Ammie ba zata yarda ba, Ammie zata je ɗakin ta domin ta dubata, hakan yasa ta wuce ba dan ta so ba. Ita kuma Rimsha Akila na tafiya ta miƙe ta shiga toilet, wanka ta yi ta fito, yau ga mayukanta da ta saba amfani da su lokacin da daddy yake nan, saman mirror chair ta zauna ta fara shafa Lotions ɗin, ga turaruka kala-kala, dama ba baya take ba wajen son kamshi, haka ta fashe jikinta sosai, sannan ta shirya cikin wasu riga da wando masu laushi na barci, ɗaya ne daga cikin kayan da suka sawo yanzu. Bayan ta gama shiri, sai ta haye saman bed ta bi lafiyar gado, tare da jan lallausan bargo ta rufe jikinta, ta yi addu'ar barci ta lumshe idanu. Ni kuma na haɗa kayana sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu a gidan daddy wato Washington DC bye 💖TRIPLET'S💖💖 E45_46 💖💖Washington DC💖💖 Zaune suke a palon kasa, Tga, John, Jay, da kuma daddy da Uncle Herry, Kamar dai kullum kowa da abin da yake yi, kowa hankalinsa na kan abin da yake yi, daddy da Uncle Herry suna shan black tea sun matso da glass table date tsakanin sofa set aky blue a gabansu, Jay da Tga suna aiki latsa waya da laptop, shi kuwa John yana kwance dan bai gama samun sauki daga horar da shi da Tga ya yi ba, yau ma kamar dai kullum ɗin sharholiyar su suke yi, kowannansu kananan kaya ne a jikinsa, bare ma Tga da shi rigar tasa ma ji yake tamkar ya cireta, saboda dama shi baya san harkar zafi ko ya take, har daddy da Uncle Herry dukka su three quarter ne a jikinsu zuwa gwiwarsu, yanzu daddy baya wani damuwa da rashin James domin kullun sai sun yi waya amma fa a na shi tunanin ne yana waya da James, a zahiriya kuma da Lion yake waya ba James ba. (To fah🤔) Lion ke shirya mashi wannan basajan domin basu son abin da zai ɗaga mashi hankali har ya yi sanadiyar taɓa lafiyarsa. Wani daddaɗar kamshin perfume suka ji, wadda basu taɓa jin irin wannan kamshin a gidan ba, har suna rige-rigen ɗago kai su kalli bene dan suga waye ne mai wannan kamshi, domin ta bene kamshin ke fitowa. Subhanallah miƙewa Tga, Jay, da kuma John suka yi lokacin guda suna kallon benen, daddy da Uncle Herry kuma ajiye cups ɗin hannunsu suka yi tare da zuba mashi idanu suna kallonsa. A hankali yake sauƙowa daga benen Musharraf na gefensa sun jero, sai murmushi yake yi. Sanye yake da wandon jeans, cikakken wando ba crazy ba, ba kuma guntu ba, har kasa kuma asalin Jeans wanda babu wani alkus a jikinsa, daga ta sama kuma yana sanye da Round neck polo shirt sky blue, yau ya yanke brown hair nan nasa, duk da cewa dama bata da wani tsawo sosai bata kai na Lion da James ba, baya barinta tayi tsawo dan tana takura mashi a cewarsa, amma yau ya yanketa kusan gaba ɗaya, wadda ta rage a kansa bata wuci kamar na yara kanana wayan da ake yi wa kitson roba ba, dan ko kusan kamuwa wadda ta rage a kansa nasa ba zata kamu ba. Kafarsa na sanye da Booth sky blue mai bala'in kyau, sai tashin kamshi yake yi, ya sanya glass baka a idanuwansa, fuskar nan tasa har wani kyalli take yi tana curly kamar wadda ya shafa baby oil, yau ya yi dressing na cikakken mutun mai hankali da ilimin tare da class. Shi ma Musharraf shigarsa kusan iri ɗaya da Michael ɗin, sai dai shi rigar sa fara ce. Basu taɓa ganin Michael a irin wannan yana yi ba, ga shi wani irin sihirtaccen gwarjini na jikin William jacop ne ya bayyana akan fuskarsa, kai da gani kasan jinin Lion ne, ya zama cikakken mutun, hannunsa na ruƙe da wayarsa, cikin natsuwa yake takawa har suka sauƙo kasa. "Hi uncle T, daddy, Uncle Herry hope you are enjoying your afternoon?" Shine abin da Michael ya faɗa, ya yi maganar cikin wata irinyar natsuwa kai ka ce Lion ne ke magana a wajen, saboda tsabar natsuwar da ya yi, da kuma yadda ya fito da words ɗin, sai ka yi zaton James ne, dan shima James daga bayan nan ne ya fara magana ya ɗaga murya, shima yana yi ne dan basaja, amma ba don haka ba, shima kasa-kasa yake magana cikin natsuwa. "Uncle T why are you stearing at me like this? Why are you people starding? Jay, John hope you are okey?". Ya yi maganar fuskarsa ɗauke da mamaki, domin yadda suka tsare shi da ido, ga shi sun mimmiƙe suna kallon shi, abin ya ba shi mamaki. Ganin sun kasa magana ya sa ya ce "Uncle ɗin James let's go" ya kai karshen maganar tare da wucewa ya nufi hanyar fita. "Where are you going?" Tga ne ya tambaya cike da izza. Ba tare da ya tsaya daga tafiyar da yake yi ba ya ce "Uncle T am i a baby?" "Michael What do you mean by your statement?!" Cewar Tga. Sai lokacin ya juyo a nutse ya ce " Yes Uncle am I a baby that you asked me where am I going". Tsabar haushi Tga ya ma rasa me zai ce mashi, wato shi ba yaro bane ya wuce a tambayi ina zai je, lallai Michael. Wucewa ya yi ya barsu da mamaki, Musharraf ya rufa mashi baya, suna fitowa harabar gidan kamar kullun jibga jibgan sojoji ne ta ko'ina a cikin gidan, ko wannan su kuma riƙe da manya-manyan bugayen bindigu, wadda da ka gansu kasan sun wuce wane da wane su riƙe su, na manya ne domin kuma bawa manya tsaro. Kai tsaye parking space ya nufa, yanzu Lion ya karawa gidan tsaro sosai saboda abubuwan da suka faru, kafin ka shiga parking space ɗin sai wata na'ura dake a wajen ta yi scanning naka sannan ka shiga, haka idan zaka fito da mota kamar dai a baya sai na'uran jikin gate ɗin ta faɗi kalar motar da aka fita da ita da kuma number motar kamar dai second gate, sannan idan ka je gate 2 ɗin ma sai ta sake maimaitawa dan tsaro. Haka Michael ya fito da wata sabuwar motar suka fito suka hau titi zuwa gate 2, sai da nauran wajen ta gama scanning na motarsu tsab, sannan gate ɗin ya buɗe kansa, yana buɗe wa Michael ya danna hanchin motar zuwa babban gate, ba ɓata lokaci jibga-jibgan security dake a wajen suka wangale masu katafaren gate ɗin, da gudun gaske Michael ya danna hanchin motar waje. "Michael ka ta fi a hankali mana". Cewar Musharraf ya yi maganar cikin yana yi na tsoro, dariya Michael ya yi yana faɗin "Uncle ɗin James kada ka damu, ko na yi gudu babu wani abin da zai faru, duk da cewa ma ban sanya alamar motar gidan mu bace, amma babu wani abu, bana son kuma na sanya ala'mar motar gidan mu ce saboda bana son magana ya koma gida akan an ganni a masallaci, idan haka ta faru nasan harbemu da gun za su yi mu dukkan mu biyu, shiyasa kaga na ɗauko sabuwar mota ba nawa da aka sanni da ita ba". Mamaki ne ya kama Musharraf, godiya sosai ya yi wa Ubangiji da ya sanya ƙwaƙwalwar Michael ta buɗu haka har yake iya fitarwa da kansa dabarar da zai bi ya tsirar wa wani abin. A haka suka isa masallaci suna ta hira cikin nishaɗi. Babbar masallaci ne sosai, da kusan ma shine babba a gaba ɗaya cikin Washington DC. Kallon Musharraf ya yi kafin ya kashe motar a parking space na masallaci sannan ya ɗauki face mask ya sanya a face nasa, ya juyo yana faɗin "Uncle ɗin James idan na gaya maka nasan za ka yi mamaki, wannan mosque ɗin fa Lion ya gina shi, da kuɗinsa, da shi da wancan babban church da muka wuce a hanyar mu ta zuwa nan, dukka shi ya gina, shi kuma James nasa mosque ɗin da church suna ta wajen jam street, nine kawai a cikinsu ban taba gina wajen wani bauta ba, amma In Sha Allah zan gina, su da suke Kristen ma sun gina bare Ni, zan gina very soon sai dai ni ba zan gina church ba gaskiya". Ya kai karshen maganar tare da buɗe kofar motar ya fito waje. *Masjidil Al Sultan* shine abin da yake rubuce a saman masallacin, "Asif who is Al Sultan?" Shiru Michael ya ɗan yi kafin ya ce "Like he is the one da yake control na mosque ɗin, domin lokacin da aka gama ginin Lion ya bani kuɗi na kawo mashi wai za su sayi wasu abubuwa na masallacin, alokacin shikuma ya tafi church dan ranar akwai church, sai ya ce in kawo wa Sultan, da na zo na tambayi waye Sultan sai suka nuna mani shi, gently man ne, yana da innocent face, baya da yawan magana, but is an old man sosai". Shiru Musharraf ya yi yana tunanin da alama Lion ba zai yi wuyar shiga addinin Musulunci ba, domin yadda yake taimakawa musulmai, duk da cewa ba iya musulmai kawai yake taimakawa ba, har da addininsa wato Kristen da kuma yan bautar gunki da sauransu, duk wasu gidan bauta yana kai musu taimako, baya ware ko ɗaya daga cikin su, amma Musharraf yana yi mashi kyakkyawar zato akan ba zai yi wuyar musulunta ba. Yau dai a masallaci suka yi sallah cikin farinciki da annashuwa, cikin natsuwa. Bayan sun idar da sallah suka fito waje, nan suka isko jama'a sosai a wajen harabar masallacin. Hannu Michael yasa a aljihunasa nan ya fito da kuɗi sosai, haka ya shiga rabawa musulman da suka fito Sallah a tare, ya zura ɗayar hannunsa cikin aljihun baya ya ciro wasu kuɗin ya bawa Musharraf dan shima ya raba sadaka. Allah sarki jinin William jacop ba dai kyautaba, gaba ɗaya Triplets suna da kyau da akwairi sosai, ba su jin kyashi wajen bayarwa, haka zalika idan za su bada basu duba cewa wanna ba addininsu ɗaya ba ba zasu ba shi ba, a'a duk da cewa basu son wata addini sai nasu hakan baya hana su bawa kowa kyauta idan suka ta shi. Ikon Allah kenan Wani bawan Allah da Michael ya bashi kuɗin, duƙawa kasa ya yi ya fuskanci gabas ya yi sujudur shukur yana hawaye, taɓa Musharraf Michael ɗin ya yi yana tambayar sa me yasa wannan mutumin kuma ya yi sujjada ba lokacin sallah ba, a takaice Musharraf ya warware mashi me sujudur shukur yake nufi. Jin haka yasa Michael ya duƙa suna fuskantar juna da mutumin, cikin mutuntawa ya ce da mutumin "Me yasa yake jin matukar daɗin dan ya ba shi wannan ɗan kuɗin?". Mutumin yana hawaye ya fara magana "Yau tun da na shigo masallaci nake ta rokan Allah da ya bani abin da za mu ci ni da family na, lokacin da na yi sujjadar karshe a sallah har hawaye sai da na yi dan yau kwana biyu ba'a yi girki a gida ba, Alhadulillah, Allah shine arrahman mai rahama akan bayinsa, shine wadda idan ka roƙe shi da kyakkyawar niya da kuma yakinin bayan shi ba mai iya baka, to zai cika maka burinƙa cikin ƙanƙanin lokaci, sai ga shi ban bar masallacin ba Allah ya biya mani bukata ta da na roƙe shi, Alhadulillah Alhadulillah, Allah ne ya bani ta sanadiyar ka, ina godiya ɗan uwana" ya kai karshen maganar tare da miƙe wa ya nufi hanyar fita daga masallaci. Dawo da kallonsa kan Musharraf ya yi domin ya yi mashi karin bayani dan gane da mutumin nan, ai kuwa tun bai tambaya ba Musharraf ya fara yi mashi karin baya ni, daga karshe ya rufe da cewa "Mutumin yana da karfin imani, idan da wani ne, kai zai ta zubawa godiya yana faɗin ka taimake shi ka bashi kuɗin sayen abinci, amma da yake wannan yana da imani ya san ya kamata, sai ya fara godewa Allah sannan ya gaya maka da bakinsa cewa Allah ne ya bashi ta sanadiyar ka, wannan shine gaskiya, idan da wasu ne cewa za su yi kai ka basu, irin mutanen nan basu da yawa sosai a duniyar yanzu". Yana kai aya a maganarsa Michael ya jawo hannunsa suka nufi mota, bai yi magana ba dan yasan dole akwai dalilin da ya sanya Michael ya yi hakan. Bayan sun shiga mota sai ya kunnata suka bar masallacin. "Michael ina kuma za mu je? Ka mance cewa za mu jira sai anyi sallar la'asar ne kafin mu koma gida?" "Uncle ban mance ba, ai ba gida za mu koma ba, kai dai ka jira ka gani" to kawai Musharraf ya amsa da shi, sai gudu yake shararawa da motar har suka fita daga kan titi suka tsallaka cikin wata unguwa, wadda da ka ganta ka san yan unguwar nan takaici ya yi masu katutu. Haka ya ci-gaba da kutsawa motarsa cikin wannan anguwar. Bakin wani gida wadda da ka ganshi kasan talauci ya yi masu katutu over, a nan ya juya kam motarsa suka sake fitowa daga unguwar suka nufi wata tampatsetsen Super market, wadda ya amsa sunan sa super market. A bakin gate ɗin shiga Super market ɗin tambarin sunan James ne a wajen, hakan na nufin Super market ɗin mallakin james ne. Ciki ya kutsa motarsa, bayan ya yi barkin ya fito, suka shige cikin shopping ɗin, kai da ga ganin wannan wajen kasan babu abin sa zaka nema ka rasa, mutun ne kawai basu saidawa. Kayan abinci Michael ya fata loda da abubuwan amfani na gida, ciki har da fridge mai ɗan girma, sai binshi da ido kawai Musharraf yake yi, duk wani abin da yasan ɗan adam zai buƙace shi a gida sai ya nunawa ma'aikatan dake binsa a baya, masu kula da masu sayan kaya dan su taimaka masu ta in da suka gaza, idan ya nuna masu sai su fitar mashi. Sai da ya lodi kaya har sai da Musharraf ya ce mashi ya isa haka nan, ina zai kai uban kayan nan haka? Bawan Allah tausayi ya rufe mashi ido, anguwar talakawan nan ya tayar mashi da hankali, mutumin da ya bawa kuɗi a masallaci nan ya tsaya mashi a ransa, kuma hakan yasa ya bi bayan mutumin har zuwa anguwar su, a nan ya ga tashin hankali, domin sosai ya rinƙa karo da yara ba takalmi a kafarsu, suna kuka riƙe da kwano a hannunsu alamar suna jin yunwa, kawai hakuri ya yi ya daure ya kawarda kansa domin ya bi bayan mutumin kada ya ɓace mashi, da suka je ya ga gidan ne sai ya juyo suka zo wannan shopping ɗin. Ɗaya daga cikin motoncin super market ɗin ne ta kwashi duk kayan da ya saya, dama suna da manyan motonci masu baya wadda idan ka yi shopping ɗin da motarka ba zata iya kwashe su ba, sai su ɗaukar maka da motorsu su kai maka har in da zaka je, kuma kyauta ne shi wannan kai kayar. ATM nasa ya bada suka ciri kuɗin kayan, sannan aka loda su a bayan motar, shi kuma shi da Musharraf suka shiga nasu motar suka yi gaba motar super market ɗin ta rufa masu baya. Kai tsaye kofar gidan wannan mutumin da ya bawa sadaka a masallaci suka nufa, a wannan karon daga ɗan wajen anguwar ya yi parking na motarsa ya fito suka kariso da kafarsa da Musharraf, wancan karon da kyar ya iya fitar da motar tasa daga unguwar ne, shiyasa yanzu ya barta a waje. Knocking na kofar gidan mutumin ya yi, kofar katako ce taci wuya sosai, wannan karamin yaro ma idan ya bugata da karfi zata ɓalle, ta sha ruwa sosai ga rana, duk ta zazzage. Daga cikin gidan wata mata ta amsa da ana zuwa, komawa gefe ya yi ya tsaya yana jiran fitowar su, yan unguwa kuma sai kallonsa suke yi. Mutumin da ya bawa kuɗin a masallaci ne ya fito, ganin su yasa ya fara ba su hakuri ya ɗauko kuɗin da Michael ɗin ya ba shi daga aljihunsa da nufi ya mai do musu da shi, dan a tunaninsa kuɗin su suka zo karɓa, Michael ya sanya face mask ga glass ba wanda ya gane wanene, nan take yan unguwa suka fara fitowa suna karisowa wajen dan su ji menene. Mutumin nan kuka yake sosai yana gaya musu idan ma wani laifi ya yi mu su to dan Allah kada su taɓa mashi familynsa shi su hukunta shi, idan kuma kuɗin su suka biyo to ga kuɗin nan dama yanzu zai je ya sawo masu abinci, yana magana yana hawaye gwanin ban tausayi, dan a irin kallon da ya yi wa dressing ɗin jikin Michael yasan ko a ƴaƴan manyan kasar ma sai wane da wane za su saka irin kayan, hakan ne ma yasa ya kara tsorita sosai da sosai. Matsowa kusa da shi Micheal ya yi ya rungume shi, dama shi ma ba baya ba wajen ruwan hawaye, nan take ya fara nasa hawaye, dan har ga Allah zuciyarsa ta yi mugun taɓuwa ganin mutanen nan cikin wannan hali, Allah sarki tun bai san menene falalar sadaka ba ma tukun nan, domin karatunsa bai kai nan ba, yana da tausayi sosai, dama ciwonsa ta mai da shi mara tausayi mara imani, ina da yakinin yawan sadaka da kyauta da yake yi ne ya sanya Allah ya cito shi daga duhun kafurci izuwa hasken musulunci. Wayan su yaran mata kanana guda biyu ne suka fito daga cikin gidan, dukkansu mata ne ba za su wuci yan shararu 6 zuwa 8 ba, sakin mutun Michael ya yi ya riƙo hannun yaran yana tumbayarsu menene sunan su, tsoro ya hana su gaya mashi sunan su, sai kallon babansu suke yi, ciro handkerchief daga aljihunsa ya yi, ya gogewa mutumin hawayen da ke a kan fuskarsa, shi ya sanya face mask a fuskarsa nasa hawayen bai bayyana ba, sannan ko kaɗan bai ji kyamar mutumin ba, duk da yake talaka yana da tsabta sosai, jikinsa tsab, shiyasa ma ya rungume shi ba tare da ya ji kyama ba, haka kuma yasa ya goge mashi hawaye da handkerchief nasa ba tare da ya ji wani abu ba. "Baba kana da yaro namiji". Michael ɗin ne ya tambaya, sai kallon shi mutumin yake yi da ya yi magana, domin yana son gane wanene, amma Michael bai bari hakan ta faru ba, saboda bai son asan ya je masallaci, idan aka sani a gida, yana da tabbacin wlh kashe shi za su yi, sai dai su kashe shi suna kuka, amma sai sun harbe shi. "E ina da yaro amma karamine 15 years yake da shi" to Michael amsa da shi sannan ya ce ya kira mashi yaron, wayan nan yara biyun da suka fitone, ɗaya daga cikin su baban ya aika ta kira mashi yaron, shi kuma Michael ya sanya wayan nan ma'aikata super market kwara biyu da suka biyo su akan su sauƙe masu kayan abincin. Ba ɓata lokaci suka fara sauƙe abin cin, da kansa ya raba abincin ya nuna masu wadda za su shigar wa da baba cikin gidansa, saura kuma su rabawa mutanen unguwa, har kasa baba ya duƙa yana hawaye, ganin farincikin da yake a kan fuskar bawan Allah nan sai da ya sanya Michael zubar da wani hawaye, ba zai iya jure ganin yadda jama'a ke ta yi mashi ruwan hawaye suna duƙawa suna zuba mashi godiya ba, dan haka sai ya kama hannun yaron baba da ya fito yanzu suka ɗan koma gefe suka bar wajen. "What is your name?" Ya tambaya yana shafa kan yaron, yaron ga shi kyakkyawa, ga innocent face irin na babansa, da gani ya samu tarbiya irin ta addinin Musulunci, ya samu ilimin addini sosai, a nutse sosai yake. "My name is Aryan" yaron ya bashi amsa, maimai ta sunan Micheal ya yi yana kokarin tunano a ina ya taɓa jin wannan suna, sai bayan wasu yan sakannin sai ya tuna ashe sunan da Musharraf ya ba shi ne farkon musuluntar shi, yar murmushin ya yi, Micheal kenan duk gidan William jacop shi kaɗan ke murmushin, ko su John basu murmushin, shima ɗin da addinin musulunci ta ratsa shi ne ya san e murmushi Sunnah ce da fiyayyayyen halitta manzon tsira manzon Rahma Annabi Muhammad (SAW) hakan yasa yake yin murmushin sosai a yanzu, bayan shi ba wani mai murmushi a cikin su, Lion da Tga kam ai dama su sai dai ma ace zuciyar kafuran farko ce ko kuma dutse ne a kirjinsu saboda kwarewar su a zafin kai, zafin zuciya, da mugunta. "Matakin karatun ka fa a ina ka tsaya?" Nan Aryan ya gaya mashi yana Jss 2 kuɗin makaranta ya kare ya dakata da karatu bai cigaba ba, shiru ya ɗan yi kafin ya sake cewa "Idan na buɗe maka business zaka iya zama har ka kula da shi ka taimaki iyayen ka da yan uwanka?". Michael kenan akwai kaifin basira, ya san cewa ka bawa mutun kuɗi ko abinci idan ya zo neman taimakon abin da zai ci ba shi ne ba, idan ka ba shi kuɗi ko abinci cikin ƙanƙanin lokaci zai cinye su, amma idan kana da hali ka taimaka mashi ka gina shi akan sana'a to nan ne ka yi mashi babbar taimako wadda koda million nawa ya samu agaba duk lokacin da ya taimaki wani ɗan adam da wannan kuɗi kai ma kana da lada sosai, kuma bashi sana'a da zaka yi hakan zai sanya zuciyarsa ta yi kwari ta ki mutuwa, zaka karfafa shi ya miƙe da kafafunsa, Michael akwai kwakwalwa wajen tunanin tun da Allah ya buɗe mashi ƙwaƙwalwarsa sanadiyar addua'o'i da Musharraf ke yi mashi, wa su addua'o'i ya tofa mashi a ruwan sha, wa su kuma a kan nasa yake tofa kashi, hakan yasa ƙwaƙwalwarsa ta fito da asalin kaifinta, gaba ɗaya yaran William jacop akwai su da kaifin kwakwalwar balai, har shi kan shi daddy yana da ƙwaƙwalwar domin lokacin da yake school kullun shine first class, mara kwakwalwa ba zai iya zama babban likita kamar shi ba, sai dai shaye-shaye da ya rinƙa yi bayan ya fara tsufa ce ta taɓa mashi lafiya, amma shima ba baya ba wajen kaifin basira. Cikin sauri Aryan ya ce "E zan yi sana'a koma wace iriya ce" "To gaya mani idan ka samu kuɗi sosai a wajen business ɗin me zaka fara yi da su?" Ba tunani ba komai kai tsaye Aryan ya fito da amsoshinsa, ta yadda zaka san abin yana ransa sosai. "Zan mai da su Suhana school, zan je in biya masu school fees, daga nan in sawo abinci sosai in kawo gida, dan baba ya daina shan wahalar neman, kullun idan ya fita sai kaga ya dawo a gajiye, wata sa'an ma sai ya dawo ya shiga ɗaki ya yi ta kuka, kuma duk saboda abinci, saboda bai kawo abinci ba, su Suhana suna kukan yunwa, ina jin zafin hakan, tom abinci shine abu na biyu da zan kawo gida, na uku kuma kullun ranar Jumma'a zan rinƙa sawa ana girka abinci sosai ana kaiwa masallaci domin wayan da basu da shi su rinƙa samu suna ci a can, na huɗu kuma zan rinƙa koyawa kannena sana'a, ma'ana idan sun sami hutun makaranta akwai in da ake koyar da sana'o'in sosai, can zan je na biya kuɗi su rinƙa koya, dan karda su taso ba su iya wata sana'a ba, suce sun dogara da baba, bayan kuma shima fama da kansa yake yi, na biyar kuma...." Michael bai bari ya karisa ba ya rufe mashi baki yana faɗin "Irin ku ake bawa jari wayan da suka san abin da suke yi, ga shi yanzu a maganar nan taka kasa na samu karin wata haske, dole nima zan nemo kwararru wajen iya girki, arinƙa dafa abinci ana kaiwa masallatai dan marasa karfi su ci". Sosai Aryan ya ji daɗin yadda Michael ya karɓe shi hannun bibbiyu, a wannan hali Musharraf ya isko su, nan ya tambayi meke faruwa, Michael ne ya labarta mashi yadda suka yi da Aryan, ba ƙaramin daɗi Musharraf ya ji ba, ya yi murna sosai hakan yasa ya kara karfafa masu gwiwa ta hanyar gaya masu falallar sadaka, duk masifar da musulmi yake ciki, matikar zai juri yin sadaka, tofa Allah subhanahu wata'ala shi ka kansa ya yi alkawarin ya ye mashi wannan damuwa, sannan aduk sadaka da mutun zai yi babu sadakar da ta fi falala irin sadakar abinci, tana da falala fiye da tunanin mai tunani, cikin kankanin lokaci Allah zai warware maka damuwar ka, matukar zaka juri yin sadakar abinci koma ya ya take. Wani karin karfin gwiwa na musamman Michael ya ji a tattare da shi, lokacin guda ya ji zai iya karar da duk wani abin da ya mallaka akan sadaka da taimakawa bayin Allah. Da wannan shawara Michael ya ce da Aryan gobe zai dawo su je ya duba irin sana'ar da zai iya sai ya buɗe mashi shago a kasuwa, sannan batun makaranta zai je har school ɗin ya biya masu kuɗin makaranta, daga haka suka koma wajen baba, already ma'aikatan Super market ɗin James sun gama rabon kaya sun shigarwa da baba nasa cikin gida, sun koma wajen aikin su, wato sun koma super market ɗin, jama'a sun watse. A kofar gidan Michael ya tsaya ya ce da Aryan ya kira mashi babansa suyi sallama, da sauri Aryan ya shiga cikin gida, shi kuma Michael ɗin suka cigaba da hira da Musharraf, yana kara gaya mashi falalar taimako da sadaka. A haka baba ya zo ya isko su, ya ce su zo su shiga cikin gida, fuska ɗauke da murmushi Michael ya ce a'a nan ma ya isa tafiya za su yi yana son sanin ko akwai wani abin da yake buƙata ne, cikin sauri baba ya ce a'a baya bukatar komai ya kara da zuba masu ruwan albarka da godiya sau ba adadi. Ganin godiyar baba ba zai kare ba ya sa Michael ya yi musu sallama, Aryan ya raka su har wajen mota, Michael yana jin kaunar Aryan a ranshi tamkar ɗan uwansa na jini, tsabar farinciki har ya rasa me zai bawa Aryan, sai ya ɗauko ruwa daga cikin motar tasa roba ɗaya ya miƙa mashi, sai murmushi Musharraf ya ke yi, haka suka ja motarsu suka koma masallaci. A ɓangaren Lion kuwa. Sai karfe 8 na safe ya farka daga barci, a hankali ya waro dara-daran blue eyes nasa, sai wani kyalli fuskarsa take yi, wow yau ya sami barci mai daɗi, ga yanayin gari ga shi kuma yana wani irin yanayi mai daɗi wadda shi kaɗai ya san menene silar shigarsa wannan yana yi, a hankali ya janye lallausan bargon dake jikinsa, shiru ya ɗan yi na mintoci yana tunanin akan mafarkin mum ɗin su da ya yi daren ji, me yasa take yawan zuwa mashi a mafarki a cikin wata iriyar suffa mai wuyar gane wa, yana buƙatar amsa akan hakan. Ya jima kwance yana ta zarin abubuwa guda biyu, na farko mum ɗinsa, na biyu kuma tafiyar da zai yi gobe. Bayan wani lokaci a hankali ya zuro kyawawan fararen kafafunsa kasa kafin ya miƙe gaba ɗaya, ya zauna a bakin gadon, bin ɗakin nasa da kallo ya fara yi, tun karfe shida na safe Tga ya gyara mashi ko ina ya feshe ko ina da daddaɗar air freshener sa mai bala'in kamshi da kyau da tsada, kasa tiles ɗin ɗakin tsabar haske kamar madubi, da yake tiles ɗin fari ne kana iya ganin kanka a ciki, ga shi yana samun gyara, sai ka rantse da Allah kafa bai taɓa taka shi ba saboda haske. Jawo laptop nasa ya yi domin ya yi bincike a cikin camerar da ya sanyawa mum ɗin sa a kofar gate ɗin shiga gidan ta, saboda yana son gane gaskiya tsakanin ita da daddy, waye ya cuci wani, sannan kuma yana zarginta da shiga irin kungiyar su James, domin wayan can mutane guda biyu da ya taɓa kamawa, ya kama sune da manyan kwayoyin maye da kuma sun yi wa wata yarinya fyaɗe, daya tambaye su shine suka gaya mashi cewa kayan mayen Josephine za su kai wa, ita tayi oder su, sai ya yanke mu su gaba na fyaɗen da suka yi, ya kuma miƙa wa Tga su dan ya yi mu su hukuncin dillancin kayan maye da suke yi, wannan dalili yasa ya sanya mata camera a kofar gidan ta, domin shi baya yanke hukunci da kai kawai, baya yanke hukunci daga jin zance daga bakin wasu, no sai ya yi bincike yake hukunci. Kunna laptop ɗin ya yi yana wani lumshe dara-daran idanuwansa alamar akwai wani abin da yake tunawa. Baki ɗauke da excuse Tga ya shigo cikin ɗakin, hannunsa ruƙe da cup mai bala'in kyau sai ɗaukan ido yake yi fari kal da shi, ɗan cup ɗin yana ɗaure ne saman wani kyakkyawan plate karami mai bala'in kyau, hot coffee ne a cikin cup ɗin, sai turiri yake yi. Kusa da Lion ya zo ya zauna tare da miƙa mashi coffee ɗin, shiru Lion ya yi bai karɓa ba kuma bai juyo ba. Idan da sabo sun saba da halinsa hakan yasa ya ce "Good morning sir" nan ma shiru aikin da yake a gaban sa kawai yake yi. Almost 10 mins sannan ya ɗan juyo da kallonsa kan Tga ɗin, calmly ya fara magana "Ni na ce maka ina buƙatar coffee ne?" Cikin sauri Tga ya ce "No sir kawai dan naga kasha jiya ne that is why na yi tunanin Maybe zaka buƙata a yanzu ma". A maimakon ya ba shi amsa sai ya ce "Tafiyar sirri zan yi, ko daddy ba zan gaya ma ba, but idan ya tambaye ka just tell him the truth akan cewa na yi tafiya, and then ka kula da lafiyarsa sosai, ni kaɗai zan je za mu yi waya". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa ya shiga toilet, bin shi da kallo Tga ya yi yana mamakin hali irin na sa, tabbas ko a magana ba zaka taɓa gane in da ya dosa kai tsaye ba, yana magana ne a murɗe kamar yadda yake shima a murɗe, yanzu maganar da ya yi a nan wajen Tga ya kasa fahimter ina maganar ta dosa kai tsaye, zaman ka lafiya shine kawai idan ya ce ka yi abu, tofa kawai ka yi shi, idan ba haka ba, ka ce sai ka binciko ka gane asalin in da abin ya dosa, tofa zaka shekara babu abin da zaka fahimta, karɓar umarni ya fiye maka sauƙi in ba haka ba ƙwaƙwalwarka ta tarwatse. Yana tsaka da tunani sai ya ji laptop ɗin Lion dake a gabansa ta yi yar kara, ɗaura cup ɗin ya yi saman bedside drawer ya jawo laptop ɗin ya fara dubawa, abin mamaki kuma abin al'ajabi da Tga bai taɓa sammani ba shine ya gani a cikin laptop ɗin. Zaro idanuwansa sosai ya yi yana kallon abubuwan dake a ciki, ɗago kai ya yi ya kalli kofar toilet ɗin, afili ya ce "Jinjina mai girma, a ya za dole ka yi tafiya, kuma ya zama dole jiya ka shiga yana mai daɗi" ya kai karshen maganar tare da fita daga wajen ya shiga bincike akan ina aka tsaya dan gane da wayan da suka kama James. A wannan hali Romeo ya fito ya same shi ɗaure da towel a kugunsa, ga kuma wani ƙaramin a hannunsa yana goge dark black curly hair sa da shi. Gaban mirror ya zo ya tsaya ba tare da ɓata lokaci ba ya shafe jikinsa da Lotions nasa masu kyau da tsada, da ga nan ya gyara gashin kansa tare da shafeshi da mayuka gashinsa masu kyau da tsada, ya fesa perfume nasa mai bala'in kamshin nan, wadda tun kafin ya iso waje perfume ɗin yake riga shi isa saboda bala'in kamshinta, already kamshin ta kama jikinsa, ko bai saka ba kamshi yake yi sosai, amma kullun sai ya sa, ya riga da ya saba. Bayan ya kammala ya wuce dressing room nasa. Komai nasa a nutse yake yi daki daki, ɗaya na bin ɗaya, a nutse ya shirya cikin Ripped Jeans blue color da high neck t-shirt black color, ya ɗaure gashin nan nasa a baya, ya bar wannan guntu na gaban goshin nasa, sai tashin fitinannen kamshi yake yi, ya yi wani masifaffen kyau, sai kyalli fuskarsa take yi, ga idon nasa wani irin idan ka gansu sai ka rantse da Allah kwalli yake saka masu saboda tsabar kyau. Ko sannu bai ce da Tga ba da ya fito, wayarsa kawai ya ɗauka ya nufi waje, palon kasan babu kowa a lokacin, kai tsaye waje ya nufa. Yana fita dubbanin jibga-jibgan sojoji dake harabar gidan suka fara ɗaga hannu suna sara mashi, ji kake dim sun buka kafa a kasa alamar girmamawa, ko mutun ɗaya bai ɗaga ido ya kalla daga cikin su ba, gaban sa kawai yake kallo, kai tsaye ya wuce cikin lambun daddy dake cikin gidan. Akwai wata rumfa mai bala'i kyau da akaiwa daddy a cikin lambun dan hutawa, da zana irin na zamani aka yi shi, an jera wasu irin kujeru wadda aka yi su da wani irin abu kamar zana, kujerun nan sun haɗu ba kaɗan ba, launin dark brown suke, a tsakiyar su kuma sai aka sanya tables mai bala'in kyau shima, gaba ɗaya rumfar kewaye take da wasu irin fitillu masu bala'in kyau suna bata hasken wuta kala biyu, su bada blue su kuma bada fari, ga shuke-shuke iri daban-daban a cikin lambun, akwai fruits kala-kala har da bishiyar tuffa wato apple abin ba'a magana sai wadda ya gani, amma dai lambun ya haɗu sosai. A saman ɗaya daga cikin kujerun ya zauna tare da tura massage akan a kawo mashi fruits da maltina. Ai kuwa ba ɓata lokaci sai da jibga-jibgan bodyguard guda uku sun doso wajen, ɗaya hannunsa na ruƙe da kwanton fruits irin wanda ake yin sa kamar sakarnan, kwandon ba shi da zurfi sai faɗi, amma yana da bala'i kyau sosai, sun shaƙe shi da fruits kala kala wayan da ba'a yanka ba, ɗayan bodyguard ɗin kuma yana ɗauke da wani katon plate mai shaƙe da fruits kala-kala wayan da aka yanka su, bayan an yanka su kuma sai aka sanya fork spoon a cikinsu ta yadda mai sha zai rinƙa ɗauka kawai yana kaiwa baki, sannan an rufe plate ɗin da wani plate shima mai kyau, dan kar wani abin ya hau kan fruits ɗin, shi kuma bodyguard na karshe ɗauke yake da plate mai ɗauke da maltina guda uku sa glass cup mai ɗan karen kyau, irin dogayen glass cup ɗin nan ne, wanda kasansu yake a baje, a ɗayar hannunsa kuma yana riƙe da tissue a cikin abin sanya tissue ɗin. Kai tsaye saman table ɗin gabansa suka zo suka ajiye mashi, sannan suka tsaitsaya a gefensa suna jiran umarni, ko kuma ko zai buƙaci wani abin. Kwantar da kansa ya yi a saman jikin bangon kujerar sannan ya ɗaga kan nasa sama tare da lumshe idanuwansa, bai ce da su ko uppan ba. Almost 10mins suna a tsaye, daga karshe sai ya yi masu alama da hannunsa akan su tafi ba tare da ya buɗe ido ba, kuma bai yi magana ba, ɗan dukar da kai kasa suka yi kafin su wuce cikin gida, a al'adar su yin hakan shine girmamawa. Shi kuwa haka ya cigaba da zama shiru a wajen idanuwansa a lumshe da alama wani abin yake tunani. (Ni kuma na haɗa kayana izuwa Nigeria dan naga yadda abin zata kaya, Lion sai na dawo, wata kila kafin lokaci ya ɗan ci wani abin Bawan Allah) Bari mu fara da maman Sadiq Katsina mu gani. Sosai suka ji daɗin wannan kuɗi da Imran ya basu, zuwa maman Sadiq ta yi ta ɓoye kuɗin har sai da Sadiq ya dawo daga wajen aiki da daddare, bayan sun ci abinci sun yi sallah ne suka zauna take gaya mashi abubuwan da suka faru, sosai ya taya Rimsha murna, a cikin zuciyarsa kuma yana kukan rashin Jehan dan yana bala'in sonta. Maman sa ne ta tambaye shi ya za su yi da kuɗin, nan fa ya kawo shawarar akan su kama hayar shagon nan da yake ɗan gaban layin nan nasu kaɗan, tun da ance za'a bada shi haya, kuma bashi da wani tsada 20k ne kuɗin hayar shekara, to su kama sai su sawo kayan provision da sauran 180k ɗin su zaba a ciki shigon, sai Yusuf ya rinƙa zama a ciki yana kula da shi, shi kuma sha'aban ya rinƙa bin shi suna tafiya gareji a tare, sosai maman Sadiq ta ji daɗin shawarar ta kuma karɓa hannu bibbiyu, shima Yusuf ya ji daɗi sosai ko ba komai zai bar zaman banza alayi, kuma zai rinƙa samu ɗan na kashe wa. Da haka suka yi ta hirarsu cikin farinciki har can dare wuraren karfe 10 sannan suka yi sallama da juna suka wuce ɗakin su, ita kuma maman Sadiq ta miƙe ta rufe kofar ɗakinta ta haye yar katifar ta ta kwanta, cike da farinciki ta yi barci. Asuba ta gari. A ɓangaren Su Rimsha kuwa. Tun karfe bakwai na safe Akila ta baro part nasu zuwa nasu Rimsha ɗin, domin yau babu school sai murna take yi za ta wuni tare da Rimsha. A palo ta isko Imran yana zaune yana kallon News a Tv, kusa da shi ta zauna suka gaisa cike da kaunar juna, sannan ta miƙe ta nufi ɗakin Rimsha tana gaya mashi ba wajen shi ta zo ba, dan haka ta tafi wajen wadda ta zo, sai murmushi kawai yake yi abinsa. Da sallama ɗauke a bakinta ta shiga bedroom ɗin, Rimsha sarkin son gayu da kwalliya, wani irin fitinannen kamshi ne ke tashi a cikin ɗakin, ta sha wankanta ta yi fes, tana sanye da doguwar riga fari tas mai bakai kyau, an yi mashi kwalliya da wasu duwatsu jajaye masu bala'in kyau, sannan ta gyare ko ina a cikin ɗakin nata, ba abin da ke tashi sai sanyin Ac da kuma kamshin air freshener sannan ga kamshin perfume dake a cikinta, sai suka haɗu suka bada kamshi na musamman, tana kwance saman lallausan bed nata ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya, an samu duniya, komai ya daidai ta, tana ruƙe da wayarta tana latse-latse. Jin sallamar Akila yasa ta ɗago tare da ajiye wayar, ganin Akilar yasa ta sakar mata wani irin cool murmushi wadda sai da fuskarta ya zaman tamkar tauraruwa mai walwalin haske a tsakiyar duhun dare, ga shi ta sanya lips balm a lallausan lips nasa, sai ta kara kyau sosai. "Aunty Akila sannu da zuwa" ta faɗa a sanyaye, murmushi ita ma Akila ta sakar mata kafin ta ce "Wow First lady gaskiya kin yi kyau sosai, wai irin wannan ɗaukar wanka haka, dole yaya Ahmad ya ce mani ranar da ya fara ganin ki bai runtsa ba, wai irin wannan kyau ko nima ba zan runtsa ba bare shi, ya ce mani ranar kwana ya yi yana tunaninki Queen of beauty, gaskiya ya zaɓi sunan daidai dake" ta kai karshen maganar tare da hayewa saman bed ɗin ta cigaba da faɗin "Amma me yasa baki saka riga da wando da muka ɗauka iri ɗaya jiyarnan ba? Wlh ba karamin kyau zai yi maki ba, kin ga dai kin fi mu hips kayan za su zauna maki sosai wlh". Miƙewa zaune ta yi fuska ɗauke da kayatatcen murmushi ta ce "Aunty Akila shi wannan dogon rigar bata yi bane?" Cikin sauri Akila ta girgiza kai tana faɗin "Sosai ma ya yi maki kyau, amma anjuma ki sanya riga da wandon sai mu yi anko, dan nima shi zan sanya idan na yi wankar rana" Gyaɗa mata kai Rimsha ta yi alamar to, sannan ta zuro kyawawan kafafunta kasa ta miƙe ta nufi Palo. "Ina zaki je Rimsha?" Ba tare da ta dakata da tafiyar da take yi ba ta ce "Palo zan je dan naji kamar yaya Imran ya fito ne, ina son mu gaisa ne sai na tambayi me zan girka mana". Da sauri ita ma Akilar ta miƙe ta bi bayan ta tana faɗin "Me za ki girma mana ne ko kuma me zamu girka? Ai abin da yasa ki ka ganni a nan yanzu kenan, dan na koyi girki". Ta kai karshen maganar lokacin da suke fitowa Palon. Yadda Akila ta barshi ɗazun haka suka fito suka same shi, zama suka yi saman sofa mai zaman mutun 3, suna fuskantar juna da shi, cikin girmamawa Rimsha ta ɗaga mashi gaisuwa. Cike da kulawa ya amsa mata gaisuwar tata, tare da tambayarta ya ta kwana, lafiya ta amsa mashi da shi sannan ta ɗaura da tambayar me za su girka. Sai lokacin ya ɗago ya kalleta, wani irin kyau ta yi mashi, fuska ɗauke da murmushi ya ce "Ki girka duk abin da kike son ci, ni bana zaɓen abinci, sannan idan ba damuwa anjuma da daddare Dr ya ce zai zo tare da kanwarsa dan ta dame shi su je yawo, to zai kawo ta nan, fatan zaku karɓeta hannu bibbiyu sannan ina son ku yi masu girki mai daɗi" cike da murna har suna haɗa baki wajen cewa "E zamu karɓeta kuma zamu shirya masu haɗaden girki". Albarka ya sanya masu sannan ya ɗaura da cewa "Rimsha baki gaya mani wani kasa kike son zuwa school ba?" Kafin Rimsha ta yi magana Akila ta rigata da cewa "Yaya Imran tare zaka kai mu, kuma Usa muke so" ɗan murmushin ya yi kafin ya ce "To heartbeat an gama, amma dai banso Usa nan ba, amma ba komai zan san yadda zan yi". Ihu Akila ta kurma tare da tashi ta rungume shi tana dariya, yana bala'in son ganin farincikin Akila, dan haka sai ya kara da cewa "Za'ayi maku komai da wuri nan da next week ko two weeks zaku tafi". Sosai Akila ta kankame shi, ita kuma Rimsha banda murmushi ba wani abin da take yi. Haka suka miƙe cike da farinciki suka wuce kitchen dan shiryawa kansu abincin safe mai rai da lafiya. A ɓangaren Jelly da Ummi kuwa, tsab suka shirya suka nufi gidan Hajiya Khadijat wato maman su Irfan. Suna zuwa ba ɓata lokaci suka wuce gidan su Irfan a tare dan suje suga gidan, da kuma tsarinsa. Daga waje suka yi parking na motarsu sannan suka fito izuwa cikin gidan. A palo suka isko Aunty tana zaune tana kallo, ta ci wankanta ta sha kwalliya, dan yanzu jikinta Alhadulillah sauki na samuwa sosai sai dai muce Masha Allah. Babu ko sallama suka faɗo cikin Palon, babu kowa sai Auntyn ita kaɗai, daddyn Jelly da Ayla sun fita shopping, shi kuma Irfan yana part nasa yana barci. Awannan karon Aunty bata wani damu ba, domin ta san ko su waye, fara zagaye palon Ummi ta yi tana faɗin "Kai Masha Allah Aunty Hadiza ki ce mini abin arziki kam har ya kai haka" ta yi maganar tana taɓe baki, kuma duk cikinsu ba wanda ya kuka Aunty har jelly dake a tare da su. Wani shu'umin murmushi Ommu ta yi tana taunar chewing gum kas-kas-kas, cike da shakiyanci ta ce "Wlh kuwa kedai Turai bari da ana zaton na mutune za'a mamaye komai, sai Allah ya yi ina raye, kuma gida dai nawa ne, yanzu dai mu haura sama dan muga ɗakunan yadda suke". Kai daga jin yadda Ommu ta yi wannan magana kasan da biyu ta yi shi, sannan kuma mawuyacin abune ayi zaman lafiya da ita, domin babu shi a tattare da ita. Aunty baiwar Allah ita bama ta su take yi ba, Jelly kawai take kallo, dan taga ta yi mata kama da yaya maik wato daddynta, sai dai kash rashin sani yafi dare duhu, yau ga jelly har cikin gidansu amma Aunty bata santa ba bare ta gane ta, sai dai tabbas taga kamannin dake a kan fuskokinsu. "Ke me kike wani kallona ido kamar na tsohuwa mayya" cewar Jelly ta yi maganar tana karewa Aunty kallo, ai kuwa maganar da ta yin nan ba karamin jefa Aunty cikin tunani ta yi ba, domin sak muryar daddynta ta ji, amma kuma bata kawo cewa Jellyn da suke nema bane, saboda ganinta da su Hajiya Khadijat da ta yi, ta yi tunanin cewa ƴarsu ce, amma dai har cikin ranta ta jinjinawa wannan kamanni na daddy da jelly ga kuma murya shima iri ɗaya, ita ma Hajiya Khadijat ta sha ruwan mamakin lokacin da ta ga Jelly, dan ita ma taga Kamannin, amma sai Hajiya Turai ta ce da ita ai yar uwan baban su Nawid ne, shiyasa ta bar zancen. "Kai baby kin cika rigima wlh, ke kuma tsohuwar mayya me kike wani ganinta? To idan ma baby ce wlh a hir ɗin ki ta fi karfinki, sai dai gani sai hange daga nesa" Cewar Ummi ta yi maganar cikin faɗa. Ommu ne ta ce "Ke ma dai Turai me abin ɓata baki a nan? Ai wannan bata kai ku yi mata magana ba, ni fa bana ɗauka ma a gidan nan akwai mutun, dan haka mu wuce dan Allah, da ku tsaya ɓata bakin ku wajen yin magana da ita ba gara ku yi da bango ba, koba komai ya fita daraja". Shekewa da dariya suka yi tare da haurawa sama, Jelly na biye da su abaya tana wani turo baki kamar biro, da ido kawai Aunty ta bi su, tana ganin ikon Allah yau iya ganin idonta. *Wannan Hajiya Hadizar ita ya kamata acewa kanwar sheɗan ba A'isha na gidan Hajiyar daɗi ba* Aunty tana zaune a wajen har suka gama dube-duben su a sama, suka sauƙo suka fice suka bar gidan, ko uppan bata ce masu ba, sai ma addu'ar neman Ubangiji ya tsare ta daga sharrinsu da take yi a cikin zuciyarta. Baiwar Allah tana ganin rayuwa. A ɓangaren Aafia kuwa babu wanda ya lura da ɓacewar tata, domin Abbi ya san tana gidansu Akil, shi kuma Akila a tunaninsa ta koma gida hakan yasa basu nemeta ba. (*Tofa Aafia kinga ta kanki, wannan shine ɗaya daga cikin illar gida biyu, mutun ya kasance gida biyu yake, yau nan gobe nan, sai ya ɓata ba wanda zai farga da wuri har sai ma duk abin da zai faru ya faru kafin a farga, ni dai ina jajanta maki kuma na haɗa kayana sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu, dan jin yadda zata kaya*) 💖TRIPLET'S💖💖 47-48 Gidan Abba. Sosai su Rimsha suka shirya haɗaɗen girkinsu mai rai da lafiya, bayan sun kammala suka jere a saman dining table, Sannan Akila ta wuce part nasu dan ta je ta yi wanka, ita kuma Rimsha ya wuce ɗakin ta dan yin wanka. After some hours da ba su fi biyu ba. Zaune suke a palo sun baje suna cin abinci suna hira, Imran, Akila, Rimsha, tamkar sun saba sosai haka suka kasance, suna ci cike da nishaɗi da kuma santi, sai hirarsu suke yi. Bayan sun gama cine, Akila ta ɗauko Alqur'ani mai girma a ɗakin Imran tana faɗin Rimsha ta kara mata karatu, dariya sosai Rimsha ta yi kafin ta ce "Aunty Akila ina da tabbacin kin wuceni a karatu" "A'a Rimsha Allah ban wuce ki ba ni dai ki kara Mani" to Rimsha ta amsa mata da shi sannan ta karɓi Alqur'ani ta fara karatu, kunna recording Imran ya yi a wayarsa yana recording na zazzakar murya nan nata. Cikin suratul Maryam take karatun a nutse, a wannan hali Akil ya shigo ya same su, saman sofa ya zauna yana gaishe da Imran, da fara'a Imran ya amsa sannan suka yi shiru suna sauraron kira'ar Rimsha dake tashi, ga zazzakar murya nan nata ba'a magana. Sai da ta kai aya sannan ta ce "Aunty Akila wani sura zan duba Maki?" Akila na ƙoƙarin yin magana Akil ya rigata da cewa "Yaya Imran wannan ita ce wadda ka gaya mani jiya a kan ka kawota gidan nan ko?" Gyaɗa mashi kai Imran ya yi alamar e. Dawo da kallonsa kanta ya yi tun kafin ya yi magana ta rigashi da cewa "Ina kwana?" lafiya ya amsa mata da shi sannan ya ɗaura da cewa "A ina kika tsaya da hadda?" Akil kenan yana bala'in kaunar ya ga mutun yana karatun Addini, ko da bai san mutunba matukar zai yi karatun addnin tofa zai taimaka mashi ba kaɗan ba. Bayan ta gaya mashi ne, sai ya ce "To zan koma Madina nan da wata mai shiga, kafin na koma sai ku rinƙa zuwa ina kara maku har ma da na boko, kullun karfe 5 na yamma zuwa shida zamu yi lesson, yanzu ma bari na baku hadda koda shafi ɗaya ne, amma fa duk wacce ta yi wasa zan zane ta, bana son wasa da karatu". Sai murna suke yi suka amsa mashi da to, tare da kawo mashi Alkur'ani kowace ta faɗi daga in da zata tashi, nan ya kara masu shafi bibbiyu dan sun ce ɗaya ya yi masu kaɗan. Bayan ya kara musu ne ya jaddada masu karfe 5 daidai su same shi a garden na gidan dan su kawo haddan su ya kara masu wani. Sai daɗi suke ji suka amsa da to tare da miƙewa suka nufi bedroom ɗin Rimsha. Suna shiga Rimsha ta ajiye Alqur'ani mai girma a saman mirror drawer, sannan suka haye gado suka fara zuba hira. Suna tsaka da hira Ahmad ya kira, cikin sauri Rimsha ta jawo wayar, tana ƙokarin yin picking kenan Akila ta ce "Kai Rimsha ki rinƙa jan aji mana kada ki ɗauka da wuri ki bari sai wayar ta kusa katsewa, idan ba haka ba yaya Ahmad zai ce kina da arha sosai, ko muna son abu ya kamata mu rinƙa jan aji akan shi". Harara Rimsha ta watsa mata kafin ta ce "Ni na ce maki ina son shi?" Yar dariya Akila ta yi tana faɗin "Ai ba ke kika ce ba, alama ce ta nuna, har da wani saurin ɗaukan kira, kai Rimsha, ki tasa Bawan Allah a gaba kina zuba mashi shagwaɓa da malamai har sai ya susuce maki ko? Wlh yaya Ahmad yana ruwa, thank God ni ba ni da saurayi amma fa duk saurayin da ya zama masoyina sunansa Sorry" ta kai karshen maganar tana dariyar iyashege. Wayar har ta katse Rimsha bata ɗauka ba ta biyewa Akila. "Aunty Akila ni fa abin da ya sanya zan ɗauki wayarsa da wuri haka, saboda ina son tambayarsa number wannan yar uwar tawa Ayla da na baki labari jiya, shine fa yasa zan ɗauki wayar". Hararar gefen ido Akila ta yi mata cike da zolaya ta fara magana "To haka ne? Amma dai kada na ji an kashe murya, ayi mashi magana kamar yadda ake yi mani, idan ba haka ba zan mashi recording naki idan kina magana da ni, na tura mashi na ce ya ji muryar ki yadda kike yi mani magana, duk da cewa ma dai voice ɗin naki ƙarshe ne a daɗi" ta kai karshen maganar tana juyawa ta bata baya. Rimsha tana ƙoƙarin yin magana kiran Ahmad ya sake shigowa a karo na uku kenan, cikin sauri ta yi picking tare da kai wayar kunnanta, a nutse ta fara magana "Assalamu alaikum Yaya Ahmad ina kwana?" Ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya amsa mata da "lafiya Lou Alhamdulila My beauty ya kika kwana?" Lafiya ta bashi amsa sannan ta ɗaura da cewa "Dan Allah yaya Ahmad number Ayla nake son ka turo Mani" To ya amsa da shi sannan ya katse kiran ya turo mata number tare da sake kiranta. Ba dan taso ba ta ɗauki wayar suka fara hira, kamar dai kullun E da a'a shine kawai abin da take bin shi da shi, bai wani damu ba, shi dama burinsa kawai ta ɗauki wayar. Har Akila ta yi barci Ahmad bai ga ji da yiwa Rimsha surutu ba, sai da ya ji ta daina amsa mashi da e da a'a ɗin ma, sai ya ce to za su yi waya anjuma, to ta ce mashi suka yi sallama. Kamar jira take yi dama, yana katse kiran ta fata kokarin gwada layin Ayla, layin a kashe, ba dan ta ta so ba, ta ajiye wayar ta miƙe ta ɗauko Alkur'ani mai girma ta fara biya karatun da Akil ya kara mata, domin tana son kafin yamma ta haddace, ta yadda zata kai babu gargada, kuma tana son ya kara mata a yau ɗin, tana son rufe haddarta gaba ɗaya, a yanzu haka tana da izu arba'in a kanta, to tana son rufe ashirin ɗin gaba ɗaya. Sosai ta dage tana karatu ita kuma Akila tana barci, ni kuma na haɗa kaya na zuwa wajen su Aafia. 🥺💔BANDIT'S💔🥺 Suna zaune cikin wannan bakin ɗaki mai cike da bakin ciki da tashin hankali, babu wanda yake iya ce da ɗan uwansa uppan, kowannensu bala'in yunwa yake ji sosai, gaba ɗayan su kusan buri ɗaya ke a zuciyoyinsu. Wannan buri kuma ba wani buri bane fa ce a kashesu su huta, amma sai dai bandits ɗin sun ki su kashe su. Suna zaune a haka har bandits nan suka zo bakin kofar wajen suka ce da su su fito, da yake sun saba sai suka yi maza suka ta shi. Aafia ta sha ruwan mamaki ganin yadda suke rige-rigen wajen fita, har suna ture juna, abin ya ɗaure mata kai, kamar waƴanda za'a bawa wani abin a wajen, sai mamaki take yi tana tafiya a hankali ta bar Rufee kwance a wajen. Bata ankara ba sai jin saukar wata shegiyar bulala ta yi a tsakiyar gadon bayanta, ihu ta kurma a guje ta bazama wajen sauran mata da suka yi gaban. Abin da yake faru wadda ita bata sani ba shine, idan bandits ɗin suka ce ku fito, to kayi maza ka yi gaba, idan ba haka ba ka tsaya baka sauri to za su zane maka jiki da shaggun bulalun nan nasu, to ita bata sani ba, ta tsaya tana tunane-tunanenta, shiyasa ta sha bulala. Can cikin wani ciyawa da suka kewaye da wasu kirare suka je suka zazzauna. Wata mata dake zaune ɗan gefe da Aafia ne yaron ta na goye ya fara tsallara kukan yunwa, cikin saurin matar da ta zauna da Aafia a ɗaki ɗazun ta sanya hannu ta toshewa yaron baki, buge mata hannu uwar yaron ta yi tana faɗin "Baki da hankali ne ke? Kashe mani yaron zaki yi? Ya zaki toshe mashi baki yana kuka?" Kallon bandits dake kewaye da su matar ta yi kasa-kasa ta ce "Wlh idan kina son yaronki to ki sanya shi ya yi shiru, na lura ke bakuwa ce a nan, amma ni dai na gaya maki idan ba haka ba zaki rasa yaron nan, domin sun tsani kukan yara, last week suka kashe wani jariri a nan wajen, to kema ki yi da taka tsan......." Bata iya kai karshen maganar ba sakamakon wani bandit da ya shigo cikin wajen ya fisgo wannan yaro daga bayar uwarsa ya fice da shi, ihu uwar ta kurma ta miƙe zata bi bayansu, bandits dake tsaye a wajen ruƙe da bindiga ne suka yi mata barazana tare da dakatar da ita ta hanyar harba bindiga a in da take yunkurin saka kafarta, cikin wani irin gigita da kiɗima tare da matsananciyar tashin hankali uwar yaron nan ta ja burki tare da komawa baya. "Koma gi zauna ko kuma yanzun nan na fasaki da bindigar nan!!" Cewar ɗaya daga cikin bandits dake a wajen, jikinta sai kerma yake yi haka ta koma ta zauna tana hawaye. Lokacin da suka saki wannan harbin bindigar tsabar tsorata yasa Aafia ta tamki matar da aka yiwa yarta fyaɗen nan wato maman Zahrau, nan take ta fara hawaye, bata taɓa jin karar harbin bindiga a gaske ba, sai dai a film, amma yau ga shi a gaban idanuwanta aka saki harɓi, abin ya gigitata. Suna cikin wannan hali wani bandit ɗin ya kariso wajen yana jan Rufee a kasa kamar shanuwa, da alama kuma ta suma, yana karisowa wajen ya wullota cikinsu ya juya ya bar wajen. Sosai A'afia ta tsanan ta kukan da take yi mara sauti, abin ya ɗaga mata hankali fiye da tunanin mai tunani, wannan bala'i ma kawai ya isa ya sanya ƙwaƙwalwar mutun birkicewa, ɗaya daga cikin matar dake a wajen ne ta ce da matar da akayiwa yarta fyaɗen "Maman Zahrau ki sanya yarinyar nan ta yi kuka kasa-kasa ko kuma ta yi shiru, idan ba haka ba, ita ma tana gab da rasa tata rayuwar" Jin haka yasa A'afia ta yi saurin toshe hakinta da hannunta, jikinta sai kermar tsoro yake yi, abin gwanin ban tausayi. Suna cikin wannan yanayi bandits guda uku suka kariso wajen hannunsu ruƙe da manya manyan tray masu ɗauke da shinkafa da miyar, layi-layi suka fara bi suna raba wa su Aafia abinci, ko da suka zo kan ta ƙin karɓa ta yi, wai ba zata iya ci ba, Mama Zahrau ce ta ɗan taɓa ta alamar ta karɓa, domin idan bata karɓa ba za su ce gidan su akwai kuɗi sosai dan haka idan dama millon ɗaya suka saka kuɗin fansa sai su kara dan kin ki cin abincinsu hakan ya nuna daga gidan daɗi kika fito kenan. Jin maman Zahrau ta taɓa ta ne yasa ta karɓi abinci, wucewa suka yi suka ci-gaba da raba wa sauran abincin. Sai bayan sun gama rabawa sun ta fi ne Aafia ta ce ita kam ba zata ci ba, to kawai maman Zahrau ta bita da shi, sannan ta ɗaura mata da cewa "Kinga idan baki ci wannan abincin ba, wlh in baki yi Sa'a ba sai gobe yi war haka zaki sake ganin abinci, sau ɗaya suke bada abinci, sai wata Sa'a idan sun sami kuɗi sosai kamar idan an fanshi wasu nan ne za ki ga sun bamu abinci sau biyu a rana, kuma kada ki yi zaton iya mu da muke nan ne kawai suka kama, a'a akwai maza suna ta baya, akwai wasu matan ma ta baya, irin wajen nan uku suke da shi, kin ga suna da mutane da dama da suka kama, ba za su iya ciyar da mu sau uku a rana ba, wani lokaci ma ba mu samun ko sau ɗayar sai dai su bamu ruwa, shima ruwan kada ki yi zaton akwai shi available ne, A'a sau biyu suke bada shi arana shima, so dan haka is better for you da ki ci abincin nan". Kallon abincin A'afia ta yi gaba ɗaya abincin dake cikin robar bai wuce ayi loma ɗaya da shi ba ya kare, amma a hakan idan suka ci kuma sai gobe, wannan wace iriyar bala'i ce, ya Allah ka kawo mana sauƙin wannan musifa da muke acikin. Ita kuwa uwar yaron da aka kwace ɗan, ta kasa ko da motsin kirki, burinta kawai taga ina yaronta yake, tana ɗaya daga cikin bakin da aka kawo yau da safe, so bata san asalin halinsu ba, sai yar dube dube take yi ko zata hango yaron nata, amma ina shiru ba shi ba alamar shi, ko kukansa da ma yake yi ta daina jiyowa. Su kuma sauran matan dake a wajen, tuni sun fara cin abinci, hannu baka hannu kwarya, ba za su Barka ka wanke hannu bama, kawai ci ake yi. Aafia tana son tashi ta isa ga Rufee dan ta dubata taga kamar bata motsi ne, amma ina tana tsoro, dan idan ka yi wata wargi tsab za su iya kashe ka. Suna tsaka da cin abincin bandit ɗin da ya ɗauki yaron matar nan ya dawo wajen hannunsa na ruƙe da zanin matar jini na zuba da ga jikin zanin, ga abu kuma a ciki sun kunso shi. Kai tsaye matar ya nufa, yana zuwa ya gefa mata yaron ya juya ya bar wajen, jikinta har kerma yake yi, da kyar ta iya buɗe zanin, wa iya zubillah yaron ne suka dafa shi, da alama cikin tafasasshen ruwa zafi suka sanya shi, gaba ɗaya fatar jikinsa ta ɗaye, sai tiririn hayaki ke fitowa daga jikin wannan yaron, gaba ɗaya jikinsa ya kwaile fatar ta cire ya yi wani jawur da shi, daga bakinsa da hancinsa jinine ke zuba daga wajen, da alama a cikin tafasasshen ruwan zafi suka sanya shi, dan ga shi, duk wadda ya ga yaro nan idan bai suma ba, wlh sai ya matse mashi kwalla, sai dai idan zuciyar da babu wani imani ko ɗigo a cikinta, innalillahi wa inna ilaihir rajiun uwar yaron nan a wajen ta yanke jiki ta faɗin, ba ita ka ɗai ba cikin wayan da suka suma harda A'afia da kuma bakin da aka kawo yau da safe a cikinsu akwai Hanan kanwar Sadiq Katsina. Duk bakin da aka kawo yau da safe sai da suka suma ganin wannan tashin hankali, wayan da suka daɗe a wajen kuma masu kuka sun sha kuka, wayan da kuma zuciyarsu ta bushe ko alamar hawaye babu a idanunsu, sai dai ja da idanun nasu ya yi kamar wuta, alamar abin ya taɓa su suma, cikin wayan da ba su yi kuka ba har da maman Zahrau ita ma baiwar Allah zuciyarta ta bushe bata jin komai. Wannan wace irinyar bala'i?, Wannan masifa dame ta yi kama? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun ya Allah ka kawo mana mafita, dayawa daga cikinmu sun saki Allah sun riki duniya gam, ya Allah ka jiƙan bayin ka ya Allah, innalillahi wa inna ilaihir rajiun astafirullah waatubu ilai. Daya wa daga cikin mutanen dake a wajen, mu samman wayan da aka kawo yau, ba wanda ya iya cin abincin dukkansu kowa ya kasa ci da suka farfaɗo kenan, sai dai wayan da suka daɗe a wajen, suma ɗaiɗaiku ne suka iya cin abincin irin su maman Zahrau. Ya Allah ka kawo mana ɗauki, yanzu a naku tunanin ire-iren maman Zahrau da suka sanya zuciyarta ta bushe babu imani babu tausayi me kuke tunani zata iya aikatawa idan aka bata makami? Allah ma ya tsare da yake ba azzaluman bawa bane sai dai bawa zalunci kansa, sai zuciyar tata ta saura da son Allah da Manzonsa, bayan su ba wani abin dake a cikin zuciyar maman Zahra, ya ilahi ya lillillahi😭 Kasan cewar ogan su mai kiran waya baya nan hakan yasa suka wuni a wajen ba wadda aka kira iyayensa, domin duk cikin bandits ɗin mutun biyar kawai ke da damar kiran waya, saura kuma aikinsu kamo jama'a ne kawai, da kuma kula da su, bayan haka ba wani abin. Jugum-jugum suka zauna ba sallar azahar bare la'asar har karfe shida na yamma sannan suka sanya su a gaba zuwa cikin ɗakunansu, dayawa daga cikin bandits ɗin basa nan, da alama wani abin suka tafi aikatawa acikin gari, domin kusan rabi da kwatansu basu nan a wajen, yan kalilan suka rage, wadda ba su fi yawan mutanen dake a wajen ba. Haka aka mai da su cikin ɗaki suka cigaba da zama jugum-jugum ita kuma Rufee da alama fa kamar babu rai ajikinta, domin ƙo motsi bata yi, kuma haka suke janta a kasa kamar shanuwa, a wannan dawo da su da suka yi, sun haɗa Aafia da kuma Hanan kanwar Sadiq waje guda, domin dama haka suke yi, idan sun tashi mai da ku, mafiyawancin lukuta suna canza maku ɗaki domin kada kudaɗe a waje guda har ku shirya masu wani abin, shayasa basu barin jama'a su sarara, tsabar rashin yarda da kai. (To mun ji ɓangaren Aafia bari mu leƙa ɓangaren su Jelly dan jin yadda zata kaya mana.) Sai murna take yi za su fita yawo da yaya Nawid, abin ba'a magana har wani kin magana take yi ma mutane, sai kauɗi take yi da rawan kai, ita adole za su fita yawo. Bayan sun yi sallar isha ne suka zauna cin abinci, da sallama Nawid ya shigo palon, zaune ya isko su saman table Ummi na kokarin zuba masu abinci su ci, yau Abbo ba a part nasu yake ba, yana part ɗin maman Afnan hakan yasa Ummi gaba ɗaya bata son fitar da Nawid zai yi da baby, dan kada ya barta cikin kaɗaici. "Baby ki tashi mu tafi mana, ba sai kinci abinci ba, za mu ci a can, Prof ya sa an shirya mana abinci". Ba tare da ta kalli in da yake ba, ta ce "Yaya Nawid kaza fa Ummi ta soya mani, ni gaskiya babu in da zanje sai na ci wannan kazar". Bin Ummi da ido ya yi, sai yanzu ya gane me matsalar da gangan Ummi ta kawo mata kaza dan bata son su fita saboda Abbo yana part ɗin su Afnan, sanin haka yasa ya samu waje saman chair ɗin tabla ɗin ya zauna yana faɗin shima a zuba mashi abincin kawai ya ci. Cikin sauri Ummi ta ce "Fitar fa ya zaku yi?" Rai a ɗan ɓace ya ce "Haba Ummi kinsan dai idan Baby ta samu kaza ba'a magana, bata kula kowa, bata kasancewa a duniyar mutane, dan haka a barshi kawai sai wata saan". Cikin mayen kaza da kuma santi ba tare da ta kalli in da yake ba ta ce "Yaya Nawid ka faɗi gaskiya, aradu kaza tafi duniya daɗi, wai yaya Nawid ka cire wannan abin da aka rufe maka a kasar gadonka kuwa? Sannan na gaya maka wannan Abbon kwarto ne amma kaki yarda, to yanzu kuma ya zama ɗan iska domin yana kallona sosai". Girgiza kai kawai Ummi ta yi babu wanda ya ɗauki zancenta da gaskiya domin suna yi mata kallon mahaukaciya, bare kuma idan ta samu kaza ai shikenan kuma, sai ta kara haukacewa da gasken-gaske. Ba wanda ya kulata suka zauna suka gama cikin abincinsu, ita kuma har lokacin tana fama da kaza, kamar wata mai aljanun kaza a kai. A ɓangaren su Rimsha kuwa, kamar yadda Akil ya basu umarnin kawo hadda da karfe 5 haka suka shirya suka yi wanka, suka yi sallah tare da cin abincin rana da suka girka suka shiryawa kansu, a palon Imran suka zauna suna jiransa. Sai 5:10 ya shigo shi da Umaisha, sai murmushi suke yi wa juna, da alama dunuyar tana yi masu daɗi, daga gani kasan sun mace akan juna. Saman sofa mai zaman mutun 2 ya zauna su kuma suka yi maza suka sauƙa kasa, Akila tana ruƙe da Alkur'ani mai girma, ita kuma Rimsha ta ce zata kawo da kai ba tare da Alkur'ani ba, sai dariya Umaisha take yi wa Akila da alama wani munafurcin suka haɗa, kasa ya ce ita ma Umaisha ta sauƙa, ba musu ta sauƙo kasa, kafin ya fara karɓar haddan nasu ne ya tambayi Akila ina A'afia bata dawo bane, E ta bashi amsa, shiru ya ɗan yi kafin ya ce to su kawo haddansu zai je gida ya same ta. Da haka suka rufe babyn Aafia suka fara bada haddansu, dukkansu sun kawo daidai, kuma ya jinjina masu, kyautar maki mai girma ya basu, sai ya ce su kara tusawa domin ya zauna a ƙwaƙwalwarsu da kyau, sai zuwa gobe da safe zai kara masu wani shafin. Sai murna suke yi suna zuba mashi godiya, a tare suka miƙe za su tafi. "Karatun boko da luttatafai fa?" Ya jefo masu tambaya, cikin sauri suka dawo suka zauna, Akila ce ta ɗauko takardunta suka fara koyan karatu, ita kuma Umaisha ta ɗauko masu littafai irin su Nahhu, muɗalaa, malumat, da dai sauran littatafan musulunci, zama suka yi suna ɗaukan karatu da kyau, har da ƙawa'idi, ahlari a ciki, sai karfe 6 kamar yadda ya faɗa suka tashi, cikin hanzari suka faɗa kitchen dan su shiryawa bakon yaya Imran girki kamar yadda ya faɗa. A tare suka fara aikin, wannan ta kama wannan, wannan ta kama wancan, sai hira suke yi Akila tana bawa Umaisha labarin saurayin Rimsha, wato yaya Ahmad, ɗan anachen Rimsha in ji ita Akilar, shine sunan da ta bashi, sai dariya suke yi, ita kuwa Rimsha ta tsare gida kam, babu alamar dariya ko wasa a tattare da ita, ta yi shiru sai ki rantse da Allah bata a wajen. Fried rice suka yi ya ji kayan kamshi, su green beans da sauransu, Rimsha ce mai basu command, ita ma wani abin sai ta buɗe takardun girkin sannan take dubawa. (Manya suna aiki fa.) "Aunty Akila ke ki haɗa mana ganye, ke kuma Aunty Umaisha ki zuba abincin a kuloli ni kuma bari na haɗa pepper chicken" to suka amsa da shi sannan suka fara aikin da ta basu, abin duk wanda ya gansu sai sun ba shi sha'awa, sosai sun haɗa kansu kaman yan uwan juna, da yake Akila da Umaisha duk basu da matsala sai suka ja Rimsha sosai ajikinsu. Bayan sun gama tsab, suka fito palo ana kiraye-Kirayen sallar mangariba, bedroom na Rimsha suka wuce, Akila ta ce a nan za ta yi wanka, ita kuma Umaisha ba dan ta so ba ta wuce Part nasu, Akil da Imran kuma sun tafi masallaci. Rimsha ce ta fara yin wanka tare da ɗauro alwala, bayan ta fito Akila ta shiga. Zama Rimsha ta yi a gaban mirror ta shafe jikinta da mayukanta masu daɗin kamshi tsab, sannan ta feshe perfume nata masu daɗin kamshi, kafin Akila ta fito har ta gama shafa mayukan da duk wani abin da zata yi a gaban mirror, saura saka kaya, lokacin ita kuma Akila ta fito ɗaure da towel a kirjinta, itakuwa Rimsha lokacin da ta fito, bayan towel da ta ɗaura sai da ta sanya ɗan karamin mayafinta da ta shiga da shi, wato gyalen abayar ta, dan bata son Akila ta ga zanen dake a kan kirjinta, shiyasa ta sanya mayafin a kanta ta rufe har kirjinta. Riga da wandon da Akila ta ce su yi anko shi, shi ta ɗauko ta sanya, kayan sun karɓeta sosai da sosai, da rigar da wandon dukka masu kama jikine, sannan rigar zuwa gwiwarta ya tsaya mata, an zuba mashi kwalliya a gaba sosai, kai da gani kasan yana da tsada sosai dan ya haɗu over, launin pink color ne da milk, haka ta sanya su, amma kafin ta saka sai da ta sanya vest a ciki, domin wuyar rigar tana da ɗan girma, idan har bata sanya vest ba wannan zane na sunan Lion zai iya bayyana kowa ya gani, dama kuma saboda zanen yasa da suka je shopping ta ɗauki dozen na irin vest ɗin nan masu kama jiki sosai kamar roba, dan bata son kowa ya gani ma bare kuma ya tambayeta me yasa zata rubuta sunansa. Bayan ta gama shiri sai da ta sake fesa turare sannan ta zura hijabi har kasa ta zauna a bakin gado tana jiran Akila, domin ta tafi sanya nata kayan ita ma. Jiran minti goma ta yi sai ga Akilar ta dawo shirye cikin nata kayar irin ɗaya suka yi anko, akalla Akila zata bawa Rimsha good 4 years da yan ɗori, amma da yake Rimsha tana da tsawo sai kansu ya yi kusan ɗaya, da kaɗan Akila ta ɗara ta, dan suma ƴaƴan Abba ba baya ba wajen tsawo. Yanzu Rimsha an fara zama ƴan mata tula-tula sun fara girma. A tare suka yi Sallah, bayan sun idar suka wuce palo dan su ɗan yi kallo. Suna zama saman sofa Rimsha ta ɗauki remote ta shiga News, Rimsha yarinya mai Sa'a duk time da ta shiga News zancen mutumin nata ake yi, yau ma ta yi Sa'a maganarsa ake yi, ga kuma hotonsa nan an kafe kamar kullum yana sanye da face mask. Kamar ance ta kalli fuskarsa, ai kuwa idanunta suka sauƙa akan nasa, ba abin da ya faɗo mata a ƙwaƙwalwarta irin yadda taga idanuwansa a zahiri cikin mafarkinta, yadda ta gansu muraran, tuna hakan yasa ta runtse idanuwanta, tana tunanin yadda yake a zahiri, wannan idan ka ganshi zaka iya mutuwa. Ji tayi ba zata iya ganin fuskarsa ba, koda kuwa a hoton ne, mugun razana ta yake yi, hakan yasa ta yi maza ta canja tasha. "A'a Rimsha me yasa zaki kashe mani jarumina ina tsaka da kallo?". Cewar Akila. Ba tare da tayi magana ba ta miƙe da sauri ta koma cikin ɗaki, daidai lokacin aka kira sallar isha. Saman dadduma ta hau tana hawaye tana Sallah, ta rasa meke damunta, tana bala'in son wannan mutumi, amma kuma duk lokacin da ta kalli even pic nasa da glass ba iya face mask ba, sai ta yi mugun razana, sai ta fi awa uku tana takure waje guda tana razana, kamar wadda taga wani dodon ko wani abin, idan kuwa tana kwayar idonsa a hoton, ma'ana babu glass wunin ranar zata yi shine ba cikin walwala ba, ta rasa menene dalili, tana sallah tana kuka, ko da ta kai sujjada, ya jima sosai tana kuka tana rokan Allah da ya rabata da son wannan mutumi a zuciyarta, ta kuma yi danasanin rubuta sunansa a kirjinta. A wannan hali Akila ta iskota, bata kawo komai a ranta ba, ganin tana sallama yasa ta yi tunanin kenan dama ƙiran Sallah da akayi ne yasa ta baro palo da gudu ta dawo ɗaki, da farko ta zaci ko wata matsalace, amma ganin tana sallah yasa ita ta tsaya kusa da ita tare da tada kabbara ta fara Sallah. Rimsha bata bari Akila taga hawayen fuskanta ba, tana idar da sallah ta miƙe ta shiga toilet, lokacin kuma ita Akila tana raka'a na uku ne, tana shiga toilet ta wanke fuskarta sosai, sannan ta fito ta zauna gaban mirror ta ɗan gyara fuskar tata, ta miƙe ta nufi palo. Bayan Akila ta idar da sallah ta yi addu'a sannan ta bi bayanta, daidai lokacin su Imran suka dawo masallaci, shi da Akil. A palon suka baje suna hira da dariya, fito da wayarsa Akil ya yi ya kira Umaisha dan ta zo su yi hira a tare, aikuwa ba ɓata lokaci sai ga ta nan ta shigo, haka suka cigaba da hira cikin annashuwa, shi kuma Ahmad sai kiran layin Rimsha yake yi amma wayar na ɗaki ta sanya ta a silent. Sai wuraren karfe 9 da Imran ya samu sakon Nawid akan ba zai samu damar zuwa ba, saboda Jelly ta samu kaza, dariya Imran ya yi sosai ya ce "Ashe kuna da maganinta a gida ma ka tsaya kana wahalar da kanka, ai nan gaba idan ta dameka da ku fita yawo kaza kawai zaka saka Ummi ta soya mata sai ka haɗa ta da shi ka huta". Shima Nawid ɗin dariya ya yi, Imran duk ɗaukansa kanwar Nawid ɗin da ya ce an kawo ta da ga family Abbo ya zaci yarinya ce da bata wuci 8 to 10 years haka ba, shiyasa ma yake yiwa Nawid tsiya irin haka. Haka suka yi ta hiransu na abokai daga bisani suka yi sallama da juna, Imran ya cewa su Rimsha su kawo masu abinci su ci, saboda Nawid ya ce ba zai samu zuwa ba, cike da murna suka kawo abincin Akil sai mamaki yake yi, yar yarinya kamar Rimshan nan ne ta iya girki, da farko ya ce ba zai ci ba, domin yana ganin kamar jagwalgwalo kawai suka yi, amma daga baya da Imran ya matsa mashi, sai ya ce a sanya mashi kaɗan, ai kuwa yana fara ci ya ce a kara mashi, sai dariya Akila ta ke yi mashi, ta ce "Wai yaya Akil ka manta ka ce duk mace da bata haura shekara talatin ba, ba zaka ci girkinta ba, domin ko masu shekara ashirin da biyar yara ne kamar mu, ba'a gama ya ye mu ba?". Harara ya wurga mata ita kuma Umaisha cewa ta yi "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun dama yaya Akil abin da ka faɗa kenan? Lallai ma, to wlh yanzu zan ko yi girki idan ba zaka ci nawa ba, ni ma ba zan ci na restaurant ba". A kule ya ce "Idan kuma na bada umarnin ki ci dole fa?" Still dai fuskarta ɗauke da murmushi ta ce "E sai na ci mana tun da kai kace, to bama dole na ba" Wani nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, Akil akwai bala'in son girma, wato tun da idan ya bada umarni zata ci shikenan ai ya huce, shi dai Imran, shi da Rimsha ban da murmushi ba wani abin da suke bin su da shi. Bayan sun gama cin abincin sun yi komai, sun tattare wajen ne, suka yi wa yaya Imran sallama, Rimsha ta wuce ɗakin ta, Akila da Akil da Umaisha suka wuce cikin gida, shi kuma Imran ya ɗan jima a palon kafin nan ya tashi ya shiga bedroom nasa, ya yi wanka ya shirya cikin kayan barci, sannan ya kwanta. Itama Rimsha wanka ta yi tare da shiryawa cikin tsadaddun kaya barcinta masu kyau launin pink color riga da wando, dan tana son pink color, sky blue, da kuma fari, sune best color ɗin ta. Bayan ta gama ne ta sake feshe ɗakinta sa air freshener sannan ta haye gado ta ja bargo tare da jawo wayarta ta fara kiran layin Ayla, amma a kashe sosai ta fara shiga damuwa akan me ya samu Ayla. Haka tana ganin kiran Ahmad amma bata ɗauka ba, saboda bata cikin yanayi mai daɗi, tana tunanin Ayla sosai. A wannan daren dai da kyar barci ya yi awon gaba da ita. Asuba ta gari. Idan muka koma Washington DC kuma. Kamar dai yadda suka tsara haka suka yi, sai da suka yi sallah la'asar sannan suka dawo gida, haka da mangariba tun karfe 6 suka fita gida, sai karfe 8 bayan sun yi sallar isha suka dawo gida, a palon Part ɗin Michael suka zauna dan yanzu dama ba su wani cika zuwa palon kasa ba, waya Michael ya yi akan bodyguard su kawo mashi kayan tea part nasa, haka kuwa a kayi ba tare da ɓata lokacin ba, sai ga bodyguard guda biyu, kamar kullun suna cikin dressing nasu na bakaken suit tare da bakaken glasa a kan face nasu, wato no respect. Saman dining table dake a cikin palon suka ɗaura kayan tea ɗin tare da wani kyakkyawar flaks mai kyan gaske, kayatatcen tea ne wadda aka haɗa shi da ganyayyaki masu kara lafiya a jiki, shine a jikin flaks ɗin, haka suka ajiye suka juya suka bar palon. Kallon Musharraf Michael ya yi yana faɗin "Uncle ɗin James ka je ka haɗa tea ɗin ni bari na je na yi wanka na duba Lion yau tun safe da muka rabu a gym ba mu sake haɗuwa ba" To Musharraf ya bishi da shi, sannan suka miƙe a tare, Michael ya wuce toilet shi kuma Musharraf ya wuce saman table ɗin dan ya haɗa tea ɗin sa. A ɓangaren Lion kuwa, lokacin da ya gama zaman shi a lambun sai ya miƙe ba tare da ya sha fruits ɗin ba, maltina kawai ya ɗauka kwara ɗaya da glass cup ɗaya ya fito daga wajen. Ji kake dip-dip-dip wani jibgegen Bature soja fari tas ya nufishi a guje, yana zuwa ya karɓi maltinan da glass cup dake a hannunsa, cikin girmamawa ya ɗaga hannu ya sara mashi tare da buga kafa, ba musu Lion ya miƙa mashi maltina dan dama dan dole ya ɗauko su, yana jin yunwa amma kuma suna da zama a white house karfe 10 yanzu kuma har 11 ta kai bai je ba, hakan yasa ya fasa shan fruits ɗin dama kuma ba wani niyar sha yake da shi ba, kawai dai bai son cin abincin safe ne yasa ya ce zai sha fruits ɗin. Kasa kasa ya yi magana kamar mai raɗa "Ku tashi motoci za mu wuce white house" da sauri sojan ya sanarwa da sauran sojojin dake a kusa, kan kace me sun haye saman bayan motoncin, wannan sojan da ya riƙe mashi maltinan shi ya buɗe mashi motarsa ya shiga cikinta, bayan ya shiga ne sojan ya zuba mashi maltina cup, cikin girmamawa ya miƙa mashi, girgiza kai ya yi alamar baya buƙata, sojan bai ji komai ba, domin idan da sabo sun saba ba zaka taɓa gane me yake so ba. Da gudun gaske suka tashi motoncin suka fice daga gidan, kai tsaye white house suka wuce, kamar dai ko yaushe duk wata abin hawa dake a kan hanyar sauka take ta basu hanya su wuce. Lokacin da suka isa white house, gidan a cike yake tab da jami'an doka sojoji manya-manyan yan siyasa da duk wasu masu faɗa a ji a kasar, gaba ɗaya ko ina ka waiga sojoji da yan sanda ne cike makil a gidan, tun da jerin gwanon motocinsa suka shigo gidan, gaba ɗaya sojojin dake a cikin gidan suka fara kamewa suna sara mashi, wani sojan kam ma, saboda kamewa sai ka rantse da Allah baya numfashin. Lion duniya Kamar dai kullum kun san mai hali baya fasa halinsa, to haka ne, Lion dai bai kula kowa ba, ko kallon in da suke ma bai yi ba, ya sanya face mask a fuskarsa ya fito, kai tsaye fadar shigaban kasa ya wuce, sojojin sa kuma suka dakata daga bakin kofa. Yana shiga cikin fadar ya wuce Roosevelt Room, nan ya isko kowa ya haɗu ana jiransa, da gani ran kowa dake cikin wajen a ɓace yake, domin Lion ya ajiye su suna ta jira, ga Tga nan tun ɗazun ya iso wajen, amma shi sai yanzu, kuma haka za su hakura ba yadda suka iya da ahi. Daga gefe kuma ga yan jaridun white house, wato yan jaridu masu fitar da abin da ke faruwa daga fadar shugaban kasar, manya-manyan mutane suna zazzaune saman tsadaddun kujerun dake a cikin ɗakin, wayan nan kujeru sun haɗu matika gaya, kuɗin wayan nan kujeru ba zai faɗu ba saboda tsadarsu, ta ko'ina Kamshi ke tashi a cikin fadar, amma Lion na shigowa kamshin perfume na jikinsa ya rinjayi gaba ɗaya kamshin da yake a wajen, sai room ɗin ya gauraye da irin kamshin perfume nasa, wani daddaɗar sanyin Ac ne ke a cikin ɗakin, wadda sanyin yana gudu daidai misali ba na wuce ka ida ba, ko wannan su akwai kayan sha masu bala'in sanyi a gabansu ga kuma kyawawan glasses cups a gabansu kusa da abin shan. Shigowar Lion yasa gaba ɗayan su suka ɗago suka kalle shi, dayawa daga cikinsu kallo ɗaya suka yi mashi suka kawar da kansu suna ɗan satar kallonsa. Bai bi ta kan kowa ba, saman kyakkyawar kuma tsadaden kujerar kusa da His Excellency ya je ya zauna, shiru suka ɗan yi kafin His Excellency ya buɗe masu taro da fara magana. Kasa Lion ya yi da kansa dan bai ma san akan me zasu yi maganar ba, lokacin da aka kawo mashi takardan bai duba ba, yana wani aikin, sai dai Tga ya sanar mashi cewa karfe 10 za'a yi zaman, iya abin da ya sani kenan, kuma dama bai nemi sanin akan me za su yi taron ba, domin ba ɗaukar maganar su yake yi ba, abin da ya zo mashi a cikin ƙwaƙwalwarsa kawai yake aikatawa. Kowa ya fara magana yana faɗan arbarkacin bakinsa akan kuɗin da za'a fitar dan kera manya-manyan makamai wadda karfinsu zai iya tashin state guda, ko uppan bai ce da su ba, kowa sai magana yake yi, shi hasalima ciwon kai suke sanya mashi wannan surutu da suke yi, ji yake yi tamkar ya bar wajen amma bai yi hakan ba, saboda akwai abin da yake son fahimtar a tattare da su. An samu bambance bambancen ra'ayoyi dan gane da fitar da wannan kuɗin, wasu sun ce yes a fitar wa su kuma sun ce a'a kada za'a fitar yana da kyau a karawa yan kasa abun yi ne, ma'ana marasa aikin yi domin a ragewa kasa talauci, tun da suna da makamai sosai kawai a buɗe masana'antu companys da dama a ɗebi ma'aikata talakawa da ba su da abin yi domin kasar su ta sake tsabtatuwa daga cutar talauci, shi dai Tga ya tsaya akan gara a sayo kayan haɗa makamai domin sun fi mashi talakawan nan mahimmanci, shi kuma His Excellency hankalinsa ya fi rajaa akan gara a buɗe masana'antu saboda ba shi da burin da ya wuce kasarsa ta cigaba da zama super pawer ta duniya, ya fi son ya ga ya fi kowacce kasa komai. Ganin sun dame shi da surutune yasa ya miƙe ba tare da ya ce komai ba ya nufi waje, bai kai ga fita ba His Excellency ya ce ina zai je ba su gama zama ba, shiru ya yi bai yi magana ba har sai da ya kai kofar fita sannan kasa kasa ya ce "Uncle please idan kasan irin wannan zama za ku yi kada ka sake kirana". Cikin sauri His Excellency ya ce "To yanzu dai gaya mani naka shawarar mu ji". A takaice ya ce a gina masana'antu, sannan ya wuce ya nufi waje abinsa, gaba ɗaya wajen tsit suka yi, domin sun san koda sun yi magana ma abanza ne tun da Lion ya ce masana'antu za'a gina tofa abin da za'a yi kenan, a ɓangaren His Excellency kuwa tuni ya yanke hukuncin abin da Lion ya faɗa shi za'a yi har ya fara shirye-shiryen rubutawa majalisa takarda dan a samu a saki kuɗaɗen da wuri a fara gabatar da aiki domin kawar wa da kasa talauci. *Allah sarki manyan kasashen kenan kullun burinsu ta ya za'ayi kasar su ta ci gaba, burinsu a kullun kasarsu ta kasance ta farko a duniya wadda zata mulki ko wace kasa kuma ta juya su yadda take so, kuma sun san cewa kasarsu ba zata taɓa ci gaba ba, har sai sun raba yan kasa da talauci da mutuwar zuciya, da hanya ɗaya kawai zasu iya yin hakan, shine su rinƙa gina masana'antu suna bawa yan kasa talakawa aiki ana sarrafa abubuwa daga masana'antun ana fitarwa kasashen duniya ana sayarwa, su ci riba kuma sun raba matasansu da zaman banza zaman kashe zuciya, ya Allah ka sanya shuwagabannin muma su farka irin haka, Allah kasa su zama irin haka, ba wai bukatarmu a ɗauki kuɗi a bamu ba, a'a a gina mana abun da zamu rinƙa zuwa muna aiki a ciki muna samun halak ɗin mu ko ya yake, ya dai kasance kullun zamu je mu yi aikin mu samu, amma idan kuɗi za'a bamu kwana biyu kuɗin sun ƙare an koma gidan jiya😭 wani kuɗin ma idan aka baka abin ko karamar buƙatarka ba zai biya maka ba, please aikin yi muke so ba kuɗin da bai taka kara ya karya ba🥺😭🙏* Lion yana fita gida ya koma ya yi wanka ya kwanta yana tunanin yadda tafiyarsa zata kaya, sai karfe 2 ya ci abinci Bawan Allah nan. A ɓangaren su Musharraf kuwa, Michael na toilet yana wanka shi kuma ya fara haɗa tea ɗin sa don ya sha, domin bashi da wani abincin da ya wuci tea, bawan Allah, yana tsoron cin abincin gidan tun da ba musulmai bane kada ya je ya ci abin da Allah ya haramta mashi ci, hakan yasa ya kikaye kansa daga tea sai fruits kawai yake laptawa cikinsa. Bayan ya zuba duk wani abin da zai bukata a cikin cup, sai ya ɗauki flaks ɗin ruwan tea ɗin, ya buɗe ya fara zubawa a cikin cup ɗin, sai zuba ruwan yake yi, amma cup ɗin taki cika, na cikin flaks ɗin kuma yaki karewa, idan ya cire flaks ɗin daga bakin cup ɗin zai ajiye sai yaga cikin cup ɗin babu komai, alamar ruwan tea ɗin bai zuba a ciki ba kenan, idan kuma ya sake mai da flaks ɗin yana zuba ruwan, tofa sai dai ya yi ta zubawa amma ba zai ga komai a cikin cup ɗin ba, abin ya ɗaure mashi kai, ya kuma tsorata shi sosai, yana tsaka da zubawa sai yaga ruwan tea ɗin ya canza kala daga brown zuwa jawur kamar jini, har wani yaukin jini yake yi, ihu ya kurma tare da sakin flaks ɗin ya yi baya zai faɗi, cikin sauri Michael da ya fito yanzu ɗaure da towel a kugunsa, ya yi maza ya riƙosa yana faɗin "Uncle ɗin james lafiya kuwa?". Kasa magana Musharraf ya yi sai sunan Allah da yake iya kira a cikin zuciyarsa, amma ya kasa iya furtawa a bakinsa, ganin hakan yasa Michael ya zaunar da shi a saman ɗaya daga cikin chair ɗin table ɗin yana faɗin "Uncle ni bansan meke damunka this two days ba, sai ka rinƙa yi mana ihu yanzu kasa ni fitowa ba shiri" ya kai karshen maganar tare da komawa cikin bedroom nasa domin shiryawa, Allah sarki Musharraf shi ya ga abin da ya gani, a hankali ya ɗaga idanuwansa ya sauke su saman table ɗin, abin mamakin sai yaga komai ya koma yadda yake, duk wasu madara da ya zuba a cikin cup ɗin duk sun koma cikin robarsu, sai lokacin kuma ya samu damar kiran sunan Allah, yana kira kuma ya samu kwarin gwiwa ya tashi ya haɗa tea dinsa ya ɗauka ya nufi cikin bedroom ɗin, yana shiga ya samu Michael naɗe saman bed ya shige cikin bargo. Da mamaki ya ce "Asif ya na ganka kana kwance? Ba wajen Lion zaka je ba ne?". Can kasa-kasa ya ce "Uncle dan Allah ka kyakeni sai da safe zan je wajen Lion ɗin, now I'm feeling sleeping over" Ya kai karshen maganar tare da janyo barkon ya rufe har kansa, abin ya kara ɗaurewa Musharraf kai, yanzu fa Michael ya fito lafiya Lou baya jin barci, amma daga shigowarsa ɗaki ba'a fi two mins ba wai barci yake ji, anya babu lauje a cikin naɗi kuwa,? Ya yi wa kansa tambayar da bashi da amsarta, ganin ba shi da amsa kuma ya sa ya ce "Asif abinci fa?" Shiru Michael bai amsa ba, da alama ya yi barci ne. Jin haka yasa ya miƙe ya koma saman sofa ya zauna. Tas ya shanye tea ɗin sa, ya mai da cup ɗin palo, ya dawo shima ya yi wanka tare da shirin barci ya kwanta a bedroom nasa. Asuba ta gari. Shima dai Lion kamar kullum wanka ya yi ya kwanta ransa fes sai tunainin James nasa yake yi, shima time to time ne dan yanzu tun da ya gano A.E.A bai sa wata damuwa sosai akan ɓatar James ɗin, jima yake yi tamkar ya dawo da James ɗin. Barci mai daɗi suka yi yau, mai cike da annashuwa, ga shi wuraren karfe 1 dare an tapka ruwan sama sosai, sai barcin ta kara armashi. A NIGERIA KUWA. Kamar kullum Rimsha na tashi karfe 6 na safe, ta zo ta gyare ko'ina tsab, daga bedroom nata har palo, sanna ta ɗaura masu abinci, yau Akila tana da glass karfe 10 tun karfe 7 ta zo suka fara aikin girki a tare, shima Akil ya bar Umaisha a kan ta zo ta rinƙa koyan girkin, dan ya ji daɗin abincin jiya sosai. Kamar jiya yauma a tare suka yi girkin, bayan sun kammala, kamar yadda suka saba suka jere a Palo, ko wacce ta wuce ɗakinta dan ta je ta yi wanka. Bayan sun yi wanka sun shirya ne suka sake dawowa suka haɗu a Palo, Imran ne ya kira Akil a waya ya zo suka haɗu suka yi breakfast a tare, Akila ta tambayi Imran ko dai su rinƙa sakawa Ammi da Abba abinci ne, e ya amsa masu da shi tare da zuba masu ruwan albarka, sai murna suke yi suna amsawa da Amin. Bayan sun kammala Rimsha ta ce Akil ya kara mata karatu shafi biyu, to ya ce mata sannan ta kara karanto mashi na jiya, sosai ya ji daɗi yadda take son karatu kuma take mai da hankalinta sosai a kan hakan. Shafi biyu ya kara mata sannan ya miƙe ya fice daga palon yana sa mata albarka, har cikin zuciyarta Umaisha ta ji wani irin bakin ciki, ta ji ba daɗi ganin yadda Akil yake yawan sakawa Rimsha Albarka, abin ya sosa mata zuciya, Akila ta lura da hakan sai addu'a take yi a zuciyarta Allah yasa kada hakan ya jawo masu matsala a tsakanin su. "Rimsha yau ku kunna kaba ɗaya fridge ɗin gidan nan, anjima za'a shigo da wasu kayan drinks ku shirya komai yadda ya kamata, ku gyara koina, saboda ina da babban bako, Saif zai zo yau". Cewar Imran, to suka amsa mashi da shi sannan ya miƙe yana sanya masu Albarka ya fice daga palon zuwa bedroom nasa, dan ya je ya yi wanka ya shirya zuwa gidan su Irfan. Su kuma ɗakin Rimsha suka wuce, ita kuma Umaisha ta ki binsu domin ta fara jin tsanar Rimsha a cikin zuciyarta, saboda Akil yana kula ta yana saka mata albarka. (Toh fah kishi kumallon mata Umaisha manya) Hira sosai yau Akila da Rimsha suka sha, sai karfe 10 Akila ta wuce school ita kuma Rimsha ta fito palo dan yin aikin da Imran ya ce su yi, wato gyaran gida da kunna su fridges da sauransu. 💖💖A WASHINGTON DC KUWA💖💖 Misalin karfe 8 na safe yana tsaye a gaban mirror ɗakisa, yana duba wasu takardun da suke a wajen, ya yi shirinsa tsab na tafiya, sai tashin kamshi yake yi, ya saki wannan dark black curly hair nan nasa bai ɗaure ba, wannan guntu na gaban yana nan shima, sanye yake da wando jeans mai bala'in kyau Black colar sai high neck t-shirt fari tas, ya yi wa kayan kyau sosai da sosai, kamar kullum fuskarsa sanye da face mask black color kyawawan fararen kafafunsa na sanye da black sos cikin white Boot mai bala'in kyau da tsada, a takaice dai yau wankan Black and white ya yi, tsabar kyau kamar shi ya yi kansa. Baki ɗauke da excuse Micheal ya shigo cikin ɗakin, ta cikin mirror gabansa ya kare mashi kallo, shima dai Michael ɗin kallonsa yake yi, ganin haka yasa Lion ya juyo suna kallon juna da kyau, ya zubawa Michael wayan nan rikitattun idanun nasa masu rikitar da ƙwaƙwalwar wadda ya kalla, ya rasa natsuwarsa, sosai yake kare mashi kallo kamar mai tuhumar shi, cikin sauri Michael ya kariso Wajen ya rungume shi yana sauƙe nauyayyar ajiyar, hannu bibbiyu Lion yasa ya riƙe shi da kyau yana mai jin matukar kaunar Triplets nasa a cikin ransa. Wani nishaɗi na musamman suke ji dukkansu biyu. Allah sarki jini ba wasa ba, dole ku ji daɗi. Sun ɗan jima a haka ba wanda ya ce da ɗan uwansa kala, daga bisani suka raba jikinsu, Michael ya koma bakin gado ya zauna yana faɗin "My Lion please i need money" a cikin natsuwa Lion ya tako zuwa wajen bedside drawer ya sanya hannunsa ya buɗe drawer ya ɗauki sarkar nan da ya ajiye mashi ya miƙa mashi, karɓa Michael ɗin ya yi tare da sanya a wuyarsa ba tare da ya tambaya daga ina ta fito ba. Sake turo ɗan bakin nan nasa ya yi murya a shagwaɓe ya ce "Lion please money" Shiru kamar kurma haka Lion ya yi mashi, daga karshe ya ɗauki wayarsa da laptop ya nufi waje, cikin sauri Michael ya miƙe zai bi bayansa, bai kai ga fita ba ya ji alert wadda ko bai duba ba yasan kuɗin da ya buƙata ne Lion ya tura mashi, wani daɗi ya ji, cike da murna ya fara ayyana irin business ɗin da zai buɗewa Aryan da kuɗin a cikin zuciyarsa. Shi kuma Lion kai tsaye palon kasa ya nufa, wani irin taku yake yi wadda duk in ya taka kasa sai dark black curlysa nan ya girgiza, ya watse daga bisani kuma ya sake haɗewa, kai ka ce hura gashin iska ake yi, amma ko ɗaya kawai dai yana yin tafiyar da yake yi ne, da alama yana sauri sosai, babu kowa a palon kasan sai wayan nan jibga-jibgan bodyguards ɗin da suke a wajen dining table, su daddy a lokacin duk suna ɗakin su, basu kai ga fitowa yin breakfast ba tukunnan. Kai tsaye wata kofa dake ta kusa da Kitchen ya nufa a maimakon kofar fita palon, yana buɗe kofar ta sada shi da wajen dawakansa, ta nan ya ratsa izuwa wani ɓangare daga ta cikin gidan, tafiya kaɗan ya yi ya shiga ta lambun daddy ya fito ta kofar sirri dake a wajen, yana fita gidan Tga da Tyrone suna tsaye da mota a wajen sun gama shirya mashi gaba ɗaya kayan sawarsa dama tun jiya da daddare a cikin bayan motar, yana fitowa ba ɓata lokaci Tyrone ya buɗe mashi gidan gaba na motar ya shiga suka bar wajen, kai tsaye airport su nufa. Ko da suka je airport ɗin bai fito daga motar ba sai da ya sanya wata dankareriyar long coat mai bala'in kyau da tsada Black colar a jikinsa, coat ɗin ta haɗu sosai, a iya gwuiwa ta tsaya mashi, wani rawani irin nasu na turawa ya ɗauko mai jikin mage ya ɗaura a wuyarsa saboda sanyi da ake yi, cikin wannan natsuwa tasa da class ɗin ya fito, already su Tga sun gama shirya mashi komai, a Airport ɗin ba kowa ne ya iya gane shi ba, kai tsaye cikin jet nasa ya je ya shiga, ba ɓata lokaci suka daga suka lula sararin samani. Sai da su Tga suka ga tashin shi sannan suka shiga mota suka juya zuwa gida, sai tunanin yadda za su kare da Brady Tga ya ke yi, dan karen baya yarda da kowa sai Lion, idan ya ga Lion baya nan ne sai kaga ya ɗan saki jiki da Michael, tunani cike fal ransu suka koma gida. Nikuma na haɗa kayana zuwa Gida NIGERIA kasarmu da gado. Misalin karfe 6:40 Imran ya shigo ɗakin Rimsha bakinsa ɗauke da sallama, zaune ya iskota ita da Akila suna shirin zuwa garden dan su kaiwa Akil haddarsu ya kara masu wani, yau bai dawo gidan da wuri bane shiyasa ba su fara karatu da wuri ba. "Rimaha ki kawo wa Saif ruwa mai sanyi da maltina, ya yi azumi kuma lokacin shan ruwa ya yi, mai sanyi sosai za ki kawo mashi kin ji? Yana ɗaki na" gyaɗa mashi kai ta yi alamar ta ji sannan ta ya fice, miƙe wa Akila ta yi ta nufi waje tana faɗin "Ki same ni a garden idan kin gama, ba zan jira ki ba dan kar yaya Akil ya ji mu gaba ɗayan mu shiru ya zo ya hukunta mu" ta kai karshen maganar tare sa ficewa daga ɗakin. Ita kuma Rimsha bayan ta gama shirinta tsab, sai ta ɗauki zumbulelen hijabinta har kasa ta zura a jikinta sannan ta yo waje. Kai tsaye Kitchen ta nufa, hijabin nata ya rufe koina a jikinta, baka iya ganin komai nata sai hannunta da ta fitar ta cikin hannun hijabin domin ɗaukar plate ɗin ruwa da kuma glass cup, sai drinks kala biyu da ta ɗaura a saman plate ɗin ɗaya maltina ne ɗayar kuma coca colar. Sai sauri take yi ta ɗauki plate ɗin ta fito waje, ta ƙosa ta kai musu ta wuce wajen Akila suna jiranta, karfe 7 daidai Akil ya ce zai karɓi haddar kafin ya wuce masallaci, idan ya dawo sai ya kara masu, yanzu kuma karfe 6:50 bata wani biya haddar sosai ba, tana saurin ta kai masu ta zo ta sake biya haddar da kyau dan kada Akila ta fita kokari. Sai sauri take zubawa ga hijabi zumbulele har kasa kamar matar liman, ta doso kofar ɗakin kenan, ba shiri ta ja wani irin birki, lokacin da kunnuwanta suka jiyo mata wani irin daɗaɗan murya da bata taɓa jin irin shi ba, a nutse wannan murya yake tashi yana bada wani irin sauti mai ratsa dukkan ilahirin ganganjikin ɗan adam mai sauraro, kira'ar Alqur'ani mai girma yake rerawa cikin suratul An'Am, kai daga jin wannan murya kasan mamallakinta karshe ne wajen natsuwa da kamala da kyau, da iya rera karatu, domin yadda yake fito da ayoyin nan ɗaya bayan ɗaya, a nutse ko wannan yake fita ba tare da kaucewa wata wasaliba, kai da ga ji kasan ya kware a kira'ar Alqur'ani mai girma. Ta jima a tsaye a bakin kofar tana sauraran wannan daɗaɗar muryar da bata taɓa jin irin shi ba, tabbas mai wannan murya ba bahaushe bane, domin yadda yake yin karatun tamkar irin limaman larabawan nan ne, babu baki na hausa ko ɗigo a wannan murya. Almost 10mins tana tsaye, bata iya motsawa ba har sai da ta ji ya kai aya, ma'ana ya kai karshen surar. Cikin natsuwa ta fara takawa dan ta shiga cikin ɗakin, zuciyarta ta ƙosa taga wanene mamallakin wannan sexy kuma cool voice ɗin. Bakinta ɗauke da sallama ta shigo, Imran yana zaune saman bed nasa ta baki baki, yana riƙe da wata yar karamar roba kamar na maganin ciwon kunne, sai juya robar yake yi yana yan dube-dube a jikinta, kamar yana leman wani abin. Nan take wani murmushi ya bayyana a fuskarta sakamakon murmushin da ya sakar mata, bata yi magana ba shi ma kuma bai yi magana ba, hannu ya sa ya nuna mata gefe ɗaga cikin ɗakin, wajen da yake Sallah, sai lokacin ya ce "Ga wanda zaki kai wa ruwan, amma akwai sanyi sosai ko? Dan kin ga azumi ya yi kuma kin san su da sabo da sanyi". Fuska ɗauke da kayatatcen murmushi ta juyar da kallonta izuwa kan baƙon. Yana zaune saman dadduma yana Fuskantar kofar shigowa, sai dai kansa a kasa yake, jikinsa na sanye da jallabiya fara tas mai bala'in kyau. Sakin plate ɗin hannun nata ta yi ya faɗi kasa, da karfi-karfi kirjinta ya fara dukan uku uku, numfashinta ya fara fita da sauri-sauri, laɓɓanta sai kerma yake yi, jikinta na ɓari, hakwaranta har wani haɗuwa suke da juna, da kyar ta iya motsa lips ɗin nata ta murya na rawa ta furta "G..A..R..." Bata iya karisa fitar da R ɗin ba ta yanke jiki ta faɗi kasa sumammiya. A zafafe Imran ya miƙe ya yi kanta yana kiran sunan ta. Shi kuwa Saif tamkar bai san da mutane a ɗakin ba, bai yi wani motsi da zai nuna cewa ya san ma da mutane a ɗakin ba, amma fa har cikin zuciyarsa ya ji sunansa da ta kira, kuma idanuwansa suna son gane mashi wace ce wannan da har zata iya gane fuskarsa, bayan kuma shi ba wanda ya san ainahin face nasa a Media, sai dai a gidansu, amma ba zai iya ɗaga ido ya kalli koma waye bane, domin bai kai matsayin GAR ya ganshi ba. Tofa ya kuke ganin wannan lamari, me ya kawo GAR Nigeria? Dama shi musulmi ne? Me ya haɗa shi da Imran? Me yazo yi? Anya shine kuwa? Ko dai mafarki Rimsha take yi? Ni dai na yi na sai mun haɗe idan mai dukka ya kai mu 💖TRIPLET'S💖💖 49-50 A zafafe Imran ya miƙe ya yi kanta yana kiran sunan ta. Shi kuwa Saif tamkar bai san da mutane a ɗakin ba, bai yi wani motsi da zai nuna cewa ya san ma da mutane a ɗakin ba, amma fa har cikin zuciyarsa ya ji sunansa da ta kira, kuma idanuwansa suna son gane mashi wace ce wannan da har zata iya gane fuskarsa, bayan kuma shi ba wanda ya san ainahin face nasa a Media, sai dai a gidansu, amma izza ba zai bari ya iya ɗaga ido ya kalli koma waye bane, domin bai kai matsayin GAR ya kalle shi ba. Da karfin Imran yake kiran sunanta amma ina ko motsawa ba ta yi ba, hankalinsa ba karamin tashin ya yi ba, gaba ɗaya ya birkice, kamar wata baby haka ya ɗauke ta fice da ita zuwa nata ɗakin, saman bed nata ya kwantar da ita, cikin sauri ya dawo bedroom ɗin nasa, yadda ya bar Lion haka ya dawo ya same shi, ko ɗago kai sa bai yi ba, tattare ruwan da drinks da Rimsha ta kawo ya yi, sannan ya mai da saman plate ɗin, shi kuma glass cup ɗin already ya fashe, Imran bai lura da ya fashe ba sai dai kawai ya ga jini na zuba daga ƙafarsa, bawan Allah tsabar kiɗima bai san lokacin da ya taka glass ɗin ba. Guntun tsaki ya ja tare da ɗaukar plate ɗin ya fice waje, bai damu da jinin dake zuba mashi a kafarsa ba, ya koma Kitchen. Sauri-sauri ya sake shiryawa Lion wani ruwan faro mai sanyi da wasu drinks ɗin, abin da ya sanya ya ɗauko mashi wasu kuma ya san halinsa sarai tsab zai iya cewa ba zai sha wayan nan ba, domin yana da tabbacin ya san da faɗuwar su kasa, hakan yasa ya canzo mashi wasu. A gaban shi ya zo ya ajiye mashi sannan ya wuce toilet dan ya wanke jinin dake zuba mashi a kafarsa ya yi dressing na wajen. Bayan ya wanke ya yi komai ya fitone sai ya ga Lion bai ko kalli ruwan da ya kawo mashi ba, bare kuma yasa ran zai sha. Cike da kulawa ya ce "Saif ga ruwan ka yi buɗa bakin mana?" Kamar dai ko yaushe shiru ya yi bai ɗago kai ba bare kuma Imran ya sa ran zai amsa mashi magana, kasancewar Imran ya saba da halin nasa sai bai wani damu ba, domin ba yau suka saba ba. Goge wajen da jininsa ya zuba kawai ya je ya yi tare da kwashe glass da ya fashe ya gyare wajen, sannan ya dawo saman gefen bed nasa ya zauna. *Nasan kowa daga cikin ku bashi da wata burin da ta wuce sanin ya akayi Imran ya san Lion? Ya akayi Lion ya kasan ce Musulmi? Ya akanyi ya zo Nigeria? Ya akayi yana musulmi kuma bai musuluntar da yan uwan sa ba? Ya akayi ya ɓoye cewa shi musulmi ne? Ta ya ma ya musulunta? Wannan tambayoyin na san sune cike a ranku, to a yanzu dai za ku samu amsoshin guda biyu, saura kuma sai gaba.* Lion dai a tare suka yi makaranta da Imran da kuma James, a lokacin ma har da Michael, idan ba ku mance ba, James ya gayawa Musharraf yana da aboki musulmi, haka zalika shima Michael ya sanar da Musharraf Lion yana da aboki musulmi, to amsar ku ta farko dai shine, Lion tun bai zama babban soja ba suke tare da Imran, tare suka yi makaranta, duk duniya Lion bashi da wani aboki biyun Imran, shi kaɗai ne friend nasa sosai, kuma shine mutun na farko da Lion ya fara yarda da shi a duniya, kuma har gobe bayan Imran ɗin bai sake yarda da wani ba, ko su Tga ba komai na sa yake gaya masu ba, amma Imran yana gaya mashi halin da yake a ciki. wannan shine amsarku ta farko. Tambaya ta biyu, me ya kawo Lion Nigeria?. Amsa ba Nigeria ya zo ba African ya zo ma'ana. A.E.I.D.S.A (1).A. America. (2) E. England. (3) I. India (4)D. Dubai (5) S. Spain. (6) A. African. Wayan nan sune kasashen da yake nema, so James yana African, sai dai bai san a takamaiman wata kasa yake ba a African, abin da kuma yasa ya zo Nigeria shi ne, ba wanda ya sani gaba ɗaya faɗin African sai Imran da yake Nigeria, wannan dalilin yasa ya zo Nigeria, kuma yana zargin James yana tsakanin Niger da Nigeria hakan nema ya bashi kwarin gwiwar nufar Nigeria kai tsaye. Wannan shine amsa guda biyu da za ku samu sauran kuma sai dai gaba, mu koma cikin story kai tsaye. Ya jima kansa a duƙe yana kallon kasa, daga bisani ya miƙe tsaye, wani tsawo ya kara sosai cikin jallabiyar nan, bakin gado ya koma ya zauna yana jawo wayarsa dake a saman bedside drawer Imran. "Saif dan Allah ka yi buɗa bakin mana?" Nan ma shiru ya sake yi wa Imran, zuba mashi ido Imran ya yi yana karantarsa na ɗan lokaci sai daga baya ya fahimci cewa ruwan Faron ne bai yi mashi ba, ba zai iya sha ba. To fah tashin hankali, babbar magana yau ake yinta, ruwan faro mai gaba ɗaya bata yi mashi ba, to ina za'a samo mashi wani ruwa yau ya yi buɗa baki? Sosai tausayinsa ya kama Imran, dan yasan dama da wuya ya iya zama a Nigeria, dan rayuwar ba ɗaya ba. Miƙewa ya yi ya nufi waje, yana faɗawa Lion yana zuwa, yana fita kai tsaye cikin gida ya nufa, bedroom ɗin Abba ya shiga, dan yasan Abba yana da dabino masu kyau tsabtatatu wadda ake kawo mashi daga Madina, da kuma ruwan zamzam. Kwali biyu na dabinon ya ɗauko tare da zamzam gora biyu masu ɗan girma, sannan ya dawo part nasa, ya wuce ya san zamzam ɗin a cikin fridge, dabinon kuma ya wuce da su ɗakinsa. Lion na zaune a in da ya barshi yana riƙe da wayarsa, kusa da shi Imran ya zo ya zauna tare da buɗe mashi kwali ɗaya na dabinon yana faɗin "Please Saif ka yi buɗa baki da wannan sai ka sha maltinan, shi kuma ruwan sai ka gaya mani irin wanda kake so, sai mu nemo maka, amma na sa maka zamzam a fridge idan zaka iya sha". Sai da ya ɗauki good 10mins sannan ya karɓi dabinon, kwara ɗaya ya ɗauka ya kai ɗan bakinsa, tare da yin Bismillah, bayan ya ci ne sai ya ajiye wayarsa a saman gadon, ya sauƙa kasa ya fuskanci gabas ya yi addu'a na masu buɗa baki, da ya gama sai ya koma bakin gadon ya zauna. Lokacin da ya ajiye wayarsa ya sauƙa dan yin addu'a shi kuma Imran ya ɗauki wayar yana kallon abin mamakin dake acikin wayar. Video Michael ne lokacin da yake zaune saman bed nasa yana ta karatan suratul Fatima da Musharraf ya koya mashi, sai kokarin haddarta ya ke yi, ga kyakkyawar fuskar nan tasa ɗauke da kayatatcen murmushi, wani mugun farincikin Imran ya ji ta kulluɓe shi, sannan kuma abin ba karamin mamaki da kuma burgewa ya yi mashi ba Na san kuma kuna son sanin ta ya akayi ya samu wannan video, kuma ya akayi ya ajiye a wayarsa yake gani, to dai ku cigaba da bibiyar TRIPLETS a hankali za ku sami amsoshin ku gaba ɗaya, amma dai Lion mutun ne mai abin ban mamaki, baka taɓa gane ina ya dosa, sai dai ka bishi a yadda ya zo maka. Abin da ya sanya kwana biyu yake matukar shiga yana mai daɗi kenan, saboda Michael ya musulunta kuma ƙwaƙwalwarsa ta samu lafiya, sannan yana ɗaukar karatun yadda ya kamata, ko da yaushe Lion yana bibiyarsu sosai, domin ya ga a ina karatun Michael ya tsaya, ranar da suka je Masallaci ma duk yana kallonsu, duk wani motsi da za su yi a gidan har ma da wajen gidan, to fa akan idanunsa suke yin shi, yana sane da komai, kawai dai shi baya shiga harkar kowa ne, a da baya kafin ya musulunta ko mai zaluncin da ake yi wa mutane baya shiga harkarsu, amma daga baya da Musulmici ta ratsa shi ne yake iya saka baki idan ana zalunci a gidan, bacin haka shi ba zaka taɓa ganin shi yana shiga har kar kowa ba, abin dake a gabansa kawai yake yi, lokacin da ya kasance musulmi alokacin ne ya kafa masu dokar hana su zina, ya ce duk mai son mata ya yi aure, domin alokacin ya san hukuncin mazinaci, a baya ba ruwansa da irin wannan baya shiga wannan harkar, koda kuwa akan titi za'ayi zinar ba ruwan shi, kunsan dai yadda turawa suke, yin zina ba wani abin azo a gani bane a wajen su, basu ɗaukar shi kamar laifi ba ne, sanna kuma lokacin da musulci ta ratsa shine ya san darajar iyaye shiyasa har yake kokarin kula da daddy, idan na ku mance ba akwai lokacin da daddy ya ce yana mamakin Lion a yanzu ya sauya yana bashi kulawa, to hasken musulunci da kuma imani tasa, kun san dai da abaya ne lokacin da zuciyar kafuran farko take a kirjinsa da Rimsha bata isa ta shiga wannan ɗakin ba, amma yanzu abin da ɗan sauki musulci ba wasa ba, amma dai still har gobe yana da bala'in zuciya wadda kuma kun san wannan halittace, haka zalika har gobe mace bata a gabansa, shi yanzu ma da za ki tambaye shi ya mace take a suffa, wlh ba zai taɓa iya gaya maki daidai ba, domin bai sani ba, kai ko halittar namiji ba dan ya kasance irin sane a jikinsa ba, da shi ma mawuyacin abune ya san shi, domin idan baku mance ba, shi baya kallon mutane kuma baya son a kalleshi, haka yake, dan haka baya ce maki ga yanayin yadda mata suke dressing da sauransu ba, a karatu dai ya karanci iya abin da ya karanta, shima dai ba wani bada himma akai ya yi ba, saboda da ya zo wajen yake karawa gaba ya ce shirmen banza, bugu da kari Musulci tasa ya kafawa su John doka masu kyau a gidan, ya kuma hana ɗaya ya zalunci ɗaya, sannan kuma ya bawa kowa yanci a cikin gidan, kuna tunanin ba dan musulci ba dan John ya kalli Blue film a gidan zai damu da shi ne? Kada ku mance yin hakan ba wani abin tsiya bane a wajen su. Mu koma cikin story mu Bayan ya zauna saman bed ɗin ne cike da murna Imran ya ce "Saif Michael ya musulunta ne?". A maimakon ya bawa Imran Amsa sai ya ce "Prof Ina buƙatar gida yanzu zan saya na koma can". Zaro ido Imran ya yi duk da cewa ya san dama Lion ba zai zauna a gidan su ba, amma bai yi tsammanin barin shi gidan da wuri haka ba, ya yi tunanin sai gobe, dama kuma dole ce ta sanya shi sauƙa a gidan su Imran ɗin, idan ba ku mance ba family William jacop basa zama a hotel sai in ya zamar masu dole, sannan kuma shi Lion tafiyar sirri ya yi baya son asan yana African ko His Excellency bai gayawa ga kasar da zai je ba, wannan dalilin yasa gwamnatin Nigeria bata yo mashi tarba ta musamman ba, da ba tafiyar siririn bace da tuni His Excellency wato kakan sa ya kira President na Nigeria ya sanya a tanada wa jikansa wajen sauƙa mai rai da lafiya, na musamman, amma tafiyar sirri ce dole ya yi komai nasa a sirrance, abubuwa biyu ne kuma yasa shi ya yi tafiyar sirri, na farko wayan da suka kama James a yanzu sun gano cewa ɗan uwansa ne, so idan suka san ya shigo neman James za'a iya samun matsala, abu na biyu kuma daddy, idan daddy yasan ga abin da yake faruwa na ya tafi neman James ne to zuciyarsa zata iya bugawa ya mutu, shiyasa ya ki gayawa su Tga ma ga in da zai je, Michael kawai ya gayawa, shima Michael ɗin massage ya yi mashi lokacin yana cikin jirgi. "Saif please ka yi hakuri sai zuwa gobe sai mu samu gida mai kyau". Shiru ya yi bai sake magana ba, a hankali ya ɗago idanuwansa yana bin ɗakin Imran ɗin da kallo, duk daular dukiya da aka narka wa wannan ɗaki, amma Lion ji yake yi tamkar yana keji, ko gidan yari, gaba ɗaya a takure yake jinsa, Nigeria ga zafin bala'i, shi kuma baya shiri da zafi ko kaɗan, kusan gaba ɗaya Imran ya kure gudun Ac ɗakin, amma Lion ya ce za fi yake ji, tun karfe uku Imran ya je Airport ya ɗauko shi, daga karfe uku zuwa yanzu karfe 7:30 ya yi wanka ya kai sau 7 saboda zafi, su Imran suna saka kayan sanyi shi kuma yana kara yin wanka domin ya sami iska, sosai Imran yake tausaya mashi domin bai saba ba. Miƙewa ya yi ya nufi hanyar fita daga cikin ɗakin, cikin sauri Imran ya miƙe ya bi bayan sa, har sun kai bakin kofar fita, sai kuma ya juyo ya dawo ya ɗauki wayarsa tare da ɗaukar face mask nasa suka nufi waje. A palo suka wuce Akila da Umaisha, ita kuwa Rimsha tana can kwance baiwar Allah,. Sai kallon shi Akila da Umaisha suke yi, sun saki baki, Akila sai kokarin son ganin fuskarsa take yi domin ta tantance wanene amma bata samu dama ba, dan kafin ta ɗago ta kalle shi ma ya wuce abinsa, dan ba tafiyar yara yake yi ba. Imran ya zo fita palon ne ba tare da ya juyo ba ya ce da Akila ta yayyafawa Rimsha ruwa, to Akila ta ce mashi tare da miƙe wa suka nufi bedroom ɗin Rimshan da sauri, dan ita a tunaninta barci Rimsha take yi. Su kuwa Lion kai tsaye waje ya nufa, dan har ga Allah ba zai iya zaman gidan su Imran ba, dole komai dare a sama mashi gida. Jerawa suka yi da Imran suna fita wajen gate ɗin, suna fita wayarsa ta fara kara, dubawar da zai yi Michael ne yake kiran shi, bai ɗauka ba har kiran ta katse wata ta sake shigowa, ita ma sai da ta kusa katsewa sannan ya ɗauka, har lokacin tafiya suke yi, shi Lion bai san ko'ina ba tafiya kawai yake yin, shi kuma Imran yana biye mashi suna ta tafiya saman titi abinsu har sun yi nisa da gida. "My Lion fatan dai ka isa African lafiya?" Michael ne ya tambaya, shiru ya yi har na tsawon minti ɗaya kafin gently ya ce "Lafiya lou Alhadulillah fatan kana karatu sosai?" Michael zai yi magana kenan Lion ya ji an fusge wayar daga hannunsa, a tunaninsa ma Imran ne, sai da ya juyo sai ya ga ba Imran bane, yan kwancen waya ne, abin ma, mamaki ya ba shi, zubawa matashin da ya kwance wayar nasan idanu ya yi, yana kallonsa yadda yake ta tikar gudu, shima Imran bai wani damu ba, domin tun da ya ga Lion bai damu ba sai shima bai wani damu ba. A ɓangaren Rimsha kuwa Lokacin da su Akila suka zuba mata, a firgice ta tashi, tana ƙokarin sauka daga gadon akila ta yi saurin riƙota tana faɗin "Rimsha lafiya? Me ya same ki? Ina zaki je?" Ina ai bata jin su kamar wadda ƙwaƙwalwarta ya taɓu baiwar Allah a zafafe ta diro kasa daga saman gadon da sauri ta yi waje, kai daga gani kasan bata a cikin hayyacinta, tana fitowa palo kai tsaye kofar waje ta nufa, daidai lokacin shi kumu Akil zai shigo, a kofar palon suka yi karo, bata wani damu dan ta bugeshi ba, ita dai burinta ta yi waje kawai. Ganin su Akila sun fito da gudu suna kiran sunan tane yasa Akil ya yi damkota, dama kuma daga ganin yadda ta buge shi bai damu ba, yasan ba lafiya ba, kokarin kwace hannunta ta yi dan ta fice daga palon, ganin haka yasa ya riƙe ta da kyau yana faɗin "Rimsha kina lafiya kuwa?". Jin abin da ya ce ne ya sa ta fashe da kuka, Allah sarki, ta razana sosai har abin ya kusa taɓa mata kwakwalwa, riƙota sosai Akil ya yi, ita ma sai ta sake mashi jikinta a jikinsa tana kuka, abin ya ɗaure masu kai sosai, bai wani damu ba, sai ya runmeta a jikinsa, dan ya lura ta birkice sosai ne, sai Allah kaɗai yasan me ye ta gani ya razana ta haka, ya faɗa a cikin zuciyarsa tare da duƙawa ya ɗauketa cak izuwa cikin palon, sosai abin ya sosawa Umaisha rai, tabbas tasan ita ma yana ɗaukarta kamar baby to amma me yasa zai ɗauki Rimsha bayan ba matarsa bace? Abin ya bata haushi kamar zata yi kuka ta wuce ta fita daga palon zuwa part nasu. Shi kuwa bai ma lura da ita ba, saman sofa ya kwantar da Rimsha sai lokacin ta fara dawowa hayyacin ta, kokarin cire mata Hijabin jikinta ya yi domin ta samu iska sosai, amma ina ta fara dawowa hayyacin bata bari hakan ta faru ba, sai ta yi maza ta ruƙe hannunsa, ganin haka shima sai ya saki mata hijabin ya dubi Akila da ta yi sumar tsaye tana mamakin yau yaya Akil ne har mace ta faɗa mashi a jiki ba Umaisha ba kuma ba ita Akilar ba, amma har ya nuna bai damu ba, kuma bai wani ɗauki action a kan hakan ba, abin ya bata mamaki sosai, dan ta san halinsa sarai, shi kuma ba da wata manufa ya yi hakan ba, saboda ya ga bata a hayyacin tane shi yasan, da tana hayyacinta ba zata taɓa yarda ko hijabinta ya taɓa ba bare kuma har jikinta, wannan dalilin yasa bai damu ba ya ɗauko ta. "Heartbeat ɗauko mani ruwa". To Akila ta ce sannan ta wuce cikin Kitchen tana tunanin ya wannan al'amari zai ka san ce, ga dai Umaisha a can ta tafi da alama kuma fushi ta yi, me yake shirin faruwa ne, ko dai yaya Akil ya kamu da son Rimsha ne? Allah yasa ba hakan bane domin ni bana son zumuncin da kuma ƙawancen mu ya ɓaci, haka ta rinƙa tunane-tunanenta har ta ɗauko mashi ruwan ta kawo mashi. Karɓa ya yi ya buɗe bakin robar ruwan, ba tare da ɓata lokaci ba ya karanta mata ayatul kursiyu kafa bakwai ya tofa acikin ruwan ya bata ta sha, ba musu ta karɓa ta sha, Allah da ikonsa kuma, tana sha sai ta zama daidai, ban da sauke nannauyar ajiyar zuciya ba wani abin da take yi. After some minutes da ba su fi goma ba, cikin natsuwa Akil ya ce "Rimsha kina lafiya?" Ya yi maganar yana tsareta da ido, lokacin ta ɗago da idanuwanta a kansu, yar murmushi ta sakar masu kafin ta ce "Kayi hakuri yaya Akil" "Hakurin me kuma Rimsha?". Shiru ta yi kamar mai tunani, can kuma sai ta ce "Babu komai bari na yi sallar mangariba ba" To ya amsa mata, da shi sannan ya miƙe ya nufi waje, yana faɗa musu akan yana zuwa, to suka amsa da shi, a tare suka wuce ita da Akila zuwa cikin ɗaki, shi kuma Akil part nasu ya koma. Bayan sunyi sallar mangariba ne za su miƙe sai suka ji ana kiran sallar isha, hakan yasa suka gabatar da sallar isha ɗin ma kafin su fita zuwa Kitchen, Rimsha tana biyewa Akila ce kawai, amma ita kaɗai tasan me acikin zuciyarta, tunani kala-kala take yi, tana son sake ganinsa dan ta tabbatar da shi ɗin ne, duk da cewa tasan ko a cikin barci aka tasheta ta ganshi to ba makawa zata gane shi ɗin ne, amma tana son sake ganin shi, tabbas ta san shine, ba makawa, domin irin sanin da ta yi wa face nasa a zane da kuma irin kaunar da take yi mashi, ya wuci tunanin mai tunani, sannan abin mamaki yadda take zana shi kullum haka ya bayyana mata a yau, duk da cewa a mafarkinta ta fara ganin ainahin face nasa, hakan yasa ta kware a zanen. Tana aiki girkin nan tana tunane-tunanenta, wayar Akila dake a hannunta ne ya fara kara, dubawa da zata yi sai taga Yaya Imran, cikin sauri ta ɗauki wayar tare da karawa a kunnanta tana faɗin "Hello yaya Imran" daga ɗayar ɓangaren Imran ya ce "Heartbeat ki ba wa Rimsha wayar". To ta amsa mashi da shi tare da miƙawa Rimsha wayar. Karɓa ta yi ita ma ta kara a kunnanta, "Hello yaya Imran" daga ɗayar ɓangaren ya ce "First lady dan Allah ki girka abinci mafi daɗi wata kila Saif zai ci, idan kin gama ki kai mashi ɗaki, ya yi azumi amma yake cin komai, saboda bai saba da kasar mu ba, ni ban ma san ya zan yi ba, narasa me zan ba shi, yanzu dai bari muga ko zai iya cin abincin kasar mu, ki yi tsantsarerren girki kin ji ko? Yanzu za mu dawo gida". To ta amsa mashi da shi, cike da zumuɗi ta fara ƙoƙarin haɗa mashi abinci mafi daɗi, sai murna take yi ta wani ɓangaren kuma har hawaye ta yi mashi, ya bata tausayi, bai saba cin irin abubuwan mu ba, zai sha bakar wuya sosai, ga shi ko ruwar Faro bata yi mashi ba, kenan sai dai ya yi ta shan maltina? Ko yaya abin zai kasance? To mu je dai zuwa. A ɓangaren su kuwa, lokacin da ɓarawon ya kwace wayar yana gudu, zuba mashi ido Lion ya yi yana mamakin wai har shi za'a kwace wa waya a hannunsa. Ni kuwa nace mamaki kake yi ne? Nigeria fa kake, to garama ka yi hankali idan ba haka ba, kai ma anemeka a rasa🤣 waya ga an sace The General of The Army Usa ɗungurunrum a Nigeria abin zai bada sugar🤣 Zura hannu kawai ya yi a aijihun jallabiyar jikinsa ya cigaba da tafiya yana kallon yadda gari yake, Imran sai wani kame jikinsa yake yi saboda sanyi shi kuma Lion zafi yake ji yana buƙatar sanyi, tun da yake bai taɓa fita cikin gari ya sake haka ba, yau ga shi ya fita ba sojoji ba komai, shi kaɗai ɗin shi, daga nan sai ya ji rayuwa ba wata kuƙami ma akwai matikar daɗi, yanzu a nan ba wanda ya san fuskarsa, ba yan jarida masu ɗaukarsa hoto, jet nasa ma ba da ita ya zo ba, ya kyaleta a Spain da jirgin kasuwa ya shigo Nigeria, hakan ma ya kara sanya tafiyar ta yi sirri sosai, abin da ya sa kuma ya fita da jet ɗin daga Washington DC domin kowa ya yi zaton Spain ya tafi, saboda yasan da cewa tabbas komai tafiyar sirrin da zai yi akwai wayan da suka sa mashi ido sosai, ciki harda irin kungiyar su James, dan haka suna ankare da motsin shi, yasan za su bibiyi a ina jet nasa ta nufa, a ina ta tsaya, shiyasa ya yi masu basaja kamar hakan. "Saif mu koma gida dan Allah". Cewar Imran domin sanyi yake ji sosai. Ba musu Lion ya juya suka nufi hanyar komawa, domin sun ɗan yi nisa da tafiyar ya fara riyo kamshin abubuwan da ake soyawa a bakin hanya, irin su kosai da doya su kifi, shi kuma baya son warinsu, hakan yasa ya juya dan su koma. Suna juyawa sai ga ɓarawon wayar ya dawo a guje, yana zuwa ya zube gwiwowinsa a kasa a gabansu, yana kuka yana basu hakuri, a nan ne Imran ya koma gefe ya kira Rimsha a waya, shi kuma Lion hannu yasa ya karɓi wayarsa, dan dama yasan ba wanda zai iya riƙe wayar sai shi, dan ba waya ce kamar ko wace waya ba, sannan kuma idan suka kunna wutar screen ɗin to ya zama dole su razana su dawo mashi da wayarsa shiyasa bai wani damu ba, hankalinsa a kwance lokacin da aka kwace wayar. Abin da ya faru yasa suka dawo da wayar shine, ɓarawon da ya kwace wayar ogansa ya kai mawa, yana faɗa mashi sun yi babban kamu, ogan yana karɓar wayar tun bai kunna wutar screen nata ba sai da ya ranaza, bai san lokacin da ya furta "Wannan wayar bata irin ƴan Nigeria ba ce, ban taɓa ganin irinta ba". Bai gama rufe baki ba, Michael ya sake kiran wayar domin da suna waya ɓarawon ya kwace wayar sai ya daina jin Lion hakan yasa ya katse kiran ya sake kira. Suna riƙe da wayar kirar Michael ta shigo nan fa suka ga abin mamaki, domin wayar ba ringin take yi kamar ko wace waya ba, no gaya mashi ta ke yi ga wanda ya kira ga kuma number da ya kira sannan ga daga location da aka kira, shine a matsayin ringintone na wayar, kasa ɗaukar kiran suka yi, domin ma ba za su iya ba, ita ba ɗaukarta ake yi kamar sauran wayoyi ba, a'a idan ba Lion ba ba mai iya picking nata, sai kuma idan akayi Sa'a aka samu masu danne danne suyi ta latse jikinta har su samu su yi picking, haka suka riƙeta har kiran Michael ta katse. Bayan ta katse ne, sai suka samu wayar ta kawo wutar screen ɗin da kanta, wani mahaukacin razana ogan nasu ya yi lokacin da ya halli abin da yake a gaban screen ɗin wayar, Hoton Lion ne a fuskar wayar, wadda kowa ya san shi da shi, wato da face mask, shi da James da Michael ne, shi kaɗai ya sanya face mask a cikinsu, suna tsaye a saman balcony ɗakinsa, sun rungume juna, sun yi kyau sosai, da sosai. Sun shagala da kallon hoton kiran Michael ya sake shigowa a karo na biyu kuma Vedio call ne na yanzun, rashin sa'ar su yasa ba su san ina suka danna ba, dan ya dakumi wayar da hannunsa, suna picking sai ganin Michael suka yi yana zaune saman dining table na palon kasa yana cin abinci, domin shima ya yi azumin litinin, ihu ogan nasu ya kurma tare da bawa wanda ya sato wayar a kan ya mai dawa mai waya wayarsa. Abin da ya faru suka dawo da wayar kenan. Cikin harshen turanci ya ce "Me yasa kake kwacewa mutane abu?" Shiru ɓarawon ya yi domin baya jin turanci ko kaɗan, sai da Imran ya gama magana da Rimsha ya dawo wajan ne ya shiga yi wa ɓarawon fassara yana mayarwa Lion da amsa, daga ƙarshe dai Lion ya ce a mai da shi makaranta a bashi sana'a, domin alamu sun nuna jahilci yasa yake sata, bai samu ilimiba kuma babu sana'ar yi, shiya jefa shi shaye-shaye da kuma sata, da haka suka yi sallama Imran zai je har gidan su gobe ya duba shi, dan ya karɓi address ɗin sa. Kamar yadda suka fito gida a tare haka suka koma, kai tsaye bedroom na Imran suka wuce. Suna shiga ya nufi toilet dan yin wanka, komai na cikin ɗakin Imran daga waje aka kawo su, hasalima daga kasar su wato Usa aka kawo su, amma Lion ya ce ba su yi mashi ba, shi gidan nema gaba ɗaya ta yi mashi kama da keji kaji, dan haka shi ba zai zauna ba, dole adaran nan a sama mashi katafaren gida wadda aka gama gina wa aka zuba komai na kasarau, ya saya ya koma can, cike da zolaya Imran ya ce "Idan ka sayi wannan gida ka zama ɗan Nigeria kenan?". Karisa shiga cikin Toilet ya yi ba tare da ya sake yin magana ba, wucewa saman bed Imran ya yi ya kwanta yana mamakin yau Lion ne a Nigeria abin da bai taɓa zato ba, a Nigeria ma a gidan su. A daddafe ya yi wanka ya fito, gaba ɗaya tsadaddun Towels dake a cikin toilet ɗin wai ba su yi mashi ba, da nashi da su Tga suka sanya mashi a cikin trolley sa ya yi amfani, ya saba da shiga dressing room ya shirya, amma yau daga cikin trolley ya ciro kaya, hakan yasa ya sake tsanar gidan su Imran, ba iya gidan kawai ba, gaba ɗaya kasar bata yi mashi ba, ransa ya ɗan ɓaci, haka ya shirya cikin wandon jeans fara tas da riga polo t-shirt blue, ya feshe jikinsa da perfume nasa mai bala'in kamshi bayan ya shafa mayukansa kenan, daga nan ya gyara gashinsa. Bakin gado ya koma ya zauna kusa da Imran yana ganin gadon ma wani local, ko gadon Bradyn sa ta fi wannan kyau. Ni kuwa nace yau dai ba yadda zaka yi Nigeria ka zo ato, dole ayi hakuri da mu. Shiru suka zauna domin Imran ya yi degree a sanin halin Lion, yasan baya son magana, dan haka suke zama shiru kamar kurame. After 1 hour. Suna zaune a in da suke ba su motsa ba, kuma ba wanda ya ce da ɗan uwansa uppan, kamar gumaka, zama da Lion sai an kai zuciya nesa, karfi da ya ji sai ya mai da ka kurma Da sallama ɗauke a bakinta ta shigo cikin ɗakin, still hijabi ne a kijinta, hannunta na ɗauke da wani kyakkyawar katuwar tray mai ɗauke da kyawawan kololin abinci, da su plates and spoons da sauransu. Wani irin lumshe idanuwanta ta yi lokacin da ta shaki Kamshin perfume nasa, ji take kamar bata a duniya, ta lula sama jannati, zuba mata ido Imran ya yi, sai da ta shaki kamshinsa son ranta sannan ta buɗe idanuwanta karaf a kan fuskar Imran, wani irin kunya ta ji ya kamata, shi kuwa bai damu ba, dan yasan daɗin kamshin perfume ɗin Lion abin so ne, kowa zai so ya yi ta shaƙarta kada ya daina. Da hannu ya yi mata nuni da shi akan ta kai mashi gabansa, jikinta sai kerma yake yi ta nufe shi, banda hasbunallahu wanimal wakil babu abin da take nanatawa a cikin zuciyarta. Gaban sa ta zo ta tsgunna cikin natsuwa ta buɗe kular abincin ta fara zuba mashi, yau ga Rimsha ga Lion waje guda, yana duke da kansa kamar yadda yake tun farko, da alama ma bai san da mutun a wajen ba. Tana tsaka da zuba mashi abin ne, a zafafe ya yi wani irin ball da gaba ɗaya tray ɗin abinci, ciki kuma ya haɗa har da hannunta, domin hannun nata yana kan tray ɗin alokacin. Tarwatse abincin ya yi har saman bed, kular miya kuma da jikin bangon wajen mirror ya bugu miyar ta watse, kusan rabi na miyar ya watsun mata a jikin milk color hijabinta, ga shi kuma miyar steew ce, su cabbage and cucumber da ta yayyaka gaba ɗaya sun watse sama suka warwasu a cikin ɗakin, a takaice dai ball da tray ɗin abincin da ya yi ta watsa komai. Abin da kuma yasa ya yi ball da abincin a cewar sa ta kawo mashi wari gaban fuskarsa ta canza mashi iskar da yake shaƙa, dama kuma da kyar yake shakar wannan iskar ba dan yana so ba, tazo ta wani kawo mashi warin steew a gaba. Tsabar razana Rimsha bata san lokacin da ta miƙe jikinta na kerma ba, a guje ta juya zata fice sai dai kuma ina tsorata ya yi mata yawa, numfashin ya rigata fita daga jikinta, saboda bala'in razana yasa ta zube kasa a wajen, shi kuma wayarsa da laptop nasa ya ɗauka ya fice daga cikin ɗakin, Imran ya rasa wajen waye zai je ɗaya daga cikin su, ga Rimsha a sume ga Lion ya yi waje da alama kuma ransa a matukar ɓace. Ganin tunani ba nashi bane yasa ya ɗauki Rimsha ya ɗaurata saman bed nasa ya fita waje dan ya bi bayan Lion. Sai dai ko da ya fito babu Lion babu alamarsa, hakan yasa ya dawo cikin gida da sauri ya ɗauki wayarsa, member Lion ya fara kira dan ya ji a ina yake ya biyo shi, amma ina har 3 miss call ya yi mashi Lion bai ɗauka ba, daga karshe dai ya hakura a ajiye wayar ya kira su Akila domin su gyara mashi ɗakinsa, ita kuma Rimsha ya yayyafa mata ruwa. Baiwar Allah nan a matuƙar razane ta farfaɗo, gaba ɗaya ta fice a hayyacinta, numfashinta sai fita yake da sauri-sauri, idan baku mance ba, tun ainahi tana mutuwar son shi kuma tana bala'in tsoron shi, hakan yasa zuciyarta ta kasa jurar ɗaukar ganin fuskarsa, haka zalika ta kasa iya cire tunanin lokacin da ya zo zai yi mata kiss a mafarki, hakan kuma ba karamin birkita mata kwakwalwa yake yi ba, Allah sarki. Wani irin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro ta saki, sosai Imran ya shiga rarrashinta yana bata hakuri tare da gaya mata kada ta damu shi Lion haka halinsa yake, Allah ya kiyayye ma yanzu bala'in zafin zuciyar nan tasa ta ɗan ragu saboda hasken musulunci da kuma imani da ta ratsa shi, amma ba dan haka ba, da Rimsha bata isa ta zo in da yake ba, yanzu ko ba komai yana ɗaukan mutane da daraja kaɗan, haka zalika yanzu ya san Allah ke yin komai, kuma laifin wani baya shafan wani. Imran bawan Allah bai san da tsohon soyayyar da Rimsha ke yi wa Lion ba, ya ɗauka iya ball da ya yi da tray ɗin abincine ya sanya ta suma, a ɗazun kuma da ta suma lokacin da ta kawo mashi ruwa, ya tauka ta razana da ganin face nasa ne, wadda hakan ba wani bakon abu bane, domin dayawa daga cikin mata matsorata suna suma idan suka yi ido huɗu da shi, to shi Imran ya zaci ita Rimsha tana daga cikin su ne, shiyasa bai wani damu ba. Sosai ya rinƙa rarrashinta, da kyar ya samu ta dawo daidai, da kansa ya tasata a gaba suka nufi Palo, a nan ta isko su Akila sun yi wanka sun dawo suna jiran ta zo su ci abinci, ai kuwa abincin da bata ci ba kenan baiwar Allah, daren ranar dai da yunwa ta kwana, haka zalika daren ranar bata yi barci ba sai wajen karfe 2 na dare sannan ne barci ya ɗauke ta, sai ajiyar zuciya take sauƙewa cikin barci. Babban abin bakincikin kuma shine, tana fara barci ta fara mafarkin shi. Wai tana zaune a palo ita kaɗai, ta yi shiru ga kamshi da sanyin Ac na tashi, su Imran basu nan sun fita, ita ka ɗai ce a cikin palon, jikinta na sanye da wando da riga sun kamata sosai, tana rungume da pillow ta shagala da kallon Tv dake a gabanta, bata ankaraba sai ta ji hannun mutun a saman wuyarta, bata wani razana ba domin kamshin perfume nasa ya isar mata da sakon ko wanene, hannu tasa ta fara shafo nasa hannun, kwanto da kansa ya yi a saman kafaɗarta yana sauƙe mata numfashinsa a hankali hankali, sai faman lumshe idanu suke yi duk kan su biyu. Sun ɗan jima a haka kafin ya zagayo ta gabanta ya zauna gefenta yana janyota saman faffaɗar kirjinsa, kwanciya ta yi ta lafe a kirjin nasa tana mai da numfashi, hannu ya zura cikin rigarta ta daidai kugunta yana ɗan shafa plat tummyn ta, sai wani yauki take yi mashi tana kara shigewa jikinsa, hakan da take yi kuma ba karamin kara birkita shi yake yi ba, dan haka sai ya cigaba da wasa da cibiyarta, a hankali ya sanya ɗayar hannunsa ya ɗago haɓarta suna fuskantar juna, gently ya matso da fuskarsa sai tin tata, tun bai karisa isowa ba, ta kurma ihu tare da farkawa daga barci, wani wahalallen zufa ne ke tsastsafo mata daga gefe da gefen fuskarta, ta yi sharkaf da fitsari sabida tsoro, wannan masifa da me ta yi kama, dafe kanta ta yi ta fara hawaye tana rokar Allah da ya sawwaƙa mata wannan bala'in kada hakan ya zama sanadiyyar taɓuwar ƙwaƙwalwarta ko kuma ma mutuwarta baki ɗaya, innalillahi wa inna ilaihir rajiun shine abin da ta fi yawan furtawa a ransa. Tana zaune a wajen ta kasa motsawa har karfe 3, sannan ne ta ja jikinta da kyar ta iya sauƙowa kasa daga saman gadon ta nufi toilet, da kyar ta iya yin wanka tare da ɗauro alwalla ta fito, doguwar riga ta zura a jikinta tare da hijabi, ta shinfiɗa dadduma ta fara sallama tana kai wa Ubangiji kukanta, dan tasan ba mai cireta a cikin wannan azabar sai shi, baiwar Allah sai kugin yunwa cikinta yake, saboda bata ci abincin dare ba, da kyar ma take iya kai sallar saboda jiri na yunwa dake ɗibarta, abin ya taɓa ta sosai, har wani ramar lokaci guda ta yi, duk ta fita a hayyacinta, kuma duk wannan masifaffen son da take yi mashi tun tana yarinya ne ya ja mata hakan. A daddafe ta yi sallah raka'a shida sannan ta rufe da shafa'i da witiri, ta zauna saman dadduma tana karatun Alkur'ani mai girma kasa-kasa, har lokacin yin raƙatainil fajir ya yi, haka ta miƙe ta gabatar da raƙatainil fajir ɗin ta, a raka'ar farko ta karanta Kulyahayyuwalkafirun, na biyu kuma ƙulhuwallahu ahad, domin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce falalar yin sallar raƙatainil fajir tafi duniya da abin da yake a cikinta, amma idan ka karanta wayan nan sururo guda biyun wato ƙulhuwallahu ahad da Kulyahayyuwalkafirun, falalar da zaka samu sai ya kai girman duniya sau biyu, dan haka kada muyi wasa da wannan dama, Allah ya bamu dacewa. Bayan ta idar da Sallar raƙatainil fajir, ta ɗan zauna kaɗan, kafin ta gabatar da sallar asuba, yin hakan da ta yi kuma yana daga cikin sunnunin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, tsakanin sallar raƙatainil fajir da kuma asuba, annabi yana zama ya ɗan bada tazara na ɗan lokacin, yin hakan ma ba karamar falala bace. Bayan ta yi sallar asuba sai ta yi askar nata, amma bata kai ga kammala askar ɗin ba barci ya ɗauketa a wajen, dan ta samu sauki sosai acikin zuciyarta, ta samu peace of mind, Alkur'ani mai girma maganin cuta komai girmanta, sallar nafila mai kawar da damuwa duk min girmanta, ta yi sallar ta roki Allah da ya shiga lamarinta hakan ya sanya ta samu peace, Baiwar Allah yana barci tana sauƙe ajiyar zuciya. A haka Akila ta iskota misalin karfe 8 na safe, yau bata samu damar tashi ta yi shara ba bare kuma wanka da gyaran ɗaki har a kai ga girki. Akila ta sha mamakin ganinta a hakan, gabanta ta karisa tana ƙoƙarin taɓa ta, sai ta ji muryar Imran daga bayan ta yana faɗin "No heartbeat kada ki taɓa ta, ki kyaleta". Cikin sauri Akila ta juyo da kallonta kanshi, yana tsaye a bakin kofa jikinsa sanye da kayan barci riga da wando, da alama yanzu ya tashi daga barci, kuma da alama da tunaninta ya kwana shiyasa yana tashi ya nufi ɗakinta kai tsaye. "Yaya Imran lafiya? Ko dai bata da Lafiya ne?". Juyawa ya yi ya nufi waje ba tare da ya yi magana ba, dan baya son su tashe ta daga barci, da sauri Akila ta miƙe ta bi bayansa, a palo ya tsaya yana bata amsa "Akila nima dai bansan meke damun Rimsha ba, amma dai tabbas na lura tana da damuwa, jiya ina da tabbacin bata samu barci ba, shiyasa take barci yanzu kada ki tasheta ki kyaleta idan ta tashi ta yi wanka muka samu natsuwa sai in ji menene damuwarta". Lokaci guda yanayin Akila ya canza, mood nata ya juya, sosai ta ji ba daɗi tana son jin meke damun yar uwarta. Ganin ta shiga bad mood yasa Imran ya ce "Heartbeat kada ki damu ba komai In Sha Allah yanzu dai zoki gyara mana palo ko?". To ta amsa mashi da shi, amma dai jikinta duk a mace, ta ji wani irin yanayi mara daɗi, ita bata son jin ance wani yana cikin damuwa ko kaɗan, hakan ba karamin ɗaga mata hankali yake yi ba. Ganin ya juya zai koma bedroom nasa ne yasa ta yi saurin cewa "Yaya Imran jiya waye ya zo ɗakin kan nan? Na gan shi da face mask ban iya ganin face nasa ba, amma dai daga ganin ga shin kansa nan ba ɗan Nigeria bane". Ba tare da ya juyo ya ce "Heartbeat kin iya gulma ashe, to Saif ne, kuma ma ya tafi abinsa, sai na je nemansa yanzu, ki yi mani addu'ar Allah yasa na gan shi". Cikin sauri ta ce "In Sha Allah zaka gan shi" Allah yasa ya faɗa tare da wuce wa cikin bedroom nasa, ita kuma ta fara aikin da Rimsha take yi, dan yanzu ita ma ta iya. To a ɓangaren su Michael kuwa, Wato Washington DC. Yau zai koma school, tun safe ya shirya tsab ya haɗa duk abin da zai buƙata, suka yi sallama da Musharraf ya fito, da motarsa ya wuce school, kuma kamar dai a baya da su copper ya tafi, Lion ya ce 100 level zai koma, bai wani damu ba, ya yarda dan yanzu ilimi yake nema ido a rufe. Michael na tafiya ba jimawa Tga ya shigo cikin ɗakin ya ce da Musharraf ya zo su ta fi, ba musu Musharraf ya biyo bayansa suka fito palon kasa, kai tsaye waje Tga ya nufa, dan yasan akwai camerori a cikin gidan, duk abin da ya yi Lion zai gani, hakan yasa suka nufi waje kawai. Kai tsaye gym ya wuce, Musharraf na biye da shi, kuma bai kawo komai a ransa ba. Tsabar tsanar da ya yi wa Musharraf, baya son shi ko kaɗan, hakan yasa ya fara bashi horon sojoji, manya-manyan karafuna ya sanya shi ya fara ɗaga wa, Bawan Allah bai iya ba, amma saboda sanin bakin hali na Tga yasa ya fara koya, kullun Michael yana bashi labarin bakin halin da mugunta irin na Tga, yau kuma ga shi nan ya tabbatar. Wani zabgegen bulalla Tga ɗin ya ɗauko ya ajiye a gefe, sannan ya ɗaurawa Musharraf wasu mayun karafuna a hannunsa ya ce dole sai ya yi tsayuwar minti talatin da su a hannunsa, Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun, a wannan hali John ya zo ya same su, cikin halin nuna ko in kula John ya ce "Uncle T what is going on here?". A kule Tga ya ce "John this guy ashe musulmi ne" a sukawane ya juyo da karfi ya furta "What??!!" Yayi maganar yana zaro ido waje. "Yes John musulmi ne, ɗazun by 5:30 na shiga bedroom na Michael zan tasheshi daga barci ya zo ya fara gym, na shiga bedroom nasa baya nan, har zan fita part ɗin sai kuma na ce bari na leƙa ɗayar ɗakin ko yana can, to a nan na gan shi yana bautansu, shi kuma Michael ban gan shi a cikin ɗakin ba, a lokacin na kira Lion bai ɗauka ba, sai daga baya ya kirani da na gaya mashi sai cewa ya yi wai na bari sai ya dawo, Musulmi fa a gidan nan, amma Lion yana cewa abari sai ya dawo, to ba zai yi wu ba, kafin ya dawo dole na fara bashi horon, sai ya yi dana sanin zuwan shi gidan nan, kai sai na ma ji dalilin da ya sa ya zo gidan nan, dan daga gani kasan turoshi aka yi, kasan musulmai yan ta'adda ne, wata kila wani abin suke shiryawa, to mun fi karfinsu, shima Michael dole ya rabu da mutumin nan, yana dawowa idan na gaya mashi musulmi ne, dole zai rabu da shi, bakin shaiɗani, mugaye yan ta'adda mu dai mun fi karfin ku" ya kai karshen maganar yana wani huci kamar zaki. Rai a matukar ɓace John ya ce "Tabbas Uncle T wuya zaka ba shi ba ɗan kaɗan ba, sai ya yi danasanin zuwan shi duniya, sai ya gwammaci da bai san familyn William jacop" ya kai karshen maganar tare da ɗaga kafa ya taka Musharraf ɗin a kirjinsa da karfi. Baya baya Musharraf ya yi Allah sarki ya faɗi kasa ga kuma karafuna a hannunsa, suka danne mashi hannun, wannan zabgegen kafuran bulalar Tga ya ɗauko, ya fara zana mashi a jikinsa wai ya faɗin, bulaka biyar masu lafiya ya yi mashi sannan ya ɗage shi ya tsaida shi, ya sake sanya mashi karfen ya ce wai sabon kirga za'a fara. Bawan Allah shi zane shi da suka yi ma bai wani dame shi ba, abin da ya dame shi nauyin wayan nan karafuna. Cike da bada umarni Tga ya fara zuba mashi kashedi da kuma dokoki kamar haka "Daga yau kullun karfe 5 na safe ka tabbatar ka zo nan ka fara ɗaga karafuna kafin na fito, na biyu kuma da yamma dole ka kasance a wajen ruwan kankara, da daddare idan kowa yana barci, dole kai ka zo wajen tsere da doki domin ku yi tsere da dawakan, ba zaka taɓa yin barci ba sai ka yi tsere da dawakan kafa 30, da rana kuma ka kawo kanka da kanka cikin tsakiyar rana ka kwanta kana kallon sama, ka kalli rana sosai, idan kuma ka sake ka gayawa Michael sai na kashe ka, ko da yake ma shima Michael ɗin idan ya san kai Musulmi ne to ba zai barka ba, zaka karɓi nasa horon". Bawan Allah da kyar ya iya amsawa da to, haka Tga ya cigaba da zabtar da shi da horon sojoji har zuwa karfe 11 na rana sannan ya kyale shi ya wuce cikin gida domin ya je ya shirya ya wuce wajen aikin Zama a wajen Musharraf ya yi ya kasa motsawa saboda gaba ɗaya ko ina na jikinsa ciwo yake yi mashi, hannunsa duk sun kumbura, da kyar yake iya numfashin, daga karshe kwanciya ya yi a wajen saboda bala'in azaba da ya sha. Allah sarki, idan muka waiwaya gida Nigeria kuma, Akil yana fita daga part ɗin Imran kai tsaye bedroom nasa ya nufa, Umaisha bata ciki, fitowa ya yi ya duba Kitchen bata nan, abin ya bashi mamaki, haurawa sama ya yi izuwa ɗakin Ammie, ton daga bakin kofa ya fara jiyo kukanta kasa-kasa, cikin sauri ya tura kofar ɗakin ya shiga, tana tsugunne a tsakiyar ɗakin, ta haɗe kai da gwiwa sai kuka take yi, hannunta na ruƙe da tovel na goge goge, ita kuma Ammie tana hakimce a saman gadon ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya tana latsar waya. Da karfi ya furta sunan ta "My wife!" Cikin sauri ta ɗago, fuskarta duk ya yi jaga-jaha da hawaye da majina, da alama dai wani abin mugunta Ammie ta yi mata. Kasa magana ta yi ta mai da kanta kasa ta cigaba da kukan da take yi, da sauri ya kariso cikin ɗakin ransa idan ya yi dubu to ya ɓaci, dan bai son abin da zai taɓa mashi ita,. Yana zuwa ya sa hannu ya ɗagota ya rungume kayansa, ba tare da ya yi magana ba ya wuce da ita suka fice daga cikin ɗakin, ko sannu Ammie bata ce mashi ba, shima kuma bai ce mata ba, sai bayan ya kai Umaisha bedroom nasu ne ya dawo ɗakin Ammie ɗin, a bedside drawer ya zauna, cike da girmamawa ya fara magana. "Ammie me ya faru yau kuma tsakaninki da yar taki?". Shiru ta yi mashi bata kula shi ba, ganin haka yasa ya riƙo hannayenta yana bata hakuri. Ta ɗan ɗauki lokaci kafin ta ce "Ka sakar mani hannu, tun da matarka ta fini muhimmanci, wato ni ban isa in hukuntata idan ta yi mani laifi bako? Shine zaka zo ka gwada mani isa akanta ko? To ka je, ina dai mace ce zaka gani iya ganin idanunka". Kara yin kasa da murya ya yi cikin sigar bada hakuri da rarrashi ya fara magana "Ammie na san ban kyauta ba, amma kiyi hakuri sharrin sheɗan ne, kuma ki dai na cewa baki isa ki hukunta Umaisha ba, kin isa har ma kin yi yawa, nima kika hukunta ni bare mamata, kuma koda ban auri Umaisha ba zaki iya mata hukunci idan ta yi maki laifi ai yarki ce, dan Allah ki yi hakuri". To kawai ta ce mashi, shiru ya ɗan yi yana tunani. "Lafiya tunanin me kake yi?" Ɗan ɗagowa ya yi ya kalleta tare da sakar mata murmushi yana faɗin "Ina kara godewa Allah da ya bani ke a matsayin uwa, gaskiya na ji daɗi, tunanin da nake yi shine anya akwai wanda ya mori uwa kamar ni kuwa?" Yar dariya ta yi cike da kirsa da makirci ta ce "Tom Allah ya yi maka Albarka ta shi ka je". Miƙewa ya yi ya nufi waje yana jujjuya abuwan da suke faruwa, ga Umaisha sai uban rama take yi, idan ya tambaye sai ta ce mashi babu komai, sannan ya fara mamaki da irin bala'in kaunar da Ammie ke nunawa Umaishan a gabansa, abin har ya fara yawa, lokaci guda kuma ya fara jujjuya kalaman Akila a cikin ƙwaƙwalwarsa, in da take yawan gaya mashi dan Allah ya mai da Aunty Umaisha gidan sa da ya gina ɗin nan dan ta samu gidan zuwa yawo. (Kai ka ji wata basira wajen Akila, wato da Ammie ta ce zata kashe Umaisha idan ta tona mata asiri shine Akila ta biyo ta wannan hanyar dan a rabawa Umaisha da Ammie gida, tab lallai jinjina Akila) Akil akwai kaifin kwakwalwa nan take ya gano lallai akwai matsala a gidan, kuma ya zama dole ya san abin yi, domin duk wani abin da ya samu Umaisha yana da kason nasa zunubin saboda shi ya kawota a karkashinsa take a zaune. Zaune a bakin gado ya iskota, har lokacin tana kuka kasa-kasa, kusa da ita ya je ya zauna tare da jawota jikinsa yana lallashinta, "Sorry my wife tashi ki shirya muje gidan Abbi mu ɗauko Aafia daga nan sai ki gaisa da Abbi, Aunty, yaya Irfan, bappa Maik, Kinji ko my pleasure?" Cikin dashashiyar muryar ta ce "Ni ba zan je ba kuma ka sake ni dan ina fushi da kai". Cikin sauri ya ɗago da haɓarta yana kallon face nata "My wife me nayi kika kike fushi da ni? Ni fa zan kai ki wajen su Abbi ne dan ki huce bakin cikin da kike a ciki". Kokarin tashi daga jikinsa ta yi tana faɗin "Akan me ɗazun zaka ɗauki Rimsha?". Ɗaure fuska sosai ya yi ya fara magana cike da izza "Kin taɓa ganin na taɓa taɓa jikin wata mace ce bayan ke da heartbeat?" Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a "To ba wai zan gaya maki ko ki yarda da ni ko akasin hakan bane, idan ma baki yarda ba ya rage naki, ni babu son wata a zuciyata sai ke, ni ban taɓa soyayya ba sai a kan ki, bayan ke kuma bana fatan na sake yin wani, ni ban ɗauki Rimsha da wata manufa ba fa ce bata a cikin hayyacinta, sannan kuma ina son ki zauna ki koyi yadda ake zama da miji, ni yau da za'a zo a gaya mani kin yi abu kaza, tofa ba zan tsaya bincike ko wani abin ba, idan kin yi nasani, idan ma baki yi ba na sani, wannan shine so na gaskiya, ka san iya adadin abin da masoyinka zai iya aikatawa da kuma wanda ba zai iya ba, ta yadda sharrin masharranta ba zai taɓa raba ku ba, baki cancanci zama masoyiya ta asaliba tun da baki san abun da zan iya yi da wanda ba zan iya yi ba" ya kai karshen maganar tare da miƙewa rai a ɓace ya nufi hanyar fita daga ɗakin. Da gudu ta miƙe ta faɗa zaman bayansa ta rungumo shi tana kara sakin wani kuka mai ban tausayi. Allah sarki zuciyoyin masoya, sai ya kasa cireta daga jikinsa, hasalima jiyowa ya yi, ya rungumeta sosai yana sauƙe ajiyar zuciya, ita ma ajiyar zuciya take sauƙewa tana kuka kasa-kasa. "Ya isa haka, ki yi shiru" ya yi maganar murya can kasa-kasa cike da so da kauna. Kara kankame shi tayi tana faɗin "Ina son ka yaya Akil, ka daina cewa ban cancanci zama masoyiya ta asali ba, zan iya mutuwa idan kana gaya mani hakan, kai baka sani ba saboda son da nake yi maka ne yasa nake kishinka, ina sonka mijina Allah ina sonka". "Baki sona My wife, da gaske baki so na" Duka ta kai mashi a kirjinsa tana kara sautin kukanta tana faɗin "Ina sonka wlh ina sonka" "Idan kina so na me yasa kike hanani hakkina? Me yasa? Tun rana ta farko ba ki sake yarda da ni ba, sai dai mu yi wasa kawai meyasa? Baki son haifa mani yara ne? Me na maki kike wahalar da ni ta wannan sigar?" Goga kanta ta fara yi a kirjinsa tana faɗin "Akwai zafi ne yaya Akil, Akwai zafi, ba wai bana son yara bane, ina so amma ba zan iya jurewa ba, akwai wahala". Bawan Allah bai damu ba sai ya rungumeta sosai a jikinsa dan yasan koma me shi ya ja, saboda dama duk yanayin da ka zo wa mace a rana ta farko, to a haka zata tafi, idan da karfi ka yi mata ya mata zafi, to a haka zata ɗauki abin har abada zata rinƙa jin da zafi kuma babu wani abin azo a gani, tun farko shi ya yi kuskure, shiyasa daga lokacin bai sake yi mata dole ba, ya barta sai ta buƙata da kanta, ya daure ya cigaba da azumi da sallar tsakiyar dare🤣 Kasa-kasa ya ce "Na sani My wife nasan ya maki zafi a rana ta farko amma ki sani ba zai kara yi maki zafi ba, ki natsu kuma ba zan takura maki ba har sai idan ke da kan ki kika bukata" ya kai karshen maganar tare da ɗaukarta cak suka haye gado yana goge mata hawaye yana rarrashin ta. (Nima na haɗa kayana dan naje na nemo masoyina James ko ya goge mani hawaye da bakin cikin rashin masoyi😭 sai mun haɗu Monday idan mai dukka ya kai mu a part ɗin su Rimsha Queen of beauty 🤨) 💖💖TRIPLETS💖💖 51-52 💖💖RIMSHA💖💖 Sai karfe 12 baiwar Allah nan ta iya tashi da ga barcin wahala da ya ɗauke ta, da kyar ta iya waro sleeping eyes nata da suka rine suka yi ja sosai saboda barci, ɗakin ta fara bi da kallo kamar bakuwa. Ta ɗan jima kwance ka fin nan ta yunkura da kyar ta miƙe zaune, gaba ɗaya jikinta ciwo yake yi ma ta, tamkar an yi mata ɗan iskan duka da itace, sai wani yauki take yi, tana haɗe gerar sama da ta kasa, nan take kuma zazzaɓi mai zafin gaske ya rufeta, wani irin sanyi mai ratsa kashi take ji yana ratsata, jan jikinta ta yi ta lallaɓa zuwa saman bed nata, haka ta kwanta tare da jawo bargo ta shige ciki. A wannan hali Imran ya shigo ɗakin ya sameta, yana shirye cikin wanda dakakkiyar shadda milk color, ɗinkin ta zauna mashi sosai a jikinsa, sai tashin kamshi yake yi, hannunsa na ruƙe da wayarsa da kuma key ɗin motarsa, zai ta fi neman Lion ne, domin tun safe yake kiran layinsa baya ɗauka, kuma wayar tana shiga, hakan ya sa ya shirya zuwa nemansa, dan bakonsa ne, kuma duk cikin abokansa ba wanda yake so biyun Lion, ya fi son shi fiye da kowa, sannan kuma saboda shi Lion ya sauƙa a Nigeria, ba dan shi ba da ba zai zo ba, hakan yasa ya zama mashi dole ya fita nemansa. Cikin sauri ya kariso cikin ɗakin ganinta a cikin bargo, bakin gadon ya zauna tare da yaye bargon yana faɗin "First lady lafiya kuwa?" Ta kasa magana hakwaranta sai garuwa da juna suke yi, saboda bala'in sanyi da take ji, ganin hakan yasa ya sanya hannunsa a saman kumatunta, jikin nata ya yi zafi jau kamar wuta. "Subhanallah" shine abin da ya iya furtawa tare da miƙewa a zafafe ya yaye mata bargon gaba ɗaya, tana cikin hijabin da ta yi sallah bata iya cirewa ba. Ɗan gyara hannun rigarsa ya yi ya ɗauketa cak suka nufi waje, ya zo zai fita palo kenan ita kuma Akila tana shigowa,. "Yaya Imran lafiya? Me yasa Meta? Ta yi maganar cike da nuna kulawa, kuma fuskarta ɗauke da tsantsan tausayi. "Heartbeat mu je ki buɗe maki kofar mota kin ji?" To ta amsa da shi tare da wucewa da sauri ta nufi parking space ɗin gidan, gidan baya ta buɗe mashi ya kwantar da ita sannan ya shiga gidan gaba da sauri. "Yaya Imran dan Allah zan biku " ta yi maganar idanunta cike tab da ruwan hawaye, gyaɗa mata kai kawai ya yi alamar to, da sauri ta shiga ta zauna a front seat. Da sauri ya figi motar, kafin su isa bakin gate mai gadi ya buɗe masu gate ɗin, a guje suka danna waje. Kai tsaye asibiti ya nufa, sai gudu yake shararawa, cikin ƙanƙanin lokaci suka isa Hospital ɗin, kasan cewar kuɗi na aiki, idan kana da kuɗi ba abin da ba za'a iya yi maka ba, kuma Dr Nawid yana nan, yau yana hospital ɗin, hakan yasa aka karɓi Rimsha hannu bibbiyu, cikin ƙanƙanin lokaci aka mata gwaje gwaje, da testses a kan me matsalar ta. Akila sarkin tausayi sai ruwan hawaye take yi, tun ma bata ji menene ke damun Rimsha ɗin ba, sai faman rarrashinta Imran yake yi. Sun kwashi almost awa ɗaya da rabi zaune a office ɗin Dr Nawid a yayin da ake bawa Rimsha taimakon gaggawa, a ɗaki na musamman. Sai da suka kara wajen minti talatin sannan Dr Nawid ya shigo bakin sa ɗauke da sallama, yana ƙoƙarin cire hand gloves dake a hannunsa, a lokacin Akila har ta yi barci kwance saman doguwar kujerar dake a cikin office ɗin, tasha kuka dan ita har ga Allah bata son ganin wani ɗan adam a cikin damuwa, tana da tausayi sosai da sosai, ga saurin kuka, da zarar ta ga abin tausayi zata fara ruwan hawaye, shiyasa ta yi wa Rimsha hawaye, kuma tana bala'in kaunar Rimsha sosai da sosai. Hannu Dr Nawid ya bawa Imran suka gaisa yana faɗin "Prof sannu da zama, na barku zaune ku kaɗai ko? Ga heartbeat har ta ga ji ta yi barci". Girgiza kai Imran ya yi yana faɗin "babu komai" yau kwata-kwata babu dariya a fuskar Imran ɗin ko kaɗan, abubuwan sun mashi yawa, ga tunanin ina Lion ya shiga, duk da ya san cewa ba wani wajen da ba haka zai je ba yananan, kawai yana son ganin shi ne dan wajensa ya zo, ga kuma rashin lafiyar Rimsha. "Dr meke damun sister na ne?" Yadda ya yi maganar kasan akwai damuwa a tattare da muryar tasa. Shiru Dr Nawid ya yi na ɗan lokacin kafin ya ce "Gaskiya Prof sister tana da matsala wadda idan ba'a yi kokarin wajen canza mata akala ba zata iya fuskantar barazana da rayuwarta" zaro ido sosai Imran ya yi yana faɗin "Me kake faɗe ne Dr? Please ka mani baya ni sosai da kyau dan in gane". Riƙo hannunsa Dr Nawid ya yi cike da sigar kwantar da hankalin ya fara magana "Prof ba wani abin bane, ciwon nata bai tsananta ba, amma idan har ba ku yi ƙoƙarin wajen ganin kun bata abin da take so bane, to za'a iya samun matsala, ciwon nata zai kara girma ta yadda zai iya huda mata zuciya". Tsare Dr da ido kawai Imran ya yi yana jiran cikakken bayanin menene asalin damuwarta. Cigaba da magana Dr ya yi "Imran akwai abin da sister take so, wadda ya tsaya mata a zuciya sosai, wannan shiya haifar mata da matsalar yawan razana rashin kuzari har ma da zazzaɓi, tana da damuwa sosai kuma ni ina ganin rashin yan uwan nan nata ne, yana da kyau ku ja ta ajiki sosai domin ku rage mata raɗaɗi, dan ma yarinyar tana da karfin imani sosai ba dan haka ba, idan wata ce wlh da mutuwa za ta yi, ba uwa, ba uba, ba yar uwa, kuma dukka lokacin guda, bayan kuma a baya a tare suke rayuwa, kai abin ba karamin abu bane, pls Prof ku ja ta ajiki, ku cire mata danuwa da tunanin da take a ciki, kada ku bari wani abu ya rinƙa razana ta ko tsorata, idan ba haka ba zata rinƙa yawan suma wadda hakan kuma zai iya taɓa kwakwalwarta, bayan haka kuma zai iya sawa ta yi paralyzed (palarais,) saboda yawan faɗuwa da zata rinƙa yi, duk wani abin da take so, dan Allah ku yi kokari ku bata shi da sauri, ni ba zan ɓoye maka ba Prof ina sonta, ina sonta fiye da son da nake yi wa Jehan, tun lokacin da na ganta na ji na fi sonta akan Jehan, idan ba damuwa zan so ka bani izinin in ɗan rinƙa kasancewa kusa da ita, domin na kara kwantar mata da hankali, a yanzu kai ne uwa kuma ubanta, so ina neman izini daga wajen ka dan neman soyayyarta" . To fa Babbar magana ga A'A SALAHUDDEEN ga kuma DR NAWID dukka kuma friend ya kuke ganin abin zai kasance? Kada kuma ku mance ita Lion take so. Allah sarki Imran shima a nashi tunanin rashin su mum ya sanya ta a damuwa haka, bai san da dakon soyayyar da ta yi na shakara 7 ba, basu kawo hakan a zuciyar su ba kwata-kwata, ba su ma taɓa tunanin tasan Lion ba, shi Nawid ya ga zanen da ta yi a kirjinta lokacin da yake dubata, sai dai ba dukkan zanne ya fito ba, ya so jan rigarta kasa kaɗan dan yaga zanen sai dai kasan cewar a lokacin idanunta biyu kuma son aure yake mata ya sa bai yi gigin yin hakan ba, dan saboda kada ta yi mashi mummunar fahimta, shiyasa sai ya bar zancen amma ya so ganin me ta rubuta a wajen, kuma ya yi alkawarin in dai ya samu dama sai ya gani. "Dr In Sha Allah zan yi kokarin ganin na sanya Rimsha farin ciki sosai, sai magana ta gaba kuma I knew kai mutumin kirki ne, idan har ka iya samun soyayyar Rimsha to wlh ko da iyayenta sun bayyana zan tsaya maka, duk abin da zai sanya ta farin ciki ina maraba da shi a Yanzu, dan haka idan har Rimsha zata yi farin cikin kasancewa da kai, to ina maraba da kai, duk lokacin da ka zo gida zaka samu ganinta, all the best my dear" ya kai karshen maganar tare da miƙawa Dr hannun, miƙo mashi shima Dr ya yi suka bugi juna kamar yadda suka saba lokacin suna primary school. "Amma Dr ba wani magani ko wani allura da za ku bata ne?" Cikin sauri Dr ya ce "Akwai sosai ma, yanzu ma na ɗaura mata karin ruwa domin akwai maleria a jikinta sosai, ina ga gidan da ta zaunan nan sauro sun taɓata, amma zamu yi treatment yanzu kuwa". Imran zai sake magana wayarsa dake a cikin aljihunsa ta fara kara. Cikin sauri ya ciro wayar tare da bin screen ɗin da kallo, dan a tunaninsa Lion ne. A'A SALAHUDDEEN shine sunan da ya bayyana akan screen ɗin wayar, murmushi ya yi kafin ya ce "Dr ga mutumin yana kira, shima yana fama da halin da muke cikin, wato soyayya, Allah dai ya fitar da mu lafiya" ya kai karshen maganar tare da yin picking call ɗin. Tun bai yi magana ba Ahmad ya riga shi da cewa "Yau ba ko sallama dan Allah Prof ka tashi zuwa Katsina ka je ka duba mani Queen of beauty ko tana lafiya ne, tun jiya bata ɗaukar wayata, ina ji a jikina wlh bata da lafiya, zan yi ta ƙoƙarin kiranta da ta ɗauka zan tambayi address kawai na turoma ka je ka gan mim ita ka jimin meke faruwa ne". Yar dariya Imran ya yi kafin ya ce "Kai AA wlh baka da damuwa, ta ya za'a yi ka bari son macen da baka da tabbacin zaka sameta, ka bari ya shiga zuciyarka da kallon ɗaya haka? Bafa kasan wacece ita ba, wata kila ma matar aure ce, duk baka yi tunanin hakan ba, kai dai kawai daga ganin kyakkyawa, baka san halinta ya yake ba, to ni wai a ina ma ka haɗu da ita ne? A Abuja ko ina? Ni dai ba zan fasa gaya maka ba, ka rabu da ita, ka kama dahir, dama nace idan ka rabu da ita sai na baka number kanwata first lady ku kulla soyayya, to ita ma na mata miji yanzu nan, sai dai na baka heartbeat, ita ma idan ka yi wasa Irfar zai maka kafa dan naga kwana biyun nan sai wani tambaya ta yake yi ya take kamar bai san Hanyar in da take ba, jiya ma har da cewa na bashi number ta, to gara ka yi sauri ka kama dahir". Ya kai karshen maganar yana murmushin shakiyanci shida Nawid sai ɗaga gera suke suna guntse dariya, domin duk abinda Ahmad yake faɗe, Nawid na jin shi, Imran ya kure Volume na wayar. "Kai Prof wlh bana son iskanci, kuna tare da Dr ko? To wlh ku fita ido na, nabi first lady da kuma heartbeat da gudu, ku baku san zafin so bane wlh, da kun sani da ba zaku ce na rabu da wadda zuciyata ke muradi ba, kun sani ni ban taɓa soyayya ba sai akanta, ko irin soyayyar secondary da ake yi ma ni ban yi ba, a kanta na fara sanin menene so, to dan Allah ku taimaka mani kada na mutu kun ji good friends my bloods". Dariyar da suke guntsewa ne suka tuntsure da shi, cike da shakiyanci Imran ya ce "Kawai ka hakura ka cigaba da shan lemon tsami" Nawid ne ya kai mashi duka a baya suka sake kwashewa da dariyar iskanci. Ji Ahmad yake yi tamkar ya shaƙosu dan haushi, yana gaya masu damuwarsa suna mai da shi ɗan iska, suna mashi dariya. "Wai me haka ne Prof? Ni na ce maku auren rage zafi zan yi ne? Son ta fa da gaske nake yi, haba mana bai kamata ku mani haka ba" ya yi maganar kamar zai saka ihu dan haushi. Tsagaita dariyar Imran ya yi yana faɗin "Wai ka mance lokacin da nake gaya maka matar da zan aura kuma jinina ta ɓata ne? Ka manta me ka rinƙa yi Mani? Ina a nan ka ce mani wai sai na hakura na koma shan lemon tsami shine nima nake mai da maka da abin da ka rinƙa yi Mani". Shi dai Nawid ɗan gulma sai murmushi yake yi yana jinsu, dan in dai irin wannan iskancin ne sun saba, da A'A da Imran, a baya idan Imran yana bashi labarin Jelly'n sa sai AA ya rinƙa cewa shi wlh bai ga macen da zai so ba a duniyar nan, shi yafi karfin ya ce wa mace yana sonta, sai dai ita ta ce tana son shi, ba kalar tsiyar da ba su yi wa Imran ba a lokacin, har ce mashi suke zai daina shan lemon tsami kenan, idan ya ce masu dama shi baya sha, sai A'A ya ce to idan baya sha meyasa zai yi aure, ba ya ga ji ne da danne abin ba, su yi ta dariya suna mashi tsiya, idan ya gaji ne sai ya tashi ya fita ya basu waje, to suma yau Allah ya kama su, kuma dukkansu akan mace ɗaya, ya kuke ganin wannan abota ta su za ta kasance? Kada ku mance abokaine tun na yaranta, tare suka yi primary school zuwa secondary daga nan suka rabu, Imran ya bar kasar, bayan wani ɗan lokacin suka sake haɗuwa shi da AA Salahuddeen a Harvard University, shi kuma Nawid a India ya karisa karatunsa, sai bayan sun dawo Nigeria suka sake haɗewa, dan dama already sun san gidajen juna, ba jimawa kuma Imran ya sake komawa dan yin degree ɗin sa ta biyu, dukka a Harvard University, shi kuma A'A England ya wuce, suka sake rabuwa, amma kullun suna waya da juna, suna matuƙar kaunar juna. Tsuke fuskar Ahmad ya yi ya ce "Haba Prof ka ajiye duk abin da ya wuce, yanzu dai ka fuskanci matsalata dan Allah" jinjina kai Imran ya yi yana faɗin "Tom Shikenan yanzu dai ka bari sai ka zo ɗin, ni yanzu ina sauri ne kasan GAR ya zo Naija, to kuma ba sai na gaya maka ba, ka dai san halinsa, wlh tun jiya ya fita gida wai gidan bata yi mashi ba, ni bansan ina ya tafi ba, so zan je duba shi ne". "What!!!" Nawid da Ahmad suka furta a tare, tare da miƙewa tsaye kamar suna a waje guda, kamar kuma abin haɗin baki. Shi dai Nawid a Tv ya san GAR sai kuma ya taɓa ganinsa sau ɗaya da ya kaiwa Imran ziyara, lokacin yana degree ɗin sa ta biyu, shi kuma A'A SALAHUDDEEN makaranta ɗaya suka yi karatu. "Kwairai kuwa GAR a Nigeria ni kai na lokacin da ya kirani ya ce mani zai shigo Nigeria karfe 3, wlh ba karamin shock na yi ba, ba don na mashi farin sanin cewa baya faɗan abin da ba haka ba, kuma bamu wasa a lamarin sa ba, wlh da na ce ba haka bane ko kuma wasa yake yi Mani, amma da yake shi dai kunsan magana ɗaya yake yi, kuma ba wasa a lamuransa ko kaɗan shiyasa ma na yarda, karfe 3 kuwa sai ga jirginsu ya sauƙa lokacin kuma already ina airport ɗin, har yau mamakin abin bai sake ni ba, duk da na ganshi da idona ni na ɗauke shi zuwa gida, kuma na san me ya zo yi, amma wlh har yanzu ina mamaki ina ganin abin kamar a mafarki ne". Ahmad murya har wani watsakewa ta yi nan take ya koma normal da sauri ya ce "Kai gaskiya Prof ka ciri tuta, har muka gama school guy nan bai taɓa daga ido ya kalle ni ba, ban san ya akayi kai yake son ka ba, kuma duk lokacin muna tare, zai zauna da kai tare, amma da zarar munzo mun same ku kuna zaune zai tashi ya bamu waje, ban san me yasa ba, kuma wlh ina masifar kaunar guy ɗin, ko sau ɗaya bai taɓa yi mani magana ba, duk da cewa kai ma ba magana ya cika yi da kai ba, amma dai yana zama da kai waje guda, dan Allah Imran a wannan lokaci ka saka baki mu zauna da shi, ko sau ɗaya ne mu yi magana". Dogon numfashi Imran ya ja tare da sauƙewa a hankali. Cike da damuwa ya ce "A'A a baya ma Saif bai tsaya ya yi magana da ku ba bare kuma yanzu da yake babban soja? Kada ka mance a baya fa lokacin bai kai haka ba amma yana da bala'in izza ina ga kuma yanzu? To wlh a yanzu izza da miskilancin Lion ta ci uban na da, ni ma ina da tabbacin Allah ne kawai ya jarabce shi da kaunata, da ya rabu da ni, kuma abin da ya sanya ni na musultat da shi, so yanzu ya san yana kan hanya ma daidaiciya kaga kuwa ba zai taɓa mantawa da ni ba, domin ni na nuna mashi daidaitacciyar hanya, ina ga wannan dalili yasa ma Allah ya jarabce shi da kaunata, kuma yasa har yanzu bai dai na kula ni ba, sannan kuma abin da ba ka sani ba game da Lion, wlh duk kansu har Michael suna da zuciya mai kyau, ba su mance alkhari, kawai dai dan suna kafurai ne, shiyasa ba zaka yi zaton hakan ba, amma ba dan haka ba suna da zuciyoyi masu kyau, musamman ma James yana da kirki sosai, shi Lion ne dama ya fisu taurin zuciya, amma shima lokacin ɗaya daɗin kira'ar Alqur'ani mai girma da nake yawan yi a school Allah yasa ya ja hankalinsa ya yadda da Ni, so ni yanzu wlh ba zan iya tinkararsa in ce kana son yin magana da shi ba gaskiya, saboda na san ma ba zai yi wu ba, kawai ka yi hakuri, ni yanzu zan tafi za mu yi waya idan na isa gida". Daga nan suka yi sallama ya kashe wayar jiki a mace. Sai mamaki da al'ajabi tare da jimami Nawid ya ke yi, wai GAR ne a Nigeria. Taɓa shi Imran ya yi, yar firgita ya yi tare da dawo da kallonsa kan Imran ɗin, a hankali ya koma ya zauna saman chair nasa yana faɗin "Dan girman Allah Prof ka taimaka ka haɗa ni da shi, ko hoto mu ɗauka" Shiru Imran ya yi yana tunanin taya zai fara tinkarar Lion da zancen, domin ya san halin kayansa, ba yau suke tare ba, Allah ne kuma ya haɗa zuciyoyinsu, Allah ne ya kaddara wa Lion Kaunar Imran ta sanadiyar kira'ar Alqur'ani mai girma da yake yawan zama yana yi a Library su, shi kuma Lion yana zama karatun a wajen, daga haka suka haɗu, daga haka Alqur'ani mai girma ta fara shiga zuciyarsa har ya ji yana son karantata, bai karɓi Addinin Musulunci ba har sai da ya samu ilimi mai zurfin gaske dan gane da addinin, sai da ya yi haddar Alkur'ani mai girma sannan ya haddace manya-manyan daga cikin littafan musulunci, ya jima yana nazari akan addinan guda biyu domin ya tantance ta gaskiya, baya yanke hukunci haka kawai da ka, sai ya yi nazari da bincike, wannan dalili yasa, ya samu ilimi sosai akan musulci haka akan kiristanci, daga karshene ya yanke wa kansa hukuncin da ta dace da shi, ya karɓi Addinin Musulunci bayan ya gano cewa ita ce ta gaskiya, amma bai wani jima da musulta ba, ya dai ɗan jima da fara bincike a kan addinan guda biyu. Story💖 "Nawid duk da nasan Lion yana kaunata ba zan iya tinkararsa da maganar ba, saboda na san ba zai yi ba, idan baka sani ba ma yau ka sani familynsu gaba ɗaya basa son mutane ko kaɗan, ka taɓa ganinsa tare da wani ko a Tv ne bayan James ko Michael?" Girgiza kai Nawid ya yi alamar a'a "To ka gani, amma dai In Sha Allah zan yi ƙoƙarin ko da da idone ka ganshi kafin ya koma" to Nawid ya amsa mashi da shi tare da zuba mashi ruwan godiya sannan suka yi musabaha Imran ya miƙe ya nufi in da Akila ke kwance yana faɗin "Za mu iya wucewa da sister yanzu ne?" "A'a Prof na yi mata karin ruwa, sai dai zuwa yamma irin karfe 4 haka" To Imran ya amsa da shi tare da tashin Akila daga barci a kan su tafi, nan fa ta ce a'a ita kam zata zauna da Rimsha gaskiya, ba dan ya so ba haka ya wuce shi kaɗai ya barsu amana a hannun Nawid ya tafi neman Lion. Yana tuki yana tunanin ai na zai fara neman Lion ne ma wai, dan dai yasan bai koma ba yana nan Nigeria, sai ya wo yake yi da motarsa bai san ina ya nufa ba, wata hanyarma sau biyu yana kewaya wa ya sake kewayowa, duk ba tare da ya sani ba, hankalinsa na can cikin tunani. Wayarsa da ke a zaune a gefensa ne ta ɗan yi kara alamar shigowar saƙo, cikin sauri ya ɗauki wayar, ganin sunan Saif ya sa ya gangara gefen titi ya tsai da motar. Buɗe massage ɗin ya yi ya fara karantawa, address ne a rubuce a jiki tare da faɗin kasame ni yanzu, jinjina kai Imran ya yi yana faɗin Alhadulillah a ransa. Cikin sauri ya juya kan motar ya nufi wannan address ɗin. 💖UNGUWAR ISHAKU ROAD💖 Tampatsetsen gida ne na gani a faɗa, hawa ɗaya ne, irin dai manya-manyan gine-ginen na nan Naija, gaba ɗaya komai dake a cikin gidan daga waje a ka shigo da su, ginin ya tsaru sosai, irin gidan nan ne da akeyi a shirya komai su Furnitures da komai sai a sai da haka, to shine, sai mamaki Imran ya ke yi, yaushe Lion kuma ya san Nigeria har ya iya zuwa ya sayi gidan nan? Yana ta tunani har ya iso bakin gate ɗin, horn ɗaya ya yi, da ya ga ba a buɗe mashi ba sai ya san e lallai babu mai gadi, hakan yasa ya fito da kansa ya shiga cikin gidan, ya wangalewa kansa katafaren gate. Bayan ya buɗe sai ya dawo ya shiga motarsa ya ja izuwa cikin gida, tsayawa zayyana maku yadda kawatuwan cikin gidan nan ya yi zai cinye mana ɗan sauran filin dake a gare mu, ku kawata yadda manya-manyan gine-ginen mu suke a ranku. Kai tsaye parking space ya wuce, bayan ya kashe motar ne ya fito ya nufi tampatsetsen kofar da zata sadaka da cikin palon, daidai zai shiga kamar an ce ya ɗago kai sama, can ya hango Lion tsaye a balcony daga shi sai Short a jikinsa, dama Imran ya san halinsa akwai shi da san tsayuwa a balcony yana kallon yanayin gari daga ta sama. Shiru ya ɗan tsaya yana tunanin ko dai ya koma ya kwaso mashi kayan sa ne, dan yadda ya ganshi da short ɗin nan ya san ya yi wanka ne, kuma ba zai iya mai da kayan da ya cire ba, kayan da ya zo da su kuma suna gidan su Imran ɗin, da alama kuma bai fita ya sai wasu kayan ba, ba karamin aikin shi bane yanzu ya ce kayan Nigeria ba su yi mashi ba, duk da cewa rabi da kwatan kayan Nigeria ma daga waje ake shigo da su. Ganin ba abin da tsayuwa zata kara mashi ne yasa ya shige cikin gidan kawai yana duba time a agogon hannunsa. 1:30 lokacin sallar azahar ta yi. Wow gaskiya palon kasar nan ta haɗu sosai, kusan komai na cikin palon fari ne da ash color, sai tashin kamshi perfume ɗin jikin Lion take yi, da alama ya ɗan zauna a palon, gaba ɗaya furnitures dake a cikin palon set biyu suna cikin ledojinsu ba'a ɓuɗe su ba, komai tsab-tsab da yake sabbine, kuma sai da aka share aka gyara mashi komai kafin ya shiga ya zauna. Abin da ya faru bayan ya baro gidan su Imran, kai tsaye bakin titi ya wuce, a nan ne ya tsaya ya kira kakansa a waya a kan ya kira President na Nigeria yana buƙatar number dillalai masu dillancin gidaje, His Excellency ya tambaye shi me kuma haɗin sa da Nigeria, nan ya ce da His Excellency Nigeria ya zo, sosai His Excellency ya yi mamaki sannan ya ɗaura da cewa to ya sauƙa a gidan Gwamnati mana, a'a ya ce baya buƙata domin aikin sirri ya zo yi, shi kawai number yake buƙata, ba tare da ɓata lokaci ba aka fara aiki a kai, cikin kankanin lokaci kakansa ya gama komai, har in da yake dillalan suka zo da motarsu suka same shi, bayan ya turawa kakansa address ɗin wajen ta hanyar tambayar sunan wajen. Kin shiga motar ya yi ya ce ba ta yi mashi ba, nan ma sai da His Excellency ya sa aka tura mashi wata dankareriyar mota daga gidan gwamnan Kaduna, su dai sai karɓar umarni suke da sun tambayi waye ne sai ace ba ruwansu. *Abun ku da kuɗi da kuma karfin mulki, kada ku mance Nigeria dai a kasan Usa take, dama kullun sai yadda suka yi da mu😭 su mulki kasarsu kuma su kulkemu, abin da suke so shi ya zama dole gwamnatin mu ta yi😭 hakan yasa a cikin wannan dare a ka yi wa Lion komai dan dole.* To daga nan ne suka wuce ya je ya ga gida je, wajen gidaje biyar aka nuna mashi, duk ya ce basu yi mashi ba, da kyar ya karɓi wannan gidan, ita ma lallaɓawa kawai yake yi ba wai dan ta yi mashi ba, haka dillalan suka saka yaransu suka share mashi ko'ina aka gyare tsab, ya shige, kuma har suka gama aikin ba wanda ya samu damar sanin wanene shi, saboda akwai face mask a fuskarsa, kuma ma bai tsaye a in da suke ba. Wannan shine abin da ya faru Mu koma kan story. 💖Imran💖 kai tsaye staircase ɗin ya nufa yana sauri sosai. Da sallama ɗauke a bakinsa ya shiga palon saman, ɗakuna uku ne a cikin palon, tunanin ta balcony da ya hango Lion ya yi, daddɗar Kamshin perfume ɗin Lion ɗin ne ta isar mashi da sakon ga ta in da Lion ɗin yake, cikin sauri ya nufi in da kamshin ta fi yawa, yana tafiya yana jinjinawa karfin perfume ɗin nan, domin kwata-kwata yau Lion bai sanyata a jikinsa ba, saboda ya baro ta a gidan su Imran ɗin, tun wadda ya sanya jiya ne ta bule gidan da daɗin kamshi. Sallama ya mashi kafin ya shiga cikin ɗakin, kai tsaye balcony ya nufa, Lion na tsaye, yana kallon birnin Kaduna, kyakkyawar halittar jikin nan nasa a waje, dan short ɗin nasa ma, iya rabin cinyarsa ta tsaya mashi, subhanallah kyawun ainahin surar Lion ba zata iya zayyanuwa a baki ba, saboda ta wuci baki ya faɗe ta, sai wanda dai ya gani a zahiri, soft skin ɗin nan nasa sai wani kyalli na musamman yake yi, ga bala'i laushi kamar bai taɓa fita waje ba, kamar fatar jariri, wannan kwantacen bakin gashi siɗif ɗin dake kwance a saman cinyoyinsa da hannayensa, ba karamin kyau ta yi ba, ga wani gashin a kwance a buɗaɗen faffaɗar kirjinsa, damatsan hannunsa kuma ba'a magana sai wanda ya gani, kallon kasa yake yi wa garin Kaduna, irin mutun ya sunkuyar da kansa kasa ya kuma ɗaga idanuwansa yana kallon waje, to haka ya yi shima, Imran yana zuwa ya miƙa mashi hannu dan su gaisa, ba tare da ya kalle shi ba ya miƙo mashi nasa hannun suka gaisa. Shiru suka tsaye kamar kurame, wayar Lion dake a cikin ɗakin ne ta fara kara tana kira mashi number mai kiransa tare da suna da location, Imran na kokarin zuwa ya ɗauko mashi wayar, ya dakatar da shi ta hanyar ɗaga mashi hannu alamar baya buƙata, bari Imran ya yi suka ci-gaba da tsayuwa shiru. Kira ta farko ta yanke ta biyu ta shigo, ita ma ta yanke sai a karon na uku ne ya juya a nutse ya nufi cikin bedroom ɗin, girgiza kai Imran ya yi yana addu'ar Allah ya shirya mashi Lion, wato haka ya ke yi shiyasa su yi ta kiran shi baya ɗagawa, sai lokacin da ya ga dama sai ya kira su. Lion duniya Yana zuwa ya duba wayar Tyrone ne ke kiransa, picking ya yi tare da kara wayar a kunnansa ba tare da ya yi magana ba, ya zauna a saman gefen katafaren gadon dake a cikin ɗakin. Ya ɗauki good 5mins wayar na kunnansa bai yi magana ba, da alama yana sauraron abin da Tyrone ɗin yake faɗe ne, a haka ya sake kara 2mins sannan ya cire wayar daga kunnansa ba tare da ya yi magana ba ya katse kirar, daidai lokacin Imran ya kariso cikin ɗakin. Saman bedside drawer ya zauna yana faɗin "Ya akayi ka samu wannan gidan a cikin daren da ka fita?" Shiru ya yi yana rubutu a wayarsa, da alama sako zai tura. "Saif ka yi breakfast kuwa?" Sai lokacin ya ɗago da kallonsa a kan fuskar Imran ɗin, kallo ɗaya ya yi mashi wadda bata fi second 2 ba, ya kawar da kallon nasa izuwa kan wayarsa. "What is wrong with you Prof?" Shine abin da ya furta cikin sanyin murya, ajiyar zuciya Imran ya sauƙe tare da jan numfashi, dama yasan da kallo ɗaya Lion zai gane yana da damuwa, dan shi haka yake kawai bala'in kaifin kwakwalwa, da gane abu cikin ƙanƙanin lokaci. "Amana ta ce bata da lafiya shiyasa, bana cikin mood". Daga nan bai sake magana ba shima Imran ɗin bai sake yin wata magana ba, tsawon minti 20 a haka sannan Lion ya fara magana cikin sanyin murya. "Gaskiya Prof ban taɓa jinjinawa ko wace kasa ba bayar tamu, amma a yau na jinjinawa Nigeria da yan cikinta". *Ni ko nace ba dole ka jinjina mana ba, ai mu saboda baiwar mu ba kalar iskancin da ba mu iya ba, idan musulci ne to mun fi kowa, haka tsiya da kaifin ƙwaƙwalwa, basira, son Allah da annabi, zalunci, ta'addancin, taimakon wata ƙasa, mu bada rayukanmu kan taimakon abin da ma bai shafemu ba, bayan ga matsala a cike a kasarmu, mun kasa kula da ita dan warwareta, sai shiga harkar da ba tamu ba, kai mu fa idan aka mana tsiya har president bamu kyalewa zage shi muke yi fes, kuma haka idan muka zage shi zai sa a nemo mu a duk in da muke, a kamo mu a ladabtar da mu, amma an kasa neman in da bandits suke a kwamuso su😭 a mana maganin su, anya wannan abin?, a Nigeria ne aka je gasar karatun Alkur'ani mai girma ɗan Nigeria ya buge manya-manyan larabawa ya ɗauko mana first ya dawo mana da ita, mu baiwar mu wlh ta wuce misali, a Nigeria ne zakaga an taɓa annabi musulmi sun fita a guje kamar mahaukata, amma hauka na son manzon Allah, a Nigeria ne zaka ga ɗan bandits ya shigo gida ya ce maka ka fita zai yi amfani da gidan, a Nigeria yan bandits suna da damar rike bindiga su kashe al'umma, amma kuma al'umma basu da damar riƙe bindiga ko wani makami dan su kare rayukansu da dukiyoyinsu, ƴaƴa da matansu😭, kai mu fa baiwar mu bata faɗuwa da baki, sai dai Allah ya mana Albarka kawai, amma ko mai muka ce za muyi, to mune a kan gaba, am proud to be Nigerian💪* Story Yar dariya Imran ya yi kafin ya ce "E haka ne gaskiya akasar mu babu abin da bamu da shi, ta ko wani ɓangare mun haɗa". Shiru ya ɗan yi kamar mai nazarin wani abin, still har lokacin hanunsa na a kan wayarsa yana typing. "Saif lafiya? Tunanin me kake yi?". Ya ɗan ɗauki lokaci kafin, ya fara magana gently "Da mutanen Nigeria za su samu wasu abubuwa kamar su kula da sauransu, da kasar ku sai ta zama ta farko a duniya, ban taɓa ganin mutane irin yan Nigeria ba, gaskiya karo na farko da abu ya taɓa burgeni a rayuwata shine yan Nigeria, amma to meyasa duk da tarin wannan ilimi da basira da kuke da shi baku amfani da shi?". Mamaki ne ya kama Imran, tunani ya shiga yi me Lion ya gani a Nigeria da har yasa yake yabon yan cikinta haka?. "Saif amma me yasa kake yabon yan Nigeria har haka? Tun da nake da kai ban taɓa jin ka ce ga abu ya yi maka kyau ba, sai yau, to why?" . Ajiye wayarsa ya yi a gefensa, da alama ya gama abin da yake yi, "Ba iya burgeni kuka yi ba, har da ɗan mamaki kuka bani". Jin abin Imran ya ke tamkar mafarki, wai yau Lion ne ya ce abu ya burge shi kai, ya zama dole mu san menene yan Nigeria suka yi haka wanda ya birge shi. "Dan Allah Saif tell me now, am desprate to hear abin da Nigerians suka yi maka, har ya birgeka haka". "Abin da ya sa Nigerians suka birgeni shine, James ya tsallake kasashe da dama, ya yi ta'addanci da yan ta'adda da dama, kungiyar da ya shiga ta sanya shi ya kashe yan ta'addan kasashe da dama, Dubai, India, Spain, England, Usa, duk ya shiga har cikin yan ta'addan su ya kashe wanda aka turoshi ya kashe, babu wata kasa da ta iya kamashi sai yan Nigeria, Nigerians akwai brain sosai fiye da tunanin mai tunani, abinciken da na yi jiya da daddare, ba karamin birgeni Nigerians suka yi ba, lokaci guda suka kama James wow". Cikin sauri Imran ya ce "Kana nufin ka gano a in da James yake ne?" Jinjina Mashi kai kawai ya yi alamar e ya gano ba tare da ya yi magana ba. Tsabar murna miƙewa tsaye Imran ya yi ya fuskanci gaban ya yi sujudur shukur dan godiya ga Ubangiji, da kuma taya aminin nasa murna, domin James ma babban abokinsa ne. (Masoya James Lion ya gano a in da yake, ko wani hukunci kuma zai yanke mashi?🤔😭) Bayan ya ɗago daga sujjadar ne ya ɗaga hannu ya rinƙa zubawa Allah kirari tare da godiya mai tarin yawa, sannan cikin zumuɗi ya ce "Saif yau she zaka ta fi ɗauko shi?". Girgiza kai ya ɗan yi kafin ya ce "Ba in da zan je ni, su Tyrone za su yi aiki, idan sun gama kashe yan ta'addan zan je na ɗauki James ɗin". "To dan Allah Saif kada ka yi wa James hukunci mai tsanani, ko iya wahalar da ya shama ka barshi a haka". Shiru Lion ya yi bai sake yin magana ba, jin ya yi shiru Imran ya san ba makawa kenan sai ya hukunta James, duk sai ya ji jikinsa ta yi sanyi, kansa har wani sara mashi ta fara yi, yana matuƙar kaunar James sosai da sosai. Jiki ba kwari ya kiƙe ya shiga toilet ya ɗauro alwala dan gabatar da sallar azahar, shi Lion already ya yi sallar tun karfe ɗaya,. Allah sarki Imran gaba ɗaya jikinsa ya saki lokaci guda, har wani zufa ke ta faman tsastsafo mashi daga gefe da gefen fuskarsa. Bayan ya yi alwala ya fito ya tsaya a tsakiyar ɗakin yana faɗin "Saif dame ka yi sallah? Dan dai nasan already ka yi sallah" Da hannu Lion ya nuna mashi wata kyakkyawar labule dake kusa da kofar toilet ɗin ba tare da ya yi magana ba. Yana ƙoƙarin juyawa izuwa wajen labulen kawai idanuwansa suka sauƙa saman mirror dake a cikin ɗakin, gaba ɗaya Mirror shaƙe yake da mayunka Lion da ya saba shafawa, ga su perfume nasa air freshener da sauransu, mamaki ne ya kama Imran daga ina wayan nan abubuwa kuma suka fito. Bai gama rikicewa da mamaki ba ma, sai da ya buɗe wannan kyakkyawar labule fari tas da Lion ya nuna mashi, yana yaye labulen wani irin kyakkyawan dressing room ne ya bayyana a wajen, da glass aka yi dressing room ɗin, kusan dai irin dressing room nasa na Washington DC, cike da mamaki ya karisa ciki, abin mamaki kaya ne shaƙe a cikin, duk kuma kayan sabbine bama a ciresu a ledarsu ba, kenan saya ya yi? Ko dai daga Usa aka zuba su a jirgi ta kawo mashi? Abin mamaki dai baya karewa a tattare da Lion, kullum cikin saka mutane mamaki yake yi. Dadduma ya zaro sai tashin fitinannen daddaɗar kamshi kayan cikin drawer suke yi, da alama sun sha perfume sun ƙoshi, shi ma daddumar sai kamshi yake yi sosai, ga shi da laushi kamar jikin bargo, fari tas, komai na Lion fari ne tas, yana son white color over. Shifiɗa daddumar ya yi tare da gyara tsayuwa ya tada kabbara ya fara sallah. Lion na zaune yana ganinsa har ya idar, ya zauna a saman daddumar ya yi askar tare da addu'ar Allah ya dawo mashi da jelly sa, Allah kuma yasa kada Lion ya yi wa James hukunci mai tsanani. Da haka ya shafa addu'ar tasa ya miƙe yana faɗin "Saif zan je hospital daga nan zan wuce gida sai da daddare zan shigo mu gaisa, amma kafin nan zan kawo maka kayan sawan ka". Ya karisa maganar yana jiran amsar Lion ɗin. "No Professor I want you to stay with me here before na koma" ya yi maganar a nutse kuma ba tare da ya kalli Imran ɗin ba. Dama already Imran yasan hakan zata faru domin Triplets a tare suka saba rayuwa, duk da cewa Lion baya wani shigarsu sosai, ma'ana baya zama da su sosai su yi hira, amma fa ko ina da wuya ka ga ɗaya baka ga ɗaya ba, ba zai iya zama a cikin wannan gida shi kaɗai ba, ba Michael ba kuma James, abin ya mashi yawa, akwai wuyar zama, sannan kuma ba kasar su ba, zama ba tare da su Michael ba zai mashi matukar wahala. "Saif i can't stay here without my Sister, ita ɗin amana ta ce, Ammie ba ta son ta zauna a gidan mu, kuma bata da kowa, ni kaɗai ke a gareta, kuma yanzu haka da nake maka magana ita zan je dubawa a hospital bata da lifiya, Dr ya ce tana buƙatar kulawata sosai, ba zan iya yin nisa da ita ko na minti ashirin ba, idan zan zauna a nan to dole da ita zan zauna....." Bai kai karshen maganar ba ya Katse shi ta hanyar ɗaga mashi hannun, sannan gently ya ce "Idan kuma na ce ina son ka zauna a nan ɗin ba tare da ita ɗin ba fa?". Wani dum-dum Imran ya ji gaban sa ta faɗi domin ya san halin Lion tsab zai iya sawa dole ya baro Rimsha a gidansu, shi kuma ya zo nan su zauna, idan hakan ta faru kuma to ba zai taɓa samun kwanciyar hankali ba, babban abin da ya kara ɗaga mashi hankali shime Dr ya ce Rimsha na matuƙar buƙatar kulawa, kada a barta ita kaɗai a gida, cos abin ya taɓa shi sosai. Tsabar shiga damuwa da tashin hankali har wani zufa ne ya fara tsastsafo mashi daga gefe da gefen fuskarsa, yana son ramawa daddyn Rimsha alkhari da ya yi masu ta hanyar kula da Rimsha da dukkannin lokacinsa, amma Lion na ƙoƙarin dakatar da shi. Dafe kansa ya yi, ga shi kuma ba halin ya ce da Lion ya yi hakuri, domin baya son kalmar sorry ko kaɗan, idan ma ya ce mashi sorry to suna iya samun babbar matsala. "30mins sun isheka ka yi anything da kake so, daga gidan ku zuwa nan" ya kai karshen maganar yana ɗago da kallonsa a kan fuskar Imran ɗin, jinjina mashi kai Imran ya yi alamar to, sannan ya ɗaura da ce wa "In Sha Allah". Shiru Lion bai sake yin magana ba, shi kuma bawan Allah Imran haka ya sa kai ya fice daga cikin ɗakin zuciyarsa cike da ciwo da kuma kunan sosai, yanzu haka zai bar Rimsha a gidansu, wlh ba zan taɓa samun kwanciyar hankali ba, domin Ammie bata son ta, yanzu bata san da zamanta a gidan bane, idan da ta sani ba zata taɓa barinta ta zauna ba, yanzu idan ya dawo wajen Lion wani abin ya faru da ita fa? Ya zai yi kenan? Bai cika amana ba gaskiya, ko dai in kai ta Maiduguri wajen Hajiya Batula ne? Ya tambayi kansa yana ƙoƙarin shiga motarsa, "No ba zan iya kai ta Maiduguri ba gaskiya ya yi nisa, to ko dai na kaita wajen Ummin Dr ne?" Nan ma sake girgiza kai ya yi alamar a'a ba zai iya yin hakan ba saboda baya son ta yi nisa da shi, kuma Dr Nawid yana son ta, zamansu waje ɗaya ba alkhari bane, domin duk yadda namiji ya kai ga son mace, komai hankalinsa da ilimin sa da natsuwarsa zaman su a wajen guda ba'a yi aure ba, ba babbar haɗari ne, kuma ba alkhari bane, saboda akwai shaiɗan yana tsaye daga gefe yana kula da komai, hakan yasa Imran ya fasa shawarar ya kai ta can. Yana ta tuki yana tunani har ya isa asibiti. Lokacin da ya shiga ɗakin ta farfaɗo ga ruwan da aka sanya mata ma ya kusa karewa, sannu ya yi mata tare da zama gefenta ya riƙo hannunta ɗaya, cikin murya irin wadda ake yiwa yara rarrashi ya fata magana, Akila na zaune saman kujerar dake a wajen tana jinsu. "Rimsha dan Allah kada ki ɓoye mani, ki faɗa mani menene yake damunki da har ya sanya ki a cikin wannan hali? Kina kewar su mum ne? Ko akwai wani abin bayan hakan?" Kasa ta yi da kanta, cikin natsuwa ta ce "Yaya Imran wlh ni ma ban sani ba" shiru ya yi yana nazarinta, Akila ce ta katse mashi shirun da cewa "Yaya Imran me yake damunta?". Girgiza kai ya yi yana faɗin "Ba komai heartbeat yanzu dai bari na kila Akil in gaya mashi idan karfe 4 tayi ya zo ya ɗauke ku zuwa gida" To Akila ta ce mashi. Ciro wayarsa ya yi ya fara kiran layin Akil ɗin, wayar ta yi ringin har ta yanke bai ɗauka ba, sake kira ya yi, wayar na gab da katsewa sannan ya ɗauka. Muryarsa cike da mayen soyayya da alama a sama yake, yana network, can kasa-kasa ya ce "Hello yaya Imran" "Barci kake yi ne? Ko dai baka da Lafiya ne?" Imran ya tambaya. (Ka ji Imran da shisshigi ina ruwanka, mutun ba gwabroba ka ce me, sai ka jiyo abin da zai hana ka barci wata rana, in dai Akil ne🤣 ko da yake ba laifin ka bane, baka san dawar garin bane🤣) "E...a'a...dai ban yi barcin ba tukunnan" jin irin amsar da ya bashi ne yasa ya yi danasanin tambayarsa, sai ya ji gaba ɗaya kunya ta kama shi, sauri-sauri ya ce "Karfe huɗu daidai ka zo asibitin Dr Nawid ka ɗauki heartbeat da kuma Rimsha zuwa gida, dan Allah akil na baka amanar Rimsha ka kula da ita sosai" ya kai karshen maganar tare da miƙewa ya fice waje kamar ya san da Akil zai tambaye shi me ya same su. Ai kuwa yana fita Akil ya ce "Yaya Imran menene ya same su kuma?" Ya yi maganar da ɗan ɗaga murya. Ba tare da ɓata lokaci ba Imran ya labarta mashi duk abin dake faruwa, sosai Akil ya tausayawa Rimsha kuma ya yi alkawarin kula da ita sosai har Imran ɗin ya dawo, da haka suka yi sallama Imran ya dawo cikin ɗakin ya kara yi wa Rimsha sannu, sannan ya musu sallama ya fita izuwa office ɗin Nawid. Zaune ya isko Nawid yana haɗa wasu takardun, saman kujerar da ya zauna ɗazun a nan ya zauna tare da miƙa mashi hannu suka gaisa sannan ya tambayi wani irin magani za'a sayawa Rimsha, ba tare da ɓata lokaci ba Nawid ya rubuta mashi magungunan da zai saya, har ya karɓi takardan sai kuma ya sake miƙawa Nawid ɗin ya miƙe yana faɗin "Na mance akwai in da zanje, Akil zai zo ɗaukar su anjima ka bashi takardan zai sawo mata maganin" To Nawid ya amsa da shi sannan suka sake yin musabaha Imran ya wuce. Sai sauri yake zubawa saboda ya kusa cin time da Lion ya bashi. Kai tsaye gida ya wuce, ya na shiga bedroom nasa ya fara haɗa kayan da zai buƙata, sai zuba sauri yake yi, ya ja trolley zuwa cikin motarsa, bayan ya kai ya dawo ya ɗauki na Lion ɗin ma, sannan ya wuce cikin gida ya sanar da Ammie zai ɗan yi tafiya na kwana biyu, zai je Abuja, shine abin da ya gaya mata, dan in ba ce mata ya yi baya nan ya yi tafiya ba, ba zata taɓa yarda baya kwana a gida ba, amma da yake tasan a baya yana zuwa Abuja, wata sain gidan su Rimsha, wata sain kuma Abba na wakilta shi zuwa taro ko wani abin. To ta amsa mashi da shi sannan ta yi mashi fatan Alkhari. Sauri-sauri ya amsa da amin tare da fitowa ya shiga motarsa. Sai bayan ya kama hanyar tafiya ne ya kira Abba a waya ya gaya mashi ga in da zai je, bai yi wa Abba karya ba, gaskiya ya gaya mashi, domin baya taɓa yarda karya ta haɗa su, kuma Abba yana da fahimtar sosai, ba kamar ita Ammie ba. Fatan alheri Abba ya yi mashi suka yi sallama. Yana katse kiran sai ga kiran Lion ya shigo, jikinsa har kerma yake yi wajen ɗaukar kiran tare da kara wayar a kunnansa. "Prof ka je Airport akwai sojojin da zaka taho mani da su" shine abin da Lion ya faɗa, kuma bai jira amsar Imran ɗin ba ya katse kiran. Juya kan motar Imran ya yi zuwa airport. Sojoji guda biyu ne masu yi masu girki, sai kuma uban kaya da suka zo da shi, carton carton, mamaki Imran ya yi wannan uban cartons ɗin kuma menene a cikinsu, yana tsaka da tunani sai jin fasasshen Muryan sojan yana faɗin suje, gaba ɗaya sojojin basa a cikin kaki, suna sanye ne da kananan kaya, Jeans da T-shirt, sai rigar sanyi da suka ɗaura a kai, sannan sun sanya face mask a fuskarsu, Turawane farare kal da su, gasu da kirar karfi kuma ya haɗu da sun ji training sosai. Gidan baya na motar suka shiga, kayan da suka zo da shi kuma, waya Imran ya yi aka nemo mashi mota mai baya ta kwashi kayan, ya shiga gidan gaba ya tada motar suka nufi hanyar gidan Lion. Duk cikin sojojin ba wanda ya ce da Imran ko sannu, shima bai yi masu magana ba, saboda ba abin da ya haɗa shi da su. A haka kamar gumaka har suka isa gidan, babu mai gadi dan haka sai Imran ya ce da soja ɗaya ya fita ya buɗe masu gate, ba musu ya fita dan suna girmama Imran sosai, saboda sun san tun da Lion ya turo shi, kuma bai ɓoye mashi a kan tafiyar sirri suka yi ba, suka san cewa yasan komai kuma yana da mahimmanci sosai a wajen Lion ɗin, so idan ya basu umarni dole su bi. Bayan ya buɗe masu gate ɗin ne suka kutsa cikin gidan. Yana kashe motar a parking space, sojan dake a cikin ya fito suka tsaya sai da da motar da ta ɗauko masu kayar ta kariso cikin gidan, sannan suka fara sauƙe kayan, shi kuma Imran yana fitowa, fitar da trolleys nasu ya yi dukka biyu ya ja izuwa cikin gida. Kai tsaye ɗakin Lion ya nufa, yana kwance saman lallausan bed nasa, ya lafe luf, gaba ɗaya jikinsa na lulluɓe da lallausan bargon mai laushi sosai da sosai kamar audiga fari kal, iya kansa ne kawai a buɗe, shima kan nasa, gaba ɗaya dark black curly hair san nan ya rufe mashi fuska, baka iya ganin komai nasa, sai kyalli gashin nasa yake yi, cikin kwanciyar hankali yake barcin sa, da ga gani yana cikin yanayi mai daɗi, a hankali yake sauƙe numfashi. Uhmm abin sai wanda ya gani, Lion ba'a magana Kai tsaye wannan kyakkyawan dressing room ɗin Imran ya wuce, a hankali yake jan trolleys ɗin dan kar ya takurawa Lion. Guda ɗaya a ajiye a cikin dressing room ɗin, wato na Lion, na shi kuma ya ja ta zuwa ɗayar ɗakin dake a kusa da wannan, a nan ya ajiye, kusan komai na cikin ɗakin irin na ɗakin da Lion ke a cikine, colors ne kawai suka banbanta, shi na Lion komai fari ne, wadda Imran ya shiga kuma komai brown ne. Bayan ya kai ya ajiye ne ya dawo bedroom ɗin Lion, saman bedside drawer ya zauna ya zubawa Lion ɗin ido, wani irin mugun kyau Lion ya ke yi mashi, yana bala'in Kaunarsa sosai, haka kawai wani tunani ya faɗo mashi a ransa, da ace Lion zai so Rimsha ya aureta da ta ji daɗi, ta huta da kuncin da take ci, ko ba komai zata samu sassauci abin da take ji a zuciyarta na rashin yan uwanta. Lokacin guda kuma ya tuntsure da dariya kamar ba lafiya, cikin sauri kuma ya toshe bakin nasa da hannayensa dan kada ya tashi Lion, miƙewa ya yi ya koma balcony ya tsaya, kasa-kasa ya ce "Amma dai tunani ma akwai hauka, yanzu kawai sai tunani ya bani cewa Lion ya auri Rimsha tab, hmmm ga ƴaƴan manya-manyan shuwagabannin manyan kasashe ta duniya, wayen da suka amsa sunayen su mata masu class, kuɗi, mulki, ilimi, kyau, yayan turawa irinsa suna haukar son shi, suna mutuwa a kanshi, amma ko ɗaga ido ya kallesu bai taɓa yi ba, sai wata Rimsha, amma gaskiya tunani baki yi mani adalci ba, anyama shi Lion yasan me so kuwa? To ni dai ban taɓa gani ba ko kusa ko alama wai ya furta wata kalma makamanciyar hakan ko tsakaninsa da James ne". Sai magana yake yi, jin motsi mutun ne yasa ya dakata, cike da tsoron kar dai Lion ne, haka ya juyo a hankali, wani irin dukan uku uku kirjinsa ta yi ganin Lion. Tsaye yake a bakin kofar balcony ɗin, kamar dai ɗazun daga shi sai wannan farar Short ɗin, dan ya ce Nigeria akwai bala'in zafi, lokacin kuma ya taso daga barcin da yake yi, ganin Imran a wajen yasa ya fito wajen dan su zauna su sha iska tare, ko kaɗan bai ji abin da Imran ɗin ya ce ba domin lokacin ya kariso wajen, kuma kasa-kasa Imran ɗin yake magana. Yan kame-kame Imran ya fara yi, wani irin razana ya yi da ganin kwayar idanun Lion, dan dama haka suke idan ya tashi barci sai ka gansu suna kyalli, bare ma idan ya ɗan zaro su, dama gasu nan dara-dara da su, abin ba'a magana, sai ka gansu suna wani irin haske suna rikita mai kallonsu, ko su James suka yi ido huɗu da shi ya tashi barci kuma ya zaro idon, suna tsorata bare kuma Imran da bai saba ba, bawan Allah yau ya ga ta kanshi. Wucewa ya yi ya zauna saman ɗaya daga cikin kujerun dake a wajen, shima Imran da ya ga bai kula shi ba sai ya wuce ya zauna gefensa. Kwata-kwata Imran bai san da zancen Lion ya tsani mum ɗin su ba, domin idan baku mance ba Lion ba kowa ya san abin da yake ciki ba, ko ya yake da mutun ba komai yake gaya mashi ba, Tga da yake uncle nasa ma, ba komai yake sanar da shi ba, hakan yasa Imran bai san da wannan zance ba, saboda bai taɓa zuwa gidan su ba, iya haɗuwa a School kawai suke yi, kuma duk cikinsu ba wanda ya taɓa gaya mashi, in ma James or Michael, yana dai mamakin da basu kula mutune, dan ba iya matane kawai basa kulawa ba gaba ɗaya ne, rashin sanin kuma yasa Imran ya aika Rimsha ta kai mashi abinci, da yasan da haka ba zai aikata ba. A ɓangaren sojojin nan kuwa, bayan sun gama sauƙe kayan ne suka kwashe su zuwa cikin Palo, a nan suka tsaye suka duba Kitchen, bayan sun gani suka zuba kayan a ciki, sannan suka ɓubbuɗe cartons ɗin, abubuwa ne na cimarsu irin kayan girkinsu da ruwan sha da dai sauransu, shirya komai suka yi a muhallinsa, sannan soja ɗaya ya koma bakin gate dan yin gadi, shi kuma soja ɗayan ya fara ƙoƙarin yin girki, ya kunna fridge dake a cikin Kitchen ɗin, dan ruwan da suka zuba a ciki ya yi sanyi. Wannan kenan a ɓangaren su Lion bari Mu leƙa ɓangaren Aafia muga a wani hali take a ciki. 💔😭BANDITS😭💔 Kwanan zaune Aafia ta yi, ta kasa iya yin barci saboda bata saba kwana a kan siminti ba, ta kasa iya barci saboda bala'in yunwa dake addabama cikinta, sai matsar kwalla take yi, kamar yadda taga rana haka ta ga dare, ita kuwa Rufee doguwar suma ta faɗa saboda azaba kuma ga jinin da ta rasa. Haka har wayenwan gari, sosai Hanan ta rinƙa yiwa mamanta kuka. Abin da ya kawo Hanan da mamanta wannan waje kuma shine, sun baro katsina ne suna hanyar Kaduna za su je duba kakanta, ta gefen maman kenan, tana asibiti ba lafiya, to za su je dubata kenan yan Kidnaping ɗin suka kamasu a kan hanyarsu ta zuwa Kd, duk da talaucin da suke a cikin, sun gwammaci gidan su akan hannun yan bandits ɗin nan, sun ci bakar wahala a ɗan kwana ɗaya da suka yi. Sai misalin karfe 8 yan bandits suka zo suka fitar da su, a wannan karon da gudu Aafia ta yi gaba, dan jiya tasha bulala. Wajen dai da suka zauna jiya, a nan suka zauna yau ma, Aafia ta sha ruwan mamaki ganin yan bandits ɗin dayawa yau, da alama sun dawo kenan. A gaban idanunsu babba daga cikin yan bandits ɗin ya fito da wani abin a cikin gora, ya bawa kowanne daga cikin bandits ɗin suka sha, kowa kurɓa ɗaya yake yi ya miƙawa na kusa da shi. Sai da gaba ɗayan su suka sha, kusan su 40 ne a wajen, sannan ogan nasu ya masu umarnin a kan su tafi, wucewa suka yi, suka kutsa da cikin daji, da alama wani aika-aika za su je yi, wannan abin da suka sha kuma ba komai bane, fa ce abune wanda zai kawar masu da tausayi da Imani, dama idan za su fita aiki sai sun sha shi domin ya ɗebe masu imani su ji daɗin aikata duk abin da za su aikata ba jin tausayi ko ɗigo a ransu. Bayan wayan can sun tafi ne kuma wasu wajen su 10 suka kariso wajen a kan mashin, ɗaya na goye da ɗaya, wani ma mutun biyu ya goya, Dukansu matasa ne da ba za su wuce daga shekara 23 zuwa kasa ba. Daga ɗan baya suka kashe mashunan nasu suka sauƙo izuwa kusa da ogan nasu, yana tsaye fuskarsa na rufe da wannan rawanin nasu. Umarni ya ba su akan su fitar da sabbin zuwa da aka kawo, su karɓi number yan uwansu bari ya kira kafin ya wuce, dan akwai aikin da zai je. Haka kuwa akayi, suka ware su Aafia a gefe suka fara karɓar numbobin yan uwansu. Ko da suka zo kan Aafia sai ta ce masu bata haddace number kowa a gida ba, a nata wautan wai tana tsoron ta bada number yaya Irfan, dan idan ta koma zai mata duka ya ce waye ce ta bi Rufee, me ya kai ta wajen, shiyasa ta ki bada number, ta ce bata da number kowa. Wani mahaukacin mari bandit ɗin ya sakar mata a kumatu, wadda ya sanyata kurma wani irin razanannen ihu mai razana kwakwalwa. "Zaki bamu number yan gidan ku ne, ko sai na fasa ki da bindiga?!!!" Ya kai karshen maganar yana sanya kafa ya hanɓareta, faɗuwa kasa ta yi tana kuka kamar ranta zai fita, cikin kuka ta ce "Wlh ni ban riƙe number kowa a kai na ba" A haukarta tana ganin idan ta ce masu hakan za su saketa ta koma gida, tana bala'in jin tsoron ta bada number ɗaya daga cikin, Abbi ko yaya Irfan, dan dukkansu ba sauki, ubanta za su ci idan suka san yawo take tafiya, bata san cewa a wannan halin da take ciki sai dai ma su yi mata kuka ba. Bandit ɗin yana ƙoƙarin sake taka mata wuya da wannan takalmar tasu mai kama da waterproof ɗin, sai ɗaya daga cikin su ya ce "Haba buba ka tsaya mana, kai daga ganin wannan kasan akwai kuɗi a gidansu, idan ka kasheta ka yi mana asara, baka ga jikinta bane? Wannan renon madara ce, ba ƙaramin kuɗi za mu samu ba, oga ina son ku bari zan karɓa maku number". Kallon shi ogan nasu ya yi ya ce "Sani zai kira wayar ni ina sauri zan fita, kada ku kuskura ku taɓa mace ko ɗaya daga cikinsu, sai na dawo" ya kai karshen maganar yana nufar hanyar dake ta tsakiyar wasu dogayen ciyayi a wajen. "Oga dabar Yellow zaka je ne?" Wannan da ya ce abar Aafia shi ya tambaya, gyaɗa masu kai ya yi ba tare da ya yi magana ba kuma bai juyoba ya ci-gaba da tafiya har ya ɓacewa ganinsu. "Dan Allah Sani kazo ka kira wayar nan yanzu dan wlh bani da kuɗi" cewar buba. Daga cikin wani ɗaki dake ɗan gefe ɗan nesa kaɗan Sanin ya fito, shima duk shigarsu iri ɗaya ne, kuma dukka matasane masu jini a jika, dan shima ba zai wuci 25 years ba, (matasa manyan gobe😭) Yana zuwa ya fara karɓar numbobin yana kira iyaye da yan uwan mutanen da suka kama, da wata wayarsa Tecno mai botir, duk ta ji jiki. Sun kware wajen yankawa mutane kuɗin da sai sun ji kaban su ya faɗi, wasu ma za su iya suma idan suka ji kuɗin da suka kira. Da suka zo kan maman Hanan, ta ruɗe ta rasa number waye zata bada, saboda Mahaifiyarta tana asibiti, idan ta bada number yan gidansu za su sake shiga tashin hankali kan tashin hankali ne, idan kuma ta ce ta gefen familyn ta na Katsina ne, wato gefen babanta, babu mai waya ma a cikinsu. Ta nutsa cikin tunani ne bubu ya daka mata wani irin mahaukacin tsawa wadda ya sata fara karato number kanin mamanta dan shi kaɗai ta iya riƙe numbersa. Suna saka number bugu ɗaya ya ɗauka, ba ɓata lokaci suka sanar mashi da abin da yasa suka kirashi, salati bawan Allah ya fari yi, a wulakance Sani ya ce "Ka ajiye salatin ka a gefe, gaba zai maka amfani, yanzu dai ku kawo kuɗin fansa ku karɓe ta ko kuma mu kashe ta" daga can ɓangaren yayan nata ya tambayi naira nawa ne, nan suka yanka mashi kuɗin da kwakwarsa suka kasa ɗauka mashi, 40 million, daga suka faɗi kuɗin wayar ta yanke dif, da alama ya suma ne, ko kuma dai ya razana ya saki wayar ta faɗi kasa ta tarwatse, ko wani abu makamancin haka. Tsaki sani ya ja yana faɗin "An jima zan waiwayeka idan ka dawo daidai" ya kai karshen maganar tare da kallon Aafia yana mai bata umarnin akan ta basu number yan gidan su, ai kuwa ta kafe akan lallai ita bata riƙe number kowa a kanta ba, hakan yasa suka tambayi sunan anguwarsu dan su nemo number da kansu, nan fa tsoro ya kara kamata, jikinta ya hau kerma, sosai take ambato sunan Allah a ranta. Suna a wannan hali Sani ya zuba mata ido suna jiran amsa, ba su ankaraba, kawai sai gani suka yi ɗaya daga cikin bandits ɗin ya kariso wajen, hannunsa ruƙe da zangegen bulala, yana zuwa ya fara zabga mata a jikinta. Irin mutanen nan ne masu gaggawa a kan abu, basu da hakuri, ga saurin hawa, shiyasa ya fara dukanta, wai ta raina masu wayo ne, sai ihu take yi tana juyi a wajen. Shi kuma buba ɗaga bindigar hannunsa ya yi sama ya fara sakin wuta, Ihu sauran yan bandits dake a wajen suka fara yi suna shewa. Nan take duk sabbin zuwa dake a wajen, wayan da ba su saba ba, suka rungumi juna suna kuka. A zafafe A'afia ma ta rungumi Hanan suna kuka kamar ransu zai fita, duk sun birkita masu kwakwale, shi kuma bandits mai zane Aafia haka ya cigaba da sauƙe masu bulala a jiki, daga Aafia har Hanan ɗin da suka rungumi juna, a tare suke shan bulalar. Cike da jin haushin abin da suka yi Sani ya dakatar su ta hanyar daka masu tsawa. Ba dan sun so ba, suka dakata, rai a ɓace ya fara magana "Yanzu me amfanin hakan? To da kuka birkita su ai Shikenan, kuna tunanin yanzu za su iya bamu amsa ne, me yasa kukam wata zubin baku abu da ƙwaƙwalwar ku ne? Dan Allah ku wuce ku bani waje a nan hai". Ya kai karshen maganar tare da wucewa ya bar wajen ransa a matukar ɓace, suma wucewa suka yi suka bar wajen, sai wani kumbure-kumbure suke yi, suka nufi in da ya kasance nan ne ɗaku nan su yake. Haka su Aafia suka ci-gaba da zama cikin kunci suna hawaye, duk sun birkice bayin Allah. Sani ya ce zuwa anjima zai dawo dan ya karisa karɓar numbobin yan uwan nasu, kafin nan sun ɗan sami natsuwa.... Ni kuma na tattara kayana zuwa gidan Abbi gobe idan mai dukka ya kai mu, sai mun haɗe gidan Abbi, masoyan yaya Imran, yaya Irfan, yaya Akil, Abba, Abbi, daddyn Jelly, Umaisha, Akila, sai ku saka A'afia a addu'a, domin kuwa wannan bala'in da take ciki, tamkar gaba ɗaya wayan da na kiran nan ne a ciki, yar uwasu ce, kanwarsu, yar cikin su, dole za su shiga matsanancin tashin hankali idan suka sami labari, Allah ka iya mana da iyawarka, Allah ka kawo mana zaman lafiya a kasar mu, Allah ka shiga lamarin mu😭😭, Ma'assalam......✍️ 💖💖TRIPLETS💖💖 53-54 🔥GIDAN ABBI🔥 *BARI MU FARA DA DADDYN JELLY* Suna fita da Ayla kai tsaye *ABC SUPERMARKET* suka wuce, yana tuki yana kallonta ta cikin mirror motar, ita kuma ya kwantar da kanta a jikin kujerar tana shakan kamshin perfume nasa, ga kuma kamshi turaren motar abin ba'a magana. "Babayn daddy tunanin me kike yi?" Ya faɗa yana dawo da kallonsa a kanta, fuska ɗauke da murmushi ta ce "Kawata kuma yar uwata Rimsha nake tunani, ko tana wani hali yanzu? Ina kewarta sosai". Jinjina kai ya yi cike da kulawa ya ce "Very soon zan kai ki wajenta, ba dai kin ce a Katsina take ba?" Gyaɗa mashi kai ta yi tana mai kai kallonta kan shi, shima ita yake kallo kuma yana tuki. Murmushi ya sakar mata yana faɗin "Yau kin yi kyau sosai kamar my jelly" "Allah sarki daddy Allah ina son kallon Jellyn nan sosai" mai da lallonsa kan hanya ya yi yana faɗin "Very soon da izinin Allah zata dawo gare mu" ya kai karshen maganar yana dawo da kallonsa kanta. "Allah yasa, kullun ina mata addu'a" ɗan zaro ido ya yi kafin ya ce "A ina kike yi mata addu'ar?" Ya tambaya yana sake kallon hanya. "A Sallah mana daddy, idan na yi sallah ina yi mata addu'a sosai" "Yaushe kika fara sallah ban sani ba?" Zaro ido ta yi yana kallon shi, dawo da kallon shi ya yi kanta yana faɗin "Amsa me, yaushe kika fara yin Sallah?" Sunnar da kai kasa ta yi tana wasa da yan yatsun hannunta, tana tunanin yaushe daddynta kuma yasan bata Sallah, kwata-kwata yau satin ta ɗaya tare da su, kuma yau take sa ran Jinin zai tafi, dan Aunty ta ce mata sati ɗaya yake yi, wata macen kuma kwana huɗu, to yau ta cika sati da fara yi. Tana tsaka da tunani kamar ance mata ta ɗago kallonta izuwa kan hanyar, daidai lokacin da shima ya kawar da kallonsa daga kanta izuwa kan hanyar, wani irin mahaukacin burki ya ja lokacin da suka kusa taka wani yaro da ya shigo titin da gudu zai tsallaka. Tsabar tsorata bata lokaci da ta faɗa jikinsa ba, tana sakin kuka, shi kuma ajiyar zuciya ya sauƙe tare da yi wa Allah godiya da ya sanya ba su buge yaron nan ba, dan ma Allah ya tsare ba wani gudu suke yi a kan hanyar ba, kaɗan-kaɗan suke tafiya saboda yasan suna tafiya suna hira hankalinsa ya rabu gida biyu shiyasa yake tafiya a hankali, da gudun haɗari. Bayan yan wasu mintuna, a hankali ya dawo da manya-manyan idanuwansa irin na Jellynsan nan a kanta, ta kankameshi sosai ta tura kanta cikin kirjinsa. "Babayn daddy are you okey?" Ya faɗa a sanyaye, cike da tsoro, da kyar kuma a hankali ta ɗago da idonta tana ayyana yadda zata ga sun taka yaron nan a kan titin, bata ma san yaro kam ya wuce abinsa da Allah ya tsare ba'a taka shi ba. Kai kallonta ta yi saman titin, sai taga wayam babu yaron, sai motoncin dake kaucewa nasu suna wucewa, dan ma Allah yasa motar tasu bata a kan hanya sosai, suna ɗan gefe. Dawo da kallonta kan fuskarsa ta yi, ya tsare ta da ido yana kallonta, yunkura wa ta yi zata tashi amma sai ta kasa sakamakon lokacin da ta faɗo jikinsa ta sanya hannunta ɗaya a jikin kujerar da yake zaune, da ya dawo da bayansa wajen sai ya ɗan danne mata hannun nata. Ko motsi bai yi ba yana ta kallon fuskarta, ita kuma tana son tashi ga shi ba hali, dawo da kallonta kan fuskarsa ta yi, still har lokacin kallonta yake yi. "Daddy hannuna zan tashi" ta yi maganar a shagwaɓe kamar yadda ya saba yi mata magana kullun, sannan ta yi maganar tana sunnar da kai kasa. Ya kasa motsa Allah kaɗai yasan me yake tunani a cikin ransa, ya kasa yin wani kataɓus. Ganin haka yasa ta koma ta kwantar da kanta a saman kirjinsa, dan ta gaji tana saman iska, ita bata zauna ba kuma bata karisa tashi ba. Wani irin yanayi mai wuyar misiltawa ya ji a jikinsa, bai san lokacin da ya kai hannunsa yana shafa kanta zuwa bayanta ba, shiru ita ma ta lafe a jikinsa, domin ya saba rarrashinta idan ta tuna da mamanta tana kuka, shi Aunty take kira ya rarrasheta dan tafi jin maganarsa sama da ko a gidan, shiyasa ta saba da rarrashin nasa, wani sain ma har rungumarta yake yi, idan ta yi shiru sai ya ce ta yi murmushi, idan ta yi ne sai ya rungumeta suna murmushi, shiyasa kwanciya a jikinsa ba bakon abu bane a wajenta ba. "Daddy hannuna yana yi mani zafi, ka danne sosai" ta faɗa murya can kasa-kasa, hannu yasa ya ɗago da haɓarta fuskokinsu su fuskantar juna. "Babyn daddy kin cika tsoro da yawa fa" murmushi ta sakar mashi tare da yunkurawa zata tashi. "Ina za ki tashi ki je?" "Wajen zama na mana daddy" ɗan ɗago da bayansa ya yi ta zare hannunta, tana kokarin komawa ta zauna, sai kuma ya jawota jikinsa mai gaba ɗaya, bata wani damu sosai ba, domin tana bala'in kaunar shi kuma ta saba. "Babyn daddy yau haka kawai nake jin bana son ki raba jikin ki da nawa, ina kewar Jelly da mummy ta sosai, komai ya dawo mani sabo yau" ya kai karshen maganar kamar zai yi kuka. Ɗago da kanta daga saman kirjin nasa ta yi suna kallon juna "Kayi hakuri daddy In Sha Allah za su dawo ka ji" ta faɗa a sanyaye. Jingina kansa da jikin kujerar motar ya yi yana faɗin "Mummy'n Jelly ta tafi in da ba'a dawowa baby, ba zata dawo ba, sai dai mu mu bita, yau kewarta ya dawo mani sabo, lokacin da ta rasu, nafi shekara uku ina jin tamkar tana a gefena, ba zan ina manta ta ba, a wannan shekara uku kullun na dawo gida ina jin motsinta, ina jin duk wani abin da take yi mani idan na dawo, daga karɓa jata har sauransu, idan na dawo gida sai in ga kamar ta zo karɓar jakata, idan na zauna cin abinci, sai in ji kamar ita take bani a baki, yau komai ya dawo mani sabo". Nan take hawayen da suka cika mashi ido, suka fara gangaro mashi a saman kumatunsa, dama kun san shi da saurin kuka idan baku mance ba. Jin ruwa ya zuba mata a saman kumatun tane yasa ta ɗago da kallonta izuwa kan fuskarsa, ganin yana hawaye ne yasa ta ɗan tashi daga kwanciyar da ta yi a kirjin nasa, ta ɗan matso ta zauna a saman cinyarsa, ta sanya hannunta tana goge mashi hawaye tana faɗin "Kayi hakuri daddy Allah ya jiƙanta da Rahma, Allah yasa ta huta, ita kuma jelly zata dawo In Sha Allah". Ji yake yi wani irin yanayi, yau ya tuna da mummy'n Jelly, ga shi sanyin idaninsa ɗaya ɗayar ma bata a yanzu, dama ita yake kallo yana rage kawar mum ɗin ta, abin ya jefa shi cikin damuwa sosai, sosai kuma yake yin wani irin baƙon yanayi lokacin da hannunta ke a saman kumatunsa tana goge mashi hawaye, a hankali ya sauƙo da wayan nan rinannun idanun nasa a kan fuskarta, ɗago kai ya yi suna fuskantar juna sosai, har suna iya jiyo numfashin juna, zubawa fuskarta ido ya yi yana jin kamar ya san mai irin fuakar nan tata, yau da ya kalleta kusa da kusa, sai ji ya yi tamkar ya santa, ko kuma mai kama da ita. Ganin yadda yake kallonta sosai ne yasa ta yi kakorin barin jikinsa, tun da ta gama goge mashi hawayen nasa, bata kai ga barin jikin nasa ba ya yi maza ya riƙota. "ina zaki ke?" Ya tambaya yana matso da fuskarsa daidai saitin tata, haka kawai ta tsinci kanta da jin tsoron shi lokaci guda ya kamata, muryar ta har sarkewa yake yi wajen furta "Daddy zan koma wajen zama nane sai mu tafi". Dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali "Baby shekarunki nawa?" Ya tambaya ya kara matso da ita saman kirjinsa. "Nima ban sani ba daddy, amma dai zan kai 15 haka ko 16 years, dan lokacin da muke tare da mamana ta ce shekaruna 12 yanzu kuma kaga rabona da ita shekara na huɗu kenan" ta kai karshen maganar tana zubar da hawaye, ta tuna mamanta. "Subhanallahi ni fa babay ba wai na tambaye ki bane dan ki yi mani kuka, kin dai kin san bana son kukan ki ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e. "To ki yi shiru ko?" Ya kai karshen maganar tare da sanya hannu yana goge mata hawaye. "Ni na tambayi shekarun ki ne domin ina son tantance shi kin kai ki zama haramun zama a jiki na ne ko dai". Shiru ta yi tana ɗan shasshekar kuka. Jawota ya yi zuwa kirjinsa sosai yana ɗan bubbuga mata bayanta alamar rarrashi. Minti biyar suka ɗauka a haka kafin ta ɗago kai da nufin ta yi mashi magana, tana ɗago kai hancinsu ya gogi na juna, domin ya rankwafo da kansa yana kare mata kallo. Wani irin shock ya ji lokacin da hakan ta faru, ita dai duk da kananan shekarun ta ta ji wani abu da batasan menene bane a jikinta, ɗan baya ta ɗan ja kaɗan tana faɗin "Daddy mu tafi ko?" Jinjina mata kai ya yi tare da fara ƙoƙarin kunna motar, zata tashi ya riƙeta dan kada ta tashi, yau gaba ɗaya ya rasa me yake damun shi, baya son raba jikinsa da tata. "Daddy zan koma saman kujera ta ce" girgiza mata kai ya yi a ya yin da yake tayar da motar ya ce "No ki yi zamanki a jikin daddynki" "Daddy to taya ya zaka yi tukin motar?". Ɗan shafa kumatunta ya yi yana faɗin "Sarkin tambaya ba, to zaki gani ai, kedai yi kwanciyar ki a jikin daddynki" to ta amsa mashi da shi tare da komawa ta kwantar da kanta a saman kirjinsa. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe tare da jan motar suka bar wajen. Tafiya kaɗan suka yi, suka isa *ABC SUPERMARKET* da ya yi parking a parking space nasu sai ta ɗago kai tana faɗin "Daddy in fita ne?" Tsareta da ido ya yi haka kawai baya gajiya da kallonta, wata sain har mamaki yake yi na rashin son daina kallonta da yake yi. "Babayn daddy kin ga ji ne da daddyn naki da har kike saurin fita?" Murmushi ta yi tana faɗin "Daddy ban ga ji da kai ba, ai naga mun iso ne kawai shiyasa na ce in fita ne". Shafa kumatunta ya yi kafin ya ce "Duk yadda aka yi mama ko baba ɗaya yaren mu ne, dan ba'a banza zaki yi wannan kyau ɗin haka ba". Yar dariya ta yi har sai da fararen hakwaranta suka bayyana, ta cusa kanta a cikin kirjinsa tana ɓoye fuska. Rungumeta ya yi yana faɗin "Ai gaskiya na faɗa ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alama e. "To waye daga cikin su ne Yaren namu?" Kasa kasa Muryar ta ke fita saboda ta cusa kanta cikin kirjinsa, tana ta jefa bawan Allah cikin yanayi. "Mama ta ce" kara ruƙeta da kyau ya yi yana ɗago haɓarta da hannunsa ɗaya, zuba mata ido kawai ya yi yana kallonta, ita kuma ta rufe ido tana murmushi. A haka kawai ya tsinci kansa da matso da fuskarsa daf da tata, daga karshe ya haɗe fuskokin nasu yana jan dogon numfashi. Jin fuskarsa a saman tate ne yasa ta buɗe idanuwanta, ai kuwa tana buɗewa sai cikin tasa idanun, da sauri ta mai da nata ta runtse su. "Babyn daddy kina kunyar daddyn ki ne?" Ya yi magana yana kara riƙota a jikinsa sosai, zuciyarsa na ingiza shi akan ya yi kissing lips nata, idanuwansa na akan lips ɗin tata, ya yin da ita kuma sai murmushi take yi tana faɗin "A'a daddy bana ji" yadda ta motsa lips ɗin nata ta yi magana kusa da shi bakaramar fusgar shi ta yi ba, gaba ɗaya ta sanya ya mance shin wai a ina ma yake? Da waye yake tare? Duk ya mance. (Sheɗan na daga gefe yana kallonsu😭) Kara matso da bakinsa ya yi kusa da tata yana ɗan goga lallausar lips ɗin nasa a saman tata, Allah ne kaɗai yasan irin abin da yake ji a cikin zuciyarsa, yau shekararsa 16 ba mace, shakara 16 kenan da rasuwar mummy jelly, lokaci guda ya canza, ya shiga wani irin yanayi mai wuyar misiltawa, riƙota sosai ya yi a jikinsa tare da ɗaura lips nasa saman tata, ya kasa janye wa kuma ya kasa aiwatar da abin da zuciyarsa ke ingiza shi da ya aikata, ita kuma jin ya ɗaura lips nasa a saman tata yasa ta waro idanuwanta, kai tsaye sai cikin nasa da suka yi jawur kamar wuta. Ba ƙaramin tsorata ta yi ba, nan take jikinta ya fara kerma ta fara ƙoƙarin kwacewa daga jikinsa, duk da cewa ba wani ilimi take da shi ba, ɗan zamanta da Rimsha ta fahimci abubuwa da dama, wadda a ciki kuma harda gudun wani namiji ya taɓa ki, sai kuma ta tuna in da Rimsha ke ce mata mum tasu ta ce mata idan mutun ya fara period namiji ya taɓa shi to zai samu ciki, tuna hakan yasa ta kara tsorata, ta fara yunkurin barin jikinsa. Riƙeta sosai ya yi, yana jin tamkar ya yi kissing nata, amma ya kasa, saboda ba halinsa bane, ba zai iya yin haka ba, idan ya tuna cewa duk abin da ya yi mata to yana nan a rubuce za'a yi wa Jellynsa hakan yana ɗaya daga cikin abin da yasa ya daure ya jure ya kame kansa bai kai ga yin kissing ɗin nata ba, jin zuciyarsa yake yi tamkar ana hura mashi wuta a cikinta, har wani sara mashi kansa yake yi, da kyar ya iya furta "Babyn daddy please ki zauna shiru kin ji? Babu wani abin da zan yi maki" da kyar ya iya kai karshen maganar yana haɗe words. Jin yadda ya yi magana kamar mara lafiya ne yasa ta san daddyn nata ba lafiya yake ba, kuma ta kara jin tsoron shi sosai a ranta, shiru ta yi tana tunanin me yake damunsa lokaci guda haka?. Shi kuma cigaba ya yi da goga lips nasa a saman tata, yana jan numfashi da kyar da kyar. Sun ɗan jima a haka kafin ya manna mata sumbata a saman lips ɗin nata, sannan ya saketa tare da kawar da kallonsa daga kanta, lokaci guda wani irin kunyarta ta kama shi, kasa-kasa ya ce "Babyn daddy je ki kiyi shopping ɗin ki dawo ina nan ina jiranki" tashi daga jikinsa ta yi, ita ma gaba ɗaya ji tayi kunyarsa ta kamata, sai wani sunnar da kai kasa take yi, cikin girmamawa ta ce "To me zan sawo daddy?". Har lokacin gefe yake kallo, ya ki kallonta ya ce "Jeki fara ɗaukar duk wani abin da ya burgeki, ciki kuma ki haɗa da jakar school irin wadda kike so, sai ki haɗa da kananan kaya zan biyo ki daga baya". To ta amsa mashi da shi, sannan ta buɗe kofar motar ta fita. Jingina kansa da jikin kujerar motar ya yi yana sauke nauyayyar ajiyar, kasa kasa ya fara magana shikaɗai "Zancen Sadiya ya tabbata, tabbas ina kaunar Ayla, ban san da haka ba sai yanzu, why soyayya zaka yi mani haka? Why?" Ya kai karshen maganar tare da sanya hannu yana shafa lips nasa, a hankali ya lumshe idanuwansa, bayan wasu yan mintoci ya sake warosu, har lokacin suna nan jawur basu koma asalin kalarsu ba. Ya ɗan jima a haka kafin nan ya fito daga cikin motar ya nufi cikin shopping ɗin. Can wajen mayukan shafawa ya hangota, zuba mata ido ya yi yana kare mata kallo, a shekaru ba zata wuci Jellynsa ba, amma jelly zata fita tsawo, ita kuma ta ɗan fi Jelly kiɓa, kuma da alama ma tama ji kin yin kiɓa, sai dai ba sosai ba, irin kibar nan mai kyau, idan ta samu natsuwa da hutu zata murmure sosai, wani irin yanayi mai daɗi yake shiga idan yana kallonta, babban kuskuren da ya yi wadda yasa har sonta ya shige shi cikin ƙanƙanin lokaci shine ɗaukarta da ya yi kamar Jelly, ya manta cewa jinin uba da ƴa daban-daban da yar da ba kai ka haifeta ba ka mai da ƴa, komai haɗa jiki da uba da ƴa za su yi ba za su taɓa jin sha'awar juna ba, sai dai idan son zuciya irin ta ɗaya daga cikinsu kuma sheɗan ya buga masu ganga, amma babu wannan a jinin uba da ƴa, ya mance da haka ya rinƙa jawota jikinsa, idan tana kuka haka yake rungumarta yana rarrashinta kamar yadda yake yi wa Jelly, da farko kin yarda take yi, daga baya ta saki jiki da shi, hakan yasa suka yi irin wannan irin sabo, ita ma a daddy take ɗaukarsa kamar yadda yake gaya mata, wannan kuskuren tasa soyayyarta ta yi mashi shigar faraɗ ɗaya. Ganin ta kasa zaɓar mai ɗin sai rawan ido take yi dan bata saba ba, a gidansu ma bata da mai ɗin bata taɓa shafawa ba. Hakan yasa ya karisa wajen yana faɗin "Babyna baki sami irin wanda kike so bane?" (Waye ya lura da canjin sunan da aka samu lokaci guda?🤣 Daga babyn daddy zuwa...🤐🤣) Shiru ta ɗan sunkuyar da kanta kasa, dan yanzu haka kawai take jin kunyarsa. Hannu ya kai yana duba wadda zai dace da kalar fatar ta, yana yi yana kallonta, sai wani yan kame-kame take yi mashi, shima dai bala'in kunyarta yake ji a yanzu. Haka ya zaɓa mata mai wadda yake ganin zai dace da skin nata, daga nan ya riƙo hannunta suka wuce wajen kaya da sauran abubuwa, komai shi ya zaɓa mata da kansa, dan tun da ya shigo ta kasa sukuni, taki sakin jiki, shima kuma bai damu da ya sata ta saki jikin nata ba, hakan da tayi ma yafi mashi, dan ya ɗan samu sassaucin abin da yake ji idan tana magana a kusa da shi. Sosai suka lodi kaya sannan suka wuce wajen biya, katinsa ya bada suka ciri kuɗin, ma'aikatan wajen suka kwasa mashi kayan zuwa cikin motarsa. Bayan sun shiga cikin motar ne ya kalleta ya ce "Sorry babyna" sai lokacin ta ɗago ta kalleshi, ganin ita yake kallo ne yasa ta mai da lallonta kasa tana wasa da yatsun hannunta, bin hannun nata da kallo ya yi, yatsun nata yan gajeru da su gwanin birgewa. Yar murmushi ya saki tare da kunna motar suka nufi gida. Suna isa ya fice zuwa part nasu, ya ki tayata kwasan kayan zuwa cikin gida, dan baya son haɗa ido da Aunty, saboda yasan halinta sarai yanzu zata sako shi a gaba da tambayar ya akayi, shiyasa ya gudu abinsa. Ita kuma haka ta kwashi kaya niki-niki zuwa cikin gida, Aunty bata a Palo, zube kayan ta yi a palon ta zauna saman sofa tana mai da numfashi, a hankali abubuwan da suka faru a mota ya fara dawo mata cikin ƙwaƙwalwarta, haka kawai take jin matuƙar kaunar daddyn nata, shiru ta yi idanuwanta suna gane mata lokacin da suka haɗa ido idanuwansa sun yi ja sosai. Yar firgita ta yi sakamakon taɓa ta da Aunty ta yi tana faɗin "Babyn daddy yaushe kuka dawo?". Fuska ɗauke da kayatatcen murmushi ta ce "Yanzu muka dawo" zama Aunty ta je ta yi a saman sofa mai zaman mutun 3 tana ɗan kishingiɗa tare da tambayar Ayla ɗin ya tafiyar tasu ta kasance. Da yake Ayla ba karatun sosai ta yi ba, kuma ba ta da wani sani akan hakan, ba waye wa, dan dai kunga yadda rayuwarya yake, ba da ban Rimsha bama da abin sai ya fi haka taɓarɓare wa, hakan yasa ta gayawa Aunty duk abin da ya faru a tsakaninta da daddy'n Jelly a tafiyarsu har suka dawo. Sosai Aunty ta ji daɗi tare da ja mata kunne akan kada ta kuskura ta sake gayawa kowa sirrin ta ne, ko ita bata ce ya gaya mata ba, amma dai ta yi mamakin jin cewa daddyn Jelly ne ya aikata hakan, ta wani ɓangaren kuma tausaya mashi take yi matuƙa, ta kuma jinjina mashi sosai, dan ya ma yi namijin ƙoƙari da ya iya tsayawa a iya haka, shekara 16 ba wasa ba, nan fa Aunty ta shiga bata shawari da kuma karin bayani akan abin da daddyn Jelly ke nufi da ita, wato yana son ta ne. (Kuji Aunty da ƙokari sai kace ya ce mata yana son ta🤔) Tun da Ayla ta ji haka sai ta ji wani irin kunyarsa ta karu mata, amma kuma ta tsinci kanta cikin matsananciyar farinciki wadda ita kanta bata san daga ina farinciki yake ba. "To tashi ki ɗauki abincinsa ki kai mashi kin ji? Dan nasan yana jin yunwa" To Ayla ta amsa da shi sannan ta miƙe ta bar niki nikin kayan nata a wajen, ta nufi Kitchen, sai murna Aunty take yi, dan daddyn Jelly yana da kirki sosai yana son ta, tana masa fatan ya yi aure ko zai rage mashi damuwa. Mai aikin su ne ta zo ta kwashe shopping ɗin na Ayla izuwa cikin ɗakinta. Ita kuma Ayla kamar yadda ta saba haka ta fito da tray mai shake da kayan abincin nasu shi da Irfan, ta ɗaura saman dining table tana kokarin tattare hijabinta ta gyara dan kada ya kayar da ita. "Ayla ki je ki yi wanka ki cire kayan nan tukunnan sai ki zo ki kai mashi abincin" Cewar Aunty, to ta amsa nata sannan ta bar abincin sama table ɗin ta haura sama (Aunty!! Aunty!! Akwai iya karawa abu gishiri da sugar 🤣) A gurguje Ayla ta yi wanka ta shirya cikin doguwar riga mai bala'in kyau launin pink da baki, ta yafa mayafin rigar a kanta, Rimsha ta koya mata sanya turare, hakan yasa take yawan sawa, kuma kullun saboda Rimshan take sakawa, idan ta sanya tana yawan tunata sosai, haka ta fito ta yi kyau sosai. Kai tsaye wajen abincin ta nufa, zata ɗauki abincin Aunty ta dakatar da ita ta hanyar cewa "Ke haka ake zuwa kai wa miji abinci (miji kuma?🤔) Babu kwalliya ba komai, wuce muje na maki kwalliya" to Ayla ta ce tana sunkuyar da kanta kasa, tana jin wani irin yanayi daddynta ya zama miji kuma?. Haurawa sama suka yi, ɗakin Aunty suka wuce ta fito da kayan make up nata ta fara tsantsara mata simple make up. "Aunty ina Inna ne?" Cewar Ayla. "Inna ai ta koma, ɗazun bayan tafiyarku yaya Irfan ya mai da ita gida, ta ce na samu lafiya zata koma" "Allah sarki har na fara kewarta" ɗauko lips balm aunty ta yi tana sanya mata a baki tana faɗin "Ke dai bari Ayla kamar zan yi kuka da zata tafi" "Ai dole ne mama fa hmmm" kallonta sosai Aunty ta yi kafin ta ce "To tashi ki tafi, ni ban ce ki tuno da zancen mama ki mani kuka ba, kada ki sa yaya maik ya zo ya mani duka, nasa mashi babynsa kuka, tashi ki je mijin ki na jin yunwa, saura idan kin je ki yi mashi shirme, ki natsu ki bi komai a nutse, kowani namiji yana son mace mai natsuwa da kamun kai, dan haka ki natsu, kuma kamar yadda kika saba wasa da dariya da shi haka za ki yi, ki zuba mashi abincin, idan ya ce ki zauna kuci kamar shekaran jiya, to ki zauna kuci tare, ina da tabbacin yaya Maik ba zai taɓa yi maki wani abin da ba daidai ba, ki kula da shi sosai, dan yanzu yana son kulawa sosai". Ita dai Ayla ba abin da take yi sai binta da to kawai. A tare duka jero zuwa palon, ita Aunty ta zauna saman sofa, ita kuma Ayla ta ɗauki abincin ta fice, sai tashin kamshi take yi abinta, ga shi make up ɗin nata ba karamin kyau ya yi mata ba. Da sallama ɗauke a bakinta ta shigo cikin palon, babu kowa shiru palon, saman lallausan Chinese carpet dake a tsakiyar palon ta ajiye abincin dan tasan ko ta kai saman table ma zai ce ta dawo da shi kasa ne, ya fi jin daɗin ci a kasa. Zama ta yi ta tankwace kafafunta tana jiran fitowarsa. Zaman minti 30 tayi sai ga shi ya fito jikinsa sanye da ƙananan kaya, wandon jeans baki da t-shirt fara, bai san da mutun a palon ba, saboda bai ji shigowarta ba, lokacin yana wanka, daya fito kuma ya shirya zai fita ne ma gaba ɗaya. Ganin ta yasa ya ɗan zuba mata ido yana faɗin "Baby yaushe kika shigo?" kasa ta yi da kanta cike da kunyarsa ta ce "Tum ɗazun" "Oky tom kin ci abincin ne?" Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a. Ɗan gefenta ya zauna yana faɗin "To zuba mana mu ci tare" to ta amsa mashi da shi tare da ɗaukar plate ɗaya ta fara zuba mashi abincin, white rice ce da steew, ha ji kayan haɗi ga nama zuƙu-zuƙu a cikinta. Bayan ta gama zuba komai ne ta turo mashi gabansa tana sanya mashi spoon a gefensa. Ɗaukar spoon ɗin ya yi ya fara ɗibar abincin, a maimakon ya kai bakinsa, sai ya kai mata saitin ɗan bakinta yana faɗin "Bari na fara baki ki ci tukun nan, idan kin ƙoshi sai ni ma na ci" kanta a kasa taki ɗagowa ta kalle shi, kuma taki buɗe bakin nata. "Baby wai me ya faru ne yau kuma? Gaba ɗaya kin canza, sai wani ɓoye mani face naki kike yi, ko dai akwai wani abin ne?". Kasa kasa ta fara magana "Babu komai daddy" "A'a ban yarda ba, me Sadiya ta gaya maki da kika shiga cikin gida? Dan nasan ba haka muka rabu da ke ba". Kara sunnar da kanta kasa ta yi, a nutse ta fara bashi labari "Aunty ta ce wai kana so na ne, kuma daga yau na daina ce maka daddy sai dai miji, kuma ta ce na rinƙa baka kulawa dan kana son kulawa". (Innalillahi Ayla ta gama tuna asiri,🤣 kai gaskiya rashin ilimi babbar ciwo ne😭) Tsareta da ido kawai ya yi yana kallon yadda take magana har ta kai karshen, ya ɗan jima yana kallonta kafin ya fara magana "To baki son daddyn naki ne?" Sai lokacin ta ɗago da kallonta a kan fuskarsa, cikin sauri kuma ta kawar da kallon nata tana faɗin "Ina son ka mana daddy". Ajiye spoon ɗin hannunsa ya yi tare da ɗan matsowa kusa da ita, ya sanya hannayensa ya riƙo nata hannayen dukka biyu kasa-kasa a nutse ya fara magana "Faɗa mani gaskiya kina son daddy ko baki son shi? Domin abin da Sadiya ta gaya maki gaskiya ce, babu karya a ciki, ina son ki, kuma auren ki zan yi ba da jimawa ba, ina son ki gaya mani gaskiya kina so na ko kuma kina da wanda kike so?" "Ina son ka daddy" "To in dai kina so na ɗago ido ki kalle Ni". A hankali ta ɗago da kallonta zuwa kan fuskarsa, wani irin cool murmushi ya sakar mata kafin ya saki hannayen nata, ya ɗauki spoon nasa yana faɗin "Za ki yi kyau da kayan amarci" Duk da bata san me ya ce ba ta ji daɗi kuma ta saki mashi cool murmushi. Ɗeban abin ya yi ya kawo mata sai tin bakinta yana kallonta, a hankali ta buɗe baki ta karɓa, wani irin daɗi suka ji dukkansu biyu, haka ya rinƙa ciyar da ita har sai da ta ƙoshi, sannan shima ya ci kaɗan ya ajiye spoon ɗin. "Daddy ya naga ka ci kaɗan?" Jan hancinta ya yi yana faɗin "Naƙo shi ne babyna, kuma daga yau ki daina ce mani daddy, ki kirani da Maik ko kuma Abdul Malik" toshe baki ta yi tana zaro ido "Daddy ni fa ba zan iya kiran sunan ka ba" "To ki kirani da baby ko mijinki duk wadda ya yi maki" da gudu ta miƙe zata bar wajen, cikin sauri ya riƙota ta faɗa jikinsa yana faɗin "Ina zaki je? Na sallame ki ne?" Ɓuye kanta ta yi a jikinsa tana dariya. Sakinta ya yi yana faɗin "Tom ki cewa Sadiya daga yau ta rinƙa barin abincin Irfan zai zo ya rinƙa ɗauka, bana son ki sake zuwa nan, ba wai dan bana son ganin ki bane, a'a kawai dai ki zauna a part naku zan rinƙa zuwa mu yi hira a can, yanzu dai tashi ki je, an jima idan na dawo ina zuwa mu yi hira" ya kai karshen maganar tare da manna mata kiss a goshi sannan ya ce "I love you". Shiru bata bashi amsa ba sai ma kokarin mikewa da ta yi daga jikin nasa, ɗan riƙo hannunta ya yi yana faɗin "Baki bani amsa ba, na ce maki I love you" "Ni ban san me zan ce ba daddy" hannu ya kai ya matse mata baki yana faɗin "Idan kika sake cewa daddy sai na...." Bai karisar da maganar ba ya yi shiru tare da sakinta ya miƙe ya nufi waje yana faɗin "Gobe dai zaki fara zuwa school" daga nan ya fice abinsa, ita kuma tattare kayan ta yi ta bawa Irfan kulan abincin da miya sai plate ɗaya da spoon ɗaya, ta ɗauki wanda suka ci zuwa cikin gida. Yadda ta bar aunty haka ta shigo ta same ta, Kitchen ta shigar da kayan sannan ta zo ta zauna tana faɗin "Aunty daddy ya ce gobe zan fara zuwa school" sai murmushi Aunty take yi ta yi mata fatan alkhari daga nan suka shiga duniyar hira tana bata labarin yadda zata rinƙa yi wa daddyn Jelly da shawarin da suka dace. A wannan Hali Abbi ya dawo ya same su, sannu da zuwa suka yi mashi, abin mamaki sai suka ga ya amsa da fara'a ya kuma ɗaura da cewa "Ina A'afia? Akil ya kirani a waya ɗazun da safe akan ta wuce ta koma kafin ya zo ya yi mata ɗan banzan duka". Cike da murnan Abbi ya sauƙo Aunty ta ce "A'afia ai bata dawo nan gidan ba, tun fa kwana huɗu da suka wuce da ta tafi gidan su Umaisha akan za su yi kwana ɗaya sai suka yi biyu, to ni daga ranar ma dana tambaya sai Irfan ya ce mani ta koma gidan da zama" wucewa Abbi ya yi ya nufi sama yana faɗin "E a gidan take dama, ina ga yaune ta fita ta ce masu zata zo nan, shine Akil ɗin ya ƙirani akan ta dawo, to na kira layinta ma a kashe, yanzu haka bai wuce tana tare da su Rufaidah bane, amma dai bari na kira Irfan ya je gidan su Rufaidah ɗin ya ɗauko ta ya mai da ta gidan yayan". Da zumuɗi Aunty ta amsa da to sannan ta tashi ta bi bayansa suka shige ɗaki a tare. 💖💖Star Lady....✍️✍️💖💖 Ita kuma Ayla ta gyara kwanciyarta a saman sofa tana murmushi, idan ta tuna cewa daddynta yana sonta, kuma ya ce zai aureta sai ta ji wani mugun daɗi, baiwar Allah ita ma tana matukar son shi sosai da sosai. (Uhm soyaya kenan, soyayya taburmar kaya, idan ka iya zama ka ji daɗi, idan kuma baka iya ba....😭💔) A ɓangaren Rimsha kuwa. Bayan Akil ya ɗaukota da ga asibiti tare da saya mata magungunan da ake buƙata. Suna zuwa gida bayan sun shiga palon Imran sun zauna ne, ya tambayeta ko akwai wani abin da take so, nan ta ce mashi school take son komawa, sosai ya ji daɗi sannan ya tambayi wani school take so, kuma a class nawa ta tsaya,. "Na gama primary 6 zan shiga Jss 1" ta bashi amsa, ba ɓata lokaci ya mata alkawarin nan da gobe zai gama mata komai domin harka ce ta kuɗi to kuma akwai su sosy, Akila bata san wainar da ake toyawa ba, dan ta shige cikin gida yin wanka, hakan yasa bata san me ake ciki ba, ta gama cin buri zata tafi Usa karatu, ga shi Rimsha ta ɓata mata komai bata da labari. Daga nan ya tambaye ta ko akwai wani abin da take so bayan school, a'a ta ce mashi sannan ya miƙe ya fita yana faɗin, anjima da daddare zai dawo ya bata magani ta sha a gabansa, to ta amsa mashi da shi. Yana fita ya kira Imran a waya ya sanar mashi da duk yadda suka yi, to Imran ya ce sannan ya ce ya amince ya yi mata komai na school ɗin kamar yadda ta buƙata, ya ɗaura da sanya mashi albarka, sannan suka yi sallama, sosai Imran ya samu kwanciyar hankali, yanzu ya samu natsuwar zai iya zama da Lion ba tare da farkaba ko tunanin wani hali Rimsha ke a ciki ba, saboda Akil na kula da ita yadda ya dace. Ita kuma Rimsha Akil na fita, ta miƙe zuwa cikin bedroom nata, wanka ta yi sannan ta shirya cikin riga da wando, wandon jeans irin palazon nan, sai riga T-shirt, da yake yau garin akwai iska mai sanyi sosai, sai ta ɗaura boyfriend jacket a saman kayan nata, ta gyara kanta ta fito zuwa kitchen, sai tashin kamshi take yi. Bayan ɗan wani lokaci Akila ta shigo suka kama aiki tare. Sai karfe 6 suka gama, wanka kowacen su ta yi suka sake shiri cikin dogon riga abaya suka nufi palo suka zauna. Zaman su ke da wuya Ahmad ya fara kiran layin Rimsha, ɗauka ta yi suka fara hira kenan sai ga Akil da Umaisha sun shigo, bata sallami Ahmad ɗin ba ta katse kiran dan kunyar yaya Akil take ji. Zama suka yi suka fara hira kamar Kullun. "Yaya Akil dan Allah ina son ka kai mu wajen gyaran gashi da kuma kunshi kaga nawa ya fara gogewa, kuma kaina ya ɗan yi datti" cewar Rimsha sarkin tsabta da son gyara kenan Ba musu yace gobe da yamma za su je ya kai ta, nan fa Umaisha ta ɓata rai dan ta jima tana ce mashi ya kai ta gyaran gashi sai dai ya ce suje toilet ya wanke mata domin yana da kishi bai yarda wata ta kalle mashi gashin sa ba, haka zai tasa ta gaba ya wanke mata da kansa, ya gyara mata har da shafa mayuka, amma yanzu rana tsaka ya ce zai kai Rimsha gyaran gashi, wlh ba zai yiwu ba. Ita ma Akila wage baki ta yi tana murmushi ta ce ita ma zata je, to ya amsa da shi, ita kuma Umaisha da ta ce zata je sai ya ce a'a bai yarda ba, kuka ta sa mashi tare da tashi ta fice daga cikin palon. Miƙewa shima ya yi ya nufi waje yana yi wa su Rimsha sallamar sai da safe dan ba zai dawo nan ba tun da Imran baya nan, sannan ya ce Akila ta kawo masu abinci ɗakin sa, to suka amsa mashi da shi. Har ya kai bakin kofa kuma sai ya juyo ya kalli Rimsha ya ce "Rimsha anjima idan anyi sallar isha kina da baƙo" zaro ido waje ta yi tare da dafe kirji ta ce "Yaya Akil baƙo kuma?" Gyaɗa mata kai ya yi yana faɗin "E baƙo, yaya Imran ya kira ni a waya ina gab da shigowa nan, ya ce mani Dr Nawid zai zo ku gaisa" ya kai karshen maganar tare da ficewa daga palo. Kallon Akila ta yi ta ce "Aunty Akila kina ji dai ko?" Dariya Akila ta yi tana faɗin "To ni dai gaskiya ba zan yarda wani ya shiga gonar yaya Ahmad ba, dole na gayawa yaya Imran, yaya Ahmad ya riga kowa". Miƙewa tayi daga saman kujerarta, ta dawo kusa da Akilar ta zauna. Hannayenta ta riƙo cikin nata, ta fara Magana cikin murya kamar wadda zata yi kuka "Aunty Akila ban taɓa haɗuwa da wata da nake bala'in kauna kamar ki ba, ko Jehan da take yar uwata ban yarda na gaya mata wani hali nake ciki ba, saboda ita ba kamar sauran mutane take ba, tana da zafi, ga faɗa, kuma bata tsayawa ta fahinci mutun take yanke mashi hukunci, idan bata son abu to ko mutuwa zaka yi ba zata taɓa fahimtar yadda kake ji akan wannan abin ba, hakan ce ta faru tsakani na da ita yasa ba zan iya gaya mata halin da nake a ciki ba, dan ba zata ɗauka ba, da ace tana nan yanzu ko me zai faru ba zan iya gaya mata ba, dan zata iya naɗa mani duka akan hakan ma. Zuba mata ido Akila ta yi tana kallon yadda take maganar, daga muryarta har fuskarta duk shaƙe suke da matsananciyar damuwa. Ba ɓoye-ɓoye ba komai Rimsha ta bata labarin halin da take ciki da asalinta da komai da komai bata ɓoye mata ba, daga karshe ta rufe da ɗan jan rigarta kasa ta nuna mata zanen sunan Lion dake a saman kirjin tata. Dogon numfashi Akila taja tana goge hawayen da suke gangaro mata a fuskarta, tabbas ta tausayawa Rimsha aihun ba kaɗan ba, kankame hannayenta ta yi a cikin tata, cikin shessheƙar kuka ta fara magana "Gaskiya Rimsha akwai ciwo sosai a cikin rayuwarki, amma da izinin Allah tun da har kika yi istihara kuma kika yi sallar dare kika roƙi Allah ya zaɓa maki abin da ya fi zama maki alkhari, still baki daina mafarkin Lion ba kuma baki daina son shi ba, sai ma karuwa da son nashi ya yi a zuciyarki, to da izinin Allah shine zaɓin da Allah ya yi maki, kuma ba a banza Allah ya kawo shi Nigeria ba, In Sha Allah kafin ya tafi zai so ki, duk da yaya Imran ya gaya mani ya bar gidan nan, amma In Sha Allah zaku haɗu kuma zai so ki har ma ya zama mijinki, zan taya ki da addu'a kuma ki yi hakuri zan gayawa yaya Imran irin dagon soyayyar Lion da kika yi a zuciyarki, wata kila ya iya taimaka maki ta wani wajen, amma gaskiya sai kin jure, domin ganin Lion a Tv ma ni tsoro yake bani bare kuma a zahiri, ai jiya wlh ban san shi bane da na sume a nan, Allah Ubangijin ya kawo maki komai da sauƙi, yaya Imran ya gaya mani cewa ma ya yi tafiya zuwa Abuja, In Sha Allah yana dawowa zan gaya mashi batun soyayyar naki nasan zai taimaka maki, kiyi hakuri amma dai kin ɗauki dala ba gammo gaskiya". "A'a Aunty Akila dan Allah kada ki gayawa yaya Imran ɗin kin ji? Dan Allah ki rufa mani asiri, saboda fa nasan da cewa idan na gaya maki ba zaki gayawa kowa bane yasa na gaya maki, dan Allah kada ki faɗa kin ji? kuma wlh ni ba son GAR nake yi ba, na gaya maki kawai yana burgeni ne, amma kinsan kema GAR ya fi karfi na, ina zai kai ni, ba ajinsa bace, ni kam kawai yana burgeni ne, a dama ji nake zan daina kallon videos nasa, amma dana ga cewa shi musulmi ne, sai nace to zan cigaba da kallon videos nasa ɗin, amma ba da nufin soyayya ba" ta kai karshen maganar cikin raunataciyar murya. Jinjina kai Akila ta yi tana faɗin "To shikenan tun da baki so ba zan gaya ba, In Sha Allah zan rufe maki siririnki kin ji?" Gyaɗa mata kai ta yi daga nan suka tashi suka nufi cikin ɗaki dan gabatar da sallar mangariba, dan tun ɗazun aka yi sallah su suna zaune suna hira ga shi har isha ta kusa. To bari mu koma wani ɓangaren tun da sallah za su yi. 💖💖Washington DC💖💖 Musharraf yana a wajen har wuraren karfe 4 na yamma, ya kasa motsawa, bawan Allah bai saba ba, kafafunsa duk sun kumbura sun yi jawur da su, har kwallah sai da ya yi. Misali karfe 4:30 Michael ya dawo daga school, kai tsaye part nasa ya nufa, a gajiye ya dawo ga shi kuma lecture biyu zai rinƙa karɓa, dan abin ya zo mashi da sauƙi, idan ya yi karatu a school daddy kuma zai rinƙa koya mashi nasa a gida tun da shima surgical doctor zai karanta irin daddy ɗin, shiyasa abubuwa suka yi mashi yawa, idan ya dawo sai su zauna da daddy yana nuna mashi wasu abubuwa dan komai ya tafi daidai. Wanka ya yi a gurguje ya shirya cikin wando three quarter fari tas da kuma riga mai karamar hannu launin sky blue, bai nemi Musharraf ba saboda yana tunanin yana barci ne, alwala yayi ya gabatar da sallar la'asar sannan ya fito Palon kasa. A nutse ya ci abincinsa ya miƙe ya nufi waje dan ya je gym ya motsa jiki zuwa karfe 5:30 ya dawo su fara karatu da daddy. Yana fita palon suka yi karo da Tga shi kuma ya dawo kenan daga wajen aiki, sannu Michael ya yi mashi ya wuce ya nufi gym ɗin. "Michael I want us to discuss something me and you" shine abin da Tga ya faɗa, ba tare da ya juyo ba, kuma bai dakata daga tafiyar da yake yi ba ya ce "Not now uncle, ka bari sai dare because i don't have time now" ya kai karshen maganar daidai lokacin da yake ɗaukar hanyar gym ɗin, sai sauri yake yi abin shi. Rai a matukar ɓace Tga ya bi bayan sa, sai wani huci yake yi. Michael na shiga ya tadda Musharraf a zaune ya haɗa kai da gwiwa ga kafafunsa sun kumbura sosai bawan Allah, cikin sauri ya kariso cikin wajen yana faɗin "uncle ɗin James what happened? What is wrong with you? What brought you here?" Ya ruɗe ya jero mashi tambayoyin. A hankali Musharraf ya ɗago da kansa kamar zai yi kuka idanuwansa sun yi ja kamar wuta, da kyar ya ce "Nothing my Asif". Michael zai sake yin magana muryar Tga ta katse shi da cewa "Ni ne na bashi horo yadda ya dace" A sukawane Michael ya juyo tare da miƙewa tsaye yana kallon Tga ɗin. "Uncle T because of what zaka bashi horo? Me ya yi maka?" Ɗaure fuska sosai Tga ya yi cike da izza ya fara magana "Because of shi musulmi ne, kuma kai kasan...." Dakatar da shi Micheal ya yi ta hanyar cewa "And so what idan shi musulmi ne? Ko akwai wata doka da tace kada musulmi ya zauna a gidan kristen ne? Faɗa mani ina ji". Zaro ido sosai Tga ya yi yana kallon Michael ɗin, hankalinsa ba karamin tashi ya yi ba, jikinsa har wani tsuma yake yi, yau Michael ne da gaya mashi magana haka? Cikin tsawa ya ce "Michael are you heard what you said kuwa? Kana cikin hankalin ka kuwa?". "Yes Uncle i heard what i said!, and so what dan na ce hakan?! look uncle be careful, ni bana shiga gonar kowa, dan haka bana son kowa kuma ya shiga nawa, ni dai na san uncle ɗin James ba mugu bane, ba zai taɓa cutar da mu ba, ina son ka sani ba wanda ya isa a gidan nan ya ce zai yi mashi wani abin na kyale shi, saboda James, dole zan riƙe wa James uncle ɗin sa, i knew James yana bala'in kaunar uncle Hosain (Musharraf) dan haka nima dole naso shi, please uncle T bana son yin sa in sa da kai, please and please mind your business!!" Ya kai karshen maganar yana mai duƙawa a gaban Musharraf. Nasan kuna son sanin a ina Musharraf ya samu sunan Hosain, to kada ku ji komai, Hosain dai sunan shine na yanka, ya bawa Michael tarihin rayuwarsa ne yasa Michael ya dai na kiransa da Musharraf yake ce mashi Hosain kamar yadda yan uwansa ke kiran shi, idan muka nutsa cikin story a hankali zaku ji tarihin Musharraf ɗin kuma. "Michael ni yau ka tsaya kake gayawa magana akan wannan banzan? Har kake cewa babu wanda ya isa ya yi mashi wani abin a gidan nan? To sai na gayawa Lion, kuma dole wannan ɗan ta'addan ya fita daga cikin gidan nan yau". "Uncle T na gaya maka, kuma abin da ya fi haka zan gaya maka, in dai a kanshi ne, kuma na faɗa ko Lion bai isa ya ce zai yi wa Uncle Hosain wani abin ba, idan kuma ya ce sai ya yi mashi wani abin, to sai dai ya haɗa mu gaba ɗaya ya yi mana a tare, kuma da kake maganar Musulmai yan ta'adda ne, baga ɗan ta'adda ba nan muna tare da shi James, kai da kanka kasan da hakan, ka san cewa har musulmai James yana kashewa, ɗan uwana ne kuma ina matukar kaunar shi kamar raina, amma ya zama dole idan gaskiya ta zo a faɗe ta, dan samun zaman lafiya, hanyar da James ya ɗauka ba daidai bane, ya zama dole mu gaya mashi gaskiya, i knew everything akan da kai akayi bincike akan abin da James yake aikatawa, kasan abubuwan da ya yi dukka, yanzu ka gaya mani da James da uncle Hosain waye ɗan ta'adda? Ga Kristen ɗin ga kuma musulmin dukkan a gaban ka, sai ka banbance, bari ka ji uncle T da Uncle Hosain ɗan ta'adda ne da kai baka saura a cikin gidan nan ba, domin idan da kashe mu ya zo yi, yadda ya shiga cikin gidan mu ya zauna, da ya jima da kashe mu, ni bana son hayani idan kuma ka matsa mani zan iya sanya gun na harbeka idan Lion ya dawo sai ya haɗa ni da uncle Hosain ɗin dukka ya kashe mu kowa ya huta!!" Yau iya ɓacin rai ran Michael ya ɓaci, har wani huci yake yi, yana magana ne cike da izza na jinin William jacop. "Michael ko kaso ko kada ka so musulmai yan ta'adda ne, gara maka ma ka rabu da wannan bakin mugun, idan ba haka ba, ta kanka zai fara, kai zai fara kashewa". "Uncle T na yarda Uncle Hosain ya kashe ni, babu ruwanka da ni, kuma yanzu ina son ka gaya mani taaddaci ɗaya da musulmai suka yi, idan har ka gaya mani ka kawo hujjoji da na gamsu, na maka alwarin da kai na zan kashe uncle Hosain!!!" Ya kai karshen maganar tare da juyowa ya miƙe suna fuskantar juna. Ba karamin razana Tga ya yi da ganin fuskar Michael ba, domin da ya ɓata rai sai ya koma sak fuskar Lion, jini ba wasa ba, bayan jininma aihuwa lokaci guda, Triplets ai dole a sami irin hakan. Yan kame-kame Tga ya fara yi, domin shida kansa idan zai gayawa kansa gaskiya ya san dai babu wani waje guda ɗaya da akace yau musulmai sun yi ta'addanci a wannan wajen, amma da yake basu son gaskiya sai ya fara kakalo karya ya ce "Ba ga shi ba musulman Pakistan suna ta kashe Indiyawa, bayan haka suna yi masu zagon kasa, sun hana indiyawa zaman lafiya, sannan ga musulman Palestine sun addabama Israel, sun farmakesu, suna kashe su, kuma ga Musulman....." Ɗaga mashi hannu Michael ya yi yana faɗin "Uncle T baka son gaskiya, kai da kanka kasan tsakanin indiyawa da yan Pakistan suwa ye suka takurawa juna, India da Pakistan duk abu guda ne daga baya aka raba, amma saboda zalunci yanzu ka gaya mani wanne daga cikin su tafi kyau? Suwaye suka fi jin daɗin rayuwa? Suwaye kasashenmu ke Maganar su? Ba India ba? Kana jin ana Maganar Pakistan ne? Ba'a maganar ta saboda kasar a mace take, Ko iya haka ya isa ka gane masu gaskiya a ciki, idan ma baka gane ba ƙwaƙwalwar ta toshe to bari na gaya maka, indiyawa ne suka takurawa musulman Pakistan, suke kashe su, su ne yan ta'adda, su haɗa ta'addancin su daga baya su ce wai Pakistan ne, kuma su suka yi kayan su da kansu, saboda sun ga Pakistan bata da manyan kasashen dake a bayan ta, batun Palestine da Israel kuma kana sane da masu gaskiya, a nan kafin Lion ya tafi sai da kuka yi magana da shi yake gaya maka musulman Palestine suna shan azaba a hannun Israel, Israel sun takura masu ya yi yawa dole ne yasa suka fito domin kare kansu, domin su nemawa kansu yanci, ko kana tunanin ban ji ku bane? To idan haka kake tunani ma ka makara, domin duk wani abin da Lion ya sani dole zan sanshi, saboda nima ai ina bincike a cikin laptop nasa, kuma wata sain idan kuna hira ai ina jin ku, to ni dai bani da matsala da ko wace addini, dan haka ba zan taɓa zagin kowa ba, kowa yana da dama ya yi addinin sa, kuma babu wanda ya isa ya hana shi, so ka fita harkar uncle Hosain!!". Rai a matukar ɓace Tga ya yi kansu, ko motsawa Michael bai yi ba yana tsaye duk da ya san cewa e tabbas Tga zai iya yi mashi dukan mutuwa, amma yasan Lion ba zai taɓa barin hakan ta faru ba, dan saboda ya san da cewa Lion ɗin ya sanya camera a wajen yana kallonsu, shi Tga shine bai san da cameran ba, na biyu kuma jiya Lion ya sanar da Michael ɗin cewa shima Musulmi ne, hakan yasa ya gayawa Tga duk maganar da ta zo bakinsa saboda ya san ba wani abin da ya isa ya yi masu, tunda mai gayya mai aiki yana tare da su. Damƙo wuyar Michael ɗin ya zo ya yi ya shaƙesa yana faɗin "Ni kake gayawa magana har kake ce mani James ne ɗan ta'adda, wato mu Kristen mune yan ta'adda kenan ba?" Da kyar Musharraf ya iya miƙewa yana kokarin cire hannun Tga ɗin daga shakar da ya yi Michael ɗin, dan da a taɓa Michael gwara shi bala'in ta kare a kansa, saboda Michael mutun ne mai kyauta, sadaka, kaunar bayin Allah, taimako, zuciya mai kyau, irinsa acikin al'umma suna da matukar amfani. A fusace Tga ya damƙo Musharraf ɗin ya haɗa kansu gwarel da na Michael ɗin, sai ga goshin Musharraf ya fashe ya fara jini, rai a ɓace ya yi wurgi ta Musharraf ɗin can gefe guda saman machine ɗin motsa kafa, ihu Musharraf ya kurma sau ɗaya sai kuma ya yi shiru kamar an ɗauke wutar nepa, da alama suma ya yi. Jin haka yasa Michael ya ji wani karfi ya zo mashi, wani kukan kura ya kurma tare da damƙo wuyar Tga ɗin suka fara kokawa. Rai a ɓace Tga ya ɗaga shi sama ya buga shi da ƙasa, wani wahalallen ihu ya saki tare sa sakarwa Tga.....✍️. Duk abin sa suke yi Lion na kallonsu ta cikin laptop nasa, abin sa ya sanya bai shiga faɗan ba, yana son kallon a iya ina hankalin da kuma natsuwar Michael ta tsaya, sannan yana son sanin shin Michael zai iya kwatawa kansa yanci ne ko yaya, a lokacin shi kuma Imran ya shiga toilet dan yin wanka. Ni kuma na haɗa kayana izuwa 🤔sai dai mun haɗu goben kawai idan mai dukka ya kai mu 💖💖TRIPLETS💖💖 55-56 *Idan kun samu typing error amin afuwa 👏 keyboard ɗin tana bani matsala sosai kwana biyun nan, to na yau ma ya fi tsananta, sai na danna A sai ya koma B😭* 🔥Washington DC🔥 Rai a ɓace Tga ya ɗaga shi sama ya buga shi da ƙasa, wani wahalallen ihu ya saki tare sa sakarwa Tga ɗin wayan nan kwarin nasu na Triplets. Duk abin sa suke yi Lion na kallonsu ta cikin laptop nasa, abin da ya sanya bai shiga faɗar ba, yana son kallon a iya ina hankalin da kuma natsuwar Michael ta tsaya, sannan yana son sanin shin Michael zai iya kwatawa kansa yanci ne ko yaya, a lokacin shi kuma Imran ya shiga toilet dan yin wanka. Ihu Tga ya fara yi yana bubbuge kwarin, amma ina kamar kara hura masu wuta akeyi, sai wani kara hawa kansa suke yi, suna bashi a jikinsa, da dai ya ga da gaske zasu lahana shi, sai ya kwasa da gudu ya bar wajen ya yi cikin gida. Yana barin wajen jibga-jibgan sojoji biyu suka iso wajen, kowannan su ya ɗaki ɗaya, ɗaya ya ɗauki Michael ɗayan kuma ya ɗauki Musharraf dake a sume, kai tsaye cikin gida suka wuce da su. Umarni Lion ya yi masu akan su kai su word room, haka kuwa suka wuce da su word room ɗin, saman kyawawa lausasan kuma tsadaddun gadajen dake a cikin word room ɗin suka kwantar da su, sannan suka juya suka fita. Da fitarsu ba'a fi minti goma ba sai ga su sun dawo tare da manya-manyan likitoci sanye da kayan aikinsu, suna zuwa suka fara duba su. Shi kuma Tga Lion ya dakatar da kwarin saboda suna da aiki gobe, yau za su bi jirgin dare zuwa Nigeria gobe za su yi wa wajen da James yake dirar mikiya, su tarwatsa kowa su fito da James, kuma Lion ya riga ya tsara cewa da Tga ɗin za'a yi tafiyar, idan ba ku mance ba kuma, baya magana ya canza, hakan yasa ya dakatar da kwarin, amma dai ya tanadawa Tga hukuncin da ta dace ya yi mashi bayan sun gama aikin da zasu yi na ɗauko James, ya zama dole ya hukunta shi saboda ya cutar da Musharraf, shi kuma baya goyon bayan a cuci mutun ba tare da ya yi maka komai ba, baya bin bayan zalinci ga koma wace addini. A ɓangaren daddy da Uncle Herry kuwa, duk wannan badakala da ake yi a cikin gidan basu sani ba, suna can cikin lambu, dan dama mayun zama a lambu ne, hakan yasa aka yi masu katafaren lambu a gidan, dan su rinƙa sakata suna walawa son ransu. Su kuma John da Jay basa nan, John ya tafi party, shi kuma Jay ya tafi yawonsa. Wannan kenan abin da yake faruwa a Washington DC kenan, idan kuma muka koma wajen*JEHAN* Wunin ranar Jehan da yunwa ta wuni, ta ki cin abincin dan ta ce lallai dole abin da ta ci shi Adiva zata ci, hakan yasa ta wuni da yunwa, dan sun ƙi yarda Adiva ta ci abincin. Ganin haka yasa Jehan ta fara zargin lallai akwai wani abin dan gane da wannan abincin, ace lallai sai ita kaɗai za'a bawa kamar ba lafiya ba, sai tunani take a kan hakan har can yamma, su Aisha dai sun ci sun ƙoshi kayan su, sunci na safe da rana. Da yamma sun yi wanka su A'isha anci uban kwalliya kamar yadda aka saba, an sha su eyelashes ga jambakin nan ba'a magana, kamar wata aljana haka ta zama domin ta lapta uban attachment a kanta. Ita ma Jehan ta yi kwalli amma bata sanya irin su eyelashes da kunba kamar Aisha ba, simple make up ta yi kamar yadda Adiva ma ta yi, ita kuma Maryam baiwar Allah, ko kaɗan bata yi kwalliyar bama. Ita kwata-kwata ma bata saki jikinta da kowa ba, da alama akwai ciwo a cikin rayuwarta sosai, ganin haka yasa Jehan ta Matso kusa da ita tana tambayarta ko lafiya. Kamar jira take yi a tambayeta sai ta fashe da kuka, da sauri Adiva ta matso kusa da ita suka fara rarrashinta. Sun ɗan jima suna rarrashinta sannan suka samu da kyar ta yi shiru. Ruwa Adiva ta ɗauko mata daga ɗan madaidaicin fridge dake a cikin ɗakin, dan ɗakin nasu kusan komai a akwai, duk gidan ɗakin su shine na uku a kyau, ɗaku nan hawa hawa ne, kamar yadda suma matan suke hawa hawa, akwai ɗakin yan 14 years, wadda ya fi kowanne kyau saboda su ne kananan yara, za'a jima ana zan zare da su, za su kawo kuɗi sosai, (a cewar Hajiyar daɗi fa tom, ba ni ba) Sai kuma ɗakin yan 15 years wadda suma nasu yana da kyau, sai dai bai kai na yan 14 years ba, dan yan 14 sune farko, daga shi sai na su Jehan, sai yan 17, haka ɗaku nan suke, na yan 14 katon freezer ne a ciki, da kuma manyan gadaje, yara su sakata su wala, kamar gidan ubansu, na yan 15 kuma mabi da shi ne. Karɓar ruwan ta yi ta sha tana sauƙe ajiyar zuciya. Sai da suka barta ta ɗan huta sannan Jehan ta ce muna jin ki me ya faru. Idonta cike tab da kwalla ta fara magana kamar haka, "Ni dai yar asalin garin Kano ce, kuma mu biyu iyayen mu suka haifa, ni da yayata wadda ita ma ta bar gida a yanzu haka, dan tare muka baro gida, wani iftilai ya afka mana mu ka rabu". A ƙage Jehan take da jin kan zance dan haka sai ta ce "Maza ki gaya mana da wuri" (D.P.O ba wasa, akwai san jin kan zance da wuri🤣) "Babana yana sai da rariya da itace a bakin kasuwar kauyenmu, yana da kuɗi sosai, saboda yana noma sosai da sosai, yana da dabbobi irinsu raguna, kuma kullum kara aihuwa ragunan nasa suke yi, sun yi yawa sosai ga awaki, amma duk da wannan tarin niimomi da Allah ya mashi, mun taso cikin bakar wahala, wai kawai dan saboda maman mu ta haifa mashi ƴaƴa mata, shi wai maza yake so wayan da zasu taya shi zuwa gona, hakan yasa ya rinƙa azabtar da mu da yunwa, ga duka da zagi, kyara idan muka zo kusa da shi, baya son ganin mu, maman mu tana shan wahala wajen neman abin da zata ba mu muci, yaya Asma'u ta sha wahala kamar ba zata yi rai ba, akwai lokacin da na kamu da rashin lafiya, kamar zan mutu, amma haka baba ya sa kafa ya yi fatali da ni, a wannan rana ma sai da ya yi mani dukan tsiya, bakin cikin yau da gobe yasa maman mu ta fara rashin lafiya, yan kauyen mu sun san baya bamu abin ci, amma basu san menene dalili ba, kuma sun yi mashi magana akan abincin, amma yaki canza hali, sai cewa ma ya yi babu ruwan kowa da gidansa, kowa ya yi harkar gabansa, maman mu kuma bata da mama sai babanta da matarsa, hakan yasa ta zaɓi zama a gidan mu da zaman gidansu, domin tasan ma ko taje sai babanta ya koreta saboda shi irin mutanennan ne ma su zafi sosai, baya ɗaukar maganarta gaskiya, kai in ta kai ce maki ma ko gidan ta je sai ya tambayi menene ya kawota, wani zubin ma daga kofar gida zai korata, ya ce ta koma gidanta, baya ma bari ta shiga cikin gida, haka muka yi ta fama da bakar wahala, kullun muna yawon neman abin da zamu ci, a haka har yaya Asma'u ta fara sata, lokacin da muka fara sanin daɗin abinci da sauransu kenan, yaya Asma'u tana shiga gidan mutane idan ta ga abu zata ɗauka ta gudu, ko abinci aka ajiye ta gani zata sace ta gudu, ta kawo mana mu ci, hakan ba karamin tayarwa da mama hankali ya yi ba, ya kara mata ciwo kan ciwo, akwai wata rana da aka biyo yaya Asma'u har gida, akan ta shiga gonar mutane ta saci masara kusan rabin buhu. Har cikin gida suka biyota masu gonar, suka jata zuwa waje suka fara dukanta, sai kuka mama take yi tana basu hakuri, amma basu kyaleta ba sai da suka naɗa mata duka kamar za su kasheta, sannan suka kyaleta suka tafi, sosai mama tasha kuka, daga karshe ta ɗaura ruwan zafi a saman kiraren da muka samo, ta tafasa ruwan ta gasawa yaya kijinta. A haka har nima na fara ɗaukar abin mutane, domin yunwa na neman kashe mu, dole idan munga abu mu ɗauka dan mu sami abin ci kada mu mutu, haka muke sata, duk abin da muka gani, ko da kuwa ba naci bane ɗauka muke yi saboda sabo da satar. Akwai wata rana da na kasa mance wa a idona, wannan ta zama rana mafi muni a rayuwata, lokacin mun girma, ina da shakara 15 a lokacin, mun je kauyen kusa da mu biki, ana biki lokacin, muka ga kuɗin wata mata a jakarta ta ajiye, muka ɗauka muka gudo zuwa gida, ashe akwai wadda ta gammu, da akazo ana cikiya ana ta kalawa wasu daga cikin jama'ar wajen sharrin sata, abin har ya kusa haifar da faɗa koma nace maki sun yi faɗa da baki ba da hannu ba, daga baya wannan da ta ganmun sai ta gaya masu cewa mune muka ɗauka. Lokacin kuma har mun sai bread da kuɗin naira ɗari biyu ce, muna tsaka da cin bread ɗin muka ji hayaniya, daidai lokacin kuma baba ya shigo, dama ita mama tana ɗaki tana barci bata san me yake fatuwa ba. Baba yana shigowa kawai ya ɗauki wani katon itace a cikin itacen da muke yo wa mama idan Allah ya bamu abin da za mu girka. Dukan mu ya fara yi da wannan itace yana tsine mana yana faɗin, tsinannu yan asara, ku tashi ku fice mani daga gida, ɗiyar banza ɗiyar bala'i, ku dai kun zame wa mutane annoba da bala'in , to dan ubanku sai ku tashi ku fita waje, bala'in da kuka jajumo suna can suna jiranku. A wannan hali mama ta fito ta same mu, kukan da muke yi ne ya tashe ta daga barcin ta, kuka ta fara yi tana kokarin kwace sandar hannun nasa, da karfi ya hankaɗeta ta yi baya baya ta faɗi kasa, mu kuma sai da ya yi mana duka sannan ya ja mu zuwa waje ya miƙa wa mutanen dake a wajen tare da gaya masu su yi mana dukan tsiya, domin mu bamu da aiki sai sata kullum, to shima ya ga ji da halin mu, haka jama'a suka hau dukan mu, bakin cikin hakan yasa mama ta faɗi ta mutu a wajen, wannan rana na kasa manta shi a rayuwata, haka suka yi mana dukan ɗari biyun su, bayan sun tafi muka dawo cikin gida da kyar, muna shigowa ni ban wani damu ba na nufi bread na da yake yashe a kasa, na ɗauka na cigaba da cusa shi a cikin baki na ina ci domin bala'in yunwa muke ji, ita kuma yaya Asma'u wajen mama ta nufa, da yake ta fini shekaru ita zata kai 18 years sai ta gane cewa mama ta rasu, mun gwammaci mutuwar mu a wannan lokaci da muka samu labari, ba karamin tashin hankali muka shiga ba, haka muka daure har sadakar uku na mama, a jama'ar unguwa, babu wanda ya kula mu, ko zaman makoki ba wanda ya yi wa mama, tun da aka je aka binneta shikenan, kuma duk saboda muguntar babana ne yasa ba masu kula mu. Babban abin tashin hankali da ya jefamu cikin matsala shine, baba ya zo ya fara kwanciya da yaya Asma'u a maimakon mama, shi ya ɓata mata budurcinta, kullun yana kwana da ita ɗaki ɗaya, tun tana kuka har ta hakura, domin idan bata yarda sun kwanta ba, baya ba mu abinci, kuma ko sun kwanta sau ɗaya yake bamu abincin a rana, duk da haka mun jure bamu damu ba, wata rana da daddare muna barci ya zo ya tasheni akan wai mu tafi ɗakinsa yau da ni zai kwana, shine yaya Asma'u ta ce ba zai yi wu ya lalata ta kuma nima ya yi mani hakan ba, zaginta ya fara yi yana faɗin ina ruwanta, idan bata yi mashi shiru ba sai ya kasheta a cikin daren nan, shine ta ce ya kasheta ɗin idan zai kashe ta, amma ni dai ba zai lalata mani rayuwa tana ji tana gani ba, haka yasa ya ɗauki itace ya buga mata ta faɗi kasa kamar baya numfashi nikuma ya jani zuwa cikin ɗakinsa, ina tsoron yi mashi wata magana dan kada nima ya buga mani itace ya kashe ni, sai na yi shiru ina kuka ina tuna abin da mama take yawan gaya mana, na muriƙe mutuncin mu duk wuya duk daɗi, idan har muka yarda muka zubar da mutuncin mu a titi bata yafe mana ba, sai kuka nake ita tuna mama, shi kuma baba ya cire mani riga zai cire mani zani kanan yaya Asma'u ta buga mashi wata itace ta baya, ya faɗi kasa kanshi ta fashe yana jini, hannu na ta riƙo tare da miƙar da ni muka fita da gudu, cikin wannan dare muka keta daji muna gudu. A hanya muna tsaka da gudu aka daki yaya Asma'u ta baya, ta faɗi kasa tana faɗin na gudu, ni bansan waye ya dake ta ba saboda duhun dare, na dai ga ta tashi suna faɗa da mutumin, a haka na gudo na barta a wajen, na fito bakin hanya, a nan nakwana, ba riga sai dai zanina dana ɗaura a saman kirjinta, washegari da safe a na rinƙa tafiya da kafa, na ci bakar wahala, jama'a suna ta yi mani kallon mahaukaciya saboda babu riga a jikina, har na shiga cikin birni wuraren la'asar haka, ban ci komai ba, kuma ban wani damu ba, saboda mun saba da yunwa, a takaice dai na sha bakar wahala ka fin na samu wasu bayin Allah su ɗauke ni, har makaranta suka sanya Ni, suna bani kulawa sosai da sosai saboda basu taba haihuwa ba, ita kuma yaya Asma'u ban sake jin labarinta ba, shekarata ɗaya cikin na biyu na yi a wajen su, na canza na fara samun ilimi, satin da ya wuce ne suka zo mani da wata magana wai suna son na haifa masu yaro, dan basu taɓa haihuwa ba, matar ba zata iya aihuwa , shine suka ce zaa sanya kwan haihuwarsu a cikina, yaron zai girma na haifa masu, wannan dalilin yasa dama suka ɗauke ni suka sani makaranta dan na iya yadda zan kula masu da cikinsu. Ban nuna masu a kan cewa ba zan yi ba, sai da na bari dare ya yi kowa ya yi barci, na kwashi kayana da yan kuɗin dake a gareni, na lalaɓa na buɗe gate ɗin gidan na gudo, ina fita na kwana a teburin mai shayin gaba da unguwar mu, da safe na wuce tasha na hau motar Abuja, ban san kowa a nan ba, kawai na hau mota, da muka shigo sai na rasa ina zan je, to ina tafiya a hanya ne muka haɗu da hajiyar da ta kawo ni nan, a takaice wannan shine kaɗan daga cikin abin da ya faru a rayuwata" ta kai karshen maganar tana kara sakin matsanancin kuka mai ratsa zuciyar mai sauraro. Har wani tsuma Jehan ta ji jikinta yana yi, ji take idan ta tamki wannan uban nasu zata iya yi mashi yankar rago, bakin mugu azzalumi, ta kuduri niyar wlh ba zata barshi ba, matukar dai yana raye sai ta nemeshi ta ɗaukawa Maryam da Asma'u da mamansu fansa, dan ire-iren su take son zama yar sanda. Duk dakiya da dauriya irin tata sai da ta matsawa Maryam kwalla, abin akwai taɓa zuciya sosai, ace uban ka da ya haifeka, kai duniya ina zaki da mu?. Rungumar Maryam ɗin ta yi tana mai bata hakuri tare da rarrashinta, da kyar suka samu ta yi shiru. Jugum-jugum suka zauna kowa da abin da yake tunani na rayuwa. After some minutes A wannan hali Zinariya ta shigo ta same su, sai tashin wani azababben kamshin perfume take yi mai sanya mutun ciwon kai, bata wani da mu da halin da suke a ciki ba kawai cewa ta yi "Ke Aisha ke da Maryam da Adiva ku shirya kuna da bako a palon hajiya nan da minti talatin, zai zaɓa ɗaya ne daga cikin ku, ita kuma Jehan sai Hajiya ta dawo musan awani part take, namu jinsin ce ko dai mazan za'a barmawa!" Ta kai karshen maganar tare da juyawa ta fice daga cikin ɗakin. Ba musu suka tashi suka hau shiri, haka kawai Jehan ta tsinci kanta da kasa hanasu tafiya, tana ji tana gani suka gama shiri suka fice daga ɗakin. Abin dake faruwa shine akwai wani tunaren da Zinariya ke shafawa idan zata zo kirawa costumers mata su zaɓa, duk wanda ya shaki Kamshin turaren to fa ba zai iya yi mata kaddama ba, dole kawai su bi abin da take so. Haka suka shirya suka fice daga cikin ɗakin har ma da yar zumuɗin su, bayin Allah sun shaki turaren Zinariya ta cuci rayuwarsu. Kasancewar Alhajin da ya zo ɗin masoyin mata masu ɗan giba ne sai ya zaɓi Maryam, domin ta ɗan fisu kiba, Adiva kam kamar Jehan take, ba su da wani kiba ko kaɗan, ɗan gara ma A'isha ta fisu auki. Bayan ya zaɓi Maryam ne A'isha da Adiva suka dawo cikin ɗakin, cikin zuciyarta Adiva kukan ɗaukar Maryam ɗin take yi, amma kuma a zahiri ta kasa nuna hakan, sai ma tsintar kanta da murmushi a kan fuskarta da ta yi, abin ya ɗaure masu kai, ga abu a cikin zuciyarsu suna ayyana wa amma yaki fitowa filli, haka ita ma Jehan ɗin ta kasance, sai kukan zuci take yi tana addu'ar Allah yasa kada ya lalatawa Maryam yaruwarta, yadda ta sha gwagwarmaya akan kare budurcin tan nan, Allah ya taya ta kare shi. A ɓangaren ita ma Maryam ɗin a zuciyar ta tana jin ba zata iya barin shi ya aika abin da yake da niya ba, amma kuma a zahiri ta kasa hana shi, sai faman shafa ta yake yi tun ma a cikin palon Hajiyar kafin su shiga daga cikin ɗakin da ya kama, dan ya ce a nan zai yi amfani da ita, sai wani murza mata breast yake yi, ga bakin nan nasa bakin kirin kamar zunubi, da alama ɗan buguwa ne. (To fa Maryam Allah ya kuɓutar da ku dukkanku na haɗa kaya na zuwa wajen mai Rimsha, sai na dawo dan ganin ya ake ciki) 🔥🔥GIDAN ABBA🔥🔥 Kamar yadda Dr Nawid ya faɗa kuwa bayan sallar isha sai ga shi nan ya zo, ya ci wanka ya sha dakakkiyar shadda blue color, ya yi kyau ba karya, amma fa ko kallo da ido bai samu daga wajen gimbiyar tasa ba, sai tashin kamshi yake yi yana ta zuba murmushi, ita kuma tana zaune saman sofa ta tsare gida ta haɗe rai, bai damu sosai ba, saboda yasan bata da lafiya...gaisuwa suka yi, daga nan suka zauna shiru, Rimsha ta yi kasa da kai shi kuma ya zuba mata idanu yana lallonta. A haka Akila ta shigo ta same su, wani irin haushin Dr Nawid ne ya kamata, dan bata son abin da zai ɓatawa Rimsha rai kwata-kwata, kusa da ita ta zo ta zauna tana ɗagawa Dr gaisuwa, da fara'a ya amsa tare da tambayarta ya school, lfylou Alhadulillah ta amsa mashi da shi, daga nan ta dawo da kallonta kan Rimsha, ganin yadda ta yi kasa da kai kamar zata yi kuka ne yasa ta ce mata "Meesha mu je ki nuna Mani in da kika ajiye kayan mun can" to ta amsa a tare suka miƙe Akila tana faɗin "Yaya Nawid ina nan dawo maka da ita" bai kawo komai a ransa ba, sai murmushi ma yake yi ya amsa mata da tayi sauri fa. Suna shiga ɗaki Akila ta ja ta rungume ta, kasa-kasa ta fara magana "Rimsha ki dai'na ɓata rai kin ji? Ba ke kaɗai ce baki son shi ba har da ni, dan Allah ki saki ranki, idan kun ɗan yi hira na 30mins sai ki ce mashi kanki na ɗan maki ciwo zaki kwanta, kinga a haka za ku rabu lafiya, amma a duniyar yanzun nan baa fitowa mutun filli anuna ba'a son shi, wlh zaki ga uwa ɗaya uba ɗaya kuka fito da mutun ma a zamanin yanzu yana iya kashe ki akan abin duniya, dan haka ki sani ba'a shedan ɗan adam, ki san taya zaki zauna da kowa, kada ki damu In Sha Allah idan Lion ya fara son mu ba sai ma kin yi masu magana ba, ina da tabbacin sunan shi ma kawai idan suka ji daga ranar wlh ko millon nawa za'a basu, babu mai kara zuwa wajen ki ko ya kira ki a waya, so dan haka ki kwantar da hankalin ki, kuma yadda kike bala'in kaunar Lion mijin mu, dan ni na bashi ke, na san wlh ba zaki taɓa son kowa ba, bana son ki nuna musu tsanar da kika yi masu a fili, duk da yake abokin yaya Imran ba zamu yi shedar shi ba, ke bama su ba, mi sali ko yaya Akil ba zaki yi shadar abin da zai iya aikatawa akan abin da yake so ba, dan haka ki natsu komai cikin taku zaki bishi, yaya Imran ya ce zai zo wajen gyaran jiki ya same gobe da yamma idan yaya Akil ya kai mu, wai da na ce ba ya tafi Abuja ba? Sai ya ce mani wai ai daga Abuja ne zai zo ganin mu ya koma, wlh daga jin zancen yaya Imran tsara kayarsa ya yi, to ni dai nawa ido, yaya Akil kuma ya ce gobe zai yi maki komai na school, da da farko na ɓata rai, amma da na ji ke kike so, na hakura idan Allah ya yi muna da rabon fita Usa ɗin zamu fita In Sha Allah, yanzu dai ki je ku ɗan yi hira, kada ya zargi wani abin, ki saki ranki kin ji?". Sosai ta ji shawaran Akila, kuma tana kara kaunar Akila sosai a ranta, saboda yadda take kara mata karfin gwiwa akan Lion, tana bata shawara mai kyau, tana nuna mata hanyar da ta dace, babu cuta ba cutarwa. Rungumar juna sosai suka yi Rimsha tana faɗin "Aunty Akila nagode, Nagode sosai kin ji ko?" "Ba komai yar uwata, wlh ni kamar yadda su yaya Akil suke yan uwana haka kema na ɗauke ki, kuma daɗin daɗawa kema haka kika ɗauke ni, har kika iya gaya mani sirrin ki da ba zaki iya gayawa Jehan da kuke uwa ɗaya uba ɗaya ba, kai na ji daɗi kuma dole na riƙi ki amana saboda kema yar amana ce, yanzu dai ki je kada ya yi tunanin wani abin kin ji?" Gyaɗa mata kai ta yi alamar to daga nan Akila ta sumbaci lallausan kumatun, yar dariya ta yi har sai da dimple nata suka lotsa sosai, sannan ita ma ta sumbaci Akilar suka yi sallama, ta koma palon. Shawaran Akila ya sanya ta samu natsuwa da farin ciki, ta ji gaba ɗaya ta saki ji, Akila yar baiwa, karama da hankalin manya, yar albarka, zama da kowa lafiya, kaunar kowa da kowa har wanda ma ya ce baya sonta, ita tana kaunar shi, ga A'afia nan bata sonta amma ita tana bala'in kaunar su dukkan su. Hayewa ta yi saman bed ta kwanta tana tunanin yadda zata kaya, tana tunanin dole yau ta yi wa Rimsha tsawuyar dare dan Allah ya dafa masu, bata son ganin Rimsha cikin damuwa ko kaɗan. Wayar Rimsha dake a gefen ta ne ya fara kara alamar shigowar kira, kobata ɗuba ba tasan mai kiran, Ahmad ne. Ai kuwa tana dubawa shi ɗin ne, picking call ɗin ta yi suka gaisa tare da fara hira suna dariya, a nan ne yake tambayar address ɗin su kamar yadda ya yi wa Imran alkawari, ba musu ta gaya mashi, abin ya ɗaure mashi kai "Kaduna kumam?" Ya maimaita. E ta amsa mashi tare da kara yi mashi baya nin in da unguwar su take. Bata gama rufe baki ba, sai ji ta yi ya ce Heartbeat, ɗan zaro ido ta yi da mamaki ta ce "Yaya Ahmad ya aka yi kasan wannan sunan?" "Heartbeat kin san da waye kike magana kuwa? A'A ne fa" zubur ta miƙe zaune tana faɗin "Yaya Ahmad, yayan Anisa?" E ya amsa mata da shi, a tsorace ta ce "Dama kai ne mai son Rimsha?". Babbar magana, Rimsha ta haɗa kuɗi da kuɗi kuma mulki da mulki faɗa, ta haɗa gwanki da Gwanki ita kuma tana can tana tunanin uban su a kuɗi da mulki, zuciyarta na a wajen Lion, wannan wace iriyar jarabawa ce? Lallai akwai rikici ba kaɗan ba, domin kuwa baban A'A SALAHUDDEEN idan ya samu labari to zai iya sanyawa a ɗaure Nawid ma da gaba ɗaya familyn sa, kuma su ɗauru ma har igiya ta saura, Ya Allah kasa Lion ya so Rimsha ya ɗauketa duk wannan rikici ta kauce, domin idan ba Lion ba babu wanda ya isa ya kwace ta daga family'n A'A SALAHUDDEEN, ga shi family'n sa basu da mutunci, sun raina talakawa, ganin talaka suke yi kamar takalmar sawarsu, yau ake yinta. Duk wayan nan zan tuka Akila ke yin sa a cikin zuciyarta, a yayin da shi kuma Ahmad sai hello yake ce mata. Soyayya mai saka Duk wani kuɗi da mutun yake ji da ita ya ajiye ta a gefe, banda haka me A'A SALAHUDDEEN zai yi da Rimsha? ga ruwa kuɗi abin da ake cewa kuɗi a tattare da shi, ga kuma uwa uba siyasa, kai anya ba mafarki nake yi ba kuwa. Akila kenan ta kasa wani kata ɓus sai tunane tunane take yi a ranta, abin ya kulle mata kai. "Heartbeat ki yi mani magana mana, dama Rimsha kanwar Prof ce?" Da kyar Akila ta iya sai ta natsuwarta ta ce "E yaya Ahmad, kanwar mu ce" "Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun rashin sani yafi dare duhu, yanzu kenan ita ce ɗazun ya ce zai bani na ce bana so, to Alhadulillah dai tun da abin ya zo da haka, ya zo mani da sauƙi, ranar Friday ina nan shigowa, nan da kwana huɗu kenan, dan Allah heartbeat ki kula mani da ita sosai kinji ko bugun zuciyar mu?" Gyaɗa mashi kai ta yi, ta ruɗe sosai tana al'ajabin abin, in dai mutun zai iya fitowa daga family'n A'A SALAHUDDEEN ya mutu akan Rimsha sosai haka, to da izinin Allah shima Lion zata iya yi wu ya so ta, kai A'A SALAHUDDEEN sune fa kasar nan gaba ɗaya a yanzu, kuma shine yaron *ABDULLAHI ABUBAKAR SALAHUDDEEN* na farko, yana da kanne mata huɗu da maza biyu, dukkansu basa a kasarnan suna England, ita kuma Anisa daddyn nasu ya rabu da maman nata ne yasa suka dawo Kaduna da zama, A'A yana bala'in kaunar Anisa sosai, saboda mamanta tana da kirki, da farko daddyn su ya so kwace Anisar, sai da Ahmad ɗin yasa baki sannan ya barta wajen maman nata, gaba ɗaya Family suna mutuwar kaunar Ahmad, shiyasa idan ya yi magana ba'a cewa aa, a yanzu haka duk cikin ƴaƴan *ABDULLAHI ABUBAKAR SALAHUDDEEN* Ahmad ne kawai yake a Nigeria sai Anisa da dama bata taɓa fita ba, suna da ruwan tsabar kuɗi abin da ake kira da asalin kuɗi ba kaɗan ba, abin ba'a magana, sannan duk cikin familyn SALAHUDDEEN Ahmad ne kawai ya ciri tuta yake iya zama da talakawa, yana da kirki sosai da sosai da kaunar mutane, yana da kyauta da saukin kai, ba shi da girman kai ko kaɗai, bai ɗauki rayuwa a komai ba, sai ita Anisa ta biyu, ita ma akwai izzar jinin baban nata a tattare da ita, sai dai itama zama da mamanta yasa take kaunar mutane, kun dai san tarbiyar uwa dole na daban yake, to wannan ma haka ne. Kamar zautatciya haka Akila ta faɗa duniyar tunani, ta ruɗe sosai, dan bata taɓa zaton hakan ba. Da Ahmad ya ga ji da magana, sai ya katse kiran, dan yanzu bai wani damu ba, tun da ya san har in da suke, idan suka mashi ba daidai ba suga diransa cikin Kaduna a daran nan, TO FA!! (Akwai cakwakiya kenan, ni dai na haɗa kaya na zuwa wajen babyn daddy da kuma daddy, wato gidan Abbi.) Su Aunty yau duniya ta samu, miji ya dawo sabo, sai tarairayar abin ta take yi, har wani liliya shi take, yau ansha soyayya an bar Ayla a Palo, almost 2 hours tana zaune a palon tana tunanin nata Babyn. Sai can ya shigo palon bakinsa ɗauke da sallama, cikin sauri ta miƙe zaune tana faɗin "Sannu da shigowa daddy" hararar wasa ya wurga mata kafin ya ce "To mummy" "Mummy kuma daddy?" Ta faɗa tana zaro ido. Saman sofar kusa da ita ya zo ya zauna yana fiskantar ta ya ce "Me ya kwantar da ke a palon nan? Kuma me kike tunani?" Sunnar da kai kasa ta yi, tana wasa da yan yatsun ta, kasa-kasa ta fara magana "Babu komai dama muna hira da Aunty ne sai Abbi ya dawo suka wuce ciki, shine sai na kwanta nima a nan ina jiranta" "To tunanin me kuma kike yi?". Yar murmushi ta yi kafin ta ce "Tunanin ka mana daddy". Bai san lokacin da ya saki cool murmushi ba, har cikin zuciyarsa ya ji wani sanyi ta ratsa shi (ko wani Namiji yana son ace ana yi da shi, ko da kuwa ba'a yi, matukar za'a ce ana yi da shi, to ba makawa zaka juya shi yadda kake so.) "Baby dama kina tunani na ne haka?" Gyaɗa mashi kai ta yi tare da faɗin "E ina tunaninka sosai ma". Cike da zumuɗi ya ce "Okey gaya mani tunanin me kike yi akan mijin naki?". Wayyo bata iya karya ba, kuma bata iya ɓoye abu ba, sai ta gaya mashi gaskiya tana ta tunanin ya za su yi idan suka yi aure. Ai kuwa bai san time da dariya ta kubce mashi ba, hannayenta ya riƙo yana faɗin "Babyna Allah wasa wasa kin iya soyayya fa, oya gaya mani waye ya koya maki? A tunani na sai na koya maki, ashe dai kin iya" ɗago da kai ta yi tana kallon kyakkyawar fuskarsa. "Daddyna Rimsha ce ta koya mani, ta iya abubuwan soyayya sosai, zama da na yi da ita ne na koya, kuma aunty ma tana daɗa koya mani wasu ai". (Rimsha tamu sarkin soyayya ba🥰 ita ta koya mata) Ɗan masowa kusa da ita ya yi yana faɗin "Da gaske?