❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E1 Tashin hankali, nan fa kallo ya koma kallon kallo a palon. Wannan ya kalli wannan, wannan ma ya kalli wannan. Gwaggo tana nema ta juya musu lissafin ƙwaƙwale. "Aunty Aisha wai me kike faɗa ne? Ki yi mana bayani dallah dallah mana!" Cewar daddyn Rimsha. Aseef ne ya katse su da cewa "Ya za'ayi mu yarda da maganarki? Ya za'ayi ki ce Josephine sister daddy ce kuma yi expecting zamu yarda, kada ki kawo mana wasa da rainin hankali a nan, dukkanmu babu yaro a cikinmu!". Ya yi maganar on a serious note! With his full confidence!. Bin shi da kallo ta yi na ƴan sakanni kafin ta ce "I thinking nima bakaga nayi maka kama da yarinya or mara ilimi ba ai! Yanzu ni ban ce ku saka mini baki a maganata ba, da Dr William nake yi first, idan har kune TRIPLETS da gaske, to idan na gama da shi zan dawo kanku, idan kuma ba ku bane, kana iya yi mini shiru dan ni ba sa'ar yin ka bace! Ka bari babanka ya bani amsa!!." "Daddy amsa us, who she is?! Otherwise I will break her legs to pieces!!". Cewar Areef, ya yi maganar cikin fushi, dan fa shi ya zo har wuya gaskiya, cin mutuncin da Gwaggo take yi wa daddynsu ya ishe shi. "James i don't know her, i have never seen anyone like her until today!". TO FAH Dawo da kallon shi a kanta Areef ɗin ya yi yana faɗin "Get out, if not I will get you out after I break your legs!!". Ko sannu bata ce mishi ba ta juyo da kallonta kan Dr William tana faɗin "Zaka bani ƴaƴana ne ko kuma sai na gwada maka nan a Nigeria kake? Ai ta Allah ba taka ba, da yake Allah ba azzalumin bawansa bane, ina zaman zamana ga shi ka kawo kanka har in da nake, kuma a yanzu zaka san da A'isha kake yi!!". A tsananin fusace Areef ya ɗaga hannu zai wanke mata fuska da wani wawan mari. Cak Lion ya rike hannun nasa tare da cewa "Kada kayi wannan ganganci, ina son kowa ya sami waje ya zauna, kuma kada na sake jin muryar kowa a palon nan, ido shi ne naku!!". Dama da wuya kaga Lion ana hayani ta family a waje ya saka baki, baya yin haka sam, shiru yake yi ya zuba musu ido, idan suka yi, suka yi, zai natsu ya gane mai gaskiya a cikinsu, shiyasa a koda yaushe yake yanke hukuncin da ta dace, dan a nutse da kuma basira da ƙwaƙwalwa yake aiki. Yanzu ma zuba musu ido ya yi tun da suke hayaniyar yana tace maganganunsu har sai da yaga Areef zai mareta ne yasa baki, shi har ga Allah a jikinsa yana jin tabbas suna da alaƙa da Gwaggo, ko da ba mahaifiyarsu ba ce, to tabbas suna da alaƙa da ita, sannan bugu da kari, sai da ya kare mata kallo da kyau ya fahimci ita ce yake kallo a tare da Josephine, to a ina? Wannan ne ya kasa iya tunawa, ya kuma kasa ganewa, amma tabbas ita ce ya kallah tare da Josephine, kuma ita ce yake kallon fuskarta a tattare da Rimsha, sau da dama idan ya kalli face ɗin Rimsha, sai ya ji kirjinsa ya buga, to ba jinin kowa yake fusgarshi a fuskar Rimsha ba fa ce jinin Gwaggo. Natsuwa ya yi sam bai tada hankalinsa ba, ya nutsa cikin tunaninsa yana aiki da basira da hankali tare da kwarin gwiwa dan ya gane gaskiya. Tamkar yanda ya faɗa, zama kowannansu ya yi a saman sofa. Sai lokacin suka lura da Brr Naurat dake ta faman binsu da kallo, ita ma ta natsu ne tana tunanin waye mai gaskiya a cikinsu?. A tsananin razane Abba da Daddyn Rimsha har suna haɗa baki wajen ambatar mummy!!. Jinjina musu kai Brr Naurat ɗin ta yi alamar yes ita ɗin ce, tana murmushi tare da sanya musu yatsa ɗaya a saman baki, alamar su yi shiru kamar yanda Lion ya ce, dan ita kanta dama abin da zata ce musu kenan, tana son ta ce musu kowa ya natsu dan a san menene gaskiya!!. Cikin sanyin murya ta ce da Lion ɗin "Jikana kai ma ka samu guri ka zauna, A'isha zo nan kusa da ni ki zauna bari na tambayeki". Sam Lion bai yi mata musu ba, dan har cikin ransa yake jin kaunar tsohuwar nan. Saman sofa ya zauna yana ɗan shafa lallausan kumatunsa. Da hannu Brr Naurat ɗin ta yi wa Rimsha alama a kan ta zo ita ma ta zauna, dan ita Rimsha kawai ta sani a cikin jikokinta, shiyasa ta kirata a kan tazo kusa da ita ta zauna. Ba musu ta nufo kakan nata. A gefenta ta zauna tare da ɗan kwantowa a kafaɗarta. Rimsha sarkin son jiki. Daddyn ma komawa ya yi ya zauna, su Akila duk samun waje suka yi suma suka zauna. Gwaggonma kusa da Brr ɗin ta koma ta zauna tana cika tana batsewa. Cikin natsuwa Brr ta fara magana kamar haka. "A'isha a iya sani na dai baki yi aure ba, kuma har na bar Nigeria baki yi aure ba! Amma yanzu ki duba waƴan nan zaratan matasa da kike ikirarin ƴaƴanki ne, a yaushe kika yi aure har kika haifo su? Sannan a ina kuma kika san shi Dr William ɗin? Idan ma har da gaske kike yi ƴaƴanki ne, to ina sone ki bamu labarin ya akayi suka zama naki? Kafin mu san abin faɗa, ba zuwa zaki yi kawai ki ce mana ƴaƴanki ne sai mu yarda ba, wannan abin dai kin san da akwai ɗaure kai, to yanzu dai ki yi mana bayani". Sarai Brr ta san cewa maganganun Gwaggo gaskiya ce, babu karya a ciki, dan ta yi wa ƴaƴanta dukka farin sani, ta kuma san irin tarbiyar da ta basu, amma sai bata nuna mata cewa gaskiyar ba ce take faɗa, sai kawai ta nuna mata a kan basu yarda ba, dan dattaku irin na dattijuwa mai adalci, ai Brr ta yi a rayuwa, mutuniyar kwarai ce sosai, kowa ya zauna da ita sai ya so ta. Shiru gabaɗaya palo suka yi, kowa jiran bayanan Gwaggo kawai yake yi. Shi dai Lion ya jingina kansa da jikin head na sofar yana binsu da idanun. Tamkar ba ta son yin magana, haka ta fara da cewa "Mummy ina so ne kafin na fara baku labari a kira mini Deen da Maik sai Azharuddin, ina son kowa ya zo nan dan kowannensu da akwai tambayar da zan yi mishi a cikin maganata". Kallon daddyn Rimsha Brr ta yi tana faɗin ya kira mata su dukkansu, yanzun nan su zo ba ɓata lokacin, dan a warware komai. Okey ya amsa cikin girmamawa. A hanzarce ya ciro wayarsa ya fara neman numbersu, dan duk yana da su a email ɗinsa. Ya kuwa yi sa'a dukkansu ya samesu. Ba ɓata lokacin ya isar musu da saƙon Brr ɗin, a in da yake ƙara jaddada musu da su yi sauri. Ba ɓata lokaci. Cikin kankanin lokacin sai ga su sun iso. Da Abbi da daddyn Jelly ne suka fara zuwa kafin Azharuddin Bature ya biyo bayansu, kowannansu da iyalansa ya zo jin cewa Brr ce take nemansu. To fah yau ake yinta, yau za'ayi cakwakiya kenan, kowa yazo, duk sun haɗu saura Hjy Batoola da Aafia ta Dr Nawid, su ne basu nan. Kowa ya natsu a palon bisa umarnin Brr Naurat. Shi ma dai Lion ya zuba musu idanu dan wannan babban case ne da yake buƙatar nazari dan tantance mai gaskiya a cikinsu!. Areef ma binsu da idanu yake yi, a matsayinsa na jami'in CIA yana ƙoƙarin tantance mai gaskiya ta hanyar amfani da ƙwaƙwalwasa da kuma basirarsa. Shi kuwa Aseef ya kwantar da kansa a saman cinyar daddyn Rimsha, dan ciwo kan nasa yake yi mishi sosai, bawan Allah sam baya son hayaniya, lokaci guda azababben ciwon kan ya sauko mishi. Tga, Uncle Herry duk sai binsu da ido kawai suke yi, amma fa dukkansu idan ka kalli face nasu, zaka ga razana da firgici a tattare da su!!. To razanar me suka yi haka?!. Dr William ɗin ma kusan haka ne, sai dai shi ya fi su dakiya da taurin zuciyar iya jure komai. Jay and John, su kuwa ko a jikinsu, su ji suke yi ma an takura musu, dan sam basu yarda da abin da gwaggo take faɗe ba, kallon mahaukaciya ma suke yi mata. Gyaran murya Brr Naurat ta yi kafin ta fara magana a nutse cikin girma da dattaku tare da nuna tsantsar kauna da farinciki na kasancewarta yau gata a cikin Nigeria, kuma a cikin iyalanta. "A'isha ga su Zahradeen ɗin sun iso, sai ki gaya mana a ina kika san wannan mutumi? Ya aka yi kuma kike da ƴaƴa a wajensa?!". Su Abbi gabaɗaya sun sha ruwan mamakin ganin Brr Naurat, sai dai ta hanasu yin magana, dan kuwa wannan case ɗin ya fi muhimmanci a gabatanta a yanzu, dole dai kowa ya haɗiye mamakinsa da murnarsa suka kasa kunne suna sauraron Brr ɗin. Kallon Abbi Gwaggo ta yi tare da fara magana a nutse. "Kai Deen zaka iya gane wannan mutumin?". Ta yi maganar tare da nuna Dr William da hannu. Shiru Abbi ya ɗan yi na ƴan mintocin da basu wuce biyar ba. Can kuma ya ce "Of course a Harvard University Washington DC ko?." Jinjina mishi kai ta yi alamar e. Amsa mata ya yi da e ya tuna shi sai dai ya manta sunansa. Tashin sense! Nan fa TRIPLETS gabaɗayansu suka tsare Gwaggo da Abbi da idanun, dan suna son fahimtar wani abin. Kada ku mance da English suke magana, dan mutanen Washington daga kan William jacob har familynsa basu jin hausa ko kaɗan. "Yauwa Deen idan zaka iya tunawa ba wannan mutumin ne ka taɓa rabamu rikici da shi ba na ya mareni na rama?". Nan ma shiru Abbin ya ɗan yi kafin ya amsa mata da anyi haka!. Dakatar da su Brr Naurat ta yi a in da take cewa "A'isha ki ɗauko mana labarin abin da ya faru tun daga farko, ki gaya mana komai dallah dallah, ba wasa muke yi a nan ba, kowa jiranki yake yi!!". Shiru ta ɗan yi kafin ta ja dogon numfashi, sannan ta fara magana a nutse kamar haka. SOME YEARS AGO. HARVARD UNIVERSITY.❤️ Zaune take a saman ɗaya daga cikin wasu kyawawan chair dake wajen garden na kusa da department nasu na surgeon Drs. Ta yi shiru a in da hankalinta yake a kan wani kyakkyawan littafi dake hannunta tana dubawa, ta nutsa cikin karatun wannan littafi. Jikinta sanye yake da wandon jeans baki da T-shirt fara tas, sam babu ɗankwali a kanta, ta saki gashin kanta irin na Naurat har baya, a lokacin sam bata sha ranar Nigeria ba, fara ce tas tamkar Naurat, babu wanda zai ɗaga idanu ya kalleta ya ce ba Baturiya bace, saboda haskenta da kyan da Allah ya yi mata, ga wannan dara daran idanun nasu na gado da suka gado wajen Dr Salman. Sai safa da marwa students suke yi a wajen, amma sam tamkar babu ita a waje, bata ɗago kai bama bare ta ga wani, da alama tana ji da shariya sosai a lokacin, tana ji da kanta over. Abin ku da turawa, su basu da matsala dan sun zauna kusa da mutun in dai nasu ne ko sun yi mishi magana, sam basu da girman kai su. Wata kyakkyawar Baturiya ce ta zauna a gefenta tare da yi mata sannu da hutawa. Ganin cewa cikin mutunci Baturiyar ta ɗaga mata gaisuwa yasa ita ma ta amsa da mutunci. Hannu Baturiyar ta miƙa mata tana faɗin "My name is Cherish Daniel what of you?". A takaice mata "A'isha Salman Sultan". "Wow are you a Muslim?". Ta tambaya fuska ɗauke da mamaki. Jinjina mata kai ta yi alamar. Sosai Cherish ta ji daɗi suka kuma kulla abota. Abotansu gwanin birgewa, bambancin addininsu baya hanasu kasancewa a tare, idan lokacin ibada ya yi, Gwaggo zata tafi masallaci, da yake Cherish tana sonta, har kofar masallaci take rakata, ta kuma zauna ta jira ta. Idan kuma ranar zuwa church ne, Gwaggo zata yi mata sallama cikin mutunci. Haka suka kasance har tsawon shakara ɗaya, Cherish tana zuwa gidan Gwaggo sosai, while ita ma Gwaggo tana zuwa gidanta time to time, dan gwaggo fa akwai ji da kai ga shariya. Wata rana Abbi ya kawo mata ziyara. Ta ji daɗin zuwan kanin nata, da yake ita ce babba a kan Abbin. Ranar sun kwana basu yi barci ba, sunata hiran gida. Cherish bata san da zuwan Abbi ba, dan ranar bata zo gidan Gwaggo ba, kuma gwaggon ma bata je gidanta ba, sai washegari ne da Cherish ta zo dan su wuce school, a nan ne ta ga Abbi, nan fa ta ce ita duniya ba wanda take so biyun Abbi, lokacin fa ba wani babba bane shi ɗin, dan Gwaggo ma bata wani girma sosai ba, kuma ita ce babba a kansa, daga Abba ne sai ita sannan Abbin sai su daddyn Rimsha da daddyn Anaya. Ita dai Gwaggo sai dariya take yi wa Cherish dan ta ce tana son Abbi, shi kuma ya sha kunu ya murtuke fuska kamar wanda aka yi wa tayin mugun abu. Nan fa ya ce zai bi Gwaggo dan ya kalli makarantarsu, a lokacin shi da Abba suna Ahmadu Bello University Zaria, dan lokacin sun koma Nigeria, sun baro Russia kenan. Abba yana soyayya da Ammiensu Imran time ɗin, suna son juna sosai har ma iyaye sun sani. Gwaggon sam bata zauna a gida nan Nigeria ba, wayon Washington DC ce ita, ko a Russia bata wani zauna da su sosai ba. Kuma ita ta zaɓi Harvard University, shi kuma Dr Salman ya amince mata, Naurat ma ta bata goyon baya sosai, dan fa su a wajensu tura ƴaƴa karatu koma ina ne ba wata matsala bane suke gani. Da farko tare da Abba zasu tafi, sai daga baya Abban ya ce shi ya fasa zai zauna a Nigeria ya cigaba da karatun kawai, Nigeria ta fi yi mishi daɗi. Sam Gwaggo bata shiga harkar kowa, bata ma ɗaga idanu ta kalli mutun a cikin school ɗin, tana yawan jin ana magana a kan dangerous boss na class nasu, wanda ya kasance shi ne gaba da kowa a class ɗin, guru ne kuma jan wuya ne a fagen karatu, sam baya wasa da karatu, ga ilimi da kaifin kwakwalwa tamkar shi ya yi wa kansa. Bata taɓa sanin wanene shi ba, sai dai ta sha alwashin a wannan karon wlh sai ta zama a gaba da shi, sai ta wuce shi a karatu, kowa ya shaida shi ne na ɗaya, to sai ta buge tarihinsa ta kafa nata, duk da tana jin ana yabon kaifin kwakwarsa a makarantar over, ga shi mafaɗaci ne number ɗaya, ga bala'i zafin rai, baya shiga harkar kowa, amma idan aka sami akasi ka shiga nasa, to ka kuka da kanka, dan sai ka yi danasanin zuwanka duniya, bashi da mutunci idan aka taɓo shi. Sosai tana yawan jin labarinsa, amma bata san shi ba kuma bata nemi sani ba!, Harkar gabanta kawai take yi. Bayan sun je school Abbi ya zauna a garden yana ta aikin latsa waya, su kuma sun shiga class nasu dan suna da lecture. Bayan sun fito daga lecture ne Cherish ta ce su je su sayo kayan cima kafin su wuce wajen Abbi. Okey Gwaggo ta amsa mata da shi. A tare suka jera zuwa super mall ɗin nasu. Ita dai Gwaggo ruwan lemu kawai ta ɗauka guda biyu a cikin cup. Ita kuma Cherish duk wasu kayan zaki sai da ta kwasa abinta, su chips ma bata bari ba! Ta ɗauki abubuwa son ranta, sai dai fa komai guda bibbiyu take ɗauka, nata ɗaya, na Abbi ɗaya kamar ya ce mata zai ci. Sun gama sayayyarsu su ka juyo kowace tana rike da nata dan su wuce garden. Gwaggo na juyowa ta yi karo da mutun a in da gabaɗaya lemun dake cikin cup ɗin hannunta ya kwarare mishi a jikinsa, daga kirjinsa har zuwa shafaffen cikinsa lemun ya wanke shi. Abin haushi ɗaya shi ne, kayan jikin nasa farare ne tas, ga lemun nata ita kuma kun sani orange color ne. Bin jikinsa ya yi da kallo idanuwansa na sanye da black glass, while yana sanye da wandon jeans fari tas da T-shirt shi ma fari, ga wani dankareren sarkar gold a wuyarsa wanda ta zo mishi har kirjinsa, irin waƴan nan sarkokin ne na manyan yara masu ji da kansu. Kunnensa na sanye da ɗankunne ɗan ƙarami, daga ta saman kunnensa ya sanya wani irin ɗan kunne na zallar zinari mai bala'in kyalli. Hannunsa na dama yana ɗaure da dankareren watch mai bala'in tsada, while ɗayan hannun nasa kuma wasu sarkokin hannune na manyan yara sanye a wajen. Da kallo ɗaya zaka yi mishi kasan e lallai yana gym, dan ga jikinsa nan ya nuna alama ta hanyar murɗewa da ya yi, yana da kirar cikakkun maza masu lafiya da jini a jika, haka zalika da kallo ɗaya zaka yi mishi kasan cewa babban yaro ne ɗan gidan manyan mutane masu faɗa a ji, dan daga samansa har kasa, komai na jikinsa masu bala'in tsada ne wanda babu na kasa da 1m. Kasancewar T-shirt ɗin jikinsa mai karamin hannu ne sosai, wani zanen tattoo dake wajen damtsen hannunsa ya bayyana, zanene na tambarin kunama, kasancewarshi jawur kamar ka taɓa jini ya zuba, sai bakin zanen tattoo ɗin ta fito zar a wajen. Babu karya kyakkyawa ne over ajin farko, ga class da ilimi!. Bin jikin nasa da kallo ita ma Gwaggo ta yi kafin ta furta mishi kalmar sorry a takaice tare kuma da nuna ko in kula. Ita dai Cherish tuni ta ja gefe guda ta takure waje ɗaya, ta wani natsu tsit ta kuma sha jinin jikinta. Da alama ta yi wa guy ɗin farin sani sosai, kuma tana mutuwar tsoron shi. Raɓawa gerensa Gwaggon ta yi da nufin ta wuce, bayan wannan sannu da ta ce mishi a takaice da kuma halin ko in kula, bata sake cewa komai ba ta kama gabanta da nufin ta bar wajen, dan ita ma tana ji da kanta over. A fusace ya juyo tare da ɗauketa da wani wawan mari wanda ya sanyata har sai da ta yi tangal tangal ta kusa faɗuwa. Diff ta ji komai ya tsaya mata, ta daina gane komai saboda wannan mari, har wani abubuwa ta gani suna gilmawa ta cikin idanunta, ga wani haske da ta gani kamar wutar lantarki. Ta ɗan ɗauki ƴan sakanni a haka kafin ta fara ganin jiri yana wani ɗebanta. Zazzaƙar murnarsa ne ya dawo da ita cikin hayyacinta a in da ya furta mata "Ke dabbar ina ce?! Babu kwakwalwa a cikin kanki ne?!". Ya yi maganar cikin natsuwa. Jin hakan yasa ta dawo dai'dai. Ɗago dara daran idanunta da suka yi ja sosai saboda marin da ta sha ta yi, tare da sauke kallonta a kan fusatatcen fuskansa. Duk da ta sha jinin jikinta na ganin face ɗin nasa a ɗaure, ga uban kwarjini mai rikitarwa, ta kuma tsorata, amma hakan bai hanata ta datse idanunta ita ma ta ɗauke shi da wani gigitatcen mari ba. Cherish da ba ita Gwaggo ta mara ba, sai da ta saki plate na kayan cima dake hannunta suka zube kasa suka tarwatse a wajen, saboda tsabar mahaukacin razana da ta yi, bata taɓa tunanin za'a iya samun wanda zata iya marin dangerous boss a cikin wannan school ɗin ba, zaratan maza ma tsoronsa suke yi bare mata. Da gudu ta watsa ta bar wajen dan ta je ta sanar da Abbi abin da yake faruwa da Gwaggon. Jama'ar dake wajen ba ƙaramin razana suka yi ba, dan dayawansu sun san waye shi, bashi da mutunci, kuma iyayensa suke goya mishi baya, a kansa zasu iya buga shari'a da kowa, ɗan gidan manyan mutane ne masu karfin murya ta faɗa a ji a kasar, yayan mahaifinsa ma shi ne president mai ci a wannan lokaci, shiyasa yake yin abin da ya ga dama. Ba'a taɓa yin wanda ya nuna mishi koda yatsa a cikin school ɗin ba, yau an wayi gari wata mace ta wanke mishi kyakkyawar jajir ɗin lallausan fuskarsa da mari a gaban jama'a. Tashin hankali, ko iyayen da suka haife shi basu taɓa dukan shi ba, sai dai su yi ta lallaɓa shi tamkar jariri, ɗan gata ne over. Ita kuwa Gwaggon hankalinta a kwance dan bata ma san wanene shi ɗin ba, sai ma ƙoƙarin sake raɓawa gefensa da ta yi dan ta wuce. Cikin fushi da ɓacin rai ya sanya kafa ya kwashe kafafunta ta zube kasa wanwar. Tsadadden belt ɗin wandonsa ya ciro da nufin ya yi mata dukan mutuwa, hakan kuma ya yi dai'dai da shigowar Abbi da Cherish. Daga can baya Cherish ta tsaya. Shi kuma Abbi, da sauri ya kari so wajen tare da rike belt ɗin na Dr William ɗin yana tambayar shi me yake faruwa. Kwashe Abbin ma da wani gigitatcen mari ya yi, dan fa ya fusata a lokacin, ransa ya yi mugun ɓaci, baya ji baya gani. Sauke musu belt ɗin hannun nasa kawai ya fara yi a jiki. Da sauri sauran jama'ar da suke wajen suka yi kansu, duk da suna tsoronsa bai hana su bashi hakuri ba, saboda mace yake duka. Ainahin Dr William baya dukan mata, kowa ya san da hakan, ɗabiarsa ce, kuma shi ya koyawa su Lion dukan mace kaskanci ne, amma ita ta raina mishi wayo ne, kuma ya tsani raini a rayuwarsa, zata zuba mishi abu a jiki ba tare da ta wani damu ba zata wani ce mishi sorry cikin nuna halin ko in kula, dole abin zai ɓata mishi rai. Uwa uba ga kuma marin da ta yi mishi a bainan nasi Da kyar aka danne shi ya hakura ya rabu da ita, badan haka ba ya yi niyar yi mata ɗan banzan dukan da ko motsawa ba zata yi daga wajen ba sai an ɗagata. Cikin fushi ya yi wurgi da belt ɗin tare da wucewa ya bar wajen yana wani huci. Bayan ya tafi ne jama'a suka taimaka mata ta miƙe, jiki ba kwari suka fito daga cikin wajen. A cikin zuciyarta, ta kuduri niyar wlh bazata barshi ba, sai ta koya mishi hankali!!. Abbi ya shiga damuwa sosai, amma ita ko a jikinta, bata wani damu ba, yanayin rayuwarta a lokacin sak rayuwar Jehan, ba maraba, dan bata shiga harkar kowa ita ma, amma idan ka shiga nata, to fa wannan faɗa ba zata kare ba har sai ta ga ta yi nasara a kan abu, haka take. Sati biyu Abbi ya yi a wajenta, tun daga wannan rana kuma bata sake yin 4 eyes da Dr William ba, har sai ranar da Abbi ya koma, bayan ta raka Abbin airport ta dawo ne ta wuce shopping dan ta sayo wasu abubuwan bukata da bata da shi a gida. Shiryawa ta yi cikin wandon jeans fari tare da high neck t-shirt, shi ma fari tas, ta gyara gashin kanta tare da ɗaura wani ɗan ƙaramin handkerchief a kan nata, shi ma fari, kafarta na sanye cikin high heel fari, from up to down dukka wankar fari ta yi. Wayarta da Atm kawai ta ɗauka sai key ɗin mota ta fito. Da yake gidan nata yana hawa na goma ne ta lifter ta sauko kasa, kowa na benensu yana harkar gabansa, babu ruwan kowa da kowa. Wucewa ta yi zuwa wajen kyakkyawar motarta, shiga ta yi ta bar gidan. Bata zame ko'ina ba sai wani tampatsetsen super market. Tana parking bata ɓata lokacin ta ba wajen fitowa daga motar ta nufi cikin wajen. Sayyayya ta fara yi babu kama hannun yaro, tamkar ba kuɗi zata biya ba, da yake already Dr Salman ya zube mata kuɗi a cikin account nata ba na wasa ba. Tana sayayya tana kewaye wajen. Kamar daga sama tana yin kwana ta wajen Lotions ta yi karo da mutun. Dankareren wayar dake hannunsa ne ya faɗi kasa. Ba tare da ta ɗago ta kalli wanene bane ta duka ta ɗauko mishi wayar. Ɗagowa da zata yi da nufin ta mika mashi suka yi 4 eyes da shi. Yauma dai kamar ranar, yana sanye da bakar glass a idanunsa, haka zalika wankar fararen kaya ne a jikinsa, sai suka yi iri ɗaya da ita. Ganin shi ne yasa ta ɗaure fuska sosai tamkar hadari, rai a matuƙar ɓace ta saki wayar tasa ta sake faɗuwa kasa. Kallon up and down ta yi mashi kafin ta ja keken sayayyarta ta raɓa gefensa ta wuce abinta. Shiru ya tsaya, ya kasa dakatar da ita, ya kuma kasa duƙawa ya ɗauki wayarsa, tunani yake yi a kan abin da ya kamata ya yi wa wannan yarinyar, dan ta yi mashi abin da ko iyayen da suka haife shi basu taɓa yi mashi ba, babu wanda ya taɓa marin shi sai ita, sam bai kamata ya kyaleta ba, kamata ya yi ya mata hukuncin da sai ta gwammaci mutuwa a kan shi!!. Ya jima tsaye a wajen yana tunani kafin ya sa kai ya wuce. Isa da takama haɗe da jin cewa cikin narkakkun dukiya yake kwana ga uban girman kai ta hana shi ya tsugunna ya ɗauki wayar tasa. Ficewa ya yi daga wajen zuwa wajen motarsa. Wasu jibga jibga bodyguards guda biyu masu sanye da black suit ne tsaye a bakin motar tasa, komai da suka sanya a jikinsu black color ne. Yana zuwa ya yi musu umarni a kan su tafi, sai wani huci yake yi, zuciyarsa na saka mishi abubuwa da dama da zai yi wa gwaggo dan ya ɗauki mataki. Ita kuwa sayayyarta ta yi sosai, sannan ta wuce wajen biyan kuɗi, sam bata sake bi ta kansa ba, tama mance da cewa sun haɗu a nan. Bayan an gama yi mata lissafi ta basu Atm card dan su ciri kuɗin nasu. Bayan an gama komai ma'aikatan wajen suka kwasa mata kayan zuwa wajen motarta, da haka ta wuce izuwa gida. Da daddare Cherish ta zo suka sha hira tare da ciye ciyensu. A gidan Cherish ta kwana, sai takurawa Gwaggon take yi da maganar Abbi, ita kuwa gwaggo da ta gaji, sai ta bata number Abbin na Nigeria, dan ta daina damunta!. Washegari haka suka shirya zuwa school, a tare suka wuce a motar gwaggo, Cherish ta bar motarta a gidan na gwaggo. Kamar dai kullum bayan sun fito daga lecture, kayan cima suka je suka sayo, a in da suka dawo garden suka zauna. Suna hira suna ci har suka kammala, sannan suka miƙe dan su koma gida. Rayuwarta ita da Cherish gwanin birgewa, kullum idan sun zauna sai ta yi ta bawa Cherish ɗin labarin ƴan uwanta tare kuma da nuna mata hotunansu. Ita ma Cherish ɗin tana yawan bata labarin ƴan uwanta da hotunansu. Ainahin Cherish ƴar kasar China ce, karatu ita ma ya kawota nan, tana da kirki fiye da tunanin mai tunani, gata da son barkonci da dariya, tana da ɗan shekaru, dan ta girmi Gwaggon ma a shekarun. Washegari suka je school a lokacin zasu fara rubuta exams, sun sha karatu sosai, dan sam basu wasa, yau kowa ka gani a department nasu, zaka ganshi yana rike da handouts sosai, dan kowa dai yasan yanda karatun likita yake, ba karatu ne na wasa ba, sai masu ƙwaƙwalwa da basira sosai. Suna tafiya suna hira, haka suka nufi cikin department ɗin nasu. Kasancewar gwaggo girman Russia ce ita, duk cikin turawan ta taso, sai ya zamana dressing nata sak nasu, tamkar ba musulma ba, a lokacin kuma da gaske bata zauna a Nigeria ba, sun dawo bai fi ta two months ba ta wuto Washington DC, so babu wani al'ada da yake tattare da ita face na turawar Russia, haka zata saki gashi ba ɗankwali abinta, duk da cewa Naurat tana iyaka bakin kokarinta wajen ganin ta basu tarbiya duk da ita ma tubabbiya ce, amma tana ƙoƙarin sosai, kuma ita kanta Brr Naurat ɗin a lokacin dressing na turawar take yi, so ba zaku ga laifin gwaggo a wannan lokaci ba!. Sun zo zasu shiga class nasu, shi kuma Dr William yana fitowa, hannunsa na rike da wata shegiyar tsadaddiyar laptop da kuma takardu, sai sauri yake yi, hakan ce ma tasa bai mayar da laptop ɗin cikin jakarsa ba, da alama wani wajen mai mahimmanci zai je. Karo suka yi da gwaggo a in da gabaɗaya abubuwan dake hannunsa harta wayarsa suka zube kasa. Hakan tasa hankalin jama'a ya yo kansu. Har wa yau idanun Dr William na sanye da wata shegiyar bakar glass na manyan yara masu class. Haka kawai tun bai ɗago kai ya kalleta ba ya ji cewa duk yanda aka yi ita ce. Ita ma Gwaggo duk da ta buge da faffaɗar kirjinsa ta yi baya tana ɗan goge kanta, bata sami damar ganin face nasa ba, amma ta ji a jikinta shi ne, saboda tsadadden ƙamshin perpume nasa wanda bata taɓa jin irinsa a jikin kowa ba sai shi ɗin. Ya fita tsawo nesa ba kusa ba, duk da take doguwa, amma Dr William yana da tsawo sosai, ga kuma cikar halitta, hakan yasa kanta ya bugi tsayayyar kirjinsa har ta ji ɗan zafi. Bakin ciki ya hana Dr William ɗagowa ya kalleta, ita kuma tsoro ne ya hanata ɗagowa ta kalle shi, tana tsoron ta ɗago ta ji saukar mari a kuncinta, ba karya tana bala'in tsoronsa, amma saboda karfin hali, da dakiya na kada a rainata, sai ta daure ta ɓoye tsoron. Cherish ce ta ce mata ta duka ta kwashe mishi kayansa ta bashi kila zai yafe mata. Kafewa ta yi a kan wlh bai isa ta tsugunna ta kwashe mishi kayansa ba, ya yi kaɗan wlh, dama haushinsa take ji kamar ta shake shi ya mutu. Abinku da babban makaranta, har wasu sun ɗaukesu a video. Tunani yake yi a kan me zai yi wa yarinyar nan wanda zai kuntatawa rayuwarta?!. Can wani tuni ya faɗo mishi a kan ya sanya a ɗauko mishi ita kawai ya yi mata fyaɗe, ya yi mata kaca kaca kuma ya ɗauketa a video ya turawa duniya, daga nan ba zata sake shiga gonarsa ba. Na'am ya yi da wannan shawara da zuciyarsa ta bashi, hakan tasa ya sanya kai ya wuce ba tare da ya ɗago ya kalli face nata ba, ya bar laptop da sauran takardun a watse a wajen. Ita ma ganin ya wuce yasa ta sanya kanta ta shige cikin class ɗin. Wasu matasan students su biyu ne suka zo suka kwashe mishi takardu da laptop ɗin nasa, suka bi bayansa da shi. Tun daga lokacin har suka gama rubuta exam suka fito, sam bata ga ko wulkawar mai kama da shi ba, hakan yana nufin shi bai ma shigo class ɗin ya rubuta exam ɗin ba. Bata san cewa tabbas ya shigo kuma ya rubuta ba, dan fa baya wasa da karatu, ga wani azababben kaifin ƙwaƙwalwa da Allah ya yi mishi, ɗan baiwa ne sosai. Bayan sun kammala suka wuce wajen sayan kayan kwalam kamar yanda suka saba. Duk abin da suke yi yau basu san ana ganinsu ba, ya sanya a saka mata idanu har lokacin da zata bar school ɗin, idan ta bar school ɗin ma za'a bi bayanta zuwa gida, dan a gano mishi address ɗinta, ya sha alwashin yau sai ya yi mata fyaɗe! Kuma fyaɗen ma gagarumi na mugunta ya yi niyar yi mata, duk da bashi da tabbacin virgin ce ita, dan su Turawa dama ba lallai ne ka sami budurwa virgin ba, musamman idan tana da saurayi, ai kuma shikenan. Amma dai ya yi niyar ko ba virgin ba ce ita sai ta gane shari ruwa ne, zai ɗanɗana mata bakar azaba kuma ya yi mata video!!. Sam ita bata kawo komai a ranta ba, bayan sun koma gida, tare suka wuni da Cherish har zuwa yamma. Sannan Cherish ɗin ta ce mata zata je gida dan akwai abin da take son yi. Okey ta amsa mata a in da suka yi sallama bayan sun rungumi juna tare da sumbatar juna kamar yanda suka saba, suna Kaunar junansu sosai, kuma suna girmama juna, ƙawancensu cikin gaskiya da amana suke yin shi. Da misalin karfe tara na dare, ta gama duk abin da zata yi, kayan jikinta ya cire tare da ɗaura towel ta shiga wanda dan ta yi shirin barci. After some minutes ta fito ɗaure da towel a kirjinta, ga kirjin nasu na gado, breast na ta a cike fam, idan ta sanya kaya sai sun yi kamar zasu fasa rigar, kuma ba wai irin masu cikar munin nan ba ne, a'a irin na Naurat ce, kyawawa ne sosai masu kyan fasali, dukka ita suka gado, haka mafiya yawansu breast nasu yake. A gaban mirror ta tsaya zata shafa Lotions nata, sai sheki kyakkyawar fatar jikinta yake yi, luwai luwai da shi, gata jajir jinin Russians. Wayarta dake palo saman sofa ne ya fara kara, alamar shigowar kiran. Da sauri ta ajiye Lotion da yake hannunta ta nufi palon, sam towel ɗin bai gama rufe mata santala santalan cinyoyinta ba. Cherish ce take kiranta a waya, picking ta yi tare da karawa kunnanta tana ɗan shafa kyakkyawar bakin gashin kanta dake ɗan digar da ruwa. Daga ɗayan ɓangaren Cherish ɗin ta ce ta duba mata shin a gidanta ta manta ɗayar wayarta da hand bag nata ne?. Tana ƙoƙarin amsawa ta ji an danna kararrawar kofar, kai kallonta a kan kofar ta yi. Ba tare da tsoro ko ɗar ba ta nufi kofar. Kasancewar tana waya hankalinta ya rabu gida biyu, sai ta mance bata leƙa mahangar kofar dan ta ga wanene ba, sai kawai ta buɗe kofar tana gayawa Cherish ta cika watsar da abubuwa, ya kamata ta rinƙa kula da abubuwanta............. Wani irin mahaukacin birki ta ja da maganar nata tare da sake wayar ta faɗi a kasa saman tiles ɗin, nan take wayar ta tarwatse, dan mummunar faɗuwa ta yi. Ba komai ne ya ja mata wannan razana ba face ganin Dr William a tsaye a bakin kofar!. A tsananin razane ta fara kallon shi from head to toe. Pajama ce launin white color a jikinsa. Abin da ya fi bata mamaki shi ne dogon baƙin gashi siɗif mai laushi da tsantsi sai sheki yake yi da ya sake har bayansa, dama yana tara gashi har haka ne? Ta tambayi kanta, bata taɓa lura da gashin ba kasancewar yana ɗaureta a bayan wuyarsa. Ta yi tsananin razane na ganin blue eyes nasa, ga shi kuma dare ne, kun san da daddare kuma yanda idanun suke, har wani kara kyalli suke yi. A koda yaushe ta haɗu da shi yana sanye da black glass a fuska, bata taɓa ganin ainahin kalar kwayar idanunsa ba sai yau, abin ya tsoratata. Daurewa ta yi cikin dakiya ta ce mishi lafiya? Me yazo yi a gidanta?. Tana magana voice nata na rawa, tamkar zata saki fitsari a wando, saboda tsoro, amma ta daure ta ɓoye tsoron. Shigowa cikin palo nata ya yi tare da mayar da kofar ya rufe har da murza key. Tamkar ba shi ba, sam yaki buɗe baki ya yi magana, duk da cewa dama tun ainahi bashi da yawan magana sam, baya son hayaniya. Ganin ya rufe kofar ya murza key ne yasa ta wage baki zata yi mishi ihu. Da sauri ya toshe mata bakin nata tare da kama hannayenta dukka biyu ya mayar da su ta bayanta da hannunsa ɗaya, dan ya samu ya ɗaure hannun nata tare kuma da ya kaita kasa ta zube a kan gwiwowinta!. Ƙoƙarin kwace kanta ta fara yi da iya karfinta, sai dai ina ya fita karfi nesa ba kusa ba, da hannu ɗaya ma idan ya riketa ba zata iya kwacewa ba. Da ya ga zata bashi matsala sai ya sanya hannu a cikin aljihun wandonsa, ya ciro wata farar handkerchief, fara tas da ita. A daidai sai tin face nata ya kawo handkerchief ɗin a in da ya.............. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E2 Ƙoƙarin kwace kanta ta fara yi da iya karfinta, sai dai ina ya fita karfi nesa ba kusa ba, da hannu ɗaya ma idan ya riketa ba zata iya kwacewa ba. Da ya ga zata bashi matsala, sai ya sanya hannu a cikin aljihun wandonsa, ya ciro wata farar handkitchef, fara tas da ita. A daidai sai tin face nata ya kawo handkitchef ɗin a in da ya ɗaure mata baki da shi. Bayan ya ɗaure ne sai ya kama hannayen nata da kyau tare da fara ƙoƙarin murɗesu baya, dan ya ɗaureta gam ya yi abin da zai yi. Tun da ya shigo ko A bai furta da muryarsa ba, tamkar kurma. Da kafarsa ɗaya ya kwashe kafafunta ta zube kasa a saman gwiwowinta, har lokacin bata dai'na yunkurin kwatar kanta ba, ga shi babu halin yin ihu. Haɗe kafafun nata ya yi a in da ya takesu da kafarsa ɗaya, dan ta kwanta shiru a kasar. Amma ina, da yake hannunta ba'a ɗaure yake ba, sai ta yunkura zata miƙe. Ganin hakan tasa sai ya take mata wuya da kafa ɗaya, hakan tasa dole ta yi sanyi, ta hakura ta kwanta shiru gudun kada ta illata kanta, koma ta kashe kanta, dan yanda ya taketa ɗin nan ba zata iya kuɓuta ba, sai dai ta illata kanta kawai. Rigar jikinsa ya fara cirewa kafin ya fito da wata ƴar ƙaramar camera da yake son ɗaukarta video da shi. Kunna ta ya yi, daga in da suke ya miƙa hannu, ya ɗaura camerar a saman sofa ta yanda zata ɗauki ita gwaggo amma ban face nasa. Bayan ya cire rigar jikinsa sai ya zame kafafun nasa daga wuyar tata tare da cire wandonsa. Tsabar ta taku a wajensa, ko motsawa ta kasayi, da kyar take numfashi. Damko kafafunta ya yi bayan ya kammala cire wandon ya rage daga shi sai short. Sake gyara camerar ya yi kafin ya hau kanta da nufin ya yi abin da ya zo yi. Sai a lokacin ta fara dawowa cikin hayyacinta, ƙoƙarin ture shi ta fara yi, shi kuma yana ƙoƙarin cire towel na jikinta. Ganin ba zata iya ture shi daga kanta ɗin bane yasa ta ɗaga idanunta sama, tana hawaye ta fara magana kamar haka. "Ya Ubangiji ina tawassuli da sunanka tsarkaka, na sani babu wanda ya isa ya yi mini abin da baka kaddara mini ba, babu kuma wanda ya isa ya hana abin da ka kaddara mini, ya Allah dan darajarka da karfin mulkinka, kada ka bari wannan bawa naka ya buɗe abin da ba hakkinsa ba, idan har musulcina gaskiya ce, dominka kuma nake yi, to ya Allah ka kare mini mutuncina! Na baka amanar kai'na, Allah ka jikaina, ka ji tausayina, bani da wayo bani da dabara, kana gani babu abin da nayi wa wannan azzalumi zai zalunceni, ya Allah tun daga farkon Alkur'ani mai girma har karshe wanda ta kasance maganaka ne a ciki, ya Allah babu a in da kayi alkawarin tallafawa azzalumi, Allah ka fini sanin cewa shi azzalumi, ina mai rokonka da tsarkakekkiyar zuciya da kuma yakinin kai kaɗai zaka kareni daga zaluncinsa, ka kare ni ya Ubangijin sammai da kassai!". Sai zuba adduarta take yi a cikin zuciyarta cike da tawassulin Allah zai karɓa mata, tana ta kuka hawaye wani na bin wani, sam tama dai'na jiyo abin da Dr William ɗin yake ƙoƙarin yi mata, hankalinta har ya fara barin jikinta saboda nutsawa da ta yi wajen adduo'i da take yi. Yana ƙoƙarin shigarta sai kuma ya tsaya cak, tamkar wanda aka yi wa allura, haka ya ji a jikinsa, nan take jikinsa ya mutu, ji ya yi wani irin mugun tausayinta ya shige shi lokaci guda. Dawo da kallonsa a saman face nata ya yi, sai kuka take yi babu kakkautawa. A hankali ya sauka daga jikin nata ya koma gefe yana kallonta. Jin nauyi ya bar jikinta ne yasa ta dawo cikin hayyacinta. A hanzarce ta zaro idanunta waje sosai. Ganin ya sauka daga kanta ne yasa ta yunkura da iya karfin da ya rage mata. A ɗari ta miƙe tsaye dan ta gudu. Wannan miƙewa da ta yi tasa ya ji wani irin azababben sha'awarta ta motsa mishi kuma, abin ku da shaiɗan, nan take ya ji karfi ya zo mishi. Cikin zafin nama shi ma ya miƙe tare da tare gabanta. Har lokacin bakinta a toshe, rikota ya yi ta kafaɗa. Duka ta fara kai mishi tare da ƙoƙarin juyawa ta gudu cikin ɗaki tun da fita waje dai ya gagara. Shi kuwa hannunta ya fara ƙoƙarin kamawa dan ya ɗaure. Yana ƙoƙarin ɗaure mata hannun nata ne ta juyo da karfin gaske a in da ta faɗa saman faffaɗar kirjinsa. Wani irin azababben kifiya na wani yanayi ne ya caki kahon zuciyarsa. Wani irin diff ya ji komai ya ɗauke mishi na wucin gadin, sakamakon saukar kyawawan tula tulan breast nata da ya ji a jikinsa, ga shi kuma shima babu kaya a jikin nasa, sai short. Ita kuwa dafa kafaɗunsa ta yi tare da barin jikin nasa, a hanzarce ta nufi kofar fita, dan ta gudu ta bar gidan, tana tafiya tana ƙoƙarin kwance handkerchief da ya ɗaure mata baki da shi. Kamar daga sama taga mutun a gabanta, har lokacin bata gama kwance handkerchief ɗin ba, ba halin ta yi mishi ihu. Zuba mata idanu ya yi yana kare mata kallo from head to toe, tun da suke haɗuwa bai taɓa tsayawa ya kalli ya face nata yake ba, sai yau. Wani baƙon yanayi ya ji a tattare da shi, ji ya yi ba zai iya yin abin da ya kawo shi ɗin ba, ya ji ma ko wani ne ya zo zai yi mata hakan, to fa sai in da karfinsa ya kare, zai tsaya mata sosai!!. BA DOLE KA TSAYA MATA BA, AN GAYA MAKA ADDU'A WASA NE? ALLAH AI YA WUCE TUNANIN MAI TUNANI, DUK WANDA YA CE YA MIƘA LAMURANSA GA ALLAH, TO ALLAH KUMA ZAI KULA MISHI DA KOMAI, NAKA WASA NE DR WILLIAM, ALLAH IDAN KA YARDA ALLAH SHI YAKE YIN KOMAI, TO FA KAI DA BAKINCIKI A RAYUWARKA KUN YI HANNUN RIGA, ALLAH UBANGIJI KA IYA MANA DA IYAWARKA, MU BA ZAMU IYA BA, BAMU DA TSUMI BAMU DA DABARA!!. Ganin face nata yasa ya faɗa zazzafar soyayyarta. Kyafta idanunsa sau biyu ya yi yana mai cigaba da kallonta. Ganin hakan yasa a guje ta raɓa gefensa dan ta wuce ta fita waje. A hanzarce ha riko hannunta ta sama wajen gwiwar hannu. Fisgota da karfi ya yi, luuu ta tafi ta faɗa jikinsa. Zubawa face nata idanu ya yi na ƴan mintoci kafin ya kai hannu ya kwance mata handkerchief ɗin daga bakinta. Karo na farko da ta saurari zazzaƙar muryarsa da kyau, a in da ya ce mata ta yi mashi shiru, shi babu abin da zai yi mata. Dogon numfashi ta ja tare da sauke nauyayyar ajiyar zuciya, tsabar jin sanyi a ranta da ta yi na jin ya ce ba zai yi mata komai ba, bata ma san time da ta kwantar da kanta a saman kirjin nasa ba, sai sauke ajiyar zuciya tare da nisawa take yi. Shi kuwa, ta kara gefa shi cikin yanayi mai wuyar fita, ga shi daga ita sai towel, kasa jurewa ya yi, sai da ya sanya hannu ya rungumota da kyau a jikin nasa. Jin hakan yasa ta yi kokarin barin jikin nasa. Amma sam bai saketa ba, ya kankameta sosai tamkar mallakinsa ce ita. Da ɗan ɗaga murya ta ce mishi lafiya?. Muryarsa can kasa kasa yana sarkewa, ya ce mata babu komai. A takaice ta ce to ya saketa, ba musu ya saketa ɗin yana binta da idanu. Da sauri ta wuce izuwa cikin bedroom nata dan ta sanya kaya. Binta da kallo ya yi, yana kallon yanda mazaunanta suke juyawa idan ta taka kafarta. Sai da ta kurewa ganinsa ne ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya tare mai da kayansa da ya cire a jikinsa, sannan ya koma saman sofarta ya zauna. A hankali ya jingina kansa da jikin head na sofar tare da lumshe idanu yana jin wani irin kaunarta daga kallon farko tana shigar shi. Ya kai 20 mins a zaune a wajen yana tunani. Kamar daga sama ya ji zazzaƙar muryarta tana faɗin "To me ka zo yi a gidana? Ya kuma baka tafi ba?". A hankali ya waro idanuwansa da suke ja sosai a kanta. Tana shirye cikin kayan barci riga da wando pink color masu kyau. Kirjinta kawai ya zubawa idanu ya rasa amsar da zai bata. Muryar tata ce ta sake katse shi da cewa, lafiya yake kuwa?. Bai san time ɗin da ya ce mata "Please can i have a green tea?". Shiru ta yi tana ɗan tunani. Tamkar zata ce mashi babu, sai kuma ta kasa faɗin hakan, dan ita mafa, tun a ranar farko da ta fara ganin shi ta faɗa mishi, ta ji tana son shi, kawai dai bata bawa hakan dama bane yasa bai yawaita a cikin zuciyarta ba, amma kam ba shakka ta faɗa!. Wucewa izuwa kitchen ta yi ba tare da ta sake ce da shi uppan ba. Green tea ɗin ta haɗa mishi, ita kuma ta haɗa nata black tea. A saman wani kyakkyawan plate ta jere two cups ɗin, cikin natsuwa ta ɗauko tare da fitowa zuwa palon. Yana zaune a in da ta barshi, bai ko motsa ba. Kawo mishi plate ɗin saitinsa ta yi dan ya ɗauki tea ɗin nasa. Ba musu ya ɗauka tare da ce mata thank you. Jinjina mishi kai ta yi ta wuce zuwa saman sofa dake ɗan nesa da shi ta zauna. Cikin natsuwa ta fara shan tea ɗin nata. Sai kallonta yake yi, ya kasa shan nasa. Sarai ta lura da hakan, amma sai ta basar ta cigaba da shan nata. After some minutes, ta gama shan nata tsab, shi kuwa rabi ya sha, dan dama ba tea ɗin yake so ba, mai tea ɗin yake son ya yi ta kallo. A nutse ta ce mishi to ya tafi gidansu mana, tana so ne ta kwanta dare ya yi. Har lokacin da akwai tsoron shi sosai a kwance a cikin idanuwanta. Zuba mata idanu ya yi na ƴan mintuna kafin ya fara magana cikin sanyin murya. "Dare ya yi sosai, kuma ni ina jin tsoron hanyar komawa, ga shi ban zo da mota ba". A shagwaɓe sosai ya yi maganar. Bata san time ɗin da dariya ya kubce mata ba, wai dare ya yi sosai yana jin tsoron hanya, lallai ya iya tsara magana, har da wani shagwaɓe murya, ko waye ya koya mashi shagwaɓa kuma? Ta tambayi kanta. Ta sani ba wani tsoron hanya, kawai iskanci ne irin nasa, da ba da kafafuwansa ya zo ba?. "A'a babu komai a hanya kawai ka tafi". Ta faɗa tana kwaikwayon muryarsa na shagwaɓar da ya yi maganar. Ɗaura cup ɗin tea ɗin ya yi a saman table da yake kusa da shi. A nutse cikin shagwaɓa ya ce "A'a, Please ki bari na yi ta kallonki, kin ji ko?". Zaro dara daran idanun nan nata ta yi, tana faɗin "Kallona kuma?!". Gyaɗa mata kai ya yi tare da gera ɗaya. Cool murmushi ta sakar mishi kafin ta ce "Meyasa to?". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Because you are so cute, very very beautiful baby!". Oho god, jin ya yabeta tuni ta kara afkawa tekun son shi, dan ya fi karfin kogin so wannan, sai dai teku. Sam bata ma san time ɗin da ta ce mishi "Same, you are very very beautiful, handsome guy, i really like your eyes color". Ɗan zaro mata su ya yi. Da sauri ta runtse idanunta dan sun bata tsoro ganin yanda suke kyalli. Muryarsa ta tsinkayo cikin kunnenta yana faɗin "I really like your eyes, your lips and your everything". Waro idanuwan nata waje ta yi tana kallon yanda ya jingina kansa da jikin head na sofar yana binta da shanyayyun idanuwansa tamkar wanda ya yi shaye shaye. Abokan faɗa sun shirya yau kam, har ma suna ƙoƙarin zama cikakkun masoya na gaskiya.......KADA KU YI COMPARING RAYUWAR NAN NIGERIA DA NASU NA CAN, DAN AKWAI MUGU MUGUN BANBANCI, RAYUWARMU DA TASU BA ƊAYA BACE SAM, SO KU DAI'NA KALLON RAYUWAR TRIPLETS DA FAMILYNSU, MA'ANA SU DR WILLIAM KENAN, KU DAI'NA KALLONSU TA SIFFAR TAMU RAYUWAR, DAN BA HAƊI, AL'ADU DABAN DABAN!!. Hannu ya miƙa mata a kan ta zo, bata musa mishi ba dan kada ku manta girman Russia ce ita ma, da ita da shi duk zani ne ta tadda muje, tafiyar duk ɗaya ce. Miƙa mishi nata hannun ta yi. Cikin nutsuwa ya jawo hannun nata alamar ta zo gare shi. Miƙewa ta yi tare da nufarsa. Tana ƙoƙarin zama a gefensa ya yi saurin zaunar da ita a saman cinyarsa. A tare suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya. Hannunsa dukka biyu ya ɗaura a saman shafaffen cikinta tare da ɗan jawota baya ta kwanta a saman kirjinsa. Ɗan leƙo face nata ya yi yana faɗin "You are the best and you are special beb!, Kuma rigimammiya". Ɗan juyowa gare shi ta yi, suna ɗan fuskantar juna kafin ta ce "Why you say that?". Ɗan shafa shafaffen cikin nata ya fara yi a hankali yana haurawa sama kafin ya ce "Ban taɓa tunanin zan kula mace ba a rayuwata, infact ni ban san menene ma yake sanyawa a so mace ba, bani da aboki, bani da kawa, only my brother Herry, shi ne kawai na kusa da ni, i have one sister, Josephine, even her ba zan ce maki ga yanda jikinta yake ba a yanzu, because in kin ganta a area da nake ma, to dad ne ya ce ta kirani or something like that". Ɗan kwanciya ta yi a gefen kirjinsa tana faɗin "But why some peoples are calling you dangerous boss?. In the first place ka nuna mani you are the boss ɗin da gaske, and now kuma naga har da shagwaɓa ashe ka iya?". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Ni ruwa biyu ne ai, a gida wajen mum da dad ina yi musu shagwaɓa, amma idan na baro wajensu, ba zaki taɓa cewa ma ina yin magana ba, bare shagwaɓa, kin taɓa kallona a class ina magana da wani ne? Or ina surutu?". Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a. Shafa gefen lallausan kumatunta da ɗayan hannunsa ya yi yana faɗin "Haka nake to, bana magana da mutane, kuma sunan dangerous, wait small, zaki san daga ina sunan ya samo asali kin ji?". Jinjina mashi kai ta yi tare da ɗan yunkurawa zata bar jikin nasa. Da sauri ya riketa yana kallon face nata. "Where are you going?". Da hannu ta nuna mashi saman sofarta ba tare da ta yi magana ba. "Saman jikina ɗin babu daɗin kwanciya ne?". Ya tambaya yana mai do da ita jikin nasa. Girgiza mashi kai ta yi kafin ta ce "Akwai daɗi, amma ai kaga babu kyau ko? Mum ta hanani yin hakan". "Why mum zata hanaki kuma? Is there any problem akan hakan?". Ya yi tambayar da mamaki bayyane karara a saman face nasa, dan su rungumar juna, kiss, da sauransu ba wani abin bane a wajensu, shi ne yasa yake mamaki da ta ce zata bar jikin nasa. "No any problem, kawai dai yin hakan kuskure, mum ta ce addini ya yi hani da hakan, so ni ba wani ilimin addinin nake da shi sosai ba, amma na iya karatun Alkur'ani mai girma sosai, saboda shi mum ta fi koya mini, amma dai koma me, is better na yi abin da ta ce koma yaya ne ko?". Maimaita kalmar addini ya yi kafin ya tambayeta ita a wace addin take. "I am a Muslim, what about you?". Ta bashi amsa with her full confidence. Murmushi kaɗan ya yi, wanda da ka gani kasan dole ya ƙaƙalota, dan murmushi bata da gurbin zama a face nasa, duba da yanayinsa ba mutun ne mai fara'a ba sam sam. "Am a Kristen, my name is William". A hanzarce ta miƙe daga jikinsa jin abin da ya ce, bata taɓa tunanin shi krista bane, duba da yanayin irin fuskarsa, yana da face mai kyalli sosai, idan ka ganshi, zaka yi tunanin yana sallah. "Why are you avoiding me like that dan na ce am a Kristen? Shin da kika ce mini ke musulma ce did i do something like that to you?". Girgiza mashi kai ta yi, sai kuma da ya yi magana ta fahimci ta yi kuskure na irin gudunsa da ta yi lokaci guda haka, yin hakan zai sanya ko da yana son shiga addinin musulunci ma, sai ya fasa, saboda zai ce dama haka musulmai suke? Dama basu son wani addini idan ba nasu ba?. Bai san mu musulmai kowa ma muna kaunarsa ba, kuma muna zaman lafiya da shi, addininmu mai sauki ne, addininmu mai ni'ima ne wanda ya bamu damar zama waje ɗaya da wanda ba musulmi ba, mu yi zaman mutunci, kamar da ƴan uwanmu musulmai muke tare, musulmai ne kawai za'a ci hakkinsu kuma su hakura, su yafe, su cigaba da zama da mutun, ai addinin musulunci babu biyunsa a duniya, ya yi ne kawai babu mai musawa sai dai wanda baya son gaskiya. Shiru ta ɗan yi tana ƴan kame kame, ta rasa abin yi. A lokacin sam bata da wani ilimin addini sosai, haddan Alqur'ani mai girma ne kawai gareta, shi ɗin ma ba dukka ba, kuma bata san fasarar ko sururori biyu daga ciki ba, so hakan yasa ta rasa me zata ce mishi, sai dai ƴan kame kame, ilimin boko ya fi yawaita sosai fiye da misali a kanta sama da na addini, matsalar da aka samu kuma shi ne, ita bata wani zauna da su Brr Naurat sosai ba, secondarynta ma, boarding school ta yi, so bata sami lokaci da iyayenta sosai ba, shi ne yasa. Ganin haka yasa shi ya miƙe ya koma saman sofar da take zaune. Kusa da ita ya zauna tare da ɗan riko hannayenta, cikin sanyin murya ya ce "Please kada ki gujeni, kin ji? I really love you the way you are, please love me the way i am, don't be angry because am a Kristen my angel, you hear?". Wani sanyi ta ji a ranta na jin kalamansa, ta ji daɗi sosai, hakan yasa ta ji cewa zata iya janyo shi a jiki har ya karɓi addinin musulunci. Dan haka sai ta juyo da kyau suna fuskantar juna, cikin sanyin murya ta ce "I really love you the way you are, so don't worry!". Sakin hannayen nata ya yi tare da buɗe mata hannu alamar ta zo gare shi. Ba musu ta faɗa jikinsa tana ɗan murmushi, shafa bayanta a hankali ya fara yi yana mai jin daddaɗar yanayi a tattare da shi. "What is your name?". Muryarsa ya daki dodan kunnanta. "A'isha". Ta bashi amsa, ɗan ɗago haɓarta ya yi yana faɗin "Nice nema, but can i call you my angel or my beauty?". Jinjina mashi kai ta yi alamar e. Ɗan kara matseta a jikinsa ya yi tare da sumbatar goshinta. Haka suka kasance suna ta hira dan sanin juna har wajen karfe ɗaya na dare. A nan ne ta ce mishi barci take ji, zata je ta kwanta. A kunne ya raɗa mata a kan cewa tare zasu kwanta a gado ɗaya, Okey ta ce mishi. Miƙewa ya yi da ita a jikinsa a in da ya gyara ɗaukarta da ya yi, ya zamana ya ɗaurata a saman kirjinsa, suka nufi cikin bedroom ɗin nata. Bai sauketa a ko'ina ba, sai a saman gadonta, murmushi ta sakar mashi kafin ta ce ta gode. Hayewa gadon shi ma ya yi, daga ɗan gefen da shi ta kwanta, ya so tambayarta me yasa har yanzu take gudun shi, amma sai kuma ya basar bai tambaya ba, sai ma ya juya mata baya, dan ya lura tamkar tana cikin damuwa na kwanansu gado guda. A can gidansu kuwa, su Uncle Herry sai neman shi suke yi, sun je bedroom nasa baya nan, hankalin daddynsu ya tashi, ga shi ya bar musu wayarsa ma a gidan, mum ɗinsa har da kuka ta rinƙa yi, tamkar yaro ne karami William ɗin, mutumin da ya kai 24 years a duniya, amma sun ɗaga hankalinsu har haka, da yake shi gaskiya ba mai yawan fita bane na farko, na biyu idan ma zai je party ko gidan rawa, yana gayawa mum ɗin nasa shi fa ya tafi waje kaza, kuma ba zai dawo ba sai time kaza, idan ya ce hakan, to time ɗin na yi zai dawo abinsa, hakan tasa suka ɗaga hankalinsu sosai da basu gan shi ba. Shi kuwa shiru ya kwanta ya kasa yin barci, baya son gaya mata ne or ta gane, amma ji yake yi tamkar a cikin keji yake, gidan nata ya yi mishi ƙarami over, duk ya takura, dan fa su gidansu, gida ne na madarar kuɗi, babban yayan daddynsu shi ne president mai ci a yanzu, ga uban kuɗi da suke da shi na wuce misali, gidansu aljannar duniya ce guda, bedroom nasa kawai ya kai girman gidan nata gabaɗaya har da palo da kitchen, so bai saba da ƙaramin waje haka ba, duk sai ya takura. Ita ma ta kasa barci saboda tsananin tsoronsa, sai taga kamar idan ta yi barci, zai yi mata wani abin, dan fa gani take yi kamar fyaɗe ya zo yi mata kamar yanda ya nuna mata tun farko. After some minutes, can duniya ta kara yin shiru sosai. Lallaɓawa ta yi ta miƙe zaune, a hankali ta matso kusa da shi, cikin sanɗa ta ɗan leƙo fuskansa, dan ta gani ko ya yi barci. Tana so ne ta yi barci, amma ta kasa, saboda tsoro, shi ne ta zo ta gani ko dai ya yi barci ita ma ta samu ta yi. Ganin idanuwansa a rufe yasa ta ɗan koma ta zauna zuciyarta na yi mata wasi wasi a kan bai yi barci ba, yana jiran ta yi barci ne kawai ya hake mata. Jin abin da zuciyarta yake raya mata ne yasa ta sake lallaɓawa ta leƙo face ɗin nasa. Duk abin da take yi yana jinta, sai dai bai motsa ba, dan shi ma yana son ta sami nutsuwa ta yi barci. Amma ina abin ya ci tura, sake leƙo face nasa a karo na uku ta yi, dan ta kasa sakin jiki ta kwanta, ta kasa yarda da ya yi barci. Jin haka yasa ya bari time da ta leƙo face ɗin nata a karo na ukun, sai ya jawo hannunta da ta kafa a jikin mattress ɗin ta gaban face nasa dan ta sami damar leƙa shi da kyau. Jawo hannun ya yi tare da juyowa gareta ta faɗa saman kirjinsa. Rungumeta sosai ya yi tare da juyowa da ita da kyau da kyau suna fuskantar juna. "My beauty, why zuciyarki bata yarda da ni ba?". Girgiza mashi kai ta yi tana faɗin ba komai. "Seriously babu abin da zan yi miki, idan ina son na yi miki wani abin, ki sani tsab zan iya yi ba tare da son ranki ba, amma i can't do that, so feel free and sleep kin ji?". Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke tare da ɗaura kanta a saman gefen kirjinsa, a hankali ta lumshe idanu bayan ta ɗaura hannunta a saman wuyarsa, ta ɗan saƙalo kenan. Shi ma nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, sai a yanzu ne ya ji zai iya yin barci, ji ma ya yi tamkar kwanciyar nan da ta yi a jikinsa, kamar ta karawa ɗakin nata faɗi da girma ne, so sai ya ji yanzu yana normal. Hannu ya ɗaura a saman bayanta tare da lumshe idanu shi ma. Ba jinawa barci ya yi awon gaba da su.......ASUBA TA GARI. Da yake bata yi barci da wuri ba, har wuraren uku suka sami barci, sai bata iya tashi sallar asuba, makara ya kamata, shi dama ba sallah yake yi ba!. Sai misalin karfe 7 na safe ta farka, a hankali ta waro idanunta, kai tsaye sai saman kyakkyawar face nasa. Sai zuba barcinsa yake yi hankalinsa a kwance, ɗan shafa lallausan kumatunsa ta yi tare da yunkurawa zata mike. Duk motsinta yana ji, dan sam bashi da nauyin barci, tun farkawarta ya farka shi ma. Jin zata bar jikinsa ne yasa ya waro idanunsa a hankali shi ma, kai tsaye sai saman face nata. Kasa kasa da murya irin na mai barci ya ce "Good morning my beauty". A hankali ya motsa laɓɓan nasa wajen furta maganar. Cool murmushi ta sakar mashi kafin ta amsa mishi da "Morning my Dr, how was your night?". Bai amsa mata ba, sai dai ya tsareta da idanu yana kallonta. Ganin hakan yasa ta yunkura zata miƙe, matsowa ya yi kusa da ita sosai tare da rikota. Can kasan makoshinsa ya furta "Can i have a one kiss my beauty?". Ɗan ɗaga idanunta sama tamkar mai tunani ta yi. Bai jira ta bashi amsa ba ya matso kusa da ita sosai tare da haɗe fuskokinsu, kafin ta yi wani yunkuri ma har ya fara kissing nata abinsa. Wani irin duniya suka lula dukkansu biyu, Baturen mutun akwai shegen iya soyayya, ya yi mata wayo sai bata hot kiss yake yi. Haka ya matseta a jikinsa tare da fara shafa mazaunanta da tun jiya suka tsole mashi idanu, kuma suke ɗaukar hankalinsa, cikin kwanciyar hankali yake yin komai. Karar danna kararrawar kofa ce ta dawo da shi daga duniyar da ya afka. Da kyar ya iya raba bakinsa da nata, idanuwansa sun yi jajir kamar wuta, murya kamar wanda ya yi shaye shaye, a hankali kasa kasa ya furta yana zuwa bari ya duba wanene. Okey ta amsa mashi tare da miƙewa ita ma ta nufi toilet jiki ba kwari. A nata tunanin Cherish ce ma, ta san ita kaɗai ce take zuwa mata gida without a permission. Toilet ta shige, shi kuma ya sauko ya nufi palo. Yana buɗe kofar suka yi ido huɗu da daddynsa, mummynsa, Uncle Herry da kuma ƴan'sanda guda biyar, masu sanye da kakinsu a jiki, jajir da su kamar tsada. A lokacin mummynsu tana da cikin Tyson, wato Tga kenan. Hakika babu maraba a tsakanin face ɗin Dr William da mummynsa, harta blue eyes ɗin nata ne ya ɗauko, kyakkyawar mace ce na wuce misali, shiyasa dukkansu suke kyawawa tamkar su suka yi kansu, tana da tsawo sosai, har ta ɗara daddynsu tsawo, a takaice dai wannan blue eyes da tsantsar kyau na wuce misali, tsawo zara zara da su, a wajen mummyn Dr William suka gado shi, ga black cuirly hair sosai, gashin nata kuma har kugunta ta baya. Da sauri mum ɗin nasa ta ce "My son, what brought you here? What are you doing in this dirty place? What happened to your eyes?". Harara ya wurgawa uncle Herry dake tsaye a gafe kafin ya ce "What are you doing here Herry?". Tun bai gama rufe baki ba Uncle Herry ya juya ya bar wajen, dan fa yasan ɗan uwan nasa sam bashi da sauki. Dawo da kallonsa a kan dad da mum ɗin nasu ya yi, ɗan ɗaure fuska ya yi yana faɗin "Mum why are you disturbing your self like that? Ni fa ba yaro ba ne, you have to be.........." Katse shi ta yi da cewa lallai shi yaro ne a wajenta, kuma ya zo su tafi gida. Make mata kafaɗa ya yi a kan shi dai ba zai tafi ba, daga karshe ma sai ya ce suje gidan yana zuwa. Sun yi sun yi ya gaya musu me yake yi a cikin wannan kurkukun gidan, local da shi. Amma ina, sam yaki faɗa, sai ce musu ma ya yi, idan basu tafi ba, shi zai yi kuka tun da haka ne. Basu da zaɓi, dole su tafi, dan suna mugu mugun son farincikin ɗan nasu fiye da komai a duniyarsu, su ne nan suka ɓata shi da kuɗi, suka sanya yana yin abin da ya ga dama, ya taka kowa, babu wanda ya isa ya taka mashi birki. Bayan sun tafi sai ya dawo cikin ɗakin, saman bed ɗin ya koma ya zauna yana tunanin abubuwan da suka faru a tsakaninsa da gwaggo tun daren jiya zuwa yanzu, mamakin kansa yake yi, tamkar ba shi ba, mace ta canza shi a lokaci guda. A haka ta fito ta same shi, jikinta na ɗaure da towel white color mai ɗan girma zuwa gwiwa. Binta da kallo ya yi babu ko kyaftawa. Har ta kammala shafa Lotions nata yana ta kallonta, da yake sam ita ma bata san kunya ba, sai ya zamana ko a jikinta, bata damu dan yana cikin ɗakin ba, haka ta shafa duk abin da zata shafa a gabansa kafin ta nufi dressing room na cikin ɗakin nata. Sai da ya ga shigarta dressing room ɗin ne ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya tare da jingina kansa da jikin headboard na bed ɗin yana sauke numfashi a hankali hankali. After some minutes. A haka ta fito ta same shi. Shirye take cikin wandon jeans baki da riga mai ƙaramin hannu pink color, ta yi matuƙar kyau sosai, ta ɗaure gashin kan nan nata a tsakiya, sai tashin fitinannen kamshi take yi. Kamshin perfume ɗin nata ne ya daki hancinsa ya sanya shi ɗagowa yana bin in da ya ji kamshin da kallo. Wow ya furta da ɗan karfi tare da ɗaga mata gera ɗaya. Murmushi kaɗan ta yi hannunta na rike da dadduma da hijabi. Ta kusa da mirror ta je ta shimfuɗa daddumar tare da sanya hijabi ta tsaya ta tada sallah. Zuba mata idanu ya yi yana kallon yanda take sallar babu ko kyaftawa. Har sai da ta kammala kaf a kan idanunsa tamkar mai karanta wani abin, bayan ta kammala ne ta miƙe tare da naɗe daddumar ta nufo in da yake zaune. Cikin sanyin murya ta ɗaga mishi gaisuwa tamkar mijinta na sunna. Fuska ba yabo ba fallasa dan baya dariya, haka ya amsa mata. Duba kyakyawan ƙaramin watch dake ɗaure a hannunta ta yi tana faɗin "Dr muna da class karfe 9:30 fa, yanzu kuma 8:30, remain 1 hour, ya kamata ka je gida ka shirya, sai mun haɗu a school ko?". Nisawa ya yi tare da miƙewa tsaye, nan take ta dawo tamkar Rimsha a gaban Lion, dan ya fita tsawo sosai shi ma, kamar dai Lion da Rimsha, gara ma Dr William da gwaggo, ratar shekaru babu yawa a tsakaninsu, shi kuwa Lion ratar shekaru dake a tsakaninsa da Rimsha suna da yawa. 31 to 32 years Lion yake da shi, ita kuma Rimsha 14 to 15 years, kun ga kuwa da akwai rata sosai a tsakaninsu, so gara Dr William da gwaggo. "Bana jin zan iya tafiya na barki, dan ban gaji da ganinki ba". Ya faɗa a sanyaye, shi kansa baya sanin time da wasu kalamai suke fitowa daga ɗan bakinsa nan, bawan Allah ya faɗa tarkon mace lokaci guda, ji yake yi tamkar ba zai iya tafiya ya barta ba. Juya idanunta sama ta yi tamkar mai tunani. Shiru ya yi yana ta kallonta. "Ai zamu haɗu a school ko?". Gera ɗaya ya ɗaga mata ba tare da ya yi magana ba, idanuwansa a shanye kamar wanda ya yi shaye shaye. "Tom shikenan ka je kawai kada ka damu ka ji my Dr?". Dogon numfashi ya ja tare da buɗe mata hannayensa a kan ta zo su yi bye bye. Da sauri ta faɗa jikin nasa tana ɗan murmushi, rungumeta gam ya yi na ƴan mintuna kafin ya ɗan sassauta riƙon nata da ya yi tare da ɗago haɓarta suna fuskantar juna. Rankwafowa kanta ya yi tare da haɗe fuskokinsu. Cikin nutsuwa ya fara kiss nata tamkar matarsa ta sunna. Ko da yake su a wajensu ai lafiya lou ne yin haka, ba wata matsala ba ce. Ya Ubangiji ka hanemu da aikata duk abin da ya zamana ka haramta shi, ka tsaremu da faɗawa taka dokokinka. DA AKWAI DARUSA DA DAMA A RAYUWAR DR WILLIAM DA GWAGGO, HAKA ZALIKA A GABAƊAYA LITTAFIN TRIPLETS KEWAYE YAKE DA DARUSA DA DAMA A CIKINTA MASU AMFANI GA AL'UMMAR MUSULMAI, WANDA DUK ZAN KAWO MUKU SHI A KARSHEN LITTAFIN NAN IN SHA ALLAH, A YANZU MA NASAN KUN KOYI DARUSA DA DAMA SOSAI DA SOSAI, AMMA AKWAI ABUBUWAN DA TUNANINKU BA ZAI KAI KANSU BA HAR SAI NA WARWARE MUKU, KU DAI KAWAI KU KASANCE DA ALKALAMIN PRINCESS TEEMA DAN KU JI KOMAI DALLAH DALLAH. ALLAH KA BANI IKON KAMMALA WANNAN LITTAFIN LAFIYA, KASA NA CIGABA DA RUBUTA MAKU LABARAI MASU AMFANI DA FAƊARKAWA, ILMANTARWA, WA'AZANTARWA, HAR MA DA NISHAƊANTARWA, NA RUBUTA MAKU LITATTAFAN WAƊAN DA BABU SHIRME KO SHIRIRITA A CIKINSU, NA GODEWA ALLAH DA BAIWAR DA YA YI MANI NA RUBUTU, HAKIKA NA SAN LITATTAFAINA BABU SHIRME A CIKINSU, SAI FAƊAKARWA DA ILMANTAR, KUMA SAIDA NE KO MY READERS?. Mayar mishi da martanin kiss ɗin ta fara yi ita ma babu kama hannun yaro, nan take tasa ya fara ficewa daga cikin hayyacinsa. Ba sai na sake faɗa ba, kunsan Turawa da soyayya, akwai iya madarar soyayya zallah. Daga ita har shi kasa tsayuwa a kan kafafunsu suka yi, hakan tasa suka faɗa saman bed ɗin. Mirginawa ya yi a in da ya yi mata rumfa da kirjinsa. Hannu ta tura cikin gashin kansa tana shafawa, shi kuma hannu ya ɗaura a saman breast nata ya fara matsa mata su ta saman riga. Haka suka kasance na tsawon mintuna 20, sosai ya yi romancing nata, sai dai bai yi yunkurin kusantarta ba, dan ta ce mashi bata son hakan, amma ba shakka yana son kusantar tata, kasancewar ya kamu da sonta da tasa baya son ɓacin ranta ne yasa ya hakura ya jure, suka yi iya romance kawai. Da kyar ya iya kyaleta ba dan ya so ba, sai dan time ya tafi, mikewa ya yi daga kanta idanuwansa tamkar wuta saboda ja. Palo ya nufa yana yi mata bye bye tamkar wanda yake cikin maye. Ita ma jiki duk a mace ta mike ba tare da ta canza kaya or something like that ba, ta gyata jikinta kawai ta karisa shirinta na tafiya school. Bayan ta kammala ne ta nufi kofar fita, a nan ne ta ga wayarta a kasa kaca kaca, sai lokacin ta tuna da time da wayar ta faɗi daga hannunta. Duƙawa ta yi ta fara haɗa wayar. A saman table ta ɗaura shi, sannan ta fito hannunta na rike da key ɗin motarta, da kuma wata yar jaka karama, kanta sam babu ɗankwali kamar ba ƴar musulma ba. After some hours. Zaune take a cikin class tana duba wasu handouts dake a gabatan, Cherish bata kariso ba tukunnan. A zahirin gaskiya ba karatu take yi ba, tunanin Dr William kawai take yi, wani sabon son shi ne yake kara shigarta. Idan ka ganta zaka yi tunanin karatu take yi, ita kaɗai tasan me take yi. Ta yi nisa cikin duniyar tunanin da ta afka, kamar daga sama ta ji an rufe mata idanu ta baya. Cool murmushi ta saki kafin ta ce "My Dr me hakan?". A hankali ya zame hannun nasa daga idanun nata yana faɗin "Waye ya ce mani ni ne?". Ya yi maganar yana zagayowa ta gabanta. Sanye yake cikin wasu shegun kaya na manyan yara, crazy jeans ne mai bala'in tsada irin wanda Areef yake son yawan sakawa, sai high neck t-shirt irin wanda Lion yake son yawan sakawa, har wa yau wuyarsa na ɗaure da wanan diamond chain ɗin mai matukar kyau. Yau dai ya saki gashin kansa bai ɗaure ba, kamar kullum black glass ce a face nasa. Abin da yasa suke son saka black glass shi da Lion shi ne, basu son yawan kallo, jama'a suna yawan tsaresu da idanu, dan kalar idanunsu abin so ne da kuma abin ban sha'awa ga mutane, ko a cikin turawa da wuya ka sami mai sky blue eyes masu girma dara dara suna kyalli da kyau tamkar nasu, so jama'a suna takura musu da kallo, hakan tasa suke yawan sanya black glass dan ma kada ayi ta kallonsu. Kusa da ita ya zauna yana ɗan rungumota a jikinsa. Gabaɗaya jama'ar dake cikin class ɗin suna karatu, sai da suka saki ido da baki suna kallonsu, ko da sunan wasa, basu taɓa ganin Dr William yana magana da maza ƴan uwansa bama bare mace, idan ka ji yana magana a school ɗin, to faɗa yake yi da wani, dukan ɗan mutun yake yi, dan fa mafaɗaci ne over ga zafin rai da taurin kai, boss ɗin ne da gaske. Shi kuwa ko kallo jama'ar cikin class ɗin basu ishe shi ba, sai ma hannu da ya sanya ya zame pil ɗin da ta makale gashinta da shi yana faɗin, shi baya son ta ɗaura gashin nan, yau saboda ita yasa bai ɗaure nashi ba, dan haka ita ma ta bar nata a haka. Jan dogon hancinsa ta yi tana murmushi ba tare da ta yi magana ba. Haka suka kasance cikin so da kauna tare da nunawa juna kulawa har Cherish ta kariso ta samesu. Ta ji tsoro kuma ta sha jinin jikinta na ganin gwaggo da Dr William a tare, ita dai ta san kullum cikin faɗa suke, abokan faɗa ne, amma ya aka yi lokaci guda suka zama abokai?. Ta tambayi kanta. Ganin bata da amsa ne yasa ta kariso wajen cike da tsoro da ɗar ɗar. Ko da ta zo kallo wannan bata samu daga wajen Dr ba, tamkar bai san da ita a wajen ba, sai kallon gwaggo kawai yake yi ba tare da ya yi magana ba, dan bashi da yawan magana!. Can ya ciro sabuwar waya a kwalinta ya ajiye mata a gabanta yana faɗin ga wayarta da ya sanyata ta fasa daren jiya. Bin wayar da kallo ta yi, waya ce iya waya, ta haɗu sosai, ga tsada na wuce misali. Hannu ta kai ta ɗauka tana murmushi. Shi dai ban da wannan kallo babu wani abin da yake binta da shi. A takaice haka suka kasance har tsawon shakara ɗaya, soyayya mai zafin gaske ne a tsakaninsu, kullum cikin kara kaunar juna suke yi, a cikin shakara ɗayan nan da suka yi, daga ƴan uwan gwaggo har nasa ba wanda ya san da suna tare, babban abin dubawa a soyayyar tasu shi ne yanda suka saki jiki wa juna, wani lokaci a gidanta yake kwana, suna romancing junansu son ransu, duk da basu taɓa kwatanta saduwa ko da sunan wasa ba, amma fa suna wuce gona da iri a wajen wasannin nasu. A wannan shekara ɗayar ta je gida hutu sau ɗaya, sai dai bata wani jima ba, sati ɗaya ta yi, shi ma a daddafe ta yi shi dan tana kewar Dr, sam hankalinta baya kan mutanen gidan, bata ma lura da Dr Salman ya kara aure ba, kanta na rawa sosai a lokacin, sam bata bi ta kan amarya ba, bata sami su Abba a gidan ba, kuma bata tambayi ina suke ba, dan a tunaninta, suna makaranta, harta daddyn Rimsha lokacin baya nan, shi ma bata neme shi ba, dan ta ɗauka yana school shi ma, bata san cewa yama bar gidan bakiɗaya ba, dan lokacin su Abba sun yi mishi wannan sharrin ya bar gida, daddyn Anaya kawai ta samu a gidan, sai daddyn jelly da yake karami, kullum tana manne da waya a kunne suna hira da Dr, ko kuma tana chatting da shi a Whatsapp, ba dare ba rana aiki ɗaya. Naurat baiwar Allah, tana fama da kanta da wahalar amarya, sam bata ta kansu gwaggon, ko da gwaggon ma ta ji Dr Salman ya yi aure, ko a jikinta, ita sam bata tare da kowa sai Dr. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E3 Haka ta yi hutun sati guda a daddafe ta dawo, ko da zata dawo, sai da Naurat ta yi mata faɗa sosai tare da nasiha mai ratsa jiki, sannan ta bata makudan kuɗaɗe, shi ma Dr Salman lokacin yana cikin hayyacinsa, dan idan baku manta ba, bayan tafiyar daddyn Rimsha sun sake samun jituwa da Na'urat har aka sami cikin Alex. To shi ma ya zubawa gwaggon makudan kuɗaɗe a account nata, tare da yi mata nasiha a kan ta kula da kanta kuma ta ji tsoron Allah a duk in da take. To kawai ta amsa musu da shi, amma sam nasihar bai shiga kunnenta ba. Har ta koma bata haɗu da su Abba ba, kuma bata tambayi ina suke ba, a lokacin yes suna school basu dawo hutu ba, dan idan baku manta ba, dama hutu suka zo gida har wannan abin ya faru a tsakaninsu da daddyn Rimsha, to yanzu sun kowa makaranta. Shi ma daddyn Anaya yana ta fama da school bai bi ta kan gwaggon ba, a takaice dai kowa yana fama da kansa, hakan ce tasa har ta koma ba su haɗu ba GWAGGO Tana dawowa daga hutu suka cigaba da gashi a ɓangaren soyayarsu ita da Dr William, sam bata hana shi ya juyata yanda yake so, ya yi wasa da ita, sai dai daga cibiyarta zuwa sama kawai ta bashi dama, ta hana shi kasan sam, dan tana mutuwar tsoron Dr Salman, saboda shi ma mutun ne mai tsananin zafin rai idan aka yi mishi ba daidai ba, to dan shi take rage wasu abubuwa, take kamewa. Yanzu suna da almost shekara ɗaya da watanni a tare da Dr William, suna zuba soyayarsu, kullum tamkar ranar suka fara haɗuwa, a koda yaushe begen juna suke yi, wasa wasa har suka zama abin kwatance a cikin school ɗin nasu, kowa da su yake kwatance ta ɓangaren soyayya. Sai dai har lokacin fa Dr William dangerous boss ne, dan baya ɗaukar raini, ko kallon gwaggo mutun ya yi sai ya yi mashi hukunci, ba shi da sauki sam. Yau babu school ta gama duk abin da zata yi a gida, ta yi wanka tana shirye cikin wando short zuwa gwiwa, da ƴar ƙaramar riga zuwa kugunta mai ƙaramin hannu. Tana kwance a saman bed nata tana aikin latsa waya, chatting suke yi da Dr William, dan idan ka ganta da waya a hannu, to da shi take magana, ko daddyn Rimsha da daddyn Anaya da suke ƴan lelenta ma, yanzu ta daina nemansu a waya, a baya sai ta kirasu fin awa uku suna hira, dan duk cikin ƴan uwan nata, ta fi kaunarsu sama da komai, dama idan baku manta ba, na gaya muku twins ɗin nan, Azharuddin da Nawazuddeen mugun shiga rai gare su, duk in da suka zauna, sai an kaunace su, aji ba'a son rabuwa da su, to ita ma Gwaggo haka ne, amma yanzu tana manne da Dr William, tama manta yaushe da rabon ta da ta kira gida, ko an kirata daga gidan kuma, sai ta ce musu tana karatun exams, ko dai tana yin wani abin, bata taɓa bawa kowa lokacinta idan ba karatu da kuma Dr William ba. Sai dai abin jin daɗi a tarayyar tasu da Dr ɗaya ne, wato duk wannan soyayya da suke zubawa, sam basu wasa da karatu, suna dagewa sosai, idan Dr William ya zo first, gwaggo ce second, idan ta zo first shi ne second, ma'ana dai duk in da ɗaya ya saka kafa a karatu, to ɗayan ma yana biye da shi, kamar abin haɗin baki, amsoshinsu a Exams ma iri ɗaya ne, dan tare suke karatu, wani lokaci a gidanta yake kwana, su kwana karatu. Rashin wasa da karatunsu shi ne nasarar da suka cinma a soyayyar tasu, kuma shi ne kawai soyayyar tasu bai sa sun yi patali da shi ba. A ɓangaren Dr William ma, iyayensa har sun gaji da tambayar a kan sauyawar da ya yi, yanzu sun zuba mashi idanu ne kawai suna kallon shi, sun yi, sun yi, su bibiyi abin da yake yi, amma yaki basu dama, hakan tasa dole suka hakura suna binshi da idanu kawai. STORYN Ta tada kai da pillow a saman bed nata daga ita sai wannan short ɗin wandon nata da kuma ƴar riga, ta rungumo pillow a kirjinta tana aikin chatting da shi. Sai zubawa Dr nata shagwaɓa take yi a kan ita tana kewarsa, sai biye mata yake yi yana bata hakuri. Tamkar daga sama ta ga ya turo kofa ya shigo, dan yana da key a yanzu. Hakan na nufin duk chatting da suke yin nan ashe yana kan hanyar zuwa, kawai yaki gaya mata ne. Da gudu ta diro kasa daga saman bed ɗin ta nufe shi, buɗe mata hannu ya yi ta faɗa jikinsa tana dariya. Rungumeta sosai ya yi yana ɗan shafa bayanta. Laluɓar hannunta ya yi a in da ya sanya mata wani shegen diamond ring mai bala'in tsada, nan take hannun nata ya fara kyalli. Bai bari ta fara zuba mishi tsalle da murna ba kawai ya ɗauketa cancak sai saman bed ɗin, tamkar dama a kusa yake. Romancing na juna suka fara yi kamar yanda suka saba, sai dai a yau dai Dr William ya zo har wuya, ya kasa jurewa ya danne sha'awarsa, dan yana tsananin sha'awarta over. Hana shi ta yi a in da ta saka mashi kuka, dole ba dan ya so ba ya rabu da ita tare da barin jikinta ya koma gefe guda a saman bed ɗin ya zauna, ya haɗa kai da gwiwa yana sauke numfashi a hankali hankali. Miƙewa ta yi jiki ba kwari ta dawo kusa da shi. Hannu ta kai tare da ɗago kan nasa tana ambatar sunansa. Kasa amsa mata ya yi, saboda mawuyacin halin da yake ciki. Rungume shi ta yi a kirjinta tana bashi hakuri tare da saka mishi kuka, sam ba zata iya jurar ganin shi a cikin tashin hankali da damuwa ba, kun san zuciyar masoya! Ba abin da ba zasu iya yi wa junansu ba, in dai sun mace a wannan soyayyar tasu! To ita dai soyayyarsa ta yi mata mummunar kamu, makauniyar soyayya take yi mishi. Haka shi ma a nashi ɓangaren, makauniyar soyayya yake yi mata! Ba zai iya ganinta cikin damuwa ba, duk yanda ya kai ga son abu, in dai bata so, to ko zai mutu! Haka yake hakura, sai dai ya yi ta fama da azabar raɗaɗi a cikin zuciyarsa, amma ba shakka zai hakura. Ganin tabbas ya shiga tsakanin damuwa sosai na wuce misali ne yasa ta ce to ya zo ya biya bukatar tasa kawai, tana magana tana kuka. Da kyar ya iya ɗago kallonsa izuwa gareta, hannu ya kai ya fara goge mata hawaye, muryarsa na rawa ya fara magana. "Ni da gaske nake sonki my beauty, ba nason abin da zai ɓata maki rai, ki bari kawai na hakura kin ji ko? Yanzu dai ki gaya mani, me zan yi na sameki? Ya zan yi ki zama matata mallakina, sai nayi yanda nake so dake babu wani sha'amaki?". Cike da murna ta ce "Aure, aure ne kawai zai sanya na zama mallakinka ba wani shamaki, hakan kuma ba zai taɓa yiwu ba har sai ka zama musulmi, ba zai yiwu na aureka kana krista ba!". Cikin sauri ya ce mata "Na yarda, na yarda zan zama musulmi, ni dai kawai ki zama mallaki na!". Sosai ta rungume shi tana murna tamkar ba gobe. Ganin tana murna ne yasa shi ma ya rungumeta sosai yana manna mata kiss a lips nata. Haka suka kasance tsawon mintuna 20, sannan ya ce ta shirya bari suje gidansu sai ya gayawa mummynsa da daddynsa abin da ya yankewa kansa, a lokacin kuma TAG yana koyan tafiya. Hakika ta yi tsananin murna, zata mallaki Dr ta. Cikin hanzari ta miƙe tare da faɗawa cikin toilet. Wanka ta yi cikin hanzari, yana zaune yana jiranta, amma shi kaɗai yasan halin da yake ciki na sha'awarta. A gabansa ta shafa Lotions nata kamar ko yaushe, sannan ta wuce zuwa dressing room. Yau da yake ya ce gidan iyayensa za su je, sai ta mutunta su ta hanyar yin complete dressing mai kyau, wandon jeans ta sanya a ciki, tare da wani T-shirt da ya saya musu iri ɗaya da shi. Bayan ta gama sai ta sanya after dress baka a saman kayan, dan ta ɗan suturta jikinta, still dai kanta babu ɗankwali ta fito. Cike da tsantsar so da kauna tare da kulawa ya fara yabon irin kyan da ta yi, murmushi ta yi kafin ta taho ta faɗa jikinsa. Yana ƙoƙarin fara kissing nata, ta dakatar da shi ta hanyar sanya hannu ta rufe mishi baki. "Haba my Dr, wai kai baka gajiya da shan lips na ne?". Lumshe shanyayyun idanuwansa da suka sauya launi ya yi, cikin sanyin murya ya bata amsa da cewa "My beauty, ya za'ayi na gaji da shan lips naki? Ai ba zan taɓa gajiya ba, ni dai yanzu Please ki bani ko kaɗan ne, kin ji ko my wife?". Harara ta wurga mishi kafin ta ce "Ai ba'a ɗaura auren ba ko?". Nisawa ya yi yana mai faɗin "To ai an kusa, kin ma tuna mini, tashi muje wajensu mummy da wuri, daga nan sai mu wuce a ɗaura aure ko?". Zata yi magana ya sanya mata yatsa a saman lips nata yana faɗin ta tashi su tafi da wuri. Ba musu ta tashi suka fice daga gidan. A motar nasu ma, basu hakura ba, sai da suka ɗan yi romancing junansu kafin ta kwantar da kanta a saman kafaɗarsa, shi kuma ya kunna motar suka bar gidan. (Yanzu kun fara ganin daga in da TRIPLETS suka yi gadon nasu jarabar ko? Da uwa da uba dukka ba sauki😂 mu je dai zuwa.) Yau dai Gwaggo ta zuba kauyanci na ganin gidansu Dr, bata taɓa tunanin daga wannan aljannar duniya ya fito ba, tana tunani dai irin normal masu kuɗin, ɗan dai'dai ɗin nan, bata san mahaukatan kuɗi karesu ba. Sake baki ta yi kawai tana ta kallon gidan abinta. Sai da ya ja hannunta suka nufi ciki, lefter suka hau zuwa hawa na uku, dan ya san confirm su mummynsa suna wajen, dan sun fi yawan zama a wajen. Ita dai sai mamakin gidan take yi, dan gida ne irin high rise building ɗin nan, ga wani haɗaɗɗen lefter mai matuƙar kyau, abin ba'a cewa komai, dan ya wuce tunanin mai tunani, idan na ce zan tsaya zayyana muku gidan Jacob Roshan ba ƙaramin aiki bane, dan kuwa sai mu kare book nan kaf a kansa kawai, dan fa ya haɗa komai, babu abin more rayuwa da ɗan adam zai buƙata babu a cikin gidan. Sai yanzu gwaggo ta sake yarda cewa so gudan jini ne, yanzu idan ban da so me Dr William zai yi da ita? Irin wannan duniyar da suke ciki, ga kuɗi, kyau, isa da takama, abin ba'a magana. Tamkar yanda Dr ya faɗa na cewa iyayensa suna hawa na uku, a can ya samesu, suna zaune a palonsu tare da Uncle Herry, Josephine da TGA, sai zuba hira suke yi. Jacob Roshan yana shan green tea, ita kuma mummynsu tana faman cin wasu korayen ganyayyaki masu karawa jiki lafiya da jini, ga wani makeken Tv dake gefe guda ta gabas maso tsakiya yana magana. Tun da suka shigo palon gwaggo take bin ko'ina da kallo, ta kasa nutsuwa waje guda, gani take yi tamkar Dr William zai cutar da ita ne a irin wannan gida, ta tsorata da ganin wannan uban daular more rayuwar. Shi kuwa, riko hannunta ya yi suka nufi saman wata luntsumemiyar sofa mai matuƙar laushi da kyau, fara kal tamkar yanzu aka cirota daga kwalinta. Komai na cikin palon sai kyalli yake yi, yana ɗaukar idanu, gal gal da su, nera ta yi kuka ta kuma zauna da kyau a wajen. Ko da suka shigo palon, sam iyayen Dr basu nuna mata komai ba, sai ma karramata da suka yi, da fara'a mummynsu ta tarbeta, shi ma daddyn nasu, fuska ba yabo ba fallasa ya tarbesu, dan gwaggo dai baturiya ce ba bakar fata ba, sak Naurat take!. Josephine ta fi kowa murnar ganin gwaggo, saboda dama yayan nata yana yawan korinta a kusa da shi, a tunaninta tun da yanzu ya fara son mata, zai dai'na abin da yake yi mata. Su Uncle Herry duk sun yi tsantsar murna ba kaɗan ba. Sam Dr William bai ɓata lokacin wajen sanar da iyayensa wace ce gwaggo a wajensa ba. A nan ne tsananin farincikinsu ya kara bayyana, sun ji daɗi sosai da ɗansu ya kawo macen da zai aura, nan take mum nasu ta ce gwaggo ta dawo kusa da ita ta zauna, tamkar za su cinyeta saboda so, sai tambayarta suke yi me take so ci a kawo mata?!. Kan ka ce me an cike mata gabanta da lodin kayan cima kala kala, masu aiki sun fara zarya a cikin palon, suna kai kawo na kayan cima. Yau dai Gwaggo taga abin mamaki, abincin ma a baki suke ƙoƙarin tura mata, saboda so, kuma duk aikin mum ce, sai wani ririta take yi. Ta ɗebo abinci a cikin spoon zata kaiwa gwaggon a baki kenan, cikin hanzari Dr ya ce "Mum kada ki bata, dan ita bata cin irin abincin mu, ba komai take ci ba!". Ɗan zaro blue eyes nata mum ɗin ta yi kafin ta ce "Why?". Ko a jikinsa ya amsa mata da cewa "Be cause she is a Muslim, so ba komai take ci ba, akwai abin da ya zamana haramun a cikin addininsu su ci, haka idan muka je restaurant cin abinci ma, sai ta faɗi abin da za'a bata, bata cin irin nawa!". BABBAR MAGANA. A tsananin razane mum da dad ɗin dukka suka mike tsaye, tamkar sun ga wani abin tsoro. Nan take kuma suka canza fuska tamkar ba su ne suke dariya a yanzu ba, sun wani uban ɗaure fuska tamkar hadari, shi daddy ma har da wani zaro idanu. Cikin tsawa mum ɗin ta ce "To musulmar zaka aura ne?!". Sosai gwaggo ta yi wani mahaukacin razana!, Ta tsorata na ganin canjin da suka yi lokaci guda, tamkar ba su ba. Shi kuwa Dr, ko a jikinsa ya amsa musu da "Yeah mum, ita nake so, ita zan aura, kuma yanzu ma da muka zo, na zo ne na gaya muku zan musulta nima, be cause we're prepared to get a marriage together, so shi ne abin da ya kawo ni!". TASHIN SENSE!!! Wani uban tsawa dad ya daka musu wanda ya sanya gwaggon mikewa da sauri. Shi ma Dr William mikewa ya yi tare da yi mata alama da hannunsa a kan ta zo. Da sauri ta tafi izuwa wajensa, jikinta sai kerma yake yi. Dr kuwa ko a jikinsa ya rumgumeta yana ɗan shafa bayanta, alamar ta kwantar da hankalinta. Mum ce ta katsesu da cewa ya sake wannan yarinya ko kuma wlh yanzu ransa ya ɓaci. A zahirin gaskiya tun da yake da iyayensa basu taɓa ɗaga mashi murya a magana bama bare har a kai ga tsawa, lalaɓa shi suke yi sosai kullum. Hakan tasa ya ji wlh yana kaunar shiga musulci, dan shi duk abin da ba'a so, to fa shi yake so. (Idan baku manta ba a baya dama Dr William ɗin ya faɗa, wannan kalma ta abin da ba'a so, shi Lion yake so, a wajensa ya gaji kalma, to hakan take!.) "Mum why are you shouting like that? You already know that idan na ce zan yi abu fa, to sai na yi, so don't west your time to say something about that issue, be cause confirm sai na musulta, dan ina son A'isha, she is my life, my everything!!". BABBAR MAGANA!! YAU AKE YINTA!! "William are you out of your sense?!" Cewar mum ɗin. Dad ne ya karɓi maganar da cewa "In dai har ka ce zaka musulta, to confirm zaka bar mani gidana! Kuma sai dai ka mance da mu a matsayin iyaye, ka nemi wasu!!". A takaice ya ce "That's good daddy, i chose A'isha and Muslim religion, wai daddy ka manta abin da ba'a so shi nake so ne? To ko dan nunawa da kuka yi baku so, confirm sai na yi!!". Ya kai karshen maganar tare da juyawa tare da gwaggon a jikinsa. "William don't go anywhere, come back and say sorry to your dad!". Cewar mum, ta yi maganar tamkar zata fashe da kuka, idanuwanta duk sun cika taf da kwallah, Allah ya gani a duk cikin ƴaƴanta, ta fi son Dr William, kuma ta san halinsa sosai, tun da ya ce sai ya musulunta, to fa babu chanji sai ya yi ne, sai dai duk abin da zai faru ya faru. TIRKA SHI. A ɓangaren shi ma daddyn, kirjinsa sai dukan uku uku yake yi, dan shi ma, ya fi son Dr William sama da kowa a cikin ƴaƴansa, ba zai iya rabuwa da shi ba, ba kuma zai iya ganinsa a cikin addinin musulunci ba, dan su irin kristocin nan ne masu tsauri a kan addininsu, ba za su iya yafe ɗansu ya musulunta ba! Gara su kashe shi da su barshi ya musulta. Hakan tasa daddyn zuciya ta ɗebe shi ya yi yunkurin kashe gwaggo da wukar da mum take yanka ganyayyakin da take ci. Cikin ɓacin rai Dr William ya tare daddyn nasa, tare da kwace wukar, har ya ɗaga a zuciye zai cakawa daddyn nasu a ciki, gwaggon ta rike shi tana kuka tare da girgiza mashi kai a kan kada ya yi hakan, kada ya kashe daddynsa. Wurgi ya yi da wukar tare da rungumeta suka nufi waje. Dafe saitin zuciyarsa dad ɗin ya yi, kan su yi wani yunkuri ya zube kasa sumamme, abin ya taɓa mishi zuciya over, kuma dama dole ya taɓa shi over, ace ɗa mafi soyuwa a gareka, ka fifita shi fiye da kowa, ka shagwaɓa shi, rana tsaka wata mace ta shiga tsakaninku, har yaron ya yi yunkurin kashe ka, saboda mace, ba dan macen da yake son ɗin ta rike shi ba, da tsab zai iya kashe ka saboda zuciya ta ɗebe shi, dole wannan abin ya taɓasu over, dan zuciyar iyaye ya wuci tunanin mutun, in ma musulmi ko Kristen, duk wanda aka ce shi ya haifi mutun, to wlh ya wuce abin wasa, zai so ɗan nan ne fiye da tunanin mai tunani, koda kuwa ba zai nunawa kowa ba, ba zai taɓa yuwuwa ace iyayen da suka haifeka ba su sonka ba, sai dai idan ba zasu nuna maka son ba, amma zuciyar iyaye daban yake da kowa, suna iya sadaukar da duk abin da suka mallaka saboda ƴaƴansu, ba'a banza da Allah ya ce bayan Allah da Manzonsa sai iyaye ne kawai za'ayi wa biyayya a shiga aljanna kai tsaye ba, so iyaye sun wuci wasa koma ya ya suke!! Fatanmu dai Allah Ubangijin ya bamu ikon bin umarninsu tare da kyautata musu!!. Ko kaɗan Dr William bai juyo ba, duk da yana jin zafin rabuwarsa da iyayen nasa, amma hakan bai hana shi dagewa dan cika burkinsa ba. Ficewa ya yi daga gidan abinsa. Shi kuma dad su Uncle Herry suka yi ƙoƙari tare da taimakon ma'aikatan gidan, suka nufi hospital da shi. Ko awa ɗaya bai yi a asibiti ba rai ya yi halinsa, dama already yana da hawan jini, sara ce ta zo a kan gaɓa. Mutuwarsa ta sanya mum nasu shiga tsananin tashin hankali, wanda har sai da ya jawo mata bugawar zuciya, ita ma ba'afi awa uku da mutuwar dad ba rai ya yi halinsa, ta bi daddyn. Hakika familyn Roshan su ga tashin hankali a wannan rana, harta yayyun daddyn da suke rike da mulki, a wannan rana sun sha kuka, an yi musu hotuna da videos suna kuka da hawayensu na rashin kaninsu da matarsa tamkar wasu yara ba adadi. Sam Uncle Herry da Josephine sun ki gayawa jama'a gaskiyar abin da ya kashe Jacob da mum nasu, sun ɓoye ne saboda suna tsananin son Dr William, kuma suma sun ji suna son su musulta, sun san cewa idan har suka sanar da jama'a gaskiya, to ba shakka yayan daddy da yake kan mulki zai sanya a kashe Dr William, dan su basu yafe jininsu, ko yaya ka taɓosu sai sun rama, koda kuwa a cikinsu kake. A lokacin da za'ayi jana'izarsu su mum, za'a kaisu mutuware, wato jana'izar kiristoci, an buƙaci da Dr William ya zo ya wuce gaba a matsayinsa na babban ɗansu, amma sam baya wajen, hasalima bai san da zancen mutuwar ba, duk da cewa labarin ya baza gari, abin ku da manyan mutane, sai dai shi bai sami labari ba, dan yana babbar masallaci jumma'ar musulmai dake garin, tun da ya bar gidan suka wuce can da gwaggon, kafin ya tafi kuma sai da ya kashe wayarsa, a cewarsa kada ma su mum ɗin su kira shi, dan confirm sai ya musulunta. TASHIN SENSE. Kasancewar ba'a sami Dr William ko a waya ba, haka aka ce Uncle Herry ya wuce gaba, Josephine ta bi bayansa, dan da aka tambayesu ina Dr William, sai suka cewa jama'a ai Dr William baya nan, sun dai ki faɗar gaskiya. Haka aka kai gawarwakinsu mum ɗin mutuware, sai kuka su Josephine ɗin suke yi tamkar ransu zai fita. A ɓangaren Dr William kuwa, suna fita Masallaci ya wuce da gwaggon, a in da ya je ya gayawa liman ga abin da yake tafe da su, ya gaya mashi aure suke son yi, kuma iyayensu basu son aure, saboda iyayensa sun ce a'a, kuma sun hana shi musulta. Duba da yanayin kasar tasu, ba musu limamin ya bashi kalmar shahada tare da tambayar gwaggo shin da gaske tana son Dr William, sosai ta tabbatar musu da hakan, ba ɓata lokacin limamin ya ɗaura musu aure bayan an fito sallar azzahar, a cewarsa, ai sun fi shekaru goma sha takwas, dan haka suna da ƴanci da kansu, suna da ƴanci su yi abin da suka ga dama, shi ne yasa aka ɗaura musu aure bayan musultar Dr. Ita kuma gwaggon a lokacin idanunta sun rufe, tana ganin kamar iyayen Dr William za su zo su rabata da shi, ba zata iya rayuwa babu shi ba, shi ne kawai yasa duk abin da liman ya ce mata, sai ta ce mishi e, dan a lokacin bata da burin da ya wuce Dr William ya musulunta, a ɗaura musu aure, su mallaki juna, shi ne yasa ta yarda, bata bi ta kan iyayenta ba, dan tana ganin suma zasu tsaya ɓata mata lokaci ne har a rabata da Dr. Bayan an ɗaura musu aure, kai tsaye gidan Gwaggon suka wuce abinsu, yau sun zama sabbin mutane. Ko da suka je gidan, komai na kayan kallo a kashe, basu sami labarin abin da yake wakana a gari ba. Rungume juna suka yi suna tsananin murna da farinciki, yau sun mallaki juna na har abada. Kissing nata ya fara yi, cike da so da kauna ta fara mayar mishi da martani. Sun ɗan yi nisa cikin abin da suke yi, tamkar wanda aka muskula ta miƙe tana faɗin "My Dr bari na kira mum ɗina na gaya mata yanda aka yi komai, dan kada asamu matsala ka ji?". Idanuwansa a runtse ya jawota jikinsa yana faɗin "A'a kada ki gaya musu yanzu, kada suma su rabani da ke, ki bari sai mun sami hutu a school, sai mu je gidan a tare ko?". Jinjina mashi kai ta yi cike da gamsuwa da kuma yarda da shi ɗari bisa ɗari, dan ta faɗa makauniyar soyayya, baiwar Allah, ba laifinta bane, laifin so ne, da bashi da adalci idan ya shiga mutun. "My Dr ka bari, bari na je nayi wanka nazo ko?". A kunne ya raɗa mata yau kam a tare za su yi. Bata yi mashi musu ba, dan sun mallaki juna, kafin su mallaki juna ma, dama wani lokaci ko tana toilet yana shiga ya yi abin da zai yi, bare kuma yanzu, ai sai abin da hali ya yi. A tare suka wuce cikin toilet ɗin. After some minutes suka fito rungume da juna, tamkar wani ya ce zai kwace musu junansu. Yau dai a tare suka yi komai, kama daga shafa lotions, shiryawa cikin kananan kaya, da yake da akwai kayansa sosai a gidan, dan idan baku manta ba, wani lokaci a gidan nata yake kwana a baya, hakan tasa ya sayi wasu kaya ya zuba a dressing room nata. Komai suke yi suna yi ne suna wasan masoya cike da so da kauna. Da zata shiga kitchen ma, a tare suka shiga da shi. Duk da cewa bai iya aikin komai na kitchen ba, amma ya tayata da hira na kalaman soyayya masu daɗi, tare kuma da tana aiki yana rungumeta, ko ya shafi mazaunanta. Kayan kwalama ta haɗa musu tare da green tea mai zafi sosai. A palo suka baje abinsu, a lokacin kuma har an kaisu Jacob mutuware an dawo, duk basu da labari. Sai da suka fara shan tea ne ta ɗauko wayarta tare da kunna data dan ta yi wa Cherish massage a Whatsapp na yau sun yi aure da Dr, sun mallaki juna, ta zo ta tayata murna. Tana kunna data sakon Cherish ɗin ya shigo wayar nata na tayata alhinin rasa iyayen saurayin nata Dr William wanda yake a matsayin mijinta a yanzu kenan. Wani irin ihu ta kurma wanda bata san time ɗin da ya fito daga bakinta ba, jikinta na kakkarwa ta yasar da wayar kasa. Cikin tashin hankali ya riko kafaɗunta yana tambayarta lafiya? Ihun me take yi. Kasa magana ta yi, nan take hawaye suka cika mata idanuwa, domin tasan Cherish ba zata taɓa yi mata karya ba, tun da ta yi mata wannan massage ɗin, to gaskiya ne, iyayen Dr William sun mutu. TASHIN SENSE!!!. Ganin taki amsa mishi tambayar da yake yi mata ne, yasa ya ɗauki wayar tata dan ya duba me ta gani take wannan ihu. Dubawa da zai yi bai san time da ya saketa ya wani irin mikewa a razane ba. Ita ma mikewa ta yi tana hawaye jikinta duk sai ɓari yake yi, abin mamaki yanzu bai fi awa biyar da suka rabu da su ba, amma ace sun mutu dukkansu biyu? Wannan dole bawa ya shiga tsananin tashin hankali. A hanzarce Dr ya wuce ya ɗauko wayarsa, cikin tashin hankali, idanuwansa suna gani bibbiyu, ya fara ƙoƙarin kunna wayar. Ya kasa saboda kerma da jikinsa yake yi, wayar ta kasa tsayuwa waje guda a hannun nasa. Daga karshe ita ta karɓa ta kunna mashi. Number uncle Herry ya fara kira, bugu ɗaya ya ɗauka. Cikin tsananin tashin hankali da razana ya fara magana yana haɗe word, a in da ya tambayi uncle Herryn ɗin ina dad da mum. Ba ɓoye ɓoye ya gaya mashi sun mutu. Ya ilahi ya lillahi, bai san time ɗin da ya saki wayar tasa ta faɗi kasa ba. Kasa tsayuwa waje guda ya yi a in da ya zube gwiwowinsa a kasa a wajen, yana wani irin numfashi mai kama da gurnanin zaki. Tsugunnawa ta yi a kusa da shi tare da ɗan rungumo shi a jikinta, sai ruwan hawaye take yi. Muryarsa tamkar mara lafiyar da ya yi shekara cikin mawuyacin hali ya ce mata. "My.....my beauty.... Don't tell me that what i heard now about my dad and mum is true, say it's not a true to me". Rarrashinsa ta fara yi tare da kara mashi karfin gwiwa. Ina ai kasa hakura ya yi, zuciyarsa ba zata iya ɗauka ba, idanuwansa sun yi jajir da su. Ta yi ta yi a kan ya tashi su je gidan, amma ina ya kasa koda motsawa, dan yana bala'in kaunar iyayen nasa fiye da tunanin mai tunani, sune duniyarsa, duk abin da yake yi musun nan yana tsananin sonsu, ace lokacin guda ya rasasu? Kai abu ne wanda zuciyarsa ba zata iya ɗauka lokaci guda ba, dan ma dai yana da taurin zuciyar ce, ai da abin ya wuce hakan. Sai da ya ɗauki almost 1 hour a durkushe a wajen, sannan ne ya iya ɗan motsawa. Da kyar ya mike. Da dafa bango ya fito palo. Da sauri ta ɗauki bakullin mota ta biyo bayansa. A takaice ita ta ja motar suka nufi gidan. Har lokacin jama'a na cike taf a gidan. Bai kula kowa ba ya wuce ciki, yana tafiya tamkar zai faɗi kasa, ya rike hannun gwaggo gam dan kada jama'a su rabasu, ta je ta ɓace mashi kuma. Kai tsaye hawa na biyu suka wuce, a nan suka sami su uncle Herry da su yayyun dad ɗin nasu, sun sha kuka tamkar ba gobe, shi kuwa Dr William ya daure, idanuwansa sun yi jajir kamar wuta, amma sam bai yi kwallah ba. Sai bayan sati biyu da mutuwar iyayen nasu ne ya fara gane kansa, nan ma da taimakon gwaggo da take kwantar mashi da hankali, ba karya ya shiga tsananin damuwa da tashin hankali na wuce misali, har wata iriyar mummunar rama ya yi, tamkar ba shi ba, iyaye ba wasa ba! Kuma dukkansu a lokacin guda, a hakan ma su Uncle Herry basu gaya mashi cewa sanadiyarsa ne yasa hawan jinin dad ɗin nasu ya tashi har ya mutu ba, sun ɓoye mashi, wata kila da sun gaya mashi shi ne sula, tashin hankali ne shi ma zai kashe shi. Haka suka kasance a daddafe har tsawon wata da rasuwar iyayen nasu, sannan ne ya ce shi ba zai iya zama a wannan gidan ba, dan idan har ya zauna, kullum zai rinƙa kwana ne cikin kunci da bakinci tare da ganin tamkar iyayensu suna tare da su a gidan kamar baya, dan haka shi zai koma ɗaya daga cikin gidajen daddyn nasu ya zauna tare da gwaggon, za su ɗauki Tga su rike tun da a lokacin shekararsa biyu da ƴan watanni. Uncle Herry da Josephine suka ce suma za su bishi, ba za su iya zama ba. Tambayar gwaggo ya yi a kan zata iya zama da familynsa, cike da murna ta ce mashi e, dan haka sai suka tattara duk wani abin da za su buƙata, suka rufe gidan tare da sallamar gabaɗaya ma'aikatan, sannan suka tafi zuwa wani gidan bene mai hawa ɗaya, shi ma ɗaya ne daga cikin gidajen daddyn nasu, ba karya ya kawatu iya kawatawa gidan. A nan suka fara sabuwar rayuwa, gwaggo da Josephine sun zama very close friend, dan a lokacin shekarunsu kusan ɗaya. Cherish tana zuwa suna rayuwar farinciki. Da Josephine da Uncle Herry duk sun karɓi musulci, gwaggo ta musultar da su, daga baya ita ma Cherish ta musulta. Rayuwa mai tsabta da farinciki suke gudanarwa a gidan. Har tsawon wata ɗaya da dawowarsu gidan sam Dr William bai kusanci gwaggo ba, dan har lokacin bai warke daga raɗaɗin rashin iyayensa ba. Ita ma Gwaggo bata wani damuwa na rashin soyayya da basu yi, dan ta san halin da yake a ciki. A tare suke yin aiki da Josephine, komai tare tamkar twins, Uncle Herry kuma kullum yana tare da TGA yana koya mishi wasu abubuwa na rayuwa. Idan suka tashi tafiya school, akwai wata mai aikin TGA ɗin da take kula da shi, dukkansu suna tafiya su bar shi. Sosai Dr da gwaggon suka mayar da hankali a kan karatu, dama already kun san basu wasa da karatu.......... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E4 *Ina yi wa ɗaukacin al'ummar musulmi ta duniya barka da sallah, Allah Ubangiji ya maimaita ma, ya karɓi ibadunmu ya sa kuma muna daga cikin ƴantattun bayi, wannan page sadaukarwa ce, barka da sallah ce ga ƴan comments section group na, ina farincikin kasancewa a tare da ku, kuma dukkanku ina ganin comments na kowa, tare da adduo'inku da yaba mani da kuke yi, tare da kwarin gwiwan da kuke kara mani, ba abin da zan ce maku face Allah ya bar zumunci, hakika kuna sakani farinciki da comments naku, hakika kuna cikin tunanina a koda yaushe ❤️* Sosai Dr da gwaggon suka mayar da hankali a kan karatu, dama already kun san basu wasa da karatu. A takaice sai da suka ɗauki almost wata biyar da aurensu kafin Dr William ya dawo dai'dai na rashin iyayen nasu da suka yi, a lokacin ma ya dawo dai'dai ne sakamakon adduo'i da kuma karatun Alkur'ani mai girma da gwaggon take yawan yi mashi. Shi ma yana koyan hadda sosai a wajen limamin da ya bashi kalmar shahada, haka su Josephine ma suna karatun addini sosai. A lokacin Josephine sunanta A'isha, dan ta ce sunan gwaggo take so a saka mata, shi kuma Uncle Herry sunansa Muhammad, TGA kuma Sudais. Suna rayuwa cikin tsantsar farinciki. Har lokacin gwaggo bata san da abin da yake faruwa a gida Nigeria ba, ita dai soyayya ya rufe mata idanu, sabgar gabanta kawai take yi. Bayan Dr William nata, bata tunanin kowa, shi ne a ranta dare da rana. A haka almost shekara guda kenan da aurensu. Yau ta kama Sunday, babu school, duk suna haɗe a gida suna hira. Cherish ma ta zo gidan nasu. Da Josephine wato A'isha da gwaggo suna kitchen suna haɗa kayan makulashe, karfi da ya ji gwaggo ta koyawa Josephine shiga kitchen, ita ma Gwaggon ba wani abin da ta iya yi face dafa tea sai ɗan snacks da ba'a rasa ba haka. Idan ta shiga kitchen hada even tea, sai ta fi 40 mins ana abu guda, amma a haka take zagewa ta shiga dan ta yi wa Dr tea da kanta, bata son ƴan aiki su yi mashi tea ɗin. After some minutes. Zaune take a saman bed nata a cikin bedroom nata tana duba wasu takardunsu, dan sun kusa fara exams, daga ita sai wando zuwa iya santala santalan cinyoyinta, da kuma ƴar riga da bata gama rufe cibiya ba, ta saki gashi har baya, tana aikin taunar chewing gum. Josephine da Uncle Herry sun ta fi yawon shakatawa, dan yau week, Cherish na palon kasa, ita da TGA, tana aikin bashi hot milk, tana bala'in kaunar TGA kamar me, sai dai shi kuma, tun yana yaro, yana da bakar zuciya na wuce misali, ga saurin fushi da taurin kai, tun yana karami idan ya ce ba zai yi abu ba, to kamar Lion yake, ba zai yi ɗin ba, sai dai a kashe shi, abin dai ba'a cewa komai. Amma da yake Cherish ta san halinsa, sai ta koyi zama da shi, tana yi mashi abin da yake so, har tasa ya saba da ita sama da yanda ya saba da su Josephine, har ɗaukarsa take yi su je gidanta su wuni, ya zama kamar ɗanta, tun Dr yana hanawa, har ya saduda, ya kyalesu kawai. Dr William, sanye yake da short irin masu kama jikin nan, kwata kwata wandon a iya rabin cikyarsa ta tsaya mashi, babu riga a jikinsa. Daga cikin ɗakin maratunsu ya fito, hannunsa na rike da wayarsa, sai aikin sauke ajiyar zuciya yake yi. Cike da so da kauna ta kalle shi tare da sakar mashi cool murmushi kafin ta ce "My Hero ya ka ji karatun?". Gera ɗaya ya ɗaga mata yana faɗin "Normal beauty, what about you?". Rufe takardun dake a gabanta ta fara yi tana bashi amsa da komai normal. "Akwai wani abin da zan kara maki ne?". Ya tambaya yana tsareta da waɗan nan shegun blue eyes ɗin nasa masu rikitar da mai kallonsu. Girgiza mashi kai ta yi kafin ta ce "Nothing gaskiya, saboda komai dai'dai nake ji, ko yanzu a fara exams kawai". "Are you sure?". Ya faɗa yana mai canza kallon da yake yi mata izuwa wani irin kallo na azababben so da kauna. Jin yanda ya yi tambayar yasa ta ɗago da dara daran idanunta izuwa kansa. Ɗan zuba mashi idanu ta yi na ƴan sakanni kafin ta ce "Are okey kuwa?". Nisawa ya yi tare da ɗan kashe mata ido ɗaya yana faɗin "Am not sure, but you have to be check me very well, so that you should now am okey or not". Ya yi maganar cikin wata iriyar murya da take nuna tsantsar so da kauna. Ƴar murmushi ta yi kafin ta ce "Okey come and sleep, let me see what to do". A hankali ya nufota, yana tafiya yana wani yarfar da hannu kamar wani ɗan baby. "My Dr, yau fa like you're feeling shagwaɓa more for me ko?". Ɗan turo mata ɗan bakin nan nasa ya yi kafin ya sake ciza ɗan red lips nasa, sannan ya ce "Ba dole ba, gabaɗaya you forget about me, kawai kina ta kula da su A'isha, ni babu mai kula da ni". Ya kai karshen maganar tare da kwanciya a saman bed ɗin ya kuma tada kai da cinyarta yana turo baki. Hararar soyayya ta wurga mashi kafin ta ce "E lallai yau rigimace ma kake ji da ita ba shagwaɓa ba, amma na san maganinka". Hannu ya kai ya ɗan shafo breast nata yana faɗin "Ga abin da zaki bani na sha sai na dai'na rigimar". A takaice ta ce "Da a baya da kake sha ni nake baka ne?". Gera ɗaya ya ɗaga tare da ɗan zaro idanu kafin daga bisani kuma ya miƙe zaune a in da ya rungumota suka kwanta tare yana faɗin to bari ya sha kayansa. Murmushi kawai take binsa da shi. Da ya fara wasa da su kuma, sai ta fara taya shi kamar yanda suke yi a baya. Nan take ta fara gigita shi da salonta. Romancing na juna suka fara yi babu kama hannun yaro, an jima ba'a haɗu ba, ya kware wajen iya wasa, duk ƙoƙarin gwaggo sai ta sakar mashi ragamar idan suka fara, bata ma wani iya jurewa su yi nisa zata sakar mashi, ta dai'na biye mashi, sai dai ta yi ta zuba mashi kukan shagwaɓa, hakan kuma kara rikita shi yake yi, yasa ya yi ta kara birkita mata ƙwaƙwalwa har ta yi kukan gaske. A takaice dai Dr bai rabu da ita ba yau sai da ya kawar da budurcinta. Ta sha bakar wahala a hannunsa, har da suma ta yi, duk ta yakushe mashi fuska, saboda ta tara faratun hannu, kun san dama turawa suna tarasu sosai, to ita ma ta tarasu zara zara, hakan tasa duk ta ji mashi ciwo a fuska da bayansa kamar ya yi faɗa da damusa. Sai dai shi kuwa sam sam bai ji tana yi ba, har sai da ya kammala abin da yake yi ne, da ya sami nutsuwa, a nan ne ya ga ɓarnar da ya yi. Ya tsorata ainun, sunanta ya rinƙa kira, amma sam bata ko motsa ba, duba da sun yi karatu mai zurfi, duk abubuwa irin haka sun karanta, hakan tasa ya sauko daga saman bed ɗin ya nufi toilet. Ruwa mai zafi ya haɗa mata kafin ya dawo cikin bedroom ɗin, ya ɗauketa zuwa toilet ɗin. Shi ya yi mata komai da kansa, sai zuba mashi kuka take yi tamkar wanda aka cewa ubanta ya mutu. Banda aikin rarrashi babu wani abin da yake yi. Duk jikinsa ta yi muguwar sanyi, dan ba karya ta wahala iya wahala, shi ma ya wahala sosai. Sai da ya samu good 3 hours yana aikin rarrashinta da lallaɓata kafin ya samu barci ya ɗauketa. Ganin ta yi barci ne yasa ya fita zuwa word room na gidan. Alluran barci ya haɗa mata tare da dawowa cikin bedroom ɗin. Alluran ya yi mata kafin nan ya ɗebo kayan aiki, da kansa ya gyara ɓarnar da ya yi tare da duk abin da ya kamata. Bayan ya kammala ya tattare komai ya mayar, sannan ya je ya yi wanka, ya shirya cikin pajama ya dawo kusa da ita ya kwanta tare da jawota jikinsa ya rungume gam yana mai jin tsantsar farinciki tare da godiya ga Allah da ya sanya shi ne ya karɓi budurcin matarsa, dama idan baku manta ba, su da wuya ka sami mace virgin a wajensu, hakan tasa ya ji tsantsar farinciki na wuce misali, ji yake yi tamkar ya mayar da ita cikin cikinsa saboda so da kauna. Haka suka kasance shi ma barci ya daukesa rungume da ita. Ba su suka farka ba sai da Josephine suka dawo can rana ya yi sanyi wuraren laasar. Josephine ɗin ce ta tashesu dan taga basu yi sallar la'asar ba ga rana na dab da faɗuwa, ita kuwa sallar la'asar ba abar wasa ba ce, Allah ya yi rantsuwa da sallar, duk halin da zaka shiga, kada ka taɓa barinta sai rana ta faɗi kayi ta. Wasu hadisai sun ce idan rana ta faɗi ma ko kayita ba'a karɓa, wasu kuma sun ce sai dai ka hakura gobe ka rama, annabi ya ce munafukai ne kawai suke bari sallar la'asar ta wucesu, dan sallah ce mai matukar muhimmanci, kada ku manta har rantsuwa da ita Allah ya yi, kunga kuwa ba abin wasa ba ce ita ɗin. Allah ka bamu ikon yinta a kan lokaci!!. Da kuka gwaggo ta tashi mashi, sabon rarrashi ya sake farawa. Sam taki kula shi, sai tambayar lafiya take kuka Josephine take yi, amma bata samu amsa ba, dan shi ma Dr yana ta faman rarrashinta ba ta kan Josephine ɗin yake yi ba. Da kyar da suɗin goshi ya samu ta yi mashi shiru. Umarni ya yi wa Josephine ɗin a kan ta fita musu a ɗaki. Ba musu ta fita, dan ta san halin yayan nata sarai, yanzu zai iya saɓa mata kamanni. Sai lallaɓa beautyn tasa yake yi, amma taki kula shi, da alama fushi take yi da shi. Da kyar ya lallaɓata ta yarda ya ɗauketa zuwa toilet dan su yi wanka. Bayan sun fito, da kansa ya saka mata kaya, sai kumbure kumburen kumatu take yi, yau babu zancen my Dr, my Dr ya yi aika aika, haushinsa ma take ji.........NI KUMA PRINCESS TEEMA MALTINA MAI SANYI NAKE SHA, YO ME YAFI RA'INA?🤔 SOYAYYA AI DA DAƊI KO? SU GWAGGO YAU DAI AN GA RIBAR SOYAYYA😂 Bayan sun yi sallah ne ya kawo mata lunch ɗaki da kansa, ƙin ci ta yi, da kyar ya lallaɓata ta sha tea kawai. Bayan ta sha komawa saman bed ta ce zata yi. Cikin hanzari ya dauketa zuwa saman bed ɗin. Haka suka kasance har tsawon kwana uku yana lallaɓata tare da jinyar kayarsa, ita kuwa sai wahalar da bawan Allah take yi. A takaice dai wannan abin da ya shiga tsakanin, ba karamar son junansu ya kara musu ba, irin soyayyarnan da ake cewa a mutu a kan juna suke yi wa junansu, abin ba'a magana. Haka suka cigaba da rayuwa tsawon shakara ɗaya da rabi. A lokacin saura shekara ɗaya da rabi su kammala school, dan ma sun ɗaura master nasu ne, ai da ba'a haka ba, da sun jima da barin school ɗin. Ga shi karatu suke yi babu wasa, ga ilimi, dukkansu akwai kaifin ƙwaƙwalwa na wuce misali, tamkar su suka bawa kansu. (Ai dole TRIPLETS su kasance suna da basira, ba'a kasa suka tsinta ba, gado suka yi daga wajen iyaye!!) Yanzu gwaggo kwata kwata ta dai'na samun labarin gida Nigeria, amma ko a jikinta, da alama ta mance da su ma bakiɗaya, abubuwa kuma sun faru da dama a gidan Dr Salman!. Haka ta yi wa Dr William zanen tattoo mai shegen kyau a bayansa, shi ma ya zana mata a nata bayan, amma ta kasa kusa da mazaunanta, ya rubuta mata sunansa a wajen, ita ma ta rubuta mashi sunata a nasa bayan. Abin gwanin birgewa na wuce misali. Babu wata matsala a tsakaninsu ko da sunan wasa. Suna rayuwar tsantsar farinciki tare da faranta ran juna. Rana tsaka ciki ya bayyana a jikin gwaggo. Nan fa bala'i ya tashi ya tsaya, nan fa Dr ya ce shi baya son ciki, baya son haihuwa, sai dai su zubar, sam shi bai shirya haihuwa yanzu ba, ita kuwa gwaggo ta ce mai rabata da cikin nan sai Allah Ubangijin da ya bata, shi kaɗai ne zai iya kwatar kayansa. Ba yanda Dr bai yi ba, ta kafe sam wlh ba zata cire cikin ba, ai ba shegu bane, da ubansu, ƴaƴan sunna ne! Dan haka dole ta haifesu kamar yanda aka haifeta ita ma!!. Shi kuma ya kafe ko da sonta ko babu sonta, ko da saninta, ko babu saninta, sai ya salwantar da cikin. Da ta fahimci hakan ne, sai ta dai'na bari suna kusantar juna, kwata kwata ta dai'na kula shi. Amma fa abin ya yi mugun ɗaure mata kai na cewa da Dr ya yi baya son haihuwa, ta san dai a baya yana yawan maganar yara, to how comes kuma sun sami cikin ya ce shi baya son yara? Ko dai dama a bayan ma yaran uncle's nasu kawai yake so ne? Abin ya sakata cikin tunani, wai baya son yara kwata kwata a rayuwarsa. Babbar magana!!. (Ashe ba a kasa Lion ya tsinci tsanar yara ba! Kunga kuwa yanzu da Lion ya ce baya son yara ai bashi da laifi ko? Dan ɗan gado ne shi ɗin, ya gada komai tsab, har ma ya ninka mahaifin nasa zafi da tsauri. Lallai akwai cakwakiya, Lion baya son yara, ga shi ya kamu da son Rimsha, ko ya za su kare?🤔 Ni dai PRINCESS TEEMA ina da Maltina mai sanyi a fridge, idan suna bala'in da na ji ba zan iya jurewa ba, sai na kora maltina ta ta kwantar mani da hankali) Wasa wasa faɗa ya yawaita a tsakaninsu har Dr ya fara ƙoƙarin illatata. Ganin zai iya illatata ita da abin da yake cikin cikin nata ne yasa ta fara ƙoƙarin barin gidan. A nan ne Josephine ta tambayeta me yake faruwa? Bata ɓoye mata komai ba, ta gaya mata, sosai Josephine ta sha kuka, dan ita tana matukar son gwaggo ta haifa musu yara, kullum tana addu'ar Allah ya bawa gwaggon ciki ta haifa musu twins, sai dai ita dama already tasan Dr William baya son yara, sam baya son hayaniya, ta san ba zai taɓa karɓar wannan ciki na gwaggon ba, dan kullum yana yawan faɗawa mum ɗinsu kafin ta mutu, yana gaya mata cewa shi da ya haifi yara, gwara ya mutu bai kula mata ba!!..... Yau ake yin ta kenan, tashin sense. Haka Josephine ta yi ta bawa gwaggon hakuri a kan kada ta je ko'ina, In Sha Allah Dr zai sauko ya so cikin, amma ina wani muguwar tsana ma ya kara yi wa cikin na wuce misali. Tsanar cikin ne ma har ya shafi ita ma gwaggon, ya tsaneta sosai. Daga karshe ma sai ya yi yunkurin kasheta ita da abin da yake cikin nata. A ranar Josephine ce ta tseratar da ita daga hannunsa, a in da ta gudu da ita izuwa ɗaya daga cikin gidajen daddynsu, wato Jacob Roshan, suka bar Dr William uncle Herry sai TGA, ita dama Cherish bata san me yake faruwa ba. A nan suka cigaba da rayuwa da gwaggon da ita Josephine ɗin, dan ta ce wlh ba zata koma wajen Dr ba ita ma, zata zauna ta kula da gwaggon, baiwar Allah tana da tausayi sosai ga kirki na wuce misali. A lokacin Cherish tana kasarsu ta je hutu. Ita kuwa gwaggo bata je hutu ba, kuma ba'a nemeta a gida ba, dan a lokacin gidan nasu ya rushe bata sani ba, tana nan ta biyewa Dr ya kaita ya barota, da ba dan Josephine ba, da bata san in da zata sanya rayuwarta ba, da kila izuwa yanzu ma ta mutu. Allah sarki rayuwa kenan. Hakika Gwaggo ta sha bakar azabar wahala na rabuwarta da Dr, tamkar ba zata yi rai ba, dan tana tsananin kaunarsa fiye da tunanin mai tunani. Shi kuwa yana can ko a jikinsa, sai ma sharholiyarsa da yake sha, da alama ya mance da ita ma, da alama fa dama ba sonta tsakani da Allah yake yi ba! Kawai ya yaudareta ne!. (Wata kila shiyasa su Lion basu jinsa sam sam a ransu🤔 to lokaci dai zai nuna mana komai, amma ni da ku duk mun san cewa alhaki kwaikwayo ne! Ga mutuwar su Jacob ma dai..hmmmm akwai abubuwa da yawan gaske, wlh wasu cakwakiyar idan aka ɓallo maku sai kun ji kanku ta buga!!) PRINCESS TEEMA..✍️❤️ Da kyar tare da addu'a da taimakon Josephine gwaggo ta dawo dai'dai, da farko da ta ji wahala na soyayyar Dr dake neman hallakata, sai ta ce wa Josephine ta yarda zata zubar da cikin kawai ta koma wajen mijinta, dan ba zata iya yin nisa da shi ba. Kasancewar Josephine tana bala'in son yaran yasa ta yi ta rarrashinta tare da yi mata dabara har ta yarda ta bar ciki. After some weeks A haka Cherish ta dawo hutu ta same su, abin kwata kwata bai yi mata daɗi ba, duk sai ta ji ta tsani Dr sosai, ta kuma tsani maza fiye da tunanin mai tunani. Zaune ta isko Gwaggon a cikin bedroom saman bed, kusa da ita ta zauna tare da fara bata hakuri. A kule gwaggon ta ce. "Cherish kin san me kike faɗa kuwa? Hakuri fa kika ce nayi? Wlh ba zan hakura ba, sai na ɗauki fansan abin da Dr ya yi mini, wlh sai na kashe shi!". Zaro kananan idanunta na ƴan China Cherish ɗin ta yi tare da dafe kirji, a ruɗe ta ce "A'isha kisa fa kika ce? Please ki dai'na batun kisa, kin san Allah ya hana hakan". "Cherish idan kika ga ban kashe William ba! To wlh ba Dr Salman ba ne ubana, William ya cuceni! Ya zalunce ni! Yanzu ki gaya mini me zan cewa ƴan uwana da iyayena? Wlh billahi ba zan zubar da wannan cikin ba, sai na haife shi! Kuma ba zan bar Washington DC ba har sai na kashe William! Wai da kike wannan magana ma Cherish kin san waye babana kuwa? Ba makawa kashe ni zai yi idan ya ji abin da ya faru da ni, dan haka kada ma ki sake kawo mini maganar na yi hakuri a nan wajen!!"................SU GWAGGO AN JI WUYA, AN TUNA DA DR SALMAN,😂 WAI SAI YANZU TAKE TUNANIN ME ZATA JE TA GAYWA DR SALMAN?🤔 SOYAYYA RUWAN ZUMA! Shiru baiwar Allah Cherish ta yi bata sake yin magana ba har Josephine ta dawo ta samesu zaune a wajen, zama ta yi suka cigaba da jira. Ita dai Cherish haka ta wuni sukuku da ita har izuwa dare, sannan ta wuce gidanta. A takaice dai haka suka cigaba da rayuwa, gwaggo tana zuwa school, sai dai bata bari su haɗu da Dr, har cikinta ya girma ya isa haihuwa, Dr bai sake nemanta ba, bai sake leƙota ba, da alama ya mance da ita, baiwar Allah, ita kuma tana ta faman dakon soyayyarsa, a kullum tana tunaninsa fiye da yanda take tunanin komai na rayuwarta. A haka har Allah ya sauketa lafiya, tashin farko ta haifo ƴan ukunta tsala tsala da su, lafiyayyun yara masu jini a jika, kyawawan gaske, jinin Roshan. Ba abin da ya fi sakata cikin tashin hankali sama da yanda ɗanta na farkon ya yi mugun kama da Dr William, harta blue eyes nasu. Biyu daga cikin yaran nata sun kasance farare ne over, ma'ana sun fi ɗayan haske, haka zalika su biyun da suka fi hasken, sun kasance kwayar idanunsu iriɗaya ne, sak irin na Dr, shi kuma ɗayan haskensa kamar na Dr ne, sannan yana kama da Josephine sak babu maraba, kai kace ɗanta ne ma, saboda tsantsar kama. Bayan ta dawo cikin hayyacinta ne ta zubawa ƴaƴan idanu, tana kallonsu, basu da maraba da familyn Dr, dukka babu wanda ya ɗaukota a cikinsu, duk su Josephine ne, jajir da su tamkar tsada, ga bala'in kyau tamkar su suka faɗi irin halittar da suke so ayi musu, abin ba'a cewa komai. A lokacin ne kuma wani bakin shaiɗani ya shiga cikin tunanin gwaggon, nan ta fara tunanin to akan me zata rike yaran Dr? Ai kawai ta kai mashi kayansa, kada ta shayar da su, dan babansu ya cutar da ita, ya ci amanarta, ya ci amanar yarda da soyayya, tun da Allah yasa sun kammala karatu last month, kawai ta bashi yaransa, ita kuma ta koma Naija, idan har ta rike yaranma ai ya cuceta da yawa............. KUSKURE KU HUKUNTA WASU DA LAIFIN DA WASU SUKA YI MAKU,❌ DR SHI YA YI MAKI LAIFI BA TRIPLETS NAKI BA! KUSKURE KI CE BA ZAKI RUKE SU BA, DAN DR YA YI MAKI BA DAI'DAI BA!! Wannan banzar tunanin ne yasa ta ɗaukesu tare da haɗa wasu kaya nata da kuma wani farar takarda da ta yi rubutu a kansa da yaren su na tatar, wato yaren Na'urat, ta haɗa da chains ɗin da Na'urat ta bata, dama chain ɗin guda shidda ne, ta bawa Josephine ɗaya, Cherish ɗaya, saura huɗu, sai ta zuba uku a cikin wani ɗan ƙaramin, bayan ta raba tambarin heart na ɗayar sarkar kenan. Sannan ta ɗebesu, sai hanata Josephine take yi tana bata hakuri, amma ina ta zuciya, shaiɗan ta buga mata ganga, kuma ta taka rawa, tukukin bakin ciki na abin da Dr ya yi mata ya dawo mata sabo, ji take yi tamkar ta kashe Dr kawai ma ta huta. Haka ta ɗaukesu zuwa gidan Dr. Da sauri Josephine ta bi bayanta, dan kada su je su yi ɓatatciya da Dr, saboda ta san halinsa. Ta kuwa yi sa'a yana gida zaune a palo, ya yi wani fresh da shi, ya yi ɓul ɓul abinsa. Babu ko sallama ta shiga palon. A saman sofa ta ɗaura yara jariran da ko kwana uku a duniya basu yi ba, nono ma sau ɗaya ta gwada basu, da ta ji zafi ta ce ba zata iya ba, ta koma basu madara, daga karshe ta kwasosu zuwa wajensa. Murje idanu Dr ya yi ya ce bai san da wannan zance ba, shi ba zai karɓi yaran ba, dan yaranta ne ba nasa ba, ta kwashesu ta fita ko kuma ya yi mata illa, ya sanyata ta yi dana sanin zuwanta duniya. Kin kwashesu ta yi, ita ma sai ta hau dokin zuciya, a in da ta shiga gaya mashi bakaken maganganu over. Abin dai sam ya zamar musu babu daɗi. Daga karshe Dr ya ɗauko sandar buka horking nasu Uncle Herry, ya ce ko ta ɗauki yaran su fita, ko ya kasheta ita da yaran. Ta dauka wasa yake yi, sai ta ce wlh ba zata ɗauke su ba, ya yi abin da zai yi!!. Babu wani tunani, babu tsoron Allah ya ɗaga sandar zai buga mata. A guje ta miƙe daga samar sofar ta nufi waje, shi kuwa yana sauke sandar sai tsakiyar kan ɗaya daga cikin jariran nan nasa. Nan take yaro ya sandare musu, ko motsawa bai yi ba, tamkar rai ya yi halinsa, amma ga jini yana malala daga kansa. Ganin hanan yasa Dr ya yi wurgi da sandar ya yi kan yaran, dan ya tsorata sosai, yasan cewa idan wani abin ya samu yaron nan, to wlh gwamnati ba zata bar shi ba, duk da uncle nasa ne yake a kan mulki, tabbas sai an hukunta shi idan ya cutar da jariri, hukunci kuma mai tsaurin gaske. Ita kuma gwaggon ta yi waje bata san me ya faru ba. Da gudu Josephine dake tsaye a bakin kofar palon tana ganin komai ta kariso cikin palon, dan ta duba jariran. A matukar haukace Dr ya kwashesu zuwa asibiti dan a duba mashi yaron ya mutu ne ko yana raye, ba shi da kwanciyar hankali da zai iya dubasu!!. Ita kuwa gwaggo, tun da ta bar palon bata sake waiwayo su ba, ta ce idan Dr ya ga dama ya kashe yaran ai nasa ne, dan haka sai ta wuce gida abinta. Tana zuwa ta hau shirin komawa Nigeria, tun da sun kammala karatu. Sai dai fa, da kyar a daddafe ta yi kwana ɗaya na rashin yaran nan. Washegari ta wuni tamkar mara lafiya. A daddafe ta kai yamma. Zuwa dare ta ji ba zata iya rayuwa babu yaranta ba, dan haka sai ta shirya ta tafi gidan Dr. Abin mamaki abin al'ajabi, ko da ta je sai Dr ya ce wlh ba zai bayar da yaran nan ba, yara dai yaransa ne! Kuma ta fita mashi a gida dama shi ba sonta yake yi ba, idan har bata fita ba, sai ya sanyata ta yi danasani mai girma. Da farko ta ki fita, sai da ta ga zai yi mata kaca kaca ne ta kama kanta tana kuka tare da danasanin sanin Dr da ta yi a rayuwarta, tamkar ranta zai fita haka ta bar gidan. A ranar Josephine ta zo har gidanta suka kwana a tare, dan ta ɗebe mata kewa. Kwana kuka Gwaggon ta yi tana danasani kai mashi ƴaƴanta da ta yi. Ita kuwa Josephine kwana rarrashinta ta yi. Abin gwanin ban tausayi, shaiɗan ya yi mummunar aika aika a tsakanin masoyan guda biyu. A takaice a cikin satin Gwaggo ta shirya ta dawo Nigeria, dan ta zo ta gayawa Dr Salman abin da yake faruwa, saboda su je su karɓo mata yaranta, ba zata iya rayuwa babu su ba, zata mutu idan ba'a karɓo mata su ba. Haka ta baro Washington ba tare da ta sake saka yaran nata a idanunta ba, bata san a wani hali suke ba, bata san ya suke a hannun Dr William ba, shin ya karɓesu a matsayin ƴaƴa ne ko yaya? Duk bata sani ba, bata sake sanin komai dan gane da su ba!!. Tana dawowa gida Nigeria ta tarar da bakin labarin da ta gwammaci mutuwa a kansa. Wato ta tarar da labarin Dr Salman ya rasu da shi da Naurat da Amarya, a yanda aka ce accident suka yi dukkansu suka mutu. Abu kaɗan ya hana ƙwaƙwalwar gwaggo bai juye ba, ga rashin iyaye, ga rashin masoyi, ga kuma uwa uba rashin jariran ƴaƴanta, ga rashin ƴan uwa. Dole ta yi hauka data ga Dr William, dan ya cutar da rayuwarta, duk shi ne silar komai a rayuwarta. Da badan son shi ba, ai da ba zata mance da kowa ba har iyayenta su rasu bata sani ba!. Tun tana kuka da hawaye, har hawayen nata suka dai'na fita. Cikin raɗaɗi da kunan rai ta nufi ɗaya daga cikin gidajen Dr Salman, in da aka ce mata nan Abba ya yi aure. Tana zuwa ta yi sa'a Abban yana gidan. Tana kuka tamkar zata mutu ta fara bashi labarin abubuwan da suka faru da ita, tun daga farko har karshe. Daga karshe ta rufe mashi da cewa, dan girman Allah ya taimaka ya karɓo mata ƴaƴanta a wajen Dr William, dan ba zata iya rayuwa babu su ba. Nan fa taga bala'i a karo na uku, dan kuwa Abba a lokacin ma bai gama dawowa cikin hanyacinsa na abin da amarya ta yi mashi ba. Dan haka sai ya yi wa gwaggo tatas, ya koreta daga gidan, wai ta zubar masu da kimar gidansu, ta je wata ƙasa ta haifi yara, shi sam bai yarda da aure ta haifesu ba, dan haka ba zai karɓo ƴaƴan shegu ba, da ace ta zo da su ma, wlh karɓarsu zai yi ya mayarwa da ubansu su, dan babu ƴaƴan shegu a kaf zuri'ar Dr Salman. Haka dai ya yi ta surfa ruwan bala'i, ta in da yake shiga, ba ta nan yake fita ba. Daga karshe ya korata waje tare da rufo gate ɗin gidansa, ya ce ta je ya yafeta a matsayin kanwa!!. A lokacin da yammane, wuraren karfe 6:30, bai yi wani tunani ba ya daketa ya koreta. Tana kuka tana rantse mashi da Allah wlh ba shegu bane ƴaƴanta, ƴaƴan sunna ne, dan Allah ya dai'na shaigantasu, amma ina haka ya sa kafa ya yi ball da ita. Ya ce bai san wannan ba. Ganin zai yi mata illah ne yasa ta baro bakin gate ɗin gidan a guje kamar mahaukaciya, tana gudu tana kuka, Ammien su Imran ta yi ƙoƙarin dakatar da Abban, amma ina, sam abin ya ci tura, yaki sauraronta, ya hau dokin zuciya, dama idan baku manta ba, a baya na gaya maku, shi mutun ne mai bala'in zuciya da zafin rai!. Bazama cikin gari gwaggo ta yi kamar mahaukaciya, da kamar zata je gidan Abbi, amma da ta tuna cewa, da Abbi da Abba halinsu iri ɗaya, sai ta gwammaci gara ta shiga duniya. Tamkar zautatciya haka ta zama. Tun tana iya gane hanyar da take tafiya a kai, har ta dai'na ganewa, ta fara ganin dishi dishi, da alama hankali ya gushe a tattare da ita. Daga karshe ma sai ta zube kasa a kasar wata bishiya ta bakin titi, kan ka ce me ta sume a wajen, saboda tukukin bakin ciki da yake cikin zuciyar baiwar Allah nan!!. Nisawa ta yi tare da goge hawayen fuskarta, sannan ta ce "Tun daga wannan suma da na yi, ban sake sanin in da kai'na yake ba, sai da na shafi shekara kwance a gadon asibiti, lokacin da na farka kuma, da fuskar kanina Nawazuddeen na fara cin karo, shi ne yake gaya mani shakarata ɗaya a sume a gadon asibiti, tsabar bakin ciki ban ko tambaye shi daga ina ya tsintoni ba, kawai na bar maganar, shi ya cigaba da kula da ni, na bashi labarin komai na daga auren da na yi, har da yayana TRIPLETS, hakuri ya yi ta bani, ya kuma biya kuɗin jirgi muka je har Washington DC, sai dai bamu sami su Dr William ba, mun yi tambayar duniyar nan, basu ko ɗaya daga cikin gidajen iyayensu da suka bari, kowa sai ya ce bai san in da suke ba. Daga karshe dai muka hakura muka dawo, zuciyata cike da kaunar yarana, ina jin tamkar zan mutu. Kullum Nawazuddeen ajiye duk wani abin da zai yi yake yi, ya dawo gida ya zauna ya yi ta bani hakuri, yana kwantar mani da hankali, a lokacin ko aure bai yi ba, shi kaɗai yake rayuwarsa shi ma. Haka muka cigaba da rayuwa a tare, na zama tamkar mahaifiyarsa, yana yi mani biyayya over, ban taɓa yin magana ya saɓa ba, ya mayar dani islami, a nan na sami ilimin addini sosai da sosai, daga nan kuma nayi danasanin abubuwa da dama na rayuwar da muka yi da Dr, da na sami ilimin addini sosai, na fahimci wani abin, na fahimci da ni da Dr mun aikata saɓon Allah sosai a cikin soyayyarmu, kila shi ne yasa Allah ya jarrabeni da wannan kaddara, dama irin wannan saɓon da muka aikata ai ba zai taɓa yiwuwa aurenmu ta yi albaraka ba". Ta kai karshen maganar tana goge hawayen fuskarta. Kowa da yake cikin palon sai da zuciyarsa ta raunata, ta kuma taɓu sosai, daddyn jelly kam kuka ya yi sosai, dan kun san shi dama, akwai shi da saurin kuka. Dayawa daga cikin jama'ar palon sun zub da hawaye. Gyaran murya Brr Naurat ta yi, cikin dattaku da girma ta ce "Dr William ka ji bayanan A'isha ko? Me zaka ce kai kuma? Bayan A'isha ta baka yaran, ka gaya mana ya ka yi da su? Ina suke? Menene kuma ya faru bayan barin A'isha gidan? Ina yaron da ka illatar da sanda? Meyasame shi? Muna jiran bayananka kai ma!!". Nan fa gabaɗaya kallo ya koma kansa. Harta ƴaƴan nasa ma shi suke kallo. Ya ɗan ɗauki ƴan mintoci kafin ya ce "Ni duk abin da ta faɗa ban sani ba, ni ban santa ba! Kuma ban taɓa ganinta ba sai yau, wata kila da wani Dr William ɗin take yi ba ni ba!"........TASHIN SENSE Brr Naurat tana ƙoƙarin sake yin magana Areef ya daka musu tsawa cikin tsananin ɓacin rai tare da tashin hankali. "Daddy kada ka mayar da mu mahaukata mana? How comes zata bada dukka wannan labari kuma ka ce karya ne? How comes ta san su kaka? How comes ta zayyano sunayen unguwar da gidajen kaka yake da sauransu?Kawai daddy ka gaya mana gaskiya!!". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa tsaye yana huci tamkar wani mayunwacin zaki. Tamkar ba Areef mai saukin kai da wasa da dariya ba. Miƙewa shi ma daddyn ya yi yana faɗin "James a said a don't know her, what do you want me to tell you again?!". Ya yi maganar cikin tsawa shi ma. Buɗe baki Areef ɗin ya yi da nufin ya yi magana. Bai kai ga yin maganar ba sai ganin Lion suka yi ya damki wuyar daddyn nasu da hannu ɗaya, ya maka shi da jikin bango tare da matse shi. Gabaɗaya ya canza lokacin guda, tamkar ba NooRin Meesha ba, idanuwansa sun yi jajir da su kamar wuta, har wasu jijiyoyi sirara ne suka fito mashi a damatsan hannunsa da kuma wuyarsa, sai wani irin numfashi yake yi mai kama da gurnanin zaki, jikinsa sai wani tsuma yake yi, ran maza ya ɓaci!. Shi kuwa Aseef miƙewa ya yi daga kwanciyar da ya yi daga saman cinyar daddyn Rimsha, ya kifa kansa da jikin hannun sofa yana hawaye, sam baya son ganin abin da yake faruwa. Sosai Lion ya shake daddy har sai da idanunsa suka juye, harshensa ya zazzago waje, yana daf da bakontan lahira. Ga shi Lion ɗin yaki ko da sassauta mashi, kuma ya ki yin magana, saboda tsananin ɓacin rai, dan daddy yana neman raina masu wayo. Can kuma cikin tsawa ya ce da daddyn nasa. "Tell us the truth, if not I'll make you regret! Me muka yi maka da zaka yi mana haka? Me bamu yi maka ba? Saboda kai muka ɓoye cewa mun musulta na tsawon shekara ɗaya yanzu, duk gudun kada mu sa ciwonka ya tashi, dan mun sanka da kishin addininka, zaka iya mutuwa idan ka ji mun zama musulmai, saboda kai muka ɓoye hakan! Duk dan mu faranta maka rai, mu kuma sauke hakkin iyaye da yake a kanmu, amma kai kuma ka gaya mana meyasa ka yi mana haka? Meyasa ka bari muka taso cikin kafurci? Ka yi mana karya! Ka ɓoye mana ainahin mahaifiyarmu, ka haɗamu da wata banza a matsayin uwa, bayan kuma sisterka ce uwa ɗaya uba ɗaya! Ka cutar da rayuwarmu! Ka cusa mana tsanar abubuwa da dama a rayuwarmu wanda bai kamata mu tsanesu ba! Ka ɓoye mana gaskiya, amma da yake, ita gaskiya komai daren daɗewa sai Allah ya bayyanata, sai ga shi Allah ya haɗani da Imran, na kaunace Imran sosai! Bana son kowa bayan TRIPLETS na, amma rana tsaka na tsinci kaina da son Imran, ta dalilinsa na dawo ainahin addinina, ta dalilinsa na tako kafata na zo Nigeria, wanda a baya ban taɓa tunanin zan zo ba, da Allah ya tashi kamaka daddy, kai ma da kafarka ka tako kazo Nigeria, ba wanda ya sanyaka dole, daga kan Imran kuma ban sake kaunar wani ɗan adam ba sai Uncle ɗin James, haka kawai shi ma rana tsaka na kaunace shi, har mamaki nake yi wani lokaci, na kasa banbance da shi da Imran wa ye na fi so a cikinsu, ashe dan Allah ya gwada mana wani aya ne yasa muke kaunarsu......". Da kyar ya kai karshen maganar saboda wani tukukin bakin ciki daya tokare mashi maƙoshi. Daga haka ya yi shiru bai sake yin magana ba, sai dai sauke dogon numfashi tamkar gurnanin zaki da yake yi, ya kuma kara shake daddyn da karfi sosai!!. Kallon Areef Abban Imran ya yi cike da tsananin tashin hankali ya ce "Areef ka dakatar da ɗan uwanka, idan ba haka ba, zai yi kisan kai, dan daddynku dab yake da ya mutu!". Ganin da gaske hakan ne yasa Areef ɗin ya nufi Lion ɗin da sauri dan kuwa da gaske ne daddyn nasu na dab da mutuwa. "Lion wlh zai iya mutuwa, dan girman Allah ka sake shi haka nan ya isa, ba kaga yanda yake numfashi ba ne?". A wani irin haukace ya damko wuyar Areef ɗin ma, da ɗayar hannunsa, ya haɗesu su dukkansu biyu yana jin wani bakin azaba a cikin zuciyarsa, tafarfasa zuciyarsa take yi tamkar an ɗaura dalma a wuta! Sam baya ji kuma baya gani, idanuwansa sun rufe, yau ne ya fito da ainahin zuciyarsa fili! Duk wajen an rasa mai iya gigin yi mishi magana, dama Areef ɗin ne kawai yake da ɗan kwarin gwiwar tinkararsa a irin wannan yanayi da yake ciki, to shi ma ga shi ya haɗa da shi ya shake. Aseef kam dama tun ɗazun daya kifa kansa da jikin hannun sofa, bai sake ɗagowa ba, duk abin da suke yi yana jinsu, amma ba zai iya ɗagowa ba, bakinciki zata iya sanyawa ya haɗiyi zuciya ya mutu idan ya ga halin da suke ciki, to gara mishi ya cigaba da runtse idanuwansa kawai zai fi mashi alkhairi, Rimsha, Jehan da Akila dukkansu guduwa suka yi, suka fita daga palon, ko wace ta san halin masoyin nata sarai, sun san me zai biyo baya idan suka tsaya, gara musu su gudu abinsu. Yau su Abba sun ga tashin hankali, an rasa mai bakin magana a cikinsu, su Imran duk sun haɗa malaman jikinsu waje guda, dan faɗar ta manya ce!!, TGA da yake jarumi ma, kirjinsa sai dukan uku uku yake yi, cikinsa na murɗawa, bare kuma saura, ai su tsoronsu a tsananin bayyane ma yake. Daddyn Rimsha ne kawai mai ɗan kwarin gwiwan da ya kalli Gwaggo ya ce mata ta yi wa Lion magana wata kila zai ɗan sassauto ya sakesu, idan ba haka ba to tabbas dukkansu zasu mutu, wlh har Areef ɗin, dan ba shakar wasa ya yi musu ba....... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E5 Daddyn Rimsha ne kawai mai ɗan kwarin gwiwan da ya yi ta maza, ya kalli Gwaggo ya ce mata ta yi wa Lion magana, wata kila zai ɗan sassauto ya sakesu, idan ba haka ba, to tabbas dukkansu zasu mutu wlh har Areef ɗin, dan ba shakar wasa ya yi musu ba. Ganin da gaske har da Areef zai iya mutuwa ne yasa ta miƙe da sauri ta isa wajen nasu. Shi kuwa Areef ɗin sam bai yi ƙoƙarin kwatar kansa ba, dan yasan duk bala'i Lion ba zai taɓa kashe shi ba! In yaga zai mutu da gaske, dole ya sake shi, sai kawai ya zuba mashi idanu yana kallonsa, kuma dama hakan shi ne dai'dai a cewarsa, ya kamata su koyawa Lion ɗin tausayi ne, idan Areef ɗin ya zuba mashi idanu yana kallonsa, to zai ji tausayinsa ya sake shi, a haka zai koyi tausayi sosai a cewarsu. Daga ɗan bayan Lion ɗin ta tsaya, gabaɗaya idanun jama'ar palon yana a kansu, kowa so yake ya ga ya Lion zai yi idan gwaggo ta yi mashi magana....... Ni ma PRINCESS TEEMA so nake yi naga ya zai yi😂 "Saif" ta ambata a hankali, tamkar bata son yin magana, kuma kamar tana jin tsoron yi mashi maganar. Hakika ya ji sunan har cikin ransa, duk fushi da yake ciki bai hana ya ji muryar mahaifiyar tasa ta ratsa dukka ilahirin jikinsa ba, dama shi already zuciyarsa ta yardan mashi cewa ita ce mahaifiyarsu!..... Ganin bai amsa ba, kuma bai sakesu bane, yasa ta ɗan kara mastowa, gabaɗaya a tsorace take da ganin yanayin da ɗan nata ya shiga, kirjinta sai dukan uku uku yake yi, amma hakan bai hana ta daure ta dafa kafaɗarsa da hannu ɗaya ba. Cikin sanyin murya ta ce "Saif ka sakesu, kada ka yi masu illa ka ji ko?". Wani irin dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali, har cikin kashi da ɓargonsa ya ji sakonta! Ya ji sautin muryarta!. Ba musu ya zame hannayensa daga wuyoyin nasu. Nan take suka zube kasa, shi daddy ya suma already dama, shi kuma Areef tari ya fara yi da karfi karfi ba kakkautawa. Uwa kenan, yau Lion ne yana cikin tsananin fushi haka har ayi mashi magana, kuma ya ji maganar ta ratsa shi? Lallai dai kam, uwa ta wuce wasa wlh!!. Da sauri daddyn Rimsha ya yi kan Areef ɗin bayan ya ɗauko mashi ruwa a cikin fridge mai sanyi. Cike da kulawa ya dafa shi tare da kafa mashi robar ruwan a baki yana yi mashi sannu. Shi kuwa Lion juyawa ya yi da nufin ya bar wajen, ya nufi bedroom nasa. Riko hannunsa ɗaya gwaggon ta yi, tana mai sake ambatar sunansa kirjinta na bugawa, dan tana tsoron kada su ce ba za su karɓeta a matsayin uwa ba, idan hakan ta kasance ba makawa zata iya mutuwa, dan tana bala'in sonsu, ko wani rana na duniya sai ta yi masu addu'a da fatan alkhairi tare da fatan Allah ya tsare mata su a duk in da suke, daidai da second guda basu taɓa barin cikin tunaninta ba, suna ranta fiye da tunanin mai tunani..... Allah sarki abin tausayi!. Juyowa ya yi gareta cikin natsuwa, zuba mata idanu ya yi na ƴan sakanni kafin kuma ya tsinci kansa da rungumeta a jikinsa. Rungume shi ita ma ta yi, tare da sauke wani nauyayyar ajiyar zuciya mai cike da tarin abubuwa kala kala a cikinsa. Nan take kuma ta fara ruwan hawaye. Wani irin sanyi shi kuma ya ji tana ratsa zuciyarsa da ya rungumeta, hakan ce ta kara tabbatar mashi da cewa lallai ita ce mahaifiyarsu, domin kuwa tun da ya taso har izuwa yau, ba'a taɓa rana guda da ya shiga cikin fushi da ɓacin rai, ace zuciyarsa ta yi sanyi lokaci guda ba, ba'a taɓa ba! Wani lokaci ma, idan ya fusata sai ya zubawa tsakiyar kansa ruwan mai tsananin sanyi, saboda ya sami sauki, dan tamkar ci da wuta zuciyarsa take yi idan ransa ya ɓaci. Amma yau rana ta farko, ya shiga ɓacin rai, daga jin voice na gwaggo kuma ya sauko cikin sauki haka, dole ba'a banza ba! Dole ita ce mahaifiyarsu ta gaskiya! Ya sami nutsuwa sosai a kanta! Yana tsananin jinta a ransa ne fiye da tunanin mai tunani! Ji yake yi tamkar ya ɗauketa a saman kafaɗarsa su yi ta kewaye duniya kawai, saboda tsantsar so da yake yi mata, ashe ba'a banza yake kaunar Rimsha ba! Ashe ba'a banza ba duk da basu son mutane, amma suka yarda da daddyn Rimsha ya zauna a wajensu, sannan kuma suka kaunace shi sosai! Ashe ba'a banza ya ji cewa dole ya tsaya tsayin daka wajen ganin ya kwatarwa da daddyn Rimsha hakkinsa na zaluntarsa da aka yi ba. Ba'a banza su Areef suke tsananin kaunar daddyn Rimsha ba, ko dan kula da mahaifiyarsu da ya yi tamkar ba gobe, ai dole ma su ji kaunarsa, uwa ta wuce wasa!!. Daddyn Rimsha ya kula da gwaggon over, shiyasa Allah dan ya saka mashi, ya jarrabi TRIPLETS ɗin da kaunarsa over!. Allah sarki rayuwa kenan, Allah mai kyauta mai kari, mai saka maka ta in da baka yi zato ba, Shiyasa ake son komai zaka yi, to ka yi shi domin Allah, dan idan ya tashi saka maka, zai yi maka babbar sakayyar da baka taɓa zato ba, a gaskiya daddyn Rimsha ɗan uwa ne na kirki da kowa zai yi fatar samun irinsa, duk bakinciki da kunci da su Abban Imran suka jefa shi a ciki, suka raba shi da mahaifinsa da Hassan nasa da suka kwanta ciki ɗaya, duk da hakan bai hana shi yana taimaka masu ba, kuma dan Allah yake yi, shiyasa da ya gamu da jarabawa na rabuwa da familynsa, sai Allah ya kare mashi familyn nasa, suka shiga hannun na gari, duk in da suka je, an rukesu hannun biyu tsakani da Allah, dan shi ma ya ruke mutane da yawa tsakani da Allah, bugu da kari, sai Allah ya bashi surukai ɗaya tamkar da million, wanda ko wani uba zai yi wa ƴaƴansa fatan samun mazajen aure irinsu, Allah ka cigaba da dafa mana, kasa komai zamu yi, mu yi shi domin ka, dan mu samu rahamarka a koda yaushe.❤️ STORY A hankali ya kwantar da kansa a saman kafaɗar gwaggon, yana sauke numfashi mai kama da gurnanin zaki. Hannu ta kai ta fara shafa lallausan gashin kansa, da yake ya rage tsawonsa ne, ya ɗan kwanto a kafaɗarta, to tana iya taɓa kansa. Jin sautin kukan gwaggon yana tashi a hankali hankali ne yasa ya ɗan ɗago kan nasa daga saman kafaɗar tata. Ganin da gaske take kuka ne yasa ya sanya hannu ya fara goge mata hawayen nata ba tare da ya yi magana ba. Tamkar jira take yi wani sabon kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro ne ya kubce mata. Zafafan hawaye ne wasu suna bin wasu a kuncinta. Hakika an cuceta ba kaɗan ba, an cutar da rayuwarta ba karya, kuma a duk wannan abin da ya faru, sam bata da laifi, duba da yanayin karantar shekarunta a lokacin, ga ƙarancin ilimin addini, sannan bata wani rayuwa da mahaifiyarta sosai ba, bata taɓa haihuwa ba sai a kan TRIPLETS ɗin, a lokacin da ta mayarwa da Dr yaran, bata gama sanin zafinsu ba, sannan zuciya ce ta ɗebeta, wanda kuma dama wannan dole ce, tama yi namijin kokarin da ta hakura ta haife cikin, duk cin amanar da ya yi mata, ta daure ta haife cikin, gaskiya ta yi namijin kokari, abin a jinjina mata nema!!. Ganin haka yasa ya ɗan raba jikinsu kaɗan tare da ɗan duƙawa ya ɗauketa cancak tamkar karamar yarinya, ya nufi bedroom nasa da ita. Gabaɗaya palon binsu da kallo suka yi, shi ma Areef binsu da kallo ya yi ya kasa motsawa, dan shi kaɗai yasan raɗaɗin da yake ji a cikin zuciyarsa. Shi dama Aseef bawan Allah sam bai ɗago kai ba ma, bare yasan me suke yi, yana kife yana kuka, Allah sarki bayin Allah!. Ita ma Brr Naurat sai bin su da idanu take yi, tana jin abin tamkar a mafarki ne!. Lion bai sauke gwaggo a ko'ina ba, sai a bakin katafaren bed nasa da yake shinfiɗe da white bed sheet mai matuƙar kyau da tsada, kamar yanda kuka sani ne, sai zuba uban daddaɗar kamshi bedroom ɗin nasa yake yi, ko'ina a gyare tsab, tsab, fes, fes!!. A gefenta ya zauna tare da ɗan juyowa suna fuskantar juna. Hannayenta ya riko cikin nasa, har lokacin zubar da hawaye take yi tamkar famfo aka bude. Cikin nutsuwa da sanyi murya ya ce "Ba zan hanaki kuka ba, ki yi sosai, dan yana rage raɗaɗi, na san duk raɗaɗin da muke ji a yanzu, ba mu kai kwatan naki ba, so just cry, cry more!". Ya kai karshen maganar tare da sakin hannayen nata ya rungumota a jikinsa yana sauke ajiyar zuciya. Kankame shi sosai ta yi tana mai cigaba da kukanta yana sauraronta, dan yasan kukan shi ne zai sa ta sami sassaucin abin da take ji a cikin zuciyarta, yau ta tuna baya, an cutar da ita over baiwar Allah. A haka gabaɗaya familyn suka shigo bedroom ɗin suka samesu, har da su Rimsha da Brr Naurat, duk sun biyo sahunsu, sun baro Dr William da yake sume, sai dai Areef ya ɗauke shi ya kwantar da shi a saman sofa, sannan suka biyo Lion ɗin. TGA da Uncle Herry suna wajen Dr William ɗin, su kuma su John wucewa suka yi nasu bedroom ɗin, wai ba za su zo ɗakin ba!. A ɗayan gefen gwaggon Areef ya zauna, ya zamana sun sakata a tsakiya. Shi kuma Aseef saman bed ɗin gabaɗaya ya haye, ya kwanta, kansa tamkar zata fashe mashi saboda ciwo, har wani jiri yake gani, yana ganin dishi dishi. Ɗago kai daga saman kirjin Lion ɗin ta yi tare da juyowa zuwa ga Areef dake gefenta. Hannu Areef ɗin ya kai ya fara goge mata hawaye yana faɗin dan Allah ta yi shiru, kukan ya isa haka nan, ba ya son ganin kukan nata, dan ba zai iya jura ba, zuciyarsa tana yi mashi zafi sosai idan yana ganin kukan. Yana magana yana goge mata hawaye, shi kuwa Lion ya dukar da kansa kasa yana tunani a kan abubuwan da gwaggon ta faɗa daga farko har karshe, yana nazari a kansu. Muryar gwaggon ne ta daki dodan kunnuwansu, a in da ta ce "Ina ɗayan ɗana? Ina cikon TRIPLETS ɗin?". Juyawa Areef ya yi izuwa ga Aseef dake kwance tamkar zai mutu, idanunsa sun yi jajir kamar jini. A sanyaye ya ce mata ga shi nan. Cikin ruɗu ta ce "Me ya same shi ya kwanta haka?". Ta yi maganar tare da kai hannu tana taɓa kansa. Turo baki ya yi tamkar yanda kuka sani ne, gidan shagwaɓa ba, ko a gadon asibiti yake sai ya yi ta, yanzu ma dai cikin shagwaɓa ya ce "Please ku dai'na taɓani, Allah idan ba haka ba in na fara kuka ba zan dai'na ba!". Shiru kawai gwaggo ta yi, dan kuwa yanda Aseef ya yi maganar sak Dr William time da suke zuba soyayya, sai ya tuna mata da baya. "My son mommarka ce fa take taɓaka, tashi ka gaya mini menene yake damunka?". Cewar gwaggon. Kara turo baki sosai ya yi yana faɗin "Ni momma to ki barni mana, bana so ne a taɓani". Girgiza kai kawai Areef ya yi, yanzu ya dai'na mamakin halin Aseef, tun da ya ji cewa daddynsu ruwa biyu ne, ɗan shagwaɓa ne ta wani fannin, ta wani fannin kuma ɗan bala'i, mafaɗaci, to kun ga kuwa shi Aseef ai shi ya yi gado, dan kuwa shi ma ruwa biyu ne, idan ka taɓo shi, ya iya faɗa, sai dai kawai ya fi Dr yawan shagwaɓa ne, dama kuma, ɗan na gada, ya fi ɗan na koya. "Tashi to ka zo na goyaka". Cewar gwaggon, ta yi maganar cikin zolaya. Ɗan ɗago kansa ya yi. A hankali ya matso kusa da ita yana faɗin "Kwanciya a saman cinyarki ma is okey my Momma". Matsa mashi waje kaɗan Areef ya yi, a nan ne ya samu dama ya kwantar da kansa a saman cinyar tata yana mai cigaba da turo ɗan bakinsa abinsa. Shiru bedroom ɗin ya yi na ɗan tsawon lokaci kafin Brr Naurat dake zaune saman sofa ta ce "To yanzu ina son sanin wani abu guda a kan wannan case ɗin". Ɗago kai dukkansu suka yi tare da kai kallonsu gareta. Lion ne ya amsa mata da cewa "No, just ki bar maganar nan a yanzu, ki bari sai gaba". Jinjina mashi kai ta yi, dan ta lura dukkansu basu a cikin nutsuwarsu. Ɗago idanu da gwaggon zata yi ne idaunta suka sauka a kan chain dake wuyar Lion ɗin, wani irin nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke wanda yasa TRIPLETS ɗin suka ɗago suna kallonta. Su daddyn Rimsha har suna rige rigen haɗa baki wajen tambayarta lafiya. Cool murmushi ta sakarwa daddyn Rimsha tana faɗin "Ina Jehan?". Da hannu daddyn ya nuna nata Jehan ɗin dake zaune kusa da Rimsha dake kusa da Brr Naurat. Alama ta yi wa Jehan ɗin da hannu a kan ta zo. Da sauri ta miƙe ta zo. Tsabar iya shege irin na Jehan ɗin a saman cinyar gwaggon kusa da Aseef ta gefe ta zauna tare da saƙalo wuyar gwaggon da hannunta ɗaya, tana wani kwaɓe fuska, tana kuma raɗa wa gwaggon magana a kunne. Binsu da idanu Areef ya yi yana tunanin irin tsiyar da ya rinƙa yi mata a kan daddynta a baya, yanzu reshe ta juye da mujiya kenan........ E NIMA PRINCESS TEEMA NA CE RESHE TA JUYE DA MUJIYA KUWA, DAN GWAGGO DA JEHAN 5 AND 6 NE, LALLAI JEHAN ZATA RAMA ABIN DA KA RINƘA YI MATA NA HANATA ZUWA WAJEN DADDYNTA😂 YANZU WASAN ZAI FARA😂 KAI ABUBUWA SUNA YI MANI DAƊI😂 AREEF KA JIRA ƊAUKAR FANSA😎🥳 DAN WLH GWAGGO DAI TANA BAYAN JEHAN💃🥳 Kome Jehan ɗin ta raɗa mata sai ga gwaggon ta fashe da dariya tana kallon Areef. Daga gani yasan gulmarsa ta kai, da wani idanunta kamar ball a cewarsa. Hannu gwaggon ta kai ta ciro sarkar dake wuyar Jehan ɗin, dama kun san nasu Jehan mai round ne, na su Lion kuma mai tambarin heart, sannan na su Jehan ɗin yana da faɗi fiye da na su Lion ɗin, kuma na su Lion zallar zinari ne, na su Jehan iya igiyar ce kawai zinari. Ciro sarkar Jehan ɗin ta yi a in da ta sanya karfi cikin dabara ta buɗe kan round na sarkar. Nan take wani tambarin ɓari na heart ya bayyana a cikin round ɗin, sai kyalli yake yi har yana ɗaukar idanu. Ciro heart ɗin ta yi sannan ta mayar da sarkar ta rufe tare da mayarwa da Jehan ɗin abinta. A hankali ta ambaci sunan Lion, ɗagowa ya yi yana kallonta. Kama sarkar wuyarsa ta yi tare da sanya ɓarin heart ɗin da ta ciro daga sarkar Jehan ɗin, ta mayar ta jona. Nan take chain ɗin ya koma tamkar ba'a taɓa raba shi biyu ba, ya zama kamar yanda yake. Sam Lion bai yi mamaki ba, dan yasan ita ce mahaifiyarsu, kuma dama yasan a wajenta kawai za'a sami rabin sarkar nan, dan har company ya je sun kasa buga mashi ɓarin da zai yi dai'dai da chain ɗin, daga karshe dai ya hakura ya bar zancen kawai, ashe yana jikin sarkar Jehan, gwaggo ta iya ajiya a in da kowa ba zai zata ba, kuma duk in da za su je yana tare da su. Cikin shagwaɓa Jehan ɗin ta ce "Gwaggo dama ashe abu kika ajiye a ciki kenan? Shi ne har da wani cemini ko za'a kasheni kada na yarda na bada sarkar nan ko? Wato yanzu dama a kan wannan abin ne har da cewa ko za'a kashe ni ko? Allah na ɓata dake". Ta kai karshen maganar tare da miƙewa dan ta bar wajen. Sake baki Areef ya yi yana kallon ikon Allah, mamaki yake yi, ashe dama ƴar rigimar nan tasa ta iya shagwaɓa kenan? Ashe da gangan take yi mashi abu kamar wata boss? Ai kuwa zai yi maganinta, ya faɗa a ransa. Bai san cewa da iya gwaggo kawai take shagwaɓar ba, bayan gwaggon ba wanda yake ganin hakwaranta ma bare shagwaɓa, sai daddynta da shi ma ba koda yaushe ba, sun fi shiri da gwaggon, mum nasu kam dama kun sani basu wani shaku ba, dan ita ta gwaggo ce. "Haba babyn gwaggo da daddynta, zo kiji wata magana". Cewar gwaggon. Kin zuwa ta yi ita a dole ta yi fushi, fuuu ta wuce zata bar wajen. Da hannu ɗaya Areef ya rikota yana faɗin "To ƴar rigima, ke kowa sai kin yi mashi ne? Sai kin nunawa kowa halinki ko?". Gwaggon ce ta ce "A'a babu ruwanka da babyna, tare ka ganmu, ka kyale mani ita, kada ka takura mata, ba wani rigimar da tayi, haka take dama". A takaice ya ce "Momma to ai ni kuma matata ce, kin ga yanzu na kwace maki ita kenan". Zaro idanu ta yi tana faɗin "Jehan ɗin tawa ce matarka? Waye ya baka ita? Wlh ba zata saku ba, a kan me? Ni ni zan bada auren Jehan, duk wanda ya bayar ba ni ba, to auren bai ɗauru ba". Jawo Jehan ɗin ya yi ya faɗa jikinsa yana faɗin "Momma uncle nane mana nima ya bani ita, ƴar rigima ba, kuma aure ya ɗauru, dan ma kin dawo da wuri ne, ai da sai dai ki zo ki ganta da ciki ko baby's". Salati gwaggon tasa, sam ƴaƴan nan nata basu da kunya ko kaɗan, shi ko kunyar iyayen Jehan ɗin su Abba da suke cike a wajen bai yi ba, kawai ya faɗi son ransa ne. Cikin fushi Jehan ɗin ta ce "Ni ka sake Ni!" Yanda ta yi maganar on a serious note, babu wasa a cikin maganarta, ya sha mamaki na jin abin da ta ce, sai dai bai kawo komai a ransa ba, kuma bai saketa ɗin ba, ita ma Gwaggo yanda Jehan ɗin ta yi maganar yasa ta fahimci da akwai matsala kenan a tsakaninta da Areef ɗin, kowa da yake palon harta daddyn Rimsha ya sha ruwan mamakin yanda Jehan ɗin ta dakawa Areef ɗin tsawa, ko a baya da take cewa bata son shi, bata taɓa yi mashi irin wannan magana a gatse har haka ba, ita kuwa ita kaɗai tasan dalilin da yasa ta yi mashi wannan magana. Gwaggon na ƙoƙarin kara yin magana Aseef ya katse su da cewa "Areef ka tuna mini ma, na ce yau zan yi wa Heartbeat surprise, har kasa na ji saukin jikina da ka tuna mani". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa zaune yana wani mustsuke idanu kamar wanda ya sha wani abin na maye. Shi dai Lion kamar babu shi a wajen, ya dukar da kai kasa kawai yana tunani. Da mamaki gwaggon ta ce da Aseef ɗin "Au kaima matar gareka?". Jinjina mata kai ya yi tare da matso da bakinsa saitin kunnenta yana mata raɗan akan ai yau ma yake son bawa matar tasa baby. Hasbunallahu. Kasa juyowa gwaggo ta yi bare ta haɗa idanu da shi, a hakan ma bata san cewa ya yi mata raɗan ne dan kada Akilar ta ji ba, ba dan Akilar tana wajen ba, ai da afili zai faɗi maganarsa, yo su ina ruwansu? Ina suka san me kunya? Ai sam basu san shi ba. Turawa ma da suke wasu abubuwa marasa ɗa'a a kan tsakiyar hanya, ai su nasu ma mai sauki ne, turawa ai iskancinsu a bayyane yake. Kawar da zancen gwaggon ta yi da cewa "To gaskiya wannan aure dai bai ɗauru ba, dan ni ban bada Jehan da Rimsha ba!". Areef zai yi magana daddyn Rimsha ya katse shi da cewa "A'a ni ai na bawa ɗana, kuma aure ya ɗauru, dan haka ba wani sharhi, Jehan matar Areef ne". Kafewa gwaggo ta yi a kan ita sam bata bayar ba, dole a zo a tsugunna a gabata a nemi aure Rimsha da Jehan, kuma sai ta tantance masu neman auren zata ba su, sai ta yi musu jarabawa masu tsanani tsauri, idan sun ci, sai a basu mata, idan ba su ci ba, shikenan ta rike ƴaƴanta, ta nema masu miji na gari. Ganin Lion yana ƙoƙarin mikewa ya bar wajen ne yasa gwaggon ta ce "Saif zauna mu yi magana ko?". Ba musu ya koma ya zauna yana faɗin "Mummy my head is penning me to much, bana son hayaniya, idan kuna yawan magana bazan iya zama a wajen ba, that's why nake son baku waje!". Hannu ta kai ta shafa kan nasa tana faɗin "Tom shikenan zamu yi maganar anjuma, je ka huta yanzu ga ji?". Ba tare da ya amsa ba ya miƙe ya fuce daga ɗakin abinsa. Shi kuwa Areef raɗa ya fara yi wa Jehan a kunne bayan ya matseta a jikinsa. Babu kunya a gaban gabaɗaya iyayenta. Ita kuwa ko kallo bai samu ta ɗago ta yi mashi ba, haushinsa ma take ji, burinta kawai ya saketa, shi kuma yaki, ya kankameta gam kamar wani ya ce zai kwace mashi ita. Nan fa hira ya ɓarke a cikin bedroom ɗin, ga Brr Naurat a wajen, ai sai ta fara basu labarin rayuwarta a Russia, su kuma suka gaya mata bayan tafiyarta Dr Salman ya rasu. Nan take ƴar tsohuwa ta fara kuka. Taruwa suka yi a kanta suna bata hakuri. Jikokin nata kuma sai dariya suke yi mata, wai ta tuna da tsohon zuwa, Imran da Irfan sai tsiya suke yi mata. Lallaɓawa Anaya ta yi ta fice daga cikin bedroom ɗin. Tamkar wata ɓarauniya haka take sanɗo. Palon kasa ta sauko, sai waige waige take yi tana neman Mark, dan ɗazun da suka shigo da daddynta, ta gan shi a palon kasan, ba halin ta yi mashi magana ne saboda daddynta. Shi kuma bai ganta ba, yana latsa waya, ba sai na sake gaya maku ba, irin halin Lion ne da Mark, abin da yake gabansu kawai suke yi, so ko mutun zai wuce ta kusa da su, sam basu ɗago kai bare su kalle shi, hakan tasa har su Anaya suka haura sama bai ɗago kai ba. Ta zo zata nufi waje ta hango shi a cikin kitchen yana aiki, wani irin tsantsar farinciki ne ya rufeta, sai sakin cool murmushi take yi. Cikin sanɗo ta lallaɓa izuwa cikin kitchen ɗin. Sarai ya ji alamar mutun, dan su suna amfani ne da sautin numfashi mutun, dan sun iya yakin sunkuru. Amma bai kawo cewa ita ba ce, ya yi tunanin Rimsha ce ko Jehan or Akila, dan sune kawai masu shigowa cikin kitchen ɗin. Hatta kariso kusa da shi bai juyo ya kalli wacece bane. Hannu ta sa ta tsaƙalo wuyarsa tare da ɗale jikinsa ta baya tana murmushi. A tsananin fusace ya juyo tare da damko wuyarta, ya dawo da ita ta gaban fuskarsa. Ta yi matukar razana na ganin yanda ya shaketa ɗin, nan take idanunta suka firfito waje, ta tsorata ainun, kirjinta sai dukan uku uku yake yi. Yana kawota saitin face nasa ya ga ashe ita ce, ga shi ta zaro mashi idanu tamkar za su faɗo kasa. Ai a dubu ya sake wuyar tata yana ɗan sunkuyar da kai kasa. Sam bai taɓa tunanin ita ɗin ba ce. Ganin tana ƙoƙarin zubawa kasa ne yasa a hanzarce ya rikota tare da jawowata jikinsa yana faɗin sorry. Ya yi maganar tare da sauke nauyayyar ajiyar zuciya, wani irin sanyi ya ji na jinta a jikinsa. "Haba my shi ne kake son kashe ni? Dan kawai nazo ganinka ko?". Ta yi maganar tamkar zata saka mashi kuka, tana yi tana turo baki. Cikin sanyin murya bawan Allah kasa kasa ya ce "Sorry my Queen, ban san ke ba ce ai, am so sorry". "Ni gaskiya ba zan hakura ba". Shiru ya ɗan yi na ƴan sakanni kafin daga bisani ya matso da face nasa daf da tata, kasa kasa kamar mai raɗa ya ce "Zaki fara ko? Wai har yanzu ba zaki dai'na wahalar da ni ba? Haba mana, kullum fa a waya sai kin yi ta yi mani kuka, kuma kin san bana son hakan, sai ki yi ta bani wahala, yanzu a zahiri ma ba zaki barni na huta ba?". (My peoples yau ga Mark ma da cewa mace sorry 🤔 duniya kenan😂 kai waye ya taɓa tunanin Mark da Lion za su furta wannan kalma ta sorry ga wani ma ba wata ba?🤔 Lallai mata mun ciri tuta, mu ɗin duniya ne, duk giman namiji da karfi izza da isarsa, muna iya juya shi son ranmu😂 dan haka dole a bimu 😂) Turo ɗan bakinta ta yi har sai da ta taɓa nasa, kasa kasa ita ma ta ce "Ai kai ne, sai ka yi ta yiwa mutun wani irin hali na basawa da bana ganewa". "Am so sorry zan dai'na duk abin da baki so kin ji ko? Amma a dai'na yi mani fushi da kuka please". Tana ƙoƙarin sake yin magana suka ji motsi a bayansu. Da sauri ya saketa, suna juyowa a tare, dan su ga wanene. Brady ne ya zo taya Mark ɗin aiki. Ajiyar zuciya Anayar ta sauke tare da wucewa da sauri, dan ta fice daga kitchen ɗin kada ma daddynta ko wani daga cikin family ya ganta. A hanzarce ya riko hannunta yana faɗin "Haba mana, ina kuma zaki je?". A takaice ta ce mashi cikin ɗaki zata koma, dan kada ma a nemeta, dama ta zo ganin shi ne kawai, tana tsananin kewarsa. Sake jawota jikinsa ya yi yana faɗin "Haba my Queen, bari na ɗan ganki tukun nan mana, kin san yanda nake kewarki kuwa? Please ki bari na ganki ko da na 1 hour ne". Sakalo wuyarsa ta fara kokarin yi, amma ina bata kai shi tsawo ba, ko ta sakalo ba zata iya tsayuwa a hakan ba, dan ko ta ɗaga kafa ba zai yi mata dai'dai ba. Ganin hakan yasa shi ya ɗan rankwafo mata da kansa kaɗan yana faɗin "Ƴar karama da ita a wajen, ba tsawo". Turo baki ta yi tare da jan gashin kansa ta wajen bayan wuyarsa. Wash ya ɗan furta kafin ya matseta a jikinsa da karfi. A can cikin bedroom ɗin Lion kuwa, sai hira ake yi, tamkar za su cinye junansu saboda tsantsar so da kauna, sai dai ko kaɗan basu taɓo hirar abin da ya faru a baya na dan gane da rayuwarsu Abba, ma'ana rayuwar gidan Dr Salman na baya, sam basu taɓo wannan hiran ba, saboda yau suna cikin tsantsar farinciki, ba su son tuna abin bakinciki. Shi dai Aseef ya makale a jikin mommansa abinsa yana ta zuba mata shagwaɓa, shi kuma Areef sai tsokanar Jehan yake yi bayan gwaggo ta gama gabatar masu da gabaɗaya uncles nasu. Shi kuma daddyn Rimsha da daddyn Anaya tamkar za su haɗiye juna, saboda kauna. Haka suka kasance har tsawo good 2 hours, kiraye kirayen sallar mangariba ne ya tashe su daga hirar ta su. Mazan suka wuce masallaci, matan kuma suka nufi bedrooms na su Rimsha. Ƴan matan kuma wato su Rimsha, suka wuce bedroom na daddynta dan su yi alwala a can. Gwaggo dai a nan ɗakin Lion ɗin ta yi alwala. Shi kuwa Lion tun da ya bar ɗakin, basu sake jin ɗuriyarsa ba. Rimsha tana shiga cikin toilet dan ta yi alwala, ta samu waje a saman chair, ta zauna ta fara tikar kuka kamar wadda aka yi wa sakon daddynta ya mutu.......... To fa kukan me kuma take yi hakan? Mu je dai zuwa. Ita ma Akila lokacin da ta shiga toilet ɗin da nufin tayi alwala bayan Rimsha ta fito, sai da ta yi kuka kamar ba gobe. Ita dai Jehan ko a jikinta, alwalarta ta yi ta fito. Umaisha ciki ya fara girma sosai, sai tura abinta take yi. Bayan sun yi sallah sun dawo ne aka haɗu gabaɗaya a palon sama. Nan fa su Abba suka ce za su wuce gida, kuma za su wuce da Brr Naurat. Suna cikin yin magana sai ga Lion ya shigo. Kusa da gwaggon ya zauna, kasa kasa ya tambayeta ya ta wuni?. Da fara'a ta amsa mashi da lafiya. Dawo da kallonsa a kan Areef ya yi kafin ya ce "Where is dad?". Yana bedroom nasa Areef ɗin ya bashi amsa. Jinjina kai ya yi ba tare da ya sake yin magana ba. Gwaggo ce ta gaya Lion ɗin uncles nasu za su koma, amma tare da ita za su tafi, kuma za su tafi da Brr Naurat. Girgiza kai ya yi yana faɗin "No momma, ke kina nan, kuma ita ma grandma a barta a nan!". Abban Imran ne ya karɓi zancen da cewa "A'a ita A'isha ta zauna a nan ɗin, dan kuna da bukatarta fiye damu, amma ita Brr zamu tafi da ita, dan mun fiku bukatarta muma, muna da bukatar mu zauna da ita, akwai abubuwa da dama da zamu tattauna da ita". Shiru ya yi bai sake cewa komai ba, gwaggon ce ta sake cewa, to shikenan hukuncin da Abba ya yanke ya yi. Miƙewa Lion ɗin ya yi tare da wucewa bedroom nasa abinsa. Cikin hanzari Areef ya bi bayansa, shi kuwa Aseef har wa yau yana kwance ya tada kai da cinyar gwaggon abinsa. Shiryawa su Abba suka yi, gabaɗayansu suka wuce izuwa gidan Abba, Jehan, Rimsha, Akila, duk sun bisu, sun bisu ba tare da su Abba sun sani ba, dan a motar Imran suka shiga, shi kansa Imran ɗin bai lura ba, dan familyn dukka sun haɗu, kuma shap ya mance da cewa su fa matan TRIPLETS ne......... Bayan anyi sallar isha, gwaggo ta idar da sallah a bedroom ɗin Lion, tana zaune a saman dadduma, su kuma sun tafi masallaci. Tana zaune a wajen har suka dawo, bakinsu ɗauke da sallama suka shigo cikin ɗakin. Su ukun dukka gwanin ban sha'awa. Fuska ɗauke da murmushi ta amsa masu sallamar tana mai binsu da kallo. Wani irin tsantsar farinciki na wuce misali take ji a tattare da ita, har wani ji take yi kamar ta mayar da su cikin cikinta, dan so da kauna. A bakin bed Areef da Lion suka zauna, shi kuwa Aseef saman bed ɗin bakiɗaya ya haye ya kwanta. Zubawa mahaifiyar tasu idanu suka yi suna ta kallonta. Sai zuba adduo'i take yi tare da askar har tsawon good 30 mins. Sannan ta shafa tare da mikewa ta dawo kusa da su. Suna ƙoƙarin matsa mata, dan ta zauna a tsakiyarsu, sai ta wuce ta zauna a saman bedside drawer. "Momma ki dawo saman bed mana?". Cewar Areef. Girgiza kai ta yi tana faɗin "Bari na zauna a nan, zan fi jin daɗin ganin fuskokinku da kyau". "To shikenan ai muma a wajen zamu fi jin daɗin ganinki our pleasure". Murmushi ta ɗan yi kafin ta ce "Son lafiya kuwa?". Ta yi maganar tana kallon Lion. Shiru ya ɗan yi na ƴan mintoci da ba su biyu ba, kafin ya amsa mata da "Nothing mum". Dawo da kallonta a kan Areef ta yi, girgiza mata kai ya yi yana nuna mata alamar shi fa Lion haka yake da rashin magana, dan haka kada ta wahalar da kanta ma wajen yin tunanin ko dai wani abin ne yake damunsa, haka Allah ya yi shi. Jinjina kai ta yi alamar gansuwa. "Son ya daddyn naku yake? Kun duba shi kuwa?". Ta sake tambayarsu Sai a lokacin ya ɗago da dara daran idanuwansa a kanta. Allah sarki soyayya, hakika Gwaggo tana tsananin son Dr har gobe, duk wannan abin da ya yi mata a baya, amma ta kasa samun natsuwa a yanzu dan yana cikin wani hali, ba zata iya sharesa yana cikin ciwo ba. Sam bata bawa Lion mamaki ba, dan dama a yanayin tarihin soyayyarsu, ya san fin hakan ma Gwaggo zata aikata, hakan ce ma tasa ya kula da lafiyar Daddyn nasu, ashe fitar da ya yi ɗazun, zuwa ya yi ya bashi kula tare da allurai, dan yasan confirm sai gwaggon ta tambayesu, ga shi kuwa ta kasa hakuri sai da ta tambaya. Jinjina mata kai ya yi yana faɗin "Yeah mum, na kula da shi". "Kai Dr ne?" Ta tambaya tana dawo da kallonta a kan Areef. "No mum, but na yi karatun a wajen daddyn". Ji ta yi tamkar ta ce musu zata je ta duba shi da kanta, zata bashi kulawa a matsayinta na Dr, sai kuma ta share, ta danne tare da kawar da zancen da cewa. "To shikenan ya kamata ku ci abinci ku kwanta ku huta ko?". Jinjina mata kai ya yi tare da faɗin "Where is Meesha?". Sai a lokacin ma ta tuna ashe babu kowa a gidan sai ita kaɗai, su Rimshan duk sun bi iyayensu, sai a lokacin kuma ta tuna ashe a labarin da Jehan ta bata, Rimsha matar Lion ɗin ne, ashe auren ta zo rabawa zancen ta sauya, sai yanzu ta tuna komai, lallau kuwa. "Son dama kai ne mijin Siha na ko?". Ta tambayi tana kallon shi. Bai amsa mata ba, kuma bai sake ɗagowa ya kalleta ba. Areef ne ya amsa mata da e. Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Ban ji motsinsu ba, kila sun bi su yaya babba ?". Nan ma shiru Lion ya yi yana kallon kasa, bai sake yin magana ba. Areef yana ƙoƙarin sake yin magana Aseef ya katse su da cewa "Kai momma har da Heartbeat ta bi su?". Jinjina mashi kai ta yi tana faɗa mashi ai dukka suka tafi. Mikewa zaune ya yi yana faɗin "Wlh i can't believe it! A kan me zata je wani waje kuma bata gaya mani ba? Ni wlh ba zai yi wu ba, gaskiya dole na je na ɗaukota!". Murmushi gwaggon ta yi tana faɗin "Yau dai sai ka hakura ka barta da iyayenta, murna take yi na ganin kakanta da sauran ƴan uwa, nima ba dan murnar ganinku ta fi yawa ba, ai da ba zan zauna a nan ba!". Kuka ya saka mata yana faɗin "Allah momma ni ba zan yarda ba, dole sai ta dawo yau, kuma sai na yi punishing nata, dama da safe ta yi mani laifi". Dariya kaɗan gwaggon ta yi dan ta ɗauka wasa yake yi, bata san halin ɗan nata ba, bata san rigimarsa ba, ai yau idan ba dawo mashi da Akila aka yi ba, to ba zaman lafiya, wannan kuka ya rinƙa yinta kenan har washegari. Waya Lion ya ɗauka ya fara kiran number Mark. Bugu ɗaya ya ɗauka. A takaice ya ce ya kawo masu abinci cikin ɗaki, sosai Mark ɗin ya yi mamaki, dan ya jima rabonsa da ya kawowa Lion ɗin abinci, sai dai ya girka kawai. After some minutes Mark ya shigo masu da abinci kala kala, a saman carpet ya jere masu. "Momma let's eat". Cewar Lion ɗin, ya yi maganar tare da miƙewa ya isa ga abincin. Make kafaɗa Aseef ya yi yana faɗin shi wlh ba zai ci ba, dole sai Akila ta dawo. Da kyar gwaggo ta rarrasheshi ya sauko, shi ko Lion ko a jikinsa, Areef ma dai bai wani kula shi ba, dan suma dukkansu kusan hakan suke ji. Shi Areef baya jin zai iya barci ba tare da ya kalli face ɗin Jehan ba, shi kuwa Lion barcin ne ma kwata kwata ba zai iya ba idan ba tare da Meesha ba, dan sun saba kwana gado guda da ita a cikin jirgin ruwa, Areef dai Allah ya taimaka dama bai taɓa kwana da ita ɗaki ɗaya ba. Shi kam Aseef na shi ai kun sani dama na daban ne, yanda suke kashe juna da love da shagwaɓa ko wani dare shi da Heartbeat nasa, yau kawai ta gudu ta barshi, ai ba zata saku ba........... E KAM BA ZATA SAKU BA, AMMA KUMA TA TAFI ƊIN😂YO ME RUWA NA NI? KO YA KUKACE MASU KARATU? ME RUWANMU? AI NAMU IDO. A tare suka fara cin abincin suna hira sama sama, Areef ya fi sakewa ya biyewa gwaggo suna zuba hira, shi kuma Aseef sai wani kumbure kumbure yake yi, shi a dole ran maza ya ɓaci, Akila ta bijire umarnin miji. Lion kuwa ba sai na faɗa ba, kun sani, magana ce baya so. A ɓangaren su Rimsha kuwa. Bayan sun isa gidan Abba ne daddynta ya ganta, faɗa sosai ya fara yi masu akan me za su baro mazajensu, su biyo su?. Kuka ta sakawa daddyn nata sosai, kuka ta gaske mai sauti da iya karfinta. Nan take kowa ya fara tambayarta lafiya kuwa? Me ya sameta take kuka?. Cikin kuka ta fara magana da iya gaskiyarta, tana yi tana kara sautin kukan nata. "Daddy wlh bana son yaya Saif, ni ba zan zauna da shi ba, ba zan sake zuwa in da yake ba, ba ruwana da shi, ba zan sake zuwa gidansa ba, dan girman Allah daddy kada kace na koma can, wlh zan mutu, ni bana son shi....." BABBAR MAGANA. Bata gama rufe baki ba Akila ta karɓi zancen da cewa "Wlh nima daddy bana son heartbeat, ni kawai na dawo gidanmu, wlh ba zan koma ba". Yau ga ikon Allah su daddy suna gani, sun ma rasa abin faɗe. Jehan ce ta katse su da cewa "Ku da dama kuke sonsu kenan, ai ni dama tun ainahi bana son shi, daddy ne kawai ya wani kakaba mani shi, kuma wlh yanzu ba ni babu shi, ya san in da dare ya yi mashi". To fa, yau ga ikon god. Ɗaure fuska sosai daddyn ya yi zai fara magana kenan Brr Naurat ta riga shi da cewa "To shikenan tun da baku son su, ku je ciki ku ku ci abinci, sai ku kwanta ku yi barci, da safe sai mu yi maganar ko". Brr Naurat akwai saurin gane abubuwa, ta gane me matsalarsu, dama ita da kanta ta yi danasanin labarin da gwaggon ta bayar a gabansu, ta san dama hakan zata iya biyowa baya, ta zan za su guji mazan nasu, dan za su yi tunanin irin abin da ya faru da gwaggon, abin da Dr William ya yi mata na cin amanar soyayyarsu, za su yi tunanin suma haka su Lion ɗin za su yi masu, tun da duk Turawan ne. TO FA BABBAR MAGANA, E DAMA DOLE ZA SU JI HAKAN AI, SABODA YANDA DR WILLIAM YA NUNAWA GWAGGON TSANTSAR SO DA KAUNA, DAGA BAYA YA CI AMANARTA, AI DOLE SU RIMSHA SU KARAYA, BARE MA ITA RIMSHA DA DAMA LION BAI TAƁA CEWA YANA SONTA BA, KUNGA KUWA AI DOLE TA GUDU DAN TA RUFAWA KANTA ASIRI, KADA TA FAƊA IRIN TARKON GWAGGO, SUN MANTA LAIFIN WANI BAYA SHAFAN WANI, SUN MANTA KOWA DA IRIN HALINSA, AMMA BA ZA KU GA LAIFINSU BA, SUNA A KAN GASKIYARSU NE❤️ Daddyn Rimsha ne ya ce "Mum zamu wuce dasu gidana na nan Kd, dama a gyare yake, nan gidan ya yi mana kaɗan, gobe da safe zamu zo". To Brr Naurat ɗin ta amsa mashi da shi, sannan ta kira shi gefe a in da ta gaya mashi kada ya yi wa su Rimsha tsawa ko faɗa a kan cewa da suka yi ba su son mazajensu, ya kyalesu zuwa gobe idan sun zo, ita zata yi magana da su. Okey ya amsa tare da yi wa su Abba sallama ya kwashesu, Rimsha, Jehan, da kuma Akilar, sai mum, suka wuce gidan nasa. Daddyn Anaya ma, ya koma gidansa da iyalansa, saura su Abbi, daddyn jelly sai Abban, Aunty ma tana nan, ita kuma Hjy Hadiza tana gida. Sune suka kwana a gidan Abba tare da Brr Naurat, kwana suka yi suna ta zuba hira. Su daddyn Rimsha kuwa, bayan sun isa gida, abinci daddy ya fita ya sawo musu, suka ci suka kammala, ko wacce ta yi wanka ta yi shirin kwanciya, da yake gidan yana da matuƙar girma, ga yelwar ɗakuna da abubuwan more rayuwa, sai kowacce ta wuce daɗinta daban, ita kuma mum ta bi daddy abinta, dan suna bala'in kewar juna. Duniya dukka sun yi barci Rimsha da Akila sun kasa yin barci, kuka yarannan suke yi tamkar za su mutu, tun hawaye na fita, har ya dai'na fita, yanda suka ga rana, haka suka ga dare, ba barci, amma duk da haka sun ki yarda ko kiran mazan nasu a waya su yi, kashe wayar tasu ma suka yi, Lion ya nemi number Rimsha a kashe, shi ma Aseef ya kira Akila a kashe, ga shi gwaggo ta hanasu zuwa su ɗauki matan nasu, ta ce yau su hakura, haka suma suka kwanta cikin kaɗaici da kewar matan nasu. Ita kuwa Jehan wlh ko a jikinta, barci ta yi har da manta a wani duniyar take, shar zuciyarta, ta bar Areef da kwana kallon hotonta bawan Allah. KAI JAMA'A YARANNAN SU RIMSHA SUNA SHA'ANINSU WLH, WAI YAU RIMSHA CE ZATA CE BATA SON LION?🤔😂 A LALLAI KUWA, AKWAI KALLO GOBE, GA SHI DAI KWANA ƊAYA KAWAI TA KASA HAKURA, SAI KUKA TAKE YI, INA GA KUMA ANYI SATI? INA GA SAI GADON ASIBITI ZA'A WUCE DA ITA😂AMMA KUMA SUNA DA GASKIYA, SU TSARE KANSU, KADA ABIN DA YA FARU DA GWAGGO YA FARU DA SU, INA GEFE NI DAI!!! JEHAN KUMA ƳAR DUNIYA, KO A JIKINTA😂 KAI LITTAFIN TRIPLETS AKWAI ƳAN AIR WLH😂 SU HEARTBEAT MA DAI AN KASA BARCI😂 KO YA ZA SU YI GOBE IDAN SUKA FITO DADDYNSU YA KALLI IDANUNSU A KUMBURE SABODA KUKA? ME ZA SU CE IDAN AKA TAMBAYESU A KAN HAKAN?😂!!!. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E6 Washegari, kasancewar mum ta san babu kayan abinci a gidan, sai bata yi ƙoƙarin tashi ta haɗa masu breakfast ba, ta bari su je gidan Abba or restaurant su karya, kwata kwata ma bata fito daga daɗin daddyn ba, suna a tare manne da juna abinsu, su kuwa su Rimsha, sun ci uban kuka tamkar ransu zai fita, idanu sun kunbura luhu luhu, har wani ja suka yi ta kasar fatar idanun, Jehan ƴar gwaggo kuwa, ko a jikinta, bayan ta tashi ta yi sallar asuba, sake mayar da barcinta ta yi, hankalinta a kwance. A ɓangaren Lion kuwa, kwana ya yi bai yi barci ba, ya kwana yana tunani tare da nazari a kan zantukan gwaggo, shi ma dai Areef bai yi barcin ba, ya nutsa cikin tunaninsa a kan maganar. Abin da ya ɗaure wa Areef kai har ya sanya shi cikin tunani shi ne, meyasa Josephine zata tsanesu? Bayan kuma ita ce ta kula da mahaifiyarsu a lokacin da take ɗauke da cikinsu? Idan da tana son kashe su, ai da tun suna cikin cikin mahaifiyar tasu zata kashe su, amma bata yi hakan ba, ta kula da su sosai, sai daga baya za'ace masu ta nemi hallakasu? Anya kuwa akwai gaskiya a wannan lamari? To meyasa Dr William ya tsaneta? Meyasa ya koreta daga gidansa, bayan kuma har TRIPLETS ɗin suka ɗan yi wayo a tare suka gansu a matsayin mata da miji da Dr William ɗin? Wannan abin akwai ɗaure kai, ya saka Areef a cikin damuwa sosai, ya sanya shi shiga cikin yanayi mara dadi, ga kewar Jehan ɗinsa, abubuwa sun haɗe mashi bawan Allah!!. Shi kuma Lion kalma ɗaya zuwa biyu ne suke mashi yawo a cikin ƙwaƙwalwasa, na farko, cewa da gwaggon ta yi TRIPLETS nata biyu daga ciki kamanninsu ɗaya, kuma dukkansu biyun blue eyes ke garesu, shi kuma ɗayan idanunsa daban, to shi dai Lion yasan su TRIPLETS da Dr William ya haifa, dukkansu idanuwansu daban daban, babu wanda idanunsu yake iri ɗaya, Areef ash eyes, Aseef brown eyes, shi kuma Lion ɗin blue eyes, kuma duk cikinsu shi kaɗai ne yake kama da Dr William kamar yanda gwaggon ta faɗa, to ya aka yi hakan ta faru?! Ina blue eyes na ɗayan?! Meyasa kuma bai yi kama da Dr William or Lion ɗin ba?! Wannan abin ya tsaya mashi a rai over, idan ya yi tunanin to ko dai ɗaya daga cikinsu Areef ba TRIPLETS nasa bane, sai kuma yaga hakan sam ba zai yi wu ba, duba da yanda suke jin bugun zuciyar juna, sannan suna da kwari da kunama, ga kuma uban shakuwa da take a tsakaninsu na wuce misali, kai bama zai taɓa yiwuwa ace ɗaya daga ciki ba cikon TRIPLETS bane! Hakan sam ba zai yiwuba! Dole dai da akwai abin da ya saɓa, kuma dole Josephine da Dr William ne za su faɗa menene ya saɓa ɗin!!. Abu na biyu da yake ta jujjuyawa a cikin ƙwaƙwalwasa kuwa, ya aka yi su Dr William suka koma Kristen? Kamkar basu taɓa musulta ba, kuma a labarin da gwaggon ta bada, har karatun Alkur'ani mai girma sun iya sosai, to ya aka yi suka canza? Canzawa mai ban mamaki haka? Ina Cherish take? Me ya rabata da su Josephine? Ina take lokacin da gwaggon zata dawo Nigeria? Waɗan nan sune tunanin da suka hana Lion runtsawa, ya rasa amsarsu, ya nutsar da brain nasa yana neman amsa cikin nutsuwa.......... NI KO NA CE AI KAI ƘWAƘWALWARKA DA BASIRARKA TA GADO CE, KA GAKI BASIRA BA KARYA, DOLE MA KA BANKAƊO GASKIYA IDAN KA SAKA KANKA, BA ABIN DA ZAMU CE MAKA FACE ALL THE BEST OUR LION!!. Hakika kuma ya shiga damuwa na rashin Rimsha a kusa da shi, shi ne ma yasa tunanin da yake na neman amsar ta kasa gudu, ya kasa samun amsa da wuri, saboda rashin Meesha a kusa da shi babbbar barazana ce ga nutsuwarsa, hankalinsa ya rabu kaso uku, kaso biyu yana kan tunanin Meesha, ɗaya kuma tunanin su Josephine, da Rimsha na kusa, wata kila a daren zai iya bankaɗo menene gaskiya, dan ya yi alkawarin bama zai tambayi daddynsa ba, saboda yana ganin kamar daddyn ba zai gaya mashi gaskiya ba, ya ce da kansa zai bankaɗo komai da komai. AFTER SOME HOURS. Da misalin karfe 9 na safe, shirye cikin wando jeans mai matukar bala'in kyau, black color, da polo t-shirt fara kal, Lion ya fito daga cikin bedroom nasa, hannunsa na ɗaure da TRIPLETS watch, still sarkan nan tana wuyarsa, ya ɗaure gashin kansa a bayan wuya, sai tashin daddaɗa kuma zazzafar kamshi yake yi, ya yi matuƙar kyau sosai, sai dai da kallo ɗaya zaka yi mashi, kasan bai sami damar yin barci daren jiya ba, dan idanunsa sun yi wani kal da su, tamkar wanda bashi da lafiya, fuskarsa ta yi wani fayau da shi. Bedroom na daddyn Rimsha in da gwaggo take ya nufa. Kasa kasa tamkar bai yi magana ba ya yi sallama, tare da shiga ciki. Areef na zaune a bakin bed nata, ita kuma gwaggon tana zaune a saman bedside drawer suna zuba hira, shi kuma Aseef yana can yana zuba barci, bai tashi ba, dan daren jiya bai yi barci sosai ba. A tare gwaggon da Areef ɗin suka amsa mashi sallamarsa, karisowa cikin ɗakin ya yi, yana taku cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, tamkar baya son taka kasa, da alama jikinsa duk a mace yake. Gefen Areef ya zo ya zauna yana tambayar gwaggo ya ta kwana?. Sai murmushi take yi ta amsa mashi da lafiya lou ta kwana, Areef ne ya fara ɗaga mashi gaisuwa, a takaice ya amsa da lafiya tare da miƙewa ya ce da gwaggon yana zuwa, zai je unguwa. "A'a zauna ina son yin magana da kai!". Okey ya amsa mata tare da gyara zama. Shi kuma Areef mikewa ya yi yana faɗin "Momma bari na je na ɗauko matata, dan ba iya jurewa zan yi ba". Ya kai karshen maganar tare da wucewa da sauri. Kafin ta yi wani magana ma ya fice abinsa. Dawo da kallonta a kan Lion ɗin ta yi tare da fara magana a nutse. "Ina Muhammad, Sudais da kuma A'isha suke?". Wato su Uncle Herry take nufi kenan. Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Just call them Herry, Josephine, and Tyson, because all of them are Kristen now, ba yanda kike tunani bane". Zaro idanuwanta waje sosai ta yi, cike da mamaki ta ce "Harda Josephine ɗin?". Jinjina mata kai kawai ya yi ba tare da ya sake yin magana ba. Shiru ta yi tana al'ajabin wannan al'amari, katse mata shirun ya yi da cewa "Momma forget about them, saboda babu mai gaskiya a cikinsu, ko kin tanbayesu, karya za su yi maki, kamar yanda suka yi mana, dukkansu bakinsu ɗaya, so forget about them, I will do something about da case, now abin da nake so da ke, kada ma ki sake yin maganar, kada kuma ki sake tambayar kowa komai a kan labarin baya, ki rufe babin kawai!". Tabbas ta sha jinin jikinta na jin abin da ɗan nata ya faɗa, ta kuma sha ruwan mamakin yanda aka yi gabaɗaya su Dr William ya zama bakinsu a haɗe, ya aka yi Josephine mace mai hankali ta biye masu? Wai menene yake faruwa ne?..... "Momma zan iya tafiya?". Ya faɗa cikin sanyin murya. "Ina zaka je?". Kai tsaye ya bata amsar gidan uncle zai je, kamar zata tambaye shi wani uncle ɗin daga ciki, sai kuma ta fasa, dan ta lura baya son yawan magana, hannu ta kai ta shafi kansa tare da fara kwararo mashi ruwan albarka da adduo'in masu ratsa jikin duk wani mumini. Wani abin sai uwa, babu wanda ya taɓa yi mashi makamancin hakan, hakan tasa ya ji wani mugun sanyi tana ratsa zuciyarsa, Allah sarki, wata kila da ace gwaggo ta rayuwa da su, da ba zai yi zafin zuciya har haka ba, da ko ma yaya ne zai rage wasu abubuwa, uwa, uwa, uwa, haka Allah ya kirata sau uku kafin ya kira uba, Allah ka karawa iyayenmu lafiya da nisan kwana, waɗan da suka rigamu gidan gaskiya kuma, Allah ya jikansu da Rahman, ya kai haske cikin kabarinsu, ya sadasu da manzon rahma. Miƙewa ya yi ya kara mastowa kusa da ita sosai, a saman cinyarta ya kwantar da kansa, a can cikin zuciyarsa kuma, yana jin tamkar ya haɗiyeta, saboda so da kauna. Ita kuwa, ta cigaba da kwararo mashi ruwan addu'a ba kama hannun yaro, tana yi tana shafa lallausan gashin kansa, ya yi shiru yana sauraronta, abin gwanin birgewa, kowa ya gansu a haka, sai ya matsa kwallar farinciki, haka ta yi wa Areef ma da ya shigo ɗazun, dan shi tun karfe 6 yana wajenta, sai hira suke yi har lokacin da Lion ɗin ya shigo. Sai da ta kai karshen addu'ar ne ya ɗago kansa tare da kai ɗan bakinsa saitin kumatunta, sumbata ya manna mata a wajen yana faɗin "I really more appreciate and happy da ya kasance kece mahaifiyarmu, i love you so much my momma". Ya kai karshen maganar tare da sake manna mata sumbata a kumatun nata. Shafa lallausan sajensa ta yi, tare da manna mashi sumbata a goshin tana faɗin "Na fika farincikin kasancewarku ƴaƴana, ina alfahari da ku, je ka wajen uncles ɗin naka ka dawo, idan ka dawo, sai ka gaya mani aikin me kuke yi? Akwai wanda ya gaje mu a karatu ne a cikinku? Ko dai babu Dr a cikinku?". Jinjina mata kai ya yi tare da miƙewa ya nufi kofar fita ba tare da ya sake cewa komai ba. Da kallo ta bishi tare da fatan alkhairi har ya fice. Yana fita Mark ya shigo mata da abinci, dan Areef ya gaya mashi ya kawo mata abinci kafin su dawo, sai su ci a tare gabaɗaya. A can gidan daddyn Rimsha kuwa. Sai misalin karfe 8:30 daddy ya fito cikin shirin kananan kaya, waje gabaɗaya ya fita, restaurant ya wuce, abinci ya sawo masu ya dawo. Kafin ya dawo mum ta jera plates da komai a saman table, tana zaune tana jiransa. Ko da ya dawo, saman table ɗin ya wuce yana faɗin su Rimsha basu tashi daga barci bane? E ta amsa mashi da shi. Jinjina kai ya yi kafin ya ce "Okey ki kyalesu duk time da suka tashi, sai su zo su ci nasu breakfast ɗin". Okey ta amsa mashi da shi. Wani irin daddaɗar kamshi perfume ne ya daki hancinsu, a tare suka ɗago kai dan ganin wanene. Jehan ce take saukowa daga saman bene, ta shirya cikin ɗaya daga cikin kayan da ta samu a cikin walldrop na bedroom nata, doguwar riga ce mai kama da baya, blue color, kaya sun yi mata matuƙar kyau, abinku da farar mace, ta haɗu da blue color, ai kunsan dole ta haska. Ta yafo gyalen kayan a kanta, light make up ne a fuskarta, sai lips gloss da ta sanya a kyawawan lausasan kananan lips nata, duk wanda ya ganta, sai ya sake waigawa ya kalleta, saboda ta fita ta yi kyau over. Kusa da su daddy ta zo ta tsaya tare da ɗaga masu gaisuwa. Cikin tsantsar so da kauna suka amsa mata gaisuwar tare da tambayarta irin wannan uban kyau haka waye ta yi wa kwalliya. A takaice ta ce "Daddy zan je naga gwaggona, ba zan iya zama ba tare da ita ba!" Ta kai karshen maganar tana yamutse fuska. Kallon mum ya yi yana murmushi kaɗan kaɗan, ya sani, ba wata gwaggon da take son zuwa ta gani, Areef take son ta je ta gani, yana ganinta da asuba da ta ɗauka mashi waya tana kallon hoton Areef ɗin, kawai bai kula ta bane, duk yana ganinsu, kuma ya yi alkawarin ba zai saka baki a maganar ba, idan suka ji uwar bari, za su mayar da kansu kamar yanda suka kawo kansu gidan, nasu wasa ne, har yanzu su yara ne, ba su san sharrin so ba, ita dai Rimsha ga idanu sun kunbura luhu luhu kamar ba lafiya ba, Akila kam ba'a magana. "Mummy ki saka baki mana, daddy ya kaini wajen gwaggona da wuri, Allah ji nake ba zan iya kara minti goma ban kalleta ba". "Gwaggo ko ko Areef surikina zaki je gani?". Mummyn ta tambaya tana ƙoƙarin zuba abincin a cikin plate. Ɗaure fuska ta yi tamkar irin basawan nan, cikin fushi ta ce "Mummy waye kuma Areef?". Galala daddyn ya saki baki yana ganin ikon Allah, Jehan akwai taurin zuciya kamar gwaggon nata, ai wanna yarinyar ba in da ta baro halin Lion, dan shi ma ya ɗauko gwaggon ta wani fannin, kamar taurin zuciyar da sauransu, tana kewar Areef kamar ta mutu a cikin zuciyarta, amma a fili ta wani dake kamar bata ma san shi ba, bayan kuma harda satan hotonsa ta yi tana ta kallo har barci ya ɗauketa. Kawar da zancen mum ta yi da cewa "To zauna mu yi breakfast tukun nan, idan kin ƙoshi, sai a kaiki wajen gwaggo naki ". "Mum nifa ba zan iya cin komai ba tare da na kalli gwaggo ba". Ta kai karshen maganar tana matsowa kusa da daddyn, shi dai sai kallonta yake yi, ƴar karama da ita wai zata yi masu wayo, kamar ba su suka haifeta ba. Mum zata sake yin magana Areef da ya shigo yanzu ya ce "Mum don't west your time, ba zata iya cin abinci ba har sai taga mijinta farincikinta, to gani na zo, nima dai na kasa cin abincin har sai na zo na ganki rigimammiya kawai". Nan take daddaɗar kamshi perfume nasa ya bule ko'ina a palon, fuskarsa ɗauke da murmushi ya kariso cikin palon. Wani irin nauyayyar ajiyar zuciya Jehan ɗin ta sauke tare da sunkuyar da kai kasa tana satar kallon shi, ya yi kyau matuka over, ji take yi tamkar ta je ta rungume kayanta, amma ina jiji da kai ba zai barta ba. Yana karisowa wajen yasa hannu ya ɗan ja kumatunta yana faɗin "Sarkin rigima, da sanyin safiyar nan ma sai kin tasa mum a gaba da rigima ko? To gani nan na zo, sai ki kyale mani mum ɗina ta huta". Harara ta wurga mashi tare da sa kai da nufin ta kowa sama abinta. Cikin sauri ya riko hannunta tare da jawowata jikinsa yana faɗin "Good morning my uncle, mum good morning". Mummy dai kunya ya hanata ta ɗago idanu ta kalle shi, kun san Jehan ce ƴar farinta, ga shi babu kunya Areef ɗin ya zo ya wani rungumeta a gabansu ko a jikinsa, dole mum ta ji kunya, shi kuwa daddy, ko a jikinsa, shi da ya kalli fin haka ma, sau nawa yana kallon Aseef yana ɗaukar Akila cancak a gabansa, sau nawa yana kallon Lion da Rimsha a garden suna sha'aninsu, Areef da Jehan ɗin ma me basu yi a gabansa? Ai shi ya ga komai, dan haka basu wani bashi kunya. "Ni ka sakeni Hai!". Ta faɗa cikin fushi, da tsawa kuma. Saketa ya yi dan shi ma baya son ya ja magana sosai a tsakaninsu, kasancewar yaga mum ta takure waje guda, duk sai ya ji wani iri. Zama ya yi a saman ɗaya daga cikin tables chars ɗin, ita kuma Jehan ɗin ta haura sama da gudu abinta. Miƙewa mum ta yi dan ta basu waje, a cewarta, ba zata iya cin abinci tare da Areef ba, dan yana surikinta, miji ga ƴar fari. Ta zo dai'dai zata hau step na stair case ta haura sama, kamar daga sama suka ji voice ɗin Lion da ya shigo yanzu yana faɗin "Ke where is my wife?".......BABBAR MAGANA, LALLAI LION DA SAURANKA, MUM ƊIN CE KE! KAI LALLAI KUWA. Baki Areef ya saki yana kallon Lion ɗin da mamaki, a cikin zuciyarsa yana faɗin "Yau Lion ne yake cewa ina matarsa? Da bakinsa yake tambayar, bama ina Rimsha ba, ina matarsa kai tsaye? Wato yanzu kenan ya yarda matarsa ce? Kenan ya yarda yana sonta? Lallai kuwa abin da mamaki, ko da yake, dama duk ɗa na halak idan ya ji irin kyautatawa da daddyn Rimshar ya yi wa mahaifinsa, to dole zai so su Rimshar suma, ko dan daddyn nasu, ai dole ma Lion ya yarda da cewa yana sonta, kuma dole soyayyarta ta karu a cikin zuciyarsa over. Sai dai sam Areef ɗin bai ji daɗin yanda har yanzu Lion baya girmana kowa ba, ya shigo musu har cikin Palo, sallama ma kasa kasa ya yi ta yanda babu wanda ya ji, ko sannu bai ce masu ba, babu gaisuwa a matsayinsu na kannen mahaifiyarsa, kawai yana wani yi masu magana tamkar shi ne ubansu, kai Lion har gobe dai akwai izzar bala'i, wato yafi karfin ya ce wa mummy mum ina kwana?! Tab lallai har yanzu da sauran aiki. Shi dai daddy, da yake yasan izzar da ta fi hakan ma Lion zai iya nuna masu, sai bai ce komai ba, idan da sabo, ai ya saba da halinsu. Mum da bata saba ba, sai abin ya ɗaure mata kai, ya yi mata wani irin banbaraƙoi, amma haka ta daure ta nuna mashi a in da ɗakin Rimshar yake. Bai sake cewa da su komai ba, ya wuce ya nufi saman tamkar shi ya gina masu gidan, akwai shi da bala'in nuna isa na wuce misali. Matsa mashi a hanya mum ɗin ta yi, ya wuce abinsa, da kallo suka bi shi, Areef yana mamakin irin tsantsar nuna wannan uban isa na ɗan uwan nasa, tamkar baza'a mutu ba.......... GASKIYA DAGA KAN LION AN RUFE ISA DA IZZA, IN DAI NUNA ISA DA IZZA NE, TO SHI KARSHE NE, SHI FA JI YAKE YI TAMKAR KOWA DOLE YA KASANCE A KARKASHINSA, KUMA DOLE AYI MASHI BIYAYYA, KO ANA SO KO BA'A SO, KAMAR SHI NE UBANSU!!. Bayansa mum ɗin ta bi, ita ma ta haura saman kenan, a in da ta wuce bedroom nata. Rimsha tana zaune a saman tsakiyar bed nata, sai kuka take yi kamar ba gobe, kayan barcin jiya ne a jikinta, wando guntu zuwa santala santalan cinyoyinta, sai ƴar riga mai siririn hannu zuwa cibiya, fararene kal kal kayan, sun yi mata kyau over, gashin kanta a sake, duk ya barbazu kamar mahaukaciya, saboda kukan da ta rinƙa yi tana burgima a saman bed ɗin, shi ne yasa gashin nata ya bazu haka, ko wanka ta kasa tashi ta je ta yi, fuska ta yi jajir kamar tumatir nunanne. A hankali ya turo kofar ya shigo, bakinsa ɗauke da sallama kasa kasa. Kamshin perfume nasa ne ya fara kai mata karo, a zabure ta ɗago kanta tare da kai kallonta izuwa bakin kofar. Ganin da gaske shi ɗin ne yasa ta miƙe da sauri tare da dirowa kasa daga saman gadon, da sauri ta nufe shi da nufin ta rungume shi, ko me ta tuna, sai kuma ta ja birki. Yana tsaye a bakin kofar yana kallonta. Zubewa kasa ta yi a saman gwiwowinta tare da sake rushewa da wani sabon kukan. Yau ga ikon Allah. Ya ɗan ɗauki ƴan mintoci kamar biyar haka, kafin nan ya tako a hankali izuwa cikin ɗakin. A kusa da ita ya tsaya, hannun rigansa ya gyara kafin ya ɗauketa cancak izuwa saman bed ɗin. Zama ya yi da ita a jikinsa, yama rasa me zai ce mata, shi dai bai san kukan me take yi ba, bai kuma san ta ya zai tambayeta ba, sai ya ɗan zuba mata idanu yana kallonta. Goga fuskarta ta fara yi a saman kirjinsa tana ɗan bubbuga kirjin nasa da hannunta ɗaya, tamkar wadda ta aikata mummunar laifi kuma tana babbar danasani. "Meesha". Ya ambaci sunanta a hankali. Kamar jira take yi ya yi magana, cikin kuka ta ce "Yaya Saif me ya kawoka gidanmu? Me kazo yi to? Ni ka tafi!". Tana kuka tana surutan. Jinjina mata kai ya yi tare da sauketa daga jikinsa, ya kuwa mike da gaske zai tafi ɗin, kofar futa ya nufa, yana taku a nutse cikin kwanciyar hankali. Da gudu ta diro kasa daga gadon, ta baya ta zo ta rungume shi tana mai cigaba da kukanta. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya juyo gareta, dama yasan ba zata iya jurewa ya fice daga ɗakin ba, ai yasan irin tsananin son da take yi mashi, da gangan ya nuna mata cewa komawar zai yi kamar yanda ta ce bata son ganin shi. Juyowa ya yi ya rungumota yana ɗan bubbuga bayanta a hankali, alamar rarrashi. Kara saka mashi kuka mai sauti sosai ta yi. Ɗaukarta ya yi suka nufi waje, dan ba zai iya jurar kukan nan nata ba. A haka ya zo ya wuce daddy da Areef a palon, ya nufi waje da ita a saman kafaɗarsa. Kai tsaye sai cikin mota, a gidan baya ya sakata, shi ma ya shiga gidan bayan, Donal ne dama ya ja motar suka zo. Har lokacin sai kuka take zuba mashi. Umarni ya yi wa Donal ɗin a kan ya fita ya basu waje. A hanzarce ya fice. Rungumota sosai ya yi a jikinsa, sai a lokacin ne ya tambayeta meyafaru take yin wannan uban kuka haka. Kankame shi ta yi, ta kasa magana, sai yii, yi, yi, take yi tamkar wata ƴar baby. "Meesha, meyasa kike son sakani a cikin damuwa ne? Kin san halin da nake ciki kuwa a yanzu?". Ya yi maganar yana ɗago haɓarta. Subhanallahi zaro idanu sosai ya yi yana kallon yanda face nata ya dawo saboda kuka, idanu a kumbure. Nan take shi ma face nasa ta sauya, ɗaure fuska sosai ya yi, cikin nuna isa da magana kai tsaye ya ce wani mai karan kwanan ne ya taɓata da har ya sakata wannan irin kuka haka? Meya sameta?. Jin yadda ya yi maganar babu wasa a tattare da shi ne yasa ta tsayar da kukan nata cak, da sauri ta waro jajayen idanun nata waje. Wani irin mahaukacin razana ta yi na ganin yanda fuskarsa take, ya ɗaureta tamau, ya haɗe geran sama da kasa, sam babu wasa ko ɗigo a tattare da shi. Nan take wani irin tsoro ya kamata, dan bata san me zata ce mashi ba, ga shi ya ɓata rai over. Narai narai ta fara yi da idanu. Tsawa ya daka mata a kan wanene ya taɓata? Me aka yi mata da har zata yi irin wannan uban kuka haka?. Kokarin barin jikinsa ta fara yi, dan ta gudu, ta koma cikin gida. Damko wuyar rigar jikinta ya yi, kasancewar rigar ɗan ƙaramin ne zuwa cibiya, sai gabaɗaya tula tulanta suka bayyana a waje. Da sauri ta koma jikin nasa ta kwanta tana mayar da numfashi, nan take ta nemi kukan nata ma ta rasa...... NI KO NACE AU, DAMA ASHE IYA SHEGE NE, DA KI GAYA MASHI ME YA SAMEKI MANA! KIGA YANDA ZAI YI BALL DAKE, DAN WLH IN DAI KIKA CE MASHI BAKI SON SHI NE SABODA DADDYNSA NA CI AMANAR GWAGGON, ZAKI YABAWA AYA ZAKINTA KUWA Wani irin shock ya ji na komawa jikinsan nan da ta yi. Kankame shi ta yi, murya a dashe ta ce "Yaya Saif ni babu wanda ya taɓani". Kai tsaye ya ce karya ne, ta gaya mashi wanda ya ɓata mata rai har ya sakata kuka haka, ko kuma ita ma ya hukunta ta, ya fara ta kanta. Shiru ta yi yana tunanin me zata yi mashi ne ya sauko? Me ya kamata ta yi mashi. Can sai ta ce "Yaya Saif ciwon ciki ne fa yasa nake kuka, tun jiya da daddare cikina yake yi mani ciwo, kuma na kasa gayawa su daddy ne, dan a lokacin suna barci, da safe kuma na kasa iya fitowa waje, kuma muryata bata fita sosai bare na yi kuka da karfi su jini". Hannu ya ɗaura a saman cikin nata. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, hankalinsa ya ɗan kwanta, da ya yi tunanin ko wani ne ya taɓata, da yanzun nan ya karɓi hukunci. Shafa shafaffen cikin nata ya fara yi yana kallon face nata, gam ta datse idanunta, dan ma kada su haɗa ido, sai sauke nauyayyar ajiyar zuciya take yi. Zazzaƙar sexy voice nasa ne ya daki dodan kunne, a in da ya ce mata "Muje gida in dubaki ko? Daga nan kuma, sai ki gaya mani meyasa baki kirani a waya kin gaya mani baki da lafiya ba, meyasa kuma kika fita ba tare da sani na ba?". Kara kankame shi ta yi tana faɗin "Kai NooRi yanzu ai na ji sauki, ni ba sai ka dubani ba, dan kada ka yi mani allura". Matso da ɗan bakinsa saitin kunnenta ya yi, kasa kasa ya ce "Alluran ne baki so?". Jinjina mashi kai ta yi tana kara lafewa a jikin nasa, har ta mance da zancen cewa bata son shi......... Yo ba dole ta mance ba, soyayya wasa ce😂 "Okey to ba zan yi maki ba, dubaki kawai zan yi". "Noorish ina gwaggona?". Ba tare da ya bata amsa ba, ya sanya hannu ya fara tattare mata gashin kanta da yake a watse. "Open your eyes". Ya faɗa a sanyaye. Turo baki ta yi tana ɗan waro idanun nata a hankali. Gyara mata kwanciya ya yi tare da ciro wayarsa, number Areef ya shiga, massage ya rubuta mashi a kan ya fito mata da hijabi. "NooRi ba zaka gaya mani ina gwaggona take ba?". Ta yi maganar tamkar zata saka mashi kuka. Matso da face nasa daf da ita ya yi, kasa kasa ya fara magana kamar mai raɗa. "Ba kin gujeta jiya ba? Dan haka kada ki tambayeni". Ɗan ɗago idanu ta yi tana kallon kyakkyawar sajensa dake a kwance luf, a hankali ta kai hannu tana shafawa. "NooRi waye ya taɓa maka sajenka?". Ɗan zaro idanu ya yi yana kallonta, ko ya akayi tasan an taba oho mata, yarinyar nan ta gama karance face nasa tsab, yanzu taɓa sajen da gwaggo ta yi ma sai da ta gane, kai Rimsha ba dai basira ba, akwai kaifin ƙwaƙwalwa. "Waye ya gaya maki an taɓa sajen nawa?". Turo baki ta yi tana faɗin "Ai nasan ba haka kake gyarawa ba, idan ka gyara ba haka yake kasancewa ba, dole bayan da ka gama gyarawa, akwai wanda ya taɓa shi, nasan yanda gyaranka yake ai". E lallai Rimsha ta daban ce, wato har ta haddace yanda yake gyara shagen nasa. Wani irin daɗi ya ji har cikin zuciyarsa, hakan na nufin yana nan a cikin ranta fiye da komai, tana sane da komai na mijin nata. Tsabar farinciki bai ma san time da ya kara matseta a jikinsa ba. "Wash Noori zaka balla ni fa". Ta yi maganar a shagwaɓe sosai. Ɗago haɓarta ya yi tare da manna mata sumbata a ɗan bakin nata, buɗe bakin nata ta yi, da ɗan karfi ta cije shi a lips nasa. Tsareta da ido ya yi ba tare da ya ce komai ba, ga face nasa kuma tamkar hadari, a ɗaure tamau. Ganin hakan yasa ta yi ƙoƙarin sake cizon nasa. Bata kai ga sakewa ba Areef ya yi masu knocking na glass ɗin motar. Da sauri ta ɗago kanta, ganin Areef ne yasa ta yi ƙoƙarin barin jikin Lion ɗin. Bai hanata ba, sai ma sauke glass ɗin motar da ya yi ya karɓi hijabin nata. Juyawa Areef ɗin ya yi ya koma cikin gida, shi kuma Lion ya miƙa mata hijabin a kan ta sanya, da sauri ta karɓa ta sanya. Umarni ya yi wa Donal a kan yazo su tafi. A hanzarce ya dawo cikin motar tare da kunnata suka bar gidan. Lokacin da suka dawo gida, da gudu Rimshar ta wuce ɗakinsu, dan tana tunanin gwaggo tana can, sai da ta shiga, taga bata nan, da sauri ta dawo izuwa ɗakin Lion, nan ma bata nan, ɗakin daddynta ta nufa kai tsaye, a nan ta sami gwaggo kwance a saman bed, ta gama cin abinci ta yi wanka. Da gudu ta haye saman bed ɗin tana dariya, shi kuwa Lion, juyawa ya yi ya fice izuwa harabar gidan gabaɗaya. Miƙewa gwaggon ta yi zaune, nan ta rungumo Rimshar suka fara hira, labari Rimshar ta fara bata na abubuwan da suka faru a baya, har da aurensu da Lion, irin rayuwar da suke yi da shi, da tafiyarsu ƙasar Russia da suka yi, sai dai ko kusa ko alama bata bata labarin Daular Mutuwa ba, da alama an shafe mata labarinsa a cikin brain nata. Sosai gwaggon ta yi mata nasiha a kan kula da miji, sannan ta kara mata da cewa, tun da har haka ne, to Lion yana sonta, dan Allah ita ma ta nuna mashi soyayya sosai, ta ga akwai ciwo sosai a cikin rayuwarsa, ta kula da shi, a yanzu tana a sahun gaba cikin mutanan da suke saka shi farinciki, dan Allah ta kasance mai saka shi farinciki sosai. Gabaɗaya sai Rimshar ta ji jikinta ya yi sanyi, ba shakka akwai ciwo sosai a cikin rayuwar TRIPLETS, ga kuɗi, ga mulki, ga mukami, ga isa da izza, ga kyau, dukka Allah ya hore masu, amma kuma tun suna cikin mahaifiyarsu suke fuskantar jarabawa, babbar bala'i ce tashi da girma cikin kafurci, hakika ba kowa da kake kallon cikin Daula na ɗumbin dukiya bane bashi da damuwa da matsaloli na rayuwa, kowa da kowa yana iya fuskantar jarabawar Ubangiji ta kowace siga a kuma lokacin da baka yi tsammani ba, so yana da kyau mu runƙa kyautatawa al'umma zato, mu kuma mayar da hankulanmu a kan abubuwan da suke gabanmu, kada mu sakawa wani mai ɗan arziki idanu, dan bamu san halin da yake ciki ba, mu kyalkyalin arzikin kawai muke gani, amma na ciki, tana ciki, Allah ka bamu dacewa, ka kuma bamu ikon cin jarabawarka a duk lokacin da ka jarrabemu. Sosai Rimsha ta ji jikinta ya yi sanyi, ta kuma yi wa gwaggon alkawarin zata yi iyaka bakin kokarinta wajen ganin ta sanya Lion farinciki. Tambayarta gwaggon ta yi a kan ina Lion ɗin yake, shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Nima ban san ina yake ba, lokacin da muka shigo dai na barshi a palon sama". Ɗaga idanu gwaggon ta yi, ta kai kallonta a saman katafaren agogon bango da yake manne a jikin bangon ɗakin, karfe 11:30 dai'dai, dawo da kallonta a kan Rimshar ta yi tana faɗin "Rimsha ashe fa mun ɗan ɗauki lokaci muna hira fa, labarin naki ne akwai tsawo, yanzu dai jeki ki duba mani Saif ɗin nan, bai ci abincin safe ba, ki kai mashi abinci ya ci dan Allah". Ta yi maganar cike da nuna kulawa ga ƴaƴan nata. To Rimshar ta amsa da shi tare da miƙewa, ta sauko kasa daga saman bed ɗin, waje kai tsaye ta nufa. Tana fita ta wuce bedroom nasu. Wanka ta tsala tare da zuba shirinta cikin wandon jeans fari tas da T-shirt pink color, ta ɗaure gashin kanta a tsakiyar kai tare da zubo jelar a bayanta, ta yi matuƙar kyau tamkar ita ta yi kanta. Perfume nata ta zuba, nan take ta fara zuba kamshi tamkar ba gobe. High heel ta sanya a kafarta, sannan ta nufo waje. A palo ta kalli ɗayar wayarta a saman sofa, cikin hanzari ta ɗauki wayar ta nufo palon kasa. Kitchen ta nufa ta ɗauko abincin Lion tare da ficewa da sauri. Garden ta nufa da abincin, dan tana tunanin zata same shi a wajen, sai dai ina baya nan, ta sha ruwan mamaki sosai. Saman table ta ɗaura kayan abincin tare da zama a saman sofa ta ciro wayarta. Numbersa ta kira, wayar ta yi ringin har ta katse bai ɗauka ba. Turo ɗan baki ta yi tare da sake kiransa, nan ma shiru bai ɗauka ba. A kule ta ɗaga wayar zata buga da kasa, ƴar kara wayar ta yi alamar shigowar sako. Cikin sauri ta fasa bugata da kasa tare da buɗe sakon. Cool murmushi ta saki ganin sunan Noorinta, tun bata ga me sakon ya kunsa ba. A hanzarce ta buɗe ta fara karantawa kamar haka. "Idan kika fasa wayar nan, babu mai saya maki wani, ke da waya har abada ƴar rigima kawai". Shi ne abin da ya rubuta mata a sakon. Ta sani sarai ba wai yana kallonta bane, kawai ya riga da ya san hali ne, ya san abin da zai biyo baya idan bai ɗauki kiran ba, ya san rigimarta sarai, shi ne yasa ya yi mata sakon tun wuri. Juya dara daran fararen Sleeping eyes nata sama ta yi, har wani walwali suka yi, ɗan girgiza kai ta yi tana magana kasa kasa ta yanda ita kaɗai zata san me take faɗa. "Allah Noorin nan nawa ya rainani da yawa". Shi ne abin da take faɗa. (E lallai Rimsha kin girma, wai NooRi ya rai'na ta?🤔 Ba shakka kin ga gadon kwanan Lion, dole ki ce haka😂) Shi kuwa, sai da ya gama ja mata rai son ransa, sannan ya yi mata massage a kan ta zo boys quarters na gidan ta same shi. Da kamar ba zata je ba, dan ta yi fushi na shanyata da ya yi tun ɗazun tana jiranshi. Sai kuma ta tuna cewa bai ci komai ba bawan Allah, yunwa yake ji ga kuma ɓacin ran da ya shiga. Tuna hakan yasa ta ɗauki abincin na nufi wajen. Shi ma bene ne mai hawa ɗaya, babu wanda ya taɓa kwana a wajen, komai na cikin wajen sabbi ne. Bakinta ɗauke da sallama ta shigo cikin palon kasan. Babu kowa sai sanyin Ac da kamshin air freshener da kuma kamshin perfume ɗin na Lion ɗin dake tashi. Haurawa sama ta yi, sai aikin turo baki take yi. Bakinta ɗauke da sallama ta shiga bedroom ɗin da ta ji kamshin perfume ɗin nasa ya fi yawa a ta wajen. Yana kwance saman bed, daga shi sai ƴar wando short zuwa kaɗan daga cinyoyinsa, ga wandon ya kama shi sosai, ya manne da fatar jikinsa, ba dan kalar wandon da yake fari ba, da ba zaka taɓa tunanin ma ya saka ba, saboda mannewa da jikinsa da ta yi. Sai dai ya ja bargon dake saman bed ɗin izuwa kugunsa. Da alama wanka ya yi, dan ga gashin kansa da akwai danshin ruwa. Daga ta sama kuma, yana sanye da ƴar riga mara nauyi, irin waɗan nan T-shirt ɗin masu laushi sosai, sannan masu kananan hannu. Tun da ta shigo ya tsareta da waɗan nan dara daran idanuwan nasa masu rikitarwa yana kallonta, tamkar zai cinyeta. Ta yi kyau ne over, ji ya yi tamkar ya tashi ya rungumota. Ita kuwa, sai aikin turo mashi ɗan bakin nan nata take yi, ita a dole tana fushi. A tsakiyar Chinese carpet dake a cikin bedroom ɗin ta ajiye abincin. Zama ta yi a gefen abincin ba tare da ta kalli in da yake ba, ta fara magana "Yaya Saif sannu da hutawa, ga abinci nan na kawo maka, ka zo ka ci dan nasan kana jin yunwa". Nisawa ya yi yana mai cigaba da kallonta, bai ce komai ba. Almost 10 mins suka ɗauka a haka, bai ce mata ko sannu ba, yana ta kallonta, ita kuma taki ɗagowa su haɗa idanuwa. Da ta ga bashi da niyar motsawa, sai ta miƙe tana kumbura kumatu ta nufi waje, ta ki yarda dai ta kalli in da yake. Ko sannu bai ce mata ba. Har ta fice daga cikin ɗakin. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da jawo wayarsa, ya yi mata massage a kan ko taku ɗaya bai yarda ta kara ba a wajen tafiyarta, ta juyo ta dawo. Tana gama karanta sakon ta zunduba ihu tamkar wanda aka kwalawa itace a tsakiyar kai, haushi kamar ta je ta shakesa, ga shi bata isa ta ki zuwa ba, dan idan har ta kara taku ɗaya ɗin ta shiga tsinuwan Mala'ikun Allah ne, har sai time ɗin da ta zo ta bashi hakuri ya kuma yafe mata, sannan Mala'ikun za su dai'na tsine mata, wannan babban musifa ce bijirewa maganar miji, ko ba daɗi ayi hakuri a bi, shi ne zaman lafiya!!!. Juyowa ta yi tana kuka da hawaye bibbiyu, da farko tafiyar yanga take yi ta kawo abincin, yanzu kuwa jan kafar take yi tana kuka dan haushi. Yana kwance in da yake, bai motsa ba. Gaban bed ɗin ta zo ta tsaya, kusa da shi, tana kuka, bata ce mashi ko kala ba. Hannu ya kai ya jawota ta faɗa jikinsa, gyara mata kwanciya ya yi izuwa saman faffaɗar kirjinsa, ɗago haɓarta ya yi ya fara lashe hawayen da ya sa suka zubo ɗin. Duka ta fara kai mashi a kirjin nasa tana faɗin "Allah Noori mun ɓata". Ta yi maganar a shagwaɓe. Kara matseta a jikin nasa ya yi tare da matse ɗan bakin nata, kasa kasa ya ce ta yi shiru ya gaya mata wani abin mai daɗi. Jin hakan yasa ta yi shiru tana shesshekar shagwaɓa tare da kumbura kumatu. "Meyasa kika cika rigima ne?". Ya faɗa a sanyaye. Turo baki ta yi bata bashi amsa ba. "Don't you know that you're my happiness? You know how sad I was before you came here? Kin san da na kalli face naki ya naji kuwa?". Da sauri ta ɗago tana faɗin "Ya ka ji to?". Lumshe idanuwansa ya yi, dan yanda ta ɗago fararen idanun nan nata, ba ƙaramin tafiya da shi suka yi ba, dan yanda ta ɗagosu, har wani walwali wal wal suka yi mashi. "NooRi to ka gaya mani ya ka ji mana?". Tana magana tana shafa lallausan bakin gashin dake kwance a hannunsa da yake rungume da ita. Bai amsa mata ba, kuma bai buɗe idanuwansa ba. Sake tambayarsa ta yi tare da saka mashi kukan shagwaɓa. Ba tare da ya buɗe idanuwansa ba, ya matso da ɗan bakinsa sai tin kunnanta, murya kasa kasa kamar mai raɗa, sai ka rantse da Allah baya motsa laɓɓansa, cikin wata iriyar murya mai tsayawa a ran masoya ya fara yi mata raɗa idanuwansa a lumshe. "Kina shigowa cikin bedroom nan, ina ganin beautiful face naki, sai na ji na mance komai, i feel like ban taɓa jin wani ɓacin rai ba, you're special!". Da sauri ta zaro idanuwanta tare da juyowa da kallonta izuwa kan face nasa sosai. Idanuwansa a lumshe, magana yake yi cike da class tare da izza, cikin kuma kwanciyar hankali da nutsuwa, a ko da yaushe babu ko ɗigon na hayaniya a cikin voice nasa, so silent zaka ji ta, bare kuma yanzu yanda yake magana kasa kasa, ya kuke tunanin muryar zata kasance? Hmmmm...... Hakika ya ji tsakanin kaunarta a ransa sosai saboda gwaggo, saboda yanda babanta ya kula da gwaggon, a haka ma bai san cewa Gwaggon ta fi son su Rimshar sama da kowa a cikin ƴan uwanta ba, wata kila idan ya san hakan, ko kasa ba zai bari Meeshar tasa ta sake takawa ba, saboda so........ Mu dai je zuwa, uwa ai ba wasa ba, bare su da suka ɗauki tsawon shakaru 31 zuwa 32 basu tare da ita, ai dole su so duk abin da uwar tasu take so fiye da tunanin mai tunani. Yau wani irin jin Rimsha yake yi a cikin ransa fiye da misali!. Sosai ta zuba mashi idanu tana mamakin kalaman da yake yi, tamkar wanda ake gayamawa. Idan a baya ne ka ce mata ya iya wannan kalamai, ba zata taɓa yarda ba, babu ma wanda zai yi gigin yarda, ko TRIPLETS nasa ba za su taɓa yarda da cewa shi yake furta kalamai haka ba. Duk da idanuwansa a rufe, a jikinsa ya ji tana kare mashi kallo, hakan yasa ya ɗaga mata gera ɗaya. Wani irin sihirtatcen kyau ya kara, ga gashin gerar nasa kullum kara cika suke yi sosai, tamkar ana saka masu taki, har ta kusa haɗe mashi, gasu a kwance luff, kyakkyawar jajir ɗin kumatunsa, wani irin laushi ne da su kamar fatar jariri, sai kyalli soft skin nasa take yi sosai da sosai, dogon hancin nan nasa, tamkar shi ya bawa kansa saboda yanda ya zauna ɗas a face nasa, sak hancin Dr William, lips nasa kuwa, ba'a magana, dan gabaɗayansu TRIPLETS Allah ya yi masu halittar lips mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali, lips nasu na saman design of heart ne, na kasan kuma yana da ɗan faɗi kaɗan, gasu jajir dasu tamkar an saka masu red janbaki, ga laushi kamar fure, ga ɗan bakin nasu ɗan karami da shi, sai dara daran idanu tamkar na Dr Salman. "Noorish, meyasa nake sanyaka farinciki idan ka kalleni?". Sai a lokacin ya waro idanunsa a kanta. A cikin idanunta ya kalli tsananin son ya ce yana sonta da take yi, tana tsananin so ta ji kalmar so daga bakinsa. Shiru ya ɗan, kafin ya ce "Ni ma ban san dalili ba, kawai dai idan na ganki, ina shiga farinciki". Wani irin yawu ta haɗiye, dan ba hakan take son ji daga gare shi ba, amma ba komai. Shi ma yasan ba hakan take son ji ba, tana so ne ta ji ya ce saboda yana sonta, da gangan ya bata wani amsa da ban, yana tsananin jin daɗi idan yana ja mata rai. "Noorish kazo ka ci abinci". Ta faɗa a takaice. "Meesha saboda ban baki amsar da kike so bane zaki nuna mani baki son cigaba da yin hira da ni?." Girgiza mashi kai ta yi tana sunkuyar da kanta ƙasa. "To meyasa zaki nuna kin gaji da hirarmu?". "Noorish ni fa nafi son ne ka ci abinci, gwaggo ta ce mani baka ci komai ba, to ka zo ka ci ga ji?". "Meesha meyasa kike koyan yin karya ne?". Zaro idanu ta yi tana kallon wuyarsa. "Yau sau biyu kina yi mani karya, ɗazun kince mani ciwon ciki ne ya saka ki yin kuka, kuma ba haka bane, na san ba haka bane, kewata ce ta saki kuka, duba da yanda action naki ya kasance lokacin da na shigo cikin bedroom ɗin naki, wanda cikinsa yake ciwo, har ya kasa yin kuka da karfi su dad su ji su kawo ɗauki, ba zai diro kasa daga saman gado da gudu har ya nufoni zai rungumeni ba, yanzu kuma kin sake yi mani karya na biyu, why?". "Noorish kenan kasan cewa ina sonka?". Ta tambaya tana hawaye, dan bata taɓa tunanin duk abin da take yi yana sane ba. Ɗago haɓarta ya yi yana goge mata hawayen, yana faɗin "Na sani mana, na san duk irin haukar sona da kika yi tun kina ƴar shekara tara har izuwa yau, kuma nima ai ina sonki ki sarkin rigima". Da sauri ta waro idanunta waje, har tana haɗe word wajen cewa "Noorish da gaske kana sona?". Jinjina mata kai ya yi yana faɗin "Yeah, i really love you so much, shikenan kin ji amsar da kike son ji?". Cusa kanta a cikin kirjinsa ta yi tana dariya, kamar ba ita ce mai zubar da hawaye a yanzun nan ba. Zuba mata idanuwa ya yi yana kallon irin tsantsar farinciki da yake a kan fuskarta. "Noorish to tun yaushe ka fara so na kai kuma?". Ta yi tambayar tana ɗan ɗago kanta. Shiru ya yi almost na tsawon 2 mins, sannan ya ce "Actually i don't know wen, amma dai abin da na sani, kin fara burgni tun time da muka tafi Russia, and ban yarda da hakan ba sai jiya, zuwa yau kuma na yanke hukunci". Lafewa ta yi a kirjin nasa tana ta sauke uban ajiyar zuciya. Zazzaƙar sexy voice nasa ne ya daki dodan kunnenta. "Ba zaki bani gift bane My Meeesha?". Da sauri ta ɗago kai tare da manna mashi sumbata a lallaudan kunatunsa. "Ya yi maka haka?". Ta tambaya tana kallon lallausar wuyarsa. Kin amsa mata ya yi, dan bata yi mashi ba, Iya sumbata kawai zata bashi? Gaskiya baya so, so yake yi yau da kanta ta yi kissing nasa. Jin ya yi shiru ne yasa ta fahimci sumbatar bai yi mashi ba kenan. "To Noorish ka rufe idanunka, sai na baka wani, tun da wannan bai yi ba". "Me idanuna suka yi maki da sai na rufe? Ina ruwanki da su?". Kuka ta saka mashi tare da komawa ta lafe a saman kirjin nasa. Shiru ya yi bai tankata ba, sai ma yatsa da ya sanya mata a cikin bakin nata. Da taga shi fa ba zai rufe idanu ba, da gaske yake yi, ya fi son ya ga komai abinsa, dan bai san kunya ba. Sai ta ɗago kai tana turo baki, sai wani kumbure kumbure take yi, ko kala bai ce mata ba, ido kawai yake binta da shi. Saƙalo wuyarsa ta fara yi, sannan ta matso da face nata dab da nasa, datse idanunta ta yi, tana ƙoƙarin fara kissing ɗin nasa ne ya dakatar da ita, tare da ce mata idan dai ba zata buɗe idanu ba, to shi baya so. Bata da zaɓi, dole da waro idanunta waje, dan furta kalmar i love daga bakin Lion ba karamin abu bane, bai taɓa faɗenta ga kowa ba bayan TRIPLETS nasa, sai mommansu a yanzu, to ba karamar kalma bace, dole a bashi tukuici mai kyau. Lips nata har kerma suke yi wajen fara kissing nasa, yana ta kallon cikin idanunta, ko motsawa bai yi ba, Allah ya gani yana matukar kaunar waɗan nan Sleeping eyes ɗin nata, suna narkar mashi da zuciya, sai ma idan ta tsorata a kan abu, ta zarosu, habawa, har rasa nutsuwarsa yake yi, sai azababen sha'awarta ta motsa mashi idan ya gansu tana a cikin tsoro. Sosai ta yi kissing nasa, sannan ta zame bakinta daga nashin, da sauri ta yunkura zata bar jikin nasa. Rikota ya yi tare da tambayarta a ina ta koyi kiss kuma?. Galala ta saki baki tana kallonsa, shi fa ya koya mata abu, amma dan neman magana yake cewa a ina ta koya. "Kai mana ka koya mani". Ta bashi amsa a takaice. "Ni na taɓa kissing naki ne?". Zaro idanu sosai ta yi, ta rasa ma me zata sake ce mashi. Tsawa ya daka mata tare da sake tambayarta a ina ta koyi kiss, dan shi bai taɓa kissing nata ba. Nan take ta tsorata, ta zaro idanu, jikinta har ya fara kerma. Rungumeta sosai ya yi tare da juyawa da ita, ya zamana ya yi mata rumfa da kirjinsa, dama burinsa kawai ya tsoratata, dan ya kalli abin da yafi kauna a tattare da ita, wato Sleeping eyes nata a cikin tsoro. Kissing nata ya fara yi babu kama hannun yaro, dan wannan tsorata da ta yi, ta saka ya shiga cikin yanayi, dole ya fanshe jefa shi da ta yi a ciki kuwa.............NIMA DOLE NA HAƊA KAYANA NA YI GABA, WANNAN LAMARI YAFI KARFINA🥳🧐 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* *💔SORRY FOR TODAY PAGE🧠🥺💔*. E7 Kissing nata ya fara yi babu kama hannun yaro, dan wannan tsorata da ta yi, ta saka ya shiga cikin yanayi, dole ya fanshe jefa shi da ta yi a ciki kuwa, kankame shi ta baya gam ita ma ta yi. A hankali ta fara mayar mashi da martanin kissing nata ɗin da yake yi. Hannu ya kai saman wuyar rigarta, a hankali ya yi ƙasa da wuyar, tare da fara shafa breast nata, sannan ya zame ɗan bakinsa daga nata da nufin ya mayar kan nipples nata. Tamkar jira take yi ya zame bakin nasa, ta ce "Noorish akwai camera a ɗakin nan ko kuma babu?". Cak ya tsaya da abin da yake yi mata, a hanzarce ya ɗago da idanunsa da suke jajir da su kamar wuta. Mikewa zaune ya yi yana sauke numfashi a hankali. Sosai ta tsorata, dan tana tunanin ko tambayar da ta yi mashi ne yasa ya rabu da ita. "Sorry Noorish". Ta faɗa tamkar zata yi kuka. "Meesha let's go". Ya faɗa tare da mikewa da sauri. A hanzarce ta ce "Noorish dan Allah ka tsaya na tambayeka". Yana ƙoƙarin shiga dressing room na ɗakin ya bata amsa da cewa yana jinta. "Na ji gwaggo ta ce yaranta masu blue eyes irin naka su biyu ne, amma kuma naga kai kaɗai ne a cikinku mai blue eyes". Cak ya tsaya, ya fasa shiga cikin room ɗin, a dubu ya juyo da kallonsa a kanta. Zaro idanu ta yi, jikinta har ya fara kerma, dan tana tunanin ta faɗi abin da ya ɓata mashi rai ne. Shi kuma mamakin ta yake, ya sani a gabaɗaya cikin palon, gabaɗaya waɗan da suke wajen time da gwaggon ta bada labarin, babu wanda ya lura da zancen da gwaggon ta ce na cewa masu blue eyes biyu, dan da sun lura, dole zasu tambaya, amma saboda kaifin ƙwaƙwalwa irin na Rimsha, ita har ta rike cewa su biyu ne masu blue eyes, lallai akwaita da basira, wato tun jiya ma abin yana cikin ranta, ta rasa waye zata gayawa ne kawai. "Kayi hakuri Noorish, ban ɗauka maganar zata saka ka ji babu daɗi ba". Girgiza mata kai ya yi yana faɗin "No baki ɓata mani rai ba, you are special My Meesha". Ya kai karshen maganar tare da karisa shiga cikin room ɗin. Shiru ta yi tana tunani, har ya fito sanye da jallabiya fara kal a jikinsa. "Let's go". Ya faɗa tare da miƙa mata hannu alamar ta zo gare shi. Da sauri ta diro kasa daga saman bed ɗin, a hanzarce ta tafi ta faɗa jikinsa tana sauke ajiyar zuciya. "Meesha pray for me more kin ji ko?". Yana magana yana shafa kanta izuwa bayanta. Gyaɗa mashi kai ta yi tana faɗin "In Sha Allah mijina, addu'a sosai zan yi maka". Hannunta ya riko tare da ɗan raba jikinsu, har lokacin idanuwansa suna nan jajir da su, yau ya so ya yi romancing nata over, amma kuma tasa ya tuna da wani abin, dole ya je ya aiwatar da abin da wuri, dan dama tun jiya abin da yake ta tunani a kansa kenan, yanzu tasa ya samu kaso talatin cikin ɗari na abin da yake nema. Da sauri ya nufi hanyar fita daga ɗakin hannunsa na ruke da nata. Mamaki take yi a kan meya faru yake sauri haka. Bai zame ko'ina ba sai ɗakin gwaggo. Zaune ya iskota ita da Aseef, sai kukan shagwaɓa yake zuba mata, ya haye mata gado tare da tada kai da cinyarta, shi dole sai an ɗauko mashi matarsa, ta ce ya yi hakuri tun da sun kira Areef a waya ya ce zai zo da ita, to ya dai'na kuka zata dawo, kwafa ya yi tare da gayawa gwaggon Allah yau ba zai kyale Heartbeat ɗin nan ba, sai ya bata wahala fiye da tunanin kowa, ita dai gwaggon, sai rarrashi kawai take yi. A gefenta ya zauna, tare da zaunar da Rimshar a gefensa. Cikin sanyin murya ya ce "Momman i want to ask you something!". Dawo da kallonta a kansa ta yi tana faɗa mashi tana jinsa. "Momma a wani gidan kaka ɗaya kika kaiwa daddy mu time ɗin? And them a wani gida kuka zauna da Josephine?". Ba tare da ɓata lokaci ko wani dogon tunani ba ta bashi amsa kai tsaye, dan bata manta komai ba, komai yana nan a cikin brain nata. Wayarsa ya ɗauko, cikin sauri ya kira Tyrone, dan dama already Tyrone ɗin ya koma shi kam. Bugu ɗaya ya ɗaga, ba tare da ɓata lokaci ba ya ce mashi ya je gidan da su Dr William ɗin suka zauna, dan gidan yana nan yanda yake, babu abin da aka taɓa a ciki tsawon shekarun nan, sai ma zuwa da ake yi ana gyara shi kowani sati, so komai yana nan normal, dan haka Tyrone ya je gidan da akwai camera a palon gidan, ya ciro mashi camerar yanzun nan, ba tare da ɓata lokaci ba, sannan ya shiga ainahin computers room da yake cikin gidan, ya duba stories, ya ɗauko mashi memory na shakaru 31 zuwa 32 baya. Okey Tyrone ya amsa da shi. Katse kiran ya yi tare da miƙewa ya nufi waje, bin shi da kallo dukkansu suka yi, harda Rimshar. Sai bayan ya fita ne Rimshar ta ce "Yaya Aseef ni ka tashi mani a saman cinyar gwaggona zan kwanta". Kin kulata ya yi, sai aikin tura baki yake yi abinsa. Gwaggon ce ta ce mata ta zo ta kwanta a gefe, ta rabu da Aseef ɗin nan, rigima yake ji dashi, yanzu ya tashi barci, ko breakfast bai yi ba, ya tsayar masu da rigimar sai an ɗauko mashi Akila. Tuna cewa Lion bai ci komai bane yasa ta miƙe tare da cewa Gwaggon a'a tana zuwa dai. Ɗakin da suka fito ta koma, abinsa ta ɗauko mashi, sannan ta dawo cikin bedroom nasa. Zauna a saman bed ta iskosa, ya sanya laptop a gaba yana ƙoƙarin kunnata. A saman carpet ta ajiye abincin, sannan ta dawo kusa da shi ta zauna. A tsananin shagwaɓe ta ce "Noorish, idan baka jin yunwa, Meeshan ka fa tana jin yunwa, ban fa ci komai ba, kuma ni da kai nake son muci abinci". Yanda ta yi maganar tasa bai san time da ya juyo gateta ba. Yana juyowa ta faɗa jikinsa tana zuba mashi shagwaɓa. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, wani irin sanyi ya ji a ransa, hannu ya kai ya shafi kanta, ƴar karama da ita, amma ta samu tarbiya sosai, ta kuma iya soyayya sosai, duk fushi da halin mara daɗi da mutun zai shiga, ta san ta yanda take kwantar mashi da hankali, yanzu ga shi dai a kage yake da ya fara binciken nan, har ya mance da cewa yana jin yunwa, amma daga zuwanta, ta zuba mashi shagwaɓa, har ya ji yunwar ta dawo sabuwa, sai ya ji hankalinsa ya kwanta sosai. "Muje to na baki abincin a baki ko?". Ya faɗa a sanyaye. Da sauri ta ɗago kanta, tana ƙoƙarin ta yi magana, sai ga Brady ya shigo ɗakin da gudu. Kai tsaye ta kanta ya bi ya haye jikin Lion ɗin, da alama bai ma lura da ita ba. Ihu ta zunduma tana ƙoƙarin ta gudu, rikota da sauri ya yi, sannan ya dakawa Bradyn tsawa a kan ya sauka mashi a jikinsa, zai haukata mashi ƙwaƙwalwar Meeshansa, yasa tana zunduma ihu haka. Haushi Bradyn ya daka masu, irin ya ji haushin nan shi ma. Hannu Lion ɗin ya ɗaga zai mare shi, ai a dubu ya diro kasa, da gudu ya nufi waje, dan ya san marin Lion fa ba wasa ba, ya taɓa marinsa sau ɗaya, a lokacin ya yi mashi ɓarna, ya kuwa wanke shi da mari, to shi ne har yanzu bai mance da marin ba, da Lion ɗin ya kara marinsa, gara ya gudu abinsa. "Kin cika tsoro Meesha, Brady is your friend, ki dai'na tsoronsa, babu abin da zai yi maki, kuma shi ba zai dai'na shigowa nan at anytime ba, yakamata ki saba". Ya kai karshen maganar tare da ruko hannunta suka mike tsaye. Wajen abincin suka nufa. Ita ta zuba masu abincin a plate. Spoon ya ɗauka tare da ɗebo abincin, yana ƙoƙarin kaiwa bakinsa, ta yi maza ta kwace tare da fara tauna. Ko sannu bai ce mata ba, ya sake ɗebo wani ya kai bakinsa. Haka suka cigaba da cin abincin cikin nishaɗi da tsantsar farinciki. A ɓangaren gidan Abba kuwa, bayan sun tashi da safe, su daddyn Anaya sun zo, haɗuwa suka yi a palon gidan Abba, sai hira suke yi, suna jiran gwaggo da TRIPLETS nata, sai daddyn Rimsha, zasu yi magana ne a kan abubuwan da suka faru a baya. Sai hira suke zubawa kamar ba gobe. Can wuraren karfe 12, daddyn Rimsha, mummy, Areef da kuma Jehan da Akila suka zo gidan. Nan fa hira ta kara armashi, abin ba kama hannun yaro. Brr Naurat ce ta dakatar da su ta hanyar gabatar masu da Alex duk da cewa baya wajen, yana gidan Lion, a kage suke da son ganinsa, amma bai zo ba, yana tare da Mark. "Zahradeen ina matanka da ƴaƴanka?". Cewar Brr Naurat, ta tambayi Abbi kenan. Cikin girmamawa ya nuna mata, Aunty, Irfan, da kuma Umaisha da take a wajen, sai ya rufe da cewa Aafia tana gidan mijinta. Murmushi Brr ta yi tare da zuba masu addu'a da ruwan albarka, sannan ta tambayi Abba ma, shi ma haka ya gabatar da nasa matar da ƴaƴan, haka shi ma ta zuba masu addu'a, sai da ta bi gabaɗaya ƴaƴan nata ta tambayesu, daddyn jelly shi ne na karshen da ta tambaya. Kallon Jelly dake zaune kusa da Ammie ta yi shiru kamar wata mara lafiya ya yi, cikin sanyin murya ya ce "Wannan ita ce kaɗai ƴata, Allah ya yi wa mahaifiyarta rasuwa, sai matar da na aura a yanzu". Ya kai karshen maganar yana juye juye dan neman Ayla, bata a wajen sam. Fuska ɗauke da mamaki ya ce "Sadiya ina Ayla take?". Da sauri Aunty ta ɗago kai tana ƴan waige waige, sam babu ita a cikin palon. Tambayar juna suka fara yi, kowa yace tun safe shi bai ganta ba. Abba ne ya ce jelly da Akila su tashi su je su dubata a ɗakunan gidan, wata kila tana can tana barci ne saboda ciki. A hanzarce suka miƙe suka haura sama. Suna tafiya Abbi ya ce "Hossain me ya sami Akila a idanunta kuma?". Girgiza kai daddyn Rimsha ya yi yana faɗin "Kuka ta yi mana". "Kukan me kuma?". Daddyn jelly ya tambaya da sauri. Zai sake yin magana su Akilar suka sauko suna gaya masu bata cikin ɗakun dukka sun duba, har a cikin toilet dukka sun duba bata ciki. Nan fa hankulan kowa ya tashi, wannan ya kalli wannan, wannan ma ya kalli wannan. Kasancewar da turanci suke magana, sai Areef ma ya saka masu baki, dan ya ji komai da suka ce, da turanci suke yin magana, saboda Brr Naurat bata wani iya hausa ba, Hausan nata a kwaɓe yake, dama bata iya shi sosai ba, sai kuma ta sake komawa ƙasar Russia tsawon shekaru, hakan tasa ɗan Hausar da ta iya ma shaf ta gudu daga bakinta, shi ne yasa suke magana da English. Mikewa suka yi gabaɗayansu, harabar gidan suka fito, duk suka rarrabu aka fara nemanta. Amma ina, shiru, babu ita babu alamarta, nan take mamanta ta fara kuka, dan ita ma tana wajen, daddyn Jelly tamkar zuciyarsa zata fashe, amma ya daure suka cigaba da nemanta. JAMA'A INA AYLA TA SHIGA⁉️ Shiru shiru fa babu ita, Areef ne ya tambayi daddyn Jelly a kan ko ta ce mashi zata je wani waje ne ya hanata, shi ne ta yi tafiyarta, nan fa ya yi masu bayani, ita Ayla bata da kowa, bata san kowa ba face su Abbi, sai su Rimsha, kuma ko harabar gidansu bata taɓa fita ba tare da shi ba, kullum tana ɗaki abinta, idan kunganta a waje, to a tare suke za su fita unguwa, ita ko waya ma yanzu bata da shi, saboda cikin nata ma ya tsani ana latsa waya a kusa da ita, dan haka in dai Ayala bata gidan nan, to wlh hannu ne ya ɗauketa, tabbas ɗaukarta aka yi!!. Tashin hankali!!! Shiru Areef ɗin ya yi kafin ya sake cewa "To waye kake tunanin zai ɗauketa? Shin kana da abokin gaba na bayyane ne?". Jinjina masu kai ya yi yana faɗin "Baban Muneer, shi ne kawai abokin gaba na wanda ya yi niyar ɗauke Jelly ya haɗata aure da Muneer a lokacin baya, to bayan shi kuma, ni bani da wani abokin faɗa". "Waye baban Muneer ɗin? Kuma a ina yake?". Areef ya sake tambaya. Kasancewar daddyn bashi da burin da ya wuce yaga matarsa ta dawo, sai ya basu labarin tsamar da take a tsakaninsu da baban Muneer ɗin, bai ɓoye masu ba, harda videon da ya yi mashi na sharri duk ya gaya masu. "Aina yake to yanzu?". Areef ne ya sake tambayarsa, nan ma basu amsa ya yi da shi dai a Kano ya barosa, so bai san a ina yake ba yanzu. Kallon Imran Areef ɗin ya yi yana faɗin "Zamu je wajen yanzu ko prof?". Jinjina mashi kai Imran ɗin ya yi. Nan take hankulan kowa ya kara tashi, ganin da gaske Ayla fa ta ɓata ne, babbar magana. Areef, Imran, da kuma Irfan ne suka nufi Kanon tare da tallafawan daddyn Jelly da ya basu number wayar babban yaronsa, wato engr Muhammad Imam, a kan idan sun je Kanon su nemesa, zai yi masu karin bayani a kan wanene Baban Muneer, zai ma kaisu har companynsa. Da farko daddyn Jelly ya ce da wuya idan baban Muneer ɗin ne ya ɗauketa, dan shi a Kano yake, sai da Areef ya gaya mashi cewa, ai zai iya turowa a ɗauko mashi ita, dan wlh mai son abinka, ya fi ka sanin hanyar kula da shi, dan ya ɗauka, shi ne sai hankalinsa ya yarda a kan hakan. Da kyar Abba ya lallaɓa matan suka koma cikin palo, su kuma mazan, wato su Abbi, sai suka fita gari nemanta, ko Allah zai sanya a ganta, daga nan su kai report station da sauransu........NIMA PRINCESS TEEMA INA TAYAKU DA ADDU'AR ALLAH YASA A GANTA ƊIN, AMMA ƁATAR AYLA BA KARAMIN ABU BANE, DAN DOLE DAI HANNU NE YA ƊAUKETA, SABODA BAIWAR ALLAH NAN KO HARABAR GIDA BATA FITA, TO WAYE YA ƊAUKETA? ALLAH SARKI, GA KARAMIN CIKI, GA UBAN LAULAYI. A ɓangaren Lion kuwa. Bayan sun kammala cin abinci, Rimsha ta kwash kayan abincin ta fitar, ta gyara wajen tsab, sai ta dawo ta haye saman bed nasa, a kusa da shi ta kwanta, tare da lumshe idanu, ba jimawa barci ya yi awon gaba da ita, saboda daren jiya bata samu damar runtsawa ba. Shi kuma Lion, yana can yana aikin latsa laptop nasa, Tyrone ya ɗauko mashi wannan memory da camera ta naɗi komai, sai dai, da kyar aka samu memoryn, dan ma dai babu nai shiga gidan nan, kuma dama ana ajiye storyn camera irin haka sosai, so suna nan a ɗakin computers ɗin, an dai ci kwakwa ne kafin a nemosu. Miƙewa Lion ɗin ya yi tare da ficewa daga bedroom ɗin. Ɗakin gwaggo ya koma, tambayarta ya je ya yi a kan zata iya tuna ranar da abin ya faru a tsakaninta da Dr William, ma'ana ranar da ta kai mashi TRIPLETS ɗin gidansa. Cikin sauri ta ce ai bazata taɓa manta wannan rana ba, biyu ga watan biyu ne. Jinjina mata ya yi da ƙoƙarinta na ruke komai na tsawon shekaru a kanta, sannan ya juya ya koma bedroom nasa. Cewa Tyrone ɗin ya yi da ya saka memoryn a laptop, ya duba mashi videon biyu ga watan biyu a shekaru 32 baya. Okey ya amsa mashi tare da fara aikin babu kama hannun yaro. Cikin ƙanƙanin lokaci ya samo video ya turowa da Lion ɗin. A hanzarce ya buɗe video, dan dama jira kawai yake yi. Shiru ya yi ya zubawa video idanu yana ganin komai kamar a gaske a gabansa ake yin komai. Tun daga shigowar gwaggon gida, tun wayewar garin ranar, har shigowar gwaggon da TRIPLETS ɗin, yanda ta faɗa, ga yanda ta kwantar da su a saman sofa, komai da komai yana gani kamar a zahiri. Dai'dai lokacin da Dr William ya bugawa jariri ɗaya santa, sai da Lion ɗin ya datse idanunsa, saboda har cikin ransa ya ji saukar wannan sandar, babu irin azabar kalolin kisa da Lion bai gani ba, amma ba zai iya jure gani ko ɗan ƙaramin bulala ne ya taɓa TRIPLETS nasa ba, shiyasa lokacin da ya ga Dr ya kwalawa ɗaya ɗaga cikinsu sandar, sai da zuciyarsa ta amsa, ji ya yi tamkar shi aka bugawa. A hankali ya waro idanunsa ya cigaba da kallon video, yana ganin gwaggo ta fice waje da gudu, shi kuma Dr William ya yi kan yaran da gudu bayan ya jefar da sandar, ita ma Josephine da gudu ta kariso cikin palon. Ɗaukar jaririn Dr ya yi, da gudun gaske ya nufi waje da shi, sai zubar da jini kansa yake yi, kai tsaye asibiti ya nufa shi da Uncle Herry, ita kuma Josephine, kan sauran jarirai biyun ta nufa, da sauri ta ɗauko ɗaya ta ruke a hannunta tana shafa ɗayan da yake kwance a saman sofar da hannunta, dan ta tabbatar da lafiyarsu. Sai ruwan hawaye take yi. Kamar daga sama wani mutun ya faɗo cikin palon, wani dogo da shi, yana sanye da bakaken kaya, long cut ce baka a jikinsa, daga ta cikin kuma T-shirt ce mai karamar hannu, ita ma baka, ya sanya wata hula mai gashi a kansa, fuskansa na a sanye da black mask, hannayensa dukka biyu suna sanye a cikin hands gloves bakake kirin suma, kafarsa na'a sanye cikin Booth baka kirin, baka iya ganin komai na daga jikin mutumin nan fa ce idanunsa da suke ashe color masu tsananin haske kamar glass, tamkar ba na mutun ba. Hannunsa na ruke da jariri sabon haihuwa cikin towel baka kirin, ga jaririn fari kal da shi, kasancewar yana jikin bakar towel ga shi fari kal, sai ya haska sosai. Kai tsaye Josephine mutumin ya nufa, yana zuwa ya miƙa mata jaririn da yake a hannunsa, karɓa ta yi, ita kuma sai ta miƙa mashi ainahin cikon TRIPLETS da yake a hannunta, tana yi tana shafa kan baby ɗaya da yake kwance. Juyawa mutumin ya yi da ainahin cikon TRIPLETS ɗin a hannunsa, ta kofar da ya shigo, ta nan ya fita, ita kuma Josephine, sai ta cirewa jaririn da mutumin ya kawo waɗan nan bakaken kayan da suke jikinsa, sai ta ɗauko wani towel fari daga cikin ɗaki ta rufe shi da shi, sannan ta kwashi bakaken kayan ta nufi waje da su. Jim kaɗan ta dawo, kusa da jariran ta dawo ta zauna tana kare masu kallo, babu wanda zai iya banbanta su, babu wanda zai iya cewa su ba TRIPLETS bane, wancan ɗin ya saje da ɗayan. Wani irin datse idanuwansa gam Lion ya yi da karfin gaske, tamkar zai fashe idanun nasu, karo na farko a rayuwarsa da ya fara danasanin gani abu, da ya sani, da bai kalli video nan ba, dan wlh ba zai taɓa yarda ace ɗaya daga cikinsu ba cikon TRIPLETS nasa bane, da bai kalla ba, da ya rufe maganar sun tafi a haka har su mutu, ba zai iya taɓa rabuwa da ko ɗaya daga cikin TRIPLETS nasa na yanzu ba, yau an zo gaɓar da ya kasa, ba zai iya ba. Toma a cikinsu wanenen jaririn da mutumin nan ya kawo? Kuma ina shi wanda aka ɗauka? Me aka yi da shi? Meyake faruwa ne? Josephine ta sadaukar da shi kenan? Ko yaya ne? Wanne ma wannan mutumin? Meyasa dukka hakan ta faru?. Wannan shi ne tashin hankali. Cikin tsananin zafin rai Lion ɗin ya ɗauki laptop ɗin ya makata da jikin bangon ɗakin, ji kake yi war, ta tarwatse, dafe kansa dake yi mashi barazanar tarwatsewa ya yi, cikin fitar hayyaci ya miƙe tsaye, wani irin azababben jiri yake gani, duniya juya mashi take yi, gara ace mashi mutuwa ɗaya daga cikinsu ya yi da wannan bakin abin da ya gani, wlh sai dai ya rufe maganar nan, amma ba zai taɓa iya rabuwa da Areef ko Aseef, su ne bugawar zuciyarsa, shi kam ya yarda sune TRIPLETS na sa, a bar mashi su kawai........ Ba shakka da akwai ciwo na wuce misali a cikin rayuwar TRIPLETS tamkar yanda Malika ta gayawa Rimsha a baya, to a hankali dai ga shi abubuwa sai bayyana suke yi, mu je zuwa dai, ku kasance da PRINCESS TEEMA, dan ni kaɗai ce zan iya warware maku wannan babbar al'amari, kun dai ga abin da Dr William ya karyata na cewa bai san gwaggo ba, to ga gaskiya ta fito, ga komai kamar yanda gwaggon ta faɗa!! Lallai akwai wani abu wai shi ruɗanin kwakwalwa a cikin TRIPLETS!!. Waje ya nufa, sam baya ganin gabansa, dan wani irin jiri da uban duhu da yake gani, ji yake tamkar zai haɗiye zuciya ya mutu kawai ya huta. Ɗakin gwaggo ya nufa, da hannu biyu dukka ya dafe kan nasa da ƙarfin gaske, yana tafiya yana huci tamkar ransa zai fita, iska mai tsananin zafi ce take fitowa daga bakinsa, ya ilahi ya lillahi!!. Da sauri gwaggo ta mike tana tambayarsa lafiya. Ina ai bai kai ga karisowa in da take ba, ya zube kasa wanwar, baya numfashi!. A dubu gwaggon ta kariso wajen da yake kwance, shi ma Aseef da yake kwance yana aikin zuba shagwaɓa, a ɗari ya sauko daga saman bed ɗin, bai ma san time ɗin da ya iso wajen ɗan uwan nasa ba. Sunansa suka fara kira babu kama hannun yaro, ina ko motsawa bai yi ba, tamkar rai ne ya yi halinsa. Fridge Aseef ya nufa da sauri. Ruwa mai bala'in sanyi ya ɗauko, tsabar shiga tashin hankali har kerma jikinsa yake yi, da kyar ya iya ɓalle bakin robar ruwan. Tashin hankali ya hana shi ma ya iya tarbo ruwan a hannunsa, da bakin rofar ya fara zazzagawa ɗan uwan nasa, ita kuma gwaggo, sai ambatar sunansa SAIF!! SAIF!! SAIF! take yi. Tas Aseef ɗin ya zazzaga mashi ruwan, amma ina ko motsawa bai yi ba. Ganin duk wannan uban ruwa mai bala'in sanyi da ya zuba mashi bai farka bane yasa ya zunduma uban ihu tare da fara jijjiga shi da karfi yana kiran sunansa da ya tashi, kada ya mutu ya barsu, ba zai iya rayuwa babu shi ba, dan Allah ya tashi. Wannan ihun da ya zunduma ne yasa Uncle T ya shigo ɗakin a guje. Ganin abin da yake faruwa ne yasa ya kariso ciki da sauri. Sai kuka Aseef yake yi tamkar ransa zai fita, bawan Allah!. Babu ɓata lokacin TGA ya naɗe hannun rigar jikinsa tare da sanya karfi ya saɓi Lion ɗin a kafaɗarsa, kai tsaye sai waje ya nufa. Da sauri suka rufa mashi baya. Bai tsaya tambayarsu me ya faru ba, kawai ya sanya shi a cikin mota tare da bawa Mark umarnin a kan ya ja su zuwa asibiti. Kafin su gwaggon ma su iso harabar gidan, har Mark ya tashi motar. Gabaɗaya sojojin da suke gidan, kowa ya nufi sauran motocin dake cikin gidan dan su rufa masu baya. Donal Aseef ya kira cikin kuka, ya ce mashi ya ɗauko mota su bi su TGA, sai ringin wayar Aseef ɗin take yi, amma ina hankalinsa baya a tattare da shi, kuma Areef ne yake kiransa, dan ya kira wayar Lion yafi sau a kirga, amma bai ɗauka ba, shi ne ya kira Aseef ɗin dan ya ji ko lafiya, saboda a jikinsa yana jin tamkar basu lafiya, kamar akwai wani abin. Amma ina Aseef ɗin ma yaki ɗaukar kiran, shi burinsa kawai Lion ya tashi....... MASU KARATU, WANNAN SHI NE ASALIN CAKWAKIYA, LITTAFIN TRIPLETS YANZU ZAI ƊAUKI ZAFI JAU KAMAR WUTA, KADA KU MANTA BOOK 4 MUKE, KUMA SHI NE LAST IN SHA ALLAH, TO MUNA FATAN AYI KOMAI A NAN A GAMA, HAR KULLUM PRINCESS TEEMA TAKU CE TA AMANA.💋 Gwaggo babu ko mayafi a kanta, daga ɗankwalin doguwar rigar jikinta, shikenan, haka ta bi su a motar Donal ɗin. Bayansu TGA suka bi, Uncle Herry kuwa, yana can yana kula da Dr William, bai ma san abin da yake faruwa ba, John da Jay kuwa basu ma a gidan gabaɗaya, sun tafi yawonsu!. Rimsha sarkin rigima, tana can tana barci ga Noorish nata tamkar rai ya yi halinsa! WANNAN KENAN, ABIN DA YAKE FARUWA A GIDAN LION, BARI MU LEƘA GIDAN ABBO, WATO WAJENSU DR NAWID, WATA KILA KAFIN MU DAWO, ABUBUWA SUN ƊAN YI SANYI, GIDAN ABBA BA SAUKI, AYLA TA ƁATA, GIDAN LION KUMA YA MA KAMA DA WUTA BAL, BAL NE MA GABAƊAYA, SABODA BALA'IN TASHIN HANKALI DA SUKE A CIKI, TO BARI MU JI GIDAN ABBO KUMA KO DA ƊAN SAUKI SAUKI. GIDAN ABBO. Gabaɗaya familyn Abbo, wato Ummi, Dr Nawid da Aafia, suna a cikin tsananin tashin hankali, suna tsaka mai wuya, yau tsawon kwana uku kenan Dr Nawid yana kwance rai a hannun Allah, ko motsawa baya yi, ga idanuwansa a buɗe garau, amma baya iya ko motsawa, likitoci daban daban Ummi ta kira, amma kowa ya zo, sai ya ce babu wani abin da yake da munsa, su basu ga ciwon komai ba, ga shi Abbo dai baya nan, shiru babu shi babu labarinsa, haka Ummi ta daure ta fara shirye shiryen fitar da Nawid ɗin kasar waje. Abin da ya faru shi ne, suna tsaye a kitchen suna aiki shi da Aafia, ranar bai je office ba, sai ya bita kitchen yana tanaya aiki kamar dai yanda suka saba, sai zuba soyayyarsu suke yi kamar ba gobe, bawan Allah lafiyarsa lou wlh, babu ko ciwon kai a tattare da shi. Haka kawai ya yanke jiki ya faɗi kasa, sai wani bakin ruwa ya fara fito mashi daga bakinsa, abin ya yi mugu mugun girgiza su Ummi, Aafia ba'a magana, ta yi mummunar rama yarinyar nan, dan kun sani, tun farkon littafin nan, tana bala'in son Dr Nawid, Ummi kuwa, shi kaɗai ne ke gareta, bayan shi bata da wani yaro, dole ta shiga tashin hankali na wuce misali, bayin Allah, wannan shi ne abin da ya faru. Sai shirin fitar da shi kasar waje suke yi. Yau ta kasance ranar Friday, bayan an sauko daga sallar jumma'a, Aafia tana zaune a gefensa a saman bed nasu, ta yi mashi alwala dan ya yi sallah ko da da idanu ne, dama haka take yi mashi kullum, tana yi mashi alwala idan lokacin yin sallah ya yi, ita kuma Ummi bata nan, tana gidan Abbin Irfan, dan suma sun san abin da yake faruwa, Abbin ne ma yake shirya masu fita kasar waje dan neman lafiyar Nawid ɗin, so ta je su yi magana da Abbin. Shiru Aafia ta zauna tana ta kallon mijin nata, shi kuma sai kallon sama yake yi, dan ko juya idanun nasa ma baya iya yi. Hawaye masu matuƙar zafi ne suke gangaro mata daga cikin idanunta, duk ta bushe ta yi wani irin baki tamkar mai cutar kanjamau, sai idanu kawai zaka gani dara dara a face nata, duk wanda ya ganta sai ya matsa mata kwallah. Yau tsawon kwana uku Dr baya motsawa, ta yi nisa cikin tunanin da take yi, kamar daga sama ta ji voice nasa yana faɗin "Aafia ba zan tashi ba, mutuwa zan yi, ki yafe mani idan na taɓa yi maki wani laifi, sannan ki roka mani gafara a wajen Ummi, ta yafe mani, ina tsananin sonku, amma ba zan rayu da ku ba, sannan ki sani wannan cuta da ta kamani........" Bai kai karshen maganar ba ya sake yin shiru ɗiff tamkar an ɗauke wutar nepa. Tun da ya fara magana, a tsakanin razane Aafia ɗin ta ɗago tana kallonsa, still idanuwansa suna kallon sama, sun kafe, bai iya motsasu, kuma bakinsa ma bata motsawa, kawai dai ga muryarsa nan tana fitowa ana magana da ita, amma sam sam babu wata gaɓa da ta motsa daga jikinsa!. Toh fa!! Ta tsorata sosai na ganin hakan, sunansa ta fara kira, Yah Nawid, Yah Nawid, amma ina shiru bai amsa mata ba, tana ƙoƙarin ta sake yi mashi magana, sai ta ga idanuwansa sun sauya color izuwa purple eyes. Zaro idanu sosai waje ta yi, tamkar idanun nata za su fito su faɗi kasa, tana ƙoƙarin gudu ta sauka kasa, sai ta sake ganin idanun nasa sun sake sauyawa izuwa bakin kirin, babu ɗigon fari ko kaɗan a cikin idanun nasa, wani irin hayaki ne mai matukar warin gaske ya fara fitowa daga bakinsa, bakin ruwa mai kaurin gaske ya fara zuba mashi daga hancinsa, haka zalika kunnuwansa ma hayakin ne ya fara fitowa. Wani irin uban ihu ta zunduma tare da sauka kasa da uban gudun gaske, a dubu ta nufi waje. Tamkar zararriya haka ta bazama izuwa harabar gidan, dai'dai lokacin kuma motar Ummi ya danno kai, ta dawo daga gidan Abbi, ta je ma bata samu ganawa da shi ba, saboda suna cikin tsananin tashin hankali na ɓatar Ayla, so suma yau ba'a zaune suke ba. Ganin yanda Aafiar ta fito a gigice tana zunduma ihu ne yasa Ummi ta dakatar da motarta ba tare da ta karisa parking space na gidan ba. A hanzarce ta fito daga cikin motar, Aafia kuwa bata ma bi ta kanta ba, ta nufi waje da gudu, tamkar ƙwaƙwalwarta ya taɓu ne, da alama ta zauce. A hanzarce Ummin ta ce mai gadi ya rufe gate ɗin, kada ya bari ta fita, sannan ta yi maza ta rikota tana ambatar sunanta, amma ina banda wannan ihu da take zunduma, babu wani abin da take yi. Da kyar Ummin ta jata izuwa cikin palo, ɗaki ta sakata ta rufe kofa, sannan ta ɗauko wayarta, cikin tsananin tashin hankali ta kira Abbi dan ta sanar da shi abin da ta zo ta tarar a gidan again. Ta yi sa'a ya ɗaga kiran, bayan ta gaya mashi, sai ya ce mata to Akil yana zuwa yanzu, daga haka suka yi sallama, sannan ta kira ƴan uwanta a Katsina ta gaya masu halin da yau kuma suke a ciki. A palonta ta zauna, ta kasa shiga ta sake duba Aafiar, shi dama Dr Nawid bata san me yake faruwa da shi ba, bata san me Aafiar ta gani ta haukace haka ba, baiwar Allah, tana zaune ta buga uban takumi tana jin yanda Aafiar take yi mata watsi da kayan ɗaki har Akil ya kariso. Tana ganinsa ta miƙe a hanzarce tana kara yi mashi bayanin abin da yake faruwa. Ina Aafiar ya tambaya, da sauri ta nuna mashi ɗakin da take, ba ɓata lokaci ya nufi cikin ɗakin. Yana buɗe kofar Aafiar tana gefo mashi kwalbar perfume a goshinsa, nan take ya fashe wajen, jini ya fara tsastsafa. Salati Ummin ta fara yi, komai na cikin ɗakin Aafiar ta yi watsi da shi, har kayan jikinta ta cire, ya rage daga ita sa underwears, suma sai ƙoƙarin ciresu take yi. Sam Akil bai damu da ji mashi ciwo da ta yi ba, karisawa cikin ɗakin ya yi tare da yin bismilah ya damkota da karfi, kokawa ta fara yi da shi da iya karfinta, shi ma saka karfi ya yi sosai ya murɗe hannayenta izuwa baya, sannan ya kaita kasa, dan ta kwanta, hakan zai taimaka mashi wajen danneta ya yi mata addu'a. Ummi kam ban da kuka babu abin da take yi. "Ummi jeki waje". Cewar Akil ɗin, dan ya lura idan bata bar wajen ba, ba zata dai'na kukan ba. Jiknta har kerma yake yi ta koma palo ta zauna. Shi kuma ya fara tofawa Aafia ɗin adduo'i har barci ya ɗauketa a wajen. Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali na ganin ta yi barci, runtse idanuwansa ya yi yana tunanin meyake shirin faruwa da FAMILYNSU ne? Ayla ta ɓata, gwaggo ta kira waya cikin tsananin tashin hankali ta sanar masu Lion yana asibiti tamkar babu rai a tattare da shi, yanzu kuma ga Aafia ta haukace, anya kuwa ba wani gagarumin bala'in bane yake shirin afkuwa? Anya lafiya kuwa? Meyasa kuma dukka abubuwan a lokacin guda rana ɗaya?! Sannan a hankali abubuwan suna ta shafar kowa da yake a cikin familyn? Wai shin menene gaskiya? Waye zai warware mana wannan rikicin?........ Alkalami PRINCESS TEEMA ce kawai zai warware maku menene ainahin abin da yake shirin faruwa dama wanda yake faruwa a yanzu, ku dai ku kasance tare da ni!!. Ganin ta yi barci ne yasa ya saketa tare da fitowa palo wajen Ummi, har lokacin sai kuka take yi, hakuri ya bata tare da tambayarta ina Dr Nawid yake bari ya duba jikinsa, sannan zai wuce gida da Aafiar dan a ragewa Ummin wahala. To kawai ta ce mashi, sannan ta wuce gaba zuwa ɗakin Dr Nawid ɗin, bayanta ya bi cike da tausaya mata. Baki ɗauke da sallama suka shiga, yana kwance tamkar yanda yake kullum, idanuwansa sun koma yanda suke, kamar basu taɓa canza launi ba, wannan hayaki da Aafia ta gani ta zauce, duk sun dai'na fita, komai ya ɓace, ya koma kamar yanda yake. A gefen gadon Ummi ta zauna, shi kuma Akil ya matso kusa da shi da nufin ya tofa mashi adduo'i. Kallo ɗaya ya yi mashi ya san cewa rai ya yi halinsa, babu rai a tattare da shi. Zaro idanu ya yi, sannan ya kalli Ummi dake ta faman ruwan hawaye, nan take zuciyarsa ta karaya, ya ji ba zai iya gaya mata cewa Dr Nawid ya rasu ba, dan shi ne kaɗai gareta, idan ta ji zuciyarta zata iya bugawa wlh, Innallilahi wa Innallilahi ilaihir raji'un, hasbunallahu wani'imal wakil. Daurewa ya yi ya tofawa gawar addu'a, sannan ya ce mata yana zuwa, to kawai ta bishi da shi. Fitowa waje ya yi ya kira Abbi a waya, ya sanar mashi wlh Dr Nawid Allah ya yi mashi rasuwa, Allah ya karɓi abinsa. Ba karamin girgiza Abbin ya yi da jin wannan bakin labarinba, dukkansu Ummin kawai suke tausaya, baiwar Allah, da ma ace tana da wasu yara ne, to da da sauki, amma shi kaɗai, ga shi Allah ya karɓi abinsa, innallilahi wa innallilahi ilaihir raji'un, yanzu ta yaya za su iya gaya mata wannan bakin labarin? Matar da kullum take zarya a kan rashin lafiyar nan tasa, ko abinci bata iya ci, ta rame fiye da tunanin mai tunani, duk ta fita a cikin hayyacinta, ta firgice kamar ba ita ba, ashe maganar da Dr ya yi wa Aafiar nan shi ne maganarsa ta karshe a duniya, ya ilahi ya lillahi. Cewa Akil ɗin Abbin ya yi a kan suna zuwa yanzu, amma kada ya bari Ummin ta gane komai. Okey ya amsa tare da katse kiran ya dawo cikin palon. After some minutes sai ga su Abbin sun iso, har da Abban Imran da daddyn jelly, shi dai Abbo shiru babu shi babu labarinsa, kuma babu wanda ya iya tunawa da shi. Wayo suka yi wa Ummin, suka ce mata za su tafi da Dr wani asibiti ne mai kyau kafin komai na su ya kammala su wuce kasar India, dan haka ta bi Akil ya kaita gidan Abba ita da Aafia, dan kada a barta ita kaɗai a gidan. Ita dai ta amsa masu da to ne kawai, amma har cikin ranta tana jin ba lafiya ba, gabanta sai faɗuwa yake yi, sai dai bata musa masu ba, ta bi Akil bayan an saka Aafia a motar, haka ya wuce da su izuwa gidan Abba, su Imran kuma, sun ɗauki hanyar Kano dama already. Suna tafiya su Abba suka kira jama'a, aka yi wa Dr wankar gawa irinta addinin musulunci, sannan aka shirya shi a cikin likkafani, dan su kai shi makwancinsa kuma gidansa na gaskiya......... To masu karatu zan dakata a nan wajen, sai Allah ya kai mu gobe. *Yau na san kwakwalwarku zata shiga ruɗu sosai, to ina mai bada hakuri a kan hakan, labarin ne yake a haka, dole kuma zan rubuta abin da na tsara tun farko, ba zan iya canza komai na labarina ba, na san ba zaku so hakan ba, amma ina bada hakuri dai!!* ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E8 Suna tafiya su Abba suka kira jama'a, aka yi wa Dr wankar gawa irinta addinin musulunci, sannan aka shirya shi a cikin likkafani, dan su kai shi makwancinsa kuma gidansa na gaskiya. A takaice su Abbi suka kai shi kabarinsa, ma'ana su suka yi jana'izarsa, sai dai duk cikinsu an rasa wanda zai iya gayawa Umminsa ga abin da yake faruwa, sai faman nuku nuku suke yi, dan suna tsananin tausayawa baiwar Allah'n nan. A ɓangaren su Imran kuwa, sun isa Kano lafiya, kuma sun haɗu da baban Muneer a companynsa, a cikin office nasa, ya yi masu iso. Ba tare da ɓata lokaci ba Areef ya fara jefa mashi tambayoyi, sai dai Areef ɗin da kallo ɗaya zaka yi mashi, kasan yana cikin tsananin tashin hankali, duk da bai san abin da yake faruwa da Lion ba, amma a jikinsa yana jin lallai ba shakka ɗaya daga cikinsu bashi da lafiya, dan bugawar zuciyarsa sauri take yi tamkar yanda na Lion ɗin take bugawa da sauri, duk ya firgice tamkar ba shi ba, har Imran ya iya ganewa, ya tambaye shi ko bashi da lafiya ne? Ko kuma tafiyar da suka yi a mota mai tsayin ne ya jijjiga shi?. A'a ya amsa masu da shi, sannan ya ɗaura masu da cewa, shi ai idan ya je kasar da bai sani ba, yana yin tafiya mai tsawo a cikin mota, dan ya zagaye wasu daga cikin states na garin, dama dai Aseef ne ko Lion, sune za'a ce ba lallai su iya jure tafiya mai tsawo a mota ba, dan basu saba ba, ko'ina za su je, to wlh suna zaune a cikin gida, basu fita yawace garinma bare sauran states dake makwabtaka da garin, amma shi ai yana yawo sosai abinsa, su kwantar da hankulansu, kawai dai yana jin jikinsa ba daɗi ne. Bawan Allah bai san cewa Lion yana kwance a gadon asibiti ba, kuma kamar yanda yake kwance bashi da lafiya, haka shi ma Areef ɗin yake tafiya da ciwo a jikinsa, da alama zuciyoyinsu a haɗe take over. Kafe masu baban Muneer ya yi a kan shi bai ma san waye daddyn Jelly ba, kallon Imran Areef ɗin ya yi, sai ya yi mashi magana da larabci a kan, su kyale shi da mutumin bari ya gyara mashi zama!. Da baban Muneer ɗin yaga za su matsa mashi, sai ya ɗauko wayarsa ya yi ƙoƙarin ɗaura videon daddyn Jelly da ya ɗauke shi a media kowa ya gani, ya yi ƙoƙarin cin zarafin familyn Dr Salman kenan. Ganin yana latsa wayar jikinsa har wani kerma yake yi, ga shi kuma sai musa masu yake yi a kan shi bai san wanenen ma daddyn Jelly ba, sai yasa Areef a cikin tunani. Duk cikin office ɗin, cikin Imran da Irfan babu wanda ya lura da abin da baban Muneer ɗin yake yi, shi kuma Areef ya lura da lallai ba abin arziki yake yi da wannan wayar tasa ba, dan kuwa ga jikinsa sai kerma yake yi, hannunsa sai ɓari take yi, dama haka mara gaskiya yake, duk in da za'aje a zo, baya ɓuya. Shammatarsa Areef ɗin ya yi ya fusge wayar da karfi, har wani miƙewa baban Muneer ɗin ya yi tare da nufin ya kwaci wayar, wani irin wawan mari Areef ɗin ya ɗauke shi da shi, nan take hakwaransa biyu suke fita daga bakinsa. Tsawa ya daka mashi a kan ya koma ya zauna, idan ba haka ba, yanzun nan ya yabawa aya zaƙinta, an gaya mashi su sha'anin wasan sa ne?. Ƙoƙarin gudu ya yi ya fita daga cikin office ɗin, Areef yana daga zaune yasa kafa ya kwashe kafafunsa, sai ga baban Muneer ya zube a kasa wanwar yana baza babbar riga, ya yi shiga ta mutunci tamkar mutumin kirki, ashe dai babbar rigar ce kawai. "Prof ɗaure mani shi mu tafi da shi, dan jikina duk a mace, i can't do anything yanzu, ina son in je gida first, dan haka mu wuce da shi gidan kawai". Cewar Areef, yana maganar yana duba wayar baban Muneer ɗin. Ganin abin da yake cikin wayar na shirin yin posting na video a media da ya yi ne ya kara ɓatawa Areef ɗin rai, sannan ya kara mashi shakku da zargin baban Muneer ɗin a cikin zuciyarsa, idan ba rashin gaskiya ba, menene na yin yunkurin posting na video daga tambayarka ina Ayla? Da farko ma cewa ya yi shi bai san daddyn Jelly ba, to a ina ya samo wannan video kuma? Ga shi dai daddyn Jelly ne a cikin videon. Ƙoƙarin kurma ihu baban Muneer ɗin ya yi, dan ma'aikatansa su kawo mashi agaji, sai dai ina, bakinsa ma ya yi muguwar kumbura, saboda hakwaransa guda biyu da suka fita, ga jini da yake malala kamar me, kun san hakori ba wasa ba, fitarta akwai azaba ga zubar da jini, bare ma shi da hakwaran suka fita ba shiri, dama gasu ba kyan gani, duk sun yi baki, saboda busar sigari, nan take bakin ta sunduma suntum, tamkar ruɓaɓɓen alala. "Areef ni fa ba zai iya ɗaura mutumin nan ba, wannan aikin sai ku". Cewar Imran. Harara Areef ɗin ya wurga mashi, da dara daran ldanun nan nasa, kafin ya ce "Prof ba zaka canza ba har gobe, ka yi auren ma baka gyaru ba?". Shi ma hararar ya wurga mashi yana faɗin "Kai kam da ka yi auren ka gyaru ne? Ko dama akwai wanda ya ce maka aure yana gyara mutun ne? Kai ma ai gaka a yanda kake da shegen mugunta kamar Saif, yanzu kawai ka kama ka cirewa mutun hakwara da mari, dan tsabar zafin zuciya". "Ka dai'na cewa kamar Saif, just call me Saif ɗin kawai kai tsaye, kuma ni ai ban san me auren bane shiyasa ban gyaru ba, amma kai fa? I think ma your wife has pregnant ma ko?". Cewar Areef ɗin. "A'a Jelly bata da ciki, muna dai fatan samu, kai ba zaka dai'na saka mani ido ba ko? Wai waye ma ya gaya maka ni ma na san menene aure?". Allah sarki shi dai Irfan, sai binsu da idanu kawai yake yi, yana ɗan murmushi, dan bashi da ta cewa, bai ma san me auren ba bawan Allah. "Ka san aure mana, kai ne ma kasa na fara sha'awar yin auren". "Ni kuma?". Ya faɗa yana zaro idanunsa irin na Jellyn nasa. "Yeah kai mana, ko na tuna maka wen aka yi hakan ne?". Ganin abin kamar wasa Imran ɗin yake yi, sai ya ce "Yeah tunan mani". "Time da ka yi dis virgin na matar taka a gida, a time ɗin ka fara saka mani sha'awar yin aure, and then yan da kuke da matar taka, rigimammiya mara jin magana, tana baka wahala, abin yana yi mani daɗi, ina jin daɗin in ga tana wahalar da kai". Ya kai karshen maganar yana switch off na wayar baban Muneer ɗin. "Wato Areef har gobe ba zaka canza ba ko Areef? Sai mutun ya kalli kamar baka san meyake faruwa ba, amma ka san komai, wato yanzu duk zaman da na yi da Jelly a gidan kasan komai ko?, Amma ban taɓa tunanin haka ba, sai mutun ya ganka kamar wani malamin islami, har ma jin daɗi kake yi idan Jelly tana wahalar da ni ko?". Mikewa ya yi yana ɗan bincika cikin office ɗin ko zai samu igiyar da zai ɗaure baban Muneer ɗin, yana tafiya yana faɗin "Ni ai har abada ba zan canza ba, an gaya maka C.I.A wasa ce? Ai ni da ido ma idan naga mutun nasan ina ya dosa, just kawai kai ne ba zaka gane nasani ba, saboda already basaja a cikin jinina take, zan iya yi maka basaja kamar mace, kuma mu zauna da kai a haka". "Da wannan murɗaɗɗen jikin naka ne zaka iya zama macen". Cewar Irfan, ya yi maganar da mamaki a kan face nasa, ya ga ne damatsan hannun Areef ɗin ma kawai abin kallo ne, sannan ga shi da tsawo da cikar halittar namiji, sannan ya ce mashi zai iya basaja a matsayin mace? Ai dole ya tambaya da mamaki a saman face nasa, dan ba gym na wasa shi ma Areef ɗin yake yi ba, jikinsa ta murɗe sosai. "No Irfan, idan nace basaja a matsayin mace, ba ina nufin zan ɗauki kayan mata or something like that in yi amfani da su ba, you are not a C.I.A, that's why ba zaka gane ba, i mean zan iya zama da kai cikin raunin zuciya like mace, you will feel like bani da wayo, ina da raunin zuciya, and ina da ragonta, like yanda mace dai take, shi ne nufina". Jinjina kai Irfan ɗin ya yi, sai yanzu ya gane nufin Areef ɗin. "Kai Prof waye ma ya ce ka ɗauka mani matata jiya ka tafi da ita? Na baka izini ne?". Ya yi maganar yana bubbuɗe drawers dake a cikin office ɗin na wajen ajiyar takardu. "Waye ya ce maka ni na ɗauke ta?". Harara ya sake wurga masu kafin ya ce "Ban samu peace of mind a daren jiya ba har sai da na bincika a motar waye ta biku, na san Lion ma ya bincika, kuma sai ka yi mashi bayanin dalilin da yasa ka kwashe mana bebs namu, ka hanamu jin daɗi". Dariya sosai Imran ɗin ya yi, sannan ya ce "Ka ce jiya na ɓata maka harka? To ni nama san ta biyo ni ne". "Ka dai ɓatawa Aseef harka, kuma wlh ba zai kyaleka ba, dan tun safe yake rigimar a bashi matarsa, kuma tun jiya da safe ya gaya mani ba zai kyaleta ba, idan suka dawo daga unguwa, sai ya yi dis virgin ɗinta, shi ne ka rusa mashi shirinsa ba? Zaku haɗu ne wlh, kasan halinsa, ni matata yarinya ce ai, sai ta girma, zan dai yi ta tsokanarta". Wani irin dariyar iyashege Imran ɗin ya yi yana faɗin "Au dama haka aka yi? Kace Allah ya kuɓutar mani da sisterta, baiwar Allah, da yanzu tana can tana fama da azaba, da Aseef ya wahalar mani da ita". "Au kai ba sister tamu ka azabtar ba kenan?". Cewar Areef Shi dai Irfan tamkar babu shi a cikin office ɗin, shiru abinsa, sai binsu da idanu yake yi, sai da ya ji sun shigo da hirar Akila da Aseef ne ya ji zuciyarsa ta yi bakinkirin, sai ya ji dama bai biyosu ba, su kuma da alama Imran ya mance da cewa Irfan ɗin shi zai auri Akilar a baya, shi dama Areef bai san waye zata aura aka fasa auren ba!. "A'a ni ban yi wa sisterku komai ba, ita ta ce mani tana son baby, ni kuma na bata, amma ina da tabbacin Akila bata cewa Aseef tana son baby ba, kawai zai azabtar da yarinya dan mugunta ba? To Allah ya kama shi, ta gudu ta koma gida". Cewar Imran. Hawa sama table Areef ɗin ya yi yana ƙoƙarin kwance camerar dake a cikin office ɗin, ya ce "Jalilar ce ta ce maka tana son baby? Yarinyar da ita da kanta ma baby ce, wannan a ina zata iya renon yaro? Ita kanta yaushe ta gama kuka ana rarrashinta? Ai da ita da Rimsha ni ban san waye gwamma ba, kai dai prof ka ji tsoron Allah, ka dai'na azabtar da ƴar mutane, kada ka je ka bata ciki, wlh wahala kawai zaku sha". "Ai jelila ba zata ɗauki ciki yanzu ba In Sha Allah, dan idan ta ɗauki ciki a yanzu, to na shiga uku, ta bakin naka ne, yanzu haka idan ta fara yi mani kuka, to sai na yi zaman rarrashi, ina ga kuma mun sami baby? Ai na shiga uku kawai, barmu dai mu cigaba da soyayya, zuwa gaba, idan ta kara girma, ta rage shagwaɓa, sai mu nemi baby, amma dai Areef kai mugun ɗan sa ido ne, waye wai ya gaya maka halin Jelly?". Shiru ya yi bai bashi amsa ba, dan tun da yake, bai taɓa tsayawa ya yi hira mai tsawon haka da wani ba idan ba TRIPLETS nasa ba, ba shi da yawan magana, amma da TRIPLETS nasa yana magana, yau ɗin ma abin da yasa ya zage yake yin maganar, saboda yana so ne ya manta abin da take a zuciyarsa na tunanin gida, abin ya tsaya mashi a rai, so yana so ne ya ɗan rage damuwar, shi ne yasa ya biyewa Imran ɗin, ban da haka, ba zaka taɓa jin ya yi magana ta tsawon minti biyu mai kyau ba, zaka gan shi kamar bai san komai ba, amma wlh babu wani abin da bai sani ba, duk zaman da su Imran da Jelly suka yi a gidan, ya san komai, duk abin da suke yi, yana sane da komai, kawai dai baya shiga harkar kowa, kuma baya da yawan magana, shi ne yasa sam yake kamar bai san komai ba. "Prof ka ji tsoron Allah, dama ni nasan abin da ya sa kayi aure kenan, amma kana musawa friend naka a kan ba auren kashe sha'awa ka yi ba". Cewar Areef. A wannan gaɓar Irfan ne ya karɓi zancen da cewa "Kowa ya sani mana, auren rage zafi ya yi, amma yana musa mana, yanzu idan ba haka ba, me na hana Jelly ɗaukar ciki? Ai idan ta samu ciki ma dole zata rage shagwaɓa, kuma daga haka zata girma". Ganin suna neman kure shi ne yasa ya ce "Ni ban hana Jelly ɗaukar ciki ba, ai ciki na Allah ne, idan Allah ya ƙaddara lokacin zuwansa, to kome zamu yi, sai ta ɗauke shi". "Yanzu mu kenan zaka gwadawa Allah ba? To ai komai sai da sanadi, mun san Allah yake bada ciki, amma ta sanadin sex ko?" Cewar Areef....... Dama wannan magana ta rashin kunya ai sai Areef ɗin, shi da bai san kunya ba.🧐 "Ni ba zan biye maku ba, dan ni nasan gaskiyar tsananina da Jellyna, ni da yanzu gado ma daban daban muke kwana da ita". Wani irin kallon Areef ɗin ya wurga mashi, irin kallon nan na bashakka haka ne, basu ma kwana ɗaki ɗaya ba iya gado daban daban ba, dakin ma daban daban suke, ɗan rainin wayo kawai. Irfan ne ya ce "A'a karshe ma dai kana palo tana cikin ɗaki, shi ne karshe ba gado ɗaya kuke kwana ba". Areef kuwa cewa ya yi "Ni prof sam ban san daga ina ka samu wannan jarabar tsiya ba, Allah dai ya bawa sister hakurin juriya". Irfan ne ya ce "Kila dai ina ga mata huɗu zai aura, dan wannan mace ɗaya ta yi mashi kaɗan". Allah sarki yau walaƙanci suke jin yiwa Imran, sun saka shi a gaba, bawan Allah. Shi kuma Imran ɗin cewa ya yi "Yanzu kai Areef har kana da bakin cewa wani yana da jaraba? To aishekenan, Allah ya kwaci Jehan, dan da kake cewa sai ta girman nan ma, duk na san zance ne kawai, bari ka samu dama, hmmm na dai yi shiru". "Irfan mata huɗu fa ka ce? A nan ku kuna auran mata huɗu kenan?". Cewar Areef ɗin. Jinjina mashi kai Irfan ɗin ya yi tare da tabbatar mashi. Girgiza kai ya yi yana faɗin "No, we are marring only one girl, mu ko biyu ma bamu yi, Just 1 is okey, amma why zaku auri mata biyu ma? Ɗaya bata isa ba? Me zaku yi da har guda biyu? I can't share my heart to two girls, i can't share my love to two girls, is better for me to share the love and the heart with my childrens and 1 girl, so that we should get more happiness". Ya kai karshen maganar yana saukowa daga saman table ɗin, ya kammala kwance camerar. Shi kuma baban Muneer baki sai kara kumbura yake yi, ya yi suntum, raɗaɗi da azaba sun hana shi ko motsawa. Imran ne ya ce "Ni kai'na ba zan iya auran mata biyu ba, but most a time zaka samu masu auren mata biyu ɗin, jaraba ce ta yi masu yawa, and then suna ganin like matan ba za su iya kula da komai nasu ba, wasu kuma rashin samun soyayya daga wajen matan ne yake kaisu ga ƙara aure, wasu kuma rashin samun farinciki ne yake saka su yin wani auren". Maimaita kalmar soyayya da farinciki Areef ɗin ya yi kafin ya ce "I think namiji shi ne yake bawa mace farinciki, i think shi ne ya kamata ya koya mata sanya shi farincikin, idan har kana sanya matarka farinciki, kana yi mata soyayya, to dole ita ma zata sanyaka farinciki, ga example a kan ni da my baby, before bata sona, amma yanzu ina mai tabbatar maka, wannan tafiya da nayi tana cikin damuwa, kuma ni na koya mata so na ɗin, ni na koya mata menene so, menene kuma farinciki, so duk abin da ka ɗaura mace a kai tun farko, a haka zata ɗaure, komai jarabar namiji, mace tana iya ɗaukarsa tsab, saboda halittarsu ce a hakan, duk yanda ka rukesu, to a haka zasu ɗaure maka har abada, idan baka bata farinciki ba, ta yaya zata baka ita ma? Idan baka kula da ita ba, ta yaya zata kula da kai? Ni ban ga wani dalili na kara aure a nan ba, is better na yi sharing love ɗina da yarana, na kuma sanyasu farinciki, seriously i love Jehan more than your expectations, then i can't share her love with other girls, she is special in my heart, bazan iya haɗata da kowa ba, dan ba zan yi adalci ba, daga kanta an gama". Ya kai karshen maganar yana ciro wayarsa dake ruri yana neman agaji. My uncle, shi ne sunan da ya bayyana a saman screen ɗin wayar. Cool murmushi ya saki kafin ya ce "My diramati, ba zata iya rabuwa da ni ba, and then kuma ba zata barni na zauna kusa da ita ba, amma for sure zan yi maganinki". Ya kai karshen maganar tare da ɗaukar kiran. Kamar yanda ya yi tsammani cewa ita ce ba daddynta ba, haka kuwa ita ɗin ce. Sallama ta yi mashi cikin nutsuwa, amsa mata ya yi yana mamakin ya aka yi ta nutsu muryarta akwai girmamawa a ciki haka? Bai san cewa mum ce ta yi mata faɗa sosai ba, lokacin da ta yi mashi tsawa a palo a gidansu da safe, bayan ya saketa ta koma sama, da mum ta haura saman, zuwa ta yi ta sameta, ta yi mata faɗa sosai tare da tunatar da ita cewa, Allah yana tsinewa mace mai ɗaga murya sama da na mijinta, sannan kuma yakamata ta sani miji ba abin wasa bane, dan ta samu yana sonta, yana biyemata a duk shirmen da zata yi mashi, to wlh gara ta yi amfani da damarta, idan ba haka ba, lokaci ya kure mata ta dawo tana danasani, Areef yana da hakuri sosai, ta sani mai hakuri fa bai iya fushi ba, fushinsa bashi da kyan gani, to wlh kada ta kuskura ta kure shi, zai yi mata ba daɗi, to shi ne nasihar ta shiga kunnan ta, dama kuma da ni da ku dukka mun san tana tsananin son shi, kawai iyashege ne irin nata, yanzu ma ba wai dan nasihar mum ɗin ce tasa ta kira shi ba, a'a tsananin kewarsa ne ya takura mata har ta ɗauki wayar daddynta ba tare da saninsa ba, ta ɓuya ta kira mijin nata............. Ni ko na ce ana so ana kaiwa kasuwa, ni idan ta yi mashi walakanci na janye shi daga gareta ato, dan samun irin Areef a zamanin nan da kamar wuya, abin sai an tona, ko ya kuka ce masu karatu? In yi wuff da abina, yo meyafi ra'ina? Miji na gari a zamanin nan wasa ne?. Gaisuwa ta ɗaga mashi cikin girmamawa. Mamaki ce tasa har ya ɗago yana kallon su Imran, tare kuma da ɗan raba wayar da kunnansa, dan ya tabbatar ita ɗin ce, shi dai yasan wannan voice nata ne, dan ko muryar kowa zai ɓace mashi, to muryar TRIPLETS nasa, daddynsa, Rimsha da kuma ita Jehan ɗin, sai gwaggo a yanzu, muryoyinsu ba zai taɓa bace mashi ba. Ya yi shiru ya kasa amsawa, sanyayyar muryarta ta sake dakan dodan kunnensa. "Yaushe zaku dawo?" Shi ne tambayar da ta sake yi mashi. "Kina son na dawo ne?". Jinjina mashi kai ta yi tamkar tana a gabansa, sannan ta ce "E ina so". "Why kike son na dawo?". Shiru ta ɗan yi kafin daga bisani ta amsa da "I want to see you close..." Sai kuma ta kasa karisawa. Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali kafin ya yi kasa da murya sosai ya ce "Meyasa kika kasa karisa maganar? Kina kewata ne?". "E a'a ni dai kawai ka dawo"............ Ji wata amsa, wai e a'a kai Jehan duniya ce. Murmushi kaɗan ya yi yana faɗin "Sai after one week zan dawo". Shiru ta yi, sai kuma ta katse kiran. Shiru shima ya ɗan yi yana ɗan murmushi, almost 2 mins, sannan ya sake kiranta. Kira na farko bata ɗaga ba, sai a na biyun ne ta ɗaga. "Ya naji kin katse kiran kuma?" Ya tambaya yana kokarin ciro wata igiya da ya gani a wajen kusa da Ac. Muryarta kamar na mai kuka, da alama kuka ta yi, ta fara magana kasa kasa. "Na ji kace sai after one week zaka dawo ne, shi ne na barka sai bayan one week ɗin". "To me kuma ya sanya ki kuka?". A takaice ta ce "Ni ba kukan da na yi!". "Am so sorry my baby, wasa nake yi maki, naja kin zubar da hawaye a banza, idan na dawo dole zan biya hawayen nan, ai nima ba zan iya yin kwana ɗaya ba tare da na ganki ba, anjuma kaɗan zan dawo, me kika ajiye mani?". Sam bata san time ɗin da murmushi ya subce mata ba, ga hawaye a face nata falala. "Duk abin da kake so". Ta bashi amsa tana goge hawayen nata. "Are you serious?". Jinjina kai ta yi tana faɗin yeah. "Okey tom shikenan, idan na dawo zan gaya maki abin da nake so ɗin, amma yanzu Please give me a kiss". Ya kai karshen maganar cikin wata iriyar murya mai kama da na shagwaɓa. Kafewa ta yi a kan ita bata iya kiss ba, jinjina kai ya yi yana faɗin "Ba zan yi maki dole ba, ki kula mani da kanki kin ji ko? Ko palo ma ni bana son ki fito, ba dan daddy da mummy ba, ai da ba zan barki ma a gidan ba, amma dai ki kula sosai kin ji my pleasure?". Kamar daga sama ya ji ta sumbaci wayar, sannan ta katse kiran ba tare da ta amsa mashi ba. Murmushi ya saki yana mayar da wayar a cikin aljihunsa, sannan ya nufi baban Muneer da yake kwance shame shame a cikin jini. Ɗaure shi ya fara yi, shi kuma Imran, mikewa ya yi tare da ciro wayarsa ya nufi waje yana faɗin "Nima dai bari na ji voice ɗin tawa pleasure ɗin, da dai bani da ita ne sai ka yi mani gori". Ko sannu bai ce mashi ba, ya ɗaure baban Muneer, sannan ya mikar da shi tsaye yana faɗawa Irfan su tafi ko?. Ko da suka fito, ma'aikatan dake companyn, sun yi ƙoƙarin hanasu tafiya da shi, amma sai Areef ya nuna masu tsab zai yi ball da su idan basu tashi mashi a kan hanyarsa ba. A hanzarce wasu daga ciki suka kira office ɗin ƴan'sanda, sai dai kafin ma ƴan'sandan su zo, sunbar company ma abinsu. Haka suka kamo hanyar Kaduna. A ɓangaren Lion kuwa, sai da ya ɗauki good 3 hours a asibiti ba tare da ya motsa ba, sai zarya likitoci suke yi a kansa, Aseef kuwa, da shegen saurin kuka kamar daddyn Jelly, sai zuba kukansa yake yi, har idanuwansa sun kumbura suntum, yaki yarda ya matsa kusa da Lion ɗin, yana zaune a saman bed ɗin, gwaggo na zaune a gefensu, ga sojojinsa suna tsaye cirko cirko a kofar shiga ɗakin, Mark ne kawai ya shigo cikin ɗakin, sai Tga dake ta faman magana da likitoci. Duk wanda ya doso ɗakin da Lion ɗin yake kwance, sai ya juya a dubu ya koma, dan waɗan nan zaratan sojojin da suke tsaye a bakin kofar, ganin su ba ƙaramin razana al'umma yake yi ba, ga su jajir da su, tamkar ka taɓa jini ya zuba, dukkansu babu wanda yake sanye da uniform a jikinsa, duk fararen kaya ne a jikkunansu, fuska kam ba'a magana, kamar na shanu! A ɗaure tamau!. Har sai da Lion ya kara good 1 awa, sannan ne likitocin suka yi nasarar saita bugawar zuciyarsa, suka kuma yi sa'a ya farfaɗo. Yana buɗe idanuwansa, da Aseef ya fara cin karo, ido huɗu suka yi da Aseef ɗin. Da sauri ya mayar da idanunsa ya lumshe, yana tariyo abubuwa da dama a cikin ƙwaƙwalwarsa. Tabbas jaririn da mutumin nan ya kawo, mai brown eyes ne, jaririn da Josephine ta miƙa mashi kuma mai blue eyes ne, shi ma ɗayan jaririn da yake kwance, blue eyes ke gare shi, wanda Dr William ya fita da shi kuma ash eyes ke gare shi, abu biyu ne suka sanya Lion zuciyarsa ta kusa bugawa a cikin wannan video da ya gani, kuma kunsan abin da zai sanya shi suma duk da irin taurin zuciyar nan tasa ba ƙaramin abu bane!!. Abu na farko, jaririn da ya ga mutun ya kawo, tabbas mai brown eyes ne, idan hasashensa gaskiya ce, to Aseef ne kenan, dan wanda yake kwance a saman sofa dai, mai blue eyes ne, hakan na nufin shi ne kenan, babban abin da ya fi ɗaga mashi hankali shi ne, ya fi kaunar Aseef ɗin sama da kansa, ya fi son Aseef fiye da Areef, ya fi son Aseef fiye da kowa, sun fi shakuwa, shakuwar da take a tsakaninsu baki ba zai iya faɗarta ba! Gara ace mashi mutuwa ya yi, da ace mashi Aseef ba jininsa bane! Ba zai iya jurar hakan ba, ko na rana ɗaya ba zai iya rabuwa da shi ba! Yana kaunar shagwaɓatinsa! Yana son ɗan rigimammensa! Yana son pleasurensa! Shi ne bugun zuciyarsu! Ko daddynsu ya fi kaunarsa sama da kowa! Ya ilahi ya lillahi, ina zai saka ransa ya ji sanyi! Josephine ta cuce shi! Ta gama da rayuwarsu, sai da suka saba! Suka taso a tare! Komai tare, shakuwa tasa har suke jin juna a jikinsu, yanzu ya Areef zai ji? Anya zai iya yarda kuwa? Babbar tambayar da Lion ɗin yake yi wa kansa shi ne, to meyasa suka yi hakan? Meyasa aka canza masu ɗayasu? Me suka yi da wancan ɗayan da suka ɗauka? Ina suka kai shi? Yana raye ne ko ya mutu? Shin Aseef mutun ne ko aljani? Cikakken mutun ne kuwa? Ko shi ne yasa yake wasu abubuwa da bana cikakkan mutane ba? Dole dai akwai dalilinsu na yin waɗan nan abubuwa dukkan, haka kawai baza'a canzasu ba! Haka kawai baza'a kawo wani yaro daban a cikinsu ba!! Ni kuma PRINCESS TEEMA abin da yake cikin ra'ina, yake kuma damuna shi ne ya Akila zata yi? Ya zata ji a ranta? Shin zata zauna da wanda ba mutun bane? Ko dai yaya? Anya zata iya rayuwa babu shi kuwa? Tana son heartbeat nata fiye da kanta, wai Meyasa Aseef ya cika mugu mugun shiga ran mutane dayawa har haka ne? Meyasa kowa ya fi son shi? Wannan ma ayar tambaya ce!!. Abu na biyu da ya sanya Lion ɗin zuciyarsa ta kusa bugawa shi ne, wannan mutumin da ya kawo wannan jariri ba kowa bane face uncle Herry, ba shakka uncle Herry ne, dan da kallo ɗaya Lion ɗin ya yi mashi, ya kalle shi da idanun basira, nan ya fahimci uncle Herry ne, duk da ya ɓoye komai na jikinsa, yana cikin shigar bakaken kaya, hakan bai hana kaifin ƙwaƙwalwa Lion ta gane cewa shi ɗin bane, saboda idanun uncle Herry, John, Jay, GTA, daddynsa, Aseef, Areef, ba za su taɓa canzawa ko su ɓoye mashi ya kasa gane su ba, ba zai taɓa kasa ganesu a ko wani irin yanayi ba, zaka gan shi wani lokaci kamar baya kallo abubuwa, amma yana sane da komai, tabbas uncle Herry ne ya kawo jaririn. Tambayar da Lion ɗin yake yi wa kansa, to ina uncle Herry ya baro daddynsu? Ina ya baro Dr? Bayan kuma a tare suka fita daga gidan a lokacin, ko dai ya yi wa Dr ma wani abin ne? Wai shin menene gaskiya? Me yake faruwa ne?!!!. Waɗan nan sune abubuwan da suka hargitsa zuciyar Lion, ace kannen babansa dukka maciya amana, kuma su rasa amanar waye za su, sai na yayan nasu, kai duniya ina zaki damu, ɗan uwa ya ci amanar ɗan uwan sa, sun cutar da rayuwarsu, to wai me suka yi da jaririn da suka ɗauka? Kuma a ina suka samo jaririn da suka kawo ɗin? Ga dukkan alamu dai suma aiki suke yi a karkashin wata kungiya, ko kuma wani, dan ga dukkan alamu umarni suke karɓa, duba da yanda suka tsara abin, a lokacin shekarasun ya yi kankantar da za su iya tsara hakan, sun yi kananan wajen shirya wannan abin, dole akwai wanda ya fisu shekaru da yake shirya masu komai, wannan dalilin yasa Lion ɗin bai ji cewa yana bukatar ya zauna da su, dan su gaya mashi gaskiya ba, dan ya san irin wannan case ɗin, ko kashe su zai yi, wlh ba za su taɓa faɗar gaskiya ba, so is better for him ya nemo gaskiya da kansa, babbar magana, ta ina zaka fara kenan? Waye zaka fara tunkara?!! Murya a dashe saboda kuka Aseef ɗin ya ce "My Lion, please ka tashi ka ji?". Kara datse idanuwansa sosai Lion ɗin ya yi, har cikin ransa yake jin muryar Aseef ɗin, yanzu idan gaskiya ta gama bayyana, shi Aseef me makomansa? Kenan idan ba mutun bane tafiya zai yi ya barsu? Ko yaya ne? Ya ilahi ya lillahi. Gwaggo ce ta matso tana faɗin "Saif ka tashi dan Allah". Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da waro idanuwansa a hankali, kai tsaye sai saman face nata kallonsa ya sauka. Shiru ya ɗan yi kafin ya kai hannu ya ɓalle karin ruwan da aka sanya mashi, ya cire, sannan ya yunkura ya mike zaune. "Saif meyasa ka cire ruwan kuma?". Cewar gwaggo. Girgiza mata kai ya yi alamar baya da bukatar ruwan. Matsowa ta yi tare da dafa kafaɗarsa tana shafa kansa da hannu ɗaya. Ɗago idanu ya yi yana kallon TGA dake tsaye a gefe guda, tun da yake da Uncle T ɗin nasa, bai taɓa tsura mashi idanu yana kare mashi kallo irin na yau ba, zuciyarsa na gaya mashi cewa har da uncle T ɗin yanzu a tafiyar su Josephine ɗin, amma yaki yarda da hakan, saboda wasu dalilan guda biyu, na farko TGA yana sonsu so na tsakani da Allah, dan an taɓa yin yunkurin harbin Lion ɗin ma da bingida, GTA ya tare, ya shiga tsakaninsu bullet ɗin ta same shi, na biyu kuma, TGA yana ɗan ƙaramin yaro lokacin da abubuwan suka fara faruwa, sai dai abin da ya sanyawa Lion ɗin shakku a kan Tga ɗin shi ne, meyake kai shi wajen Josephine a yanzu? A gaban idanunsu zai nuna baya son Josephine, amma a bayan idanunsu zai saci kafa ya je wajenta, ga uncle Herry ma, a gaban idanunsu yana nunawa baya sonta, amma a bayansu kuma 5 and 6 suke da ita. Wannan abin akwai matukar ɗaure kai over. Ganin ya mike zaune ne yasa uncle T ɗin ya kariso wajen nasa da sauri, shi ma Mark karisowa wajen ya yi yana yi mashi sannu. Zuro kyawawan fararen kafafunsa kasan gadon ya yi ba tare da ya ce masu komai ba. A hanzarce Mark ya bashi takalmar dake kafansa, dan ya sanya, saboda ya san halin Ogan nasa da bala'in kyankyani. "Momma let's go". Shi ne kawai abin da ya iya furtawa, sannan ya mike tsaye. Daga Mark har TGA kallon gwaggo da ya kira da momman suka yi, mamaki Mark yake yi, tambayar kansa yake yi wacece gwaggo kuma? Shi dai ya shiga duhu. Wani irin jiri yake gani da ya mike, har wani layi yake yi. Ganin hakan yasa da sauri Mark da Tga suka yi ƙoƙarin tallafa mashi. Hannu ya ɗaga masu alamar baya bukata, sannan ya juyo da kallonsa a kan Aseef dake ta binshi da kallo. Alama da hannu ya yi mashi a kan ya zo ya tallafa mashi su fita, Allah sarki sam baya son Aseef ɗin ya fahimci komai, ya zai ji a rayuwarsa? Ya zai yi da ransa idan ya san gaskiya?. Mikewa ya yi, duk jikinsa a mace, ya nufo Lion ɗin. Ɗan rungumo shi Lion ɗin ya yi yana shafa kansa gwanin ban tausayi, haka suka nufi waje. Da sauri gwaggon ta mike ta rufa masu baya, su Tga suka rufa mata baya. Shi dai Mark kansa ta shiga duhu....... NI KO NA CE MARK BA KAI KAƊAI BA, KOWA MA KANSA TA SHIGA DUHU, WAI KAI DAN MA BAKA SAN ABIN DA MUKA SANI BA, AI DA DUHUN DA ZAKA SHIGA MA BA ZAI FAƊU BA!!. Suna fita sojojinsa suka rufa masu baya izuwa wajen motocinsu. Lion haka kawai yake jin babu daɗi zuciyarsa, tunanin Rimsha dake ta faman sheka barci a gida ne ya faɗo mashi a cikin ƙwaƙwalwarsa, nan take ya ji kirjinsa ta buga, tasbihi ya fara yi a cikin zuciyar nasa, dan ya samu salama, abubuwan sun yi mashi yawa, tunani yake yi bai kamata ya yi nisa da duk waɗan da suke da kusanci da shi ba, dan a wannan point da suke a yanzu, kamata ya yi ya haɗe familyn gwaggon gabaɗaya waje guda, domin kuwa, a yanzu koma suwaye suke bibiyar rayuwarsu, sun san ya san komai, ba shakka za'a cutar da su, kuma tabbas familyn gwaggon za'a cutar, dan familyn daddynsu kam suna da hannu dumu dumu a kan komai, so yana da kyau ya haɗa gabaɗaya ƴaƴa da jikokin Dr Salman waje guda, sannan a saka masu matakan tsaro, idan ba haka ba, za'ayi masu ɗauki ɗai'ɗai!!. Babbar magana. Wayar Aseef ne ta fara kara dai'dai lokacin da suka shiga cikin motar. A hanzarce ya cirota daga aljihunsa, ya sha ruwan mamakin ganin uban miss call na Areef, dan lokacin da Areef ɗin ya yi ta kiransa, sam bai ji ba, baya a cikin hayyacinsa. My uncle, shi ne sunan da ya bayyana a saman screen ɗin wayar. A hanzarce ya ɗauki kiran, a lokacin kuma har motocin nasu sun fara tafiya, sun fito daga asibitin, yana zaune kusa da Lion, shi da gwaggo sun saka Lion ɗin a tsakiya a gidan baya na motar. A hand-free ya sanya wayar, daga ɗayan ɓangaren daddyn Rimsha ya ce "Aseef kuna tare da Akila ne? Ta zo asibitin ne?". Jin tambayar daddyn Rimshar yasa Lion ya juyo da kallonsa a kan wayar. "A'a uncle, ni tun da kuka tafi da ita jiya, ban sake ganinta ba, na kira numberta da safe ma a kashe". "E ba shakka wayarta a kashe, muma mun kira bata shiga, amma ina zuwa". A hanzarce Aseef ɗin ya ce "Uncle lafiya dai ko? Meyasameta? Bata gidan ne? Ina ta ce dama zata je?". Ya yi maganar a rikice. "A'a babu abin da ya sameta Aseef, ka kwantar da hankali, ina zuwa zan sake kiranka". Bai jira masar da zai bashi ba, kawai ya katse kiran. TOH FAH INA AKILA KUMA TA SHIGA⁉️ Karɓar wayar Lion ɗin ya yi, cikin sauri ya fara kiran number Rimsha, dan dama ya kawo wa ransa za'ayi wa matan familynsu gwaggo ɗauki ɗai'ɗai, kuma idan basu yi saurin ɗaukar mataki ba, duk za'a kashe matan ne, dan da alama babu wasa a lamarin masu aikata hakan, bare ma da suka san yanzu asirinsu na gab da tonuwa, ai sai dai wanda Allah ya ƙaddara kwanansa na gaba, amma za'a zubar da jini kam ba kaɗan ba!, Kuma dole hankalinsa zai tashi, saboda a halin yanzu Rimsha ta fi kusa da shi sama da kowa, kuma ga shi shi ne yake shirin bankaɗo gaskiya, shi ne babban makiyin mutanan, ko dan a sanya shi ya rusina, za'a iya yi mata wani mummunar abin, so dole ta kasance a tare da shi a ko da yaushe, rayuwarta yana cikin hadari sosai, da alama ya yi shigar sauri wa mutane, bai shirya ba ya shiga yakin, hakan kuma zai wahalar da shi da na kusa da shi ba kaɗan ba!!. Sai kiran wayar yake yi, amma ina bata ɗauka ba, number Areef ya kira, su kuma a lokacin sun kamo hanyar Kaduna, babu network sam, number bata shiga, tsaki ya ja tare da dakawa Mark tsawa a kan ya taka motar nan da sauri su kai gida da wuri, dan ya duba ya tabbatar Rimsha tana gida or not. Babbar magana. Mikawa gwaggon wayar Aseef ɗin ya yi, cikin sanyin murya ya ce "Momma ki gayawa dukka uncles namu yanzu ba sai anjuma ba mu haɗu a gida, dukkansu da ƴaƴansu gabaɗaya". "Saif meyake faruwa ne? Ɗazun Abban Imran ya kirani ya ce Ayla matar uncle naku Maik ta ɓata, daga baya ya sake gaya mani mijin Aafia ya rasu, ita kuma Aafiar bama su san a wani point zasu ajiye ta ba, yanzu kuma na ji Nawazuddeen yana tambayar Aseef ina Akila, me dukka wannan ne?". Nisawa ya yi kafin ya ce "Momma babu komai, just tell them what i said kawai, and ki yi sauri ki bani wayar ina son in gayawa Areef a duk in da yake, ya yi sauri ya zo gida ina son yin magana da shi......." Bai kai ga rufe baki ba Mark ya ja wata mahaukaciyar burki, waddata sanya su suka tafi luuuu suka buga kansu da jikin sofar motar, shi ma Mark ɗin sai da ya buga kansa da jikin steering motar. Kusan a tare suka ɗago kawunansu tare da kai kallonsu a gaban motar, dan suga menene ya sanya Mark ɗin taka irin wannan burki haka................... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E9 Kusan a tare suka ɗago kawunansu tare da kai kallonsu a gaban motar, dan suga menene ya sanya Mark ɗin taka irin wannan uban burki haka. Ko da suka ɗago kansu, babu komai a wajen, kan hanyar wayam, da mamaki Aseef yake kallon Mark ɗin, bawan Allah shi kuma wata halitta ya gani tsaye a tsakiyar hanyar, shiyasa ya yi kokarin kauce mata, ashe gizo kawai aka yi mashi, da alama an shirya masu hakan ne domin su yi accident, sai kuma Allah ya karesu da kariyarsa. Aseef ɗin zai yi magana, Lion ya dakatar da shi, sannan ya ce da Mark ɗin su tafi kawai. Kunna motar ya yi suka cigaba da tafiya, ita kuma gwaggon ta kira su Abba kamar yanda Lion ya ce mata, daga haka babu wanda ya sake yin magana a cikin motar. Har sun kusa isa gida, kome Lion ya tuna, sai ya karɓi wayar Aseef ɗin ya turawa Areef massage a kan ya tsananta addu'a sosai a duk in da yake, kada ya bari askar ta kubce daga bakinsa, dan fa akwai gagarumin matsala ba kaɗan ba. Motarsu na yin parking a cikin gida, motar su daddyn Rimsha ma ya shigo cikin gidan, gabaɗaya familyn sun haɗu waje guda, ita ma Akilar sun ganta, ashe makwabtansu ta shiga, ta je su gaisa ne, dan kunga tun da ta yi aure, ai bata je ba, shi ne yanzu da dama ya samu, sai ta leƙasu. Ita kuma Ayla shiru, babu ita babu labarinta. Mark yana kashe motar Lion ya fita daga cikin motar, bai bi ta kan kowa ba ya wuce cikin gida da sauri. Kai tsaye bedroom nasa ya nufa, ya sha ruwan mamakin ganin Rimsha tana zuba barci har iyanzu, kai kallonsa a kan agogon bangon dake manne a cikin ɗakin ya yi. Almost 4 to 5 hours tana zuba barci, anya barcin nan na lafiya ne kuwa? Ya tambayi kansa. Karisawa cikin ɗakin ya yi, cikin nutsuwa ya haye saman bed ɗin, hannu ɗaya ya sanya ya tallabo kanta, sannan ya sanya ɗayar hannunsa ya shafa kyakkyawar face nata. Cool murmushi ta saki har sai da dimples nata suka yi wani irin lotsawa mai matuƙar ɗaukar hankali. Cikin magagin barci ta fara faɗin "Kai Noorish ka bari mana". Kamar tasan shi yake taɓata. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya kai ɗan bakinsa ya sumbaci lallausan lips nata, sannan ya kankameta gam a kirjinsa, yana mai jin wani irin tsananin kaunarta tana ratsa shi. Ya ɗan ɗauki lokaci a hakan kafin ya mayar da ita a hankali ya kwantar, sannan ya diro kasa ya nufi toilet, ita kuma, cigaba da barcinta ta yi cikin kwanciyar hankali. Hakika tabbas an so ɗaukar Rimshar kamar yanda Lion ɗin ya yi tunani, Malika ta ɓoyeta, ko da aka zo ɗaukarta ba'a ganta ba, Malika ta lulluɓeta da nasu siddabarun na aljanu, a gaskiya Malika tana kaunar Rimsha sosai, sannan kuma tana kula da ita sosai, sau da dama tana tare mata abubuwa da dama wanda idan ba ta gaya maku ba, ba zaku taɓa zaton ita ce ta tare ba, so ake ta karfi da ya ji a ladabtar da Lion, so suke su rufe mashi baki a kan case ɗin, so dole suna son yin amfani da rauninsa, dan su sanya ya rusina, sai dai kuma kash, dukka raunin nasa baza su taɓu ba, barema Rimsha da take tare da Malika, ba zata taɓa taɓuwa ba, sai dai idan shammatar Malikar aka yi, tun da dukka abune na tsafi da aljanun, so babu abin da ba zai iya faruwa ba. Wanka Lion ɗin ya yi, sannan ya fito ya shirya cikin kanana kaya, wando three cuter fara kal, da T-shirt sky blue bara nauyi, bai ɗaure gashin kansa ba, ya saketa. Wayarsa ya zo ya ɗauka a saman bed, number Areef ya sake gwada kira, still dai bata shiga, zama ya yi a bakin bed ɗin, number Mark ya kira a kan ya zo ya gyara mashi bedroom nasa, ya kwashe laptop da ya fasar nan. Yana katse kiran ya ji saukar hannayenta a saman kugunsa ta wajen flat tummynsa, ta rungume shi ta baya, a hankali ta kwanto da kanta a saman bayansa, da murya irin na mai barci ta fara magana. "Noorish shi ne baka tashe ni daga barci ba ko?". Nisawa ya yi, har cikin ransa ya ji sassauci na abin da yake ji, ya ji sanyi sosai, hannun nata ya riko ba tare da ya yi magana ba. "Noorish na yi mafarkin wani waje, in gaya maka ina ne?". Tana magana kamar wadda barci bai isheta ba. Juyowa ya yi a hankali, sannan ya jawowata ta dawo saman kirjinsa, zubawa face nata idanu sosai ya yi. Idanunta a rufe ruf take zuba surutu, sai guntun murmushi dake a saman face nata, ga dimples nata duk sun lotsa sosai, sai ta kara kyau matuƙa. "Meesha tun da na bar gidan nan baki tashi daga barci ba?". Ya faɗa cike da tantamar irin barcin da ta rinƙa zubawa kamar ba gobe, abin da bai sani ba shi ne, Malika ce ta sakata yin wannan barci, dan da ta farka, to babu abin da zai hana Josephine bata ɗauketa ba! Saboda yanzu farautar rayuwarta suke yi tamkar ruwa mai sanyi a sahara mai tsananin zafin rana, a gefe guda, ga Queen of Daular Mutuwa tana nemanta ruwa a jallo, daga ɗayan gefen kuma, su Josephine suna nemanta ko ta halin kaka ne su ɗauketa, dan hawai su karyar da zuciyar Lion ɗin, hakan tasa Malikar ta sakata wannan uban barci kamar ba goben, har sai da ya dawo, sannan ta tafi ta basu waje, shi ne ma Rimshar ta iya farkawa. "Noorish ban tashi ba, nifa yanzu na tashi, dama ka fita ne? Shi ne baka tashe ni na raka ba? Na ɓata da kai to". Ta kai karshen maganar tana haɗe mashi fuska, irin ta yi fushin nan. "Open your eyes first, sai ki kalli cikin idanuna ki ce mun ɓata". Make mashi kafaɗa ta yi. Hannu ya kai ya shafi lallausar wuyarta dake kara ɗaukar hankalinsa a koda yaushe. "Open your eyes". Ya faɗa yana gangaro da hannun nasa izuwa kirjinta. A hankali ta waro idanun bata tare kumbura kumatu. Zubawa juna idanu suka yi, yau ɗaya ta iya dakewa ta kalli cikin kwayar idanunsa, anya ita ce ta iya wannan juriya na kallon cikin idanunsa kuwa? Anya babu sa hannun Malika a ciki kuwa? Shi ma ya ɗan yi mamakin yanda ta zuba mashi idanu tana kallon shi, babu ko kyaftawa. "Noorish meyasameka?". Ta yi maganar tana kai hannunta a saman kumatunsa. Riko hannun nata ya yi tare da manna shi da jikin kumatunsa ba tare da ya saki ba, ya haɗe hannayen nasu waje guda a wajen, shiru bai yi mata magana ba, ita kuma sai kallon mamaki take yi mashi, taga ya yi wani irin rama ne, ita dai tasan kafin ta yi barci, ba haka ta barshi ba, ga idanunsa sun kara girma, alamar ya rame kenan. Baki ɗauke da sallama Aseef ya shigo cikin ɗakin. Juyawa ta yi tana kallonsa, sai kuma ta yunkura zata bar jikin Lion ɗin, sai dai bai sake ta ba, yana rike da ita, yana ta kallon face nata, shi kaɗai yasan me yake ji a duk lokacin da yake kallonta. Sam Aseef bai bi ta kansu ba, saman bed ya haye abinsa, ya kwanta tare da ciro wayarsa ya fara aikin latsawa, sai dai fa ya sha ruwan mamakin na ganinsu a manne da juna, kawai baya son ya yi magana ne, dan kada ya katse masu jin daɗinsu. Mark ne ya sake shigowa cikin ɗakin, kallo ɗaya ya yi masu ya kawar da kansa gefe, sannan ya wuce dan ya yi aikin da ya kawosa. "Meesha zaki raka ni ƙasar China?". Ya faɗa a sanyaye, tamkar bai san da Mark da kuma Aseef a cikin ɗakin ba. Jinjina mashi kai ta yi tana faɗin "E zan raka ka". Shiru ya yi yana tunanin a ina zai sami Cherish? Dan ba shakka duk yadda aka yi, tana da sa hannu a duk abubuwan da suke faru, saboda very close friend ɗin gwaggo ce, ya za'ayi daga haihuwar gwaggon shikenan ace Cherish ta ɓace? Ko dai dama ita ma ba mutun ba ce? Wannan abin da akwai ruɗani, dole ya nemo jigon haɗa wannan rikicin dukka. Sallamar Areef ce ta dawo da shi daga duniyar tunanin da ya afka, tun da Areef ɗin ya shigo, ya tsare shi da idanu har ya kariso cikin ɗakin, a saman bedside drawer ya zauna yana faɗin "Kai Aseef momma tana nemanka kana nan ko?". Turo baki ya yi yana faɗin "Ni ba zan je ba, kuma fushi nake yi da su, saboda sun ce wai ba zan yi punishing na Heartbeat ba, a kan me zata fita bata tambaye ni ba? Ni gaskiya ba zan kyaleta ba!". Sake Rimshar Lion ɗin ya yi yana mai dawo da kallonsa a kan Areef dake kare mashi kallo shi ma. "Me kake zuwa yi a wajen Josephine time da kake zuwa wajenta?". Shi ne tambayar da Lion ɗin ya wurga mashi. Miƙewa daga jikinsa Rimshar ta yi, sannan ta nufi kofar fita. Hannunta Areef ɗin ya riko yana tsokanarta "Sister yau kin mance da ni ko? Wato ma fita zaki yi kamar baki ganni ba ko?". Katse shi Lion ɗin ya yi da cewa "Saketa ta wuce, sannan ka juyo ka bani amsa ta". Kasa sakin nata Areef ɗin ya yi, dan shi ya ji ne ma kamar bai san wacece Josephine ɗin ba, baya son a kawo mashi maganarta, dan haka sai ya ce "Wai kai Lion ka bari mu gaisa da ita mana". Sosai Aseef ya yi mamakin abin da Areef ɗin ya yi, shi dai a iya saninsa ya san cewa Areef ɗin yana yawan tsawatar mashi a kan kada ya kuskura ya rinƙa rungumar Rimsha, or ya kamata hannunta a gaban Lion, idan ba haka ba, to za su yi babu daɗi da Lion ɗin, dan wannan uban kishin nasa, to ya aka yi yau shi kuma Areef ɗin da kansa ya rike mata hannu, kuma har Lion ɗin ya ce ya saketa, amma yaki, anya kuwa babu wata alamar tambaya a nan?. Shi kuwa Lion ɗin sam bai ɗauki zafi ba, saboda ya lura, yanzu koma ta halin ƙaƙa, so ake a kai shi ƙasa, so ake a rinƙa fusata shi, yana ɗaukar zafi, har ta kai ta kawo zuciyar ta kasa ɗauka, ta buga ya mutu kowa ya huta, tun da ya fahimci haka kuwa, to ba shakka zai yi taka tsantsan wajen ganin ya danni zuciyarsa ba zai ɗauki zafi ba!! Wannan shi ne yaki sunkuru, Lion dai yana faɗa da aljani, shi baya ganinsu, amma su kuma suna ganin duk wani motsinsa. Hannun Rimshar ya riko tare da jawota ta dawo jikinsa, cikin sanyin murya ya ce da Areef ɗin "Now amsa me". Ita dai Rimsha yau tana ganin abin mamaki, ta lura yau gabaɗaya TRIPLETS ɗin a tsai tsaye suke magana da junansu, kamar ba lafiya ba, magana suke yi kai tsaye kawai. "Saif ni ba wani abin da nake zuwa yi gidanta face gaisuwa, shi kawai nake zuwa yi". Aseef ne ya amsa da cewa "Ba wani gaisuwa, akwai dai abin da yake kaika, Allah gara ma ka rabu da matar nan, duk da cewa ta taimakawa Momma a baya". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa zaune yana wani yamutse fuska. "Anywhere zamu koma Washington gobe idan Allah ya kai mu, kuma gabaɗayanmu zamu tafi, saboda mun gama abin da ya kawo mu Naija, so idan mun bar Naija, mun barta kenan har abada!". Cewar Lion. Da sauri Rimsha ta ɗago kai tana kallonsa, da mamaki fal a face nata ta ce "Noorish to ita kuma gwaggo fa?". Shiru ya yi bai amsa mata ba. Areef ne ya amsa mata da cewa "Da Momma da ke da my baby, Heartbeat, dukka zamu tafi da ku mana, ai ku kun sallami Naija kenan". Zaro dara daran idanuwan nan nata ta yi, a tsorace ta ce "To daddyna da mummyna fa?". Aseef ne ya amsa mata da "A nan zaki barsu mana". Sam bata san time ɗin da ta furta, "Na shiga uku na! Wlh ni ba zan je ko'ina ba, sai dai ku tafi ku barni". Bata san time ɗin da ta furta hakan ba, sai da ta ga irin kallon da Lion ya wurga mata ne, nan ne ta fara tunanin wai shin me ta faɗa nema?. Gwaggo ne ta katsesu ta hanyar shigowa cikin ɗakin bakinta ɗauke da sallama. Ita ma tun da ta shigo Lion ya tsareta da idanu yana kare mata kallo, wani irin tausayinta ma yake ji a yanzu, an cuceta ba kaɗan ba. Da sauri Rimsha ta bar jikinsa, ta nufi gwaggon tana dariya. Rungume juna suka yi, a tare suka kariso cikin ɗakin. A gefen gado kusa da Lion ta zauna, ita kuma Rimsha ta zauna a gefenta tare da kwanto da kanta a saman kafaɗunta. "Saif kuzo muje palo, akwai maganganu da zamu tattauna da su Abban Imran and Brr". Cewar gwaggon kenan. Jinjina mata kai ya yi yana faɗin "Ki shirya gobe zamu koma ƙasarmu". Har tana haɗe word wajen cewa "Wace ƙasa kuma?!". Shiru ya yi bai bata amsa ba. Areef ne ya amsa mata da kasar da ake nufi, wato Usa. "A'a ni zan zauna a cikin ƴan uwana, ku dai ku koma, duk time ɗin da kuka sami lokaci, sai ku kawo mani ziyara". Miƙewa Lion ɗin ya yi ba tare da ya sake yin magana ba, ya nufi waje abinsa, dan ya san babu abin da zai hana su tafi da ita, ta gama zantukanta dukka, Nigeria kam sai ta barta..........Babbar magana. Miƙewa suka yi dukkansu suka rufa mashi baya. A palo suka isko su Abba gabaɗaya, sai hira suke yi, amma ga dukkan alamu, suna cikin matsananciyar damuwa. Saman sofa Lion ya zauna yana kallon baban Muneer dake a tsakiyar palon, Areef ya ɗaure shi da igiya kamar ba lafiya ba, ga bakinsa a kumbure suntum. Da kallo ɗaya ya yi wa baban Muneer ɗin ya fahimci koma me wannan dai ba mai laifi bane, amma sai bai tambayi meyayi suka ɗaure shi haka ba, ya zuba idanu kawai yana kallonsu, dan shi ciwo ma kansa take masa. Tun ɗazun Akila sai jin sautin Muryar Ablah kanwar Haroon take yi ana kiranta, tun ana kiranta daga nesa har ta ji an matso kusa, sai ta ji kamar a harabar gidan ma ake kiranta. Mikewa ta yi tare da gaya masu tana zuwa, tana fita daga palon shikenan ɓat ta ɓace tamkar wata aljanna, an ɗauketa. To fah. Su kuma jama'ar cikin palon, Brr Naurat ce ta yi gyaran murya tare da fara yin magana cikin dattaku da nutsuwa. Nasiha ce mai ratsa jiki ta yi wa Ummin Dr Nawid, sannan ta ce mata ko sun ɓuyo mata yanzu, gaba dole zata sani, to gara su gaya mata kawai, ta yi hakuri Allah ya yi wa Dr Nawid rasuwa. Yadda suka yi tunanin Ummin zata ɗauki abin, sai ya zamana ba haka ta ɗauka ba, sai ma wani irin murmushi wadda da ka ganta, kasan dole aka ƙaƙalota, shi ta saki kafin ta ce "Dama ni bani na bawa kai Nawid ba, Allah ne ya bani shi, kuma duk yanda nake son shi, na san Allah ya fini son shi, ni ba zan taɓa butulcewa Ubangijina wajen yin kuka ko makamancin hakan dan ya karɓi rayuwar Nawid ba, na yi imani ya fi kowa sanin zuciyata, kuma a hakan ya ɗauki ran Nawid, ina farinciki da hakan, kuma ina kara godiya ga Allah, duk wanda bashi da yaro, ina rokan mashi Allah da ya bashi masu albarka, ni kuma ina rokan Allah daya kara mani hakuri, ina farinciki cewa ɗana ya rasu a ranar jumma'a, yanzu kawai ku kai ni naga gawarsa, zan yi mashi addu'a". Baiwar Allah, kowa yasan maganar nan ma da take yi, da kyar take fita, karfin imani ne kawai, da kuma yarda da ƙaddara, ta yarda da Allah shi ne mai yi, tana tawassuli da sunayensa tsarkaka, Allahu Akbar, a gaskiya samun uwa irinta a wannan zamani, zai yi matuƙar wahala, Imran da yake iya matsayin aboki a wajen Dr Nawid ma, sai da ya shiga tsakanin tashin hankali na wuce misali, bare kuma uwar da ta haifesa, kuma shi ne kawai ɗanta, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allah ya kara mata hakuri, a gaskiya ta nuna jarumta da karfin imani. Sosai suka tausaya mata, kowa sai addu'a yake yi mata, ita kuma Aafia, sai da suka samu aka yi mata alluran barci, sannan ne suka sami zaman lafiya, in ba haka ba, sai buge buge take yi masu. Brr Naurat ɗin ce ta sake shigo da maganar case ɗin daddyn Jelly bayan ta sanar da Ummi ai an rigada an kai Dr Nawid makwancinsa, sai dai su je makabartan Ummin ta ziyarce shi a can kawai. Tambayar baban Muneer Brr Naurat ta yi, a kan shi ya ɗauki Ayla ko ba shi ba? Idan shi ne, ya dubi girman Allah ya dawo da ita, dan tana da karamin ciki wlh. Girgiza masu kai ya rinƙa yi a kan shi wlh ba shi bane, amma bakinsa bata iya yin magana, dan ya kumbura sosai. Rimsha ce ta katse su da cewa "Nashiga uku, Ayla ta sake ɓata?! Allah dai yasa ba Daular Mutuwa suka mayar da ita ba, shikenan wlh kasheta za su yi, dama Duna ya gaya mana in dai muka kuskura muka bari muka dawo wannan gida, to wlh babu mai iya fitar da mu, wayyo mummyna!!". Ta kai karshen maganar tare da mikewa da sauri ta faɗa jikin daddynta tana sakin wani irin kuka mai tsuna zuciyar mai sauraro. Tabbas an shafewa Rimsha tunanin Daular Mutuwa a cikin ƙwaƙwalwarta, yanzu ba ita ce ta yi maganar ba, Malika ce ta yi maganar, dan ita ta san Ayla tana can, bata da wata hanya da zata bi ta gaya masu Ayla tana can, dole sai ta hanyar shiga jikin Rimshar, saboda ita ce kaɗai ta taɓa zuwa Daular Mutuwar bayan Aylar, kuma tana son su san cewa head of the familynsu gabaɗaya wato Dr Salman yana can, shi ne yasa ta bi masu ta wannan hanyar ta shiga jikin Rimshar kawai. Kowa na cikin palon mamakin jin sunan Daular Mutuwa yake yi, nan take Imran da Areef suka tuna da labarin da ta taɓa basu a baya, tabbas sun tuna da zancen, dan haka sai suka fara bawa jama'ar palon labarin irin ukubar da su Rimshar suka sha a wajen, shi ma daddyn Jellyn, sai a lokacin ya tuna da cewa tabbas Ayla ta taɓa gaya mashi zancen Daular Mutuwar nan, sosai abin ya dawo masu cikin kwakwalensu. Ganin hakan yasa Malikar ta fita daga jikin Rimshar, tun da sun tuna komai, sai ta kyalesu ta koma gefe kawai tana kallonsu. Jin sunan Daular Mutuwa yasa Hjy Umaiya ta yi wani irin firgita sosai, a tsananin razane ta fara tambayar ina Akila, Akil, da kuma Imran?. Da mamaki suke tambayarta lafiya, bata iya bawa kowa amsa ba, ita dai kawai tambaya take yi ina yaranta. Imran ɗin ne ya ce "Ammie gamu nan ai, lafiya meyake faruwa?". Banda girgiza kai babu wani abin da take yi. "Kai ina Akila? Ya ban ganta a nan ba?". Cewar Akil. Nan fa suka fara waige waige. Shi dai Lion binsu da idanu kawai yake yi, ya rasa meyasa gwaggo ta ce sai dai yazo anyi magana da shi, suna ta surutu suna kara mashi ciwon kai a banza. Wasa wasa suka fara neman Akila, shiru babu ita babu labarinta, nan fa Hjy Umaiya ta birkice masu, ta yi masu karamar hauka, faɗi take yi wlh Queen ta dawo mata da ƴarta, idan ba haka ba, to a wannan karon za su yi kare jini biri jini!!. Zuba mata idanu kawai suka yi suna kallon ikon Allah. Brr Naurat ce ta tambayi Abban Imran wai matar nan tasa lafiyarta kuwa?. Shiru shi ma ya yi ya kasa yin magana, dan kuwa bai san me zai ce ba. Gwaggo ce ta miƙe ta riko Ammien tana tambayarta lafiya? Wacece kuma Queen?. Cikin kuka ta basu amsa da mahaifiyarta ce, kuma ita ce shugabar wannan Daular Mutuwar da Rimsha ta ambata a yanzu. Daga Imran har Areef sai da suka zaro idanu tamkar idanun nasu zai faɗi kasa, irin wannan bala'i na cikin Daular Mutuwar dukka Ammie ta ce uwarta ce shugabansu? Lallai kuwa, akwai cakwakiya. Ita kuwa Rimsha miƙewa zaune ta yi tana karewa Ammien kallo, sai a yanzu komai yake dawo mata sabo, sai a yanzu take kallon tsananin kama na Ammien da kuma Duna, hakan na nufi duna ɗa ne ga Queen? Ko kuma ɗan uwanta ne? Dan sun yi kama sosai......WATA SABUWAR CAKWAKIYA KENAN, ME KUMA YA HAƊA AMMIEN DA DAULAR MUTUWA?. "Abba menene ya haɗa Ammienmu da Daular Mutuwa?". Cewar Imran, da yake shi yasan labarin Daular a wajen Rimsha. Zubawa Abban idanu kowa ya yi yana jiran amsa daga gare shi. "Imran nima ban san me zan ce maku ba, amma ita Ammien taku ce kawai zata iya yi maku bayani". Juyo da kallonsu a kanta suka yi, yau suna ganin tashin hankali, labarin yau kuma ya juya ta kansu Imran.......... TRIPLETS GIDAN SURPRISE, YAU KUMA LABARIN MU YA JUYA TA KAN SU IMRAN, SHIN AKWAI WANDA YA TAƁA TUNANIN QUEEN MAHAIFIYAR AMMIENSU IMRAN CE? TO YAU MA DAI SABUWAR BABIN CAZA KWAKWALWA MUKA BUƊE😂 KU DAI KU KASANCE DA PRINCESS TEEMA KAWAI, NI CE KAƊAI ZAN WARWARE MAKU WANNAN CAKWAKIYA!. Cikin kuka da tashin hankali ta fara magana kamar haka. "Hakika kamar yanda na gaya maku cewa Queen mahaifiya ta ce, to ba shakka hakan ce, mun kasance kabilar igbo mazauna garin Enugu, kuma mun kasance kiristoci ne, karatu ya kai ni Kaduna state, a nan na haɗu da Abbanku, dama already tun kafin na tafi karatu, na san da gidan Daular Mutuwa, kakana ne ya kirkireta, kowa ya san kabilarmu da tsafi kamar baza'a mutu ba, to muma muna ɗaya daga ciki, Mahaifiyarmu, wato Queen, ita kaɗai kakana ya haifa, Shiyasa da ya mutu, sai ta gaji karagar mulkinsa a Daular Mutuwa, ni da kai'na ina zuwa har cikin Daular, kuma a lokacin babu wani abu na tsafi wanda ban iya ba, duk wata tsubbace tsubbace na iya nima, da ni da kanwata, sai kuma wani ɗan uwan mamana, mune na kusa da ita a Daular, a takaice dai na san komai, Allah da ikonsa, da Allah ya so ni da rahama, sai ya jarrabeni da son karatu, ita kuma kanwata, tana tare da Queen a cikin Daular, a gabana za'a yi tsafi da mace, a gabana ake komai na abubuwan subbace subbace da siddabaru, ko a jikina, dan lokacin zuciyar kafurci ne ke gareni, manyan mutane ne suke zuwa cikin Daular dan a biya masu bukatunsu, da akwai manyan manyan gidan matsafa da suka dogara da Daular, akwai abubuwa da dama wanda ni a yanzu na mance da shi ma gabaɗaya, kuɗi kuwa, habawa ai idan munaso ma mukam, zamu iya yin gadon kuɗi ku kwanta, muna da arziki na wuce misali, mu da mumuke bawa wasu ma, manyan mutane daga kasashen dake makwabtaka damu, suna zuwa neman arziki da abin duniya a wajenmu, wasu su kawo ƴaƴan ƴan uwansu mu yi masu kuɗi da su, wasu kuma ƴaƴan cikinsu, abubuwa dai da dama, mun shahara a duniyar tsafi. To a takaice dai sai Allah ya ƙaddara na tafi Kaduna state karatu, a can na haɗu da Abban Imran, wasa wasa muka fara soyayya, ina son shi sosai kasancewarsa Bature, kun san turawa da mugu mugun shiga rai ga farinjini, ga kyau na wuce misali. Daga karshe dai na musulta, saboda da shi, da ya kasance Allah yana sona da rahma, sai Allah ya saka mani kaunar addinin sosai, na yi karatun Alkur'ani mai girma sosai da sosai, ina jin alokacin da akwai abin da ya ɗaukewa Queen hankali, shi ne yasa bata lura da abin da nake yi ba, idan ba haka ba, wlh duk wani motsinmu tana gani a cikin madubin tsafinta, amma ga mamakina har na musulta, na kuma yi karatun addini, kuma bata gane ba. To a takaice dai, lokaci da muka yi hutu, sai Abban ya ce zai bini muje gidanmu ya gaida iyayena, daga nan ayi maganar aurenmu, da yake ni wlh na mance da ya gidanmu ma suke, sai na yarda mashi kawai, na ce muje, ba tare da sanin iyayensa ba, muka kama hanyar Enugu, a ranar naga bala'in da ban taɓa gani ba, dan da muka je gida, Queen ta ce wlh dani da Abban duk kashemu zata yi, to dama na gaya maku already nima a lokacin na iya tsafe tsafen nasu dukka, hakan tasa na yi fito na fito da mahaifiyata, dan na kare Abba kada su kashe shi, duk da na musulta, hakan bai hana ni na haɗa kayan tsafina dan muyi faɗa da ita ba, domin a lokacin a cewata, tsafin ne kawai zai kwacemu daga hannunta, mun sha azaba ta yanda sai da muka koma yin karatun Alkur'ani mai girma, sannan muka iya kuɓuta daga hannunta, a nan ne na kara yarda cewa tsafin ma dukka shirmen banza ne, tun da ga shi ya kasa kuɓutar da mu daga hannunta, karatun Alkur'ani mai girma ne ya kuɓutar da mu, tun daga lokacin sai na kara nesanta kaina da tsaface tsafacen, ita kuma Queen ta sha alwashin da ni da duk waɗan da suka tallafa mani, sai taga bayanmu, ni kuwa na ce mata idan ta fasa bata cika Queen of Daular Mutuwa ba, abin ya yi tsananin kona mata rai, dama kun san yanda kabilar igbo suke da tsananin zafi idan aka ce yau ga nasu ya musulunta, to haka nima dangina suka ɗauki wannan zafin, akwai wani ɗan uwanmu da dama shi zan aura, to da ya ji abin da ya faru, sai ya ce shi ma ba zai kyale Abba da gabaɗaya familynsa ba. In takaice maku dai haka muka baro garin Enugu babu daɗi, da kyar ma muka iya kaiwa airport muka dawo Kaduna, babban abin da ya kara sakawa naji ina son addini musulunci sosai, shi ne yanda iyayen Abba suka karɓeni, basu ji kyamata ba, dan na kasance Kristen kuma ƴa ga magicians, sam ba su guje ni ba, mahaifinsa Dr Salman yana da kirki sosai, ita kuma matarsa Amarya tana da bakar zuciya, sai dai ni ba zata iya cutar da ni ba, saboda already a dafe nake, jinin Queen ce ni, ta dalilina ma asirin da ta yi wa Dr Salman ɗin ya karye, dan wannan a jininmu yake, mune gidan asiri, mune asiri da kanta, duk girman asiri in dai ina wajen, to ba zai yi tasiri ba, ni ban san me Queen ta yi mana a jininmu tun muna yara ba, to haka gabaɗaya su Imran suka taso, ba'a iya cutar da su, saboda jina ne su, in takaice maku ita kanta amaryar sai da ta zo ta kaunace ni fiye da ƴarta Batula, ta soni tamkar ta yi mani numfashi, a gidansu Abba na cigaba da rayuwata har muka yi aure, ƴan uwansa dukka suna kaunata sosai, barema Dr Salman bawan Allah, yana sona sosai, a lokacin ya ce mani yana son matarsa Naurat, amma bai isa ya je kasar Russia ya ce zai ɗauketa ba, idan ya je, ƴan uwanta za su kashe shi, dole ya hakura da ita, sosai a lokacin suka nemi ɗan uwansu Nawazuddeen wanda ni banma san shi ba, na dai ji labarin ya bar gida, amma basu gan shi ba, bayan aurenmu da Abban Imran, daga nan abubuwa suka fara faruwa, haɗarin da Dr Salman ya yi shi da amarya, ina da tabbacin da sa hannun Queen, a lokacin na cewa Abban Imran zan sake komawa ruwa, wato zan haɗa kayan tsafina, dan na yi maganin Queen, saboda idan ba fito na fito muka yi ba, in dai ban rushe Daular Mutuwa ba, to ba zata barni ba, dan ba zata iya yafe ni ba, sosai Abba ya yi mani nasiha, ya kuma yi mani faɗa a kan ko bayan ransa bai yarda na sake komawa tsafi ba, kamar yanda na barta, to ya zamana na barta kenan har abada, sosai naji nasiharsa, dan haka sai na hakura, muka cigaba da rayuwa muna karatunmu cikin farinciki, amma mutuwar Dr Salman ya girgizani, ina tuna bawan Allah nan, mutun mai farar zuciya, sai dai fa har gobe ina jin kamar bai mutu ba, ina ji kamar wata sharrin Queen ta haɗa mana, amma dai Allah masani. (Masu karatu i hope yanzu kun fahimci dalilin kasancewar Dr Salman a Daular mutuwa?) Tun daga wannan lokacin muka cigaba da yin rayuwarmu cikin farinciki, na rike kannan Abba kamar kannena, na mance da tawa kanwar da mahaifiyata, na sami sabuwar ahali, a haka muka kasance har Abbi wato Deen shi ma ya yi aure, ya auro wata ƴar Katsina da suka haɗu ita ma a school, ita ce mahaifiyarsu Irfan, mafadaciya ce sosai, da ta nemi ta kawo mani wargi, na taka mata burki, akwai wata rana da na yi mata dukan mutuwa har sai da aka kai ta asibiti, daga lokacin aka rabamana gida da ita, Abbin ya ɗauketa zuwa ɗaya daga cikin gidajen Dr Salman, in takaice maku labari ni ban sake waiwayar iyayena ba har rana mai kanata yau, na rufe babinsu, kuma nasan wlh Queen ba zata rabu da ni ba, ba shakka ita ce nan ta ɗauki Akila, kuma ita ce ta ɗauki matar Maik, sai dai fa sun canzawa Daular Mutuwa tasu waje, bata a in da na santa da, tun kafin na bar gida dama na ji suna shirye shiryen kara mata wasu matakan tsaro, sannan kuma su canza mata mazauni, a yanzu ita Rimsha ita kaɗai ce zata iya gaya maku in da Daular Mutuwar take, saboda ita ce ta shiga cikin ta kwanannan, amma kuma a gaskiya duk wanda ya shiga Daular Mutuwa ya fito da rai, to dole a jinjina mashi!! Dan duk yanda kuke tunanin Queen ta wuce hakan wlh, sam bata san menene imani or tausayi ba!!. Masu karatu yanzu kun fahimci dalilin da ya sanya waɗan nan dodannin suke zane su Abba? Kun fahimci menene ainahin tushen matsalar? Bari na kara maku wata haske, a duk shekara dama already kun san da cewa dodannin suna zuwa gidan Abba, abin da yasa suke zuwa kuma, saboda tun bayan haihuwar Akila, lokacin sauka daga kan karagar mulkn Queen ya yi, kuma dole sai Ammien su Imran ɗin ce zata karɓi mulkin, dan ita ce babbar ƴarta, ita kuma kunga ta musulta, tama ki yarda ta sake haɗa hanya da su, wannan karya doka da ta yi ne yasa mukarraban Queen ɗin suke zuwa su zaneta, Queen ɗin ma tana zuwa gidan, amma ana ɗaukar lokaci sosai kafin ta zo, har ga Allah tana kaunar Ammien su Imran, shi ne ma yasa bata kashe ɗin ba, ta ke bata wahala dai kawai, kuma tun da Queen ɗin take zuwa kawowa Ammien ziyara, bata taɓa haɗuwa da su Akila ba, saboda rikonsu da addini, sai dai mukarraban tane suka taɓa haɗuwa da Imran, shi ma an samu akasi ya shigo ba tsarki a jikinsa ne, ya gama shan lemon tsaminsa bai yi wankar tsarki ba ne ya shigo cikin palon, kun tuna lokacin da suka taɓa zane shi ko? To lokacin ne suka san Imran ɗin, ai kunga shi Akil yana shigowa suka gudu, saboda yana da tsraki, kuma a lokacin ƙira'ar karatun Alqur'ani mai girma yake sauraro. Abin da ya faru a yanzu a wannan shekara Queen ɗin ta zo kawowa Ammien ziyara da kanta ne, a nan ne kuma taga Ayla, dama kunsan already tana neman Ayla, Rimsha, da kuma Kausar, shi ne yasa ta ɗauki Aylar, da ace Rimsha tana wajen, da ba makawa har da ita za su ɗauka, ita kuma Akila abin da ya sanya Queen ɗin ta iya ganinta har ta ɗauketa duk da tana karatun Alqur'ani mai girma, anyi katari ne da Queen ɗin ta kawo ziyarar dai'dai lokacin da Akilar take period, wato bata da tsarki, shi ne yasa ta samu damar ɗaukarta, ita Kausar dama already sun ɗauketa da jimawa, dan ba wani riko da addini ke gareta ba, yanzu Rimsha, Imran, Akil, su Queen take hari, ita Rimsha kun sani saboda karya mata record na gidanta da ta yi ne yasa suke son kamata, su Imran kuma, saboda ƴaƴan Ammie ne, idan baku manta ba dama Queen ɗin ta ce ba zata taɓa barin Ammie da duk wanda ya goya mata baya or yake kaunarta su zauna lafiya ba, shi ne yanzu dataga su Imran, sai take son ɗaukesu gabaɗaya, kuma dukkansu tsafi take da niyar yi da su............. (Jama'a za'ayi tsafi da Shaikh Akil fa😂mahaddacin Alqur'ani mai girma, mu gayawa Queen ba zata iya bane? Ko kuma mu bari duniya ta gaya mata? Dan in har ta ɗauki waɗan nan malamai guda biyun, wato Akil da Imran, to tana tsaka mai wuya, dan fa Alqur'ani mai girma ba wasa ba!!) Allah sarki Ammie duk zaneta da dodannin nan suke yi, ba zata iya tuna wannan ba, saboda goge mata shi ake yi a cikin ƙwaƙwalwata, baiwar Allah, ita ma ta sha kuncin rayuwa ba karya, kuma hakika Allah yana sonta da rahma, har ta fito daga kabilar igbo, kuma matsafiya, sannan ta musulta, ta kuma rike addinin da kyau, kai gaskiya ta zama zakarar gwajin dafi! Ba abin da zamu ce mata face Allah ya daɗa kareta daga sharrin Queen! Amma dai Ammie ta yi kokari na wuce misali!". Salati su gwaggo suka sanya, abin gabaɗaya ya sanya sun rasama ina za su kama, sun rasa abin faɗe. Ita kuwa Ammien, kuka take yi sosai tana faɗin wlh a dawo mata da Akilarta, ta san ba makawa kasheta Queen zata yi, dan ba imani ne da ita ba, in kuma ta kashe Akila, to wlh ba zata rabu da su ba! Shi ma Aseef kuka ya saka masu a kan wlh shi dai a nuna mashi ina ne wannan Daular Mutuwa ya je ya ɗauko matarsa, dan wlh shi ba zai yarda ba, in suka taɓa ko da mayafinta ne, duk sai ya kashe su........... E LALLAI ASEEF BAI SAN SUWAYE NE A CIKIN DAULAR MUTUWA BA, JAMA'A MU GAYA MASHI NE, KO DAI MU BARSHI YA JE ƊAUKO AKILA?😂 HAR DA WANI CEWA ZAI KASHESU HMMM QUEEN TA WUCE TUNANIN NAI TUNANI. ita kuwa Rimsha, ganin Ammien Imran tana zaune kusa da Abba dake kusa da daddyn tane, yasa ta bar jikin daddyn nata da gudu, a dubu ta je ta ƙanƙame gwaggo tana ihu a kan tashiga ukunta, su taimaketa, tun da an ɗauki Ayla, yanzu ita kenan za'a ɗauka next, wlh bata son koma Daular Mutuwa, kashe mutane ake yi a can! Umaisha ma dai guduwa ta yi daga kusa da Ammien, saboda sun tsorata da jin labarin Daular Mutuwa. Yau Ammie ta zama dodo a wajensu, har surukanta suna gudunta. Rimsha baiwar Allah, tamkar zautatciya ta zama masu a cikin palon, sai surutai take zubawa marasa kan gado. Riketa sosai gwaggo ta yi tana ambatar sunanta, ina ai tun da ta ji Queen na kawo wa Ammie ziyara, shikenan kuma ta birkice, zunduma ihu take yi tsakaninta da Allah, ita kaɗai tasan bala'in Daular Mutuwa, su dan basu sani bane, bata fatan ta sake komawa can baiwar Allah......GA ABIN DARIYA, GA ABIN TAUSAYI. Karin wani haske, zaman Rimsha a gidansu Imran, Malika ce ta taimaka mata har tasa Queen bata ganta ba, Malika ce tasa Ammien ta ce bata son Rimshar, ta yi hakan ne kuma dan bata son Rimshar ta zauna da Ammien inuwa ɗaya har Queen ta kawo ziyara ta ganta su ɗauketa, to kun ji yanda aka yi da kuma dalilin da yasa Ammien ta ce bata son Rimshar, Malika ce sila, na san kowa yana son sanin ainahin wacece Malika, to muje dai zuwa, lokacin sani ya kusa.......... LALLAI AKWAI CAKWAKIYA, AYLA TANA TSAKA MAI WUYA, NA FARKO SUN KARYA RECORD NA QUEEN, NA BIYU KUMA TA ZO TA SHIGA CIKIN FAMILYN DR SALMAN A MATSAYIN SURUKA, FAMILYN DA QUEEN TA FI TSANA FIYE DA KOWA A DUNIYA, ITA MA RIMSHA TANA TSAKA MAI WUYA, DA CAN BAYA QUEEN BATA SAN CEWA RIMSHA ƊAYA DAGA CIKIN FAMILYN DR SALMAN BANE, KAWAI TANA NEMANTA NE DAN RECORD NATA DA SUKA KARYA, YANZU KUMA, TA GANE TANA ƊAYA DAGA CIKIN FAMILYN DR SALMAN, KUNGA KUWA BA ZATA KYALETA BA, LALLAI AKWAI CAKWAKIYA, AKILA KAM BA'A MAGANA, GATA ƳAR AMMIE, GATA JIKAR DR SALMAN, TAB AKWAI CAKWAKIYA, ITA KUMA RIMSHA, GA SU JOSEPHINE A GEFE SUNA HARINTA, WASAN YANZU ZAI ƊAUKI ZAFI JAU, HAR YANZU AKWAI SAURAN RINA A GABA BA KAƊAN BA, DAN HAR YANZU BASU SAN CEWA DR SALMAN YANA RAYE BA, GA KAUSAR ƳAR YARABAWA MA QUEEN TA DAUKETA, TA YI TSAFI DA SUNE KO SUNA RAYE? ALLAH MASANI, SAI KUMA ALKALAMIN PRINCESS TEEMA, WAI SHIN YANZU A INA MA DAULAR MUTUWA TAKE? RIMSHA ZATA SAN HANYA NE? KADA KU MANTA DAJI SUKA BIYO, SU KANSU BASU SAN WANI HANYA BANE, TSAWON KWANAKI SUKA SHAFE SUNA TAFIYA, ZATA IYA SANIN TA INA SUKA FITO NE MA? WAYE ZAI JE ƊAUKO AYLA DA AKILA? NA BARKU HAKA NAN, KADA NA KARA CAZA MUKU KAI, MA'ASSALAMA!!. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E10 Date: 20/4/2024 Ihu sosai take zunduma, sai ƙoƙarin dannanta gwaggo take yi, amma ina, taki tsayawa. Da dai Lion ya lura ita fa Rimsha sam bata a cikin hayyacinta, ta ruɗe masu ne sosai, ga shi sai tumurmusa masu jikin mommansu take yi, kamar wadda ake hurawa wani abin a kunne, haka take tsalle tana ihu, sai ya kai hannu ya rikota da hannu ɗaya, a lokacin kuma su Abba duk sun yunkura zasu karɓeta daga hannun gwaggon, saboda gwaggon ba zata iya riketa ba. Ganin Lion ya riketa ne yasa kowa ya fita harkarsu, dan duk wanda ya kwana ya tashi a wannan gidan, to yasan waye Lion, so basu ma son wani abin ya haɗasu, basu yarda hanya ta haɗasu. Jawota jikinsa ya yi, ya haɗa hannayenta dukka biyu da take ta faman yarfarwa tana ihun nan, haɗesu ya yi ya rike da hannunsa ɗaya yana tofa mata addu'a, saboda ya samu ta nutsun mashi. Shiru palon ya yi na ƴan mintoci, ban da kukan Rimshar da yake tashi kasa kasa, babu wani motsi da zaka ji a palon, tamkar babu mutane, kowa ya zubawa Brr Naurat idanu, ita kaɗa suke jira ta yanke hukunci, daga nan sai a san abin yi. Shi kuwa Lion, sai da ya tabbatar ta dawo dai'dai, sannan ya dakata da tufa mata addu'a yana kallon face nata, idanunta a rufe ruf, da alama ma barci ya ɗan yi awon gaba da ita. A hankali ya ɗago da kallonsa izuwa kan Brr Naurat dake ta kallon shi ita ma. Kowa binsu da idanu yake yi sosai, sun ƙagu su ji menene abin da zata ce. Ita kuma shiru ta yi tana nazarin maganganun Ammien, ta ɗan ɗauki lokaci kafin ta fara magana cikin nutsuwa. "Tun farko kune ma muka yi kuskure, ko in ce shi Abba shi ne ya yi kuskure, tun da ka san ga daga in da ka ɗauko mace, ai da sai ka san irin babban matakin da ya kamata ka ɗauki, wani faɗan ai baka isa ka yi shi kai kaɗai ba, tun kafin ka shiga gidanka da kuka zauna, sai ka sanya ayi maka saukar Alqur'ani mai girma, ayi walima ayi maku adduo'i, ta yanda zaku ɓacewa ita Queen ɗin gabaɗaya, karfin addu'a zai taimaka maku Allah ya tsareku, sauran ƴan uwanka ma, sai ka gaya masu su ga halin da ake ciki, sai suma su shirya su tsananta addu'a, tun da a gaban idanunka Queen ɗin ta sha alwashin ba zata rabu da kai da familynka ba, sai baka yi hakan ba, ka ɗauka abin wasa ne, yanzu koma me ya faru da ƴan uwanka, to laifinka ne, dan su basu san ma daga ina take ba, suna rayuwarsu ne yanda suka saba, kuma shi karatun Alqur'ani sai wanda yake da kokari sosai ne yake iya yinsa kullum, saboda shaiɗan ba zai barsu ba, amma kaga idan sun san da wannan matsala, dole za su yi taka tsantsan sosai, dole zasu yi ƙoƙarin yin addu'a sosai, za su kula da askar, dan su kare kansu daga irin wannan musifu haka". Ta kai karshen maganar tana mai kara jinjina wannan al'amari, dan ita wlh sam bata taɓa tunanin ire iren waɗan nan matsafa akwaisu a gaske a zahiriya ba, kun san Turawa dama, su sam basu damu da irin waɗan nan shirme ba, to yau dai ga shi ta samu gagarumar matsafiya a cikin surukanta!. (Anya da Brr Naurat tana nan a lokacin zata yarda Abba ya auri Ammien kuwa?🤔 Shiyasa Allah ya kawar da ita a lokacin, ta koma kasar Russia, domin rabon su Imran da yake a tsakanin Abba da Ammien, kun san shi fa rabo har kisa yanayi, to Allah ya ƙaddara akwai auren ne, shi ne ya matsar da Brr Naurat, dan yasan ba zata taɓa yarda da auren ba!!) A hankali sautin zazzaƙar muryar Rimsha ya fara tashi, kasa kasa take magana ta lafe a jikin Noorish nata. "Noorish Allah ni bana son komawa Daular Mutuwa, please kada ka bari Queen ta ɗauke ni, Allah Duna ya ce mani cinyeni zata yi idan na sake komawa". Tana magana wasu siraran hawaye suna zubo mata a kuncinta. Shafa face nata ya yi tare da goge mata hawayen, a hankali ya motsa laɓɓansa, ba sai na sake faɗa ba, dama kun sani already shi idan yana magana, kasa kasa yake yinta, idan ba kana kusa da shi sosai ba, to ba zaka taɓa jin meyake faɗa ba, a yanzu ma haka ne, duk cikin palon ban da Areef dake zaune kusa da shi sosai, to babu wanda ya ji abin da ya ce mata, kasa kasa ya yi maganar. "Babu wanda ya isa ya mayar mani dake can, just calm down kin ji ko?" "Noorish Allah tsoro nake ji". Ta yi maganar tare da kankame shi sosai. Tabbas yaga tsananin tsoro kwance a cikin idanunta, hakan ya kara tabbatar mashi da cewa ba ƙaramar ɓarna suke aikatawa a cikin wannan Daular Mutuwar ba!,. "Meesha bai kamata ki ji tsoron wani abin ba idan kina a tare da ni, ba zan bari ayi maki komai ba". Ya yi maganar yana mai cigaba da goge mata hawayen da suke ta gangaro mata. "Is okey, a tsayar da kukan nan haka nan". Ya kai karshen maganar yana ɗago da idanuwansa izuwa kan Brr Naurat dake kallonsu. "Brr just close this case like that, ni ban ga abin dawo da abin da ya wuce ba, a have alot of things da nake son zuwa na yi, so momma I will going to leave". Cewar Lion ɗin. "No Saif, wannan ba shi ne maganar da na kiraka ka zo mu yi ba, tsaya ka ji maganar mana". Cewar gwaggon. Shiru ya yi bai sake magana ba. Rimsha ce ta sake ce mashi "Noorish am feeling hungry too much". "Okey you can go and eat". Ya bata amsa. Su Imran dai mamakin Lion ya hanasu yin magana, wai yau shi ne ya zauna yake hira da mace haka, macen ma ƴar yarinya kamar Rimsha, komai ta ce mashi zai bata amsa, mutumin da a baya sai ka yi magana goma sannan yake bada amsa ɗaya, ba ya taɓa baka amsa a kan kowace magana, wani lokaci ma amsar ma ba zaka samu ba, amma ita Rimsha kowani maganarta sai ya amsa, Allah mai iko!!. Zaro idanu ta yi tana faɗin "No ina tsoro sosai gaskiya, ba zan iya zuwa kitchen ba". Shiru ya ɗan yi kafin daga bisani kuma ya sake cewa "Jeki cikin ɗaki, a cikin trolleyna da muka je Abuja dake ɗin nan, ki duba zaki ga wani littafin adduo'i, ki ɗauko ki kawo mani bari na koya maki wata addu'a dan ki rage tsoro". Kasancewar a palon sama suke, sai ta ji tsoron ya ragun mata, dan daga palon suna iya hango cikin bedroom ɗin nasa, so tana jin motsin mutane, dan haka sai ta miƙe ta nufi cikin bedroom ɗin. Su kuma suka cigaba da tattaunawa, ana mai da yanda aka yi wasu abubuwa a baya. Da shigarta ɗakin bai fi da minti uku ba, ta zunduma wani irin uban ihu mai tsananin rikita ƙwaƙwalwa. Mazan dake a cikin palon suna yunkurin mikewa su nufi cikin bedroom ɗin, sai gata ta fito a guje. Tsayawa suka yi suna kallon ikon Allah, kowa ya yi tunanin wani abin ne ya kamata, ko Queen ce ta ɓullo a gabanta, amma sai suka ga akasin haka, gata ta fito lafiya lou hannunta na rike da wasu hotuna tana zunduma ihun kuma again. Bata zame ko'ina ba sai wajen daddynta, jikinsa ta faɗa tare da miƙa mashi hoton, tana kuka tana faɗin "Daddy wlh tallahi wannan ma ɗan uwan su Queen ɗin Daular Mutuwa ne, na gan shi a cikin Daular Mutuwar, sunansa baba, muna zama muyi hira da shi ni da su Ayla, Allah ban manta shi ba, wayyo nashiga uku, yanzu kenan har ɗakin yaya Saif akwai ƴan Daular Mutuwa a ciki, daddy Dan Allah mu koma gidanmu na Abuja kawai, ni dai wlh bana son Daular Mutuwar nan". Tun da ta fara surutan nan suka zuba mata idanu, baiwar Allah duk ta firgice yau. Shi kuwa daddy karɓar hoton ya yi dan ya kalli wanene. Ai kuwa yana gani ya yi wani irin zabura, a hanzarce ya sauketa daga jikinsa tare da miƙewa tsaye yana faɗin "Daddy kuma a Daular Mutuwa?!!". Da sauri shi ma Abba ya karɓi hoton yana kallo, zaro idanu shi ma ya yi ganin cewa hoton Dr Salman ne, to su a saninsu mutuwa Dr Salman ya yi, ya haka kuma, anya Rimsha shi ta gani kuwa? Wannan shi ne tambayoyin da suke yi wa kansu. Masu karatu idan baku manta ba, time da Lion ya je Abuja, akwai wasu hotuna na familyn daddyn Rimsha daya kwasa daga ɗakin mum, kun tunasu? To a cikin waɗan nan hotunan ne da akwai hoton Dr Salman, shi ne yanzu da ta je ɗaukar littafin addu'ar, sai taga hoton, ita kuma kunga yanzu tunanin Daular Mutuwa kaf ya dawo mata a cikin ƙwaƙwalwata, ta san Dr Salman a can, tana tsaka da kallon hotunan ne, sai taga hotonsa a ciki, kunga kuwa dole ta birkice ai, tun da ita dai a Daular Mutuwa ta san shi, yanzu kawai taga hotonsa a cikin trolleyn Noorish nata, ai dole ta yi hauka, dole ta yi tunanin ko dai ƴan Daular Mutuwa sun fara biyota har nan ne kuma, to shi ne abin da ya faru. Mamaki ya hana kowa magana, sun jima shiru kamar waɗan da ruwa ya cinyesu, sai al'ajabin wannan al'amari suke yi. Can Brr Naurat ta ce "Meesha kin tabbatar shi kika gani a can?". Da sauri Lion ya ɗago idanu yana kallon Brr, saboda ya ji sunan da ta kira Rimsha da shi, shi dai yasan sunansa ne, shi kaɗai yasa mata wannan suna. (Brr Naurat ya da haka kuma? Ina ruwanki da sunan masoya?🧐) Tamkar Brr tasan kallon me yake yi mata, sai ta ce "Ka yi mani kishi, na yi shiru bai yi magana ba, har da sake mata suna, to ba zai yiwu ba, nima dole ka sake mani suna, kuma nima da wannan suna zan kirata, dan ni ce uwar gida ai, duk ido zan saka maku". Kawar da kallonsa ya yi ba tare da ya yi magana ba, wannan tsohuwa akwai sa ido, ya faɗa a cikin zuciyarsa, a cikin jirgin ruwa fa ta ji yana faɗin Meesha, shi ne har ta rike sunan, Brr kenan!. Cikin kuka Rimshar ta ce "Brr wlh shi ne, shi ne baba na Daular Mutuwa, Allah ban manta shi ba, kullum yana zaune a ɗakinsa, ya tsufa, muna zuwa mu yi hira da shi". Ammie ce ta karɓi zancen da cewa "Ba shakka tun da Rimsha ta faɗi haka, to wlh haka ne, ni dama na ce wannan accident ɗin shirya shi Queen ta yi, ai kunga ko gawar Dr dama ba'a kawo mana ba, sai dai aka ce babbar motar da ta bi ta kansu ta yi raga raga da su over, sai dai kasusuwansu, to wlh ba shakka Dr Salman yana raye, kuma yana cikin Daular Mutuwar kamar yanda Rimshar ta faɗa!". Jin ance wannan baban kakanta ne yasa ta sake zunduma ihu tana faɗin "Wlh ba kakanmu bane, shifa yaron Queen ne, dan Allah ku dai'na cewa kakanmu ne, a Daular Mutuwa fa yake, wai daddy ka san Daular Mutuwa nan kuwa? Wlh ina gaya maka shi ma baban namar mutane yake ci, dan Allah ku dai'na cewa kakanmu ne, ni kam zan mutu yau". Ganin suna neman su juyawa Meeshansa kwakwalwa, suna neman su sanyata ta birkice gabaɗaya, sai ya miƙe tsaye tare da nufar in da take, hannu yasa ya saɓeta a kafaɗarsa, sai kuka take yi, ya wuce da ita izuwa bedroom nasa. Jama'ar palon ma babu wanda ya lura da su, sai jajanta wannan al'amari kawai suke yi a tsakaninsu. Yana shiga ya shinfiɗeta a saman bed nasa, sannan shi ma ya haye. Rikota ya yi tare da fara yi mata raɗa a kunne, kan kace me, sai gata ta koma sakin murmushi, ga guntun hawaye a gefe, ga murmushi kuma a gefe, jim kaɗan ka fara dariya har da kyakyatawa, tamkar ba ita ce yanzu take zunduma ihu a palo ba, kome Noorish ɗin nata yake ta gaya mata a kunnen?. Juyowa ta yi da kyau ta shige jikinsa tana faɗin "Amma Noorish ba'a jirgin ruwa zamu tafi ba ko?". Shiru ya yi yana kallon kyakkyawar face nata, duk hawaye ya bubbushe. "Bakison tafiya a jirgin ruwa ne?". Jinjina mashi kai ta yi tana faɗin "Ina tsoron mu nutse kasa ne". Shiru ya ɗan yi na ƴan mintoci kafin ya ce "Ba kina son shiga cikin ruwa ba? Idan mun nutse ai sai ki yi wanka ko?". Turo baki ta yi tana faɗin "A'a ba irin wannan ruwa ba". Shiru ya yi yana ta kallonta. "I like your lips". Ya faɗa a sanyaye. Ɗago idanunta da suke jajir saboda kuka ta yi, kai tsaye cikin idanunsa ta kai kallonta, ya tsareta da ido sosai. "Noorish nima lips naka suna yi mani kyau over". Gyara kwanciyarsa ya yi, a in da ya rage tsawonsa, ya zama face nasu tana dai'dai da juna. Zubawa juna idanu kawai suka yi, suna zuba kallon tsantsar so da kaunar juna. Romeo and Juliet kenan!. Sun ɗan ɗauki lokaci a haka kafin ita ta kawar da kallonta tare da shigewa cikin jikinsa tana dariya. Hannunsa ɗaya ya ɗaura a saman bayanta yana shafawa tare da ɗan ciza laɓɓansa na kasa kaɗan. A can palo kuwa, cigaba da maganar neman mafita ta yanda za'a ɗauko Dr Salman suka rinƙa yi. Sai can Areef ya ce masu dan Allah su bar mutane su huta haka nan, ai sun san cewa ko babu kowa nasu a cikin Daular Mutuwar nan, in dai Lion ya ji abin da ake aikatawa a ciki, to zai san yanda za'ayi a ruguje gidan, ballantana da akwai nasu har rayuka uku a ciki, bugu da kari kuma da akwai matar Aseef a cikinsu, ai dole ko ba zasu yi rai ba, dole su fito da su, dan haka shi dan Allah su dai'na damunsa da zancen wannan gida ta Mutuwa, idan suna magana, jikinsa har tsuma yake yi, ji yake yi ba zai iya hakuri ba, ji yake yi a yau zai tafi ya ɗaukowa Aseef matarsa, ya kuma kashe Queen ya ɗauko Dr Salman. Gwaggo ce ta danne shi, dan ba shakka suna kara ɓata mashi rai idan suna maganar, ji yake yi tamkar ya tashi ya tafi a lokacin. Miƙewa ya yi yana faɗin "Baby yunwa nake ji, na dawo baki bani abinci ba". Ya yi maganar yana kallon Jehan. Harara ta wurga mashi, zata yi magana idanunta suka sauka a kan mummynta, fasa yin maganar kawai ta yi. Wucewa ya yi yana faɗin "Dan Allah kowa ya je ya ɗan huta, kunga lokacin yin sallar mangariba ta kusa, ku huta kafin lokacin ya cika, maganar nan ta isa haka, tun da mun gano matsalarmu, to In Sha Allah zamu yi maganinta cikin gaggawa". Ya kai karshen maganar tare da sauka izuwa bedroom nasa. Gwaggo ce ta haɗa kan gabaɗaya matan, ta ce masu su je bedroom nata su huta, ina nufin su Ammie, Mummyn Rimsha, Aunty, da kuma mummy Anaya kenan, sune suka bi gwaggo, su kuma su Jelly, Anaya, Zaira, Umaisha, Jehan, suka wuce bedroom nasu Rimsha, Imran shi ya raka su Abba boys quarters na gidan, sannan ya wuce izuwa harabar gidan, dan ya sha iska abinsa, Aafia kuwa tana ɗakin gwaggon, dan dama tun shigowarsu aka kaita can, sai zuba barci take yi baiwar Allah, har wa yau, uncle Herry yana tare da Dr William a ɗakinsa, Dr William ɗin ya farfaɗo, amma ƴaƴan nasa sam sun ki zuwa wajensa, bare ma Lion, sam baya son haɗa hanya da su, ɗan gara Areef ma, time to time yana zuwa ya duba shi, wani likita Lion ya sanya aka kawo yana kula da shi, amma shi ko leƙawa yaki ya yi, daddyn kuma ba shi da burin da ya wuce ya ga yaran nasa, yana tsananin kaunar TRIPLETS nasa fiye da tunanin mai tunani, Aseef kam kowa ya sani, ɗan baruwana ne, yana can wajen gwaggo, dan haka shi yama mance da Dr William abinsa, yanzu ma da kyar suka lallaɓa shi ya wuce bedroom nasa, ban da haka ya ce shi wlh sai ya je Daular Mutuwa ya ɗauko matarsa. Wanke Jehan ta je tayi, bayan ta fito ta duba time, karfe 6:10pm, mangariba ya kusa, ga shi Areef ya ce mata yana jin yunwa. Sauri sauri ta shirya cikin kananan kaya, sannan ta ɗaura after dress a samansu, sai binta da kallo su Jelly suke yi, ita kuwa, basu isheta kallo ba, ba wanda ya sami kallon arziki a cikinsu daga wajenta, tamkar ba ƴan uwanta bane, kun santa dama da iya tsare gida da jiji da kai, to ko sannu bata ce da su Umaisha ɗin ba, haka ta gama abin da zata yi, ta zuba perfume kamar ba gobe, sannan ta fito izuwa cikin kitchen, kafanta na sanye cikin flat shoe mai matuƙar kyau na Rimsha, dan ita bata da kaya a gidan har yanzu, kuma bata ce a saya mata ba, dana Rimsha kawai take amfani, duk da sun yi mata kaɗan, haka take sanyawa. Abinci mai rai da lafiya ta shirya mashi a saman tray, sai dai dukka zaɓinta ta ɗebo, dan ita bata ma san irin abincin da yake so ba, shi ne yasa ta ɗauka mashi zaɓinta. Ɗauka ta yi ta nufi waje, kai tsaye bedroom nasa ta nufa. Baki ɗauke da sallama ta shiga ɗakin, wayam babu kowa a ciki, bata yi mamaki ba, dan tasan halinsa da son ƴan uwansa, wata kila ya tafi wajensu ne. A saman carpet ta ɗaura mashi abincin, sannan ta koma saman bed nasa ta bakin ta zauna, sai kallon ɗakin take yi, ko'ina tsab kamar sabo, sai tashin daddaɗar kamshi mai kwantar da hankali yake yi, ga sanyi Ac mai ratsa zuciya. Ta ɗan yi nisa cikin tunanin irin kyawawan halayensa da kuma tsanar madarar kyau da Allah ya yi mashi, kamar daga sama ta gan shi a gaban mirror yana tsaye, ya bata baya, kugunsa na ɗaure da white towel mai matuƙar kyau, daga wanka ya fito, jikinsa duk danshin ruwa, ga gashin kansa yana ɗan zubar da ruwa. Kallo ɗaya ta yi mashi ta yi saurin kawar da kanta gefe guda, har cikin ranta ta tsorata da ganin kyakkyawar kuma kakkarfar surar jikinsa, suna da halitta mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali over. Ganin kamar baya kallonta ne yasa ta mike a hankali dan ta bar ɗakin, saboda ta lura shi fa tsab zai iya yin komai a gabanta, dan ba kunya ne da su ba. Tana tafiya tana tunanin irin yanayin jikinsa da ta gani, duk da kallo ɗaya ta yi mashi, amma ya tsaya mata a rai, jikin nasa kamar madara, soft skin nasa luwai luwai da shi. A dai'dai tsakiyar ɗakin, bata yi aune ba sai ji ta yi ya rungumeta ta baya tare da zuro hannayensa a saman shafaffen cikinta, a hankali ya kwanto da kansa a saman shoulder ɗinta. Dogon numfashi ta ja tare da saukewa a hankali, ya sanya mata sanyin gashin kansa a wuya. "Hyyy baby, ina zaki je kuma?". Ya yi mata maganar a cikin kunne. "Zan fita ne na baka waje ka shirya". "Ni nace maki ina son ki bani waje ne?". Ya kai karshen maganar tare da sumbatar lallausan wuyarta. Shiru ta yi bata bashi amsa ba. "Ina abin da kika ajiye mani? A waya kin ce kina kewata, na dawo kuma shi ne ba zaki zo ki ganni ba, sai da na roka ko? Na rokanma kin zo kuma zaki tafi tun ban ganki ba, kin san adadin kewarki da nake yi kuwa? Kin san me nake ji kuwa?". Hannayenta ta ɗaura a saman nasa dake saman flat tummynta, kasa kasa ta ce "To ka bari sai ka gama shiryawa zan dawo, sai muga juna". "Why ba zaki zo ki tayani shiryawa ɗin ba? Yakamata ace kin saka mani kaya da kanki, please mana my baby". Kasa jurewa ta yi, dan wlh tana tsananin kewarsa sosai, ga shi yanda yake yi mata magana a cikin kunne kasa kasa, duk sai ya kara tsumata, hakan yasa ta kasa jurewa, a wannan karon ta kasa dannewa sai da ta juyo ta faɗa saman faffaɗar kirjinsa da kyau. Ajiyar zuciya ya sauke tare da rungumeta da kyau da kyau, tamkar wani ya ce zai kwace mashi ita. Da yake ita tana da tsawo sosai, Kamar gwaggo take, tafi Rimsha tsawo, sai tsayinta ya kai ta kwantar da kanta a saman ɓul ɓul ɗin breast nasa. Hannu ya kai saman bayanta yana ɗan shafawa izuwa mazaunanta masu burge shi, kowa yasan matan turawa basu da halittar mazaunai sosai, shiyasa dirarren halittar su Rimsha yake ɗaukar hankulan TRIPLETS over, suna son mazaunan nasu sosai, barema Rimsha, Jehan, Akila, Umaisha, sun fi kowa diri a cikinsu, tamkar su suka yi wa kansu....... "Baby". Ya ambata a hankali, kasa kasa ta amsa mashi da na'am. "Zaki tayani saka kayan?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce e zata taya shi........... JEHAN DUNIYA, BAFA ABIN DA YARINYAR NAN BATA IYA BA, KAWAI TSIYA CE IRIN NATA, SAI TA NUNA KAMAR MA BATA SAN KOMAI BA, SABODA SHEGEN JAN AJI DA TSARE GIDA. Ɗaukarta ya yi cak, sai cikin dressing room ya sauketa, dressing room ɗin nasa sak irin na Lion. "Ki zaɓa mani kaya to". Ya faɗa tare da harɗe hannayensa a saman kirjinsa. "To ka rufe idanunka". Ta faɗa tare da wucewa izuwa wajen kayan nasa. Ba musu ya rufe idanuwan nasa, yau wani irin daɗi yake ji, saboda ta bashi kulawa, babu tsawa, babu tsiwa, babu haɗe fuska, bai san cewa ita ma sonsa yana neman yi mata illa bane yasa ta nema wa kanta mafita, yasa ta saduda ta fawwalawa Allah ta dawo ta fara kula da shi...... NI KO NA CE WAYE YA GAYA MAKI SOYAYYA WASA CE? DA KI CIGABA DA JAN AJI MANA, DA KIN MUTU A KAN SON SHI😂 KEBAKI GA AYA A KAN GWAGGO BANE? HAR YANZU SON DR WILLIAM NATA TAKE YI BAIWAR ALLAH, SO AI BA'A YI MASHI GARAJE! YANZU ZAI YI MAKA ILLAH, BA'A WASA DA ZUCIYA!. Wandon jeans baka da T-shirt sky blue masu matukar kyau ta ɗauko mashi, kusa da shi ta dawo, yana tsaye ya datse idanunsa yana jiranta. Kasa kasa ta ce "To ai ka fini tsawo, kuma ni ban san ta yaya zan sanya maka kayan bama". Idanunwansa a rufe ruf ya bata amsa da cewa "To yanzu dai kin yarda na buɗe idanuna? Sai na nuna maki yanda zaki saka mani". E ta amsa mashi da shi. Buɗe idanun nasa ya yi tare da matso da chair dake kusa da wajen watchs nasa, ya zauna a saman chair ɗin yana kare mata kallo. Ita kuma babu abin da take kallo a jikinsa saman da ɓul ɓul ɗin breast nasa, mamaki suka bata yanda suke ɓul ɓul kamar na mace. Jehan akwai dakiyar zuciya, ba irin Rimsha ba, da Rimsha ce ba zata iya tsayuwa tana ganinsa babu riga a jikinsa haka ba, tun da Rimsha take da Lion bata taɓa ganin surar jikinsa babu riga ba, ba zata iya ba, ita kuwa Jehan kun sani ba sai na sake faɗa ba, fin haka ma ta gani, ita da har video ta yi wa babban mutun tsirara a gidan Hjyr daɗi, ko kun manta ne? To na tuna maku,.....