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e. "Wow ki ce na shirya kenan ba? Zan sha soyayya ko?" Yana magana yana kallon yadda take guntse dariya, Zata yi magana muryan Abbi ya katse su yana faɗin "Kai kai kai kwarto a gidana da tsakar rana ban sani ba! Maik me nake ganin nan". Da yake sun saba wasa haka, sai ya fara murmushi yana ɗan shafa kansa. Aunty kuma dake biye da Abbin a baya, sai murmushi take yi ta ce "A'a yayana ba kwarto bane, matarsa ya biyo kamar yadda kai ma ka biyo matarka" "Yauwa Sadiya gaya mashi gaskiya dai, ni mata ta na biyo" Ita kam Ayla kamar zata nitse kasa saboda kunya. "Maik Sadiya kun saka mani kanwata jin kunya haka ba, gaskiya baku kyauta ba, Aliya ta so ki zo abin ki, kai kuma Maik kada na sake ganin ka a nan, kawai ka zo zaka tsara mani yar kanwata, to wuce ka tafi mun san halin ku maza". Gaba ɗayan su kayatatcen murmushi ne akan fuskokinsu. Da gudu Ayla ta miƙe zata gudu wajen Abbi, da sauri daddyn Jelly ya riƙota yana faɗin "Au sai kika yarda da yaya Deen, za ki bar mijinki ki gudu wajen shi? Kina ji fa cewa ya yi kada na sake zuwa wajen ki, zaki yarda da hakan? Zaki yarda daddyn ki ya yi maki nisa?" Kallon Abbi ta yi sannan ta dawo da kallonta kan shi, gera ɗaya ya ɗaga mata alamar yana jiran amsa. Kasa-kasa ta ce "A'a ka yi hakuri ni nafi son zama da kai". Tafi Aunty ta sa tana rangaɗa guɗa, shi kuma Abbi cewa ya yi "Eyeee to ba ku isa ba, dole ku zo ku shiga da ga ciki, ni za ku yi wa tsiya, Maik Aliya lallai kun riƙa, ke wato kin fi yarda ki zauna da shi, to wlh Jumma'a mai zuwa ina ɗaura maku aure sai ki bishi ku je ku zauna a part nasu, amma ni ba za ku min iya shege a nan ba". Sai dariya suke gaba ɗayan su, ita kuma Ayla ta sunnar da kai kasa tana jin wani irin farinciki mai ratsa jiki a tattare da ita, sosai dukkansu suka ji daɗi, domin burinsu dama ta samu farinciki da natsuwa, ta rinƙa mance damuwar da take a ciki, wannan dalilin yasa ma dukkansu suke yawan wasa da ita, shima Abbi ya san tarihinta domin daddyn Jelly ya gaya mashi komai, Aunty kuma da suka shiga ɗaki yanzu ta gaya mashi cewa daddyn Jelly na son ta, ba karamin farinciki ya ji ba, domin ya san zata samu kulawa sosai wajen shi. Kasa kasa ya ce "Babyna kunya ta kike ji ne?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e, zai sake yin magana aunty ta riga shi da cewa "Yaya Maik yanzu dai na dawo bayan Ayla, ka sakar mana hannu atom". "Wai ke Sadiya duk wannan hali da nake a ciki ba ke kika jefa ni ba? Ina zaman zamana kika sani yin soyayya ba shiri, to kuma yanzu sai dai ki zuba ido, wai ma hannunki na riƙe ne ko hannun matata?" Ya tambaya yana zaro mata idon nan nasa cikin wasa. Cikin sauri Abbi ya tari numfashin su da cewa "Dakata ai hannun matata ya fi karfin ka riƙe matso nan Halima ta" dariya suka yi, ta faɗa jikinsa tana faɗin "To ni dai mijina ko ina zan bugi kirji in ce nawa ne, kai kuma taka har yanzu for sale ce" wani irin kallo ya wurgo mata da dara-daran idanun nan nasa kamar ball, yana ƙoƙarin yin magana kenan Abbi ya riga shi da cewa "Mai da wukar, Aliya taka ce kai kaɗai ba for sale ba ce, ni dai na baka ita amana, ka kula mani da ita sosai, idan kuma ka shirya ranar Friday sai a ɗaura auren a wuce wajen, idan ya so daga baya za'a yi su walima da sauransu, tun da tana son ka, ta faɗawa Auntyn ta da bakinta tana son ka ni ban ga wani abin ɓata lokaci ba". Sakin hannayen nata ya yi yana faɗin "Ai gaskiya yaya Deen matar nan taka yar sa ido ce, ni ko na yi auren ma ba zan zauna a nan ba, zata saka mani ido sosai, kuma gaskiya ina son abar mani baby na tayi karatu" ya kai karshen maganar tare da nufar hanyar fita daga palon. "Kai dawo nan, yanzu Halimar kake cewa yar sa ido a gaba na? To baka isa ba, dawo maza ka kwashi albarka ko ka yi Sa'a auren naka ya yi albarka ku haifo mana wani Hosain ɗin tun da wancan ya guje mu" Jin sunan Hosain yasa ya juyo yana faɗin. "Yaya Deen in dai albarka Sadiya mai sa ido ne bana so, kuma ta dai'na sakawa matata ido, sannan Hosain fa ya tura mani later kafin wayan nan abubuwa su faru, shine ashe ya samawa company na wannan contract ɗin a lokacin, ko yana ina bawan Allah nan oho, ni bani wayarka ma bari na kira Imam in ji ya ake ciki" Miƙa mashi wayar Abbi ya yi yana faɗin "Ai Hosain zuciyar bala'i ke gare shi, kyale shi idan suka gama guje gujen nasu za su dawo ne ma, muna nan muna jiran su, kuma duk halin da muke ciki yana sane, abin yana bani mamaki, kaga hakan ya nuna cewa yana kusa da mu kenan" Karɓar wayar daddyn Jelly ya yi yana faɗin "Haka ne yaya Deen, shikenan ai tun da yana cikin ƙoshin lafiya ba wata matsala, amma dai ni ɗin ne kasan ba zan iya jure rashin shi ba, domin tsakani na da shi yafi kusa akan tsakanin shi ɗaku". "Haka ne Maik to yanzu ya batun auren dai" Jin haka yasa Ayla ta wuce sama da sauri abinta. Bin ta da kallo daddyn Jelly ya yi har sai da ta kurewa ganin sa, sannan ya ce "Yaya Deen ka kunya ta mani mata fa, ni ina son a barta ta yi karatunta, amma dai za mu yi magana idan muka haɗu a masallaci sallar mangariba" ya kai karshen maganar tare da ficewa da sauri. "Gaskiya Halima na ji daɗi da Maik zai yi aure, koba komai zai saku natsuwa, kwata-kwata fa shakarunsa ba za su wuci 38 years ba, amma ya azabtar da kansa da zama ba mata" "38 years kuma Abbi?! Kai ya naji shekarun nasa kaɗan?" Yar dariya Abbi ya yi yana faɗin "Wlh 38 years ya ke da shi zuwa 39 haka". "To ita kuma Jelly shekarunta nawa?" Aunty ta kara jefa mashi tambaya tana mamaki "Ina jin 16 years take da shi, kin san Maik tun yana ɗan shekara 20 ya yi aure saboda bala'in Hadiza, hakan yasa ma bayan ya yi auren ya tattara ya koma Kano da zama, dan ya ɗan hutawa fitinarta, da aurensa bai fi shekara ɗaya zuwa biyu ba suka Haifi Jalila, ranar kuma da mahaifiyarta ta haifeta a ranar Allah ya karɓi rayuwar uwar, daga lokacin Maik ya mai da hankalinsa ga kasuwancinsa, yana kula da Jalila sosai da sosai, ba yadda ba mu yi da shi ba akan ya yi aure amma ya ki, na so ɗaukar Jalila na riƙe mashi ita, nan ma yaki yarda, yan uwan mamata sun zo ɗaukarta daga Katsina suma yaki basu, akwai wasu yan uwan maman nata a Kano, suma sun jarraba ɗaukarta amma yaki yarda, haka ya shawala ya reni kayarsa, daga karshe kuma Allah ya raba su, Maik bai taɓa rabuwa da Jalila ko daidai da na rana ɗaya ba, sai wannan ɓatar da ta yi kinga kuwa dole ya shiga tashin hankali". Sosai Aunty ta tausaya mashi ta kuma kudiri niyar sai ta sanya shi agaba har sai ya yarda anyi auren nan da wuri, zata rinƙa gyara mashi Aylarsa sosai har sai ya kasa hakura ya ce a ɗaura kawai. (Kai Aunty kema ba baya ba🤔🤣 wai sai ya kasa hakura ya hmmm 🤣) Wucewa Abbi ya yi ya nufi kofar fita, yana yi mata sallama, cike da so da kauna, yau ansha love komai ya wuce kamar ba'ayi ba. Yana tafiya ta zauna saman sofa tana godiya ga Allah da sauƙaƙa mata komai, abubuwa suka zo mata cikin sauƙi. Zaman minti 10 ta yi a wajen sai ga Hajiya Hadizatu ta faɗo mata cikin palo babu ko sallama, bata bi ta kan ta ba kawai ta haye sama abinta, binta da ido kawai Aunty ta yi tana mamakin jahilci irin nata. Ɗaki ɗaya daga cikin ɗaku nan dake a sama ta shige ta kwanta a saman bed wai ta dawo gidan mijinta. (To fah akwai rigima kenan, Hajiya Hadizatu manya, mu dai bari mu matsa gaba ato) A ɓangaren daddyn Jelly kuwa yana fita part nasu ya wuce, a palo ya tsaya ya kira Engr Muhammad Imam da wayar Abbi, a nan ya samu sakon da ya birki ta mashi ƙwaƙwalwa, wannan sakon kuma ba wani saƙo bane fa ce baban Muneer ya tura wa Engr Muhammad Imam wannan Video na daddyn Jelly, ya kuma ce ya bawa daddyn Jelly nan da sati uku idan bai bayyana ya kawo Jelly an ɗaura masu aure da Muneer ba, to kamar yadda ya turawa Engr Muhammad Imam wannan video haka zai turawa duniya baki ɗaya. Babbar magana. Har wani jiri daddyn Jelly ya fara gani bawan Allah, zama ya yi a saman sofar su yana hawaye, yana dana sanin wannan rayuwa tasa, sosai Engr Muhammad Imam ya rinƙa bashi hakuri tare da gaya mashi shi ya goge video ma daga wayarsa, kuma yasan shiri aka yi mashi, yasan halinsa mutumin kirki ne shi, yasan na zai iya aikata hakan ba. Godiya ya yi wa Engr sannan suka yi sallama ya kashe wayar ya zauna yana tunanin mafita, haka kawai zuciyarsa ke gaya mashi ya gayawa yan uwansa halin da yake a ciki, ko da akwai wani abin da za su iya taimaka Mashi da shi, shiru ya yi yana tunanin waye ya kamata ya gayamawa, haka kawai ya tsinci kansa da yanke wa kansa hukuncin ya gayawa Imran, domin Imran shine yasan komai nasa, yafi yarda da shi sama da kowa, kuma yasan Imran ya san halinsa dan haka zai masa kyakkyawar fahimta. Ba tare da dogon tunani ba ya kira layin Imran ɗin, bugu ɗaya ya ɗauka a lokacin yana tare da Lion, shi yana kwance saman gadon, shi kuma Lion yana zaune a bakin gado yana latsawa, dan aiki yake yi sosai akan case ɗin James da batun zuwan su Tga. Ba tare da ɓata lokaci ba daddyn Jelly ya sanar da Imran duk abin da yake faruwa, tashin hankali iya tashin hankali Imran ya shiga, har wani miƙewa zubur ya yi zaune a tsakiyar gadon, nan take zufa ta fara tsastsafo mashi daga gefe da gefen fuskarsa, a ruɗe ya furta "Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun wannan wace iriyar bala'i ce" ko kallon in da yake Lion bai yi ba, kamar ba shi a ɗakin. Sosai ya rinƙa bawa daddy hakuri yana bashi baki. Bayan sun gama wayar ya zauna shiru ga zufa sai kara tsastsafo mashi yake, fuskarsa ta yi sharkaf, gaba ɗaya jikinsa ya yi la'asar, dama akan wannan dalili Jellyn sa ta bar gida? Ya ilahi ya lillihi, nan take ya fara ganin jiri, ɗakin na juya mashi, haka idanuwansa ma suka fata juya mashi kamar fanka, dafe kansa dake matsanancin sara mashi kamar zai fashe ya yi yana ambato sunan Allah. Ba tare da ya ɗago ya kalle shi ba ya kyasta mashi wayan nan fareren dogayen kyawawan yatsu nasa a fuska, gently ya ce "Prof be a man mana, why ka ke yin abu like Asif? Even Asif ba zai yi hakan ba? Tell your uncle da ya turo mani da number guy ɗin, zan duba case ɗin because of you". Saboda farin ciki Imran bai san time da ya kurma ihu ba, kallo ɗaya Lion ya mashi ya haɗiye ihun yana faɗin "Wow thank you so much, i really appreciate, i really like this my uncle, yana da...." Bai kai karshen maganar ba Lion ya ɗaga mashi hannu alamar ya ishe shi haka nan, baya son surutu. Bai wani damu ba tun da Lion ya shiga case ɗin ya san 2 hours ya yi yawa za su damko baban Muneer kuma ya sha bugun maza, domin duk abin da daddyn Jelly ya faɗa Lion yana jin su, hakan yasa ya ce zai shiga case ɗin, domin daga maganar mutun yake gane mai gaskiya da kuma mai karya a cikin su, yana aiki da ƙwaƙwalwarsa sosai, da ƙwaƙwalwa yake tace abu, so ya gane daddy jelly yana da gaskiya daga cikin maganar tasu. Sai zumuɗi Imran yake, ya kira daddyn Jelly ya ce ya tura mashi number baban Muneer, kin tura mashi daddyn Jelly ya yi dan yana tsoron kada Imran ɗin ya kira shi ya ce zai zage shi ko wani abin, shi kuma ya ji haushi ya saki Video wa duniya, hakan yasa ya ce shi ba shi da number a kansa, bai san cewa mai gayya mai aiki ne na shiga case ɗin ba. Daga jin maganar daddyn Jelly na bai da number a kansa Lion ya san karya yake yi, abin kuma ba karamin haushi ya bashi ba, dan bai son mutun makaryaci, dan haka sai ya ce da Imran ya kyale shi ba zai yi aikin ba, Imran kamar zai yi kuka ya ce kada ya damu zai samo mashi number a hankali, shiru ya yi bai sake magana ba, daga haka Imran yasan cewa e fa ba zai shiga case ɗin bane, domin baya magana biyu. Tsabar takaici har sai da idanuwan Imran suka cika da hawaye, ko ajikin Lion sai ma miƙewa da ya yi ya shiga toilet dan yin wanka. Yana shiga toilet Imran ya fara zubar da hawaye, kafin Lion ya fito ya sha kukansa dan bakin ciki. Shiryawa ya yi cikin wata kyakkyawar tsadaddiyar jallabiya fara tas, ya feshe jikinsa da wannan fitinanniyar perfume ɗin nasa, sannan ya gyara dark black curly hair sa tare da sanya black face mask a face nasa, ya dauki wayarsa ya nufi waje yana faɗin "Remain 20mins ayi sallar mangariba ka same ni a masallaci" daga nan ya fice abinsa. Da kyar Imran ya iya miƙa wa ya fito ya nufi nasa ɗakin, wanka ya yi ya shirya shima cikin jallabiya fara, sauri-sauri ya fito dan har an fara tada hiƙama da yake akwai masallaci a unguwar tasu, suna ji ta lasfiƙa. Duk wanda Lion ya wuce shi sai ya juya ya kallesa dan ya ga waye mai wannan kamshin turaren, perfume ɗin tana da karfi ne sosai. Bayan sun yi sallar mangariba da isha ne suka fito zuwa gida, yau Imran kamar wadda ruwa ta cinye shi haka ya zama, so silent, shi kuwa Lion ko a jikinsa, dan dama shi zaman shiru ita ya fi kware wa, bai iya magana ba, baya ma zama a in da ake surutu. Suna tafiya kamar gumaka, daidai za su shiga kwanar da zai sada su da gida, dan da kafa suka fito, Lion ya sa an kawo mashi mota kirar *Bugatti cantodieci* daga gidan gwamnar Kaduna, sanna ya sai wata sai dai ita bata iso bane, amma idan zai je masallaci da kafa yake tafiya dan saboda samun lada, kuma masallacin ba nisa, ya san cewa idan mutum ya je masallaci da ƙafarsa, iya adadin kurar da ta hau kafarsa iya ladar da zai sa mu, kuma sunnar annabi ne ma zuwa masallaci da kafa, hakan yasa kawai ya zaɓi zuwa da ƙafarsa ya bar motar. A daidai wannan kwanar wasu yan jagaliya suka tare su, irin matasan nan ne masu shaye-shaye yan kwacen waya, da yake darene sai Allah yasa suka tare gamonsu. Duka duka tsawon dogon cikinsu ma bai wuci a kirjin Lion ya tsaya ba, shi ma Imran ɗin da kaɗan ya haura kirjin Lion ɗin da tsawo, wasu yan guntaye a gabansu amma a haka suka zaro wasu ruɓaɓɓun wuƙaken su suna cewa su Lion su kawo wayoyin hannunsu da kuɗi. (Kwacen waya ko ina, Kasata!! Kasata!!😭😭 Allah ka kawo mana sauƙi) Hannu Lion yasa ya buɗa su daga kan hanyarsa zai wuce, ma'ana yasa hannu ya matsar da su daga kan hanyarsa, dan ya san idan ya ce zai dake su to wlh duka ɗaya zai yi masu ba za su sake moruwa ba, wasu ruɓaɓu da su, shi kuma yau bai fito da niyar dukan kowa ba, hakan yasa ya buɗa su zai wuce. Da gaske wannan yaron babba mai ɗan tsawon cikin nasu ya yi yunkurin caka wa Lion wukar hannunsa a ciki Wani wawan damka Lion ya yi wa hannun yaron tare da murɗeta baya, ji kake kass kashin ta ɓalle, tuni yaron ya saki wukar ta faɗi kasa yana kurma ihun azaba, da hannu ɗaya Lion ya yi wurgi da shi kefe guda, a guje sauran suka juya za su gudu, a zafafe Lion ya damko biyu daga cikinsu ya haɗe kansu ya buga da karfi suka yi gwarel, sai ga jinin ya fara malala daga goshin su. Yunkurin yin ihu suka yi, ya toshe masu baki tare da yin wurgi da su gefe, nan suka sume a wajen Da farko bai yi niyar dukansu ba, amma da ya ga da gaske suna iya cakawa mutun wuka a kan yar waya shiyasa ya musu duka ɗaya ba tashi, kwata-kwata bai ɗauka haka abin yake ba, bai ɗauka za su iya kashe rai akan yar waya ba. Biyun da suka gudu ma, taku biyu ya yi ya damkosu, dukkan su duka ɗaiɗai ya musu suka sume a wajen, ganin jama'a sun fara taruwa a wajen ne saboda ihun da yaro na farko ya yi, dan ma dai sauran ya toshe masu baki, hakan yasa suka wuce cikin gida, shi kam Imran ko ajikinsa, domin hukuncin da ya fi haka ma yasha ganin Lion yana yi. Suna shiga cikin gida Lion ya bawa wannan soja mai gadi umarni akan ya tattaro mashi sumammun masu kwacen wayar ya kawo su cikin gida, dole ya koya masu hankali da har za su iya kashe rai akan waya, dole su fiskanci hukunci. Da haka ya wuce izuwa cikin gida, kai tsaye ɗakin Lion ɗin suka wuce, yana shiga ya cire jallabiyar jikinsa, ya rage daga shi sai Short da singlet farare tas kamar yanzu ya cirosu daga ledarsu. Saman gado ya hau ya kwanta yana tunanin yadda zai je ga James gobe. Shi kuma Imran saman bedside drawer ya zauna yana tunanin daddy'n jelly. Ni kuma na haɗa kayana zuwa wajen bandits😭 😭💔BANDITS😭💔 Su Aafia suna nan a wajen cike da tashin hankali da damuwa, sun yi kuka har sun gaji, daga ƙarshe suka hakura suka fawwalawa Allah komai. Ɗaya daga cikin bandits ɗin ne ya zo ya damko wuyar hijabin jikin Hanan ya miƙar da ita da nufin ya tafi da ita, da sauri mamanta ta tashi ta riƙotana tana kuka da hawayenta tana faɗin "Ina za ku kai min ita? Na shiga uku na, dan girman Allah ku yi hakuri, ku rufa mani asiri, ku tausaya mani, ku kyale mani ita". Kafa ɗan bandit ɗin nan yasa babu tausayi bare imani ya dake maman Hanan ɗin ta faɗi kasa tana kuka, ƙoƙarin kwacewa ita ma Hanan ɗin ta yi dan ta je wajen mamanta, wani wawan mari ya sakar mata a kumatunta tare da janta da karfi suka nufi wajen ɗakunansu. Kankame maman Zahrau Aafia ta yi tana kuka kamar ran ta zai fita, ga shi yau kwata-kwata ba su basu abinci bama, yunwa kamar zai kashe su, ita ma maman Zahraun a wannan gaɓar duk taurin zuciyar ta sai da ta yi wa Hanan kwalla, dan tasan lalata mata rayuwa za su yi. Da gudu maman Hanan ta kuma tashi ta yi kansu dan ba zata iya bari a tafi mata da Hanan ɗin ta tana ji tana gani ba. Kankame Hanan ɗin ta yi tana kuka sosai kamar ba zata rayu ba, har wani kwazura maƙoshin ta yake yi saboda kukan da take yi. Gaba ɗaya wayan da aka kama da suke ganin meke faruwa ba wanda bai yi wa Hanan kuka ba, domin yarinya ce karama, kuma idan suka tashi yi ma mace fyaɗe ba ruwansu da budurwa ce ko matar aure, shigar karfi suke yi mata, lokacin da suka yi wa Zahrau fyaɗe yarinyar nan Allah ne kawai ya kaddara zata rayu, amma ba don haka ba, taci bakar wuya, tana suma tana farfaɗowa, ba wanda ya yi tunanin zata kawo yanzu bata mutu ba, kuma tun da suka yi mata fyaɗen bata sake samun lafiya ba, kullun tana cikin ciwo baiwar Allah, Allah ne kaɗai yasan me yake damun ta, domin ba likitan da zai dubata, sai gayyar paracetamol da suke ɗura mata idan jikin nata ya tsananta. Da karfi ɗan bandits ɗin nan ya hankaɗe maman Hanan ɗin ta sake faɗuwa kasa, duk da haka bata daddara ba, uwa ba wasa ba, sake miƙewa ta yi ta kankame yarta, tana faɗin "Ku sakar mun ita, ku yi wa uwarku da ubanku ku sakar mani ita, ba zan haɗa ku da Allah ba domin baku san shi ba, da kun san shi ba za ku yi abin da kuke yin nan ba, da iyayen ku zan haɗa ku dan sukam kun san su, to dan dajarar iyayenku ku sakar mani yarinya ta, kada ku yi mata wani abin, ni ku yi mani duk abin da kuke so, amma ita ku sake ta". Buba ne ya fito daga cikin ɗakin nasa, rai a matukar ɓace ya sanya bindiga ya harbi maman Hanan a kirji, ji kake dam ya fasa mata kirji, nan take ta zube kasa gawa, ihu Hanan ta kurma daidai lokacin da numfashinta ya ɗauke ta sume a wajen. Duka jama'ar dake a wajen wayan da suka kama ihu suka fara kurmawa, sun ga tashin hankali iya ganin idon su, Aafia kam tuni ta sume saboda tsananin tashin hankali, ita kuma Rufee wannan ihun nasu ya yi sanadiyar farfaɗowar ta daga doguwar sumar da ta yi. Babu imani ba tausayi ɗan bindigar nan ya fara jan Hanan dake sume a kasa zuwa ɗakin nasu, Sani na kwance a ciki yana jiran akawota dan a hannu yake, ta suman ma ba za su kyaleta ba. Ita kuma maman Hanan biyu daga cikin yan bindigar ne suka ja gawarta izuwa wani waje daga can gefe in da suke tara gawarwaki wayan da suka kashe, a nan suka jibgeta a wajen. Idan Allah yasa yan uwanta sun kawo kuɗi da wuri, su sami damar ɗaukar gawar, idan kuma basu kawo da wuri ma har namar jikinta ya daddage to Shikenan. INNALILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJIUN WANNAN MASIFA DA ME TA YI KAMA?, YA ALLAH KA KAWO MANA ƊAUKI, Sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu, a gidan Su Akil dan jin yadda zai yi idan ya ji A'afia bata gidan Abbi, na barku lafiya😭😭 💖💖TRIPLETS💖💖 E 57-58 *Idan kun samu typing error amin afuwa 👏 keyboard ɗin tana bani matsala sosai kwana biyun nan, to na yau ma ya fi tsananta, sai na danna A sai ya koma B😭* 💔😭DEDICATE TO ALL JAMES FANS💪 🔥GIDAN ABBA🔥 AKIL & UMAISHA💘 Yana fita daga part ɗin Imran kai tsaye cikin gida ya nufa. Kwance saman gado ya iskota tana ta kuka kamar me. Hayewa saman gadon ya yi yana faɗin "Wife lafiya me ya faru me?" Kin yi mashi magana ta yi, ta cigaba da kukanta abinta. Ɗagota ya yi tare da mannata da kirjinsa yana faɗin "Haba Wife me ya yi zafi haka?" Har lokacin kin magana ta yi, hannu ya kai zai goge mata hawaye, cikin rashin sa'arta da wawtarta ta buge mashi hannun, wai bata son ya goge mata hawayen, ai kuwa rai a matukar ɓace ta sauke ta daga jikinsa, har da hankaɗa ta ya yi, a fusace ya ce "Ni zaki bugewa hannu?!" Girgiza mashi kai ta yi tana faɗin "A'a ka yi hakuri" Rai a ɓace ya sauƙo daga gadon ya nufi hanyar fita daga cikin ɗakin. "Yaya Akil dan girman Allah ka tsaya ka ji". Kin tsayawa ya yi ya fice daga ɗakin, da gudu ta sauƙo kasa daga gadon ta bi bayansa, yana ƙoƙarin fita daga palon ita kuma ta fito daga cikin bedroom ɗin. Ganin ya yi mata nisa kuma ko ta mashi magana ba zai tsaya ba, sai ta faɗi kasa tare da kurma ihu kamar wadda ta faɗi da gaske ta ji ciwo, ai kuwa cikin sauri ya juyo. Ganinta a kasa yasa ya dawo da sauri yana faɗin "Wife me ya faru? Me ya same ki?" (Kaɗan ka gani in dai kaidin mata ne🤣) Kara sautin kukan nata ta yi, cikin shagwaɓa ta ce "Yaya Akil kafata tana yi mani zafi sosai" da sauri ya kai hannunsa kan kafar nata yana shafawa yana faɗin "Sorry Wife bari na ɗauke ki muje ciki sai na duba maki ko?" Jinjina mashi kai ta yi tana wani turo baki, shikuma ya rikice ya ɗauka da gaske ne, (uhmm mu da muka san maganin ku.) Cak ya ɗauketa suka wuce cikin ɗaki, saman gado ya kwantar da ita tare da cire mata gaba ɗaya kayan jikinta, ya rage daga ita sai pant and bra kawai, sai sannu yake ce mata, ita kuma sai kara narkewa take yi tana wani turo baki tana jinjina mashi kai, goganku fa ya rikice, ba shiri ya fara mammatsa mata kafar tata, sai wani wash take cewa kamar da gaske. Idan ta ce wash sai ya ɗago ya ce mata "Sorry my wife da zafi ko?" A shagwaɓe take ɗaga mashi kai alamar e, daga karshe har hura mata kafar da bakinsa ya koma yi, daga ta cikin zuciyarta sai dariya take yi mashi, daga waje kuma sai kara narke fuska take yi. Tun yana mammatsa mata iya kafafunta har ya fara haurowa sama izuwa cinyoyin ta, daga nan fa labari ta sauya, shima ya fara ramawa, idan ya zo cinyoyinta a maimakon ya matsasu kamar yadda yake matsa kafafun a'a sai ya kama shafasu a hankali hankali yana wani sauke ajiyar zuciya, ita kuma sai kara narkewa take yi dan tasan ba abin da zai yi mata, sai dai su yi wasa kawai kamar kullun. Daga ƙarshe dai kwanciya ya yi ta bayanta tare da ɓalle bra ɗin tata ya fara wasa da breast ɗin ta, ba ɓata lokaci ita ma ta juyo ta fara mai da mashi da martani, nan take suka manne juna, ya fara tsotsarta ta ko'ina, yana yi tana mai da mashi da martani, dan a cewar ta ba abin da zai yi mata. Cikin dabara ya zame pant ɗin tata, haka ya shammace ta sai dai ta ji ya shige ta abinsa, kuka ta fara yi mashi tana bubbuga shi akan ya kyaleta da zafi, ta riga ta tsorata da na farko, so haka take jin na biyun ma da zafi. Shi kuwa bai saurareta ba aikinsa kawai yake yi, sai da ya fanshe wuyar da ta bashi na tsawon lokaci tana hana shi kanta, sau uku ya yi abinsa, ta yi kuka har ta godewa Allah daga karshe ta hakura. Sai bayan ya sami natsuwa ne ya shiga rarrashinta kuma, kin kula shi ta yi tana kumbure-kumbure, bakin sa ya ɗaura saman nipple ɗin ta ya fara sha yana matsa ɗayar yana yi mata murmushi, dukan wasa ta kai mashi a baya tana faɗin "Ni ka sake mani kayana". Cire bakin sa ya yi yana faɗin "Kayan ki ko nawa ni da yarana?" Hannu ta sake ɗagawa zata kai mashi duka, ai kuwa ya yi maza ya jawota ta faɗa saman jikinsa. "Wife yau kin biya ni sosai, naji matukar daɗi kuma nayi farinciki, Allah ya yi maki Albarka yasa na jefa kwallo a raga, mu samu baby's kyawawa kamarki, to yanzu ki shirya gobe muje a wanke maki kan naki, amiki kunshin kema, dan kin sani farinciki kema dole na saki" . Shiru ta yi zantukan Akila suna dawo mata a ƙwaƙwalwarta in da take ce mata, "Aunty Umaisha wlh na karanta a book ɗin Princess Teema da za ta yi next wadda bata saki ba ma ni kaɗai ta bamawa, wlh ta rubuta a cikin duk macen da bata bawa namiji chaskale to ba zai rinƙa yi mata abin da take so ba, amma idan kina gyara kanki kina bashi chaskalewa Allah tsab zai yi maki abu, kuma musamman idan kika samu miji mai bala'in sha'awa, to tanan zaki yi amfani ki more shi, ki san hannunki da kyau, Allah tsab zaki juya shi, ke akwai abubuwa da dama acikin book ɗin sai ta fara sakin shi zan tura maki ki karanta zaki gane, ni dai dan Allah ki kula mani da yaya Akil na kamar Auta jannat da kuma Jahiz na book ɗin Princess Teema, ke anzuba abubuwa sosai hmmm" duka Umaisha ta kai mata tana faɗin "Ke heartbeat kin zama yar iska daga karanta book" "Ba dole ba, ai ina tausayawa saurayin da zan riƙe a masoyi na, wlh ya banu, ni ai wannan sabon littafi na Princess ya gama dani, amma taki bani book 2 na karanta, wlh Princess ta ce idan mijinki ya yi kwana biyu bai sami chaskalen nan ba to haka kawai zaki ga yana jin haushin ki, sai ki rasa me kika yi mashi, idan kin tambaye shi sai ya ce maki babu, da zarar kin mashi abu kaɗan sai faɗa, ke koma baki yi mashi komai ba sai ya jangwalo kaɗar dan kuyi, saboda yana jin haushi, amma da kin bashi ko bai nuna maki yana jin daɗi ba, zaki ga ranshi fes ba faɗa ba komai, kuma karin wani haske in dai baki gyara to gara ma kada ki bashi, dan idan kin bashi haushin ki zai kara ji". Maganganun ne kawai ke dawo mata a cikin ƙwaƙwalwarta, ta yarda da zancen Akila ga shi nan yanzu duk bala'in kishin nasa daga samun chaskalen ya ce ta shirya da ita za'a tafi saloon da gyaran jiki, gaskiya dole na koma Akila ta kara mani wani lecture, ko kuma nima na tafi wajen Aunty princess ta bani book ɗin. Tayi nisa cikin tunanin da take yi bata ankara ba, kawai sai ji tayi ya sureta zuwa toilet. Sai zumuɗi yake yi, farinciki a cike fal ransa, da kansa ya yi mata wanka, farincikin da yake a ciki ko ranar farko bai shiga ciki haka ba. Bawan Allah ya ja tsawon lokaci yana gwauro kuma ga shi da mata a gida. Bayan sun yi wanka da kansa ya shiryata cikin kayan barci, suka yi sallah a tare, dan anriga anyi Sallah a masallaci. Bayan sun kammala ne suka ci abincin da Akila ta kawo masu, yau tsabar tarairaiya a baki ya bata, murnar sa ba zai misaltuba. Bayan sun gama komai ya kwantar da ita a gado ne ya ce mata yana zuwa, fita ya yi zuwa palo ya kira Abbi a waya akan maganar Aafia, nan Abbi yake sanar mashi ai bata nan gidan, shi ma sanar da Abbi ya yi akan bata nan bata dawo ba, sosai suka shiga tashin hankalin musamman ma da Akil ya ce yau kwananta uku bata gidansu, shi a tunaninsa ai ta koma ne, shi kuma Abbi ya ce ai tun ranar da ta tafi taya Umaisha kwana bata dawo ba, Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun nan fa hankalinsu ya yi mugun tashi suka fara kiran yan uwa su ji ko akwai wanda ya ganta. Kowa ce masu yake rabon sa da ita tun kwana uku da suka wuce, cikin ɗaki Akil ya koma ya ce da Umaisha ta yi barci yana zuwa, ko da ta tambaye shi lafiya, sai ya ce mata ba komai zai je ne su yi hira da Abba yana kiran shi, to ta amsa mashi da shi tare da jan bargo ta lulluɓu, kiss ya manna mata a goshi sannan ya fita da sauri. Kai tsaye motarsa ya je ya shiga zuwa gidan Abbi, a harabar gida ya same su sun yi cirko-cirko suna jiransa, ga Irfan da daddyn Jelly, Ayla da Aunty, ita kam Hajiya Hadizatu tana kwance tana barci abinta, bata ma san me ake ciki ba, kuma Abbi bai ma san da tana cikin gidan ba, da yamma ta fito ta dafa abin da take son ci ta koma ɗakin da ta ce shine nata, daga nan kuma bata sake fitowa ba. A cikin wannan dare suka fara neman Aafia, sun je gidan su Rufee nan Maman ta ke gaya masu ai ita ma kwana uku kenan bata dawo gidan, hankalin su idan ya yi dubu to ya tashi a wannan rana, sun ga tashin hankali ba Jelly kuma yanzu ba A'afia kuma dukkansu yan mata bala'in ya musu yawa. A ɓangaren ita kuma Aafia lokacin da Sani ya tashi da niyar ya yi amfani da Hanan da ya ga fuskarta sai ya ce ai ba ita yake son a kawo mashi ba, wancan rainon madara yake so, wato Aafia, haka wannan ɗan bandit ɗin ya dawo da Hanan ya ɗauka mashi Aafia da ita ma take a sume. Babu Imani ba tausayi ya lalata Aafia, ya yi amfani da ita, bakin azaban da ta jine yasa ta farfaɗo daga sukan da tayi, kuka ta fara yi tana ƙokarin turesa daga jikinta, saboda mugunta yawu ya tofa mata a fuska tare da taintsinka mata maruka wadda ya saka ta natsuwa dole. Ba karamin wahala ta ci ba, daga karshe bayan ya gama sai buba ma ya zo wai yana son kwanciya da ita, da kyar Sani ya hana shi domin tana zubar da jini over, yana da matukar wahala ma ta rayu, a haka suka jata zuwa ɗakinsu suka kwantar da ita, jininta zuba yake yadda kasan bada ga jikin mutum jinin ke zuba ba, da alama ya ji mata ciwo matuka, saboda ya afka mata ba da son ta ba, ta kame jikinta ya yi mata shigar karfi shiyasa. A ɓangaren ita kuma Rufee kafarta har ya fara yin wani irin ruwa fari, ya sunduma sumtun kai kace balabalo aka hura sai aka cusa a cikin su, haka suka zama, ita ma ta ci bakar azaba, banda hawaye ba wani abin da ke zuba daga face nata. Idan muka koma ɓangaren bokan ta kuwa, Tabbas ya kwance aikin da ya yi wa Abbi amma da ya zo yi wa daddyn Jelly sai taki yuwa, daddy'n Jelly ya fi karfinsa, aikin ba zai kama shi ba saboda karfin askar da yake yi, idan akayi aikin to zata iya faɗawa ne a kan wanda yake tare da shi, ma'ana makusancinsa, (waye kuke tunani kenan?) haka bokan ya yi aikin daddy'n jelly ɗin sannan ya ɗauko Aiki akan Akil, nan yaga ikon Allah domin duk aljanin da ya gayawa sunan Akil ya nuna mashi hotonsa sai ya ce da ya yi wannan aiki gara bokan ya kashe shi, domin Akil ba zai kamu ba, gidan su Akil ma ya fi karfin su shiga, ko kusa da gidan ba su isa su je ba domin akwai uban nin su a iskanci a gidan, da bokan ya ce to su tsaya idan Akil ɗin ya fito sai su aiwatar da aikin, nan suka ce ba zai yi wu ba, na farko Akil yana da karfin addu'a a tattare da shi, domin babban alaramma ne, na biyu kuma Akil jinin Umaiya ce, babu wani ɗan iska farurin aljani da ya isa aduniyar nan ya kawo wa jinin Umaiya wani wargi, ita kanta Umaiya bata san menene a tattare da su ɗin ba, har ga Allah bata sani ba, ita dai gata nan ne kawai. A ɓangaren su Akil kuwa sun sha wahala wajen neman Aafia a daren nan, daga karshe dai suka hakura kowa ya wuce gida da nufi gobe zasu shigar da kara da duk abin da ya dace, duk wannan abin da ake yi, Akila, Rimsha, Imran, Hajiya Hadizatu, duk basu san meke faruwa ba, suna can ɗakin su. A takaice dai kamar yadda su Akil suka ga rana haka suka ga dare. Washegari tun safe karfe 6 ya fice daga gidan suka dasa daga in da suka tsaya. A WASHINGTON DC KUWA. After 2 hours. Michael ya dawo daidai dan shi bai ci bakar wuyar da uncle Hosain ya ci ba, hakan yasa ya yi saurin dawowa daidai, kuma ya samu kulawar manyan likitoci sosai da sosai. Cikin part nasa ya miƙe ya shiga ya bar Musharraf kwance a saman bed nasa yana barcin wahala bawan Allah, ya farfaɗo sai Dr ɗin suka yi mashi alluran barci dan ya sami hutu. Da yake karatu na a ran Michael sosai, sai ya wuce part nasa ya yi wanka ya sake saka kananan kaya ya fito izuwa wajen da suke karatu da daddy, da yake daddy bai san me ya faru ba sai bai wani tambayi Michael me ya faru ba bai zo da wuri ba. Karatu kawai suka fara yi kuma yana fahimtar sosai, a nan ne daddy ya ce ya kamata suna yi suna practical, to Michael ya ce dan shi ji yake yi komai ma zai iya, kwakwalwarsa zata iya ɗauka. Tga daddy yasa ya kawo mashi monitor lizard dan su gwada tiyatar ciki a kansa, daidai lokacin kuma su Jay suka dawo daga yawon da suka tafi, kai tsaye wajen da daddy ke karantar da Michael ɗin suka nufa, wato wajen basket ball ɗin Michael ɗin. Gaba ɗayansu tsayawa suka yi suna son ganin yadda daddy zai yanka monitor lizard nan kuma ya tashi, kayan Aiki daddy yasa John ya kwaso mashi, cike da kwarewa ya fara da yi wa monitor lizard ɗin allura na kashe zafi sannan suka ɗaure kafafunsa, ya gama gyara komai dai, sannan ya fara tiyatar. Dukkansu zaba ido suka yi har da uncle Herry ga Tga a gefe suna kallon yadda wannan tiyata ke gudana, daddy yana yi yana yi wa Michael baya ni ta yadda zai fahimtar da kyau, badan okey sir ba abin da Michael yake cewa. Haka daddy ya kammala ya ɗinketa kuma ta tashi, tafi suka sa suna faɗin "Well done, good job daddy" da yake shima daddy ba kasafai ya cika murmushi ba, baya murmushi sai ta ƙuƙe mashi, dariya kam shima ba'a magana baya yi kwata-kwata, da alama daddy ma boss ne lokacin da yake tashen sa. "Michael a kawo wata monitor lizard ɗin mu sake gwadawa domin ka fahimtar da kyau". Cikin sauri ya ce "No daddy ni ba sai an sake nuna mini ba, already na haddace komai, dan haka uncle T ya kwanta a bani wuka mai kaifi sai na fara gwada tiyatar cikin a cikinsa, shi kuma John zan gwada na zuciya a kansa, ni fa bana son wannan ɗan karamin wukar, kato mai kaifi za'a bani, kaga cikin uncle T akwai tauri" (To fa tashin hankali) Zaro ido John ya yi yana tunani yadda daddy ya yi wa wannan monitor lizard tiyata a gaban su suna gani, sannan yanzu Michael ya ce suma su kwanta ya yanka su haka, tab ba gwara daddy ba aikin sane ya saba, daya yanka monitor lizard ɗin ya ta shi, ya yi rai, Michael kuma fa? Yanzu yake karatun abin daga nuna mashi sau ɗaya wai ya iya, yazo ya yankasu shikenan su kasa tashi su mutu. Shi kuma Jay bin su kawai yake yi da ido, yana mamakin iskanci irin na Michael, shi komai aka karantar da shi sai ya ce a kan uncle T da John zai gwada, wannan wace irinyar bala'i ce. Uncle Herry kuwa, baya baya ya yi ya bar wajen dan shi iskancin Michael ya fi karfin sa, yaro da ankoya masa abu sau ɗaya sai ya ce shi lallai sai ya gwada kuma a kan su. Tga ne ya ce "Michael are you mad? A cikina zaka gwada tiyatar ma kenan? To ni monitor lizard ne? Kai bakaga ko daddy da yake kwararren likita ma da dabba ya gwada bane? Kai ne shararre ɗan nema shine zaka ce sai a jikin ɗan adam zaka gwada? To baka isa ba, ni kaga tafiya ta ma, barin kasarma zan yi anjuma kaɗan, ka dai'na kallona ko ka huta, haba wannan bala'i dame ta yi kama" ya kai karshen maganar tare da wucewa ya bar wajen. Shi dai Michael ko a jikinsa suka cigaba da abin da suke yi shi da daddy, daddy'n yana lallaɓashi akan ya gwada da wata monitor lizard ɗin, da kyar ya yarda, da ya kafe sai dai akan John zai gwada, amma da daddy ya lallaɓa shi, sai ya yarda da zai gwada akan monitor lizard ɗin. Haka aka kawo mashi wani monitor lizard ɗin ya kwanta ya fara yin komai kamar yadda daddy ya yi, an kuwa yi Sa'a akwai kaifin ƙwaƙwalwa yana ɗinketa sai ga shi ta tashi, sosai daddy ya ji daɗi yana faɗin "Dama na san zaka iya, jinin jacop Roshan babu jahili mara ƙwaƙwalwa, dukkan mu haka muke ba da bala'in kaifin ƙwaƙwalwa". Uncle Herry da ya dawo yanzu ne ya karɓi zancen da cewa "Of course, blood of Jacop Roshan is not easy, ba wasa ba". Shi dai Michael haka kawai ya ji bai ma son Roshan ɗin nan, dan daga jin sunan shine bakin mugun family'n su, da alama shi Tga ya gado (To fa🤔) "Daddy please stop talking about this Roshan, let's continue our practical" ba su wani damu ba dan ya ce bai son hirar kakansu Roshan, dan saboda har yanzu suna ɗaukar Michael kamar ƙwaƙwalwarsa bata dawo normal gaba ɗaya ba, hakan yasa ko ya ce baya son wani basa damuwa. Haka suka ci-gaba da karatun har karfe 6:30 daidai, bedroom nasa ya wuce ya sake yin wanka ya shirya cikin kananan kaya masu kyau, full Jeans har kasa da kuma T-shirt kamar dai yadda ko wani cikakken musulmi yake dressing, yanzu ya daina yawan saka crazy ma, dressing nasa yake yi na cikakkun mutane masu cikakken hankali. Bayan ya gama shirinsa ya feshe jikinsa da perfume mai daɗin kamshi, sannan ya fito, word room ya fara shiga ya duba Musharraf, har lokacin barcin wahala yake yi Bawan Allah. Kan shi Micheal ya shafa yana faɗin "Allah ya saka maka uncle, In Sha Allah zaka samu lafiya" ya kai karshen maganar yana manna mashi kiss a goshinsa. Daga nan ya wuce zuwa waje, kai tsaye parking space ya nufa, kamar yadda suka saba fita zuwa masallaci, haka yau ya fita shi kaɗai, duk sai ya ji babu daɗi, tunani yake yi anya zai iya rabuwa da Musharraf kuwa? Yanzu ma zuwa masallaci shi kaɗai ma ya ji wani iri, ba dan sallar farilla bane da ba zai je ba, amma haka ya daure ya nufi masallacin. Sai da ya yi sallar isha sannan ya dawo gida, lokacin su kuma Tga jirginsu ya ɗaga zuwa Naija, karfe 7 daidai suka tashi. Sai da Michael ya kara shiga word room ya duba Musharraf sannan ya dawo palo suka ci abincin dare, lokacin kuma karfe 8:40, part nasa ya koma bayan sun kammala. Yana shiga ya kwaso takardunsa na makaranta, kafin ya fara karatun boko sai da ya tusa karatun Alqur'ani mai girma suratul humaza da Musharraf ya gaya mashi yau da asuba, bayan ya tusa kaman sau uku sai ya rufe tare da yin addu'a kamar yadda Musharraf ya koya mashi, sannan ya buɗe takardun sa ya fara dubawa yana nazari akansu, abin da ya shige mashi duhu sai ya shiga goggles ya duba, idan ya duba bai gane ba ma sai ya kira Lion a waya akan ya mashi karin bayani, da yake Lion yana son ya yi karatun sosai haka zai zauna yana mashi bayani dalla dalla. Ta ko'ina Michael yana samun taimako a kan karatu, daga daddy har Lion, ga Musharraf shiyasa a take yake haddace duk wani abin da aka koya mashi Sai wutaren karfe 11 sannan ya tashi ya yi wanka ya yi shirin kwanciya tare da tattare takardun ya mai da su in da suke, shiryawa ya yi cikin wando dogo da riga mai ƙaramin hannu, kayan ba su da nauyi, suna da kyau sosai launin brown colar, kalar gashin kansa kenan. Bayan ya gama ne sai ya fesa air freshener a ɗakin nasa tare da rage gudun Ac ya fito waje, kai tsaye word room ya sake nufa, kamar dai ɗazun Musharraf na ta barci har lokacin, yanzu ma addu'a ya yi mashi tare da manna mashi kiss a goshi ya gyara mashi bargon da likitocin suka rufesa da shi, ya haurar mashi zuwa saman kirjinsa sannan ya koma bedroom nasa. Addu'ar barci ya yi ya kwanta tare da kiran Lion video call dan suka ga juna. Umm jini ba wasa ba. A lokacin Lion ya na zaune a tsakiyar bed nasa, ya yi sallar isha tare da wanka ya shirya cikin kayan barci launin sky blue masu shegen kyau, ba karamin kyau ya yi wa kayan ba, ga idanuwansa nan sun yi wani irin yanayi mai kayatar da mai kallonsu saboda yana jin barci, barci ne a cike a cikinsu amma bai kwanta ba, yau idanun nasa sai suka yi kama da sleeping eyes, sai wani lumshe su yake yi, ga red lips nasa nan har wani ja suka kara suna kyalli kamar ya shafa lips balm, shi dama haka face nasa take, tana sheki kamar me, soft skin ɗin nan nasa ba'a magana wajen laushi da sheki. "My Lion barci kake ji ne?" Da gera ya amsawa Michael ɗin akan yes barci yake ji. "Okey to ka kwanta mana" ɗaura wayar ya yi a gaban laptop dake a gabansa domin ya sami dama yana aiki yana kallon Michael ɗin da kyau "I can't sleep now" Cikin sauri Asif ya ce "James ko?" Gera ɗaya ya ɗaga mashi alamar e. "Allah zai biya ka da gidan aljanna My Lion" sai lokacin ya dawo da kallon shi kan Micheal ɗin daga kan laptop ɗin, ba karamin daɗin furucin da Asif ya yi ya ji ba, amma ba wanda ya iya gane cewa ya ji daɗin hakan saboda bai nuna alama ba. "Yaushe zaka dawo?" Michael ne ya tambaya. Sai da ya ɗauki 1mins sannan ya ce "I don't know but know good night" ya kai karshen maganar yana ƙoƙarin katse kiran "I really missed you my Lion" shine abin da Asif ya faɗa wadda yasa Lion dakatawa bai katse kiran ba. Kallon kasar ido ya yi mashi kafin ya ce "Ba zaka canza ba kenan?" Cool murmushi Asif ya sake yana faɗin "Yah in dai akan kune ina nan yadda nake" Shiru ya yi mashi bai sake magana ba. Sai hira Asif yake yi mashi amma yaki tankawa kawai aikinsa yake yi, idan da sabo sun saba, hakan yasa Asif bai damu ba, can kuma sai ya ce "Asif you have class by 7, so good night" ya yi maganar a sanyaye. Mamaki ne ya kama Michael, yaushe Lion kuma yasan suna da class karfe 7, kenan yana bibiyarsu ne? Ko me. Yana tsaka da tunani ya ga Lion zai katse kiran "I love you" shine abin da ya furta jinjina mashi kai Lion ya yi tare da katse kiran ya ajiye wayar a gefensa ya cigaba da abin da yake yi. Sai wuraren karfe 1 na dare sannan ya ajiye laptop ɗin ya fito palonsa ya ɗauki maltina da glass cup ya zauna saman sofa, bayan ya sha ya ɗan jima a wajen yana tunanin rayuwa, haka kawai ya ji lallai yana son taimakawa yan Nigeria, domin ya san suna da kwakwalwa da basira kawai masu taimaka masu ne suka rasa. Sai wuraren karfe 1:50 sannan ya miƙe ya shiga cikin ɗakinsa. Kara fesa air freshener ya yi bayan wanda Imran ya fesa mashi, sannan ya kure gudun Ac, sanyayyar sanyin Ac da kuma kamshin air freshener ne kawai ke tashi, abin ba'a magana, ya kayatar matuka. Ya haye saman lallausan bed nasa ya yi addu'ar barci ya kwanta, tun da ya zo Nigeria baya shiga cikin bargo saboda zafi, haka yake kure gudun Ac ya kwanta, amma sai ya ce a hakan ma zafi yake ji. Yana kwanciya ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi, asuba ta gari. Washigari su Akil suka shigar da rahoto da komai wa yan sanda dan gane da Aafia, kamar yadda ya yi wa su Rimsha alkawari haka ya kai su gyaran jiki da kunshi tare da wanke kai, kuma har da Umaishansa ya haɗa. Suna a wajen gyaran jikin ne Imran ya zo ya same su, a nan Akil ke gaya mashi abin da yake faruwa na ɓatar Aafia, ta shiga tashin hankali sosai shima, sannan ya fara tunanin ko dai bibiyar family'n su ake yi ne, ga Jelly shiru yanzu kuma Aafia anya lafiya kuwa?. Tunani cike fal ransa ya karisa cikin saloon ɗin wajen su Rimsha, tana zaune ta bakin kofa a palo kenan, da yake ciki da palo ne, to a can jiki ake gyaran kai da jikin, palon kuma na zaman wayan da suka yi rakiya ne, akwai kujeru har da Ac, wajen gyara ne babba na ƴaƴan manya. Imran ya samu an gama wa Rimsha nata ana yi wa Akila da Umaisha kuma suna ciki, ta yi kyau sosai da sosai, kunshin ba karamin kyau ya yi mata ba, amma sai da suka goge ɗan ragowar nata da ya rage a kafar tata kafin su yi mata wani, ga shi ta sha gyaran jiki, an kara fito mata da soft skin ɗin nan nata sosai da sosai, sai wani kayatatcen sheki take yi, abin ba'a magana. Imran. Lokacin da idanunsa suka sauƙa a kanta sai da ya ji wani irin, sai da gabansa ya faɗi, ta fito kamar tauraruwa mai haske a sararin samaniya cikin hudun dare. Kujerar gefenta ya zo ya zauna, ya jiki ya fara yi mata, da fara'a ta amsa mashi da sauki. Rimsha kenan idan kaga fara'arta to da Imran ne ko Akila, su kawai take yi wa dariya a yanzu. Hannayenta ya riƙo cike da kulawa ya fara magana "Rimsha zuciyata ta kasa yarda cewa ba wani abin da yake damun ki, dan Allah ki gaya mani menene yake da munki? Ni fa yayan ki ne, idan har baki gaya mani ba waye kike da shi yanzu a duniyar nan da zaki gaya mawa?" Sunnar da kanta kasa ta yi tana ɗan mutsu mutsu da hannunta alamar bata ji daɗin riƙeta da ya yi ba. Ganin haka yasa ba musu ya saki mata hannun nata yana kara nanata mata tambaya akan me yake damun ta. "Yaya Imran ba wani abin da yake damu na, idan da akwai da zan gaya maka". Nisawa ya yi kafin ya ce "Amma me yasa da kika ga Saif kika suma? Me yasa a ganin sa na biyu ma kika suma? Ranar da hakan ta faru naje bedroom naki da daddare dan na duba ki saboda sumar da kika yi, ina tsoron kada ya ja maki wani ciwon da cikin dare, shiyasa na shiga ɗakin ki da daddaren, na same ki kina kuka kina faɗin Allah ya cire maki son shi ki huta, wanene wannan? Tun jiya na kasa runtsawa saboda kina cikin damuwa, abin ya tsaya mani a raina, idan na barki haka to tabbas ban riƙe amana ba, sannan duba da abin da Dr ya ce na akwai abin da kike so wadda ya haifar maki da matsalar nan, da kuma abin da nagani kuma naji da kunnena kina faɗa daren ranar, hakan yasa na tabbatar da e da gaske akwai wanda kike matukar so ne, dan Allah kada ki ɓoyewa yayan ki wanenen? Ko dai Saif ɗin ne?". Zaro ido sosai waje ta yi, nan take ta ji numfashinta na fita da sauri sauri, dafe kanta ta yi tana faɗin "A'a yaya Imran ba shi bane, ni babu wanda nake so". "Rimsha ko ki ƙi ko ki so Saif shine wanda kike so, domin daga kiran sunan sa kin razana, sannan ranar nan da kika kawo mashi ruwan sha, yanayin yadda kika kira sunan sa kafin ki suma hakan ya kara tabbatarwa da lallai akwai wani abin a kasa wadda sai yanzu na gane menene, yanzu haka da ga gida nake na je ne ba wanda ya ganni, na bincika dan na gano menene ke damun ki, a cikin kayan da kika zo da shi naga zanen fuskar Saif wadda wannan zanen kuma ba jiya ko yau aka yi shi ba, ya ɗan jima, hakan yasa na kara tabbatarwa da e tabbas Saif kike so, na tambaye ki ne kawai dan ina son in ji da ga bakin ki, akwai hujjoji da dama wadda suke nuna e lallai Saif shine mutumin da kike so, amma meyasa zaki ɓoye mani? Nifa yayan kine, bugu da kari kuma ni kaɗai ne wanda zai iya haɗa ki da Saif a faɗin Nigeria, ko dai so kike ki cuci abokina ne? So kike ki hana shi samun zankaɗeɗiyar mace kamar ki" ya yi maganar sa ta karshen cikin raha, kuma ya yi ne dan yasa ta dariya saboda yaga ta shiga matsanancin yanayi mara kyau. Ai kuwa tana jin maganar tasa ta karshen sai da ta yi murmushi, gyara zama ya yi ya ci-gaba da magana "E mana naga alama so kike ki hana Abokina samun mace ɗaya tamkar da million, amma fa Jelly na tafi tom, nima jelly ta ɗaya ce tamkar da million a waje na, kina son kiyiwa Lion bukulu ko? Ki yi mashi bakin cikin samun wannan zankaɗeɗiyar, kyakkyawar, kuma.....". Bai karisa ba ya yanke maganar yana kallonta Dariya ta yi har sai da dimple nata gefe dukka biyu suka lotsa sosai, cikin dariya ta ce "Yaya Imran ka bari bana so". Ɗan kwanto da kansa kaɗan ya yi ya leƙo fuskarta yana faɗin "Eyee waya ganta a gidan Lion matsayin amarya, wow gaskiya abin fa zai bada wani kala mai kayatarwa, ni dai koma me ni zan rako ango sayan baki". Ya kai karshen maganar yana dariya Hannu tasa ta rufe fuskarta tana ta dariya, ga flowers da aka zana mata a hannun nata ba'a magana, sun fito sosai, da ta rufe fuska ba karamin kyau ta yi ba. Zuba mata ido ya yi yana kallon tsantsan farincikin dake a kan fuskarta, wadda tun da suka haɗu bai ganshi a tattare da ita ba, hakan yasa ya fara tunanin ya zama dole ya san taya zai ɓullowa lamari har ta samu kusanci da Lion, dan ta dawwama a cikin farinciki haka, a nasa tunanin idan ta samu kusanci da Lion shikenan one day one time zai fara sonta, bai san cewa abin dai to ga shi nan ne, yana ɗaukar kamar zuciyoyin iri ɗaya ne. Sosai ya nutsa cikin tunanin yadda zai ɓullo wa abin, har aka gamawa su Akila gyaran jikin, suka fito palon wajen suka same shi, gaisawa suka yi sannan ya biya masu kuɗin suka fito suka isko Akil cikin mota zaune yana jiransu. Yana ganin su ya fito wai zai je ya biya kuɗin, Akila ce ta gaya mashi yaya Imran ya biya, to ya amsa da shi sannan suka shiga cikin mota, Imran ya tambaye shi ya batun school na Rimsha, nan ya gaya mashi ai kamar yadda ya yi alkawari to ya cika, gobe zata iya fara zuwa, amma da kayan gida zata je kafin nan a bata uniform daga baya. Sosai Imran ya ji daɗi sannan ya musu sallama ya tafi. Sayyaya Akil ya kai su, suka sayi kayan makarantar Rimsha, irin su jaka da takalmin da sauransu, sai murna take yi, har suka dawo gida bakinta ya ki rufuwa. Bayan sun dawo ne, suka haɗu su ukun suka fara aikin girki da gyaran part ɗin Imran ɗin, shi kuma Akil ya wuce aikin neman Aafia. Suna aikin suna hira, Akil tana ba su lecture akan maza, ita kam Rimsha kunya kamar zata nutse cikin kasa, sai wani yan kame-kame take, tana gyaran kayan miya, ɗan zungurar ta Akila ta yi tana faɗin "Ai ina gaya maki ne yadda zaki shawo mana kan mijinmu idan Allah ya kaddara, ki rikita mana shi, sai ya fara kuka yana baby ina son ki, kin san nifa Hajiya Batula mummy'n Aunty Abla ta gama gaya mani abubuwan gyran jiki idan na yi aure, kuma ina karanta wani book na Princess Teema, so nasan abubuwa da dama, dan haka ku kasa kunne ku saurare ni, ga shi ma Hajiya Batulan ta ce zata zo biki gidansu wannan Dr Nawid da ya zo jiyan, da muka yi waya da ita da safe ta ce mani zata zo biki a gidan, zata kawo mani ziyara duk da cewa Ammie bata son ta, amma zata zo, kanwar Abba ce fa, yar autan su, ina matukar kaunar ta, idan ta zo sai ta kawo mani dilka mai bala'in kyau da gyara jiki, da kuma su humra masu bala'in kamshi, a mai duguri take aure, wayyo Allah idan aurena ya zo, zaku ga gyara, akwai abubuwa, sai dai babu mijin, sai tarin wayan nan samari marasa lissafi akai, (🤣) duk ba su yi mani ba, shiyasa bana kula kowa, ni fa ina ji a jikina mijina wani shahararren sarki ne, irin shalele ɗan gatan nan, baby ina kake ne ka zo mu yi aure in tarairaya ka kamar yadda mummy Abla ta ke wa daddy Abla, ta ce habibi ga shuwayi (shayi) nan na kawo maka, ita fa mummy Abla bata kiran shayin ma kai tsaye idan zata gayawa daddyn Abla, wlh sai ta kara lanƙwasa shi ta wani ce suuwayi, sau biyu ina zuwa gidan ta, na ga abu iya ganin ido na, yaya Imran ya yi wa Ammie wayo ya kai Ni, nima yanzu ina son babyna ya zo mu yi aure na fara lanƙwasa sunan shayi". Ta kai karshen maganar tana kwashewa da dariya ita da kanta. Sake baki Umaisha ta yi tana kallon ikon Allah wajen Akila, Akila ta fi karfinsu, wai shuwayi kai jama'a. Ita kuma Rimsha yar dariya ta yi kafin ta ce "Aunty Akila ni fa ba ni ba zancen aure kawai ki kyale ni". "Uhm shi kuma fa? Ina zaki kai mana shi, kuma wlh kin ji na gaya mani irin mijin mun nan sai da lanƙwasa sunan shayi, idan ba haka ba, kina ji kina gani za'a kwace maki shi, dan ma sa'an ki ɗaya baya kula kowa, da mazan da matan duk ba su ishe shi kallo ba, amma fa ki sani wlh sai kin dage, ta fannin gyara bani da matsala da ke, kina yi sosai, sai dai sauran harka, shi kuma karki ji komai zan gayawa mummy Abla zata ɗaura ki a network, zaki rikita mana oga da salon soyayyar ki". Umaisha kam ai tuni ta fara ɗibar lecture saboda ta ga abin fa e yana da amfani dan jiya taga amfaninsa iya ganin idonta. Sai zuba masu zance Akila take yi, da yake bata san da zancen ɓatar A'afia ba, kuma Akil ne ya kara gayawa su Irfan akan kada a gayawa Akila da Umaisha za su shiga tashin hankali sosai da sosai, hakan yasa ba'a gaya masu ba. Suna tsaka da aiki ruwan sama ya ɓalle, da gudu Rimsha ta fita zuwa cikin ruwan nan, sai mamaki su Umaisha suke yi, suka tsaya a bakin kofar palo suna ta kallonta. Daga karshe dai Akila ma shiga cikin ruwan ta yi dan abin ya kayatar da ita sosai, haka suka rinƙa wanka cikin ruwa. A ɓangaren su Lion kuwa. Su Tga sun sami isowa Nigeria, sai dai ba su shigo da wuri ba, saboda sun ɗan tsaya a Spain na ɗan lokaci dan karɓar wani saƙon na Lion, sai wuraren karfe 3 na yamma suka shigo. Motar da Lion yasa aka kawo mashi daga gidan gwamnan Kaduna yasa sojan dake yi masu girki ya je da motar Airport ya ɗauko su, kunna map sojan ya yi ya tafi ɗauko su Tun da ya ɗauko su a hanya suke karewa Nigeria zagi har suka iso gida, kai tsaye parking space sojan ya wuce da su, Tga ne da Tyrone, yana kashe motar suka fito waje suna karewa gidan kallo. A harabar gidan daga ɗan gefe can Tga ya ga wayan nan yan kwacen wayar da Lion yasa aka shigo da su, da alama kuma Lion ɗin ya mance da su, dan suna ta ɗan gefe sun yi kneel down a cikin rana, abin da ya sa Tga ma ya gansu saboda da suka fito daga cikin motar, ya tsaya kewaye gidan yana kwaɓe fuska kamar wadda ya ga kashi, wai gidan kwata-kwata bata wuci lambun daddy ba, kewayen da yake yi ne yasa ya gansu, ai kuwa ba ɓata lokaci ya tambayi sojan dake a bakin gate me suka yi? Nan ya gaya mashi abun da suka gaya mashi da bakinsu sun aikata, ɗaure fuska sosai ya yi yana kare masu kallo, kamar wasu almajirai yan datti da su, duk sun yi Tsuru-tsuru da su, da alama yunwa ya ci ganiyarsu sosai ne. "ka ajiye mani su ina zuwa, bari na yi wanka na ɗan huta, zan zo in basu horo, dan dama hannuna yana ɗan yi mani kaikaiyi ga shi kuma ba za mu sami damar isa ga James yau ba sai gobe zamu yi masu diran safiya, yanzu dare ya yi ba mu shigo da wuri ba, hannuna na kaikayi sosai zan zo na sosa akan su" Cewar Tga kenan, kamar dai yadda kuka sani ne ya yi magana cikin harshen turanci, yana kai karshen maganar kuma ya wuce cikin gida. (Yan kwacen waya Allah ya jiƙan ku😭) A palo ya isko Tyrone yana tsaye yana yan kalle kalle "What are you waiting for?" Tga ya tambaya yana nufar staircase ɗin, bin bayan sa Tyrone ya yi yana faɗin "You am waiting for". A tare suka haura sama, suma dai kamar Imran da kamshin perfume ɗin nasa suka gane ɗakin da yake. Suna ƙoƙarin shiga cikin ɗakin, shi kuma Imran na fitowa, karo suka yi da shi, ya ɗan yi baya yana faɗin "Sorry". Wani wawan damka Tga ya yi mashi a wuya, rai a ɓace ya ce "Who are you?!". Allah sarki Imran ya ji shaƙar manya ya kasa magana, sai zare ido yake yi kamar zai mutu, kara matse mashi wuyar da karfi Tga ya yi dan mugunta, kuma abin da yasa ya yi mashi hakan kawai dan ya ganshi ne da kayan Hausawa wato shadda, hakan yasa yasan cewa shi musulmi ne, kuma ko ban faɗa ba kunsan kiyayyar musulmai dake a zuciyarsa. Da gaske kashe Imran ya yi niyar yi, ya shaƙesa sosai, sai zaro ido waje Imran yake yi yana ƙoƙarin cire hannun Tga ɗin daga wuyarsa, amma ina ya kasa, saboda ba riƙon wasa ya yi mashi ba. Kamar daga sama suka ga Lion ya damki hannun Tga ɗin, tun bai yi kokarin ɓanɓareta daya wuyar Imran ɗin ba, Tga ya yi maza ya saki Imran ɗin, ya buɗe baki zai yi magana kenan Lion ya kai mashi wani irin wawan duka a gefen kumatunsa, wadda yasa nan take ya zube kasa akan gwiwowinsa jini ya fara zuba daga bakinsa ciki kuma har da hakwaransa guda biyu da suka fita, idan baku mance ba dama Lion yana jin haushin abin da Tga ya yi wa Musharraf, saboda shi ma a yanzu musulmi ne, ba zai so a taɓa musulmai ɗan uwansa ba, to shima da biyu ya yi wa Tga wannan dukar, na daga ɗaya ba ƙari. Imran na tangal tangal yana kokarin faɗuwa Lion ya riƙoshi tare da ɗan manna shi da jikinsa ya sanya hannu yana ɗan shafa masa wuyar tasa, ya ji wuya sosai. Dawo da kallonsa kan Tyrone ya yi da wayan nan dara daran blue eyes ɗin nasa, tun bai yi magana ba Tyrone ya wuce da sauri ya koma palo ya ɗauko mashi ruwa mai sanyi ya kawo. Karɓa ya yi ya buɗe tare da kafa wa Imran ɗin a saitin bakinsa, sosai ya karɓi ruwan ya fara sha. Bayan ya sha ya samu natsuwa ne Lion ya sake shi tare da wucewa ciki abinsa. Wucewa Imran ya yi ya fita ya nufi in da za shi yana mai kara waigo Tga, yau ya ci bakar wuya, ya ji kamshin lahira, daga yin karo a rashin sani kawai sai yunkurin kisa, tab lallai wannan akwai bakar zuciya. Tga dai ya ɗan jima a haka kafin nan ya ɗan wastsake ya yi ƙoƙarin miƙewa, sai da Tyrone ya dafa mashi sannan ya miƙe suka karisa cikin ɗakin. A balcony suka isko Lion yana tsaye yana kallon gari. Ɗan gefensa suka tsaya har suna haɗa baki wajen cewa "Good evening sir". Ya ɗauki lokacin da akalla zai kai 10mins kafin ya fara magana gently in a cool voice ba tare da ya kalli in da suke ba "What Imran did to you da har kake kokarin kashe shi?" Murya na sarkewa ya ce "Ya buge ni ne". "General ina hana ka zalinci amma baka son daina wa ko? I want you to know something, shifa zalunci baya ta ɓa kai mutun ga nasara, I knew ba wai dan ya bugeka ne yasa ka yi kokarin kashe shi ba, kai kasan dalilinka so as from now babu ruwanka da shi, kome ya yi maka ka gaya mani, sannan ka sanar da sojojin nan su canza position daga wajen da suke ɗin nan, su matsa zuwa gaba" To Tga ya amsa da shi sannan ya ciro wayar sa daga aljihunsa, ya kira Captain ɗin da ya jagoranci sojojin da suka zo da su ɗin. Da sojoji 10 kawai suka zo, saboda sun ce gaba ɗaya state ɗin da James yake a ciki ma su kaɗai sun ishe state ɗin, bare ma iya wajen da yan ta'addan suke zasu yaƙa, hakan yasa suka ɗauki sojoji kaɗan, suma dan sun san ba shakka sai sun yi musayar wuta ne da yan ta'addan shiyasa. A takaice dai yau su Tga a Naija suka kwana, tun da ya zo ya yi wanka ya cire riga ya fara yawo haka, dama kunsan halinsa baya son zafi, daga shi sai Three quarter yake yawo, haka ya je ya kama wayan nan yan kwacen wayar ya rinƙa azabtar da su, yasa sojan dake girkin nan ya saka mashi wani karfe a wuta ta yi jawur ya rinƙa sanya su suna danme karfen da hannunsu, sun sha azaba sai ihu suke yi, sun gwammaci mutuwar su akan azaban da Tga yake yi masu. Lion kuwa lokacin sallar mangariba suka fita shi da Imran kamar yadda suka saba zuwa masallaci, Tga bai ma san sun fita ba, yana wajen azabtar da yan kwacen waya, shi kuma Tyrone yana zaune da sojan dake a bakin gate suna hira. Sai da aka yi sallar isha Lion ya dawo gida, shi kuma Imran ya nemi iznin zuwa gidan Abbi dan ya ji ya ake ciki batun case ɗin Aafia, bai dai gayawa Lion abin da ke faru ba, ya dai ce mashi zai je ya gaishe da uncle ɗin sa, da haka suka yi sallama. Tga kuma sai da ya tabbatar ya gama gashewa yaran nan hannayensu sannan ya musu azabar da sai da suka fita hayyacin su kafin ya kyalesu zube a wajen, ya shige cikin gida, yana zuwa ya yi wanka ya fito ya ci abinci ya shige ɗakin kasa ya kwanta abinsa ,sai barci dan gobe akwai babban aiki a gabansu. Shi kuma Tyrone tare da sojoji biyun nan ya kwana, Imran kuma karfe 9 daidai kamar yadda suka yi da Lion haka ya dawo. Yayi mamakin ganin Lion ya yi barci tun karfe 9, abin ya bashi mamaki sosai, wanka ya yi ya shirya shirin barci ya kwanta a gadonsa. Har ya fara barci sai kuma ya tuna da abin da ya faru tsakaninsa da Tga ɗazun, cikin sauri ya miƙe ya zo ya sanyawa kofarsa Key abinsa, ya koma ya kwanta ya yi barci. (Asuba ta gari mutane na!!🥰🤗) Washigari, cikin zumuɗi Rimsha ta shirya yaya Akil ya kaita school, bayan sun yi girki sun ci sun ƙoshi kenan, sai daɗi take ji. A ɓangaren Aafia kuwa, lokacin da ta ɗan farfaɗowa ta basu number yaya Irfan dan taci bakar azaba, kuma har lokacin jinine ke zuba daga jikinta, Sani ne ya karɓa ya kira, lokacin da kiran ya shiga Irfan na wanka daddyn Jelly ne ya ɗauki kiran, nan suke gaya mashi su suwaye ga kuma wadda suka ɗauka sannan suna bukatar kuɗin fansa naira million 50, daddy'n jelly bai wani damu sosai ba, tun da ya ji idan sun bada kuɗin za'a sake ta, lafiyarta kawai ya fara tambaya tare da gaya masu su kula da ita, tsabar rashin Imani sai cewa Sani ya yi ai tana nan cikin ƙoshin lafiya da aminci, daddyn Jelly bai yarda ba ya ce abata waya, ba musu suka bata wayar. Muryar ta ya dashe sosai saboda kuka da ta rinƙa yi ga kuma bakar azaba, da kyar ta iya fara magana, ba karamin tashin hankali daddyn Jelly ya shiga ba jin yadda muryar ta ya yi, rai a matukar ɓace ya ce "Me suka yi maki? Sun dake ki ne?" Cikin kuka take faɗin "Mutuwa zan yi yaya Irfan, zan mutu!" A tunaninta Irfan ne, bala'i yasa bata iya gane murya ba, nan take daddyn Jelly ya fara hawaye yana faɗin "Ba zaki mutu ba zaki dawo yau ɗin nan zaki dawo gare mu". A haka Irfan ya fito ya same shi, cikin sauri ya ce "Bappa Maik me yake faruwa ne?" Ba ɓoye ɓoye daddyn Jelly ya gaya mashi abin da yake faruwa, karɓar wayar ya yi suka fara magana da Sani, nan ya ce Millon 50 ya yi yawa basu da shi amma za su bada millon 3, ƙoƙarin hana shi daddyn jelly ya yi dan yana tsoron kada suce za su nemi ragi suje su kashe Aafia a banza, gara kawai a basu abin da suke so. Da Irfan ya ga daddyn Jelly zai ja masu bala'i millon 50 sai ka ce hauka sai ya fice daga Palon ya shiga ɗakinsa ya rufo kofa ya sa key, sai bugawa daddyn Jelly yake hankali a tashe, kin kulashi Irfan ya yi ya cigaba da magana da su. Daga karshe dai suka shirya akan millon 5 suka ce anjima da daddare ya kawo kuɗin dajin gabashin birnin gwari, to Irfan ya ce mashi tare da ce mashi ba ita kaɗai bace su biyu ne aka ce sun fita, da yake Sani ya san abin da ya yi mata, sai ya ce e su biyun dukka za'a fito maka da su bakin dajin ka ɗauke su, daga nan suka yi sallama, Irfan ya zauna yana tunanin me ya fitar da A'afia har suka kamata, ai na ma suka ganta, innalillahi wa inna ilaihir rajiun , shi kuma daddy jelly yana tsaye a bakin kofa yana bugawa. A ɓangaren su Tga kuwa, tun karfe 7 suka shirya tsab cikin fararen kaya, Lion ya sanyawa Tyrone wata yar karamar camera a botirin gaban rigarsa, dan ya samu damar ganin duk abin da zai faru idan suka je wajen. Karfe 8 daidai suka nufi wajen da James yake, a cikin garin Kadunar ne, sai dai kwai ɗan nisa tsakaninsu, kuma cikin daji ne wajen sosai. Diran mikiya suka yi wa wayan nan yan ta'addan, kafin sun farga sun musu rubdugu, kashe su kawai suke yi ba wasa, lokacin da yan ta'addan suka farga suka fara musayar wuta, sun yi nasaran kashe masu soja ɗaya, amma su kuma sun kashe su ba kaɗan ba, yan ta'addan suna da yawa, hakan yasa Tga ya yi amsani da kananan boma boman nan ya tashi wasu daga cikin ɓangarori na gidan, da kyar suka samu damar kutsawa izuwa cikin gidan. Suna shiga asalin ɗakin da James yake suka ja burki babu shiri, duk abin da suke yi Lion na kwance saman bed nasa yana kallonsu. Yan ta'addan sun ɗaure James a saman wata kujera a tsakiyar ɗakin, kamar ya mutu domin baya numfashi, ga kuma ogansu nan yan ta'addan yana zaune a saman kujera daga can gefe da James ɗin, fuskarsa ogan nasu sanye da mask baki, manya-manyan jiga-jigan yan ta'addan ne kusan su goma masu kirar basawa, suna kewaye da James ɗin a tsaitsaye, ɗaya daga cikin su ya sanya mashi wuƙa a wuya duk da ma baya numfashin, ɗaya kuma yana ruƙe da camera, ya yin da sojojin su Tga kuma suke waje suke ɓarin wuta. Buga bed Lion ya yi ya furta kash da ɗan karfi, kasa-kasa ya fara yi wa Tyrone magana, da yake ya sanya Bluetooth headphones a kunnensa hakan yasa yake jin maganar da Lion ɗin yake faɗe dan sun yi connecting. "Tyrone kada ka bari su sanyawa James Camera, suna yin yunkurin hakan ka harbi James ɗin!" Jinjina kai Tyrone ɗin ya yi alamar to. Ai kuwa kamar sun ji me Lion ya ce sai suka fara ƙoƙarin kunna cameran ɗaya daga cikinsu yana faɗin, "Ka kunna mu nunawa duniya yadda zamu yi mashi yankar rago, mu za'a taɓa? Dole su ɗanɗani zafin kuna". "Tyrone shoot James on his chest now" shine abin da Lion ya faɗa, kamar da gaske haka Tyrone ya ɗaga gun ɗin hannunsa ya sai ta James ɗin, nan take kuma ya ji ba zai iya ba. "I can't sir I can't shoot James i can't!!" Ya kai karshen maganar tare da sauke gun ɗin nasa daga saita James ɗin da ya yi yana girgiza kai kamar zai yi kuka. "Tyrone i said shoot him, idan baka harbe shi ba suka sanya mashi camera to zamu rasa shi har abada, domin kuwa CIA za su fasashi, ka harbe shi a chest nasa ta gefe wajen ɗan sama kusa da shoulder sa". Kasawa Tyrone ya yi ya fara hawaye dan ba zai iya harbin James ba har ga Allah, dai dai lokacin kuma suka datse network dake a wajen. A zafafe Lion ya diro kasa daga saman bed nasa, har wani tsuma jikinsa yake yi, dressing room nasa ya shiga, cikin yan mintocin da ba su fi 5 ba sai ga shi ya fito sanye da long coat da kuma wata iriyar hula kamar na sanyi ya sanya a kansa ya ɓoye gashin kansa, da kuma Black face mask, hannunsa na ruƙe da pistol gun, a zafafe yake taku cikin zafin nama ya fice daga ɗakin. Kai tsaye wannan motar tasa ya je ya shiga, da kansa ya ja motar da wani irin mahaukacin gudu, ya fice tare da kunna map a wayarsa, duk wannan abin da ake yi Imran yana barci a ɗakinsa. Sosai Lion yake sharara gudu akan titi. Tafiyar 30mins ya yi ya isa wajen, saboda gudun da yake sherarawa, yana isa wajen ya tarar da bakin gani, domin kuwa kamar yadda suka faɗa sun yi wa James yankar yaro a gaban kowa, ga shi kwance cikin jini malalan. Abin da ya faru shine da suka yi ƙoƙarin yanka James ɗin sai Tga ya buɗe masu wuta, wani daga cikin yan bindigar ya shigo ɗakin ta baya ya harbi Tga ɗin da kuma Tyrone ɗin, duk ya harbe su, kuma a kafa ya harbe su dan baya son kashe su, yana son suga mutuwar ɗan uwansu a gaban idonsu, bayan ya harbe su ne kuma suka zube kasa, su kuma yan ta'addan suka kwantar da James ɗin suna ƙoƙarin yanka shi, Tga ya daure ya miƙe a zafafe tare da ɗaukar bindigarsa dake a kusa da shi ya fara yi masu ɓarin wuta, hakan yasa suka sake harbin shi a ɗayar kafar tasa shine, ya faɗi kasa, suka kuma kwantar da James Tga yana ji yana gani suka yi mashi yankar rago. INNALILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJIUN, WAYYO TRIPLETS WAYYO JAMES 😭 Lion na shigowa wajen yan ta'addan suka miƙe tare da taitashi da gun ɗin hannunsu, ba tare da ɓata lokaci ba a fusace rai a matukar ɓace ya harbi ogansu dake a zaune saman kujerar, da wannan kattin muryar ta su suka kurma ihu tare da........✍️ BAZAN IYA CIGABA BA, NAYI BAKIN CIKI DA YAU YA KASANCE BA JUMMA'A BA, INA SON HUTAWA SABODA NAYI KUKAN MUTUWAR JAMES KAMAR TAREEF NE AKA CE MANI YA MUTUM!! NA JI RAƊAƊI HAR CIKIN ZUCIYA TA BA KAƊAN BA, YAYA MICHAEL ZAI JI IDAN YA JI CEWA JAMES YA MUTU, YAYA DADDY ZAI YI, KUNA TUNANIN ZA SU IYA RAYUWA KUWA? WANI HUKUNCI LION ZAI YI WAYAN NAN AZZALUMAN? INNALILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJIUN SAI DAI MUN HADU GOBEN KAWA!!!😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭😭 💖💖TRIPLETS💖💖 *Idan kun samu typing error amin afuwa 👏 keyboard ɗin tana bani matsala sosai kwana biyun nan, to na yau ma ya fi tsananta, sai na danna A sai ya koma B😭* *💔😭DEDICATE TO AUNTY RIFAT 🥰DAMA NACE ZAN MAKI KYAUTAR PAGE ƊIN MASOYIN KI, KIN FI KOWA SON JAMES DOLE NA BAKI WANNAN PAGE ƊIN!!* 59-60 Lion na shigowa wajen yan ta'addan suka miƙe tare da sai ta shi da gun ɗin hannunsu, ba tare da ɓata lokaci ba a fusace rai a matukar ɓace ya harbi ogansu dake a zaune saman kujerar, da wannan kattin muryoyin nasu suka kurma ihu tare da buga kafafu a kasa, Lion bai bari sun yi wani yunkuri ba ya yi masu rubdugu, ya nuna masu kwarewa a wajen aiki, ya nuna masu ba a banza ya zama The General of The Army ba, wani irin kisan walakanci ya yi masu, dukkansu ba wanda ya harba a wajen mutunci, daga wanda ya harba a baki bullet ɗin ta fito ta keya, sai wanda ya harba a gabansa, dukkan su takwas dake a cikin wajen ya kashe su, dama su goma ne Tga ya kashe biyu daga ciki, suma sun yi yunkurin harbin Lion ɗin lokacin da yake harbinsu, da yake dai ya kware a bakin aiki sai ya rinƙa kauce masu, kun dai san kafin Mutun ya taka matsayin THE GENERAL OF THE ARMY ba karamin abu bane. Bayan ya kashe su dukka ne ya wuce ya nufi ogan nasu dake a sama kujera wadda ya harba farkon shigowarsa, mai da pistol gun nasa ya yi a cikin aljihun wandonsa ta baya, sannan ya saɓi mutumin a kafaɗar sa suka fita waje. Kai tsaye cikin bayan motarsa ya je ya sanya shi, bayan ya kwantar da shi ne sai ya zaro gun ɗin daga aljihunsa tare da saita daidai saitin kirjinsa ta sama, in da dai ya ce Tyrone ya harbi James, nan ya saita ya harbi mutumin, sai bayan ya harbe shine ya furta "Kayi kuskure sosai James!" Ya kai karshen maganar tare da juyawa ya koma wajen su Tga. Har zai shiga ɗakin kuma sai ya dakata tare da kiran sojoji uku daga cikin wayan dake ɓarin wuta a wajen akan su zo, da gudu suka karaso kabansa suna risinar da kai kasa, wucewa cikin ɗakin ya yi ba tare da ya yi masu magana ba, cikin takunsu na sojijin yaki suka bi bayansa. Tga da Tyrone ya nuna masu akan su ɗauke su zauwa cikin motar, su saka Tyrone a baya Tga a gaba, domin Tga ya fi shan wahala, kuma dama shi bashi da koshin lafiya, karfin hali kawai ya yi, amma yana fama da zazzaɓi saboda hakwaransa biyu da suka fita, danma a lokacin ya je ya yi allura ne yasa bakinsa bai kumbura ba, bayan allura kuma ya sha magani, to wannan fitar hakwaran ne tasa mashi zazzaɓi mai zafi, kuma duk da haka ya daure ya zo cetar James. JINI BA WASA BA. Har lokacin akwai sauran yan ta'addan a gidan, saboda gidan akwai lunguna sosai a cikinsa. Wayan nan sojojin suna kokarin ɗaukar Tga da yake har lokacin bai suma ba, kuma bai fita hanyyacinsa ba, saboda bullet ɗin bata zauna a jikinsa ba, fita ta yi shiyasa abin ya ɗan ragu mashi, ganin za su ɗauke shi ne yasa ya ce "Lion James, please help him, please check maybe he is alive!" Ba tare da ya kalli in da suke ba ya ce "Uncle this is not James, so ka kwantar da hankalin ka wanda na harba a hannu farkon shigowa shine James, kwana biyu da suka wuce, ba na gaya maka wayan da suka kama shi sun san waye suka kama ba? To sun gane waye suka kama ne ta hanyar wani ɗan ta'addan da ya zo yana dukan shi a fuskarsa, sai wanna fake face ɗin nasa ta goce, shine suna cire face ɗin suka ga ainahin face nasa, to wannan da suka yanka babban yaron James ɗin ne, shine suka sanya mashi fake face ɗin James ɗin dan su tayar mana da hankali, amma su sun san ba za su iya kashe James kai tsaye ba, saboda muna kewaye da su, lokacin da nake bincike ne na samu daman gane cewa sun gane James, amma batun sanyawa baban yaron sa fake face na san, wannan kuma sai da na zo nan na sani". Abin da ya faru lokacin da Lion ya ga video ta hanyar camerar da ya sanya wa Tyrone a gaban botirin rigarsa, da yake yana ƙage da aikin alokacin, bai tantance cewa e ba James bane, sai da ya shiga mota yana zuwa ƙwaƙwalwarsa ta fara tariyo masa yanayin jikin wannan da kuma na James ɗin, a nan ne sai ya gane ba ɗaya bane, abin ka kuma da baban soja cikin kankanin lokaci ƙwaƙwalwarsa ta tariyo mashi mutanen dake a wajen, a nan ne ya fahimci wanda yake zaune a ɗayar kujerar da ogansu ke zama tabbas shine James, daga yana yin jikinsa ya gane, alluran barci suka mashi sanna suka rufe mashi fuska da mask, da Lion ya shigo wajen kuma, kallo ɗaya ya yi mashi ya gane tabbas shi ɗin ne, shiyasa ma ya harbe shi a hannu dan kada su harbe shi su, wannan shine abin da ya faru!! Ba karamin daɗi Tga ya ji ba, har wani nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe, haka sojijin suka ɗauke su zuwa cikin motar. Kamar yadda Lion ya tuƙo motar ya zo haka ya tuƙata ya bar wajen tare da su Tga da James dake kwance rai a hannun Allah, ya sha harbin bindiga sau biyu, hannu da kuma kirji, haka suka tafi suka bar sojojinsu suna karisa sauran aikin. Kai tsaye gida ya nufa da su, yana parking motar a parking space na gidan ya fito a zafafe tare da buɗe gidan baya na motar ya saɓi James a kafaɗarsa zuwa cikin gida, har lokacin akwai wannan mask ɗin a fuskar James ɗin. Jini sai tsiyaya yake yi, duk in da suka wuce sai jini ya zuba haka ya wuce da shi ɗaya daga cikin ɗakunan kasa. Saman bed mai shinfiɗe da farin bed sheet tas ya kwantar da shi tare da sanya hannunsa ya tsage rigar James ɗin daga farko har ya direta. Kamar yasan hakan zata faru ya taho da wasu kayan aikinsa, da yake dama su basu wani cika rabuwa da A box da sauran kananan tafi da gidan ka na kula da lafiya ba. Cikin zafin nama yake takowa ya fito daga ɗakin izuwa nasa ɗakin. A box da sauran kayan aiki ya ɗauko ya nufo waje, daidai Palon saman suka yi karo da Imran lokacin kuma karfe 11 rana ta yi. Daga ganin yadda Lion yake Imran ya san ba lafiya ba, dan haka sai ya yi saurin bin bayansa. Lokacin da Lion ya dawo ɗakin da James ke kwance, ya tarar da Tga da kuma Tyrone, sojan dake a bakin gate ne ya taimaka masu zuwa cikin gida, shi Tga ma kwata-kwata baya iya tafiya, gara Tyrone da yake kafa ɗaya aka harba yana iya jan kafar tasa. Kokarin cire bullet ɗin jikin James Lion ya fara yi, su kuma suna kwance a gefen James ɗin, shi kuma Imran da ya shigo da ya ga meke faruwa ai sai ya fara ruwan hawaye, da sauri ya kariso wajen gadon, da farko bai gane cewa James bane, sai da ya matso kusa sosai, saboda duk sun saɓa mashi kamanni, fuskar tasa ta suntuma sosai, idan ba ka yi mashi farin sani ba, ba zaka taɓa gane cewa shi ɗin bane, yan ta'addan nan sun zalunce shi sosai. Sosai Lion yake aiki babu kama hannun yaro dan cewa rayuwar ɗan uwansa, yana yi yana haɗa zufa, da sauri Imran ya kara gudun Ac dake a ɗakin, amma duk a banza, domin kuwa bai dai na zufar ba, kamar ma kara mashi ake yi, ganin haka yasa Imran ya wuce bedroom nasa ya ɗauro alwala ba ɓata lokaci ya fara gabatar da sallar nafila yana rokar Allah da ya bawa James lafiya, ya tashi kafaɗunsa. Sai wuraren karfe 1 Lion ya samu ya iya kammalawa da James, ya yi nasarar cire bullet ɗin, sannan ya mashi dressing na wajen, sai barci James yake yi domin alluran da suka mashi tana da karfi sosai da sosai wata kila zai iya kai wa dare kafin ya farka. LION Bayan ya kammala ne ya nufi su Tga da nufi ya yi Tga dressing ɗin wajen tun da shi babu bullet ɗin a jikinsa, shi kuma Tyrone ya cire mashi bullet ɗin, amma duk azaban da Tga ya ke a ciki, bai hana shi ya ce lallai shi baya son a duba shi ayi treatment ɗin shi a Nigeria ba, saboda wai Nigeria me suke da shi da har za'a duba mashi lafiyarsa a nan, shi baya son kasar ma gaba ɗaya, shi tunda ba wani ciwo sosai ya ji ba zai iya tafiya a jirgi kawai a mai da shi Usa daddy ya je ya duba shi, Lion bai wani damu ba, dan dama baya son matsi sosai, dama ganin gidan yake yi ta yi mashi karama, da kaɗan tafi palon kasarsu na Usa, shi ji yake yi ma da kyar yake numfashin a gidan, duk girmanta amma wai ta yi karami, so da suka zo ɗan jiya kawai ji ya yi kamar sun toshe mashi iskan da yake shaƙa, dama ga zafi, hakan yasa ya ce to su wuce amai sa su, ba musu kuma suka ce to, cikin kankanin lokaci aka yi masu komai, amma kafin su tafi an cire wa Tyrone Bullet ɗin kafarsa, sannan Lion ya ɗan gyara masu wajen suka tafi, shi Lion ba zai yi wu su tafi da wuri haka ba saboda James jikinsa ya yi tsakani sosai, sai ya ɗan sami lafiya. Yau sai misalin karfe 3 Lion ya samu ya yi sallar azahar, saboda busy da ya yi yawa. Bayan ya yi wanka ya yi sallah ne ya zauna saman bed nasa yana tunanin yadda zai yi da James. A wanna hali Imran ya shigo ya same shi, sannu ya yi mashi tare da tambayar ya jikin James, jinjina mashi kai kawai ya yi ba tare da ya yi magana ba. Gefensa Imran ɗin ya zauna yana faɗin "Lion dan Allah ba dan ni ba, kada ka yi wa James hukunci mai tsanani, ni nasan ba haka kawai ya shiga wannan ta'addancin ba, akwai dai dalili, kai ma fa kasan James yana da zuciya mai kyau, ka tausaya mana". Shiru ya yi na tsawon mintoci kamar 10 haka kafin ya fara magana gently. "Prof James ba ɗan ta'adda bane, kamar yadda ka ɗauka, amma dole zan hukunta shi, dole ya karɓi hukunci mai tsanani domin ya yi mani laifi, ya sayar mana da rayuwarsa". Zaro ido Imran ya yi yana faɗin "Ban gane ba, dan Allah ka yi mani baya ni dallah dallah". Na san kowa a ƙage ya ke dan jin cikakken bayani akan James da wannan sarkakiya, to ni *PRINCESS TEEMA* bari na warware maku cikin kwanciyar hankali, maza ku biyo ni. JAMES dai ba ɗan ta'adda bane kamar yadda kuka ji Lion ya faɗa, abin da ya faru shi ne ku saurara ku ji, ya shiga ƙungiyar ta'addancin kala-kala, haka zalika ya kashe mutane kala-kala, sai dai duk mutanen banza yake kashe wa ba na kirki ba, alokacin da Lion yake bincike akan wani mutumi da James ɗin ya kashe ne wadda Lion yake yiwa kallo mutumin kirki, to alokacin ya fara fahimtar cewa duk mutanen da James yake kashe wa na banza ne ba na kirki ba, hakan yasa ya dakata da bincin ina James ɗin ma yake tukunnan, sai ya fara binciken waye James ɗin mai gaba ɗaya? Waye yake saka shi wannan aiki, a nan ne ya gane cewa James shi ne (DOA) DETECTORATE OPERATIONS ARIF na CIA gaba ɗaya, CIA kuma wata katafaren hukumar Row ce ta kasa da kasa, James ya shiga ne tun yana makaranta, da farko ya shiga ne dan kuɗi, daga baya ya koma kishin kasa, sannan ya zo ya shiga cikin manya-manyan yan ta'adda na duniya, domin ya rinƙa kashe su, to lokacin da ya fara sanin daɗin rayuwa ya fara jin tsananin kaunar yan uwansa, yana jin ba zai iya rabuwa da su ba, alokacin ne ya fara ƙoƙarin neman ta ina zai fita CIA, babbar matsalar shine idan aka shiga ba'a fita, domin kafin ka shiga sai ka sa hannu akan ka sayar masu da rayuwarka, idan ka amince da hakan to za su yi maka tiyata su dasa maka wani abin mai kama chemical kakar kuma bom haka yake, da na ura yake aiki, idan kayi wargi kaɗan mai sarrafa nauran zai iya fasa ka, abin da kuma yasa suke yin hakan domin idan yan ta'addan sun kama nasu idan ya ji wuya ya yi ƙokarin tonawa hukumar tasu asiri hakan zai sa su danna wanann abin su tarwatsa mutun ya mutu har lahira, dan kada ya fitar da sirrin hukumar har a iya far musu a gane ina suke, shine amfanin wannan makami mai kama da bom ɗin, ana danna na'uran zata fashe kamar bom ta kashe mutun, ko wani ɗan cikin CIA yana da ita a kirjinsa, shiyasa Lion ya ce kada su Tga su bari a sanyawa James Camera, domin ana sanya mashi CIA da su gani, su kashe shi dan kada ya tonawa hukumar asiri, kamar aljanu haka suke, sai ka zauna a tare da su baka san su bane, idan suka ga James acikin wannan hali to suna iya danna wannan naura abin da suka sanya mashi a kirjinsa ya tarwatsa shi kamar bom ya mutu, haka yasa Lion ya ce Tyrone ya harbi wajen da wanan abin yake, suna harbi wajen abin zai ɗauke daga jikin na'uran CIA kamar network, yana ɗauke wa kuma James ya tsallake layi ɗaya, shine Tyrone ya kasa yin harbin, yanzu babban tashin hankali shine tayaya za'ayi James ya fita daga cikin CIA (ROW)?, domin TRIPLETS ba za su yarda da sayarda ransa da ya yi ba, hakan ma yasa yake ɓoyewa Lion kada ya sani, shiyasa yake yi masu basaja dan kada su gane, ya ci bakar wuya kafin ya zama DOA ya sayar da ransa ya rinƙa shiga cikin kungiyoyin yan ta'addan, kuma abin da yasa da sun bashi contract na kashe wani zai yi sauri ya aiwatar da aiki, dan dama dukka yan ta'addan ne kashe su yake son yi, ya yi aiki tukuru dan tsabtace kasarsa kamar wani baban soja, ya wahala iya wahala, yanzu baraza ɗaya ta rage shine fita daga CIA, babbar matsalar ma Allah ne kaɗai ya san ina da ina suke sakawa mutun wasu abubuwa a jikinsa na tarwatsa sa, lokacin da Lion ya gane hakan ya ji haushi sosai kuma ya kiduri niyar hukunta James ɗin hukunci mai tsanani ta yadda gobe ko hauka yake yi ba zai sayar da rayuwarsa ba, idan aikin cetan kasa yake son yi ya shiga hukumar soja mana, ko siyasa. Batu akan wayan nan sojoji guda biyu da ya kama ya yi masu hukinci a ranar da Lion ya turo a tarwatsa kungiyar su kuma, suma duk gurɓatattune dan ya san su a wata dabar da ya taɓa shiga ya kashe mataimakin mai wannan dabar, shiyasa duk kunguyar dabar da ya shiga suke bala'in ji da shi, dan ya samu kwararren training kamar soja, har mamaki suke yi yadda idan ya kalli abu sau ɗaya zai iya rufe ido ya sa bindiga ya saita abin ya harba, a takaice dai JAMES ya fi Tga ma a samun cikakken horo, shiyasa yake iya dukan Tga ɗin, James jarumin gwarzon namijine sosai, har ya kusa kamo Lion a manya-manyan ayyuka domin cetar kasarsu, dan shima Lion kafin ya taka matsayin da ya taka sai da ya yi ayyuka fin haka. Abin da ya faru aka maka shi a Nigeria kuma da har Lion yake jinjina wa yan Nigeria shine, bayan ya kammala kashe gaba ɗaya dabar su dake a Spain ya biyo sahu dan ya karisa wayen dake a Nigeria, ba gaba ɗaya wayen dake a Nigeria bane yan Nigeria, no akwai turawa yan uwansu a ciki, wayan da suke haɗe da baban fatan mu, su dai sun ɓuya ne a cikin wannan gidan suna bawa bakaken fata umarnin da su kashe ko kada su kashe, to ya biyo ne ya shiga cikincin dan ya kashe su, ya yi amfani da ogansu dake dabar Usa wadda bai kashe shi ba, kuma dama bai kashe shi bane ya bar shi, ya ɗaure shi a asalin office nasu na ROW dake a karkashin kasa a Usa, dayawa daga cikinku zaku iya tuna wannan office ɗin, in da ya hukunta wayan nan sojojin, to ya bar wannan ogan nasu na dabar da ya yi ɓaɗɗa kama a ciki ne saboda ya cigaba da gaya mashi ina sauran yan ta'addan suke, shiyasa ya yi aiki sosai ya shiga jikin ogan nasu ya so shi sosai ta yadda baya ɓoye mashi komai, ya mai da shi babban yaronsa, to da wannan dama yake amfani yana mashi wayo yana kashe yan daban, wata sain haka kawai zai kashe wasu daga cikinsu idan ogan ya tambaye me yasa ya kashe su, sai ya ce ai ya gano su yan leken asiri ne wata kungiyar ta'addancin ne, hakan yasa ya zama ko ya kashe wani a cikin su ba'a tambayarsa dalili, kuma hakan ne yasa ya zama makusancin su saboda a tunaninsu yana da baiwa yana kama masu yan leken asiri, babu san yana yi masu kisan mummuƙe bane. Yana shigowa Nigeria da kallo ɗaya yan daban Nigeria suka yi mashi suka kama shi, suka ce lallai ba ɗan ta'adda bane wannan, ya gaya masu waye ya turo shi, daga karkashin wace hukuma yake, wannan shine abin da ya sa Lion ya jinjinawa kaifi kwakwalwa ta yan Nigeria, yan kasashe da dama basu iya gane cewa James ba ɗan ta'adda bane, babba ne a cikin hukumar CIA, amma yan Nigeria da kallo ɗaya sun yi ram da shi, abin ya sa Lion ya jinjinawa Nigerians. Shi kuma wanda yan ta'addan nan suka yiwa yanka rago, ba kowa bane fa ce shine DIA babban mataimakin James ɗin ne awajen aiki, lokacin Lion ya gane hakan ya yi farinciki ganin James ba ɗan ta'adda bane, so kuskuren da James ya yi a wajen shine yadda ya shiga cikin yan ta'addan tsundum, kuskure na biyu kuma ɓoye masu da yake yi, kuskure na uku kuma sayar da rayuwarsa da ya yi. Duk guje gujen da yake yi yana yi ne dan kada TRIPLETS nasa su gane ne, saboda yasan ba za su taɓa yarda da hakan ba, kuma yanzu ma ba za su yarda da hakan ba, ya yi aiki sosai wadda ko General ba zai gwada mashi aiki ba, wannan dalili yasa Lion ce wa Tga James ya fi karfin sa, abin da ya yi abune mai kyau amma Lion ba zai taɓa yarda da hukumar CIA ba domin a yanzu haka James ba mallakin su bane, mallakin CIA ne domin ya riga da ya sayar masu da kansa. BABBAR MAGANA, A TAKAICE WANNAN SHINE WANENE JAMES DA KUMA HALIN DA YAKE CIKI A YANZU, KO BAN ZURFAFA BAYANI BA ZAKU IYA FAHIMTAR INA AKA DOSA!! MU KOMA CIKIN LABARINKU. Story Shiru ya yi na tsawon mintoci kamar 10 haka kafin ya fara magana gently. "Prof James ba ɗan ta'adda bane, kamar yadda ka ɗauka, amma dole zan hukunta shi, dole ya karɓi hukunci mai tsanani domin ya yi mani laifi" Zaro ido Imran ya yi yana faɗin "Ban gane ba dan Allah ka yi mani baya ni dallah dallah". Shiru ya yi, ya ɗan jima a haka kafin ya bawa Imran labari sama-sama kamar yadda dai na gaya maku waye James ɗin. Ba ƙaramin daɗi Imran ya ji ba, sai dai kuma idan ya tuna cewa Lion ya ce sai ya yi mashi hukunci mai tsanani na sai da kansa wa CIA da ya yi, sai gaba ɗaya ya ji kuma jikinsa ya mutu, baban damuwar ma ba su san iya kar abubuwan da CIA suka sanyawa James ɗin ajikinsa ba, sai dai Lion yana bincike akan me da me suka yi mashi, dan ya san ta yaya za su iya samu su fitar da shi daga hukumar. (Ni kuma na haɗa kayana zuwa wajen RIMSHA wata kila kafin na dawo su Lion sun ɗan gama jira) 🔥RIMSHA🔥 Sai zumuɗi take yi yau ta je school, fuskarta har wani kyalli yake yi saboda tsantsan farincikin dake a tattare da ita. Karfe 2 na rana daidai ta dawo, Akil ne ya je ya ɗauko ta, duk da busyn nan da yake a ciki, hakan bai hana shi kula da amanar da Imran ya bashi ba, ko da ya ɗauko ta bai tafi ba, ya tsaya yana kallonta har ta shiga part ɗin Imran, sannan ya juya kan motarsa dan suje su san yadda za'a kai kuɗin karɓar Aafia da Rufee, da farko yan ta'addan sun ce da daddare za'a kai kuɗin, daga baya kuma suka sake fasawa wai da rana za'a kawo, hakan yasa ya ce to shi zai kai ya karɓo A'afia ɗin. Kada ku mance Jinin Umaiya basa taɓuwa ta daɗi Ko menene a jinin Umaiya oho? Waye ma ita ɗin? Mu je dai zuwa akwai labari agaba. Rimsha tana shiga cikin palon yaya Imran ta tarar da Akila, a lokacin ta gama yi musu girki ta yi wanka. Tana ganin Rimsha da sauri ta zo ta rumgumeta tana faɗin "Welcome my dear" ita ma Rimsha rungumarta ta yi tana mata oyoyo tare da tambayarta ya gida, nan ta ce mata ai ita ma karfe 12 ta dawo daga school, shine ta ce bari ta yi masu girkin abin da ta iya dafawa wato shinkafa da miyar steew, ita ma Umaisha yanzu da Akil ya fahimci me yake faruwa tsakaninta da Ammie sai idan zai fita, sai su fita tare ya kawo Part ɗin Imran ya ce ta zauna kada ta koma Part nasu sai ya dawo, abin da ya sa kuma bai kai ta gidan saba, saboda babu kowa kuma yanzu yana busy ba zama yake yi ba, ita kaɗai a gidan zata ji tsoro sosai, ya ce sai ya gama abin da yake yi, ma'ana kenan sai sun gama da case ɗin Aafia, zai mai data gidan nasa kafin su koma Madina, hakan yasa yake barinta suna zama a tare gaba ɗaya a part ɗin Imran ɗin tun da shi baya nan. Wanka Rimsha ta fara shiga kafin komai, ko da ta je yin wanka sai faman shafa sunan Lion take yi, ita kaɗai kamar zautatciya sai murmushin take yi a toilet, har wani lumshe ido take yi kamar shine yake shafa mata wajen, abin da ya bata mamaki kuma ya ɗaure mata kai shine yadda akayi sunan yake matsawa zuwa saman tula-tulan da kyau a nata ganin, bata san cewa asali ma akan su ta yi zanen ba, lokacin dai basu girma bane suna kanana, sai take ganin kamar baa kansu bane, abin da bata sani ba shine, kullun breast ɗin nata kara cikowa suke yi, wajen da ta yi rubutun yanzu duk ya ciko sosai, shiyasa take ganin kamar rubutun na matsawa ne. Bayan ta yi wanka ta ɗauro alwala ta fito ɗaure da towel a kirjinta, sai santin dark black curly hair ta Akila da Umaisha suke yi, ga shi jiya sun sha gyara gashin har wani kyalli yake yi, kunshintan nan ba'a magana. Shiryawa ta yi tsab cikin Pakistan wando fari rigar blue gyalen ma blue, ba karamin kyau ta yi ba, sai ta saje da indiyawa abinta, simple make up ta ɗan yi tare da feshe jikinta da perfume ta zo ta yi sallah. Bayan ta idar ne Akila ta ce suje su ci abinci, to ta amsa da shi dan dama tana jin yunwa sosai, 1k ɗin da Akil ya bata dan sayan abu a school, bata sayi komai ba, ta dawo da shi a jakarta, dan bata saba ba, abin da ta saba shine tafiya da abinci daga gida, kuma yau saboda zumuɗi bata ɗauki abincin ba, duk kuɗin da daddynta yake da shi bai koya masu saye sayen abin da ake sayarwa a shop na cikin school nasu ba, hakan yasa yanzu ko ba'a basu kuɗi ba sun saba, duk wani kayan cima su biscuit, chocolate, har ice cream, yogurt duk daga gidan mun ɗin su ke shirya ma su a lunch box ɗin su, KUMA HAKAN YA FI SHINE DAIDAI, KADA A SABA BAWA YARO KUƊI, KODA BISCUIT ƊIN NE ARINƘA SAYA MASHI SAI ANA SANYA MASHI A BOX ƊIN NASA, DOMIN BAKA DA TABBACIN ZAKA RAYU DA YARONKA HAR YA KAI MUNZALIN YIN HANKALI, TO YA DAI KAMATA DUK ABIN DA YAKE SO ASAYA A BASHI, KADA A RINƘA BASHI KUƊIN KAI TSAYE!!! Suna ƙokarin fita daga cikin ɗakin ne wayar Rimsha ya fara kara, haka kawai ta ji gabanta na faɗuwa, kamar ba zata ɗauki wayar ba, sai kuma ta koma ta je ta ɗauka, new number ta gani, zubawa number ido ta yi tana mamakin ita dai tasan cewa Yaya Ahmad da Aunty Akila ce kawai ke da number wayarta, ko Imran bata da number wayarsa, tana ta tunane tunane har wayar ta katse, yana katsewa sai ga saƙo ya shigo, Ki kunna data, shine kawai abin da aka rubuta a saƙon. Cike da tsoro ta kunna data, tana kunnawa video call yana shigowa tare da wani sakon a WhatsApp, sakon ta fara karantawa da wannan number kuma. Yaya Imran ne ki ɗauki kiran, a wajen heartbeat na karɓin number ki, shi abin da ta gani a WhatsApp ɗin. Bata san time da murmushi ya suɓuce mata ba, da har ta tsorata sosai. Picking na video call ɗin ta yi tana murmushi, wani irin muguwar kaɗuwar gaba ta ji lokacin da dara-dara sleeping eyes nata suka sauƙa akan Lion ba yaya Imran ba, yana zaune a gefen gadonsa yana ɗan latsa wayarsa, kansa na a kasa, da alama abu mai muhimmanci yake yi, da alama kuma bai san Imran ya sa mashi camera ba, har wani shocked ta ji jikinta ya yi, ta kasa motsawa, yau ga shi nan a gabanta ba face mask, kamar a mafarki, sai faman lumshe dara-dara blue eyes nasa yake yi, kamar mai jin barci, wayan nan zara zaran eyelashes ɗin nasa, da ya lumshe ido sai ki gansu kamar ya sanya na kari sabo tsawon su. Hannu tasa ta toshe bakinta tana bin jikinshi da kallo shi kuma Imran yana bin fuskar ta da kallo, yana jin matsanancin farinciki yau ya sakata farinciki, zuba mata ido kawai ya yi yana kallon yadda take bin Lion da kallo, da wayan nan dara daran sleeping eyes ɗin nata, kwata-kwata bata kawo a ranta cewa Imran ɗin yana kallonta ba, dan kunga ya juya mata cameran. Ganin ta yi shiru tana kallon waya ba wani motsi ne yasa Akila ta zo ta leƙa wayar tana faɗin "Me kike kallo kika natsu haka kodai....." Bata karisa maganar ba ta ɗauke wuta sakamakon sauƙa da idon ta ya yi akan Lion, ita kuma Umaisha tuni ta yi waje tun lokacin da Akila ta ce su tafi cin abin, sai tayi gaba. Suna tsaka da kallonsa basu ankaraba sai gani suka yi ya ɗago wannan fusataccen fuskar nasa, kai tsaye kuma sai kan Imran ya sauƙe idanunsa, yadda kasan su yake kallo saboda saitin cameran yake kallo, razana tasa Rimsha ta saki wayar tata ta faɗi kasa, ba ita kaɗai ba har ta AKILA kwarjininsa ya razanata sosai da sosai, da kyar ta iya jan numfashi tare da haɗiyar wata wahalallen yawu ta ce "Rimsha aiki na gaban ki, wlh dole ki suma ashe haka yake da bala'in kyau, kai kai kai tab sai ki shirya wannan fusataccen fuskar kamar zaki, gaskiya sai kin dage, innalillahi kina ganinsa, wlh ni da nake kallonsa cikin face mask ban zata haka bala'in kyau nasa ta kai ba, ga gwarjinin bala'in, ni nayi nan Allah yasa kada na kara ido huɗu da shi, ya tsaya a iya nan kawai". Ta kai karshen maganar tare da nufar wajen. Har ta kai kofar fita kuma sai ta ga Rimsha fa ba ta motsa ba, da sauri ta dawo ta taɓa ta tana faɗin "Ke lafiya?" Ashe suman tsaye ta yi, irin abin nan da ake cewa fitar ruhi na yan mintuna, shi Rimsha ta yi, kamar wadda ta suma haka ta kasance, bata ji kuma bata gani, sai da Akila ta zaunar da ita saman bed tare da kawo mata ruwan sanyi dan tasha zuciyarta ya yi sanyi, kafa mata robar ruwan ta yi a bakinta bayan ta buɗe, tanayi yana yi mata dariya, cike da zolaya ta ce "Rimsha dama ba za ki iya ba kika fara? Tab ai kuwa tom da sauran suma a gabanki, Allah ya nuna mani ranar da zai ga zanen nan kuma in ga ta tsiya, wata kila mutuwa zaki yi ranar ko? In Sha Allah sai ya ga zanen nan zaki yabawa aya zakinta kuwa, ke ba yar soyayya ba" tana magana tana dariya. Rimsha kuwa sai da ta ɗauki good 20mins kafin ta iya dawowa daidai ta watsake, da taimakon Akilar, bayan ta watsake ma ta jima zaune a wajen, ita wannan fusataccen fuskar tasa ce ke matukar razana ta, idan ta kalli wannan fuska sai ta ji kamar ita ya zo kashewa, bayan fuskar kullun a fusace ga kuma bala'in kwarjini a tattare da shi, sannan ga dara-dara idanunsa masu wani irin yanayi na rikitar da wanda ya kalla, abin sun haɗu da dama ne akan fuskar tasa. Bayan ta tawo daidai ne suka lallaɓa zuwa palo, Akila ce ta dawo ta ɗauki wayar suka wuce Palo. Suna zama Akila ta fara dube dube a wayar, sai taga hotuna da videos nasa kusan guda 20 Imran ya turawa Rimsha, wata hoton ma tun suna school. Ba karamin rikicewa suka yi ba, kuma bin da ya kara rikita su shine hoton TRIPLETS da Imran ya toro, James ne ya ɗauke su hoton suna kwance a saman katafaren bed ɗin Lion ɗin , har ma da wani shot video da James ɗin ya ɗauke su suna a bedroom na Lion, Michael yana kwance saman bed yana zancen yana son kuɗi, shi kuma Lion yana zaune a befen bed ɗin a lokacin yana latsa laptop, James ɗin kuma yana faman serving na Lion abincin, bayan ya ɗauke su su biyu, sai ya juyo da camerar ya ɗauki kansa. Wannan hoto da video na TRIPLETS ba karamin tashin kan su Rimsha ya yi ba, dama su uku ne, shine abin da suka iya faɗa kawai, ga su da yake jini ba wasa ba sai su ka yi masu kallon kama ɗaya, sun razana sosai. Wunin yau dai abin da suka yi ta kallo kenan, kuma ganin videos ɗin da pics ɗin yasa Rimsha ta rage tsoron fuskarsa, saboda ta yi ta gani sosai, ta wuni tana gani. (Yau fa Rimsha duniya ta samu, an samu sabon Film, Imran nata kara hura mata wuta, zaki yi bayani, ki biye mashi ke dai ya kai ki ya baro, ki zama ba tsuntsu kuma ba tarko, dan ina da tabbacin daga ke har Imran ɗin naushi ɗaya ya isa Lion ya tura ku in da ba'a dawowa🤣) Bari mu waiwaye gidan ABBI tun da ita dai Rimsha yau duniya ta samu. Wani uban kwalliya ta ci, da yake ita mace ce mai gyran jikinta sosai, tana shan kunun larabawa, wato alkama da farar shinkafa, sai hakan yasa ba zaka taɓa cewa ta haifi su Irfan ba, ga shi ba laifi tana da kyanta daidai gwargwado kuma ya haɗu da gyara, dan gaskiya Hajiya Hadiza tana kashewa jikinta kuɗi ba wasa, shiyasa take bala'in shiri da Hajiya Batula wadda ta kasance kanwar su Abbi ce, ita ce autar su, tana aure ne a Maiduguri, duk wata macen da take gyaran jiki a kusa da su, zaka tarar da wuya idan bata san Hajiya Hadiza ba, gata da son kunshi, makirci, kistsa, ba abin da bata iya ba. Yau wasu shegun riga da sket ta saka, sai ta dawo kamar yarinya yar 25 years, tayi kyau ba karya, akwai ta kuma da son cin chewing gum, haka ta zuba wasu shegun chewing gum nan a bakinta masu bala'in kamshi, sai wani kas-kas-kas take abinta, kayan nata sun bi shap ɗin ta sun zauna, da yake akwai shape ɗin, ita Umaisha ta gado akwai sss sosai, saboda tsabar gyara har surgery na tumbi ta biya aka yi mata, sai cikin nata ya koma plat kamar na budurwa yarinya karama, hakan ya bata daman sanya duk irin ɗinkin da take so kuma ya zauna mata daidai, sai tashin wani shu'umin kamshin perfume na Hajiya Batula da ta haɗa nata take yi, tana kwance saman bed nata tana ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya tana wani shan kamshi, sai da ta ji fitowar Abbi sannan ta sanya wani shegen flat shoe a kafarta mai shegen kyau ta fito waje. Tana fitowa suka haɗu da shi da aunty zai wuce Aunty zata raka shi, tsabar iya kirsa da makirci har kasa ta tsugunna irin ladabin nan ta ce "Ina wuni sahibina?" Kamshin perfume ya daki hancin Abbi, tsabar kyan da ta yi ma da farko bai gane wace ce ba ce, ya ɗauka wata baby yar cakwai ce, sai da ya ji Muryarta ya gane. Bata barshi ya yi dogon tunani ba ta miƙe tare da karɓar jakar hannun Aunty tana faɗin "Kai kanwata bari na hutasheki, kinga kin jima kina yi mashi rakiya, yau bari na karɓa maki, ki huta kema, amma sahibina gaskiya wannan kanwar tawa akwai ta da kirki, baka ga da na dawo gidan nan yadda ta rinƙa ɗawainiya da ni ba, har da ce mani fa ta yi na zaɓi ɗakin da nake son zama, gaskiya ina kaunar ta sosai sahibina, dole kuma na kula da ita" ta kai karshen maganar tana jan mashi dogon hancinsan nan. Yau Aunty taga karuwanci da tsakar rana ido da ido, Allah sarki Abbi Hajiya Hadiza bata bari ya yi wani yunkuri ba, ta yi saurin saye bakin nasa da salon kirsan ta, ya sami wasu abubuwa da Aunty ke jin kunya bata yi mashi, irin wasa da sauransu, har wani jan hancinsa hanjiya Hadiza ke yi, tana wani langwaɓar mashi da kai kamar yarinya, nan take ta rikita bawan Allah nan. Har yana haɗe words wajen ce mata "Khadija yaushe kika dawo?" Jin haka ya yi mata magana a nutse ba da faɗa ba yasa ta kara narkewa da kashe murya (kamar tsohuwar kwartuwa) tana zuba mashi kirsa da makirci, Aunty dai yau taga tsantsan bariki data ci uban na Rufee, har wani shafa mashi wuya Hajiya Hadiza take yi, da yake ta yi wa kayanta farin sani, ita kuma Aunty kunga bakuwa ce, ba komai ta sani ba, Hajiya Hadiza ta san lagonsa fes, tasan ta yadda zata bi da shi ta zautar da shi. Da Aunty taga ana ƙoƙarin runguma a gabanta sai ta sa kuka ta juya ta koma ɗakinta. Ɗan waigawa ya yi ya kalleta yana faɗin "Me ya faru Halima?" Ya zauce da kirsan Ommu har baya son yin magana sosai. (Mata bala'in ne wata zubin, kai kuji makirar mace tab🤔🥺) Cike da kirsa da makirci ta ce "Sahibi ka je ka rarrasa mani kanwata ta yi shiru, tana da kirki bana son ta ɓata rai" tana magana tana rungume shi, shiru ya ɗan yi, shi kaɗai yasan me yake ji. "Hadiza wai yaushe kika dawo ne?" Shine abin da ya iya faɗa, kara shigewa jikinsa ta yi tana shagwaɓe fuska tare da turo baki kamar yarinya ta ce "Sahibi wai meyasa kake tambaya ne? To koma me ka je wajen aiki ka dawo akwai wani abin dana tanada maka, sannan sai mu yi hiran ko rabin raina? Yanzu dai kafin ka tafi ka rarrashe mani kanwata ka ji?". Bawan Allah nan ya rasa bakin magana, domin harshen Ommu karfi ke kareta kamar reza, haka ya juya ya karɓi umarnin ta zuwa wajen Aunty dan ya rarrashe ta. Yana tafiya ta saki wani shu'umin murmushi kasa-kasa ta ce "Yarinya da Hadiza bage maganin maza kike yi, ke baki ma ji sunan ba, maganin maza, sai na dafaki ta hanyar da ba wanda zai taɓa yarda kina dafuwa, ke yau kika gani, mu kuma mun ga jiya munga yau har ma da shekaran jiya, ki jira ki gani, Hadiza bata zama da kishiya, nan gidana ne ni kaɗai". Ta kai karshen maganar tare da wucewa cikin ɗakinta tana ayyana yadda zata rikita Abbi da yamma idan ya dawo. (Tofa Aunty gara maki Rufee da wannan hamshakiya, ba abin da za mu ce sai dai Allah ya kuɓutar da ke😭) Kuka Abbi ya iskota tana yi, ta haye saman bed nata tana kuka, gefenta ya zauna yana faɗin "Halima lafiya kuwa?". Cikin kuka ta ce "Haba Abbi akan me zaku ci mani fuska haka?" Yar dariya ya yi kafin ya ce "Haba Halima! Kefa kika bawa Hadiza dama ta zaɓi ɗakin da take son zama, bai kamata yanzu kuma ki dawo sheɗan yana zuga ki kice wani abin ba, kamata ya yi kema ki so ta kamar yadda ta so ki, kuma kamar yadda kika faro tun farko, ki duba ki gani fa yadda take yabon ki, baki ga matsa mani da ta yi akan lallai sai na rarrashe mata kanwarta kafin na fita ba, amma ki yi hakuri, idan na dawo zamu zauna mu yi magana kin ji ko?" Bai jira amsarta ba yana kai karshen maganar ya manna mata kiss a goshi ya miƙe ya fita. KADA KU GA LAIFIN ABBI, MAKIRAR MACE BA WASA BA, KAWAI KU TAYA AUNTY ADDU'AR ALLAH YA KWACE TA, AMMA MAKIRAN MATA SUN WUCI TUNANIN MAI TUNANI, BA BOKA BA MALAM SUKE MALLAKE GIDA, SU KUMA JUYA DUK WANDA SUKE SO, KUNA DAI GANI TA HANA ABBI MAGANA, SAI WANI RUFE MASHI BAKI TAKE YI, DUK WANI ZAFIN NAMIJI SAI DAI IDAN BAI HAƊU DA MAKIRAR MACE BA, TUNI ZATA JUYA SHI, KO SHEƊAN TSORON MAKIRAN MATA YAKE YI BARE MUTUN, ALLAH DAI YA RABA MU DA IRIN SU Yana fita aunty ta kara rushewa da wani sabon kukan tana faɗin "Ya Allah na wannan wace iriyar masifa ce, matar nan tun zuwanta ta ce bata so na, hasali ma bata kula ni ba, amma yanzu ta zo ta ce mashi wai tana so na, kuma zata kula da Ni, har da wani cewa nayi ɗawainiya da ita na bata zaɓin ɗaki, ta kashe ni ta gama da ni, Allah ka mani sakayya da gaggawa!!!" KUNJI ABUN DA YA FARU DA AUNTY JIYA KENAN BA RI MU DUBA WAJEN SU IRFAN MU DAWO. Daga karshe dai Irfan da ya gama waya ya buɗewa daddyn Jelly kofa tare da gaya mashi yadda suka yi da bandits ɗin, sannan kuma ya ce Akil ya ce zai bada kuɗin, zai cire daga Account nasa, sai su kai su ɗauko Aafia ɗin. Har wani nauyayyar ajiyar zuciya daddyn Jelly ya sauƙe dan ba karamin tashin hankali ya shiga ba, ƴa budurwa a hannun yan bandits ɗin nan, abin dole akwai tashin hankali. ALLAH SARKI BA KU MA SAN AN GAMA LALATA MATA RAYUWA BA😭. AFTER SOME HOURS👌 Aunty da Ayla ce zaune a palo suna hira, yanzu sun ɗan samu sauki a ransu tun da su Akil za su je ɗauko Aafia ɗin. Sai hira suke yi Aunty na kara koya mata yadda zata zauna da mijinta, yadda zata yi da daddyn ta. A wannan hali ya shigo bakinsa ɗauke da sallama ya same su, saman sofar kusa da babynsa ya zauna yana faɗin "Sadiya me ya same ki naga idon ki sun kumbura sun yi ja haka?" Murmushi ta yi kafin ta ce "Babu komai yaya Maik". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Saboda A'afia ce?" Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a ba komai. Dawo da kallonsa kai Ayla dake ta faman ɓoye fuska ya yi "Baby wai har Yanzu baki dai na jin kunya ta bane?". "Ina wuni daddy" shine abin da ta ce mashi, hannu yasa ya ɗan buge mata baki, cikin sauri ta rufe bakin nata da hannun ta tana yin kasa da kanta. Dariya Aunty ta yi kafin ta ce "Kun dai fi kusa ni bari ma na kawo maku abinci ku ci sai ku ji daɗin yin hirar" cikin sauri ya ce "A'a Sadiya ba sai kin kawo ba ni ba zan ci ba". Bawan Allah damuwar rashin A'afia da kuma halin da suka sami labarin tana ciki ne ya hana shi cin abincin. "To idan ma ka ƙoshi ai babyn taka bata ƙoshi ba, taki cin abinci tun safe" ta kai karshen maganar tare da miƙewa ta nufi dining table dan ta ɗauko mashi abincin. "Baby baki ci abinci ba, me yasa?" Ɗan satar kallon shi ta yi, nan take kuma abubuwa da Aunty ke gaya mata akan abin da zata rinƙa gaya mashi, ya faɗo mata a cikin ƙwaƙwalwarta, tuna haka yasa sai ta ce "Kai nake jira daddy muci tare". Ɗan waro dara-daran idanun nan nasa waje ya yi yana faɗin "Haba dai?" Ya yi maganar cike da jin daɗin furucin ta da kuma tsantsan kaunar ta. Gyaɗa mashi kai kawai ta yi yana murmushi. A gabansu aunty ta zo ta ajiye mashi tray ɗin abincin tana faɗin "To aci lafiya" ta kai karshen maganar tare da hayewa sama ta ba su waje. Ƙoƙarin fara zuba masu abincin ya yi, cikin sauri ta sauƙo ta karɓe shi tana faɗin "Daddy ka bari na zuba mana, ba aikin ka bane ai" ɗan leƙo fuskarta ya yi yana faɗin "Ya naga yau kin kara tsantsan kyau ne?" Hannu tasa ta rufe fuskarta tana dariya. Riƙo hannayen nata ya yi, har yanzu ya kasa dai'na taɓa mata hannu saboda da haka suka saba, ya saba riƙeta, amma dai yanzu baya yarda ya rungumeta idan yana rarrashinta, sai dai ya goge mata hawaye kawai. Janye hannun nata daga kan fuakarta ya yi yana faɗin "Ni da fuskar baby na ne zaki rufe Mani? Ina ruwan ki?" Zata yi magana kenan wayarsa ta fara kara, cikin sauri ya saketa tare da fito da wayar daga aljihunsa domin dama yana jiran kiran su Irfan dan ya fita zai je ya haɗu da Akil su je wajen yan bandits ɗin kai kuɗin. Miƙewa tsaye ya yi tare da yin picking call ɗin yana kara wayar a kunnansa,. A ruɗe Irfan ya fara magana cike da tashin hankali. "Hello bappa, mun samu nasarar karɓo su Aafia sai dai kuma kamar fa ta rasu bata da rai, bata numfashi, amma dai mun nufi hanyar asibiti da su yanzu, ka same mu a can, kuma dan Allah kada ka gayawa Abbi, ka bari tukun nan sai mun ji me likitoci za su ce, dan ina ji a jikina doguwar suma ta yi" ai tun Irfan bai karisa magana ba daddyn Jelly ya fice cikin sauri. Kai tsaye part nasu ya koma ya ɗauki key ɗin motar Irfan ɗin ya shiga da gudu ya bar gidan, yana tafiya a hanya ne Irfan ya tura mashi address ɗin asibitin, ba ɓata lokaci ya isa can. Wani katafaren private hospital ne, yana isa kuma lokacin motar Akil ɗin ta danno hanci cikin asibitin, a tare suka yi parking na motocin a parking space na hospital ɗin. Akil ya riga kowa fitowa, fuskar nan tasa babu alamar sauki ko kaɗan, yau a ɗaure take tamau, haka suka fito da Aafia da kuma Hanan, Aafia kamar babu rai a jikinta, fuskar nan ta yi wani Yellow kamar bata da jini, ita kuma Hanan bata suma ba, idon ta biyu. Nasan zaku so jin ya akayi ya zama A'afia da Hanan, to ku saurara, Irfan ya gayawa yan bindigar su biyu ne ba ita kaɗai ba, shine da suka tashi fito da su bakin dajin, in da suka yi da Irfan zai kawo kuɗi ya ɗauke su, sai suka ɗauki Aafia da kuma Hanan a maimakon Rufee, abin da yasa kuma suka ɗauki A'afia da Hanan ɗin, domin Hanan ita kaɗai ta kula Aafia, lokacin da ta farfaɗo daga sumar da ta yi, ta rungumi Aafia suna kuka, hakan yasa bandits ɗin suka yi tunanin cewa tare suke, kuma a hannun Hanan ɗin Aafia ta yi wannan doguwar somar, Rufee kuma bata iya magana ma bare ta je in da Aafia take, maman Zahra kuma ta yi iya kan nata rarrashin sai suka kyale Aafia ɗin da Hanan shiyasa da suka tashi, sai suka ɗauke su a tare. Hanan bata suma ba, amma bata a cikin hayyacinta sosai, saboda kiɗima da kuma tashin hankali da take a ciki, har yanzu tana ganin kisan da aka yi wa mamanta a cikin idonta ya ki gogewa, kuma abin ya ɗan taɓa mata kwakwalwa. Gaba ɗayan su cikin hospital ɗin suka wuce da su, da farko anki karɓarsu saboda ana tunanin ƴaƴan malam Shehu ne, sai aka ki karɓar su, Dr's ɗin suka fara cewa aa sai sun bi layi sun yanki kati da sauransu. Da yake daddyn Jelly ya san halin likitocin mu na yanzu, sai ya nuna masu fa e lallai akwai ruwan kuɗin, hakan yasa nan take suka karɓe su babu zancen bin layi bare kuma yankar kati, duk an mance wannan, suka karɓe su hannun bibbiyu zuwa ɗaki na musamman tare da fara duba su. Sai zarya a bakin kofar ɗakin Akil da Irfan, daddyn Jelly suke yi, har wani zufar wahala ne ke tsastsafo ma bayin Allah nan, tashin hankali iya tashin hankali sun shiga, bukatar su kawai suji ke matsalar, kuma Aafia ɗin tana raye ne ko dai ta mutu da gaske. Suna wajen har karfe 5 na yamma, sannan babban likitan ya fito yana faɗin "Sannunku" a ƙage Akil ya ce "Dr yaya me yasa me ta? Tana raye ko?" Ya yi maganar a ruɗe. Jinjina kai Dr ya yi irin alamar akwai damuwa, a tsanake ya ce "Kuyi hakuri fyaɗen da aka yi mata ne yasa ta zubar da jini sosai wadda ya haifar mata da rashin jini har ya kai ta ga doguwar soma, sannan kuma wanda ya yi mata fyaɗen ya ji mata babban rauni wadda sai an dage za'a shawo kan matsalar, idan kuma ba mu yi Sa'a ba muna iya rasa ta ko kuma kwakwalwarta ta ɗan taɓu, koma ta haukace baki ɗaya....." Wani irin Jiri Akil ya fara gani lokaci guda, nan take gaba ɗaya fuskarsa ya wanke da zufa, idan baku mance ba yana da bala'in zuciya, dafe kansa ya yi yana maimaita kalmar fyaɗe, shikenan sun lalatawa kanwarsa rayuwa, Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun, kafin su daddyn Jelly su farga ya zube kasa wanwar. Dama idan baku mance ba, ya gaya mata idan har ya bincika ta taɓa sanin Namiji to zai kasheta, tun daga wannan lokaci ya kama kusani cewa ba zai iya ɗaukar wannan musifar ba. Da sauri su daddyn Jelly suka yi kansa, suna addu'ar Allah yasa ba haɗiyar zuciya ya yi ya mutu ba, ɗakin da su Aafia ke a kwance nan aka shiga da shi, akwai sauran gadon da ba kowa, a nan aka kwantar da shi, ba ɓata lokaci shima likitocin suka dukufa akan sa, dan ceto rayuwarsa. Sosai zuciyarsa ke bugawa da karfi-karfi, Irfan da daddyn Jelly sunga tashin hankali iya ganin idon su yau, daddyn Jelly sarkin saurin kuka, to yau ya yi kukan har ya ga ji ya daina. Da kyar suka iya zama saman kujera, a nan suka yanke shawara a kan su rufe maganar iya su ukun kawai, kada kowa ya ji, ko Abbi ba za su gaya mashi ba, sai dai su ce mashi dukanta yan bandits ɗin suka yi har ta suma, a kan wannan shawara suka tsaya. A ɓangaren Jelly kuwa wato gidan Abbo. Sai shirya shiryen bikinta da Nawid Hajiya turai take yi, yau saura kwana goma cikin wa'adin da ta ɗeba na time ɗin bikin, har kayan da jelly zata saka ranar bikin duk ta sayo, sai shiri take yi, Hajiya Batula zata zo daga Maiduguri dan gyara Amarya nan da kwana biyar masu zuwa, duk wani kayan bukata Ummi ta sayo su, a ɓangaren Abbo kuwa yana ta faman shirya ta yadda zai yi ya ɗauketa ya maidata gidan sa a Abuja, domin Ummi dai ta ce sai anyi wannan aure, kuma idan ya cika yin jayayya da ita asirinsa zai iya tonuwa, shiyasa kawai ya yanke shawarar ɗauketa ana gobe biki, daga ɓangaren ita kuma Hajiya Jelly bata da masaniyar duk wannan abin da ake yi, ita dai tana ganin mata suna zuwa yin aiki tukuru, na gyare gyare gida, su yin cincin da sauransu, ita dai banda cin kaza ba wani abin da take yi, idan mata ta yi mata wani gani ta wanke ta tas soso da sabulu, haka Hajiya Turai zata basu hakuri ta ce kada su yi mata wata magana, suna ji suna gani kamar yarinya take gaya masu magana haka suke hakura ba yadda za su yi. a ɓangaren shi kuma Nawid yana can yana faman yadda zai shiga zuciyar Rimsha ya yi kane kane abinsa, ya yin da shima Ahmad yake ƙoƙarin kafa tasa gwamnatin a zuciyar Queen of beauty, sai dai kuma duk ba ta tasu take yi ba, yanzu ma dukufa ta yi akan karatun ta kawai, ta mai da hankali ga makaranta, idan ma sun kira waya Akila ke ɗauka, idan sun ce ta bawa Rimsha, sai ta ce masu tana barci ko wani abin, dan bata son abin da zai ɓatawa Rimsha rai, ta fi son ta ganta cikin farinciki, idan ta yi waya da Ahmad tana shiga cikin bakin kuma haka take wuni, shiyasa Akila ke shiga tsakanin su....✍️ Sai mun haɗu Monday idan mai dukka ya kai mu a gidan Abbi dan jin ya wannan al'amari zai kasance I'm waiting for Hot comments my yan Amana, JAMES Fans!!! * 💖💖TRIPLETS💖💖 *Idan kun samu typing error amin afuwa 👏 keyboard ɗin tana bani matsala sosai kwana biyun nan, to na yau ma ya fi tsananta, sai na danna girki sai ya koma kirki 😭* E 61-62 After one days🥰 🔥GIDAN ABBA🔥 A yanzu Rimsha ta goge ta zage da karatunta babu kama hannun yaro, kuma hakan bai hana ta mafarkin Lion da take yi ba, kullun tana mafarkinsa kamar yadda ta saba, sannan wayan nan hotuna da Imran ya turo mata sun zame mata kamar Tv, kullun tana manne da waya tana kallonsu, shi kuma Imran, duk time da ya sami dama yana fakon idon Lion ya ɗauke shi hoto ko video ya tura mata, hakan yasa ta tara hotonsa sosai da sosai. Yauma kamar kullun tana zaune cikin ɗakinta, ita kaɗai misalin karfe 3, Akila bata dawo daga school, ta baza takardunta a gaba tana dubawa, da alama an basu assignment ne, hankalinta ya dukufa akan takardun nata, wayarta dake a gefen ta ne ya fara kara, tana dubawa sai taga yaya Imran ne kuma video call. Wani kayatatcen murmushi ta saki kafin ta ɗauki wayar tare da yin picking na call ɗin, kamar dai yadda ya saba nuna mata Lion, to yau ma haka ne, sai dai yau ya sha bambam, domin yau kwance ta gan shi yana barci, ba ƙaramin burge Imra yake yi ba idan yana barci, hakan yasa ya kirata dan ita ma ta gan shi. Kasancewar idanuwansa a lumshe, hakan yasa ta kurawa zara-zaran eyelashes nasa ido, suna da tsawo masha Allah, a hankali ta dawo da kallonta kan wannan lallausan red lips ɗin nasa, ga bakin nasa ɗan karami, laɓɓansa na sama design of heart ne, kuma yana da ɗan tudu kaɗan, while na kasan kuma ya ɗan ɗara na saman kaɗan, kuma shi na kasan yana da ɗan faɗi kaɗan, daga kasan Lips ɗin nasa kai ka ce an zana mashi wani abine aka fito da shape ɗin laɓɓan sosai, amma kuma haka suke, haka Allah ya halitta mashi su kamar an fito da su da zane, yau sosai ta kura mashi ido tana kare wa kyakkyawar face nasa kallo, hancin nan nasa ba'a magana, bai yi dogo irin zut ɗin nan ba, a'a wani irin ne nashi akwai kara amma ba irin wannan kara mara kyan gani ba, soft skin ɗin nan nasa ba'a magana har wani sheki yake yi, hasken sa ya kafara fitowa, jikinsa kamar madara, cikin kwanciyar hankali yake sauƙe numfashi, da alama yana jin daɗin barcin da yake yi. Almost 30mins tana kallonsa kafin Imran ya fice daga cikin ɗakin. Sai bayan ya fita ne ya juyo da camerar kan fuskarsa, ɗan sunnar da kanta kasa ta yi tana yan kame-kame. "Our first lady, fatan dai ana karatu sosai? Kada ki zo tunanin Saif ya hana min ke karatu, gara ki zage dan Saif baya son mutumin da bai yi karatu ba". Ɗan motsa kyawawan laɓɓanta ta yi, nan take dimple ɗin ta suka lotsa dukka biyu, hakan ba karamin kara fito da kyan fuskarta ya yi ba. "Yaya Imran ina karatu sosai ma" jinjina kai ya yi kafin ya ce "Heartbeat bata dawo ba ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e. "Okey idan ta dawo ki ce mata na ce ta bawa dolly abinci tunda ke kina tsoro, sannan yayan ku Akil zai taho da wata kanwar mu Aafia, za ku kwana da ita, gobe zai wuce da ita da Umaisha gidansa, fatan ba zata takura maki ba?" Da fara'a akan face nata ta ce "E yaya Imran, yaushe zata zo?". Shiru ya ɗan yi kafin da bisani ya ce "E to yanzu ma zaki iya ganin su, bata da lafiya ne, ku kula mana da ita sosai" To ta amsa mashi da shi, sannan ya mata fatan alkhari akan Lion kamar yadda suka saba, daga nan suka yi sallama. Ajiye wayar ta yi a gefenta ta cigaba da duba takardun nata. A ɓangaren su Aafia kuwa, kwana ɗaya da wuni ɗaya ta yi kafin ta farfaɗo, ita kuma Hanan dama bata suma ba, hakan yasa jikinta ya yi kyau sosai, dan ta sami kulawar likitoci, da farko Akil daya farfaɗo ya dawo cikin hayyacinsa ya yi yunkurin korin Hanan ɗin, dan ya ɗauka ita ma tana daga cikin kawayen Aafia, daddyn Jelly ne ya dakatar da shi, ya ce mashi koma kawar Aafia ɗin ce su yi hakuri su karisa aikin da suka fara domin su sami ladan gaba ɗaya, ya bari ta sami lafiya tukun nan, dan a yadda suke ganin tan nan a cewar su idan ya koreta a yanzu ba zata iya gane gida ba, saboda bata gama dawowa daidai ba, ba don ya so ba ya hakura suka zuba ido suna jiran tashin Aafia. Baiwar Allah lokacin da ta farfaɗo da kukan azaba ta tashi, tana ihu kamar zautatciya tana surutai akan bata so ya rabu da ita, kada ya cutar da ita, yaya Irfan zai kasheta, yaya Akil zai kasheta, ita bata so ya kyaleta, idan yana so ya sa bindiga ya harbeta, amma kada ya keta mata haddinta, sosai take kuka tana sambatu. A wannan gaba har Irfan sai da ya zubar mata da kwalla, shi kuwa Akil sosai idonsa suka ciko da kwallar amma bai bari sun zuba ba, idanun nan nasa sun yi jawur kamar wuta, bawan Allah sai sara mashi kansa ke yi, ya rasa meke yi mashi daɗi a duniyar nan, shi kam daddyn Jelly ai ya jima ma da fara nashi kukan, tunma bata farfaɗo ba, da ta farfaɗo tana wannan sambatun kuma, sai abin ya kara taɓa mashi zuciya. A wannan rana dai sun sha kuka, sai rarraahinta suke yi, har shi kansa Akil ɗin yau rarrashinta yake yi, dan duk wani mai Imani ya ga halin da take a ciki, sai ya zubar mata da kwalla. Bayan komai ya lafa ta dawo daidai ne, can yamma kusan mangariba. Bayan sun sha rarrashinta da kyar suka samu ta hakura ta fawwalawa Allah komai. Misalin karfe 8 na dare gaba ɗayan su suna zaune har da Abbi da Aunty, Ayla da Kuma Hajiya Hadizatu wato Ommu, duk sun zo dubata dan Akil ya kira su ya gaya masu yan Kidnaping ɗin sun yi mata duka sosai sun ji mata ciwo tana asibiti, bai gaya masu cewa sun yi mata fyaɗe ba, sun rufe abin iya su AKIL DADDY'N JELLY, IRFAN, AAFIA ƊIN SAI HANAN iya su kawai suka san da zancen, su Abbi sun zo ne gaba ɗaya dubata, sai kukan munafurci Hajiya Hadizatu take yi, har da jan hanci, ita adole yarta ta sha wuya, bayan kuma tun da ta dawo Nigeria bata nemi ƴaƴan nata ba, amma yanzu ta zo tana cikawa mutane kunne da kuka, ko da ta zo asibitin ma kuma ita Aafia ɗin bata ko yi mata wani kallo sosai ba, dan magana ta gaskiya ba su wani son ta, domin tun asali bata ja su ajiki ba, bata wani kulawa da su, hasalima idan Abbi ya yi mata wani laifi ce mashi take a gabansu ta yi nadamar haihuwa tare da shi, kuma akan su take sauke haushin laifin da ya yi mata, ta yi ta yi masu masifa tana zaginsu, wata sain ma har da duka, abin da ya fara haɗa su faɗa sosai da Abbi har ta kai ga zage-zahe ma shine, lokaci da ta sa mi cikin Umaisha ta ce sai ta zubar, ba zata haifi wannan ciki ba, dan ta ga ji da haihuwa cikin talauci, sun sha faɗa sosai tsakaninsu, kuma duk da haka bata fasa yunkurin zubar da cikin ba, sai dai da yake Allah ya ƙaddara sai Umaisha ta zo duniya sai da ta zo, duk wani maganin zubar da ciki da ta sha a banza ta shashi, haka ba dan ta so ba ta raini cikin, Aafia da Irfan sun ci bakar wuya a hannunta, duka, zagi yayan matsiyaci kamar ba ƴaƴan ta ba, haka ta rinƙa azabtar da su da laifin babansu wadda shima ba laifin sa bane dan ya sami karayar arziki ne, kuma abin da ya jawo hankan ta fara faruwa, tun lokacin da ya sami karayar arziki ta ce ya saketa, shi kuma ya ki yarda, shine ta fara azabtar da shi, da shi da ƴaƴan nasa dukka, idan daddyn Jelly ya yi magana ta ce za su yi dambe, alokacin shima bai wuce 18 years to 19 ba, bayan ta haifi Umaisha kuma, ta ki yarda ta shayar da ita nono, ba yadda Abbi bai yi ba, amma ta ki yarda, daga karshe Umaisha dai madara ta sha, kuma tana da shekara uku Ommu ɗin ta bar masu gidan, wai ta ga ji da talauci. A lokacin gaba ɗaya yan uwan Abbi suna da kuɗi sosai, shima karayar arziki ya samu ba dan haka ba yana da kuɗi sosai, shiyasama ai ta yarda ta zauna har ta haifi su Irfan ɗin, dan yana da kuɗi sosai da farko, a lokacin dukka yan uwansa sun ki bashi kuɗi ya farfaɗo da kansa ne saboda Hajizan, dan ita ya sa suka ki taimaka Mashi, dan sun san ko da sun ba shi ruwa zai sake koma, kaso 80 cikin ɗari na karayar arziki da ya samu ma suna zargin ita ce sila, dan alokacin da yake da kuɗin ba shi da aiki sai kai ta kasashen ketare ita da yan uwanta, ta tafi yawon buɗe ido, ta barshi da yara a gida, yana wahalar raino, hakan yasa su Abba suka ki taimaka Mashi har sai da ta bar gidan, lokacin shima daddyn Jelly yana da makudan kuɗaɗe na gadonsu, sai dai yana makaranta kuɗin suna wajen Abba, shi ya so bawa Abbi kuɗin dukka, saboda shi yasan halin da Abbi yake a ciki, dan gida ɗaya suke, Abbansu Imran ne ya hana shi, haka suka zuba wa Abbi ido kawai, haka kuwa suka yi, bayan tafiyar Ommun ne Abba ya bashi jari, lokacin kuma daddyn jelly ya bar Kaduna saboda bala'in Hadiza, yana ji yana gani tana azabtar da su Irfan da kuma yayan sa, ga shi ba halin ya yi magana, ta yi abinci ta hana Abbi, ga shi ba kuɗi ke gare shi ba, Hajiya Umaiya bata son su bare ya je gidan Abba ya ci abinci, domin farkon auren Hajiya Umaiya tana girki sosai, komai tsab-tsab, kuma ta iya girki, sai bayan ta Haifi Akila ne abin ya fara juye mata kwakwalwa, da farkon auren su, tana bala'in son yan uwan mijinta, dan sun mata komai, sun so ta sosai, daga bayane kamar ba lafiya ba, ta riƙiɗe ta koma wata iriya da ita. NA SAN KO BAKU SAMI DOGON BAYANI BA, KUN FAHIMCI IN DA LABARIN YA DOSA, KUN FAHIMCI WASU ABUBUWA DA SUKA FARU A BAYA A GIDAN ABBI, TO IN SHA ALLAH MUNA TAFIYA ZAN WARWARE MAKU KOMAI. Daga Kano daddyn Jelly ya aikowa da Abbi kuɗi, haka suka haɗa shi da Abba suka ɗan farfaɗo da Abbin, da Hosain ya tashi shine ya yi mai kankat ya zubawa Abbi ruwan kuɗi, wannan ya sa Abbi ya farfaɗo, haka ya cigaba da rainon ƴaƴansa har Allah ya raya mashi su, bai yi aure ba har sai kwanakin can da ya auri aunty, shima kusan kamar daddyn Jelly ne, ya shafi shekara kusan sha biyar ba mata tun bayan tafiyar Ommu, kafin daga bisani ya auri aunty, lokacin da Umaisha ta girma ma a yan tsakanin nan Abbi ya sake gamuwa da karayar arziki ta yan damfara wadda har ta kai ga yana ƙoƙarin sayar da kamfanin sa, sai da ɗan uwansu Husain ya taimaka Mashi idan baku mance time ɗin ba, a takaice kenan Abin da ya sanya su Aafia basu damu da Ommu ba. Story. Har da wani rungume Aafia Ommu ta yi tana kukan munafurci, daga Aafia har su daddyn Jelly sun yi mamakin ganin Hajiya Hadiza na kuka akan su Aafia, Irfan kam sake baki ya yi yana mamaki, yana ganin ikon god. Sai da Abbi ya rinƙa rarrashin Ommun sannan ta yi shiru tana wani faɗi kamar zakanya. Bayan wasu mintuna komai ya lafane, Akil ya tambayi Aafia wace ce kuma Hanan, kawar ta ce ko waye. Allah sarki Aafia da kyar Muryar ta yake fitowa, haka ta fara basu labarin yadda suka haɗu da Hanan ɗin, da kashe mata mahaifiya da yan bandits suka yi dukka ta basu labarin komai. Daddyn Jelly ya fi kowa tausaya mata, da yake shi zuciyarsa a kusa take, yanzu yake iya kuka akan abu, haka zalika yanzu zaka mashi abu ƙarami ya ɓata mashi rai, sai dai da yake bawan Allah ne yana ƙoƙarin a ko da yaushe yana ɓoye ɓacin ransa, ba zaka taɓa sanin ya ɓata rai ba, amma da ga ta ciki shi yasan me yake ji, suna yi mashi kallon mai hakuri sosai, hakan yasa ma idan ya fito da ɓacin ran sa fili suke mamaki, har su ce e lallai abin da aka yi mashi, abune nai girma, kuma daɗin daɗawa baya shiga harkar kowa. Abbi ne ya dubi Hanan dake kwance saman bed nata tana kuka, Aafia ta tuna mata da mamanta, a nutse ya fara tambayarta yar ina ce ita, tana kuka ta fara basu labarin gidansu, da irin halin babanta, da komai bata rage wani abu ɗaya ba, hakan yasa suka kara tausaya mata sosai da sosai, Abbi ya ce to idan ta samu lafiya ta huta, za su rakata har zuwa gida Katsina sai su gayawa babanta abin da ya faru, sannan su ruke shi alfarman ya basu ita su dawo da ita gida, Abbin ya ce zai riƙeta kamar yarsa, cikkin sauri Ommu ta katse shi da cewa "Ba dai kamar yarka ba Abbi, sai dai ka riƙeta dai, amma ƴaƴan ka sun wuce ka haɗa su da wata bare, ai yan gida daban ne". Duk cikin ɗakin ba wanda ya tanka mata, da ido kawai suka bi ta da shi, bata wani damu ba, dan tasan ba son ta suke yi ba dama. Bayan an sallame su Akil ne ya wuce da Aafia gida, ya je ya ɗauki Umaisha, basu ma kwana ba a daren suka wuce gidansa wadda yake a ta anguwar da Lion yake, ba su da nisa sosai, nan ya mai da su, su biyu a cikin gidan kawai, Akila ta ji daɗi sosai, kuma ta yi kukan dan kafin ta je gidan Akil sai ya kwana biyu, saɓanin da da suke tare da Umaisha kullun, da farko Ammie ta ki yarda ya ɗauki Umaisha ɗin, sai da ya ce mata ai gidansu zai mai data, ta zauna a can, shine ta yarda, da yake ba fita take ba, sai bai wani damu ba, dan yasan ba zata je gidan sa ba, ita kuma bata kawo cewa zai yi mata karya ba, domin bata taɓa kama shi ya yi mata ba ko da sunan wasa. A ɓangaren ita kuma Hanan, gida su Abbi suka wuce da ita, Aunty sarkin tausayi, tuni ta riƙeta kamar kanwa, Abbi ya ce narar Saturday za su je Katsina wajen iyayen Hanan ɗin, da wannan zancen suka rufe maganar. A hanyar asibiti kafin su dawo gida daddyn Jelly ya sayi waya mai kyau, dama kuma already yana da sim card nasa da ya cire a wancan wayar tasa da ta lalace. Washegari tun safe daddyn Jelly yana kwance a ɗakinsa bai fitoba, ko da Irfan ya kawo musu breakfast ya kasa fitowa ya ci, yana kwance, da alama yana cikin wata damuwar ne. Misalin karfe 3:30 na rana, Aunty, Hanan, Ayla, suna zaune a palon kasa, Ayla da Hanan sun zama kamar yan uwan juna, sun haɗa kai sosai, sai hira Hanan da Aunty suke yi, ita kuma Ayla sai bin su da uhm, hmm kawai take yi, da alama ita ma akwai abin da yake damunta. Dukkansu kaya color ɗaya suka sanya, Hanan ta saka blue abaya na Aafia, dan ta girmi Ayla, kayan Ayla sun yi mata kaɗan, sai ta sanya wadda Aafia ta bari, ita kuma Ayla abayar da suka sawo a shopping ita da daddy'nta, mai shegen kyau blue color ta sanya a jikinta tare da yafa mayafin abayar. Aunty da ta lura da hakan sai ta ce "Yau tun safe ban ga yaya Maik ba, ko lafiya?" Cikin sauri Ayla ta amsa ta da cewa "E nima tun ɗazun na ke son tambayar ina ya tafi". Dariya sosai Aunty ta yi kafin ta ce "Dama na tsokalo zancen Yaya Maik ne dan na gane meke damunki, to dai yanzu na gane, wato dai kewar mijin naki kike yi, shine muna magana kina yi mana shiru ko? Eyeee dole Abbi ya zo gobe a ɗaura auren nan, wlh dole na zuga shi, ina na isa, tun ba'a je ko'ina ba har kin fara kewa ko?". Kifa kai ta yi a bayan Hanan tana murmushi kasa-kasa, ita kuma Hanan da kallo ɗaya zaka yi mata kasan tana cikin matsanancin damuwa sosai, kawai daurewa take yi tana hiran da su, kuma dama Aunty da gangan take kara jawota da hira, dan saboda ta mance da damuwar da take a ciki. "To amarya ta ango jeki part nasu ki duba mana ko lafiya bai leƙo mu ba yau, amma fa kada ki daɗe". Cewar Aunty kenan. Da sauri ta miƙe ta nufi kofar palo, har zata fita kuma, sai ta fasa, ta dawo ta haura sama, jim kaɗan ta fito sanye da hijabinta har kasa launin blue, kalar abayar jikinta, sai murmushi take yi, an sami abin da ake so, za'a je duba masoyi. Kai tsaye part na Irfan ta nufa, da sallama ɗauke a bakinta ta shigo Palon, babu kowa, dan haka sai ta nufi ɗakin daddyn nata kawai. A bakin kofa ta yi sallama, yana daga kwance ya amsa mata, yana ƙoƙarin ce mata yana zuwa da yake baya son ta shigo ɗakin, saboda ba wani kayan kirki bane a jikinsa, daga shi sai Short da singlet. Bai kai ga ce mata yana zuwa ba kawai ta shigo mashi ɗakin, da yake yana kwance, kuma ya ɗan ja bargo zuwa kugunsa dan akwai ɗan sanyi garin, hakan yasa bata gane cewa short ne kawai a jikinsa ba. Kusa da gadon ta zo ta tsugunna tare da faɗin "Ina wuni daddy". Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe tare da miƙewa zaune yana kallonta, while ita kuma tana kallon kasa. "Lafiya lou baby, yau tun safe ban ganki ba, kewarki ta dame ni, kuma na kasa fita, yanzu ma kuma na kasa ce maki kije Palo dan ina son ganin face naki sosai". Ya kai karshen maganar yana ɗan leƙo fuskarta. "Daddy to lafiya yau baka fito ba?" Ta faɗa a sanyaye. Nisawa ya yi kafin ya ce "Yau Jelly take cika shekara 16 daidai, yanzu haka shekaran ta sha shida da awa bakwai da suka ɗauru a kai, da safe aka haifa mani ita, ina kewar ta sosai, ɓatar ta ya dawo mani sabo, ban taɓa rabu da jalila daidai da rana ɗaya ba, sai ranar da ta ɓata, shekara sha 16 muna tare, ba dare ba rana, kin ga ai dole yau daddy ba zai iya fita ba". Ya kai karshen maganar cikin raunataciyar murya kamar zai yi kuka. Allah ya gani bawan Allah yana bala'in kaunar jelly fiye da kansa, Allah kaɗai ya san me yake ji a cikin zuciyarsa, musamman yanzu da ya ga halin da Aafia ta faɗa, ya kara tayar mashi da hankali sosai da sosai, jiya kwana ya yi yana Sallah yana rokan Allah akan duk in da jelly take Allah ya tsare mashi ita, zuciyarsa ba zata iya jure makamanciyar abin da ya faru da Aafia ya faru da Jelly'n sa ba, idan hakan ta faru ya san shikenan tasa ta zo karshe, mutuwa zai yi, wannan dalili yasa ya kwana yin Sallah jiya, yana sallah yana kuka yana gayawa Allah bukatunsu, bayan ya gama ya yi karatun Al Qur'ani mai girma har sai da lokacin yin sallar asuba ta yi, sannan ya yi sallah ya ɗan kwanta, karfe takwas daidai ya farka, dan ya sa alam ta tashe sa takwas daidai. Shiru Ayla ta yi tana tunanin zan tukan Aunty na yadda take gaya mata yadda ake yi wa miji idan yana cikin damuwa. (Aunty kin yi kuskure da baki gaya mata cewa dukka wannan shawara ta barshi sai bayan aure ba, kin ce haka zata rinƙa yi mashi kawai, ya kama arinƙa banbance mana, saurayin da za'a aura daban, miji daban atom) Sosai ta nutsa cikin tunani tana tariyo zancen Aunty a kanta, can kuma sai ta ce "Daddy da farko dai kayi hakuri, In Sha Allah baby jellynmu zata dawo, na biyu kuma..." Bata karisa maganar ba sakamakon matsowa da ta yi ta riƙo hannayensa tare da ɗago kanta, ganin shi da ga shi sai Short da singlet ne yasa ta yanke maganar bata karisa shi ba, kwata-kwata bata yi zaton ba kaya masu ɗan girma a jikinsa ba. Cikin sauri ta miƙe dan ta bar ɗakin, kankame hannunta ya yi a cikin nasa ya ki bari ta tafi. KADA KU GA LAIFIN AYLA BATA DA ILIMI KUMA YANZU DA AUNTY KE WAYAR MATA DA KAI, SAI TANA NUNA MATA AKAN KOMAI ZATA IYA YIWA DADDYN JELLY DAN MIJINTA NE, A NATA TUNANIN AI SHI DADDYN JELLY BA ZAI YI MATA KOMAI BA, SHIYASA BATA WANI DAMU BA TAKE BATA WAYAN NAN SHAWARWARI, TO SHI DADDYN JELLY DUTSE NE? KU TAYA NI JI DA GANI, KADA KU MANCE SHEKARA SHA 16 YANA GWAURO🤣 AI SAI DAI MUCE ALLAH YA TSARE!. "Ina zaki je baby?" Ya faɗa yana matse mata hannunta cikin nasa, wadda shi kansa ma, bai san yana yin hakan ba. Cikin in'ina ta ce "Ba...ba... ko'ina daddy". Wani irin shauki yake ji a tattare da shi, shiru ya yi yana jin yadda zuciyarsa ke azalzalansa, (sheɗan na gefe😭 Allah ka rabumu da tsinanne🤲) A hankali ya tsinci kansa da jawota jikinsa, kusan a tare suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya, hannu yasa ya laluɓo wayarsa da ya saya jiya dake saman bedside drawer, idanuwansa har sun rikiɗe, yana jin matukar sha'awa ba na wasa ba, har wani rufewa idanun nasa suke yi. Rungumeta ya yi a jikinsa tare da fito da number Abbi ya fara kira. Bugu ɗaya Abbi ya ɗauka, muryarsa da kyar take fita ya fara magana "Yaya Deen ina kake?". A ɗan ruɗe Abbi ya ce "Maik lafiya? Ya naji ka haka? Ko dai baka da lafiya ne?" Nisawa ya yi tare da kara matseta a jikinsa, ita kuma bata wani damu ba, domin ba'a gaya mata harancin yin hakan ba, sai ma lafewa da ta yi a jikin nasa. "Yaya Deen ina lafiya, dan Allah ina kake yanzu". "Gani nan tun da na fito daga masallaci sallar azahar na tsaya muke tattaunawa da malam liman akan ya ɗaura auren nan naka gobe Jumma'a dan ba zan iya bari wannan dama ta kubceba ato, Allah bashi idan aka ɗaura auren sai ta cigaba da zaman ta a Part ɗin namu tana zuwa school ɗin, amma dai da aure a kanta, dan ba zan lamunci wannan rike hannun ba". Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce "Yaya Deen ka ce da liman tun da la'asar ya kawo kai idan an fito sallah kawai a ɗaura auren, daga baya za'ayi duk wani abin da ya rage". Cike da murna Abbi ya amsa da to, dan dama burinsu kenan, ya yi aure ko zai samu natsuwa sosai. Ba tare da ya katse kiran ba ya ajiye wayar a saman bedside drawer, daga ɗayan ɓangaren Abbi ne ya katse kiran. Dawo da wayan nan rinannun idanun nasa ya yi a kan fuskarta.Ta lumshe ido tana shakar kamshin jikinsa. "Baby kin ji shawarar da na yanke ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e. "Idan hakan bai yi maki daɗi ba kiyi hakuri, ba zan iya cigaba da saɓawa Allah ba na taɓa ki da nake yi, na san cewa ba zan iya ganinki ban taɓa ki ba, shiyasa kawai gara a ɗaura mana auren in yaso ki zauna da su Sadiya har sai na tashi komawa Kano mu tafi, kinga idan akayi aure ko na taɓaki ba wata matsala". Ɗago da kaita daga kirjinsa ta yi, a nutse ta ce "Daddy duk abin da ka yi daidai ne, dan Aunty ta gaya mani, ba zaka taɓa yin abin da zai cutar da ni ba". Wani irn daɗi ya ji a hankali ya ɗago da hannunsa ya shafi face nata yana faɗin "Ban san yaushe, kuma a ina na kamu da azababben so da kuma kaunar ki ba, kina rikita ni dayawa". "Daddy nima ai ina sonka sosai" "A'a nawa ya fi yawa, kawai ina zaman zamana kin zo kin rikitani" yar murmushin ta yi zata yi magana kenan suka ji muryar Hanan a palo tana doka sallama. Ayla ce ta amsa mata daga cikin ɗakin. "Ayla Aunty ta ce wai ba ta ce kada ki daɗe ba? To ki dawo hiran ya isa haka" shine abin da Hanan ta faɗa. Ayla zata yi magana daddyn Jelly ya rigata da cewa "Ki je ki ce mai ita ya riƙe abarsa, dan haka Sadiya ta barmu mu sha iska" yana magana yana sha fuskarta. To Hanan ta amsa da shi tare da ficewa ta koma cikin gida. Shiru suka yi kamar wayan da aka cewa su yi shiru, ya zuba mata ido yana kallon kyakkyawar fuskar ta, yayin da ita kuma take kallon mirror dake a cikin ɗakin. "Baby ta shi ki hauro gadon gaba ɗaya" ya yi maganar kasa kasa. Da yake yana ta bakin gadon ne, kuma yadda ya jawota jikinsa kusan rabin jininta yana ta kasan gadon ne, kanta ne ke kwance a saman kirjinsa, shiyasa ya ce ta dawo saman bed ɗin gaba ɗaya. Ba musu ta miƙe ta haye saman bed ɗin gaba ɗaya, tana hawa ya kara jawota jikinsa tare da cire hijabin jikin nata dan hijabin yana takura mashi, baya shafa face nata da kyau. "Babyna baki ce komai ba akan auren da za'a ɗaura mana nan da minti goma zuwa Ashirin ba?" Ɗagowa ta yi tana kallon face nasa a sanyaye ta fara magana "Daddy Aunty ta gaya mani abin da ake nufi da aure, kuma na yarda saboda ina son yin rayuwa da kai ta har abada, kana da kirki sosai, kana son farincikina, dole nima zan so ka sosai daddyna". Hannu yasa ya matse mata ɗan bakin nan nata, a hankali ya lumshe idanunsa tare da buɗesu a saman face nata, har lokacin yana ruke da lips ɗin tata. "Waye daddy?" Ya faɗa da wata iriyar murya wadda da ka jita ba sai an gaya maka ba kasan a kusa yake. Shagwaɓe fuska ta yi zata yi mashi kuka dan ya matse mata lips sosai, shi kuma zafin da yake ji a jikinsa ne yasa ya ɗan matse mata lips ɗin tata da ɗan karfi, hasalima bai san ya matse da karfi ba, dan jikinsa ke azalzalarsa. Sai da ya ga ta fara hawaye sannan ya sake lips ɗin tare da kara matseta sosai a jikinsa, ya matso da face nasa daf da tata har suna iya shakar numfashin juna, ya kasa kyafta ido daga kallonta, ita kuma wuyarsa take kallo. "My baby ba zan ga ji da faɗe ba kina rikita ni sosai" ɗago da idonta ta yi izuwa cikin nasa idon, kamar ta kara ingiza zuciyarsa ne, har wani zirr yake ji a jikinsa. Dawo da kallonsa ya yi kan laɓɓanta, a hankali ta fara motsasu ta ce "Daddy ni ban san ma taya nake rikita ka ba, ni wlh ban ma san me rikitawan ba, amma dai tom ka gaya mani menene?". Kasa jurewa ya yi, lokaci guda ya haɗe bakinsa da tata ya fara bata hot kiss, mutuwar kwance ta yi, domin bata taɓa jin wani abu makama mancin hakan ba, kuma bata taɓa gani ba, ita dai tasan Rimsha ta taɓa gaya mata mafarkin Lion da ta yi na zai yi kissing nata, to bata ma san me kiss ɗin yake nufi ba, sosai ta shiga duniyar tunani tare da mutuwar kwance. Shi kuma sosai yake kissing nata, ya kankameta a jikinsa yana fitar da wani irin numfashi, sai wasa yake da harshensa a bakinta cike da kwarewa. Kiran sallar la'asar ne ya dawo da su cikin hayyacin su. A hankali ya zame bakinsa daga tata, sai kuma me, wani irin kunyarta ne ya kama shi, ita ma duk da bata san me hakan yake nufi ba, ta ji matsanancin kunyarsa ya kamata, Ayla bata san kiss ba, duba da yadda ta ta so, ba abinci a gidansu ma bare kuma Tv kallo da zata kalla ko a Film ne, bata da kawa ko yar uwa, daga mamanta dake kwance ba kafiya sai ita ɗin, rayuwarta rabi a wajen bara, rabi kuma a Daular Mutuwa ta kare, baiwar Allah bata san komai ba sai wanda Rimsha da Aunty suka koya mata, dan ma Allah yasa tana sa natsuwa da sanyin hali, ba dan haka ba ai da shikenan kuma sai dai muce Allah ya tsare. Shiru ta lafe a jikinsa tana tunanin menene daddy ya yi mata, shi kuma yana kankame da ita yana lumshe da idanunsa, dan baya son buɗewa bare su yi ido huɗu. Suna zaune a wajen ya kasa motsawa, yana ji har aka idar da Sallar la'asar, ba shi ya tashi motsawa ba har sai da wayarsa ta fara kara alamar shigowar kira. Da kyar ya iya kai hannu ya ɗauki wayar, tamkar wadda aka zarewa laka, haka ya dawo. Picking na call ɗin ya yi tare da kara wayar a kunnensa, ya kasa magana ya yi shiru yana jiran wanda ya kira ya yi magana. Daga ɗayan ɓangaren Abbi ya ce "Hello Maik an ɗaura fa, yanzu muka gama, saura na kira su Irfan na sanar da su". Jinjina kai kawai ya yi tamkar Abbi na a gabansa, daga nan ya maida wayar saman bedside drawer ya ajiye, jin bai yi magana ba yasa Abbi ya yi tunanin ko ba lafiya yake ba kawai yana ɓoye masu ne, cikin sauri ya kamo hanyar gida, dan ya zo ya duba ɗan uwansa lafiya ko yaya ake ciki. Shi kuma bayan ya ajiye wayar, sai ya sa hannunsa ha ɗago da fuskarta suna fuskantar juna, idonta a lumshe ta kasa buɗe wa dan tana matsanancin jin kunyarsa. Kamar mai raɗa haka ya furta sunan ta babyna, kasa-kasa ita ma ta amsa mashi, da murya ciki ciki, da alama dai ita ma jikinta ya karɓi saƙo yadda ya kamata. "Yanzu fa kin zama matata, halak na, ni kaɗai" yana magana yana jingina kansa da jinin headboard na gadon tare da ɗaga kan nasa sama kamar mai tunanin wani abin. Hannunta dukka biyu ta zura ta bayansa ta kankameshi da kyau, a shagwaɓe ta ce "Daddy shikenan dama haka kawai akeyin aure? Ni na zaci da ake cewa igiya uku akan mutun, na zaci sai an ɗaure shi da igiya uku ai kafin nan ya zama matar aure". Tana magana idanuwanta a lumshe ya yin da hannayenta ke a saman bayansa ta ɗaura su, tana ɗan yawo da su a wuraren. Nisawa ya yi tare da ɗago kansa daga jikin headboard ɗin, da kyar ya waro idanunsa gaba ɗaya a kan face nata. Ran kwafo da kansa ya yi izuwa daidai saitin face nata, kasa-kasa ya kira sunanta, tana ɗagowa ya zura harshensa cikin bakinta tare da kankame ta sosai a jikinsa, wannan ya wo da hannun nata da take yi a bayansa, ba ƙaramin kara rikita shi take yi ba. Shima zura hannayensa ta bayanta ya yi, ya hauro da hannunsa ɗaya ta daidai kanta, a hankali ya ɗan ja kan nata baya ta yadda zai sami damar yi mata kiss sosai, while ɗayar hannunsa kuma, yana ta kugunta ta bayan, ya tallaɓo ta da kyau. Ita dai idonta a lumshe sai karɓar saƙo kawai take yi. Almost 5mins suna a haka kafin ya saketa, suna sauke numfashi a hankali hankali kusan a tare kuma. Sun ɗauki 10mins a haka kafin ya ce "Baby ki yi wa daddy afuwa kin ji?" "Daddy afuwar me kuma?". Ta yi maganar tana ƙoƙarin zame hannunta daga bayan nasa. Riƙo hannunta ɗaya ya yi cikin nasa, ɗayar hannun nasa kuma, ya yi amfani da shi yana shafa kanta zuwa wuyarta da ta kwantar masa a saman kirjinsa. Yana ƙoƙarin yin magana, suka ji sallamar Abbi a bakin kofa. Kallon face nata ya yi, ko ajikinta bata wani damu ba, ɗagowa ya yi ya amsawa Abbi sallamar. Bai gama rufe baki ba, Abbi ya shigo a ruɗe yana faɗin "Maik me yake damunka? Ya na ji muryanka can kasa? Baka da lafiya........" Bai kai ga karisa maganar ba idonsa ya sauka akansu gaba ɗaya, kasa da kai daddy'n jelly ya yi dan ya rasa bakin magana, kuma har ga Allah bai so barin Abbi ya shigo ɗakin ba, kawai dai ya kasa yin magana sosai ne, kuma shima Abbin yana ruɗe ne, burinsa kawai ya shigo ya ga wani hali ɗan uwansa ke a ciki da yake magana kasa kasa haka, da kyar ma ya iya tsayawa har sai da Maik ɗin ya amsa mashi sallamar, amma jikinsa har tsuma yake yi, akan ya zo ya ga ɗan uwansa. Ganin haka yasa Abbi juyawa da sauri har kamar zai faɗi, ya fice daga ɗakin, yana fita kuma a tare suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya shi da daddyn Jelly ɗin. "My baby jeki kiyi wanka ki yi Sallah time na kurewa, idan kin yi sallah sai ki kawo mani abinci na kin ji? Amma fa daga yau idan zaki zo nan, kada ki saka mani manyan kaya bana so, kisa kanana sai ki ɗaura hijabi a sama, anjuma da daddare ma dole muje shopping dan na saya maki kananan kaya sosai, dan ina son su, suna kuma birgeni" ya kai karshen maganar tare da manna mata kiss a goshi. Murmushin ta yi tare da miƙewa daga jikin nasa ta sauƙo kasan gadon, zuba mata ido ya yi yana kare mata kallo, yau ba hijabi a jininta, dan ya cire mata, kalle kayarsa yake yi sosai. Hannayensa dukka biyu ya ɗaura a saman hips nata ta gefe dukka biyun, ya riƙosu yana faɗin "Baby ke fa zaki yi kiba kaɗan idan kika huta kika samu kula da abubuwan da suka dace" yana magana yana kare ma breast nata kallo, masha Allah da su, dan duk tafi su Rimsha shekaru, kuma ta fisu cika, barema yanzu da ta fara samun kulawa da kwanciyar hankali, sai kara cika take yi abinta, abin sai dai Masha Allah. "Baby baki ce komai ba?" Murmushin ta yi kafin ta ce "Daddy ai bansan me zan ce bane" "Yau shawarar Sadiya ya kare kenan?" Dariya ta yi har sai da fararen hakwaranta suka bayyana, tana ƙoƙarin yin magana ya rigata da cewa "Tom kullun idan kika yi sallar isha ki zo na fara koya maki soyayya sai karfe 10 zamu tashi ki je ki kwanta, amma fa kada ki ce da sadiya soyayya zan koya maki, kice kawai karatu zan fara koya maki, idan ta ce na me, ki ce mata na Alqur'ani mai girma, daga nan sai ki zo mu koyi soyayya ko?" To ta amsa mashi da shi, tana ƙoƙarin ɗaukar hijabinta, sunkuyawa da zata yi, wuyar abayar jikinta ya yi kasa, zubawa kyawawan breast naya ido ya yi yana kare masu kallo. Duk sun cukuikuye hijabin nata, kamar anyi yaki akan shi. Haka ta ɗauka ta miƙe ta zura a jininta, ji yake yi kamar ya jawota jikinsa ya yi wasa da breast ɗin nata kaɗan, amma kuma sai ya share kawai dan lokacin yana yi masu nisa basu yi Sallah ba. "Daddy na tafi" shine Abin da ta faɗa tana ƙoƙarin nufar waje. "Baby haka zaki tafi babu yiwa mijinki kiss na bye-bye?" Ju yo wa ta yi ta ce "To ai daddy ban iya ba" Alama ya yi mata da hannu akan ta zo. Matsowa gabansa ta yi, zata duƙa ya yi saurin nuna mata saman cinyarsa akan ta zauna. Ba musu ta zauna tana kallon kyakkyawar kwantacen gashin dake a gefe da gefen fuskarsa, ga kuma wani dake kewaye da ɗan bakin nan nasa, ya yi round. Matso da bakinsa ya yi saitin saman tata tare da ɗan kamo lips nata na kasa ya fara sha cikin salo. Kaɗan ya sha ya sake ta yana faɗin "Wannan shine kiss, kuma shi zaki rinƙa yi mani kullun idan kika zo, shine gaisuwata kin ji ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar ta ji. "To shikenan ta shi ki je ko?" Miƙewa ta yi da sauri ya nufi kofar kita. Har zata fita sai kuma ya kira sunanta a hankali, juyowa ta yi tana kallonsa. "Baby kada ki gayawa wani abin da muka yi fa, wannan sirrin mijin ki ne kin ji ko?" To ta amsa mashi da shi sannan ta fice, abin da ya sa ya yi mata wannan magana kuma, saboda yasan duk mutumin da zai zo ya gaya maka ga yadda suka yi da wani makusancinsa, to ba makawa haka kaima yake ɗaukar yadda kuka yi ya gayawa wani, to dik abin da Aunty ta gaya mata, haka take gaya mashi ba ɓoye ɓoye, ya san cewa tsab zata iya gayawa Aunty ga yadda suka yi, kuma ya san Aunty da shegen tambaya kamar me, shiyasa ya yi saurin dakatar da abin ma da wuri. Da kyar ya iya miƙewa ya shiga toilet dan yin wanka, yana wanka yana tunanin wai yau shine da mata, Allah mai yin yadda ya so da bawansa. A ɓangaren ita kuma Ayla, tana shiga palo ta sami Aunty da Hahan har ma da Abbi, suna zaune suna hira, haka kawai ta tsinci kanta da jin kunyarsu, kasa ta yi da kanta tare da tsugunnawa ta ce "Abbi ina wuni" Ɗan murmushin ya yi kafin ya ce "Sai yanzu kika ga Abbin ko?" Shiru ta yi tana tunanin lokacin da ya shigo ɗakin daddyn Jelly, daddy'n Jelly ɗin ne ya rufe mata baki da hannunsa, dan yasan zata yi mashi magana, shine yasa ya rufe mata baki, dan bai son ta yi magana a wannan lokaci. "Ayla tashi ki je ki yi alwala ki yi sallah, kyale Abbin kin nan hai" cewar Aunty. Ɗan ɗago kai ta yi karaf suka haɗa ido da Abbi, murmushi ya yi kafin ya ce "Amarya je ki ki yi alwala ki yi sallah lokaci na kurewa". Da sauri ta miƙe zuwa sama. Tana shiga ta zauna a bakin bed nata ta fara hawaye tana faɗin "Ina kewarki yar uwata, ina kewarki Rimsha, yau ga shi na yi aure amma bani da wanda zan gaya mawa, kafin su Abbi ke kaɗai nake da shi a duniyar nan, ina kika shiga, dan Allah ki zo ki taya ni murna kin ji ko?". Abin tausayi haka ta zauna ta rinƙa kuka har karfe 5, sai da ta tuna daddynta ya ce ta kawo mashi abinci, sannan ne ta miƙe da sauri ta faɗa toilet dan yin wanka. Su Aunty kuma suna palo suna hira suna dariya, while ita kuma Hajiya Hadiza tana can tana zuba barcinta dan ita bata takurawa kanta. A ɓangaren Lion kuwa. Zaune yake gefen Areef (James) yana ƙoƙarin haɗa wasu alluran da zai yi mashi, amma sai ya farfaɗo zai yi mashi, abin da kuma yasa yake haɗa alluran yanzu shine abinciken irin alluran da suka mashi da ya yi lokacin farkawarsa ta yi. Imran kuma yana ɗakinsa yana wanka. Bayan wasu mintoci da ba za su wuci 30 zuwa 40 ba. A hankali ya fara motsawa tare da fara yin sambatu kasa-kasa. "Is time for praying, i want to pray, Sallaht!! Sallaht!! Sallaht!!" Kalmar da James ya farka da ita keman abakinsa. Ko kallon in da yake Lion bai yi ba, shi kuma sai kara cigaba da sambatu akan Sallah yake yi. Sun kwashi good 10mins a haka kafin Lion ya miƙe tsaye tare da goya hannunsa a saman kirjinsa yana karewa jikin James ɗin kallo. Lokaci guda James ya kurma wani irin razanannen ihu mai tarwatsa kwakwalwa mai sauraro, ko motsawa Lion bai yi ba. Bayan ya yi ihun kuma, a zafafe ya yunkura zai miƙe, da alama bai dawo cikin hayyacinsa ba, bawan Allah yaci bakar wuya a hannun mutanen nan. Hannu Lion ya sa ya mai da shi ya kwantar, sake ƙoƙarin miƙewa ya yi, a karo na biyu ma mai da shi Lion ya yi ya kwantar, da ya ji ana mai da shi, sai ya saka karfi da gaske yana son miƙewa, kuma idanunsa a rufe, gently Lion ya ce "Areef you are saved now, you are together with your Triplets, open your eyes and see" ya kai karshen maganar tare da same hannunsa dake a saman kafaɗun James ɗin. Jin sexy voice na ɗan uwan nasa ya sa ya natsu ya kwanta shiru tare da waro idanunsa a hankali, kai tsaye sai saman kyakkyawar fuskar Lion ɗin, while shima Lion ɗin shi yake kallo. Wani irin nauyayyar ajiyar zuciya James ya sauƙe, can kasa-kasa ya furta "Please my blood I want to pray". Zuba mashi ido Lion ya yi na yan mintoci kafin ya kawar da kallonsa izuwa saman diamond watch dake a hannunsa, dan duba time, 8:30 pm, already anma yi sallar isha, ba tare da ya yi magana ba, ya wuce izuwa cikin toilet dake a cikin ɗakin, lumshe ido James ya yi yana sauke ajiyar zuciya, daga ta cikin zuciyarsa kuma yana yi wa Allah godiya da ya kuɓutar da shi, lokaci guda kuma wani tunani ya faɗo mashi a ransa wadda ta sanya idanuwansa suka cika da kwalla tab, har suna gangarowa, zafin da zuciyarsa ke yi mashi tana ratsa dukkanin ilahirin jikinsa, abubuwa da dama suna mashi yawo a ƙwaƙwalwarsa, nadama da dana sani da dama suna gudana a cikin kansa. A wannan hali Lion ya fito ya same shi, hannunsa ɗauke da ruwa a cikin roba mai ɗan faɗi, bai damu ba dan ganin James ɗin yana hawaye, dama ya san za'ayi hakan, kuma yasan me James ɗin yake yi wa hawayen. Saman bedside drawer ya ɗaura ruwan tare da fara yi mashi alwala yar shafa. Tsab ya yi mashi ya kammala sannan ya ce mashi, zai iya fare yin sallar sa daga kwance. Yunkurawa ya yi, ya miƙe zaune tare da jingina da jikin headboard na gadon, sai bin Lion da ido ya ke yi, shi kuma Lion ya ki yarda su haɗa ido, dan ba abin da zai hana shi hukunta James matukar ya mashi wasu tambayoyi wadda ya bashi amsar abin da yake zargi akansa, to sai ya yi mashi hukunci mai tsanani. BABBAR MAGANA MENENE WANNAN? AKWAI SAURAN RINA A KABA KEMAN. A haka James ya ɗan fuskanci gabas ya gabatar da sallar sa, bayan ya kammala ya koma ya ɗan kishin giɗa. Alluran da ya haɗa ya ɗauko tare da fara yi mashi a hannunsa, bayan ya ɗaure hannun ya nemi jiniya kenan. Bayan ya yi mashi alluran ya gama ne ya fara yan bincike a jikin James ɗin, dan ya gano me da me CIA suka sanya mashi a jikinsa, ko ya tambaye shi ma, ba zai sani ba, saboda kafin su sawa mutun abubuwan nasu, sai sun mashi alluran fita hayyaci, so James ba zai san me da me ne a jikinsa ba. "Da wani face ka shiga CIA?" Shine tambayar da Lion ya fara yi mashi. Ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Fake face". Wani nauyayyar ajiyar zuciya shima Lion ɗin ya sauke, kuma har cikin ransa ya ji matukar daɗin amsar, kenan CIA ba su san ainahin kamannin James ba? Zai iya fita cikinsu kuma ba za su iya gane shi ba, sai dai idan sun tsawaita bincike sosai, dan suma ba baya ba wajen aiki da ƙwaƙwalwa da zallar basira, amma dai dukka haka abin ya zo da sauki tun da basu san asalin face nasa, kuma idan suka sa kafar wando ɗaya da Lion a bincike da rufe sirrin gidansu ya ceto James, to fa sai ya kai su kasa, wanan shine wasan kwakwalwa za'ayi bana karfin dantse ba. AKWAI KALLO "Me yasa idan zaka kashe rai ka ke yin video da asalin face naka?". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Ina son ajiye tarihi ne, bana son ya zamana nayi amfani da fake face wajen ajiye tarihina, kuma kafin na kashe mutun sai na nuna mashi asalin face na, dan ya san waye ya kashe shi". Jinjina kai Lion ya yi tare da komawa gefen bed ɗin ya zauna yana faɗin "Ka huta zuwa da safe sai ka gaya mani me ya haɗa ka da G.M.A". Wani irin muguwar faɗuwar gaba James ya ji lokaci guda, abin ma ya bashi mamaki, ya akayi Lion ya iya bankaɗo duka wayan nan abubuwa haka. NI KUWA NA CE KA MANCE MATSAYINSA KENAN THE GENERAL OF THE ARMY. Yana tsaka da tunani bai ma san time da Lion ya fice daga cikin ɗakin ba. Yana shiga bedroom nasa ya isko Imran wadda ya shigo a lokacin dan duba shi. Toilet ya nufa yana faɗin "Prof ba ri na yi wanka sai ka raka ni, akwai wasu magunguna da neke buƙatar sayawa James, wadda bamu da su a nan" To Imran ya ce tare da komawa saman bedside drawer ya zauna yana sauke ajiyar zuciya, shi kuma Lion ya shige wanka. A ɓangaren Jehan kuwa Suna zaune shiru saman bed ɗin nan na Adiva, duk jininsu a sake, Adiva tana ji kamar ta je ta kwace Maryam a hannun Mutumin nan, amma ba hali, ita kuma Jehan ta yi shiru tana ambato sunan Allah a zuciyarta, kuma da alama ta fara nasara, dan kamar turaren Zinariya ya fara sakinta, yayin da shi kuma wancan ɗan iskan Alhajin ya shiga da Maryam cikin ɗaya daga cikin ɗakuna uku dake a cikin palon, kuma kusa da shi. Sai tunani Jehan take yadda zata ceci Maryam, domin zuciyarta ba zata iya jurewa, Maryam ta sha gwagwarmaya wajen kula da mutuncinta, ta wahala sosai yarinyar nan, kamata ya yi ta kai wa mijinta wannan mutuncin nata. Almost 5mins suna zaune a haka, can kuma kamar an sikari Jehan ta diro kasa daga saman gadon, sauri-sauri ta ce "Adiva where is your phone?" Da sauri Adiva ta miƙa mata wayar, karɓa ta yi ta nufi waje da sauri. "Jehan where are you going?" Cewar Adiva ɗin, ta yi maganar kusan a tare da A'isha, sai dai ita A'isha da hausa ta yi tambayar. "Adiva follow me, come and show me the room that you went to". Da sauri Adiva ta diro kasa ita ma, dan tun da ta ji Jehan ta ce hakan sai ta samu karfi, kuma ta san cewa Jehan ɗin ta tuna wata hanya ce da za su ceci Maryam. A'isha kam gyara kwanciyarta ta yi domin tana tsoron bala'in Hajiyar daɗi, kuma da alama ita turaren Zinariya bai sake ta ba. Suna shiga Palo Adiva ta ce da Jehan nan ne wajen da suka zo, sun kuma yi sa'a har suka zo ban ba wanda ya gansu a cikin gidan, kowa yana ɗakinsa, haka su Zinariya ma, suna office nasu. "Adiva there are many rooms in this palour which one have they enter?" Shiru Adiva ta ɗan yi kafin ta ce "I don't know, because mu a nan palon muka barsu". Jinjina kai Jehan ta yi tana faɗin "Okey go back to our room am coming". To Adiva ta amsa da shi, sannan ta nufi bakin kofar Palon. Har zata fita sai kuma ta juyo, murya a raunace ta ce "Jehan please kada ki yi wani abin da zai sanya a raba ni da ke, ke kaɗai ke gareni yanzu, sannan dan Allah kada ki yi abin da zai ja wo maki wata matsala, ki kula mana da kanki dan Allah ko dan saboda su Rimsha, suna buƙatar ki". Ba tare da ta yi magana ba kawai ta mata alama da hanu akan ta tafi dan ta jiyo shessheƙar kukar Maryam a cikin ɗakin dake bayanta. Ba musu Adiva ta wuce, tana addu'ar Allah ya sanya kada wani abin ya sami Jehan ɗin. A zafafe Jehan ta nufi ɗakin da take ji yo kukukan Maryam ɗin kasa-kasa, a bakin kofar ta tsaya ta kunna Cameran wayar Adiva dake a hannunta sannan ta saita video record, tana saitawa kai tsaye ta afka cikin ɗakin ba ko sallama, ta kuwa yi Sa'a kofar a buɗe ba su sanya key ba. Yau taga tashin hankali iya ganin idonta, amma da yake, dan ceto ta zo sai ta daure ta kawar da kanta, ta ruƙe wayar ta yadda ba zai gane Video take yi mashi ba. Lokacin da ta kutsa cikin ɗakin, a zafafe Alhajin nan ya ɗago sirara haihuwar uwarsa, ga shi ɗan baki da shi kamar zunubi, wannan shine tashin hankali da Jehan ta gani, babbar nasarar da ta yi kuma shine juyo da face nashi da ya yi dan ya kalli waye ya buɗe mashi kofar, ta yi nasarar ɗaukar fuskarsa karara a jikin wayar Adiva da ta kunnawa Camera, ga shi kuma yana tsirara, abin ya bata yadda take so. "Ke lafiya kika shigo mana ɗaki?" Ya yi Maganar har lokacin bai sauƙa daga kan Maryam ba, dama Jehan na gaf da shikowa shi kuma ya hau kanta yana kokarin shigarta. Cikin dakiya Jehan ta ce "Magana nake son yi da kai". Ɗaukar bargon da suke ɗaurawa a saman bed ɗin ya yi, ya ɗan rufe jikinsa ya miƙe cikin fushi ya fara masifa "Ke mahaukaciyar ina ce? Kin taɓa gani an shigowa mutun ɗaki haka?..." Katse shi ta yi da cewa "Ɗakin ka ko dai ɗakin gidar Hakiyar daɗi, ko ma dai ace hotel". Tsawa ya daka mata "Idan ma ɗakin waye ba dai kuɗi na biya dan na biya buƙata ta ba? Dan haka ki fita a ɗakin nan ko kuma na haɗa dake!!" Karo na farko a rayuwar ta da ta saki kayatatcen murmushi, sannan ta ɗago mashi da wayar daga irin riƙon da ta yi mashi na karya gane, tun da ta sami abin da take so, ya amsa da bakinsa cewa e ya zo gidan Hakiyar daɗi biyan buƙatarsa da ƴaƴan mutane, sai ta ɗaga mashi wayar dan ya gani, a sukawane ya fara ɓoye fuska tare da yin yunkurin kamata, a guje ta yi waje. Cikin matsanancin tashin hankali ya zura jomparsa ya bi yo bayanta, tana tsaye a palon tana jiran fitowarsa, dan suyi ta ta kare a nan. Yana fitowa ta kara waya a kunne cike da izza ta fara wayar karya "Hello Rimsha akwai Video da na tura maki yanzu, ki yi download na shi ki ɓoye a wajen sirri, idan kin ji wani abin ya same ni to ki saki video wa duniya, kuma kafin nan ki turawa gwaggo ma ta ajiye dan kada mu sami wata matsala, ni yanzu zan goge WhatsApp ɗin gaba ɗaya ki yi maza ki ɗauki video....." Bata kai karshen maganar ba ta watsa da gudu zuwa bayan kujera, ta yi hakan ne kuma sakamakon ganin da ta yi Alhajin ya nufota da nufin ya kwace wayar. Cire wayar ta yi daga kunnenta, tana yi mashi kallon wulakanci ka fin ta ce "Kai, na fika tantiranci wlh, ko ka tsaya mu yi maganar mutunci ko kuma wlh ka san saura ba sai na gaya naka ba". Ya shiga tashin hankali iya tashin hankali, ya yi danasanin zuwansa gidan Hajiyar daɗi yau, har wani jiri yake ji, ya ma rasa ya akayi bai kulle kofar ɗakin nasu ba. Ni kuwa nace ikon Allah ne yasa baka kulle ƙofar ba, mugu, Allah ya yi ba zaka lallata yar mutane ba, an gaya maka Ubangijin na barci ne? To idan ma kana tunanin haka sai ka farka yanzu, Allah ne ya ceci Maryam ta sanadiyar Jehan ba kowa ba, bakin azzalumi, ka killace ƴaƴan ka a gida ka lallaɓo nan dan lalata ƴaƴan wasu dan jaraba, da sannu Allah zai yi maganinku gaba ɗaya. Rai a matukar ɓace ya ce "To me kike so na baki ki goge video nan?" Shiru ta ɗan yi na yan mintoci ka fin ta ce "Na san halinku manyan nan, ina jin daddyna yana faɗa, zaku iya sawa a kashe mutun ko a ɓatar da shi ba? Shiyasa na turawa mutane na video, kuma yanzu a gabanka ma zan goge number kowa dake a wayar, zan yi formating na wayar baki ɗayar ta, amma dai ka sani idan wani abin ya same mu wlh zaka tsinci wannan video a media kamar yadda ka ji da kunnenka na gayawa yan uwana, haka zaka ganshi a Media ka rasa ta ina ya fito, kuma idan ma kayi maganar da wayan dake a gidan nan, ka ce ga abin da na yi maka, nan ma zaka ganka a media tsirara, to gara maka ma ka natsu, ni ba wani abin nake so ba fa ce ka rabu da Maryam ka wuce ka tafi salin alum, kuma kada ka sake dawowa gidan nan, kada na sake yin ido huɗu da kai, idan kuma ka bari muka sake yin ido huɗu, to ba sai na yi magana ba!!!". Zai yi magana sai ga Zinariya ta zo wucewa "Ke Jehan me kike yi a nan kuma?" Cewar Zinariyar kenan. Jehan na ƙoƙarin yin magana Alhajin ya ce "A'a Zinariya ni na saka aka kirata, magana muke yi" cikin sauri Zinariya ta ce "Haba Alhaji wannan fa ajiyar wani ce, wani ne ya yi bukkin nata, shiyasa Hajiya ta ce abarta sai ya dawo baya nan yana England, dan Allah ka yi hakuri ka bar ta, ba ga wata ka zaɓa ba, ko baka zaɓi ko ɗaya bane?" "A'a na zaɓa har ma na gama abin da zan yi, ita dai wannan magana kawai muke yi da ita, ba wani abin bane, yanzu kuma zan tafi ma, ke baki ga ma a palo muke yin maganar bane? So ba wani abu kada ki damu" jinjina kai ta yi tana faɗin "To dai ku yi sauri Jehan ta koma ɗaki, dan hanjiya ta ce ko waje kada ta fito, amma idan wani kyauta zaka bata ai kamata ya yi mu zaka kawowa ko? Ko ka mancen yadda tsarin gidan yake ne? Ai kai iyaka kawai ka zaɓi mace, mu gaya maka farashi ka biyamu ka shiga da ita ciki, ka mance ba'a bawa yaran kuɗi a hannunsu ne?" "Sorry Zinariya na mance ne, kin san yarinyar da na zaɓa ne ta bani labarin wannan ɗin ta ce ai tana da kirki, shine dama ne ce bari na yi mata kyauta akira mani ita, amma ba komai zan kawo maki kyautar office naki kafin na wuce" ta ji kuɗi sai bata tsawaita magana ba sai ta ce to, ta wuce bata kawo komai a ranta ba, dan alhazawan sun saba yin haka, idan sun zo suka ji yarinya ta yi masu daɗi suna yi masu kyauta sosai, kuma ba su kaɗai ba har da sauran yaran dake a ɗakin gaba ɗaya, amma kyautar office ɗin Haniyar daɗi ake kaiwa, idan bata nan kuma zinariya ta karɓa, basa yarda abawa yaran kuɗi, sannan kuma da kuɗin take yin amfani ta sayawa yaran kayan sawa da kuma kayan mata sosai da sosai, ta yi ta ɗirkawa yara abubuwa, idan ta ga yarinya bata cika yadda ake so ba, har alluran shakafashe tana sawa ayi masu, wasu kuma alluran breast or hips, idan alluran ya tashi sai ya yi masu illa a jiki, idan suka sami wata matsala a gefen titi hajiya take sawa a je a jefar da su, idan kuma yarinya aka samu akasi ta yi ciki, zubarwa ake yi, wata daga haka take mutuwa!!. Zinariya na barin wajen Maryam ta fito sanye da kayanta Baiwar Allah jikinta sai kerma yake yi, da sauri ta nufi wajen da Jehan ke tsaye. Rungumeta Jehan ta yi tana mai kara yi wa wannan Alhajin kashedi, sosai Alhajin ya sha jinin jikinsa domin kwata-kwata bai ga alamar tsoro a kan fuskar Jehan ba bare ya ce zai zare mata ido ko ya yi mata barazana, idonta a bushe yake tana tsaye cikin dakiya tamkar wata jarumar sojan yaki, amma a zahirin gaskiya a cikin zuciyarta sai tariyo abin da ta gani ƙwaƙwalwar ta ke yi mata, abin ya ɗaya mata hankali sosai, wannan wace iriyar jarabawa ce, Allah ka sa mu cinye wannan jarabawar, abin da take faɗe kenan a cikin zuciyar ta. Riƙo hannun Maryam ta yi suka bar palon suka nufi ɗakinsu suka barshi a nan tsaye yana tsaka da warwara a cikin zuciyarsa. Suna shiga cikin ɗakin da gudu Adiva ta taso ta kariso wajen su tana faɗin "Jehan ba abin da ya same ki ko?" Gyaɗa mata kai Jehan ta yi tana faɗin "Babu komai Adiva yanzu dai ki raka Maryam bayi ta yi wanka dan naga jikinta sai kerma yake yi, ba zata iya tafiya ita kaɗai ba, nima kai na nayi mani ciwo zan ɗan kwanta, idan ya sakeni sai mu yi magana kun ji?". DOLE KANKI YA YI CIWO IRIN WANNAN KASADA DA RAYUWA HAKA, BAKI SAN WAYE ALHAJIN BA? BAKI SAN ME ZAI IYA YI BA? FAROOQ MA IYA VOICE NASA KIKA YI MASHI KARYAR KIN ƊAUKA YA AIKO A KASHE KI, TO INA GA WANNAN DA YA KASANCE DA GASKE KIN ƊAUKI VIDEO NASA, KUMA TSIRARA, YA KUKE GANIN WANNAN WASA?, KUNA TUNANIN ANYA ZAI BARTA KUWA? KU DAI DUBA YANAYINSA KU GANI!!!!. Riƙo Maryam Adiva ta yi suka wuce toilet ita kuma A'isha ta miƙe zaune tana binsu da kallo tana mamakin me Jehan ta yi ta karɓo Maryam cikin ƙanƙanin lokaci haka, ko kallon in da take Jehan bata yi ba, ta haye gado abinta ta kwanta tare da ajiye wayar Adivan a gabanta tana sauke ajiyar zuciya, yau taga abin da ya fi karfin ganinta, ta ga abin da ya kwance mata lissafi kwakwalwata gaba ɗaya, har wani sarawa kanta ke yi mata idan ta tuna da wannan abin. Adiva ma bayan ta kai Maryam toilet sai ta dawo ta haye bed ɗin kusa da Jehan ɗin ta kwanta suna fuskantar juna, ita kuma A'isha ta kasa wani kataɓus ta zuba masu ido kawai dan har ga Allah ta yi matukar mamakin Jehan, kuma ita Hajiyar daɗi ta riga da ta saye ta. Maryam kuma bayan ta yi wanka ta ɗan samu kwari, sai ta fito ɗaure da towel da ake sanya masu a toilet ɗin, tana ƙoƙarin ɗaukar kananan kayan da aka basu Jehan ta katseta da cewa "Ki ɗauki abaya a cikin kayan Adiva". Ba musu ta ɗauki abayar ta sanya, kuma ya yi mata daidai da yake duk kusan shekarun nasu ɗaya, kawai dai ɗan tazarar watanni ne a tsakani. Kusa da su ta zo ta kwanta, suka yi shiru kowa da abin da yake ayyana wa a ziciyarsa, bayin Allah Allah ya kuɓutar da ku. Ni kuma na haɗa kayana sai mu haɗe da ku a gidan Abbi gobe idan mai dukka ya kai mu yau na sha typing, har zafi hannuna yake yi mani😭🥺 💖💖TRIPLETS💖💖 *Idan kun samu typing error amin afuwa 👏 keyboard ɗin tana bani matsala sosai kwana biyun nan, to na yau ma ya fi tsananta, sai na danna girki sai ya koma kirki 😭* BY FATEEMA MUSA (PRINCESS TEEMA) E 63 💖GIDAN ABBI💖 Ayla Bayan ta fito daga wanka, doguwar riga ta zura tare da hijabi, ta shinfiɗa dadduma ta tayar da Sallah. Bayan ta idar ta shafa mayukanta tare da perfume nata, ta ɗauko wasu riga da wando ta sanya, wandon jeans ne blue color, akwai stones a jikinsa sosai daga ta kasa zuwa sama wurin gwiwa amma, shi kuma rigar irin wayan nan t-shirt ɗin ne masu ɗan tsawo wadda ya tsaya mata iya cinyoyinta, kayan sun fito mata da shape nata sosai. Gaban mirror ta tsaya tana kallon kanta, ta yi kyau sosai, ga shi dama Aunty ta gyara mata gashin kanta jiya, ta wanke mata shi kafin suje asibiti wajen Aafia, sai sheki gashin nata yake yi. Hijabi ta ɗauka ta zura a jikinta har kasa, sannan ta nufi Palo. A wannan karon Hanan kawai ta samu a palon, "Aunty Hanan ina Abbi da Aunty ɗin kuma?" Ta tambaya tana nufar dining table ɗin dan ta ɗaukawa mijinta abinci. "Wata mata ta zo ta kira Abbi, wannan mata da a asibiti ta ce ni da yaran Abbi daban daban, to ita, ta zo ta kira shi, ita kuma Aunty ta haura sama tana kuka". Shiru Ayla ta ɗan tsaya a gaban table ɗin tana tunanin wannan bala'i na cikin gidan nan, haka jiya kafin su tafi asibiti sai da suka yi dirama, Aunty ta ce lallai Abbi a ɗakin ta yake dan haka a ɗakinta zai je ya shirya, ita kuma Hajiya Hadiza ta ce bata san da wannan zance ba, da kirsa da makirci ta ja Abbi zuwa ɗakin ta, a can ya yi wanka ya shirya, sosai Aunty ta sha kuka, a haka dai suka lallaɓa suka ta fi hospital ɗin. Ta ɗan jima a tsaye kafin ta shiryawa daddynta kuma mijinta abinci ta ɗauka a ƙaton tray ta nufi waje tana faɗin "Idan Aunty ta fito ki ce mata na kai wa daddy abinci" to kawai Hanan ta amsa mata da shi, da sauri ta wuce dan ta ɓata lokaci. Da sallama ta shigo cikin palon, kamar dai ɗazun baya nan, yana cikin ɗakin. Saman carpet ta ajiye abincin sannan ta nufi ɗakin nasa. Da sallama ɗauke a bakinta ta shiga cikin ɗakin, yana tsaye a gaban mirror yana gyara hular kansa, yau ba wankar kananan kaya ya yi ba, dakakkiyar shadda fara tas ya sanya tare da kyakkyawar hula baka, ya yi kyau sosai, sai kamshi yake zubawa. Ta cikin mirror ya hangota, zuba mata wayan nan idanun nasa ya yi yana kare mata kallo. Kusa da shi ta zo tana ƙoƙarin tsugunnawa ya yi saurin juyowa ya rungumeta yana faɗin "Wannan shine irin Welcome ɗin da zaki rinƙa yi wa mijinki, daga yau na soke tsugunnawa, idan ina zaune ne, kai tsaye ki haye saman cinyata ki zauna tare da yi mani kiss, idan ina tsaye kuma rungumeni zaki ki, idan ina kwance kuma a saman kirjina zaki zo ki kwanta, kina ji ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e. "Good amma kin san cewa gobe zaki tafi school ko? Tun tanar Monday ya kamata ki fara zuwa, amma saboda matsalolin da muka tsinci kan mu a ciki yasa ba mu sami damar zuwanki school ba, amma yanzu gobe dole na kai ki, dan lokaci na kara tafiya ne kin ji ko?" "E daddy na ji, kuma ina godiya" juyo da ita ya yi suna fuskantar mirror, wani irin faɗuwar gaba ya ji lokacin da ya ga fuskarta a cikin mirror, sai ya ga wani irin muguwar kamannin tsakanin ta da maman Jelly, sake waro ido ya yi yana kallonta da kyau, ya jima yana yi mata kallon fuskar kamar wadda ya sani, amma ya kasa tantance fuskar waye ne sai yau, tabbas mugun kama ta yi mashi da mummyn Jelly, ga shi har kamannin Jellyn ma ya bayyana a face nata. Wa kuke tunanin Ayla zata kasance? Shin kenan maman Jelly ita ce mamanta? Ko kuma dai yaya? Domin dai maman jelly bata da kanwa, kuma bata yaya, ita kaɗai ce wajen iyayenta? Wannan shine cakwakiya!. Juyo da ita ya yi suna fuskantar juna, tsab ya kare mata kallo, tabbas ba karya idanunsa ke yi mashi ba, kamannin maman Jelly ce a face nata, abin ya ɗan ɗaure mashi kai. "Baby asalin da waye kike kama mama ko baba? Sannan kuma asalin ku yan wace jaha ce?". Ya yi maganar a ɗan ruɗe. "Daddy ni ban san daddy na ba, amma dai bana kama da mamana sosai, kuma ni dai bayan nan Kaduna, ban san wani gari kuma ba, sai da muka je Daular Mutuwa daga nan muka je Ilorin". Wayarsa ya ciro ya fara fito da hutunan daya ajiye a Email nasa, yan uwan maman Jelly ne da dama, sai kuma maman Jelly ɗin da kuma na jelly, duk hoton yan uwan maman Jelly da zai ga ni sai ya ga suna kama da Ayla, abin ya ɗaure mashi kai sosai, yau dai ga kamannin sun bayyana ƙarara, tunani ya fara yi to ko dai Umaima tana yare ne? Babbar magana. Nuna mata hotunan ya fara yi yana tambayarta ko ta taɓa ganin mutun ɗaya daga cikinsu, ita ma tasha mamakin ganin duk suna kama da ita, musamman ma mummyn Jelly, kamanninsu ya yi yawa, sai ma taga kamar mamanta lokacin da take budurwa. Duk ta ce mashi bata sansu ba, bata taɓa ganin ƙo ɗaya daga cikinsu ba, jiki ba kwari ya karɓi wayar tasa ya maida aljihunsa tare da riƙo hannunta ya ce "Muje ki bawa mijinki abinci a baki ko? Yau amarya ta ce zata bani abinci a baki, su Imran ma sun ce za su zo suyi mani murna dan Abbi ya gaya masu, sun ce za su zo, amma nace su bari sai gobe domin yau ranar ki ce, shiyasa na yi maki shigar manyar kaya, na fito a angona, kuma daga nan har dare muna tare". Ya kai karshen maganar daidai lokacin da yake ƙoƙarin zama a saman lallausan carpet ɗin. Gefensa ta zauna tare da zuba mashi abin cin, jikinsa duk a mace saboda tabbas Ayla tana kama da mummyn Jelly har ma da Jelly sosai, kada ya zo ya yi abin da ba shi ba, dan tunanin da ya fi yawa acikin kwakwalwarsa shine ko dai mummy'n Jelly na raye yarta ce Ayla, ko dai da cikinsa ta tafi ne, daga baya ta haifi Ayla, dan ya san mummyn Jelly bata da kanwa ko yaya, abin ya bashi mamaki sosai, kuma ya kashe mashi jiki, ya kuma kudiri niyar fara neman mahaifiyarta tun da shi baban nata bata san shi ba. A baki ya rinƙa bata abinci tana ci har sai da ta ƙoshi, sannan shima ya ci nasa, bayan sun kammala sun tattare komai ne ya kama tannunta suka wuce cikin bedroom nasa, domin kada Irfan ya dawo da abokansa ya same su. Soyayya mai tsabta suka shigayi babu kama hannun yaro, sai dai bai wuce gona da iri ba, ko breast nata bai yarda ya taɓa ba, dan jikinsa amace yake da ita, yana tsoron ya kasance wadda ta zama mashi haramun ya aure ne ya aure, domin wannan kamanni dake akan face nasu ba'a banza ba, dole akwai wata alaka mai karfi, kamar ta yi yawa, wannan dalili yasa ya ce dole ya nemo mamanta dan su ji waye babanta shin shine ko kuma waye? Dama yana mamakin irin bala'in kaunar ta da yake yi, abin yana ɗaure mashi kai. A ɓangaren Irfan kuwa lokacin da ya sami saƙon cewa daddyn Jelly ya auri Ayla, har kwallah sai da ya yi, domin yana bala'in sonta fiye da tunanin mai tunani, kullun da sonta yake kwana yake tashi, bai gaya mata bane saboda yana yi mata kallon yarinya, ya hakura sai ta kara girma ne, wunin ranar dai kaf bai fita waje ba, yana ɗaki yana kwance kamar mara lafiya. Su Akil kuwa murna awajensu ba'a magana, Imran ya ce ya ɗauki nauyin kayan lefe, amma ina daddyn Jelly ya ce wannan huruminsa ne, Akil ya ce to shi zai sayawa amarya komai da komai na kayan ɗaki da Kitchen, nan ma daddyn Jelly yaki yarda, ya ce zai yi wa matarsa komai da komai, haka suka hakura ba dan sun so ba suka kyalesa, amma kowannensu ya dunkule kuɗi makudai ya zuba mashi a account nasa, sosai ya yi masu godiya, tare da fatan alkhari. A ɓangaren Rimsha kuwa After one day. Misalin karfe 8 na dare, tana zaune a palon Imran tana dube dube a takardunta kamar dai kullum, ita kuma Akila tana ta faman latsa waya tana daga kwance sama sofa, ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya. Suna hira jefi jefi, da yake kowa da akwai abin da yake yi. "Rimsha menene mafarkin ki? Me kike son ki gani an miki yanzu a rayuwar ki na jin daɗi da morewa?" Cewar Akila, ta yi maganar tana dawo da kallonta izuwa kan Rimshan. Yar murmushi ta yi har sai da dimple nata suka lotsa sosai kafin ta fara magana. "Aunty Akila ina son in ganni a cikin daji daji haka, a irin wannan bakin teku na turawa, ina zaune ina kallon ruwa da tsuntsaye, sannan ina shakar iska mai daɗi, daga jefe kuma ga irin wannan bukka da turawa da suke yi a bakin ruwan nan, wanda zaki ganshi kamar da tampol ne ko me suka yi shi, to shi dai, haka nake...." . Bata kai karshen ba Akila ta katse ta da cewa "Eyeee ah..ah..ah ga yar soyayya mai lasisi, wato dai haka ki ke so ko?, to daga nan kuma sai ga GAR da gajeren wando ko?, ke kuma da singlet nasa, rabin Tula-tulan dukka a waje, dan abin ya fi bata armashi, to daga nan sai ya zo ya yi sama dake zuwa cikin wannan ɗakin bukkar, ya baki jikin ki sai kin ce kin tsanesa kin tsani soyayya, ke Rimsha ina rabaki da zancen soyayyar nan kwata-kwata ke bakya ji ko? Wato har da kina shakar iskan wajen ko? To ki jira zaki shaka da tushe, wlh ina ga in wannan GAR ɗin ya rike ki, sai kin gane annabi ya faku, kinga wannan ɗan bakin naki, wlh ba zai iya fitar maki da ihu ba ranar, kina ganinsa namijin duniya, wlh ki fita sabgar irin mazan nan, dan hannu ɗaya zai sa ya ɗaga gi sama ya jefa saman gado kamar kayan wanki, ga ki yar firitu dake sai shegen son shaukin soyayya, to wlh zaki ga shauki ganin idon ki, wato ma ke har da ganin tsuntsaye ko? To wlh na gaya maki zaki yi bayani, ke nifa tun da na kalli yadda Bgs ya kare da Hiyana a Duk Karfin Izzata na fita sabgar maza masu training ɗin nan, haka zalika ba cire sojoji a lamurana, barni na sami ɗan baby wanda ya iya zuba Love ya iya rarrashi wadda ina kuka shima yana yi, mu rarrashi juna, ni yar Abba da Ammie rabani da irin TRIPLETS dukkansu babu na wasa a cikinsu, wlh kina ganin kirar jikinsu baki ga alamar wasa ba, ke yo......" Bata kai karshen maganar ba Ammie ta shigo palon ba ko sallama, ta shigo duba Akila ɗin, domin ta je ɗakinta bata nan, kuma ta san cewa Imran baya nan Akil baya nan, ina Akila zata je da daddaren nan, ita da ko da rana ma bata fita, bare kuma yanzu dare, shine da bata ganta ba, ta duba Part ɗin Akil bata a ciki, shine ta zo nan. Jin shigowar mutun yasa gaba ɗayarsu suka ɗago kai, a razane Ammie ta dakawa Rimsha wani irin mahaukacin tsawa "Me ya zaunar dake a cikin gidan nan? Ba nace ki fita ba?!!." Akila jiki na kirma ta miƙe daga kishingiɗar da ta yi, ita ma Rimsha miƙewa tayi daga zaman da take, dukkansu sun tsorata, sai kerma jininsu ke yi. "Ke zoki fita a cikin gidan nan ko kuma yanzun nan na kashe ki!!!". A razane Akila ta ɗaura hannu a saman bakinta tana hawaye, tsawa ita ma Ammie ta daka mata akan ta rufe mata baki. Zube gwiwowinta kasa ta yi tana kuka ta fara magana "Ammie ki yi hakuri, wlh Rimsha bata da kowa, idan ta fita gidan nan cikin daren nan ina zata je? Dan girman Allah Ammie ki yi hakuri kin ji?. A zafafe Ammie ta karaso cikin ɗaki sai huci take yi, hankalin ta ya yi matukar tashi, karo na farko da ta fara wanke wa Akila fuskarta da mari tare da daka mata wani mahaukacin tsawa wadda ya sanyata miƙewa a guje ta nufi waje. Ita ma Rimsha tana hawaye ta ɗauki wayarta ta nufi waje da gudu. Akila ta nufi chikin gida while ita kuma Rimsha ta nufi waje, ga shi bata ɗauki ko hijabi ba haka ta fita da gudu tana yi tana kuka hawaye bibbiyu. A ɓangaren Jelly kuwa, yau saura kwana shidda biki, abubuwa duk sun kankama, kuma yau Hajiya batula ta zo, ta rage kwana ɗaya a cikin wayan da ta ɗiba. Sosai ta fara gyaran Amarya, amma ta yi mamakin ganin Jelly sosai, ta ce tana mata kama da Hassan da Hossain, wato yayyunta, sai kallonta take yi, tana ji tamkar jininta ne, dan kamannin ya yi yawa, ba iya su kaɗai take kama da su ba, har da Abla yar Hajiya Batula ɗin, sun yi kama sosai, jini ba wasa ba, ga idonta irin na daddynta sak. Har hotonta Hajiya Batula ta ɗauka akan idan aka gama biki ta koma zata nunawa Abla da kuma Akila da Imran, dan Akila da Imran sune kaɗai masu zuwa wajen ta, ko Akil baya zuwa, sai ma da ta yi tunanin Imran sai ta kara ganin kamannin fuskarsa akan fuskar jelly ɗin, da yake jini ba wasa ba, kunsan ko wani lokaci da irin siffar da ɗan adam ke kallon ɗan uwansa ɗan adam, kowa da irin kallon da yake mata, wani anasa ganin ka yi mashi kama da wani, wani kuma sai kaga bai ga wannan kamanni ba wani yake gani a tattare da kai, to ita dai Hajiya Batula ganin jininsu kawai take yi wa Jelly, da yake bata san da ɓatar Jellyn ba, hasalima bata san Jelly ɗin ba, ta dai san Maik ya yi aure, amma bata san ya mace ya samu ko namiji ba, tun da Imran ya ke zuwa wajen ta, bai taɓa gaya mata ga irin abin da daddy'n jelly ya haifa ba, bai taɓa bata labarin ahli ba, sai dai hirar yaushe rabo, shiyasa bata san da labarin Jelly, Aafia, Umaisha, har Akil, duk bata san mata suke ko maza ba. Sai gyaran Amarya ake yi babu kama hannun yaro, ita kuwa jelly ko a jikin ta, bama su isheta kallo ba, wata shain ma, ana mata gyaran tana cin wani abin, ko kaza ko wani abin. Shi kuma ango Nawid yau yake son zuwa wajen Rimsha, sai zumuɗi yake yi, ya ji daɗi rana ta farko ta kula shi har ta zauna suka yi hira sama sama, hakan yasa ya ce yau zai koma su sake zantawa ko Allah zai sa ya yi nasara. A ɓangaren shima A'A SALAHUDDEEN yana can yana shirye shiryen sa, gobe Jumma'a zai diro cikin Kaduna dan ya ga Rimshan sa Yayin da ita kuma Rimshan tana fita ta kama hanyar titi, tana tafiya tana kuka, bata san ina ta nufa ba, kawai tafiya take yi har ta yi ɗan nisa, Horn ɗin motar da ta ji abayanta ne yasa ta juya da sauri, bata iya ganin su waye ne dan sun haske mata wutar motar. Cigaba da tafiya kawai ta yi tunda bata gane su waye bane, da sauri Imran ya buɗe kofar motar ya fito yana faɗin "Thank you Saif". Gabanta ya sha da sauri yana faɗin "Sorry our First Lady" kuka mai sauti ta kara saki tare da faɗa wa jikinsa tana faɗin "Ya Allah ka ɗauki raina na huta". Buge mata baki Imran ɗin ya yi tare da faɗin "Muje kada mu ɓatawa Saif lokacin, yanzu ma ba dan ya ga hawayena ya zuba ba, da ba zai yarda mu zo mu ɗauke ki ba, da kyar ya yarda, dan ma dai Akila ta kirani agabansa ne, kuma ya ji duk abin da ya faru, Allah ya rufa asiri kuma muna kusa, mun je sayawa James wasu magunguna, ba dan haka ba ai da kin ɓace Mani, yanzu dai muje, idan muka isa gida za mu yi magana, kada mu ja ya ce ba zaki zauna mashi a gida ba, da kyar da ma ya yarda, sai da na sha kuka ina gaya mashi baki da kowa, ke marainiya ce, idan na barki zaki iya faɗa wa mugun hannu har a lallata maki rayuwa, shi kuma baya son zina shiyasa ma ya yarda". Ya kai karshen maganar tare da riƙo hannunta suka nufi motar. Tun basu kariso wajen motar ba Kamshin perfume nasa ya daki hancinta, har wani lumshe sleeping eyes nata ta yi tare da sake buɗe su a hankali. Abin mamaki a maimakon Imran ya shigar da ita gidan baya dan tana tunanin Lion ɗin a gaba yake, sai ta ga ya buɗe mata gidan gaba, Lion yana baya, a cikin zuciyarta ta ce ashe ko a ina yake wannan sarauta dai tana nan, yanzu duk yadda suke da Imran ba zai iya zama a front seat kamar friend ba, sai dai ya zauna a baya Imran ya zama driver sa, tab lallai wannan akwai izza da isa wai, tunani cike fal ranta ta shiga gidan gaban Imran ya rufe kofar, ya zagayo ya shiga mazaunin driver ya tada motar. Muryarta na kerma ta ce mashi "ina wuni GAR" dan sunan da ta san shi da shi kenan Bayan Kamshin perfume nasa da zaka ji wadda zai tabbatar maka da ya cikin motar, to ba wani abin da zaka ji na daga motsi, kamar bai san da shigowarta ba bare kuma har ta sa ran zai amsa mata, shi da bai ma jin Hausa, yana zaune ya kwantar da kansa saman kujerar motar tare da lumshe idanuwansa kamar mai tunani. Black face mask ne a face nasa tare da puffer jacket ajikinsa, daga ta ciki kuma wata kyakkyawar tsadaddiyar Round neck t-shirt ne launin Ash color, wandon jeans para tas ce daga ta kasa. Kasa kasa Imran ya ce mata ko da sunan wasa kada ta sake yin gigin yunkurin yi mashi magana, idan ba haka ba, zai iya sumar da ita ko kuma ya ce baya son ganinta dole ta bar gidan, to ta amsa da shi tana sauke ajiyar zuciya, da yake darene bata sami damar ganin koda kayan dake jikinsa ba bare fuskarsa. Ahaka suka nufi wani ƙaton pharmacy dake ɗan gaba da gidansu Imran ɗin, pharmacy ne mai girma sosai. 💖💖TRIPLETS💖💖 E 64 Kasa kasa Imran ya ce mata ko da sunan wasa kada ta sake yin gigin yunkurin yi mashi magana, idan ba haka ba, zai iya sumar da ita ko kuma ya ce baya son ganinta dole ta bar gidan, to ta amsa da shi tana sauke ajiyar zuciya, da yake darene bata sami damar ganin koda kayan dake jikinsa ba bare fuskarsa. Ahaka suka nufi wani ƙaton pharmacy dake ɗan gaba da gidansu Imran ɗin, pharmacy ne mai girma sosai. A parking space nasu Imran ya yi parking, tun bai gama kashe motar ba Lion ya fice abinsa, domin sauri yake yi, zuba mashi ido Rimsha ta yi tana kallon yadda yake tafiya, da yake akwai haske sosai a wajen, daga ta cikin zuciyarta kuma, mamaki take tana faɗin, "Ashe dai haka tafiyarsa yake cike da izza da isa, wadda duk wanda ya ganshi dole ya matsa ya bashi hanya, dan bai ga irin takun yara ba, ashe dai ba a iya Tv yake irin wannan tafiya ba, haka tafiyar take". Taɓa ta Imran ya yi yana faɗin "Rimsha ki natsu, duk yadda kike tunanin Saif ya wuci nan, dan haka ki kama kanki, ko da sunan wasa na gaya maki kada ki kuskura kiyi gigin yi mashi magana, kada ki bari hanya ta rinƙa haɗa ku, dan wlh tsab zai iya take ki, ya yi ball dake na dai gaya maki, yanzu dai bari na je na biya kuɗin maganin dan shi bashi da kuɗin Nigeria, shiyasa ya zuba mani kuɗi sosai a account na tun kafin ya zo, dan ba ya son wani abin haushi na canza kuɗi ko makamancin hakan, ki jiramu muna dawowa yanzu". To ta bishi da shi, cikin sauri ya fita daga cikin motar. Yana fita wayar Lion dake a saman kujerar baya, in da ya zauna kenan, a nan ya barta, fara ringing wayar ta yi, juyowa Rimsha ta yi yana kallon wayar dan ya kawo hasken screen ɗin yana ta faman kirar number mai kira, haka kawai ta tsinci kanta da sanya hannu zata ɗauki wayar dan ta gani, ita da aka ce mata ko hanya kada ta bari ya haɗa su, amma tana neman kirawa kanta ruwa, domin kuwa koya ta taɓa wayar idan ya zo zai san ta taɓa shi. (Ina iyeyen Rimsha? sai ku ja mata kunne, idan ba haka ba, da alama za'a mata bugu ɗaya ba tashi) Bata kai ga ɗauka ba kiran ya katse, nan take hotonsu su uku ya bayyana a saman kyakkyawar fuskar wayar, dukkansu fuskar nan a ɗaure tamau, saboda tsabar rashin ji irin nata har da sako kanta dan ta kare masu kallo, kamar bata da hoton su su ukun a wayarta, da yake dai wannan na kan screen ɗin nasa, fuskokinsu ya fito sosai a cikin hoton, kansu a haɗe, hakan yasa yafi kyau, shiyasa ma ya sanya a gaban screen na wayarsa. Hannu ta kai bari ta ɗauki wayar ta kare masu kallo, sai ji tayi aka ƙoƙarin buɗe kofar motar, har ga Allah bata ga alamar dawowarsa ba, a sukawane ta mayar da kanta tare da runtse ido tana karanto duk addu'ar da ta zo bakinta, dan neman tsari daga wajen Ubangiji, Allah yasa kada ya yi tunanin wani abin ya ce zai mata hukunci, da ta shiga uku da lalace kuwa, bugu ɗaya ba zata sake moruwa ba. Zama ya shigo ya yi a in da ya tashi, dama abin da ya sanya ma ya fita, saboda Imran ba zai gane irin magungunan da yake so ba, kuma idan Imran ne ya je, zai ɓata mashi lokacin sosai, shiyasa kawai ya tafi da kansa, dan ko wace minti ɗaya a cikin rayuwarsa yana lissafa me zai yi da ita, baya asarar lokacinsa abanza, baya wasa da time, shiayasa idan ka ɓata mashi lokaci koda minti ɗaya ne sai ya maka hukunci ba kaɗan ba. Kamar yadda ya zauna ɗazun haka yanzu ma ya zauna, tare da lumshe idanuwansa, ita kuwa sai shakar kamshin perfume nasa take yi tana lumshe idanu, tana kara jin wani balaƴaƴƴen azababben kaunarsa na kara ratsa dukkannin ilahirin jikinta. TO FA KINA DA AIKI GASKIYA A haka Imran ya dawo ya same su hannunsa na ruƙe da wata babbar leda fara tas mai tambarin pharmacy ɗin a jiki, da alama magungunan ne a cikinsa. A gefensa ya ajiye maganin tare da kunna motar suka bar wajen, suka nufi gida. Suna isa gida, Imran ya yi parking a parking space na gidan, da gudu sojan dake bakin gate ɗin ya kariso wajen tare da buɗe masu kofofin motar gefen Imran da gefen Lion, ganin Rimsha yasa ita ma ya buɗe mata kofar, amma ya sha ruwan mamakin ganinta tare da su, abin da bai taɓa gani ba, Lion a kusa da mace, to wacece wannan? Ya tambayi kansa, har suka shige cikin gida ba tare da ya sani ba, ya yi mutuwar tsaye a wajen. A palon kasa Rimsha ta tsaya, Imran ya nuna mata saman sofa ya ce ta zauna, shi kuma ya bi bayan Lion zuwa ɗaki James dan ya kai mashi maganinsa. Bayan ya kai mashi ya dawo palo ya ce su je sama, ba musu ta bi bayansa, ɗaya daga cikin ɗaku nan dake a saman Imran ya wuce da ita, dan ba zai iya barinta a kasa ba, duk da akwai mai gadi, hankalinsa ba zai kwanta ba, gara ta kasance a sama kusa da shi. Suna shiga ɗakin ta zaro ido tana bin ɗakin da kallo, komai na cikin ɗakin kusan irin na bedroom ɗin daddy'n ta a Abuja ne, ta sha mamaki sosai. Saman bed Imran ya ce ta zauna, bayan ta zauna sai ya zauna a gefenta, a nutse ya fara magana. "Kamar yadda na gaya maki ɗazun, ki natsu wlh ina kara jaddada maki Saif zai iya yin ball da ke idan kika bi ta hanyar wucewarsa, ki kula sosai, ba sai kin gaida shi ba idan kun haɗu, baya son hakan, sannan kuma nasan da son da kike yi mashi, amma ki daure ki danne kada ki rinƙa yawan kallonsa, idan kika bari ya gane kina kallonsa wlh nan ma mun shiga uku, tun muna school nasan baya son kallo, ga shi da shegen bala'in kyau na fitar hankali, amma ya haramtawa kowa kallon face nasa, to kema ki kula da wannan, zaki iya shiga ko'ina a cikin gidan nan, amma banda ɗakin dake na farkon nan, shine nasa, kada ki yi gigin shiga tom, idan kina son leƙawa ki bari sai in ya fita, dan time to time yana fita, to ki bari sai baya nan, na san ba zaki iya cin irin abincinsu da suke girkawa a nan ba, saboda ba na kasar mu bane, dan haka kina da damar shiga Kitchen ki girka abinda kike so babu mai hana ki, amma dai ki kula, domin gases nasu na girki da sauran kayan aikinsu ba irin na Nigeria bane, na kasar su ne, a kasar tasu ma na musamman ne, to ki kula kada ki yi ɓaran ɓarama, na yi wa Akila massage akan ta haɗa maki kayanki dukka a cikin trolley ki, Akil zai je da sassafe ya ɗauko maki dan zaki tafi school gobe, yana da kyau ki kwanta ki yi barci, da safe zamu sake tattauna duk abubuwan da suka dace, ko kuma idan kin dawo daga school, yanzu dai ki kwanta bari naje wajen shi na duba Triplets nasa, Areef bashi da lafiya, idan Allah ya kai mu da safe kema sai ki je ki duba shi". To ta amsa mashi da shi tare da yi mashi alkawarin zata kula anya kuwa zaki kula? Keda wayarsa ma aka kira duk wannan bala'in tsoron sa dakike amma saboda gulma da fitina wai zaki duba ki gani ba? Baki san ko tsinke ya ajiye wani ya taɓa sai ya gane ba?🤔 Gara to ki shiga hankalin ki natsu. Miƙa wa Imran ya yi yana sanya mata albarka ya fice daga ɗakin zuwa wajen su James. Yana ƙoƙarin shiga ɗakin James ɗin ne wayarsa ta fara kara, dubawa da zai yi sai ya ga Dr Nawid ne, fasa shigar ɗakin ya yi ya koma saman sofa ya zauna tare da yin picking na call ɗin. Daga ɗayan ɓangaren Nawid ya ce "Hello Prof ykk" nisawa ya yi kafin ya ce "Dr ina lafiya ya su Ummi?" "Su Ummi suna lafiya, please Prof gani a cikin gida, ka ɗan yi mani iso wajen Rimsha tun da kai baka ban". Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe wannan shine chakwakiya, ɗan satar kallon kofar ɗakin James ya yi kafin ya fara magana "Sorry Dr Rimsha bata nan". Ɗan zaro ido Nawid ya yi yana faɗin "Bata nan kuma? To ina ta je?" Shiru Imran ya ɗan yi, dan har ga Allah baya son abotar su ta sami matsala, kuma ba zai iya yi wa Rimsha dole ba, abin da yasa ya bawa Nawid ɗin ma izinin zuwa wajenta, dan bai san akwai wadda take so bane alokacin, yanzu kuma da ya sani ba zai yi gigin yin hakan ba, sannan kuma A'A SALAHUDDEEN ya kira shi jiya ya sanar da shi, Rimsha ita ce yarinyar da yake so, kuma ranar Friday gobe kenan yana nan zuwa, dukkansu abokai ne tun na yarinta, ba zai so wani abin ya sami abotarsu ba. "Prof da wata matsala ne? Ko dai iyayen Rimsha sun bayyana ne?". Cewar Nawid. Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali, kan sa ta kulle, har wani jiri yake ji. "Dr iyayen Rimsha ba su bayyana ba, kuma tana nan, amma yanzu ta dawo gidan GAR ne da zama, saboda wata yar matsala, sai dai ka zo gidan ka ku gaisa, kuma ni zan so ka bari sai da safe ne kazo domin yanzu ta yi barci......." Bai bari Imran ya kai karshen maganar ba ta dakatar da shi da cewa "Gidan GAR fa kace?! Tab ina a'a wlh, angaya maka na shirya mutuwa yanzu ne? Ai ko masu gadin gidansa banson yin ido huɗu da su, bare kuma har na shiga har cikin gidan na zauna hira da Rimsha, dama dai a waje ne za mu haɗu, in ganshi da face mask da glass kamar yadda ya saba, to zan iya rokarka ka nema mani alfarma mu yi hoto da shi, amma gidan sa fa, kai a'a to me ma ya kai Rimsha gidan?". Jin haka yasa Imran ya ji a ransa ya sami hanyar da zai rabu da abokansa lafiya kuma ya raba su da Rimsha lafiya, dan haka sai ya ce da Nawid "Dr GAR shi ya ce akawo mashi ita, na bashi labarinta ne, sai ya ce akawota, to da ta zo gaban shi kuma sai ya ce daga yau a gidan zata zauna". Da yake ba wanda ya san da labarin Triplets sun tsani mace saboda mum ɗin su, basu fitar da sirrin gidansu waje, ba wanda ya san cewa ba su son mum ɗin tasu, sai Nawid ya yarda akan cewa Lion ne ya ce akawota, A razane ya ce "Prof sai da safe, ko Rimsha ita ce autar mata ta duniya gaba ɗaya, to na hakura da ita, GAR fa tab ina wlh na hakura da Rimsha, ta yi zamanta a can bari na koma na karɓi zaɓin da Ummi tayi mani, dama yau saura kwana biyar a ɗaura aure, sannan kuma dan Allah Prof ka yi ƙoƙari ko ɗaurin aure ne ka zo ka ji?" Jinjina kai Imran ya yi yana faɗin "In Sha Allah zan zo ɗaurin aure kam, tun da ba zai wuci minti 20 ba". To Nawid ya ce sannan suka yi sallama, Miƙewa Imran ya yi yana mai jin daɗi ya rabu da Nawid lafiya, sai dai kuma ya zuba karya da sunan Lion , idan ya gane kuma fa? Kun dai san halinsa, ta yi wu ma ya sanya camera a cikin Palon, idan ya zo yana dube dube zai iya gani, dan baka gane gabansa bare bayansa. Da sallama ɗauke a bakinsa na shiga ɗakin, daidai lokacin Areef ya gama shan magungunan sa, ba laifi jiki yana ta yin kyau yana samun sauki, duk kumburin face ɗin nan nasa ya sauƙa, amma daga ta cikin jikinsa yana jin ciwo sosai, dan ba ƙaramin wahala suka bashi ba. Hannu ya miƙawa Imran dan su yi musabaha, da murmushi Imran ya miƙa mashi hannu yana faɗin "My Areef bawan Allah sannu da jiki". Fuska a ɗaure tamau kamar fuakar Saif Areef ya amsa da "Prof i really Missed you wlh". Imran bai damu dan ya ga face nasa a ɗaure ba, dama ya san James ba shi da wani sakin fuska shi ma, idan kaga yana murmushi to ya yi wani babban aikin alkhari ne, amma shi ma baya da sakin fuska ko kaɗan, a baya ma da yake yi, dan saboda basajar da yake yi ne, dan dole yake murnushin. Yar hirar an jima ba'a haɗu ba Areef da Imran suka yi, shi kuma Lion ɗakinsa ya koma ya yi wanka ya yi shirin barci ya kwanta abinsa. Sun ɗan jima suna hira kafin su yi sallama Imran ya wuce nasa ɗakin ya yi wanka tare da shirin barci shima ya kwanta. Shima Areef gyara kwanciyarsa ya yi dan ba halin yin wanka saboda raunikan dake a jikinsa, ba zai yi wu a zuba masu ruwaba, sai dai zuwa gobe ko jibi haka, amma yana shan wahala ba kaɗan ba, ga azaban ciwo ka kuma rashin wanka, abin ya haɗe mashi, daɗin abin dai ɗaya Lion na kula da shi sosai da sosai, kuma ya ce gobe zai iya kai shi toilet ya yi wanka. A ɓangaren Rimsha kuwa, Imran na fita, toilet ta shiga ta yi wanka, ta fito, haka ta maida kayan da ta tuɓe ta kwanta, yau wani mugun farinciki take ji na taga masoyinta, sai wani murmushi take yi tana shafa Tula-tulan ta saboda sunansa dake a wajen, cike da nishaɗi da murmushi akan face nata barcin mai daɗi da annashuwa ya ɗebeta. To asuba ta gari My people, bari mu leƙa masoyan nan, wato babyn daddy da kuma daddynta. 💖💖GIDAN ABBI💖💖 Yau a tare suka yi sallar mangariba da isha, bayan sun idar ne suka zauna suka yi askar tare da kara koya mata karatun Alqur'ani mai girma daga in da ta tsaya, tun da ta kawo abinci bata koma ba, Aunty kuma bata ce a kirata ba, dan ta san halin daddy tsab zai ce ina ruwanta da matarsa ba zata dawo ɗin ba, ta dawo wurin mijinta kenan, hakan yasa ta zuba masu ido kawai tana jiran dawo wanta. Bayan sun gama karatu ne ya ce "Baby mu je shopping yanzu ko sai anjima?" Kasa ta yi da kanta tana wasa da yatsun hannunta irin yadda Rimsha keyi, mafi yawancin abin da Ayla ke yi duk a wajen Rimsha ta koya, dan Rimsha ita ce malamarta ta farko, sai dai kullun Rimsha na gaya mata, ta koyi rufe sirrinta amma bata kulawa sosai. Hannayen nata ya riƙo cikin nasa. "Baby menene kuma? Ko kina son wani abin ne?". Faɗa wa tayi saman jikinsa tana murmushin, rungumeta ya yi yana faɗin "Babyn mijinta me ya faru ne? Me akayi kuma". "Ba komai daddy kawai dai har yanzu ina mamaki ne akan aure". Ɗago haɓarta ya yi tare da gyara zamansa a saman daddumar daga zaman tahiya izuwa zaman cin abinci, ya mannata da kirjinta sosai, kasa kasa ya fara magana "Baby har yanzu kina mamaki akan aure kenan?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e, dan ita da gaske ɗauka take yi aure sai an ɗaurawa mutun igiya guda uku tukun nan, bayan haka sai anyi ta abubuwa, a daɗe ana yi, mutane su taru, dan tana gani wata sain a unguwarsu idan mutane suka taru, idan ta tambaya sai ace mata aure ake yi, ita kuma taga nata ba mutane, kuma ba'a ɗaura mata igiya ba, shine abin ya ɗaure mata ka. "Menene yasa kike mamakin auren namu baby?" Bata ɓuye mashi ba ta gaya mashi abin da take expecting ta gani game da aure, murmushi ya yi tare da ɗaukarta suka koma saman bed nasu. Kwantar da ita ya yi sannan ya cire kayan jikinsa, ya rage daga shi sai Short da singlet, hayewa saman bed ɗin ya yi tare da kwanciya gefenta ya ɗan ja masu bargo kaɗan, a cikin kunne ya ke mata raɗa a hankali hankali ya yin da ita kuma idanunta ke a lumshe. "Baby aure akwai igiya kamar yadda kike tunani, amma ba irin igiyar da kika sani bane, kawai dai zaki iya kiransa da igiyar ne, kuma wannan igiya mijinki kawai ke da shi, shi zan baki ba ɗaura maki ba, amma nan gaba kaɗan zan warware maki, yanzu kuma bari na fara nuna maki abin da ake nufi da auren kacokam nasa". Ya kai karshen maganar tare da sanya hannunsa ta saman kayin gadon, ya kashe switch na ɗakin, nan take duhu ya mamaye ko'ina, ya yi hakane kuma dan baya son suna haɗa ido, kunyarta yake ji, kuma ita ma yana son ta saki jiki da shi, kada ta ji kunya. Jawota jikinsa ya yi tare da haɗe bakinsu waje guda ya shiga bata hot kiss, yana yi yana shafa bayanta, da yake a soyayyarsu ta ɗazun ya koya mata yadda ake yin kiss ɗin, kuma ya ce idan yana mata ta rinƙa mayar mashi da martani, ai kuwa bata ɓata lokaci ba wajen fara mai da mashi da martani babu kama hannun yaro. Wani irin shauki ya ji, bai san time da ya zura hannunsa cikin rigarta ba, a hankali yake yawo da hannunsa saman shafaffen cikinta tare da zura mata yatsarsa cikin cibiyarta yana mata kamar tafiyar tsutsa, yana kara tayar mata da tsikar jikinta, kankame shi ta yi idanunta suka ciko da kwallah dan jikinta na yi mata wani iri, kuma bata san menene bane, hakan yasa ta fara kwallah saboda bata saba ji ba, kuma ga shi ta kasa tantance menene jikin nan nata ke yi mata. Bata kara shiga wani irin yanayi ba sai ma da ta ji hannunsa saman breast nata, nan take jikinta ya karɓi saƙon, hawayen da ya cika mata ido sosai ne ya fara zubo mata, ta riƙe daddyn nata da kyau, ga shi ta kasa magana, domin har laɓɓanta kakkarwa suke yi kamar mai jin sanyin, shi kuma riƙe shi da take yin nan ba karamin kara ingiza shi take yi ba, hakan yasa ya shiga murzar breast nata da ɗan karfi karfi, abun ku da sabon abu, basu taɓa haɗuwa da irin wannan lamari ba, shi kuma sai murza mata kan su yake dole dole ya fito mata da kansu, hakan yasa ta fara jin zafi yana ziyartar ta, kara gudun hawayenta sosai tayi yana kara kankame shi ta kasa magana. Kamar a mafarki ta ji ya kai bakinsa saman nipple ɗin ɗaya, yana masu wani irin sha ba kaɗan ba, zafi suke yi mata dan haka sai ta sa mashi kuka mai ɗan sauti, ya fita hayyacinsa sosai baya jiyota, kuma ba da karfi sosai take kukan ba, haka ya cigaba da murzar kayansa, idan yana shan wannan sai ya riƙi wannan yana murzawa, ita kuma ta cigaba da kukanta. Bayan wasu yan mintuna, cikin zafin nama ya rabata da kayan jikinta, cikin fitar hayyaci ya mance da zancen kamannin ta da mummy'n Jelly ya yi ƙoƙarin shirgarta, sai kuma kamar wadda aka zubawa ruwa ya dawo hayyacinsa, cak ya dakata tare da komawa gefe ya kwanta ya jawota jikinsa, yana sauke wani irin numfashi wadda idan ka ji shi sai ka tausaya mashi, shi kaɗai yasan irin azabar da yake ji a cikin jikinsa. Ita kuma har lokacin bata dai'na kuka ba, yanzu da ya dawo cikin hayyacin sa, har cikin ransa yake jin kukan nata. Da kyar ya ce "Am so so sorry babyna, ki yi shiru, ki daina kuka, daddy ya tuba ba zai kara ba, ayi mashi afuwa ko? Kinga garin in nuna maki me ake nufi da aure ni kin kashe Ni, ba zan iya yi maki wani abu a yanzu ba, domin inason ki yi karatu ki ɗan kara girma tukun nan kafin ki san menene wannan abin, ba zan iya a yanzu ba, kin yi karama, zan baki wahala sosai idan na fara, da wuya ki iya ɗauka saboda raguwa ce ke ajin farko, yanzu tun ba'a je koina ba har kin fara yi mani kuka ko?". Goga kanta ta fara yi a saman kirjinsa tana faɗin "Daddy zafi na ji ai, jikina kuma yana yi mani wani iri kamar ana soka mani allura, kuma...." Bai bari ta karisa ba ya haɗe bakinsu yana wasa da harshensa a cikin bakin nata, a hankali ya sake mai da hannunsa saman breast nata, a wannan karon shafasu ya rinƙa yi saboda ɗazun ya mata da karfi dole zata ji zafin, abin da bata taɓa yi ba, rana ɗaya kawai, ai ko da hankali ya bi mata su sai ta ji wannan ɗan zafin bare da karfi. Sun jima a haka kafin sallamar Hanan ta katse su, abinci ta kawo masu, kallon Ayla ya yi ya ce ta ce Hanan ɗin ta ajiye a palo, dan shi ba zai iya ɗaga murya ba, ita ma Ayla tasha kuka muryar sai a hankali, da kyar ta iya cewa ta ajiye abincin a Palo, Hanan ta sha mamakin jin voice ɗin Ayla kamar tana kuka, amma bata yi magana ba, ta je ta ajiye masu abincin saman carpet kamar yadda Ayla ta faɗa, sannan ta fice ta koma cikin gida. Sai bayan tafiyar Hanan da kamar minti, ashirin sannan ya saketa ya miƙe yana faɗin "Sauƙo mu je na yi maki wanka muje shopping da wuri mu dawo time na tafiya, kuma idan bamu je a daren nan ba to sai jibi, dan gobe idan kin dawo school muna da baki, su Imran za su zo" To ta amsa mashi da shi tare da laluɓawa a cikin duhun ta sauƙo, ba kaya a jikinta ya yi da shi kuma daga shi sai Short. Sai da ya bari ta sauƙo da gangan ya kunna wutar ɗakin dan ya kare mata kallo, hannu tasa ta rufe fuskarta tare da kame jikinta waje guda, hannu ya buɗe mata yana faɗin "Zo na lulluɓe kaya na tun da kunyata kike ji" da sauri ta tafi ta faɗa jikinsa tana ɓuye fuska. "Baby kunyar me kike ji? Kaya na ne fa, kawai dan na kunna wuta na karewa abina kallo sai ki fara ɓoye mani kyakkyawar face na ki hana ni gani complete?". Kin magana ta yi, tayi shiru abinta, raba jikinsu ya yi tare da riƙon hannunta suka nufi toilet yana faɗin "To zan ga karshen kunya tun da ni zan wanke kayan tas". Ita dai taki magana, dan ya tuɓeta gaba ɗaya ya gama kalleta ba kaya, ta rasa bakin magana. Suna shiga toilet ya saketa tare da fara haɗa masu ruwan wankan, sai ɓoye fuska take yi, ita adole kunya take ji. Bayan ya gama ya shureta sai cikin baff ɗin wankar. Fes ya wanke kayarsa kamar yadda ya faɗa, ga shi kuma ya iya wankar sosai, saboda yana yi wa Jellynsa. Bayan ya gama ya naɗota a towel zuwa saman bed ya kwantar da ita, sannan ya dawo ya yi nasa wankar. Bayan ya fito ya ɗauki wayarsa ya kira Abbi akan ya gayawa Aunty ta bawa Hanan kayan Ayla ta kawo mashi, salati Abbi ya yi kafin ya ce "A'a lallai dole ka ce a ɗaura aure, to kai ba zaka bari sai an gama biki ba kafin ta tare a part ɗin naka? Ka fa san mutane za su zo gobe". Katse kiran ya yi dan ya san wannan zance na Abbi Aunty ce ta saka mashi a baki, ba maganar sa bane. Gaban mirror ya tsaya ya shafe jikinsa da mayukansa tare da feshe jikin da perfume nasa, ta cikin mirror yana kallon duk abin da take yi, sai mutsu mutsu take tana satar kallonsa, wani kayatatcen murmushi ne ya bayyana a kan face nasa ganin yadda take satar kallonsa. Bayan ya gama ya ce "Baby fitar mani da kayan sawa na?". To ta amsa da shi tare da miƙewa ta karisa wajen drawer kayar. Wasu kananan kaya wandon jeans baki da t-shirt blue masu shegen kyau ta fito mashi da su. "Shi kike son mijinki ya sa maki?" Ya tambaya yana tsareta da ido ta cikin mirror ba tare da ya juyo ba, Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e, Juyawa ya yi yana faɗin "To shikenan kawo mani na saka" to ta amsa da shi tare da nufarsa da kayan. Ko da taje sai da ya kara jawota jikinsa ya matseta, jin bananarsa na ƙoƙarin miƙewa ne yasa ya yi sauri ya saketa tare da fara shiryawa sauri-sauri. Ita kuma saman bed ta koma ta zauna. Tana zama sai suka ji sallamar Hanan a palo "Ɗauki hijabinki kije ki karɓo kayan naki". To ta amsa da shi tare da miƙewa ta sa hijabi ta fito. Kafin ta dawo ya saka kayansa yana gyara gashin kansa. Zama tayi bakin gadon tana ƙoƙarin fara saka kayan, a nutse ya tako zuwa in da take ya karɓi kayan ya fara saka mata, doguwar riga ce, sai pant da hijabi. Kunya ne ya kamata kuma ta yi mamakin ya akayi ya iya sakawa mace pant?, (ni kuwa nace baki san shi ya reni jelly bane? Har jelly ta kai 15 years shi yake yi mata wanka) Sauri-sauri ya shiryata tare da riƙo hannunta suka fita, da motar Abbi suka tafi shopping ɗin. Ni kuma na haɗa kayana sai mun haɗu daku a hanyar shopping gobe idan mai dukka ya kai mu!!. 💖💖TRIPLETS💖💖 E 65-66 Sauri-sauri ya shiryata tare da riƙo hannunta suka fita, da motar Abbi suka tafi shopping ɗin. Wani katafaren super market suka nufa, yana tuki a hankali yana kare mata kallo. "Baby bana gajiya da kallonki gaskiya, ko dai yau zaki taya daddy kwana ne?" Hannu tasa ta rufe fuska tana mirmishi. "E mana zaki taya ni kwana ne?" Gyaɗa mashi kai ta yi tana faɗin "E daddy, ai duk abin da ka ce shi zan yi". Wani irin sanyi ya ji aransa tana ratsa shi, hannu ɗaya ya sa ya jawota jikinsa yana zuba mata albarka, sai Amin take amsa mashi da shi har suka isa Super market ɗin. Tana ƙoƙarin fita ya riƙo hannunta yana faɗin "Ina kuma zaki je?" "Daddy naga mun iso ne zan fita". Ɗan jan hancinta ya yi kafin ya ce "Haka zaki fita ba tare da kin bawa mijinki hot kiss ba? Ko so kike idan na shiga Super market ɗin naje ina wani tunani ba na kiss naki ba? Kamata ya yi ki bani hot kiss da zai riƙeni ya hanani tunanin komai har sai mun gama shopping mun dawo cikin mota, sai ki kara mani wani da zai ruƙe ni har izuwa gida". To ta amsa mashi da shi tare da matsowa kusa da shi, ita dai baiwar Allah kome ya ce mata, sai dai ta ce mashi to, bata taɓa cewa aa ko kuma sai anjima, to take cewa kuma a lokacin zata yi mashi abin da ya bukata. Matso da fuskarta ta yi daf da tasa, sai kuma ta kasa shan bakin nasa, wani irin kunya ne ta ji ya lulluɓeta sakamakon ya tsareta da wayannan idanuwan nasa. Ganin hakan yasa shi ya matso ya kama lips nata na kasa ya fara sha kamar wanda ya sami sweet, zura harshenta cikin bakinsa ta yi, ta fara yi mashi yadda yake mata, tana jujjuya harshen tata tare da wasa da nasa, nan take ya birkice mata, hannu yasa ya rungumota sosai tare da damkar breast nata ta cikin Hijabin. Daga shi har ita wani irin numfashi suke fitarwa mai cike da tsananin buƙatar juna, sosai suka yi romancing na juna kafin su raba jikinsu ya buɗe kofar motar ya fito, sai wani lumshe ido yake yi, da alama ba dan ya so ba ya rabu da ita, ita kuma duk ya fara koya mata duk wani abun da ake cewa soyayya, yanzu kusan rikita juna suke yi, dan kamar yadda ya ce mata idan ya mata abu to ta maida mashi da martani, hakan take yi, shiyasa yake kara narke mata, ya yi ta bata wuta ita ma tana narke mashi, hakan yasa idan sun haɗe suke murjan juna son ransu. Da kallo ɗaya zaka yi masu kasan cewa e lallai wayan nan a kusa suke, daga shi har ita yanayinsu ta sauya, barema shi yadda idanun nan nasa suka rikiɗe izuwa ja sosai, hakan yasa zaka gane yana tsananin bukatar mace, gaba ɗaya a takure yake saboda bananarsa da ta miƙe sosai, ba dan sun riga sun zo ba, da sai dai su hakura, amma da yake yasan idan ba su sayi kayan yau ba, zai iya kai jibi kafin su saya, hakan yasa ya hakura ya fito daga cikin motar duk da yanayin da yake a ciki. Ɗan rungumota a jikinsa ya yi suka shige ciki, duk wanda ya kallesu sai ya sake waigawa ya kallesu saboda ba karamin kyau suka yi ba, sun dace da juna sosai da sosai. Suna tsaka da shopping ne wayarsa ta fara kara, dubawa da zai yi sai ya ga ansanya Ahmad, da yake tsohon sim nasa ne a wayar, akwai numbobin mutane sosai. Ƴar murmushi ya yi tare da yin picking na call ɗin, ya kara wayar a kunnansa yana faɗin "Hello Ahmad". Daga ɗayan ɓangaren A'A ya ce "Yaya Maik ina wuni?" Lfylou ya amsa da shi. "Yaya Maik gobe In Sha Allah zan shigo Kaduna, amma ba lallai na kariso wajen ka ba, dan ba da wuri zan shigo ba sai can yamma, kuma ba zan kwana a nan ba, wucewa Abuja zan yi, wai Yaya Maik har yanzu ba'a gane mani ƴata ba?". Ajiyar zuciya ya sauke tare kai kallonsa kan Ayla dake zaɓan wasu kayan barci, hannu yasa ya karɓi wanda ta zaɓa ya mayar tare da ɗauko mata wani mai raga raga wadda da shi da babu kusan ɗaya ne, yana yi yana magana da AA "Ahmad wlh Jalila har yanzu shiru, amma ku cigaba da taya mu da addu'a In Sha Allah zata bayyana, zan tura maka hoton ta ma ko zaka haɗu da ita a hanya, dan na san baka santa ba, sai ku haɗu ka kasa gane ita ce, dan zumuncin naku sai a hankali, tun da nace ba zan bawa mummy ita ba shikenan kuka gujeni yau wajen shekara 10 kenan, to dai ku yi mana addu'a". Nasan kowa zai so jin me yake tsakanin daddyn Jelly da A'A, to a yanzu dai ba za ku samu dogon bayani ba, amsa ita ce Ahmad dai kanin Mummy'n Jelly ne, amma ba uwa ɗaya uba ɗaya ba, su ƴaƴan bappanu ne, da baban mummyn Jelly da baban A'A uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, sannan sun yi zama a Kano a tare before su Ahmad su koma Abuja, muna magana ne shekaru 16 baya kenan, sannan idan baku manta ba na gaya maku duk cikin familyn A'A SALAHUDDEEN Ahmad shi kaɗai ne mai son shiga mutane, hakan yasa shi kaɗai yake kiran daddy a waya, wayan da suke son karɓar Jelly kuma ya hana, yan uwan mummynta ne ta wurin uwa, sai kuma kakanta wadda ta haifi mummyn nata, ita ce mummyn da yanzu ya ce dan ya hana ta Jelly shine suka dai na kula shi, to yana magana ne akan mummyn mummyn jelly ɗin. Kafin su yi kuɗi sosai, akwai tsiraru a cikinsu dake tare da daddyn Jelly ba iya Ahmad ba ne kawai, daga baya ne da nera ta zauna sosai da sosai, dama da guntun girman kansu sai kawai suka dasa daga nan!!! A TAKAICE KENAN SU AHMAD DAI FAMILYN MUMMYN JELLY NE, SANNAN SAURA BAYANI ZAI ZO MAKU DAGA BAYA, NA SAN YANZU MA KUN ƊAN FAHIMCI WANI IN DA MUKA DOSA, MU KOMA CIKIN STORYN MU Ahmad "To yaya Maik muna addu'a sosai amma za mu kara, ka gaida mani da su Abbi" To ya amsa da shi, ya kuma yi maganar ya ɗauko wa babynsa wani pant da breziya mai shegen kyau dake makale, ga kuma kokon bra ɗin ɗan daidai tata breast ɗin. Sallama suka yi da Ahmad ya mai da wayar aljihunsa ya shiga ɗiba mata kayan da ransa ke so, duk babu wani kayan arziki da ya ɗauka mata, wandunan ma iya cinya suka tsaya mata wayen da ya ɗauka, ƴan riguna masu kananan hannun kuma a iya cibiga suke tsayawa mutun. Sosai ya ɗebi kaya son ransa, sannan suka tafi wajen biya, bra kawai dozin uku ya ɗeba mata, dan baya son ta bar mashi kayansa a buɗe har wani ya ga alamarsu, ya fi so ta rufe mashi ya zo ya buɗe kayansa da kansa ya murjesu son ransa. Bayan ya biya kuɗi, ya kwashi kayan da kansa zuwa mota, a gidan baya ya shirya kayan sannan suka shiga, a wannan karon ba su ɓata lokaci ba ya ja motar da sauri dan lokaci ya ta fi kuma da alama Ayla na jin yunwa sosai, dan sai hamma take yi, kuma wannan hamma dai bana barci bane. Suna isa gida bayan sun yi parking na motar, ya fito ya kwashe kayan zuwa part nasu, kai tsaye ɗakinsa ya nufa yana faɗin, ta ɗauko masu abinci yau a ɗaki za su ci, to ta amsa da shi sannan ta ɗauka masu abincin ta biyo bayansa. Saman carpet ɗin tsakiyar ɗakin ya ajiye kayan tare da zama ya fara zuba masu abinci, ko kayan jikinsa bai rage ba saboda ya lura babynsa na jin yunwa, idan bai bata abinci ta ci ta ƙoshi ba, ba zai sami kwanciyar hankali ba. Sosai ta ci abinci dan da gaske ta ji yunwa, bayan ta ƙoshi ne shima ya ci nasa, sai da ya ƙoshi sannan ya fara duba kayan, ita kuma ta tattare masu wajen, ta ɗibi kayan abincin zuwa Palo. Lokacin da ta kai kwanikan ta dawo ta isko shi ya fitar da wani kwali ya ajiye a gefe, sannan ya mai da sauran kayan. Gefensa ta zo zata zauna, miƙa mata kwalin ya yi yana faɗin "Saka wa mijinki wannan in gani tukun nan" to ta amsa da shi tare da karɓa ta ɗaura saman gado ta nufi toilet, yana zaune yana jin yadda ta sakarwa kanta ruwa tana wanka. Wayarsa ya ciro ya fara kallon hotunan Jellynsa wani gun ya yi murmushi, wani kuma idonsa ya ciko da kwalla, kwata-kwata ya mance da zancen zai turawa Ahmad hoton. Yana a haka har ta fito ɗaure da towel a kirjinta, zuba mata ido ya yi yana kallonta, gaban mirror sa ta zauna, sai da ta gama shafe jikinta da Lotions nasa masu kyau da kamshi da tsada, sannan ta fesa perfume nasa, sai kallonta yake yi ta tafi da imaninsa, tunani ya fara yi anya zai iya hakura ya barta ta kara girma kuwa? Ko dai ya buɗe kayansa a daren nan ne?. Sai tunani kala kala yake yi bawan Allah. Bayan ta gama ta zo ta ɗauki kwalin kayan da ya bata ta buɗe, wani riga ne wadda ake cewa baby komai ya yi ready, domin duk namijin da ya kalli mace da wannan riga, matukar yana da lafiya to dole ya buƙaci chaskale. Ɗaga rigar ta yi tana kare mashi kallo, dogone har kasa, amma net ne, sai wani pant karami, babu bra ba komai, ana ganin tula-tula tsirarar su. Haka ta kwance towel ɗin jikinta ta sanya wannan riga da pant ɗin a gabansa, dan haka ya nuna mata, kuma bata ɗauka yin hakan ma wani abun bane, dan ɗazun ma shi ya sanya mata kayan mai gaba ɗaya, sai kallonta yake yana ji kamar ya ɓare kayarsa a daren yau ɗin nan, dan ya karaya, yana ji ba zai iya hakuri har ta kara girma ba, yana buƙatar kayarsa. Bayan ta gama sawa ne ta ce "Daddy ai wannan rigar gara kawai mutun bai saka kaya ba". Miƙewa yayi tare da manna mata kisa a goshi ya nufi toilet yana faɗin "Ki hau gado ki kwanta ki jira ni ina zuwa". Kamar dai ko da yaushe to ta ce mashi, toilet ya shige ita kuma ta haye bed abinta ta ja bargo ta rufe jikinta zuwa wuyarta. After 45mins ya fito ɗaure da towel a kugunsa, a lokacin kuma har barci ya yi awon gaba da ita, bai lura da ta yi barci ba, shiryawa ya yi cikin nasa kayan barcin sannan ya haye bed ɗin, sai tashin kamshi yake yi. Kusa da ita ya kwanta tare da shigewa cikin bargon shima yana kare mata kallo, baya gajiya da kallonta ko kaɗan, ko da yaushe ji yake tamkar a lokacin ya fara ganinta, ya ɗan ɗauki mintoci yana kallon yadda take sauke numfashi a hankali hankali ka fin yasa hannu wajen switch ya kashe wutar ɗakin. Yana kashe wutar wayarsa ta fara kara, yana dubawa sai ya ga Abbi ne, ko bai ɗaga ba ya san Aunty ce, da yake shi ma ɗan yi ne, sai ya yi picking call ɗin, ai kuwa hasashen shi gaskiya ne ita ce, yana ɗauka ta ce "Hello yaya Maik ina wuni?" Lafiya ya amsa mata da shi. "Yaya Maik ina Ayla? ka saketa ta dawo mana dare ya yi". Hannu yakai yana shafa face nata kafin ya ce "Wai ke Sadiya dole dole sai kin sa mutun yin maganar da bata dace bane? Ina ruwan ki da Ni? Allah idan baki fita harka ta ni da matata ba sai na yi maganin ki, ta dawo wajen mijinta ne, ko kina da magana ne?" Cikin sauri ta ce "E mana ina da magana, Allah idan baka sako ƴar kanwata ta dawo ba ina zuwa yanzu in ɗauki abata." Abinma dariya ya bashi wai har da cewa zata zo ta ɗauki abarta, da yake ya iya tsiya sai ya ɗan taɓa kumatun matar tasa tare da kai mata wayar kusa da ita dan ita ce ma zata bawa Aunty amsa shi kalamansa sun yi wa Aunty girma, kanta zai fashe idan ta ji. Ai kuwa yana taɓata, can kasa kasa cikin magagin barci ta ce "Daddy ka bari mana" hannu ya kai saman nipple nata ya ɗan matsa da karfi, da ɗan karfi ta furta "Wash daddy da zafi fa" ta kai karshen maganar tare da waro idanunta tana turo ɗan baki tana magana kasa kasa, akan da zafi ya daina, tun zafin ɗazun bai sake ta ba, ai ba shi ya sallami Aunty ba, ita ta sallami kanta, bai ma san time da ta katse kiran ba, dan tun da babynsa ta fara wash da zafi ya ɗaura wayar saman bedside drawer ya fara murzar kayansa dama kamar jira yake yi. Idonta cike da barci ta fara biye mashi suna yi har barcin nata ya watse gaba ɗaya, daga nan suka shiga murjan juna da kyau da kyau. A wannan karon ma, ya yi ƙoƙarin shiga ta, kuma da gaske, sai dai kukan da ta sa mashi da karfi ne yasa ya dakata bai shi ga ba, ya fasa dan yana yi mata kallon yarinya sosai, idan ya shigeta sai ta sha bakar azaba ba kaɗan ba, duk da cewa ita ma mummyn Jelly lolacin da ya aureta 15 years take da shi a duniya, sai dai shi ma lokacin bai wani girma ba 20 years yake da shi, kuma a ranar da ya aureta aka kai mashi ita, a ranar ya buɗe kayansa, amma bata yi mashi kuka kamar na Ayla ba, ita Ayla ƙoƙarin shiga mawai ya yi ta fasa wannan kuka ina ga kuma an yi mai gaba ɗaya? To ba za dai mu haɗa ta da mummyn Jelly ba, dan lokacin mummy'n Jelly da shi da mummyn Jelly kusan shekarun nasu ɗaya, ita kuma Ayla 16 years ne da ita, shi kuma 38 to 39 akwai banbanci. Haka ya hakura ya kyaleta, amma sun yi wasa sosai wadda ya sanya shi samun natsuwa, ya samu kwanciyar hankali, baya son abin da zai sanya matarsa kuka ko da sunan wasa, baya son abin da zai sa ta fara tsoron sa, shiyasa yake binta a hankali yake fara koya mata soyayya kala kala, dan ta san daɗin shi ta yadda ba zata iya yin fushi da shi ba ko da ya mata mai kankanta, so yake ya sa ta mace akansa yadda ko barci ba zata iya yi ba sai tana gefensa, ya kuma yi sa'a ya kware wajen yin hakan, shiyasa yanzu tun ba'a je ko'ina ba, tana son kwanciya a jikinsa sosai, bata son abinda zai raba su, yanzu ma haka tana kwace ne a saman kirjinsa, ya rungumeta sosai yana sauke numfashi a hankali. Bayan wasu ƴan mintuna, sai ya ɗauketa zuwa toilet suka yi wanka, ya kashe hasken wutar toilet ɗin, sai ya kunna hasken wayarsa, dan yana son su yi wanka tare, idan ta ganshi haka kuma yasan zata razana sosai, shiyasa ya kashe wutar ya kunna na wayarsa, ita ma wayar a can gefe ya ajiyeta yadda hasken ba zai haska su sosai ba. Da yake ɗan soyayya ne ajin farko, acikin baff na wankan ma bai kyale ta ba, haka ya jawota jikinsa ya murji iya son ransa kafin ya kyaleta su yi wanka suka fita. Amma dai tasha kuka har idanunta suka yi ja sosai, saboda tula tulan ta sun sha murza da tsotsa har kan nipple ɗin suka yi ja. Shi ya fara shiryawa cikin wasu kayan barcin kafin ya zo ya sanya mata nata, ɗaya daga cikin wadda suka sawo. Rungume da ita a kirjinsa suka kwanta, yana shafa bayanta a hankali tare da gaya mata zafafan kalamai a cikin kunnenta har barci ya yi awon gaba da ita. Shi kuma ya ɗan jima yana tunanin yadda zai ɓareta a ledarta, ta yadda ba zai yi mata ciwo sosai ba, baya son abin da zai sa ta ji ba daɗi ko kaɗan, yana matuƙar kaunar ya ga tana farinciki, dan ta sha bakar wahala na rayuwa, ya kamata yanzu ta huta, dan ma tana da tawakkali ne, da wata ce da mawuyacin abune a sameta daidai haka. Ya jima a haka kafin shima barci ta yi awon gaba da shi rungume da ita a kirjinsa kamar wani ya ce zai kwace mashi ita. A ɓangaren Nawid kuwa, wato gidan ABBO. Yana komawa gida kai tsaye ɗakin Ummi ya wuce, nan ya isko Hajiya Batula da Ummi suna yi wa Jelly magana, da alama nasiha suke yi mata. Da sallama ɗauke a bakinsa ya shigo cikin ɗakin, da fara'a dukkansu suka amsa Mashi, saman bedside drawer ya zauna tare da gaida su, nan ma da fara'a suka amsa. Dawo da kallonsa kan Jelly ya yi, cike da kulawa ya ce "Baby kinga yadda kika yi kyau kuwa? Wow mummy Abla muna godiya sosai da gyara mani amarya ta" miƙewa Ummi ta yi ta fice abinta, ita ma mummy Abla miƙewa ta yi tana murmushi ta fita. Kasa ya yi sosai da murya ya ce "Baby ki yi wa yaya Nawid naki magana mana? Ko dai kina fushi da ni ne?" Ɗago wayannan idanun nata ta yi, lokaci guda sai ya ga yau ta mashi kama da Imran sosai, abin ya bashi mamaki, an mata dilka da sauransu, da ta yi kyau over sai tsantsan kamaninsu da Imran ya fito, jini ba wasa ba. Da mamaki ya ce "Baby yau kin yi mani kama da wani aminina Prof, bari ma na kira shi na gaya mashi, yau kanwata kuma matata ta yi kama da shi, ba dan ina kishi ba da na tura mashi hoton ki ai, amma ba zan iya ba, duk da shima yana da matar sa, amma ta ɓace a Kano nemanta muke yi, kusan kullun sai munje Kano amma shiru". Ita dai ko sannu bata ce mashi ba, da alama yau bata jin yin magana ko kaɗan. Waya ya ciro ya fara kiran layin Imran, sai dai bai ɗaga ba, a lokacin da kiran ya shigo ya bar wayar a saman bedside drawer ya shiga wanka dan ya shirya ya yi barci, lokacin da ya fito kuma kiran ya jima da katsewa, ya ma mance ya sanya kayan barcinsa kawai ya yi kwanciyarsa. Shi kuma Nawid ganin ba'a ɗauki kiran bane yasa ya ajiye wayar yana tunanin ko dai prof ya yi barci ne. Matsowa kusa da ita ya yi tare da riƙo hannuayenta ya fara magana kasa kasa, "Baby yau ba zaki yi wa mijinki magana bane? Ko baki so na ne?". Kwace hannunta ta fara yi first kafin ta ce "Yaya Nawid wani sabon munafurci kake shiryawa kenan?". Zaro ido ya yi yana mamakin kalaman ta, munafurci kuma, ya maimai ta tambayar. "E mana munafurci, kana tunanin ban ji abin da kace ranar bane?" Ta faɗa tana mashi kallon sama da kasa, yau babu shirme a maganarta, iya gaskiya take faɗe, duk da cewa dama kullun gaskiyar take faɗe, to da shirme a maganganunta shiyasa basa ɗaukarsu akan gaskiya ce, amma yau clear take magana, kamar yadda kowa yake yi, babu shirme babu shagwaɓa. "Baby me na faɗa ranar kuma ni Nawid?". Ɗaure fuskar nan sosai tayi, ance gado ba karanbani ba, abubuwa da dama ta ga ji babanta, ciki harda tsare gida idan ta yi niyya, da kuma faɗa idan ka taɓota, tana da zafi da kaifin harshe idan ka shiga harkarta, amma akwai shagwaɓa na bugawa a jarida tare da sangarta. "Kana tunanin ban ji me ka ce bane? To bari ka ji na ji komai, nanar fa ina ji kana waya, kana faɗe cewa zaka yi soyayyar karya dani ta yadda zaka sa wancan kwarton ya dai na kulani, wato da gaske kasan da cewa shi kwarto ne, amma saboda zalinci shine kaki ka dakatar da shi daga abin da yake yi mani ko? Ni na sani har yanzu ba so na kake yi ba, domin na sani cewa duk wanda bai soka da safe ba, da rana ya zo ya ce yana son ka to karya yake yi, kai da bakinka ka faɗi wannan kalmar ranar, ko shima kana tunanin ban ji bane? To idan haka kake tunani ka makara, na ji, kuma kai baka so ni da safe ba, da farkoma agaban kowa da kowa ka ce baka so na, ko ka mance ne? To idan ka mance na tuna maka, ka ce baka sona baka son ganina, ni mahaukaciya ce, to ni mahaukaciya ce dan haka ka rabu da ni, ka koma wajen wadda ba mahaukaciya ba, ka koma wajen wadda kake so, idan ba haka ba, wlh sai na yi maka abin da baka taɓa za to ba". Ta kai karshen maganar tare da miƙe wa ta fice daga cikin ɗakin. Mutuwar zaune ya yi tunani ya fara yi, baby ta samu sauki ne? Kenan ta dawo cikin hayyacin ta? Dan wannan maganganun nata ba su yi kama da mara lafiya ba, sun fi kama da cikakken mutun mai lafiya, to me yake shirin faruwa ne?. Jiki ba kwari ya miƙe ya nufi ɗakinsa, can cikin kasan zuciyarsa, wani bala'in kaunar ta ne yake ta so mashi, lokaci guda ya kamu da azababben sonta (Ni kuwa nace ba dai lokaci guda ba, tsohon tsumine ya tashi, dama ka jima a ciki, kawai dai kasa ruwan ido a gaba ne yasa baka fahimci hakan ba) Yau da kyar ya yi wanka ya yi shirin barci ya kwanta, ko da ya kwanta barci ya ki zuwa har wuraren karfe uku na dare, da kyar barci ya yi awon gaba da shi. A ɓangaren Rimsha kuwa wato gidan Lion. Sai asubar ta farka, barci ya yi daɗj, wanka ta yi tare da ɗauro alkawala, raƙatainil fajir ta fara yi kafin ta yi sallar asuba, bayan ta idar ta zauna karatun Al Qur'ani mai girma tare da askar, ta nutsa cikin karatun da take yi sai ji tayi daga bayanta ance kin ɓata, kin tsallake aya ɗaya. Da sauri ta juya, Malika ce ke zaune mata saman bed nata tana murmushi, yau ta zo mata da doguwar riga pink color saɓanin na baya. "Malika ke ce?" Gyaɗa mata kai ta yi alamar e "Shine tun ranar baki sake dawowa ba, me yasa?" Ta tambaya tana rufe Al Qur'ani dake a wayarta, tana fita daga cikin App ɗin. Kara faɗaɗa murmushinta Malika ta yi kafin ta ce "Na dawo mana, an gaya maki na taɓa yin nisa dake daidai da minti goma ne? Idan kina tunanin haka to ki daina". Gyara zamanta ta yi suna fuskantar juna ta ce "To ya ni bana ganin ki? Tun fa ranar lokacin a ilorin ban sake ganinki ba, ina kika shiga?". "Kai Rimsha akwai ki da yawan tambaya, idan an gaya maki kuma sai ki tsorata". Murmushin ta yi har sai da dimple nata suka lotsa sannan ta ce "A'a Malika yanzu ai na san wace ce ke, to ba zan tsorata ba, kawai ki gaya mani". Miƙewa ta yi ta dawo kusa da ita saman daddumar ta zauna tare da riƙo hannayenta kafin ta fara magana nutse "E kamar yadda na gaya maki ban taɓa nisa dake daidai da awa guda ba, kullun ina tare dake, amma bari na baki misali, ranar da Ayla ta daki wannan Jami'u ɗin, ai kin san ba karfin ta bane, domin bata da karfin da kuma kwarin gwiwa tare da dakiyar zuciyar da zata iya bugawa wani ɗan adam wannan katako, ba zata iya yi mashi duka ɗaya ya suma ba, to wannan ranar ma ni ce na shiga jikin Ayla, kin tsorata da ni ne, shiyasa bana bayyana maki kai na, abu na biyu wadda ya faru jiya, ba Akila ta kira Imran dan ra'ayin kanta ba, ni na saka ta yin hakan, domin tana kuka ta rikice tunanin kiran Imran bai zo mata ba, kamar yadda kema tunanin bai zo maki ba, ga waya a hannunki amma baki iya kiranshi ba, abu na uku kuma na ban dariya da mamaki, shine ba fuskar ki maman su Imran ke gani ba, fuskata na ainahi take gani shiyasa bata ganinki, ni nake bata tsoro shiyasa bata son ki, ni kuma na yi mata haka ne saboda wani dalili wadda nan gaba kaɗan zaki san shi, yanzu dai ya masoyin naki? Bani labarinsa duk da cewa nasan komai, amma ina son jin labari daga bakin ki, amma fa gaskiya yana da kyau sosai, jiya a wajen pharmacy nan na ganshi, wow dole ki mace akansa, ni lokacin a Ilorin da kike ta maganarsa ban ɗauka haka yake ba, sai jiya na mashi kallon tsab, ranar da kika kai mashi ruwa yana azumin nan ma, randa ya zo kenan, na so ganin face nasa, amma da yake yana duƙe ban sami gani ba, yanzu dai bani labari, kin san ina son labari sosai". Ta kai karshen maganar tana dariya kasa kasa. Shiru Rimsha ta yi tana al'ajabin wannan abun, abin ya ɗaure mata kai, wato dai duk in da take Malika na wannan wajen? Kai amma gaskiya Malika tana da kirki sosai. "Tunanin me kike yi Queen of beauty A'A? Kin fa san shima Ahmad ɗin ni na sanya shi ya bi wannan hanyar ba dan ya so ba, ni na shiga jikinsa na sanya shi ya ji tausayinku, bayan ya ji tausayinku sosai ne sai na fita na koma gefe ina kallonku". Nisawa ta yi kafin ta fara magana "Malika ina godiya sosai gaskiya, kuma ina mai baki hakuri akan ihun da na yi maki ranar" "Wayyo Rimsha kada ki damu yanzu dai ki kulawa Saif da kanki fa, ai dan ma ba zan iya shiga cikin jikinsa bane, da na sanya shi ya yi maki kiss kamar yadda kika yi mafarki ranar". Zaro ido Rimsha ta yi tana faɗin "A ina kuma kika ji na yi mafarkinsa?". Jan dogon hancinta Malika ta yi tana faɗin "A lokacin da kike gayawa Ayla mana, kin san me nake so da ke?" Girgiza kai ta yi alamar a'a. "Good, abin da nake so dake shine kibi shawarar da Imran ya baki akan Saif kada ki yi mashi shisshigi, idan ba haka ba, zai iya halakaki, ni ba zan iya shiga jikinsa ba, kuma ba zan iya kwatarki a hannunsa ba idan yana baki a jikinki, domin ya fi karfin mu, yana da ayoyin da duk musulcin aljani matukar zai cuci wani to yana tsoron su, kin san akwai ayoyin da koda aljani musulmi ne zai ji tsoron su, Al Qur'ani mai girma maganin komai da kowa ne, sannan magana ta gaba akwai ciwo sosai a rayuwar shi ko in ce maki a rayuwarsu su ukun dukka, ki kula sosai, dan kamar yadda Imran ya gaya maki Saif ya wuci gaban tunanin ki, to haka ne, dan haka ki kula, bana son wannan kyakkyawar face ɗin naki ta saɓa kammani, dan idan ya yi maki mari ɗaya ba zaki ganu ba". Ta kai karshen maganar tana murmushi. Murmushi ita ma Rimsha ta yi tana ƙoƙarin yin magana sai ta ga Malikar ta ɓace ɓat, hakan kuma ya yi daidai da shigowar Imran cikin ɗakin bakinsa ɗauke da sallama. Da fara'a a kan face nata ta amsa mashi sallamar tare da ɗaga mashi gaisuwa, amsawa ya yi tare da tambayarta ta kwana lafiya. Da lafiya ita ma ta amsa mashi sannan ya ce ta tashi suje ta gaisheda Areef, to ta amsa da shi sannan ta miƙe, ya yi gaba ta bi bayansa. Da sallama suka shiga ɗakin, idonsa biyu yana askar, lokacin kuma karfe 6 tayi. Gefensa Imran ya zo ya zauna tare da miƙe mashi hannu akan su yi musabaha, hannu shima Areef ɗin ya miƙa mashi suka gaisa, Imran ya tambaye shi ya ji, Alhadulillah ya amsa da shi. Daga ɗan gefe Rimsha ta tsaya tana faɗin "Ina kwana yaya Areef?" Sai lokacin ya kai kallonsa kanta, lafiya ya amsa mata da shi tare da dawo da kallonsa kan Imran yana faɗin "Ki zo ki zauna kusa da yayan ki mana, dan na san ko ba'a faɗa ba ke kanwar Prof ce tun da na ganku a tare" Duk wannan magana suna yin shine cikin harshen turanci, abin da yasa kuma ta gaishe shi da turanci dan ta ga Imran turanci ya yi mashi, hakan yasa ta gane kwata-kwata basu jin Hausa. Juyowa Imran ya yi yana kallonta ya ce "Rimsha ki zo ki zauna mana?" To ta amsa da shi tare da karisawa kusa da shi ta zauna tana tambayar Areef ya jiki? Alhadulillah nan ma ya ce mata, daga nan suka shiga hirar duniya shi da Imran, ita kuma sai satar kallon shi take yi dan jini ba wasa ba kallon kamannin Lion take yi mashi. Suna tsaka da hira sai ga Lion ya shigo dakin bakinsa ɗauke da sallama, time na yiwa Areef allura ya yi, miƙa mashi hannu Imran ya yi suka yi musabaha, ita kuma Rimsha sai kallon shi take yi, amma bata yi mashi magana ba, dan ta ji zancen Imran sosai. Yana sanye da wando three quarter fara tas da Round neck polo shirt mai bala'in kyau, ya ɗaure dark black curly hair san nan a baya, wannan guntu na gaban goshin ya sake ta, da alama kuma ya kara rage mata tsawo, domin yau bata wuce mashi iya sajensa ba, saɓanin kwana biyu da suka wuce ya kai mashi har gemu, kamar kullun sai tashin wannan fitinannen kamshin perfume nasan yake yi. Hannun ta Imran ya kamo suka koma gefe saman sofa dake a cikin ɗakin suka zauna dan su bashi waje ya yi aikinsa ya fita, baya son ɓata lokaci. Sai kallon shi Rimsha keyi, zafi zafi cikin zafin nama ya yi abin dake gabansa, bayan ya kammala ne ya ɗan zubawa Areef ɗin wayan nan dara-dara blue eyes ɗin nasa na yan mintoci kafin ya ce "How are you feeling now?" Jinjina kai Areef ya yi kafin ya ce "Alhadulillah am felling better" daga nan bai sake magana ba, ya ɗebo magunguna ya fara buɗesu yana tarawa a hannunsa, bayan ya kammala ya buɗe fridge dake a wajen ya fito da ruwa mai sanyi ya miƙawa Areef ɗin ya sha. Sai da ya tabbatar ya yi mashi duk abin da ya dace sannan ya nufi waje akan anjima zai zo ya kai shi toilet ya yi wanka. Magana ta gaskiya Rimsha dai daurewa kawai ta yi, amma har fitsari take ji saboda tsananin rikitata da kwarjininsa ya yi, ta ruɗe sosai, ga shi ko ta kansu bai biba, bayan gaisawa da Imran da ya yi, shima gaisuwar yana yi hankalinsa na a kan kirjin Areef in da ya harbe shi da gun ranar, yana tunanin za ayi wa wajen tiyata gobe ko jibi, dan ya na ji tamkar akwai wani abin a wajen. Yana fita Rimsha ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya wadda ya sanya Areef da Imran ɗagowa da kallonsu kanta lokaci guda. Da hannu Areef ya yi mata alama akan ta zo, ba musu ta je kusa da shi ta tsaya, nuna mata in da ta zauna ɗazun ya yi akan ta zauna, nan ma ba musu ta zauna tana kallon Imran da yake jinjina mata kai akan ta zauna ba wata matsala. "What is your name?" Shine abin da Areef ya fara tambayarta. "My name is Rimsha" ta bashi amsa. Jinjina kai ya yi yana faɗin "Good nice name" ya yi maganar tare da ɗan yin shiru kafin kuma ya sake cewa "Do you love my brother?" Zaro ido suka yi daga ita har Imran a lokaci guda, girgiza kai ta fara yi alamar a'a. Murmushin kaɗan ya yi kafin ya fara magana a nutse "Ni fa jami'in CIA ne, da kallo ɗaya wadda bai fi sakan uku ba nake gane abu, na samu horo ta ɓangarori da dama ta yadda kallo ɗaya zan yi wa mutane ɗari na fitar da ɓarawo da kuma mai gaskiya a cikinsu, mara ƙwaƙwalwa da tunani bai isa ya tunkari CIA ba ma bare ya shiga cikin ta, Jami'ai ne dake amfani da zallar kwakwalwa da basira, ko mai shara ba zaka iya zama a hukumar CIA ba har sai idan zaka iya gane ɗan ta'adda a cikin miliyoyin mutane, wadda yake share mana office namu ya goge, daidai yake da D.O.P na yan sanda a wajen iya aiki, to ni kuma ina matsayin DOA mutane biyu ne kawai a samana a cikin hukumar, kin ga kuwa ai na wuce duk yadda kike tunani, tun da Lion ya shigo ɗakin nan kike kallonsa, acikin kwayar idon ki akwai tsantsan Kaunarsa, abin da ya sa na tanka maki saboda da kallo ɗaya da na yi maki na fahinci da iya gaskiyar ki kike son shi, akwai mata da dama da suka yi mashi abin da ina da tabbacin ya fi wadda kika yi mashi na soyayya, sun mutu a kanshi, akwai masu cewa idan bai ce yana son su ko da sau ɗaya bane sai sun sha guba sun mutu, wa su sun sha da gaske an kai su asibiti, wasu kuma ba su sha ba, shi kuma ko kallo basu ishe shi ba, akwai wadda lokacin muna school Prof bai gaya maki bane? A gabansa ta zo ta tsaya da poison a hannunta, wai idan bai ce yana son ta ba zata sha, a zafafe ya miƙe ya damki wuyarta da hannunsa ya ɗura mata gubar gaba ɗaya abankinta tare da toshe mata hanci, ranar da kyar na kwaci yarinyar a hannunsa, na miƙata aka kai ta hospital, tun ba mu kai haka ba, tun muna school ake mutuwa akanshi bare kuma yanzu, cos ban taɓa kula ko da mace ɗaya masu masa irin wannan haukar son ba, saboda nasan ba dan tsakani da Allah suke son shi ba, kuma mu mace ta yi mana babbar illar da yarda da ita zai zame mana abu mawuyaci a rayuwar mu, ban san me yasa nake jin a jikina matan Nigeria sun fi matan mu amana da mutunci ba, da kallo ɗaya na yi maki na gane da iya gaskiya kike son Lion, ba dan wani abu nasa ba, kuma ina da tabbacin ba zaki cutar da mu ba, saboda Imran mutumin kirki ne sosai, sanadiyarsa ni da Lion muka musulunta Muna matukar kaunar prof fiye da tunanin ki, da Lion da Michael sun azabtar da zuciyoyin masu son su da dama, ni bana cutar da zuciya, idan mace ta ce tana so na, bana wulakantata duk da cewa sun mana illa, na kan nuna mata ne cewa ni bana da damar yin soyayya ta yi hakuri, da lalama da kuɗi muke rabuwa, mu matan mu mafi yawanci kuɗi suke so ba mutun ba, hakan yasa nace maki da wuya a kasar mu a sami mai yi mana son gaskiya, so koma dai me ni bana cutar da zuciya saɓanin Lion da Michael, ga mu da farin jini bala'i, duk in da muka shiga sai an so mu, amma haka Lion da Michael suke cin uban duk zuciyar da take son su, in ma mace ko namiji, basu cire ko ɗaya ba, yanzu haka zaman da kika yi a cikin gidan nan, da a baya ne baki isa ko kusa da gidan nan kin zo ba, amma da muka musulta muka san cewa laifin wani baya shafan wani shiyasa Lion ya rage tsana da ya yi wa mutane, wlh ina da tabbacin da a baya ne, ko mutuwa kike yi sai dai ya sanya bindigarsa ya karisa ki gaba ɗaya, ba dai ki zo mashi gida ba, ko da kuwa tare aka haifeku rana ɗaya da prof bama kanwa ba, cos yanzu gaskiya ya sassauta, ko in ce maki mun sassauta, addinin musulunci addini ne mai sauki, laifin wani baya shafan wani, a da lokacin da muke kan mummunar hanya muna ganin komai daidai ne, hakan yasa muka yi wa mata kallon ɗaya, amma yanzu Alhamdulila mun rabe ku, na yi maki alkawarin cewa zan taya ki yaki akan abin da ki ke so, sai dai fa akwai matuƙar wahala, dan Lion tun muna yara baya tanƙwaruwa, sannan zuciyarsa kamar dutse take baya juyuwa, amma fa yana da zuciyar zinari sosai, kawai dai shi na saban ne, ina son ki da ɗan uwana, dan tabbas matan Nigeria kuna da kirki, yanzu dai ina son ki daina yawan kallon shi da kike yi, dan in ya kama ki wlh mai kwatarki ma ina ji sunan sa gawa, ni dai kinga yanzu ba lafiya ke gare ni ba bare nayi yunkurin kwatarki, na biyu kada ki rinƙa bari hanya ta haɗa ku, a hankali za mu san ya zamu ɓullowa abin ni da Prof, idan kika cika haɗa hanya da shi wata rana za'a iya ɗaukar gawarki na gaya maki" Shiru ya yi yana jan numfashi yana ɗan hutawa. Ita kuwa ta yi kasa da kanta tana hawaye, wai yau ita ce ta zauna da ɗaya daga cikin yan uwan GAR suna magana haka cikin mutunta juna, kai wannan abin ta rasa taya zata kira shi, lallai Areef ya cika cikakken musulmi mai imani, mutumin kirki ne sosai da sosai. Ban so dagatawa a nan ba, naso kai karshen tattaunawar Areef da Rimsha tare da Imran, dan jin yadda zata kaya, Sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai 💖💖TRIPLETS💖💖 E 67-68 Ita kuwa ta yi kasa da kanta tana hawaye, wai yau ita ce ta zauna da ɗaya daga cikin yan uwan GAR suna magana haka cikin mutunta juna, kai wannan abin ta rasa taya zata kira shi, lallai Areef ya cika cikakken musulmi na kwarai mai imani, mutumin kirki ne sosai da sosai. Imran ne ya sanya hannu yana goge mata hawayen dake a kan face nata. "Ki yi shiru Rimsha ki dai'na zubar da hawayen ki, haka Allah yake lamuransa". Juyowa ta yi da kallonta izuwa kan Imran ɗin ido cike tab da kwalla murya a dashe ta fara magana "Yaya Imran ba bu wanda ya taɓa fahimtata irin yadda yaya Areef ya fahimceni lokaci guda, ko Jehan da muke uwa ɗaya uba ɗaya, kai ba Jehan ba, ko daddyn mu ya kasa fahimtata akan kallon video yaya Saif da nake yi a Tv, har hana ni sai da daddy ya yi, ni ban san ta ya ya zan gaya maka ba, amma dai abin da na sani shine ina son shi, ban taɓa ganin fuskarsa ba before ya zo nan, amma a haka nake kwatatan ta yadda zai iya kasancewa a zahiri na zana shi, kuma kai da kanka ai kaga zanen, kai da bakinka ka ce shi na zana, amma ba tare da na sanshi ba na zana shi kuma ya fita daidai yadda na zana, har mahaukaciya Jehan take ce mani akan shi, ta dake ni ta zageni dukka akan shi, amma ko sau ɗaya ban taɓa jin na dai'na son shi ba, ka san cewa mutun baya sanyawa kan shi soyayya ko?" Gyaɗa mata kai ya yi alamar e, shima idanunsa sun cika da kwalla, wannan irin jarabawa Allah dai ya bata ikon cinye shi, amma akwai wahala, abune mai matukar wahala, wannan shine faɗa tsakanin mutuwa da rayuwa, domin idan Lion bai so ta ba, tana iya mutuwa yadda ta kamun nan, shi kuma mawuyacin abune ya so ta gaskiya. To fa yau ake yin ta. "Yaya Imran ni nasan da cewa Allah ne ya jarrabeni ta wannan hanyar, ina kuma fatar na ci wannan jarabawa". Jawota ya yi jikinsa yana rarrashinta dan kukan da take yi ya yi yawa, ita kuma ta jima ne tana son ta sami wadda zata amayarwa abin da ke cikin ta na yadda take ji akan Lion, Akila yarinya ce, kansu kusan ɗaya ko da ta bata labarin yadda take jin Lion a ranta ba ta wani fahimci yadda take ji ba, amma yanzu da ta samu ta gayawa su Imran kuma suka fahinceta, ta ji sauƙi a ranta, baiwar Allah shine silar kamuwarta da cutar da Dr ya ce yake damun ta, ta azabtu sosai da soyayyan bawan Allah nan, tun tana da shekara 9 a duniya take fama. Areef da ba jin hausa yake yi ba sai bai gane me suka faɗa ba, kawai dai yana ganin suna magana, amma yadda ya ga tana hawaye ga Imran shima idonsa ya ciko da kwalla, sai ya fahimci koma me akan Lion suke magana, kuma tana bashi labarin irin son da take yi wa Lion ɗin ne, dan haka sai ya tambayi Imran ɗin akan ya faɗa mashi me ta ce. Ai kuwa Imran bai ɓoye mashi komai ba ya zayyana mashi duk abin da ta faɗa. Hannunsa da bai ji ciwo sosai ba ya sanya ya riƙo nata hannun, da yake shi ba laifi yana da tausayi, cikin harshen turanci ya fara yi mata magana a nutse. "Me yasa kike son Lion har haka? Kuma me yasa yanzu kike yin kuka? Ya kamata ki daina yin kuka ki yi godiya ga Allah, bari ki ji wani abun al'ajabi da mamaki, daga ni har su Lion ba wanda yake kaunar Africa da yan cikinta abaya, bamu son bakaken fata fiye da yadda baki zato, a baya da zamu haɗu da bakin fata ko a rashin sani ya ɗan taɓa mu, to muna iya kashe shi, dan ba mu son su, amma haka kawai na tsinci kai na da kauna shiga hukumar CIA, daga nan na yi wa kaina alkawarin shafe yan ta'addan dake kewaye da mu, sanadiyar haka na zo Nigeria, sanadiyana kuma Lion ya zo Nigeria, har gobe ina mamakin ya akayi muka yarda da Prof lokaci guda duk da yana bakin fata, amma dai na san Allah ne ya so mu da rahma shiyasa ya haɗa mu da shi kuma ya sanya mana kaunarsa har muka musulta, mu ko turawa yan uwanmu bamu yarda da su ba, kwata-kwata ba mu son kowa sai mu kaɗai kan mu, gidan mu ko shekara goma zaki yi a ciki ba zaki taɓa ganin baƙo ya zo ba, dan bamu so, amma a haka muka yi accepted na Prof harma muke kaunarsa fiye da uncles ɗin mu, time da Prof ya gaya mani Lion ya yabawa yan Nigeria, wlh ba dan nasan waye Prof ba da ba zan yarda ba, na san cewa ba zai yi mani karya ba, shiyasa na yarda, amma nayi mamaki, nima kuma yanzu ga shi haka kawai naji ina son ƴan Nigeria, ina son zama cikin kasar ku, akwai daɗi kuma ina son ki kasance matar ɗan uwana, saboda ke yarinya ce, na farko baki san yaudara ba, babban abin da yasa ma na aminta dake kenan, yara duk abin da za su gaya maka daga cikin zuciyarsu kai tsaye yake fitowa, inma karya ko gaskiya, daga karkashin zuciya yake fitowa, duk abin da zai fito da ga karkashin zuciya kuma ai kinga ba batun dogon bincike akan shi dan hakan yake, sannan yanzu ke baki ma san cewa ki so Lion dan kuɗin sa ko kyansa ba, ɗan gara kyau ma yara suna son abu mai kyau, amma ke tun ma baki san face nasa ba kika fara son shi, kuɗi kuma a yanzu yadda kike ɗin nan me zaki yi da kuɗi bare ace dan kuɗi zaki so shi, sai Maganar mukami, ina da tabbacin a wayan nan ƴan shekarun naki baki ma san me THE GENERAL OF THE ARMY'S yake nufi ba, yanzu ke ina da tabbacin duk wani soja mai kaki ajiki kallon abu guda kike yi masu, saboda bama ki san mukami ba bare ace dan shi kike son shi, duk wace zata so Lion to fa abayar ki ce ina da wannan tabbacin, ba zai taɓa samun mai yi mashi son tsakani da Allah kamar ke ba, ni abin da baki sani ba ma shine, da shekarunki nayi amfani na san cewa e son gaskiya kike yi wa ɗan uwana, In Sha Allah yadda kika sha wahala akan shi, Allah ba zai bari wuyarki ya tafi abanza ba, za mu yi nasara, kin wahala sosai my sister, sai dai nace maki Allah ya bamu iko da nasara, Allah muka ruƙe kuma za mu yi nasara...." Kiran wayar Imran da akayi ne ya dakatar da shi daga maganar da yake yi, suka yi shiru dan bawa Imran damar ɗaukar call ɗin sa. Ganin sunan Saif ne a kan screen ɗin wayar ya bayyana bayan ya duba ne yasa ya miƙe ya ce yana zuwa ya nufi waje. Cigaba da magana Areef ya yi "Me yasa kike saka irin wannan manyan kaya haka? Ga shi sai zufa kike yi" ya yi maganar yana nuna hijabin jininta. Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauƙe, cikin muryar kuka ta ce "Haka muke yi a nan Nigeria, a kasar ku ne ko musulma sai dai ka ganta ba ɗan kwali bare hijabi, masu imani sosai ne sai kaga sun saka ɗan karamin hijabi, mu kam a nan har kasa muke saka wa mu rufe jikin mu". Jinjina kai ya yi yana faɗin "Good, amma dai ya kama ku rinƙa sassautawa kanku dan wannan wahala ne ai" Shiru ta yi tana ɗan ɗari ɗarin amsar da zata bashi kada ya ɓata mashi rai, amma da ta tuna gaskiya ce zata faɗa, daga ƙinta kuma sai ɓata, sai ta daure ta ce "A'a Yaya Areef, wannan shiga ita ce daidai, ita ce annabi Muhammad (S.A.W) ya koya mana, gaba ɗaya jikin mace al aura ce, ya kamata ta rufe ko'ina nata, iya fuska kawai aka yarda ta bari a buɗe, shima ai kaga akwai dalili mai karfi, wannan shiga tamu ta nan shine shigar musulci, annabi ya ce mace ta sanya dogon hijabi, ta baya yana taɓa kasa, ta gaba kuma, ya kai idon sahu". Sosai ya ji daɗin bayanan ta, kuma shi kanshi shigar tata ba karamin burgeshi ta yi ba, kawai dai dan ya ga tana haɗa zubane yasa ya yi mata magana, zufar kuma ta samo asaline saboda kukan da ta yi. Sakin hannun nata ya yi yana faɗin "Ki yi mani addu'a na sami lafiya muje ki raka ni yawo a sassan kasar ku, dan ina son yawace koina da ina kafin mu koma kasar mu, ina son ganin kasar nan taku sosai, dan a yan kwana biyu da na yi a freedom nan, ba ƙaramin daɗin garin na ji ba". Zata yi magana kenan Imran ya shigo bakinsa ɗauke da sallama yana ruƙe da wayar Lion a hannunsa, sai mirmishi yake yi yana kallon screen ɗin wayar, da alama video call yake yi da wani. Kusa da Areef ya zo ya zauna tare da miƙa mashi wayar yana faɗin "Aseef want to see your face". Fuska ba ya bo ba fallasa ya karɓi wayar. Wani irin kayatatcen Mirmishi ne ya bayyana akan face nasa lokacin da ya kawo wayar sai tin face nasa. Ba komai ne ya sanya shi wannan murmushi ba face ganin Aseef da ya yi zaune cikin library ga takardu a gabansa, da alama karatu yake yi tukuru, shima cool murmushi ne ɗauke a saman face nasa. "My blood Nigeria ya yi maka daɗi ko?" Aseef (Michael) ya tambaya. Gyaɗa mashi kai Areef ya yi kafin ya ce "Over my blood over, idan akwai abin da ya fi over ma to shine, I really like Nigeria and Nigerians, they are good people's sosai". Shiru Aseef ya ɗan yi kafin ya ce "Okey i will join you In Sha Allah, but not now, I have exams next month, if am done, i will try to join you, am not happy at all, All of you kun tafi Nigeria kun barni, dan ma am together with uncle Musharraf yana ɗebe mani kewa, if not da kewa ya yi mani yawa sosai, a really missed guys". Zuba mashi ido Areef ya yi na yan mintoci kafin ya ce "What is wrong with you?" Kara faɗaɗa mirmishi kan face nasa ya yi yana faɗin "Nothing blood". "Am I your mate? Am i playing with you? I said what is wrong with you?" Ya yi maganar yana ɗaure fuska sosai. Cikin dariya Aseef ya ce "You're my mate and you're playing with me, what is next?" Dafe kai Areef ya yi Aseef ya san takan tsiya, idan ya bi shi da karfi ba zai gaya mashi me yake damun shi ba, ga kuma damuwa karara akan face nasa bawan Allah, dan haka sai ya ajiye duk wata zafa ya fara yi mashi magana kamar sa'annin juna, suka koma TRIPLETS ɗin kawai, tun da ya ga yanzu Aseef ɗin ya warke garau tamkar bai taɓa yin ciwo ba, yanzu dole su goga kafaɗa. "My blood you knew i really love you, and you knew am worried about you? Please tell me what is wrong with you, if not you will put me in to bad mood" Yar dariya Aseef ya yi kafin kuma ya ɗaure fuska sosai, nan take yanayin sa ya sauya, yanzu dai cike da shagwaɓa ya fara magana "My James Uncle T ne yake bawa uncle Musharraf wahala, everyday idan na tafi school, before na dawo sai ya bashi horon sojoji, idan na tambayi uncle Musharraf ɗin what is happened to him sometimes nake ganin face nashi da kuma bodynsa somehow, sai ya ce mani nothing, kuma i knew there is something behind between him and uncle T dan na taɓa kama shi yana sanya uncle Musharraf ɗaga gun Ak, kuma tana cike da bullet sosai, ranar har ciwo sai da hannun uncle Musharraf ya yi, ina son gaya wa Lion amma bana son wata matsala ta faru a gidan kuma, kasan Lion zai bawa uncle T punishment mai tsanani, hakan kuma zai ɗaga wa daddy hankali, ina da tabbacin Lion yana busy this two days ɗin nan, i think that is the reason why baya bincinkan camarorin gida, da kuma abin da yake faruwa Kum......." Bai kai karshen ba Areef ya dakatar da shi cikin tsawa "What uncle did to Uncle T da har yake ba shi horon sojoji Kuma?". "My blood you already knew that gaba ɗaya yan gida they hate Muslim people's, so the reason why uncle T ke azabtar da shi kenan, because he is a Muslim". Rai a matukar ɓace Areef ya ce "Ya zama dole uncle T ya karɓi hukuncin zalincin da yake yi, before na tafi sai da nace mashi ya sauƙe wannan rawanin zalinci dake a kansan nan ya ajiye, amma yaki, yanzu dai zan gayawa Lion please ya sanya a kawo mani uncle na nan kasar, idan na sami lafiya sai mu koma tare, in na dawo Allah sai na sanya uncle T ya kwance wannan rawanin zalinci dake a kansa ya ajiye...." "My blood why zaka raba ni da uncle Musharraf, you know shi kaɗai nake gani yake rage mani kewar ku fa". Girgiza kai ya yi yana faɗin "No Aseef ya zama dole na ɗauki uncle, ko so kake na barshi uncle T ya cigaba da wahalar da shi ne?" Girgiza kai ya yi alamar a'a. "To ka gani, idan ka gama Exam ai kai ma zaka bi yo mu sai mu koma a tare, so kada ka damu, ka mai da hankali sosai akan karatu." To Aseef (Michael) ya amsa da shi, daga nan suka cigaba da hira, sosai Areef ya bashi labarin Rimsha bai ɓoye mashi komai ba, dan dama haka suke, da James da Michael sirrin su kusan ɗaya ne, abin da ɗaya ya sani da wuya ka ji ɗaya bai sani ba. Wani irin daɗi Aseef ya ji ya ce sam Areef sai ya nuna mashi a ina Rimsha ɗin take, ai kuwa bai hana shi ganin ta ba, da hannu ya yi mata alama da ta dawo gefensa ta saman pillow da yake kwance su yi magana da ɗan uwan shi, ba musu ta miƙe ta je. Ba ƙaramin farinciki Michael ya ji ba, da alama ma ya fi Areef murna, dan har da dariya ne akan face nasa ba iya mirmishi ba. Ita ta fara ce mashi good morning, sai daɗi yake ji, ga fara'a palala a face nasa, ya amsa mata gaisuwar tare da tambayar ya take, lafiya ta amsa mashi da shi, "My Name is Aseef what of you?" Farinciki yasa bakinta ya ki rufuwa "My name is Rimsha" ta bashi amsa. "Wow Rimsha nice name, cos the way am seeing your face like you are under 15 years" Ya yi maganar yana tsareta da wayan nan brown eyes ɗin nasa, ba ƙaramin mamaki Imran ya sha ba, dan ya san halin Michael sarai lokacin da suke school, amma ya akayi yau yake magana da Rimsha haka? Abin da bai sani ba shine ƙwaƙwalwar Michael ta da da ta yanzu ba ɗaya hace, da kamar ma za'a ce ba shi bane, yanzu kuwa shine, cikakken mutun mai imani da natsuwa, yanzu ne ainahin wanene shi ta bayyana. "Yah Yaya Aseef am under 15 years, am 14 by age" Shiru ya yi yana tunanin shekarun Lion da nata shekarun, anya kuwa hakan zata yi wu kuwa? Ya tambayi kansa, Areef ne ya katse shi da cewa "What are you thinking?". Ɗaga kai sama ya yi tare da juya manyan idanun nan nasa, kai a ɗage ya dawo da kallonsa kan Areef ɗin, ya kashe mashi ido ɗaya tare da ɗaga gera ɗaya kamar wasu munafukai, Areef bai san time da dariya ta suɓuce mashi ba, dan ya gano hanyar da Aseef yake, wato idan Allah ya ƙaddara abin da suke fata, na Lion ya yarda ya auri Rimsha zuwa ɗaya zai yi mata ba dawo sai dai a ɗauki gawarta, wato ta yi mashi karama, hakan yasa Areef satar kallon ta, ita kam ba abun da ta gane, tama yi kasa da kanta tana wasa da yatsun hannunta. Dawo da kallonsa kan Aseef ɗin ya yi har lokacin yana ɗage da kai sama yayin da idanunsa kuma suke a gefe yana kallon Areef ɗin, da larabci Areef ɗin ya fara magana bai san cewa Rimsha tana jin larabci ba, ba kuma ya son ta ji abin da suke cewa ne, shi James yana jin yaren china amma Michael baya ji, larabcin ma James ɗin ya mance ne Michael baya ji, sai yana yi mashi kamar tare suka koyi komai. "Kai Areef baka da kirki, me yasa zaka yi wannan tunani, ai zata girma...." Bai karisa maganar ba Aseef ya dakatar da shi da cewa "Which kind of language is this?". Shafa fuskarsa ya yi sai lokacin ya tuna ashe Aseef fa yanzu yake koyan karatu, hakan yasa ya dawo magana da English ɗin kawai, tun duk wani baƙon yaren da yake ji Aseef baya ji sai English. "My blood tayi ko? Kana ganin ta dace da Lion?" Cikin sauri Aseef ya jinjina kai yana faɗin "Yah sosai ma, saboda shi is so beautiful and she have innocent face, the way am looking at her like she is so silent, zata iya hakuri da mu, you knew yanzu wadda zata iya hakuri da mu ne muke buƙata, but seriously i pity her more than your expectations, saboda magana ta gaskiya you knew mu da muke TRIPLETS nasa ma, bamu taɓa gane ina ya dosa, kullun a murɗe yake, yana cikin gindayar da mutane, duk duniya ba wanda yake iya cankan ga abin da zai yi ko wanda ba zai yi ba, sai kana zaton shi a nan sai ka ga ya ma wuce nan, to be honest zata sha bakar wuya, ni for my on bana ji a jikina Lion zai bari ta zauna kusa da shi ma, bana jin wannan abin zai yi wu, amma anywhere shawarar da zan baku dai a nan ita ce, kada ku sanya yarinyar nan ta je kusa da shi ya yi mata kisan farat ɗaya, ku ɗauki alhakinta banza, wlh ni na sani idan ba wani kwakwaran dalili, kai in jin ko harbina da bindiga aka zo yi ta tare mani Lion ba zai barta a kusa da shi ba, ba zai yarda da ita ba, ko me zata yi mashi, amma zan taya ku thinking na wani solution ɗin wata kila mu dace, kuma ku yi tunani mai zurfi kada ku zo ku yi dana sani, for my on choice yarinyar ta yi sosai" dawo da kallonsa kanta daga kan Areef ya yi ya cigaba da cewa "My sister kin dai ji abin da na faɗa, iya gaskiya na gaya, ni bana karya, so is better for you ki iya takunki, ki ɗauki action mai kyau, dan bana son mu rasa wannan innocent face ɗin naki, ina ga ko daddy bai yi wa Lion irin sanin da ni na yi mashi ba, saboda ni nafi zama tare da shi, ko Areef ba zai gaya mani asalin wanene shi ba, duk da cewa nima ban san shi ciki da waje ba, dan ba komai zaka iya ganewa a tattare da shi ba, amma na san abubuwa da dama shiyasa kika ji na faɗi haka, so ki kula, idan da son samu ne ma, ki yi zaman ki sai na zo Nigeria sai mu san abin yi". Areef ne ya tari numfashinsa da cewa "Yah Aseef abin da ka faɗa dukka gaskiya ce, ni kaina da abayane kace mani zan iya zama da mace haka mu yi hira, wlh zan ce karya ne kuma never in my life, so amma musulci ba wasa ba, In Sha Allah Lion zai so ta, ya yi aure muma mu yi aure, mu cika addininmu, amma na san ba nan kusa bane, yanzu ma abin da muke so ai ba zai ko kusan samuwa ba, shiyasa nace mata kada ta bari hanya ya rinƙa haɗa su, ta bari sai na sami lafiya, idan na sami lafiya shikenan, zan iya shiga ɗakin sa na kwanta kuma na kirata ta kawo mani abu, ko ta zo kuma ba zai ce komai ba, saboda kasan baya shiga abin da bata shafe shi ba, idan muna tare zan iya kiranta ba zai yi magana ba, amma yanzu dai bari na sami lafiya first". Jinjina kai Aseef ya yi yana faɗin "Shawara mai kyau, hakan ma ya yi, kuma dama shiyasa nace ta bari sai nazo Nigeria, Lion baya kallon mutane da abubuwa, abin da yake gabansa kawai yake yi, amma ina da tabbacin idan tana yawan zama kusa da mu, wata rana dole zai so ganinta, kuma dole zai samu kwanciyar hankali a tattare da kasancewar a gidan, saboda idan ya ga muna tare da ita, zai ce e lallai tana da kirki, kuma zai so sanin wace ce ita da har muke tare da ita haka, zai yi bincike a kanta ko da bai gaya mana ba, kuma ina fatan daga nan shima zuciyarsa zata aminta da ita". Jinjina kai shima Areef ya yi alamar gaskiya Aseef ya faɗa. Kada ku mance duk wannan magana da suke yi, suna yi wa Rimsha kallon a matsayin kanwar Imran uwa ɗaya uba ɗaya ne fa, to ya kenan idan suka ji cewa shima Imran tsintota ya yi? Ba abin da ya haɗa su kuma bai san ina ƴan uwanta suke ba, kuna tunanin za su yarda da ita kenan? Kuna tunanin za su bari ɗan uwansu ya aure ta? Saboda fa kirkin Imran yasa suke sonta, dan kun ji sunce Imran mutumin kirki ne, suna son shi fiye da tunanin mai tunani, a cewarsu dukka family Imran mutanen kirki ne kamar shi, BABBAR MAGANA. Miƙewa Imran ya yi ya nufi waje dan Akil ya kira shi yana kofar gida ya kawo kayan Rimsha. Bayan ya karɓo ya dawo ne ya zo ya ce mata ta tashi ta je ta shirya zuwa school, to ta amsa mashi da shi, tare da yi wa Areef sallama da fatan samun lafiya sannan ta wuce ta barshi suna hira da Aseef nasa. A gurguje ta yi wanka ta shirya cikin abaya blue color tare da hijabi ba mayafin rigar ba, time ya tafi almost 8:5 yanzu, sun zauna hira da su Areef, Imran ma bedroom nasa ya wuce dan ya yi wanka ya shirya ya zo ya kaita school. Bayan ta gama shiri ne ta fito palo, wani irin nishaɗi ta ji lokacin da hancinta ya shako mata daddaɗar kamshin perfume nasa, da alama ya wuce a palon, zama saman sofa ta yi tana rataye da hannu ɗaya na school bag ɗin ta a kafaɗa, ga hijabinta har kasa launin blue kalar rigarta, ta yi kyau sosai, ba wani make up ko kaɗan a face nata, soft skin ɗin nan nata sai wani sheki yake yi, colan skin ɗin nata ya kara fitowa sosai, sai wani murmushi take yi ita kaɗai zaune shiru, idan ta tuna maganganun Aseef in da yake cewa mawuyacin abune Lion ya barta ta matso kusa da shi, sai ta ji gabanta na faɗu wa, me yasa kowa a cikin shawarar da zai bata sai ya ce mata kada ta haɗa hanya da shi? Ta tambayi kanta a cikin zuciyarta. Bata kai ga samin amsar tambayar ba Imran ya fito yana faɗin "Let's go". Shirye yake cikin manyan kaya na wani haɗaɗen yadi mai kyau coffee colar, kayan sun mashi kyau sosai, shima yana da kyakkyawar saje irin na daddyn Jelly, daga wajen bakinsa kuma akwai kewayayyen gashi mai kyau sosai a wajen, kamar dai daddyn Jelly. Gaba ya yi ta bi bayansa, a palon kasa suka hango Lion saman dining table yana latsa laptop ga kuma kayan abinci a gabansa, amma bai fara ci ba, sojan dake yi masu girki ne tsaye akansa yana jiran umarni kawai ya zuba mashi abincin. Shirye yake cikin wasu shegun tsadaddun kaya, wandon jeans ne ask color mai bala'in kyau, daga ta sama kuma high neck t-shirt ne white color, rigar ta kama jikinsa sosai hakan yasa kakkarfar surar jikinsa daga ta sama ta bayyana, ya ɗaure kyakkyawar gashin kan nan nasa a baya, kamar dai kullun wannan guntu na gaban goshin nasa yana nan, while face nasa na sanye da black glass mai bala'in kyau, idan kaga lips ɗin nan nasa, sai ka rantse da Allah yasa lips stick, har wani kyalli suke yi saboda yana ɗan ciza su time to time, gaba ɗaya kamshin perfume nasa ne ya gauraye gaba ɗaya cikin palon. Rimsha da aka ce kar tana yawan kallonsa, amma ta kasa ɗauke idanunta daga kanshi, sai kallonsa take yi sosai, ji take tamkar ace ya zama nata, shi kuwa yana fuskartar gefe bai ma san suna yi ba, ya dai san mutane sun shigo palon, amma bai nemi sanin koma su waye bane. Kasa kasa Imra ya ce mata ta je ta yi sallama da Areef yana zuwa bari su yi magana da Lion, to ta amsa mashi da shi sannan ya nufi ɗakin Areef ɗin, tana tafiya tana waigo Lion, ba ƙaramin tafiya da imanin ta ya kara yi ba, ya ruɗa mata kwakwalwa yau ɗin nan sosai da sosai. Tana shiga ta sami Areef ya gama magana da Aseef yana latse latse a wayar Lion ɗin, daga ɗan gefa ta tsaya tana gaya mashi zata tafi school, dawo da kallonsa kanta ya yi kafin ya ce "Okey waye zai kai ki?" "Yaya Imran" ta bashi amsa. Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Idan ya kai ki dawowa yake yi ko?" Jinjina mashi kai ta yi alamar e, girgiza kai ya yi kafin ya ce "Haka ba zai yi wu ba gaskiya, dole ki samu tsaro sosai, saboda yanzu ke ba kamar sauran mata bane, nasan ba za'a rasa maza masu karan kwana da zaku yi maki magana ba, ni bana son haka, komai namu saboda ne wadda mu kaɗai muke fara amfani da shi, dan haka Lion ma sabuwar mace za mu sama mashi wadda ba wanda ya isa ko da sunan wasa ya yi gigin yunkurin tinkarar ta bare ma har ya ce yana sonta, bari Prof ya zo, sojan dake bakin gate ya kai ki school, Prof ya je ya nuna mashi school ɗin, kuma ya yi gadin ki sai an tashi ya dawo da ke, zan gayawa Lion ya karo wasu sojojin guda biyu wadda za su rinƙa tsaron bakin gate ɗin, daga yau wancan ya zama mai tsaron ki, kuma nasan a wannan gaɓar Lion zai yarda, domin ya sani cewa duk wanda yake tare da mu, idan bamu ba shi tsaro ba mun ɗauki alhakinsa, kuma ma yasan wannan dokar mu ce, kuddin mutun yana a karkashin mu to yana cikin tsaro". To ta amsa mashi da shi tare da yi mashi godiya. Tana rufe baki sai ga Imran ya shigo bakinsa ɗauke da sallama. Kusan a tare ita da Areef suka amsa sallamar, kamar yadda ya gayawa Rimsha haka ya gayawa Imran, haka kuwa akayi, da sojan suka tafi, sai bayan sun tafi ne da Lion ya shigo karɓar wayarsa a hannun Areef ɗin, a nan ne yake sanar da Lion alfarman da yake nema, yana son abar wancan sojan ya rinƙa bawa sister Imran tsaro, shiru Lion ya yi bai yi magana ba, har ya gama abin da zai yi, zai fita ne sai ya ce "Idan sojan ya dawo ka sanar da shi nan da leƙa waje ban yarda ya sake yi ba, nan ba kasar su Prof bane? Before sister tasa ta zo nan waye ya ke bata tsaro? Ko a ƙarƙashin mu take ne? Idan ka sake yi mani irin wannan ranka zai ɓaci, ai ba a karkashin mu suke ba bare mu basu tsaro" Ya kai karshen maganar tare da ficewa abinsa. Sai lokacin Areef ya tuna ashe ba kasar su ba ne, kuma ashe basu cike takardan zama a karkashin su ba, tunani ya fara yi ta yadda zai samawa Rimsha wannan takarda ta cike, idan ta cike shikenan tana karkashin kulawar Lion, ba zai bari wani abin ya same ta ba, addu'a ya fara yi Allah yasa Lion ya zo da takardan, idan ya zo da takardan wlh sai ya ɗauko mata ta sanya hannu ko me zai faru, lokaci guda kuma wani tunani ya faɗo mashi, ina maman su Prof take da har ta bar sister Prof a nan, da ya ke kuma su yin hakan ma ba wani abu bane a wajen su, sai bai wani damu ba, bai kuma kawo komai a ransa ba, ya san su a wajen su ma yarinya tana iya barin gidan iyayen ta koma gidan saurayinta ta zauna, kuma iyayen suna gani ba wani action da za su ɗauka akan hakan. Tunani cike fal ransa har barci ya yi awon gaba da shi. Imran kuwa suna fita sai da suka sayawa Rimsha abin da zata yi breakfast da shi, sannan ya bata 1k lokaci ya kure sun zauna hira da Areef bata yi girki abin da zata ci ba, tun da bata iya cin nasu ba. Bayan sun je school ɗin Imran ya dawo ya barsu ita da wannan sojan a school ɗin, kowa sai kallonta yake yi, kowa yana son sanin wace ce ita, da soja yake gadin ta, sojan ma kuma Bature ga shi fari tas da shi kyakkyawa mai kirar jarumai, daga student har malamai sai kallonsu suke yi. Da lokacin shiga class ya yi, har cikin class ɗin sojan ya shiga, ya zauna a kujeran da malami yake zama yana fuskartar ɗaliban, fuskar nan tasa babu alamar wasa ko kaɗan, shiyasa gaba ɗaya ɗaliban suka razana, class ɗin ya yi tsit tamkar babu kowa, ga Rimsha yar firitu agab shi, dan bata kai kirjinsa tsawo ba, da kaɗan ta ɗara cikinsa tsawo, amma a haka yake bata tsaro, duk in da ta je yana biye da ita, kai Allah ka bamu arziki mai albarka. A ɓangaren su Ayla kuwa, yau zata fara zuwa school, sosai mijinta ya shirya ta, kamar yadda yake shirya jelly ta tafi school haka ya shirya ta ita ma, ta yi kyau sosai, shima ya shirya cikin wata haɗaɗɗiyar yadi ash color, ya yi mashi kyau sosai da yake yana da haske. Da farko ma cewa ya yi shi zai yi mata girki tayi breakfast, dan akwai kitchen a part ɗin nasu, amma sai Aunty ta rigashi ta aiko masu da abinci, ba dan ya so ba, ya zuba mata girkin Auntyn tayi breakfast sannan suka fito suka nufi cikin gida, sun jero kamar wasu taurari. A bakin kofar shiga palon su Abbi suka yi karo da Irfan yana fitowa, har wani faɗuwar gaba ya ji ganin su da ya yi a tare, bawan Allah har yar rama ya yi, kakalo mirmishi dole ya yi tare da miƙawa daddy hannu yana faɗin "Barka da safiya bappa". Da fara'a daddy ya miƙa mashi hannu yana faɗin "Irfan baka da lafiya ne?" Girgiza kai ya yi kafin ya ce "A'a bappa lafiya ta lou, yanzu shiga na ciki ma sai da Sadiya ta tambaye ni ko bani da lafiya ne, wai me kuka gani kuke tambaya tane?". Ayla ce ta caɓe zancen da cewa "Yaya Irfan ka rame ne mana, ina kwana?" Dogon numfashi ya ja tare da sauke wa a hankali kafin ya ce "Lafiya lou Aliya kin tashi lafiya?". Lafiya ta amsa mashi da shi, sai wani kauce masu yake yi, baya son ganin fuskar Ayla, shi kuma daddyn jelly ya tsai da shi akan lallai sai ya gaya mashi menene yake damun sa, kafewa ya yi akan lallai shi ba abin da ke damun sa, haka suka hakura suka kyale shi ya wuce su kuma suka shige cikin palon. Zaune suka isko Aunty saman dining table, cikin zolaya daddy ya ce "Sadiya kina cin ye mani kuɗi sosai fa, yanzu tun ban tashi barci ba kin haye saman table kin fara ciye ciye ko? So kike yi ki ja mani wata matsala ko? Wai ba ance kada ki rinƙa cin abubuwa masu nauyi ba har sai kin kara samun sauki ko? Shine kike ta ɗurawa da sanyin safiya salon ki jamin sake mai daki asibiti na kashe kuɗi na ko?." Hararar wasa ta wurga mashi kafin ta ce "Kai da nake renonka ɗin ne zaka yi mani wata magana? Ni fa yanzu Aunty babba ce, ka zama kanina Yaya Maik tun da ka kame mani yar kanwata ka shige da ita part naku na zama aunty babba". Harara shima ya wurga mata da manyan idanun nan nasa yana karisawa wajen table ɗin, "Ina kwana?" Ta faɗa tana murmushi. "Yanzu kenan kika tuna da gaisuwar ko? To ni dai kin shirya wa matata lunch box nata ne, ko kuma in shiga kitchen da kaina?". Kai kallonta kan Ayla dake tsaye ta sunnar da kai kasa ta yi, sai wani ƴan kame kame take yi, "Yaya Maik yanzu ni da nake Aunty babbama ni ce zan shirya maku lunch box ko?" Ɗaukar apple ya yi kwara ɗaya ya wuce ya nufi kitchen yana faɗin "Da dai ban iya girkin bane da sai ayi mani rigima, amma tun da na iya matata ta wuci gori". "Eyeee irin wannan soyayya haka? To ni dai dawo na shirya mata, ai na san yau zata je school, dan haka na shiryawa yar kanwata komai da komai, Ayla wai kame kamen me kike yi ne? Ki je kitchen ki ɗauko box ɗin naki mana". To ta ce tana ƙoƙarin nufar kitchen ta jiyo voice nasa daga ciki yana faɗin "No bari na ɗauko mata da kai na, sai ma na binciki me a ciki tukun nan, dan ita ba komai zata ci ba yanzu". Murmushin kawai Aunty ke yi ta ce da Ayla ta zo mana me ya tsai da ta a can, ba musu ta kariso wajen table ɗin cike da kunya suka gaisa, cikin raha kasa kasa dan kar daddy ya ji Aunty ta ce "Ke jiya da kika wani ce mani daddy da zafi baki ji kunya ba sai yau ko? A lallai yarinyar nan". Ta kai karshen maganar tana dariya. Ita kuma Ayla hannu tasa ta rufe fuska tana tunanin a yaushe ta ce wa Aunty daddy da zafi kuma, bata san cewa a gigin barci ta yi maganar ba. Lunch box ɗin ya ɗauko ya fito yana faɗin "Ina yaya Deen?" "Yana barci bai tashi ba" Aunty ta bashi amsa. Hararar ta ya yi kafin ya ce "Ke kuma har kin tashi kin haye saman table ko?" "E mana ka sani ko dalili ya sanya ni hawa saman table ɗin? Kai ma fa yaya maik wlh wasa wasa ka iya sa ido". Ɗan zaro ido ya yi kafin ya ce "Serious fa abin da nake tunani ne ya saki cin abinci da sassafen nan? Ba likita ya ce ba zaki sake iya ɗaukar ciki ba?". Guntun tsaki ta ja tana turo baki ta ce "Da farko dai ban san me yasa nake jin yunwa safe da dare daga jiya zuwa yau ba, na biyu kuma likita bai isa ya yanke hukuncin abin da ya shafi Ubangiji ke bayarwa ba, Allah ke bada haihuwa ba wani ba, so babu likitan da ya isa ya ce ba zan haihuba ko zan haihu, wannan hurumi ne na Aarahman". "Haka ne zancen ki gaskiya, to Allah dai yasa abin da muke tsammani ne, mu dai mun wuce sai na dawo" ya faɗa yana barin wajen table ɗin tare da riƙo hannun Ayla da ɗayar hannunsa ɗayar kuma ya ruƙe mata lunch box ɗin suka fice daga palon, da kallo Aunty ta bisu har suka fita, sai fatan Alkhari take yi masu a zuciyarta. Yau ma kamar daren jiya, da motar Abbi suka fita, tana zaune a front seat ta kwantar da kanta tana kallon hanya. "Me babyn daddynta take tunani ne?" Ya tambaya yana kallonta ta cikin mirror motar, dawo da kallonta kan shi ta yi tana murmushi, "Daddy kai nake tunani mana". "Da gaske?" Ya yi maganar cike da jin daɗi, kuma ya yi magar daidai lokacin da ya ɗauki titin makarantar tasu. "E daddy da gaske kai nake tunani". Cool murmushi ya saki tare da jawota jikinsa yana kara gudun motar dan su isa da wuri ya samu ya rungumeta da kyau. A kuwa cikin ƙankanin lokaci suka isa makarantar, yana kashe motar ya rungumeta da kyau a jikinsa yana faɗin "Baby zan yi kewarki sosai wlh, yanzu sai fa karfe ɗaya zaki dawo, kai anya zan iya kuwa?". Tana daga lafe a kirjinsa ta ce "Daddy nima fa ina jin kamar ba zan iya jimawa ban ganka ba". Wani irin daɗi ya ji burinsa ya fara cika, haƙarsa ta fara cin ma ruwa, ɗago haɓarta ya yi tare da haɗe bakinsu waje guda, nan take suka shiga bawa juna hot kiss. Sun shagala da kiss na juna agogon dake ɗaure a hannunsa ta buga mashi karfe 8 ya yi, da kyar ya iya zame bakinsa daga nata tare da sake ta yana faɗi "Muje na kai ki". To ta amsa da shi, kusan a tare suka fito suka nufi cikin school ɗin. Cikin ƴan mintunan da ba su wuci goma ba ya gama komai ya fito ya shiga motarsa zuwa gida ya bar ta a school ɗin, har ga Allah yana kewarta fiye da tunanin mai tunani, haka ya koma gida ya kwanta cike da damuwa. After some hours 👌 Gidan Lion. Bayan Rimsha ta dawo daga school, tare da sojan nan, cikin gida ta nufa kafin ta shiga bedroom nata Imran ya dakatar da ita ya ce ta shirya da wuri su je gidan babbansa su yi wa daddyn Jelly murna ya yi aure. To ta amsa da shi, cike da zumuɗi ta shige cikin bedroom nata. Tsabar murna zata fita anguwa a gurguje ta yi wanka ta shirya cikin wasu riga da wando masu ɗan karen kyau, rigar pink color ce zuwa gwiwarta ya tsaya mata kamar Pakistan, yayin da wandon kuma ya kasance fari tas mai stones a jiki, wandon dai pencil Jeans ne, while shi kuma rigar yana da ɗan faɗi daga ta kasa, da ta saman shi kuma ya kamata, gyalen kayan fari ne tas kalar wando, light make up ta yi ta gyara gashin kanta tare da ɗaure shi a tsakiyar kanta, sai tashin kamshi take yi, zubawa hannunta ido ta yi tana kallon yadda lallen hannun nata ya rage baki yake ƙoƙarin gogewa, da yake tana taɓa ruwa sosai, tunani ta fara yi dole yau ko gobe ta ce yaya Imran ya kai ta ayi mata wani. RIMSHA SARKIN SON LALLE DA GYARAN JIKI Da wannan tunani ta ɗauko farin hijabi daga cikin trolleynta ta fito Palon. Babu kowa a palon, haka kawai ta ji cewa tana son ganin ɗakin Lion ɗin nan, ba ko tsoro ta lallaɓa izuwa bakin kofar ɗakin, bata kai ga leƙawa ba ta ji motsin Imran yana ƙoƙarin fitowa daga nasa ɗakin, da yake kusa ne hakan yasa ta ji motsin nasa. A sukawane ta gudu ta koma saman sofa tana sauke ajiyar zuciya, Malika ce ta bayyana a gefenta tana faɗin "Ke Rimsha bakya jin magana ko? Wlh da kin leƙa ɗakin nan da yau kun yi ido huɗu da shi, domin kuwa yana zaune yana fuskantar kofar shigowa, da kuma hakan ta faru..." Bata kai ga karisa maganar ba ta ɓace abinta, dan ta isar da saƙon da take son isarwa, kuma ba sai ta karisawa Rimsha abin da zai iya faruwa ba idan da ta leƙa ɗakin, ta sani ita da kanta. Tana ɓacewa kuma Rimsha ta fara jiyo muryan Imran dake tsaye a ƙanta yana faɗin "Muje mana ina ta yi maki magana kin yi shiru". Yar firgita ta yi tare da miƙewa tsaye tana faɗin "Kayi hakuri yaya Imran". Ba komai ya ce mata tare da wucewa gaba ta bi bayansa. Ɗakin Areef suka fara shiga, yana zaune ya jingina da jikin headboard na gadon, yau ya sha wanka, har wani kyau ya kara, hasken fatarsa ta kara bayyana, yana sanye da singlet fara tas da shot, sai dai ya jawo bargo ya rufe cinyoyin sa, ba ƙaramin razana da kallon kyakkyawar surar jikinsa Rimsha ta yi ba (ni ko na ce dan ma baki ga na Lion ba, ai da sai suma!) Ta razana sosai, har wani kerma jikinta yake yi, shi kuwa zuba masu ido ya yi yana kare mata kallo, dan ɗazun yana kwance bai kalleta sosai ba. A cikin zuciyarsa ya ce kai ashe karama ce sosai, tab akwai aiki a gabansu. Gefensa Imran ya zauna yana tambayar shi ya jiki, da sauki ya amsa, ita ma ta gai da shi, fuska ba ya bo ba fallasa ya amsa. Sanar mashi da in da za su je Imran ya yi, shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Da ina da lafiya ai da munje tare" murmushi Imran ya yi ya ce "Ba komai idan ka samu lafiya zamu je, zai kai ka wajen dukka yan uwana" Sosai ya ji daɗi dan ba ƙaramin so yake yi wa Imran da ƴan uwansa ba, duk da bai san kowa daga cikin su ba, daga Imran ɗin sai Rimsha da yake yi wa ganin kanwar Imran ɗin ce, amma duk da bai san su ba, yana bala'in kaunar su sosai. Sallama suka yi, suna yi mashi Allah ya kara sauki, shi kuma yana yi masu adawo lafiya, da haka suka wuce. Da motar Imran ɗin suka tafi, a hanyane ya ce mata "Rimsha kina da farin jini sosai da sosai kowa son ki yake yi, kina burge duk wanda ya zauna dake" murmushi kawai ta yi ba tare da ta yi magana ba. "Kina jin yunwa ko?" Ya tambaya yana sauƙa daga kan titin da suke zuwa na gidan su Abbi ɗin. Gyaɗa mashi kai tayi alamar e tana jin yunwa "To ki yi hakuri, an shirya mana abin ci a gidan Bappa zamu je mu ci, su Akila ma duk Akil ya kai su tun karfe 12 na rana, yanzu mu kaɗai suke jira". Wani irin daɗi ta ji, zata haɗu da Akila da Umaisha. Suna isa gidan tun bai gama kashe motar ba ta fito, dan ita burinta kawai ta ga su Akila. Tsayuwa ta yi tana jiransa har ya kashe motar ya fito suka jera izuwa cikin gida. Tun a bakin kofar palon suke jiyo hayaniya alamar suna haɗe a palon kenan, Imran ne a gaba tana bin shi a baya. Da sallama ɗauke a bakinsu suka shiga cikin palon, wani ihu Ayla dake zaune kusa da daddy ta kurma tare da miƙewa ta nufeta tana faɗin "Rimsha!! Rimsha kece?!!" Ita ma Rimsha ihun sunan Ayla ɗin ta yi suka rungumi juna suna dariya kamar zautattu. Malika dake tsaye a bakin kofar shigowa ba wadda ke ganin ta dan bata bayyana a yadda za'a ganta ba, da ɗan karfi ta ce "Rimsha ki ɗan yi nisa da Ayla dan kada wannan bala'in ya taɓa ki" a razane Rimsha ta zaro ido tana kallon ta. Malika ta gane cewa karin bayani Rimsha ke so, dan haka sai ta ce "E abin da kika ji haka ne, akwai wadda ta bawa wani boka aiki shi kuma ya sanya aljanu yan uwa na yin wannan aiki, ba za su iya taɓa wadda aka ce ayi wa aikin ba, yana da riƙo da askar masu karfi, dan haka kan Ayla za su sauke wannan aikin nasu, bana son ki yi kusa da ita dan zata iya mutuwa akowani lokaci k..... Sai mun haɗu Monday idan mai dukka ya kai mu 💖💖TRIPLETS💖💖 E 69-70 Malika ta gane cewa karin bayani Rimsha ke so, dan haka sai ta ce "E abin da kika ji haka ne, akwai wadda ta bawa wani boka aiki shi kuma ya sanya aljanu yan uwa na yin wannan aiki, ba za su iya taɓa wadda aka ce ayi wa aikin ba, yana da riƙo da askar masu karfi, dan haka kan Ayla za su sauke wannan aikin nasu, kuma kinsan a cikin aikin ma har da wadda duk macen da ta raɓe shi da sunan soyayya zata mutu, bana son ki yi kusa da ita dan zata iya mutuwa akowani lokaci, ko kuma wani mummunar abin ya sameta". Nan take Rimsha fara hawaye abin ya taba ta sosai da sosai, da yake sun jima suna kewar juna sai kowa ya yi tunanin kukan ɗaɗin haɗuwa da yar uwar tata take yi. Ita kuma tana son tambayar Malika amma tana tsoron yin magana kada su yaya Imran su yi mata kallon mahaukaciya tun da ba kowa ke kallon Malika ɗin ba. Ganin tana kuka ne yasa Imran ya sanya hannu ya raba ta da jikin Ayla ɗin, sai murmushi Ayla ke yi bakinta yaki rufuwa, ita kuma Rimsha wannan murmushi da Ayla ke yi, yana kara tayar mata da hankali ba kaɗan ba. Gaba ɗaya family suna haɗe a Palon, mazan sun yi shigar mayan kaya matan kuma abayas, Abbi, daddy'n jelly, Aunty, Irfan, Akil, Akila, Umaisha, Aafia, Ayla amarya, a gaba ɗaya ƴan gidan, Hajiya Khadijat ne da kuma Hanan sune basu a waje, ita Hajiya Khadijat ma bata gidan, ta tafi gidan Ummin Nawid wuni, ita kuma Hanan tana wanka. Akila ce ta taso ta rungumeta tana rarrashinta, a haka suka karisa cikin palon suka zauna, saman sofa ɗaya Ayla da Rimsha suka zauna, while daddyn Jelly na gefensu, Aafia baiwar Allah da yake tana samun kulawa sosai wajen Akil har kumatu ta yi, saɓanin a gidan nasu da bata gaba bata baya, kullun a yadda take, ba cigaba, amma yanzu Akil na kula da ita sosai, hakan yasa kaso 70 cikin 100 na damuwar da take a ciki na rabata da budurcinta da aka yi ta ragu mata, a yanzu dai ta dai'na yawan tunanin sosai, ta fawwalawa Allah komai, ta dukufa da karatun dake a gabanta, Amarya Umaisha kam ba'a magana, dan ƙibar da ta yi ma a yan kwanakin nan ba kaɗan bane, kumatun nan sun ciko sosai, da yake dama tafi Aafia diri da kuma kiɓa, ita kuma Aafia ta fita tsawo, Umaisha akwai hips da breast sosai kamar Rimsha da Akila, su ukun nan shape nasu kusan ɗaya, sai dai wadda ta fi ƙiba a ciki afi yawan ganin nata. Sai hira suke yi cike da annashuwa da farinciki, suna ta gaggaisawa da juna, ita kuma Hanan tana wanka, bata fito ba. Daddy'n Jelly bawan Allah tunanin Jellyn sa kawai yake yi, ga ƴan uwanta sun haɗu amma bata nan, abin sam bai yi mashi daɗi ba, ya jefa shi cikin tunani. Kasa hakuri Rimsha ta yi dan tana son yin magana da Malika, dan haka sai ta miƙe tana faɗin "Yaya Imran ina zuwa zan je wajen mota na dawo". Bata jira amsar shi ba ta fice da sauri abinta. Tana fita Aunty ta fara tambayar a ina Imran ya samo yarinya kyakkyawa haka, wato magana suke akan Rimsha, bai ɓoye masu ba, ya gaya masu gaskiya yar Nawazudden ce, nan fa daga Abbi har daddyn Jelly suka fara godiya ga Allah da ya kawo masu ƴar Nawazudden har cikin gida, ashe da rabon su ramawa Nawazudden abubuwan alkhari da ya yi masu, ba ɓoye ɓoye da yake bappanun sune, hakan Imran ya fara basu labarin irin wahalar da Rimsha da Ayla suka sha kamar yadda Rimsha ta gaya mashi. Duk cikin palon ba wanda bai matsa masu kwallaba, nan fa daddyn Jelly ya kara ɗaura ɗamarar kula da amaryarsa sosai, dan tasha wahalar rayuwa ba kaɗan ba. Ita kuwa Rimsha tana fita waje ta fara ƴan waige waige tana neman Malika, can jikin motar Imran ta hangota tana tsaye ta harɗe hannu a kirji tana ɗan murmushi kamar kullun. Da sauri Rimsha ta karisa wajen ta. Cike da tashin hankali ta fara magana "Malika menene yake faruwa? Dan Allah ki gaya Mani, wlh idan Ayla ta mutu zan iya shiga tashin hankali da zai iya zama sanadiyar rayuwata, kin dai ga nima bani da lafiya ko? To dan Allah ki tausaya Mani, yanzu haka da karfi karfi zuciyata ke bugawa, kirjina ciwo yake yi mani, dan Allah ki ji tausayin mu Malika". Tana magana idanuwanta cike tap da kwallah. Matsowa Malika ta yi ta dafata tana faɗin "Rimsha bana son ganin ki cikin damuwa, bana son abin da zai taɓa ki, amma abin da na gaya maki akan Ayla gaskiya ce, ina son ki sani ba laifi na bane, kuma kema ba laifin ki bane, dan haka kiyi hakuri kamar yadda kika saba karɓar kaddarori da jarabobi to a wannan karon ma dagewa zaki yi ki karɓi mutuwar Ayla. Tashin hankali, wani irin duhu Rimsha ta fara gani yana gilma mata ta cikin idanunta, jiri ta fara gani mai karfi yana ɗebanta, wani irin juyi duniyar yake yi mata, nan take ta fara ƙoƙarin zubewa kasa a wajen. Cikin sauri Malika ta tareta tana faɗin "Rimsha kada ki faɗi, wai baki ji abin da Dr ya ce bane? Ko kin mance ne? Idan fa kika cigaba da sanya damuwa a ranki har kina yawan faɗuwa ki suma zaki sami paralyse, to dan haka ya kamata ki kula, ki zama mai karɓar kaddara a duk yadda ta zo maki, kuma ai ba ce maki na yi aikin ya kamata ba, bai kai ga kamata ba, a takaice ma bokan bai kai ga kammala aikin ba, so kinga akwai damar da za'a iya kuɓutar da ita, kin san fa wadda ta bada aikin cewa ta yi amata aikin da duk macen da ta raɓe shi da sunan soyayya to ta mutu, sannan kuma shi a sanya mashi son ta ita wadda ta bada aikin kenan, ita kaɗai zai so, to kinga aikin ba zai kama shi ba, ita kuma Ayla abin da yasa zai kamata ta mutu, saboda ta raɓe shi da sunan soyayya ne, dole aikin ya faɗi akanta. Cikin sauri har tana haɗe words ta ce "Yanzu dai Malika ki gaya mani taya ya Ayla yar uwata zata kuɓuta daga hannun wayan nan azzaluman?" A takaice Malika ta ce "E kuna da hanya biyu koma in ce ɗaya, domin ɗayar ba lallai ta yi amfani ba, bari na fara gaya maki wadda ba lallai ta yi amfani ba, askar, yin addua da zama da alwala shine hanya ta farko kuma shine ba zai yi amfani ba, abin da ya sa na ce ba lallai ta yi amfani ba, saboda Ayla ba zata iya ba, ba zata juri yi kullun ba, saboda bata saba ba, acikin askars da muke da su ma kwata-kwata guda uku Ayla ta iya, so yanzu ko kin ce mata ta rinƙa yi ba zata iya yin shi kullun ba, zata rinƙa mancewa, kuma Kinga bokan yana kan yin aikin, zai iya kammalawa ko wani time daga yanzu, wannan shine hanya ta farko, wadda ba zata yi wani amfani ba, hanya ta biyu wadda zata yi amfani kuma shine the best solution da kuke da shi a yanzu, domin daga yanzu zuwa ko wani lokaci bokan nan za su iya kammala wannan aiki, ina kara jaddada maki, wannan hanya dai ba wata bace fa ce a sami haɗuwa tsakanin Ayla da AbdulMalik, jininsu ya haɗu, ta haka ne za'a iya samin nasara, amma shima fa idan ba'a yi yadda ya dace ba ana iya samun matsala". Kwata kwata Rimsha bata gane irin haɗuwar da Malika take nufi ba, dan haka sai ta ce "Ai yanzu ma suna haɗe gida ɗaya, baki gani suna tare a palo bane? Ko dai ba AbdulMalik ɗin a cikinsu ne? Ko ba su bane ƴan uwan Ayla ɗin?". Nisawa Malika ta yi kafin ta fara bata labarin yadda akayi Ayla ta zo gidan da kuma wanene AbdulMalik sannan ta yi mata karin haske akan irin haɗuwar da take magana akai. Babbar magana shiru Rimsha ta yi tana tunanin ya za'ayi ta gayawa Ayla ga abin da Malika ta ce, kai ina hakan ma ba zai yi wu ba, to waye ya dace ta gaya mawa?. Ganin haka yasa Malika ta saketa tana faɗin "Kiyi tunani mai kyau, ki nutsar da brain naki, ki ceci kawar ki ƴar uwan ki, na barki lafiya zan je gida, amma zuwa gobe zan dawo". Tana kai karshen maganar ta ɓace ɓat, hakan kuma ya yi daidai da fitowar Imran, dan ya ji ta shiru, ita da ta ce tana zuwa yanzu, amma shine ta je ta jima haka, shine ya fito duba ta, bayan shima ya gama gayawa su Abbi wacece ita ɗin. Ganin ta wani sukuku ya sa ya tambayeta ko lafiya, me ya tsayar da ita a wajen nan?. Ta kasa magana sai dai ta yi gaba ya bi bayanta, ta rasa waye zata fara tunkara da wannan maganar, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, wannan ba magana ce da zata faɗu ga kowa ba, ta ya za'ayi ta fara tunkarar wani ta ce mashi me to? Ta ce tana son daddy'n jelly da Ayla su yi kwanciyar aure ne ko kuma dai me? Wannan magana tafi karfin ƙwaƙwalwarta, Malika ta kai ta ta barota a wannan fannin kam. Suna shiga palo daddy'n jelly da Abbi har suna haɗa baki wajen cewa "Zo nan Rimsha" abin ya bata mamaki, ya akayi suke mata wannan kira haka har suna haɗa baki, bayan kuma ɗazun da ta shigo banda mirmishi da suke yi mata, ba su wani kulata sosai ba. Kusa da Abbi ta je ta zauna ta kasa wani motsin kirki kirjin ta sai dukan uku uku yake yi, wannan magana tafi karfinta, waye zata sanarwar? Ko Imran ɗin ta sanar wa ba zai iya tunkarar daddyn Jelly da maganar ba, magana ce wace girmanta ya fi karfin katon dutse, har gara ɗaukar katon dutse akan furta ta, ko abokan juna yana da wuyar furtawa a tsakanin su bare kuma ace ta gaya wa Imran shi kuma ya gayawa bappansa, to ta ina ma zaa fara? Su ce mashi ya kwanta da Ayla ne ko dai yaya?. Wanann shi babbar magana. Su kuwa banda mirmishi ba wani abin da suke yi, sai hira ake zubawa, cikin dabara Irfan ya kira Akila akan ta zo ta raka shi waje, suna fita su Imran suka fara gulmarsu suna dariya. Aunty ce ta ce kowa ya zo su haye saman dining table aci abinci, Akil ba kunya ya ce shi a kasa zai zauna ya ciyar da babynsa a baki, a saman table ɗin nan ba zai ji daɗin bata abaki da kyau ba, salati Aunty ta yi tana tafa hannu, hararar ta daddyn Jelly ya yi yana faɗin "To zaki fara saka wa mutane ido ko? To wlh ki fita tun wuri, yau gabaɗayansu ma a nan za su kwana". Abbi ne ya caɓe zancen da cewa "Maik ina rabaka da shiga harkar matata! Ka kiyaye ni tom, idan ba ka yi wa Halima biyayya ba zaka shiga wuta!". Gaba ɗaya palon suka sa dariya, Aunty kuwa har da kara bubbuɗe hanci ita a dole matar yaya babba ce. "Yaya Deen da gaske Sadiya ƴar sa ido ce, yanzu ba ga shi daga zuwan su Akil har zata saka masu ido ba". Hararar shi Abbi ya yi yana faɗin "Ina Hanan ɗina ne? Naga kowa ban ganta ba". Aunty ne ta ce "Hanan tana ɗaki tana wanka" jinjina kai Abbi ya yi yana faɗin "Gobe za mu je gidansu In sha Allah, idan muka dawo kuma kinga na haɗa yara uku kenan". Ɗan zaro ido Aunty ta yi yana faɗin "Ƴara uku kuma? Waye da waye?" Da hannu ya nuna mata Rimsha yana faɗin "Da Rimsha da Hanan ɗin da kuma Aliya". Cikin sauri daddy'n jelly ya ce "A'a yaya Deen ni zan ɗauki Rimsha gaskiya, ka bari ni zan riƙe ta, a waje na zata zauna kafin mu nemo su mummynta da ƴar uwarta, idan ya so kai sai ka riƙe ƴar uwar tata". Girgiza Abbi ya yi kafin ya ce "A'a kai da a yanzu baka da gida, kai ma fa riƙon ka nake yi tukun nan". Dariya Aunty ta yi tana ƙoƙarin yin magana Akil ya rigata da cewa "Aunty wai ina abin cin ne? My wife tana jin yunwa". Miƙewa Aunty ta yi ta nufi saman table tana faɗin "Bari naje na kawo wata kila baby ne ke jin yunwa ba wife ba, karna yi wa ɗan jikana rowa". Rimsha kam miƙewa ta yi tare da riƙo hannun Ayla ta ce "Ayla ina ne ɗakin ki? Ina so ne in je ban ɗaki". Satar kallon daddyn Jelly ta yi kafin ta ce "Muje na kai ki" ta kai karshen maganar tare da miƙe wa suka nufi sama. "Baby ina zaki je ba tare da kin nemi izinin mijinki ba?" Cewar daddyn Jelly, da sauri ta juyo tana ƙoƙarin dawowa. Dakatar da ita ya yi ta hanyar cewa "A'a raka mana first ladyn mu" kasa Rimsha ta yi da kai, ba abin da yake yi mata yawo a ƙwaƙwalwarta face zancen Malika, ga shi kuma shine kawai hanyar da za su bi wajen tseratar da Ayla. Suna shiga ɗakin ta rungume Aylar tare da fashewa da kuka, sosai ita ma Ayla ta rungumeta tana hawaye, ita duk a tunaninta kukan sun jima basu haɗu bane Rimsha take yi. Sun ɗan jima a haka kafin su raba jikinsu su koma bakin gado suka zauna. "Rimsha ki je toilet ɗin mana?" Girgiza kai ta yi kafin ta ce "Ayla babu wani toilet da nake son zuwa, keɓewa kawai nake son mu yi, mu samu dama mu yi hira". Sake rungumeta Ayla ta yi suna masu matuƙar jin kaunar juna. A palo kuwa, sai hira suke yi, Akil babu kunya a gaban kowa da Aunty ta kawo mashi abin cin ya fara bawa Umaisha a baki, ita ma Umaisha ɗin da yake ta saba, yanzu ya koya mata, sai bata ji kunyar Abbi ba, sai cin abincin su suke yi, shi dai Imran daya ga haka sai ya miƙe ya fice waje bawan Allah. Yana fita ya hango Akila da Irfan can wajen flowers suna hira, jikin motarsa ya koma ya tsaya yana hawaye, soyayyar Jelly ce ta dawo mashi sabuwa, Akil ya tuna mashi da lokacin baya idan ya je Kano, a baki yake bawa Jelly abinci, tana ci tana zuba mashi shagwaɓa, yanzu kuma da ya fito ya sake cin karo da su Irfan, sai ya sake tuna idan ya zo dawowa Kaduna yadda Jelly ke biyoshi waje tana yi mashi kukan shagwaɓa akan kada ya tafi ya kwana, hakan yasa shi hawaye, wani irin azababben son tane ke kara taso mashi, ji yake yi kamar zai mutu, zuciyarsa na mashi zafi sosai. Yana tsaye a wajen bai ga lokacin da daddyn Jelly ya fito ba sai jin muryarsa ya yi yana faɗin "Dama nasan kuka ka fito yi Imran, tun da naga irin kallon da ka yi wa su Akil nasan sai ka tuna Jelly, saboda abin da kuka saba yi da ita kenan, ni kaina ina ganin Akil ya fara bawa Umaisha abinci kai da Jelly ne kuka faɗo mani a raina, kayi hakuri komai zai wuce In Sha Allah, idan har Jalila tana raye ina da kyakkyawar yaƙinin zata dawo gare mu, idan matar kace, to ba makawa sai ka aureta". A zafafe Imran ya ɗago kai jin yau daddyn Jelly ya kira Jelly da sunanta kai tsaye wato Jalila, baya kiran sunan domin sunan wadda ta haifi mummyn Jelly ɗin kenan, saboda ta yi mashi kara, ta yi mashi abubuwa da dama shiyasa ya yi mata takwara, familyn mummy'n Jelly basa son aurensa da Hajiya Umaima wato mummyn Jelly amma haka mamanta ta dage sai da akayi aure, wannan dalili yasa ya yi mata takwara kuma yake girmama sunan, harta mahaifin mummyn Jelly baya son auren, kuma kafin ya yarda ayi auren sai da ya kafa wa mummyn Jelly sharaɗin akan idan ta fita gidan shi ta fita kenan, kada ya sake ganin kafarta, haka saboda son da take yi wa daddyn Jelly ta ce ta amince, ta yarda, wannan shine dalilin da yasa daddyn Jelly baya zuwa gidan sirikansa, kuma hakan yasa ma yaki yarda ko hutu Jelly ta je gidan, domin yasan basu sonta, kakanta mace kawai ke sonta, sai kuma kawunta Ahmad wato A'A. Goge hawayen fuskarsa ya yi kafin ya ce "Ba komai daddy ina hakuri ai, kuma ya zama dole na yi hakuri, amma dai idan na tuna ta dole zan yi kuka, ban taɓa son wani abu a rayuwata kamar yadda nake son jelly ba, tun tana ƴar shekara 2 zuwa 3 Allah ya zarabceni da sonta, na tabbatar mawuyacin abune na so wani abin kwatan makamancin son da nake mata, kullun sai na yi mafarkinta daddy, kullun na kwanta, daurewa kawai nake yi ina shiga cikin mutane mu yi hira da dariya, amma ni kaɗai na san me nake ji a cikin zuciyata, Allah ya gani ina kaunar jelly fiye da raina, ya Allah ya dawo mani da ita". Yana magana wasu hawayen suna biyo kuncinsa. Tunani daddyn Jelly ya fara yi da ace ya aura mata Muneer da ba makawa Imran mutuwa zai yi, irin wannan kauna da yake yi mata tun ma bata san wace ce ita ba, lallai ba abanza Allah ya jarabci jelly da kaunar shi ba ita ma, Allah ne kaɗai yasan dalilin da ya sanya ya sakawa Jelly sha'awar gudu ta bar gida dan kada ayi auren nan, Allah mai hikima mai iko. Ya jima yana tunani shessheƙar kukan da Imran yake yi ne ya dawo da shi daga duniyar tunanin da ya faɗa, cikin sauri ya kariso wajen tare da rungumar shi yana ɗan bubbuga mashi baya a hankali yana rarrashinsa. Irfan da Akila kuwa suna can gefe suna zuba hirarsu, while su Akil kuwa suna tsakar Palo shi da Umaisha yana bata abinci a baki tana zuba mashi shagwaɓa, Abbi kuwa ya haye saman table Aunty tana serving nasu shi da Aafia. A ɓangaren su Rimsha kuwa, sun ɗan warware suna hira kenan Hanan ta fito daga toilet ɗaure da towel a kirjinta. "Rimsha kece?" Shine abin da Hanan ta faɗa tana zaro ido, da sauri Rimsha ta miƙe tana faɗin "Hanan ke ce kuma a nan? Ina su yaya Yusuf da yaya Sadiq?". Nan take fuskanta ya sauya jin an ambaci Yusuf da kuma Sadiq, ta tuna da gida ta kuma tuna mamanta, hawaye ta fara yi tare da tsugunnawa a wajen. Da sauri Rimsha da Ayla suka kariso wajen suka fara rarrashinta. Da kyar suka samu ta yi shiru, bayan ta yi shiru Rimsha ta tambayi me dalilin yin kuka, nan take ta bata labarin abin da ya faru da mutuwar mamanta da yadda akayi ta zo gidan. Sosai Rimsha ta tausaya mata ta kuma bata hakuri. Bayan wasu ƴan muntuna Hanan ta gama shirinta cikin doguwar rigar Aafia sannan ta yi masu sallama ta fice waje izuwa Palo wajen su Abbi. Tana fita suka dasa hirarsu, Rimsha tana son ta kwatanta gayawa Ayla wannan magana amma ta kasa, kuma abin da ya sanya ma bata karfafa akan ta faɗa wa Ayla ɗin ba, ta san cewa ba wani abin da Ayla zata iya yi, hasalima ba zata fahimceta ba, tun da ba wani ilimi take da shi ba, ko da ma tana da ilimi ai ba zata je ta ce da daddyn Jelly ya kwanta da ita ba. Wannan maganar shi ya kamata a gayamawa, sai dai ba hanyar yin hakan. Sai fara'a Ayla take yi tana gayawa Rimsha yadda take son mijinta, ita kuwa Rimsha banda to da a'a sai wani magana kuma ta ɗan yi murmushi, banda hakan ba wani abin da take bin Ayla da shi. Shi kuwa daddyn Jelly da kyar ya iya rarrashin Imran suka dawo cikin Palo, bayan sun je ɗakin daddy ya wanke face nasa kenan. Saman dining table suka haye, Aunty ta zuba masu abinci, da kyar Imran yake iya taunar abincin, ba dan kada ya ce ba zai ci abinci ba daddyn Jelly ya ɓata rai da ya cire hannunsa, shi kuma daddy yana son cewa a kira mashi matarsa ta zo ta ci abinci, amma ya kasa faɗa saboda Imran, baya son wani abin kuma ya jefa Imran ɗin cikin damuwa, hakan yasa ya hakura ya daure suka ci abincin a haka. Bayan sun kammala daddy ya miƙe ya ce da Akil ya zo waje su yi magana, sai tsokanansu Aunty take yi daddyn Jelly na bata amsa har suka fita. Suna fita daddy ya gayawa Akil ya kamata ya daina duk wani kulawa da yake bawa Umaisha a nan har sai sun koma gida, idan ba haka ba kuma to yana iya sawa su rasa Imran, sosai Akil ya ji tausayin ɗan uwansa, kuma har ga Allah bai kawo a ransa cewa hakan zai iya haifarwa da Imran ɗin matsala ba, a yanzu shima ya san zafin so, dan yana bala'in kaunar Umaisharsa, da abaya ne yake ganin kamar hauka kawai Imran yake yi, yanzu kuma ya gane cewa ba hauka bace, so na iya sanya mutun ya yi abin da ma bai san ya yi ba. Bayan sun gama magana da Akil ya wuce ya samu Irfan da Akila, sai hira suke yi suna dariya. "Akila wuce cikin gida Kinji?" Cewar daddy, kasa ta yi da kanta tare da wucewa da sauri. Bayan ta tafi daddy ya gaya mashi cewa kada ya rinƙa nuna soyayyar Akila a fili har sai Imran ya tafi, sunkuyar da kai kasa ya yi yana faɗin "Bappa bafa soyayya muke yi ba". Wucewa daddy ya yi yana faɗin "Kai dai ka sani, ni kaga tafiya ta". Murmushin Irfan ya yi tare da bin bayansa shima ya dawo cikin gida. Saman table ya hango Akila ta zauna tana cin abinci, karisawa wajen ya yi shima ya zauna tare da fara magana ƙasa ƙasa "Heartbeat baki ce komai ba". Irfan kenan, shi kuma daddy'n jelly yana shigowa saman sofa ya zauna suka cigaba da hira shi da Aunty da Abbi. Su Umaisha kuma a lokacin sun wuce sama. Kasa da kai Akila ta yi tana faɗin "Yaya Irfan ai ban san me zan ce bane". Ɗaukar spoon ya yi ya fara cin abincin dake a cikin plate ɗin nata kafin ya ce "To in gaya maki abin da zaki ce ne?" Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a. "A'a kuma heartbeat?" Gera ta ɗaga mashi alamar e, tana murmushi, su Abbi kam kamar ba su san da zaman su a saman table ɗin ba, hirar su kawai suke yi. Ɗan leƙo face nata ya yi yana faɗin "To shikenan ki ce wani abin ko kuma na gayawa Abbi kawai a ɗaura mana aure Friday mai zuwan nan" ajiye spoon ɗin hannunta ta yi ta miƙe da sauri ta haye sama tana murmushi, binta da kallo ya yi yana ƴar dariya shima, duk abin da suke yi Aunty na kallonsu, shi kuma Irfan ya mance ma da su Abbi a palon. Akil kuwa an takura mashi yana son shan love kamar yadda ya saba, amma yau ba hali, domin wani abin ba zai yi wu ya yi shi a gaban Abbi ba, duk da yake bappansa amma ai uba ya wuci wasa, shi ya haifi Umaisha ɗin komin yaya akwai kunya. Akila kuwa tana hayewa sama ta fara duba wani ɗaki su Rimsha suke ciki, sai da ta buɗe ɗakuna biyu ana uku ne ta gane su, da gudu ta shiga ɗakin tare da faɗa wa saman bed tana dariya. Suna ƙoƙarin tambayarta ko lafiya sai ga Umaisha da Aafia da Hanan da suka fito daga ɗakin Aunty suma sun shigo. Miƙewa Akila ta yi ta rungumo Aafia tana dariya kamar zautaciya. Rumgumeta Umaisha ma ta yi tana faɗin "Aunty Akila gaya mani me kuke kullawa da yaya Irfan? Naga yau har da dariya ya yi, shida kwata-kwata baya dariya, kullun zakiga face nasa a ɗaure, wlh tun ɗazun na tsaya a window ɗakin Aunty ina kallon ku". Hararar ta Aafia ta yi kafin ta ce "Wato har ta zama Aunty Akila kenan saboda gulma, ke Umaisha wlh ni bansan ma a wani mataki zan ajiyeki ba" Umaisha na ƙoƙarin yin magana wayarta dake a hannunta ya fara ringing, tana dubawa sai taga my life, cikin sauri ta yi picking tare da kara wayar a kunnen ta tana faɗin "Yaya Akil har ka fara kewata ko?". Daga ɗayar ɓangaren daddy'n jelly ya ce "Bawa auntynki wayar". Wani irin kunya Umaisha ta ji ya kamata jin voice ɗin bappanta ne ba mijinta ba. Cikin sanyin jiki ta miƙawa Ayla wayar, karɓa Ayla ta yi tare da karawa a kunnenta ta ce "Hello". Wani nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce "Baby zamu je masallaci an kira sallar la'asar, kafin na dawo ki kawo mani abinci ɗaki na kuma ki zauna ki jirani, amma kafin nan ki yi Sallah tukun nan". Kamar dai kullun to ta amsa mashi da shi, sannan ya katse kiran ya bi bayan su Akil da tuni sun riga da sun wuce masallaci, shiyasa ma su Umaisha suka dawo cikin ɗaki kenan, Aunty ta ce je ta ce masu su je su yi Sallah ga su Abbi can za su tafi masallaci. A yanzu Aafia ta zama so silent kamar ba ita ba, kuma da alama har yanzu aikin da Rufee ta yi mata yana jikinta, da yake dai Rufeen bata nan ne bare ta bata command sai hakan yasa ba zaka gane akwai sihirin a jikinta ba. Zama suka yi a saman bed ɗin suka fara hira, Hanan ne ta fara miƙewa ta ce bari ta yi sallah dama da alwalanta, cikin sauri Rimsha da Ayla suka miƙe a tare suma dan su je su yi alwala su yi Sallah, A'afia da Akila kuwa kwanciya suka yi wai basu Sallah yau, ita kuma Umaisha waje ta fice zuwa wani ɗakin da ta yi alwala tun da su Rimsha sun shiga cikin wannan toilet ɗin, daga Umaisha har Aafia ba wacce ta nemi Ommu a cikinsu, da alama ma sun mance da ita. Umaisha tana fita kai tsaye wajen Aunty ta nufa, har kasa ta je ta duƙa ta bata hakuri tare da neman ta yafe masu duk abubuwan da suka yi mata abaya, a lokacin Aunty ta ɗauro alwala zata fara Sallah kenan, da fara'a akan face nata ta ce ta yafe masu ba komai, godiya sosai Umaisha ta yi mata sannan ta wuce cikin toilet na ɗakin auntyn ta yo alwala a cikin kafin ta dawo wajen su Rimsha suka yi sallah. After 30min. Bayan sun idar da sallah meƙewa Ayla ta yi ta nufi kofar fita tana faɗin "Rimsha ina zuwa daddy ya ce na kai mashi abinci ɗakinsa" ta kai karshen maganar tare da ficewa daga ɗakin. Cigaba da hurarsu suka yi suna dariya. Wayar Akila dake a gefenta ne ya fara kara, tana dubawa sai taga yaya Irfan, ɗauka tayi tare da karawa a kunnenta tana faɗin "Hello yaya Irfan". Kasa kunne su Aafia da Umaisha suka yi dan su ji me yaya Irfan zai ce wa Akila, kullun sai ɗaure masu fuska da basu umarnin ya iya, yau kuma har da dariya suka ga yana yi wa Akila, dole su kasa kunne dan su ji ko me yake gudana. Daga ɗayan ɓangaren ya ce "Hello Heartbeat kin ki cin abinci ko?" Girgiza mashi kai ta yi tana faɗin "A'a yaya Irfan na ƙoshi ne.." katse ta ya yi da cewa "Ban yarda ba, maza ki fito ki ci abinci ko kuma na kawo maki har ɗakin na zauna na yi gadinki sai kin ci kin ƙoshi ko kuma na yi maki ɗure". Hannu Umaisha da Aafia suka sanya suka rufe bakinsu suna mamaki, wato dama yaya Irfan ya iya magana da lallaɓa mutun haka, har da wani cewa in yi gadin ki sai kin ci kin ƙoshi, kai wato mu yake yi wa jan ido kenan? Aafia ke wannan tunani a cikin zuciyarta, ita kam Umaisha ma ta kasa yin tunanin ma, jin abin take yi tamkar mafarki. Akila kuwa shagwaɓe murya ta yi tamkar zata yi kuka ta ce "Allah yaya Irfan na ƙoshi ne" "To me yasa kike ƙoshi bayan kuma alokacin kika fara cin abincin?" Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Yaya Irfan ba kai ne kasa na ƙoshi ba, ka zo ka gaya mani maganar da ta sanya naji na ƙoshi, maganar ce ta cika mani ciki na". "Da gaske maganar ce ta ƙosar dake?" Ya yi maganar yana gyara kwanciyarsa a saman bed nasa, dan tun da suka dawo masallaci ya wuce bedroom nasa, kuma dama shi ma'aboci zama a ɗaki ne. "Da gaske fa yaya Irfan maganar ce ta cika mani ciki" ta yi maganar a shagwaɓe sosai, dama ita ba baya ba wajen iya shagwaɓa, ga iya saurin kuka kamar me, tana yi tana turo baki, dama kuma ga ɗan bakin nata irin nasa sak. "Anya heartbeat ranar da aka ɗaura mana aure zaki iya cin abinci kuwa?" Kukan shagwaɓa ta sa mashi tana faɗin "Yaya Irfan ka daina zancen nan mana, ni Allah zan maka kukan gaske". Sake baki su Umaisha suka yi suna kallon ikon Allah, Akila tafi karfin su, ita ma Rimsha yau taga iya shege wajen Akila, yadda take zuba shagwaɓa kamar yarinya karama, a ɓangaren Irfan kuwa, duk ta rikita bawan Allah, sai wani kankame pillow a kirjinsa yake yi yana juyi shi kaɗai a saman bed, ya ƙanƙame waya a kunne kamar ita ya ƙanƙame. A ɓangaren su Akil kuwa, da suka dawo masallaci a palo suka zauna, da Abbi, Akil, Imran, sai Aunty, shi ma daddyn Jelly ya wuce part nasu ya ce masu yana zuwa, haka shima Irfan ɗakinsa ya wuce dan ya je ya yi waya da Akilar. Ita kuwa Ayla tana shiga bedroom ɗin daddyn nata, ta ajiye kayan abincin a saman carpet sannan ta cire hijabin jikinta da suka yi sallah tare da zama gefen bed hannunta ruƙe da hijabin tana jiran daddynta, lokacin daddyn nata bai kai ga dawowa masallaci ba kenan. Da zamanta bai fi minti biyar ba sai ga shi ya shigo bakinsa ɗauke da sallama, kasa ta yi da kanta tana amsa mashi sallamar. Karisowa cikin ɗakin ya yi tare da rage kayan jikinsa, ya rage daga shi sai shot da singlet. Saman carpet ɗin ya zauna tare da zuba abincin a plate ya ce "Maza sauƙo ki ci, ni na ci nawa kece daman zan bamawa, yau Rimsha ta zo an mance da daddy ko?" Daga saman gadon ta zamo ta faɗo jikinsa tana dariya. "E mana baby, Rimsha ta zo an mance da miji" yana magana yana shafa kanta tare da matsar da plate ɗin abincin dan kada ta zubar ko ta ɓata jikinta. "Daddy Allah ban mance da kai ba, ina hira da Rimsha ma kai nake tunani wlh". Wani irin daɗi ya ji tare da riƙota sosai a jikinsa yana faɗin "Baby kina rikita daddy da kalamanki Allah kuwa". "Daddy da gaske nake faɗa maka ba wasa ba" ta faɗa tana shafa bayansa, kara natseta sosai ya yi a jikinsa yana faɗin "Babyn daddy sarkin son jiki, kina son jiki sos Turo baki ta yi a shagwaɓe ta ce "Daddy ai jikinka kawai nake so, idan ba jikinka ba ai kaga bana kwanciya a jikin kowa ko?". "Hakane babyn daddy, kuma hakan ba ƙaramin daɗi yake yi mani ba, ina kaunar matata saboda yadda kike bani mahimmanci na musamman, hakan yasa ma dole....." Ya kasa kai ƙarshen maganar sakamakon hannun ta da ɗaura a saman gabansa tana ƙoƙarin miƙewa, ita kanta sai da taji wani iri a jikinta saboda ta ji tabbas ta taɓa wani abin, amma sai ta basar ta gyara zamanta a saman carpet ɗin tana mirmishi ta ce "Daddy ni fa bana wani jin yunwa, ganin Rimsha yasa na ji gaba ɗaya na ƙoshi, sai dai kuma da alama Rimsha tana cikin damuwa sosai daddy, tun da ta zo bata yi mani murmushi ko sau ɗaya ba, kuma ba haka muka saba ba, tana murmushi sosai Allah daddy". Ta kai karshen maganar tamkar zata yi kuka. Jawota jikinsa ya yi ya shiga bata hakuri tare da yi mata alƙawarin zai sanya Imran ya yi confirming me yake damun Rimsha ɗin, da haka ya rarrasheta har ta daina damuwa ta saki jikinta kamar da. Abincin ya jawo ya fara bata abaki yana yi mata kalamai masu daɗi tare da yabonta, sai murmushi take yi har ta ci abinci sosai ba tare da ta sani ba. Bayan ta kammala ne ya bata ruwa ta sha, tana ƙoƙarin miƙewa ta tattare kayan abinci, cikin sauri ya jawota jikinsa yana faɗin "To ai sai ki zo ki bawa daddy kuma na shi abincin ko?". Cikin nuna koin damu ta ce "To daddy bari na zuba maka sai na baka" miƙewa ya yi da ita ajikinsa suka faɗa saman bed yana rungume da ita a kirjinsa. Juyawa da ita ya yi ta koma saman bed ɗin shi kuma ya yi mata rumfa kirjinsa, bai san dalilin da yasa haka kawai yake yawan jin kunyarta ba, baya son suna haɗa ido, hakan yasa idan da daddare ne sai ya kashe wutar ɗakin, idan da rana ne kuma baya taɓa yarda su haɗa ido, the way aka ce sun haɗa ido to yana kasa yi mata duk wani abin da ya yi niyya, duk sai ya ji kunyarta ta kama shi. A yanzu ma kawar da kallonsa ya yi izuwa saman wuyarta, murya kasa kasa ya ce "Rufe idanunki" ba musu ta rufe, domin bata taɓa yin musu da shi ba, komai ya ce mata to kawai take cewa, hakan yasa kuma ako da yaushe sonta yake matukar ninkuwa a cikin zuciyarsa, domin bata ce mashi a'a ba kuma ta ce mashi sai anjima, bata ce mashi ina zuwa, bata ce mashi kaɗan jira, sha yanzu magani yanzu take yi mashi, shine to, wannan to da take amsa mashi da shi, Allah ne kaɗai yasan irin farincikin da yake ji, haka zalika Allah ne kaɗai yasan irin ladar da take samu na sanya mijinta farinciki da nishaɗi, irinsu ake yi wa lakabi da matan aljanna ko kuma mace aljannar duniya ko dai mace ta gari, Allah ka sa muna daga cikinsu, kunllun burinta daddynta ya yi farinciki. Bayan ta rufe idanunta ne ya sanya hannunsa ɗaya a saman idanun nata ya rufesu da kyau, ɗayar hannun nasa kuma saman breast nata ya ɗaura tare da fara matsa su, a hankali kuma ya matso da lips nasa saman tata tare da fara kissing nata. Kamar yadda ya gaya mata haka ta yi, yana fara kissing nata ta fara mayar mashi da martani duk da idanun nata a rufe, bata mance kalma ɗaya daga cikin maganarsa ba, duk abin da ya ce idan ta yi mashi yana jin daɗi to tana ƙoƙarin ta yi mashi domin ya ji daɗin kamar yadda shima yake sanya ta ji daɗi. Wani irin daɗi ya fara ji tana ratsa shi sosai, cigaba da murjan breast ɗin nata ya yi yana fitar da numfashi da sauri sauri. Rimsha kuwa Imran ne ya zo ya sata a gaba dole ta fito ta ci abinci ba dan ta so ba A ɓangaren su Akila kuwa, gaba ɗaya ta gama haukatar da Irfan, ta rikita bawan Allah nan, shi kaɗai a ɗaki ya zama kamar zautatce, har wani irin numfashi yake sauƙewa kamar wadda ya sami biyan buƙatarsa, ita kuwa sai kara shagwaɓe murya take yi tare da yi mashi kukan shagwaɓa, Umaisha ta ɗauki lecture har ta gaji, wani lecture ma ya wuci tunanin ta, Akila bata ji kunyar idanunsu ba take rikita masu ɗan uwa, A'afia kuwa ji take yi daga yau ta daina ganin yaya Irfan da wani girma, saboda yadda ya zage yake zuba kamalan love tamkar ba shi ba, ga shi kuma wayar Akila a volume take, suna iya jiyo duk abin da yake faɗe, ita kam Rimsha ta ma rabu da su yanzu, tana can duniyar tunanin mafita akan yadda zata yi da case ɗin Ayla, abin ya shigeta sosai. A ɓangaren su Abba kuwa, sai hira suke zubawa a palo suna tattaunawa akan waye zai ɗauki Rimsha, Abbi dai ya ce shi zai riƙeta, Aunty kam ko ajikinta, koma ƴaƴa dubu Abbi zai kawo tsab zata ruƙe su da amana tamkar kanneta, bata da wata matsala a rayuwa. Cikin dabara Akil ya zame ya fice daga palon ya nufi waje. Yana fita ya kira Umaishansa a waya akan ta zo cikin mota ta same shi, baafi minti 5 ba sai gata ta fito, cike da jin kunya ta wuce su Abbi zuwa waje, duk abin da suke yi a gidan Aunty na ganinsu tana jiran zuwa dare ne duk ta yi masu tsiya idan sun haɗu a dining table, da yake a nan za su kwana kamar yadda daddy'n jelly ya faɗa. Tana shiga cikin motar ya jawota jikinsa tare da sauƙe ajiyar zuciya, ita ma rungume shi ta yi sosai tare da zura hannunta ɗaya cikin rigarsa ta kasa tana mashi wasa da cibiyarsa. "Wife na sha kewa sosai fa yau, mun kai minti 30 fa yau ba tare da juna ba" ya yi maganar yana shafa kanta zuwa wuyarta da yake ba ta sanya hijabiba ta fito. Murya kasa kasa ta ce "Yaya Akil Allah ina yawan tunanin idan muka koma Madina ka koma school ya ya zanyi da rayuwata, kaga a nan Naija baka da aikin komai sai dai mu wuni manne da juna, amma a Madina kuma zaka je school ina...." Bai bari ta kai karshen maganar ba ya ɗaura yatsansa a saman lips nata yana girgiza mata kai alamar baya ma son jin maganar. Shiru ta yi tana sauƙe numfashin a hankali, cikin salo da dabara ya cusa hannunsa cikin rigarta ta fara wasa da abubuwan da ya fi so a jikinta wato breast, ga shi kuma ya yi babbar sa'a tana da halittarsu sosai, daidai da jikinta, dan gaskiya Umaisha dirarriya mace ce ajin farko, kamar ita ta yi wa kanta surar jikin nata, hakan yasa take kiɗima shi sosai, kuma idan ya damketa baya yi mata ta daɗi, kullun sai ta yi mashi kuka, har yanzu ta kasa sabawa, sai iya yi mashi wasa, nan kam ita ce akan gaba, amma da anzo asalin zance sai kuka. A ɓangaren Lion kuwa, bayan ya gama abin da yake yi fita ya yi tare da sojan dake yi mashi girki, bai dawo ba sai bayan sallar la'asar. Da ya dawo ɗakin James ya fara shiga ya miƙa mashi wata sabuwar waya kyakkyawar gaske mai tsada, akwai sim card na Nigeria da komai a cikin wayar, Michael na yawan damun shi akan ya haɗa shi da Areef ɗin ne yasa ya sai mashi waya dan ya huta. Yana bashi wayar ya wuce bedroom nasa. Wanka ya fara yi ya shirya cikin pajama white color, ya yi kyau sosai sai dai kamar kullum fusataccen fuskar nan tasa a ɗaure sosai kamar hadari, ya saki wannan dark black curly hair nasa bai ɗaure ba, idanuwansa duk sun yi jawur da alama akwai wani abin a kasa. Saman bed nasa ya haye, ya gaji sosai yana kwanciya ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi. Minti biyar da fara yin barcinsa ya fara mafarkin da ya saba na mum ɗin su, sai dai a wannan karon bata zo mashi da wayan na yi fararen kayan nata ba, ta zo mashi ne da jajayen kaya kalar jini, yau tana ruƙe da wata katuwar wuƙa mai kaifin gaske, haka zalika yau ba faɗa suke yi da ɗayar matar da suke zuwa mashi a tare ba, yau ita kaɗai ta zo mashi fuskar nan tata a ɗaure, idanunta sun yi jawur kamar jini. Akan shi ta tsaya cikin tsawa ta fara tambayar shi akan menene yasa yake bincike akan G.M.A ya gaya mata ko ta kashe shi, kamar dai kullun yau ma dai kallon sama da kasa ya yi mata sau ɗaya tare da kawar da kansa gefe tamkar bai ganta ba, a fusace ta ɗaga wuƙar zata burma mashi a ciki, da hannu ɗaya ya ruƙe wukar tare da zaro mata idanunsa, ba ƙaramin tsorata da ganin idanunsa ta yi ba, hakan yasa da sauri ta janye wuƙar daga hannunsa, janye wukar da ta yi kuma yasa wukar ta yanke shi a hannu, nan take jikinsa ta fara zuba, ɗan ciza laɓɓansa na kasa ya yi, idanun nan nasa sun yi jawur da su, rai ka matuƙar ɓace ya nufeta gadan gadan, a zafafe ta juya zata gudu, yana ƙoƙarin damkar wuyarta kirar wayarsa take saman bedside drawer ta farkar da shi daga barcin da yake yi. A hankali ya waro idanunsa masu ɗauke da barci, ji ya yi gaba ɗaya jikinsa na yi mashi ciwo, tunani ya fara yi akan tabbas zargin da yake yi akan Mummynsu ya fara tabbata, tabbas tana da alaƙa da G.M.A domin dama yana yawan mafarkinta akan abubuwan tsafi, hakan yasa ya fara zarginta, to yanzu kuma daya bincika ya gano cewa James na ɗaya daga cikin members na ƙungiyar wannan dalili yasa kara faɗaɗa zarginsa akan ta, domin James bai san taya ya akayi ya shiga wannan kungiya ba, dole dai da wani makusancinsa aka haɗa baki aka shigar da shi ta hanyar bashi wani abin ya ci, tabbas james ya je wajen Josephine sosai abaya, har cikin gidan ta ya sha zuwa sau ba adadi, hakan yasa Lion ya fi zargin ita ce ta ba shi abin sha wadda ta sanya wa wannan kambun na tsafinsu. Masu son sanin menene G.M.A wata kungiya ce ta shan jini ta matsafa dake a cikin New York City wato dai can kasarsu, Areef ya tsinci kansa a cikin wannan ƙungiya ba tare da ya san ta ya ya akayi ya faɗa ba, tun bai musulunta ba yake a cikin kungiyar, bayan ya musulunta ya yi ƙoƙarin fita amma ba hali domin akwai abin da suka sanya mashi a jikinsa, babbar matsalar kungiyar duk yadda kuka kai ga sabo da mutun kana iya shanye mashi jini, Areef yana jin kwaɗayi tare da sha'awar jini aduk lokacin da dodan tsafin nasu ya juyo ta kansa, da yake dai Allah yana son shi da rahma duk lokacin da hakan ta fara faruwa mashi yana iya ka bakin ƙoƙarin sa wajen ganin ya karanta duk adduar da ta zo bakinsa, idan ya sami dama ya yi hakan kuma to fa yana iya kaucewa wannan kuduri na dodan tsafin nasu na son ganin lallai sai sun sanya shi shan jini, babbar abin burgewa da kuma jin daɗi shine, duk wani ɗan ƙungiyar dolene ya rinƙa kasancewa kusa da ƙungiyar amma banda Areef, shi bai taɓa zuwa ba, hasalima bai san a ina ƙungiyar take ba, kuma babu abin da suke iya yi mashi, saboda karfin musulunci, kawai dai sometimes suna samun dama su ɗan yi control nasa, amma bayan haka ba wani abin da suka isa su yi mashi, sun yi sun yi sun kasa saka shi shan jini, haka zalika da suka yi ƙoƙarin shan jininsa su kashe shi ma sun kasa, ya zama tamkar kaddararsu, yanzu so suke yi ma su cire shi daga cikin kungiyar, da yake Allah ba azzalumin bawansa bane, sai suka kasa cire shi daga ƙungiyar har Lion ya farga ya fara bincike akan su, yanzu babban abin dake a gaban Lion shine ya gano abin da suka sanyawa Areef ɗin suke sanya shi ya rinƙa jin sha'awar shan jini time to time, yanzu kwata-kwata Lion ya ajiye zancen CIA a gefe ya gano babban case da ya kamata ya fara dakatarwa tukunnan, idan ya gano in da suka sanya wa Areef sha'awar shan jini ya lalata wajen sai ya binci a ina ma kungiyar take gaba ɗaya ya sanya sojojin su yi masu diran mikiya su tarwatsa shegu, abin da yake ta fama kenan yanzu, bawan Allah idan ka ganshi ba zaka taɓa cewa yana cikin damuwa ba, dan kullun a haka yake, fuska a ɗaure, amma Allah ne kaɗai yasan raɗaɗin dake acikin zuciyarsa, dan ma dai daɗin abin ɗaya shine Areef bai taɓa shan jini ba, Allah na tsare shi, a takaice dai G.M.A sun ɗauko kaddararsu kuma sanadiyar tarwatsewansu baki ɗaya a doron duniya wato Areef kenan, dan idan Lion ya gano su ba zai yi masu ta daɗi ba!. STORY Ya ɗan jima kwance idanunsa biyu yana haɗa maganganun mummyn nasu dana daddynsu, zancen daddy ya tabbata gaskiya, kenan mummy matsafiya ce, tana ƙungiyar matsafa, sannan kuma da gaske ne kenan ta ba da su ayi mata kuɗi da su da suna yara? Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun, har ga Allah har cikin zuciyarsa baya jin zai iya kashe Mahaifiyarsu da hannunsa, duk da baya son ta saboda abin da ta yi masu, amma tabbas ba zai iya kasheta da hannunsa ba, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, kuma irinsu kamata ya yi a kashe su domin basu da wata amfani a duniya, idan ban da kashe rayuka da lalata al'umma ba wani abin da suke aikatawa. Da kyar ya miƙe zaune a tsakiyar gadon, wannan wace iriyar bala'i ce, wace iriyar jarabawa ce, uwar da ta haifesu, gaskiya abin akwai ciwo sosai, sai mutun ya kai zuciya nesa idan ba haka ba zai iya mutuwa da bakin ciki, zuciyarsa zata iya bugawa. A ɓangaren shi kuma Areef yana karɓar wayan bawan Allah Michael ya fara kira dan yana da numbersa akan sa, bawan Allah mai zuciyar zinari, an cutar da rayuwarsa sosai ba tare da ya sani ba, kawai dai yana ji wata sain kamar ana control na jikinsa ne, yana jin kamar ana amfani da shi, haka zai daure ya yi ta addu'a har sai abin ya sake shi. Bugu ɗaya ya yi wa Aseef, Aseef ɗin ya yanke kiran ya kirashi domin ya ga number bata kasar su bace so ya yi tunanin dama Lion ne ko kuma dai shi Areef ɗin, shiyasa ya katse kiran shi ya kira, dan idan ya yi picking call ɗin Areef ɗin ba za su samu jituwa ba ta hanyar network, network zata rinƙa yi masu gargada tana yanke masu magana, shiyasa mafi yawancin lokaci shine mai kiran Lion ba Lion ke kiransa ba, dan su sami network mai kyau su yi magana yadda ya kamata. Yana ɗauka ya ce "Assalamu alaikum My Tiger" daga can ɓangaren yana kwance daga saman bed nasa wani cool murmushi ya saki tare da gyara kwanciyarsa yana faɗin "Blood ka sayi waya kenan?" E Areef ya amsa mashi da shi. "Wow dama na yi tunanin kai ne that is why na yanke kiran" shima Areef ɗin fuska ɗauke da murmushi ya ce "Where is dad? I want to talk with him". Miƙewa daga kwanciyar da yake ya yi ya diro kasa daga saman katafaren bed ɗin nasa, daga shi sai shot da singlet, yanzu ya kara natsuwa sosai, ainahin haiba da kalama ga kwarjini da farinjini na jininsu na kara bayyana a tattare da shi, ya dawo sak Triplets nasa, jini ba bawa ba sai rikiɗewa yake yi yana komawa kamannin Lion, dama sun fi kusa, duk da yanzu yake gym sosai, amma yanayin kirar jikinsa dukka iri ɗaya ne, duk suna da kirar jarumai, sai dai jikin Lion da Areef ya fi nasa murɗewa, saboda sun jima suna gym, shi kuma sai yanzu ya mai da hankali yana yi, shima abaya yana yi amma sai randa ya ga dama yake shiga ya ɗaga karfe ɗaya biyu ya ajiye ya fita, amma yanzu kamar yadda kowa yake dagewa ya yi haka shima yake yi, kuma mafi yawancin lokuta a tare da Musharraf suke yi, domin shima Musharraf yanzu ya saba da ukubar da Tga yake bashi. Yana fita kai tsaye ɗakin daddy ya nufa, kwance ya isko shi yana kallon news a makeken Tv dake manne a jikin bangon ɗakin, miƙa mashi wayar ya yi tare da nufar waje yana faɗin "Daddy it's James" tsabar farinciki daddy jikinsa har kerma take yi wajen sanya wayar a kunnensa, suka fara magana. Shi kuma Aseef yana fita Palon kasa ya nufa, can ya hango Musharraf a cikin kitchen, da fara'a ɗauke akan face nasa ya karisa cikin Kitchen ɗin yana faɗin "Uncle what are you cooking for us?" Shima Musharraf murmushi ne ta bayyana akan face nasa kafin ya ce "Am cooking Nigeria food, rice and beans with steew, ba shine abin da na saya jiya a kasuwa da muka je ba" jawo kujera Aseef ya yi ya zauna yana faɗin "Okey yau zan ci African food kenan" yana magana ya murmushi. "Ai da wuya ka iya cin irin abincin mu, kai da damu ka je kasuwar ma ko fita a mota ka kasa yi saboda karnin nama da su ganyen miya da sauransu, ina ga kuma na dafa, na san ba zaka iya ci ba". Miƙewa ya yi ya karisa wajen Musharraf ɗin tare da sanya hannu ya fara taya shi wanke Tomatoes da yake yi. Abin da bai taɓa kwatanta makamancin shi ba a rayuwarsa, ko Kitchen ɗin gidan baya shiga, bai iya komai ba sai dai jibga-jibgan sojojin nan su dafa su kai palo su jere a saman table, bodyguard kuma su yi serving nasu suci, amma yau saboda Musharraf shine a cikin kitchen har da sanya hannu yana wanke Tomatoes, sojojin dake a cikin Kitchen ɗin ba ƙaramin mamaki suka sha ba, abin ya girgiza su, har sanya hannu suka yi a idanunsu suna murjesu dan su tabbatar da gaske ne abin da suke gani, ko sau ɗaya ba su taɓa ganin ɗaya daga cikin ɗan gidan a kitchen ba bayan Areef, Areef shi kaɗai ya taɓa shiga kitchen, a takaice ma ko serving abinci da kansu ba su iya shi ba, sai dai ci kawai. Ganin sojijin sun saki baki suna kallon shi ne yasa ya ɗan watsa masu ragowar ruwan wanke Tomatoes ɗin dake a hannunsa yana faɗin "Me kuke yi mani irin wannan kallo haka?" Cikin sauri suka yi kasa da kansu suna faɗin Sorry sir. Kayatatcen murmushi ya saki tare da matsowa kusa da su yana faɗin "Ku kalle ni iya son ranku ni ba Lion bane bare ku ce bana son kallo, kuma ku yi mamakin ku a bayyane ba a cikin zuciya ba, Allah kenan mai yin yadda ya so da bawansa, ni yanzu ma kunga African food zan koma ci, amma kada ku gayama daddy!". Kallon juna suka fara yi suna masu maimaita kalmar sunan Allah da ya kira, abin ya ɗaure masu kai to wani Allah kenan Michael yake nufi? Nasu na church ko wanne, ma'ana Jesus kenan. Kyasta masu yatsunsa ya yi a saman face nasu yana faɗin "Daga yau mun zama friends ku ɗauka a haka kuma, da mai kuɗi da talaka dukka Allah ne ya yi su, kuma babu wanda ya fi wani agaban Allah sai wanda ya fi ka jin tsoron sa ya kuma fika yin bautarsa, dan haka kuma ya kamata ku san da hakan, kuma duk yadda kuka ga na zama yanzu ku sani Allah ne ya hukunta hakan, na gane cewa da talaka da mai kuɗi duk ɗaya ne ta sanadiyar addin musulci addini mai niima kuma ina maku fatan shigarta dan ku samu rahmar Ubangiji" ya kai karshen maganar tare da wucewa ya koma gaban manya-manyan gases dake a cikin kitchen ɗin. Jugum jugum suka tsaya, sun rasa me za su yi, biyu daga cikinsu tabbas sun gamsu da zancen Aseef domin sun san abin da zai canza familyn William jacop daga izza da isa da taka mutane su koma sauƙin kai har su iya shiga kitchen gaskiya ba karamin abu bane, kuma lallai yana da kyau aduba wannan abin saboda ba abin wasa bane, hakan yasa biyu daga cikin huɗun masu nazari da tunani suka fahimci e tabbas wannan Addinin Musulunci koma ya yake akwai matukar gaskiya da kuma tausayi a cikin sa, ga shi dai yadda yau Aseef ya shigo Kitchen har da yi masu dariya, abin da ko hakwaransa ba su taɓa gani ba, abaya kullun face nasa a ɗaure kamar hadari, kwata-kwata basu ishe shi kallo ba, biyu daga cikin su kuma shiru suka yi suna nazari akan kalaman da ya yi masu. "Sir please zan iya magana?" Ɗaya daga cikin su ne ya yi magana, har wani zaro idanu waje sauran suka yi, domin sun san a baya basu isa su yi wa ɗaya daga cikin TRIPLETS magana ba. Yana neman ta ina ake kunna gas ɗin dan ya kunnawa Musharraf ya amsa da "Yes kana da damar yin maganar ka, ai yanzu na gama gaya maku dani da ku duk ɗaya ne a wajen Allah, so kawai yi maganar ka kai tsaye". Dukkansu sun sha jinin jikinsu yayin da shi kuma ya rasa ma ta ina zai kunna gas ɗin dan bai iya ba, sai faman dube dube yake yi. "Sir gaskiya na ji ina son wannan addinin musuluncin da ka faɗa, dan naga yana da kyau" a tare suka juya shida Musharraf. Musharraf na ƙoƙarin nufar sojan Aseef ya dakatar da yana faɗin "Wait uncle, bari na tambaye shi, kana son addinin musulunci ne saboda ina cikinsa ko kuma dai har ga Allah ya shiga ranka?". Kasa ya ɗan yi da kansa kafin ya ce cikin girmamawa "Sir saboda kana cikine yasa nima naji ina son addinin sosai". Juyawa ya yi ya cigaba da abin da yake yi yana girgiza kai ya ce "No Robertson bamason musulci ka har sai idan saboda Allah zaka yi shi, kada ka ji sha'awar addinin musulunci saboda wani, kada ka shigeta saboda wani, komai zaka yi a rayuwa ka yi shine dan Allah, domin saboda idan ka shiga wata matsalar Allah ya fitar da kai, kaga duk abin da muke da shi aduniyar nan, wlh bata isa ta fitar da mu cikin matsala da damuwa ba idan muka shiga, so ka yi abu saboda Allah, domin Allah shi kaɗai ne mai cetan bawa daga wata wahala ko bala'in, haka zalika idan ka yi addinin musulunci saboda Allah zaka shiga gidan aljanna, gidan da babu mai iya kwatanta maka makamancin ni'ima da daɗin dake a cikinta, so duk time da ka ji cewa yes saboda Allah kuma saboda addinin ya cancanta a so shi a kuma shige shi to muna maraba da baƙoncin ka, ka natsu ka duba cancanta, ni a gaban kowa zan iya bugar kirji na ce wlh duk wanda ya fahimci addinin musulunci to yasan dole ta cancanta a shigeta kuma ayita saboda Allah, sai dai mutane marasa son gaskiya kuma ɓatattu ne za su ce bata cancanta ba". Shiru Musharraf ya yi yana mamakin kai fin ƙwaƙwalwa irin na Michael, da ace ya jima da shiga addinin Musulunci da a yanzu ya zama babban malami, ƴaran William akwai kaifin ƙwaƙwalwa sosai gifted su. KUYI HAKURI DA KIRAN SU DA JAMES DA MICHAEL DA NAKE YI WATA SAIN, SABODA HAR YANZU AKWAI WAYAN DA IDAN NA KIRA SUNAN SU NA MUSULUNCI BASA GANE AKAN WAYE MUKE YIN MAGANA, SHIYASA NAKE SHIGO DA SUNAN SU NA KAFIRCI, AMMA A HANKALI HANKALI ZAMU ZAME SUNAN KAFIRCI MU BAR NA MUSULUNCI IDAN JAMA'A SUN SABA DA NA MUSULUNCI FATAN KUN FAHIMCE NI!!!. "Ɗaya daga cikin sojojin ne ya sake cewa "Sir ni na yarda har ga Allah wannan addini yana da kyau, domin yau shekarata 8 ina tare da ku, na san da cewa duk abin da kuke yi mai kyau ne, baku kula abin da babu kyau, so ina da kyakkyawar yaƙinin cewa tun da ka shiga wannan addinin to tabbas shine addinin ƙwarai, dan haka nima zan shiga..." Da sauri Robertson ya tari numfashin sa da cewa "Sir nima zan shiga saboda Allah ɗin". Sosai Michael (Aseef) ya shiga matsanancin farincikin, da sauri ya karisa wajen da suke ya rungumosu yana faɗin "Alhadulillah Alhadulillah Allah ya kuɓutar da ku daga duhu zuwa haske, Allah ya nufe ku da rahma, na yi maku murna sosai, uncle Musharraf ka basu kalamar shahada". To Musharraf ya amsa da shi tare da matsowa in da suke, su kuma saura biyun sai nazari suke yi akan hakan, da alama ba su yarda ba, amma kuma sun sha mamakin ganin yau Aseef (Michael) ya rungumi sojoji biyun nan, suna jin suma kamar su karɓi Addinin amma sai kuma sheɗan yana zuga su. Ɗaga kai Aseef ya yi ya dubi cameran dake a cikin kitchen ɗin ya ce "My Lion mun sami karuwa a addinin Musulunci, Allah Alhamdulila" ya kai karshen maganar tare da juyowa ya kalli biyun da basu karɓi musulcin ba. Ba kyama ba cutarwa dan ba su musulta ba, cikin mutunta juna ya ce "Tese zo ka nuna mani yadda ake kunna gas ɗin nan, kai kuma Iron ka kawo mani pot bari na ɗaurawa uncle ruwa, dan na ji ya ce da ruwa ake dafa shinkafar, am very happy yau zan ci African food".Ya kai karshen maganar yana murmushi. Sun kasa motsawa sun tsaya tare da sunkuyar da kansu kasa suna mamakin abin. Cikin sauri Aseef ya matso kusa da su tare da riƙo hannayensu yana faɗin "Iron lafiya? Me ya faru kuma na ga kun tsaya kuna sunkuyar da kan ku ƙasa?". Cikin girmamawa Iron ya ce "Sir all my though zaka bamu punishment ne, zaka tsane mu dan mun ki karɓar addinin da ka kawo mana, a tunani na zaka sanya a...." Bai kai karshen maganar ba Aseef ya ɗaura ya tsaya ɗaya a saman ɗan ƙaramin bakinsa yana faɗin "Shiiiiiiiiiii ya isa haka, me yasa zan wahalar da ku? Addinin musulunci addini ne mai sauƙi, addini ne wadda bai hana kowa ya yi addininsa ba, bai takurawa kowa ba, hasalima addinin musulunci ne kawai ya bawa kowa dama ya yi abin da yake son yi dan gane da addininsa matuƙar ba zai ci zarafin wata addini ba ko kuma abin da suke amfani da shi wajen yin addininsu, ni ba zan ki ku ba, ba kuma zan baku wahala ba, domin na san shiriya ta Allah ne, kuma addinina mai sauƙi ne tare da kamala, addinina ya bani dama na kyautatawa makwabcina ko da kuwa kafuri ne, so banga dalilin da zai sa na ki ƙu dan kun ƙi addini na ba, yanzu dai ku kawo mani abin da na ce maku, kada ku damu ina kaunar ku kamar koda yaushe". Hawaye Iron ya fara yi yana faɗin ya yarda zai karɓi musulcin saboda Allah kuma saboda kyawun addinin, farinciki a wajen Michael da Musharraf ba'a magana, a tare suka basu kalmar shahada suka karɓa suna masu yaƙini mai kyau da kuma yi wa addinin kyakkyawar za to. Suna tsaka da wannan farinciki uncle Herry ya faɗo cikin kitchen ɗin a ruɗe yana faɗin "Michael where are you? Naje ɗakin ka baka nan, na zo zan wuce na hangoka a nan, what are you doing here?". Hankali kwance Aseef ya ce "Uncle what is happening? Na ganka a ruɗe" "Michael since yesterday Tyson (TGA) bai dawo ba, mun kira number sa a kashe". Jinjina kai Aseef ya yi yana faɗin "Okey uncle go into your room zan kira Lion a kan hakan". To uncle Herry ya amsa da shi tare da ficewa daga ɗakin, hankalinsa a tashe kwata-kwata bai ma lura da wayan da suke a cikin kitchen ɗin ba ya fita kawai. aikin gabansa kawai Aseef ya cigaba da yi yana ƙoƙarin ɗaura ruwa a pot, dan Robert ya kunna mashi gas ɗin. Ganin hakan ya sa Musharraf ya ce mashi ya je ya kira Lion ɗin mana, girgiza kai ya yi yana faɗin "I can't go anywhere uncle, kyalesu ina da tabbacin koma a ina yake Lion ya sani, Allah yasa ma shine yasa aka ɗauke shi zuwa headquarter aba shi jikinsa da wahala da kyau". NI KUMA NA HAƊA KAYANA TARE DA AJIYE ALKALAMI NA SAI ALLAH YA KAI MU GOBE!!. 💖💖TRIPLETS💖💖 E 71-72 Ganin hakan ya sa Musharraf ya ce mashi ya je ya kira Lion ɗin mana, girgiza kai ya yi yana faɗin "I can't go anywhere uncle, kyalesu ina da tabbacin koma a ina yake Lion ya sani, Allah yasa ma shine yasa aka ɗauke shi zuwa headquarter aba shi jikinsa da wahala da kyau". Shiru Musharraf ya yi suka cigaba da aikin da suke yi, su Iron sun tsaya suna kallon ikon Allah, har yanzu mamaki bai sake suba, yau ɗaya daga cikin TRIPLETS ne a Kitchen, kai abin ya yi mugun basu mamaki wadda ba za su taɓa mancewa ba. Aseef ne ya ce masu su zo su haɗu su yi aiki a tare mana, tunda yanzu sun zama friends, har suna haɗa baki wajen maimaita sunan friends, ɗaga masu kai kawai ya yi alamar e friends, da sauri suka matso suka sanya hannu su ka fara aiki a tare. Kasa jurewa Aseef ya yi, baya son warin abubuwan da Musharraf ke zubawa a girkin, ji yake yi tamkar zai yi amai, bai taba zama a wajen da ake yin girki ba, ga shi kuma baya son Musharraf ya fahimci cewa yana kyamar abincinsa, da kyar yake jan numfashi, har wani canza launi idanuwansa suka yi saboda bakar wahalar da yake sha ta sanadiyar rashin jan numfashi da yake samu. Cikin dakiya ya ce "Uncle who teach you how to cook?". Musharraf yana ƙoƙarin juya kayan miyar dake soyuwa ya ce "Na yi makaranta ai, a school na koyi duk wayan nan abubuwa". Kasa sake yin magana ya yi saboda wani irin amai da ya zo mashi, da sauri ya nufi waje har yana yaɗawa da gudu, kai tsaye bedroom nasa ya nufa, yana shiga ya wuce toilet, amai ya fara shararawa kamar ba gobe, yana yi yana dafe cikinsa saboda yadda take murɗa mashi ba kaɗan ba, nan take zufa ta fara tsastsafo mashi daga gefe da gefen fuskarsa. Shi kuma Musharraf bai ma lura da lokacin da ya fita ba, sai juyawa kawai ya yi yaga baya nan, bai kawo komai a ransa ba, sai ya ci-gaba da aikinsa kawai. Sosai ya yi aman nan har sai da ya sami sauƙi sannan ya sakarwa kansa shower dan ya yi wanka kila ya ɗan sami sassaucin abin da yake ji a cikin zuciyarsa da kuma jikinsa baki ɗaya. Bayan ya yi wankar ne ya fito ya shirya cikin wando three quarter baki da yar riga mara nauyi, mayukansa ya shafa tare da perfume nasa sannan ya nufo waje. Yana fita ya wuce ya sanar da sojijin dake gyara masu bedroom nasu akan suje su wanke mashi toilet nasa tare da gyara bedroom ɗin, cikin girmamawa suka amsa da okey sir, sannan ya wuce izuwa ɗakin daddy, yana son komawa kitchen ɗin amma ya kasa dan saboda ba zai iya sake jin wannan wari na su kayan miya da sauransu ba. Kwance ya isko daddy har lokacin hira suke yi da Areef, daddy ya yi ya yi akan su yi video call amma Areef ya ki yarda saboda yasa cewa idan daddy ya ganshi hankalinsa ba ƙaramin tashi zai yi ba, zai iya ja ma ciwonsa ta tashi, ga shi kuma basu kusa. Saman bed ɗin ya haye tare da kwanto da kansa saman cinyar daddyn yana kallon Tv, a hankali daddy ya fara shafa kyakkyawar brown hair sa tare da gangarawa har izuwa bayansa, sai faman lumshe idanu yake yi tamkar mai jin barci, a ɓangaren daddy kuwa yana matukar jin kaunar ƴaƴan nasa kamar ransa. Sun kwashi 1 hour bayan shigowa Aseef ɗin kenan suna waya da Areef, daga karshe suka yi sallama daddy ya miƙawa Aseef wayar, karɓa ya yi tare da gyara kwanciyarsa a jikin daddyn nasa ya kara wayar a kunne suka fara hira da Areef ɗin. Suma sun jima suna hira kafin ya ce anjima zai kira shi yanzu zai je ya ci abinci ne, da haka suka yi sallama ya miƙe daga kwanciyar da ya yi yana faɗin "My daddy am coming". Yana ƙoƙarin sauƙa daga gadon daddy ya riƙoshi tare da manna mashi kiss a goshi yana faɗin "I really love you my son" kayatatcen murmushi ya saki kafin shima ya yi wa daddy kiss a kumatu sannan ya diro kasa daga saman gadon ya fito waje. Kai tsaye palon kasa ya nufa, wani irin fitinannen kamshi air freshener ne ke tashi a palon, da alama Musharraf ya kammala girkin da yake yi kenan, domin dama haka dokar gidansu yake, idan an kammala girki sojijin nan za su tattare ko'ina sannan su feshe ko'ina da turaren da ya dace da shi, su mai da komai mazauninsa, na wankewa su wanke na gogewa su goge, shiyasa a koda yaushe komai na gidansu yake kasan cewa tamkar ba'a taɓa taɓa su ba, kai ka ce sabbine daga ledarsu aka fito dasu saboda tsabar gyara da kula da suke samu. Ba kowa a palon da alama Musharraf ya wuce part nasu dan dama bai cika zama a palonba, saboda takurawar da Tga yake yi mashi. Juyawa ya yi izuwa part nasu, da sallama ɗauke a bakinsa ya shigo cikin palon nasu. Saman table ya hango Musharraf yana zaune yana cin abinci, ya yi wanka ya canza kaya, ba ƙaramin kyau ya yi ba abinsa. Karisawa saman table ɗin ya yi ya zauna yana faɗin "Uncle sorry na barka kai kaɗai ko?" Murmushin ya yi kafin ya ce "My Aseef don't worry". Hannu ya kai ya karɓi spoon dake a hannun Musharraf ɗin tare da ɗibar abincin ya kai bakinsa, wani irin yanayi ya ji tare da danasanin kwatantawan da ya yi, ba tare da ya tauna abincin ba ya haɗiye tare da ajiye spoon ɗin ya yi maza ya ɗauki glass cup dake cike da ruwa dake a gaban Musharraf ɗin. A zafafe ya kafa cup ɗin a bakinsa yana shan ruwan, sai sorry Musharraf yake ce mashi, to kawai yake amsawa da shi, jiki ba kwari ya miƙe ya nufi saman sofa ya kwanta yana faɗin "Uncle get ready fa on Monday zaka tafi Nigeria wajen JAMES". A zafafe Musharraf ya ɗago yana kallon shi. "Aseef an gane James ne?" Jinjina mashi kai ya yi alamar e an gane shi, ajiye spoon dake a hannunsa ya yi tare da miƙewa ya sauƙa daga saman table ɗin ya tsunguna ya yi wa Allah sujudur shukur, dan nuna godiya da farincikinsa ga Allah subhanahu wata'ala. Bayan ya ɗago sosai ya yi wa Areef addu'a tare da fatan Allah ya tsare shi a duk in da yake, sai amsawa da Amin amin Aseef yake yi. Bayan ya kammala ya koma saman table ya cigaba da cin abincinsa yana ayyanawa a ransa ya zama mashi dole idan ya je Nigeria ya koma wajen ƴan uwansa, idan ba haka ba zai shiga matsala babba. While shi kuma Aseef kewa kawai yake yi wa tunani, zasu barshi shi kaɗai bawan Allah. Bari mu koma Nigeria dan jin wani hali suke a ciki GIDAN LION💖 Ya jima yana tunanin yadda zaayi ya iya kashe mahaifiyarsa da kansa, da abaya lokacin da yake kristar ne, to da sab zai iya kasheta, amma yanzu ya san mahimmancin iyaye, addinin musulunci ya gaya mashi waye iyaye, sanadiyar hakan nema har ya fara tunani a ransa zai iya yafewa mummy ɗin tasu, amma yanzu kuma ta yi laifin da idan ya tabbata hakan ne, da gangan ta aikata hakan, ba kuskure ko wani abu makamancin haka bane, to dole ne akasheta kamar yadda za'a kashe kowa dake a cikin kungiyar, babban matsalar shine yau ita ce rana ta farko da ya fara shiga damuwa dan yayi tunanin zai kashe wata, abin yasa shi ya ji kwata-kwata bashi da wata kuzari, amma kuma abin mamakin duk da wannan laifi da Josephine ta aikata, ta fi daddy samun waje a zuciyar Triplets, why basa son daddy? Daurewa kawai suke yi suke bashi kulawa kamar yadda addinin musulunci ya koyar da su, amma ba wai dan suna jin kaunarsa a cikin zuciyoyinsu ba. Kyawawan fararen kafafunsa ya fara zurowa kasa kafin ya muƙe zaune yana kallon ɗakin, har lokacin idanunsa ba su koma daidai ba, sun yi jawur da su, tunani yake yi me yasa komai zai faru sai dai ya faru da Areef ko Aseef? Me yasa shi basu tunkararsa da ire-iren hakan? To menene banbancinsa da su Areef ɗin? Bayan kuma tare suka zo duniya, ɗan gara Aseef ma ace gaba ɗaya rayuwarsa ya yi tane tamkar ba mutunba, saboda ciwonsa, amma Areef fa? Abaya tare suke yin komai, lokacin da suke zuwa school tare suke komai, kaya iri ɗaya, karatu tare suke yi, abin da ya karanta shi Areef ya karanta, karatun addini tare suka yi, bincike akan addinan gaba ɗaya har suka fitar da na gaskiya a tare ne, to me yasa shi duk ka irin wannan abin ake tsoron tunkararsa da shi?. Ya jima a hakan kafin ya miƙe ya nufi toilet dan ya yi wanka da ruwa mai zafi sosai ko zai sami kwarin jikinsa. Bayan ya yi wanka ya fito sake shiri ya yi cikin pajama sky blue a wannan karon kam ya ɗaure gashin kansa ya bar wannan guntu na gaban goshin kawai. Yana kammala shiri ya fito ya nufi kasa wajen Areef, kwance ya isko shi yana latsa wayar tasa. Gefensa saman bed ɗin ya zauna tare da ɗan janye lallausan bargon da ya rufe jikinsa zuwa wuyarsa da shi, zubawa kirjinsa wajen ciwon nan nasa wayan nan dara-dara blue eyes ɗin nasa ya yi, shima Areef ɗin zuba mashi Ash eyes nasa na ƴan mintoci ya yi kafin ya ce "What is wrong with my blood?". Kallon gefen ido Lion ya mashi kasa kasa a nutse ya ce "Au zaka gwada mani aiki ne?" Ƴar murmushi Areef ya yi kafin ya ce "Ni na isa in gwada maka aiki ne? Kawai dai naga kana cikin damuwa ne yasa na tambaya, amma ai ba batun na gwada maka aiki, ban kai nan ba". Shiru Lion ya yi mashi na ƴan mintoci kafin gently ya ce "What is G.M.A?" Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya fara magana. "G.M.A lokacin da na fara cin karo da ɗaya daga cikin members na kungiyar, a lokacin na kashe shi, yadda kuma akayi na gane, wani aiki naje to bayan na gashe waƴan da zan kashe zan bar wajen kenan sai a ka harbo mani bullet ɗin nesa, da alama suna kallona daga nesa, Allah ya tsare bullet ɗin bata same ni ba sai ta sami mutumin ɗin a kafa, ya faɗi kasa yana kuka, da sauri na karisa wajen sa, a maimaƙon naga jini na zuba daga wajen da aka harbe shi, sai naga wani farin ruwa ne yake zuba, abin ya ɗaure mani kai, sake harbin bullet da akayi ne yasa na ƙira hukumarmu akan su harbi koma waye ke mana harbin nesan nan, haka kuwa akayi suka harbesa, kasan CIA ko bata je waje ba muddin ɗaya daga cikin ma'aikatan ta za su je waje to tabbas kamar suna wajen ne, suna iya ganin komai. Bayan sun harbi mutumin nan ni kuma na fara binciken sauri akan waddake a gabana, daga karshe dai na ɗaukesa muka je cikin daji na yi bincike akan ya akayi farin ruwa yake fita a jikinsa a maimakon jini, a nan ne na gane cewa member ne daga cikin G.M.A abin ya ɗaure mani kai, ban ɓata lokaci ba waje kashe shi a wajen na tafi na bar gawar, daga nan sai na fara bincike akan suwaye su, a ina kuma suke? Me suke aikatawa? A nan ne na gane kungiya ce ta shan jini wadda ke a cikin New York, sai dai har yanzu na kasa gane a ina ɗaya taka maimai kungiyar take". Shiru ya ɗan yi yana mai da numfashi. Jinjina kai Lion ya yi tare da ɗaukar wata ƴar karamar na'ura ya dasawa Areef ɗin a kirjinsa daidai wajen ciwon nasa, ƴar kara Areef ɗin ya yi saboda azaba. Miƙe wa Lion ɗin ya yi ya fara haɗa abubuwan da zai buƙata, da yake Lion in dai fagen aikin likitoci ne to ba baya ba, ya kware sosai kamar babban likita, domin zance ma kusan ya karanci aikin sosai, kuma ya mai da hankali sosai wajen koyan abubuwa da dama daga wajen daddy, hakan yasa ya iya abubuwa da dama dan gane da kula da lafiyar jikinsu. Komawa ɗakinsa ya yi ya ɗauko laptop nasa ya dawo, connecting na wannan na'uran ya yi da laptop nasa, nan take ya fara bincike akan lafiyar Areef ɗin da kuma abubuwa dake a jikinsa, a zafafe yake aikin, da kallo ɗaya zaka yi mashi kasan a ƙage yake da ya kammala aikin. Good 1 hour ya ɗauka yana wannan binciken nasa kafin nan ya tattare komai ya kashe laptop ɗin nasa. Wayarsa ya ɗauko ya kira Dr Tyrion bugu ɗaya Dr ya ɗauka, ba tare da ɓata lokacin ba ya sanar da Dr yana son da shi da wasu likitoci uku su dira a cikin Nigerian daga nan zuwa gobe da yamma, dan aikin da za'ayi wa Areef ba shi da time da zai iya yin wannan aiki, akwai abubuwa sosai a gabansa, kuma zai fi son ma dama manyan likitoci su yi mashi wannan aikin don shi ya fi bawa aikin sojan shi mahimmanci. Bayan ya gama waya ne ya dubi Areef dake bin shi da kallo a nutse ya ce "Yanzu dai ka bar CIA har abada, kuma kasani sai na baka hukunci mai tsanani na laifin sayar da rayuwar ka da kayi, kana tunanin rayuwar taka ce kai kaɗai? Baka san cewa muma muna da hakki a kan ka bane? Iyayenka fa? Duk baka yi tunani akan wannan ba, good ka kyauta daka bani bakar wahala, ban taɓa aiki mai wahala ba irin aikinka, good 2 weeks na ɗauka ko barci bana samu bare kuma cin abinci all because of you, babban abin haushin ma sai ina bincinken ina kake sai na sake cin karo da wata ɓarna da kayi, dole na dakata nayi settle komai, kayi abubuwan dana kashe wutar bansan adadi ba, Allah dole na hukuntaka saboda gobe, ko da sunan wasa kada ka sake yi mana irin wannan gangamin, baka tunanin wani hali Aseef zai shiga? Bawan Allah da bai san komai ba sai kaunar mu, baya magana ɗaya biyu ba tare da ya kira mu a ciki ba, duk baka tuna haka ba kenan!". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa ya fice daga cikin ɗakin. Shiru Areef ya yi yana tunani, shi da kansa ya san ya yi babban kuskure, yasan cewa idan wani abin ya same shi to ba makawa daddy mutuwa zai yi, bayan daddy kuma Aseef, Aseef shine mutun na biyu da zuciyarsa zata iya bugawa idan ya ji wani abin ya same ni, gara Lion yana iya jurewa, amma shima sai ya ji ajikinsa ba kaɗan ba, babu wani ɗan adam da ya isa ya ce tun da rayuwarsa ne zai yi abin da ya ga dama da ita, hakan ba zai yi wu ba, saboda akwai haƙoƙin mutane da dama a tattare da wannan rai ɗin naka, na farko Ubangijin mu, Allah ya bamu wannan rayuwa ne domin mu bauta mashi ba dan mu sai data ga wani ko wata ba, bayan nan akwai iyayenka, suna da hakki akan wannan rai ɗin naka, sannan ƴan uwanka, to kada ya zama kana tunanin cewa ai ranka ne kana da damar yin abin da kake so da shi, a'a ba haka bane!!. Yau sosai Areef ya yi nadama ba kaɗan ba, har hawaye sai da ya zubar, kuma a shirya yake da ya karɓi duk wani hukuncin da Lion zai yi mashi, domin yasan ya aika babbar kuskure mai girma, da ya mutu ta wannan hanya da bashi da amsoshin da zai bawa Aseef da daddy a ranar gobe kirayama dan dai yasan mawuyacin abune su biyun nan su rayu bayan mutuwarsa, sannan ba shi da amsar da zai bawa Ubangijin sa. A ɓangaren su Jehan kuwa, barcine ya yi awon gaba da su dukkansu tun lokacin bayan da suka gama rikici da wannan Alhajin. Barcin awa biyu suka yi Jehan ta farka, nan ta sami Aisha idabunta biyu itama ta farka tana zaune ta buga uban tagumi. "Aisha me yake faru na ganki kin yi shiru haka?" Ta tambaya tana kare mata kallo. Nisawa Aisha ta yi kafin ta matso ta ruƙe hannayen Jehan ɗin cike da damuwa tab a ranta ta ce "Jehan zan gaya maki ainahin abubuwan da suke faruwa a cikin gidan nan wadda ba kowa ya san da hakan ba, da farko abin da yasa ban gaya maki ba dan ina tunanin kema kamar mu ce, kema hakura zaki yi ki bada jikinki domin bamu da wata mafuta, wannan gidan da kike gani ba gidan arziki bane, wlh Allah wannan gidan bala'i ne Jehan, na san idan suka san cewa nasan wannan sirrin za su iya kashe ni ko dai su jefar da ni, kai da wuya ma su jefar da ni nasan kashe ni za su yi, Jehan sanadiyar cetar Maryam da kika yi tasa na samu karfin gwiwa na cewa sanadiyyar ki zamu iya barin gidan nan har mu kai kara ga hukuna cewa ga abin da ake yi a cikin gidan nan..." Dakatar da ita jehan ta yi da cewa "Kin san hanyar fita daga gidan nan ne?" Girgiza kai ta yi tana faɗin "Kamar yadda aka kawo ki da tsakar dare, haka ake kawo kowa da tsakar dare, sannan babu wani alhajin da ya isa ya fita da ke da rana sai da daddare, bugu da kari magana ta gaskiya babu wanda idan ya shigo gidan nan yake sha'awar fitarta, shiyasa hajiya bata damuwa take bari a fita da ƴan matan, dan tasa ta asirce su ba zancen fita, amma na sha mamaki tun da na ga kin ceci Maryam nasan dole akwai nasara a tattare da ke, wlh asiri suke yi wa mutun ya zauna a cikin gidan nan, ina da tabbacin hakan ne, ka zauna kayi ta bada jikinka, lokacin dana fara yin hakan, da aka kawoni ina sabuwa, duk time dana kwanta da wani, zan kwanta ne cike da annashuwa da farinciki, idan mun gama abin da zamu yi kuma nadama tare da dana sani ne zai biyo bayan abin a tattare da ni". Shiru Jehan ta zuba mata idanu tana jiran ta ji me yake faruwa. "Jehan kamar yadda kika sani ne ana fita da yarinya, Alhazawan nan suna zuwa da ita su kwana da ita a hotel da sauransu, amma fa ki sani ba kowani Alhaji bane yake zuwa ya kwanta da yarinya dan biyar bukatar kansa, a'a akwai masu zuwa su kwanta da yariya dan bokansu matsafansu sun basu wani abin su zaubawa mace a cikin cikinta dan samun kuɗi ko nasara ko dai wani biyan buƙatunsu, kuma duk wannan hajiya ta sani, domin kafin ya fita da yarinya sai ya bawa hajiya makudan kuɗaɗe ya gaya mata ga irin aikin da zai yi da yarinyar, da yake ba ƴaƴan ta bane, sai ki ga ta yarda ta karɓi kuɗin ta bada yariyar, ki sani fa wannan abin da suke zubawa mace a cikin cikinta wlh idan ya yi wuta in suka dawo da yarinya ta kara kwana biyu sai gawa, akwai kawata da muke wannan ɗakin kafin ku zo sunanta Zuwaira, yarinyar nan so silent, bata da hayaniya, to ranar da wani aljaji ya tafi da ita da daddare, bai dawo da ita ba sai washegari da daddare, lokacin da ta dawo nan wlh sai kin matsa mata kwallah, a nan ne take bani labarin abin da yake faruwa, domin ta ji duk yadda Hajiya ta yi da wannan alhajin, ta ji yadda suka yi da hajiyar daɗi, kuma ita ma ta gani da idanunta, lokacin da ya gama amfani da ita, ta ga wani bakin abu a cikin gabanta kamar garin lepton, abin ya so ya yi kama da kasa haka, tun daga lokacin ta fara jin ciwon ciki, shi kuma alhajin ya ɗauki kuɗi makudai ya bata sannan ya ce ta je ta yi wanka, haka ta je ta yi wanka ta wanke gabanta ta zo ta kwanta, da yamma ya sake dawowa ya yi amfani da ita ya sake zuba mata wannan abin, ga shi na safe da ya zuba mata ma sai ciwo cikinta yake yi mata, haka ba imani ya sake mafani da ita ya zuba mata, wlh yarinyar nan in takaice maki bata yi kwana biyu da dawowa ba ta rasu, hajiyar daɗi ta sa aka fita da gawarta ban san ina suka kai ba, cos a yanzu ba kowa yake yin zinar ba ma tsakani da Allah, wasu musamman ma manyan mutanen nan, wlh wani abin suke sanyawa mutun a jiki dan samun wani abu da suke nema, wani kuma su lalata mashi hanji ya ruɓe ya mutu, wani abin kuma idan suka saka maka ka haukace daga nan a rasa gane kanka, to yanzu dai ya kamata masu yin zinarma su kula dan yanzu ba zina kamar na da ake yi ba, kinga a ɗakin bayan mun nan, yarinya ƴar shekara goma sha huɗu wani alhaji ya ɗauke ta, yarinyar nan ya tafi da ita, wlh jehan virgin ce yarinyar nan, bata san komai ba, ga ƙananun shekaru, dan rashin imani ya je ya yi amfani da ita ta gaba da kuma ta baya, kuma ya zuba mata wani abin ta bayanta, wlh karki so kiga yadda yarinyar nan ta kare a cikin gidan nan, Allah sai kin yi mata kuka, kuma ita kam ma marainiya ce, iyayenta sun rasu ta gudun wa wahalar matar uban tane, ranar da yarinyar nan ta rasu na yi mata kuka ba kaɗan ba, so akwai abubuwa sosai da suke faruwa a cikin gidan nan, ciki kuma har da sayar da ƙodar mutane, sannan akwai kwashewa ƴara kayan cikinsu, abubuwa dai wayan da ba za su kirguba JEHAN laifukan da ake yi acikin gidan nan ba za su faɗu ba, a kama yaro aje a sayar da ƙodarsa makudan kuɗaɗe, idan ya fara rashin lafiya ko yarinya ta tashi a aiki sai aje wani garin a jefar da ita, kuma mafi yawancin lokaci idan sun cirewa yaro ƙodarsa ne suke zuwa wani garin su jefar da shi, sai ki ji ana cewa an tsinci yaro ɗan gari kaza a gari kaza, amma an tsinceshi lafiyarsa kalau ana neman iyayensa, ba wata lafiyarsa kalau, ba ta yadda za'ayi su saci yaro kuma su kai shi wani gari su jefar da shi ace ba wani abin da suka yi mashi, dole akwai dai wani abin, kamata ya yi idan yaron ku ya ɓata kuka gane shi, first abin da zaku fara yi akai shi asibiti ku biya ko nawa ne a chaje maku shi fes, ku tabbatar babu wani abin da ya rasa daga wani sassa na jikinsa, sannan kuce lafiyarsa kalau, domin akwai wani abin da idan aka cire a jikin mutun ba lallai ne ya yi ciwo a bayyane ba, kuma ma ya kan iya ɗaukar tsawon lokaci bai yi ciwo ba." WATA SHARI'AR SAI A LAHIRA, ALLAH ALHADULILLAH DA YA KASANCE AKWAI LAHIRA, RANAR DA ZA'A KWATAWA MARA KARFI HAKKINSA A WAJEN MAI KARFI, RANAR DA DUK WANI AZZALUMI ZAI ƊANƊANI KUƊARSA, ALLAH KA MANA SAKAYYA DAIDAI DA ABIN DA AKE YI MANA, WANI ABIN IDAN KANA JINSHI WLH SAI KA RANTSE DA ALLAH BA A DUNIYA KAKE BA, DUK WANDA YA GA YANA ZAUNE LAFIYA ACIKIN GIDANSA, YANA CI KO MA YAYA NE YANA SHA KO BA YAWA, TO YA GODEWA ALLAH KUMA YA ZAUNA A IN DA YAKE, WANNAN BALA'IN TA DUNIYARMU TA YAU SAI DAI ALLAH YA KAWO MANA SAUKI. TO IYAYE NA JUYO TA KANKU KALUBALE GARE KU WAƳAN DA ƳAƳAN SU SUKE ƁATA DA KUN GANE SU SHIKENAN AN WUCE WAJEN, AZO YARO KWANA ƊAYA KWANA BIYU YA ZAMA BABU SHI YA MUTU, TO DAN HAKA SAI KU KULA, A KULA DA YARA MASU ZUWA MAKARANTA, DAGA MATA HAR MAZA, YANZU SAYAR DA ƘODAR MUTANE HAR A ASIBITOCI ANA YI SOSAI, SAI A YI MAKI KARYAR ZA'AYI MAKI AIKI WATA MATSALA NA DAMUNKI, DAGA NAN SU SACE MAKI ƘODA, TO DAN HAKA SAI KU KULA, DA ZARAR AN YI MAKI AIKI A WANI ASIBITIN KIKA SAMI LAFIYA, TO KI GARZAYA MAZA IZUWA WATA ASIBITIN DAN A YI MAKI SCANNING NA KAYAN CIKIN KI, KI TABBATAR KOMAI YANA NAN KAFIN KI SAMU KWANCIYAR HANKALI, ALLAH YA MANA MAI KYUA!!!. STORY💖 Yau dai Jehan ta ji abin da ya kwance mata lissafin ƙwaƙwalwar ta, tunani ta fara yi tabbas akwai wata kawarta Zuhra da ta taɓa gaya mata cewa an sacewa yayan mamanta ƙodarsa a asibiti yanzu haka sun kai kara kotu da suka gane kenan, ashe abin da gaske ne sosai har haka, wato Hajiyar daɗi har da dillancin ƙodar ƴaƴan mutane suke yi kenan? Wannan wace iriyar bala'i ce, wato su kuma Alhazawan nan sai su zubawa ƴar mutane kayan tsafi a cikin cikinta saboda son abin duniya, siyasa ko dai kuɗi ko wani buƙata, innalillahi wa inna ilaihir rajiun wato dai kowa kuɗi kowa kuɗi, ko ta halin ƙaƙa sai anyi kuɗi, wannan bala'i da yawa take, yanzu bayan laifin zinar ma har da na shirka suke haɗawa waje guda, ga laifin cutar da yayan mutane a zuba masu wani kayan tsafin a ciki, ya ilahi ya lillihi wannan duniya ina zaki je damu, TO MATA MASU ZINA SAI DAI MUCE A KULA, IDAN BA HAKA BA ZAKI MUTU BA TARE DA KIN SAN DALILI BA, KU TUBA KU DAINA DOMIN SAMUN RAHMA WAJEN UBANGIJIN KU, KUMA KU TSIRA DAGA SHARRIN IRE-IREN WAYAN NAN ABUBUWA, WANNAN MA KAƊAN KUKA JI, AKWAI ABUBUWA DA DAMA DA AKE YI TA HANYAR ZINA WADDA ZAI ZAMA SANADIYAR RAYUWARKI CIKIN ƘANƘANIN LOKACI, TO DAN HAKA AKULA A TUBA KO DAN A TSIRA DA RAI. Ko motsin kirki Jehan ta kasa, tunaninta kawai ta ya ya za'ayi ta ruguza gidan Hajiyar daɗi, tabbas ko mutuwa za ta yi sai dai ta mutu amma ba zata bar wannan gida ba sai ta rusa shi, ya zama mata dole ta azabtar da rayuwar Hajiyar daɗi, ta jata akan titi, ta yi rayuwar walaƙanci, bai kamata wannan tsinanniyar mata ta yi mutuwar farad ɗaya ba, dole ta azabtu matuka, to ta wani hanya ya kamata mu fara? JEHAN ta tambayi kanta a cikin zuciyarta, yayin da ita kuma Aisha ta zuba mata idanu tana jiran ta ji me zata ce. Sun jima a haka kafin su Adiva su farka daga barcin da suke yi, ganin su jugum-jugum yasa Adiva ta tambayi menene yake faruwa? Jehan bata ɓoye mata ba ta gaya mata dan ta samu haɗin kansu su san yadda zasu rushe wannan gida na azzalumai. A haka Zinariya ta shigo ta same su, umarni ta bawa Adiva akan ta shirya da daddaren nan zata yi baƙo, rai a matuƙar ɓace Jehan ta ce "Babu in da Adiva zata je". Kallon sama da ƙasa Zinariya ta yi mata kafin ta ce "To sai ki hana mu gani" ta kai karshen maganar tare da juyawa zata fice daga ɗakin. Dakatar da ita Jehan ta yi da cewa "Ke tsohuwar kilaki, ina mai tabbatar maki da hakan, kuma zaki gani, ba ma Adiva ba, duk cikin mu huɗu dake a cikin ɗakin nan babu wanda zai sake zuwa wajen wani tsinanne kafurin banza, idan kuma kuka matsa sai kun alaƙanta mu da hakan, to wlh ina mai maki rantsuwa da sunan Allah sai na zama sanadiyar rayuwar duk wata marakunya da ta shigo gaya mana akwai baƙo, bayan haka kuma mu haɗa da baƙo duk sai munci ubanku, ƴan iska tsinannu, wlh ina da tabbacin babu abunda kuka isa ku yi mana, domin babu in da karya ta taɓa ɗauruwa akan gaskiya, tun daga farko Al Qur'ani mai girma har karshe ta, maganar Allah ne a cikinta, kuma babu a in da Allah ya yi alkawarin taimakawa azzalumai, sai dai ma ya ruguje daular zalunci, wlh idan baki tuba kin koma ga Allah ba sai kin yi mutuwar walaƙanci, mutuwar kare ma sai ta fi taki daraja, shegu kafuran banza tsinannu, duk abun da kuka ga dama ku zo ku yi Mani, kuma ina son ki buɗe kunnanki da kyau ki saurare ni dukana da kuka yi wlh baku yi shi abanza ba, ki jira kiga karshen iskanci, ku karyar iskanci kuke yi, da JEHAN kike magana, ƴar fari a wajen jaru kuma jajirtatcen jan wuyar namiji, ubana ɗayane tamkar da dubu, baya da tsoro gaskiya kawai ya sa a gaba ya kuma riƙeta, to akan haka ya renemu, ki rubuta ki ajiye wlh nice zan zama sanadiyar rugujewar wannan gidan". Duk wannan magana da take yi cikin harshen turanci ta yi shi, hakan yasa Zinariya bata wani fahimci kan zancen ba, dan bata yi wani karatu ba, amma dai ta gane zaginta Jehan take yi, dan haka sai ta dawo cikin ɗakin rai a makutar ɓace ta ɗaga hannu zata mare ta. Yau iya ɓacin rai ran Jehan ya ɓaci, jikinta har ɓari yake yi saboda baƙinci, zuciyarta sai tafasa yake mata, idanunta sun rufe bata ji bata gani, yau zuciyarta ta bushe babu alamar tsoro ko kaɗan a cikinta, dan duk zuciya mai imani idan ta ji abin da ake aikatawa a gidan Hajiyar daɗi sai ta girgiza, a fusace ta ruƙe hannun Zinariya tare da zabga mata wani mahaukacin mari mai doɗe kunne na wucin gadi, wani irin dum Zinariya ta ji, kunnuwanta sun daina jiyo mata sautin komai saboda marin da ta sha wajen D.P.O. Wani irin daɗi su Adiva suka ji, dama ita Adiva tasan halin jenan sarai akwaita da ɗaukar zafi kuma bata ɗaukar raini ko kaɗa, idan ka kawo mata wargi yanzun nan zata sa kayi nadama, akwaita da jan ajinta bata shiga abinda bai shafeta ba, ko wanda ya shafetan ma idan ba mai girma sosai ba bata kula shi, mace ce ita mai class sosai. Good 3mins Zinariya ta ɗauka tsaye a wajen dafe da kuncinta tana hawaye, kwata-kwata bata iya jin sautin komai kunnenta ya doɗe, Jehan kuwa tana tsaye tana huci kamar wata zakanya, yau sun kureta, bata san laifin da suke aikatawa ya kai har haka ba. Bayan minti biyar ne Zinariya ta dawo daidai, sai ta yi yunkurin damkar wuyar jehan ta daketa, ai kuwa Jehan bata bata wannan damarba zullewa ta yi tare da kwashe kafafunta sai ga Zinariya a kasa ta zube. Cikin fushi ta miƙe ta nufi waje tana faɗin "Ki jirani ina zuwa". Guntun tsaki Jehan ta ja kafin ta ce "Sai kin zo ɗin, ina jiranki, fita ɗakin nan ne babu wace zata sake fita dan wani ɗan iska banza ya zo ganinta, wlh idan kuka yi wasa duk sai mun dafa ruwan zafi mu saluɓe fatar jikin duk ɗan iskan da ya zo gidan nan yayi gigin tunkarar mu da sunan ya zo biyan buƙatarsa, ba dai muna da cattle na dafa ruwan zafi a nan ba, to ku jira ku ga sabon ta'addancin ƴan mata, ƴan iskan kawai, ai karyar iskanci kuke yi, wlh duk ƴan gidan nan sai na hure masu kunne na yi masu wa'azi su farka mu haɗa karfi da karfe muci uban ku dan ubanku. Tana magana tana huci, haka ta koma bakin gado ta zauna tana jiran Zinariyar ta dawo, yau ashirye take ta ci uban duk wanda ya kawo mata wargi. (TO FAH BABBAR MAGANA JEHAN DAI TA ƊEBO DA ZAFI, TAYI ABU CIKIN FUSHI, NI DAI NA HAƊA KAYANA ZUWA GIDAN ABBI DAN JIN YA AKE CIKI, WATA KILA KAFIN MU DAWO ZINARIYA TA DAWO MUGA SHOW TSAKANINTA DA D.P.O. TA MAMAN YASMIN.) 💖GIDAN ABBI💖 A ɓangaren Akila, duk ta gama ruɗar da Irfan, bawan Allah ya kasa hakuri miƙewa ya yi ya zura jallabiya a jikinsa sannan ya nufo kofar fita. Yana fita bai tsaya ko'ina ba sai cikin gida, waya na makale a kunnensa yana karɓar sakon kalamai nata tare da shagwaɓa kala kala, a palo ya isko Abbi, Aunty, Imran, da kuma Rimsha da take cin abinci Imran ya tasa ta a gaba. Bai wani bi ta kansu ba ya wuce ya haura sama, da kallo Abbi ya bishi kawai, bai wani damu ba kuma bai tambaye shi ina zai je ba. Bai yi sallama ba kawai ya faɗa ɗakin, Aafia da Hanan suna zaune a ta bakin gado suna hira, ita kuma Akilar ta bawa kofar shigowa baya tana rungume da pillow a kirjinta, ga waya na makale a kunnenta yayin da hannunta ɗaya ke a jikin headboard na gadon tana wasa da yatsunta, sai hira take zuba mashi. Da hannu ya nunawa su Aafia hanyar fita daga cikin ɗakin ba tare da ya yi magana ba, ba musu suka fice da sauri. A hankali ya tako zuwa bakin gadon, cikin dabara ya haye saman bed ɗin tare da matsowa kusa da ita, bata taɓa zaton zai zo ba, sai zuba mashi shagwaɓa take yi, jin ya yi shiru baya magana ya sa ta kara shagwaɓe murya ta ce "Yaya Irfan shine ka barni ina ta magana ka yi shiru ko? To wlh na yi fushi kuma ba zan ci abincin dare ba, ba zan sake kula ka ba". Tana magana tana turɓune fuska irin na shagwaɓa Zuba mata ido kawai ya yi yana kare mata kallo ya kasa magana, ba abin da yake kallo sai kyakkyawar sajenta dake kwance a gefen lallausan kumatunta, yana ɗan kawar da idanunsa karaf sai kan breast nata da yake tana kwance wuyar rigar tata ta ɗan yi kasa, hakan kuma ya yi daidai da juyowanta dan ta duba wayar ta gani ko ya katse kiran ne tun da ta ji shiru. Karaf suka yi ido huɗu, ba ƙaramin tsorata ta yi ba, a zafafe ta wage baki zata yi mashi ihu dan a tunaninta aljanine, cikin sauri ya sanya hannunsa ya rufe mata baki yana girgiza mata kai. Dafe kirjinta ta yi tare da fara ruwan hawaye dan har ga Allah ta tsorata sosai, a hankali ya zame hannun nasa daga bakin nata, kasa kasa ya ce "Sorry, am so so sorry". Kuka ta sa mashi tana bubbuga kafa a saman gadon, hannu ya kai ya fara goge mata hawaye yana faɗin "Tuba nake yi my heartbeat, ba zan kara ba". Turo baki ta yi tare da zuro kafarunta kasa zata sauƙa daga gadon, da sauri ya riƙota yana faɗin "Ina kuma zaki je? Ba nace na tuba ba?". Kara shagwaɓe murya ta yi ta ce "Ni ka sake ni mun ɓata da kai ai, tun da zaka zo ka tsorata ba abin da na yi maka". "Haba matar Mijinta, yanzu fa kika gama ce mani ke jarumace ko dai kin mance ne?". Wani irin kallon soyayya ta yi mashi wadda ya sanya shi sauƙe nauyayyar ajiyar zuciya, juya fararen idanunta tayi tare da turo baki kamar biro ta kara narke murya ta ce "Yaya Irfan Allah ba zan kyaleka ba, sai na rama". "Kai heartbeat ki rufa mani asiri, yanzu ma baki ce zaki rama ba ma ya na kare dake bare kuma kin ce zaki rama, ai sai ki haukatar da mijin naki". Saboda iya shege irin nata sai ta sanya hannu ta rufe fuskarta ta na faɗin "Yaya Irfan ni kunya nake ji idan kana zancen mijin nan, ni ka daina bana so, idan ba haka ba Allah kuka zan yi maka". Akila ta gama tafiya da imaninsa, bawan Allah bai taɓa yin soyayya ba sai akan ta, ya so Ayla sosai amma ba su yi soyayya ba, abun da bai saba ba sai ya ke jin sa a wata duniya ta musamman, ga shi kuma ya yi sa'a ya haɗu da kwararriya a fagen soyayya, ta kware sosai, idan tana magana ma har wani lanƙwasa magana take yi kamar dai Hajiya Batula da mijinta, kamar yadda take gaya maku Hajiya Batula take yi, ita ma yanzu haka take yi wa Irfan, ko kiran sunan sa zata yi sai ta wani lanƙwasa sunan ta sanya mashi salo na musamman, hakan ba ƙaramin kara rikita shi yake yi ba, shiyasa ya fito ya zo domin yaga yadda take maganar nan da idanunsa dan ya tabbatar da cewa ita ɗin ce ba wata ba. Sai dai fa, akwaita da bala'in kunya sosai da sosai, amma fa kunyar ba asalin kunya da kuka sani bane, wannan shi ake kira da kunyar rashin kunya, domin da gangan take cewa tana jin kunyar domin ta kara haukata masoyin nata, da gangan take rufe ido ta rinƙa ce mashi bata so tana jin kunya dan ya kara narke mata, mafiya yawancin maza suna son hakan, kaso 80 cikin ɗarinsu suna son irin hakan, sai macen da ta iya fahimtar sune zata gane hakan, ita Akila da yake ta yi degree a fagen soyayya duk ta gama sanin lagon maza, hakan yasa take yi wa Irfan wannan tsiya wai tana jin kunya. "Heartbeat kina kara mani soyayyarki sosai a cikin zuciyata". "Yaya Irfan na ce maka Allah kunyar maganar nan nake ji fa, wai ba zaka daina yi mani ba?" Ta faɗa tana kara rufe fuskarta da hannunta sosai. Riƙo hannayen nata ya yi ya buɗe fustar tata yana faɗin "To waye ne yanzu ya gama ce mani zai bani abincin dare a baki?". Ƙoƙarin tashi ta yi dan ta gudu, wai kunya take ji, riƙota sosai ya yi ya dawo da ita ya zaunar yana faɗin "Eyeee wato a awaya ba'a jin kunya har da cewa za'a bani abinci a baki, shine yanzu kuma gani ido da ido a maimaƙon a zubamani kalamai masu daɗi da suka fi na waya shine zaki gudu ko?". Kawar da kallonta gefe ta yi ba tare da ta yi magana ba, "Au ba zaki yi wa mijin naki magana bane?". Shiru ta yi mashi taki yin magana, hancinta ya ɗan ja tare da sakin hannayen nata ya diro kasa daga saman gadon ya koma saman bedside drawer ya zauna yana faɗin "To juyo mu yi magana kin ji gimbiyata? Heartbeat namu gaba ɗaya". Ba musu ta juyo suna fuskantar juna sai dai taki yarda ta haɗa idanu da shi, kasa take kallo abinta. Hira ya fara janta da shi dan ta saki jiki su zuba soyayya son ransu. A ɓangaren Akil kuwa sosai suke murjan juna shida Umaisha a cikin mota, duk ta kiɗima shi ya fita a hayyacinsa, bashi da wata buƙata da ya wuce ya ji shi a cikin jikinta, Akil irin jarababbun mazan nan ne na ƙin karawa. Shi ma daddyn Jelly romancing nata ya yi sosai amma bai kai ga shigarta ba, saboda ya yi wa kansa alkawarin sai ta kara girma, sosai ta rinƙa yi mashi kuka akan breast nata suna yi mata ciwo, duk bakinsu ya yi ja sun sha murza. Rarrashinta ya fara yi yana bata hakuri akan ba zai kara ba, rungume shi ta yi tana faɗin "Daddyna ina son duk wani abin da kake so, amma wannan yana yi mani zafi ne sosai". Runtse idanunsa ya yi dan baya son su haɗa ido, kasa kasa da kyar ya ce "Baby anya zaki iya ɗaukar ciki kuwa? Gaskiya kin cika ragwanta sosai" ya kai karshen maganar tare da sauƙa daga kanta ya koma gefe ya kwanta yana kara jawota jikinsa. "Daddy dama ina son in tambaye ka". Jinjina mata kai ya yi alamar yana jinta domin ba zai iya cigaba da yin magana ba. "Daddy na na ji ance idan mutun ya yi aure ne yake samun ciki ya haihu, tom nikuma naga har yanzu ban sami cikin ba kuma ban haihu ba, ina son kuma na haifi baby Nima". A hankali ya waro wayan nan dara daran idanun nasa wadda suka sauya launi akan face nata, da kyar ya iya fara magana "Baby kina son Haihuwa ne?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e. Jinjina mata kai ya yi kafin ya ce "Zaki haihu In Sha Allah amma sai kin kara girma, yanzu ba zaki iya ɗauka na bama bare kuma baby". Shiru ta yi tana nazarin kalamansa, Me yake nufi da ba zata iya ɗaukar shi ba, kamar zata sake yin magana sai kuma ta fasa ta kwantar da kanta a saman kirjinsa tana sauƙe numfashi a hankali hankali. After some hours da basu biyu ba. A'A SALAHUDDEEN ne ya kira Imran a waya akan ya shigo garin Kaduna, address ɗin gidan Abbi Imran ya tura mashi kana ya zo nan ya same su, baafi minti 20 ba sai ga shi ya zo, a lokacin kuma su Akil duk sun dawo palo, shima Irfan ya sauƙo tare da Akilar, sai wani ɓoye fuska na rashin kunya take yi, dan ma kada ya takura mata sai ta gudu kusa da Abbi ta zauna, ita ma Umaisha kusa da Abbi ta zauna, Aafia kuma kusa da Aunty while ita kuma Hanan tana kusa da Rimsha dake zaune a gefensu Imran, shi ma Irfan ɗin kujerar kusa da Imran ɗin ya zauna, sai hira suke yi ko wani masoyi yana satar kallon masoyiyar sa, a haka A'A ya iso ya same su. Da yake bai san su Abbi a fuska ba sai dai a bakin daddyn Jelly yake jin sunan su, sai bai gane su ba, lokacin kuma daddyn Jelly sun yi barci rungume da juna shi da amaryarsa a part nasu. A takaice A'A bai san cewa Imran ɗan yayan daddyn Jelly bane, a family'n daddyn Jelly gaba ɗaya daddyn kawai AA ya sani domin idan baku mance ba kun dai san yadda zumuncin su yake, ba wani zuwa gidan yan uwa suke yi ba, shima A'A ba mazauni bane bare ace watara zai haɗu da Imran a Kano, sunan su Abbi ma sanadiyyar ɓatar Jelly A'A ya sa ni, daya kiran daddy sai yake gaya mashi cewa yana Kaduna gidan Abbi ga shi ga shi abin da ya faru da Jelly, to kun dai ji rashin zumuncin su. Gaisheda Abbi da Aunty A'A ya fara yi kafin nan su gaisa da Imran, Irfan, Akil, bayan sun gama ne su Aafia suka ɗaga mashi gaisuwa. Cike da fara'a ya amsa tare da tambayarsu ko suna lafiya, da lafiya suka amsa mashi, Rimsha ce kawai bata gaishe shi ba, Imran ya sha ruwan mamakin me yasa bata gaishe da A'A ba, Allah sarki baiwar Allah basu san cewa tana can duniyar tunani bane, hasalima bata san da shigowar Ahmad ɗin ba, buƙatar ta kawai ta sami hanyar da zata kuɓutar da Ayla. Taɓa ta Imran ya yi yana faɗin "Rimsha tunanin me kike yi ne haka?" Wata iriyar firgita ta yi wadda sai da kowa na wajen ya ɗan tsorata. Imran, Abbi, Akil, A'A, har suna haɗa baki wajen tambayarta ko lafiya, ta kasa magana sai dai kawai suka ga hawaye ya fara bin kuncinta, Subhanallah suka furta suna haɗa baki. Imran ne ya fara jawota jikinsa yana faɗin "Rimsha lafiya? Me ya faru? Me akayi maki". Cike da tashin hankali A'A ya miƙe ya kariso wajen suka haɗu suna rarrashin ta tare da tambayar menene yake faruwa, ta kasa magana sai kara karfin gudun kukan nata take yi, Aunty Abbi duk kowa ya yo kanta suna rarrashinta amma ta ki yin shiru kuma ta ƙi yin magana, abin ya ɗaure masu kai. Da yake Akil yana da basira ga ilimi sai ya yi amfani da hakan ya ce "Yaya Imran ku kyaleta ina ga abin da yake damunta bai shafi namiji ya sani bane, kasan ance ciwon ƴa mace na ƴa mace ce to dan haka ku kyaleta ta keɓe da Aunty ko kuma Heartbeat tun da ita ce kawarta sai ta gaya mata abin da yake damunta, idan abune wanda ya kamata mu sani sai a gaya mana, idan kuma bai kamata ba sai su rufe kayansu tare da bata shawari mai kyau, na san Aunty ba zata bata shawara na banza ba". Abbine ya amsa da "E gaskiya Akil kana da gaskiya ina ga hakan za'ayi " Girgiza kai Imran ya yi yana faɗin "No babu wani abin da Rimsha zata iya gayawa Akila wadda ba zata iya gaya mani ba, dan haka ina zuwa ku bamu five minutes" ya kai karshen maganar tare da miƙewa ya riƙo hannunta suka fita waje, cikin sauri A'A ya yi yunkurin bin bayansu, Irfan ne ya riƙoshi tare da ce mashi "Cool down bro, idan ka je zata iya kin faɗa mashi menene yake damunta, dan haka ka yi hakuri, yanzu zasu dawo ai". Zama A'A ya yi saman sof tare da buga uban tagumi zuciyarsa na yi mashi zafi, to menene yake damun masoyiyar tasa? Ya tambayi kansa a cikin zuciyarsa. Imran kuwa yana fita bai tsaya ko'ina ba sai wajen motarsa, buɗe gidan baya na motar ya yi ya shigar da ita sannan shima ya shiga ta ɗayar ɓangaren. A nutse ya fara tambayarta menene yake damunta, cikin kuka ta ce mashi babu komai, girgiza kai ya yi tare da sake tambayarta a karo na biyu, nan ma babu komai ta ce mashi, ya sake tambayarta a karo na uku, shima ta ce mashi babu komai, ransa a ɓace yasa hannu zai buɗe kofar motar ya fita. Cikin sauri ta riƙo hannayen nasa tana faɗin "Yaya Imran dan Allah kayi hakuri zan gaya maka". Juyowa ya yi suna fuskantar juna ya ce "To faɗi ina jinki". Nisawa ta yi tare da fara ba shi labarin duk yadda suke yi da Malika bata ɓoye mashi ba, sai dai cikin hikima ta sakaya maganar. Duk da sakayawa da ta yi ya fahimtar sai dai bai yarda da zancen ba, idan baku mance ba daga Imran har Akil manyan malamaine, akwai ilimin addini sosai, sai dai Akil ya ma fi Imran ɗin ilimi addinin sosai, har cikin zuciyarsa bai yarda da zancen boka ba haka ita ma Malika bai yarda da zancen ta ba, ga shi kuma Malika ta tafi ta cewa Rimsha sai gobe zata zo bare kuma Rimsha ta kira ta domin ta tabbatarwa da Imran gaskiya take faɗa. Goge mata hawaye kawai ya yi tare da ce mata zai gayawa daddy, ya yi mata haka ne dan ta yi shiru amma ba wai dan ya ɗauki abin serious ba, hasalima suna fita daga cikin motar ya watsar da maganar suka koma cikin gida. Suna shiga cikin palo A'A ya miƙe yana tambayar me yake damunta ko bata da lafiya ne. Shiru Imran ya ɗan yi kafin ya ce "E cikin ta yake yi mata ciwo, amma ba komai ku yi hakuri kun san yarinya ce kuma bata saba da gidan nan ba shiyasa ta fara kukan ciwon cikin". Tsab Akil ya gane ba gaskiya Imran yake faɗe ba domin yayiwa yayan nasa farin sani, ko bai ga idanunsa ba ya yi karya sai ya gane, da kallo ɗaya ya yi wa Rimsha kuma ya fahimci tabbas tana cikin damuwa sosai dan haka sai ya kudura a ransa cewa sai ya tambaye ta me yake damunta anjuma da daddare. Zama suka yi suka cigaba da hira, sai lallaɓa ta suke yi, har da su Abbi ma, A'A kam baa magana ya fi kowa lallaɓata, da ta yi motsi zai tambayeta lafiya, daga karshe dai kwanciya ta yi a saman cinyar Imran tana sauƙe ajiyar zuciya har barci ya yi awon gaba da ita. Hirar duniya suka fara yi har aka kira sallar mangariba ba, a tare mazan suka fita zawa masallacin, a hankali Imran ya kwantar mata da kanta a saman sofa ya bi bayansu zuwa masallaci, matan kuma gaba ɗaya suka wuce sama dan yin alwala su yi Sallah..... NIKUMA NA HAƊA KAYANA SAI GOBE IDAN MAI DUKKA YA KAI MU 💖💖TRIPLETS💖💖 E73-74💖 Hirar duniya suka fara yi har aka kira sallar mangariba ba, a tare mazan suka fita zawa masallacin, a hankali Imran ya kwantar mata da kanta a saman sofa ya bi bayansu zuwa masallacin, matan kuma gaba ɗaya suka wuce sama dan yin alwala su yi Sallah. Bayan sun yi sallah sun dawo ne, A'A ya buƙaci yana son keɓewa da Rimsha su yi magana dan zai wuce Abuja a daren nan, alokacin kuma ita ma ta tashi har ta yi sallah abinta, suna zaune a palo suna ƴar hira da su Aunty, amma ita hankalin ta na akan Ayla ce. Imran bai hana A'A ba kuma bai taka mashi birki ba, da kansa ya kama hannun Rimsha suka fito waje, saboda yana son ta rabu da kowa lafiya, domin ɗan adam ba'a shaidar sa, musamman akan abin da yake so, to ba'a yi mashi shaida ta ɓangaren zuciya. Sun ɗauki minti talatin a tsaye bayan e da a'a ba wani abin da take ce mashi, bai damu ba saboda ya san halinta ne rashin son magana, kuma yasan yau bata da lafiya, hakan yasa ma bai ja ta da hira sosai ba, kaɗan suka tattauna suka yi sallama, makudan kuɗi ya ɗauko ya bata, amma taki karɓar, ba yadda bai yi da ita ba, amma ta kafe ta ce bata so, haka ya hakura ya wuce da kuɗin, har lokacin kuma bai sami haɗuwa da daddyn Jelly ba, domin daddy dai barci ne mai nauyi ta kwashe su, bai farka ba sai lokacin da ake kiraye kirayen sallar Isha, a lokacin ya farka kuma A'A ya wuce Abj time ɗin. Wanka ya fara yi kafin nan ya ɗauro alwala ya zo ya fata gabatar da sallar mangariba dake a kansa, bai tashi Ayla ba ya kyaleta tana barcinta abinta. A ɓangaren Rimsha kuwa bayan A'A ya tafi sun yi sallama sai ta juya zata koma cikin gida, ido huɗu suka yi da Akil wadda ya fito yanzu, rai a ɓace ya ce "Waye kuma wannan?" Kasa ta yi da kanta tana ƴan kame kame, sake maimaita mata tambayar ya yi a karo na biyu. Cikin in..ina ta gaya mashi waye ne, tsawa ya daka mata tare da yi mata gargaɗi akan idan ya sake ganin ta tsaya da wani namijin sai ya ƙaryata, wannan sam ba tarbiya bace, kuma ita yarinya ce bai yarda da hakan ba, ta tsaya ta natsu ta yi karatu, duk wadda yake son ta to ya zo ya same su, idan sun duba hankalinsa da yanayinsa sun san tushensa sai su bashi damar hira da ita, kuma hirar ma a cikin Palo za su yi, ba'a keɓe a harabar gida ba, dan idan ta sake yin gigin tsayawa da wani namijin sai ya yi mata duka. Kasa ta yi da kanta tana bashi hakuri tare da gaya mashi cewa abokin yaya Imran ne, domin Imran ya gaya mata alakar dake a tsakaninsa da A'A. Dakatar da ita ya yi cikin fushi kun san halinsa da zuciya dama, baya son abin da zai kaucewa Shari'a hakan ya sa ya ce mata ko da yaya Imran ɗin ne da kansa yake sonta sai ya fara neman izini daga manyanta dan haka shin dai ya gaya mata kada ta bari ko da sunan wasa ya sake ganin ta da wani namijin sun keɓe suna magana, baya son hakan. Sosai ta rinƙa bashi hakuri tare da yi mashi alkawarin ba zata sake ba, sai cizan yatsa yake yi, ya so ace ya fito ya sami A'A da sai ya daka mashi warning akan kada ya sake kula mashi kanwa, idan aurenta yake son yi to ya bari sai ya sami izini daga wajen su Abbi bayan sun yi bincike akan waye shi ya halinsa yake, amma abin haushin A'A na barin gidan shi kuma ya fito, bai san suna waje ba da tun ɗazun zai fito. Cikin natsuwa ya fara tambayarta menene yake damunta? Kin faɗa mashi ta yi tana ɓoye ɓoye, da ƴan kame kame. Dabara ya yi mata ta hanyar amfani da ilimin da Allah ya bashi, ya ce mata ai sun yi magana da Imran to yana son ya ji daga bakin tane. Jin hakan yasa ta gaya mashi gaskiya abin da yake faruwa, shiru ya yi yana nazari akan maganar. A iya zaman da ya yi da ita ya fahimci ita mace ce mai addini ga ilimin boko da Arabia, sannan akwaita da gaskiya da amana, bata da hayaniya, yasan da cewa tabbas abin da ta gaya mashi hakan ne, kuma yasan da cewa sihiri gaskiya ce sannan kuma suma aljanu akwai masu gaskiya masu amana wayan da basu cutar da ɗan adam, idan ma suna tare da kai to sai dai su tallafa maka, ya san cewa Rimsha ba zata yi mashi karyar aljana ba, saboda Rimsha yarinya ce, kawai ma dan tana da tsawo da kuma dirarren jikine yasa ake yi mata kallon kamar ƴar 16 years alhalin 14 years ke gareta. Sun ɗauki lokaci mai ɗan tsawo tsaye a haka kafin ya yi kasa da murya cikin natsuwa da ilimi ya fara magana "Duk abin da kika faɗa na yarda gaskiya ce, ina son idan wannan Malikar ta dawo ki tambaye ta wace ce ta bada wannan aiki, sannan ki tambayeta waye da waye aka yi wa aikin ko zaayi wa, babban abin da yasa na gasgata maganar ki, na san dai ke a ƴan shekarunkin nan baki ma san abin da ake nufi da aure ba, soyayya ma baki san ma'anar ta ba, ba zance baki yin soyayya ba, amma baki san menene ma'anar yinta ba a yanzu, so ba zaki iya zama ace ki tsara wannan karya ba, ta ya ma kika san kwanciyar aure da har zaki tsara hakan? Sam wannan ba karya bace gaskiya ce zalla, amma yanzu kin san me nake so da ke?". Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a. "Good, idan muka koma cikin palo yanzu, zan gayama Aunty kina son yin magana da ita, zan kuma gaya mata da ta ɗauki maganar da mahimmanci, idan kuka keɓe da ita ki gaya mata hakan ki ce na ce ta gayawa Abbi, idan kika yi hakan shikenan ƴar uwarmu kuma amaryar bappanmu zata tsira". Ya kai karshen maganar yana riƙo hannunta dan su koma cikin gida, gaba ɗayansu kallon yarinya suke yi wa Rimsha, shiyasa basu wani damu ba suke ruƙeta, musamman ma Imran a yarinya kuma kanwa uwa ɗaya uba ɗaya ya ɗauke ta, hakan yasa har rungumarta yake yi. A ɓangaren ita ma Rimsha ta ɗauke su ne tamkar ƴan uwanta, tasan ba zasu cutar da ita ba, musamman ma Imran da Akila sun fi shiga ranta, hakan yasa ta fi sakin jiki da su, shiyasa bata damu ba koda sun ruƙe mata hannu, kuma bata damuwa dan Imran ya rumgumeta, Akil ne da bata saba da shi sosai ba, kuma ta ga yana da zafin kai sosai, shine take ɗan ja baya da shi dan tsoro ma yake bata. Zaune gaba ɗayan su a palo suka isko su aunty sai zuba masu tsiya take yi, kusa da ita Akil ya zo kasa kasa ya ce ta kira Rimsha suje ɗaki akwai maganar da za su yi, kuma ta ɗauki maganar da mahimmanci. To ta masa mashi da shi tana murmushi, shi kuwa Imran hankalinsa na a kan wayarsa, Abbi da Irfan kuma suna hira, while su Umaisha ma suna tasu hirar ita da Akila da A'afia da Hanan, sun lula duniyar hira babu kama hannun yaro. Miƙewa Aunty ta yi ta ruƙo hannun Rimsha suka haura sama, da ido kawai Abbi ya bisu yana tunanin ko dai ba lafiya bane, to me yake damun Rimsha ne? Ya tambaya acikin zuciyarsa tare da cigaba da hirar da suke yi shi da su Irfan, su Akila kuwa suna duniyar hira basu ma lura da Aunty da Rimsha da suka haura sama ba. Kusa da su Akil ya zauna suka cigaba da hirar. Wayar Akila dake a gefenta ne ya ɗan yi kara alamar shigowar sako, ɗaukar wayar ta yi tare da cire password ɗin wayar. Tasha ruwan mamakin ganin saƙo da unknown number, ɗan taɓe baki ta yi tare da buɗe saƙon dan ganin me ya kuntsa. "Assalamu alaiki warahmatullahi taala wa barkatuhu, barkar ki da dare ya bugun zuciyata, amincin Allah ya kara tabbata agareki tauraruwar mata ta duniya, gaskiya yau kin yi kyau sosai da sosai, kallon farko soyayyar farko, kada na cika ki da surutu na barki lafiya sai zuwa anjima zaki ga saƙona ya shigo, yanzu dai ina son ki san da zama ne, saƙo daga ƁOYAYYEN MASOYI". Shine abin da yake rubuce a cikin saƙon, ɗago kai ta yi tare da kallon su Irfan dake a zaune saman sofa while su kuma dama suna kasa a tsakiyar carpet ɗin ne. Hira kawai su Irfan suke yi, babu wanda yake ruƙe da waya ma a cikinsu sai Imran, shi kuma ya duƙar da kansa kasa yana kallon wayar da alma wani abin ya ke kallo ma, ba ma taɓa screen ɗin wayar yake yi ba bare kuma ta ce shine ya yi mata irin wannan wasa, ɗayar hannunsa ma tana ɗaure saman sofa da hannu ɗaya ya ruƙe wayar tasa, shi kuma Irfan wayarsa tana zaune kusa da shi bai taɓa ta bama bare kuma har ya kai ga rubuta saƙo, shi kam Akil wayar ma tana cikin aljihu, dawo da kallonta kan su Aafia ta yi dan taga ko dai sune suke yi mata irin wannan wasan. Sai taga gaba ɗayansu babu ma wadda waya yake a hannunta, dukkansu wayoyinsu na a zaune a gefensu, to waye wannan? Ga kuma dai number unknown number ce bare ta ce, zata kira dan ta ji wanene, amma koma waye da alama ya yi mata farin sani ko kuma yana da alaka da ita, domin hausar da ya rubuta mata sak irin hausar Kaduna ce. Tana tsaka da mamaki sako ya kara shigowa, cikin sauri ta duba, unknown number ɗazun ce dai, saƙo ne yake rubuce kamar haka. "Haba heartbeat me yasa zaki wahalar mani da kanki wajen waige waigen neman waye ya turo maki saƙon, to ki daina wahalar mani da kan ki bana so, and then please ki ɗan yi mani murmushi zan ji daɗin hakan sosai kin ji my angel? Saƙo daga ƁOYAYYEN MASOYI". Babbar magana. Cikin sauri ta sake ɗago kanta ko zata gane wanenen, kamar dai yadda suke ɗazun haka suke yanzu ma, shi Imran ma da alama wani news yake karantawa a wayar tasa, domin ya tattara hankalinsa kaf akan wayar, ya natsu yana kallon screen ɗin. Kawar da kallonta gefe ta yi domin tasan Imran dai ba zan yi mata wannan abinba, suna uwa ɗaya uba ɗaya, to waye kenan?. Kamar zata yi kuka ta sake mayar da wayar zata ajiye. Sake turo mata saƙo ya yi a karo ba uku kenan. Da farko kamar ba zata buɗe ba, amma sai ta daure ta buɗe saƙon, saƙone kamar haka. "Heartbeat ba nace ki yi mani murmushi ba? Amma shine zaki ɗaure fuska? Idan kika yi kuka sai na ɗauke ki mun ta fi dake duniyarmu, ba zaki sake ganin kowa na daga ƴan uwanki ba, ki yi mani murmushi kuma ki daina neman waye mai turo maki sako dan ba zaki ganni ba, yanzu dai ayi mani murmushi ko kuma na zo na ja wannan ɗan bakin mai kama da birro, na kuma yi maki caƙulƙuli". Bata san time da kayatatcen murmushi ya kubce mata ba, wai bakinta kamar biro, shine abin da ya bata dariya, tana yin murmushin baafi minti 1 ba sai ga sakon shi ya kara shigowa. "Gaskiya wannan murmushi ya tafi da ni my angel, kin iya murmushi sosai, wow rufe idanunki bari na baki hot kiss a kumatu mu gani ko na iya". Cikin sauri ta ajiye wayar tare da tare kumatunta da hannayenta dan wai kada ya yi kissing nata, ai kuwa ji ta yi tamkar anyi kissed na kumatun nata, zaro idanu waje ta yi tana karanto duk wani addu'a da ya zo mata bakinta. Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun ta fara faɗe tana zare ido. A ɓangaren su Rimsha kuwa, kamar yadda suka yi da Akil haka ya gayawa Aunty, ita ma Aunty da yake akwai ilimin addini, ta fahimci maganar sosai da sosai, hakan yasa bata ɓata lokaci ba wajen kiran Abbi a waya akan ya zo ɗaki, ita kuma Rimsha ta ce ta koma palo kada ta damu. Abbi bai ɓata lokaci ba wajen zuwa ɗakin, ba ɓata lokaci Aunty ta gaya mashi abin da yake faruwa, sosai ya sha ruwan mamaki tare kuma da yi wa Allah subhanahu wata'ala godiya sosai akan Allah ya so su da rahma, Allah ya kaddara ɗan uwansa bashi da rabon shiga wahala a karo na biyu, dukkan su sun yarda da zancen Rimsha, domin wannan bama zance ce da za'ayi karya akan ta be, me riba idan akayi karya akan gakan? Me ribar mutun da daddyn Jelly ya yi dis virgin ɗin Ayla? Cos wannan ba magana ce ma da za ace karya bace. Amma Abbi ya yi alkawarin bayan komai ya lafa zuwa jibi dole ya kira babban malami a yi masu saukar Al Qur'ani mai girma a gidan, tare da yi wa gaba ɗaya ƴaƴan karatu a kansu domin Allah ya kara tsare su Da haka Aunty ta ce Abbi ya kira daddyn Jelly ya turo mata Aylar yanzu, to Abbi ya amsa da shi tare da kiran layin daddyn. Lokacin da kiran ta shigo yana kan dadduma ya idar da sallar mangariba yana jiran a tada kabbarar sallar isha ya je masallaci tun da an yi kira tun minti 7 da suka wuce. Ganin Yaya Deen ne yasa ya yi saurin ɗaukar wayar, ba tare da nuna wasa ko wani abu makamancin hakan ba, Abbi ya ce ya turo mashi Ayla yanzun nan, sannan kuma idan suka fito sallar isha ya tsaya a bakin masallaci yana son yin magana da shi. Tom ya amsa da shi tare da katse kiran ya miƙe ya haye saman bed ɗin. Tana kwance kamar yadda ya kwantar da ita, sai zuba barcinta take yi cikin kwanciyar hankali, da alama barcin ya yi mata daɗi, dan yadda take sauƙe numfashi a hankali hankali. Fuskarta ya fara shafawa a hankali hankali, can kasa kasa a saitin kunnenta ya fara kiran sunanta yana shafa face nata. Cikin magagin barci a shagwaɓa ta ce "Uhm uhm daddy ka bari mana". Bakinsa ya kai saitin tata yana faɗin "Uhm uhm daddy ba zai bari ba har sai kin tashi". Jin voice nasa ya sa ta gane ba mafarki take yi ba, cikin sauri ta waro idanunta da suka yi ja saboda barci, karaf sai cikin nasa idanun, da sauri ya kawar da kallonsa, domin har ga Allah yana jin kunyarta, baya son su rinƙa haɗa ido, shi mutun ne mai kunya sosai. "Baby ta shi ki je Abbinki yana kiranki, daga nan sai ki yi wanka ki yi sallah ki kawo mana abincin dare". To ta amsa mashi da shi tare da yunkurawa zata miƙa, matsa mata ya yi dan ta miƙe. Bayan ta miƙe sai da ya rungumeta tare manna mata kiss a goshi yana faɗin "Ki kula mani da kanki". To ta amsa mashi da shi tare da cewa "Kai ma ka kula mani da kanka daddyna". Wani irin daɗi ya ji ta rufesa, cike da murna ya diro kasa daga saman bed ɗin, da kansa ya sanya mata hijabinta tare da rungumota sosai a jikinsa suka yi sallama. Cikin gida ta wuce while shi kuma ya wuce masallaci. A palo ta isko Aunty tana tsaye tana jiranta, su kuma su Aafia sun haye sama dan suje su yi Sallah. Tana shigowa Aunty ta riƙo hannunta suka wuce bedroom nata, wanka ta sata ta yi tare da gyare jikinta sosai, turatuka masu kamshi Aunty ta bata akan ta sanya, tsadaddun humrane masu shegen daɗin kamshi. Ayla ta sha mamakin ganin hakan, amma sai bata wani damu ba, ta yi duk wani abin da Aunty ta ce mata, sababbin kayan barci masu kyau da tsada Aunty ta fitar daga cikin kayan lefenta ta miƙa mata akan ta sanya. Ayla baiwar Allah bata musu da koma waye, to ne yake rabata da kowa, to ta ce tare da karɓa ta buɗe su. Wani ɗan iskan rigane wadda ba zai wuci gwiwa ba, sai kuma pant nasa wadda dukkansu jikinsu yana da tsantsi sosai, sanann gaban rigar a buɗe ana iya ganin pant ɗin da kuma cibiyarta zuwa iya saitin kasan kirjinta tsagun rigar ta tsara, ta bayar rigar kuma an kwashe bayan sosai, daga kafaɗarta har izuwa tsakiyar bayanta walam ne, haka rigar take. Cikin natsuwa ta sanya kayan, ba karamin kyau ta yi ba, sai tashin wani gigitatcen kamshi take yi. Bayan ta gama ne Aunty ya bata hijabi har kasa ta ce ta sanya ta yi sallah, karɓa ta yi tare da sanyawa ta shimfuɗa daddumar Auntyn ta tayar da Sallah. Ita kuma Aunty ta wuce kitchen dan ya shirya masu abinci mai daɗi. After some minutes. Dukkansu sun dawo daga masallaci sun haɗu a palo banda daddyn Jelly wadda kwata kwata ma bai dawo gidan ba. Shirya masu abinci a saman table Aunty ta yi tare da cewa su zo su ci, sannan ta ɗauki na daddyn Jelly da amaryarsa wadda ta shirya masu na musamman ta ajiye masu a saman carpet dake tsakiyar palon sannan ta kira Ayla akan ta zo ta ɗauka. Ba musu ta sauƙo kasa ta ɗauka jikinta na sanye da hijabi har kasa while kayan barcinta kuma na daga ta ciki. Rimsha ta saki jiki sosai yanzu, domin Aunty ta karfafa mata gwiwa akan ta kwantar da hankalin ta a cikin daren nan komai zan daidai ta, to ta amsa cike da kunya, sai tsokananta auntyn take yi. Su Abbi gaba ɗaya hayewa saman dining table suka yi, Aunty ne ta yi serving nasu dukkansu. Kusan a tare suka fara cin abinci, Umaisha tana zaune kusa da mijinta, da yake darene kuma wutar wajen dining table ɗin blue light ne ba'a gani sosai, sai Akil ya zura hannunsa ta kasan table ɗin yana shafa cinyoyin matarsa yana cin abinci da hannu ɗaya, ita ma time to time tana shafa masa gabansa duk kuma suna cin abinci. Shi kuwa Irfan ya zauna kusa da Akilarsa sai janta da hira yake yi amma taki biye mashi, domin zuciyarta tana can duniyar tunanin waye wannan masoyin ɓoyen?. Duk wani motsi idan ta yi sai ya yi mata massage akan ta yi kyau da ta yi kaza ko kuma ta gyara kaza, to waye ne wadda yake iya kallon duk wani abin da take yi?, Abin ya yi mugun ɗaure mata kai ba kaɗan kaɗan ba. Su A'afia kuwa abinci kawai suke ci, A'afia da bata da yawan cin abinci sosai ma yanzu zagewa take yi ta ci sosai dan idan bata ci ba zata sami matsala da Akil, duka zai yi mata, ya hana su wasa da cin abinci, akan haka har dukansu ya taɓa yi, shiyasa yanzu basa wasa da cin abinci, sosai suke bada himma. Bayan sun kammala cine Imran ya miƙe tare da ce da Rimsha ta shirya su wuce. Aunty da Abbi har suna haɗa baki wajen cewa ina kuma za su je, za su koma gida Imran ya basu amsa, nan fa Abbi ya ce a'a sai dai ya tafi ya bar Rimsha domin ita ta zo kenan. Dawo da kallon shi kanta ya yi, kamar zata yi kuka ta yi kasa da kai, Imran ya rasa ya zai yi sai ya ce "Bappa kayi hakuri gobe zan tattarota da kayan ta dukka na dawo da ita, amma dan Allah yanzu ka barmu mu kowa a tare kamar yadda muka zo, kuma dan Allah kada ka tambayi dalilin". Kallon Rimsha Abbi ya yi domin ya tambaye ta ko tana son ta bi Imran, bai kai ga tambayar ta ba, sai ya kalli tsantsan kaunar hakan a kan face nata, dan haka sai ya ce tom su tafi, domin baya son su yi mata abin da ba zata ji daɗin sa ba, kuma a tunaninsa, ai a gidan Abba suke, wato dai gidan su Imran ɗin, hakan yasa bai damu ba ya ce su tafi. Riƙo hannunta Imran ya yi suka fice daga palon suna yi masu sallama. Yana fita ya kira daddyn Jelly a waya akan ya fito su yi sallama za su koma, daddyn Jelly ya so hana su komawa, ya so suma su kwana cikin ƴan uwansu, amma sam Imran ya ki yarda, domin yasan tabbas Lion yana kewarsa, kara kawai yake yi mashi yasa bai kira shi a waya ba, kuma yasan ita ma Rimsha tana kewar Lion ɗin, kunyarsa kawai take ji yasa bata ce mashi su koma gida ba. Haka daddyn Jelly ya hakura ba dan ya so ba, ya ce masu baya gida kuma yana da ɗan nisa da gida, su je kawai sai sun sake haɗuwa. Da tom Imran ya amsa da shi sannan ya katse kiran ya shiga mota suka bar gidan. Su Abbi kuwa bayan sun kammala cin abincin, saman sofa suka dawo suka zauna aka dasa hira daga in da aka tsaya. Yanzu Imran ya tafi Akil sai abin da ya cigaba a pagen nunawa matarsa kauna, dama baya son jefa ɗan uwan nasa a cikin damuwa ne yasa ya daure baya tumurmusan soyayyarsa, yanzu kuma Imran ɗin baya nan. Kusa da Wife ɗin sa ya zauwa dama suna cin abinci ta yi ta yi mashi tsiya ta hanyar taɓa mashi gaba, so a kusa yake, shi hiran nan ma da suke yi ba hakan yake so ba, so yake kawai su shige cikin ɗaki da abarsa su murji juna son ransu, amma yanzu su Abbi sun takura masu. Akila da Irfan kuwa sai hira suke yi, amma kuma ga dukkan alamu kaso 80 cikin ɗari na hankalinta yama a kan wayar tane, tana ta fama da saƙon ɓoyayyen masoyi, duk wani motsinta yana gani, kanta ya kullu, ga shi ta kasa gayawa wani wannan magana, tabbas ba yaya Irfan bane, kuma ma ba ɗaya daga cikin ƴan gidan nan bane, to waye ne?. Ta shiga ruɗani abin ya kuma ƙulle mata kai sosai, lallaɓawa Irfan ya yi cikin dabara ya kirata akan ta zo su je waje. Cikin dabara suka zame zuwa waje abinsu. Suna fita ya riƙo hannayenta yana tambayarta me yasa bata bashi abinci a baki ba, kashe wayar tata gaba ɗaya ta yi dan ma kada saƙon ɓoyayyen masoyi ya sake shigo mata waya ya raba mata hankali gida biyu. Bayan ta kashe sai ta tattara hankalinta gaba ɗaya izuwa kan ɗan uwan nata, cike da kulawa ta ce "Yaya Irfan ai dan su Abbi sunanan ne, badan haka ba da na baka ai". Jin ƴadda take magana ne yasa shi ƴin murmushin, domin tun ɗazun rabon da ta yi mashi magana haka, amma da yake yanzu dare ne kuma sun fito wajen da akwai ɗan duhu duhu sai ta saki jiki ta fara yi mashi hira, dan baya samun ganin face nata sosai. Abin mamaki kuma abin al'ajabi sai ta ga wayarta ta kunna kanta da kanta. Wayar na kunnuwa kuma saƙon ɓoyayyen masoyi ne ya shi go, a wannan karon da turanci da kuma hausa ya rubuta mata saƙon, ba gaba ɗaya hausa ya yi mata ba. "Meyasa kika kashe wayarki? I don't like that, so ki kula, yanzu dai na kunna abata" ɗago idanu ta yi ta kalli Irfan dake a tsaye ya zuba mata idanu, kallon hannunsa ta yi kwata kwata ma babu waya. A tsorace ta ce "Yaya Irfan ina wayarka?" Hannu ya sanya a aljihunsa tare da ciro wayar ya mika mata yana faɗin "Ga shi nan, ya naga kamar yanayin ki ya sauya?". Girgiza mashi kai ta yi alamar ba komai, amma wannan lamari ya fara sakata a cikin ruɗani, ta yaya za'ayi ta kashe wayarta kuma a kunna mata? Wannan wace irinyar abu ce. Bincike ta fara yi a wayar Irfan, bawan Allah kwata kwata ma bai taɓa turawa mutun saƙo ba, yanzu ta ma dai na zarginsu, domin ba ta yadda za'ayi ta kashe wayarta tana ruƙe da shi a hannunta kuma ace mutun ya kunna mata ba tare da ya karɓi wayar ba, ba zai yi wu ba dole wannan aiki sai dai Aljani. Miƙa wa Irfan wayar sa ta yi tare da kakalo murmushin dole tana son tasa kada ya kawo zargin komai a ransa. Ta kuma yi sa'a bai kawo komai a ransa ɗin ba, suka cigaba da hiransu. Ɓoyayyen masoyi dai bai kyaleta ba sai da ya sake yi mata saƙo akan kada ta rinƙa yi wa ɗan uwan nan nata murmushi, shi kaɗai zata rinƙa yi wa murmushi, sannan shi ba zai hana ta kula kowa ba, shi zai kwata wa kansa ƴanci ta yadda ita da kanta ba zata sake yarda da kula kowa ba, so yanzu ta yi hiranta da koma waye, yana nan tafe ya ɗauketa kowa ya huta. BABBAR MAGANA. Wannan saƙon ya razana ta sosai kenan wai duk abin da take yi yana kallonta? Yanzu ta gama saddakarwa gamo ta yi wlh. Jikinta har kerma yake yi ta ce "Yaya Irfan mu koma cikin gida sanyi nake ji" mamaki ne ya bayyana akan face nasa, sanyi kuma, ya tambaya yana kare mata kallo. Ganin yadda jikinta ke kerma ne yasa ya yarda e sanyi take ji, amma ya yi mamakin hakan domin yau garin kwata kwata ba bu sanyi, sai ma zafi da ake yi dan an kwana biyu ba'ayi ruwan sama ba. Bai wani damu sosai ba, ya riƙo hannunta suka nufi cikin gida, amma ya sha mamakin ganin yadda jikinta yake ta faman kerma a lokaci guda. Suna isa bakin kofar palo ya saki hannun nata ya juya ya nufu part nasa yana faɗin "ki je ina zuwa" to ta amsa mashi da shi sannan ta wuce da wuri. Binta da kallo ya yi yana mamakin sauyawar ta a lokaci guda haka, to me yake damun tane? Ya tambayi kansa da kansa, tambayar kuma da bashi da amsar ta. Jikinsa a mace ya juya izuwa part nasa dan ya yi wanka yana jin zafi, abin da ya kara bashi mamaki kenan, shi yana jin zafi yana son ya zuba ruwa a jikinsa, ita kuma ta ce sanyi take ji, wannan abin abin dubawa ne. Ita kuwa tana shiga palo da kyar ta iya yi wa su Abbi sannu sannan ta wuce sama, sai sauri take zubawa, basu kawo komai a ransu ba, sun yi tunanin fitsari ne yasa take sauri hakan. Tana shiga bedroom ɗin nasu ta haye saman bed tare da jan bargo ta shige tana mai da numfashi, yau ta ji abinda ya girmewa shekarunta. Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun, tana tsaka da tunani ta ji shigowar saƙo wadda ko bata duba ba ta san shi ne ɓoyayyen masoyi ba, innalillahi wa inna ilaihir rajiun ta fara furtawa Baiwar Allah, kin ɗaukar wayar ma ta yi bare kuma har ta duba saƙon, gaba ɗaya ji take yi kamar ta yi ta kurma ihu har sai muryarta ta daina fita ko zata ji sauƙi. Kiran wayar tata aka fara yi, a hankali ta kai kallonta kan wayar, wannan number dai ta unknown ita ce ke kiranta, dafe kanta ta yi tare da fara hawaye. Har kiran ta kashe bata ɗauka ba, wata kirar ne ta sake shigowa, ita ma ta kashe, sai a karo na uku ne ta ɗauki kiran murya kamar zata yi ihu ta ce "Waye ne dai Allah?" Daga ɗayar ɓangaren wata zazzakar murya wadda tana da tabbacin da wuya asami mai irin muryar nan a cikin mutane, a nutse ya amsa mata da "Heartbeat da farko dai sai dai in ce maki am so so sorry, na tuba ba zan kara ba, na sanya my angel cikin damuwa, ayi mani afuwa na tuba ba zan kara ba". "Waye kai?" Ta faɗa tana matse kwallar da ta taru mata a cikin idanunta. Daga ɗayan ɓangaren a nutse ya ce "Masoyinki na gaskiya, ni ban zo wajen ki da nufin na cutar da ke ba, dan haka ki saki jikin ki, ki yi hakuri ki daina tsorona hakan ya isa". Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauƙe kafin ta ce "Amma da gaske ka bani tsoro, to dan Allah ta ina kake ganina har kake ganin duk abin da nake yi?". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Kada ki tambaye ni please kin ji? Ba zan iya yi maki karya ba, kuma bana son na gaya maki gaskiya yanzu, abin da nake so dake kawai ki saki jikinki ki dai'na damuwa kin ji ko?". To ta amsa mashi da shi. "Ina ɗan yin wani aiki ne, idan na kammala zan kira ki kinji ko? Idan ma ban kira ki ba zaki ga saƙona saboda ba ko da yaushe na cika kiran mutane mu ƴi magana ba, yanzu ma dan na ga kin shiga damu sosai ne, hakan yasa na kira ki, ki kula mani da kanki sosai and then ki daina tunanin cewa waye yake maki kaza waye yake yi maki kaza, dukka nine mai yi, ni nake controlling na wayar ki, so ki daina damuwa, sai an jima". Yana kai karshen maganar ya katse kiran ba tare da ya jira amsar ta ba, miƙewa ta yi tana tunanun wannan zazzakar murya, anya akwai irin muryar nan a cikin diniyar mutane kuwa? Ta tambayi kanta, ga shi kuma a nutse yake magana ɗaya bayan ɗaya yake fitar da duk wani word, ga voice ɗin nasa kamar na yara. A zahirin gaskiya muryarsa ya tafi da ita sosai, yana da zakin gaske, kuma daga ji koma waye ne, inma mutun ko aljani yana da kamala da natsuwa sosai. Akila tafi danganta shi da Aljani, domin abubuwan da yake yi ɗan adam ba zai yi shi ba, lokaci guda ta ji wani irin azababben son shi ya shigeta, tunani ta fara yi akan massages nasa da yake cewa shi ba zai hana ta kuka kowa ba, amma zata dai'na kula kowa dan ra'ayin kanta, abin da kawai yake so shine ta dai'na yiwa kowa murmushin nan nata mai kayatarwa baya son gani, shi kaɗai yake so ta rinƙa yi wa murmushi. Hannu tasa ta rufe fuskarta tana murmushi, abin ya ɗaure mata kai, baiwar Allah ta sami shigar soyayyar farat ɗaya, wannan lamari ya zata kaya. KADA KUGA LAIFINTA DOMIN FAƊA DA ALJANI BABU RIBA, DUK ABIN DA BAKA IYA GANINSA ZAKA IYA DANGANTA SHI DA ALJANI, TO BATA GANIN SHI BATA SAN WAYE BANE, MAI YI WU WA ALJANI NE DA GASKE, KUMA KO NI NA JI WANNAN ZAZZAKAR MURYA DOLE NA FAƊA TARKON KAUNA,🤨🤣 ITA FA ZUCIYA BATA DA KASHI🙄😒 DA ZARAR KA YI MATA ABIN DA TAKE SO ZATA KAMU DA SON KA CIKIN ƘANƘANIN LOKACI, TO DAGA KARSHE SAI DAI IN CE JUSTICE FOR ƊAYA DAGA CIKINSU KO MA DUKKANSU, JUSTICE FOR IRFAN OR MASOYIN ƁOYE OR DUKKANSU. Ta jima zaune a saman bed ɗin kafin ta diro kasa sai murmushi take yi ita kaɗan, ta sami kwarin gwiwa da jikinta baki ɗaya, voice nasa ya gigita ta sosai da sosai (Dan baki ji voice ɗin yaya Saif bane our Lion da kince na ɓoyayyen masoyi babu daɗi😌) Sai yawon voice ɗin nasa yake yi mata a cikin kunnuwanta, zan tukansa ne kawai yake dawo mata cikin kunnenta, ya iya tsara kalamai. Kai tsaye palo ta fito kamar wata zautatciya sai murmushi take yi. Tana zuwa ta faɗa jikin Akil tana dariya, da yake ya san abin da yake tsakaninta da Irfan kuma ya ganta da waya a hannu, sai ya yi tunanin cewa kila da Irfan ta yi waya yasa take wannan murmushi baki ya ki rufuwa har haka. Suna zaune a wajen sun lula dunuyar hira sai ga Hajiya Hadizatu ta dawo, cike da kirsa ta yi sallamar tana wani taunar chewing gum, dama ita ba baya ba wajen cin chewing gum, yadda kasa dan ita akayi company chewing gum ɗin. Jikinta na sanye da wani dandantsetsen lace maroon color, ɗinkin A shape ne, kayan sun zauna a jikinta sosai, kyanta ya kara bayyana, ga wasu shegun gwalagwalai da ta yi kwalliya a hannunta da wuyarta, ta je taya yar uwarta murnar bikin Nawid ne a can ta wuni, kafarta na sanye da wani kafurin plat shoe mai ɗan iskan kyau, Hajiya Hadizatu ba baya ba wajen kashewa kanta kuɗi da sayan abubuwa masu kyau da tsada dan ta yi kwalliya da su, shiyasa take ƴar caras da ita, ta kuma yi sa'a tana da kyan jiki ga shape kamar me, ta yafo mayafin nan kalar takalminta wato white color, ga wani haɗaɗɗe kuma tsadadden hand bag irin na ƴan matan nan, shi ta ratiyo abinta. Da gudu Umaisha ta tashi ta nufita da nufin ta rungumeta, cikin sauri Akil ya ruƙeta yana faɗin "A'a ki yi mani a hankali, ko so kike yi ki jiwa kanki ciwo ki jefani cikin tashin hankali ne?". Ɗaure fuska sosai Ommu ta yi, a walakance ta fara yi masu kallon walaƙanci. Sai da ta kare masu kallo tsab kafin ta tsai da kallonta akan Akil ɗin, kallon sama da ƙasa ta yi mashi kafin ta ce "Kai kuma waye? Daga ina da har zaka damatar mani da ƴata ta cikina daga zuwa ta rungumeni?". A takaice ya ce mata "Mamallakin ƴar a yanzu, kuma har zuwa illah Masha Allah". Kara ɗaure fuska ta yi tare da daka mashi tsawa "Kai ɗan talakawa ka iya bakinka kuma ka sakar mani ƴa tun da kai a gidanku ba'a baka tarbiya ba, baka iya girmama manya ba". Ransa idan ya yi dubu ya ɓaci, to ko Abbi ai ba zai gwada mashi kuɗi ba shi kaɗai ma bare kuma ace hadda iyayensa, lallai rashin sani ya fi dare duhu, Ommu bata san waye Akil ba, shiyasa har take ce mashi ɗan talakawa, bata san cewa shi kaɗai ma yafi gaba ɗaya masu kuɗin family'n ta kuɗi ba. A takaice ya ce "Wife ku je ɗaki" ya kai karshen maganar tare da sakin hannunta. A tare suka miƙe da nufin su tafi ɗakin, "zo nan Umaisha" Ommu ta faɗa cike da gadara da nuna isa, rai a ɓace Akil ya daka mata tsawa akan ta wuce ɗaki, kun san halinsa ya tsani a nuna cewa an fishi a waje, kallon Abbi Umaisha ta yi kamar zata yi kuka, jinjina mata kai ya yi alamar ta tafi ɗaki ta bi umarnin mijinta. Da gudu ta wuce ɗakin su Aafia suka bi bayanta Miƙewa Abbi ya yi, kusan kuma a tare suka miƙe da Aunty, a nutse ya ce "Akil ku je part ɗin Irfan ka ji?". A kule Akil ya ce "Bappa ni gida zan wuce domin already raina ya riga da ya ɓaci, ba zan iya kwana a nan ba" ya kai karshen maganar tare da haurawa sama. Zuba mashi idanu suka yi suna kallonsa har ya kurewa ganinsu. Jim kaɗan ya dawo ruƙe da hannun Wife wato Umaisha, bai bi ta kan kowa ba ya nufi hanyar fita daga Palon. "Kai karamin mara kunya mara tarbiya ina kuma zaka kai mani ƴa? Ko dai ita ma ƴar taka ce?" Cewar Ommu kenan. Yana matukar mutuntata tare da jin kunyarta saboda Umaisha da kuma Irfan, ba dan haka ba yau da sai ya tsintsin ka mata maruka, kuma yasan darajar iyaye domin shima ba zai so ayiwa tasa uwar haka ba, dan haka sai bai kula ta ba, ya fice abinsa. Tana ƙoƙarin sake yin magana sai ga Aafia ma sun fito tare da da Akila da Hanan, Hanan zata yi masu raki za su koma, Akil zai mai da Akila gida sannan ya wuce da Umaisha da Aafia gidansa. Cikin sauri Ommu ta biyo su waje tana faɗin "Ku wuce cikin gida Aafia ke da Umaisha". Bayansu shima Abbi ya bi ya fito waje, ita kuma Aunty ta haura sama abinta dan bata son hayaniya. Kallon Abbi Aafia ta yi wadda shima yanzu ya fito ya biyo bayansu. Cike da nuna isa da izza Abbi ya ce "Wuce Aafia ki bi yayanki ku koma kamar yadda kuka zo". Da sauri Aafia ta nufi cikin motar dan ma kada Ommu ta sake yi mata wata magana. "Idan kuka bi wannan marakunya yau sai dai ku nemi wata uwar ba dai ni ba". Cewar Ommu kenan. A fusace Abbi ya ce "Ku tafi abunku dama ai ku baku da uwa, ko kun manta ne? Ita ce ta reneku? Dan haka kamar yadda ta tafi ta mance daku ta rufe babinku, kuma ku rufe tata, ni ubanku ina mai baku umarni ku tafi". Da sauri Irfan ya fito daga part nasa jin hayaniya a harabar gidan, ganin Ommunsu a wajen yasa ya gane ba Alkhari ake yi a wajen ba, hakan yasa ya ji wani irin ɗaci tare da ɓacin rai ya lulluɓe shi, zuciyarsa na mashi zafi tamkar zata fito waje hakan ya ke ji, har wani irin jiri mai karfi yake ji tana ɗebarsa, tunani ya fara yi akan yaushe Ommunsu zata yi hankali ta fara yin abubuwan Alkhari ne? Cike da karayar zuciya ya juya ya kowa cikin ɗakinsa, yasan ba zai iya tunkarar wajen ba, zuciyarsa zata iya bugawa, domin gaba ɗaya familyn su haka suke, suna sa zuciya sosai da sosai, sai dai na wani ya fi na wani, amma duk wanda ka taɓa a cikinsu ba baya ba wajen zafin kai da zafin zuciya, kuma hakan yasamo asaline na gadon shi da suka yi daga iyayensu, kakansu Abbi bafilatanin dajine mai bala'in zuciya, haka ita ma kakansu mace, akwaita da zuciya ba kaɗan ba, har suka zo suka haifi mahaifinsu Abbin shima yana da bala'in zuciya dan ya gado dukka biyu, Abban su Imran ya fi kowa zuciya a cikinsu, yana da zafi idan ka taɓo shi, shine ya fi gadan kakansu da kuma babansu, sanadiyar auren Ammie ya zama haka, wadda Allah ne kaɗai yasan sanadiyar sauyawarsa lokaci guda haka, amma idan kuka cigaba da bin alkalamin princess Teema zaku ji komai har ma da tarihin Abba, a nan ne zaku gane yafi kowa zuciya a cikinsu, daga Abba a zuciya sai Hosain, wadda shima yana da bala'in zuciya sosai, laifi suka yi mashi yasa ya tafi ya bar masu gidan ya yi zuciya bai sake waiwayarsu ba, bayan shi kuma sai Abbi, Abbi ma akwai zafi idan ka taɓa shi, daddyn Jelly ne kawai mai ɗan sanyi a cikinsu, amma Hajiya Batula ma ba baya ba wajen zuciya, shiyasa yaranma suke da zuciya sosai, Akil shine ya ɗauki rabi daga zafin zuciyar Abba, shi kuma Imran irin daddyn Jelly ne, Irfan kuma irin Abbinsa. "Wai ma tsaya shin wannan ɗin wanene?" Ommu ta tambaya tana kallon Akil da yake zaune a gaban motarsa yana jiran su Aafia su shiga ya wuce abinsa. A fusace Abbi ya ce "Mijin Umaisha ne ko kina da magana ne? Mijinta ne kuma ƴaƴanta". Rai a matukar ɓace Ommu ta juya ta koma cikin gida, domin taga Abbi ya hasala, ransa ya ɓaci, kuma ta san halinsa sarai idan ransa ya ɓaci tsab zai yi mata wankin babban bargo ya kuma koreta daga gidan, ta san shima ba baya ba wajen iya faɗa da masifa, hakan yasa ta shafawa kanta lafiya ta nufi cikin gida dan ta sami damar zama daram a cikin gida, yanzu ba zata yi sa in sa da shiba har sai ta gama mallake shi a tafin hannunta sannan ta fara juya shi kamar abaya. Akil kuwa rai a ɓace ya tada motar Aafia tana ɗagawa Hanan hannu suka yi sallama, Aunty kuwa tun da aka fara wannan rigima ta wuce ɗaki abinta, saboda bata son ganin faɗar tasu. Sai da Abbi ya ga tafiyarsu sannan ya juya tare da riƙo hannun Hanan suka wuce izuwa cikin gida. Suna shiga palo ya sake hannun nata yana faɗin "Jeki ɗakin ku ki kwanta abinki". Ya kai karshen maganar tare da wucewa ɗakin Aunty, yau ransa ya ɓaci sosai, Ommu na san kure hakurinsa. A ɓangaren Irfan kuwa, sai bayan ya ji tashin motar Akil sun bar gidan sannan ya jawo wayarsa ya kira layin Akila. Ringin ɗaya ta sanya hannu zata ɗauka, abin mamaki sai taga wayar ta ki yin picking, ta yi ta yi abin ya ci tura, daga karshe ma sai ta ga an yi rejected na call ɗin, abin ya ɗaure mata kai. Tana tsaka da mamaki sai ga saƙo a cikin wayarta, ko bata duba ba tasan baƙon masoyinta ne wato ɓoyayyen masoyi. Cikin sauri jikinta har kerma yake yi dan ta duba saƙon sa, a yanzu haka kawai take tsintar kanta da bala'in dakon jiran saƙonsa ko kiransa, tana matukar son jin voice nasa, musamman idan yana cewa heartbeat tamu, abin ba ƙaramin daɗi yake yi mata ba, tamkar dan bakinsa akayi sunan heartbeat, ya iya kira sosai. "Sorry my angel ba zan iya bari ki ɗauki waya a yanzu ba, ki yi hakuri sai kin je gida kin ji ko? Idan anje gida sai ayi hira da yaya Irfan ɗin". Shine abin da wanann saƙo na ɓoyayyen masoyin nata ya ƙuntsa. A hankali ta tsinci kanta da furta "To ai kaima ina son jin voice naka!". Ta yi maganar tana turɓune fuska irin na shagwaɓa tare da turo baki. Da haka suka isa gida, bai sake yi mata saƙo ba kuma bai kira ta ba. A kofar gida Akil ya sauƙeta tare da tsayawa yana kallonta har sai da ta shiga cikin gida sannan ya juya kan motarsa zuwa gidansa. Ita kuma tana shiga cikin gida kai tsaye ɗakin Ammie ta wuce, da sallama ɗauke a bakinta ta shiga cikin ɗakin, Ammie na kwance saman bed nata. Jin sallamar ƴar tata ɗaya tilo a mata yasa ta miƙe zaune tana faɗin "Akila ya naga kin dawo? Ba Akil ya ce Abuja kuka tafi ba? kuma kwana zaku yi". Gigiza kai Akila ta yi tare da tafiya da gudu ta faɗa jikinta tana dariya. "Lafiya dai ko Akila?" Ta kasa magana dariya kawai take yi, haka kawai idan ta tuna yaya Irfan ko saƙonnin baƙon masoyinta sai ta fara murmushi, a zahirin gaskiya kuma a ganinta Yaya Irfan take so, shi kuma baƙon masoyi yana burgeta ne kawai, kuma voice nasa yana yi mata daɗi, sannan kuma a matsayin aboki kawai ta ajiye shi duk da bata san waye shi ba. Yar hira kaɗan suka yi da Ammie sannan ta wuce ɗakinta, wanka ta fara yi tare da shirin kwanciya sannan ta haye saman bed nata bayan ta yi alwalar barci kenan. Tana kwanciya ta jawo wayarta ta fara kiran layin Irfan. Bugu ɗaya ya katse ya kirata, jujjuya fararen idanunta ta yi tamkar tana a gabansa. "Matar Mijinta kun isa gida lafiya?" Ya yi maganar da murya tamkar mai jin barci. Nauyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe kafin ta ce "Lafiya lou mijin matarsa, daga ɗan dawowa na har na fara kewarka mijina". Shima nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Heartbeat wato dai a waya za'ayi mani hira har da kirana da miji amma a fili sai ayi ta rufe mani fuska ko?". Ƴar dariya ta yi irin na soyayya mai cike da salo na jan hankali, cikin shagwaɓa ta ce "Kai ko yaya Irfan ka fara kenan?". "Ba wani zancen na fara kenan, gaskiya ce na gaya maki ai, tukun nan ma ba wannan ba me yasa tun ɗazun ina kiran wayar ki bata shiga?". Mamaki ne ya bayyana akan face nata, to me yasa zai ce wayarta bata shiga bayan kuma ita a kunne wayar tata take, kuma akwai Network. Nan take kalaman baƙon masoyinta ya fara yi mata yawo akunne na cewa gaba ɗayanta tana karkashin sarrafawarsa da kuma kulawar shi ne, ba iya wayarta ne kawai yake a ƙarƙashin kulawar shi ba, har ita kanta, kenan babu wanda ya isa ya kira wayarta har sai idan baƙon masoyinta ya so? Kenan idan baya son ta yi magana da mutun zai iya hana wa? To wai ma waye shi? Wannan ko a aljanunma ya cika tantiri. BABBAR MAGANA HEARTBEAT ALLAH YA KUƁUTAR DAKE. Jin ta yi shiru ne yasa Irfan ya ce "Heartbeat ya kika yi shiru?" Nisawa ta yi kafin ta ce "Sorry yaya Irfan ina kallon wani abinne ya ɗauke mani hankali". Jinjina mata kai ya yi kafin ya ce "Tom Shikenan, amma banso kuka koma gida a yau ba, na so gobe da safe na fara yin karin kumallon safe da kyakkyawar face ɗin matata". Cool murmushi ta saki kafin ta ce "To amma zaka zo gobe ai na ganka ko?". E ya amsa mata da shi sannan suka cigaba da zuba kalaman soyayya son ransu, sai faman birkita bawan Allah take da salon soyayya da kuma shagwaɓarta, duk ya susuce mata sai zuba mata kalaman da shi kanshi bai ma san ta ya suke fita daga bakinsa ba, bai san yaushe ya iya su ba. Misalin karfe 10 daidai wayar tasu ta katse kit kamar an ɗauke wutar nepa, mamaki ne ya kamata suna tsaka da macewa juna suna zuba love amma waya ta katse, ƙoƙarin sake kiran shi ta yi, amma ina wayar a kashe yake nuna mata, shima ya yi ƙoƙarin sake kiranta, shima abin da yake nuna mata shi yake nuna mashi, wato dai wayoyinsu a kashe. Jin wayarta a kashe ne yasa ya ajiye wayar tasa ba dan ya so ba ya jawo bargo ya rufu ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi. A ɓangaren ta kuwa tana jawo bargo wayar tata ta fara kara. Daga ta cikin bargon ta zuro hannunta wajen saman bedside drawer ta ɗauki wayar, ba tare da ta kalli number ba ta yi picking call ɗin. Sexy voice nasa ta ji yana cewa "Ayi barci my angel, hirar ta isa haka, yaya Irfan ɗin nan naki yana bani tausayi, ni ma dai ina bama kaina tausayi, so good night". Yana kai karshen maganar ɗif ya kashe wayan ba tare da ya jira amsar ta ba, nauyayyar ajiyar zuciya ta sauƙe tare da zuro hannunta ta maida wayar saman bedside drawer ta ajiye tare da lumshe idanuwanta tana tunanin duniya. A ɓangaren daddyn Jelly da Ayla kuwa, tun da ta kai mashi abinci baya nan sai ta cire hijabin jininta ta zauna saman bed tana jiran shi. Bai dawo gidan ba har sai 10 na dare, lokacin da ya dawo already ta yi barci, kuma bata haura saman bed ɗin ba, sai ta kwanta a baki bakin gadon, da alama ba da niyar barci ta kwanta ba, barcin ne kawai ya sawwareta. Kallo ɗaya ya yi mata ya kawar da kansa gefa tare da ajiye kayan dake hannunsa a kusa da kayan abincin da ta kawo masu, wani irin mugun tausayin tane ya dira mashi a ransa, nan take idanunsa suka sauya launi. Kayan jikinsa ya fara ragewa kafin ya wuce toilet dan yin wanka. Wanka ya yi ya fito ya shirya cikin kayan barcinsa masu kyau da tsada, sai tashin fitinannen kamshi yake yi, ya yi wani fresh da shi, a daren nan face nasa ta yi wani fayau haka kamar bashi da lafiya, ƙara gudun Ac ya yi tare da feshe ɗakin da air freshener. Bayan ya kammala komai ya kariso kusa da ita ya zauna ta gefenta tare da jawo ledojin da ya shigo da su. Ɗayar ledar wadda ta kasance karama daga ciki, ita ya fara buɗe wa, kyakkyawar waya ce kirar Iphone 15 a cikinta, ciro wayar ya yi daga cikin kwalinta sai ɗaukar ido take yi. A nutse ya miƙe ya je ya sanyata a charji sannan ya kashe wutar ɗakin tare da kunna hasken wayarsa. Hannu yasa a hankali yana tashinta daga barcin, cikin natsuwa yake kiran sunanta, da alama gaba ɗaya jikinsa a mace yake yau. Da yake ta sanya a ranta shi take ji, sai ta yi saurin tashi, jawota jikinsa ya yi yana mata magana kasa kasa a kunne. Bai kyaleta ba har sai da ya tabbatar ta fita daga magagin barci idanunta sun buɗe, sannan ya kyaleta tare da bata umarnin akan ta sauƙo suci abinci. Ba musu ta sauƙo, da kansa ya zuba masu abinci ya kuma ciyar da ita sai da ta ƙoshi sannan shima ya ci kaɗan. Bayan sun kammala ne, ya ɗauko leda guda ɗaya daga cikin wayan da ya shigo da su ya miƙa mata yana faɗin "Ga sadakinki baby, ban so baki kuɗi ba, akwai abin da naso baki a matsayin sadaki, amma dole tasa na baki kuɗi, but ban fasa baki wannan abin da nayi niyar ba, amma sai mun koma Kano". Kamar dai kullum da to ta amsa da shi tare da buɗe ledar, sababbin kuɗaɗe ne rafa rafa 500k ne cif cif, da yake ita bata san kuɗi dayawa haka ba, sai bata iya gane naira nawa bane ciki, dan haka sai ta mai da kuɗin cikin kedar kawai tare da miƙa mashi ta ce babu abin da zata yi da shi ta bashi kyauta bata so. Murmushi kawai ya yi tare da karɓa ya ajiye a gefe sannan ya jawota cikinsa suka miƙe suka hau gado bayan ya tattare wajen da kansa kenan. Suna kwanciya cikin salo ya fara wasa da ita kamar yadda suka saba, kamar dai kullum duk abin da ya yi mata sai ta mai da mashi da martani, ba ƙaramin kara haukata shi take yi ba. Sun ɗan jima suna romancing na juna kafin daga bisani ya yi addu'ar saduwa ya shigeta a hankali, kuka ta fara yi mashi tare da kankameshi tana faɗin zafi take ji, dan Allah ya kyaleta, shi kanshi sai da ya yi mata hawaye, saboda ya san waye shi, ta yi kuka kuma shima ya yi, idan baku mance ba yana da saurin kuka ga tausayi, Musamman kuma yanzu da ya kasance da abar kaunarsa ce take a wannan hali dole ya yi mata kuka. Duk iya ƙoƙarin da ya yi wajen ganin ya yi mata a hankali sai da ya gaza, ya kasa jurewa ya daure ya yi mata a hankali saboda wani irin ni'ima dake a gareta, hakan yasa ta ci bakar wahala a hannunsa har da suma, kuka kuwa ba'a magana, kafin ta suma ta yi kuka har voice nata ya daina fita, haka zalika shima ya yi mata kukan da bai san yaushe ya fara ba. Yana bala'in kaunarta kuma har ga Allah bai so kawar mata da budurcinta a yanzu ba, kawai dai ya bi maganar Abbi ne, ba dan haka ba da ba zai yi ba har sai ta kai 18 years da ya faɗa. Sai bayan ya sami natsuwa ne ya sauƙa daga kanta tare da kwanciya a gefenta, yana kwanciya kuma wani mugun zazzaɓi mai zafin gaske ta rufe su gaba ɗayansu lokaci guda, ita tana sume ma amma jikinta ya yi zafin zazzaɓi kamar wuta. Da kyar ya iya jan bargo ya rufe su, sai rawan sanyi yake yi, abin ya ɗaure mashi kai sosai, zazzaɓi lokaci guda haka, wani irin azababben ciwon kai ne ta dira mashi lokaci guda, sunan Allah ya fara ambata a zuciyarsa, ya yin da jikinsa ke kara tsananta zafi sosai, ita kuwa da yake tana sume ba zaga fahimci ya karfin zazzaɓin tata yake ba. TO ME YAKE SHIRIN FARUWA DA SU CIWO LOKACI GUDA HAKA? KUMA CIWO MA MAI TSANANIN GASKE HAKA. TO NI DAI NA AJIYE ALKALAMI NA SAI MUN HAƊU GOBE IDAN MAI DUKKA YA KAIMU... 💖💖TRIPLETS💖💖 E75-76💖 Da kyar ya iya jan bargo ya rufe su, sai rawan sanyi yake yi, abin ya ɗaure mashi kai sosai, zazzaɓi lokaci guda haka, wani irin azababben ciwon kai ne ta dira mashi lokaci guda, sunan Allah ya fara ambata a cikin zuciyarsa, ya yin da jikinsa ke kara tsananta zafi sosai, ita kuwa da yake tana sume ba zaga fahimci ya karfin zazzaɓin tata yake ba. Da kyar ya iya samu barcin wahala ta ɗauke shi, ba shi ya farka ba sai da hasken rana ta sauƙa mashi akan face nasa, bawan Allah ko sallah bai yi ba, abin ya ɗaure mashi kai, tamkar a mafarki ya ji abin, tunani ya fara yi wannan wace iriyar barci ne ta ɗauke shi haka, tamkar ya bar duniyar baki ɗaya, kuma duk abin da ya faru jiya da daddare ji yake yi tamkar mafarki ne. Da kyar ya iya waro dara daran idanuwansa wadda har lokacin suke ja sosai, kai tsaya kan face nata ta sauƙe idanun nasa. Har wani hasken wahala ta kara yi, ta yi wani fayau da ita, abin ya bashi mamaki yadda face nata ya yi tamkar ba ita ba. Lallaɓawa ya yi ya maiƙe zaune tare da jan bargon jikin nasu kasa, kawar da kallonsa gefe guda ya yi cikin sauri lokacin da idanunsa suka sauƙa akan aika aikan da ya yi mata. Jininta ya zuba sosai baiwar Allah, ɗan ciza laɓɓansa ya yi tare da yarfar da hannunsa gefe yana lumshe idanunsa alamar sam bai ji daɗin abin da ya aikata ba. Da kyar ya iya furta "Am so so sorryyyyyyyyyy my baby" ko motsi bata yi, har lokacin tana sume. A hankali ya zuro kafafunsa kasa ya miƙe tsaye ya nufi toilet. Good 1 hour ya ɗauka yana zubawa jikinsa ruwa mai zafi ko zai zami sassaucin abin da yake ji a jikin nasa. Bayan ya gama ya yi wankar tsarki tare da ɗauro alwala, Alhamdulila ya ɗan sami kwarin jikinsa, ya warware, ko da ya fito bai je in da ta ke ba, jallabiya ya zura a jikinsa tare da shumfuɗa dadduma ya tada Sallah. Bayan ya idarne ya miƙe ya iso gare ta, tsayawa ya yi ya zuba mata idanu na ɗan lokaci kafin ya wuce izuwa cikin toilet ɗin. Jim kaɗan ya fito ya zo ya ɗauketa cak kamar ƴar baby ya nufi toilet ɗin da ita, gaba ɗaya bed sheet nasu ya ɓaci da jini. Cikin makeken baf ɗin wanka dake a cike da ruwan zafi ya tsundumata, ruwan akwai zafi dai dan gasa jiki. Yana sumdumata ta farfaɗo, ta kuma farka mashi da sabon kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, rarrashinta ya fara yi yana bata hakuri, ina da alama ma bata sauraron shi, kuka kawai take yi. Da ya ga haka sai ya kyaleta ya shiga buɗa mata kafafunta ruwan zafin na ratsata, ƙanƙame shi kawai ta yi tana kuka tare da zuba mashi sambatu wadda bata ma san me take faɗe ba. Haka ya gasa mata jikinta sosai da sosai kafin ya naɗo kayarsa a towel suka dawo cikin ɗaki, saman carpet ya kwantar da ita, sannan ya cire bed sheet dake a gadon tare da ɗauko wani ya shimfuɗa sannan ya kwantar da ita a saman bed ɗin. Har lokacin kuka take yi mashi, sai dai kuma muryar tata baya fita sosai, muryar ta dashe sosai da sosai saboda kukan da ta sha daren jiya. Duƙufa ya yi akan rarrashinta babu kama hannun yaro, idanunta a runtse taki buɗewa, hakan kuma da ta yi ya fi mashi, domin kuwa shima baya son ya haɗa idanu da ita, wani irin kunyarta yake ji shima. Sun kwashi good 30mins a haka, sai rarrashinta yake yi, da kyar ya samu ta iya hakura ta yi shiru. Haka ya rinƙa lallaɓata kamar wata baby. Yana ƙoƙarin kiran Abbi a waya dan ya sanya Hanan ta kawo mashi kayan tea sai kawai ya ji sallamar Hanan ɗin a Palo. Ajiye wayar ya yi tare da miƙewa ya nufi Palon, tsaye take a tsakiyar palon ga kayan abinci jere a saman katon tray dake a hannunta. Gaishe shi ta yi ya amsa da kalma ɗaya sannan ya karɓi kayan abincin ya wuce ciki da sauri, ita kuma ta juya ta koma part nasu. Saman carpet ya ajiye tray ɗin tare da ɗaukar tray ɗin jiya ya fitar da shi palon, already Hanan ta rigata ta tafi a lokacin, saman table dake a palon ya ajiye sannan ya koma ciki. Tea mai zafi ya haɗawa babyn tasa sannan ya haye saman bed ɗin, saman bedside drawer ya ɗaura cup ɗin tea ɗin tare da ɗagota ya mannata da kirjinsa kafin ya ɗauko tea ɗin yana faɗin "Babyn daddy ki yi hakuri ki sha ko?". Idanunta a runtse ta girgiza mashi kai alamar a'a ba zata sha ba, da kyar ya fara lallaɓata har da yi mata kukan shagwaɓa sannan ya samu ta buɗe bakin nata wadda yanzu ya yi mata mugun nauyi, ga shi kwata kwata bata jin daɗin komai ya shiga bakin nan nata. A hankali ya fara zuba mata a ɗan bakin nata, haka ta daure ta rinƙa sha sakamakon taga hankalinsa ya tashi sosai, ya shiga damuwa, sai rarrashinta yake yi, har da yi mata kukan shagwaɓa, hakan yasa ta jure ta sha mai ɗan yawa. Sosai ya ji daɗin shan da ta yi, sai da ya tabbatar cikin ta ya ɗan cika sannan ya ajiye cup ɗin tare da kwantar da ita ya diro kasa daga saman bed ɗin. Kananan kayan da suka sawo shekaran jiya ya fitar mata da guda ɗaya, doguwar riga ce tana da ɗan kauri kaɗan. Dawowa saman bed ɗin ya yi ya sanya mata rigar, bayan ya saka mata ne ya ɗauketa cak. Bai direta ko'ina ba sai tsakiyar carpet ɗin, har lokacin taki buɗe idanunta, wani irin mugun tausayin daddyn nata ne ta ji yana shigarta, sai hidima yake yi da ita, sannan gabanta zafi yake yi mata kamar me, duk jikinta ciwo yake yi mata, dan ma Allah ya sa ya gasata da ruwan zafi sosai, da ba dan haka ba ai ko motsi ba zata iya ba. Taɓa wuyarta ya yi yana faɗin "Baby har yanzu akwai zazzaɓi ajikin ki fa, ki gama cin abincin nan mu je hospital". Yana magana yana zuba mata wani haɗaɗɗen ferfesu wadda Aunty ta shirya masu, ya ji kayan kamshi da kuma ya ji, sai tashin kamshi yake kamar me. Ɗaukar spoon ɗin ya yi tare da fara ɗebo ferfesun yana kai mata shi a bakinta, har lokacin taki buɗe idanunta, haka zalika taki buɗe baki ta karɓi ferfesun. Kasa kasa cikin sigar rarrashi ya ce "Babyn daddy ki yi hakuri ki ci abincin ko? Ko dai kina son daddy ya yi maki kuka ne?". Idanu a rufe ta girgiza mashi kai alamar bata so ya yi kuka. "To idan baki son daddy ya yi kuka buɗe baki daddy ya baki abinci ko?" A hankali baiwar Allah ta buɗe bakinta, zuba mata ya yi tare da mai da spoon ɗin cikin plate dan ya ɗebo wani. Haka ya rinƙa bata tare da lallaɓata, har ta ci sosai ba tare da ta sani ba, sai da ya tabbatar cikinta ya cika sannan ya kyaleta tare da mayar da plate ɗin cikin trya ya ajiye. Kusa da ita ya zauna tare da rungumota a jikinsa yana gaya mata kalamai masu daɗi tare da rarrashin ta yana faɗa mata ya tuba ba zai kara ba. Saboda daɗin kalaman da yake yi mata yasa har ta mance da abin da ya faru ta buɗe idanunta. "Daddy kai baka ci abinci ba ai to". Ta faɗa tana ƙoƙarin ɗagowa daga jikin nasa. Ihu ta saki lokacin da ta yi yunkurin tashi tare da koma ta lafe a jikin nasa tana hawaye. "Subhanallah baby me ya faru kuma?" Ya tambaya yana ɗago haɓarta. Runtse idanunta ta yi tana hawaye ta ce "Daddy zafi zafi nake ji, zafi sosai". Nisawa ya yi har ga Allah yana matuƙar jin tausayinta domin yasan waye shi, kuma har cikin zuciyarsa bai so kusantar ta a yanzu ba, yasan idan ya yi gigin yin hakan zasu iya samin gagarumar matsala, ba zata iya jure bukatarsa a yanzu ba, ta yi karama, ba wai kawar da budurcinta yake cewa ta yi karama ba, no abin da zan biyo baya bayan sun yi kwanciya ta farko shi yake gudun mata, tabbas ba zata iya ɗaukar karfin sha'awarsa ba, saboda kananun shekarunta sannan kuma raguwace ajin farko, ga saurin kuka, daga ita har shi kuma muddin aka fara to fa ba za su iya hakuri da juna ba, sai dai nashi jarabar ta ninka tata sau ba adadi, yana daga cikin dalilin da yasa ya ki yin wani aure ya zauna yake fama da azumi da sallar dare, itama mummyn jelly ba karamin kwakwa ta ci a hannunsa ba, bawan Allah shi yasan waye shi. Rarrashinta ya fara yi tare da zuba mata kalamai da nasihohi har ta hakura ta yi shiru, rungumeta sosai ya yi a jikinsa yana ɗan bubbuga mata bayanta. "Daddy bayana kafafuna duk suna yi mani ciwo sosai". Ta yi maganar kamar zata yi kuka. Miƙewa ya yi tare da kwantar da ita a saman bed ɗin, tattare kayan abincin ya yi tare da fitarwa izuwa Palo, bayan ya dawo ne ya haye saman bed ɗin, bawan Allah kwata kwata tausayinta ya hana shi cin abinci, yana jin yunwa amma ya kasa samun sukunin da zai iya natsuwa ya ci abincin, dan gaskiya yana da zuciyar tausayi sosai. A hankali ya fara yi mata tausa yana matsa mata cinyoyin nata zuwa bayanta, sai sauke numfashi mai kama da nishi take yi a hankali hankali, har cikin ranta take jin matukar daɗin matsa mata jikin da yake yi, lumshe idanuwanta ta yi tana ta faɗin wash a cikin zuciyarta. Ya jima yana yi mata tausa ba tare da gajiya wa ba, sai da ita da kanta ta ce ya bari sannan ya bari tare da komawa kusa da ita ya kwanta yana kara yi mata sannu. Mirginowa ta yi ta shige cikin jikinsa tana kankame shi. "Daddy jikinka yana yi mani daɗin kwanciya" ta faɗa a shagwaɓe. Kara kankameta ya yi sosai, sai sokinsa breast ɗinta suke yi a kirjinsa, hakan ba ƙaramin daɗi yake yi mashi ba. "Baby jikin daddy ai mallakin ki ne ke kaɗai, dan haka ki yi kwanciyar ki yadda kike so". Cikin sauri ta ce "Daddy ni kaɗai kuma? Jelly fa idan ta dawo? Ai itama zata kwanta a jikinka". Girgiza kai ya yi yana faɗin "Ai ko karfe biyun dare aka gane jelly ba zan kara minti gomaba za'a ɗaura mata aure da Imran ta kuma bi mijinta ko zan sami kwanciyar hankali, tun tana ƴar shekara 13 Imran ya so na aura mashi ita, na ki yarda a lokacin nace sai ta girma, sai ta kammala secondary school, yanzu kuwa na yafe karatun ta je gidan mijinta ta yi kawai, hakan zai fi mani kwanciyar hankali, dan haka jikin daddy naki ne ke kaɗai". Kankame shi ta yi tana goga kanta a kirjinsa, wani irin azababben kaunarsa ne yake kara ratsata, tana matukar kaunar mijin nata kamar yadda shima ya mace mata. Haka suka kasance manne da juna suna hira cike da so da kuma kauna, sai lallaɓata yake yi yana rarrashinta, da zarar ta ɗan motsa zai tambayeta menene, ko ta ce mashi babu komai baya yarda sai ya bincika da kansa. A ɓangaren su Imran kuwa, suna isa gida kai tsaye ɗakin Areef suka fara shiga, yau dai yana zaune ne saman bed ɗin nasa, ya jingina kansa da jikin headboard na gadon yana latsa wayarsa. Jin sallamarsu yasa ya ɗago kansa yana kallonsu, haka kawai yau tun da yaga Rimsha da safe yake jin sha'awar shan jininta, tun lokacin yana ƙoƙarin kawar da kallonsa daga kanta, amma abin yana ba shi wahala sosai. Hannu ya miƙe mata akan ta zo, daga ita har Imran sun tsorata da ganin yanayinsa a wannan dare, domin su ba a real ash eyes suke ganin idanunsa ba, idanun nasa ya riƙiɗe masu, ganin idanun suke yi kamar glass, da yake darene sai Imran ya yi tunanin ko dai yanzu shima idanunsa sun koma irin na Lion ne, domin idanun Lion suna kara kyalli da daddare, sai dai abin da Imran bai sani ba, ash eyes da blue eyes akwai banbanci nesa ba kusa ba. Rimsha kam jikinta har kerma ya fara yi saboda tsoro, bata taɓa kallon masu kalar idanunsu ido da ido ba sai akan Areef ɗin dan Lion har yanzu bata sami damar yin ido huɗu da shi ba, kuma yana ɗaya daga cikin abin da yasa ko a mafarki taga idanun Lion tana tsorata, a iya Tv take kallo, to yau sai ga shi ma idanun Areef ɗin ya canza mata launi. Amma da yake Imran yana nan, sai ta daure ta karisa wajen Areef ɗin tana karanta duk wata addu'a da ta zo bakinta, a gefensa ta zauna tana kallon kasa. Hannu ya kai ya riƙo hannayenta, ji yake yi ba abin da yake so a duniya da ya wuce ya sha jininta, sai kallon halittar jikinta yake yi, Imran ya kara tsorata da yadda yake mata wani irin mayen kallon nan, ga shi kuma bai san da zancen cewa Areef yana kungiyar shan jini ba, Lion ya ɓoye mashi, idan baku mance ba, shi Lion yana da sirrin da ko Triplets nasa ba kasafai suka cika sanin cikinsa ba, duk yadda suke da mutun ba komai yake gaya mashi ba, idan ka ji yana magana da mutun tofa maganar ta shafe mutumin ne. Wani irin azaba Areef yake ji a cikin jikinsa sakamakon ingiza shi da suke yi akan ya sha jininta, matse hannunta ya yi cikin nasa da karfi tare da datse harshensa da hakwaransa, sosai Rimsha ta tsorata tare da tsananta adduar da take yi a cikin zuciyarta. Shi kuma Imran ganin hakan yasa ya ce "Rimsha ta shi ki je ɗaki ki kwanta dare ya yi". Tana son ta tashi ba hali domin ya kankame mata hannu yana wani irin datse harshen sa da karfi. Lokaci guda kuma ya sake ta da sauri tare da juyo da kallonsa izuwa bakin kofar ɗakin, ba komai bane yasa ya yi saurin sakinta haka face kamshin perfume ɗin Lion da ya ji, Lion bai kai ga shigowa ɗakin Bama, kamshin perfume ɗin ne ta riga shi shigowa, shima Lion ɗin dama baya gidan yanzu ya shigo ne sai ya ce bari ya fara duba ɗan uwan nasa kafin ya wuce sama. Ita kuwa Rimsha yana sakinta ta miƙe da sauri ya faɗa jikin Imran jikinta na ta ɓari Baiwar Allah. Karin wani haske akan wannan al'amari, kwata kwata kungiyar da suka kama Areef wato G.M.A basa son Kamshin perfume na Lion, basa son shi ko kaɗan, shiyasa da ya doso su zasu gudu daga jikin Areef ɗin, wannan perfume ɗin na Lion kuma daga kasar Dubai yake sawa a buga mashi, perfume ne mai kyau over. Da wannan sexy voice ɗin nasa ya yi sallama can kasa kasa, Imran ne ya amsa mashi sallamar yayin da shi kuma Areef ya kwantar da kansa a jikin headboard na gadon tare da runtse idanunsa, da alama bai so ganin Lion a yanzu ba. Gefensa Lion ya zo ya zauna, jikinsa na sanye da wandon jeans navy blue da kuma farar high neck t-shirt yau ya ɗaura wannan jacket ɗin nasu a saman kayan, da alama yau ba shi da lafiya, domin dai duk zafin da ake yi a Nigeria yau ya sanya jacket a saman kayan jikinsa, bugu da kari ga face nasa ta yi wani fayau tare da ƴin wata ƴar rama wadda zai tabbatar maka bashi da lafiya, bawan Allah abubuwa sun yi mashi yawa akansa ba kaɗan ba, mutun ɗaya yake ɗebe mashi kewa tare da rage mashi damuwa shine Asreef, Aseef bawan Allah yana kiran shi video call ya yi ta yi mashi hira yana rage mashi damuwar da yake a cikinta, Areef kuma kullun kara mashi damuwa yake yi, domin kullun kara binciko wasu abubuwa da Areef ɗin ya aikata yake yi, duk kuma abin da ya binciko sai ta sanya shi damuwa, a yanzu ma daya tsananta bincike ya gano cewa, Areef ya sami kansa a wannan kungiyar ne sanadiyyar kashe wannan mutumi da ya yi, bugu da kari kuma tabbas Josephine ta zama hanyar shi garshi kungiyar, sai dai ita ma Josephine ɗin bata a cikin kungiyar wata makusanciyarta ce wadda suka kasance friend ita ce ke a cikin kungiyar, kuma abin da suka yi wa Areef shi suka yi wa Josephine ɗin ita ma, yadda suke control na Areef ita ma haka suke tata, sai yadda suka juyata, ga shi ita ba musulma bare abin ya zo mata da sauƙi, ba addu'a ba sallah ba komai, shiyasa ta fi Areef shan wahala a hannunsu, kuma sune suka bata abin da ta zubawa Areef ɗin a cikin abin sha ya sha ta haka ya shige su, dan su ɗauki fansa mutumin su da ya kashe yasa suka saka shi a kungiyar, sai dai da yake akwai Allah a ransa sun kasa cutar da shi. Ɗazun Lion ya gama final bincike akan su, a nan ne ya sami waɗan nan amsoshin wadda suka yi mugun ɓata mashi rai, sai dai daɗin abin ya sanya sojoji runduna guda da su shirya zuwa yakar wannan ƙungiya saboda ya gano a in da ƙungiyar take, sannan kuma ya kira Sultan wato limamin babbar masallacin sa da ya gina a kasarsu, ya ce Sultan ɗin ya tara malamai su yi masu addu'a ayi sauƙar Al Qur'ani mai girma domin ƴakar wannan ƙungiya ba abu bane mai sauƙi, kuma ga shi sojojin dukka kafurai ne bare ace za su yi addu'a, dole ne sai su Sultan sun yi masu addu'a dan su sami nasara, Lion ya bawa sojojin umarni akan cewa ranar Friday su tunkari kungiyar, domin a ranar duk wani ɗan kungiyar yana wajen suna taro. Abin farinciki ɗaya da Lion ya samu a wannan bincike shine mahaifiyarsu dai bata a cikin kunguyar dan ra'ayin kanta, kuma abin da ta bawa Areef ma ya ci, bada saninta bane domin control nata akeyi, hakan yasa ya ce ranar Friday ba zai bari ta je kungiyar ba, domin kada sojojin nan su haɗa da ita su kashe, yana da ƴakinin idan suka ruguza kungiyar to duk wani abin dake a jikin Josephine da kuma Areef zasu mutu. STORY Zubawa Areef idanu sosai ya yi tare da miƙawa Imran hannu dan su yi musabaha. Ɗan sakin Rimsha Imran ya yi tare da miƙo mashi hannu suka gaisa cikin mutunta juna. "Why ka je ka daɗe Prof?" Ya faɗa cikin sanyin murya yayin da yake kai hannunsa saman goshin Areef ɗin dan yaga sai faman haɗa zufa yake yi, ya zaci ko zazzaɓi yake yi, bai san cewa G.M.A ke bashi bakar wahala ba. Rimsha kuwa sai kare mashi kallo take yi, yau wuni zumbur bata sami ganin shi ba, tasha kewa sosai da sosai, ba dan tana kunyar Imran bama da ta ce su dawo time da suke gidan Abbi, ba abin da ya fi burgeta sosai a tattare da shi sai laɓɓansa da gashin kansa, sun fi komai burgeta, yana da wasu irin halittar laɓɓa ne masu matukar kyau da jan hankali tare da kayatar da duk wanda ya kalla, duk wanda ya kallesu sai ya ji yana sha'awar ko da ɗan taɓasu da hannunsa ne, ga su da laushi kamar me. Da kallo ɗaya kuma Rimsha ta yi mashi ta san ya rame, sai mamaki take yi akan me ya same shi ya rame haka, bata san lokacin da ta furta "Bawan Allah ko me yasa me shi ya rame haha? Ko dai bashi da lafiya ne? Allah sarki". Bata san cewa a bayyane take yin maganar ba har sai da ta kalli Imran da Areef suna kallonta, shi kuwa Lion hankalinsa na akan jikin ɗan uwan nasa, da alama ma bai san da tsayuwarta a ɗakin ba, kuma dama kun san halinsa abin da yake a gabansa kawai yake yi, Allah mai iko kuma da yaren turanci Rimsha ta yi maganar, da yake dama basu damu da yin magana da hausa ba daga ita har Jehan ɗin. Da gangan Areef ya ce "Rimsha ke da waye kike magana?". Ɗan zaro ido ta yi tare da fara ƴan kame kame, kashe mata ido Areef ya yi yana nuna mata alamar akan ta faɗi gaskiyar da waye take yi, amma ina tsoro ya hana ta faɗe, Areef ya san cewa idan har ta furta cewa magana take akan Lion ya rame to tabbas ko Lion bai ɗago ya kalleta ba, zai sa a ransa cewa koma wacece ita tabbas yana da mahimmanci a wajenta, kuma Areef ya san da cewa tabbas zai ji daɗin hakan a ransa ko da bai nuna ba, kuma dole ma sai ya jita a ransa, saboda ko daddy baya taɓa iya fahimtar halin da Lion yake ciki, amma ita da kallo ɗaya har tasan yana cikin damuwa kuma ya rame, abun da kuma ba samun damar kallonsa kullun take yi ba, duk wanda aka yi wa haka, dole sai ya ji wani abu a zuciyarsa, musamman mutun irin Lion wadda yasan ba kowa ne yake iya fahimtar shi ba, amma rana ɗaya a sami mai fahimtar shi da kallo ɗaya haka, kai abin fa abin duba wane. Tsoro ya hana Rimsha magana, Areef ya yi iya yinsa akan ta ce da Lion take magana, amma ina ta kasa, daga karshe ma sai ta kawar da kallonta daga kan Areef ɗin, ba ƙaramin haushin hakan Areef ya ji ba, ji ya yi kamar ya mareta dan haushi, shima Imran bai ji daɗin abin da ta yi ba, shi kuwa oga yana ta faman buɗe magumguna da zai bawa Areef ɗin, sai dai kuma da alama akwai abin da yake tunani dan gane da Areef ɗin, domin kwata kwata baya tare da su, hankalinsa ya yi nisa sosai. Bayan ya gama ɓare magungunan ne ya miƙawa Areef akan ya sha tare da fitar mashi da ruwan sha. "Jikeki ki kwanta Rimsha, sai da safe". Cewar Imran. To ta amsa da shi tare da wucewa da sauri ta fice daga ɗakin. Tana fita ba jimawa Lion ya gama abin da yake yi shima ya fita ya nufi bedroom nasa ya bar Imran da Areef ɗin. Daidai zai shiga bedroom nasa sai ya ji kamar ana magana a ɗakin Imran, tunani ya yi akan ya bar Imran a ɗakin Areef, kamar zai shiga sai kuma ya fasa ya wuce bedroom nasa, domin ba komai ya cika kulawa ba. Yana shiga bedroom nasa Rimsha ta fito daga ɗakin Imran ɗin ta wuce tata ɗakin hannunta ruƙe da jacket da ta ɗauko a cikin ɗakin. Bata san jacket ɗin waye ba, ita dai ta yi wanka ta yi shirin kwanciya ne sanyi ya dameta shine ta shiga ta duba ko Imran yana da jacket, ita bata da shi ko guda ɗaya, basu saya ba, da ta shiga kuma, sai ta yi karo da wannan jacket ɗin mai kamshin perfume ɗin Lion, perfume ɗin da ta fi kauna a rayuwarta, hakan yasa ta ɗauki jacket ɗin ta tsaya a tsakiyar ɗakin tana surutu ita kaɗai, shiyasa Lion da ya zo wucewa ya ji ana magana kasa kasa a cikin ɗakin. Tana fitowa daga ita sai wasu shegun kayan barci masu shegen kyau launin sky blue riga da wando, kayan sun zauna ajikinta sosai, kana iya ganin ainahin shape na jikinta, ɗakinta ta koma tare da sanya jacket ɗin a jikinta. Har gwiwarta jacket ɗin ya kai mata, hakan ya bata tabbacin cewa ba jacket na Imran bane, domin tsawon Imran da kaɗan ya fi tata, tunani ta fara yi anya ba jacket ɗin Lion bane, tuna haka yasa wani irin kayatatcen murmushi ya kubce mata. A fili ta furta "Ko yanzu na mutu Allah ya cika mani burina ɗaya, yau na saka rigar GAR" wayarta ta ɗauko ta fara ɗaukar hoton a cikin wannan dare. Sai da ta yi hotuna kala 15 sannan ta haye gadon zuciyarta cike da farinciki mara misaltuwa. Da haka barci ya kwanshe ta. Misalin karfe ɗaya na dare, duniya dukka suna barci shi kuma Lion yana tsaye saman dadduma jikinsa na sanye da farar jallabiya tas, sai ta shin kamshi yake yi. Sallah yake yi yana karanta manya manyan surori irin su Bakara Ali Imran nisai, yana karatun idanunsa sunyi ja sosai da sosai, babu abin da yake sanya idanun Lion suyi ja haka sai karatun Al Qur'ani mai girma wadda duk zuciyar mumini idan ta karantata kuma ta san ma'anar ta, to dole ta zubar da kwallah, domin kuwa Al Qur'ani mai girma ita ce ke nunawa bawa ainahin girman Ubangijin mu, dole duk wani bawan da zai ji girman Allah da kuma abubuwa na Ni'ima da Allah yake yi wa bayin sa, wasu su butulce, wasu kuma su sanya kafa su dake, wasu su yi amfani da shi wajen gaya wa wasu su kuma ba zasu yi amfani da shi ba, wasu kuma zasu ɗauka ne kawai su ajiye a ƙwaƙwalwarsu ba tare da sun yi amfani da koda aya guda ɗaya ba, suje su yi ta sha'anin su kamar ba su san me zai faru a gaba ba, su mance akwai tashin alkiyama, akwai lahira, kafin lahira akwai kwanciyar kabari wadda babu wanda ya san shekaru nawa za'ayi a cikinta, idan ka yi aiki mai kyau duk shekarun da zakayi a kabari kana cikin ni'imar Allah subhanahu wata'ala, idan kuma kayi aiki mara kyau duk shekarun da za'ayi kana cikin bakar azaba mara misaltuwa ne daga hannun Mala'iku, babu mai citonka, babu mai jinka, kai kaɗai zaka kasance cikin wannan duhu da bakar azabar, bayan kabari mai duhu da firgitar da bawa za'ayi busan kawo na fitowa daga kabarin wadda a nan ne ake cewa zafsi zafsi takai takai uwa zata mance da ɗanta ƴa ta mance da uwarta, lahira ba wasa bane, Allah zai sauƙo mana da rana daidai saitin kawunanmu, waƴan da suka yi aikin Alkhari sune kawai zasu shiga ƙarƙashin inuwar alarshin Ubangiji mai girma, bayan nan fa akwai gadar siraɗi wadda take shinfiɗe a samar wutar dajannama, kaifi tafi reza siranta kamar gashin kai, a haka zamu bi ta kanta mu wuce, bakar duhune a wajen wadda baka iya ganin koda ɗan yatsarka, aikin Alkhari da muka yi shine zai zo ya haska mana hanya mu wuce, idan ka yi kuskure faɗawa cikin wuta zaka yi, jama'a me zamu nema a duniya da har zai sanya mu manta waƴan nan dukka? Mulki? Kuɗi? Koko Duniya? Ko kuma me? Idan mulkine to a wannan rana ta tashin alkima Allah zai tara mutane duniya baki ɗaya waje guda ya yi mana tambayar da babu wadda ya isa ya motsa bare ya bada amsa WAYE SARKI A YAU shine tambayar da Allah zai yi mana, ina mulkin take a nan? Sarakuna shuwagabanni dukka babu wanda ya isa ya yi motsi ko kaɗan, Allah da kanshi yake sake cewa shine mai mulki a yau, babu wani sai ki sai shi, idan kuɗi ko duniya yake saka mance lahira, to dukka a nan zamu tafi mu barsu kamar yadda bamu san lokacin da zamu zo duniya ba, haka ba zamu san lokacin tafiya lahira ba, ƴan uwana ya kamata ku sani, Allah baya kama bawa akan laifin da bai sani ba, amma mutun ya sani ya take sani babbar haɗari ne, irin shi mummunar kamu Ubangijin yake yi mashi, da kuma malaman da za su karantar amma su ba zasu yi amfani da abin da suke karantarwa ba, waƴan nan idan ba su tuba ba, wlh Ubangiji ba zai yi masu kamu mai kyau ba, waƴan da suke sanin Allah ya ce, sai dai su gayawa bayi Allah ya ce ayi kaza ayi kaza su kuma ba zasu taɓa kwatanta yin hakan ba, ku ji tsoron Allah kada ku gyara wa wasu goben su ku kuma taku ta taɓarɓare, sai anyi magana sai kuce ai bature ya ce do what I say don't do what I do, wlh ku kiyayi wannan kalma idan ba haka ba zata kai ku ta baro ku, Allah ka kiyashe mu ka kuma rabamu da sharrin zuciya, amma dai zuciya bata da ƙashi, duk abin da zaku yi, ku tabbatar tsakani da Allah kuke yin shi, kada ku yi abu dan a yaba maku, zaku tashi a ranar gobe kiyama kun baro duniya da aikin lada sosai kun je lahira babu ko ɗaya, domin ba domin Allah kuka yi ba, dan haka mu kula dan Allah, ayi koma saboda Allah. Ya jima yana Sallah tare ka karatu, idan ya yi raka'a biyu ya yi sallama sai ya zauna kusan minti 20 yana rera karatun Al Qur'ani mai girma da wannan zazzakar murya tasa. Sai Misalin karfe 2:30 bayan ya sallame daga sallar ne ya tashi ya fito Palo, can kasa kasa ya fara jiyo kamar ana magana. Juyo waƴan nan dara daran blue eyes ɗin nasa ya yi izuwa kofar ɗakinta domin daga nan maganar take fitowa. Kamar zai sauƙa kasa, sai kuma ya fasa ya ce bari ya gani waye mai maganar nan, domin ɗazun ya ji magana kasa kasa yanzu ma haka, Kuma yanzu dare ta tsala sosai waye mai magana haka. Ya yi Sa'a kofar ɗakin tata a buɗe, tura kofar ya yi ta yadda zata buɗe mashi dukkan saboda ya sami damar ganin cikin ɗakin gaba ɗaya ba tare da ya shiga ba. Zaune take a saman dadduma ita ma tana karatun Al Qur'ani mai girma bayan ta idar da Sallah, ta bawa kofar shigowa baya tana fuskantar gabas, kallo ɗaya ya yi wa cikin ɗakin ya juya ya bar wajen, dama buƙatarsa ya ji maganar me ake yi kasa kasa tun ɗazun, sannan kuma waye mai yin maganar, tun da ya ga sallah ake yi to Shikenan baya bukatar wani abin kuma, dan haka sai ya juya ya nufi kasa. Kai tsaye ɗakin Areef ya nufa, yau kwata kwata ya kasa samin kwanciyar hankali, sai tunanin Areef ɗin yake yi, abin ya tsaya mashi a rai sosai, haka kawai yake jin kamar wani abin na shirin faruwa. Kasa kasa ya yi sallama a bakin kofar ɗakin tare da shigowa ciki. Kwance yake a saman bed ɗin nasa, sai zuba barcinsa yake yi hankali kwance, cikin natsuwa yake sauke numfashinsa, kai daga gani kasan wannan barcin na musamman yake yi, amma kuma babban abin da ya sanya Lion ya kasa runtsawa yake jin tamkar akwai abin dake shirin faru ko kuma ma yake faruwa shine jikinsa yana yi mashi wani irin yanayi kamar ana azabtar da ɗaya daga cikin Triplets nasa, idan baku mance ba abaya na gaya maku, duk abin da ya sami ɗaya, to dukkansu suna iya jin yanayi makamanciyar wannan a jikinsu, hakan yasa ya kasa runtsawa. A ɓangaren Aseef ma haka ne, bawan Allah ya kasa runtsawa, daya ga ji sai ya tashi ya ɗauro alkawala ya fara gabatar da sallah ko zai sami sassauci, shi ma Musharraf yana a saman dadduma suna sallar dare tun da barci yaki zuwa. Lion ya jima tsaye tare da kunna wutar ɗakin yana karewa Areef kallo, daga karshe sai ya kariso bakin bed ɗin tare da zama kusa da ɗan uwan nasa yana mai cigaba da kallon face ɗin ɗan uwan nasa. Bai taɓa zubawa abu ido yana kallonsa haka ba sai akan Areef, ko lokacin da suke tare gaba ɗayansu, da kallo ɗaya yake yasu ya gane idan suna cikin damuwa ko makamancinsa, amma bai san me yasa yau ya zubawa Areef idanu sosai yana kallonsa har haka ba. Ko motsawa irin wadda masu barci suke yi shi Areef baya yi, tamkar wadda babu ruhi a jikinsa, ba dan numfashin dake futa daga gare shi ba, to da zaa iya cewa babu ruhi a tattare da shi. A hankali Lion ya fara tufa mashi addu'a, yana karatu yana tofa mashi, shiru har lokacin baya wani motsawa bayan numfashin, Lion bai wani damu ba ya cigaba da tofa mashi addu'a, daga karshe dai ya yi addu'a mai tsawo kafin ya tofa a hannunsa sannan ya shafa wa Areef ɗin a face nasa. Wani dogon numfashi Areef ɗin ya ja tare da saukewa a hankali, nan take numfashinsa ta sauya, nan take ya koma ainahin yadda yake barci before. Abin da yasa Lion ya yi mashi addu'a, ya lura da cewa gangar jikinsa ne kawai a nan, sai numfashin da suka bar mashi domin su kawar da hankalin mutane, amma zance ta gaskiya Areef baya a Nigeria kwata kwata, sun ɗauke shi suna can suna azabtar da shi, daga kungiyar G.M.A kenan. Bawan Allah yana dawowa daidai kuma ya cigaba da barcinsa kamar yadda kowa yake yi, fuskar nan tasa ta kara haske sosai, miƙewa Lion ya yi tare da karanto addu'a sosai ya kara tofa mashi sannan ya fice daga cikin ɗakin. Yana fita ya nufi sama, daidai zai shiga ɗakinsa kuma, sai ya ji alamar motsi a ɗakin Imran, ƴar mamaki ya yi akan me yake damun ƴan gidan nan ne, yau kowa bai yi barci ba, kasan cewar yana bala'in kaunar Imran sosai sai ya shiga bedroom ɗin nasa. Kasa kasa ya yi sallama, Imran yana zaune a tsakiyar bed nasa, idanunsa biyu kuma bai amsa sallamar ba, abin ya ɗan bawa Lion mamaki. Prof ya ambaci sunansa a hankali, ɗago kai Imran ya yi yana kallonsa, da yake blue light ne a cikin ɗakunan gidan gaba ɗaya, kuma mafiyawancin lokaci basu kashe wutar ɗakin sai hasken wutar ta saje da kwayar idanunsa. Juyawa ya yi ya nufi waje, bin bayansa da kallo Imran ya yi, har zai fita ba tare da ya juyo ba ya ce "Kazo ɗaki mu yi magana". Ya kai karshen tare da ficewa abinsa. Nauyayyar ajiyar zuciya Imran ya sauke tare da dirowa kasa daga saman bed ɗin, jikinsa na sanya da kayan barci masu kyau launin black color, bayan Lion ɗin ya bi yana sauƙe ajiyar zuciya. Da sallama ɗauke a bakinsa ya shigo cikin ɗakin, Lion na tsaye a tsakiyar ɗakin jikinsa na sanye da kayan barci riga da wando, ya cire jallabiyar jikinsa yana ruƙe da waya yana latsawa. Saman bed nasa Imran ya haye ya kishingiɗa yana mai faɗin "Saif me kake yi har yanzu baka yi barci ba?". Shiru ya yi na ƴan mintoci kafin ya ce "What is wrong with you Prof?". Shiru Imran ya ɗan yi yana tunanin ya faɗa mashi ne ko kada ya faɗa mashi, ya san halinsa sarai, na farko idan ya gaya mashi idan dai ya aminta to tabbas matsalar a cikin kwana ɗaya zata warware da izinin Allah, na biyu kuma idan ya gaya mashi bai Aminta da zancen ba tofa sai dai ma ya yi mashi faɗa akan zancen, babban abin da yasa Imran yake ɗari ɗarin gaya mashi kuma, saboda ya taɓa cewa zai shiga case ɗin daddyn Jelly ya ki bada number, ya kuma san halinsa sarai idan har ya ce ba zai yi abu ba, to fa ya rufe babin wannan abin. Shiru Lion ya yi yana jiran amsa daga bakin Imran ɗin, almost 5mins ya ji Imran shiru bai bashi amsa ba, hakan yasa ya juyo tare da juyo da kallonsa izuwa kan Imran ɗin. Wani irin wahalallen yawu Imran ha haɗiye domin har ga Allah ko shi kwarjinin Lion yana matukar razana shi, musamman idan ya zuba maka wayan nan dara daran idanun nasa masu rikitar da mai kallonsu. Ai Imran bai san time da ya gaya mashi cewa yana damuwa ne akan ɓatar matarsa ba, maganar gaskiya ba wannan ce ta sanya shi a damuwa ba, maganar daddyn Jelly na videonsa dake a hannun baban Muneer shi yake sanya shi tunani, ya rasa ina zai sa ransa akan wannan abin, idan wannan video ta fita da wani ido ma'aikata a banki za su kalli Abbansa? Da wani ido jama'a zasu kalli family'nsu? Wannan ne babban abin da yake damunsa, amma ya rasa me yasa da Lion ya zuba mashi idanu ku sai ya rikice ya gaya mashi ɓatar Jelly ya sanya shi damuwa sosai acikin wannan dare har haka, tabbas ya shiga damuwa sosai ɓatar jelly, to amma ɓatar tata ta riga da ta zame Mashi jiki. Kawar da kallonasa jefe Lion ya yi, ya ɗan ɗauki mintuna kafin ya ce "A ina ta ɓata kuma a yaushe? Shekarunta da kuma yanayinta". "A Kano state ta ɓata irin wata uku zuwa biyar haka baya, she is 16 years old, kyakkyawar gaske ce..." Maganar ce ta makale sakamakon juyo da idanunsa da Lion ya yi izuwa kansa. "Wata uku zuwa biyar kuma har yau ba'a iya gane ina take ba?" Lion ya tambaya yana kara tsare shi da idanun. Tabbatar mashi da hakan Imran ya yi, jinjina kansa ya yi yana mai kara ganin laifukar da shuwagabannin ya kamata su gyara masawar suna son cigaba a rayuwar kasarsu. Gyara kwanciya Imran ya yi yana faɗin "Ina kewarta, serious ranar da ta dawo a ranar za'a ɗaura mana aure, ba zan iya sake hakura ba, na sha bakar wahala a ɓatarta, ban taɓa tunanin zan yi rai in kawo har yanzu ba tare da an gane ta ba, ban taɓa tunanin a yanzu bata zama mallakina ba". Juyo da kallonsa Lion ya yi kan Imran ɗin, kasa kasa ya ce "Ban san da kai da Areef waye ya fi wani jaraba ba". Hararar wasa Imran ya yi mashi kafin ya ce "Ga ka nan kuwa, kai ai inaga duk duniya ba wanda zai fika, daɗin abin dai ɗaya shine da Allah yasa bakasan da abin ba, baka ma san soyayyarba da wlh ƴar mutane ta shiga uku, ina ga sai gawarta, kai daga ganin wannan idanun naka kai kanka idan zaka gayawa kanka gaskiya kasan da hakan, ni ina mamakin ka ma wlh, mutum kamar wani dutse ko karfe, kwata kwata baka da wani shauki sai na harbi da bindiga". Yau da alama ƴan mutuncin Lion suna kusa tun da har ya tsaya Imran yake wannan hirar da shi, ko da yake yana bala'in kaunar Imran ɗin over, basu hira har haka, magana ɗaya biyu idan ta yi yawa uku ce kawai take haɗa su, ba Imran kawai ba, bai taɓa yin magana da wani ta wuce magana uku ba sai akan wannan case ɗin na Areef, a nan ne ya ke iya zama yana ɗan magana mai tsawo da Areef ɗin wadda take iya kai har tambayoyi kala huɗu ko biyar yake yi mashi. "Prof seriously i will make you regret". Ya kai karshen maganar tare da nufar Imran ɗin. A guje Imran ya miƙe ya rungume shi yana dariya yana faɗin "Ni ai haka zaka yi hakuri ka kyaleni, kuma ai gaskiya na faɗa, wlh serious ba wasa bane ni ba yadda kuke tunani bane, ni fa kawai ina son ta ne amma duk kun saka mani idanu, Allah ni ba wani abin da zan mata, sister ta ce fa". Rungume shi shima Lion ɗin ya yi yana faɗin "Yana da kyau kayi hankali da waƴan nan halittun, mata ba abin yarda bane, even mazan ma all ban cire maka kowa ba, don't believe everyone to come closer, prophet Muhammad SAW was said ba wace ta kai uwa son ƴaƴanta, amma kuma a duniyar yau uwa ita ta cuci ƴaƴan nata, idan har uwa zata yi hakan waye kake tunanin a waƴan nan halitu na mata zasu ruke maka amana?". Shiru Imran ya yi yana tunani, raba jikinsu Lion ya yi yana kallon face ɗin sa, gently jiki a mace domin yau daga maganar Lion ya fahimci abin da ya daɗe yana zarginsu na cewa basa son mum ɗin su. "A gaskiya idar har uwa ta cutar da ƴaƴanta da kanta kuma da saninta da gangan to tabbas babu da wanda wannan zuciya zata sake yarda a duniya, ba mace ba har maza ba zaka sake yarda da kowa ba, domin uwa ta wuci komai da ake tunani a duniya, ita ce take bada rayuwarta domin ƴaƴanta su rayu, amma a duniyar yanzu son abin duniya yana jefa iyaye cikin bala'i tare da danasani daga baya mara amfani, uwa a zamanin yanzu sai wadda Allah ya so ta da rahma, amma iyayen yanzu sa....." Bai karisar da maganar ba Lion ya ɗaga mashi hannu yana faɗin. "Is okey, uwa ita ce karshe soyayya a duniya na ɗan adam, so idan ta yi breaking heard na ƴaƴanta they can't trust anyone again, so na dai gaya maka be careful akan waƴan nan halittu, ni ba zan hana yin aure ba, saboda Sunnah ce, but yana da kyau kasan me kake yi ka ajiye batun cewa sister kace, uwa ta fi sister ita ma ta ci amana bare kuma sister, you have to be very very careful". Jinjina mashi kai Imran ya yi alamar to "Zan tura maka wata number ka turawa wannan number pic na yarinyar zai ɗaura hotonta a system ya yi searching na irin face nata a gaba ɗaya fuskokin dake a Nigeria, amma zai ɗauki ɗan lokaci domin kuna da yawa a kasar, dan ma dai gudun system ɗin yafi gudun jirgin sama ne, hoton irin face nata kawai zai bincika, idan ya bincika sai mu san a ina take". Tsabar daɗi Imran bai san time da ya sake rungume shi ba, yau zuciyarsa fes, dama yasan idan Lion ya san da haka a cikin 24 hours zai nemo mashi Jellyn sa, suna da kayan aiki sosai, akwai wata shegiyar computer dake a gidansu a ɗakin bincikensa, idan ka sanyawa wannan computer sunan kasa da kuma abin da kake buƙa ta, kamar yanzu idan suka sanya hoton jelly da sunan kasarta suka ce suma buƙatar masu irin wannan face ɗin, searching system ɗin zai fara yi sosai akan fuskokin dake a Nigeria, da gudu gudu zai rinƙa searching ɗin, ba kamar kwakwalwar ɗan adam yake ba, akwai saurin yin aiki, abin da yasa basu gane ina James yake da wuri ba lokacin da ya ɓata saboda basu san a wani kasa ta ka maimai yake ba, wannan dalili kuma yasa Aseef ya ce duk ma in da Tga yake Lion ya sani. Number Tyrone Lion ya tura wa Imran ɗin akan ya tura mashi hoton Jelly shi zai yi mashi bincike akan ina take. Daga haka suka yi sallama kowa ya wuce, Lion ya haye saman bed, shi kuma Imran ya wuce ɗakinsa ya je ya kwanta. Washegari sai mi salin karfe 8 Rimsha ta farka daga barcin da ya ɗauketa tun bayan sallar asuba, da yake bata sami damar yin barcin dare sosai ba shine sai ta biya da barcin safe. A hankali ta waro idanunta, ta ɗan jima kwance tana kallon sama, yau barcin ya yi mata mugun daɗi sakamakon Kamshin perfume ɗin Lion dake a jikin jacket ɗin jikinta da ta sanya, ji ta yi tamkar tare da shi ta kwana, yau mafarkinsa ma na musamman ta yi. Shiru ta kwanta tana tunanin mafarkin nata, abin ya kayatar da ita sosai, domin yau har taɓa kyawawan lallausan laɓɓan bakinsa ta yi a mafarkin, abin ba ƙaramin burgeta ya yi ba, bugu da kari na sharri irin na mafarki har da ce mata ya yi tana buƙatar lips ɗin ne, (oho Rimsha duniya.🤣) Tuna hakan yasa ta sanya hannu ta rufe fuskarta dan rashin kunya wai kunya ta ji, hannu ɗaya ta kai saman tula tulanta tana shafawa tana tunanin sahibin nata. Wani irin ƙugin yunwa cikinta ya fara yi, dama tun daren jiya tana jin yunwar bata wani ci abincin kirki a gidan Abbi ba sakamakon kewar ganin Lion da ke damunta, dannewa ta yi ta kwanta barci da yunwan dan ta ji kiwuyar shiga kitchen ɗin, kuma bata son ta bawa Imran wahala, ta san idan ta ce mashi tana jin yunwa a daren zai sake fita ya nemo mata abinci, dan haka sai hakura ta kwanta. A hankali ta miƙe zaune tare da zuro kafafunta kasa sannan ta miƙe tsaye gaba ɗaya, hanyar fita daga cikin ɗakin ta nufa kai tsaye. Har ta kai bakin kofa sai kuma ta juyo ta shiga dressing room dake a cikin ɗakin. Jim kaɗan ta fito ba tare da jacket ɗin ba, da alama cire shi ta yi ta ajiye, kai tsaye waje ta nufa tana faman gyara hular barci dake a kanta. A hankali take tafiya har ta sauƙo palon kasa, wani irin bakin yunwar safe ne ke nukurkusan cikinta, kai tsaye kitchen da Imran ya nuna mata ta nufa dan ta dafa abin da zata ci. Tana saƙo kafarta a cikin kitchen ɗin da wannan sojan dake yi masu girki ta fara cin karo, yana tsaye a gaban gas daga shi sai Army three quarter trouser, daga ta sama kuma Army t-shirt ne a jikinsa, sai faman aikinsa yake yi, sai faman zuwa kwai a cikin ɗanyen namar da ya markaɗa yake yi yana kwaɓawa. Wani irin warine ya daka mata kofofin hancinta, kamshin abin cin nasu ji tayi yana mata wani irin wati kamar zuciyar zai fito waje da ta shaƙa, su suna jin warin nata abin ita ma warin nasu take ji. Daurewa ta yi ta gwada shiga cikin kitchen ɗin, sojan yana tsaye kamar gunki, tamkar bai san da shigowar mutun ba, dama kuma haka suke aikin gabansu kawai suke yi a gidan, basa shiga wani aikin da bai shafesu ba. A guje ta sa kai ta fita kitchen ɗin sakamakon wani amai daya yunkuro mata, still har lokacin sojan nan bai ɗago kai ba, kamar ba shi a wajen. Kai tsaye sama ta nufa tana toshe da baki dan kada ta yi masu amai a cikin palo. Sosai take gudu domin amai ya ci karfinta bata ganin gabanta, bata ankaraba tana isa tsakiyar palon sama ta yi karo da mutun, wani irin baya baya ta yi ta faɗi kasa. Kamshin perfume nasa ya isar mata da sakon koma wanene dan haka sai ta kasa ɗago kai ta kalleshi, tsabar tsorata kuma tasa gaba ɗaya ta nemi amai ɗin da take jin ta rasa, amai ya tafi kwata kwata bata jinshi. Shi kuma yana tsaye bai motsa daga in da yake ba sakamakon wayarsa da ta buge mashi ya faɗi a saman cinyarta bayan ta faɗi ita ma kenan. Jin yana tsaye shiru ne yasa tayi ƙoƙarin ɗago kanta ta kalli ko me ya tsayar da shi, dama kuma jira yake yi ta ɗago kai ya bata lafiyayyen mari wadda zai saka ta jin kamshin mutuwa, da yake Allah ba azzalumin bawan sa bane sai ya aiko masu Imran a daidai lokacin kafin ta ɗago kan nata. Ganin abin da yake faruwa ya sanya Imran karisowa wajen da sauri yana faɗin "Rimsha lafiya me ya kawo ki nan..." Bai kai karshen maganar ba idanunsa suka sauƙa a kan wayar Lion dake a saman cinyarta ga shi kuma Lion ɗin yana tsaye yana fuskartar hanyar fita daga palon, so yake ta yi gigin miƙo mashi wayar nan na lahira ya fita jin daɗi, idan kuma bata miƙo mashi wayar ba nan ma ball da ita zai yi domin ya fi karfin ya duƙa ya ɗauki wayar sannan kuma baya son dukanta tana zube a kasa haka, idan ya ce zai daketa a haka to zai iya kasheta ba tare da ya sani ba shiyasa yake son sai ta ɗago tukun nan ta sha mahaukacin mari. Imran ne ya ɗauki wayar tare da ce mata ta wuce ɗaki, cikin sauri ta miƙe zata gudu, "Come here!" ya daka mata ƴar tsawa. Tsorata da razana da jin voice nasa ya sa ta yanke jiki ta faɗin ƙasa sumammiya a wajen. Kallonta Imran ya yi kafin ya maido da kallonsa a kan Lion ɗin, ganin ta suma ya sa Lion ya wuce ya nufi waje dan ya lura wannan yarinya idan ya ce zai taɓa ta ma mutuwar tsaye zata yi mashi a wajen, yanzu daga magana ma ta sume masu a waje, ina ga kuma tasha marinsa ai shikenan kuma sai mutuwa. Zura wayar a aljihu Imran ya yi kafin ya nufi wajen da take sume, hannu yasa ya ɗauketa cak, duk jikinta ya saki ta yi wani irin da ita, da kyar Imran ya iya kai ta bedroom nata domin yanzu ya tashi barci jikinsa babu kwari. Saman bed nata ya kwantar da ita yana faɗin "Ko wani tsautsayi ya saki haɗuwa da Saif da sassafen nan, shin me ma ya fito dake oho?". Sai surutu yake yi kasa kasa da haka ya fita daga cikin ɗakin ya bi bayan Lion domin ya kai mashi wayarsa. A palon kasa ya iskoshi saman table yana cin abinci, ba ƙaramin mamaki Imran ya sha ba ganin yau yana cin abinci da safe haka. Gefensa ya zo ya zauna tare da ajiye mashi wayarsa a gefen nasa, shiru Lion bai kula shi ba har ya kammala cin abin da yake yi sannan ya miƙe tare da ɗaukar wayar tasa ya nufi kofar fita, sojan da yake yi masu girki wadda kuma shine yake serving nasa abin ce, shine ya bi bayansa dan bayan girki da serving ma shi ne driversa, ɗayan sojan kuma yana bakin gate ne kawai, baya motsawa ko nan da can. Har ya kai bakin kofa ba tare da ya jiyo ba ya ce da Imran "I don't want to see this girl again, idan ta bari muka sake haɗuwa...." Bai karisa magana ba sai ya ce "Ka tashi mu tafi yau da kai zamu yi tafiyar, kai zaka ja motar". Godiya ga Allah Imran ya yi domin yasan cewa saboda shine ma yasa yau Lion bai take Rimsha ba, ba dan haka ba da wani zancen ake yi yanzu, duk da basu wani hira sosai amma Lion yana dannewa yana yi mashi kara sosai, saboda har ga Allah yana kaunar Imran fiye da tunanin mai tunani, yau ba da ban Imran ba da tabbas ko Rimsha bata mutu ba kaɗan ne zai rage mata na rai a jikinta, ko Areef ne ya yi mashi irin bugewar da Rimsha ta yi mashi har wayarsa ta faɗi sai ya wanke mashi fuska da mari bare kuma wata bare, kuma badan sumar da ta yi ba da sai ya doɗe mata kunne da mari koda guda ɗaya ne dan gobe ta kula amma Allah ya taimaketa ta suma. Har bakin mota sojan dake yi masu girki nan ya rakasu, Imran ne ya ja motar shi kuma Lion kamar kullun wanan izza tana nan gidan baya ya shiga. Da gudu Imran ya figi motar suka bar gidan, dan Lion baya son tuƙin mota a hankali, hakan ba karamin ɓata mashi rai yake yi ba ya fi son yaga ana sharara uban gudu da mota. "Saif ina muka nufa ne?" Imran ya tambaya yana kallonsa ta cikin mirror motar. Ya jima kafin ya fara magana a nutse "For now dai ka fara zuwa gidan cin abinci ka sayi breakfast daga nan mu wuce babbar masallacinku ina son nayi magana da malamanku". Sosai Imran ya ji daɗi ko ba komai Lion a duk in da yake yana daraja malamai na ko wace kasa, yana mutuntasu, kafin musulunci ta zauna a zuciyarsa sosai aikawa yake yi a ɗauko mashi malaman a kawo mashi har wani gidan hutawarsa dake a cikin daji ta bakin ruwa, wajen babu mutane haka kawai ya zaɓi da ya je ya yi gini a can, amma yanzu da musulunci ya ratsa shi yana iya tashi da kansa ya je ga malamai, yana kuma girmamasu. Babban abin farinciki wadda ya sanya Lion zai je wajen malamai shine dan su yi wa Areef addu'a tare da sauƙar Al Qur'ani mai girma, duk da ya sanya a kasarsu ana yi masu amma bai ishe shi ba, yana so a nan ma ayi masu. A ɓangaren Rimsha kuwa, good 3 hours ta ɗauka a sume kafin Allah ya sa ta farfaɗo, baiwar Allah har wani wiki wiki ta yi kamar wadda ta ci uban gudu ta ƙoshi, ta tsorata ainun ba kaɗan ba. Da kyar ta iya sauƙowa daga saman bed nata ta nifi toilet, wani irin wahalallen jirine yake ɗebanta saboda yunwa da take ji, sai faman dafa bango take yi domin ta isa toilet lafiya ba tare da ta taɗi ba. Allah ya taimaketa ta shiga toilet lafiya ta yi wanka ba tare da ta faɗi ba, tana fitowa ta nufi wajen trolley ta dake a cikin dressing room na ɗakin, sauri sauri ta shirya cikin wata daguwar riga abaya black color, ta yi kyau sosai sai dai har lokacin jiri sosai take ji. Bayan ta gama shiri fes sai tashin kamshi take yi, da kyar ta lallaɓa ta nufi waje. Kitchen ɗin ta sake komawa dan har ga Allah yunwa take ji, sai dai a wannan karon tana tafiya ne tana sanɗa kamar wata ɓarauniya, sai lallaɓawa take yi dan kada su sake haɗu, yau gaba ɗaya yasa ta ji bata son sake yin ido huɗu da shi, tsoronsa ya sa zuciyarta ta sake yin nesa da shi sosai, gaba ɗaya ta ji jikijta ya mutu, bata fatar rana irin ta yau ta sake zuwa a cikin rayuwarta, sai dai kuma fa son shi da kauna shi kara ninkuwa ya yi a cikin zuciyarta, wani irin azababben son take yi mashi wadda baki bai isa ya iya furtawa ba. Har ta fito palon kasa babu kowa, Kitchen ta sake wucewa nan ma babu kowa, duba kayan abinci ta yi da wasu abubuwa da zata buƙata, kwata kwata babu indomie bare su supaght amma dai akwai dankalin turawa dan suna cinsa suma, sannan akwai nama da kuma kwai sosai da sosai, nama da kwan (eggs) sun fi komai ma yawa a cikin kitchen ɗin, sai wasu kalolin cimar da bata taɓa ganin irinsu ba, tunawa ta yi da yadda ta ga sojan nan yake haɗa ɗanyen kwai da ɗanyen nama waje guda yana kwaɓawa, wani iri ta ji ajikinta, abicinsu sai su, bai dafa namanba ya zuba ɗanyen kwai ya kwaɓa kafin ya yi shi kamar yam balls ya soya bayan ya zuba kayan haɗi kenan. Guntun tsaki ta ja a fili ta ce "Allah ya kiyaye, ba a dafa nama ba ake soyawa, shima soyawar sai a rasa dame za'ayi sai da kwai, bayan nan a zuba wasu shegun kayan haɗi marasa kan gado, Allah ya sawwaka ya kiyaye na ci irin wannan abincin, anyama waƴan nan suna da maggi kuwa? Naga ranarma kamar kazarsu ba maggi, ko dai wani abin suke sakawa a matsayin maggi ne? Oho dai matsalarsu ce, amma anya abincin nan zai yi karni kuwa? Na san dai GAR ba zai taɓa cin abu mai karni ko wari ba, dole dai akwai yadda suke yi wa wannan irin abincin nasu dan kada ya yi wani abin da ba shi ba". Ta ɗan jima tsaye tana surutanta kafin ta wuce ta ɗaura ruwa a saman gas da wani ɗan ƙaramin kyakkyawan pot mai shegen kyau da tsada, sai kyalli jikin pot ɗin yake yi tamkar yanzu aka fitar da shi daga kwalinsa. Bayan ta ɗaura sai ta ɗauko dankalin turawa ta ɗebo daidai yadda take buɗakata tare da ɗebo kwai guda uku sai nama kuma ta ɗauki na kaza, bata ɗauki kazar gaba ɗaya ba sai ta yanki rabi ta mayar da rabi cikin freezer, sannan ta buɗe drawers dake a cikin kitchen ɗin dan neman irin su Maggi da su mai (oil) ta sami mai amma bata sami maggi ba sai dai wasu kayan haɗin wadda bata ma san tayaya ake amfani da su ba, ajiye wa ta yi ta koma wajen ɗayar freezer a nan ta sami fresh kayan miya masu kyan gaske, tattasan manya manya Tomatoes ɗin kam zaka ce mutun ya tsara shi, dan ko ance ka yi halittar Tomatoes da kanka ba zaka wuce yin manya manya masu kyau fresh kamar su ba, ga attarugu manya da su chilling pepper, albasar su ma wani irin smoot jikinsa yake gasu manya farare tas. Ɗebar abin da take buƙata ta yi ta koma gaban gas ta fara aikinta. Bayan ta haɗa abubuwan da zata buƙata dan yin jalof ɗin dankalin, ta gyara komai ne ta wuce ta fita a kitchen ɗin, ɗaki ta koma ta duba jakar school nata ta ɗauko 1k da Imran ya bata tare da ɗaukar hijabi har kasa ta sanya a jikinta ta nufo waje dan ta je ta sayi maggi. Tana fitowa ta isko sojoji guda biyun nan, da mai yi masu girki sai kuma mai gadin gate ɗin suna zaune saman wasu lafiyayyun luntsuwa luntsumar kujeru masu kyau da tsada a bakin gate ɗin. Sannu ta yi masu zata wuce ta fita sojan dake yi masu girki ya daka mata wani mahaukacin tsawa wadda ya sanyata yin baya a sukwane. "Where are you going?!!" Ya faɗa fuskarnan babu annuri ko kaɗan, ita bata san cewa gidan Lion sai da izininsa ake shi kuma sai da izinin sa ake fita ba, shiyasa ranar da Akil ya kawo mata kayanta sai da ya kira Imran akan ya zo ya karɓi kayan sun hana shi shiga. Cikin rawar murya ta gaya mashi maggi zata sawo a waje, tsawa ya kuma daka mata akan ta wuce ta bashi waje ta koma cikin gida ko kuma ya yi kwallo da ita, sojan dake tsaron gate ɗin ne ya dakatar da su da cewa ta koma bari ya saya mata maggin, shi har ga Allah Rimsha ta yi mashi, tun ranar da ya fara ganinta, shiyasa ya yi mata sauƙin kai har da cewa zai je ya sawo mata maggin. Da mamakin sojan dake yi masu girki yake kallonshi, miƙewa ya yi ya nufi waje, tana tsaye tana kallonsa jikinta sai kerma yake yi, har ga Allah tana tsoron sojoji sosai amma a haka zuciyarta tayi mata rashin adalci ta kamu da son GAR. Har ya kai bakin kofa zai fita sai kuma ya juyo cikin harshen turanci ya ce ta bashi kuɗin Nigeria dan shi dollars ne ke gare shi, kuɗin kasar su gaba ɗaƴansu suke da shi, tun da suka zo basu fita waje ba bare kuma su ce zasu je canjin kuɗi. Cikin sauri ta miƙa mashi 1k dake a hannunta, jujjuya kuɗin ya yi yana karewa kuɗin mu kallo kafin ya ɗago ya tambayeta me sunan abin da zai saya mata sannan kuma a ina zai saya mata ɗin. Cike da tsoro ta ce mashi ko ta zo su tafi tare ne? Girgiza mata kai ya yi ya ce ta zauna a gida domin fitarta sai ya fi zama masu haɗari akan nasu fitar, duk wanda ya shigo gidan idan suka bari ya fita ba da sanin Lion ba sai ya hukuntasu, sannan kuma su har ga Allah suna yi mata kallon tana da matukar muhimmanci tun da har Lion ya iya bari ta zauna agidansa abin da a baya ko da gigin wasa basu taɓa ganin makamancin hakan ba, basu san cewa darajar Imran ta ci ba, Imran ya yi wa su Lion abin da ba zasu iya mashi wani wulakanci ba shiyasa kawai take gidan. Wucewa sojan ya yi ya fita shi kuma ɗayan yana zaune kamar wani gunki yana latsa waya, fara zagaye gidan ta yi tana ƴan dube dube, ba karya gidan ya haɗu iya haɗuwa. Can ta hango kamar mutane ne a ta bayan wajen garden ɗin gidan, da sauri ta karisa wajen, waƴan nan masu kwacen waya da Lion ya kama ne, suna zaune sun gama cin abincin da sojan ya basu. Ganita yasa suka fara kallonta daga sama har kasa, cikin rawar murya suka gaisheta dan a tunaninsu matar gidan ce da yake ta zumbula hujabi har kasa kamar wata matar liman. Mamaki ne ya kamata akan me ya kawo su gidan nan kuma, sun ci bakar wahala kamar ba gobe sun koɗe sosai, bayan abinci da ake basu ba wani abu kuma da ake basu sai horar wa, yanzu ma an barsu ne su gama cin abinci, da zarar sun gama sojan nan zai zo ya dasa daga basu wahala da yake yi, bayin Allan har sun gwammaci da basu zo duniya ba saboda bakar wahala da suka sha a gidan THE GENERAL OF THE ARMY'S duk sun rame sun zama kamar kashi da rai. Da sauri ta juya ta bar wajen ta koma bakin gate ta tsaya, bayin Allah nan sun bata tausayi sosai da sosai. Ta jima tuna tsaye a wajen kafin nan sojan ya dawo, shi kuma ɗayan ko ɗaga ido bai yi ya kalleta ba, kuma dama shi ba ya ganin abin da ba'a gabansa take ba, ma'ana abin da bai shafeshi ba, horon Lion ne shi, sun fi kusa da Lion shiyasa ya ke yin ɗabiu irin na Lion ɗin, yake kwaikwayon ogan nasa. Miƙa mata pack na maggin ya yi tare da canjin 200 pack ya saya mata, karɓa ta yi tana mashi godiya, ya sha tafiya kafin ya cinma shago, danma dai ba tafiyar yara yake yi ba, dakunsa ɗaya daidai yake da koma na ƴara. Wucewa ta yi ta koma cikin gida, da ido ya bita har ta kurewa ganinsa sannan ya koma saman kujerar da yake zaune ɗazun ya zauna yana faɗin "Mark i really like this girl, the way she is talking the way she is walking hey i like everything about her". Ba tare da mark ya ɗago ya kalle shi ba ya ce "Are you fall in love?" Cikin sauri ya girgiza kai alamar a'a shi ba son ta yake yi ba domin suma da alama babu aure ko soyayya a tsarinsu, bai ji kunya ba ya gayawa mark shi dai kawai sha'awar ta yake yi ba soyayya ba. Jinjina mashi kai Mark ya yi tare da miƙewa ya koma cikin gida. RIMSHA Tana tsaye a gaban gas tana faman juya jolof ɗin dankalinta da bai ji wani kayan haɗi sosai ba sai gayyar tattasai da nama da kwai, ba su curry da sauransu wayan da ta saba, sai dai nasu wadda bata san ya ma ake amfani da su ba, sai kawai ta yi girkinta a haka. Tana tsaka da aiki kamar daga sama taga an ɗauki tukunyar dankalin nata daga kan gas ɗin sai cikin abin zuba shara aka wurga, a razane ta ɗago kanta tare da juyowa dan taga wanene, wannan Mark ɗin ne mai yi masu girki, yana tsaye fuska babu annuri ko kaɗan, da hannu ya nuna mata hanya akan ta fita masu a kitchen ɗin nan, duk ta buɗe masu ko'ina da warin abincinta shiyasa ya ɗauki tukunyar gaba ɗaya ya jefa a abun zuba shara. Bakin cikine yasa ta rushe da kuka tare da wucewa da gudu ta haura sama, tana shiga bedroom nata ta faɗa saman bed tana kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, baiwar Allah tana jin yunwa sosai kukan nata ma baya fita sosai. Sai da ta yi kuka mai isarta sannan ta miƙe ta ɗauki wayarta ta fara kiran layin Imran, bugu ɗaya ya ɗauka, cikin kuka ta gaya mashi yunwa take ji kuma ta yi girkinta soja ya zubar mata. Hakuri Imran ya bata tare da ce mata yanzu Akil zai zo ya ɗauketa suje gidansa su wuni sai ya dawo zaizo ya ɗauketa, cike da murna ta amsa mashi da to sannan suka yi sallama. Shiryawa ta yi fes ta fito waje, kai tsaye gardin na gidan ta nufa ta zauna a saman ɗaya daga cikin kyawawa kuma tsadaddun kujerun dake a wajen, tana zama ta fara kiran Akila a waya dan ta turo mata number daddyn Jelly su gaisa da Aylarta. Sau uku tana kiran layin Akila amma Akila bata ɗaga ba har Akil ya iso, sojan nan ya hana shi shiga gidan ita kuma ya hanata fita, domin idan baku manta ba dokace ba'a shiga ko fita sai da izinin Lion. Kuka ta fara yi tana kiran layin Imran, ta gama cin burin yau zata wuni da su Umaisha amma sojan nan yana son hana ruwa gudu. Bugu ɗaya Imran ya ɗauka, cikin kuka ta gaya mashi wai ba zata fita ba har sai Lion ya bada izinin ta fita, hakuri ya bata tare da ce mata yanzun nan zai je ya yi magana da Lion ɗin yana cikin mota shi kuma Imran yana cikin banki zai ciro masu kuɗi, da haka suka yi sallama da ita akan ta bashi minti biyar yanzu zai fito daga cikin banki ya sami Lion a mota kada ta damu........... Nima dai na wuce sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai , LONG PAGE HOT COMMENTS 🔥 💖💖TRIPLETS💖💖 E77-78💖 Bugu ɗaya Imran ya ɗauka, cikin kuka ta gaya mashi wai ba zata fita ba har sai Lion ya bada izinin ta fita, hakuri ya bata tare da ce mata yanzun nan zai je ya yi magana da Lion ɗin yana cikin mota shi kuma Imran yana cikin banki zai ciro masu kuɗi, da haka suka yi sallama da ita akan ta bashi minti biyar yanzu zai fito daga cikin banki ya sami Lion a mota kada ta damu. Shiru ta zauna tana ta hawaye ga bakar yunwar da take ji, shi kuma Akil ransa ya yi mugun ɓaci dan haka sai ya wuce abinsa ya koma gida tun da abin ya zama raini wayo. Koda Imran ya koma mota ya gayawa Lion bukatarsa, sai da Lion ya ɗauki good 20mins kafin ya ɗauki wayarsa ya yi sojan massage akan ya bar Akil ya tafi da ita. Bayan minti ɗaya da tura saƙon sojan ya sake turo mashi saƙo akan Akil fa ya tafi, gayawa Imran ya yi Akil ya wuce, sosai Imran ya ji babu daɗi, kuma yasan halin Akil ko ya ce ya dawo ya ɗauketa wlh ba zai dawo ba, dan shi ba'a yi mashi walaƙanci a waje ya kuma koma wannan waje, babbar damuwar Imran ɗaya Rimsha tana jin yunwa, bai ɓoyewa Lion ba ya gaya mashi cewa Rismha tana jin yunwa kuma ta yi girki sojan ya zubar mata ga shi kuma su ba yanzu zasu koma gida ba kuma bata iya cin kalar abincin su ba. "And so what?" Shine abin da Lion ya ce mashi, bai damu ba dan dama yasan za'ayi hakan, jan motar kawai ya yi yana ta tunanin Rimsha har suka bar bankin suka nufi babbar masallacin Jumma'a. A ɓangaren gidan Abba kuwa, Akila na tsaka da barcinta misalin karfe 8 na safe wayarta ta fara kara, hakan ya yi sanadiyar farkawarta daga barcin ta mai shegen daɗi da take yi. Daga ta cikin bargo ta sako hannunta ta ɗauki wayar tata a saman bedside drawer ta mai da hannun nata cikin bargon. Idanunta duk barci ta yi picking call ɗin, murya can kasa kasa ta ce "Hllo mijin matar shi". Daga ɗayar ɓangaren Irfan ya sauƙe nauyayyar ajiyar zuciya kafin ya ce "Matar Mijinta ba dai har yanzu barci kike yi ba?". Turo baki ta yi kamar tana a gabansa ta ce "Yaya Irfan Allah ni sai ka biyani barcina". "Heartbeat kin fara ko? Zaki fara rikitani ko?" Kara shagwaɓe murya ta yi cikin salon magana mai jan hankali ta ce "Allah ni da gaske nake yi yaya Irfan ka biyani barcina, haka kawai ka kama ka tasheni daga barcina mai daɗi, to ba zan yarda ba kawai ka biyani" ta kai karshen maganar tare da fashewa da kukar shagwaɓa har da wani ƴarfe hannu da kafafu kamar tana a gabansa. Ai kuwa ba shiri ya fara rarrashinta, duk ta ruɗa bawan Allah, har wani haɗe words yake yi wajen rarrashin nata, kin yin shiru ta yi har sai da ya ce mata to ga shi nan zuwa yanzun nan sai ya goyata ta mai da barcin, sannan ne ta yi shiru tana kara turo baki kamar biro. Sallama suka yi akan bari ya shirya yanzun nan ya zo, cike da murna ta katse kiran dan tana son ganin yayan nata kuma masoyinta, yana ranta sosai, daga daren jiya zuwa yau ta yi kewarsa sosai. Tana katse kiran tana ƙoƙarin ajiye wayar idanunta suka sauƙa akan massages da suka shigo, ɗan taɓe baki ta yi kafin ta fara buɗe massage ɗin, wasu tun karfe biyar aka turo su, wasu kuma karfe 6 wasu 7, na farkon ta fara karantawa kamar haka. "Amincin Allah tabbata a gareki my angel, ina fatan kin tashi lafiya, kuma ina fatan Allah yasa mafarkina aka yi jiya da daddare dan nidai nayi mafarkin ki gaskiya, na yi mafarkin ina goye da angel ɗina, so fatan kema dai kin yi nawa, na barki lafiya sai kuma anjima". Sake buɗe sako na biyu ta yi "My angel sarkin barci kuma sarkin shagwaɓa, ina matukar kaunar wannan shagwaɓar taki, ina son jin yadda kike cewa I love you please ko zaki faɗa mani ko sau ɗaya ne?". Daɗin massage ɗin yasa bata san time ɗin da ta furta I love you a fili ba, sai dai kawai jin word ɗin ta yi ya fito fili, ƴar murmushi ta saki kafin ta buɗe next massage "A gaskiya kin iya furta kalmar so my angel" cikin sauri ta duba time da ya aiko sakon 7:5 yanzu kuma 8:12 ne mamaki ne ya kamata yaushe ya ji ta ce i love you bayan yanzu ta yi maganar, massage ɗin kuma tun awa ɗaya baya ya turo, bata kara ruɗewa ba sai da ta ga massage na gaba in da yake cewa. "Sarkin ruɗewa, kina mamakine dan nace kin iya cewa i love you tun baki faɗa ɗin ba? To ki daina saurin ruɗewa ki rinƙa yin tunani kafin ki ruɗe, mafiyawancin abin da nake faɗa dangane dake hasashen sa kawai nake yi, yanzu ma na yi hasashen zaki ce i love you ɗin ne yasa na yi maki wannan massage ɗin tun kafin ki faɗa, cos bana son ki rinƙa yawan ruɗewa shiyasa na gaya maki ta yadda zaki gane, idan ba haka ba muka cigaba a haka na san wata rana sai na kai yi asibitin kwakwalwa saboda ruɗewa, so kada ki rinƙa ɗaukar komai na daga magana ta kamar nasani ne na faɗa, hasashe nake yi kuma kowa zai iya yin hakan, idan hasashena gaskiya ce ki ajiye mani hot kiss zan zo na karɓa anjima da daddare, bye sako daga ɓoyayyen masoyi, Majoon ɗin Laila kuma Romeo'n Juliet". Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauƙe kafin ta ajiye wayar tana faɗin "To meyasa baka bar mani hanyar da zan yi maka reply ba? Ina son ganin nima ina yi maka reply". Ta kai karshen maganar tare da sauƙowa kasa daga saman gadon ta nufi toilet dan ta yi wanka ta shirya yaya Irfan nata yana zuwa, sai dai fa ba yaya Irfan ɗin take tunani ba ɓoyayyen masoyi take tunani, shine a cikin ƙwaƙwalwarta da zuciyata, ya iya tsara kalamai da kuma kula, daga gani yana da wasa da dariya bayan iya soyayya, daga gani gwanine wajen iya kula da mace, domin kuwa daga saƙonninsa zaka fahimci hakan. Bayan ta yi wanka ta fito ta ɗan gyara bedroom ɗin nata sannan ta shirya cikin wata atamfa pink color da ratsin baki ɗinkin riga da sket, kayan sun zauna a jikinta sosai da sosai, takalma plat shoe baki ta ɗauko tare da mayafi shima baki sannan ta feshe jikinta da perfumes nata masu daɗi, simple make up ta yi ta yi kyau sosai ba karya. Saman bed nata ta zauna farinciki ya sa kwata kwata bata jin yunwa a yanzu, bata da burin da ya wuce yaya Irfan ya zo ta ganshi. Sai murmushi take yi ita kaɗai, tana zaune a wajen wayarta ta fara kara, cikin sauri ta ɗauki wayar dan a tunaninta yaya Irfan ne, tana duba mai kiran sai ta ga unknown number, cikin zunuɗi ta ɗauki kiran domin har ga Allah tana kewar jinsa. Cikin sanyin murya ya ce "Assalamu alaiki warahmatullahi taala wa barkatuhu my angel". Ɗan ciro wayar ta yi daga kunnenta tana duba screen ɗin dan ta ji muryar ya yi mata kama dana wani da ta sani, tabbas jiya da ta ji muryar ta ji kamar ta taɓa jin makamancin wannan zazzakar murya a rayuwarta sai dai ta rasa a ina ne, to yau ma da ta sake jin voice ɗin nasa da kyau ya sake fito mata karara kamar ta taɓa jin wannan murya, mamakine ya kamata. Jin ta yi shiru yasa ya ce "Lafiya kuwa heartbeat me yasa kika yi shiru?". Kakalo murmushi dole ta yi kamar yana a gabanta, cikin sanyin murya ta ce "Wlh ina tunani ne na ji muryarka ya yi mani kamar na san shi". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Mai yi wu wa amma dai da kamar wuya gaskiya, yanzu dai bama wannan ba gaya mani me zaki ci na kawo maki?". Ƴar waigawa ta yi ko zata ga ta ina yake kallonta da har yasan bata ci komai ba. "Heartbeat na gaya maki ki daina wahalar mani da kanki, Shiyasa fa ɗazun na gaya maki mafiyawancin lokaci hasashen abu nake yi akan ki, duk da wata zubin idan bana aikin komai e tabbas ina tsayuwa in kalli duk wani abin da kike yi amma ba ko yaushe ba, wani sain canka kawai nake yi saboda na yi maki farin sani, na san abubuwan da zaki yi da wadda ba zaki yi ba, hakan yasa ma hasashen nawa yake zuwa gaskiya". Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauƙe kafin ta ce "To dan Allah ka gaya mani sunanka ka ji abokina? Sannan ka gaya mani waye kai?". Nisawa ya yi tare da faɗin "Wow gaskiya na ji daɗi sosai da kika kirani da abokinki, daga aboki sai na zama masoyi daga nan sai miji". Ƴar murmushi ta yi yana faɗin "Uhm to ni dai yanzu ka gaya mani sunan ka". "Heartbeat sarkin rigima, ke dole sai kin ji sunana ko? To nima kawai ki kirani da Heartbeat ɗin ki". Turo baki ta yi a shagwaɓe ta ce "Ni ban yarda ba sunanka na gaskiya zaka faɗa Mani". "Heartbeaaaaaaat.... kina rikitani da wannan shagwaɓar taki fa, nima kuma na iya idan baki kyaleni haka na samu na yi aikin dake a gabana ba tabbas sai na yi maki kuka". Yarfe hannu ta fara yi mashi tare da fara magana kamar zata yi kuka "Allah ni ba zan yarda ba, kawai ka gaya mani sunanka idan ba haka ba tom kuka zan yi maka Nima". "Uhm uhm heartbeaaaaaat Allah ki bari idan ba haka ba yau ba zanci abinci ba, kuma ai nace zan gaya maki sunan nawa ko? To ki kyaleni haka nan ko dai na yi maki kuka soyayyane? Kuma ko kin rarrasheni ba zan yi shiru ba". Wow ta furta a fili, jin yadda yake zuba shagwaɓa yasa ya kara ciro wayar daga kunnenta tana bin screen ɗin da kallo, har ga Allah shagwaɓarsa ya yi mugun tafiya da imaninta, abin ya kayatar da ita. "Heartbeaaaaat me yasa kuma kika yi shiru? Kina son na yi kuka ne? Ko dai kina son na zo na same ki ne? Ni gaskiya na kiraki ne mu yi hira na ji muryar bugun zuciyata, dan haka ki yi mani magana masu daɗi idan ba haka ba zan yi maki kuka kuma sai kin goyani". Ya kai karshen maganar a shagwaɓe kuma da alama shima ya turo baki kamar yadda take yi saboda yadda ya fitar da maganar tasa ya nuna alamar kumatunsa a kunbure ya kuma turo baki. "Ni dai dan Allah ka gaya mani sunan ka kaji ko masoyin ɓoye?". Ƴar dariya mai ƴar sauti ya yi wadda ya sanyata lumshe idanunta tare da sake buɗe su a hankali, wannan dariya tasa bakaramin ratsa dukkan ilahirin jikinta ya yi ba, wani irin bakon yanayi ta fara ji a jikinta dan gane da shi yana ratsata, cike da kulawa ta ce "Yanzu ba zaka gaya mani sunan naka ba?". "Heartbeat you have to much of complain and silly questions, i told you ni ma ki kirani da Heartbeat naki kawai, sunana kuma zan gaya maki but not now, for now dai just call me your Heartbeat". Jinjina mashi kai ta yi tana faɗin "Okey my Heartbeat i really like this name, My Heartbeat wow so lovely name". "Wow my Heartbeat kin ji sunan da ya fito daga bakin ki kuwa? Kamar dan bakin nan naki aka yi shi". Cool murmushi ta saki tana ɓuye fuska da hannunta ɗaya. Shima a nashi ɓangaren murmushi yake yi. "Heartbeat zan je wajen school idan na dawo before ma na dawo zaki ga massages ɗina, idan kuma na dawo zan kira ki, Kin amince na je school ɗin?". Kai ta gyaɗa mashi tana faɗin "E ka je adawo lafiya". Shagwaɓe murya ya yi kafin ya ce "Heartbeat ki kula mani da kanki sosai, kuma ki sani ina da kishi sosai da sosai kawai dai ina dannewa ne saboda bana son takura maki a yanzu, amma nan gaba zan ɗaura heartbeat nawa akan hanya, yanzu dai wani fata zaki yi wa mijinki idan zai fita?". Tana bala'in son shagwaɓarsa ba karamin tafiya da ita yake ba, ya kware a iya shagwaɓa sosai da sosai, haka zalika ya iya tsara kalamai kamar dan shi aka yi su, ya san duk ta yadda ake rarrashin mace, bata san lokacin da ta narke mashi suka rinƙa zubawa juna shagwaɓa tare da kalaman sosai ba, daga karshe dai ta yi mashi addua'o'i kamar haka. "Allah ya rabaka da sharrakin duk wani abin halitta mutun or aljani komai, Allah ya haɗaka da alkhari dake tattare da duk wata abin halitta, Allah ya biya maka buƙatunka na alkhari tare da cika maka burinka na alkhari, Allah ya rabaka da mama da baba tare da duniya baki ɗaya lafiya, Allah ya tsare mani kai daga faɗawa duk wani abin da Ubangijin mu ya hanemu da aikata shi ya kuma baka iko da aikata duk wani abin da ya umarce mu da mu aikata, ka kula mani da kanka sosai sannan kuma kada ka barni da kewarka sosai, idan ka jima baka kirani ba zan yi kuka, ni please ka bani real number ka ka ji?". Nisawa ya yi cikin sanyin murya mai tattare da natsuwa tare da jan hankali ya ce "Heartbeat kin gama yi mani komai a duniya, wannan addua'o'i da kika yi mani serious ba zan taɓa mancewa da su ba, a really love, ina fatan ki zama mallakina na har abada ni kaɗan, ba zan so na rasaki ba domin idan hakan ta faru zan shiga tashin hankali wadda wata kila ya zama sanadina, gaskiya ba zan mance da wannan rana ba, sannan na yi maki alkawarin ba zan taɓa barinki da kewana ba bugun zuciyata, tabbas zan kira ko kuma na tura maki saƙo, fata na dai ki kula mani da kan ki, kuma kada ki yi wa yaya Irfan wannan kayatatcen murmushi naki, idan ba haka ba kika yi mashi murmushi to ki rubuta ki ajiye tabbas zan yi kuka da hawayena, ni ba zan taɓa hanaki yin hira da shi ba for now, amma dai kada ayi mashi murmushi". Jinjina mashi kan ta yi tare da faɗin "Shikenan tom zan yi kokari na kiyaye duk wani abin da kace bakaso ko kake so, amma tom ka turo mani hotonka mana in gani, na san cewa ni kam ka san ni tun da har ka kamu da sona, to tabbas ka sanni, please kai kuma ina son ganinka ka ji?". "Heartbeaaaaat ba zan bari ki ganni ba har sai kin kamu da sona kamar yadda nake jin naki azababben soyayyar, sannan kuma ni ba hoto zan tura maki ba, kai na zan kawo maki har gida kin ji ko?". Gyaɗa mashi kai ta yi kamar tana a gabansa, jin bata yi magana ba alamar bata ji daɗi bane yasa ya ce "Am so sorry my bugun zuciya zan tura maki hotona kin ji ko? Ton da hakan kike so zan tura maki da daddare yanzu dai please ki yi murmushi bana son idan kina magana dani face ɗin nan naki ya zauna babu murmushi, kuma kin ga ai ina son murmushi naki sosai ko?". E ta amsa mashi da shi "To arinƙa yi mani murmushi zan ji daɗi sosai da sosai, yanzu dai zan tafi sai na dawo ko?". To da amsa mashi da shi, shiru suka ɗan yi na ƴan mintoci kafin ya ce "I really love you more than your expectations". Ya yi maganar cikin wata iriyar shagwaɓa mai mugun janhanlin mai sauraro tare da kwantarwa da masoyi zuciyarsa. "Heartbeat" ya ambaci sunan ta, "Na'am my heartbeat" ta amsa. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce "Heartbeat ina matukar san in ji kalmar soyayya ta fito daga bakinki zuwa gare ni kin ji ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi tare da cewa "I love my heartbeat". Wani irin numfashi ya ja tare da saukewa a hankali kafin ya ce bye my heartbea. Bai katse kiran ba har sai da ta amsa mashi da bye ɗin ita ma, kiss ya yi wa jikin wayar tasa kafin ya katse kiran. Shiru ta zauna a saman bed ɗin tana tunanin a ina tasan wannan voice ɗin, tabbas koba wannan muryar bane ta taɓa jin makamanciyarta a tare da wani na kusa da ita, to waye zai iya kasancewa? Ta mance ba zata iya tunawa ba. Ta jima zaune a wajen tana jujjuya kalaman heartbeat nata a cikin ƙwaƙwalwarta kafin Irfan ya kirata a waya akan ga shi ya zo yana ƙofar gida. Da sauri ta ɗauki wayarta ta fito, ta yi Sa'a palon kasa babu kowa, Ammie tana cikin ɗakinta, cikin sauri ta wuce waje dan ma kada wani abin ya dakatar da ita. Zaune ta isko shi a cikin motarsa yana ɗan latsa wayarsa, ganinta yasa ya fito daga cikin motar da sauri tare da zagayawa ya buɗe mata ɗayar ɓangaren, sai kallonta yake yi ya kasa cire idanunsa daga kanta dan gaskiya babu karya ta yi kyau sosai yau ɗin nan. Front seat ta zauna shima ya koma nashi ɓangaren ya zauna, cikin natsuwa ta ɗaga mashi gaisuwa, da faraa ya amsa tare da tambayar ya ta kwana daren jiya, kanta na kallon kasa ta amsa mashi da lafiya tare da ce mashi tana jin yunwa. Ɗan leƙo furkarta ya yi cike da zolaya ya ce "Za'a bani abincin a baki idan muka je wajen cin abincin?" Hannu tasa ta rufe fuska tana ƴar dariya ta manta yadda suka yi da Heartbeat nata yanzu, ya ce mata ko murmushi kada ta yi bare kuma dariya, to ga shi dai ta mance ta yi dariya. "Yaya Irfan Allah ka bari bana so" ta faɗa tana kara rufe fuska, hannayenta ya riƙo dukka biyu yana faɗin "Allah heartbeat wannan tsiyar taki ta isheni maza buɗe idanunki ki kalleni". Make kafaɗa ta yi tana kara runtse idanunta. Hannun yasa cikin wasa yana ƙoƙarin buɗe mata idanun nata da gaske, faɗawa saman kirjinsa ta yi tana dariya tana faɗin "Allah yaya Irfan zan yi maka kuka idan baka kyaleni ba". Mutuwar zaune ya yi har ga Allah babu wata macen da ta taɓa kwanciya a jikinsa sai Umaisha lokacin da take karama, lokacin da Ommu ta tafi ta barta, a lokacin ya sha goyanta sosai, bayan ita babu wata da ta taɓa zama a jikinsa, ko Aafia bata kwanciya a jikinsa sai dai ya riƙo hannunta, ita ma Umaisha da ta kai 10 years ta daina kwanciya a jikinsa sai dai ya riƙo hannunta, yau rana ɗaya Akila ta kwanta mashi ajikinsa, abin ya sanya shi sumar zaune, ya kasa motsawa saboda wani irin yanayi daya tsinci kansa a ciki. Jin ya yi shiru ne yasa ta ɗago kanta tare da shagwaɓe murya ta ce "Yaya Irfan zanyi maka kuka Allah idan ba mu tafi wajen cin abinci ba". Wannan shagwaɓa tata ba karamin sake haukata shi ta yi ba, haka kawai ya tsinci kansa da rungumeta sosai a jikinsa, bata wani damu ba saboda tana yi mashi kallon yayanta kamar yadda take kallon su Imran, kuma idan baku manta ba ta saba kwanciya a jikin Imran da Akil sosai da sosai shiyasa shima Irfan ta ɗauke shi kamar su Akil ɗin. Itama rungume shi ta yi tana kara zuba mashi shagwaɓa, rankwafo da kansa ya yi a daidai sai tin tata kafin nan ya ambaci sunanta da wata iriyar murya wadda ta sanya ta jin faɗuwar gaba tare da ɗagowa da kanta cikin sauri, tana ɗagowa fuskarsu ta haɗu waje guda sakamakon ranƙwafo da kansa da ya yi daidai tata. Kuskure ne dan kuna causing da mutun kuma kuna soyayya da shi kice zaki ruƙe mashi hannu ko ki kwanta a jikinsa, wannan babbar kuskure domin kamar yadda ya ji sha'awar yin soyayya dake a matsayin ku na causing haka zai ji sha'awar jikinki ya kuma ji felling akan ki, so wannan kuskure kwatanta abin da Akila ta aikata, yaya uwa ɗaya uba ɗaya daban, jinin dake guda a jikin ki da nashi iri ɗaya ne domin daga waje guda kuka sami jinin, sai dai wata hikima ta Ubangiji da yake banbance jinin dan samun maslaha, Allah mai ni'ima akan bayinsa, ya yi mana ni'imar banbantawa yaya da kuma kanwa jinin sune bayan kuma daga waje guda suka sami jinin, Allah ya banbanta mana ne saboda dalilin da dama, kaɗan daga ciki kuma akwai cutuka, kamuwa da cutuka, idan jininku ya kasance iri ɗaya sak to idan ɗaya ya kamu da cuta kuna gida ɗaya zaka iya ɗauka kai ma cikin sauki, amma idan jininku ba ɗaya ba, ba kallai ka kamu da wannan cuta cikin sauri ba, Ubangijin ya yi mana niimomi da dama me yasa mu ma ba zamu zage dantse wajen gode mashi ba?. Zuba mata idanu ya yi yana ƙare mata kallo, ita kuma kirjinsa take kallo yayinda hannunta yake a saman butir na rigarsa tana wasa da shi. Heartbeat ya sake ambatar sunan ta da murya can kasa kasa, na'am ta amsa mashi da shi ba tare da ta ɗago ta kalle shi ba. "Heartbeat ina sonki sosai, ban taɓa yin soyayya ba sai a kanki, ban taɓa zama da mace kamar haka ba sai a kanki, ban taɓa zama nayi hira da mace ba sai a kanki, ban taɓa ruke hannun wata mace ba bayan su Aafia sai a kanki, ina yi maki soyayyar da bana yi wa kaina ita, please ki ruƙe mani amana,! idan na narasaki zan shiga mawuyacin hali, ba zan ɓoye maki ba, na taɓa son wata wadda bata san ina yi ba, amma Allah bai kaddara ba, ta yi aurenta, akwai wannan tabon a zuciyata, dan Allah ki kula mani da kanki domin zuciyata ba zata iya sake ɗaukar wani taboba, komai kankantar wannan tabon kuwa zuciyata ba zata iya ɗauka ba, zan cutu matuƙa wata kila kuma sai dai in ce Allah ya bamu kyakkywar karshe" ya kai karshen maganar cikin wata iriyar murya mai kama da wadda zuciyarsa ta karaya da abu. Ɗago kanta tayi hawaye na zuba daga kumatunta yayin da shi kuma idanunsa suka yi jawur kamar jini, amma da yake soyayya yana ganin hawayen idanunta ya sa ya ji hankalinsa ya tashi, gaba ɗaya ya rasa natsuwarsa, cikin sigar rarrashi ya ce "Haba my heartbeat menene kuma ya faru kike kuka? Me akayi maki?". Duka ta kai mashi a kirjinsa tare da rungume shi sosai tana faɗin "Yaya Irfan meyasa zaka ce haka? Meyasa kake tunanin cewa ni zan barka? Me yasa zaka yi mani haka? Kana ganin hakan adalci kayi mani ne?". Har ga Allah a cikin zuciyarsa yana jin tamkar wani abu zai faru shiyasa ma ya yi mata wannan maganar, amma da ya ga tana kuka sai ya ajiye zancen a gefe ya shiga rarrashinta babu kama hannun yaro. Sun ɗan jima a haka kafin nan su dawo daidai, daga nan suka cigaba da soyayyarsu, gudun kada wani abin ya gifta a tsakaninsu na daga sharrin shaiɗan yasa ya ce mata ta tashi daga jikinsa bari ya kunna motar suje wajen cin abinci, to ta amsa mashi da shi, har ga Allah yana jin matukar daɗin kwanciya a jikinsa da ta yi amma gudun kada sheɗan ya yi galaba a kansu ne yasa ya ce ta tashi ba dan yana son su je wajen cin abincin yanzu ba, sai dan yana son ta bar jikinsa domin kula da addini da kuma al'adar mu. Kunna motar ya yi suka bar wajen, kwata kwata ta manta da cewa bata gayawa Ammie ba, kawai ita dai ta bi yaya Irfan ɗinta abinta. TSAKANIN YAYA IRFAN DA ƁOYAYYEN MASOYI WAYE KUKE TUNANIN ZAI YI NASARA? KO DAI DUKKANSU ZASU RASA NE? MU DAI JE ZUWA, ITA DAI AKILA GABA ƊAYA TANA SON SU KO MA DAI ACE BATA SAN ME TAKE SO BA TA KAIMAIMAI!!. A ɓangaren su Jehan kuwa, bayan fitar Zinariya bai fi da minti ɗaya ba Jehan ta miƙe tana ruƙe da wayar Adiva ta shiga toilet, su kuma suna zazzaune a bakin bed ɗin suna jiranta. Tana shiga ta ajiye wayar hannunta a saman gefen baff ɗin wanka, sannan ta cire kayanta ta yi fitsari, bayan ya gama abin da zata yi dukka sai ta ɗauki wayar tana ƙoƙarin gyara kayanta, a juge su Adiva suka faɗo cikin toilet tare da banko kofa A'isha ta sanya sakata. Da mamaki Jehan take kallon su kafin ta ce "Lafiya Adiva, Maryam me ya faru kuka biyo ni cikin toilet haka?" Ta faɗa tana kare masu kallo. Sai haki suke yi tare da jan numfashi sama sama, Aisha ce ta ce mata "Jehan wlh Zinariya ce suka dawo ita da ƴar gold hannunsu na ruƙe da wasu shegun bulalu shine muka gudu kuma...." Bata kai karshen maganar ba suka ji an murza key ɗin kofar ta baya alamar an rufe su a ciki kenan. Zinariya ce ta rufe kofar tana faɗin "Dan ubanku yunwa ne zai halakaku acikin toilet ɗin nan, ba ku ba fita waje shegu marasa galihu". Sai surfa uban masifa take yi har suka fice daga ɗakin. Zama a gefen baff ɗin wanka Jehan ta yi tare da kunna wayar Adiva ta fara dube dube akan shedun da ta tara na gidan nan, duk hirar da Aisha ta yi mata ranar akan abin da Hajiyar daɗi take yi na daga sayar da kodar mutane da saurasu, dukka Jehan ta yi recorded na komai a cikin wayar ta ajiye, ga kuma video wannan Alhajin shima babbar shaida ce a gare ta, bayan haka kuma ta yi video Zinariya in da take magana da Alhajin akan ba ya zaɓi yarinyar da yake so ba? Dan haka ya wuce ɗakinsa, shima wannan babbar shaida ce wadda in dai ana bin gaskiya da adalci iya waƴan nan sun isa a kashe Hajiyar daɗi tare da ruguje magoya bayanta, sannan kuma ba iya haka Jehan ta tsaya ba, har da office nasu ta ɗauka hoto da video da kuma wasu tsirarun mutanen dake a cikin gidan, ta tara shaidu da dama wadda zata ruguje Hajiyar daɗi da su, sai dai kashe wayar Adiva babu kati kuma babu data, tana son ta yi posting na wasu daga cikin shaidunta wa duniya kowa ya gani amma babu hanyar yin haka sannan kuma bugu da kari basu da network a cikin gidan, Network ɗin nasu ya zo ya ɗauke ya zo ya ɗauke haka yake, kuma Jehan bata wani damu sosai ba, domin tasan idan ta fara posting nasu a Media ma to tabbas Hajiyar daɗi zata fara bincikar waye mai yi masu hakan, idan suka kamata kuma da wuya su barta da ranta, hakan yasa bata damu ta nunawa duniya abin da yake faruwa ba har sai ta fita daga cikin gidan. Zama suka yi a gefe gefen baff ɗin wanka dake a cikin toilet ɗin, tunanin makomarsu kawai suke yi, abin yana damunsu, ga shi waƴan nan shegu sun rufesu a cikin toilet ɗin ma baki ɗaya. Miƙewa Jehan ta yi tare da hawa saman baff ɗin ta keƙa window toilet ɗin, bata iya ganin komai a wajen sakamakon kura da ya baibaye window ta waje, guntun tsaki ta ja tare da komawa ta zauna tana faɗin "A'isha dama sun taɓa yi maku irin haka ne su rufe ku a cikin toilet?". Shiru Aisha ta ɗan yi kafin ta ce "E sun dai taɓa yi wa wata yarinya wadda ta zagesu lokacin Hajiya bata nan, shine sai suka rufe yarinyar a cikin toilet sai da ta yi sati ba ruwa babu abinci, ranar da suka ji Hajiya zata dawo shine suka yi maza suka zo suka buɗe yarinyar, wlh time da suka buɗe yarinyar nan ko miƙewa bata iya yi sai da aka ɗaga ta aka kaita cikin ɗaki, wannan ma fa tana shan ruwan cikin toilet ɗin kenan, da Hajiya ta dawo sai suka ce ai bata da lafiya ne, da haka maganar ta mutu, Hajiya ta kira wasu daga cikin likitocin ta aka duba yarinyar akayi jinyarta ta warke, wlh Jehan idan hajiya bata nan Allah waƴan nan tsinannun suna iya yin kisan kai su ce kwanan mutun ne ya kare na gaya maki". Shiru Jehan ta yi tana ƙoƙarin saving na recorded da ta yi wa maganar Aisha na yanzu, duk wani tambaya da zata yi wa Aisha sai ta kunna recording dan ta naɗi komai domin samun hujjoji da sheidun yadda zata rushe wannan tsinanniyar gidan. Bayan tayi saving ne sai ta ce "Tom mu dai dan ubansu dole su buɗe mu ko kuma mu karya kofar muga uban da za'ayi shegu tsinannu duk sai na ci ubansu, ba akwai hitter a cikin toilet nan ba?" Cikin sauri Aisha ta gyaɗa mata kai Alamar e akwai. "Yauwa jona mana ruwan zafi ki gani, zamu bubbga kofar da iya karfin mu, idan suka zo suka buɗe mu suna nuna alamar zasu cutar da mu muyiwa shegu wanka da tafasasshen ruwan zafi fatar jikinsu ta saɓule mu kuma ci uban shegu sai muga uban da ya tsaya masu, shima wadda ya tsaya masu idan ya zo idan da dama sai mu haɗa da shi, yanzu dai abin da nake so da ku shine ku cire tsoro, kuna jin wannan shegen tsoron wlh ba abin da zamu cimma, baa zama gwani kuma baa cinma buri sai an cire tsoro, suma sai da suka cire tsoro suka iya kafa wannan tsinanniyar gidan, tsoron Allah kawai ya kamata bawa ya ji ba tsoron wani daga cikin halittun Allah ba, babu wani ɗan adam da ya isa ya kashe ko ya raya sannan kuma basu da wuta basu da aljanna to dan haka mai wuta da aljanna kowai zamu ji tsoro, dolene kawai sai kun cire tsoro mu tunkari matsalar mu, ko zamu mutu ko mu yi rai, idan kuka ruƙe Allah kuka fara faɗa akan gaskiya da ƙwatarwa kanku ƴanci to bai kamata ku ji tsoron wasu shegun banza ba, ƴan adams ne fa kamar ku, dan haka ku ajiye tsoro a gefe muyi faɗa domin mutuncin mu, addininmu, darajar mu, ƴaƴan gobe masu tasowa, da kuma ƴancin mu". Ta kai karshen maganar tana kare masu kallo, duk sunyi wani jugum jugum da su suna binta da ido "Jehan zan baki shawara ina son ki sani Hajiyar daɗi fa ba kamar yadda kika ɗauketa bane, wlh faɗa gaba da gaba da ita ba abune mai yiwu ba, tun da kikaga wannan gida ya kafu tsawon lokaci kamar yadda Aisha ta faɗa to ina ga wlh akwai sa baki manya manya na wasu sassa daga kasarnan, to kinga ba lallaine bama ko mun fita da shaidar mu sami wata hukuma ta kula mu har ta dafa mana, kuma wlh idan kikace zaki yi fito na fito da ita zamu iya rasa rayuwarmu gaba ɗayanmu, ko da yaushe na sanki kina amfani da ƙwaƙwalwa why a nan kuma kike son ki yi amfani da karfin cin abinci bayan kuma kin fi kowa sanin cewa lallai anan ne ya dace da ki yi amfani da ƙwaƙwalwarki". Cewar Adiva kenan, kuma ta yi maganar murya ɗauke da damuwa fal ranta. Ajiyar zuciya Jehan ta sauke kafin ta fara magana cikin harshen turanci dan ta san Maryam da A'isha basa ji, kuma abin da zata faɗa sirri ce tsakaninta da ƴar uwarta Adivar. "Adive i knew what am going kin gane? Ki kwantar da hankalin ki yanzu ai ba yakarsu za mu yi gaba da gaba ba, saboda ma ba ta yadda za'ayi mu yake su muna cikinsu, shiyasa kika ga duk wani hujjoji dana tara ban bari su A'isha sun gani ba saboda suma ban yarda da su ba, kuma kema ba wai na yarda dake ɗari bisa ɗari bane, no ban yarda dake ba, kuma abin da yasa ban yarda dake ba shine kin kwana biyu a nan kafin na zo mai yiwu wa sun canza maki wani abin daga tunaninki a yadda na sanki, shine kawai..... Juya harshe ta yi cikin harshen Hausa ta cigaba da cewa "Ina son ne yanzu mu nuna masu jan ido, mu nuna masu ba su isa suce zasu rinƙa bamu umarni son ransu ba, fitowa zamu yi mu nuna masu mu fa mun fi karfin su, yanzu muma idonmu ya buɗe, ba wai nace mu fito mu yaƙesu kai tsaye ba, a'a juyamu da suke yi suna mana abin da suka ga dama shi nake son mu dakatar da su first, idan muka yi faɗa da su sau ɗaya sau biyu wlh ko ba komai zasu fara jin shakkar tunkararmu da wani rainin hankalin, kuma ba komai ne zasu rinƙa kwasowa suna kawo mana ɗakin nan namu ba, sannan bugu da kari ba ko da yaushe bane zamu na kin yarda da maganarsu ba, wata sain mu yarda amma fa idan muka je wajen wadda yake bukatar mu to a nanne zamu nuna mashi asalin bariki, yanzu yakin zai fara ne daga kan masu zuwa nan wajen dan biyan buƙatarsu da mata, ba da su Zinariya zamu fara ba, zan gaya maku dabarun da zaku na bin dan tsira daga hannun azzaluman nan wato Alhazawan nan". To suka amsa mata da shi tare da shirya yadda zasu ɓollowa lamarin, wannan ta kawo nata shawarar wannan ma ta kawo tata shawarar, haka suka rinƙa haɗawa Jehan tana tantance shawarar da za su ɗauka suyi amfani da ita, daga karshe dai suka yanke shawara ko wani dare misalin karfe ɗaya idan kowa ya yi barci za su fita su rabu izuwa sauran ɗakunan domin su sami damar da zasu tattauna da sauran waƴan da ke a cikin gidan, dan su haɗa kai su haɗa karfi da karfe su gudu tare su tsira tare, wannan kuma shawarar Jehan ce ta kawo, kuma dukka sun aminta da shawarar tata kuma sun ɗaura ɗamarar yakin ba kaɗan ba. Da haka ko wance ta zauna jugum jugum a gefe da gefen baff ɗin wanka suka buga uban tagumi suna tunanin yadda za'ayi su fita daga cikin toilet nan, ga yunwa ya fara addabawa rayuwarsu, dukkansu fuskokinsu abun ban tausayi, sun yi wani wiki wiki da su, Jehan ce kawai mai ɗan kwari a cikinsu, Adiva kam da yake bata shiga tashin hankali sosai kamar na su Jehan ba sai ta shiga damuwa sosai, dan ma dai Jehan na kara kwantar mata da hankaki ko da yaushe ne, badan haka ba, da akwai matsala. Idan muka koma ɓangaren gidan Abbi kuwa Idan muka koma ɓangaren gidan Abbi kuwa zaune suke misalin karfe 9 na safe, Abbi ne da Aunty kawai a palon sai hiransu irin na masoya suke yi cike da girmama juna da kuma mutunta juna, sai zolayarta Abbi yake yi ita kuma tana biye mashi, abin gwanin ban sha'awa da burgewa. Da akan yau za su je gidan su Hanan wato Katsina, amma da yake daddyn Jelly baya cikin natsuwarsa yau sai Abbi ya ce su bari sai ranar Monday, hakan yasa aka ɗaga tafiyar domin dama da shi da daddyn Jelly da Irfan da Imran sai Akil za su tafi da Hanan ɗin. Hanan kuwa tana ɗaki a kwance saman gadonta tana kallo a wayar Aunty, yanzu damuwarta ya ragu sosai da sosai. Wani irin fitinannen kamshi perfume ne ya daki hancin su Abbi, cikin sauri ya ɗago kansa kusan a tare da Aunty suka kai kallonsu saman benen dan daga nan kamshin yake fita. A hankali take sauƙowa, kafarta na sanye da bedroom slippers jikinta na sanye da wasu shegun riga da wando, wandon jeans ne ya natseta sosai ta yadda ya fito mata da ainahin surar jikinta, while shikuma rigar ya kasance irin t-shirt ɗin nan ne masu kananan hannun wadda ba su wuce kafaɗarta ba, skin na matar nan sai wani sheki yake yi, ya ji gyara iya gyara kamar wata ƴar 25 years, ta fito a cikakkiyar macenta, hajiya Hadiza ba dai ɗaukar wanka ba, ga jikinta kuma mai shegen kyau kamar ita ta tsarawa kanta, gata gwana wajen cin chewing gum, yanzu ma tana taku tama wani kas kas kas da chewing gum, aunty kuwa kullun sai iya kwalliya da lace da atamfa or shadda, ko irin kananan kaya masu ɗan fasalin nan bata sawa, ita gata malama ta sha sunnah ta ƙoshi sai iya saka manyan hijabai kamar wata matar liman, a gida ma zumbula hijabi take yi abinta. Tuni Abbi ya kafe Ommu da ido ya kasa ɗaukewa, yadda take taunar wannan chewing gum ɗin ya ilahi ya lillihi ba'a magana dan taunar ma da salo da rangwaɗa ake yi. Ta gaban Abbi ta zo ta wuce sannan ta koma hefensa saman hannun sofa ta zauna tare da rankwafo da kanta daidai da tasa, cikin salo da rangwaɗa ta ɗan hura mashi chewing gum ɗin a fuska. Wani dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali, har lokacin ya kasa ɗauke idanunsa daga kanta, gata bata yawan yin make up irin na haukarnan wadda idan miji ya zo ma zata ɓata mashi jiki, no ita simple make up take yi wadda zai kara tsatso mata da kyanta kuma ba zai ɓata wa mijinta jiki ba, ya kalla ya ji daɗi ya shafa face ɗin tata ya ji sanyi a ransa, ya rungumeta ya ji nishaɗi ba wai ya rungumeta Foundation ko powder ta ɓata mashi riga ba. Kas kas ta kara kyasta mashi chewing gum a kan fuska tare da sanya hannunta a saman idanunsa ta rufe mashi ido tare da kashe murya cike da kirsa da kisisina ta ce "Kai Sahibina irin wannan kallo haka ai sai ka kwashe mani kayan nawa gaba ɗaya, to ni dai gaskiya ban yarda ba Allah kuwa". Aunty kam sake baki ta yi tana kallon ikon Allah, ta kasa koda motsawa daga in da take, yadda kasan Tv haka ta mayar da Ommu da kallo, yau ga ɗanyen karuwanci tsagwaransa. Murmushi Abbi ya yi tare da cire hannun nata daga saman face ɗin nasa ya ce "Kai Hadiza ki kyaleni na kalli kayana". A zahirin gaskiya Abbi bai san time ɗin da ya furta hakan ba, kawai dai ya ji maganar ce ta fito mashi daga bakinsa. Matso da bakinta ta yi kusa da kunnansa kasa kasa ta ce "Tashi muje ɗaki sai ka kalli kayan naka da kyau da kyau zai fi ko?". Wani irin daɗi ya ji tana ratsa shi da sauri ya dawo da kallonsa kanta, kashe mashi ido ɗaya ta yi tare da sake hura mashi chewing gum ɗinta mai shegen kamshin nan akan face nasa tana sakin wani makirin murmushi, gaba ɗaya Abbi ya susuce ya birkice tare da rasa tunaninsa. Ita kuma Aunty mamaki take yi akan Ommu ta ci matsu da riga da wando, gani take yi ai Ommu ta yi girma ta sanya riga da wando, wannan sai yara irinsu Ayla, a tunanin Aunty fa kenan, amma kuma ga shi nan da idanunta ta ga yadda riga da wandon ya tafi da imanin mijinta, tana ganin yadda ya susuce lokaci guda har da wani zuba kamalan da bai san yana yi ba, GASKIYA DRESSING WA MIJI KANANAN KAYA DUNIYA NE, MACE DAI BATA TSUFA, IDAN TANA GYARA KANTA IRIN HAJIYA HADIZATU WATO OMMU TO LAFIYA LOU ZATA KARA DA KOMA WACE IRIYAR MACE CE!!. Miƙewa Abbi ya yi tare da niƙo hannunta yana faɗi "To muje ki nuna mani". Make kafaɗa ta yi kamar karamar yarinya, cikin yanga da kisisina ta ce "Ni aa kafin mu shiga daga ciki sai ka fara ɗaukata munje sayan sire, sai na ci sire tukun nan". "Haba Hadiza baga nama a gidan nan ba, kuma ga kanwarki Halima ta iya gasa nama sosai zata yi maki ai, yanzu dai ki zo mu tafi". Halima kuma Aunty ta maimaita a cikin zuciyarta tana tunanin wato ita ce ma zata yi masu tsiren dan cin mutuncin da cin fuska, ita kuwa Ommu abun nema ya samu sai ta sake kashe murya ta ce "Kuma fa hakane sahibina, ni da nake da kanwa ƴar albarka mai kaunata ai na manta ne, Halima ki gasa mani ya gasu sosai, kuma dan Allah ki cika mashi yaji sosai dan abin ya haɗu mani biyu ya ji ta sama ya ji ta kasa abin sai ya fi yi mani yadda nake so". (Waye ya gane bakar maganar da Ommu ta gayawa aunty a nan?) Tana kai karshen maganar bata tsaya ta jira amsar Auntyn ba ta wuce sama Abbi ya bi bayanta, wani irin dukukun bakin cikine ya tasowa aunty, da gudu ta miƙe ta yi sama. Tana zuwa ta faɗa ɗakinta tare da nufar gaban mirror tana kallon kanta dan ta ga dame Ommu ta fita. Tabbas babu abin da Ommu ta fita sai ma wadda ita ta fi Ommu, matsalar shine wayewarsu ita da Ommu daban daban, Ommu ta san duniya sosai da sosai, duk wani makirci ta iya shi sinka sinka, Aunty kuma ta kwankwaɗi hadda ta ƙoshi, banda jawo aya da hadisi ba wani abin da ta iya, da zarar ka taɓota zata faɗa maka suratul Maryam or Yusuf irin su Aaraf, an'am, sai kuma ta koma maka ɓangaren hadisai, Shikenan bata iya soyayya ba bare kula da miji bayan kiss da runguma sai girki, idan tana yi wa su Ayla nasiha kullun nasihar ɗaya ce shine kada su cewa miji a'a, komai ya ce matukar bai saɓawa Allah ba to kada suce a'a, kullun aikin kenan, shiyasa Ayla banda to ba wani abin da ta iya cewa daddyn Jelly, Allah ma yasa shima daddyn ba baya ba a fagen zuba love da shikenan Ayla ma tabi sahun Aunty. Tsab ta karewa kanta kallo, tafi Ommu hips, ga shi ita ma breast nata a tsaitsaye suke dan bata taɓa shayarwa ba, bugu da kari breast nata na ainahine Ommu kuma nata sai da akayi shaye shayen magunguna tare da wasu shafe shafe sannan suka ciko, nata breast ɗin ya fi na Ommu kyau da ɗaukar hankali, sannan ta fi Ommu kyau, kawai dai Ommu ta fi ta hasken fata ne, kuma shima kaɗan ne. Kuka ta sa tare da faɗawa saman gadonta tana tsinewa Ommu akan abin da ta yi mata na rikita mata miji da ta yi. A ɓangaren daddyn Jelly da babynsa kuwa, barcine mai daɗi ya kwashe babyn tasa saboda wahalar da kuma gajiyar dake a tattare da jikinta. Zuba mata idanun nan nasa ya yi yana ta kare mata kallo, wani irin azababben sha'awar tane yake taso mashi, ji yake yi kamar ya sake shigarta a yanzu, sai dai kuma yana tausaya mata, yana son ya barta koda na kwana ɗaya ne ta ɗan huta dan tasha bakar wahala, dan ma dai tana da tawakkali da haukuri ga kuma kaunar shi ne har yasa ta hakura haka, sannan kuma akwai yarinta sosai akanta shiyasa. Ya jima yana kallonta kafin ya sanya hannunsa ya kara jawota jikinsa sosai tare da lumshe idanunsa yana mai jim tsantsar kaunarta na ratsa ilahirin gangar jikinsa. A hankali ya fara shafa breast nata yana ɗan burza kan nipple ɗin tata a hankaki hankali, wani irin sauƙi na musamman yake ji tana ratsa shi, cikin natsuwa ya matso da bakinsa kusa da tata tare da capko lips nata ya fara tsotsa yana jan numfashi. A hankali ta fara motsawa alamar tana son tashi, cikin sauri ya kyaleta dan baya son ya tasheta daga barcin da take yi, sai ya hakura ya lumshe idanunsa yana ɗan shafa bayanta har shima barci ya ɗauke sa. Idan muka koma ɓangaren su Jelly kuwa wato gidan Abbo, Nawid dai wani sabon kula da tattalin so yake bawa Jelly, amma kuma ita ko kallo bai isheta ba, A ɓangaren Abbo kuwa sai shirya ta yadda zai ɗauketa ana gobe ɗaurin aure yake yi, yau saura kwana uku a ɗaura auren, komai ya kankama Ummi uwar biki uwar amarya kuma Uwar ango abin ba'a magana busy kamar network, duk wani tsumi dake karawa mace ni'ima sai da ta sanya hajiya Batula ta bawa Jelly, sannan kuma ga maganin karin girmar breast da aka haɗa mata da kuma fito da shape abin ba'a magana duk wanda ya kalli Jelly sai ya waiga ya kara kallonta breast ɗin nan nata sun cika kamar an hura balo balo, dama hips kam ba baya take ba akwai shi sosai, amma da aka kara fitar mata da shape ɗin ta sai ta kara wani mugun kyau abin ba'a cewa komai, ta zama wata ƴar cas caras da ita, mutanen Maiduguri sun fito da ita, Nawid fa duk ya bi ya susucewa da ruɗewa sosai, kullun cikin lafazata da kuma lallaɓata yake yi, amma duk na banza bata kula shi kuma bata zama inuwa ɗaya da shi, akwaita da riƙo a zuciyarta, tun da ta ruƙe ya ce baya sonta shikenan. Yauma dai kamar kullun misalin karfe 5 na yamma tana zaune ita kaɗai a ɗakin Ummi tana buga game a wayar Umm, yayin da ƴan biki keta faman hidima na jeka ka dawo, anata girke girke soye soye da sauransu. Tana kwance ta baje a saman bed na Ummi, sanye take da wani haɗaɗe doguwar riga launin sky blue ta yi kyau sosai, kanta ba ɗankwali gashin kan nan nata ya sha gyara sosai sai kyalli yake yi, kai idan ba ka yi wa Jelly farin sani sosai ba to bazaka taɓa gane cewa ita ɗin bace, saboda wani ruwan kyau da ta kara, komai ya ciko zamzam. Ta yi nisa cikin game da take yi, bata ji sallamar kowa ba bata ji motsi ba sai gani ta yi an kwace mata wayar tata, cikin sauri ta ɗago kanta dan ganin wanene. Yana tsaye sanye da suit baki ya ɗaura kayan aikinsa a jikinsa sai wani kayatatcen murmushi yake sakar mata. Wani mugun kallo ta bishi da shi tare da miƙewa zaune tana faɗin "Ka bani wayata yaya Nawid". Zama ya yi a gefen gadon yana ƙoƙarin riƙo hannunta, cikin sauri ta zuro kafafunta kasa tare da miƙawa ta nufi waje abinta ta kyale shi nan wurin zaune ruƙe da wuya a hannunsa yana binta da kallo yana haɗiyar yawu. Tana fita sai kuma ya ji ihunta, da sauri ya miƙe ya bi bayanta dan yaga menene. Kwance ya iskota a tsakiyar palo tana kuka dafe da cikinta, da sauri ya kariso wajen tare da tallabota yana faɗin me ya sameta bayan yanzu ta fito daga ɗakin Ummi lafiya. Hakan kuma ya yi daidai da shigowar Abbo cikin palon shima ya dawo daga wajen nasa aikin. Da sauri ya kariso cikin palon yana tambayar me yake faruwa ne, me ya sameta. Jin hayaniya yasa Ummi ta fito daga kitchen ta zo palon, itama tana ganin abin da yake faruwa ta yi maza ta kariso wajen tana ambatar me yake fatuwa ne? Me ya sami baby. Kuka take yi sosai hawaye bibbiyu, duk Nawid ya birkice sai faman dubata yake yi ko zai game me matsalar tata, shima Abbo ya ruɗe sosai, Ummi kam ba'a magana da yake ta fi su sonta, ita tun ainahi tsakani da Allah take sonta, amma daga Abbo har Nawid akwai dalilin da ya sanya suke son nata. Nawid yana ƙoƙarin ɗaukarta dan su shiga daga cikin ɗakinsa kada ƴan biki su taru masu a kai, bai kai ga ɗaga ta ba sai suka ga jini a jikin kayan ta, da yake kayan tata sky blue ne kalar mai haske hakan yasa jinin ya fito ɓaro ɓaro. Kallon Ummi Nawid ya yi kafin ya ce "Ummi girma ne ya zo mata fa, period ta fara yi, zan kaita ɗakina na dubata tare da yi mata allura In sha Allah nan da minti biyar zuwa goma zata ware ta koma daidai". Da ɗan karfi Abbo ya furta "Period kuma?!!". Ba ƙaramin mamaki jin yadda ya maimaita kalmar Ummi da Nawid suka yi ba, kamar ba lafiya ba. Jaddada mashi period Nawid ya yi, nan take wani zufa ya fara tsastsafo mashi daga gefe da gefen fuskarsa kamar ba lafiya ba, cikin lokaci ƙanƙani ya sauya ya fita hanyyacinsa, zuba mashi ido Ummi da Nawid suka yi suna kallon ikon Allah, daga jin sunan period ya canza haka, to anya kuwa lafiya? Tambayar da ko wannansu yake yi a cikin zuciyarsa kenan. Da dai Nawid ya ga matarsa tana ƙoƙarin sume masu a wajen sai ya fita batun Abbo ya saɓi kayarsa a kafaɗa suka wuce da ita cikin bedroom nasa, saman gado ya shimfiɗeta tare da ɗauko A box ya fara duba ta dan ta sami saukin wannan ciwon. A ɓangaren Ummi da Abbo kuwa, tambayarsa Ummi ta yi akan ko lafiya ya sauya daga jin baby ta fara period, ya kasa amsa mata tambayar tata sai ma wucewa da ya yi izuwa cikin ɗakinsa ya rufo kofa har da murza key, cike da mamaki Ummi ta wuce ta koma Kitchen dan ta cigaba da abin da take yi, abin da yasa kuma bata bi bayan Abbo ba saboda ƴan biki, bata son wata hayaniya ga jama'a cike a gidan, shiyasa kawai ta kyale Abbon ta wuce abinta, amma ta kuduri niyar bayan biki sai ta ji dalilin daya sanya ya shiga damuwa dagajin baby ta fara period. Shi kuwa Abbo yana faɗawa ɗakinsa ya fara safa da marwa yana zarya tare da tunanin ta yadda zai ɓullowa wannan lamari, a fili kasa kasa ya fara magana shi kaɗai kamar zautatce "No banso kiyi mani haka ba wannan yarinya, bamso yin amfani dake a cikin gidan nan ba, na fi son sai na mayar dake gidana na Abuja idan yaso ki fara jinin a can ta yadda zan biya buƙata ta hankalina a kwance, amma kin zo kin fara jini a nan wadda ya zamar mani dole yau na aiwatar da kuɗirina a kanki idan ba haka ba ina cikin bala'i, ga shi gidan nan cike yake da jama'a ban kuma isa in tsallake yau ba tun da jinin ranar farko muke buƙata, gaskiya baki yi mani adalci ba amma ba komai zaki ɗanɗani kuɗarki wlh, sai kin zama dake da gawa duk ɗaya ne, banbancin kawai dai ke zaki kasance kina numfashi ne, ita kuma gawa bata numfashin bacin haka ba wani banbanci, wlh sai kin yi danasanin zuwarki duniya". Sai sambatu yake yi shi kaɗai da alama ya fara zaucewa ya fara fita hanyyacinsa. A ɓangaren Rimsha kuwa data ga ji da zama sai ta koma cikin gida ta fara dube dube a cikin kitchen ɗin ko Allah zai sanya ta sami wani abin da zata iya ci kada yunwa ya hallakata. Ta yi rashin sa'a domin kuwa babu komai a cikin kitchen ɗin wadda ya yi daidai dana kasarmu idan ba nama da kwai ba sai dankali, bata daddara ba domin bata da wani zaɓi tana jin yunwa, haka ta sake ɗibar nama ta dafa tare da soyawa, a wannan karon ta yi sa'a Mark bai zubar mata da abincin ba domin iya nama ne kawai bai yi masu wari ba. Bayan ta gama ta zuba a plate ta ɗauka ta wuce ɗakinta. Saman bedside drawer ta ajiye plate ɗin tare da fitowa dan ta ɗauki lemon ko ruwa da zata haɗa da shi. Har zata sauƙa palon kasa sai kuma ta ɗan hango cikin ɗakin Lion domin kofar a buɗe, a hankali ta lallaɓa izuwa bakin kofar ɗakin, kamar wata ɓaraubiya haka ta leƙa cikin ɗakin, ganin ba kowa ne yasa ta shige ciki, dama kuma tasan basu nan kawai dai dan tabbatar da tsarone yasa ta fara leƙawa. Tana shiga ta fata kalle kalle, ko'ina tsab kamar ba'a taɓa amfani da komai na ɗakin ba saboda gyara, sai tashin kamshi yake yi, tsalle ta buga tare da direwa a saman katafaren bed nasa tana dariya kamar zautaciya, da ɗan karfi ta furta "Yau ni ce GAR na gidan nan dole kowa ya bani respect" ta kai karshen maganar tare da kwashewa da dariya ta mirgina ta kara muginowa, yarinta ta ji gado mai daɗi har wani lumshe idanu take yi alamar barci take ji. Ta jima kwance a gadon nasa tana surutai kafin ta miƙe ta gyara mashi gadon tsab kamar yadda ta samu sannan ta wuce dressing nasa, nan ma ta yi iya taɓe taɓen abin da take so kafin ta fito izuwa wajen mirror sa. Duk wasu drawers dake a ɗakin sai da ta buɗe su ta leƙa me a ciki, a wajen drawers na mirror ne ta ga wani pistol gun, tsabar rashin ji irin tata sai da ta ɗauki gun ɗin nan ta gani sannan ta maida, tana ƙoƙarin rufe drawer kuma idanunta suka sauƙa akan wannan ɗan akwatin na mum ɗin su wato Josephine, hannu tasa ta ɗauko akwatin ta fitar tare da fara ƙoƙarin buɗewa, sai dai ina ta kasa domin Lion ya sanyawa akwatin matakan tsaro sosai. Ba dan ta so ba ta mayar da akwatin ta ajiye sannan ta cigaba da taɓa mashi abubuwansa, bata taɓa tunanin ko zai gane ba, ita dai duk abin da ya yi mata kyau sai ta taɓa shi. Harta kayan sawarsa sai da ta taɓa, takalmarsa, watch's nasa komai dake a cikin ɗakin sai da ta bi ta taɓa sannan ta shiga toilet, nan fa taga duniya, dan toilet basa duniya ne guda, irin su shower gel da yake amfani da su ma kawai abin kallone, mayukan wanke gashin nan nasa duniya ne guda, yana kaunar gashin nan nasa sosai hakan yasa yake kashe mashi makudan kuɗaɗe dan gyaranta. Duk wasu gel da suka burgeta da mayukan goge baki masu kamshi da tsada sai da ta taɓa, wani irin kwalbar turaren baki ta gani mai siffar sojoji ya ɗaga hannu irin jaruman sojijin nan, haka akayi design na kwalbar, ɗaga kwalbar ta yi tare da ɗaga hannunta kamar yadda aka kera kwalbar sannan ta ce "Kai nima fa soja ce jaruma mai jini a jika kuma kakkarfa" ta kwashe da dariya tare da mayar da kwalbar ta ajiye sannan ta fito waje Bayan ta gama duk taɓa mashi abin da zata taɓa ne ta buɗe fridge nasa dake a cikin ɗakin kuma ta ɗauka mashi abin shansa guda ɗaya ta koma bedroom nata. (Shin kuna ganin duk da ta gyara komai Lion ba zai gane an shigo ɗakin ba kuwa? MY MUM KIN KI JAWA ƳAR NAN TAKI KUNNE KO? TO GA SHI DAI YAU TANA GAƁA KUNA RUWA SAI KU KAWO ƊAUKI IDAN DA RABO KU RAGE DA RAI IDAN KUMA BABU ALLAH YA JIƘAN RAI😭. Amsa na gare ku ni dai na koma gidan Abbo.) Misalin karfe 12 na dare abin mamaki gaba ɗaya ƴan bikin nan sun yi barci mai nauyi kamar waƴen da aka zubawa maganin barci, harta Nawid da Ummi sun yi barci mai nauyi, a takaice dai babu wata halitta mai rai a cikin gidan wadda bata yi barci mai nauyi ba sai Abbo, harta Jelly ta yi barci mai nauyin gaske. Fitowa Abbo ya yi daga ɗakinsa jikinsa na sanye da wasu kaya kamar na matsafa launin ja kalar wuta, abin mamaki shine kansa da dogon gashi har kafaɗa sannan kwayar idanunsa sun sauya launi izuwa dark purple kamar ba shi ba, hannunsa na ruƙe da wani ɗan karamin kwarya bakinkirin kamar zunubi. Kai tsaye ɗakin jelly ya nufa yana taku cike da isa da izza kai daga gani kasan akwai abin da ya yi wa ƴan gidan shiyasa yake tafiya haka dan yasan ba za su tashi daga barci ba. Yana shiga ya tura kofar tare da wuce wa ya haye saman bed ɗin jelly dake kwance kamar gawa saboda barci, wata zabgegiyar wuƙa ya zaro daga ta cikinsa, wuƙace mai kaifi sai kyalli take yi kamar madubi, a gefe ya ajiye wuƙar tare da kwaryar tasa sannan ya cire mata kayan jikinta tas ya mata tsirara haihuwar uwarta, sannan ya buɗe mata kafafunta da kyau kamar yadda ake yi wa maza kaciya............. Ya ilahi ya lillihi😭😌 sai dai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu 💖💖TRIPLETS💖💖 E79-80💖 Yana shiga ya tura kofar tare da wuce wa ya haye saman bed ɗin jelly dake kwance kamar gawa saboda barci, wata zabgegiyar wuƙa ya zaro daga ta cikinsa, wuƙace mai kaifi sai kyalli take yi kamar madubi, a gefe ya ajiye wuƙar tare da kwaryar tasa sannan ya cire mata kayan jikinta tas ya mata tsirara haihuwar uwarta. Bayan ya gama sai ya buɗe mata kafafunta da kyau kamar yadda ake yi wa maza kaciya, ɗaukar wannan zabgegiyar wuƙar ya yi yana ƙoƙarin tura mata a tsakiya gabanta dan wuƙar gabaɗaya ta shafi jinin period da take yi. Bai kai ga sa mata wuƙar ba kamar daga sama ya ji an buɗe kofar ɗakin, a razane ya ɗago kansa tare da kai kallonsa izuwa bakin kofar ɗakin, Nawid ne ya turo kofar daga shi sai shot da singlet a jikinsa, mamaki ne ya kama Abbo ya akayi Nawid bai yi barci ba, duk irin tsafe ƴan gidan da ya yi akan ba za su farka ba sai gobe da safe. Ni kuwa nace ai ka makaro domin Nawid dai abokin Imran ne, duk kuma wanda zai zauna da Imran da Akil to ko baya so dole zai koyi yawai ta yin askar da zama da alwala, to dan haka babu wata sharri data isa ta taɓa su. Abin da ya fito da Nawid kuwa bakar yunwa ce ta tashe shi mai matukar nukurkusan cikin, ya zo zai wuce ɗakin jelly ya shiga wajen Ummi dan ya tashe ta ta bashi wani abin da zai ci dan baya son abincin da ƴan biki suka dafa, to zai wuce ne ya jiyo kamar motsi a ɗakin Jellyn shine ya ce bari ya duba ko dai ita ce idanunta biyu tana zuba rigimar da ta saba, har ma ya tsara yadda idan ya sameta idanunta biyu zasu zauna su sha hira har asuba, ya samu ya lallaɓata har ta hakura ta amshi soyayyarsa. Ba ƙaramin razana ya yi da ganin Abbo a ɗakin ba, dan ma dai shi a ainahin suffar Abbon yake kallon shi, ba a irin wannan suffa ta su ta matsa fa. Murya na rawa ya ce "Abbo me ya kawo ka ɗakin baby kuma?". Rai a matuƙar ɓace Abbo ya diro kasa daga saman gadon, Nawid yana yi mashi kallon sanye da jallabiya a jikinsa, ni da ku kuma masu karatu mun san a ainahin suffar da yake a yanzu wato dai wannan shiga ta matsawa. "Fita a ɗakin nan Nawid!!" Ya faɗa da tsawa tare da nunawa Nawid ɗin hanyar fita, abin mamaki sai ya ga Nawid yana tsaye bai ta fi ba, abin ya ɗaure mashi kai domin a iya saninsa ya san cewa babu wanda ya isa ya yi mashi musu idan yana wannan suffa ta natsafa, sai ga shi Nawid dai tsafin bata yi aiki a kansa ba, kuma hakan ta samo asaline daga askar na safiya da maraice da yake yi wadda Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya bamu akan idan mun karanta shi da bayan sallar la'asar to har izuwa sallar asuba washegari kenan Allah zai turo malaika ya kula damu tare da tsaremu babu wata sharri da zata samemu a wannan bayan la'asar ɗin zuwa asuba, bugu da karin annabi ya ce duk wanda ya karanta wannan addua kuma ya rasu kafin asuba to Ubangiji da kansa ya yi ma wannan bawa albishir da gidan aljanna, haka idan ka karanta shi daga asuba zuwa la'asar Allah zai tsareka babu wani abin sharri da zai same ka, kun dai ga Nawid da yamma ya yi askar nasa, da daddare babu abin da ya yi amma Allah ya tsare sa, ga kuma karin ni'ima idan ka rasu bayan karanta wannan askar ɗin Ubangiji da kansa ya yi maka alkawarin gidan aljanna, Allah kasa muna ciki Amin ya Allah, ASKAR ƊIN YANA DA YAWA KUMA AKWAI TSAWO IN SHA ALLAH ZAN SAKA MAKU SU A ƘARSHEN PAGE NAN, KU LIZIMCI YINSU DOMIN SAMUN UBANGIJIN RAHMA YA KARE MU, SAFIYA DA MARAICE, ALLAH YA BAKU DACEWA. Tsawa Abbo ya sake daga mashi, amma ina Nawid ko kaɗan bai ji tsoro ba tamkar ma ba da shi Abbo yake yi ba, abin ya ɗaure wa Abbo kai sosai. Wucewa Nawid ɗin ya yi ya nufi gadon, hawaye ne yake zuba a idanunsa sosai da sosai wani na bin wani, wannan abin takaici har ina, zuciyarsa wani irin tafasa take yi mashi, abin kunya yau ya kama Mahaifinsa da hannunsa yana ƙoƙarin ketawa matar da zai aura haddinta, wannan abin babbar bala'i ce ga Nawid. Kayan ta ya ɗauka ya maida mata jikinta da Allah yasa ma green light ne a cikin ɗakin ba white light ba, hakan kuma yasa baka iya ganin mutun sosai. Idan baku manta ba Jelly bata kwana a ɗakin da babu wuta, hakan yasa Ummi ta sanya aka saka mata green light a ɗakin yadda dai zata samu ganin ɗan haske, Ummi bata son barinta da white light a cikin ɗakin domin annabi ya hane mu da yin hakan, ba kyau kwana da wuta a kunne a ɗaki. Tsab ya mai da mata da kayan ta tare da sanya mata pant nata mai ɗauke da always a jiki. Bayan ya kammala ne ya sauƙo kasa tare da ɗaukarta a saman kafaɗarsa ya nufo hanyar fita, Abbo yana tsaye yana kare mashi kallo sannan kuma yana mamakin ya akayi Nawid ya bijirewa umarninsa duk da a tsaface ya bashi umarnin, abin ba ƙaramin tayar mashi da hankali ya yi ba. Daidai Nawid zai wuce da ita ne kuma Abbon ya tare shi yana faɗin "Nawid ka ajiye yarinyar nan ka fita a ɗakin nan ko kuma in kashe ka!!". Ko kallon in da yake Nawid bai yi ba tsabar takaici da bakin ciki, zuciyarsa wani irin azababben raɗaɗin zafi take yi mashi, kai tsaye ya sa kai ya nufi waje abinsa. Damƙo wuyar singlet ɗinsa ta baya Abbo ya yi tare da daka mashi wani razanannen tsawa sannan ya fito da wuƙar tasa yadda Nawid ɗin zai iya gani ɓaro ɓaro ya ce mashi ko ya sauƙe jelly ya fita a ɗakin ko kuma yanzun nan ya kashe shi. Rai a matukar ɓace ya ce "Abbo ka kashe ni sai ya fi mani sanyi akan na barka ka lalatawa yarinyar mutane rayuwarta, Abbo why? Why zaka yi mana haka? Me muka yi maka? Wannan wace iriyar bakar bala'in rayuwace, Abbo ka cucemu, Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun". Furta Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun da Nawid ya yi ya sanya Abbo sakinsa ba shiri dan kada ya ƙone, cikin sauri Nawid ya fita waje ɗauke da ita a saman kafaɗarsa. A zafafe Abbo ya bi bayansu akan lallai sai ya hanasu tafiya. Da dai Nawid ya ga da gaske Abbo yake yi hana su tafiya zai yi, sai ya wuce da Jelly waje, kai tsaye cikin motar sa ya kwantar da ita a gidan baya, sannan ya fara ƙoƙarin tare Abbo akan ya rabu da su. Kusan kokawa suka yi kafin Allah ya bawa Nawid Sa'a ya tura Abbon a cikin ɗakinsa ya rufo kofar ɗakin tare da murza key ta baya. Bubbuga kofar da karfi Abbo ya fara yi yana ƙoƙarin karya kofar, bai damu ba dan yasan dukka ƴan gidan ba zasu tashi ba sai da safe, hakan yasa ma yake ta faman buga kofar da karfi karfi. Nawid kuwa cikin sauri ya faɗa ɗakin Ummi, sai barci take zubawa abinta, key ɗin motarta ya ɗauka tare da wayar ta ya fito waje, da yake ya rufe Abbo a ɗakinsa ba halin na ɗauki nasa key ɗin motar Shiyasa ya ɗauko na Ummi kawai. Yana zuwa ya ɗauki jelly izuwa cikin motar Ummi tare da nufar bakin gate ya buɗe gate ɗin da kansa yayin da shi kuma Abbo yake ƙokarin karya kofar ɗakin ya fito, shima mai gadin gidan yana ta shan barci har da shi Abbo ya tsafe. Da gudun gaske Nawid ya figi motar suka bar gidan ya kuma bar masu gate a buɗe. Kai tsaye gidansu Imran ya nufa domin bashi da biyun Imran a duniyar nan bayan iyayensa. Sai gudu yake shararawa yayin da ita kuma Jelly take ta sharara barcinta abinta bata ma san me yake gudana ba. Yana zuwa kofar gidansu Imran ya tsayar da motar tare da fito da wayar Ummi ya fara kiran layin Imran ɗin da yake ya haddace number. A lokacin da kiran ta shigo wayar Imran yana kwance saman gadon Lion suna hira shi ko in ce yana yi wa Lion hira yayin da shi kuma Lion yake ta fama da aiki a kan bincin case ɗin Jellyn a laptop nasa, domin kuwa Tyrone ya turo masu akan cewa tabbas Jelly tana Kaduna kusa da su a unguwa kaza gida mai kala kaza, Lion kuma yana kara dubawa ne dan ya tabbatar da hakan ne ita ɗin ce, a daidai lokacin yana bincike a gidan su Nawid ɗin kenan, kuma kusan duk abin da ya faru a gidan ya gani sakamakon wani camera da yake a palon su Abbon, bai kalli abin da ya faru tsakanin Abbo da jelly a ɗaki ba, amma dai ya kalli faɗar Abbo da Nawid ɗin dukka wadda suka yi a Palon, dan a iya palon ne akwai camera, so sun datsi cameran gidan ne, amma kuma da Nawid ya fito da wayar Ummi Lion ɗin ya bibiyi cameran wayar domin yanzu ba technology da ta fi sauƙi kamar ta datsar camerori da kuma wayoyin mutane dan aga halin da suke a ciki, shi kuma Imran yana kwance a gefensa yana jiran ya gama bincike ya gaya mashi in da Jellynsa take ya je ya ɗaukota. Bari mu koma baya kaɗan kafin mu cigaba, lokacin da Lion da Imran suka dawo gidan karfe uku ne na rana, tun a Palon kasa suka rabu da Imran, Lion ya haura sama shi kuma Imran ya wuce wajen Areef, bayan ya duba shi sai ya wuce wajen Rimsha dake ta famar aikin barci, yau ta ci nama har ta shiga uku, ba komai a gidan na ci da ya wuce nama. Lion kuwa yana sako kafarsa a cikin bedroom nasa ya gane cewa tabbas an shiga cikin ɗakin, ta yadda akayi ya gane kuwa shine, wani kamshi ya ji saɓanin nasa kamshin, bacin haka kuma yana sako kai a cikin ɗakin dara daran idanunsa suka sauƙa a saman drawer mirror dake rabi a buɗe bai gama rufuwa ba. Perfume na Lion tana da karfin bala'i wadda zata iya rinjayar ko wace iriyar kamshi, amma kuma duk wannan karfin tata Lion yana iya tsame wata kamshin da ta gifta ta cikin tasa, hakan yasa ya tsame kamshin perfume ɗin Rimsha. Shiru ya ɗan yi yana tunanin kamshin waye? Ya san tabbas bana Imran bane, ba kuma na Areef bane, kuma ma yasan Areef ba zai zo mashi ɗaki ba duk da cewa yanzu yana iya takawa kaɗan kaɗan amma dai ba zai iya haurawa saman benen nan ya zo ɗakinsa ba, kuma wannan kamshin bana perfume ɗin su Mark bane. Lumshe dara daran idanunsa ya yi yana tunanin wani mai karan kwanan ne ya shigo mashi ɗaki, shida ko sojojinsa bai yarda su shigo mashi bedroom ba idan ba ƴan uwansa ba, Imran shine bare ba ɗaya daga cikin Triplets nasa ba wadda yake shiga mashi ɗaki, bayan Imran babu wani ɗan adam dake shiga bedroom nan, dan Lion ba shi da yadda da mutun ko kaɗan, in ma mace ko ba miji. Cikin natsuwa ya karisa cikin ɗakin, abun ku da babban soja yadda kasan a gabansa Rimsha ta yi duk abun da ta yi a ɗakin nan, duk wani abin da ta yi haka yake Imagine a cikin ƙwaƙwalwarsa, duk abin da ta taɓa kwanciya da ta yi a saman bed nasa, bayan ta tashi duk wasu abubuwa da ta taɓa mashi haka yake kallonta gata nan tana yi, ɗan ciza laɓɓansa na kasa ya yi kafin nan ya zauna a saman bed ɗin nasa tare da yi wa Imran massage akan ya kawo mashi kanwar nan tasa nan yanzu. TOH FA BABBAR MAGANA. Ai kuwa Imran ba dan ya so ba ya tasheta daga barci, jin ance Lion na kiranta ne yasa ta fara karanta duk wata addu'a da ta zo mata a bakinta, ba ƙaramin tashin hankali ta shiga ba. Sauƙowa kasa daga saman gadon ta yi jikinta sai kerma yake yi da haka ta ɗauki hijabi har kasa ta zumbula ta bi bayan Imran tana ta jero addua'o'i a ranta dan ta san abin da ya aikata Mashi. Suna shiga cikin ɗakin tun basu kariso ba Lion ya dakatar da su tare da faɗin "Ka miƙa wa Mark ita". Kallon shi da kyau Imran ya yi yana zaro ido kafin ya dawo da kallonsa kan Rimshar wadda take tsaye bata ma gane nufin Lion ɗin ba. "Rimsha me kika aikata bayan bamu nan?" Cewar Imran, "Prof" Lion ya ambaci sunansa can kasa kasa da wannan sanyayyar muryar tasa yayin kuma da yake rubuta saƙo a wayarsa, Imran ya gane nufinsa wato su fita mashi a ɗaki baya son wata magana. Salati Imran yasa tare da riƙo hannunta suka fito waje, suna fita a tsakiyar palon ya tsaya ya fara tambayarta me ta aikata. Cikin rawar murya ta fara gaya mashi komai na abin da ta yi, bata ɓoye mashi komai ba.... Ai kuwa bai bari ta karisa gaya mashi maganar ba ya tsinketa da wani wawan mari, ji kake tas. Cikin sauri ta dafe kuncinta, rai a matukar ɓace ya fara magana "Me yasa bakya jin magana? Me yasa duk abin da na gaya maki baki amfani da shi? Yanzu kin san me nufin Saif kuwa? To cewa ya yi na miƙaki wajen tsinannen kafurin sojan nan wadda hukuncinsa gara mutuwa, kin san waye Saif kuwa? Da zaki shiga ɗakinsa ki yi mashi wannan shirmen kuma ki yi tunanin ba zai gane ba? Hankalinki ɗaya kuwa? To wlh bari ki ji abin da baki sani ba, Saif baya magana kuma ya sauya, idan kikaga yau baki karɓi hukunci daga hannun wancan kafurinba to wlh sai dai idan mutuwa Saif ya yi dan ina mai tabbatar maki idan duniyar nan dukka gatanki ne basu isa su tankwara Saif kuma ya tankwaru ba, baki taɓa ɓata mani rai irin na yau ba Rimsha, so kike yi zuciyata ta buga na mutu ki huta ko? Da wanne zan ji fisabillilahi? Naji da ɓatar Jelly ce ko kuma na ji da wannan bala'in da kika jefa kan ki a ciki?" Zubewa kasa ta yi akan gwiwowinta tare da sakin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, tana kuka tana bashi hakuri. Bashi da zaɓi dole ya hakura ya duƙa ya rungumota tare da fara rarrashinta yana bata baki. Duk abin da suke yi Lion yana jinsu domin a palon sama suke, kuma a kusa da bakin kofar ɗakin nasa suke, sai dai ko kaɗan bai ji cewa zai iya sauya magana ya dakatar da Mark daga bata hukunci ba, dole ta karɓi hukunci, dan ma ta yi sa'a shima yana cikin yanayi mara daɗi ne ga abubuwa sun sha mashi kai da shi zai bata horon da sai ta gwammaci muguwa, gobe ko da kuɗi aka bata ba zata yi gigin tinkarar ɗakinsa ba. Haka Imran ya ja hannunta zuwa Palon kasa, ya san cewa Lion ya tsani kalmar sorry, akan cewa sorry ma zai iya harbe Rimshar kowa ma ya huta, shiyasa Imran ɗin bai yi gigin yunkurin ce mashi ya yi hakuri ba, kuma yasan ko ma ya faɗa ɓata bakinsa zai yi dan dai Lion ba zai canza magana ba, hakan yasa kawai ya hakura ya miƙawa Mark ita. Already dama Mark ya sami massage ɗin Lion akan ya bata horon tsallen kwaɗo mai kyau, ta ɗauki good 3 hours tana tsallen kwaɗo tana kewaye gidan duk girmansa kuwa, kada ya kyaleta har sai ta kasa tafiya da kafafunta. Ai kuwa haka Mark ya sanyata yin tsallen kwaɗo, Imran ya kasa jurewa sai ya koma cikin gida ya nufi ɗakin Areef yana matsa mata kwalla, Mark kuwa da yake ya saba bawa katti ma horo bare ita, sai ya zama ko a jikinsa, sai ma kara nishaɗi da yake idan yana basu horo. Ko minti 20 Rimsha bata yi tana wannan frog jump ɗin ba ta faɗi kasa, ciro belt Mark ya yi akan zai zaneta, ga belt ɗin nasu nan ba sai na gaya maku ba, shegen azabar zafi ke gare shi kamar me. Yana ƙoƙarin zaneta sai yaga fa bata numfashin, duƙawa ya yi a gabanta tare da sanya hannunsa a bakin kofofin hancin ta, ai kuwa bata numfashin, guntun tsaki ya ja tare da miƙewa ya nufi cikin gida. Jim kaɗan ya fito da ruwar roba a hannunsa ya zo ya zuba mata, a razane ta farfaɗo tana sambatu, tsawa ya daka mata tare da bata umarni akan ta cigaba da yin tsallen kwaɗon. Haka tana kuka ta cigaba da yi, duk kafafunta sun kunbura. Imran kuwa yana shiga ɗakin Areef ya gaya mashi abin da yake faruwa, rai a ɓace Areef ya ce "Prof dafa mani bari na tashi ka gani, me za'a hukunta a jikin yarinyar nan fisabillilahi, muje wajen Mark ɗin dan kaniyarsa". A tsorace Imran ya ce "No Areef bana son ku sami matsala da Saif akan Rimsha, pls ka yi hakuri kawai mu jire". ƴar tsawa ya dakawa Imran ɗin da ɗan karfi "Prof kana da hankali kuwa?! Kasan me kake faɗe kuwa? Mu kyaleta fa kace? Kasan waye Mark kuwa? To ina son ka sani Lion yanzu haka ma ya mance da ita, shi haka yake idan ya ce a bawa mutane horo to rufe babinsu yake yi domin yasan sojojin sa zasu hora wadda ya ce a bawa horon da kyau, ba za su ɗaga mashi kafa ba, dan haka kada ka damu muje na karɓeta a hannun Mark ɗin Lion ba zai gane ba". To Imran ya amsa da shi sannan ya dafa mashi ya miƙe da kyar. A hankali Areef yake taka kafar tasa tare da dafa kafaɗar Imran ɗin, yana jin zafi sosai bawan Allah amma haka ya daure, abun ku da babban jami'in, idan da wani ne ya ji raunukan da Areef ya ji to da sai ya fi wata uku baya iya motsawa sai dai a kwantar a tayar, amma da yake shi ya sami horo mai kyau jarumin sadaukin namiji ne sai yake daurewa yana takawa, ko da zafin haka yake jurewa. Sun jima suna tafiya kafin su fita palon, a kalla za su ɗauki 7 mins kafin su fito waje saboda a hankali Areef yake tafiya. Yana fita ya ɗaure fuska sosai cike da bada umarni da izza ya ce wa Mark ɗin ina Rimsha. Cikin girmamawa Mark ya nuna mashi akan tana ta baya wajen garden ta zaga da frog jump zata zago. Wucewa Areef ya yi yana cigaba da ɗingisa ƙafarsa har ya isa wajen, da hannu ya yi mata alama akan ta tashi ta zo, kasa tashi ta yi saboda kafarta sun kumbura suntum sun yi ja, tana ma zaune ne a wajen dan ta kasa cigaba da yi, shine ta zauna tana jiran Mark ɗin idan ya ji ta shiru sai ya zo ya kasheta kawai dan ta ga ji ba zata iya ba. Areef yana ƙoƙarin yi mata magana idanunsa suka sauƙa akan ƴan kwacen waya dake kwance plat suna kallon rana, bayin Allah kullun cikin horarwar Mark suke. Da mamaki Areef ya tambayi waɗan nan fa, nan fa Imran ya gaya mashi su waye ne, shima kuma Imran ɗin ya sha mamaki domin bai taɓa tunanin cewa har yanzu suna gidan ba, abin da basu sani ba shine Lion ma kwata kwata ya mance da batunsu a gidan, shiyasa bai sallamesu ba, tun da ya miƙa su hannun Mark ya mance da su. Umarni Areef ya yi masu akan su tashi su tafi, da Imran ya tambaye shi akan me zai ce su tafi bayan kuma Lion ne ya basu wannan aiki, nan ma dai sake jaddada mashi Areef ya yi akan cewa yana da tabbacin Lion ya rufe babinsu ya mance da su, idan za'a shekara ana ajiyesu a gidan to in dai ba wata rana Allah ya kaddara suka yi ido biyu da Lion ɗin ba ya ce a sallamesu to har su mutu suna nan. Jinjina kai Imran ya yi yana mamaki shi dai yasan tabbas ba wata mantawa da Lion ya yi da su, dan yasan halinsa sarai, amma da yake ɗan uwansa ne ya faɗin hakan sai ya ja bakinsa ya yi shiru kawai. "Prof sake ni ka kira mani Mark" cewar Areef. "Zaka iya tsayuwa kuwa Areef?" Jinjina mashi kai ya yi alamar e zai iya, to Imran ya amsa mashi da shi sannan ya wuce ya nufi wajen Mark ɗin. Zuba mata idanu Areef ya yi yana kallon yadda take ruwan hawaye Baiwar Allah, abin ba ƙaramin konawa Areef rai ya yi ba. Suna a haka har Mark da Imran suka dawo wajen. Gaban Areef Mark ya tsaya cikin girmamawa ya ce ga shi nan. Ɗan kame jiminsa Areef ya yi ya tsaya da kyau tare da dagewa ya ɗauke Mark ɗin da wani bahaguwar mari domin shi dai Areef bahagone, da left hand yake aiki. Har wani jiri Mark ya gani na lokacin guda, ji ya yi tamkar Lion ne ya mareshi, ya ji hannun maza, cikin ƙanƙanin lokaci idanunsa suka yi jawur kamar jini. Rai a ɓace Areef ya ce da Mark ɗin maza ya ɗauki Rimsha ya kai mashi ita ɗakinta, cikin girmamawa ya amsa da to sannan ya wuce ya nufeta, dan yasan ba'a yi wa TRIPLETS gardama, idan Areef ya yi magana to tamkar Lion ne ya yi, a haka Lion ya gina gaba ɗaya sojojinsa akan lallai su rinƙa jin maganar TRIPLETS nasa tamkar yadda za su ji nasa maganar. Girgiza kai ta fara yi alamar bata son Mark ya taɓa ta, ganin haka yasa Areef ya dakatar Mark ɗin daga ɗaukar tata, kallon Imran ya yi yana jiran karin bayani akan me yasa Rimsha bata son Mark ya ɗauke ta, nan fa Imran ya gaya mashi addini ya yi hani da hakan kuma mu a al'adar mu ma ba'a yarda da hakan ba. Jinjina kai Areef ya yi yana mai kara yabawa Nigeria, koba komai Nigerians suna tsare mutuncinsu, addini, da kuma al'ada, duk da suna aikata laifuka amma mafi yawanci a ɓoye suke yi, ba su fitowa ɓaro ɓaro su yi abu tsaɓanin kasashen turawa. "Prof ka ɗauketa to ka kaita ɗaki sai ka zo ka dafa mani in koma ciki na gaji, kuma kaga yau za'ayi mani aiki Drs sun kusa diro Naija, bai kamata na jijjiga jinin jikina sosai ba". To Imran ya amsa da shi kafin ya nufeta, sosai take kuka bai tsaya rarrashinta ba saboda yana tausayin Areef sosai, yasan cewa ya ga ji da tsayuwa ga alama nan har haɗa zufa yake yi. Imran yana ɗaukar Rimsha suka bar wajen shi kuma Areef ya umarni Mark daya ɗauki waƴan nan ƴan kwacen wayar ya fitar da su zuwa waje ya sasu a abin hawa a kai su gida. Shima dai Mark ɗin to ya amsa da shi kafin ya wuce ya fara aiwatar da umarnin na Areef. Saman bed nata Imran ya kwantar da ita sannan ya dawo ya tallafawa Areef suka koma cikin ɗaki. Bayan sun koma ne Areef ya ce ya je ya rarrashin masa matar ɗan uwansa ya bata hakuri komai ya wuce wata rana In Sha Allah zata zama ita ce mai controlling na zuciyar Lion ɗin baki ɗaya, zata zama sai abin da take so, for now dai ta yi hakuri duk da bai san laifin da ta yi da ta cancanci wannan hukunci daga wajen Lion ɗin ba. Imran na ƙoƙarin gaya mashi laifin da ta yi, ya dakatar da shi ya ce baya buƙatar ji, shi dai kawai ya je ya rarrasheta ta yi shiru ta yi hakuri. To Iman ya amsa mashi da shi tare da yi mashi godiya suka yi sallama. Yana shiga ɗakin nata ya iskota har ta yi barcin wahala, ruwan zafi ya ɗebo a toilet tare da ɗauko ɗan ƙaramin towel ya zo ya fara gaza mata kafafun nata. Jin ana taɓa ta yasa ta farka, cool murmushi Imran ya sakar mata tare da faɗin Sorry sister, ita ma murmushi ta ƙaƙalo tana kara bashi hakuri, ba komai ya ce mata sannan ya cigaba da gasa mata kafafun nata har sai da suka ɗan rage mata zogin da suke yi mata. Bayan ya kammala ne ya kara yi mata faɗa sosai tare da ja mata kunne akan ta kiyaye Lion, alkawari ta yi mashi akan zata kiyaye daga haka suka yi sallama ya wuce bedroom nasa dan ya je ya yi wanka. Misalin karfe 6 na yamma Drs suka iso, kuma a wannan yamman suka fara aikinsu dan Lion ba shi da wata buƙata da ta wuce ɗan uwansa ya tashi, yana son Areef ya tashi dan su yi aiki a tare, yana son mayar da Areef soja tun da ya cire shi a C.I.A kuma Areef ya sami horo na bugawa ajarida wadda zai iya bugawa da manya manyan sojiji na kasa da kasa, kuma yana da ƙwaƙwalwa ta Family'n William jacop. Misalin karfe 8:30 bayan sun yi sallar isha Imran ya sawo masu abin ci shi da Rimsha suka ci suka ƙoshi sannan suka yi sallama akan sai da safe, yanzu kafafun nata sun ɗan saki amma ba dukka ba dan har yanzu bata iya takasu kuma hakan ya ja mata zazzaɓi har sai da Imran ɗin ya saya mata magani. Bayan sunyi sallama ne ta shiga toilet ta yi wanka tare da yin shirin barci ta kwanta, shi ma Imran ya wuce ya je ya yi wanka ya yi shirin barci sannan ya wuce izuwa ɗakin Lion, daidai lokacin shima Lion ya yi wanka ya shirya karfe tara da rabi a lokaci. Hayewa saman bed Imran ya yi yana karewa Lion kallo, ba ƙaramin kyau kayan barcin suka yi mashi ba, launin ash color mai haske ne, shi dai yana son abu mai haske sosai, haka kamshi ma ba sai na kara gaya maku ba, mayen son kamshi ne na bugawa a zarida. Zama ya yi a gefen bed ɗin tare da jawo laptop nasa sannan ya gayawa Imran an turo mashi in da Jelly take amma yanzu zai bincika ya tabbbatar da gaske ita ɗin ce domin ba wani ganin ƙoƙarin su Tyrone yake yi ba a fagen iya bincike, kawai ma dan abubuwa sun sha kansa sosai ne yasa ya ce Tyrone ya yi aikin. TOM KUN JI ABIN DA YA FARU A GIDAN LION BAYAN DAWOWARSU, YANZU MU KOMA CIKIN LABARI. Jin ringing na wayarsa ya sa Imran ya ɗan miƙe daga kishingiɗar da ya yi yana ƙoƙarin ɗauko wayar a in da ya ɗaurata saman bedside drawer, shi kuma Lion ganin Nawid yana kira da number Ummi ne ya sa ya bibiyi waye yake kira, idan baku mance ba ya datsi wayar baki ɗaya. Ganin Nawid ne yasa Imran ya ɗauki call ɗin yana faɗin "Dr lafiya kira da daren nan haka?". A hanzace Nawid ya ce "Prof wani taimako nake son ka yi Mani" duk abin da suke faɗe Lion yana jinsu dan ya gano cewa Imran Nawid ya kira, abin kuma ya ba shi mamaki ganin Imran ya san Nawid amma kuma bai san cewa yarinyar da yake nema tana tare da Nawid ɗin ba, zuba masu ido Lion ya yi dan ya ji karshen zance, yana son ganewa shin da gangan su Nawid suka saceta ne ko yaya, idan da ganganne to yana da kyau a hukunta su. "Dr wace iriyar taimako ne? Ka faɗa ina jinka". "Prof wata matsala muka samu a gida, yanzu dai na kawo maka kanwata da zan aura please ka fito ina ƙofar gida, ka zo ka karɓeta ka haɗata da Heartbeat su kwana zuwa da safe idan mun gama settle na problem na gida sai in zo in ɗauketa". Ɗan dafe kai Imran ya yi yana faɗin "Kash Dr wlh bana gida kuma Akil ma baya gida, amma ka kaita wajen ƴan uwan Abbo ko Ummi mana". Shima Nawid ɗin dafe kai ya yi yana faɗin tom shikenan, da haka suka yi sallama. Imran na ajiye wayar ya juyo da kallonsa zuwa kan Lion dan ya tambaye shi ko Jelly'n ne aka gane, wani irin razana ya yi sakamakon idanunsa da suka sauƙa cikin dara daran blue eyes ɗin Lion, idanun Lion sun tsorata shi sosai, bai yi tunanin Lion na ganinsa ba, kuma abun da yasa ya kara tsorata Lion ya tsare sa ne da idanun nasa alamar kamar yana karantarsa, ya kuma ɗan zaro idanun nasa, kuma kunsan idanun Lion da daddare suna kyalli, shiya kara tsorata Imran. "Prof kwata kwata brain naka sai a hankali". Shine abin da Lion ya faɗa, juya idanu Imran ya yi yana sauƙe ajiyar zuciya dan ya tsorata ainun. Mai da kallonsa kan laptop nasa Lion ya yi, almost 5mins sannan gently ya ce "Ka sake kiran wannan friend ɗin naka da kuka yi waya yanzu ka ce ya kawo maka yarinyar nan ta kwana". Tun da Imram ya ji Lion ya faɗi haka jikinsa ya bashi Jelly ce, wani irin zabura ya yi bawan Allah jikinsa har kerma yake yi wajen ɗaukar wayarsa ya fara kiran layin Ummin, sai dai ina wayar bata shiga, ba network, kamar zai yi hauka ya diro kasa daga saman gadon zai nufi waje, dakatar da shi Lion ya yi tare da ce mashi ya sake kiran layin. Sauri sauri ya sake kira, kira ta farko number ta shiga, ringin biyu ta yi Nawid ya ɗauka, tsabar sauri Imran har haɗe words yake yi wajen gaya mashi unguwar da zai zo ya same shi ya kawo yarinyar, to Nawid ya amsa mashi da shi sannan suka yi sallama. Zarya ya fara yi a cikin ɗakin yana haɗa zufa, girgiza kai Lion ya yi yana yiwa Imran kallon mara hankali mara sanin ciwon kai, daga haka ya kashe laptop ɗin tare da karisa hayewa saman bed ɗin ya kwanta ya bi lafiyar gado dan ya huta. Imran kuwa sai zarya yake yi a wajen har tsawon minti 30 kafin kiran Nawid ya sake shigowa cikin wayarsa alamar ya iso kenan, da sauri ya nufi waje har yana haɗawa da gudu. Lion kuwa idanunsa a lumshe kamar mai barci. Yau Imran bai jira soja ya buɗe mashi gate ba, da kansa ya buɗe gate ɗin ya fita, sojan kuwa bai hana shi fita ba saboda yasan tsakaninsu da Lion. Yana fita ya sami Nawid ya fito daga cikin motarsa shima yana ta zarya a wajen, cikin sauri ya karisa wajensa yana faɗin "Ina take Dr?" Buɗe mashi gidan baya Nawid ya yi yana faɗin gata nan tana kwance tamkar babu rai a jikinta. Kallon farko da Imran ya yi mata tabbas bai ganeta ba saboda gyara da ta sha da kuma yunkurin tsafi da akayi niyar yi da ita, abin ya ɗan taɓa ta, amma da ya zuba mata idanu ya gane ita ɗin ce. "Prof dan Allah ka ɗauke ta zan wuce gida ne dan akwai babbar bala'in da na baro a gida". Cewar Nawid ɗin ya yi maganar tare da komawa cikin motar dan yana sauri kada Abbo ya karya kofar ya je ya hakewa ɗaya daga cikin yaran bikin da suka zo ko kuma wani mummunar abu ta faru a gidan, hakan yasa yake sauri. Ɗaukarta a kafaɗa Imran ya yi kwata kwata ya kasa yin magana, yana son yin magana da Nawid amma ya kasa saboda wani irin nauyi da harshensa ya yi mashi, sannan kuma shima Nawid ɗin yana sauri ba damar su yi magana. Yana fitar da ita daga cikin motar Nawid ya figi motarsa da gudun gaske ya bar wajen, shi kuma Imran da kyar ya iya nufar cikin gida da ita, ita kuma tanajin ɗumin jikin Imran ta farka tsafin da Abbo ya yi mata na barci ya saketa sakamakon idan baku manta ba jinin Umaiya ba komai yake iya taɓa su ba. Tana farkawa kuma da sabon kukan ciwon ciki ta farka Mashi, jin kukanta yasa ya yi sauri ya karisa cikin palon da kyar.......nima da kyar na iya kawowa nan kafin na dasa aya. I need your prayers my people's 😌 GA ASKARS ƊIN DA NACE ZAN RUBUTO MAKU👇 NA FARKO ﴿قُل هُوَ اللهُ أحَدٌ...﴾ ﴿قُلْ أعُوذُ بِرَبِّ اْلفَلَقِ...﴾ ﴿قُلْ أعُوذُ بِرَبِّ النَّاسِ...﴾ [ثلاث مرات] NA BIYU أصْبَحْنَا وَ أصْبَحَ المُلْكُ لِلَّهِ، وَ الحَمْدُ لِلَّهِ، لَا إِلَهَ إِلَّا اللهُ وَحْدَهُ لَا شَرِيْكَ لَهُ، لَهُ المُلْكُ، وَ لَهُ الحَمْدُ، وَ هُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ، رَبِّ أسْألُكَ خَيْرَ مَا في هَذَا اليَوْمِ وَ خَيْرَ مَا بَعْدَهُ، وَ أعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا في هَذَا اليَوْمِ وَ شَرِّ مَا بَعْدَهُ، رَبِّ أعُوذُ بِكَ مِنَ الكَسَلِ، وَ سُوءِ الكِبَرِ، رَبِّ أعُوذُ بِكَ مِنْ عَذَابٍ في النَّارِ وَ عَذَابٍ في القَبْرِ.(١)وَ إذَا أمْسَى قَالَ: أمْسَيْنَا وَ أمْسَى المُلْكُ لِلَّهِ. وَ إذَا أمْسَى قَالَ: رَبِّ أسْألُكَ خَيْرَ مَا في هَذِهِ اللَّيْلَةِ وَ خَيْرَ مَا بَعْدَهَا، وَ أعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا في هَذِهِ اللَّيْلَةِ وَ شَرِّ مَا بَعْدَهَا. NA UKU اللهم بِكَ أصْبَحْنَا، وَ بِكَ أمْسَيْنَا، وَ بِكَ نَحْيَا، وَ بِكَ نَمُوتُ، وَ إلَيْكَ النُّشُورُ.(١)وَإذَا أمْسَى قَالَ: اللهم بِكَ أمْسَيْنَا، وَ بِكَ أصْبَحْنَا، وَ بِكَ نَحْيَا، وَ بِكَ نَمُوتُ، وَ إلَيْكَ المَصِيْرُ. NA HUƊU اللهم أنْتَ رَبِّي لَا إلَهَ إلَّا أنْتَ، خَلَقْتَنِي وَ أنَا عَبْدُكَ، وَ أنَا عَلَى عَهْدِكَ وَ وَعْدِكَ مَا اسْتَطَعْتُ، أعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَنَعْتُ، أبُوءُلَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ، وَ أبُوءُ بِذَنْبِي فَاغْفِرْ لي فَإنَّهُ لَا يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إلَّا أنْتَ. NA BIYAR اللهم إنِّي أصْبَحْتُ أُشْهِدُكَ، وَ أُشْهِدُ حَمَلَةَ عَرْشِكَ، وَ مَلَائِكَتِكَ، وَ جَمِيْعَ خَلْقِكَ، أنَّكَ أنْتَ اللهُ لَا إلَهَ إلَّا أنْتَ وَحْدَكَ لَا شَرِيْكَ لَكَ، وَ أنَّ مُحَمَّداً عَبْدُكَ وَ رَسُولُكَ. [أرْبَعَ مَرَّاتٍ] Na shida أللهم مَا أصْبَحَ بِي مِنْ نِعْمَةٍ، أوْ بِأحَدٍ مِنْ خَلْقِكَ، فَمِنْكَ وَحْدَكَ لَا شَرِيْكَ لَكَ، فَلَكَ الحَمْدُ وَ لَكَ الشُّكْرُ.(١)و إذَا أمْسَى قَالَ: اللهم مَا أمْسَى بِي... NA BAKWAI اللَّهُمَّ عَافِنِي فِي بَدَنِي، اللَّهُمَّ عَافِنِي فِي سَمْعِي، اللَّهُمَّ عَافِنِي فِي بَصْرِي، لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ، اللَّهُمَّ إِنِّي أَعُوْذُ بِكَ مِنَ الْكُفْرِ، وَالْفَقْرِ، وأَعُوْذُ بِكَ مِنْ عَذَابِ القَبْرِ، لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ.[ثَلاثَ مَرَّاتٍ] NA TAKWAS حَسْبِيَ اللهُ لَا إلَهَ إلَّا هُوَ عَلَيْهِ تَوَكَّلْتُ وَهُوَ رَبُّ العَرْشِ العَظِيمِ [سَبْعَ مَرَّاتٍ] NA TARA أَصْبَحْنَا وَ أَصْبَحَ المُلْكُ لِلَّهِ رَبِّ العَالَمِيْنَ، اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ خَيْرَ هـَذَا اليَوْمِ: فَتْحَهُ، وَنَصْرَهُ وَ نُورَهُ، وَ بَرَكَتَهُ،وَ هُدَاهُ، وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا فِيْهِ وَ شَرِّ مَا بَعْدَهُ. و إذا أمسى قال: أَمْسَيْنَا وَأَمْسَى المُلْكُ لِلّهَِ رَبِّ العَالَمِيْنَ، اللَّهُمَّ إِنِّي أسْأَلُكَ خَيْرَ هـَذِهِ اللَّيْلَةِ، فَتْحَهَا، وَنَصْرَهـَا، وَنورَهـَا وَبَرَكَتَهَا، وَ هُدَاهـَا، وَ أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا فِيْهَا وَشَرِّ مَا بَعْدَهـَا. 💖💖TRIPLETS💖💖 E81-82💖 Yana fitar da ita daga cikin motar Nawid ya figi motarsa da gudun gaske ya bar wajen, shi kuma Imran da kyar ya iya nufar cikin gida da ita, ita kuma tanajin ɗumin jikin Imran ɗin ta farka, tsafin da Abbo ya yi mata na barci ya saketa sakamakon idan baku manta ba jinin Umaiya ba komai yake iya taɓa su ba. Tana farkawa kuma da sabon kukan ciwon ciki ta farka Mashi, jin kukanta yasa ya yi sauri ya karisa cikin palon da kyar. Duka ta fara kai mashi a baya tana sambatu tana faɗin "Yaya Nawid ni ka saukeni, ɗan iska kawai, bana ce kada ka kuskura ka taɓa ni ba, wlh sai na gaya wa Ummi, na ce bana sonka ana dole ne? Mugu kawai ka sauke ni bana so". Raunin zuciya ya sa Imran ya kasa karisawa da ita ɗakinsa, ya kasa haurawa saman benen, a palon kasa ya sauketa, idanunta a rufe amma tana surfa masifa, ganin abin Imran yake yi tamkar a mafarki, tabbas yau Jelly'nsa ce a gabansa, ya kasa motsawa daga in da yake ma bare kuma a kai ga ya yi mata magana. Bayan ta gama surfa masifar tata ne ta juya tare da buɗe idanunta akan zata tafi ɗakin Ummi dan ita duk a tunaninta a a gidan Abbo suke. Tana juyawa kuma sai ta tsaya turus dan taga yanayin tsarin palon ba irin nasu Ummi bane, cikin sauri kuma ta juyo dan ta tambayi Nawid ɗin ina ne nan kuma. Kai tsaye sai cikin idanun Imran idanunta suka sauƙa, zuba mashi idanu ta yi tana kallonsa, nan take kuma ta dafe kanta tare da sakin kuka mai sauti, kafin Imran ya yi wani yunkuri ta sukale kasa sumammiya. Da sauri ya yi kanta yana ambatar sunanta, ina ta sume. Jikinsa har kerma yake yi wajen ɗaukarta tare da tattara duk karfin da ya saura mashi ya haura sama da ita. Kai tsaye ɗakinsa ya wuce da ita, a saman bed nasa ya kwantar da ita tare da sauƙowa ya ɗauko ruwa mai sanyi daga cikin fridge nasa dake a cikin ɗakin, da yake gabaɗaya ɗakunan gidan akwai fridge a ciki. Saman gadon ya dawo tare da buɗe bakin robar ruwan ya tarbo ya shafa mata a fuska, shiru bata motsa ba sake ɗebo ruwan ya yi ya shafa mata, nan ma shiru, sai a karo na uku ne ta ja dogon numfashi tare da fara sambatu idanu a rufe. "Ni gidansu yaya Imran za ka kaini, idan kuma ba zaka kaini can ba to na tafi, kai ka yanka ni kuma sai kace wata rago? Ba zan shiga ɗakin ba, tun da naga ka matsa na shiga na san ba alkhari bane a cikin ɗakin" sambatun maganarta ta karshe da mutumin daya ɗauketa da nufin zai taimaka mata ta karɓo school bag ɗin sai ya kaita gidan shi yana ƙoƙarin lalata mata rayuwa, shine magana ta karshe da ta yi fitar ta gidan kenan su Ummin Nawid suka bugeta da mota. Dafe kai Imran ya yi idanunsa sun yi jawur, da kunnansa ya ji irin gwagwarmayar da ta sha, dukka kuma akan shi domin kuwa sunan sa ne abu na farko data fara ambata, ashe ma Kd ta zo kuma saboda shi Baiwar Allah, abin da kenan yake faɗi a cikin zuciyarsa. Jin ta ki daina sambatun ne yasa ya ambaci sunanta kasa kasa a kuma nutse, shiru bata amsa ba kuma bata daina sambatun da take yi ba. Ganin haka yasa ya sanya hannunsa ya tallaɓota a kirjinsa yana mai sake ambatar sunanta, har lokacin bata ji shi ba, sai da ya ɗan ambata da karfi sannan ta tsaya cak da surutan da take yi tare da waro idanunta waje, tabbas ta gane voice nasa domin kuwa ba zata taɓa mance muryarsa ba, tun tana karama take jin muryar nan tasa, kamar hadda haka ta haddace voice ɗin nasa. Ido cikin ido take kallon shi yayin da shima yake kallonta cikin ido babu ko kyaftawa, dukkansu ba bu wanda ya iya kyafta ido daga cikinsu saboda tsabar farinciki. Sun jima a haka sai da ya ga hawaye na bin gefe da gefen fuskarta ne yasa ya ɗan kyafta idanunsa tare da sake ambatar sunanta a hankali. "Yaya Imran" ta ambata a hankali tare da ɗago da hannunta izuwa saman face nasa domin ta tabbatar da shi ɗin ne, gyara mata kwanciyarta a jikin nasa ya yi tare da riƙo hannun nata ya kai saman kukatunsa yana faɗin "Taba ki ji nine Jelly'na nine ba wani ba". Kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro ta saka mashi, shi kuma rungumeta sosai ya yi a jikinsa, a hankali hawayen da suka cika mashi idanu suka fata gangaro mashi a saman kuncinsa. Dukkansu suna ruwan hawaye waye zai rarrashi wani a cikin su to?. Cikin kuka ta ce "Yaya Imran ina ka tafi ka barni? Ina kaje baka zo Kano ba? Daddy wai zai aura mani wani mutum shine na gudu na zo Kaduna dan na gaya maka, ina tafiya wasu suka kwace mani school bag na, shine wani kuma ya ce in zo ya bani school bag ɗin a gidansa, da muka je ya ce sai na shiga ɗakinsa ni kuma naki yarda dan daddy ya hana ni, shine ya ce zai yanka ni, tun ɗazun yake ta yi mani masifa wai lallai sai na shiga, dana ga zai dake ni shine na gudu na fito waje daga nan kuma ban sake ganin kowa ba, ina ka tafi yaya Imran?" Tana magana tana kara tsananta kukan da take yi. Imran bawan Allah kuka ya ci karfinsa ya kasa magana, banda kara matseta da ya yi a jikinsa ba wani abin da ya iya taɓukawa. "Yaya Imran kayi magana mana ko dai ba kai bane? A'a kai ne ma tabbas kai ne, dole kaine!". Muryarsa ta dashe bata fita sosai, da kyarma ya iya cewa "Nine matata nine, ki kyaleni nayi kuka sosai yau". Ɗan ture shi ta yi tare da ɗago kanta tana hawaye tana faɗin "A'a yaya Imran, ba zaka yi kuka ba, ban yarda ba, ka daina bana so dan Allah ka bari ka ji? Idan baka bari ba zan gayawa daddy kana kuka". "Ki bari na yi kuka kin ji? Na tara kukan sosai a cikin zuciyata, yau ɗaya ki bari nayi sosai har sai ya ishe ni kinji ko?". Duka ta fara kai mashi a kirjinsa tana faɗin "Bana so bana son kukan, ni ka daina, dan Allah ka bari bana so". "Na bari matata na bari, tun da baki so na bari kin ji ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar ta ji. "To shikenan kema ki daina kukan kin ji ko?" Ya faɗa yana mai ɗago hannunsa izuwa saman face nata dan ya goge mata hawayen fuskarta. Ita ma kai nata hannun ta yi sama face nasa ta fara goge mashi hawayen tana faɗin "Yaya Imran ai bani nake kawo kukan ba, shine yake zuwa da kansa, wlh bani na kira shi ba". Harshe yasa ya lashe hawayen nata tas kafin ya ce "To na shanye hawayen dukka kada ki bari wani ya fito kin ji ko?" gyaɗa mashi kai ta yi alamar e ta ji. Zuba mata idanu ya yi yana kallon yadda ta kara wani sihirtaccen kyau na fitar hankali, ita ma kallon shi kawai take yi tana mai matuƙar jin kaunar yayan nata har cikin zuciyarta. To fah kenan yanzu jelly ta mance da su Nawid? Kenan yanzu bata san waye su ba? Ta dawo daidai ba ta san rayuwar da ta yi a baya ba, kun dai ga daga wajen da wannan mutumin ya ɗauketa daga nan ta faro rayuwarta na yanzu, su Nawid duk ta mance su kun dai ji tace ɗazun ne mutumin yake yi mata magana, kenan duk waƴan nan watanni da ta ɗauka a gidan Ummi sun goge bata san da su ba, babbar magana mu dai je zuwa. "Jelly" ya ambaci sunanta can kasan maƙoshinsa, na'am ta amsa mashi da shi. "Kin san wahalar da na shi bayan ɓatar ki kuwa?" Ɗago da waƴan nan dara daran idanun nata kamar ball ɗin ta yi izuwa cikin nasa idanun, a raunace ta fara magana "Yaya Imran ina kewar daddyna sosai, ina son ganin shi, amma dan Allah kada ka gaya mashi ina nan ka ji ko? Idan ka gaya mashi wlh aure zai yi mani da wani, ni kuma bana son kowa, kai kaɗai kawai nake so, dan Allah idan kana da hoton daddyn ka bani na kalla ka ji ko? Ina jin zuciyata tana yi mani zafi sosai". Hannu yasa ya kwantar da kanta a saman kirjinansa yana kara jin kaunarta tana ratsa shi sosai. Kwanciya ya fara yi da ita a jikinsa kafin nan ya ce "Daddy ya ajiye batun aurenki da wani ki daina damuwa, yanzu haka da nake maki magana ko yanzu na kira shi nace mashi gaki mun gane ki, to ina mai tabbatar maki a daren nan zai cire sadakin ki da kansa ya miƙawa Abbi a ɗaura mana aure, ki zama mallakina ni kaɗai, dan haka kada ki damu da safe zamu je wajen su". Kara shegewa jikinsa ta yi cikin shagwaɓa ta ce "Kenan yaya Imran yanzu daddy zai yi mana aure?" Jinjina mata kai ya yi alamar tabbatar mata da maganar tata. "Jelly daddy ya sha bakar wahala sosai ɓatar ki, idan munje gida gobe ki bashi hakuri, ki nemi yafiyarsa, wlh ya wahala fiye da tunanin ki, ya yi fama da rashin lafiya sosai". Zubur ta miƙe daga jinin nasa hankalinta a tashe ta ce "Dan Allah Yaya Imran ka kaini wajen shi yanzu ka ji? Ina dai ba zai yi mani aure da wani ba?" Gyaɗa mata kai ya yi alamar e "To dan Allah ka kaini wajen shi ka ji? Ina son ganin daddyna ina kewar shi wlh, Wayyo Allah". Ta kai karshen maganar tare da fara sabon kuka Jawota jikinsa ya yi ya shiga rarrashinta tare da nuna mata dare ya yi ta kwanta su yi barci zuwa gobe sai suje, da kyar ta yarda ta kwanta a jikinsa, bargo ya ja masu tare da yi masu addu'ar barci ya shafa mata sannan ya kankameta sosai a jikinsa kamar wani ya ce zai kwace mashi ita, ko juyawa zai yi tare suke juyawa tana manne a kirjinsa, ita ma dai kankame shi ta yi kamar an ce mata zata rasa shi ne. Da haka barci ya ɗauke ta, shi kuwa ya kasa barcin kwata kwata, kallonta kawai yake yi domin bai kashe wutar ɗakin ba, hakan ya bashi damar kallon kyakkywar fuskarta da kyau, kwata kwata ya kasa runtsawa. A ɓangaren daddy'n jelly kuwa, bari mu ɗan koma baya kaɗan wunin yau kenan. Sai misalin karfe 11 na rana ya farka daga barcin da ya ɗauke sa, da mamaki sai baiga Ayla a saman gadon ba, cikin sauri ya miƙe zauna yana ƴar wawwaigawa ko zai ganta. Can ya hangota saman kujerar mirror ta rarrafa ta tafi wajen, bata iya takawa da kafafunta sai dai rarrafe, bayan ta tashi daga barci ne ta rarrafa ta shiga toilet ta yi wanka sannan ta fito da kyar ta iya hawa saman mirror chair ma ta zauna tana shafa mayunkar Daddyn nata. Wani irin muguwar faɗuwar gaba ya ji kamar wani abin na shirin faruwa da shi, Allah sarki Uba da ƴa a jikinsa yana jin duk abin da zai faru ko yake faruwa da Jellynsa, innalillahi wa inna ilaihir rajiun ya karanta tare da sauƙowa kasa daga saman gadon da sauri ya karisa wajenta. Yana zuwa ya sanya hannu ya karɓi mai da take riƙe da shi ya shiga shafa mata, yana yi yana ƙaƙalo mata murmushin dole dan ta yi farinciki, amma shi kuma ba farincikin bane a cikin zuciyarsa, ban da muguwar faɗuwar gaba ba wani abin da yake ji, amma haka ya daure ya kakalo murmushi dan ta yi farinciki. Kwance towel ɗin jikinta ya yi ya fara shafeta da mai har saman breast nata, yana shafa masu mai yana kuma matsasu, amma kuma yaki yarda su haɗa ido da ita saboda wani irin kunyarta da yake ji, ita ma dai daga jiya zuwa yau bata son su haɗa idanu saboda wani irin kunyarsa da take ji. Bayan ya gama ne ya zube gwiwowinsa a kasa a gabanta dan ya rage tsawonsa ya zama daidai da tata, kuma baya jin shakkar yi mata duk abin da yake so dan gane da soyayya cikin kuma har da duƙa mata saboda yasan Ayla yarinya ce so silent, and then yanzu take ɗaukar karatu, so a yadda suke ɗin nan duk abin da ya koya mata akan shi zata tashi, yasan babu wani zancen raini a tsakaninsu, ba zata raina shi ba dan yana duƙa mata, dan kuwa daga yanayin mutun kake iya gane waye shi me kuma zai iya aikatawa, da dama daga cikin mu muna ganin idan namiji ya duƙa mana shikenan mun raina shi girmansa ya zube, shiyasa wasu maza basu taɓa yarda su nuna cewa suna son abuma bare kuma har a kai ga zancen duƙawa, ba dan komai ba sai dan kada a raina su, so dan miji ya duƙa maki ba raini bace soyayyace, amma wata daga nan sai ta raina shi tana ganin ai har duƙawa yake yi a gabanta, kuskure ne yin hakan, soyayya take ja ayi komai da bai kaucewa Shari'a ba, dan haka ki duƙawa miji ba raini bane shima ya duƙa maki ba raini bane. MAZA KU YI MAZA KU KOMA IRIN LARABAWAN NAN DA TURAWA, ANA DUƘAWA ANA MIƘO FURE, MU KUMA KU DUƘA KU MIƘA MASHI KUNU🤣🤣 WASA NAKE YI, KI DUƘA KI MIƘA MASHI KAYAN DAƊI IRIN SU BLACK TEA AND COFFEE 😌🙃. Bayan ya zube gwiwowinsa ya rage tsawonsa ta yadda zai yi daidai da tata saboda ita tana zaune saman chair ne. Kwanto da kansa a saman cinyarta ya yi tare da riƙo hannayenta a cikin nasa. Kwace hannu ɗaya ta yi tare da fara shafa kyakkyawar gashin kansa tana matukar kaunar daddyn nata. "Babyn daddy ayi wa daddy afuwa ko" ya faɗa ba tare da ya ɗago kan nasa ba. "Daddy to ka saka mani kaya ka ji ko?" Ɗan ɗago da kan nasa ya yi ya saci kallonta yana faɗin "E yanzu kuwa dan ma muje asibiti". Zaro idanu ta yi kamar zata yi kuka ta ce "Daddy ni bana son asibiti, ina tsoron su yi mani allura ka ji?" Zura hannayensa ya yi ta kugunta ta baya ya ɗan riƙota yana faɗin "To shikenan bari na sanya Abbi ya kira mana likitarsa ya turo mana nurse mace ta zo ta duba mani ke kin yarda?" Gyaɗa mashi kai ta yi tana faɗin "E daddy amma ita ma ba zata yi mani allura bako?" Sai lokacin ya kalli fuskarta kai tsaye, cikin sauri ta rufe idanunta dan kunyarsa da take ji. "Baby da allura da kuma abin da na yi maki daren jiya wanne ya fi zafi?" Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Daddy ni ai sau ɗaya ma aka taɓa yi mani allura lokacin bani da lafiya sosai, mamana ta roƙi wata makwabciyar mu ta kai ni asibiti, amma gaskiya akwai zafi allura sosai kuma shima...." Ta kasa fitar da shima abun da ya yi mata akwai zafi sosai fiye da allura, maganar ta kasa fita baiwar Allah, sai ta yi shiru. "Baby ina matukar kaunar ki, duk abin da ake buƙata a tattare da mace kafin ta cika mace ta gari kin haɗa shi, kina kaunar daddy kamar yadda yake son kuwa?" Cikin sauri ta ɗaga mashi kai tare da fara shafa kyakkyawar gashin dake a matsayin sajensa izuwa wajen kewayayyar gashin dake a bakinsa. "Daddy Allah ina son wannan gashin, yana yi maka kyau sosai da sosai, nima kuma yana yi mani kyau sosai da sosai". Ta faɗa tana mai cigaba da shafa gashin kewayen bakin nasa. Hannun nata ya riƙo tare da kaiwa ɗan bakinsa ya yi mata cizon soyayya har sai da ta ce "Wash daddyna akwai fa zafi". Wash ɗin nan da ta ce yasa ya miƙe tare da riƙo hannunta ya sauƙeta kasa. Kara ta saki tare da kankame shi dan har ga Allah ta ci bakar wuya a hannunsa, bata iya taka kafarta. Sorry ya ce mata tare da duƙawa akan ta hau bayansa, ba musu ta haye ya goyata tare da juyi da ita a cikin ɗakin yana mai jin matukar farinciki abinsa, abin gwanin ban sha'awa da kuma burgewa. Ya jima yana juyi da ita tare da gaya mata kalamai masu daɗi kafin ya sauƙeta a saman bed nasu ya ɗauki wayarsa ya kira layin Abbi. Lokacin kuma shima Abbi yana hannun Hajiya Hadiza, idan baku manta ba mun ɗan koma baya ne dan ku ji abin da ya faru wunin ranar a gidan na Abbi, kafin mu kai daren da jelly ta dawo, kuma idan baku manta ba Hajiya ta zo ta ɗauki Abbi ɗazun a palo. Sau biyu yana kiran Abbi amma shiru bai ɗauka ba dan shima baya duniyar mutane, ɗan kallon babyn tasa ya yi baya son fita ko nan da palo ya barta ita kaɗai a ɗakin, hakan yasa ya kira layin Irfan, shima Irfan a lokacin yana hannun Akila tana zuba mashi shagwaɓa son ranta, duk ya birkita bawan Allah, suna a cikin mota suna zaune, yau Akila ta hana shi komawa, kuma Allah ya rufa masu asiri Ammie tana ta zuba barcinta bata tashi ba. Ganin kiran bappan nasa wadda ya fi kauna yasa ya ɗauki kiran, badan daddyn Jelly bane ya kira shi da ba zai iya ɗaukar kiran kowa ba bayan Abbi, amma da yake yana bala'in kaunar daddy shiyasa dole tasa ya ɗauki kiran. Sallama ya yi tare da ɗagawa bappan nasa gaisuwa. Daga ɗayan ɓangaren daddy ya ce ya turo mashi da number Aunty idan yana da ita, to ya amsa da shi tare da katse kiran ya tura mashi number. Number na shigowa daddy ya fara kiran layin tata, da yake ita tana da number daddyn ta ɗauka a wayar Abbi sai ta gane cewa shine, a lokacin da kiran ya shigi ta gama shan kukanta akan abin da Hajiya Hadizatu ta yi mata, ta sha kukanta son ranta tana kwance saman gado. Tana ganin kiranshi ta ɗauka, bai jira dogon gaisuwarta da kuma sallamar ta ba, kawai ya ce "Sadiya Maik ne please ki saka Hanan ta kawo wa baby kayanta". Da yake ita ma bata cikin mood mai kyau sai kawai ta amsa mashi da to, ba dan haka ba da sai ta tsokane shi, amma da sai ta ce to ya dawo mata da kanwarta haka ya isa, shima dai yau baya jin jan magana da ita shiyasa kawai ya yi mata maganar a takaice. Miƙewa ta yi ya shiga toilet, furkarta ta wanke sannan ta fito ta nufi ɗakin su Hanan ɗin. Kwance ta isko Hanan tana duba wasu littattafan A'afia kamar tasan me aka rubuta a ciki. "Hanan tashi ki ɗauki kayan Ayla masu kyau ki kaiwa mijinta". Shine abin da aunty ta faɗa tana ƙoƙarin juyawa ta bar wajen. "Aunty ina wuni?" Shine abinda Hanan ɗin ta faɗa, a takaice aunty ta amsa sannan ta wuce ta koma ɗakinta. Miƙewa Hanan ta yi sauri sauri ta ɗauki kayan ta fito. Shi kuma daddy yana gama magana da Aunty ya rubutawa Abbi massage akan suna buƙatar likita mace dan ta zo ta duba mashi babynsa. Bayan ya tura saƙon sai ya mayar da wayar saman bedside drawer ya jawota jikinsa yana shafa bayanta a haka Hanan ta yi masu sallama a palo. Yana ƙoƙarin miƙewa ta riƙe shi tana faɗin "Daddy Hanan ce fa, ni ka bari zan je in karɓo kayana". Wani irin mamakine ya kama shi, wato Ayla ta fara kishin shi kenan? Gaskiya ba ƙaramin daɗi abin ya yi mashi ba, bai san time da ya runhumeta sosai yana matse ta a jikinsa ba, sai yanzu ya kara tabbatar da tana son shi so irin na aure, da yana mata kallon kamar tana son shi so irin na uba da ƴa ce kawai. "Daddy bari na je na karɓo ko?" Girgiza mata kai ya yi kafin ya ce "No baby ba zaki iya tafiya ba, kuma idan kika fita yanzu Hanan zata tambayi me ya same ki, kin ga kuma wannan sirrin mijinki ne, daga ke sai ni, tun da baki so nayi magana da ita Hanan ɗin ne kice ta ajiye kayan a palo ta ta fi, idan ta tafi sai na je na ɗauko ko?" Gyaɗa mashi kai ta yi tana ɓoye fuskarta a kirjinsa. "To ki ce ta ajiye kayan ta tafi". Ɗan ɗago kanta ta yi daga kirjin nasa tare da ɗaga murya ta ce "Hanan ki ajiye kayan a saman sofa zan zo in ɗauka". To Hanan ta amsa mata da shi, sannan ta ajiye ta tafi. Duk wanda ya zauna da Aunty sai ya koyi kalmar to ko yana so ko baya so, tafi kwarewa a iya amsa to kawai, bayan shi babu wani action kuma, yanzu ga shi Hanan ma ta koya. Sai bayan tafiyar Hanan da kamar minti 5 haka sannan Ayla ta kyale daddy ya je ya ɗauko kayan ya zo kuma ya sanya mata ya shirya kayarsa tsab, abin gwanin ban sha'awa, har lokacin kuma bai daina jin wannan faɗuwar gaba da yake ji ba, sai dai addu'a da yake yawaita yi a cikin zuciyarsa yasa ya sami kwarin gwiwa akan ba wani abu na sharri da zai faru da su. Haka suka cigaba da zuba soyayyarsu son ransu. After some hours, bayan Abbi ya gane kansa ne ya kalli massage ɗin daddy sai ya kira Dr akan ya turo masu likita mace yanzu. Ba'a ɓata lokaci ba sai gata ta zo, aunty ce ta yi mata jagora zuwa part ɗin Daddyn, da yake yasan da batun zuwar likitar sai ya ce su shigo, a lokacin kuma Ayla na kwance a saman kirjinsa yayin da shi kuma yake jingine da jikin headboard na gadonsun. Kunya ne ya kama Aunty ganinsu a haka, daddy ko kunya bai ji ba bare kuma ya yi wani ƙoƙarin raba jikinsa dana Aylar, sai ma wani kara riƙota da ya yi, sai da Dr ta ce zata yi aikinta sannan ne ya kwantar da ita ya miƙe jikinsa na sanye da farar jallabiya. Hararar wasa ya wurgawa Aunty yana faɗin "Ko dai kina da abin faɗe ne?" Murmushi ta yi kafin ta ce "A'a yaya Maik ni na isa? A'a sai ma anjuma" ta faɗa tare da juyawa ta fice abinta, dan bata cikin yanayi mai daɗi idan ta biye mashi hawan jini zai saka mata. "Yallaɓoi ka ɗan bamu waje ko?" Cewar Dr. Girgiza kai ya yi kafin ya ce "Aa duk abin da zaayiwa baby ayi shi a gabana ina gani". Shiru Dr ta yi bata sake yin magana ba dan tasan irinsu daddyn Jelly baa jayayya da su akan matansu, idan suka ce ba za su yi abuba to ba za su yi ɗin bane. Dubata Dr ta fara yi shi kuma ya koma kusa da ita ya zauna tare da kwantar mata da kanta a saman kirjinsa yana shafa face nata. A haka har Dr ta gama dubata sannan ta ɗago ta kalle shi ta ce "Sir akwai alluran zazzaɓi da kuma magunguna da zan bata, amma dan Allah sir a yi ƙoƙarin a bata kulawa sosai sannan ta rinƙa shiga ruwan zafi sosai, bacin haka kuma a ɗan barta ta huta, ina nufin kada a kusanceta kamar na sati guda haka, idan ba haka ba za'a iya samin babbar matsala". Jinjina mata kai ya yi alamar okey. Kuka ta sa mashi tana faɗin "Daddy kai fa ka ce ba za'ayi mani allura ba, amma to naji ta ce zata yi Mani, please daddy wlh bana so". Rungumeta sosai ya yi yana faɗin "Ba zaayi maki ba, Dr bamu magani kawai ban da allura baby bata so". To Dr ta ce sannan ta rubuta mashi magani tare da nuna mashi yadda za'a sha maganin, karɓa ya yi tare da tambayarta kuɗin aikinta, bayan ta gaya mashi ya karɓi account number ta ya zuba mata kuɗinta har da kari, ta yi mashi godiya suka yi sallama ta tafi. Tana tafiya ya kwantar da babyn tasa ya ɗauki waya ya kira Aunty akan a kawo mashi abinci ya karya, dan sai yanzu ya ji kamar zai iya cin abinci, buƙatarsa ta biya ya ji ba wata babbar matsala ne ya same babyn tasa ba. A ɓangaren su Irfan kuwa, yau sun sha soyayya iya soyayya da AKILA har sai karfe 1 na rana sannan suka yi sallama ya dawo da ita gida daga yawon da suka tafi, sun je wurare daban daban, wuraren wasanni wajen yawo na masoya, abin ba'a magana dan sun mace wa junansu sosai yau, ta kara narka zuciyar Irfan a tsantsan kaunar ta. Lokacin da ta dawo gida a palo ta sami Ammie tana tsaye, da sallama ɗauke a bakinta ta shigo cikin Palon, da yake lokacin da Ammie ta tashi bata same ta ba ta kira layin ta akan ina ta tafi, shine ta yi mata karya akan tana gidansu Anisa kawarta kanwar A'A kenan, tun lokacin a waya Ammie ta yi mata faɗa sosai akan kada ta kara yin hakan, ta fita babu tambaya, da yake dai dama abaya bata taɓa yin hakan ba, ta fita babu tambaya, shiyasa Ammie taba ɗauki wani mataki ba, ta ce tun da bata taɓa yi ba bari ta ɗaga mata kafa na yau kawai, ita kuma Akila ta ɓoyewa Ammie ainahin in da suka je ne dan saboda tasan Ammie ta tsani family'n Abba sosai, idan ta ji da Irfan suke a tare to ba makawa raba su zata yi. Rungume Ammie ta je ta yi da gudu tana bata hakuri, ita ma Ammie rungumeta ta yi tana mai karɓar hakurin tata tare da ce mata kada ta kara. To ta amsa da shi daga nan ta saki Ammie ta koma ɗaki. Sai kuma me? Tana shiga ɗaki ta fara duba wayarta ko zata ga saƙon ɓoyayyen masoyi, amma ina shiru bai tura mata komai ba, abin ya dameta sosai da sosai, haka ta wuni sukuku, bai tura mata saƙo ba bai kuma kira ta ba har dare, bayan ta ci abincin dare ta kwanta yaya Irfan ya kirata, ta kasa ɗaukar kiran nasa saboda begen ɓoyayyen masoyi take yi, ba zata iya magana da kowa sai shi, duk ta rasa natsuwarta wadda har da hawaye ta fara yi, ta shiga damuwa ainun, tana jin Irfan yana ta kiran ta amma ta ki ɗauka, a yadda take ji ma ba zata iya yin magana ba sabo ɗacin da zuciyata yake yi mata. Haka Irfan ya ga ji ya hakura ya kyaleta dan yana tunanin wata kila barcine ya ɗauke ta. Ita kuwa ta kasa barci har dare ya tsaya, daga karshe ma miƙewa ta yi zaune a tsakiyar gadon tana tunanin mafita, babbar damuwar ba tama da number sa bare ta kira shi ko ta yi mashi massage. Wasa wasa har ta kai karfe 2 dare tana zaune tana ruwan hawaye ta kasa runtsawa. Soyayya tabarmar kaya kenan, abin da Akila bata sani ba shine, asalin wadda zuciyarta yake so ba yaya Irfan bane ɓoyayyen masoyi ne, shi kuma yaya Irfan soyayyar yaya da kanwa take yi mashi, a nata tunaninta da yarinta irin tata a aboki ta ɗauki ɓoyayyen masoyi, bata san abin ya wuce haka ba. Sai misalin karfe 2:20 ya kira layinta, lokacin da kiran ya shiga a razane ta kai hannunta ta ɗauki wayar a saman bedside drawer, jikinta har kerma yake yi saboda tsananin kewarsa da kuma kaunarsa ya haɗu kuma da zumuɗin ya kirata yanzu. Da kyar ta iya picking na call ɗin sakamakon kerma da hannunta yake yi. Ko da ta ɗauki kiran shiru ya yi mata bai yi magana ba, muryarta har ya dashe saboda kukan da ta sha, can kasa kasa ta ce "Hello". Ya ɗauki tsawon minti 10 shiru bai amsata ba, ita ma shiru ta yi tana jin yadda yake motsi alamar akwai abin da yake yi, domin har karar Tv dake magana a kusa da shi tana ji, shine dai ya ki yin magana. Cigaba da kukanta ta yi tana goge hawaye da majina da tissue dake saman bedside drawer kusa da ita. "Kin dai san bana son kukan nan naki ko?" Shine abin da ya faɗa, kuma ya yi maganar kasa kasa kamar wadda baya son furta maganar. Cikin sauri ta goge hawayen nata tare da dakatar da kukan nata tana faɗin "Kayi hakuri". "Me yasa kika yi mani alkawarin da kika san ba zaki cika ba?". Zaro idanunta waje ta yi a ɗan tsorace ta ce "Me na yi maka kuma?" Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Daga yau na yi niyar fita daga harkarki amma kuma sai na kasa yin hakan, shiyasa kika ga tun da muka yi waya da safe ban sake kira ki ba, kuma ban turo maki sako ba saboda na saka a raina zan rabu da ke ne dan baki ɗauke ni da mahimmanci ba". Kuka ta sa mashi tana faɗin "Me nayi maka da zaka ce mani hakan?" A wannan karon da ɗan ɗaga murya ya fara magana kuma da alama ransa a matukar ɓace "Me yasa kika ce ba zaki yi wa Irfan dariya ba kuma kika yi mashi har ma da kwanciya a jikinsa? Me yasa zaki yi mani hakan? Kin dai san ina da kishi kuma na gaya maki tun da wuri, ni ban shiga hakkin ki ba na barki kina hira da shi dan naga kina son hira da shi ɗin, amma me yasa ke kuma zaki baƙanta mani rai har haka? Me yasa da kuka je wajen cin abinci kika bashi abinci a baki? Me yasa zaki bari ya taɓa jikin ki lokacin da ya goge maki ice cream a bakin ki? Kin san ya naji kuwa? Kinsan adadin tafasar da zuciyata ta yi kuwa? Kin san irin cikin azabar da na wuni yau kuwa? Do you know how much i love you kuwa? Meyasa kike kokarin tarwatsa mani zuciyata? Me nayi maki? Laifi nayi ne dan nace ina son ki? Amma dai ba komai dole na koyawa zuciyata kin ki ko zan huta!!". Sosai Akila take kuka kamar ranta zai fita, ta kasa magana saboda bata da abin da zata gaya mashi. Sun ɗauki tsawon minti goma a haka kafin ya ce "Heartbeat ki daina kukan nan haka ya isa bana son ji, kina kara mani ciwo akan ciwo kin ji ko?" A wannan karon ya yi maganar tasa cikin sanyin murya da kuma sigar rarrashi. "Heartbeat ba zan iya yin shiru ba, ba zan iya ba". Kara yin kasa da muryarsa ya yi cike da shagwaɓa da sigar rarrashi ya fara magana "Bana son kukan ki ko kuma in ganki a cikin damuwa, hakan kuma yasa ma na kiraki yanzu saboda naga kin kasa barci kina cikin damuwa har da kuka wadda nima zuciyata ta kasa juran hakan, ki daina ki yi shiru ko kuma nima na fara yi maki nawa kukan, kuma ni gaskiya ina da wuyar rarrashi gara ma ki sani". Kwanciya ta yi tare da rungume pillow a kirjinta ta ja bargo ta shige ciki tana faɗin "Heartbeat kasan wahalar da ni da ka yi yau kuwa? Tun karfe ɗaya na rana da na dawo cikin gidan nan nake cikin bakin ciki da ɓacin rai na ganin baka kirani ba, me yasa zaka yi mani hakan? Meyasa ka zaɓi ka wahalar da Heartbeat taka? Ko dan kasan na damu da kai ne? Muna hira da yaya Irfan amma kai nake tunani, komai nake yi fa kai nake tunani, why zaka yi mani hakan?". Nisawa ya yi kafin ya fara magana a nutse tare da yin kasa da murya cikin salo da zai nuna maka ya san me yake yi "Heartbeat duk wahalar da kika sha baki kai ni ba, yau zuciyata kamar zata fashe nake ji, na wuni cikin tashin hankali da rashin natsuwa, na sha wahala, idan na rufe idanuna kawai ke nake gani kina kwance a karjin Irfan kina yi mashi dariya, heartbeat ya kike so na yi da rayuwata ne? Baki san yadda nake da zafin kishi da kuma zafin zuciya bane shiyasa, wlh tun da naje school yau na kasa iya komai, duk lecture da aka yi mana a banza ya tafi, ban iya jin me suke faɗe ba, ke kawai nake tunani, ba zan ɓoye maki ba yau kin cutar da zuciyata sosai da sosai". "Na tuba ba zan kara ba ka ji? Kada ka sake yi mani hakan kai ma, idan ka sake yi mani hakan ya zo da karar kwana zan iya mutuwa wlh". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Nima kada ki sake rungumar wani a gaban idanuna ko da kuwa su Yaya Akil ne, bana so, ni kaɗai kawai zaki runguma, kuma ina nan zuwa har gida nan ba da jimawa sosai ba, amma dai ba yanzu ba kuma ba a kwanakin nan ba, za'a ɗan jima". Jinjina mashi kai ta yi tana kara tabbatar mashi ba zata kara ba ta tuba. To ya amsa mata da shi tare da tambayarta ina Ammie da Abba, Akil da kuma Imran. Su na ɗaki ta bashi amsa, kara tambayarta ya yi suna lafiya ko? Nan ma e ta amsa mashi da shi. Shiru ya ɗan yi kafin ya sake cewa "To ayi mani dariya mana ko zan ji sanyi a raina". Tana daga cikin bargon ta turo baki tana faɗin "Ni ba zan yi ba, kuma daga yau ma na daina yin dariya". "Kai innalillahi menene a bayan ki yake tafiyar nan heartbeat?!" Ya faɗa da ɗan karfi. Ihu ta kurma tare da miƙewa ta fito daga cikin bargon, a sukwane ta diro kasa daga saman gadon tana zare idanu kuma har lokacin wayar tana a kunnenta. Karo na farko data fara jin sautin dariyarsa mai ɗaukar hankali, tun da ta ji yana dariya tasan da gangan ya yi mata hakan dan haka sai ta sa mashi kuka ita kuma. "Am so so sorryyyyyyyyyy my heartbeat, na tuba ba zan kara ba, amma dai idan kika sake cewa ba zaki yi mani dariya ba to fin hakan ma sai na yi maki". Zama ta yi a gefen gadon tana dafe kirjinta dan har ga Allah ba ƙaramin tsoratata ya yi ba, a tunanin ta ma snake ne ko wani abin tsoron. Sosai ya shiga rarrashinta tare da bata hakuri yana kara gaya mata ba zai kara ba, da kyar ta yarda ta koma saman gadon ta kwanta tana zuba mashi shagwaɓa. Dariya ya yi yana gaya mata idan wani abin ne ma zai taɓa ta ai shine na farko da zai fara tare mata shi dan kada ya taɓa ta, to ta amsa mashi da shi Daga karshe dai shima shagwaɓar ya fara zuba mata abin gwanin burgewa dan ya iya shagwaɓa tare da rarrashin mace, duk abin da zai sanya mutun farinciki ya iya shi sosai, ga iya saka mutun dariya, hakan ma yasa Akila ta yi saurin kamuwa da kaunarsa ba kaɗan ba, hakan yasa ba zata iya jure rashin jin wannan zazzakar murya tasa ko kuma daddaɗar massages ɗin nan nasa masu kwantar wa da mutun hankali duk ɓacin rai ɗin da yake a ciki ba. Sun sha hira sun biya missed na juna da suka yi wunin yau, ba sune suka kwanta ba sai karfe huɗu na asuba sannan ne ya ce ta kwanta ta samu barci awa ɗaya da ya rage shi kuma bari ya yi nafilar da ta hana shi yi tun ɗazun, da haka suka yi sallama cike da kaunar juna, a wani ɓangare na zuƙatansu kuma suna bakin cikin zasu yi missing na juna. Suna katse kiran ta ɗaura wayar saman bedside drawer tare da runtse idanunta ba jimawa barci ya yi awon gaba da ita. Asuba ta gari, nima kuma na dasa aya sai gobe idan mai dukka ya kai mu zamu haɗu a Washington DC dan mu ji wani hali Musharraf da Aseef tare da su daddy suke a ciki....... Ma'assalam ✍️🥱 💖💖TRIPLETS💖💖 E83-84💖 💖WASHINGTON DC💖 Yau yana da class karfe 8 tun karfe 6 ya tashi ya nufi gym, good 1 hour ya ɗauka yana motsa jikinsa kafin ya sha ruwan lemon cup ɗaya sannan ya wuce ya koma cikin gida yana ta faman haɗa zufa. Kai tsaye toilet ya kufa ya yi wanka tare da fitowa ya shirya cikin shigarsa ta mutunci ta cikakken musulmi. Bayan ya kammala sai tashin kamshi yake yi, ya yi wani irin kyau na musamman, ba zaka taɓa cewa Michael na baya bane, ya zama cikakken gwarzon namiji, yanzu haka jikinsa ta fara murɗewa irin na ƴan uwansa saboda baya wasa da gym, safe da yamma dukka sai ya yi, da yake shi yafi siffantuwa da Lion yanzu sai ya dawo kusan kammanin Lion ɗin sak, kuma kamannin Josephine ya kara bayyana karara akan face nasa, da kallo ɗaya zaka yi mashi ba sai ka tambayi me a tsakaninsa da Josephine da kuma William ba saboda kammani, ta kowani ɓangare akwai Kamannin iyayen nasu a tattare da shi, kusan ma zaace shi kaɗai ne ya ɗauko kamanin su dukkansu, domin kuwa Lion dai da iya daddy kawai ya siffantu sai dai kama ta jini da idan ka gan shi ka ga Josephine zaka san e lallai akwai jini, shi kuma James ainahi da Michael ɗin suke ɗan kama, amma ba sosai can can ba, shi kuma Michael idan ka kalle shi kallon farat ɗaya sak fuskar Josephine zaka gani, idan kuma ka kalleshi da kyau zaka kalli fuskar daddy, kuma kunga Lion ya suffantu da daddy kaɗan shiyasa Michael yake kama da shi Lion ɗin, idanu kuma kowa da tasa, Lion dai idanun daddy ne blue eyes, brown eyes kuma na Josephine ne, dan ita ke da brown eyes irin na Michael, shi kuma James idanunsa irin na Tyson ne wato TGA kenan. Ƴan kwana biyun nan Aseef yana busy sosai saboda shirye shiryen Exams, baya zama sosai hakan yasa ya bar gashin kansa ta taru sosai har ta ɗan sauƙo mashi a bayan wuyarsa, kuma ba karamin kyau ta yi mashi ba, shine dai kawai baya so yake askewa. Yanzu ma tsayawa ya yi a gaban mirror yana ƙoƙarin fara rage tsawon gashin nasa, daga ta bayansa ya ji Musharraf yana faɗin "A'a my Aseef ka bar gashin nan dan Allah, wlh ba karamin kyau ya yi maka ba". Fuska ɗauke da kayatatcen murmushi ya juyo da kallonsa zuwa kan Musharraf ɗin yana faɗin "To shikenan Uncle ai duk abin da kake so nima ina son shi, yanzu dai ina kwana?". Murmushi Musharraf ya yi yana faɗin "Lafiya lou my pleasure what about you? How was your night?". "Am fine uncle, kasan me nake so da kai?" Girgiza mashi kai Musharraf ya yi alamar A'a. "Good, uncle tun da Allah yasa tafiyarka Nigeria yau bata yi wu ba sai jibi ina son daga yau zuwa jibin nan mu fita tare, akwai abubuwa da zamu je mu yi ciki kuma harda shopping zan je na yi maka". Jinjina kai Musharraf ya yi alamar to. "Okey uncle ka shirya da wuri mu fita tare ka je ka kalli school namu, daga nan kuma sai mu wuce yawo, yanzu dai je ka shirya bari na duba daddy mu gaisa" ya kai karshen maganar tare da wucewa ya nufi waje, shi kuma Musharraf ya wuce zuwa nasa bedroom ɗin. Aseef yana fita kai tsaye bedroom na daddy ya nufa, babu ko excuse ya faɗa cikin ɗakin, tsaye a gaban mirror ya isko daddy yana shafa mayukansa masu balain tsada da kuma kyau, kyakkywar farar towel ne ɗaure a kugunsa da alama wanka ya fito. Mutuwar tsaye Aseef ya yi yana kallon zanen tattoo dake a bayan daddy, zanen Lion ne wato zaki ita ce daddy ya zana a bayansa ta buɗe baki da waƴan nan zabga zabgan hakwaran nata, daga gefen kafaɗarsa kuma zanen kunama ne. Shi kuwa daddy jin an shigo mashi ɗaki ne yasa ya ɗago blue eyes ɗin nan nasa ta cikin mirror dan ya ga wanene, dama kuma ya san cewa Aseef ne, dan ba bu mai shigo mashi ɗaki da safen nan sai Aseef. "My son what happened? Why are you looking at me like this?" Ya faɗa yana ƙoƙarin juyowa. "Daddy I saw something like tattoo on your back". Ya faɗa da mamaki a face nasa. Jinjina mashi kai daddy ya yi alamar yah tabbas tattoo ne. "Daddy tattoo? Do you know what tattoo means?". Juyawa daddy ya yi tare da cigaba da abin da yake yi yana faɗin "Do you know my name before?". Girgiza mashi kai Aseef ya yi mamaki ya hana shi yin magana. "My name is dangerous Boss, i want you to know my story before, alokacin da nake da 20 to 35 year, mummyn ku ita ce first parson da ta fara sanya William ya risinar da kansa kasa, time da muke school yadda ka kalli Romeo haka nake, kowa tsorona yake ji a school, wannan tattoo da ka gani ba irin tattoo da kake tunani na shahrarrun ƴan iskan duniya bane, no wannan tattoo ne da yake nuna cewa mune manya a cikin school na mu a time ɗin, ni before ko wine bana sha, sanadiyar bakin cikin da mum ɗinku ta saka mani me yasa na fara shan wine dan na rage damuwa, a lokacin da muka yi tashe, muna kula da lafiyar mu sosai da sosai domin karantun lafiya kuke yi a time ɗin, duk soyayyar mum ɗin ku ya sanya na zama haka, lokacin dana fara ganinta a school ranar da ta fara zuwa a sabuwar student, faɗa ya fara haɗani da ita, bata san cewa mune manya a school ɗin ba, ta zo zata wuce ta jefar mani da ledar sweet a gabana, da nace ta ɗauke shine ta ki saboda tana ji da kai a lokacin ita ma, ni kuma zuciya ta ɗebeni na mareta, ai kuwa ita ma bata yi kasa a gwiwa ba ta ɗaukeni da marin da na kasa mantawa da shi har yau, dayawa daga cikin matan school namu suna haukar so na saboda kyan da nake da shi, kuma kowa yana tsorona amma sai ga mum ɗin ku ta mareni a ganan kowa da kowa, raina ya yi mugun ɓaci ba kaɗan ba, ban san time da na fara dukanta ba dan haushi, da kyar su HERRY suka ruƙe ni, daga nan ne fa muka saka kafar wando ɗaya da ita a school ɗin, kullun idan ta zo sai na takurawa rayuwarta, ga shi kuma kasa da mu take, lokacin muna kusa da shekarar kammala wa, ma'ana saura shekara ɗaya mu gama, na saka mata ido na dameta, duk abin da take yi sai na takura mata, daga takura ya zama soyayya har ya kai mu ga aure, abin da ya sa kaga ban cire tattoo ɗin nan ba saboda ina tuna lokacin samartakan mu, mu biyar ne a lokacin, amma yanzu uku sun mutu remain me and herry, sannan wannan kunamar da kaga na zana a kafaɗata ba ni na yi ba, mummynku ta zana mani da hannunta, ina matukar kaumarta fiye da tunaninka, shiyasa na kasa goge wannan tattoo ɗin dan ita ta yi mani kuma tana kaunar shi, shiyasa na barshi dan in rinƙa tunata da shi, mutuniyar kirki ce, daga baya ne ta canza kamar ba ita ba". Ya kai karshen maganar yana hawaye, da sauri Aseef ya kariso wajensa tare da fara rartashinsa yana bashi hakuri, rungume juna suka yi. Sun ɗan jima a haka kafin nan Aseef ya sake shi yana gaya mashi zai ta fi school, to ya amsa da shi suka yi sallama Aseef ya manna mashi kiss a goshi kafin shima ya mannawa Aseef ɗin a kumatu, Aseef yana matuƙar kaunar daddynsa while shima yana kaunar ƴaƴan nasa, Allah ne kawai yasan dalilin da yasa su basu wani son shi sai Aseef ɗin, shima Aseef dan yana sabon mutun ne Shiyasa, babu komai a ransa sai kaunar mutane. Aseef na fita daddy ya zauna saman table chair yana hawaye, yau ya tuna da soyayyarsa ta baya, ya tuna irin diramar da suka kwasa da Mummynsu a school, tsumin soyayyarta ta taso mashi, ji yake yi kamar ya ganshi ga shi ga ita sun koma kamar lokacin da suke zuba soyayya a school nasu, mum ta haɗu over, daga baya kuma kome ya tuna sai ya goge hawayen nasa ya miƙe ya cigaba da abin da yake yi kamar ba shi ba. Shi kuwa Aseef yana fita part nasa ya koma. A palo ya isko Musharraf yana tsaye ya shirya cikin kananan kaya, ya yi kyau over, sosai Aseef ya ya bawa kyan da ya yi sannan suka jera suka fita zuwa palon kasa. "Uncle mu wuce ko mu tsaya mu yi breakfast?" Cewar Aseef. Musharraf na ƙoƙarin amsa mashi magana sai suka ji uncle Herry ta bayansu yana faɗin "Michael wai ya har yanzu TGA shiru ne?". Juyowa Aseef ɗin ya yi yana kallonsa fuska ɗauke da murmushi ya ce "Uncle Herry uncle T yana nan dawo soon, wani aiki suka tafi" to uncle Herry ya amsa da shi. Dawo da kallonsa kan Musharraf ya yi yana kara tambayar shi, shin su yi breakfast ne ko dai su wuce kawai, da yake Musharraf ya san halinsu sarai basu cin abinci a waje dan tsabar shegen kyankyani da suke da shi kamar me, basu yarda su ci abincin da wata hannu ta girka bayan sojojin gidan, suma sojojin dan saboda suna kallon duk yadda suke yi masu girkin ne Shiyasa, suna kallon komai a tsabtace suke yin sa, ba dan haka ba da ba zasu iya ci ba, Triplets gabaɗayansu ne masu wannan shegen kyankyani kamar me, harta James mai ɗan saukin kan, idan kana son ka ga ɓacin ransa to ka kawo datti a filin da yake, yanzun nan zai haɗa maka jini da majina a fuska, sun yi mugun tsanar abin kyama ko datti. Musharraf ya san ko sun fita Aseef ba zai taɓa yarda ya ci abinci a wani waje ba, sai dai ya kai Musharraf ɗin wajen cin abinci shi kuma ya zauna har sai sun dawo gida ya ci, yasan halinsa sarai, sanin hakan yasa ya ce a'a su hakura su yi breakfast a gida tukun nan su fita, to Aseef ya amsa da shi sannan suka nufi dining room shi kuma uncle Herry ya koma bedroom nasa. Suna zuwa wajen waƴan nan jibga jibgan bodyguards ɗin suka fara sara masu kamar yadda sojojin gidan suke yi masu. Shafa kumatun ɗaya daga cikin bodyguards ɗin Aseef ya yi yana faɗin "Wai ku bakwa gajiya da tsayuwa ne? Haba mana ku rinƙa samun huto, kowace rai tana son hutu fa my people's". Mamaki ne ya kama bodyguards ɗin nan, har wani kallon kallo suke yi wa junansu. Zama Aseef ya yi yana faɗin "Bodyguards shidda kuje ku kwanta ku huta idan karfe 2 na rana ta yi sai ku zo ku karɓi ƴan uwanku shiddan nan suma su je su huta sai can dare ku haɗu gaba ɗaya ku kwanta ku huta. Abin nufi a nan Aseef ya raba masu aikin kenan, bawan Allah mai adalci yanzu kwata kwata baya son yaga wani ko wata suna wahala, Allah sarki musulci duniya ne wlh, babu abin da ya kai shi daɗi, kuduba kafin ya musulta shine fa yake cewa zai yankewa masu girki hannu da wuƙa, yanzu kuma ya musulta yau an wayi gari har hira da wasa da dariya yake yi da su, Allahu Akbar, Allah Alhamdulila da ya kasance muna a cikin adddinin musulci, zama musulmi babbar ni'ima ce wadda ba kowa yake samun wannan damar ta ni'imar ba. Tsabar mamaki da farinciki bodyguard ɗin nan sun kasa magana, sai kallon juna kawai suke yi. Ganin haka yasa Aseef ɗin ya sake ce masu "Mamakin me kuke yi? Ni ɗin dai Michael nine, kuma nine na baku wannan hutun, duk kuma wanda ya zo saman table ya ce ina sauran, ku ce nine na basu hutu, wai ni kam shin mu nawane ma a gidan nan da bodyguards uku ba zasu isa su yi serving namu abinci ba? Kawai dai sai an wahalar da bayin Allah a rayuwar nan ta duniya, kai kaɗai sai ka ce sai ka tattare komai ya zama naka, to idan da kowa sai ya tattara komai ai da mu kam ma kwata kwata duniyar ma ba zamu zo ba, Allah mai iko, to daga yau ma na raba ku, bodyguards huɗu ne zasu yi serving na abincin safe, idan mun gama breakfast su tafi suje su kwanta su huta, sai kuma idan lokacin cin abincin rana ta yi, kafin mu zo saman table sai bodyguards huɗu waƴan da zasu yi serving abincin rana su kuma sai suzo su kara gyara table ɗin kafin mu zo, da daddare ma haka, kun ga ku sha biyun nan kowa da hurhuɗu zaku yi aiki". Zube gwiwowinsu a kasa suka yi tsabar murna da farinciki har da hawaye suka yi, bayin Allah ashe suna gajiya da tsayuwar da suke yi na 24 hours ɗin nan, ashe suna shan wahala sosai. Ganin sun zube a hasa suna hawayene yasa Aseef ya miƙe shima ya tsugunna a gabansu yana tambayarsu ko lafiya? Ko dai hutun ne basu so?". Har wani ja baya suka yi ganin shima ya zube gwiwowinsa a ganansu, sun tsorata sosai, addu'a suke yi kada Lion ya ga Michael ya zube a gabansu ko wani daga cikin gidan ya ce sun yi wa Michael ɗin wani abin ne a kashe su a banza. Da kyar Aseef ya shawo kansu suka yarda suka kuma gane cewa e lallai Aseef ɗin ne, kuma shi ne ya zama mai adalci haka, sun yi murna sosai, Aseef bawan Allah da kansa ya yi ta goge masu hawaye yana mai gaya masu addinin musulunci addinine wadda ya ƴanta ko wani ɗan adam, dan haka suma ƴantattune, suna da ƴanci, nan take biyu daga cikinsu suka ce ai sun san addinin musulunci sosai, suna ƴawan ganin musulmai a Media sun san musulmai suna da kirki sosai, addinin akwai adalci sosai dan haka su zasu musulta. Ba karamin daɗi Aseef ya ji ba, a wajen ya basu kalmar shada tare da basu kyautar makudan kuɗaɗe, sosai su ka yi farinciki fiye da tunanin mai tunani, su kuma sauran sai nazari da tunani suke yi akan addin. Da haka Aseef ya ce suma waƴan da basu musultar ba su bashi account number bari ya yi masu kyauta domin yau ranar sadaka ce, yau duk sadakar da zai yi yana fatan Allah ya bawa Musharraf ladan, uncle Musharraf zai yi wa sadaka. Haka kuwa akayi, dukkansu saura goma da basu musultar nan ba sai da Aseef ya sanya masu kuɗi a cikin account nasu, sannan ya ce huɗu su tsaya a wajen table saura takwas ɗin kuma suje su huta wa ransu sai da rana. Da haka suka yi sallama Aseef ya ciro wayarsa ya kira number Lion. Yau karo na farko a duk rayuwar da Aseef ya yi da Lion yau ita ce rana ta farko da ya kira Lion kira ta farko ya ɗauka, wannan shine zai nuna maka Lion yana cikin damuwa, domin dama ya faɗa maku Aseef ne kawai mai ɗebe mashi kewa da kuma rage mashi damuwar da yake a cikinta, mutane sun kasa ganewa duk tarin makudan dukiya da kake da shi ba zata iya yi maka komai ba idan kana cikin wata matsala ko jarabawa ta Ubangiji, amma sai mutane su dage sai sun yi kuɗi ta ko wace hanya, su dai kuɗi kuɗi kawai, suna ganin kamar shi ne kwanciyar hankali da farinciki, tabbas kuɗi yana sanya farinciki kuma yana maganin wata damuwar, amma fa ba kowanne ba, kuma idan ta hanyar da bata dace ba aka sami kuɗin sai ma karawa mutun azaba da zai yi a maimakon maganin matsala, kuɗi bata isa ta warware maka kaddarar da Ubangiji ya ɗaura maka ba, yanzu tambaya a nan shine wani irin kuɗi ne su Lion basu da shi? Ga kuɗi ga mulki isa da duk wani abin da bawa yake ganin shine jin daɗin duniya, sune ke mulkar kasar baki ɗaya tun da kakansu ke a kan kujerar president, ga Lion da babbar muƙamin da babu biyunsa, sannan ga jarumta na iya tunkarar komai da zai kawo masu matsala, uwa uba ga makudan kuɗaɗe da su kansu basu san iya kan shi ba, amma kuma sai me, ga shi dai kullun suna cikin damuwa, daga Lion har James ɗin kullun suna cikin damuwa, Aseef ne kawai bawan Allah wadda bai san komai ba sai kaunar mutane, shine kawai yake cikin farincikin da har yake sanya ƴan uwan nasa farinciki, yanzu wani idan ya ga mutun irin Lion ko ya ji labarinsa sai ya ce shikenan su kam ba zasu taɓa shiga damuwa ba, dan suna da kuɗi, to ga dai shi nan kullun cikin binciko wani matsalar suke yi suna shiga damuwa. "Hello Lion" kamar dai kullun wannan halin tasa tana nan idan aka yi mashi magana sai ya jima kafin ya amsa. "Aseef what is going on?" Shine abin da Lion ya tambaya bayan ƴan mintoci kenan. "Lion please ina son kasa Tyrone ya tura wa duk wani maaikacin da muke biya albashi a gidan nan sadaka, tun da shine dama mai biyansu albashi, a hannunsa komai yake, to ya sanya masu kuɗi a account nasu da nufin Allah ya bawa uncle Musharraf lada ka ji ko?" Shiru Lion ya ɗan yi na ƴan mintoci da ba za su wuci 5 ba. Can kuma sai ya ce "Okey what about your Exams?" Nan Aseef ya gaya mashi e next week zai fara exam ɗin yanzu ma school zai ta fi, to Lion ya amsa da shi tare da ce mashi ya kula da kansa, daga nan suka yi sallama. Yana ajiye wayar suka fara cin abinci shi da Musharraf a cikin plate ɗaya saboda tsananin kaunar juna da suke yi, sauri sauri suka ci abincin dan karfe takwas ta kusa. Suna kammalawa suka wuce izuwa parking space na gidan. Yau ma dai tare da su Lucky Aseef ya tafi, sai dai kuma yau su Lucky dukkansu a gidan baya suka zauna, uncle Musharraf ya zauna a gidan gaba. Da gudu Aseef ya figi motar suka hau titin zuwa bakin gate ɗin gidan, basu wani ɓata lokaci ba suka fice daga gidan. Sai da suka fita Aseef ya tuna bai bawa Brady abinci ba, hakan yasa ya juyo da kan motar ya dawo ya ba shi abincin, dan ya san Brady baya yarda da kowa a gidan idan ba Lion ba sai kuma shi, to ko wani ya kai mashi abinci ma ba zai ci ba. Bayan ya bashi abincin ne kuma suka wuce Harvard University. Suna zuwa Aseef ya kai Musharraf office ɗin ɗaya daga cikin malamansu wanda suke shiri da shi sosai, da ya kai shi ma sai da ya gayawa uncle ɗin nasa ya kula mashi da uncle Musharraf sosai da sosai bari ya yi attending lecture yana zuwa. Da haka suka yi sallama ya bar su Lucky kuma a wajen motarsa suna gadi. After 2 hours ya dawo ya ɗauki Musharraf suka bar school ɗin zuwa shopping kamar yadda ya faɗa. Sosai Musharraf ya ɗauki duk kayan da yake so, ciki kuma har da jallabiyas da dama, bayan shi kuma ya kwashi tsaraba yadda yake so, yana ɗauka Aseef yana kara mashi wani, duk abin da ya ɗauki guda ɗaya sai Aseef ya kara mashi uku akansa. Sun zo daidai wajen sayar da kayan sanyi Aseef ya yi karo da wani black guy, ɗan baya kaɗan Aseef ya yi kafin ya ce sorry, shi kuma guy ɗin sai ya ce kayi hakuri sannan ya wuce, shiru Aseef ya yi yana kallon guy ɗin har ya wuce yana kuma maimai ta kalmar kayi hakuri da guy ɗin ya ce. Taɓa shi Musharraf ya yi yanan faɗin "Kana mamakine dan ka ji ya yi Hausa?" Juyowa ya yi yana faɗin "Uncle Musharraf what is Hausa?" Nan Musharraf ya gaya mashi Hausa tana ɗaya daga cikin yarukan Nigeria. Murmushi ya yi yana faɗin lallai sai an koya mashi yaren nan, ko Musharraf ya koma za su rinƙa yin lecture Hausa ta waya, to Musharraf ya ce, kuma ya ji daɗi zai koyawa ɗaya daga cikin TRIPLETS Hausa. Haka suka kammala sayayyarsu suka wuce zuwa masallaci domin azahar ta yi, ko da suka je Masallaci a mota suka bar su Lucky su kuma suka shiga ciki. Bayan sun idar da sallah ne suka fito, suna fita suka haɗu da Aryan yana ƙoƙarin shiga Masallaci hannunsa na riƙe da kwalin dabino mai ɗan girma. Ganinsu yasa ya kariso wajen da sauri dan yanzu ko Aseef yana sanye da face mask Aryan ya riga da ya san shi, yana gane shi, su kuma Triplets dama duk in da zasu je da face mask a fuskarsu. Yana zuwa Aseef ya miƙa mashi hannu suka gaisa yana tambayar shi akan me bai zo ya yi sallah a cikin jam'i ba? Ya yi maganar kuma yana karɓar dabinon sadaka dake a hannun Aryan ɗin, ko wace rana Aryan yana zuwa da dabino ya raba sadaka yana addu'ar Allah ya kai wa Aseef ladar, dan Aseef ya yi masu komai a rayuwa, yanzu ga shi shagon da Aseef ya buɗe masu ta kara kirman sosai saboda sada da suke yi tare da kyautatawa al'ummar Annabi. Aryan bai taɓa tunanin cewa Aseef zai ci wannan dabino ta sadaka ba, sai kuma ya ga ya deɓi guda shidda ya bawa Musharraf uku ya riƙe uku, duk da yake dabinon a wanke take sai da Aseef ya sake wanketa tas sannan ya sa ɗaya a bakinsa yana yi wa Aryan faɗa akan ko me yake yi kada ya kuskura ya sake bari Sallah ta sake wuce shi, idan ba haka ba zai bashi hukunci mai tsanani domin yanzu a kani na jini Aseef yake ɗaukar Aryan, shiyasa idan ya yi ba daidai ba Aseef ɗin yake cewa zai hukunta shi. Hakuri Aryan ya bashi tare da yi mashi alkawarin In Sha Allah sallah ba zata taɓa sake wuce shi ba, zai rinƙa ƙoƙari ya zo akan lokaci, yanzu ma toilet ya shigane Shiyasa, amma ya zama dole ya rinƙa bin jam'i matukar yana son cigaba a rayuwarsa. Jinjina kai Aseef ya yi kafin su sake gaisawa da Aryan ɗin daga nan kuma suka rungumi juna, bayan sun raba jikinsu ne kuma Aryan ya rungumi Musharraf dan shi Aryan a yayan Aseef yake kallon Musharraf, bai damu da cewa Musharraf baki ne akan hasken Aseef ba, shi dai kawai tun da ya gansu a tare kuma kullun suna a tare shikenan, amma fa batun kyau, Musharraf fa kyakkywar gaske ne, shiyasa da farko JAMES ya kira shi da balarabe, kuma yana ɗaya daga cikin dalilin da ya sanya Aryan ya yi tunanin ko dai yayan Aseef ɗin ne dan kyau dake a gare shi shima. Sallama suka yi Aseef ya ce Aryan ya je ya yi sallah kada lokaci ta kure, to ya amsa tare sa wucewa cikin masallaci, su kuma suka sauƙo kasan stap ɗin zuwa wajen motar su. Kamar yadda aka saba jama'a ne sosai suka taru a wajen motar suna jiran isowarsu dan Aseef ya saba yi masu sadaka, yana zuwa kuwa ya zaro kuɗi ya fara raba masu kamar ko da yaushe, yau duk sadakar da ya yi yana addu'ar Allah ya bawa Musharraf ladan ne. Sosai yau ma ya yi sadaka, sai da ya sanya gaba ɗaya mutanen dake a wajen farinciki sannan suka shiga mota zuwa gida. Suna a kan hanya ne yake gayamawa Musharraf gobe kuma a account ɗin Areef zai ɗebi kuɗi ya zuba a account nasa dan kuɗin sa ya yi kasa, kuma ya ga ji da karɓar kuɗi a wajen Lion, zai bar Lion ya sha iska na kwana biyu, yanzu zai koma account ɗin Areef daga nan kuma sai account na uncle T, duk sai ya kwashi kuɗinsu ya yi ta sadaka ko Allah zai sanya suma su musulta, bare ma uncle T. Sai dariya Musharraf yake yi mashi tare da yi mashi addu'ar Allah dafa mashi ya gama karatun shi shima ya kama aiki dan ya tara kuɗin kansa, dan ma Allah yasa ƴan uwan nasa suna matukar kaunar junansu, kuma basu damuwa dan wani ya taɓa dukiyarsu ma bare kuma shi da yake cikonsu, wata zubin daddy da kansa yake cewa Aseef ɗin ya zo ya ɗebi kuɗi a account nasa iya yadda zai buƙata, da yake daddy ba abin da yake yi da kuɗin suna zaune, tsawon shekaru yana aiki, ya tara makudan kuɗaɗe, kuma yanzu ma kullun sai kuɗi ta shigo Account nasa saboda babbar hospital ɗin dake Washington DC tasa ce, shi ya gina kayansa da kansa, kullun cikin kuɗi yake ko bai je aiki ba, ga uncle T shima akwai kuɗi sosai, kuma dukkansu Aseef ya san sirrin bankin su, dan shine bashi da aiki sai dai a bashi kuɗin, shiyasa dan ya rage masu wahala suka nuna mashi komai na daga siririn account nasu, ya ciri kuɗi time da yake so dukka ga card nasu a cikin ɗaki. Suna zuwa gida ya fara mayar da su Lucky ɗakin su kafin nan ya wuce izuwa part nasa, soja ɗaya ne ya kwasan musu sayyayar da suka sawo izuwa part nasu. Aseef yana shiga toilet ya wuce ya yi wanka sannan ya zo suka ci abincin rana bayan shima Musharraf ɗin ya yi wanka kenan. Bayan sun gama cin abinci ne suka zauna Aseef ya ce Musharraf ya fara koya mashi yaren Hausa, to Musharraf ya amsa da shi sannan suka fara da gaisuwa. Idan Musharraf ya ce ina kwana sai Aseef ya ce innkowa saboda harshen a lanƙwashe take ba ta taɓa furta kalma makamanciyar Hausa ba, abin ma dariya ya rinƙa bawa Musharraf har da hawaye saboda dariya, kunsan idan aka ce yare ba naka ba to fa sai a hankali zaka sha wahala wajen iya furta shi, ai kuwa Aseef dai ya sha bakar wahala har haɗa zufa ya yi wajen dole dole sai ya yi hausa shi. Wunin ranar dai a haka suka wuni a koyan Hausa, kuma a iya gaisuwa kawai suka tsaya, shima bai zauna daidai ba kawai dai ayi sha'ani. Har lokacin sallar la'asar ya yi sannan suka wuce masallaci, daga masallaci kuma suka wuce yawata gari dan Musharraf ya ga koina kafin ya koma, har white house sai da Aseef ya kai shi, amma fa da suka je white house Musharraf ya ga ikon Allah, domin kuwa ya ga yadda ake nuna kiyayya karara, karara suka nuna mashi kiyayya dan shi bakar fata ce a cikinsu, da Aseef ya lura da haka sai ya ce su tafi kawai dan baya son hayaniya kuma baya son abin da zai ɓatawa Musharraf ɗin rai, shima Musharraf ɗin tafiyar ta fi mashi alkhari. Suna barin white house suka sake lulawa duniyar yawo har cikin New York basu bari ba.........nu kuma na haɗa kayana zuwa NIGERIA dan na ga me yake gudana, wata kila kafin mu dawo su Musharraf ma sun dawo. # GIDAN LION🦁 Yau dai Rimsha ta riga Imran tashin daga barcin safe, ba laifi kafar tata ta ɗan sake ta, ita kuwa jelly ko tashi sallar asuba ta kasa yi, Imran ba dan ya so ba ya kyaleta ta cigaba da barcinta. Misalin karfe 7 na safe Rimsha ta fito, ta ci wankanta cikin wandon jeans palazo, ta kasa a buɗe ta sama ya matseta, sai ƴar T-shirt da ta sanya a jikinta, ta yi kyau matuka kamar ba ita ba, yanzu da yake tana girma wani sihirtaccen kyau take karawa, ga shape nan kamar me ba'a magana, akwai hips irin mum ɗinta, sannan akwai tula tulan breast irin na gwaggo, ga breast ɗin tata a sama sannan ga su da faɗi sosai alamar ba zasu kwanta ba, komai zamzam tamkar ita ta yi kanta, sai tashin wani fitinannen kamshi take yi, da kyar ta sha bakar wahala ta ɗaure wannan curly hair nata, yana da tsantsi sosai baya ɗauruwa ta daɗi, bayan ta ɗaure shi sai ta sanya turban cap a kanta mai shegen kyau launin blue kalar jeans ɗin jikinta, shi kuma rigar jikinta karine tas kamar yanzu ta ciro shi daga ladarsa. Tana fito palon sama ta nufi hanyar sauka izuwa palon kasa, har zata wuce sai ta hango bedroom na Lion a buɗe, lallaɓawa ta yi ta nufi wajen da nufin ta leƙa ta ga ko zata samu ganinsa, ai kuwa bata kai ga leƙawa ba ta ji takun manya ta bayanta yana haurowa saman benen, ya je ne dama ya bawa Areef magungunansa da Dr Tyrion ya bada ya rinƙa sha, an samu an yi mashi aiki cikin nasara yanzu sauƙi kawai suke jira. Ai kuwa ko ba'a faɗa mata ba tasan cewa tabbas Lion ne mai wannan taku, da wani irin mahaukacin gudu ya watsa ta shiga bedroom nata, tana shiga shi kuma yana shigowa cikin palon, lumshe dara daran blue eyes ɗin nan nasa ya yi, tabbas ya ga geftawar abu kamar mutun ya shiga bedroom nata, sai dai bai san daga ina ta fito bane. Shiru ya ɗan tsaya, jikinsa na sanye da wasu irin kaya masu haukata kwakwalwar wadda ya kallesu, riga da wando ne dukka iri ɗaya, launin ash color mai ashe ne, sai walwali kayan suke yi, rigar ya yi kamar T-shirt amma ba t-shirt bane, suna da bala'in laushi sosai, da alama kuma kayan barci ne, sai tashin wannan sihirtaccen kamshin nan nasa mai kwantar da hankalin mai shaƙa yake yi, ya ɗaure dark black curly hair nan nasa a bayan wuyarsa, sannan ya bar wannan guntu na gaban goshin, kallo ɗaya zaka yi mashi ka gane jikinsa a mace yake domin kuwa ga shi nan dai sai wani faman lumshe idanu yake yi kamar mai jin barci. Bedroom nasa ya shige domin kuwa kwakwalwarsa ta gaya mashi wace ce ta gifta ɗin, dan yasan ba Imran bane, bai damu ba saboda yasan ai tana zuwa wajen Imran, so ya yi tunanin daga ɗakin Imran ɗin ta fito. Ita kuwa tana shiga bedroom nata ta laɓe a bakin kofa tana kallonsa ta mahangar kofar, shi kuma baya ganinta, a yaune ta samu damar kallon fuskarsa sosai a zahiri, ba a camera ba, ba kuma a hoto ba, wani irin sake haukacewa da kaunarsa zuciyarta ta yi, ji take yi kamar ta je ta rungume shi, har wani zogi zuciyarta take yi mata, baiwar Allah. Ta jima tsaye a wajen tana tunani kafin ta sake fitowa ta nufi palon kasa. Babu kowa a palon dan haka sai ta shiga cikin kitchen ta ɗebi fruits a wani kyakkywar plate mai shegen kyau da tsada ta fito ta nufi waje harabar gidan baki ɗaya. Tun da ta fito sojan dake tsaron gate ɗin nan ya zuba mata idanu, yana zaune shi da Mark kamar dai jiya, sai hira suke yi. Ganin ya yi shiru yana kallon wani waje ne yasa Mark ya juyo dan ya ga me yake kallo ya ɗauke mashi hankali haka, ganin ita ce kamar wata tauraruwa a tsakiyar duhun dare ne ya sa ya daka mata tsawa akan ina zata je? Jikinta har ya soma karma ta ce garden zata je, daga nan bai sake yi mata magana ba ta wuce ta nufi garden ɗin, shi kuma gate man ya bita da ido kamar wani tsohon maye yana wani lashe baki. Sai da ta kure wa ganin sa ne ya ce "Mark i really like this girl, she is so cute". Shiru Mark bai yi magana ba kuma bai ɗago ya kalle shi ba, sauƙe ajiyar zuciya ya yi yana mai sake maimai tawa Mark abin da ya faɗa. Sai lokacin mark ya ɗago kai cikin sanyin murya ya ce "You are not serious, Sister babbar aminin oga ce fa, ban taɓa ganin oga ya tsaya yana magana da wani kamar yadda suke magana da brother ɗin yarinyar can ba, ko tsawar da na daka mata yanzu ma dan na san ba wanda zai ji ne shiyasa, amma ba dan haka ba da ba zan yi mata ba, zan baka shawara kada ka bari idanunka ya sake kallon yarinyar nan, if not lahira zata yi baƙo, kasan dai yadda oga yake kaunar brother ɗinta dole idan abu ya sameta bro ɗin nata ya shiga damuwa, idan kuma ya shiga damuwa dole oga zai tanka maganar dan na lura baya son yaga friend ɗin nasa a cikin damuwa, to ni dai na baka shawara idan ka ɗauka ka tsira akasin haka kuma ka san sauran". Shiru gate man ya yi yana nazarin maganganun Mark. Ita kuwa saman ɗaya daga cikin kyawawan kujerun dake a wajen ta je ta zauna, wani irin daɗi ta ji lokacin da hancinta ya shaƙo mata kamshin perfume ɗin Lion, alama ya nuna yana yawan zama a wajen kenan, dan kuwa gaba ɗaya wajen kamshin perfume nasa ne yake tashi. Cikin natsuwa ta fara yankawa kanta fruits ɗin tana sha, already a wanke suke daga fridge ta ɗebo su. Har wani lumshe idanunta take yi daɗin apple na ratsata ga kamshin perfume ɗin abin begenta dake karawa abin armashi. A ɓangaren su Imran kuwa sai karfe 9 jelly ta farka daga nauyayyar barcin da take yi, Imran bai san ma tana period ba shiyasa ma ya yi kokarin tashinta da asuba ta yi sallah. Tana buɗe waƴan nan dara daran idanun nata kai tsaye sai cikin idanunsa, yana zaune a tsakiyar gadon ya tsareta da ido tana kallonta. Sai tashin kamshi yake yi, ya yi wanka ya shirya cikin wata dakakkiyar shadda milk color. Wani kayatatcen murmushi ta sakar mashi tana faɗin "Yaya Imran baka tashe ni ba sai da na tashi da kai na". Shima murmushin ya sakar mata kafin ya ce "A'a na tashe ki mana, ke ce dai kin gaji sosai kika ki tashi". Turo ɗan bakin nan ta yi, a shagwaɓe ta ce "Yaya Imran wajen daddyn fa?" "Tashi ki je kiyi wanka ki yi sallah ki shirya mu tafi". Miƙewa ta yi tana faɗin To. Sai kuma me tana tashi suka kalli jini a wajen da ta kwanta, ihu ta kurma mashi tare da rungume shi dan tana mugun tsoron jini, kuma a tunaninta ciwo ta ji, idan ta ga jini har jiri take gani, shima dai rungumeta ya yi yana mamakin daga ina wannan jinin kuma. Bai kai ga yin magana ba ya ga jinin gaba ɗaya ya ɓata mata kayan jikinta, a nan ne ya gane jinin menene sai dai kuma matsalar ta yaya zai yi mata bayani ta gane dan yasan halinta sarai. Can dai wata dabara ta faɗo mashi akan ya kira Akila ko kuma Rimsha ɗaya daga cikinsu ta yi mata bayani, dan yasan idan su ne suka yi mata magana zata ɗauki maganar da mahimmanci saɓanin shi da suke tare a baya ko da yaushe. Haka kuwa aka yi, ya kira layin Akila bata ɗauka ba lokacin tana waya da ɓoyayyen masoyinta, kiran Rimsha ma ya yi a waya, a lokacin ita kuma ta gama shan fruits nata har ta dawo cikin gida tana kwance a bedroom nata, bugu ɗaya ta ɗauka ya ce ta zo ɗaki ta same shi, to ta amsa mashi da shi sannan ta fito ta zo. Jelly na kwance a jikinsa tana kukan bata son ganin jinin nan, mamaki ne ya kama Rimsha akan wace ce jelly kuma. Alama ya yi mata da hannu akan ta kariso saman gadon, da sauri ta kariso. Cke da jin kunya ya gaya mata abin da yake faruwa da kuma wace ce jelly sannan ya ɗaura da cewa ta yi wa jelly'n karin bayani akan jinin. Abin da bai sani ba shi ne ita ma Rimshan bata taɓa yin period ba, shekarunta 14 ita kuma jelly 16, jelly ita ce sa'ar JEHAN 16 suke da shi, amma dai da yake ta yi karatun addini sosai, kuma ta samu karin haske wajen mummynta sai ta amsa mashi da to. Da kyar Jelly ta yarda ya saketa ya fice daga ɗakin dan ya basu waje su ji daɗin yin magana, ya san halin Rimsha sarai da shegen kunya, idan yana nan ba zata yi wani magana ba. Yana fita ta riƙo hannun Jelly ta fara yi mata bayayi ta yadda zata fahimta, a nan ne Rimsha ta fahimci e tabbas ita ma jelly ta karanta, sai dai rashin uwa ne yasa bata samu wanda zai iya fayyace mata komai ba, ita dai ta karanta mace tana jini kamar yadda suma su Rimshan suka karanta, Allah dai ya taimaka su mummy ta yi masu dalla dalla yadda za su fahimta ne shiyasa suka iya gane komai. Sosai Jelly ta fahimta sannan Rimsha ta riƙe hannunta ta sauƙo kasan gadon ta nufi toilet dan yin wanka, ita kuma Rimsha sarkin son tsab ta gyaran bedroom ɗin ta fara yi tare da cire bed sheet ɗin ta sauya wata. Kafin jelly ta fito ta gyare ko'ina tsab tare da feshe ko'ina da air freshener masu daɗin kamshi, ita kanta jelly da ta fito sai da ɗakin ya burgeta ina ga kuma Imran. Zama ta yi a saman mirror chair tana kallon mayukan Imran dan bata ma iya shafawa ba, idan baku mance ba komai daddy ne yake yi mata, ba abin da ta iya sai karatun makaranta kawai, ko abinci a baki daddy yake bata. A takaice dai daga karshe Imran shi ya zo ya shafa mata mai sannan ya ce Rimsha ta kawo mata kayanta kala ɗaya doguwar riga mai ɗan girma wadda zai yi wa Jellyn, domin kunga jelly ta girmi Rimsha. To Rimsha ta amsa da shi sannan ta nufi hanyar fita daga ɗakin, har zata fita sai kuma ya ce mata ta shirya yanzu za su je gidan Abbi, da murna ta amsa mashi da to sannan ta fice. Bayan ya gama shafa mata mai ɗin ya ɗago yana karewa surar jikinta kallo, daga ita sai towel a kirji wadda bai gama rufe mata cinyoyinta ba, wani irin yanayi ya shiga lokaci guda, ita kuma bata ma san yana kallonta ba, hankalinta na can wajen mirror tana kallon face nata, ita da kanta ta yi wa kanta kyau bare kuma shi, shi kuwa ji yake yi tamkar ya........Kayarsa, ya ƙosa su je wajen daddy a shafa fatiha ko kiss ne ya samu ya yi mata ko zai rage zafin da yake ji. TOH FAH TEAM ƊIN IMRAN, ANYI WALKIYA MUN GANKU, ASHE DAMA HAKA KUKE? DAMA WATO DAN RASHINTA A KUSA NE YASA KUKA KOMA SO SILENT KO? E LALLAI AKWAI AIKI A haka Rimsha ta dawo ta same su, hannunta ɗauke da abaya pink color, ita ma ta sauya kayan jikinta zuwa abaya black color tare da yafa gyalen abayar a kanta, ba ƙaramin kyau ta yi ba. Jin sallamar ta ne yasa Imran ya dawo hayyacinsa tare da miƙewa ya fice daga cikin ɗakin da sauri yana faɗin su shirya su same shi a wajen motarsa, to suka amsa mashi da shi. Kayan ma jelly bata iya sawa da kyau ba sai da Rimsha ta taya ta, godiya ta yi mata tana tambayarta sunan ta, "Sunana Rimsha". Ta bata amsa, sake maimai ta sunan jelly ta yi sunan ya yi mata mugun daɗi. Bayan sun kammala suka fita zuwa parking space na gidan, zaune cikin mota suka isko shi yana jiransu, ya je ya yi sallama da Lion ya kuma duba jikin Areef sannan ya dawo cikin motar ya zauna. Gidan baya Rimsha ta je zata shiga, cikin sauri ya ce mata A'a ta dawo gidan gaba su haɗu su biyun dukka, to ta amsa da shi tare da dawowa gidan gaban suka zauna a tare, jelly tana matukar kaunar Rimsha tun da ta fara ganinta shiyasa ta yarda suka zauna a tare. Da gudu ya ja motar suka bar gidan, sai tambayarsa Jelly take yi nan gidan waye ne, ko dai shine gidansu, bakin abin magana ya ki yin shiru kwata kwata, haka ya rinƙa biye mata har suka isa gidan Abbi, ita kam Rimsha hanya kawai take gani abinta. Yana kashe motarsa a parking space na gidan suka fito suka jera zuwa cikin gida, gaba ɗaya kayan da jelly ta sa sun sake ɓaci da jini saboda bata sanya always ba, amma ba su lura da jinin ba, da yake ta baya ne kuma jerawa suka yi zuwa cikin palo. Bazata Imran yake son yi wa daddy shiyasa bai kira shi a waya ba. Da sallama ɗauke a bakinsu suka shiga palon, Aunty, Abbi, sune kawai a palon suna breakfast a saman table, da yake shima Abbi bai san jelly ba sai bai gane ta ba. Da fara'a suka tarbe su tare da yi masu iso, saman sofa suka zauna, sai tambayar ina daddy yake Jelly take yi, har da wani cewa ko dai yana Kano ne?. Abbi na ƙoƙarin yin magana aunty ta ce "Wannan yarinyar ta taɓa zuwa gidan nan ita da wata ƴar uwar Ommu, sun zo lokacin har ta ce mani mai idon mayu" kallon tsab jelly ta yi mata kafin ta ce "Ba dai Jalila ba sai dai wata" jelly bakin dai yana nan bai mutu ba, ba'a yi mata ya kyale. Aunty zata sake yin magana Abbi ya katse ta da cewa "Imran wace ce wannan mai tsananin kama da Maik? Ko dai Jelly ce?". Gyaɗa mashi kai Imran ya yi alamar e, zubur Abbi ya miƙe yana mai kabbara ga ubangiji tare da ciro wayarsa da sauri dan ya kira daddy. Lokacin da kiran ta shigo wayar daddy yana tsaye a gaban mirror yana gyara hular kansan ya yi waka ya shirya cikin manyan kaya zasu fita shida babynsa, ita ma ta yi wanka tana sanye da doguwar riga black color, dukkansu sun yi kyau sosai da sosai. Ganin kiran Abbi ne yasa ya ɗauka da wuri. "Maik ka zo palo yanzun nan ka same ni". Shine abin da Abbi ya ce, wani irin faɗuwar gaba ya ji, da sauri ya nufi hanyar fita yana faɗin "Baby ta so muje Abbi na kiran mu, kuma yadda ya ce na yi saurin nan da alama akwai abin da yake faruwa". Miƙewa ta yi ta fara dingisa kafa dan har yanzu bata gama warwarewa sosai ba. Ganin zata ɓata mashi lokaci ne yasa ya ɗauketa cak kamar yadda yake ɗaukar Jelly suka fita. Tun da ya doso palo gabansa ke faɗuwa, sunan Allah kawai yake ta kira a cikin zuciyarsa. Suna shiga palo bai lura da su Imran ba ya nufi saman sofa ya ajiye Ayla, ɗagowa da zai yi idanunsa sai a kan fuskar Jelly dake zaune kusa da Imran tana ta kallon shi tun da ya shigo dan ta tabbatar da shi ɗin ne dan gaskiya ya sauya sosai. Wani irin ɗagowa ya yi da sauri dan ya tabbatarwa da idanunsa abin da yake gani ne, ita ma miƙewa ta yi tsaye tare da nufo shi da gudu ta faɗa jikinsa tana ambatar sunan sa wato daddy. Mutuwar tsaye ya yi kamar wadda aka zarewa laka a jiki, Abbi kam abu ya yi mashi daɗi har da ciro waya ya fara yi masu Video, a wannan hali Hajiya Hadizatu ta sauƙo kasa ta samesu, yau tana sanye ne da shadda yellow color, ta ci kwalliya da alama fita zata yi. Kallon walaƙanci ta yi masu kafin ta ce "Matsiyata an taru kenan ba? Dan anga mijina yanzu ya wuce tsara shine duk aka tare mashi a gida". Ɗago kai Jelly ta yi daga jikin daddynta ta kalleta sama da kasa kafin ta ce "Yaya Imran wace ce wannan kuma kamar wata busasshen kifi, fuska kamar na big da muke kallo a discovery". Jelly kenan bata barin ko ta kwana, ka yi mutunci da ita ma ya ka kare bare kuma rashin mutunci ta haɗa ku, ai gidan shi ka zo in dai jelly ce, tsab zata wankeka soso da sabulu, bata barin magana ta faɗi kasa ba tare da ta bada amsa ba Guntse dariya Aunty ta yi shi kuma daddy sai lokacin ya ɗan samu karfi da ya sanya hannu ya ɗan bude mata baki, kuka ta sa mashi tana kara rungume shi, ita kuwa Hajiya Hadiza ran ta ya yi muguwar ɓaci, wato ita ce mai kamar an busar da kifi ga kuma fuska kamar alade ba, lallai idan ta kyale yarinyar nan ta cuceta, a zafafe ta yi kan daddy da nufin ya fisgo Jelly ta yi mata ɗan iskan duka duk da bata san wace ce bace kuma bata kalli face nata da kyau ba sakamakon tana manne da jikin daddynta. Sai wani huci Ommu take yi jelly ta ɓata mata rai, gadan gadan ta mufe ta........... Sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu. 💖💖TRIPLETS💖💖 E85-86💖 Sai wani huci Ommu take yi jelly ta ɓata mata rai, gadan gadan ta mufe ta, da sauri Abbi ya tare ta yana faɗin "Amma dai Hadiza baki da hankali ko?, Me zaki daka a jikin yarinyar nan". Jelly kuwa tana daga kwance a jikin daddynta ta ce "Kai ni zaki daka ma kenan? Amma dai baki da hankali ko? To id...." Bata karisa ba daddy ya rufe mata baki tare da kara rungumeta sosai yana mamaki wai har yanzu dama jelly bata canza ba kenan?. Shi kuwa Imran zuciyarsa har ta fara dukan uku uku dan Ommu zata bugi jelly, kuma dama ba bari shima zai yi a dake ta ɗin ba, shima daddynta fa bai yi kasa a gwiwa ba wajen sakinta ya juyo dan ya ga karshen rashin kunyar Ommu, idan ta yi gigin yunkurin taɓa ta wlh yau sai ya tsintsin ka mata mari sai dai duk abin da zai faru ya faru. Ommu kuwa a kule ta ce "Matsiyata dama ba dole ayi haka ɗin ba, idan ba ku yi ba ai ba ku cika ƴaƴan talakawa ba". Shi kam daddyn Jelly mamaki ya hana shi yin magana, wai me Ommu ta gani a tattare da sune da take ce masu ƴaƴan talawa, ko dai wani sabon iskanci ne,? Domin kuwa Ommu ta yi masu farin sani tun iyayensu wato kakannin su Jelly suma raye kenan, tasan irin ruwan kuɗin da suke da shi kamar me, to kodai dan daddyn Jelly ɗin ya dawo gidan da zama ne?. Shi kuwa Imran da abin ya ɓata mashi rai sai ya ce ya mata "Idan kina da account bani bari na baki koda 10 million ne ki rage zafi domin na ga kina da buƙa ta" ya kai karshen maganar tare da juyowa da kallon sa izuwa kan bappan nasa wato Abbi. "Bappa ka yi hakuri amma ba zan iya juran wannan cin mutuncin ba, Irfan abokina ne kuma ɗan uwana, amma kuma ko da iyayen mu ne suka kauce hanya addini ya bamu dama mu yi masu gyara ta yadda za su fahimta, ina matukar kaunar Irfan kuma muna girmama juna, duk abin da ya faru shekaran jiya ina sane, to yana da kyau mu taka mata birki domin ba yara bane mu, ta zo ta same mu cikin kanne mu, ku kuma cikin ƴaƴanku ta haɗa mu ta ci mana mutunci saboda ita bata san mutunci ba, to wlh ya isa haka, dama saboda Irfan ne muke yi mata hakuri, wlh ba dan haka ba wannan da tana prison yanzu, duk abin da ya faru a gidan bayan tafiyar mu ranar Akila ta gaya mani a waya, wlh Allah zan iya cewa Ommu kin zama mace mai saa ta farko da Akil ya ɗagawa kafa, ina mai tabbatar maki badan Irfan ba da babu abin da zai hana Akil ya sharara maki maruka wadda za su sanya ki manta hanyar da ki ka nufa, su sanya ki gani taurari, su sanya kunnuwarki doɗewa, ni ki bani account number bari na cireki daga kangin tsiya da kuma talaucin nan ko zamu samu sake a gidan bappanmu idan muka zo!!". Ya kai karshen maganar rai a matukar ɓace, dama an ce mai hakuri bai iya fushi ba. Sakin Jelly daddy ya yi yana faɗin "Rimsha ku je sama wajen Hanan ko, babyn daddy ta shi ku je ko?". To suka amsa da shi, da kyar Ayla ta miƙe, da sauri Aunty ta zo ta dafa mata suka wuce sama, domin ita ma Aunty bata son tsayawa a wajen dan bata ma son jin hayaniyar tasu. Dawo da kallonsa a kanta daddy ya yi tare da ɗaure fuska nan yau shima ransa ya yi mugun ɓaci, yau karo na biyu kenan da take cin mutuncin su a gaban ƴaƴansu to gaskiyar Imran ne yana da kyau su taka mata birki domin iskancin nata ya fara wuce misali. "Hadiza ina ganin mutunci ki ne nima dan saboda Irfan, yaron kirki, Allah ya rufa mishi asiri ba ke kika raine shi ba, wlh nasan da ke kika ba su tarbiya ƴaran nan da sai sun zama kannen sheɗanu, yanzu ke ba abin kunya bane ma ki ɗauko kafar ki da sunan wai kin dawo gidan nan? Wlh ta bakin Imran kin yi babbar sa'ar Akil aure ta sauya shi, ba dan haka ba ko yaya suke da Irfan sai ya dalla maki mari, idan ma baki yi sa'a ba sai kin wuce gadon asibiti, yanzu tsabar rashin kunya ƴaƴan yaya babban ne talakawa? Ke kin sani a gaba ɗaya cikin mu a tsabar kuɗi dai daga Hosain sai Yaya babba wato Abban su Imran, ko dai dama baki san su Imran ƴaƴan yaya babba bane? To idan baki sani ba yanzu ki sani Akil kawai zai iya sayan Familynku baki ɗaya, sannan bugu da kari ƴaƴan Umaiya ce wadda ta ma fi yaya babba kuɗi, kuma ke kin sani ko ada baya da yaya ki ka kwaci kanki a hannun Umaiya? To ki sani barewa ba zata yi gudu ɗan ta ya yi rarrafe ba, tun wuri ki fita har karmu idan ba haka ba zaki yi dana sani, yadda ki ka san Umaiya a da to yanzu Akil ne photo copyn ta, shiyasa ki ka ji munce maki kin ciri tuta tun da har Akil ya iya danne zuciya ya kyaleki!!!". Cikin sauri Ommu ta ce "Yanzu kenan Umaisha ɗan gidan Yaya babban ta aura?". Ba wanda ya tanka mata a cikinsu, cikin zumuɗi ta ce "Kai amma Alhadulillah da ya kasance ba ƴaƴan Matsiyata ƴar cikina ta aura ba, kai abin ya min daɗi". Tana gama magana ta juyawa ta nufi sama, sai daɗi take ji. Girgiza kai daddy ya yi tare da komawa ya zauna a saman sofa, shima Abbi zama ya yi a saman sofa yana mamakin hali irin na Aunty, Baiwar Allah mace mai sanin Yakamata, bata son hayaniya, mafi yawancin mata suna son su ga ana ci wa kishiyarsu mutunci amma ban da Aunty, da zarar sun fara faɗa zata wuce ɗakinta dan ma kada ta ga abin da yake faruwa, bata son hayaniya kuma bata son abin haushi, tana da zuciya mai kyau sosai, har cikin ransa yau Abbi ya ji wani irin mugun daɗi abin da Aunty ta aikata, ta san abin da take yi. Shi kuma Imran sama ya haura domin ya je ya kira su jelly. Jim kaɗan sai ga Ommu ta fito riƙe da wayarta ta canza shiga zuwa doguwar riga, da alama ya fasa fitan kenan. Kusa da Abbi ta zo ta tsaya tare da miƙa mashi wayarta tana faɗin "Saka Mani number Umaisha ko kuma na mijinta a nan bari na kira shi ya kawo mani ita yanzun nan zan yi magana da ita". Kallon daddyn Jelly Abbi ya yi, mamaki ya hana su magana, tun da ta dawo bata nemi yaran ba sai da ta ji Umaisha na auren Akil sannan ne zata ne me su dan ta ji ruwan kuɗi. Sosai daddy yake addu'ar kada ta lalatawa yaran nan aurensu, dan yasan halinta sarai, zata iya kai Umaisha ta barota, kuma kun san tsakanin uwa da ƴa, sannan Ommu ba ruwanta da wai ƴar cikinta ce, idan bukatar ta ya biya shikenan ai. Ƙin saka mata number Abbi ya yi, ya ce bashi da shi, ba dan ta so ba ta hakura ta koma sama tana tunanin yadda zata yi. Tana komawa ba jimawa sai ga su Imran sun sauƙo kasa, jelly ta canza kaya zuwa doguwar riga ash color, shi kuma Imran yana manne da waya a kunne yana magana da Akil akan su zo gidan Abbi yanzu an gane Jelly. Aunty na rungume da Ayla suka sauƙo kasa. Jikin daddy jelly ta je ta haye tana zuba mashi shagwaɓa akan tana kewarsa, da hannu ya yi wa Ayla alama akan ta zo ita ma, ba musu ta je dan dama bata taɓa yin musu da shi ba. Ta gefen jikinsa ya jawota yana faɗin "Babyn daddy wannan ita ce Jelly" jin abin da daddy ya ce yasa Jelly ta yi saurin ɗago kai tana maimaita sunnan da daddy ya kira Ayla da shi. Kamar wadda aka yi wa allura haka Jelly ta diro kasa ta yi zaman ƴan bori a tsakiyar carpet ɗin tare da fara wuwwurga kafafu a kasa tana ihu kamar ba lafiya ba, daddy ya san me take yi wa ihu, wato dan ya kira Ayla da babyn daddy shi ne take kuka, sunan babyn daddy sunan Jelly ɗin ne da yake kiranta da shi lokacin suna Kano. Imran ne ya yi saurin marisowa wajenta tare da riƙota yana faɗin "Jelly menene?". Cikin kuka ta ce "Yaya Imran daddy fa yanzu ya daina so na, kana ganin wata babyn ya samu". Babbar magana wai ɗan sanda ya ga gawar soja, dama shi daddy already yasan za'ayi hakan, yasan ba zata taɓa yarda da Ayla ba, shiyasa ya ce tana dawowa za'a ɗaura mata aure da Imran kowa ma ya huta. Cikin sigar rarrashi Imran ya ce "Jelly wannan fa mummynki ce ba wai wata ba, mummy zaki ce mata". Cak ta tsaya da kukan nata tare da ɗago idanu da sauri ta sauƙe akan Ayla ɗin. Kallon minti ɗaya ta yi mata kafin kuma ta kwashe da dariya kamar wata zautatciya, daddy kam ko ajikinsa dan ya san halin kayarsa, in dai jelly ce to fin hakan ma zata yi, sai ta sa ka ka yi tunanin ko kaine mahaukaci, wlh tsab jelly zata sanya ka fara tunanin anya kana lafiya kuwa? Anya kai ba mahaukaci bane kuwa?. Shi kuwa Imran da yake har yanzu yana da sauran karatu akanta sai ya ce "Jelly lafiya kike dariya kuma?" Kara sautin dariyar tata ta yi har da rike ciki, kamar ba ita ba ce mai yin kuka yanzun nan. Sai da ta yi dariyarta mai isarta sannan ta ce "Amma yaya Imran a sanina dai kafin mu zo nan lafiya lou kake, ya akayi kuma yanzu ka canza kamar mara lafiya?" Ɗan kallon kansa ya yi dan ko zai ga abin da ta gani a tattare da shi da ta ce mashi ba shi da lafiya. Shikam daddy a zuciyarsa cewa ya yi kaɗan ka gani Imran ba dai jelly ba, wata rana sai ta sanya ka tuɓe wando a cikin jama'a, Abbi kuwa ban da murmushi ba abin da yake yi, ita kuwa Aunty yau ta ga duniya a wajen jelly, ta ga abin mamaki, Rimsha kam ko a jikinta, Hanan ce ma ta ɗan tsorata da ganin abin da jellyn take yi. "Jelly wai me yake faruwa ne?" Cewar Imran, cikin dariya ta ce "Yaya Imran wannan ƴar karamar yarinyar da bata wuce na kamata na haɗiyeta na kora ruwa bace mummyna? Wai ka manta mummyna ta rasu ne? To idan ka manta na tuna maka, mummyna bata nan wannan kuma ai ko mai....." Bata karasa ba ta ja birki sakamakon karewa fuskar Ayla kallo da take yi. Zubur ta miƙe tana faɗin "Ya na kalli tana kama da mumnyn kuma?" Da yake ta san fuskar mumnynta a hoto, da sauri ta koma jikin daddy tana tambayarsa ya akayi take kama da mummynta kuma. Daddy bai san time ɗin da ya ce mata "kanwar mummyn ki ce ai". Imran yana ƙoƙarin gaya mata ita ce matar daddy, daddy ya yi saurin dakatar da shi domin kuwa yasan a yanzu dai jelly ba zata taɓa yarda da Ayla matarsa ba, for now dai a barta a kanwar mummyn kawai zai fi, sai ta kara hankali idan ta je gidan mijinta, idan ba haka ba yanzu zata yi masu karamin hauka. Suna a haka wayar Imran ta fara kara, hannu yasa a aljihun nasa ya ciro wayar, Nawid ne yake kiransa, picking ya yi tare da manna wayar a kunnensa. Maganar minti 5 suka yi, sannan Imran ya ce sai kun zo, daga nan suka yi sallama, hakan kuma ya yi daidai da danno hancin motar Akil cikin gidan. Zama Imran ya koma ya yi a saman sofa, ita kuma Jelly tuni ta rungumi Ayla sun fara hira a matsayin kanwar mummynta, dama ta jima tana cewa daddy ya kai ta wajen ƴan uwan mumnynta ko kuma ya kawo mata su gida ta gansu, amma kullun sai ya rinƙa ce mata zai yi zai yi amma bai taɓa yi ɗin ba, sai ga shi yau ta ga kanwar mummyn nata ai farinciki ba'a magana, har da rungumar Ayla ta yi suna ta hira. A haka Akil ya shigo ya same su, tare da Akila, Umaisha da kuma A'afia suke tafe, duk ya haɗo kansu dan su zo su sake kulla zumunci. Sai murna suke yi kamar me, daddy ne ya ce da Akila ta tashi ta je ta ɗauko mashi kuɗi a cikin drawer mirror a ɗakinsa ta kawo mashi, to ta amsa mashi da shi tare da miƙe wa da sauri ta nufi waje. Tana shiga palon suka ci karo da Irfan zai fito, cikin sauri ta yi baya zata faɗi, yana ƙoƙarin riƙota ta kauce mashi ta faɗi kasa, bata son ya taɓa ta dan kada ɓoyayyen masoyi ya ɓata rai. Yadda ta kauce mashin ba ƙaramin mamaki ta ba shi ba, amma kuma bai kawo komai a ransa ba ya duka yana son ɗagota tare da yi mata sannu, kin yarda ya ɗagota ta yi, nan ta ce mashi a'a ya bari zata tashi, bai damu ba dan shima dama ba wani son cika taɓa jikinta ya yi ba, dan tsaro. Bayan ta miƙe suka gaisa ya tambayeta yaushe suka zo, nan ta gaya mashi yanzun nan kuma daddy ne ya aiketa su Imran suna palo, da Muryarsa ya ce to ta ɗauko saƙon daddyn sai su wuce zuwa cikin gidan tare, to ta amsa da shi sannan ta wuce zuwa bedroom ɗin na daddy tare da taimakonsa wajen nuna mata bedroom ɗin. Kuɗi ta ɗauko mashi wadda a kalla zasu iya kai 500k, Irfan na tsaye har ta fito suka jera zuwa cikkn gida. Kamar yadda ta barsu haka ta shigo ta same su, sai hira ake zubawa kamar ba gobe, miƙawa daddy kuɗin ta zo ta yi tana faɗin "ga shi nan bappa". Karɓa daddy ya yi tare da miƙawa Abbi ya ce ga sadakin Jelly, a matsayinsa na waliyin Imran, yana neman alfarmar da a ɗaura auren nan yanzu, Allah sarki kuruci dangin hauka, jin hakan yasa jelly ta rungume shi tana dariya tana faɗin zata zama matar yaya Imran, zata zama matar yaya Imran, shi kuwa Imran kasa da kansa ya yi duk kunya ta rufe shi, nan take Akil da Irfan suka fara tsokanarsa, aunty ce ta ce da Jelly ta ta so ta zo su ɗan yi magana. To jelly ta amsa da shi tare da tashi ta je, har ga Allah duk wanda ya zauna da Aunty dole zata shiga ransa domin tana da halayya masu kyau, kowa ya zo gidan ita yake so ba Ommu ba, tana da tarin masoya ciki kuma har da ƴaƴan Ommu ɗin, domin Irfan yana kaunarta sosai saboda kirkinta, haka su Aafia ma, suna sonta, kowa nata ne bata da mugunta ko kaɗan. Miƙewa Abbi ya yi ya ce su je waje bari ya kira makwabtansa sai a ɗaura auren. A tare gaba ɗaya mazan suka fita, su kuma matan suka cigaba da hira Aunty tana yiwa Jelly nasiha akan ta natsu, tare da kara mata haske a kan abubuwa. Mu koma baya kaɗan, lokacin da daddyn Jelly ya ce su haura sama, time da Ommu take yi masu rashin mutunci, da suka shiga aunty ta kalli jini a jikin jelly hakan yasa ta saka jelly ta shiga toilet ta wanke jikinta ta bata sabon pant da kuma always ta saka, wannan dalilin yasa jelly ta fara kaunar Aunty, saboda kirkinta, bata share mutane. Bayan ta saka always ɗin Aunty ta kara bata doguwar rigarta ta sanya a jikin ta, wannan shine abin da ya faru bayan shigarsu ɗaki. MU KOMA IN DA MUKE A STORY. Suna tsaka da hira aka sako waƙar bodyguard na Salman Khan a Tv, a ɗari Jelly ta miƙe tare da kure Volume na Tv ta fara tikar rawa. Sai murmushi kowa yake yi yana kallonta, jawo hannun Rismha ta yi akan ta taso su yi, ai kuwa Rimsha bata ki ba suka shiga yin rawa a tare, sake jawo hannun Ayla ta yi, nan fa ita kuma Ayla ta saka kuka dan ba zata iya ba, jelly a tunaninta dan bata so ne yasa take kuka saboda idan baku mance ba halin jelly ɗin ce, idan bata son abu sai ta kama kuka, to tana tunanin kamar kowa ma haka ne, shiyasa sai ta kyale Ayla ɗin kawai suka cigaba da rawa da Rimsha, miƙewa ita ma Akila ta yi suka fara takawa a tare, da kaɗan da kaɗan Umaisha ma ta bi bayansu suka bar Aafia, Hanan da kuma Ayla sai Aunty, sun zuba masu idanu suna kallon yadda suke taka rawa kamar ba gobe, abin ba ƙaramin ƙayatarwa ya yi ba. HAPPINESS IS FREE. A can waje kuma ana famar ɗaura aure. After some minutes. Bayan an ɗaura aure an dawo a palo suka sake ba je wa, Imran, Akil ba wanda ya tuna da Ammie zata karɓi wannan aure ne ko ba zata karɓa ba, sannan idan baku mance ba, jelly tun kafin ta san waye Hajiya Umaiya ta nuna bata son ta, idan baku mance ba bakar muguwa munafuka take kiran Hajiya Umaiya, ya kuke tunanin wannan zama zata kasan ce? Anya Ammie zata karɓi Jelly kuwa?. Ko dai zata gasa jelly kamar yadda ta gasa Umaisha? Mu dai je zuwa. Sai murna suke yi, duk fuskar wadda ka kalla a cikin palon nan zaka kalli tsantsan farinciki a tattare da shi. A wanann halin su Nawid suka iso suka same su, shi da Umminsa da kuma Hajiya Batula. Abin da ya faru a gida bayan komar Nawid da ya kawo wa Imran Jelly shine, da ya koma bai sami Abbo a gidan ba, abin ya ɗaure mashi kai, kwata kwata babu Abbo babu alamar sa, kuma ga kofar ɗakin a rufe kamar yadda ya rufe Abbo ɗin, shi ne da ya dawo ya buɗe kofar, to ta ina Abbo ya fita?. Ransa cike da tunani tare da mamaki ya kwanta kawai, amma ya kasa yin barci har wayewan gari. Da gari ya waye ne Ummi ta tambayi ina baby, sai ya ce tana gidansu Abokinsa, bai gaya mata me ya faru, me Abbo ya aikata ba, ya rufe abin shi kaɗai domin bai kawo a ransa cewa tsafi Abbo zai yi da jelly ba, ya yi tunanin raping ɗin ta kawai zai yi, shiyasa ya rufe maganar dan a cewarsa abin kunya ne ya faɗi hakan, ya rufawa mahaifinsa asiri. Nan fa Ummi ta fara faɗa akan me zai ɗauki baby ya kaita wani waje, ita ba ta yarda ba sai dai su je gidansu abokin a tare, hakuri ya rinƙa bata akan bari ya je ya ɗauko babyn, ina ta ki yarda ta ce sai dai su tafi tare, haka kuwa akayi shine suka taho tare, shi kuma Abbo shiru ba labarinsa, Allah kaɗai ya san ina ya tafi, ita ma Ummi bata neme shi ba, saboda ana hidimar biki tasan ba zama yake yi a gidan ba. STORY💖 Hannu Nawid ya miƙawa dukka mazan cikin palon, ɗaya bayan ɗaya suka gaisa, su kuma matan suka gaisa da baki, ya sha mamakin ganin jelly a jikin daddy, kamar zai magana sai kuma dai ya danne ya yi shiru, ita ma Ummi gaisawa suka yi da mutanen cikin Palon, ita kuma Hajiya Batula mamakin ganin su daddyn Jelly ya hana ta magana, shima daddyn ido kawai ya bita da shi dan bai san me zai ce mata ba, Abbi ne kawai ya ce "Batula dama kin san hanyar gidana? Kin san in da nake shine baki taɓa zuwa ba?". Shiru ta yi ta kasa magana, abubuwan da suka faru a baya ne kawai suka fara dawo mata a cikin ƙwaƙwalwarta. Hannu Abbi ya sa ya nuna mata sofa akan ta zauna, ba musu ta zauna gaba ɗaya palon suka yi shiru. Ummi ne ta katse masu shirun da cewa "Baby kin san shine da kika zauna a jikinsa?" Ta yi maganar tana kallon daddy da jelly ke a jikinsa, Jelly kam ko kallon in da take ma bata yi ba, domin bata sansu ba. Imran ne ya ce "Ummi babanta ne ai". A razane suka miƙe a tare ita da Nawid, kallon juna suka yi kafin su sake kallon Imran ɗin. Abbi ne ya ce masu su zauna sai ayi magana a nutse, ba musu suka zauna, Imran Abbi ya fara tambaya akan me ya faru a ina kanwar Hadiza wato Ummi ta san Jelly?. Nan Imran ya basu labarin duk abin da ya faru daga lokacin da Nawid ya kira shi a waya akan zai kawo mashi jelly har zuwa yanzu. Kallon Ummi Abbi ya yi kafin ya tambayeta me ya faru, a ina kuma ta sami jelly da har ta riƙeta na tsawon wannan watanni. Ita ma dai Ummi ba ɓoye ɓoye ta fara basu labari tun daga farko har izuwa yau da take zaune a gabansu. Lokacin da ta kai karshen maganar ba wanda bai nisa ba a cikin Palon, haka zalika ba wanda bai yi hamdala ga Allah ba, ita ma jelly sai da ta ɗago ta kalli Ummin ɗin, nan take ta ji Kaunar matar ta kamata, Ummi mai zuciyar imani, duk da jelly ta manta su amma tana kaunar Ummi, bare ma da Ummi ta bada labarin irin zaman da suka yi, sai ta kara jin tana son Ummin sosai. Shiru palon ya ɗan yi na tsowon mintuna kafin daddyn Jelly ya fara magana a nutse, "A gaskiya bani da bakin da zan iya gode maki na wannan abin da kika yi Mani, sai dai na yi maki addu'ar Allah ya baki gidan aljanna, kai kuma Nawid ina mai baka hakuri domin ba'afi minti 20 ba dana cika alkawarin dana ɗauka na aurawa Imran auren jelly, yanzu jelly matar Imran ce, amma kuma a matsayina na mahaifi a garesu na baka auren Aafia kuma a yanzu za'a ɗaura ba sai anjuma ba". Gaba ɗaya palon zubawa Daddyn Jelly idanu suka yi. Ita dai Aafia bata damu ba, idan baku manta ba tana bala'in kaunar Dr Nawid tun suna school da su Rufee, hakan yasa bata wani damu ba dan ance za'a aura mata shi. Shi kuwa Nawid kallon ƴan matan dake wajen ya yi yana son tantance wace ce Aafia a cikinsu, ganin hakan yasa daddy ya ce "Ga Aafia ɗin nan mai black dressing". Kwata kwata Nawid bata yi mashi ba, amma ba yadda zai yi, yama fi son Hanan akanta, domin A'afia irin siraran matan nan ne, shi kuma ya fi so ya ga ko'ina a cike. Ba dan ya so ba ya karɓi aurenta, Daddyn Jelly dai shi ya sake biyan sadaki, a ranar aka ɗaura auren, jin abin suke yi kamar mafarki Nawid dai zuciya bata so ba, sai dai kuma ya cire son jelly a zuciyarsa, domin yasan irin son da Imran yake yi mata, sai dai bai san ita ɗin ba ce, amma kullun idan sun haɗu Imran ba shi da magana da ta wuci na jelly'nsa matarsa hakan yasa ma ya cire ta zuciyarsa, kuma koda an ɗaura mashi aure da ita kafin su gane iyayenta, idan ya san cewa ita Imran yake so to zai saketa, dan shi zai bawa wani labarin irin son da Imran yake yi wa Jelly ba dai wani ya ba shi ba. Karin wata Haske Abbo shine wannan alhajin da yake neman Aafia ruwa a jallo a baya, wadda ya yi sanadiyar mutuwar Yusuf yayan Rufee, kuma shine wannan man ɗin na school ɗin su A'afia wadda ya kashe Amal kanwar Rufee ɗin, akwai abin da yake so a tattare da Aafia wadda shi kaɗai ya barwa kansa sani, ya rasa Aafia ce sanadiyar koma warta gidan su Akil wadda babu wani ɗan iskan matsafi ko aljanin da ya isa ya nufi gidansu Akil ɗin, hakan yasa Aafia ta kubcewa Abbo, amma ba dan haka ba, kowani motsi zata yi akan idanunsa take yi, akwai wani mata ki da yake son ta kai ne dan ya yi amfani da ita, shiyasa ya rinƙa bibiyarta yana kula da ita. Ya kuke ganin wannan abin zai kasance, daga karshe dai ga Aafia zata koma gidan Abbon baki ɗaya, to mu dai je zuwa, ni dai na yi gaba sai kun zo. Yau murna a wajen ƴan gidan ba'a magana, sun yi wunin cikin farin ciki, while ita kuma Ommu tana cikin ɗaki tana zuba barcinta dan ita bata wani damu da fita waje ba, bata fitowa palo sosai sai dai idan wani abin zata ɗauka. After some hours, bayan sallar la'asar rana ta yi sanyi, sun yi sallah sun ci abinci sun zauna suna hira, Ummi ta ce da Nawid su koma gida. Miƙewa ya yi suka sallami su Abbi tare da yi masu godiya sosai da sosai zasu tafi, Abbi ya ce su wuce da Aafia, mamaki ne ya kama Ummi, a nata tunanin sai sun kawo lefe da sauran abubuwan biki, Abbi ya ce kada su damu abawa Nawid matarsa daga baya za'a kawo mata kayanta da abubuwan da ake buƙata, har kasa Ummi ta duƙa tana yi wa Abbi godiya tare da fatan alkhari, shima godiya ya yi masu na riƙe jelly da amana da suka yi, rungume Jelly Ummi ta yi tana mai kara jin kaunarta har cikin ranta, ita ma jelly sosai take kaunar Ummin duk da bata iya tuna rayuwar da ta yi a gidan nasu ba, amma dai ta na jin a jikinta tabbas ta taɓa rayuwa da su kamar yadda suka faɗa. Har wajen mota gaba ɗaya family suka rakosu, sai kuka Aafia take yi, lokaci guda an rabata da ƴan uwanta, bata taɓa tunanin wannan zuwan da su yi zata rabu da ƴan uwanta ba, abin ya yi mugun taɓa mata zuciya, sai rarrashinta Ummi take yi tare da rungumarta suka zauna a gidan baya na mota, shi kuma Nawid gaisawa suka kara yi da su Imran sannan suka yi sallama bayan ya zubawa su Abbi godiya, ya shiga gidan gaba na motar, ayya Ummi ta ɗauka da Aafia da jellyn ɗaya ne, bata banbanta su ba ta rungumo Aafia kamar Jelly, a haka suka bar gidan, Nawid ya ja mota. Duk wannan abin da ake yi Ommu tana sane amma bata leƙo ba, jirama take yi mutane su ragu ta jawo Umaisha ɗaki ta ɗaurata akan hanya dan su sami kuɗi, ita idan ba magana ta kuɗi ake yi ba, to ba zaka same ta a wajen ba. Jama'a wai shin ina Ommu take kai kudi ne? Me take yi da sune? Tana ji aka aurar da Aafia, amma bata wani damu ba, da ma taga ɗan ƴar uwarta ta aura sai ta ɗan ji haushi domin a nata ganin Nawid ba shi makudan arziki sosai. Bayan tafiyar su Nawid ne su Abbi kuma suka juya za su koma cikin gida, cikin dabara Akil ya jawo Umaisha suka shige cikin motarsa dan shi fa baya iya zama 2 hours bai murjesu ba wato tula tula, idan bai taɓa su ba har zazzaɓi yake yi, Abbi yana ganinsu suka shiga cikin mota, amma sai ya yi kamar bai gansu ba, kuma tunani ma ya yi akan su zo su wuce gidansu kada su yi masu abin kunya a nan, yara kamar wasu chewing gum kullun suna manne. Shi kuwa Imran ango na Jelly, yana son keɓewa da matarsa amma ba hali domin kuwa shi ba irin su Akil bane, yana da kunya sosai, daddyn Jelly da ya fahimci hakan sai ya ce da jelly'n ta je ɗakinsa ta ɗauko mashi agogonsa. kamar ta san ɗakin nasa ganin Akila ta fita waje ɗazun da ya ce ta ɗauko mashi kuɗi, haka ta wani miƙe da sauri ta nufi wajen ita ma, kuma dama yasan bata san ɗakin nasa bane yasa ya aikata dan kawai ta fita Imran ya bi bayanta su je su ɗan tattauna, dan gaskiya Imran ya wahala akanta sosai, yana da kyau yanzu su sami lokaci sosai a tare. Tana fita kuwa Imran ya zame cikin sanɗa ya bi bayanta, da yake part biyu ne a gidan, daga nasu Irfan ɗin sai na su Abbin, hakan yasa tana fita ta nufi ɗayan part ɗin, shima yana fita ya bi bayanta. A palon ta tsaya da yake ɗakuna uku ne a cikin palon, ta tsaya tana tunanin wanene na daddy'nta, daga ta baya ya runhumeta tare da kwanto da kansa a saman kafaɗunta. "Yaya Imran" ta ambata tana ƙoƙarin juyowa, "Waye ya gaya maki nine?" Ya yi maganar tare da juyo da ita suna fuskantar juna. "Ba wanda ya gaya mani kawai a cikin zuciyata na ji cewa kai ɗin ne". Ranƙwafo da kansa ya yi a saman tata suka haɗa goshi, har cikin ido take kallon shi, yayin da shima yake kallon cikin idanunta. "Jelly kin san yadda yaya Imran yake son ki kuwa?" Turo ɗan bakin nan nata ta yi har yana taɓa nashi, cikin shagwaɓa ta ce "E ai nima ina son ka ko?". Wani dogon numfashi ya ka lokacin da bakinta ya taɓa nasa. A hankali ya ɗan fito da harshensa yana lasan saman lips nata, ƙoƙarin kwace kanta ta yi domin ta raba jikinta da nashi, riƙeta sosai ya yi tare da capko lips nata na kasa ya fara tsotsa, zaro idanunta ta yi tana kallonsa, cikin sauri ya sa hannunsa ya rufe mata idanun nata dan kunyar kallon cikin idonta yake yi a yayin da yake kissing nata. Da karfi ta ture shi tana faɗin "Wlh sai na gaya wa daddy kai ɗan iska ne, wato abin da ake yi a film shine zaka yi mani ko? Wlh bana sonka tunda dai haka ka ke, kuma dole na gayawa daddy abin da ya ce kada na yarda wani namiji ya yi mani ka yi mani yau". Ta kai karshen maganar cikin kuka tare da juyawa da sauri dan ta koma cikin gida. Da sauri ya riƙota yana mai bata hakuri akan dan Allah kada ta faɗa ya tuba ba zai sake ba, kin yarda ta yi har da rantsuwa sai ta faɗa. Yana cikin bata hakuri ta kwace kanta da karfi, da gudu ta juya zuwa part ɗin su Abbi, dafe kansa ya yi yana tunanin jama'ar dake a cikin palon, dama dai iya daddy ne to da da ɗan sauki, amma har da su Akila a wajen fa, tuna hakan yasa ya juya da sauri ya je ya shiga motarsa tare da kiran Rimsha a waya akan ta fito da sauri su tafi domin a gaskiya ba zai iya haɗa idanu da jama'ar palon ba, kuma yasan ba makawa jelly sai ta faɗi wannan magana, me ma ya kai ni yi mata kiss a gidan nan? Ya tambayi kansa a cikin zuciyarsa. A haka Rimsha ta fito ta same shi, cikin sauri ya ce ta shiga su je, ai kuwa ba ɓata lokaci ta shiga, da gudu ya figi motar suka bar gidan suka nufi gidan Lion, kunya ta kore shi a gidan. Yana shiga gidan Lion sai ya ga ba motar Lion ɗin, hakan ya tabbatar mashi da Lion baya gidan kenan, kallon gateman ya yi tare da tambayarsa Lion ya fita ne? E ya amsa mashi tare da ce mashi sun fita tare da Mark, jinjina kai ya yi kafin ya ce da Rimsha su je su duba jikin Areef sannan su wuce bedroom nasu. Jerawa suka yi zuwa cikin gidan. Kwance su isko Areef, da kallo ɗaya Imran ya yi mashi ya san ba lafiya ba domin kuwa gaba ɗaya ya sauya kamar ba shi ba, abin da kuma yake faruwa shi ne, G.M.A sun gane Lion yana son cire Areef daga cikin su, ya sanya ta ko'ina ana yi wa Areef ɗin saukar Al Qur'ani mai girma, ga addua'o'i, shima Lion ɗin kwata kwata yanzu baya barcin dare, kwana kai wa Allah kukansa yake yi, yana gayawa Allah damuwarsa, azumi kuwa ba'a magana, yana yi wa Areef azumi sosai ga sadaka da karatun Al Qur'ani mai girma, duk fitar da yake yi kwanakin nan gidajen gajiyayyu da gidan marayu yake zuwa ya raba masu makudan kudaɗe, hakan yasa ya sakarwa Aseef ma kuɗi dan su yi ta sadaka ta ko'ina, saboda ya san duk girma bala'i da masifa da bawa yake a ciki, sadaka tana ruguje sharrin ta kawo Alkhari, wannan faɗar Allah ne, ƴan uwana mu lizimci yin sadaka ko yaya take, bata kaɗan ba ta yawa, abin da kake renawa wlh wani kuma ita ce abu mafi girma a rayuwarsa. Lion ya fahimci kafin su fitar da Aseef daga cikin wannan bala'i sai sun tashi tsaye sosai, idan ba haka ba suna ji suna gani za su rasa ɗan uwansu lokaci guda, hakan yasa Lion yake cikin matsananciyar damuwa a kwanan nan, kwata kwata baya cikin kwanciyar hankali, kawai dai ba'a iya gane mashi ne shiyasa ba wanda ya san yana cikin damuwa. G.M.A. sun gane ana ƙoƙarin cire Areef daga tarkon da suka sanya shi, shiyasa suke takura mashi kwanan nan, suna azabtar da bawan Allah nan fiye da tunanin mai tunani, kuma kada ku manta duk abin da Areef zai ji a jikinsa su ma TRIPLETS za su ji a jikinsu, yana ɗaya daga cikin abin da yasa Lion ya kara shiga tashin hankali, domin yasan Areef ya fi su shiga cikin wannan azaba da suke ji a jikin nasu. A yau shugaban G.M.A gaba ɗaya ne da kansa ya zo jikin Areef yana azabtar da shi, shiyasa yau ya fi shiga bala'i fiye da kullun, kuma ogan nasu kun san ya fi sauran haɗari, abin da ya sa kuma ya shiga jikin Areef ɗin yau da kansa, dan saboda ya ga sauran idan suka shiga jikin na Areef da Lion ya zo kusa da Areef ɗin za su gudu saboda perfume nasa, to shine yau shi ogan ya zo da kansa dan ya samu ya azabtar da Areef yadda ya kamata. Imran ya tsorata ji ya yi kamar kada su karisa cikin ɗakin, amma kuma sai ya daure suka karisa kusa da gadon. Jin sallamarsu ya sanya Areef ɗago kansa tare da waro idanunsa da suka kara girma yanzu, dama ga su da halittar manya manyan idanu abin sai ya zama abin tsoro. Yana ɗago idanu kai tsaye sai kan Rimsha, wani irin zirrrrr ya ji a jikinsa, cikin sauri ya miƙe zaune yana kare mata kallo, wani irin karfin bala'i ya ji ta zo mashi lokaci guda kamar wani doki. A zafafe ya damki wuyarta da karfi ya shaƙeta, nan take kuma idanuwansa dukka suka sauya launi daga ask color izuwa jawur kamar jini, fuskar nan tasa har wani ja ta yi, kumatunsa har kerma yake yi, ba shi da wata burin da ta wuce ya ga ya zuƙe mata jini tas. Da sauri Imran ya yi kansa yana ambato sunansa tare da fara yunkurin kwaceta daga hannunsa. Yana daga zaunen da hannu ɗaya ya yi wurgi da Imran ɗin gefe guda, ita kuma tuni ta fara fita a hayyacinta, idanuwanta duk sun yi jawur sun firfito waje, ga shi gidan babu kowa, soja ɗaya ne kawai ya rage wadda yake a bakin gate, Lion ya fita tare da ɗayan sojan. A yadda Areef yake yanzu ko sojoji goma basu isa su danne shi ba bare kuma soja ɗaya, mai kwatar Rimsha a hannunsa sai Allah sai kuma Lion. Ba ƙaramin buguwa Imran ya yi ba, da karfi ya matse idanunsa saboda azabar da ya ji, amma da ya ga Rimsha tana ƙoƙarin mutuwa sai ya sake miƙewa ya nufi Areef ɗin, da iya karfinsa ya sanya hannunsa a kan na Areef dake a wuyarta yana ƙoƙarin ɓanɓaro hannun nasa. Da karfi Areef ya shaƙo shi da hannunsa ɗaya ya sake wurgi da shi ta baki kofa, hakan kuma ya yi daidai da shigowar Lion cikin ɗakin, domin karfe 5 ta cika ya dawo bawa Areef ɗin magani. Sake miƙewa Imran ya yi bai lura da Lion ɗin ba ya sake nufar Areef ɗin, har kasa ya duƙa yana mashi magiya akan ya sake dan Allah kada ya kashe ta wlh bata da kowa, sake riƙo shi Areef ya yi ya haɗa kansu da Rimsha ya buga da karfi, wani irin azababben ihu Imran ya saki ita kuma Rimsha diff kake ji kamar babu rai a jikinta, kai daga ganin wanann karfi kasan ba iya Areef shi kaɗai bane. Da karfi ya sake hankaɗe Imran ɗin, yana ƙoƙarin zubewa kasa da sauri Lion ya tare shi ya faɗa saman faffaɗar kirjinsa, nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ɗauki Imran ɗin cak ya kwantar da shi a saman carpet dake a gaban bed ɗin na Areef. Yau da yake ogan G.M.A da kansa ne sai bai gudu ba dan Lion ya zo, yana jin azaba saboda kamshin perfume ɗin na Lion ɗin, amma saboda taurin kai ya dage sai ya sha jinin Rimsha ya ki guduwa, Imran kuwa sai numfashin sama sama yake yi, amma dai ya ji mugun daɗi da Lion ya dawo, kuma ya sami kwarin gwiwa akan koma yaya Lion ba zai bari Areef ya kashe Rimsha ba, ko dan addinin Musulunci zai taimaketa. Gently Lion ya tako zuwa gaban gadon, hannu ɗaya ya sanya da nufin ya ciri hannun Areef daga shakar da ya yi wa wuyarta, amma Areef ya ki sakinta, sai ma kara matse ta da ya yi, ɗan ciza laɓɓansa ya yi kafin ya murɗe hannun Areef ɗin da ɗan karfi, nan take ya saki wuyar tata, yana numfashin kamar nishi. Tana ƙoƙarin zubewa kasa Lion ya riƙota da hannu ɗaya dan idan ta faɗi kasa akwai matsala, tana faɗuwa za su zuƙe mata jini kaf. Ɗaga ta ya yi da hannu ɗaya ya ɗaurata a saman kafaɗarsa, ya juya da niyar ya nufi waje da ita. A zafafe Areef ya diro kasa daga saman gadon tamkar ba shi ne mara lafiyar da aka yi wa aiki ba, Allah sarki ba shi bane, kun san dama G.M.A a cike suke da bakin cikin dan Lion yana shiga masu hanci da kudundune, to yau suna ganin sun sami damar da za su ɗauki fansa akan Lion ɗin tun da ga shi ya zo, shiyasa gabaɗayansu suka zo suka taru a jikin Areef ɗin suka kara mashi karfi kamar kosasshen doki. Ganin haka yasa Lion ba tare da ya yi magana ba ya yi wa Imran alama da hannu akan ya miƙe ya karɓe ta su fita, da sauri Imran ya miƙe ya zo ya karɓeta suka fita. A zafafe Lion ya juyo suna fuskantar juna da Areef, daga kasa ya fara kallon Areef ɗin zuwa sama, G.M.A sun kara mashi girma kamar ba shi ba. Lumshe dara daran blue eyes nasa ya yi kafin ya juya da nufin ya bar ɗakin domin tausayin ɗan uwan nasa yake yi, yana jin kamar ba zai iya dukan Areef ɗin ba saboda yau jikinsa a mace yake. Yana juyawa Areef ya nufo yi gadan gadan, yana ƙoƙarin shaƙo shi ta baya, a sukwane Lion ya duƙa kasa tare da juyowa ya kai mashi wani irin duka a gefen kirjinsa wadda ta sanya shi yin baya. Wani irin kukan damusa Areef ya yi alamar dukan ta yi mashi zafi. Da iya karfinsa ya nufi Lion, sai wani irin abu yake yi kamar horo. Zuba mashi ido Lion ya yi sai da ya iso ya ɗaga hannu yana ƙoƙarin kaiwa Lion ɗin shaƙa a wuya, wani irin damƙa Lion ya yi mashi tare da ɗaga shi sama ya yi wurgi da shi a saman gadon, bai barshi ya miƙe ba ya sanya hannunsa ya shaƙesa da karfi tare da zaro mashi wayan nan dara daran blue ɗin nasa sannan ya daka mashi wata irin mahaukaciyar tsawa mai rikita ƙwaƙwalwa, nan take Areef ya natsu sit kamar babu shi a ɗakin. A hankali Lion ya zame hannunsa daga riƙon da ya yi mashi a wuyar tasa, yana mai jin zafi a zuciyarsa, a zahirin gaskiya Lion ya fi Areef jin ciwo da kuma ɗacin halin da yake a ciki. Juyawa Areef ɗin baya ya yi yana mai watsa dark black curly hair sa, shi kuma Areef wani irin numfashi yake fitarwa tamkar gurnanin zaki, daga ji kunsan ba lafiya ba, bawan Allah.......... Nima haka na ajiye alkalamina sai mun haɗu Monday idan mai dukka ya kai mu. 💖💖TRIPLETS💖💖 E87-88💖 Juyawa Areef ɗin baya ya yi yana mai watsa dark black curly hair sa, shi kuma Areef wani irin numfashi yake fitarwa tamkar gurnanin zaki, daga ji kunsan ba lafiya ba, bawan Allah. Lion ya ɗan jima a haka kafin ya juyo tare da zama a gefen ɗan uwan nasa ya fara tofa mashi addua'o'i yana shafa mashi,. Wannan abin da ya faru ba karamin ɓatawa Lion rai suka yi ba, yau da ido huɗu ya yi da su to wlh sai dai wasu ba dai su ba, yanzu idan ya ce zai dake su a jikin Areef ba za su taɓa tsayawa ba, sai dai ma ya daki Areef a banza, domin kuwa da zarar sun ga zai dake su to wlh gudu za su yi su barshe ya yi ta jibgan Areef ɗin a banza, shiyasa bai wani saki jiki wajen dukan Areef ɗin ba. Ya jima yana yi mashi addu'a har barci ta ɗauke shi, sannan ne ya miƙe tare da gyara mashi kwanciya ya jawo bargo ya rufe shi zuwa kirjinsa tare da kara gudun Ac dake a ɗakin sannan ya nufi waje yana mai jin sauƙi a jikinsa, alamar sun rabu da Areef ɗin kenan. Yana fita bedroom nasa ya wuce kai tsaya, toilet ya shiga, wanka ya yi tare da shiryawa cikin pajama launin white color, ya yi kyau sosai, sai dai kuma kallo ɗaya zaka yi mashi ka gane tabbas bashi da lafiya saboda rama da ya yi, amma ba zaka taɓa gane cewa yana cikin damuwa ko yau ransa a ɓace ba, domin kullun a haka fuska take a ɗaure. Saman bed nasa ya hau ya kwanta yayin da manyan malamai suke ta fama yi masu saukar Al Qur'ani mai girma, a daidai lokacin ne kuma Aseef ya kira shi a waya, kuma video call. Bawan Allah har wani nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin nan ya ɗauki kiran. Yau karo na farko daya ɗan zaro ido lokacin da ya ɗauki kira Aseef. Kayatatcen murmushi ne ɗauka akan fuskar Aseef ɗin yayin da kuma ya zaro brown eyes nasa tamkar yana kallon wani abin, Lion ya san me yake yi mawa, shiyasa shima ya zare mashi ido sai su zama iri ɗaya kawai. Shiru Lion bai yi magana ba yayin da shi kuma Aseef yake zaune a saman bed nasa daga shi sai shot jikinsa babu riga, wata iriyar gashi ne mai bala'i kyau ga tsantsi kwance a saman faffaɗar kirjin nasa, shima dai breast ɗin nasa tamkar na ƴan uwan nasa ne, bul bul da su. Kallo ɗaya Lion ya yi mashi sannan ya kawar da kansa gefe yana tunanin shi kuma Aseef me ya je ya jajuɓo masu, domin daga ganinsa akwai wata a ƙasa, dama kuma shi ɗan nema ne, ya iya rigima idan aka taɓa shi. "Lion please and please smile now, smile for me even for one time in my life". Ya faɗa yana kara faɗaɗa murmushin nasa. Lion yana ƙoƙarin kunna laptop nasa, ba tare da kalli Aseef ɗin ba ya ce "What is smile?". Aseef bai yi mamaki ba dan Lion ya ce bai san menene murmushi ba, domin kuwa tun da suka girma suka yi wayo, bai taɓa ganin koda makamancin murmushi komai kankantarta akan fuskar Lion ba, kullun fuskarsa a yanayi ɗaya take, wato a fusace, a ɗaure kamar hadari. "My lion look at my face, look at the way am smiling, to haka zaka yi, I'm very sure idan ka yi murmushi or dariya idan a kusa da mutane kake to ba za'a rasa waƴan da za su suma ba saboda kyan ka, please maybe ma nima zan iya suma saboda kyanka, ni nama rasa ya zanyi, kwata kwata even your teeth ban taɓa gani a waje ba, idan zaka yi magana baka buɗe baki sosai bare mutun ya ga hakwaranka, sai dai ka yi maganar da wani ma zai ce baka motsa Lips naka ba, anya kuwa ma kana da hakwara kuwa? Sannan anya kana da harshe ma kuwa?". Ya kai karshen maganar tare da ɗaga kai sama kamar mai tunani. A zahirin gaskiya wannan magana da Aseef ya yi ta karshe na cewa ko Lion yana da hakwara da harshe, ya yi tane da sa ran ko Lion zai yi murmushi, da gangan ya yi, amma ina sai ya ga akasin haka, kuma gaskiyar Aseef ne ko hakwaran Lion ba su gani a waje, domin idan zai yi magana ba zaka taɓa cewa ma yana motsa lips nasa ba, saboda kasa kasa yake fitar da words, hakwara ma ba su gani bare kuma murmushi, da girmansu da wayonsu dai bai taɓa makamancin murmushi ba, wata kila da suna yara sun yi, kun dai ji yanzu shi bai ma san me murmushi ba. Lion duniya ne gaskiya wai "Aseef what is going on on your side?" Shi ne abin da Lion ya faɗa, "Lion wai yanzu da gaske ba zaka yi murmushi ba? Wlh ina matukar so na ga murmushi kane fa". Sai lokacin ya dawo da kallonsa kan wayar tasa. "Aseef i said what is smile?". Ɗan turo baki ya yi yau ya tuna da shagwaɓa ta baya, "Kai Lion ai na ce maka ga shi nan akan face na ina yi ko?, to kamar haka zaka yi mani". "Aseef i don't know how to do this nonsense, cox idan ba ka kyaleni da shirmen nan naka ba i will going to block your number, because I don't have time for nonsense, ko wani 1 second in my life yana cikin lissafi, so ka kyaleni". Shiru Aseef ya yi dama ya san Lion ba zai taɓa yin murmushin ba bare kuma dariya, shi haka yake kullun, su kuma suna son ganin ace yau ga shi koda ɗan murmushi ne ya yi wadda zai sanya kyawawan hakwaransa bayyana, amma ina abin ya faskara. Haka Aseef ba dan ya so ba ya kyale zancen murmushin ya ɗauko wata hirar dan ya sanya ɗan uwan nasa farinciki. A ɓangaren Imran kuwa, bedroom nasa ya wuce da Rimsha, yau ba dan jinin Hajiya Umaiya ne yake gudu a jikinsa ba, to da tabbas da wuya ya yi rai, dan saboda ba iya wurgi da shi kawai Areef ya yi niyar ya yi ba, sun yi niyar shan nasa jinin shima, Allah dai ya tsare shi ne kawai ta dalilin mamarsa. Saman bed ya kwantar da Rimshan tare da kwanciya a gefenta yana mai da numfashi. Kwanciyar 5 mins ya yi kafin ya samu da kyar ya yunkura ya miƙe ya nufi toilet. A gurguje ya yi wanka dan ya ɗan sami karfi, shiryawa ya yi cikin kananan kaya sannan ya ɗauki Rimsha suka wuce hospital dan a duba lafiyarta. Sun yi sa'a Baiwar Allah da suka je asibiti ba wata babbar matsala ta samu ba, kawai shakar ne da aka yi mata ta ji wuya, bayan haka ba su taɓa wani abin na daga halittarta ko wani cutar wa ba, sosai Imran ya ji daɗi da jin hakan. A ɓangaren JELLY kuwa, tana baro part ɗin su Irfan garden ta nufa, da yake garden ɗin yana ta gefen part ɗin su Abbin ne. Saman ɗaya daga cikin kujerun dake a wajen ta yi zaman minti 20 kafin ta miƙe ta nufi cikin gida. Kamar yadda ta bar su daddy haka ta koma ta samesu, jikin daddy ta je ta haye tare da fara kuka. Abbi duk ya rikice da ganin kukar tata, nan take ya fara tambayarta me ya faru, waye ya taɓa ta, amma saboda iskanci irin nata ko sannu ba wanda ta ce wa, shi dai daddy yanzu yana nadamar abubuwa da dama da ya rinƙa barinta tana yi time da take karama, bai taɓa zaton zata girma tana yin abin ba, ciki kuma har da shagwaɓa da kuma kuka babu dalili, dan jelly idan tsiyarta ta motsa haka kawai zata zauna ta yi ta kuka kamar wadda ta rasa iyayenta, sai ta yi mai isarta sannan ta yi shiru, ga shi bata jin rarrashi ko kaɗan, idan ta fara to sai ta kai in da take bukatar tsayawa, sannan ta tsaya. A yanzu ma haka ne, sai tambayarta gaba ɗaya jama'ar palon suke yi, duk sun taru a kanta, amma taki cewa kowa ko sannu, abin ya ɗaga masu hankali sosai, sun rikice kada wani abin ne ya faru, amma saboda iskanci irin na Jelly taki ciresu a duhu, ta kyale su sai bugawa zuciyarsu take yi, Akil kam har da zuwa ya duba waje ko zai ga wani abin da ya sanya ta kuka tun da daga wajen ta fito, kuma dai shima daga wajen ya dawo yanzu ba daɗe wa, shi bai ga komai ba, amma dai ita ta shigo tana kuka. Sosai daddy ya rinƙa dannarsu akan su je su zauna su kwantar da hankalinsu yana da tabbacin ba wani abin da ya sameta, iya shegene kawai, amma ina sun ki, kowa ya dage sai lallaɓata yake yi tare da yi mata kalamar rarrashi ko zata faɗi abin da akayi mata, Irfan har da zagewa yana rarrashinta, Abbi ma baa magana, Hjy Batula Aunty duk sai kara shagwaɓa ta suke yi. Daddy dai da ya ga ba su gama sanin halin Jelly ba sai ya barsu ya zuba masu ido domin yanzu su san halinta dan saboda gaba. Kuma babban abin mamakin shine kukan nata babu hawaye, ta yadda ma zaka san tsagen iskanci ne yake yi mata yawo akai, ko ɗingon hawaye babu, kai bama alamar hawayen a waƴan nan busassanun idanun nata masu gashin ido a tsaitsaye. Sun kwashi good 30mins a haka sai fama suke yi da ita, Akil dai ya koma gefe ya zauna dan idan ya ce zai biye mata to tsab zai karyata a gaban baban nata, gudun kada ayi hakan ne yasa ya koma gefe kawai ya kyale su. Sai da ta kara wani minti goma sannan cikin kukan nata ta ce "Daddy bani wayarka". Daga nan ne fa kowa ya koma mazauninsa ya zauna Aunty kam ta rasa a wani mataki zata ajiye Jelly, shi kuma daddy godiya ya yi ga Allah da ya sa suka ga halin nata a fili, Ayla Baiwar Allah yau ta ga iskanci mai lasisi, mamaki ya sa bakinta ma ya gaza rufuwa, shi kuwa daddy miƙa mata wayar tasa ya yi kamar yadda ta buƙata. Karɓa ta yi har lokacin bata dai na kukan ba, da yake wayar ma akwai password sai ta rubuta sunan ta, tana rubutawa wayar ta buɗe, dama ta san shine pin na daddyn nata tun a tsohuwar wayarsa. Contract nasa ta shiga, dealing number Imran ta yi, tana rubutawa sunan sa ya bayyana a yadda daddy ya yi saving, my son, kiran number ta fara yi. Lokacin da kiran ya shigo kuma suna asibiti shi da Rismha, bata daina kuka ba har ya ɗauki kiran, kuma ya ɗauki kiran ne da tunanin ko dai daddy ne tun da number sane. A nitse ya ce "Hello Bappa" cikin kuka ta ce "Yaya Imran ina kake?". Jin kukanta ya sa ya ruɗe shima sosai, hankali a tashe ya ce "Jelly menene yake faruwa? Me akayi miki kuma?". Hannu daddy ta kama ta zura a bakinta tare da gyara kwanciyarta tana mai juya kukan nata izuwa tsantsar na shagwaɓa har da turo baki kamar ba ita ba, gaba ɗaya palo sun mayar da ita Tv harta Akil yau yana ganin ikon Allah, su Aunty kam ba'a magana sun sami Tv ai, Abbi ma dai ta ɗaure mashi kai tare da jefa shi cikin tunanin anya tana da lafiya kuwa. "Yaya Imran ya naga har yanzu baka shigo palo ba? Ina son ka shigo ne fa na yi maganar akan idon ka" ta faɗa tana tsotsar yatsan daddy da ta sanya a cikin bakinta. Ɗan dafe kansa Imran ya yi kafin ya ce "My wife please ki rufa mani asiri kada ki faɗa kin ji ko? Na yi maki alkawarin ba zan kara ba, idan kika faɗa wlh zaki ja mani abubuwa da dama, ciki kuma har da raini tsakanina da kanne na, wato su AKILA". "To ni ba kanwar ka bace? Ai nima raina ka kenan zai yi ko? Tun da ni ka yi wa abin, ni a kaina baka ji kada na raina ka ba? Sai su Akila?, To ni dai gaskiya sai na faɗa ka shigo ko karka shigo yanzu kuwa zan gaya sai anjuma" . Diff ta katse kiran tare da kwashewa da dariya kamar ba ita ba. Miƙewa Akil ya yi tare da karasowa wajen yana faɗin Irfan ya zo ya riƙe mashi ita bari su yi mata ruƙiya wata kira aljanun kan nata za su tafi. Cikin sauri daddy ya ce bari ma ya riƙeta da kanshi domin idan aljanun suka tafi sai ya fi kowa murna. Zuba masu ido ta yi tana kallon ikon Allah. Ai kuwa har Akil ya gama ruƙiyarsa ba bu wani motsin da zai nuna maka da aljanu a kan Jelly, lafiya lou take kawai dai iskanci ne kwando kwando ta tara a kan nata, shiru palon ya yi suna kallon ikon Allah. Miƙewa ta yi daga jikin daddy ta haye sama abinta kamar wadda aka kira hannunta na riƙe da wayar daddynta wadda Imran yake ta kira tun ɗazun, bawan Allah duk ta rikita shi, sai addu'a yake yi Allah yasa kada ta faɗa Tana shiga ɗakin Hanan ta yi picking na call ɗin tare da hayewa saman gado tana faɗin "Yaya Imran ɗina ina kewar wlh, dan Allah ka dawo cikin palo ka ji?". Nauyayyar ajiyar zuciya bawan Allah ya sauƙe kafin ya ce "My wife kin faɗa ne ko baki faɗa ba?" Juya waƴan nan dara daran idanun nata ta yi kafin ta ce "E na faɗa kuma daddy ya ce zaka zo ka same shi". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "To shikenan da daddare zan zo sai na bawa daddyn hakuri kema kuma ki yi hakuri ba zan sake ba". Shiru itama ta ɗan yi kafin ta ce "Yaya Imran dama idan mutun ya yi wa matarsa kiss sai ya bawa babanta hakuri ne? Ina cewa da zarar an ɗaura aure kun zama mallakin juna". Imran ya kasa magana, ya rasa ma ta ina zai fara, ya rasa wani amsa zai bawa yarinyar nan, ya rasa me zai ce mata, anya jelly ba zata haukata shi ba wata rana kuwa? Anya kuwa tana lafiya?. Turo baki ta yi cikin shagwaɓa tare da yin kasa da murya ta ce "Yaya Imran kai fa mijina ne ba zan tona maka asiri ba, amma dai kada ka sake cinye mani bakina haka, ya yi yawa fa, kuma dama ina son yi maka wasan kafin a kai ni gidan kane shiyasa na yi maka haka, na yi karatun islamiyya ai, kuma ina kallon film sosai, sannan daddy da kansa lokacin da zai aura min Muneer ya gaya mani me ake nufi da aure, so ka ga ai na sani, amma dai yaya Imran kana da tsoro dayawa fa, i am the winner a wannan game ɗin". Ta kai karshen maganar tana dariya. Bawan Allah bai san time da murmushi ta suɓuce mashi ba, cike da so da kuma kaunarta ya ce "Amma dai gaskiya kin gama da ni, kin saka ni na gudu na bar gidan, amma ba komai zan rama ne, bari na damke ki zaki yi bayani da yaren da ke kanki baki san shi ba". Dariya ta yi ta mirgina ta mirgino kafin ta ce "Yaya Imran ba wani bayanin da zanyi mijina yaya Imran zai kwace ni daga hannunka ai". "Da gaske?" Ya faɗa yana ɗaga gera ɗaya kamar tana a gaban shi. Jinjina mashi kai ta yi tana faɗin "E da gaske". Jinjina kai shima ya yi kafin ya ce "To Shikenan ina nan zuwa gidan ai, a nan zamu ci abincin dare, wani irin kwalliya zaki yi wa mijinki?" Ƴar dariya ta yi har sai da hakwaranta suka bayyana. "Wani irin kwalliya kake so Yayana?" Shiru ya yi yana tunani, can kuma sai ya ce "Wando da riga masu kyau sai ki sanya hijabi a sama dan kada kowa ya kalla mani ke" murmushi ta yi kamar ba ita ba, ta nitsu sosai ta ce "Tom an gama amma dai...." Sai kuma ta yi shiru. "Amma dai me My jelly?" "Ba komai yaya Imran" "Gaskiya ban yarda ba, akwai dai wani abu, gaya mani menene?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Amma dai zaka kawo mani chewing gum da kuma ice candy ko?". Cool murmushi ya saki yana faɗin "Iya shi kaɗai kike so ko dai akwai wani abin?" "Shi kaɗai nake so, sai kuma ganin fuskarka, Allah ina kewarka sosai". "Allah sarki muna asibiti ne da Rimsha, amma dai yanzu za mu baro asibitin, idan mun fito sai mu wuto nan kawai". Ɗan kiƙewa ta yi a zabure tana faɗin "Me ya kai ku asibiti kuma?" Tana magana tana kara zare idanun nan nata sosai, "Ɗan ciwon kai ne yake damun Rimsha, amma dai an bata magani yanzu zamu taho". Koma wa ta yi ta kwanta tana kara dafe kirjinta domin ta ɗan ji sauƙi jin ba wata matsala ba ce ta faru. "My jelly zaki bi yaya Imran naki idan na zo ko?" Shiru ta yi mashi bata amsa ba, a can cikin zuciyarta kuma tunanin kalar tsiyar da zata yi mashi shi da daddy take yi, dan ta yi niyar sai ta yi masu tsiya sosai da sosai. "My jelly baki jina ne?" Ya faɗa daidai lokacin da yake miƙawa Dr hannu suna gaisawa akan za su wuce shi da Rimsha, tun da Allah yasa ta farfaɗo kuma ta dawo cikin hayyacinta, Allah ya takaita abin saboda addu'a da karatun Al Qur'ani mai girma da take yawan yi. "Yaya Imran ka bari sai ka zo ɗin ka ji ko?". To ya amsa mata da shi sannan suka yi sallama, ta ɗaura wayar a saman bedside drawer tare da gyara kwanciyarta ta kwanta tana tunanin kiss da ya yi mata ɗazun, wani irin yanayi ta ji a jikinta. A can palo kuma, cigaba da hiransu suka yi, da farko sun yi niyyar bin bayar Jelly ɗin, amma daddy ya dakatar da su a in da yake gaya masu su fita harkarta, domin lafiya lou take, iskanci ne kawai. Hakan yasa suka kyaleta aka cigaba da hira, miƙewa Akil ya yi ya fice waje dan ya amsa kiran da ake yi Mashi, Umaisha, Akila, Hanan, a tare suka miƙe dan su haura sama su bawa iyayen nasu fili su tattauna. "Aunty Ayla muje ko?" Cewar Umaisha, ɗan satar kallon daddy ta yi domin ba iya tafiya zata yi ba. "Umaisha ku je Batula zata zo tare da ita". Shi ne abin da daddy ya faɗa, to suka amsa da shi kafin su wuce sama. Dawo da kallonsa kan Hjy Batula daddy ya yi yana faɗin "Batula ƴaƴanki nawa ne a yanzu?" Duk kunya ya isheta, ta zubar da ƴan uwanta, shiyasa tun da ta shigo palon ta kasa sakewa saboda kunyarsu da take ji. "Ƴaƴana uku, biyu maza ɗaya mace, akwai HAROON da HARISH sai ABLA ita ce auta". Addua sosai Abbi da daddy suka yi wa ƴaƴan nata tare da ita kanta, sannan suka ce ta saki jikinta komai ya wuce ai, ajiyar zuciya ta sauke kafin ta yi masu godiya sosai da sosai. "Batula taimakawa Ayla ta bi bayan ƴan uwanta zuwa sama". Cewar daddy. To ta amsa da shi tare da tambayar wace ce Ayla ɗin. A takaice sama sama Abbi ya bata labari, sosai ta yi murna sannan ta yi wa daddy gaisuwar rasuwar mummy jelly kafin ta riƙo hannun Ayla ɗin dan su nufi sama. Ƴar kara ta saki lokacin da ta miƙe, girgiza kai daddy ya yi Ayla raguwa ce ta karshe, hakan yasa yake cewa tayi yarinya, ba wai shekarun yake dubawa ba, shi yasan me yake dubawa yasa yake kiranta da yarinya. Ganin abin da ya faru yasa Hjy Batula ta gane me ya wanzu a tsakanin yayan nata da kuma matar tasa, hakan yasa ta kara Kaunar Ayla sosai da sosai, cikin dabara ta taimaka mata suka wuce sama, miƙewa ita ma Aunty ta yi dan ta bi bayansu, shima dai Irfan miƙewa ya yi ya fice daga Palon dan ya ba su waje su sha hirarsu. Bayan Hajiya Batula ta kai Ayla ta dawo, nan fa suka ba ke hira su uku, Abbi, daddy, da kuma ita Hjy Batular, sai hiran baya suke yi. Misalin karfe 6:30 Imran ya shigo tare da Rimsha, yadda su Akila suka bar su Hjy Batula haka su Imran suka zo suka same su. Tambaya Imran ya yi akan ina su AKILA, suna sama Abbi ya bashi amsa, cewa Rimsha ya yi akan ta bi su sama su zauna tare shi kuma bari ya duba Irfan yana zuwa. Da haka suka rabu, sai kallon Rimsha Hjy Batula take yi, ɗazun ribibi sun yi yawa, bata samu damar ganin Rimshan ba sai yanzu da su Nawid suka tafi, komai ya saitu. "Batula lafiya kike kallon Rimsha haka?" Cewar Abbi, ajiyar zuciya ta sauƙe kafin ta ce "Wlh ta yi mani kama da Baban su HAROON ne, sosai fa shiyasa nake kallonta". "Babansu Haroon kuma?" Cewar Daddyn Jelly, E ta amsa da shi. "To ko dai suna da dangantaka ne?" Cikin sauri ta girgiza kai tana faɗin "Kai ina baban su Haroon ba shi da wasu bakin ƴan uwa da ban sansu ba, kama dai ce kawai, shima kamar ai hancin ne da ido sai yanayin fuska". To masu karatu kada ku mance Mummy'n Rimsha ƴan uwan mahaifinta ƴan Maiduguri ne, kuma a halin yanzu can ta tafi neman ƴan uwan nata, zata iya yi wu suna da alaƙa da mijin Hjy Batula, mu dai je zuwa dan jin yadda wannan cakwakiya zata warware mana. Haka suka ci-gaba da yin hirarsu while su kuma ƴan matan suna sama suna zuba iya shege san ransu, AKILA ta tasa su a gaba tana koya masu shagwaɓa kirsa da kisisina na jan hankalin miji, Aunty dai ta saki baki tana kallon yadda Akila ke zuba masu lecture. Riƙo kunnan jelly da kyau Akila ta yi tana faɗin "Wlh ki natsu ki sanya mani yayana cikin farinciki, kin san dai yanzu ba zan bi bayanki ba sai an buga football, idan yaya Imran ya cinye kwallon sai na dawo bayanki, amma dai yanzu gaskiya ina bayan ɗan uwana, ki saurareni da kyau, fagen shagwaɓa ba sai na koya maki ba wannan kece shugaba, kin kware ta wannan hanya, sai dai mu koma salon iya magana, iya magana yana sanya miji ya yi abu ko bai yi niya ba, idan kina magana da shi kuma ki rinƙa ɗan yin wasu abubuwa kamar karamar yarinya, hakan zai ja hankalinsa ba kaɗa ba, amma fa ki tabbar kin iya yin hakan sosai ta yadda zaki sanya shi jin daɗi ne ba wai ki ɓata mashi rai ba, dan wata idan ance ta yi abu kamar yarinya sai ta je tana yi mashi shirme da hauka tasa ya ji kamar ya ɗauketa da marin da sai ta suma a wajen dan haushi, to na dai gaya maki ba haka ake yi ba, yanzu idan kina son ce mashi ku fita zuwa anguwa, ba kawai zuwa zaki yi ki ce mashi yaya Imran zamu fita zuwa anguwa ko? Ba haka zaki yi ba, zuwa zaki yi ki kwanta a jikisa, dama gaki da shegen san jiki kamar mage, to idan kika kwanta, ki yi ta yi mashi kukan shagwaɓa ki na ɗan jan hancinsa, idan ya ce maki lafiya, ba haka kawai zaki ba shi amsa ba a'a, cikin salo mai ɗaukar hankali ki juya idanun nan na ki, ki yi mashi fari kafin kice kyau ka yi mani mijina aljannata, shiyasa na ji ina son in zo in yi ta kallon fuskar ka ina ɗan jan wannan kyakkywa kuma dogon hancin naka, wlh ko bai nuna maki ba sai ya ji daɗi a cikin ransa, ki cigaba da zuba mashi shagwaɓa da wasanni na taɓa wasu ɓangarori daga jikinsa, sai kun yi nisa kun lula duniyar da ba zai iya yi maki musu ba a can, sannan ki gaya mashi abin da kike so ta sigar da dole ya amince ko da baya so ɗin, sannan kuma kada ya kasance lullun ta hanya ɗaya zaki rinƙa bi wajen isar mashi da saƙon abin da kike so, idan ya zamana ta hanya ɗaya ne to zai gane ki ya zama watara ma da kin zo kin fara yi mashi ma zai ce kawai ki faɗi abin da ya kawo ki dan yasan ba haka nan ba, so akwai hanyoyi da dama da zaki rinƙa isar mashi da saƙo ba tare da ya gane hakan ba, ciki kuma har da girki tare da kula da shi a lokacin da yake cin abincin, idan da dama ki rinƙa bashi a baki, kuma kada ki yarda ya zamana sai kina son abu a wajensa ne zaki nuna mashi soyayya, a'a kullun ya zama cikin zuba mashi sabon salon soyayya mai rikitarwa kike yi, mace bata tsufa kuma bata girma a gaban mijinta, dan haka ki saki jiki ki kula da shi, wlh miji ko tsohone yana son kulawa, sai kuma batun sanya kaya, kada ki yarda ki ce zaki sanyawa yaya Imran ɗina manyan kaya, idan na ji kin yi hakan zamu haɗu dake ne, idan kuna ɗaki ku biyu, ki samo wasu shegun kayan barci masu birkita tunani da kuma lissafin ƙwaƙwalwar ɗan Adam, su zaki ɗauko ki sanya ki taho gare shi, wani lokaci kuma kada ki zo kai tsaye, ki rinƙa ɗan yawo ta gabansa kamar mai yin wani abin, zaki ga da kansa zai jawoki jikinsa dan ya ƙosa ki zo ke kuma kin ki, kinga gidan yaya Imran ke kaɗai ce, to dan haka duk wasu manyan kaya ki ajiye su a gefe guda, ki kwaso shegun kaya dan a buga harka, sannan kada ki rinƙa sanya breziya da daddare, ina ki barsu su kai mashi saƙon suna da buƙatar shi, idan ya gansu a tsaitsayen nan ba karamin haukace miki ya birkice maki zai yi ba, kada ki kuskura ki bar mani kwakwalwar yaya Imran ta zauna shiru har ta yi tunanin wani abin, idan yaya Imran zai yi wani tunani to ya zamana tunaninki ne ke kaɗai da kuma kayan abubuwanki, ga ki dirarriya, dan haka ki diranwa tunaninsa a ko da yaushe ki......" Bata karisa ba Aunty ta rufe mata baki da hannunta tana salati domin yau ta ji abin da ya fi karfinta. Gaba ɗaya cikin ɗakin babu wanda bai nisa ba, wasu kam irin su Rimsha har da jan dogon numfashi. "Akila shekarunki nawa?" Cewar Aunty, ta yi maganar tamkar ba lafiya ba, muryarta cike da mamaki tab, bata taɓa jin karatu irin na Akila ba, ba wanda ta taɓa jin yana bada irin wannan shawari sai a bakin Akilar. Cire hannun Auntyn Akila ta yi daga bakin nata tana faɗin "Aunty me ya faru? Shekaruna ai ɗaya ne da Umaisha 18 to 19 muke". Mamaki ya hana Aunty sake yin magana. Akila na ƙoƙarin sake tambayar auntyn ko dai lafiya. Sai ta ji wayarta ya yi kara alamar shigowar sako. Wani irin sihirtaccen kayatatcen murmushi ne ya bayyana akana face nata domin tasan sakon abin son ta abin begenta ne wato ɓoyayyen masoyi. Zuba mata ido gaba ɗaya ɗakin suka yi har da jelly mai ɗaukar lecture ma binta da ido ta yi, yau Jelly ta natsu tsit tamkar ba ita ba, duk cikinsu harta aunty ba wanda bai karu da karatun nan da Akila ta yi masu yanzu ba, sai saka zancen a ransu suke yi, kowa yana saƙa yadda zai yi wa masoyinsa, ita kuwa Rimsha har ta hangota tana yi wa Lion hakan, ita kam Hanan ta dai ɗauki karantun ta ajiye a cikin zuciyarta dan bata da masoyin ma bare kuma ta ce zata yi tunanin yi mashi, ta dai ajiye ne sai Allah ya kawo mata sai ta yi mashi, Umaisha kam jirama take yi suyi sallar mangariba ta je ta zubawa mijinta kala kala sala sala abin data koya na yau, ita ma dai Aunty ta ɗauki wasu daga ciki, ta kuma yi niyar kwatanta yi wa Abbi ta gani. Ɗaukar wayarta Akila ta yi ta buɗe saƙon nasa, sai murmushi take yi, a cikin zuciyarta ta fara karanta saƙon nasa. "My heartbeat gaskiya ke karshece wajen iya soyayya, wannan irin lecture haka? Anya idan muka yi aure zaki barni na fita kuwa? Gaskiya na ji daɗi kuma na mori mata sosai da sosai, Allah ya mallaka mani ke my heartbeat ɗita ɗaya tamkar da billon, nasan kina kewar voice na, amma ki yi mani afuwa zuwa karfe 10 dare zan kira ki ko? Yanzu abubuwa sun ɗan sha kai na ne, amma ayi mani afuwa gimbiyata". Duk sun zuba mata ido suna kallon yadda take murmushi tana kallon screen ɗin wayarta, a tunanin Umaisha da Irfan take yi, shi take yi wa wannan murmushi, saƙonsa take karantawa, dan a iya saninsu shi kaɗai ne saurayinta. Suna a haka har aka kira sallar mangariba, a tare suka miƙe dan su je su yi alwala, jelly dai kwanciya ta yi dan bata Sallah, ita kuwa Akila bayan ta yi alwala kafin ta yi sallah sai da masoyin ɓoye ya tura mata massage akan ta yi masu addu'a sosai idan ta yi sallah, dama already ya saba faɗa mata hakan, duk idan zata yi sallah sai ya yi mata massage akan idan ta yi, ta yi masu addu'ar zama mata da miji su mallaki juna, kuma haka take yi, duk in ta yi sallah sai ta yi masu addu'a akan zama mata da miji, daren jiya ma har istihara ta yi akan su shi da Irfan, tana addu'ar Allah ya zaɓa mata wadda ya fi zama mata alkhari a cikinsu, amma abin mamaki shine duk da bata san waye masoyin ɓoye ɗin ba tana ji a jikinta shine zaɓin da Allah ya yi mata, saboda ta fi samun kwanciyar hankali idan ta kasance suna hira da shi, sannan tana yawan mafarkin wata kyakkyawar face ɗin a matsayin tasa, ba barcin da zata yi ba tare da ta kalli wannan fuska ba, sai dai kuma wannan fuska data Abbanta take yi mata kamanni, shine babban abin da yake damunta, wadda take mafarki a matsayin fuskar masoyin ɓoye kamar Abbanta dan dai shi yaro ne kawai, kuma mafarki ai zata iya mai da mutun yaro ta kuma mai da shi babba. Bayan sun yi sallar isha ne Jelly ta tsara wankarta sosai, ta shirya cikin irin kayan da Imran ya ce yake buƙata, Aunty ta bata wani pant ɗin tare da Always dan ta sanya, karɓa ta yi ta sanya a jikinta sannan ta nufi palo tana gayawa Akila ta tafi wajen yaya Imran dan tun ɗazun yake kiran layin daddy da wayar ke a hannunta. To AKILA ta ce tare da kara ja mata kunne akan ta natsu ta yi abin da ya dace, kada ta yi mashi shirme, dawowa ta yi ta ringume Akilar kafin su yi sallama, ta rungumi Ayla sannan ta rungumi Rimsha tare da Umaisha suka yi sallama. Jelly na fita massage ɗin Masoyin ɓoye ya shigo wayar Akila, cikin zumuɗi Akila ta duba, saƙo ne kamar haka. "Heartbeat ɗina wannan yarinya da ta fita yanzu ta yi mani kama da brother na fa, sai dai ba sosai ba ido ne ya yi kama". Shiru ta yi tana haɗa maganganun a cikin ƙwaƙwalwarta, tunani take yi koma waye masoyin ɓoye nan tana ji a jikinta na kusa da ita ne, kuma da wuya idan ma ba ɗan uwanta bane domin a mafarki tana kallon shi mai kama da Abbanta, yanzu kuma ya ce idanun Jelly kamar na ɗan uwansa, to kenan akwai alaƙa a tsakaninsu ne ko yaya. Tana tsaka da tunani massage nasa ya sake shigowa. "Heartbeat ki ɗauki duk abin da zuciyarki zata gaya maki a kaina, amma dai am sorry to say kamar ni ba mutun bane, but kada ki ji tsoro kin ji ko? Ni bana cutar da kowa sai dai ya so kowa da alkhari, sisterki da ta fita yanzu abin da yasa na yi magana akanta saboda tana da manyan idanu sosai kamar wannan ɗayar sister ta ki wato Rimsha, girman idanun nasu yasa nake ganin kamar brother na, amma ba wani abu bane, ni dai fatana kada ki gujeni". Wurgar da wayar tata ta yi jin ya ce shi ba mutun bane, nan take jikinta ya fara kerma, da sauri ta diro kasa daga saman gadon ta yi waje wanjensu Abbi dan ma kada ya kamata. (TO FA YAU DAI GA AKILA NA GUDUN MASOYIN ƁOYE🤣🙃) Su Umaisha kuwa ganin ta fita yasa suma suka miƙe suka fice suka bar wayar tata a tsakiyar gado, ita ma Ayla tana jan kafa a hankali haka ta bi bayansu. Suna fita wayar ta kawo wutar screen da kanta daga nan kuma ta shiga massage da kanta ta goge massages ɗin ɓoyayyen masoyi na karshe daya turo na cewa shi ba mutun bane, wayar da kanta ta goge saƙon sannan wani saƙo ya shigo na ɓoyayyen masoyi akan wasa yake yi mata shi mutun ne, daga nan wayar ta yi switch off na kanta da kanta. To fa Babbar al'amari kenan A ɓangaren Jelly kuwa, bata sanya hijabin kamar yadda Imran ya ce mata ba, ta dai sanya wasu shegun riga da wando da Aunty ta bata daga cikin kayan lefenta, su ta sanya a jikinta sai tashin kamshi take yi, duk ilahirin shape da wasu halittu na jikinta sun bayyana, kayan sun matseta sosai ne saboda ta fi Aunty cikar halittu. A palo ta isko su daddy, Abbi, daddy, Auntyn, Irfan, Hjy Batula, da kuma Akil, sai hira suke yi, shi kuma Imran yana zaune a garden na gidan yana jiranta, tun da suka dawo sallar isha ya wuce can. Kada ku manta duk abin da ake yi Ommu tana sane tana jinsu kawai dai fitowa ne bazata yi ba dan bata jituwa da dangin na Abbi. Zuwa ta yi ta rungumi daddy tare da yi mashi kiss a goshi, shima kiss ɗin ya yi mata, wucewa ta yi ta nufi waje ba tare da ta yi wa kowa magana ba domin bata sansu ba. "Jelly baki gaishe da su yaya Deen ba". Cewar daddynta, juyowa ta yi fuska ɗauke da murmushi tana faɗin "Daddy i don't know them ai, among of them who is Yaya Deen ɗin?". Da hannu ya nuna mata waye yaya Deen a cikin su, juyawa ta yi zuwa jiki Abbin ta haye tana faɗin "Yaya Deen good evening?" Akil ne ya ce mata "Bappa zaki ce not yaya Deen, he is your uncle not your brother". Ɗan kallon Akil ɗin ta yi kafin ta ce "Okey tom uncle good evening". Jelly ba dai son jiki ba, ta ce bata san su ba, amma ta hayewa Abbi jiki ta kwanta. Da fara'a Abbi ya amsa sannan ya tambayeta wannan kwalliya da ta ci kuma sai ina, ba ko kunya ta gaya mashi yaya Imran ne yake kiranta kuma shine ya ce ta yi mashi kwalliya haka, yau duk rashin kunya irin na Akil sai da jelly ta sanya shi jin kunya, domin a irin yadda yake kallon Imran ustadz bai kai shi har zuwa wannan layin na sanya mace yin wasu dressing ɗin ba. Shi kuwa Abbi danasanin tambayar tata ya yi domin ta fara bashi labarin har irin kayan da Imran ya ce ta sanya mashi, da dai daddy ya ga zata tonawa yaron shi asiri sai ya ce ta tashi ta tafi surutun ya isa haka. Ba musu ta miƙe tare da miƙawa daddyn wayarsa ta fice abinta, da ido daddy ya bita yana mamakin tare da tausayawa Imran, dan yana da aiki babba a gabansa. Tana fita ta nufi garden ɗin sai wani kwas kwas take da takalmarta mai tsawo. Gaba ɗaya wutar garden ɗin a kashe, wajen a akwai duhu, ɗan tsorata ta yi da ganin wajen haka, amma sanin cewa Imran yana wajen yasa ta karisa wajen da confidence nata. A tsakiyar wajen ta tsaya tana ƴan waige waige ko zata ga alamunsa, amma ina shiru. Tana ƙoƙarin juyawa sai ta ji an rungumeta ta baya, nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce "Yaya Imran ka bani tsoro fa". Murya can kasa kasa ya ce "Sorry my wife, ai so nake na tsorataki dama, amma kuma sai na ji na kasa". Ɗan murmushi ta yi kafin ta ce "Da ka tsorata ni kuwa da mun ɓata". Juyo da ita ya yi suna fuskantar juna a duhu, a hankali ya jawota jikinsa tare da riƙota ta bayanta yana haɗe goshinsu waje guda. "Meyasa baki sanya hijabin da nace ba?" Ya yi maganar cikin wata irinyar murya mai kwantar da hankalin mai sauraro. Sarkin son jini, kwantar da kanta a kirjinsa ta yi a shagwaɓe ta ce "Yaya Imran ai ni bana son hijabin ne". Wani irin yanayi ta jefashi yadda ta yi maganar nan tata. Riƙota da kyau ya yi suka zauna a saman ɗaya daga cikin kujerun wajen tana a saman cinyarsa. A daidai saitin kunnenta ya kawo bakinsa, cikin raɗa kamar wani zai ji su ya ce "Zaki bi mijinki mu tafi tare?" Tana daga lafe a kirjinsa ta ce "E zan bika mana". Wani irin daɗi ya ji wadda ya sanya shi natseta a jikinsa sosai da sosai. "Yaya Imran zaka ɓallani fa". Ta faɗa a shagwaɓe. "My wife zaki bawa mijinki damar yin kissing naki? Na yi ko sau ɗaya ne?" Girgiza mashi kai tayi alamar bata so, shiru ya ɗan yi kafin ya ce "To shikenan tun da baki so, ni ma bana so dan bana son abin da bakya so". Ya kai karshen maganar tare da fara shafa bayanta yana mai jan wani irin numfashi yana sauƙewa a hankali hankali. Jin abin da ya ce yasa ta ɗago kanta daga kirjin nasa tare da gyara zamanta ta haɗe fuskokinsu waje guda. "Yaya Imran ni fa matarka ce, me yasa zaka tambaye ni dan zaka yi mani abin da ya kasance halak ɗin ka?" Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe ba tare da ya yi magana ba ya haɗe bakinsu waje guda ya fara bata hot kiss, shiru ta natsu tana karɓar saƙon da yake aika mata da shi, while a can cikin gida kuma, sun koma saman table dan cin abincin dare. 💖💖TRIPLETS💖💖 dedicated to AISHA BAITA JIDDAH 💘 (MUMMO RIMSHA) E89-90💖 Jin abin da ya ce yasa ta ɗago kanta daga kirjin nasa tare da gyara zamanta ta haɗe fuskokinsu waje guda. "Yaya Imran ni fa matarka ce, me yasa zaka tambaye ni dan zaka yi mani abin da ya kasance halak ɗin ka?" Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe ba tare da ya yi magana ba ya haɗe bakinsu waje guda ya fara bata hot kiss, shiru ta natsu tana karɓar saƙon da yake aika mata da shi, while a can cikin gida kuma, sun koma saman table dan cin abincin dare. Akil ba kunya ya rinƙa bawa Umaisha abinci a baki kamar yadda suka saba, yau sai wani yauki Umaishar take yi mashi kamar mace mai karamin ciki, Hjy Batula ta lura da hakan, shiyasa ma ta zage take ta faman turawa Umaishar duk abin da take buƙata, har da tambayarta ko akwai wani abin kwaɗayi da take buƙata, kamar an ce mata cike Umaisha ke da shi, Abbi ma dai ba'a barshi a baya ba, tsab ya gano ƴar tasa kamar akwai ajiya a jikinta, shiyasa shima yau yake bata kulawa ta musamman, oga Akil kuwa ya san komai domin ko wani motsi na matarsa tsab ya san komai, sai dai wani sain nuna mata yake yi kamar bai san komai ɗin ba, dan su cigaba da zaman lafiya, dama kuma haka ya dace namiji ya kasance, ba komai ne zaka rinƙa nunawa mace ka sani ba, domin mata ba su son ka rinƙa nuna masu kamar kai ka san komai ɗin kana fariya, idan hakan tana kasancewa to da wuya a rinƙa samun jituwa a tsakaninku. Akila kuwa duk ta susuce ta zama wata sukuku da ita, tunanin abin da masoyin ɓoye ya ce mata ne gabaɗaya ya birkita mata kwakwalwa, ta zama kamar ba ita ba, Irfan ya yi rarrashin duniyar nan akan ta gaya mashi mene ne yake damun ta, amma ina taki gaya mashi, ba dan ya so ba ya kyaleta. A ɓangaren gidan Lion kuwa. Lokacin da Areef ya farka daga barcinsa, ya farka ne yafiya lou kamar babu wani abin da ya faru, sai dai fa ya farka da ciwon jiki, gabaɗaya zafi jikinsa yake yi mashi, wayarsa ya ɗauka dake a saman bedside drawer ya duba time, 6:40 pm dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali kafin ya fara duba cikin wayar tasa, miss calls ɗin daddynsu ne da Aseef a cike a ciki, gobe Musharraf zai ta so shiyasa Aseef yake ta kiran shi a waya dan ya ji jirgin ina zai bi domin da jirgin kasuwa zai zo, ya bi jirgin Spain ne ko yaya. Layin Imran ya fara kira akan ya aiko mashi Rimsha ta ɗebo mashi drinks a freezer dake a kitchen, na cikin bedroom nasa sun kare, tun ɗazun ya so cewa a kawo mashi, amma bai sami dama ba, Saboda lokaci jikinsa na ya mashi ciwo sosai. Number Imran bata shiga hakan yasa ya ce bari ya kira Lion, bai kai ga kiran Lion ɗin ba kiran Aseef ta shigo, ɗaukar kiran ya yi video call ne, dan Aseef bai cika kiransu normal call ba, sai dai video call dan ya gansu su gan shi. Har lokacin bawan Allah murmushi ne akan face nasa, ya fito ne daga gym yana nufar cikin gida, iya singlet da shot ne kawai a jikinsa, sai haɗa zufa yake yi, kewar ɗan uwan nasa ne ta takura mashi ya sanya shi ya kira shi dan suga juna ko ya ɗan ji daɗi. Areef bai san time da murmushi ta subce mashi ba ganin ɗan uwan nasa yana murmushi. "Aseef daga ganin face naka akwai wata a kasa, so what is this?". Kara faɗaɗa murmushin sa ya yi kafin ya ce "Ina murna ne na ɗan iya kalmomi almost 10 a cikin yaren Hosa (Hausa)" kunsan harshen nasa ne a lanƙwashe take akan yaren Hausa, shiyasa bai iya kiran Hausar ba. Girgiza kai Areef ya yi yana mamakin yau Aseef ne da karya, to fa babbar magana, abin da bai taɓa kwatantawa ba, za su iya rantsewa da Allah koda a bayan Aseef ɗin ne, zasu iya bugan kirji suce bai taɓa yin karya ba, haka yake duk abin zai fito daga bakinsa to gaskiya ce, hakan yasa duk gidan bayan Lion idan ya yi magana babu mai musa maganar tasa, domin kuwa idan sun musa ma kansu suka yi wa, shi dai gaskiya ya faɗa. Sosai Areef ya zuba mashi idanu dan ya karanci me a fuskar tasa da ya yi mashi karya akanta yau, abin ya ɗan ɗaure mashi kai. Ganin Areef yana ta kallon shi ne yasa ya ɗan kawar da wayar daga saitin face nasa yana faɗin "Why are you looking at me like this? What are you looking for?". Murmushi Areef ya saki domin ya kuma ganowa karara akwai abin da Aseef ya ɓoye mashi, da alama kuma damuwa ce domin wannan murmushi da take kan face ɗin nasa ta dole ce, ba kamar murmushin da ya saba yi masu bane, idan baku manta ba shima Lion lokacin da Aseef ɗin ya kirashi da kallo ɗaya ya yi mashi ya ce to me Aseef kuma ya jajuɓo masu, kunga kenan akwai dai wani abin a kasa kamar dai yadda suke tunani, amma ya kafe akan lallai shi bashi da damuwar komai, amma kuma da alama Lion ya san da damuwar shiyasa ma bai tambayi dalilin shigarta ba. "Aseef where is uncle Musharraf?" Cikin sauri ya dawo da wayar saitin face nasa yana faɗin "Uncle yana cikin gida yana karisa shirye shiryensa dan kaga jirgin safe zai bi ai". Ya yi maganar tamkar zai yi kuka, jinjina kai Areef ya yi domin ya gano me matsalar dama kuma ya yi mashi tambayar ne dan ya bugi cikinsa ya gano me ainahin damuwar, sai dai kuma koma yaya ba zai iya barin Musharraf a Usa ba tun da basu nan, yasan halin ƴan uwansa sarai, ko daddy idan ya san Musharraf musulmi ne yana iya kashe shi da kansa, gara idan da suna nan ma, ko Lion ba zai bari ayi mashi wanin abin ba tun da ya kasance musulmi. Sun jima suna hira Areef yana kara karfafa mashi gwiwa akan ya gama exams ya zo ya same su, tare kuma da kwantar mashi da hankali akan kada ya damu da tafiyar Musharraf, shi dai kawai ya tsaya ya yi karatu, da haka suka sha hira na ƴan uwa masu masifar kaunar junansu kafin su yi sallama Areef ya kira Lion bai ɗauka ba, hakan yasa ya yi kokarin ya miƙe da kansa yana jan kafa ya fito Palo, shi kuma Aseef toilet ya wuce dan yin wanka bayan ya ɗaura wayar a saman bed nasa kenan. Babu kowa a palon da Areef ya fito, a hankali yake jan kafarsa da yake a kirji akayi mashi aikin, shiyasa ma yake iya takawa a hankali, da kyar ya haura sama ya nufi ɗakin da yake zaton ita ce ta Lion ɗin, Sakamakon kamshin perfume nasa da ya yi yawa a ɗakin. Babu kowa a cikin ɗakin sai saukar ruwa dake tashi daga toilet alamar yana wanka kenan. Saman gado Areef ya haye ya kwanta yana sauke numfashi ya kawo da kyar. Idan muka koma gidan Abbi kuwa, IMRAN & JELLY sosai ya yi kissing nata son ranshi, bata hana shi ba, kuma bata yi mashi kuka ba domin bata a hayyacinta, ya gama kashe mata jiki dukka, tuni ya sanya ta ta lula duniyar sama jannati, ba ta ma san time daya zura hannunsa a cikin rigarta ba, sai dai ta ji wani irin yanayi mai wuyar misiltawa ya kara ninkuwa mata a jikinta, kankame shi ta yi tana sakar mashi wani irin numfashi wadda ke kara rikitar da shi. Hakan yasa ya kara birkice mata yana aika mata saƙonni babu wasa, daga karshe ma kwantar da ita ya yi a saman kujerar ya yi mata rumfa da kirjinsa tare da ɗage rigarta sama ya capco nipple nata ya fara tsotsa kamar sweet. A wannan lokacin ne kuma ta samu damar sakar mashi kuka domin nipples ɗin sun fara yi mata zafi, ya murjesu sosai sannan kuma ya zo yana tsotsa mata. Can kasa kasa ya fara jiyo kukan nata, da kaɗan da kaɗan har ya jiyo sautin tata da kyau, idanunsa a rufe, da kyar ya koma gefenta ya zauna tare da jingina kansa da jikin headboard na kujerar yana sauke wani zazzafar numfashi. Ita kuwa cigaba da kuka ta yi duk da ya kyaleta ɗin ma, ba ita ta yi shiru ba har sai da ya rarrasheta sannan ta yi shiru, amma fa ya sha fama wajen rarrashin nan nata kafin ya samu ta yi shiru. Rumgumeta ya yi suka yi shiru, ban da saukar numfashin su dake tashi a hankali babu wani abin da zaka ji a wajen. A cikin gida kuwa, sun kammala cin abinci lafiya lou, Akil ya ce su za su koma gida sai jibi za su zo, kiransa gefe guda Hjy Batula ta yi dan su yi magana, da yake yanzu da ya yi aure ya yi sauki sosai sai ya bi goggon tasa, da a baya kafin ya yi aure ne kuwa da ba zai je ba sai dai ta yi maganar tata a nan. Sun ɗauki minti talatin suna magana kafin ya dawo cikin palon, sallama suka yi wa su Abbi, sannan ya rungumo matarsa a gaban kowa, ba kunya haka suka nufi waje. Ba su kai ga fita ba muryar Ommu ta katse su da cewa "Umaisha zo mu je ɗaki ina da magana dake". Gaba ɗaya palon zuba mata idanu suka yi, mamaki ne ya kama su dama tana cikin gidan nan, Hjy Batula kuwa mamaki ne ya kamata dama Hadiza yar kawarta matar yayanta ne ko yaya abin yake ne bata gane ba. Abbi kuwa ɓata rai ya yi ya ce maza su wuce su tafi dare ya yi, meyasa tun da safe da suka zo bata fito sun yi maganar ba sai yanzu? Haka ba dan ta so ba tana ji tana gani Umaisha suka wuce da mijinta, sai dai kuma ta ci alwashin dole ta nemi number Umaisha ko ta halin yaya ne ma, ta waya ma abin zai fi tafiya mata daidai a cewarta. Salati Hjy batula ta sanya, dan sai yanzu ta gane wace ce Hajiya Hadiza, tun tana amrya amrya tun da ta haifi Irfan yana jariri rabon da su sake haɗuwa sai yanzu, shiyasa ma bata gane ta ba, shekaru wajen 27 ai ba wasa ba, dole zata canza. Har wajen mota yau ma suka raka su AKil, ya bar Akila a nan ta kwana dan ta nace lallai da Jelly zata kwana yau, ga shi kuma basu isa suce Akila su tafi da Jelly ɗin su je gida su kwana ba, saboda Ammie ba zata yarda ba, shiyasa kawai suka barta su kwana da Jelly'n a nan shi ya san me zai gayawa Ammie idan ta tambayi ina Akilar. Akil dai bai samu damar sallama da Imran ba, domin Imran baya nan duniyar, yana can sama jannati, haka ya ja mota suka wuce shi da matarsa su Abbi kuma suka koma cikin palo. Imran dai bai dawo da jelly ba sai wuraren karfe 10 na dare, sannan ya dawo da ita cikin gida, lokacin babu kowa a palo, daddyn Jelly ya wuce part nasa shi da Aylarsa, shi ma Irfan ya wuce part nasa bayan ya yi ya yi akan Akila ta gaya mashi menene yake damunta taki ya, haka ya hakura damuwa cike fal ransa ya wuce part nasa ya kwanta kawai, amma dai barci ta gagara zuwa mashi, sai tunanin heartbeat yake yi, yayin da ita kuma take tunanin wani na da ban. --- Saman table Imran ya haye tare da zuba masu abinci shi da amaryarsa, shima dai kamar Akil, a baki ya rin ƙa bata tana ci tana zuba mashi shagwaɓa, idan da sabo ya saba bata abinci a baki tun bata kai haka ba, kullun idan ya je Kano daddy ya huta, shi ne mai bata abincin, hakan yasa suka saba sosai. Su kuwa su Rimsha suna ɗakin Hanan, da ita Rimsnan da Akila sai Hanan da kuma Hjy Batula dake ta yi masu karin lectures, Aunty kuwa ta shige ciki ita da mijinta abinta, dan yau Hjy Hadiza ta kyale mata abin, da alama akwai abin da take shiryawa ne Shiyasa bata bi ta kan Abbin ba. A takaice dai Imran sai karfe 11 suka baro gidan Abbi shi da Rimsna bayan ya yi wa Jelly alkawarin gobe zai zo da Rimsha ya haɗa su suje wajen lalle da gyaran gashi, dan dama tun kwana biyu da suka wuce Rimsha take damunsa akan tana son ayi mata kunshi. Abin da ya sanya Imran bai tafi da Jelly ba shi ne ba'a gidansa yake ba, ba zai iya bari a kaita gidansu kuma baya nan ba, saboda yasan irin kiyayyar da Ammie take yi wa familyn Abbansu, wannan dalili ya sa ya ce da daddy a barta a nan zuwa next week, daddy bai musa mashi ba domin shima dai har cikin zuciyarsa baya son yar tasa ɗaya tilo a duniya ta yi nisa da shi bayan rabuwarsu na ƴan watanni, abin akwai wahala amma ya zai yi, ya zama dole wata rana hakan ta faru. Da haka dai suka yi sallama ya ɗauki Rimsha suka koma gida, amma sai da ƴan sandan kan hanya masu kamen dare suka tare su suna tambayarsu daga ina suka fito, ina Imran zai kai karamar yarinya kamar Rimsha a cikin daren nan, domin babu alamar kamanni a fuskokinsu bare ace ƴan uwa sa ce. Ba musu ya gaya masu, barinsu suka yi suka wuce bayan sun gama ƴan dube dubansu a cikin motar dan tabbatar da babu wani abu na cutarwa da Imran ɗin ya ɗauko, sai da suka tabbatar babun ne sannan suka basu iznin wucewa, lokacin da suka dawo gida, Lion na tsaye a balcony bedroom nasa, bai yi barci ba, yana riƙe da cup mai shegen kyau a hannunsa, da alama coffee yake sha, kun san kuma coffee tana ɗaya daga cikin abin da yake sha idan yana cikin farinciki, to wannan ma haka ne da alama daren yau dai yana cikin farinciki, sai dai kamar kullun ba'a ganewa, kuma da alama farinciki tasa tana da alaƙa da samun nasara akan aikin Areef da yake yi. Kallo ɗaya ya yi wa su Imran ya mai da kallonsa kan wayar dake a hannunsa, bathrobe milk color ce a jikinsa, ya ɗaure dark black curly hair nan nasa a baya, ya bar wannan guntu na gaban goshin, kamar dai kullun sai tashin fitinannen kamshi perfume ɗin nan nasa yake yi, da yake dare ta yi sosai ga kuma blue light a wajen, sai fuskarsa ta kara wani irin haske saboda ba hasken rana mai disashe hasken duk wata haske. Cikin gida su Imran suka wuto sai kallon saman Rimshan take yi tana kallonsa, duk da ba wani kallon face nasa da kyau take yi ba. A palon sama suka rabu da Imran, kowa ya wuce bedroom nasa dan yin wanka ayi shirin barci. Haka kuwa akayi kusan a tare suka yi wanka suka shirya cikin kayan barci. Rimsha ta kwanta bayan ta sanya kayan barci riga da wando launin navy blue, shi kuma Imran launin purple ya sanya, ita Rimsha ta kwanta tare da ɗaukar wayarta tana dubawa, uban miss call na A'A ne turun wadda za su kai miss call 66 mamaki ne ya kamata, ita yau kwata kwata ma ta mance da wata waya, shere miss call ɗin ta yi ta shiga hotuna, kamar kullun sai da ta kalli gabaɗaya hotunan Lion sannan ta ajiye wayar tare da yin addu'ar barci ta kwanta. Shi kuma Imran sai da ya kira layin daddy suka zuba soyayya da jelly har 1 sannan ya ce su yi barci bayan ya sha shagwaɓa iya son ranta sannan ta kyale shi, bawan Allah rungume da pillow yana murmushi ya yi barci. Washegari bayan sun karya kamar yadda ya faɗa haka ya ce Rimsha ta shirya su je sayayya daga nan ayi mata kunshe sai gyaran gashi ita da kanta baya kitsuwa saboda tsantsi, to ta amsa da shi sannan ta shirya. Kafin su fita sai da suka fara shiga wajen Areef duk da a tsorace suke da shi, amma Imran ya yi imanin ba wata matsala domin Lion ko zai mutu ba zai taɓa barin ɗan uwansa a cikin matsala ba, yana bala'in kaunarsu fiye da kansa, sune komai nasa, idan ya ga fuskokinsu ma musamman Aseef har wani daɗi yake ji da yake dai ba'a gane mashi ne kawai, kuma a zahirin gaskiya Lion ya fi kaunar Areef akan Aseef, abin da yasa jama'a suke ganin kamar ya fi son Aseef saboda Aseef a mai rauni sosai ya taso, ya tashi da wannan ciwo wadda yasa gaba ɗaya familyn William jacop suka ja shi a jiki sosai, hakan yasa shima Lion ɗin ya fi kusanci sosai da Aseef ɗin akan Areef, amma ko da yanayin yadda suke mu'amala ya ci ace mai hankali yasan cewa ya fi son Areef, saboda Areef na farko ma ya fi su saurin shiga ran mutane, duk da dukkansu akwai bala'in farinjini, amma shi Areef sauƙin kansa da rashin ja da manya ga son mutane yasa ya fi shiga rai, shi kuma Aseef kunsa yadda dai yake a baya idan ba Lion ba, ba wanda ya isa ya bashi umarnin akan abu, ko Areef sai dai ya lallaɓa shi su rabu lafiya, sannan kaifin ƙwaƙwalwa da basira yasa Lion ya fi kaunar Areef dan yana son mutane masu brain sosai, to Areef fa akwai ƙwaƙwalwa kamar dai Lion ɗin, ku da kun gani, mara ƙwaƙwalwa ba zai iya kwatanta abu ɗaya a cikin waƴan da Areef ya yi ba. Da sallama ɗauke a bakinsu suka shiga cikin ɗakin, yana zaune a saman bed nasa, yau ya zuro kyawawan fararen kafafunsa kasan bed ɗin. Ya ilahi ya lillahi Rimsha ta ruɗe da kanin kafafunsa, musamman yatsunsa ga kunba (farce) kafar tasa sai wani kyalli suke yi farere tas kamar madara, Allah ya yi masu halitta wadda ina da tabbacin ko su aka ce su yi halittar kansu ba za su yi ya wuce hakan ba, saboda sun hallitu kyau iya kyau, kuma Allah da ikonsa dukkansu TRIPLETS ɗin halittar kafarsu iri ɗaya haka zali hannunsu har yatsun hannayen nasu iri ɗaya. Sai kallon kafafun nasa take yi, ganin haka yasa cikin zolaya ya ce "Kafar Lion ya fi nawa kyau fa". Hannu tasa ta rufe fuskarta tana murmushi. Zuba mata idanu ya yi sai kallonta yake yi kafin ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya sannan ya ce "Rimsha you are so very very beautiful, gaskiya ina matukar son ki da ɗan uwana, I don't know the reason why nake jin kin kwanta mani a raina, you are very lucky gaskiya, ban taba expecting cewa akwai wata rana da zan bawa mace goyon baya akan abu ba, and also my brother he is very lucky idan har ya same ki, cos na san ba zaki bani kunya ba, and then ba zaki taɓa ɓatawa ɗan uwana zuciyarsa ba, daga ni har su muna da bukatar mu sami soyayya wadda zata goge mana memory mu ta baya, mu iya soyayyar daddynmu kawai muka sani, yana da kyau yanzu mu san wani, am very sure ɗan uwana zai samu irin wannan soyayya a tattare dake, na san zaki yi mamakin faɗa da nake yi akan ɗan uwana ba akan kai na ba ko?" duk da na zayyano kyawawan zaton da nake yi maki, nasan zaku yi mamakin me yasa ni ban ce ina sonki ba sai dai in ce ina sonki da Lion, to kada ki yi mamaki, ki sani ɗan uwana ya yi mana abun da ba zamu iya biyan shi ba, sai dai mu yi mashi addu'a, yana kaunar mu fiye da kansa, kullun cikin yi mana abin da muke bala'in so yake yi, bamu taɓa ce mashi muna son abu ya ce mana a'a ba, idan kuma kika ga ya ce mana a'a to tabbas wannan abun ya bincika ba Alkhari bane a gare mu, idan muna cikin damuwa baya iya barci har sai ya fitar da mu, ɗazun na ce maki soyayyar daddy kawai muka sani ne domin ban yi niyar jan magana dake ba, amma a zahirin gaskiya soyayar da Lion yake yi mana tafi ta daddy, so kin ga kuwa yana da kyau muma duk abin da muka san zai zama na Alkhari a gare shi, to ya kama mu tsaya sosai wajen ganin mun sama mashi shi, sannan bugu da kari shi mutun ne mai wuyar sha'anin, shawo kansa akwai bakar wahala, idan muka samu ya yarda dake shikenan, amma yardar ne wahalar domin zuciyarsa ta fi cutuwa akan abin da mace ta yi mana sama da tamu zuciyar, bai iya gaba ba kamar yadda bai iya so ba, abubuwa biyun nan duk wanda yake yi to fa yana yi ne da gaske babu wasa, idan ya so ka to da gaske ne kuma zaka ji matukar daɗi, haka idan ya kika ba zai taba yi wuya ya sake son ka ba, mawuyacin abune ya waiga ya kalli mace, kai ina da wuya ma hakan ta kasan ce, amma muna sa ran hakan a tattare dake, shi wani irin bahagon mutun ne wadda duk yadda kuke ba zaki taɓa gane ina ya dosa ba, so na san abubu da dama akan shi, shi ne ma dalilin da yasa na tsaya akan ki, domin kina ɗaya daga cikin irin mutanen da yake so, na farko kina da tarayya mai kyau da kuma kyakkyawar zuciya, na biyu hankali, kina da hankali sosai, na uku ilimi, na huɗu son addini da kuma aiki da abin da addini ya koyar da mu, na biyar iya soyayya." Ya yi magana ta karshe na iya soyayya yana ɗaga mata gera ɗaya. Ɓoye fuska ta yi a jikin Imran tana murmushi. "Kina mamakin yadda aka yi na san abubuwa akan ki ko?". Cikin sauri ta ɗago da kan nata tare da gyaɗa mashi kai alamar e tana mamaki. "Zan gaya maki amma ba yanzu ba, sai dai kuma ki sani babu abin da ban sani ba a kan ki wadda Prof ya sani, sai dai prof ya ɓoye mani cewa ke ba kanwarsa bace, ni kuma na gano hakan ne ta wata hanya da shima sai nan gaba zan gaya maki, yanzu dai ina zaku je?". A wannan karon Imran ne ya bashi amsar in da za su je ɗin, shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Okey amma dai ya kamata mrs Saif ta dai'na fita gaskiya, cos tun da gyara za ku je tom ayi gyara sosai zan sanya Lion ya biya kuɗin gyaran ta hanyar da bai yi zato ba, kai dai prof idan ka ga kuɗi a account naka kada ka kira shi ma bare ka tambaya har ya gane plan na ne, Rimsha kada ki kuskura na ji ko na gani kin kula wani ko kin kalli wani, dan nima ina da bala'i kishi kamar ɗan uwana, to amma yau Monday me ya hana ki zuwa school?". Imran ne ya amsa mashi da shi ya hanata zuwa dan za su je shopping da sauran su, sosai Areef ya ɓata rai in da ya yi wa Imran ɗin faɗa sosai akan kada ya kuskura ya sake wannan gangancin dan za su fita ya hanata zuwa school, ba za su hakura da fitar sai ta dawo ba, ita ma faɗa ya yi mata sosai akan kada ya sake jin ta yi hakan. To ta amsa da shi sannan suka yi sallama, da kyar Areef ɗin ya miƙe dan ya rakasu, Imran yana ce mashi ya bari ya bari shi kuma ya ce a'a gara ya rinƙa takawa a hankali hankali zai fi mashi. Haka dai ya rakasu har harabar gidan sannan ya dawo ya zauna a palon kasa dan ya ɗan huta, har cikin zuciyarsa ya rasa dalilin da ya sanya yake kaunar Rimsha, har mamaki abin yake ba shi, ta shiga zuciyarsa farat ɗaya, amma dai ba wa kansa yake yi wa kaunar tata ba, ɗan uwansa yake yi wa, dan shima Lion ɗin ya samu farinciki a rayuwarsa, su kuma kullun Lion ɗin yana cikin sanya su farinciki, shi ne dai bashi da mai sanya shi sai dai su ɗin, to yana da kyau ya samu gaskiya, duk da abune mai matukar wuya, amma Areef yana sa ran tabbas da izinin Allah za su yi nasara, tun da har Aseef ma ya sa baki za su yi nasara, yanzu dai fatan ya samu lafiya kawai yake yi. Imran kuwa gidan Abbi ya wuce ya ɗauki Jelly, Hanan da kuma Akila suka wuce. Wajen gyaran jiki suka fara zuwa aka yi masu su dulka da sauransu. Yaran nan sun dawo kamar wasu taurari, daga nan sai kunshi da aka zana masu mai shegen kyau, Rimsha kamar wata tauraruwa haka ta zama, ga wannan curly hair nata ya sha gyara sai santin shi su Akila suke yi, da haka suka wuce shopping in da ya saya masu atamfofi da laces dan baya son irin shigar da Rimsha take yi a gidan nan nasu, saboda ya lura sojojin nan sun fara saka mata ido, ga shi kuma wani lokaci suna fita su barta a gidan ita kaɗai, kada wata rana su fita sojojin su cutar da ita, kuma idan suka cutar da ita ko da Lion ya hukunta su ko kashe su ma ya yi sun riga da dai sun cuceta dai, abin da ya wuce ba zai dawo ba, to maganin bari kada a fara, kuma ya duba gaba ɗaya kayanta dukka kanana ne, abayas ɗin ma basu da yawa sosai, wannan dalili yasa ya saya masu atamfofi da laces dan ayi mata ɗinkin hausawa ta rinƙa dressing mai kyau tana rufe jikinta dan gudun matsala. Daga wajen shopping ɗin suka wuce wajen ɗinki dan su bada kayan ɗinki. Da suka je Imran yaki yarda taila ya gwada su, shi da kansa ya karɓa ya gwadasu sannan ya gayawa tailan size nasu ya rubuta, sosai Rimsha ta ji daɗi da Imran ya yi hakan, domin dama a cikin zuciyarta ba yarda zata yi tailor ya taɓa ta ba. Tailor ya faɗi kuɗinsa Imran ya yi mashi transfer sannan suka wuce suka nufi gida. Sai misalin karfe 4 na yamma Imran suka dawo gidan Lion bayan ya mayar da su jelly da niki nikin kayan da suka saya gidan Abbi, ansha yawo ansha shopping da gyara, sun yi kyau fiye da tunanin mai tunani bare ma Rimsha kam ba'a magana, duk wanda ya kalleta sai ya sake waigawa ya kalleta. Suna shiga cikin palo kamar yadda suka saba ɗakin Areef suka fara shiga, baya nan, da mamaki suka fita suka haura sama. A Palon sama suka isko shi yana zaune saman sofa yana shan coffee. Kusa da shi Imran ya je ya zauna ita kuma Rimsha ta nufi bedroom nata dan ta ajiye niki nikin kayan hannunta bayan ta gaishe shi kenan. "Wannan murna da faricnikin fa na menene?" Cewar Imran, yana tambayar Areef ɗin. Fuska ɗauke da murmushi Areef ya ce "Daga yanzu zuwa ko yaushe zaka iya ganin uncle Musharraf da nake gaya maka, baka ga babu motar Lion a waje bane? Ai ɗauko mani shi Mark ya je yi a airport". Murmushi shima Imran ɗin ya yi zai yi magana kenan suka ji sallama a bakin kofar palon, a tare suka kai kallonsu wajen, Musharraf ne da Mark dake a bayansa ya yi mashi jagora ne zuwa cikin gida, sun je ɗakin Areef ɗin baya nan shi ne suka bi yo shi nan sama. Sai murmushi Areef yake yi tare da yi masu iso, shi kuma Imran a razane ya miƙe tsaye yana faɗin "Yallaɓoi dama kai ne uncle Musharraf ɗin?". Sai lokacin Musharraf ya lura da Imran dake wajen, jinjina mashi kai ya yi alamar e shi ne. Cike da murna ne ko tashin hankali ne Imran ya kasa gane wa, da karfi ya kwalawa Rimsha kira yana faɗin "Rimsha ki zo ga daddynki" ya yi maganar da turanci da yake yanzu ba su cika yin magana da hausa ba saboda su Areef ɗin da basaji, yaren, so sai turancin kawai ya bi bakinsu suma. Wani irin miƙewa Areef ya yi yana mamaki daddyn Rimsha kuma? Allah sarki shine dalilin da ya sanya Areef yake kaunarta kenan. Ita kuma jin abin da Imran ya ce ne yasa ta fito da gudu yayin da shima Musharraf ɗin ba shi da burin da ya wuce ya ganta ɗin, domin a nasa tunanin dukka family'n sa sun mutu basu raye, shiyasa time da ya dawo Nigeria ya ga gidansa a rufe da kwaɗo sai kawai ya zaɓi da ya bar kasar baki ɗaya tun da ba wanda ya rage mashi a cikin su mummy, kuma dama a tunaninsa yasan da wuya ƴan adawa su kyale mashi family'n sa tun da shima sun yi yunkurin kashe shi Allah ya tseratar da shi, wannan dalili yasa ya bar kasar gabaɗaya da nufin kuma ya barta kenan ba zai kara dawowa ba. Ganin tabbas da gaske daddyn tane yasa ta kwansa a guje ta faɗa jikinsa tare da sakin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, shi dai Areef ya kasa magana, sai ma murmushi da yake yi domin yanzu ya kara samun karfin gwiwa wajen taimakawa Rimsha akan abin sonta, tun da ta kasance ƴar cikin Musharraf to halin kirkinta ma ya wuci hakan domin duk abin da Musharraf ya rinƙa yi wa Aseef suna sane da shi, shi kuma Areef Allah ne kawai ya jarrabe shi da kaunar Musharraf ɗin ba ma wai dai abubuwan da ya yi masu ba. Rimsha an sha kuka kamar ba gobe, shima Musharraf sai da ya yi kwalla, Areef da Imran ne suka rinƙa rarrashinsu, da kyar suka yi shiru, duk fa wannan abin da suke yi Lion yana bedroom nasa yana jinsu, sai aikin latsa waya yake yi kamar babu shi a gidan. Bayan sun yi shiru komai ya lafa ne daddy yake tambayarta ina su mummy, nan take gaya mashi ita ma bata sani ba, ita kaɗai ta rage, daga nan ne sama sama ta shiga bashi labarin abubuwan da suka faru har izuwa yau, ya sha kuka kamar ƙaramin yaro. Akan siyasa aka tarwatsa mashi farincikinsa, wannan bala'i dame ta yi kama, kowa duniya kawai ya sa a gaba. Shi dai Mark yana tsaye ne kawai yana binsu da ido dan ba jin me suke faɗe yake yi ba, shi dai kawai ya ga ana magana ana kuka, shima dai Areef kukan kawai yake ganin ake yi, bayan haka baya gane komai tun da ba yaren yake ji ba, amma dai ya fahimci labari Rimsha take bayarwa, sai daga baya bayan komai ya lafane an sha kuka an koshi sannan Imran yake mayarwa da Areef abubuwan da suka faru, sosai Areef ya jinjina kai tare kuma da yi wa kansa alkawarin idan ya samu lafiya dole ya bankaɗo gaskiya, dole ya yi bincike akan suwa ye suka yi wa Uncle nasa hakan, a cikin rayuwar Areef idan ka cire TRIPLETS nasa to Musharraf shine mutun na biyu da yake kauna, haka Allah ya jarabce shi, hakan kuma yasa ya yi alkawarin biwa uncle ɗin nasa hakkinsa, ba zai bar Nigeria ba sai ya yi wannan aiki koda kuwa ita zata zama aikinsa ta karshe a duniya ko a hukumance. Shiru suka ɗan yi na ɗan lokacin, sai shesshekar kuka Rimsha take yi ta lafe a jikin daddynta, zama daddy ya yi ta zauna a saman cinyarsa tare da kwantar da kanta a kirjinsa idanunta sun yi jawur saboda kuka, suma su Imran komawa kowa ya yi ya zauna, Areef dai abin ya yi mashi daɗi sosai da Rimsha ya kasance ƴar Musharraf. Katse masu shirun daddy wato Musharraf ya yi da tambayar a ina Rimsha take zama yanzu, wannan karon da turanci suke maganar. Nan Imran ya ba shi labari yadda ake ciki, ai kuwa daddy ya ji babu daɗi, cike da jin haushi kuma cikin yaren turanci dan ma Areef ya ji ba sai an fassara mashi ba, ya fara magana "Ba zai yi wu Rimsha ta zauna cikin zaratan maza haka ba, ba zan yarda da hakan ba, dan haka ta kwashe kayanta mu je na mai data gidana na nan Kd, ban yarda ta zauna a nan ba, maza tashi ki kwaso kayan ki mu tafi". Ya kai karshen maganar tasa cikin izza da nuna isa akan ya isa da ita. Ita kuwa cikin zumuɗin ganin daddynta yasa ta miƙe ta shige ciki dan ta haɗo kayanta, sai faɗa daddy yake yi akan me Imran bai kai ta gidansu ba ko kuma gidan Abbi da zai kawo ta nan cikin maza, ga Areef bashi da lafiya kuma yasan halin turawan nan sarai wasu basu da hankali idan sojojin nan suka yi mata wani abin fa, idan baku manta ba Musharraf suna da kwantaciya a kasa tsakaninsa da Lion na marinsa da Lion ya taɓa yi, hakan yasa Musharraf ɗin baya son Rimshan ta zauna a nan dan sanin bakin halin irin na Lion. Shi dai Areef sai ƙoƙarin dannan daddyn yake yi domin Lion na gida, shi kuma Lion idan yana waje ba wanda ya isa ya nuna yana da izza ko kuma ya nuna yana da iko da wani matukar yana waje, idan yana wajen to shine sarki, shi ne zai yi iko da kowa, idan ka yi gigin kin hakan to fa ka shirya kukan da mutuwa ta fi maka sauki, hmmm kuma ga shi a cikin gidan Lion ɗin daddy ke nuna izza yana magana son ransa har da nuna isa, ai da wuya daddy ya wanye lafiya da Lion ɗin. Ai kuwa Rimsha tana fito da trolley ta akan su tafi Lion ya fito daga cikin ɗakin daidai lokacin kuma da daddy ya miƙe akan su tafi. Tsare Musharraf ɗin da waƴan nan idanun nasa masu rikitar da ɗan adam ya yi, sannan gently in a cool voice ya fara magana "Ke wuce ki koma ciki, kai kuma wuce a mayarda kai in da ka fito, magana kake yi akan tana zaune a cikin maza ko? To kasani daga yau ta zama ƴar aikina, even gyaran bedroom ita zata yi, abinci komai dare idan ban ci ba to bazata yi barci ba dole sai ta kawo mani, kuma ta jira na ci sannan ta yi barci idan na bata izini, kamar dai yadda ka ga bodyguards na gida haka zata zama mana ƴar aiki, turawa basu da hankali ka ce ba? zan gwada maka kuwa, zaka ga karshen zama a cikin maza". Cikin sauri Areef ya ce "No Lion please ka kyale shi ya zauna to, idan ya so sai su zauna da yarinyar tasa, you know fa ina kaunarsa....". Wani kallo ya wurgawa Areef ɗin wanda ya sanya shi haɗiye maganar tasa ba tare da ya karisa ba. Tsawa ya daka masu akan ya gama magana Musharraf ya wuce a mai da shi Airport ya koma Washington DC, daga yau ya mashi hannu riga da Rimsha tun da har da nuna masu izza a cikin gidansa, to ya rabasu ya ga karshen tsiya, kuma dole ta zauna a cikin maza ta yi masu aiki domin ba shi kaɗai zata yi wa aiki ba, harda su Areef da su Mark sai ya ga karshe rashin kunyar Musharraf, zama cikin maza yanzu ta fara karo wasu sojoji ma zai yi su kara yawa a gidan su kai ko su 12 ta yadda zai tabbata yes a cikin zaratan mazan take zaune ita kaɗai mace bakinciki ya kashe Musharraf ɗin su gani. Ba yadda Areef bai yi ƙoƙarin fahimtar da shi ba akan ya yi hakuri ya kyaye Musharraf, amma ina baya magana biyu, sai ma tsawa da ya kara daga masu wadda ta sanya Rimsha kwasowa a guje tare da sakin trolley ɗin nata ta rungume daddyn tana kuka kamar ranta zai fita, duk yadda take son zama kusa da Lion to bai kai rabin son kasancewa da iyayenta, tana son kasancewa da daddy ta da yanzu kewarsa ya yi mata katutu. Shi dai Areef ya ji daɗi da Lion ya ce Rimsha ta zama ƴar aikinsa daga yau, amma bai ji daɗin raba uba da ƴa da ya yi ba, bai kyauta ba suna tsaka da kewar juna na tsawon watanni, yau da suka haɗu kuma ya zo ya raba su, abin ya ɓatawa Areef rai. Shi kuma Imran cikin sanyin murya ya ce "Saif it's my uncle, pls stop telling him that, please and please, evan for the sake of me" ya yi maganar tamkar zai yi kuka, domin abin ya taɓa mashi zuciya sosai, ganin daddyn Rimsha yake yi tamkar Abbansa, kuma ya ji zafin rabasu da Lion ɗin ya yi shi da Rimshan. Shiru Lion ya yi har kamar ba zai sake magana ba. Sun kwashe tsawon good five minutes a tsaye a wajen, sai kuka Rimsha ta ke yi, shi kuma daddy yana kankame da ita a kirjinsa. Har sun fidda ran zai sake yin magana, sai kuma suka ji sexy voice nasa can kasa-kasa ya ce "I dnt care even if it's your father not your uncle, am done talking". Tashin hankali, zaro ido waje Imran ya yi ya rasa bakin magana, shi kan shi daddy raba jikinsa da tata ya yi yana kallon fuskar ta, taci kuka har ta godewa Allah, duk idanun nata sun kunbura luhu-lugu, har wani ja kasar idanuwan nata suka yi, saboda kukan da ta sha, shi kuma Lion juyawa ya yi ya koma bedroom nasa. Areef kuwa girgiza kai kawai yake yi domin dama yasan in dai Lion na waje ka gwada izza a wajen to ba makawa sai ya saka ka kuka, a tsarinsa koma a ina koma waye shi ne sarki, ba'a isa a nuna isa a kusa da shi ba Musharraf ya yi kuskure. Mark kuwa cewa daddy ya yi ya wuce su koma airport kada Lion ya sake fitowa. Juyawa daddy ya yi a yaune yake dana sanin sanin su Lion da ya yi a rayuwarsa, cikin kunan rai tare da raunin zuciya ya ce "Imran ga amanar Rimsha, sannan a yau saboda Rimsha zan gaya maka cewa ni ne Hosain, na san kasan labarin kanin Abbanka Hosain, to ni ne, na gaya maka hakan ne kuma domin ka kula da Rimsha kanwar ka ce, kada ka bari komai ya same ta, sannan kuma kada ka gayawa su Yaya babba cewa Rimsha ƴata ce, kada ma ka gaya masu ka ganni, akwai dalili yin haka, sai Allah ya kaddara saduwarmu ko idan kun zo in da nake zan gaya maka komai, yanzu dai gata nan ka kula mani da ita". Ya kai karshen maganar tare da juyawa wajen Areef, shima ya bashi amarnar Rimsha sannan ya wuce zuciyarsa cike da tunanin ya Rimsha zata rayu a cikin shegun kafuran sojojin nan, ga shi Lion ya ce Za'a karo wasu sojojin, ya san halinsu sarai basu da imani, da tsawa kawai za su sanya Rimsha mutuwa ba tare da ta shirya ba, ga shi basu ɗauki zina kamar wata laifi ba ce, amma kuma kasan cewar tana hannun Areef da Imran yasa ya ɗan sami kwanciyar hankali tare da kwarin gwiwa akan da izinin Allah babu abin da zai same ta, sai dai kuma yana jin bugun zuciya idan ya tuna cewa ƴar aiki Rimsha zata zama, yasan babu wanda ya isa ya canzata a wannan ƴar aiki da Lion ya kira ta da shi, sai shi Lion ɗin da kansa, kuma yasan aiki a karkashin waƴan nan masu taurin zuciya ba karamin abu bane, Allah nema kaɗai yasan irin aikin da zata yi wa su Mark kuma, Allah dai ya sa ba barinta da wankin kayan aikinsu masu hangen bala'in tauri da takalmarsu za'ayi ba. Sai tunani kala kala Musharraf yake yi har suka fita. Ita ma Rimsha kuka take yi kamar ranta zai fita, rungumeta Areef ya yi yana rarrashinta, tana ji tana gani daddy ya wuce ya fita, da sauri Imran ya bi bayansa dan ya raka shi waje, sai dai fa duk jikin Imran ya mutu jin cewa Daddyn Rimsha shine Hosain kanin mahaifinsu, lokaci guda Imran ya ji cewa lallai yana son sanin ainahin tarinhin abin da ya raba kan wannan family har haka, me ya rabasu kenan, wannan gaba na tun ba'a san za su zo duniya ba, sun rarrabu kashi kashi ta yadda yanzu ƴaƴansu sun ta so amma basu san cewa iyayensu bane, kenan bayan daddy ma akwai wani ne ko kuma yaya, shin su nawa ne ma a wajen iyayen nasu, ina Hassan ɗin Hosain ɗin yake?. Wannan shine tambayoyi da Imran yake yi wa kansa da kansa, wadda kuma ba wanda zai iya ba shi wannan amsa sai Abbansa, domin shi ne yaya babba a cikin su Abbin gaba ɗaya, yasan komai kenan. Allah sarki Areef sai fama da rartashin ta yake yi, yau Rimsha ta ci kuka kamar ba zata rayu ba, har wani sarkewa numfashinta yake yi, gata ga daddynta amma an sake rabasu, ita ba ƴar aikin Lion da zata zama bane ma ya dameta, duk da ta san cewa yi wa Lion aiki babbar bala'i ce domin sai mai dakiyar zuciya irin sojojin nasa za su iya, amma dai duk da haka abin bai taɓa ta sosai ba kamar yadda rabata da daddy ya taɓata. Allah sarki sai kokarin Areef yake yi da ita akan kada ta suma. Daga karshe ma zazzaɓi ne mai zafi ya rufeta kwance a jikin Areef ɗin, kafin Imran ya dawo jikinta ya yi zafi jau kamar wuta, da yake tana kwance a jikin Areef ɗin sai bai ji zafin da jikin nata ya yi ba, har sai da Imran ya dawo yana ƙoƙarin ɗagata daga jikin Areef ɗin dan ciwon dake jikinsa kada ta fama mashi, a nan ne ya ji jikin nata ya yi zafi kamar wuta. "Subhanallah Rimsha lafiya, zazzaɓi ne fa a jikinki". Shine abin da Imran ya faɗa bayan ya ɗago ta. Yunkurawa Areef ya yi wadda gaba ɗaya jikinsa ta yi la'asar saboda raba uba da ƴa da Lion ya yi, tsawon watanni ba su tare wannan wace iriyar bakar zuciya ce a kirjin Lion? Shine tambayar da Areef ya yi wa kansa, mutun yana ji yana gani ya raba uba da ƴa suna kuka dukkansu amma ko kaɗan Lion bai ji wani alamar tausayi ba bare ya tausaya masu, tamkar ma ba shi ya yi hakan ba. Hannu Areef ya kai ya taɓa wutarta, zafi jau kamar wuta, ko motsin kirki ta kasa yi, ta zama wata sukuku sai yadda suka yi da ita, duk yadda Imran ya juyata haka take juyawa tana daga kwance a jikinsa. Baiwar Allah......... 💖💖TRIPLETS💖💖 E91-92💖 Hannu Areef ya kai ya taɓa wutarta, zafi jau kamar wuta, ko motsin kirki ta kasa yi, ta zama wata sukuku sai yadda suka yi da ita, duk yadda Imran ya juyata haka take juyawa tana daga kwance a jikinsa. Baiwar Allah. Ɗagowa Areef ya yi ya kalli Imran ɗin kafin ya ce "Take her to hospital, ni ba zan iya dubata yanzu ba, because gaba ɗaya am very weak". Jinjina mashi kai Imran ya yi sannan ya saɓe ta a kafaɗarsa ya nufi waje da ita, shi kuma Areef ya koma ya zauna a saman sofa yana sauke numfashi a hankali. Abin mamaki kuma abin al'ajabi shi ne da Imran ya zo fita gidan gateman ya hana shi fita, mamaki ne sosai ya kama shi tare da tambayar gateman ɗin akan me zai hana shi fita, cikin girmamawa ya ce "Am sorry sir oga ya ce kada na kara barin wani ya shiga ko kuma ya fita gidan nan ba tare da izinin sa ba, ko da kuwa kune". Imran ya gane matsalar wato yau ran Lion ya ɓaci, ba rashin lafiya ba ko mutuwa Rimsha zata yi sai dai ta mutu, dan mugunta da ganganma ya hana a fita da ita saboda yau babanta ya yi maga da izza kuma yana wajen, shine zai sauƙe akan ƴarsa kenan, Babbar magana. Shiru Imran ya ɗan tsaya kafin ya juya kan motar ya dawo cikin gidan, haka ya sake ɗaukarta suka koma ciki domin yasan tun da Lion ya ce haka to fa ko Areef a wannan karon sai dai ya ce da Rimsha ta yi hakuri, amma babu wanda ya isa ya canza wannan magana daga ba za su fita daga gidan ba, lallai Lion ya shirya mugunta kenan. A palon sama ya isko Areef a nan kuma ya gaya mashi abin da Lion ya ce, Areef bai yi mamaki ba domin kuwa ya san tun da suka yi haka da Musharraf tofa sai dai addu'a dan tabbas Musharraf ya ɗan ɓata mashi rai gaskiya ita kuma Rimsha sai dai suce Allah ya kwaceta daga hannunsa kawai, amma dai zata ci bakar wahala ba ɗan kaɗan ba. Haka Areef ya daure ya ce da Imran ya ɗauko mashi A box a ɗaki bari ya duba ta, dama kunsan jami'ai irin haka ba su rasa iya wani sashe na aiki a ɓangaren lafiya domin kula da kansu idan bullet ya taɓa su ko makamancin hakan, to shima Areef hakan ne ya iya aikin likita duk da ba sosai bane. Ɗakin Rimshan suka wuce, a nan Areef ya dubata tare da yi mata alluran zazzaɓi, amma fa sun sha dirama kafin ayi wannan aluran, sai da Imran yasa karfi ya danneta kafin nan Areef ya samu ya danna alluran ya yi mata, cikin alluran da ya yi matan kuma har da na barci domin ta ɗan samu ta huta wata kila idan ta tashi ƙwaƙwalwarta ta ɗan yi fresh. A haka suka barota a cikin ɗakin tana barci suka koma palo suka zauna, sosai suka nutsa a duniyar hira a tsakaninsu, duk wannan abin da suke yi Lion yana jinsu domin ai a palon saman suke. A ɓangaren gidan Abbi kuwa, bayan sun koma gida da suka yi sallar mangariba suka ci abinci ne suka wuce ɗakinsu while ita kuma Akila Akil ya zo ya ɗauketa ya mai da ita gida, yanzu ya rage daga Jelly sai Hanan, su biyu ne kawai a cikin ɗakin. Yau wani irin wanka na musamman aunty ta ci, sai tariyo kalaman Akila a cikin ƙwaƙwalwarta take yi, wata magana da Akila ta sake gayawa Jelly safiyar yau ne ya tsaya mata a ranta, maganar kuma ba wata bace fa ce cewa da ta yi, ba sai kin tambayi mijinki wani irin dressing yake so ki rinƙa yi mashi ba, a cikin kayan da yake saya maki a nan zaki gane, idan ke amarya ce ki duba cikin kayan lefenki ki gani, abin da ya fi so shi zai saya maki dayawa, idan kuma kun jima da shi to zaki ga idan kun je sayan kaya zai yi ta cewa ki ɗauki kaza ki ɗauki kaza, to wani abin ba sai kin tambaye shi ba, da kansa zaki ga ya fi damuwa da saya maki irin shi dan yana so. Wannan magana ta tsayawa aunty a rai domin kuwa Abbi ya zu ba mata riga da wando masu shegen kyau sosai a cikin lefenta, a cikima ta ɗauki ɗaya daren jiya ta bawa Jelly, kenan Abbi yana son a rinƙa yi mashi dressing na riga da wando? Sannan ga uban wasu shegun kayan barci daya zuba mata wadda a kalla za su iya kai kala 20 saboda yawa, kenan shima Abbi yana so a rinƙa sanya mashi? Tabbas Akila ta faɗi gaskiya ko kala ne miji yake so zaki ga idan zaku sayi abu zai rinƙa ce maki ki ɗauki kalar can tafi kyau kuma zata yi maki kyau, bawai dan zata yi maki kyau ɗin bane, aa shi dai ya fi son ganinki da wannan kalar ne, amma sai kaga wasu mata dan ya ce ga kalar da zata yi maki kyau sai ta ce a'a ba zai yi mata kyau ba, aa ya yi haske sosai ko kuma ya yi duhu ko dai ya yi kalar fatar ta, complain dai kala kala idan bata son kalar abin da ya zaɓa mata ɗin, dama ba dan ya yi maki ke kyau ba yasa ya ce ki ɗauka, shi ne dai kalar da ya fi so, to dan haka sai mu lura. Wasu shegun kayan barci Aunty ta ɗauko wadda kusan da su da babu duk ɗaya ne, haka ta sanya a jikinta kuma ta bi shawarar Akila bata sanya bra ba, ta sake su abinta, sai tashi wani fitinannen kamshi take yi, lokacin da ta shirya Abbi yana ɗakinsa baya nan, hakan yasa ta ɗauki wayarta tare da sanya hijabi ta fito zuwa ɗakin nasa, a lokacin ita kuma Ommu tana can tana saƙa ta yadda zata karɓi 10 million a hannun Akil ta hanyar Umaisha. Bakinta ɗauke da sallama ta shiga cikin ɗakin Abbin, baya ɗakin yana toilet yana wanka, cire hijabin jikinta ta yi ta ajiye tare da nufar gaban mirror tana kara feshe jikinta da wasu kalar perfume ɗin nasa. A haka ya fito ya sameta, bayan ta ya fara kallo, da farko ma ya zaci Ommu ce domin sirantar ko ace yanayin jikinsu kusan ɗaya, sai da ya ga tsawon da kuma tudun bayan ne ya fahimci ba Ommu bace, gabaɗaya kunya ta kama Aunty, bata saba ba, ta kasa juyowa su yi ido biyu da Abbin, har wani yarrrr jikinta yake yi saboda kunya. Shi kuma Abbi ya tsare ta da ido sosai yana kare mata kallo daga sama har kasa, ta yi kyau iya kyau kuma ta tafi da imaninsa fiye da Ommu, domin dama babu haɗi ta fi Ommu komai, kawai rashin ɗaukar wankar shegun dressing da bata yi ne yasa ake mata kallon kamar ba komai ɗin. Ta kasa juyowa shi kuma Abbi ya kasa cire idanunsa daga kanta, da dai taga ba zai daina kallonta ba kuma yaki karisowa cikin ɗakin yana tsaye a bakin kofar toilet, sai ta hakura ta juyo a hankali tare da fara kallon kasa ta ki haɗa ido da shi. Ya ilahi ya lalliahi ai kuwa ashe bai ga komai ta baya ba sai da ta juyo ta gaba, cikin sauri ya kariso wajen da take tare da rungumarta a jikinsa, wani nauyayyar ajiyar zuciya suka sauƙe a tare, tunani ta fara yi kenan gaskiyar Akila? Lallai kam to ita ina zata iya irin waƴan nan dressing da Ommu ke yi, ai sai yara ita kunya ba zai barta ba. Tana can tana tunani shi kuwa Abbi yana sabgar gabansa dama daga shi sai towel.... na haɗa kayana zuwa wajen daddyn Jelly dan na basu waje. Sai lallaɓa Aylarsa yake yi suna kwance saman bed nasa tana kwance a saman kirjinsa, amma fa sai da aka yi wa Jelly dabara na cewa Ayla zata kwana da Ommu ne sannan ta yarda da rashin Ayla a ɗakinsu, ba dan haka ba, ba zata taɓa yarda Ayla ta kwana da daddynta ba, duk da an ce mata kanwar mummynta ne, amma ta yi mugun raina Ayla ɗin sosai, kuma da farko ma taki yarda ta kwana da Hanan, ta kafe sai da daddy zata kwana, sai da Abbi ya yi mata dabara tare da lallaɓata sannan ta yarda su kwana da Hanan ɗin. "Babyn daddy daddynki yana cikin wani hali, zaki iya taimaka Mashi?" Ya tambaya yana shafa bayanta. Tana daga lafe a kirjinsa ta ce "Daddy sosaima, zan taimaka maka". Ajiyar zuciya ya sauke har ga Allah ba zai iya jure sati guda da Dr ta ce ba, yau kwana uku ma ji yake yi kamar zai mutu saboda azababben sha'awarta dake damunsa, to ina ga an cika sati, ai sai dai a kwashe shi sai asibiti kawai. "Baby kanki nake so ki bani kin ji ko?" Ya yi maganar can kasan maƙoshinsa. Da yake bata san me hakan yake nufi ba sai ta ce "To daddy na baka ai". Kara matseta sosai ya yi a jikinsa, Baiwar Allah bata gama samun sauƙi ba amma yana ƙoƙarin sake tsunduma ta cikin wani yanayin kuma. Juyawa da ita ya yi izuwa saman bed ɗin ya yi mata rumfa da kirjinsa, nan take ya fara murzanta son ranshi, a wannan karonma ta ci bakar wahala a hannunsa, ta yi kuka kamar mene ne, amma dai Allah ya takaita ba suma, bata suma ba, sai dai fa ta wahala zallar madarar wahala, sai nishi take yi tana kuka kasa kasa da kyar da kyar, kuka kuma mai taɓa zuciya, Daddynta yana neman kasheta shi da kansa. Shi kuwa sai aikin rarrashi yake yi, duk ya birkice mata kamar ba shi ba, amma kuma ya kwashi daɗi iya son ransa, yau nema ya san ya kwanta da ita, ranar farko bakar wahala shima yasa saboda...... Da kansa ya yi mata wanka kamar dai yadda ya saba yi mata, magungunarta ya ɗebo ya bata ta sha sannan suka kwanta bayan shima ya yi wankar kenan, rungumota sosai ya yi a jikinsa kamar na ce zan kwace mashi ita, da haka barci ya yi awon gana da su sai sauke ajiyar zuciya irin na wadda yaci kuka ta ƙoshi take yi. A ɓangaren Akila kuwa, yau ma dai masoyin ɓoye ya hanata yin waya da Irfan, idan Irfan ya kira sai ya ji wayar a kashe yayin da shi kuma masoyin ɓoyen sai misalin karfe 10 ya kirata a waya. Gaba ɗaya ta mance da abin da ya faru jiya a gidan Abbi, ta mance ya ce mata shi ba mutun bane, hakan yasa ta ɗauki kiran tasa cikin zumuɗi. Sallama ta yi mashi kamar ko da yaushe, cikin fara'a ya amsa mata sallamar tata tare da yi mata barka da dare, bakinta ya ki rufuwa saboda murmushi ta amsa mashi da lafiya Lou fatan shima haka ne?. Ya ɗan yi shiru kafin ya amsa mata da lafiya Lou Alhamdulila ina su Akil da kuma ango Imran, ta sha mamakin jin wannan tambayar tasa, amma sai bata yi gigin tambayarsa a ina ya san cewa Imran ya yi aure ba, kawai sai ta ce mashi suna nan lafiya lou. "Heartbeat ɗin heartbeat ɗinta me ya same ki? Yau na ji gabaɗaya kin sauya". Cikin shagwaɓa ta ce "Kai ne mana". Da sauri ya ce "Subhanallah ni kuma my heartbeat?" Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e shi ɗin dai. "Heartbeat me na yi maki kuma?" Nisawa ta yi kafin ta ce "Me yasa kaki ka bayyana mani kanka? Me yasa kake bawa zuciyarta wahala? Haba mana bugun zuciyata why kake azabtar da ni kuma kake ikirarin cewa sona kake yi?". Ɗan dafe kansa ya yi yana faɗin "Nayi kuskure matata amma ki yi mani afuwa kin ji ko? Ba zan sake ba, kuma zan tura maki hotona yanzu, amma me yasa kike da tsoro haka ne? Ni mutun ne ba aljani ba kawai jiya na yi maki zolaya ne na tsakanin masoya, amma tuba nake yi Gimbiyata". Wani irin daddaɗar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce "To shikenan Heartbeat ɗi na, komai ya wuce amma dai ina matukar son na ganka, ka turo mani pic naka please". "Zan turo maki amma ki yi mani murmushi tukun nan ko my pleasure?". Wani kayatatcen murmushi ne ya subce mata tare da sanya hannunta ta rufe face nata tana faɗin "Uhm Uhm yanzu dai sai da ka saka ni Murmushi ko?". Wani irin shagwaɓe murya ya yi cikin salo mai jan hankali tare da kwarewa a iya shagwaɓa ya ce "Uhm uhm ba dole na sanya bugun zuciyata murmushi ba, kin san yadda nake ji a cikin zuciyarta idan kika yi murmushi kuwa?" Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a tamkar tana gaban shi. "My heartbeat idan ki ka yi murmushi ji nake yi duniya ta tsaya mani cak, ji nake yi tamkar bana a duniyar nan, wani irin baƙon yanayi ne ke ratsa zuciyarta har izuwa gabaɗaya sassan da jini ke gudana a jikin nawa, ina tsintar kaina a cikin wani irin farinci wadda ba zai misaltu a gare ni ba, ina jin kamar an yi mani albishir ne da gidan aljanna, please my bugun zuciya keep smile kin ji ko matar Heartbeat ɗin ta". Wani irin daɗi ta ji a cikin zuciyarta, har wani irin sanyi kamar an zuba mata kankara take ji yana ratsata, jinta take yi a sabuwar duniya, kara narke mashi ta yi suka cigaba da zubawa juna kalaman soyayya da Kauna, gabaɗaya ya sanya ta ta mance da zancen hoto, dama kuma da gangan ya yi hakan domin baya son tura mata hoton nasa a yanzu, yana tura mata zata gane shi, shi kuma ba haka yake so ba, yana so ne sai ta kamu da son shi wadda ba zata iya rabuwa da shi ba, sannan sai ya kawo mata kansa har gida su ga juna, kuma yana so ne ta so shi tsakani da Allah ba tare da ta san waye shi ba. Ya kware wajen iya shagwaɓa da soyayya, hakan yasa yau har kukan daɗi Akila ta yi mashi, domin ya fita iya soyayya da komai nesa ba kusa ba, hawaye babbiyu yau ta yi mashi kuka, cikin sigar shagwaɓa kuma ya rarrashi kayarsa, yana bala'i kaunarta fiye da tunanin mai tunani, sai dai kuma akwai shi da zuciya da kishi tare da neman magana, da gangan wani lokaci yake tsorata domin yana jin daɗin yin hakan, yana jin daɗin yaga yana tsoratata tana zuba mashi kukan shagwaɓa, hakan ba karamin daɗi yake yi mashi ba. Sai misalin karfe 1 na dare sannan ya ce ta kwanta shiru kada ta yi magana, duk abin da zai faɗa bai ce ta bashi amsa ba, ta dai yi shiru har barci ya ɗauketa, amma ta bar mashi wayarta a kunnnenta yana makale domin ta saurari abin da zai na gaya mata ɗin har ta yi barci, okey ta amsa mashi da shi sannan ta yi abin da ya faɗa ɗin dukka tare da kara jawo bargo ta shige. Wasu shegun zafafan kalamai ya fara faɗa mata a kunnenta, yana yi yana haɗa mata da shagwaɓa, sai murmushi take yi har barci ya ɗauketa fuska ɗauke da murmushi, shiru ya yi yana sauraran yadda numfashinta ke sauƙa a hankali hankali har karfe biyu na dare, sannan ne ya kace kiran cike da begenta, bai gaji da jin muryarta ba, haka zalika wannan shagwaɓar tata baya isarsa, baya gajiya kwata kwata, ita ma ta iya soyayya sai dai ko rabin shi bata kai ba, tana bashi kulawa iya iyawarta. Cike da kewarta shima ya kwanta tare da jawo lallausan bargo ya shige ciki, ya rufe har kansa. A ɓangaren su Jelly da yaya Imran ma dai an sha waya har karfe 1 sannan shima ya ce ta kwanta ta yi barci dan saboda tashin asuba, yasan halinta sarai bata tashin asuba ta daɗi idan ana tashinta, amma fa shi a nashi ɓangaren da rungumar pillow ta barshi ya kwana, ta zuba mashi shagwaɓa da soyayya son ranta, ta bar bawan Allah da matse pillow domin ta jefa shi cikin wani irin yanayi mai wuyar misaltuwa. A ɓangaren Rimsha kuwa, ba ita ta farka ba sai karfe 8 na dare, baiwar Allah ta tashi lafiya Lou sai dai ciwo da jininta yake ɗan yi mata. A hankali ta sauƙo kasa ta nufi toilet. Wanka ta fara yi kafin ta ɗauro alwala ta zo ta gabatar da sallar mangariba da kuma isha, sannan ta shirya cikin wando da kuma riga kamar yadda ta sa ba, yau garin akwai iska da hadari da alama ruwan sama za'ayi, hakan yasa ta ɗauki jacket data ɗauko a ɗakin Imran ta sanya a jikinta ta fito palo dan ta yi magana da yaya Imran. Da sallama a bakinta ta shiga ɗakin nasa, baya nan hakan yasa ta wuce kasa dan tasan yanan tare da Areef a ɗakinsa kenan. Sallama ta yi masu a bakin kofar, har suna haɗa baki wajen amsa mata sallamar tata tare da bata izinin shigowa, cikin natsuwa ta shigo cikin ɗakin. Areef na zaune saman gado da gabaɗaya jikinsa, shi kuma Imsan yana zaune ne a bakin gadon, Areef ya jingina kansa da jikin headboard na gadon yana fuskartar Imran ɗin, shigowarta tasa gabaɗaya suka zuba mata idanu cike da tausayinta fal ransu. Gaishesu ta zo ta yi kafin Areef ya yi mata alama akan ta zo kusa da shi ta zauna, shima dai Areef kallon ƴar baby yake yi wa Rimsha kamar Imran ɗin, kuma gaskiya ce yarinya ce 14 years da ƴan hayaniya ne fa ke gare ta. Ba musu ta koma gefensa ta zauna domin tun da ta ga daddynta ya yarda da su, sai ita ma ta kara yarda da su dama can already ta yarda da su, karawa kawai ta yi a yanzu. Ɗan kwantar mata da kanta ya yi a jikinsa Imran yana hana shi kada ya fama ciwonsa amma ina bai damu ba, shi dai burinsa kada ta shiga damuwa tunda Imran ɗin ya gaya mashi halin da take ciki na rashin lafiya na abinda Dr ya ce, shiyasa shima baya son barinta ta shiga damuwa. Wayarsa ya ɗauko ya fara kiran layin da Aseef ya sai wa Musharraf jiya kafin ya baro Usa, bugu ɗaya daddyn ya ɗauka domin shima ya ƙagu ya yi magana da Rimshan kuma ya kira layin Areef ɗin bata shiga. Juya kiran Areef ya yi ta koma video call, bawan Allah yana cikin jirgi ba su sauƙa ba, murmushi Areef ya sakar mashi kafin ya ce "Uncle please promise me akan ba zaka shiga damuwa ba? Na maka alkawari sai in da karfi na ya kare, amma tabbas zan bawa sister kulawa sosai". Jinjina kai daddy ya yi yana faɗin "James in dai Rimsha a hannunku take kai da Imran, to ba zan taɓa shiga damuwa ba". Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce "Uncle just call me Areef not James, ni musulmi ne, amma kada ka bari kowa ya sani a gida, a baya ma abin da ya sa ban gaya maka ba, ina tunanin zaka iya gaya wa wani ne, ciki kuma har da Aseef a lokacin, zan gaya maka dalilin da yasa bana so a san ni musulmi ne, amma ba yanzu ba, yanzu ka yi magana da gimbiyar TRIPLETS tukunnan". Daddy bai kawo komai a ransa na sunan da Areef ya kira Rimsha da shi na gimbiya TRIPLETS ba, ya ɗauka kawai dan hankalinsa ya kwanta ne yasa ya ce hakan, dan haka sai bai wani damu ba, shi kuma Areef ya juya wayar zuwa kan fuskar Rimsha da ta kwantar da kanta a saman kafaɗarsa ta gefen kirjinsa ya yi. Ganin daddynta yasa ta miƙe cikin sauri tana faɗin "Daddy daddy please ka dawo ka ji? Daddy idan baka dawo ba zan iya mutu wa, babu JEHAN babu MUMMY babu GWAGGO, ni kaɗai na saura daddy, dan Allah ka dawo mu nemo ina suke" tana magana tana hawaye. Katse kiran Areef ya yi ba tare da ya bar daddy ya yi magana ba, rai a ɗan ɓace ya fara magana "Rimsha me yake damun ki ne? Me yasa kike son tayarwa da uncle hankali ne? Ki sani uncle yana bukatar kwanciyar hankali fiye da ke, ko so kike ki saka mana shi a cikin damuwa ne? Ki ja wani ciwon ya kama mana shi ko? To zamu ɓata dake in dai zaki rinƙa yi wa Uncle kuka, kuma ba zan sake haɗa ku a waya ba". Hakuri ta fara bashi akan ba zata kara ba, ta tuba. "Okey ki yi mani alkawarin ba zaki sake cewa uncle wani abin da zai tayar mashi da hankali ba? Ki yi mani alkawarin farinciki zaki rinƙa sanya shi kullum?". Da sauri ta fara gyaɗa mashi kai akan ta yi alkawarin farinciki zata rinƙa sanya daddyn. "Good to jeki ki kawo mani wayarki, sai ki dawo ku yi magana da uncle ɗin kin ji?". Okey ta amsa mashi da shi sannan ta miƙe da sauri ta fice daga ɗakin, shi dai Imran ya kasa magana domin kuwa ba ƙaramin daɗin yadda Areef yake kaunar Rimsha ya ji ba, shima a yanzu kauna na daban yake yi mata bayan jin cewa ƴar uwarsa ce, kun san Imran dama yana bala'in kaunar ƴan uwansa sosai da sosai. Da sallama ta dawo cikin ɗakin lokacin kuma Areef ya sake kiran daddy dan su cigaba da magana da ita. A in da ta tashi a nan ta koma ta zauna, cikin girmamawa ta miƙa mashi wayar tata shi ma ya miƙo mata nasa dan su cigaba da magana da daddy, karɓa ta yi tare da kawo wa saitin fuskarta, ai kuwa zancen Areef gaskiya ce, ta ɗagawa daddy hankali har kwallah sai da ya yi, ga idanunsa nan akwai alamar kwallah a ciki. Hakuri ta fara bawa daddyn tare da ƙoƙarin nuna mashi ta hakura zata zauna da ƴan uwanta, kamar dai yadda suka yi da Areef haka ta yi ƙoƙarin nunawa daddy cewa tana farinciki. Shi kuma Areef ba tare da ta gaya mashi password na wayar ba, da kansa ya buɗe wayar ya shiga cikin domin ya sanya mata number daddynta, ganin uban miss call na number da aka rubuta Yaya Ahmad ne yasa ya ɗago ya kalli Imran tare da tambayarsa waye kuma Yaya Ahmad a cikin familynsu. Sai da gaban Imran ya faɗi domin yasan halin Areef sosai da sosai, zai iya sanyawa a ɗaure A'A akan Rimsha, komai kuɗin dangin su A'A kuwa, duk da cewa kusan suke da mulkin NIGERIA a yanzu, tsab Areef zai iya ɗaure gabaɗaya familynsu, abin da su Areef ɗin sune ke juya kasar Nigeria koma ace Africa baki ɗaya, yah gwamnatin kasar su ke mulkar Nigeria da sunan an bamu ƴanci, to waye gwamnatin kuma? Ai kunga sune gwamnatin tun da kakansu ne akan mulki, to kunga a gwamnatan ce za su ɗaure A'A ɗaurin da ba zai iya fitowa ba ma kuwa. Cikin sigar da Areef zai fahimtar Imran ya gaya mashi waye A'A me kuma ya haɗa shi da Rimsha sannan da abin da yake so a wajen ta, da yake Areef akwai kwakwalwa sosai sai bai tuhumi Rimsha akan me yasa take kula shi ba, ya yi amfani da abin da ya gani na ganin yawan miss call nasa a wayarta, which means kenan Rimsha bata ɗaukar kiransa, idan bata ɗaukar kiransa kuma ai bata damu da shi ba, idan kuma bata damu da shi ba babu so kenan. Number A'A ɗin ya kira tare da sanya wayar a hand-free, bugu ɗaya Ahmad ya ɗauka murya can kasa kasa ya ce "Rimsha sai yau kika tuna da ni ko? Wai me na yi maki ne kike neman kashe Ni? Kin manta alkawari da ki ka yi mani ko?" Cikin yaren Hausa ya yi maganar so Areef bai fahimci me yake faɗa ba, dan haka sai ya fara magana cikin yaren English. "Hyyy man that's is not Rimsha, kanin mijijta yake magana ko kuma in ce maka yayanta zaka fi fahimta, bana son ka sake kiran wannan number a rayuwarka, ka mance da wace ce Rimsha a rayuwarka, zai fi zama maka alkhari if not zaka yi regretting zuwanka duniya". Ita kuwa Rimsha ko a jikinta, a lokacin kuma ta gama magana da daddynta sai wani murmushi take yi, dama kunsan ba son A'A take yi ba, shiyasa bata wani damu ba dan Areef ya karta mashi warning, Shiru A'A ya ɗan yi kafin ya ce "To ai Rimsha bata da wani yaya idan ba Imran ba, cos ba zan daina kiranta ba domin ita nake burin na aura". Yana kai karshen maganar diff ya katse kiran. Tab an ce rashin sani ya fi dare duhu, A'A ya yi abu a duhu kuwa, bai san da waye yake magana ba. A'A yana katse kiran kuma sai ga shi ya kira number Imran, ba musu Imran ya ɗauki kiran, cikin yaren Hausa suka fara magana a in da Imran ɗin yake gaya mashi waye ne ya kira shi da number Rismha yanzun nan, wani irin mahaukacin razana A'A ya yi, jikinsa har kerma yake yi, lokaci guda ya dibirbirce ya fita hayyacinsa, sai faman haɗa words yake yi wajen magana, da kyar ya iya tambayar ya akayi wayar Rismha ta shiga hannun ɗaya daga cikin familyn William jacop, a nan ne Imran ya gaya mashi me yake gudana sai dai ya ɓoye mashi cewa Areef kawai ke son Romshan ban da Lion, ce mashi ma ya yi Lion ne yake sonta da kansa, kuma shi ya ajiyeta a gidan, tuni A'A ya yi wurgi da soyayyar Rimsha domin ya sani ba shi da yadda zai yi ya iya tunkarar Lion ba, ba zai iya ba, ubansa ya yi kaɗan, hakan yasa shi ma ya hakura da ita ya fawalawa Allah kawai, da haka suka yi sallama sannan A'A ya rubuta sakon ban hakuri na Long page ya tura ta layin Rimsha dan Areef ya gani. Har lokacin wayar na hannun Areef yana tunanin kalar bakin hukuncin da zai yi wa A'A sai ya ga sakon ban hakuri tare da yin alkawarin ya fita harkar Rimsha har abada, guntun tsaki ya ja kafin ya goge saƙon bayan ya karanta kenan. (OH LION YANA ZAUNE ANA TA YI MASHI KARYAR WAI SHI YA AJIYE RIMSHA A GIDAN, IMRAN ƊAN DUNIYA NE YASEEN🤣 BARI WATARANA YA JI LABARI YA DAMKESU ZA SU YI BAYANI) Imran yana gama magana da A'A kiran Lion ya shigo wayar tasa akan ya sanya Rimsha ta kawo mashi abinci ɗaki sannan idan ya gama ta je ta gyarawa su Mark ɗakinsu aikinta ya fara daga yanzu. Cikin tashin hankali Imran ya kalli Areef in da yake gaya mashi abin da Lion ya ce kenan. Jinjina kai Areef ya yi kafin ya ce "Ta je ta yi, a yadda Lion yake a yanzu ba wanda zai iya shawo kansa, kasan yau ne ranar da abin ya faru, ba zan iya tinkararsa ba nima, amma bari a kwana biyu, zan gwada shawo kansa akan ya hakura ya kyalata ta yi iya aikinsa kawai ban da na su Mark, ba zan yarda tana shiga ɗakin wasu ba, a matsayina na wadda aka bawa amanarta dole na kula da ita fiye da kaina, uncle ya yarda da ni ne yasa ya bani amanarta, to nima ba zan zuba mashi kasa a ido ba, yanzu dai ta je ta yi duk abin da ya ce mata, Rimsha ki je kitchen ki ɗauki abincinsa ki kai mashi, idan ya ci sai ki kwashe kayan abincin ki mayar kitchen ɗin, sannan ki je ki gyarawa su Mark ɗakinsu ko?". A lokacin ta gama magana da daddy kenan saƙon ya iso mata, Allah ya tsare daddy bai ji ba, da zuciyarsa zata fashe idan ya ji da gaske aiki zata yi kuma harda kartin nan su Mark zata yi wa aiki. Jiki ba kwari ta miƙe ta fito ta nufi kitchen, already abincin a shirye yake, Mark ya shirya mashi komai, sai sheki kayan da aka zuba abincin yake yi, tamkar yanzu aka fito da su daga ledarsu. Da kyar ta iya ɗaukar abincin saboda tray ɗin ya yi girma sosai, a lokacin kuma karfe 10 ta yi. Kirjinta sai dukan uku uku yake yi, ba ƙaramin razana ta yi ba, sai ambato sunan Allah take yi a cikin zuciyarta, aiki a karkashin irin su Lion sai da ambato sunan Allah domin a samu kwarin gwiwa. Faɗuwar gabanta tare da bugawar zuciyarta kara ninkuwa ya yi lokacin data nufi kofar ɗakinsa, sosai ta tsananta ambatar sunan Allah da take yi. Muryarta sai kerma yake yi yana wani sarkewa ta yi sallama a bakin kofar, shiru bai amsa ba kuma yana zaune a bakin bed nasa, jikinsa na sanye da kayan barci masu shegen kyau launin sky blue mai haske, sai latsa laptop yake yi ya ɗaure gashin kannan nasa, wannan fitinannen kamshi perfume ɗin nasa ne ya kauraye gaba ɗaya cikin ɗakin, ya yi kyau sosai tamkar shi ya yi kansa. Ta ɗauki almost 30 mins tana tsaye tana yi mashi sallama amma kamar babu shi a cikin ɗakin, sai da ta ji zata iya faɗuwa saboda gajiya, sannan ta daure ta kutsa cikin ɗakin cike da tsoron me zai biyo baya da ta shiga babu izininsa. Saura kaɗan ta saki tray ɗin abincin ganin shi da ta yi, a hakan ma ba fuskarsa kai tsaye ta gani ba, a'a yana duke yana kallon laptop nasa, kawai dai jikinsa ta gani ya razana ta duk da yana cikin kayan barci, ba ainahin surar jikinsa ta gani ba, kamshin perfume nasa kuma ba ƙaramin kwantar mata da hankali ya yi ba, ya sanyata ta shiga wata duniya. Da kyar ta iya karisawa gaban lallausa kuma tsadadden Chinese carpet ɗin dake a ta gaban katafaren gadonsa ta ajiye tray ɗin, abin da ya sa ta kai wajen kuma ta ga su Imran a wajen suke cin abinci har shi ma Areef ɗin, a saman irin wannan carpet ɗin na ɗakinsu suke cin abincin. Bayan ta ajiye ta tsaya a gefe tare da ɗaga mashi gaisuwa, tamkar babu shi a cikin ɗakin, latsa laptop nasa yake yi cikin matsuwa da kwanciyar hankali tare da aji. Rimsha ta kwashi tsawon 40 mins tana tsaye a wajen nan ba tare da ta motsa ba, shi kuma aikin gabansa kawai yake yi, idan da saboda duk mai yi mashi aiki ya saba da hakan, idan baku manta ba haka bodyguards na gidansu suke fama da shi, wani lokacin ma ya gama zamansa suna tsaye ya ɗauki tsawon awa ko sama da haka, daga karshe kuma ya tashi ya bar wajen ba tare da ya ci abincin ba, shi dai halinsa sai shi. Har hamman barci ta fara yi tsaye a wajen, shi kuwa saboda bakar mugunta sai da ya kara minti goma sannan ya miƙe a nutse ya shiga toilet, ta kasar ido ta bi shi da kallo zuciyarta yana mugun kara tsananta bugu da yake yi, tamkar zai fasa kirjinta ya fito, tana mutuwar tsoronsa fiye da tunanin mai tunani. Brush ya yi sannan ya fito ya zauna a kusa da tray ɗin, ba tare da ya yi magana ba ya yi shiru, cikin sauri ta duƙa tana ƙoƙarin zuba mashi abincin. Wani irin razana ta yi jin sexy voice nasa ya ce ta miƙo mashi wayarsa dake a saman bedside drawer, da sauri ta miƙe ta ɗauko mashi wayar ta dawo ta miƙa mashi, ba tare da kalle ta ba ya karɓi wayar ya fara latsawa. Ita kuma ta ɗauko wani cup mai shegen bala'in kyau wadda shi kaɗai ma kawai ya ishi mutun ya kwashi mintoci yana kallonsa, da alama kuma cup ne mai bala'i tsada, kuma da alama dai cup ne na musamman, sai kyalli yake yi fari tas da shi, zuba mashi hot green tea na kasarsu mai shegen kamshi ta yi, sai tiriri yake yi, a nutse ta tura mashi a gabansa, sannan ta fara zuba mashi abinci a plate mai shegen kyau, kuma plate ɗin irin cup ɗin ne, da alama set ne, ta san cewa shine abin da yake buƙata tun da shi aka shirya a saman tray ɗin. Ɗaukar tea ɗin ya yi ya fara sha domin ya fi buƙatarsa da zafi sosai, a hankali yake kai cup ɗin saitin ɗan bakinsa yana kurɓa. Ita kuwa sai faman zuba mashi duk wani abin dake a saman tray ɗin take yi a cikin plates, bai wuce sha biyar ya yi wa tea ɗin ba ya dawo da kallonsa saman abincin da take zuba mashi domin ya gani kar ta cika mashi abinci sosai saboda ba wani ci sosai ke gare shi ba. Lokacin da dara daran blue eyes nasa ya sauƙa a saman hannunta da take zuba mashi abincin, wani irin wurgi da cup ɗin hannunsa ya yi ya miƙe da sauri ya nufi toilet. A razane ita ma ta miƙe tare da dafe saitin zuciyarta dake yi mata barazanar tarwatsewa, Baiwar Allah faɗuwar gaba da bugun zuciyar ma kawai zai iya sanya ta ta mutu ba tare da ta shirya ba. Shi kuwa amai ya rinƙa kwarawa kamar zai amayar da hanjin cikinsa, har wani ja idanunsa suka yi, tunani ta fara yi akan me ya sanya shi yin amai ne haka?. Tana tsaye tana tunani har ya fito ya sameta. Kasa kasa ya motsa laɓɓansa ya ce ta zube gwiwowinta a kasa. Cikin sauri ta yi kasa jikinta na ta ɓari sosai, dama ga zazzaɓi. Rai a ɓace ya kara kallon hannun nata, a rayuwarsa ya tsani zanen lalle kamar me, kyamar abin yake yi fiye da tunanin mai tunani, wannan dalili ta sanya shi yin amai dan ya ci abin da ta taɓa da hannunta mai lalle. Gaban mirrorsa ya nufa ya ɗauko wani chemical dake a cikin drawers na wajen, ya dawo wajen da take duƙe. Gently ya ce mata ta bashi hannunta, jininta na karma ta haɗe hannunta dukka biyu ta miƙa mashi. Babu tausayi ko kaɗan a face nasa haka ya zuba mata wannan chemical ɗin a hannayenta. Wani baƙin azaba ne ya dira mata lokaci guda wadda ya sanyata sakin wani irin kuka mai sauti tare da ratsa duk wata zuciya mai imani da tsautsayi, amma fa shi kokaɗan babu alamar tausayi a face nasa, ta yi mugun ɓata mashi rai ba kaɗan ba. Nan take hannayen nata suka fara zubar da jini sakamakon chemical ɗin ya farfasa mata fatar jikinta. A takaice ya ce ta yi mashi shiru ko kuma ya take wuyarta a nan, ba shiri ta ja bakinta ta yi shiru, tana jin azaba ta haɗiye kukan nata kamar an ɗauke wutar nepa. Bayan ya gama zuba mata chemical ɗin ya rufe robar tare da maida shi mazauninsa yana faɗin ta goga hannun nata da kyau dan tsabar rashin imani da baƙin mugunta. Hawaye wani na bin wani haka ta fara goga hannayen nata cikin na juna chemical ɗin yana kara ratsata. Sai da ya tabbatar gaba ɗaya zanen lallen ya fita sannan ya ce ta miƙe ta je ta cinye abincin nan duka, kada ta rage ko kwara ɗaya, sannan ta kwashi kayan abincin ta je ta zubar da su a bola baya son ya sake ganinsu dan ta taɓa da hannunta kai lalle. BABBAR MAGANA taya za'ayi ta cinye abinci kula guda, kula ma kuma ba ƙarami ba, sannan ga sauran kuloli na su ferfesu da sauransu, ga kuma su fruits, kun dai san halinsa idan ya yi magana whikenan babu wanda ya isa ya sanya shi ya sauya ko da kuwa me zai faru. (DA RABON CIKIN RIMSHA ZAI FASHE YAU) Da kyar ta iya miƙewa ta nufi wajen abincin, tana mai danasanin zuwanta duniya ma baki ɗaya, ƴar tsawa ya daka mata akan ta fara wanke jinin hannayenta ta daina ɓata mashi ɗaki, kuma ta yi maza ta fara gyara mashi ɗaki wajen da chemical da kuma jininta ya ɓata kafin ta zo ta cinye abincin. Ta rasa ya zata yi, ta rasa a ina zata wanke hannun nata da ya ce ta wanke, shin in je toilet nawa ne ko dai yaya? Ta tambayi kanta da kanta. Ganin babu mai bata amsa yasa ta nufi waje tare da runtse ido tana mai jiran jin wani tsawar tasa, ai kuwa hakan ne ta faru domin kuwa sai lokacin idanunsa suka sauƙa akan kunshin kafarta, wannan dalili yasa ta sake jin voice nasa ya ce ta dawo ta ɗauki chemical ɗin da kanta ta zubawa kafarta ta goge kunshin nan, Allah sarki kunshin da aka yi mata jiya jiya. Tana hawaye ta dawo da kanta ta ɗauki chemical ɗin daga wajen da taga ya ajiye, shi kuma komawa saman bed nasa ya yi ya zauna tare da cigaba da latsa laptop nasa kamar ɗazun. Ita kuma da kanta ta zubawa kanta chemical tana kuka ta goge wannan kunshi na kafarta tas, sannan ta miƙe kafar tata sai jini yake yi ta nufi waje. Tana fita bedroom nata ta nufa, tana shiga ta zube gwiwowinta a kasa tare da sakin wani marayar kuka, tana cikin yi sai ta tuna da abin da ya ce ne ta zo ta gyara mashi ɗaki, hakan yasa ta miƙe da sauri ta nufi toilet nata. Wani irin bakin azaba ta ji lokacin da ta zuba ruwa a kafar tata da hannun nata, wani irin zogi da raɗaɗi suke yi mata, jikinta har lokacin kerma yake yi, ita tunanin yadda za'ayi ta cinye abincin da ya ce ɗin nan ne ma yake damunta. Haka dai ta wanke kafar tata da hannun nata duk sun yi jawur da su, chemical ɗin duk ya tsastsage mata soft skin nata, duk wanda ya ganta a halin da take a ciki sai ya tausaya mata tare da matsa mata kwallah. Da kyar ta iya jan kafarta ta koma ɗakin nasa, gyara wajen da ya baci da chemical da kuma jininta ta fara yi, sai da ta gyare shi tsab, sannan ta zauna ta fara cin abicnin kamar yadda ya saka ta. Shi kuwa tamkar babu shi a ɗakin, ya fasa cin abicin ya hakura, dan already ta riga da ta tayar mashi da zuciya, komai ya ce zai ci yanzu amai zai sanya shi, idan baku mance ba dukka TRIPLETS shegen bala'in kyakkyanin ke gare su na fitar hankali, amma ɗan gara Areef da yake ya rayuwa a wurare daban daban wadda hakan ta sanya kyakkyanin tasa ta ragu, Lion da Aseef kam ba'a magana kyankyaninsu ya wuci tunanin mai tunani, ya wuci misali. Wani irin wahalallen amai ne ya zo mata lokacin da ta fara cin abincin nasu, amma saboda bala'in tsoronsa yasa ta haɗiye amai ɗin, ta daure ta fara cin abincin, wani irin ɗanɗano ne abinci nasu yake da shi wadda ita dai bai yi mata ba kwata kwata, haka abincin nasu ya yi mata. Tun tana ci da ɗan daɗin rai har ta fara kuka mai sauti, wlh tamkar babu Lion a cikin ɗakin nan, da kukan nata ma ya isshe shi tsawa ya daka mata akan ta dai'na damunsa ko kuma ya taketa a nan, ta gama cin abincin nan ta je ta gyarawa su Mark ɗaki. Yau taga bala'i da tashin hankali, bata taɓa tunanin rashin imaninsa ya kai har haka ba. Tana tsaka da cin abincin tana kuka hannunta kuma yana jini har lokacin, 💖💖TRIPLETS💖💖 E93-94💖 Yau taga bala'i da tashin hankali, bata taɓa tunanin rashin imaninsa ya kai har haka ba. Tana tsaka da cin abincin tana kuka hannunta kuma yana jini kaɗan kaɗan har lokacin. A haka Imran da Areef suka shigo suka same ta. Wani irin bakin ciki Areef ya ji lokacin da ya ga me yake faruwa, Rimsha cikinta ya cika kamar zai fashe, ga shi kuma yanzu ne ma ta ci rabin abincin dake a cikin kular, ga kuma su ferfesu a gefe sannan ga fruits da su drinks, a ina zata zuba su kuma? Ga shi ya ce ko ɗiko na abin dake a kan tray ɗin kada ta tage mashi. Imran kam kasa jurewa ya yi ya saki Areef ya juya da sauri ya fice daga cikin ɗakin dan gudun kada zuciyarsa ta buga, shi kuma Areef ya ma rasa me zai ce, ya rasa ta ina zai fara yi wa Lion bayani akan ya yi wa Allah ya rabu da yarinyar nan haka. Sosai ya tsare Lion da ido yana kallonsa yayin da ita kuma take lodan abinci, tamkar Lion bai san ana ganinsa ba, kamar bai san da shigowarsu ɗakin ba, aikin gabansa kawai yake yi. Wucewa Areef ya yi izuwa in da take zaune, a gefenta ya zauna tare da ɗaukar spoon suka fara cin abincin tare, ko sannu Lion bai ce masu ba, shi kuma Areef bai lura da hannun nata ba. Da kyar da zufa suka kammala cin abincin nan, dukkansu sun kasa shan ruwa saboda bala'in ƙoshi, ita kam magana ma ta kasa yi sai nishi sama sama take yi. Da hannu Areef ya yi mata alama akan ta kwashe kayan abincin ta fita da su waje, tana nishi da kyar da makyarkyata ta miƙe tare da ɗaukar kayan ta fice tana jan kafa. Zuba mata ido Areef ya yi yana kallon yadda kafarta ya yi wani irin tsage tsage yana fitar da jini kaɗan kaɗan, tunawa ya yi da ɗazun kamar ya ganta da kunshi a kafarta, kenan chemical Lion ya zuba mata a jiki dan baya son ganin kunshin, Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun wannan wace iriyar bala'i ce, ya faɗa a ransa tare da miƙewa da kyar shima saboda ciwonsa ya haye saman bed ɗin na Lion yana tunanin ta yadda zai ɓullo wa Lion dan su warware wannan matsala a tsakaninsu. Ita kuwa tana fita bedroom nata ta wuce da kayan abinci, saman carpet ta ɗaura tray ɗin tare da nufar toilet da gudu ta rinƙa sheƙa amai kamar wadda aka yi wa wahayin aman. Amai take zubawa babu kama hannun yaro, baiwar Allah tun tana iya gani sosai har idanunta suka rufe, wani irin jirine ya kwasheta tana ƙoƙarin zubewa kasa a cikin toilet ɗin Imran da ya shigo tun ɗazun ya tsaya yana kare mata kallo, cikin zafin nama ya tarota ta faɗa jikinsa tana jan numfashi da kyar da kyar. Zuba ruwa a cikin baff ɗin wanka ya yi tare da surka na zafi dana sanyi sannan ya ɗauketa kacokam ya sumdumata cikin ruwan. Sai sauke wahalallen numfashi take yi, wani irin yanayi ta tsinci kanta mai wuyar fassarawa. Shi kuma juyawa ya yi ya fita daga cikin toilet ɗin dan ya bata dama ta yi wanka ko zata samu karfin jikinta. Yana fita ya wuce bedroom na Lion, nan ya isko Areef kwance saman bed, daga baya ya tsaya yau iya ɓacin rai ya shiga ɓacin rai fiye da tunanin mai tunani, akan kanwarsa kam ba zai iya juran wannan walaƙanci ba, dole su bar gidan nan yau. Cikin natsuwa ya ce "Saif zan ɗauki kanwata mu koma gida tun da Areef yana nan!" Shiru Lion bai tanka mashi ba, dama kuma yasan ba zai tanka a yanzu ba, sai time da ya ga dama. Haka kuwa akayi sai da Imran ya ɗauki tsawon 20 mins a tsaye kafin nan gently ba tare da ya ɗago ba ya fara magana "Ba bu in da zaka je har sai na bar Nigeria, sannan kuma wannan yariya ƴar aikin muce, idan kuka matsa mani to wlh daga nan har Washington DC zata tabbata a ƴar aiki, so zaka iya komawa bedroom naka!!". Ya yi maganar with he's full confidence tare da nuna isa tamkar shine wanda ya haifi Imran ɗin, wannan isa da ya nuna ma ko Abban Imran baya nuna shi ba Shiru Imran ya yi domin ba yadda zai yi, ba ta yadda zai fita gidan ba tare da izinin Lion ba, kuma ma ko da ya fita Lion yana zaune a cikin ɗaki zai sa a dawo da shi, wannan wace iriyar bakar kaddara ce? Ya tambayi kansa, shi kuwa Areef kashewa Imran ɗin ido ɗaya ya yi tare da yi mashi alama akan kada ya sake magana, domin idan ya sake magana za'a iya samun matsala, zai jawa Rimsha wata bala'in ce, gara kawai su kyale shi zuwa nan da kwana biyu idan ya sauƙa ya huce to sai su tunkare shi da zancen ta daina yi wa su Mark aiki, amma yanzu kam su kyale shi tukunnan tun da a yaune abin ya faru. Jiki ba kwari Imran ya juya ya fice daga bedroom ɗin ya koma na Rimsha dan yaga wani hali take a ciki baiwar Allah. Ta gama wanka sai faman dafa bango take yi dan ta fito daga toilet ɗin, wani azababben ciwo kanta yake yi mata, wani irin duhu duhu take gani a cikin idonta, lokaci guda gabaɗaya ta sauya tamkar ba ita ba. Riƙota Imran ya yi suka kariso cikin ɗakin, saman bed nata ya zaunar da ita tare da ɗauko mata wani abaya daga cikin kayanta sannan ya zo ya sanya mata a jikinta kafin ya ce ta kwance towel ɗin bari ya je ya maida cikin toilet , ba musu ta ɗan miƙe ta kwance mashi, nan take ta fara rawan sanyi na zazzaɓi. Bayan ya mai da towel ɗin cikin toilet ya dawo ya bata maganin da Areef ya bata ɗazun, sannan ya ce ta haura saman gado ta kwanta, haka ta haura ta kwanta ya ja bargo ya rufa mata tare da yi mata addu'ar barci ya fito ya barta kwance, zuciyarsa cike fal da tunaninta. Bedroom nasa ya wuce a in da ya je ya yi wanka shima ya haye gadonsa tare da kashe wayarsa dan yau baya jin zai iya hira da jelly ɗin ma, yana cikin yanayi mara daɗi. Shi kuma Areef yau a ɗakin Lion ya kwana, a tare suka kwana. A ɓangaren Akil da Umaisha kuwa, kwance Umaisha take saman gado daga ita sai wata ƴar shegiyar riga mai ƙaramin hannu wadda ta tsaya mata a iya cinya, ba pant kuma babu bra a jikinta, haka zalika kwanciyar da ta yi yasa rigar ta yi sama, santala santalan cinyoyinta a waje, sai wani yauki take yi tana wani kara bin lafiyar gado, da alama cikin nata ɗan son jikine. Ɗaure da towel a kugunsa ya fito daga toilet, yayin da yake riƙe da wani karami kuma yana goge kansa da jikinsa da shi. Wani irin yawu ya haɗiye ganinta da ya yi a haka, wurgi da towel ɗin hannunsa ya yi ya haye saman gadon yana faɗin "Wife kina haukata yaya Akil sosai". Juyowa ta yi suna fuskantar juna, turo bakin nan ta yi cikin yauki da shagwaɓa ta ce "Yaya Akil dan Allah ka matsa mani jikina ciwo yake yi mani". Bakinsa ya kawo saitin kunnenta yana faɗin "Yanzu zan baki abin da ya fi matsa jiki, gwaggo batula ta wani ce mani wai na barki sai babynmu ya yi kwari idan ba haka ba zan iya zubar da cikin, ina ba zan iya ba, Allah zai tsare mana babynmu dan haka ajiye zancen gwaggo Batula a gefe, bari na kara mani wani babyn dan mu sami twins tun da wanan ɗin bai yi girma ba, 2 weeks ne kawai, bari yau na karo guda biyu, idan kin kasa haihuwa sai na taya ki". Ita ma da yake yar nema ce sai ta mirgino ta shige jikinsa, riƙeta sosai ya yi tare da kawo bakinsa daf da kunnenta kasa kasa kamar wani na yi masu laɓe ya ce "Wife kin san fa aka ce mace tafi daɗi idan tana da ƙaramin ciki, dan haka bari na shanye daɗin dukka na more kafin ki haife cikin na kara maki wasu, dan Allah ƴaƴa dozen nake so". Ita dai bata yi magana ba sai wani nanukar jikinsa take yi ɗan cikin nasu ma da gulma wai ɗumin jikin babansa yake son ji kullun, shiyasa take ta wani kara shige mashi jikinsa, shi kuwa ganin haka yasa ya fara bata a jikinta ba kama hannu yaro. A ɓangaren gidan Abba kuwa yau ma kamar kullun Akila dai an zuba love da masoyin ɓoye fiye da tunanin mai tunani, sai dai kuma fa yau ma sai da ya saka ta kuka da salon soyayyarsa, haka kuma ya zauna ya zama mata kamar karamin yaro, yana zuba shagwaɓa yana rarrashinta har sai da ta yi shiru, sannan ya yi mata kamar jiya, ya ce ta bar wayar manne a kunnenta bari ya zuba mata zafafan kalamai har zuwa ta yi barci. Haka kuwa akayi, ya kasheta da kalaman da sai da ta yi mafarkinsa, wani irin barci ta yi mai cike da nishaɗi tare da begen masoyin nata. Idan muka koma gidan LION kuwa, a wannan dare dai Imran ne ya sake miƙe wa da kansa ya je ya yi sauran aikin Rismha da bata kammala ba, sannan ya dawo ya kwanta. DREAM (Mafarki) Misalin karfe biyu na dare, zaune take a cikin palonsu na sama, daga ita sai wandon jeans guntu zuwa santala santalan cinyoyinta, ta sama kuma wata yar riga ce mara nauyi wadda ta tsaya mata a iya cibiyarta, hannunta riƙe yake da wani tsadadden haɗadɗen cup mai shegen kyau wadda ke ɗauke da custard da spoon a ciki, a hankali take ɗeba da spoon tana kaiwa ɗan bakin nan nata, sai wani murmushi take yi tana cikin nishaɗi sosai. Daga ta bayanta ta ji ya zuro mata hannu izuwa saman wuyarta, ko bata juya ba ta san wanene domin kuwa kamshin perfume nasa ya isar mata da saƙon wanene ɗin, ɗebar custard ɗin ta ta yi zata kai bakinta, cikin sauri ya sanya hannun nasa a bakinta ya rufe mata, a lokacin kuma tana gab da kai spoon ɗin cikin ɗan bakin nata, hakan yasa custard ɗin ta zuba mashi a hannunsa. Ƴar kara ya yi mata a shagwaɓe, da sauri ta ajiye cup ɗin tare da riƙo hannun nasa in da custard ɗin ya taɓa ta lashe tas sannan ta cigaba da lasar hannun nasa. Ɗaukar ɗayar hannunsa ya yi ya ɗaura a saman shafaffen cikinta yana shafawa a hankali,. Cikin nata a shafe tamkar bata taɓa zuba abinci a ciki ba. Wani irin dogon numfashi ta ja tare da sauƙe wa a hankali, matso da ɗan bakinsa ya yi saitin kunnenta, kasa kasa ya ce "Meesha mu je ciki in baki wani abu mai daɗi kin ji ko?" Ɗan juyo da face nata ta yi da nufin ta yi magana, bata kai ga yin maganar ba ya manna mata kiss a kumatunta yana faɗin "Please mu je mana, abun daɗi fa zan baki". Okey ta ce mashi tare da miƙe wa ta juyo suna fuskantar juna, wani irin ihu ta kurma da ganin cikin kwayar idanunsa, a razane ta farka daga barcin da take yi, sai haɗa wani uban zufa take yi tamkar ba gobe, da alama zazzaɓin nata ya sauƙa, jikinta har kerma yake yi. Da kyar da addu'a da ambato sunan Allah ta samu ta mai da barci, domin ba zata iya tashi ta yi nafila ba saboda rashin lafiya da take a ciki, ta kasa tashi hakan yasa ta gwammaci komawa kawai ta kwanta zai fiye mata alkhari. Da kyar ta samu ta iya mayar da barcin nata, cike da danasanin mafarkin Lion da ta yi a yau. Washegari sai karfe 7 ta samu dama ta iya tashi daga barcin wahala da ya ɗauketa tun bayan sallar asuba. Wayarta da Imran ya ajiye mata a saman bedside drawer ta fara dubawa, nan fa ta sami miss call na new number har kala uku, ko wani number kuma ya mata miss call zai kai guda biyar. Shiru ta ɗan yi tana tunanin waye zata fara kira a cikinsu, daga karshe dai ta yanke shawarar bari ta kira ta farkon da ta fara kiran nata ta ji ko wanene. Bugu ɗaya aka ɗauki kiran, cike da zumuɗi ta ce "Hello Rimsha". Duk da halin da take a ciki hakan bai hanata sakin cool murmushi ba, cike da so da kauna ta ce "Anaya ke ce dama?" Daga ɗayan ɓangaren ta ce "E Rimsha nice na ga jiya baki zo school bane shi ne yanzu na gama shiri daddy zai kai mu sai nace bari na kira number da kika bani na ji ko lafiya". Daga jin yadda take magana tana cikin matuƙar faricniki tare da jin daɗin samun Rimshan a waya. Kara faɗaɗa murmushin Rimsha ta yi kafin ta ce "Anaya wlh kaina ne kawai yake ciwo Shiyasa ban zo ba, amma gobe zan zo In Sha Allah". "Subhanallah Allah sarki Rimsha Allah ya baki lafiya, to idan na dawo school zan ce daddy ya sanya driver ya kawo ni gidanku sai na duba ki ko? Wannan shine numberta ki yi saving kin ji?". "To Anaya amma sai na fara gayawa yaya Imran zaki zo tukun nan, idan ya yarda to Shikenan sai na kiraki na gaya maki" to Anaya ta ce sannan suka yi sallama sai murmushi Rimsha take yi, baki ya ki rufuwa, haka ita ma Anaya ɗin, tana matukar Kaunar Rimsha sosai, ita ma Rimshan tana matukar kaunar tane sakamakon ta ce Anayar tana yi mata mugun kama da Jehan, tamkar ƴan biyun Jehan ce ita, harta shekarunsu kusan ɗaya ne, sai dai Jehan ta ɗan fi Anaya kaɗan amma bacin haka komai har tafiyarsu yanayin magana komai iri ɗaya, sai dai kuma Anaya tana dariya, ita kuma Jehan ba sai na sake faɗa ba, kunsan kwata kwata bata ma san me murmushi ba bare kuma dariya, wannan shine kawai banbancin Anaya da Jehan,. Kada ku mance JEHAN da Nawazudden take kama sosai. ANAYA AZHARUDDEEN SALMAN SULTAN nasan daga jin sunan kun san wace ce Anaya a wajen su Rimsha, sai dai kuma ita Rimshan bata sani ba, domin bata san wanene Azharuddeen ɗin bama, daddynta kawai ta sani, sai kuma yanzu da ta san cewa su Imran ma ƴan uwanta ne. To musan waye Azharuddeen kaɗan a tare, nasan daga jin karshen sunansa na SALMAN SULTAN kun fahimci cewa ɗan uwane ga NAWAZUDDEN SALMAN SULTAN, to Azharuddeen dai shine Hasan ɗin Nawazudden, Professor ne lecturer a jami'ar Ahmadu Bello University Zaria, sai dai mazaunin cikin garin Kaduna ne, a nan yake shi da family'nsa baki ɗaya, yana da gida a zaria a in da yake sauƙa ya kwana sai ranar Friday ya dawo cikin Kd wajen family'nsa, shararren mai kuɗi ne na bugawa a jarida, bayan Professor ne kuma yana da kampanoni da dama a faɗin kasar nan wadda take amsa sunan SALMAN SULTAN, ƴaƴan sa uku, babba namiji ɗaya mai suna Feroz shine babba mai shekara 18 yanzu a duniya, sai kuma Anaya mai shekara 15 a duniya, sai autarsu Zaira mai shekara 14 sana'ar Rimsha kenan, da yake matarsa babbar likita ce sai ta ɗauki hutun haihuwa tun daga kan Zaira ta ce ta yi auta ba ƙari. Azharuddeen wato Hassan yana bala'in Kaunar ƴaƴan nan nasa fiye da tunanin mai tunani, hala zalika yana kaunar ƴan uwansa su Abbi, da su yake kwana da su yake tashi, yana yawan bibiyar lamuransu, shi ya rayu da su na tsawon lokaci, daga bayane ya zame kansa daga garesu, amma Daddyn su Rimsha tun yana yaro ya barsu, hakan yasa da wuya su iya gane shi a yanzu, idan dai ba shi ne ya ce masu shine wane ba, amma fa lokacin da ya fito takarar shugaban kasa sunansa ya fara yawo a duniyar Africa baki ɗaya, har gida PROF AZHARUDDEEN ya zo dan ya ganshi ido da ido domin ya tabbatarwa da kansa wannan kamanni dake a kan fuskokinsu, amma ko da ya zo Daddyn Rimsha ya ce sam ba shi bane Hosain, sunane kawai ta yi iri ɗaya wadda kuma ana iya samun hakan a cikin jama'a tunda dai duniya da faɗi take, Azharuddeen ya ji ne kawai amma bai yarda ba, abin da kuma yasa ya kyale daddyn ya tafi dan saboda kada ace sai yanzu da daddyn ya yi kuɗi ya zama wani shi ne za su neme shi, hakan yasa kawai suka kyale shi, amma ba su cire tuhumar akan cewa shine Hosain ba, haka zalika suma su Abbi sun tuhumeshi ne saboda sunansa, suma ya musa masu saboda wani dalili nashi da bamu sani ba, wata kila sai gaba za su buɗe mana komai mu sani. WANNAN SHINE TAKAITATCEN WAYE AZHARUDDEEN SALMAN SULTAN IN KIYA HASSAN A YANZU, SAI MUN SHIGA CIKIN LABARIN KUMA ZAMU SAN AINAHIN TOSHEN KAN ZANCE AKAN FAMILY'N. Ajiye wayar ta yi bayan sun gama magana da Anaya, cikin sanyin jiki ta sauƙo kasa daga saman gadon ta nufi toilet, ruwa mai zafi sosai ta zuba ta yi wanka da shi, sannan ta fito bayan ta ɗauro alwala dan ita kullun cikin zama da alwala take. Shiryawa ta yi cikin riga da wando kamar yadda ta saba, sannan ta sanya takalmin flat shoe mai shegen kyau, ta yi kyau sosai kamar ka sace ta ku gudu ka je ka ajiyeta kayi ta kallo dan kyau, sai wani kara cika take yi kwana biyun nan, tamkar ba ita ba, idan ta yi murmushi Yanzu wani irin lotsa dimple nata yake har wani irin rami yake yi saboda ta kara kumatu, har lokacin hannunta basu dai na yi mata zafi ba, hannun ya fi yi mata zafi domin dayawa ya zuba mata chemical ɗin a hannu, a kafa kuma ita ce ta zuba da kanta, so kaɗan kaɗan ta zuba, ba sosai ba, da hannu da kafar duk sun kumbura, kun san idan fatar mutun ta tsage dole wajen ya kumbura, a hakan ma dan daren jiya da tana barci Areef ya shigo ɗakin ya shafa mata magani, da yake jiya taci wuya sosai, da ta kwanta ko motsawa bata yi ba, wani irin barci mai nauyi ne ya ɗauketa, hakan yasa bata ma san time da Areef ya shafa mata maganin ba. A hankali ta fito palon sama, kamar kullum babu kowa a palo, wuce wa ta yi ta nufi kasan benen dan ta je ta gaishe da Areef, sai tashin kamshi take yi abinta. Da sallama ɗauke a bakinta ta shigo cikin ɗakin, yau yana zaune ne a saman sofa set dake a cikin ɗakin, daga shi sai singlet fara tas da three quarter zuwa gwiwa, ya yi wanka, kai Allah ya yi wa TRIPLETS halitta, wani irin sihirtaccen kyau na musamman ne ke gare su, sai kallon shi take yi, yau ma kamar jiya cikin zolaya ya ce mata "Da gaske Lion ya fini kyau, amma dai jiya da nace maki kafarsa ya fi nawa kyau wasa nake yi maki, halittar kafarmu duk iri ɗaya, amma dai ya fini kyau sosai gaskiya". A yau dai bata ɓoye fuska ba, sai ma ɗan ɗaure fuska da ta yi jin ya amfaci sunan Lion, ta tuna azaban da ta sha daren jiya ne. Kamar dai ko yaushe, gefensa ya nuna mata ta je ta zauna yana faɗin "Dan Allah Rimsha ki yafe wa ɗan uwana, kada ki ce zaki dai'na son shi saboda abin da ya faru jiya, duk abin da ya ɓata mu zamu gyara, shi kuma zai biya ki amma sai gaba, ina sa ran haka, kiyi hakuri saboda mu kin ji ko?". Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e ta ji. Wayarsa ya ɗauko ya fara kiran layin Aseef video call, dama tun ɗazun Aseef ya takura mashi akan ya haɗa da RIMSHA ya ce mata sorry da abin da ya faru,. Allah mai iko wai yau family'n William jacop ne za su cewa wata sorry, sorry ma kuma ga mace, tab lallai musulci duniya ne, musulci daban take, idan Allah ya yo ka a musulmi to ko tabbata ka yi kana gode mashi baka biya shi ba, addini mai sanyi, mai sauƙi, tausayin na kasa, girmama iyaye, kamanta adalci, rashin wariya, kaunar juna, Allah mun gode maka da ka yo mu a musulmai. Yanzu haka a yadda Lion yake nan Addinin Musulunci ta sanyaya mashi zuciya sosai da sosai, da lokacin da yake kristar ne Rimsha ta sanya shi amai, da sai dai muce Allah ya jiƙanta, dan ko bai kasheta ba, to wlh ba zata sake moruwa ba, amma da yake akwai sanyin musulci a ransa sai ya tsaya a iya chemical, yanzu ga shi saboda musulci Aseef ya ce a kira mashi ita ya bata hakurin abin da ɗan uwansa ya yi mata, yanzu sun san da cewa ba komai ne idan suka yi ya zama daidai ba, dole akwai abin da ba daidai ɗin ba, kuma idan sun san sun yi ba daidai ɗin ba, suna kokarin su gyara, idan wannan murɗaɗen ɗan uwan nasu ne ya yi wadda shi ya fi karfin ba da hakuri, kuma idan ka ce mashi hakan zaka karɓi hukun dan baya son wannan kalma ta sorry, to idan shine ya yi abin da ba daidai ba, su biyun suna kokari su gyara su kuma bada hakuri a madadinsa, BAYIN ALLAN. Bugu ɗaya Aseef ya ɗauki kiran, yana zaune a saman table yana cin abincin, yau wani irin azababben kyau ya yi, idanunsa na sanye da wata shegiyar glasa mai bala'in kyau da tsada baka mai ɗan girma, jikinsa na sanye da high neck t-shirt maroon color da wandon jeans fara tas, bayan sarkar da Lion ya ba shi akwai wasu karkar zinari guda biyu a wuyar tasa, daga hannunsa ma akwai sarkar hannu masu bala'i kyau da tsada, yau ya yi wa gashin kansa penti, amma daga ɗan gefene ya sanya purple color ya tura iya gefen kunnensa, kunsan gashin nasa yanzu ta yi tsawo, kuma Musharraf ya ce kada ya aske, shine ya barta har kalata yake yi yanzu, ba karamin kyau ta yi mashi ba, sai tashin wani irin fitinannen kamshi yake yi, ga kwarjini bala'i a tattare da su, sannan ga farin jini na fitar hankali. Cikin sanyin murya ta ce "Good morning yaya ASEEF". Maimaita kalmar yayan ya yi kafin ya amsa mata, sosai Rimsha take kallonsa saboda na gaya maku shi ya fi kama da Lion akan James. Zubawa sarkokin wuyarsa idanu ta yi, kamar ba zata yi magana ba sai kuma ta ce "Wannan sarkar ta so ta yi kama da nawa, sai dai kuma akwai banbanci sosai da sosai, nawa complete ne kuma nawa round ne ba mai Heart ba, amma nima nawa yana kyalli kamar haka". Fuska ɗauke da murmushi ya ce "ina naki ɗin yake, kawo bari na gani". Okey ta amsa mashi da shi sannan ta ɗan yi kasa da wuyar rigarta ta fito da sarkar, ɗan murmushi ya yi kafin ya ce "Akwai bambanci da namu sosai, na farko naki ba real zinari bane, akwai miss, namu kuma zinari ne zalla, baki ga saman tambarin nakin baya wani kyalli sosai kamar igiyar ba ne? Kuma sarkar ma ba su yi iri ɗaya ba, cox kawai dai chain ɗin ne ya so ya yi kama, wannan sarkar mummy'n mu ne ta bamu, ina son shi sosai, na ki ma ya yi kyau sosai, in saya maki wani zaki sanya?". Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e Shi dai Areef ido kawai yake bin su da shi ya wani riƙe masu waya kamar wani ɗan aikinsu. "Tom shikenan zan sa Prof ya saya maki zinari mai shegen kyau irin namu sai ki saka, duk da na san da wuya a sami sak irin namu domin namu mummy da kanta ta je aka buga mata, ita ta zaɓi design da take buƙata da kuma time da date a jiki, amma dai ba za'a rasa mai kama da shi ba, da a ce ina free ma da na je da kaina company na basu nawa in ce a buga mani irin shi sai na zo maki da shi, amma dai yanzu ma ko an saya maki wani zan sanya a buga maki wani irin namu na zo maki da shi kin ji ko?". Fuskarta ɗauke da fara'a ta ce "E naji kuma ina godiya sosai da sosai". Rimsha ya ambaci sunanta da wata iriyar murya wadda sai da ya sanya Areef kallonsa, ita ma dai ta yi mamakin yadda ya kwantar da muryarsa kasa kasa ya amsaci sunanta. "Rimsha ki yi hakuri da abin da ɗan uwana ya yi maki kin ji ko? Kada ki riƙe shi a zuciyarki, ki yafe mashi dan Allah, shi haka yake, shi sarki ne, amma mu bamu son hakkin kowa ya kama shi, musamman ma hakkin ke ɗin nan, bana so ya kama shi, idan baki yafe mashi ba ina da tabbacin Allah zai bi maki hakkinki domin wannan a rubuce take, to dan Allah ki yafe mashi sannan kuma ina mai matukar farinciki da kika kasance ƴar uncle Hosain, na ji daɗi fiye da tunaninki, kuma ina matuƙar ji dake kema tamkar uncle, ki kula mana da kanki ƴar kanwar mu, banda rashin ji, ayi karatu sosai, daddynki yana can yana barcin gajiya, ni kuma zan tafi school yanzu ina da exams, yau zan yi na ukun karshe, so please pray for me kin ji ko gimbiyar TRIPLETS?". Murmushi Areef ya yi, tana ƙoƙarin yin magana ya rigata da cewa "Aseef kana da sata fa, yanzu ina ruwanka da sunan da nake kiranta da shi da zaka sata mani? Kaima ka kawo naka sunan mana, daga na baka labari shikenan ka sace mani suna". Kallon gefen ido ya yi mashi a yayin da idanun nasa suke a cikin glass. With full confidence ya ce "Ka gaya mani menene banbancina da kai? Idan ka gaya mani zan daina yin abin da kake yi". Hararar wasa Areef ya yi mashi kafin ya ce "Na fika kyau mana, kuma na fika karfi sannan na fika iya cin abinci". Dariya sosai Aseef ya yi kafin ya ce "Kuma ka fini neman magana ba, ni ka bari Gimbiya ta yi mani magana zan wuce school time na tafiya". Kallonta Areef ya yi alamar ta yi magana Aseef na jiranta. "Our Queen kin yafe wa ɗan uwana? Dan mu zaki yi ba dan shi ba kin ji ko?". Cikin sanyin murya, a nutse ta ce "Ni dama ban riƙe shi a zuciyata ba, na yafe mashi Allah ya ya fe mu tare". Wani haɗaɗɗen murmushi ya sakar mata kafin ya yi mata sallama ya miƙe daga saman table ɗin ya nufi waje yana sallamar Areef. Bayan Areef ya katse kiran ne ya ce mata "Ki je ki ɗauki abinci ki kaiwa Lion, ki kula sosai wajen zuba mashi abinci, nima ina nan zuwa bedroom ɗin nasa yanzu, baya cin abinci sosai, dan haka kaɗan zaki zuba mashi, yanzu dai ɗauko magani a cikin A box ɗin can bari na shafa maki a ciwukan naki". To ta amsa mashi da shi sannan ta miƙe ta ɗauko ta kawo mashi, har zai shafa mata sai kuma ya fasa domin idan ya shafa mata ta je zubawa Lion abinci ya ji warin maganin nan to wata azaban zai sake yi mata, shi idan zai ci abinci ya fi son ya ji iya kamshin abincin ne kawai, idan ya ji wani kamshi a wajen bayan wannan da kuma perfume to za'a samu matsala, shiyasa sojojinsa suke matukar taka tsantsan akan kada wani kamshi ya saɓa dana abincinsa idan za su kai mashi abincin, haka zalika bodyguards suma suna taka tsantsan sosai wajen gani babu wani kamshi a tattare da su idan za su zuba mashi abinci, abin da suke wanke mashi kwanikansa ma abu ne na daban, Lion yana da bala'in tsarine a rayuwarsa wadda duk wanda zai zauna da shi to sai ya kai zuciyarsa nesa kamar nisan sama da kasa kafin ya iya zama da shi. Jiki ba kwari zuciyarta sai bugawa yake yi, haka ta hakura ta yunkura zata miƙe, ɗan riƙota ya yi ya shiga kara mata karfin gwiwa akan zata iya kada ta sare. Bai kyaleta ta tafiba sai da ya ji ta sauƙe nauyayyar ajiyar zuciya alamar ta samu kwarin gwiwa kenan, sannan ya kyaleta ta fito ta nufi Kitchen. Mark ta samu a kitchen ɗin ya gama haɗa abincin Lion yana haɗa na Areef da na Imran, sannu ta yi mashi, bai amsa ba kuma ita ma bata damu ba domin dama ba wani son yi mashi magana take yi ba. Wucewa ta yi zata ɗauki abincin, wani irin tsawa ya daka mata wadda ya sanyata dafe saitin zuciyarta take yi mata barazanar faso kirjinta ya fito waje tsabar bugawa da yake yi da karfi karfi. "Ke mahaukaciyar ina ce da zaki ɗauki abincin oga ba tare da kin wanke hannayenki ba? So kike yi ki ja mani wata bala'in ko? Idan baki matsa mani a nan kin je kin wanke hannunki ba sai na ɗauke ki da marin da sai ya sanya ki ganin mutuwa ido da ido!!". Duk wannan magana da Mark yake yi bai fa juyo in da take ba bare ya kalleta, ta wutsiyar idanunsa ya kalli zata ɗauki abincin, shi haka Allah ya yi shi, kusan irin Lion yake, idan yana abu baya ɗauke kallonsa a kan abin da yake yi, baya da yawan magana kullum gum kamar kurma, kamar dai ogan nasa, haka zalika baya shiga shirgin kowa, aikin gabansa kawai yake yi, sai dai idan kai ne ka shigo gonarsa, sannan ne fa zaka yabawa aya zaƙ, idan baku manta ba na gaya maku Mark renon Romeo ne, to fa shima sai a hankali kusan irin ogan nasa ne, sai dai ko rabin ogan bai kai ba a iya tsari, izza, izaya, ka'ida, da nuna isa akan koma waye. Wucewa ta yi ta je ta wanke hannunta fes, sannan ta dawo ta ɗauki abincin, yau ma da kyar kamar zata faɗin saboda nauyin tray ɗin, Allah sarki bata saba ba. Ba'a kayan abincin jiya aka zuba mashi abinci ba, wasu sabbine launin sky blue, kayan abincin jiya ma a ɗakinta ta barsu Imran ne ya fitar da su, kuma da ya fitar zai mayar Kitchen ɗin sai ya manta ya barsu a saman table na palon sama. Tun da ta doshi kofar ɗakinsa gabanta ya kara tsananta bugun da yake yi, ziciyarta tamkar zata fito waje saboda tsoro. Sallama ta yi mashi a bakin kofar ɗakinsa, kamar dai jiya shiru bai amsa ba, yana zaune saman sofa set dake a cikin ɗakin, ya yi shiru yana latsa wayarsa, jikinsa na sanye da three quarter launin Ash color, daga ta sama kuma yau army t-shirt ne a jikinsa, ba ƙaramin kyau ya yi wa kayan ba, ya saki dark black curly hair ɗin nan nasa har kafaɗarsa, kamar dai kullun sai tashin fitinannen kamshi yake yi, da alama kuma yau sarautar tasa ma ta fi ko yaushe, da alama dai akwai abin da ya faru, ko a gidansu na Washington DC ko kuma a wajen aikinsu, domin ya sanya a rufe mashi TGA a cikin ɗaki na tsawon kwanaki ana hora shi, dan Tga ya shiga gonarsa sosai a ƴan kwanakin, to yau da safe ya sanya a fitar masa da Tga ɗin domin dole ko da yana cikin rashin lafiya na horon da ya sha dole ya jagoranci tawagar da za su dimfari G.M.A jibi Friday, sannan ya sanya sojojinsa zarata mada katti guda biyu a kofar gidan Josephine akan su tsareta ko nan da kasuwa bai yarda ta je ba, da yake tasan halin ɗan nata, sai bata yi gardama da sojojin nasa ba, ta hakura ta zauna a gida, dan ta san ba ƙaramin aikin sa bane ma ya sanya a ɗaureta da sarka, kuma dole ta ɗauru tun da ta riga da ta zubar da girmanta na uwa a idanunsu, hakan yasa kawai ta hakura take bin ɗan nata sau da kafa kamar rakumi da akala. (Kai gaskiya Lion duniya ne, anya akwai biyunka kuwa? Yanzu duk wannan bala'i da zafin rai na Josephine ka sanyata natsuwa bata shirya ba, shiru kake jin Josephine, kada ku mance labarinta da daddy ya bada lokacin da suke school, kunga kuwa mafaɗaciya ce sosai tun da har ta iya marin William a lokacin, sannan duk tsagerancin da Dangerous Boss wato William ya yi amma Lion ya nitsar da shi yanzu kamar ba dangerous Boss ba, Allah ku yarda da maganata, Lion ɗan duniya ne na bugawa a jarida, ko da yake hakan ma ya fi tun da su suka riga da suka zubar da girmansu na matsayin iyaye a idanun yaran nasu, kuma dama mafi yawa kun san turawa haka suke da ƴaƴansu, wasu ma ƴaƴan suke komawa iyayen suna bawa iyayen nasu umarnin tare da controlling ɗinsu, bare kuma abu ya haɗu da Kristanci, ai sai dai muce Allah dai yasa mu dace) STORY Da yake jiya taga bai amsa mata sallamarta ba, sai ta yi tunanin yau ma bari kawai ta shiga ɗakin nasa kai tsaye. Wani irin sanyi ta ji ya ratsa dukkannin ilahirin jikinta lokacin da ta sako kafarta a cikin ɗakin, ko'ina na ɗakin fes saboda Imran ya zo ya gyara mashi tun kafin ta tashi barci, da alama kuma sai ya hukunta ta na tsallake aikinta da ta yi na gyaran ɗakin nasa, domin time da Imran ya gyara ɗakin baya nan yana cikin toilet, da ya fito kuma sai da ya ce da Imran ɗin aikinsa ne da zai yi, kunga kenan zata karɓi hukunci domin duk abin da ya yi magana akai to ta shafe shi ne. Yau daki kallon in da yake dan tana tsoron ya kamata tana kallonsa tun da baya son kallo, kuma da yake ya haɗu ne ma da yau yana saman sofa ne suna kusa, dan sofar kusa da carpet ɗin da take ajiye abincin, shi ne ma ya kara sawa taki kallon nasa. Tazo daidai zata wuce shi ta je ta ajiye mashi abincin ne, ya daka mata ƴar tsawa na cewa ya ce mata yana da buƙatar abinci ne, ko an gaya mata ana kawo mashi abin da bai bukata bane?. Wannan tsawa da ya yi mata ne ya yi sanadiyar mugun tsoratata da har ta saki tray ɗin abincin ya faɗi kasa komai na ciki ya tarwatse. BABBAR MAGANA. Gaba ɗaya fruits dake a ciki sun watse, wani apple ne ya yi tsalle ya dake shi a kirjinsa kafin ya dawo ya bugi screen ɗin wayar hannunsa, da yake ba wani riƙe wayar ya yi sosai ba sai wayar ta faɗi kasa a saman carpet dake tsakiyar set ɗin. Gaba ɗaya abincin sun zube kaza gudarta tana kwance mashi a tsakiyar ɗaki, ga shi jikin kazar duk kayan haɗi da akayi baking nata da shi. Tiles nasa fari tas sai kyalli yake yi duk ya ɓaci jaga jaga da miya. Jikinta wani irin mugun kerma yake yi, ta kasa tsayawa akan kafafunta a in da ta durkushe a wajen domin tasan ba makawa zata hukuntu ba kaɗan ba, jiya ma da ba wani abin ta yi mashi ba ya azabtar da ita har haka, ina ga kuma yau da ta ɓata mashi ko ina na ɗaki, bayan haka kuma ta sanya apple ya dake shi a kirji sannan ya patale mashi wayar dake a hannunsa, ya ilahi ya lillahi, ita wlh ko da faɗuwar gaba da tsinkewar da zuciyarta keyi tare da bugawa ma kawai ya isa ya kasheta ba tare da wani hukunci nasa ba. Shi ne ta gudu ne ko ta tsaya? Idan ta gudu ma ina zata je a duniyar nan ta tsirawa hukuncinsa? Ya ilahi ya lalliahi!.. A zafafe ya ɗago kansa ya................. Alhadulillah Alhadulillah Alhadulillah, Allah na gode maka da ka bani iko da dama na kammala book 2 na wannan littafin, kuskuren dake a ciki Allah ka ya fe mana, gyaran dake a ciki kuma Allah kasa mu yi amfani da shi, Allah ka ba mu dace wa, nan na kawo karshen book 2 sai mun haɗu a book 3 idan Allah ya kai mu nan ba da jimawa ba dan jin yadda wannan cakwakiya zata warware. Keep praying for me My people's, one love 💗 💘 SSG Palace Gujungu