(Ita Jehan harta gogan nasu ma ta san ya yake abinta😂😂) Ganin tana ta satar kallon kirjin nasa da mamaki a face nata ne yasa ya kai hannu ya jawota jikinsa. Zaunar da ita a saman cinyarsa ya yi, cikin sanyin murya ya ce "Sun yi maki kyau ne kike ta kallonsu?". Hannu ta kai tana shafa kyakkyawar bakin gashin dake kwance a kirjin nasa. "A'a sun ban mamaki ne". Ta bashi amsa. Shi kuma jin saukar lallausan hannunta a kirjinsa ne yasa ya furta ash tare da datse idanunsa yana mai kara kankameta. (Da alama zancen Imran gaskiya ne, da ya ce wa Areef ɗin dan bai samu dama a wajen Jehan ɗin bace yasa yake cewa zai barta sai ta girma😂) Jin abin da ya furta ne yasa ta yi saurin zame hannunta daga wajen tare da yin ƙoƙarin barin jikin nasa, kankameta ya yi tare da riko hannun nata ya ɗaura a saman breast ɗin nasa, kasa kasa ya ce "Ina zaki je?". Ɗago idanu ta yi tana zubawa face nasa kallo, idanunsa sun sauya launi izuwa jajir, shi ma ya zuba mata idanu yana kallonta. Kasa kawar da kallonta ta yi, shi ma ya kasa kawar da nasa kallon. Almost 5 mins suna a haka, kirar sallar mangariba ce ta dawo dasu daga duniyar kallon soyayyar da suka faɗa. Da sauri ta sauke idanunta kasa tare da yunkurawa zata miƙe, sam bai hanata miƙewa ba, dan baya wasa da lokacin Sallah, tun da ankira sallah, to komai dole ya tsaya sai ya yi sallah. A hanzarce ya miƙe tare da karɓar kayan da ta fito mashi da su ɗin, cikin sauri ya sanyasu, ita kuma ta nufi waje. Ko da ya gama shiryawa ya fito, bata a cikin ɗakin, waje shi ma ya nufa dan zuwa masallaci, a palo ya ci karo da Lion ma ya fito. Babban abin burgewa da TRIPLETS shi ne. ba su wasa da lokacin sallah, kome suke yi, in dai an kira sallah, to bari suke yi su je su yi sallah, shi ne yasa a koda yaushe Allah yake karesu daga duk wata musifa da zata tinkaresu, dan Ubangiji ya ce duk wanda ya tsayar da sallolin farillah guda biyar ɗin nan a rana, yana yinsu a kan lokaci, yana kula da su, yana yinsu yadda yazo a rubuce, to ba zai taɓa taɓewa ba, ba dan haka ba, wlh da TRIPLETS izuwa yanzu ba zasu kai labari ba, da angama da rayuwarsu, amma saboda riko da addini, gasu nan a tsaye gam, ko jijjiga basu yi ba bare rashin lafiya, kai addinin musulunci duniya ne jama'a, TRIPLETS suna mugun burgeni wajen riko da addininsu, yanzu dai da wani ne yanda Areef yake da Jehan, yanda bata taɓa bashi fuska ba sai yau, da wlh ko ya ji an kira sallah ba zai rabu da ita ya tafi masallaci ba, ko yaya sai ya tsaya ya ɗan cigaba da wasa da ita tun da yau dama ta samu, amma shi ina, sallah tana gaba da komai a wajensa, ya fifitata sama da komai, bayin Allah, Allah Ubangiji ka bamu ikon riko da addininmu hannu goma goma ma idan akwai, ka bamu ikon tsayar da sallah a kan lokaci, dan yin sallah a kan lokaci, tana tare manya manyan musifu dake dinfaro bawa. Gabaɗaya mazan fitowa suka yi suka tafi masallaci, su kuma matan suka yi sallah a gida, bayan sun dawo daga masallaci ne kowa ya wuce bedroom nasa, da yake boys quarters ɗin ɗakuna uku ne a kasa, ɗakuna biyu a sama, sai daddyn Rimsha da daddyn Anaya suka ɗauki ɗaki ɗai'ɗai a sama, kasan kuma Abban Imran ya ɗauki ɗaki ɗaya, Abbi ma ya ɗauki ɗaki ɗaya, daddyn Jelly duk da yake gauro, sai ya zauna a ɗaki ɗayar, haka matayensu suka kawo masu abinci a cikin ɗakunnansu, ma'ana su mummyn Rimsha kenan, zaman gidan Lion ya kamasu dole, dan dole sai an shawo kan wannan matsala, komai ya dai'daita kafin su koma gidajensu, shi kam Akil ya ce wlh gidansa zai koma, ba Queen ba ko ubanta da ya mutu ne ya zo ya ɗauke shi yana jiransu, dan haka sai ya ɗauki Umaisha suka nufi gidansa da yake cikin unguwar, bai san cewa ba iya Queen kawai ake gudun mashi ba, akwai su Josephine a gefe guda, Imran ma ya ɗauki jelly suka bi Akil ɗin, ya rage saura Irfan kawai, shi dama yayan Anaya Feroz baya kasar, yana Uk abinsa. Bayan sun yi sallar isha, su daddyn Rimsha kowa ya wuce ɗaki da matarsa, su kuma su Rimsha, suna ɗakin gwaggo suna tayata hira bayan sun kammala cin abinci kenan, yau a tare da gwaggon da Brr Naurat suka ci abincin, sun baro mazajensu a ɗakunnansu. Misalin karfe 9 dai'dai, sanye cikin kayan barci ash color masu matukar kyau da tsada Areef ya fito daga cikin bedroom nasa ya nufi na gwaggo, dan ya je ya yi mata sai da safe ita da Brr Naurat, sai tashin kamshi yake yi. Dai'dai zai shiga ɗakin, ita kuma Jehan tana fitowa, zata koma bedroom nasu ne, ta ce ta gaji da surutun Brr Naurat, gara ta je ta kwanta, kun san dama ita ma bata son yawan surutu. Kayan barci ne riga da wando a jikinta, sai ta ɗaura hijabi a saman kanyan. Karo suka ɗan yi, baya kaɗan ya koma, dan a tunaninsa ma Anaya ce, dan idan baku manta ba, Anaya tana kama da Jehan ɗin sosai, ganin ita ce ba Anaya ba yasa ya ce "To a bani hanya na wuce". Gyara tsayuwarta da kyau a bakin kofar ta yi, ta tare mashi hanya tana faɗin "Ba zaka shiga maki ɗakin gwaggo na ba, barci take yi yanzu, ka tafi sai da safe". Ɗan shafa kansa ya yi yana tuna lokacin da ya yi mata irin haka a kan tazo zata shiga bedroom na daddynta, wato yanzu ita ma ta rama kenan, Jehan duniya. Amma da yake ya fita iya duniyanci, sai ya masto da face nasa dab da ita, kasa kasa ya ce "Da gaske? To idan momma ta yi barci, ai ke baki yi barci ba ko? Dama ni ai ke nazo ɗauka ba wajen momma nazo ba, muje bedroom ki bani abinci a baki, ni kuma na baki abin daɗi sarauniyar rigima ta duniya". Matsa mashi a hanya ta yi tana faɗin "A'a gwaggo bata yi barci ba, ka shiga". Kugunta ya damko tare da jawota jikinsa. "Baby waɗan nan balls ɗin naki suna saka ni shiga wata duniya, kuma suna sani ɗaukar chaji". Da yake bata gane nufinsa ba, a tunaninta da magana yake yi a kan idanunta, bata san a kan breast nata yake magana ba, sai ta ce mashi "To ba sai ka ciresu su dai'na kallonka suna saka maka chajin ɗin ka huta ba". Ai kuwa tana rufe baki ya kai hannu ya capko ɗaya yana faɗin "Bari dai na sa su sauke mani chaji, ai ban isa in ciresu ba, dan sune first thing da suke ɗaukar hankalina a jikinki". Jin yanda ya capko su bata san lokacin data kware baki zata kurma mashi ihu ba, dan bata yi tsammanin a kansu yake magana ba, ya wani capko mata su da karfi, har cikin ranta ta ji zafi. Ganin zata yi mashi ihu ne yasa ya rufe mata baki tare da ɗaukarta cak bayan ya saki breast ɗin nata, kai tsaye bedroom nasa ya wuce da ita. Suna barin wajen ita kuma Anaya ta fito dan ta je wajen Mark ɗin ta, tana kewarsa over, itama kayan barcin ne a jikinta, sai dai ita ma ta ɗaura hijabi mai ɗan girma a samansu. Rimsha kuwa da tana ganin kamar bata girma ba, sai bata wani sanya hijabi a saman kayan barcin nata ba, haka ta kwanta a saman cinyar gwaggo tana zuba hira da Brr Naurat abinta, ta mance da Noorish nata, bata sani bama ya ci abinci ne ko bai ci ba, ita dai kawai ta samu hira mai daɗi. Can gwaggo ta ce mata "Rimsha Saif ya ci abinci kuwa?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Nima ban sani ba". Brr Naurat ce ta karɓi zancen da cewa "To tashi kije ki duba". To ta amsa da shi tare da mikewa ta nufi waje, bedroom ɗin ya rage daga Brr Naurat, sai Zaira kanwar Anaya, da kuma Aafia dake kwance, sai gwaggo. A dai'dai tsakiyar palo ta ci karo da Lion ɗin zai nufi bedroom nasa, sanye yake da kayan barci a jikinsa, da alama daga gadin ya fito, hannunsa na ruke da wayarsa. Wuceta ya yi ba tare da ya yi magana ba, tamkar bai ma kalleta ba, da sauri ta bi bayansa tare da rungume shi ta baya. A tsananin fusace ya fisgota ta dawo ta gabansa, hannu yasa ya shake mata wuya sosai yana bin kayan jikinta da kallo. Sai a lokacin ta gane me yasa ya yi mata hakan, tsananin tashi ne da shi kamar me, ya ji tsananin zafi na fitowa da ta yi da wannan kayan barcin nata ba tare da hijabi ba, kana iya hango shatin tula tulanta gabaɗaya, dan kayan basu da wani kaurin kirki, ga shi ita bata sanya breziya, tana ɗaukar kanta ƴar karamar yarinya sosai har a yanzu, bata kawo cewa ransa zai ɓaci sosai idan ta fito a hakan ba. Yana rike da wuyar nata ya jata har izuwa cikin ɗakin, a saman sofa ya hankaɗeta ta faɗi, cikin fushi ya ɗaga hannu zai ɗauketa da mari, tuna cewa idan fa ya mareta wlh tsab zata iya sumewa ko mutuwa, yasa ya fasa, ya sa kai ya wuce izuwa saman bed nasa ba tare da ya sake kallon in da take ba. Har ga Allah ransa ya yi mugun ɓaci, yana da tsananin kishi na wuce misali, ga shi yau gidan nasu a cike da mutanen, su Irfan, Imran duk suna nan, abin ya kona mashi rai over, abin da kuma yasa bai biye mata ya daketa ba na biyu, baya son a ƴan kwanakin nan ya rinƙa ɗaukar zafi, idan yana zaukar zafi, yana zuciya, za'a samu matsala, shiyasa kawai ya wuce saman bed nasa ya kyaleta a saman sofar, ba dan haka ba, yau da ya zaneta sosai. Ta sha jinin jikinta sosai, kuma ta ji babu daɗi. Jiki ba kwari ta miƙe ta nufi saman bed ɗin, hayewa ta yi tare da kwantar da kanta a saman bayansa, kirjinta dai dukan uku uku yake yi, amma haka ta daure, ta zuro hannayenta ta saman kirjinsa, cikin sanyin murya tare da shagwaɓa ta fara magana......... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E11 Date: 21/4/2024 cikin sanyin murya tare da shagwaɓa ta fara magana. "Kayi hakuri Noorish, ba zan sake ba". Shiru ya yi bai kulata ba, tamkar babu shi a cikin ɗakin. Ganin bashi da niyar kula tane yasa ta dawo da gabansa, ta kwanta tare da shigewa jikinsa, hannu ta kai tana shafa sajensa, kwaikwayon abin da yake yi mata na wasa da lips nata ta fara yi mashi ita ma, yatsanta ɗaya ta ɗaura a saman lips ɗin nasa, tamkar zata sanya mashi kuka ta ce "Please mana My Noorish, na tuba, ba zan sake ba, kasan fa Allah bana son ɓacin ranka, kuma......." Kasa karisa maganar ta yi saboda wani irin kallo da ya wurga mata. Da sauri ta zame hannunta daga saman lips ɗin nasa, a hanzarce ta shige cikin kirjinsa ta lafe tana mai sauke numfashi, a hankali hankali wasu siraran hawaye suka fara bin kuncinta, bata san time ɗin da kukan mai gabaɗaya ya kubce mata ba. Har cikin zuciyarsa yake jiyo sautin kukan nan nata, wani irin ba daɗi ya ji a ransa, kukan mace yana da tsananin tasiri a zukatan maza, komai zafin da namiji zai ɗauka, in dai mace ta iya kuka mai tsuma zuciya (kukan munafurci ba😂😂) to wlh nan take take iya sanya zuciyar namiji ya yi sanyi. Shi ma dai wannan kukan nata ta yi tasiri a zuciyarsa, dan kukan haɗe yake da shagwaɓa ga shi ta iya kuka mai ratsa zuciya, ga salo. Hannu ya ɗaura a saman kanta, cikin sanyin murya, kasa kasa ya ce "Why Meesha? Why zaki fita da irin wannan kayan? Kuma babu hijab" "Kayi hakuri, ba zan sake ba". Ta faɗa cikin kuka, da murya a shagwaɓe. Ɗago haɓarta ya yi tare da tsura mata idanu, yana tsananin kaunarta sosai, ta rigada ta shige can cikin zuciyarsa bawan Allah, ta zama rauninsa, ba zai iya ganin hawayenta ba. "My Meesha sarkin rigima, in dai rigima ce, to daga kanki an rufe kofa, yanzu me na kuka ni da ba dukanki na yi ba?". Turo ɗan bakin nan ta yi tana hura kumatu. Sumbatar lips ɗin nata ya yi, ɗago kai ta yi tare da sumbatar lallausan kumatunsa. Masto da face nasa dab da tata ya yi, cikin salo ya haɗe bakinsu waje guda. Kissing nata ya fara yi babu kama hannun yaro. A tare suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya, sun yi kewar juna, tun a jirgin ruwa rabonsu da jin ɗumin juna har haka, tun da suka dawo matsaloli suke ta faru, sam basu samu lokaci a tare ba sai yau. Hannu ya kai saman wuyar rigarta, a hankali ya cire botiran rigar gabaɗaya ba tare da ya zame bakinsa daga nata ba. Wani irin nisawa ya yi lokacin da ya sauke hannunsa a saman lallausan tula tulanta. Ita kuma mike mashi ta kara yi tare da kara nutsewa a cikin jikinsa tana sauke numfashi a hankali hankali. Duk wata gajiya tasa sai da ya sauke mata yau, romancing nata sosai ya yi, har sai da ta rinka yi mashi kuka sosai, dan yana yi mata abin da yake fin karfin shekarunta ne, yana juyata son ransa, gata ƴar karama dai'dai wasa. Sai da ya sami ɗan salama, ya ɗan ji nutsuwa ta ɗan sauka mashi, sannan ya rabu da ita, tare da komawa ya kwanta, ya jawota jikinsa yana mai lashe hawayen kukan da take yi. "Meesha sarkin ragwanta". Ya faɗa kasa kasa. Dukan wasa ta kai mashi a kirji bam tana faɗin "Duk ba kai bane kake sakani kukan, sai ka rinƙa yi mani abubuwa da zafi zafi". Hannun nata ya riko, da yake su kwata kwata a rayuwarsu basu san menene kunya ba, kai tsaye sai a saman Heronsa ya sauke hannun nata, ta miƙe sosai, tana tsaye gam, kasa kasa ya ce mata. "Tun ban baki wannan ba kike kuka haka?". Ihu ta zunduma mashi, lokacin guda kuma ta ɗauke diff kamar an ɗauke wutar nepa, ta ji abin da ya fi karfinta, duk da cewa akwai kaya a jikinsa, abin bana wasa bane, ya wuci lissafin ƙwaƙwalwarta, ita dai tasan yes idan an yi aure ana having sex, Akila ta gaya mata, amma bata taɓa sanin ya heron Noorish ɗin nata yake ba ma, shi kansa Noorish ɗin ma tsoronsa take ji bare kuma bananansa? Tab sai Akila ta dawo ta kara mata lecture sosai, sai dai kuma abin mamaki shi ne, da gwaggo da mummynta duk kallon kamar mai yaron ciki ma suke yi mata, basu taɓa kawowa a ransu cewa har yanzu babu abin da ya shiga tsakaninta da shi ba, a tunaninsu ta san komai izuwa yanzu, har fatan su samu nutsuwa mum take, dan tana son ta gyara yar tata, ta ji babu daɗi da suka yi aure bata nan, a cewarta basu sami gyara ba, to shi ne take fatan su samu nutsuwa, waɗan nan matsaloli duk su kau, zata ajiye ƴaƴan nata ta yi masu nasiha, sannan ta tsumasu sosai. (Ni kuwa nace tab to su Rimsha kam har yanzu virgin ne, kada ayi masu wani jike jike da tsome tsome 😂 in yi masu karin bayani ne ko dai na kara gaba readers?😂) Jin cewa ta suma ne yasa ya saki hannun nata tare da cigaba da shafa bayanta har barci mai tsananin daɗi ya yi awon gaba da shi. A ɓangaren Jehan da Areef kuwa, tun da ya ɗauketa, bai zame da ita ko'ina ba sai cikin bedroom nasa, a saman bed ya kwantar da ita, sannan ya kashe wutar ɗakin tare da rufe kofar. Kusa da ita ya dawo ya kwanta. Ganin ya kwanta ne yasa ta yunkura dan ta gudu, kamar yana kallonta ya kuwa capkota, ga ɗakin da duhu sosai, saboda kashe wutar da ya yi, kuma bai kunna blue light ba, saboda shi tun ainahinsa baya son haske sosai. "Ina zaki gudu ki je?". Ya raɗa mata a kunne. "Ɗakinmu mana". Ta bashi amsa tana ta ƙoƙarin raba jikinsu da juna. "To yau dai a ɗakin babynki zaki kwana, ƴar rigima, sai ki barni na yi ta barci ni kaɗai ko?" Zata yi magana wayarsa ya fara kara, hannu ya kai ya laluɓota a saman bedside drawer, ganin number Usa ba ƙaramar mamaki ya sha ba, shi dai yasan bayan his excellence, ba shi da number kowa daga Usa a yanzu, ga shi kuma ba ainahin wayarsa bace a hannunsa, da ainahin wayarsa ce, zata nuna mashi suna kai harma daga in da aka kira shi, ma'ana area da aka kira shi. Kamar dai ba zai ɗauki kiran ba, ko me ya tuna, sai kuma ya ɗauka. Yana ɗauka ya sanya a hand-free yana mai cigaba da shafa mazaunanta. Muryar macece ta cikin wayar ta fara da cewa "Baby good evening?". Da sauri ya waro idanu yana kallon wayar, ita ma Jehan ɗin ɗago kai ta yi tana kallon shi, sai surutu wacce ta kira wayar kuma take zuba mashi. Da alama parrot ce. Ganin yanda Jehan ɗin ta ɗago a hanzarce tana kallon shi ne yasa bai ma san time ɗin da ya katse kiran ba, shi dai bai san wacece bace har ga Allah. Ƙoƙarin barin jikinsa Jehan ɗin ta yi. A hanzarce ya rikota yana tambayarta ina zata je, kin yi mashi magana ta yi, da karfi ta sanya karfinta zata kwaci kanta tare kuma da fara ruwan zafafan hawaye, labarin gwaggo ne kawai ya dawo mata a cikin ƙwaƙwalwata, kenan yanzu da gaske suma TRIPLETS amanarsu za su ci? Ta tambayi kanta da kanta, gudun irin haka yasa sam bata son soyayya, kuma bata kula kowa, amma Areef ya zo ya shiga rayuwarta, yanzu ga shi har wata ne take kiransa da baby a gabanta, hakan yasa ta kara karfin gudun kukan nata har yana fitar da sauti kaɗan kaɗan. Yadda kuka ga Lion a kan kishi, haka ita ma Jehan take da bala'in kishi over, haka gwaggo ma take da wannan kishi, kun san ita Jehan abin da yasa wani lokaci ɗabi'unta suke kusan kamanceceni da Lion, saboda wasu halaye na gwaggo da ta ɗauko, shi kuma Lion gadan halayen gwaggon ma mai gabaɗaya ya yi, a cikin jikinsa yake, shiyasa nasa ya fi over. Wani irin bakin ciki ne ya turnuke mata zuciya, haushin Areef ɗin ma gabaɗaya take ji, cikin tsawa ta ce "Ni ka sakeni!". Yadda ta daga mashi tsawan abin ya kona mashi rai, sai ya sanya hannu ya damko wuyarta da kyau, cikin fushi shi ma ya daka mata tsawa tare da fara magana cike da ɓacin rai "Ni sa'an wasan ki ne? Har ni zaki dakawa tsawa haka? Kuma ina yi maki magana kina ce mani ke tafiya zaki yi, to na saki wuyar take, ki tafi in gani! Ko motsi ma ki sake yi in gani". Ya kai karshen maganar tare da zame hannunsa daga wuyar tata. Kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro ta saki tare da komawa ta kwanta shiru, zuciyarta zafi yake yi mata, tamkar an ɗaura shi a saman garwashin wuta, ji take yi tamkar ta haɗiyi zuciya kawai ta mutu kowa ya huta. Kasancewar shi Areef na daban ne, yana da zuciya mai kyau, kuma yasan ya kamata, ya iya rarrashin mace, yasan cewa a yanzu shi ne ya yi mata laifi, ya san cewa tana son shi ne yasa take kishinsa, idan bata son shi, ba zata yi kishi har haka ba, a yanzu dai shi ne ya yi mata laifi, tun farko ma meyasa zai ɗauki kiran waya suna a tare da ita? Ai dare lokacinta ne, dan haka ya shiga hakkinta, shi ya ja koma me ya faru, bawan Allah yana da dogon tunani, ya san yakamata, yana da nutsuwa da hankali, sai ka rantse da Allah daddyn Rimsha ne ya haifeshi, saboda halinsu iri ɗaya, shi ya yi sa'a, halin familyn gwaggon ya ɗauko, amma da yake jini ba wasa ba, akwai wasu ɗabi'u nasa da suke kama da family William kamar yanda shi ma Lion da ya ɗauko family William gabaɗaya da akwai wasu ɗabi'u nasa irin na familyn gwaggon, irinsu kyauta, sadaka, jinkan nakasa da sauransu, ba sai na sake faɗa maku ba, kun ji da kunnanku Aseef ya ce su daddynsu basu kyauta, su idan ba pastor ba, to babu wanda yake cin kuɗinsu, amma su TRIPLETS suna da kyauta sosai. A hankali ya matso kusa da ita, ta bashi baya tana ta murzan kukan kishin mijin nata, wata ta kira shi da baby a gabanta, bata ma san wacece bace, amma take irin wannan kishi, shi kansa bai san wacece bace, kila his excellence ne ya bata numbersa, dan tsohon nan ya iya haɗa aure. Tallabota ya yi da hannayensa dukka biyu, sannan ya ɗagota da kyau izuwa saman faffaɗar kirjinsa, rungumeta sosai ya yi, kafin ya kai hannu ya kunna lamp dake saman bedside drawer, nan take haske ya gauraye wajen gadon nasu. Cikin nutsuwa ya fara magana "Am so sorry my baby, na san nayi laifi, amma ki yi hakuri". Tamkar ba da ita yake yi ba, ta share shi, ta cigaba da zuba kukanta. Ɗan bakinsa ya kai saman face nata, hawayen ya fara lashewa, yana yi yana ɗan bubbuga bayanta alamar rarrashi. A dai'dai lallausan lips nata ya tsayar da tongue nasa, cikin kwanciyar hankali ya fara lashe lips ɗin nata. Turo baki ta yi tare da ɗan ture shi kaɗan, cikin kuncin zuciya ta ce "Ni banaso, ka rabu da ni, ka je can ka yi wayarka, babynka tana jiranka". Bata gama rufe baki ba aka sake kiran wayar. Guntun tsaki ya ja tare da kai hannu ya ɗauko wayar, picking call ɗin ya yi, tare da sanya wayar a hand-free, cikin faɗa ya tambayi yarinyar wacece ita?. Tamkar yanda ya yi hasashe ne, his excellence ne nan ya bata number, jikarsa ce, yana son ta auri ɗaya daga cikin TRIPLETS. Warning ya daka mata da babbar muryar a kan idan ta kuskura ta sake kiran numbersa, to sai na lahira ya fita jin daɗi, yanzu haka kawai ta sanya ran matarsa farincikinsa ya ɓaci, wlh a kan hakan ma ba zai kyaleta ba, sai ta yi zaman prison ko na shekara ɗaya ne, dan ɓatawa Jehan rai ba abin wasa bane. Cikin ɓacin rai sosai ya yi magana, yana gama kora mata jawabi ba tare da ya jira amsarta ba, ya katse kiran tare kuma da kashe wayar gabaɗaya. Ransa ya ɓaci sosai, yana tunanin irin ruwan bala'in da zai surfawa his excellence da safe, a kan me zai rinƙa bawa ƴan'mata numbersu? Su sunce mashi ya nema masu matan aure ne? Meyasa baya bada number Lion ko Aseef, sai dai numbersa shi kaɗai? Wato shi his excellence ya renawa wayo ko? To wlh zai yi maganinsa ne! Sai surfa bala'i yake yi a cikin zuciyarsa. Ganin ransa ya ɓaci sosai ne, kuma ta ji duk abin da ya faru a tsakaninsa da yarinyar, dan a hand-free ya sanya wayar, hakan yasa ta koma ta kwanta a jikinsa, cikin sanyin murya ta ce "Kayi hakuri". Sai a lokacin ya dawo da kallonsa a kanta, nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, tare da kara rungumeta da kyau da kyau. Ita ma rungume shi ta yi tana ɗan shafa bayansa. "My baby ki dai'na saurin yin fushi haka mana, kin san fa ni ke kaɗai nake so". Jinjina mashi kai ta yi tare da dawo da hannunta da gaba wajen kirjinsa, botiran kayan barcin jikinsa ta fara ɓallewa tana faɗin "Ni ba zan dai'na yin fushi ba in dai zaka rinƙa magana da mata". Haɓarta ya ɗago yana faɗin "Idan da ni mai kula mata ne, da a yanzu matana sun fi dubu, ke kaɗai ce kika yi mani a rayuwata, bayan ke banga wata ba, rigimammiya sarkin kishi kawai". Ya kai karshen maganar yana sumbatar lips nata. "Kai ma ai rigimammen ne". Ta yi maganar tana buɗe kirjinsa, ta gama cire botiran rigar. Shafa lallausan gashin dake kwance a kirjin nasa ta fara yi tana kara lafewa a jikinsa. Wani irin daɗi mara misaltawa ya ji, hannu ya kai ya kara gudun Ac, tare da ja masu bargo, sannan ya kashe lamp ɗin, dan na gaya maku shi baya son haske ko kaɗan, ba kaman Lion da yake iya barci da lamp a kunne ba, shi baya iyawa. Cikin dabara ya laluɓi laɓɓanta, da wani irin salo na daban ya fara kissing nata, shi already babu abin da bai sani ba dan gane da soyayya, saboda shi kunga ya yi rayuwa a wajaje da dama, ya zauna da mutane daban daban, ya iya salon soyayya kala kala. Bata hana shi ba, sai ma biye mashi da ta yi, ta cigaba da shaga gashin dake kwance a kirjin nasa, tana wasa da tongue ɗinta a cikin bakinsa. Sosai ta kara sakawa ya shiga wata duniya, cikin tsananin sha'awarta ya fara ɓalle mata nata botiran rigar bayan ya mayar da hijabin jikinta wuyarta. Zame bakinsa daga nata ya yi dan ya sami damar sauke nauyayyar ajiyar zuciya, rabata da hijabi da kuma rigar jikin nata ya yi, sannan ya kara jawowata jikinsa sosai. Wani irin dogon numfashi ya ja lokacin da hannunsa suka sauka a saman lausasan tula tulanta, a hankali ya fara wasa da su, kara shigewa jikinsa sosai ta yi tana karɓar irin wannan zazzafar sakon da yake aika mata ɗin. Ɗan bakinsa ya kai a saman nipples nata, tongue nasa ya fitar a in da ya fara wasa da nipples ɗin nata, kewaye ɗan kansu ya fara yi da tongue ɗin nasa, yana matsa ɗayan breast ɗin kuma da ɗayan hannunsa. Wani irin yanayi ta fara ji wanda ya fara wuce lissafin ƙwaƙwalwarta, ta kasa gane wani irin abu take ji a jikin nan nata ne, ji take tamkar kankara ake manna mata, tun daga tsakiyar kanta har izuwa tafin kafarta take jin wannan abin. Juyi ta fara ji mashi tana zillo tana son kwace kanta, dan bata taɓa jin makamancin wannan yanayi ba. Kara kankameta ya yi, ya cigaba da abin da yake yi, da ya ga tana neman katse mashi jin daɗinsa, sai ya haye kanta tare da yi mata runfa da faffaɗar kirjinsa. Cikin dabara ya shammaceta, ba tare da ta ankara ba ya rabata da wandon kayan barcin jikinta. Ba ƙaramin daɗi ya ji ba ganin cewa babu pant a ciki, saman mararta ya ɗaura hannunsa, wani irin ɗauke wuta ta yi na ƴan mintoci. Lokacin da ta dawo dai'dai, can a gabanta ta tsinkayo shi yana wasa da wajen. Kuka ta fara yi mashi, cikin fitar hayyaci take faɗin "Yah Areef ka bari dan Allah, jikina yanayi mani wani iri, please ka ji mijina, wayyo gwaggona". Haka take ta zuba mashi kuka da surutai. Yana jinta sarai, amma bai dai'na wasa da ita ba, saboda ta haɗa duk wani abin da yake da bukata a tattare da mace, ba shi da niyar yin sex da ita a yanzu, amma fa zata sha wasa, dan sai ya koya mata son wasar tasa sosai, har yazamana idan bai yi mata bama, ba zata iya barci ba... BABBAR MAGANA. Kuka ta cigaba da yi mashi, shi kuma juyata ya cigaba da yi son ransa, daga karshe ma tongue nasa ya zura a gaban nata, wasa ya fara yi da wajen sosai da sosai. Wani irin ihu ta zunduma mashi cikin fitar hayyaci, ta rasa ina zata sanya ranta, sai ƙoƙarin janye jikinta take yi, amma ina ko kusa ko alama ba zata iya ba, dan ba rikon wasa ya yi mata ba. Sosai yake juya tongue nasa a wajen, ba shiri ya fara zuba mata sambatu shi ma, da alama shi ma yanzu ya fita a cikin hayyacinsa, jikinsa har wani tsuma yake yi, gabaɗaya tsikar jikinsa ta tashi zara zara, bukatar kawai ya ji shi ya shigeta, ya shiga cikin jikinta sosai, sai dai ba zai yi gigin yin hakan ba, saboda lokacin da suka je yin sallar Issha, Lion ya ce mashi gobe za su tafi Enugu state, so ba zai iya yin dis virgin nata a yau ba, dan idan ya yi hakan bai kyauta mata ba, na farko bashi da tabbacin zai dawo a raye! Na biyu kuma ba zai so ace ya yi dis virgin nata kuma bata sami kulawa daga gsresa ba, ya tafi ya bari wasu su kula da ita, su yi jinyarta, sam ba zai so haka ba, waɗan nan dalilan ne suka sanya ya daure ya cije bai shigeta ɗin ba, amma iya kurewa ta kure hakurinsa gaskiya, ya zurfafa da yawa a wasan nasa, kuma daɗi ne ta rinjaye shi, daɗi ne tasa har ya zurma da yawa haka ba tare da ya ankara ba, shi Lion da yake yasan kansa, yasan idan ya zurma fa to ba zai iya rike kansa ba, sai ya zama ko kusa ko alama baya tunkarar gaban Rimsha idan suna wasa, a iya tula tulanta kawai yake tsayawa, suma bai cika taɓa su ba, ko kiss baya son yi mata sosai, sai dai sumbata, dan yasan idan ya fara kissing nata, zai kai hannu ya taɓa tula tulanta, daga nan kuma labari zai canza, to shiyasa yake takaka tsantsa sosai, bawai dan baya sonta ko baya son wasa da ita ba, a'a izuwa yanzu kowa yasan Lion yana tsananin kaunar Rimsha, kuma yana da karfin sha'awa sosai, a kullum yana tsananin sha'awarta over, kawai tsaro ne yasa yake kawar da kai, kuma dama ai sai kana son mutun zaka yi sha'awarsa!, Shi kuwa Areef, tashin farko ya zafafa a wasan nasa, kunga kuwa dole a sami matsala. Idanuwansa tamkar wuta saboda ja, ita kuwa DPO, sai kuka take yi mashi. Wani irin juyata ya yi tare da kara zura tongue ɗin nasa da kyau a HQ ɗin nata, sanna ya kai hannu yana matsa mata tula tulanta da karfi karfi, kan kace me tuni ta sume mashi, shi kuma da yake lokacin yana dab da samun nutsuwa ne yasa ya tsananta wasan sosai har ta sume bai sani ba. Sai da ya samu nustuwa ne ya lura da ta sume, mamaki yake yi wai a iya wasa da suka yi ne har da sume mashi, da wani ɗan bakinta na tsiwar nan a wajen, ga fuska jaga jaga da hawaye, ashe duk iya tsiwar tata ko wasanin sa kawai ba zata iya ɗauka ba? Ya faɗa a cikin zuciyarsa tare da matsowa yana lashe hawayen nata. Kissed na lips nata ya yi kafin ya miƙe ya saɓeta a kafaɗarsa suka nufi toilet. Wanka ya fara yi mata, tun da ya tsundumata a cikin ruwan ta farfaɗo, kuka ta cigaba da yi mashi, bai kulata ba har sai da ya kammala, ya naɗota a towel. Saman bed ya mayar da ita ya kwantar, sannan shima ya je ya yi wanka. Yana fitowa ya wuce dressing room. After some minutes ya fito sanye cikin wasu kayan barcin white color, hannunsa na ruke da wasu kayan kuma, kayan barcinsa ya ɗauko mata. Kusa da ita ya zo ya zauna, cikin sigar rarrashi ya ce "My baby menene abin kuka kuma daga wasa? Ban fa yi dis virgin naki ba bare ki yi mani kuka, shi ne dai nasan da akwai zafi, amma wasa ai babu zafi sai dai daɗi ko?". Ya kai karshen maganar yana kunna lamp dake bedside drawers ɗin. Harara ta wurga mashi kafin ta ce "Allah ba zan kyaleka ba, zan rama ne". Hannu ya kai yana zame towel ɗin dake jikinta yana faɗin "Tom shikenan zamu gwada watarana, sai ki rama mu gani". Kankame towel ɗin da karfi ta yi tana faɗin "Ni kada ka cire mani kaya". Matsowa dab da ita ya yi, kasa kasa ya ce "Kaya kuma na nawa? Ai babu abin da ban gani ba, yanzu kinga idan nazo yin dis virgin naki ma nasan hanya, tongue ɗina ya nuna mani hanyar, dan haka kawai ki sake mani abubuwana na moresu, na kuma baki baby's masu kama dake, kyawawan gaske masu manyan idanu kamar ball". Zaro idanu ta yi tana mamakin rashin kunya irin na TRIPLETS, duk rashin kunyarta ashe bai kai kaso 1 cikin ɗari nasu ba, su kwata kwata basu ma san me ake kira da saya magana ko a ɓoyeta a faɗeta ta wasa siga ba, ba kai tsaye ba saboda kunya, su basu san wannan ba, kawai maganarsu suke yi kai tsaye, yanzu fa ba ƙaramin aikin Areef bane da ya tuɓe mata kayan jikinsa rankatakaf abinsa, babu ruwansu su kam, Allah mai iko. Ganin ta afka duniyar tunani ne yasa ya zame towel ɗin tare da kara matsowa kusa da ita, sosai ya zubawa kyakkyawar surar jikinta idanu, a hankali ya kai hannu ya shafi jajir kuma lausasan tula tulanta, hakan ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta afka, cikin sauri ta ce "Wai ba zaka rabu dani ba? Kuma.....". Bai bari ta karisa maganar ba ya zura tongue nasa a cikin bakinta, yana zurawa ya rungumota sosai suka kwanta a tare, ya janyo masu bargo, sannan ya zuro hannunsa daga ta cikin bargon ya kashe lamps ɗin. A kunne ya raɗa mata cewa yau ba kaya zata kwana, ya fi so ya ji komai suna tsokalinsa. Shiru ta yi bata kula shi ba, tana jinsa yana mammatse mata breast nata har barci ya yi awon gaba da ita. Tana yin barci ya lallaɓa ya kwantar da ita, miƙewa ya yi tare da duba time, 1:30am dare ta tsala sosai. Kasan gadon ya diro, da sauri ya nufi waje. Kai tsaye garden na gidan ya nufa. Bakinsa ɗauke da sallama ya shiga, Lion yana zaune a wajen yana aikin latsar waya, kusa da shi ya zo ya zauna, ba ɓata lokaci suka fara tattaunawa a kan tafiyar da za su yi gobe, dan Lion yasa a bincika mashi ta ina Daular Mutuwa take a yanzu, kuma ya sanya ayi masu addu'a sosai, dan yanda ya kalli Rimsha ta rikice hakan nan, yasan ba'a banza ba, taga bala'i ne. A ɓangaren Anaya kuwa, time da ta fito daga cikin bedroom na gwaggo, kai tsaye wajen Mark ta nufa, baya a kitchen time ɗin, dan haka sai ta fito waje harabar gidan. Tafiya ta fara yi tana ƴan waige waige dan nemansa. Ta wajen pool na gidan ta nufa. Can ta hango shi shi da Alex a wajen pool suna zaune a saman ɗaya daga cikin kyawawan kujerun dake a wajen. Da sauri ta karisa wajen, da yake bata san cewa Alex uncle nata ne kanin daddynta ba, sai tana zuwa ta faɗa jikin Mark ɗin tana murmushi. Shi ma Alex ɗin bai san cewa ƴar yayansa bace, ya ɗauka ma matar Mark ɗin ce ko dai wata makusanciyarsa, tun da basu gama sanin juna da Mark ɗin ba, bai san abubuwansa da kuma jama'arsa ba, dan haka sai ya bisu da idanu kawai. Cikin shagwaɓa ta ce "My na yi kewarka sosai fa". Shafa face nata ya yi tare da ɗan sumbatar kumatunta. Sai kallonta Alex ɗin yake yi, tabbas ta yi mashi kama da Brr Naurat, dan idan baku manta ba, daddyn Rimsha da daddyn Anayar duk da Brr Naurat suke kama, Anaya da Jehan kuma suka yi kama da mahaifan nasu, kunga dole a sami kamanin Brr Naurat a fuskar Anaya da Jehan ɗin, tamkar zai tambayi Mark ɗin wacece wannan kuma? Sai kuma ya fasa, da ya gaji da shagwaɓar Anayar ma, sai ya miƙe ya sabu waje abinsa. Haka suka murji soyayyarsu son ransu, sai zuba mashi shagwaɓa take yi, shi kuma yana biye mata, tana tsaka da yi mashi magana, bata ankara ba sai jin saukar lips nasa a saman tata ta yi, ga shi tana kwance a jikinsa, kun san su a wajensu hakan ce soyayya. Bata hana shi ba da farko, daga baya da ta tuna da maganganun da Rimsha ta yi mata a school, sai ta yi maza ta mike daga jikin nasa tare da komawa gefe da sauri. Da mamaki yake kallonta, kafin ya yi magana da gudu ta bar wajen, kirjinta sai dukan uku uku yake yi, fatan ta ɗaya, shi ne kada ta samu ciki kamar yanda Rimsha ta ce mata idan wani ya taɓata zata samu ciki.. BABBAR MAGANA. Tana shiga cikin gida, kai tsaye ɗakinsu Rimshar ta nufa, a lokacin kowa ya yi barci, saman bed ta haye tare da kudundunewa a cikin bargo, nan take ta fara hawaye tare da danasani. Shi kuwa Mark, wayarsa ya ɗauka ya fara kiran numberta, amma ina taki ɗagawa, daga karshe dai ya hakura ya kyaleta, dan bashi da zaɓi. A haka barci ya yi awon gaba da ita. A ɓangaren shi kuma Aseef, da kyar da makyarkyata ya samu barci ta yi awon gaba da shi, Allah sarki, yana tsananin kewar Heartbeat nasa, har wani zazzaɓi mai tsananin zafi ne ya rufe shi, a haka dai barci ɓarawo ya ɗauke shi. Ummin Nawid ƴan uwanta na Katsina sun zo sun ɗauketa, dan sun sami labarin rasuwar Dr Nawid, abin gwanin ban tausayi. After one day. Haɗe suke gabaɗaya a palo, a yau ne su Lion suka shirya tafiya Daular Mutuwa, suna hira a palon na ban kwana da ƴan uwan nasu. Gwaggo ce ta ce da Lion "Amma Saif ba da Rimsha zaku tafi ba? Naga ita kaɗai ta san hanya ai". Kai kallonsa a kanta ya yi, tana kwance a saman cinyar daddynta. Shi ba don hanyar ma yasa yake son tafiya da ita ba, saboda su Josephine yasa yake son tafiya da ita, baya son barinta a nan, dan kada su Josephine ɗin su yi mata wani abin, hankalinsa zai fi kwanciya idan ya tafi tare da ita. "Yeah momma da ita zan tafi......" Bai gama rufe baki ba ta zunduma ihu tare da miƙewa tsaye tana faɗin "Wlh ni ba zan je Daular Mutuwa ba, in dai a kan Daular Mutuwa ne to wlh sai dai mu ɓata da yaya Saif ɗin, kowa ya kama gabansa, ni sai dai idan gawata za'a mayar can, amma da kafata, wlh ba zan je ba, na shiga uku na lalace, wayyo daddyna kasheni kawai gwaggo take so aje ayi, kila ta gaji da ganina ne a duniya, daddy ka gaya mata kai kana sona tun da ita ta dai'na sona, mummy dama nasan ke kinfi kowa sona, ki gaya masu kada su taɓa maki ƴarki". Ta kai karshen maganar tata tare da watsawa a guje ta nufi cikin bedroom nasu, sai kuka take yi tamkar ranta zai fita. Shiru palon ya yi, babu wanda bai tausaya mata ba, harta shi kansa Lion ɗin ya yi mugun tausaya mata, ba'a banza take waɗan nan surutan ba akan Daular Mutuwar, baiwar Allah. Miƙewa Areef ya yi ya bi bayanta izuwa cikin ɗakin nata, su kuma suka cigaba da tattauna yanda za'ayi. Yana shiga ya sameta kwance a saman bed, ta yi shiru ga hawaye a jaga jaga a saman face nata, sai tunanin yanda ta baro Daular Mutuwar take yi. Saman bedside drawer ya zo ya zauna, cikin zolaya ya fara magana "Rimsha ƴar Queen of Daular Mutuwa fa ta ga Yaya Saif naki, kuma ta ce idan ba shi ba wlh mutuwa zata yi, ita shi take so, Queen ɗin kuma ta ce ta kwantar da hankalinta babu shakka sai ta mallaki Lion ko ana ha maza ha mata". A dubu ɗari ta mike zaune, tare da zaro idanunta waje tamkar zasu faɗi kasa, kome ta tuna, sai ta zunduma ihu da iya karfinta tana faɗin "Ni wlh babu wanda yaya Saif zai sake aura, ni kaɗai na ishe shi, Allah koma Queen ɗin ce bata isa ta taɓa mani shi ba, ai ba tsoronta nake ji ba, a kan shi zan iya yin komai, shegiyar mata mai bakar aniya, wlh azumi da tsayuwar dare zan yi mata, dan taga yaya Saif na kyakkyawan gaske ko? Bakar azzaluma, to wlh yaya Saif yafi karfinta, kuma shi baya son aljana, Allah idan ta sake ta kalle shi da ido ma kawai, sai na kwakwale mata idanu!!". (Ko a ina zata gan Queen ɗin har ta ga idanun da zata kwakwale mata ɗin?🤔 Anya Rimsha ƙwaƙwalwarta bai taɓu ba kuwa?) Tana magana tana ihu. Areef me zai yi? Ai yau dariya har da rike ciki, Allah mai iko, kamar ba yanzu ta gama cewa ita ta dai'na son yaya Saif ɗin ba, in dai a kan Daular Mutuwa ne, to wlh babu ruwanta da shi, amma daga jin batun zai auri ƴar Queen, har ta mance bala'in dake cikin Daular ta fara kishi kuma, kai jama'a Rimsha tana yin son ranta. Ganin irin dariyar da yake yi mata ne yasa ta kara tsananta kukan nata. Tana ƙoƙarin sauka daga saman bed ɗin idanunta suka sauka a saman face ɗin Lion, yana tsaye a bakin kofar shigowa bedroom ɗin. Wani irin yawun wahala ta haɗiye, nan take ta yi shiru, dan yanda ta ga face nasa babu almun wasa a tattare da shi, nan take ta haɗe malaman jikinta waje guda ta nutsu tsit. Wani irin muguwar harara ya wurgawa Areef dake kallonshi yana dariya. A takaice ya ce mata "Zoki wuce mu tafi". Ba musu sumui sumui ta sauko kasa daga saman gadon ta nufe shi. Gaba ya yi ta rufa mashi baya, kai tsaye bedroom nasa ya wuce, cikin jin kunya ta keta jama'ar dake a cikin palon ta bi bayansa zuwa bedroom ɗin nasa............ ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E12 Date: 22/4/2024 Gaba ya yi ta rufa mashi baya, kai tsaye bedroom nasa ya wuce, cikin jin kunya ta keta jama'ar dake a cikin palon ta bi bayansa zuwa bedroom ɗin nasa. A zaune a bakin bed ta isko shi, kusa da shi ta zauna tare da kwanto da kanta a saman laps nasa. Nisawa ya yi tare da kai hannunsa yana goge mata guntun hawayen dake a saman face nata. "Meyasa kike son yin kuka sosai ne?". Ya yi maganar yana mai da kallonsa a saman zanen sunansa dake saman tudun tula tulanta da suka ɗan bayyana saboda yanayin kwanciyar da ta yi. Hannu ya kai wajen yana ɗan shafa zanen, kasa kasa ya ce "I really like it". Ɗan turo baki ta yi tana mai kamo hannunsa ɗayar dake a saman kumatunta. "Noorish ni dan Allah kada ka bari a mayar da ni Daular Mutuwa ka ji ko?". Dawo da kallonsa a saman face nata ya yi, zuba mata idanu ya yi na tsawon mintocin da a kallah zasu kai biyar, kafin ya ja godon numfashi sosai ya fara magana a nutse. "I will going to miss you my Meesha, ba zan tafi da ke ba, kuma babu wanda ya isa ya kai min ke can, stay with your dad and mum safe, ki kula mani da kanki sosai, don't come out without hijab, even wajen momma zaki je, you now i hate that, so be careful kin ji ko? I really love you from the button of my heart". Ya kai karshen maganar yana shafa lallausan wuyarta. Nan take ta ji jikinta ya yi mugun sanyi, mikewa ta yi zaune tare da faɗawa jikinsa da kyau. Rumgumeta sosai ya yi, ji yake yi tamkar idan ya tafi ya barta, wani abin zai iya faruwa da ita, yana jin tamkar za'a rabasu. "My Noorish i really love, ban taɓa son wani abu a rayuwata kamar yanda na so ka ba, tun ban san wacece ni ba nake dakon sonka, hotonka kawai idan na gani yana ɗaukata tsawon lokaci ina cikin tsananin farinciki, a duk lokacin da na tunaka, ina jin tamkar ba'a duniya nake ba saboda daɗi, ban taɓa kawowa a ra'ina zan ganka ido da ido ba, ban taɓa kawowa a ra'ina zan zauna a kusa da kai ba, amma duk da haka, a kullum sonka karawu take yi a cikin zuciyata, bani da abin da zan ce ga Allah sai dai Alhamdulillah, Alhamdulillah daya mallaka mani kai a matsayin miji, ya kuma sa kana sona nima, ko yau na mutu wlh nayi farinciki, burina kuma ya cika, ka kula mani da kanka sosai ka ji?". Ta kai karshen maganar tana ruwan hawaye sosai. Kara matseta sosai a jikinsa ya yi, da wata iriyar murya wanda bai san yana da ita ba, cikin tsananin so da kuma kaunarta ya fara magana "Hakane my Meesha, duk abin da kika faɗa gaskiya ce, kin soni tun baki san ke kanki wacece ba, na shaida hakan ni da kaina, amma fa ki sani a yanzu na fi sonki sama da yanda kike sona, ban taɓa tunanin zan ɗaga idanu na kalli wata ƴa mace ba a rayuwata sai a kanki, ranar da na fara ganin zanen sunana a kirjinki, abin ya tsaya mani a ra'ina sosai, sai dai a lokacin zuciyata a rufe ruf take, kece da kanki kika nemo key ɗinta, kika buɗeta, kika shiga cikinta, sannan kika mayar kika rufe, you are so special my Meesha". Ɗago kanta daga saman kirjin nasa ta yi, face nasa ta zubawa idanu sosai tana kallon shi, hawaye wasu suna bin wasu a saman kuncinta. Shi ma ita yake kallo, sun tsare juna da idanu babu ko kyaftawa. Almost 5 mins suna a haka, sannan ne ta matso da face nata dab da tasa, lallausan lips nasa ta sumbata, tare da kai hannu ta sakalo wuyarsa. Ganin yana bata wahala ne dan ya fita tsawo sosai, yasa ya rankwafo mata kaɗan, hakan ya bata damar samu ta fara kissing nasa cikin nutsuwa. Kara kankameta sosai ya yi, yau wani irin kiss take yi mashi tamkar babu gobe, cikin salo ya shiga mayar mata da martani shima, tamkar zasu cinye juna. Sun jima suna kissing na junansu kafin nan ya zame bakinsa daga nata, kasa kasa ya ce "Zan tafi, time ya cika, ki kula sosai my happiness". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa da ita a jikinsa. Kai tsaye palo ya nufa, har lokacin su daddy suna zaune suna ta mayar da zantuka. A tsakiyar palon ya sauketa, kunya tamkar zata shige cikin kasa, shi kuwa ko a jikinsa, sai ma kallon gwaggo da ya yi yana faɗin "Momma pray for us, zamu tafi". Ya kai karshen maganar tasa tare da nufar hanyar sauka kasa. Gabaɗaya family suka rufa mashi baya, gwaggo idanunta sun cika taf da kwallah, ƴaƴanta har guda biyu zasu tafi Daular Mutuwa, waje mafi haɗari da bata taɓa jin biyunsa ba, ji take tamkar ta dakatar da su, sai dai kuma mahaifinta yana a can, tana kaunarsa shi ma, dole su je su ɗauko mata shi, hakan yasa ta danne ta jure, Aseef sai kuka yake yi a kan shi gaskiya zai bisu, ba zai yarda su tafi su barshi ba, koma yaya ne sai dai su tafi tare. Da kyar Lion ya shawo kansa ya hakura, suka ce mashi ya zauna ya kula da gwaggo da ƴan gida. Shi kuwa Areef yana can yana haɗa kaya, sam bai sanar da Jehan da shi za su tafi ba. Bayan ya kammala haɗawa ne ya fito waje harabar gidan, a nan ya sami kowa da kowa, kai tsaye cikin mota ya fara nufa, sai da ya ajiye jakar tasa, sannan ya fito, kusa da gwaggo ya zo, cikin nustuwa ya ce mata "Momma be strong please, just pray for us, everything will going to be normal In Sha Allah". Har lokacin idanunta cike tab da kwallah, addu'a ta fara zuba masu babu kama hannun yaro, sai amin amin kowa yake amsawa da shi. Bayan ta kai karshen addu'ar ne, ba zato ba tsammani Jehan ta saki baki tana kallon jama'a, sai ji ta yi ya jawota ta faɗa jikinsa, rumgumeta sosai ya yi yana faɗin "Zan tafi my baby, ki kula mani da kanki sosai kin ji ko?". Tamkar zata yi kuka ta ce "Dama har da kai za'a tafi Daular Mutuwar ne? Shi ne baka gaya mani ba?". Kara matseta sosai ya yi a jikinsa yana faɗin "Am so so sorry, mantawa nayi". Dukan wasa ta fara kai mashi a kirjinsa tana faɗin "Ni bana son kaje, dan bana son wani abin ya sameka, ni dai ka fasa zuwa"."Da gaske baki son wani abin ya sameni?". Da sauri ta gyaɗa mashi kai "E bana son wani abin mana ya sameka, ni bana son na rabu da kai". "To shikenan, pray for us, In Sha Allah babu abin da zai same mu". Ya kai karshen maganar yana mai kara matseta sosai a jikinsa. Da alama sun mance da cewa a gaban family suke. Haka suka cigaba da zubawa juna kalaman kauna har sai da ya ishe su, while shi kuma Lion yana magana da gwaggo da kuma daddyn Rimsha. Bayan sun gama zuba kalaman love ɗin ne ya saketa tare da nufar wajen motar tasu, sam yaki yarda ya juyo su haɗa idanu da ita, dan baya son ganin kukanta, ita kuwa hawaye wani na bin wani. After some minutes Lion ya kammala maganarsa da su gwaggo, sannan ya juya ya nufi wajen motar, har Donal ya buɗe mashi kofar motar zai shiga, da gudu Rimsha ta tafi ta faɗa bayansa, tana sakin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Cikin kukan nata tana faɗin "Noorish ni zan bika, bazan iya bari ka tafi kai kaɗai ba, gara muje tare kawai, gara komai zai faru ya faru a kan idona, ina tare da kai, ko mutuwa zan yi, nafi son na mutu a hannunka, please Noorish". A hankali ya juyo ya rungumeta, har cikin ransa shi ma baya son rabuwa da ita, rabuwarsu babban ciwoce a gare shi, yasan zai sha wahala sosai, amma ba shi da zaɓi, dole ne ya barta a gida, dan bai san me zai je ya tarar a wajen ba. Hakika har cikin zuciyarsa yake jin wannan kuka da take rerawa, amma sam ya kasa yi mata magana, ganin haka yasa daddynta ya kariso wajen, hannu yasa ya karɓeta daga jikin Lion ɗin. Ihu take zunduma masu bana wasa ba, faɗi take yi "Daddy ka ce ya tafi da ni, bana son ya barni, bana son rabuwa da shi". Wucewa ya yi ya shiga cikin mota zuciyarsa na yi mashi zafin rabuwa da ita, shi kuma daddy wucewa da ita ya yi izuwa wajensu gwaggo. Yana zuwa gwaggo ta karɓeta suka hau rarrashi, amma ina, taki yin shiru, ihu take yi tana faɗin ita wlh zata bi mijinta........... RIMSHA MANYA MAI MIJI, TATTABARA UWAR SOYAYYA❤️😂 Da gudu Jehan ta juya ta bar wajen, ta koma cikin gida, dan ba zata iya ganin tafiyarsu ba, shi ma Aseef da sauri ya bar wajen, dan ba zai iya jurewa ba, dama da kyar Lion ya lallaɓa shi ya yi masu shiru. Mark ne ya nufi motar su Lion ɗin, dan ya ja su su tafi airport. Dai'dai zai buɗe kofar motar, Anaya ce ta zunduma ihu tana faɗin "Nashiga ukuna! Dama my da kai za'a tafi? Wlh ba zan iya jure rashinka ba! Ka dawo wlh ba zaka je ba, Rimsha fa ta ce mutuwa ake yi a can". Yau ga ikon Allah, iyaye dai suna ganin tsantsar rashin kunya ta yayan zamani, amma da yake duk jirgi ɗaya ya kwasosu, wato duk jinin turawan ne, sai ya zama ko a jikinsu, basu damu da abin da ƴaƴan nasu suke yi ba. Da gudu Anayar ta tafi wajen Mark ɗin, ta kuwa yi sa'a dai'dai lokacin ya juyo domin ya kalleta. Tana zuwa ta faɗa saman kirjinsa tana kuka, ita wlh ba zata bari ya tafi ba, ai ta ji Rimsha ta ce mutuwa ake yi a wajen. Shi dai Azharuddin Bature, wato daddynta, baki ya saki yana ganin ikon Allah, a iya saninsa bai taɓa sanin ƴarsa tana soyayya ba, kwatsam sai ya ganta da wani? Lallai kuwa ya yi sakaci ba kaɗan ba. Ita dai Brr Naurat ko a jikinta, daɗi ma ta ji na cewa duk jikokin nata sai auren family suke yi, zumunci na kara ninkuwa. Babu kunya Mark ya rungumeta sosai, kasa kasa ya fara rarrashinta. Ina ai kin sauraronsa ta yi, sai kuka take zuba mashi. Daddyn Rimsha bawan Allah, yana ganin abubuwa, shi ne dai ya sake zuwa ya kama Anayar, daddynta kam ya kasa motswa daga in da yake, duk ya yi la'asar, mamaki kamar zai kashe shi, wai ace kamar su Anaya sun san so? Shi yana matsayin daddynta sam bai san da zancen ba?! Abin ya bashi mamaki, sai kallon mummynta yake yi, ita ma shi take kallo, dan bata san komai ba............. Ni kuwa nace ta ina zaku sani? Ku ba ƴan boko ba, mummynta tana wajen aiki, kai kuma daddynta baka gari, ai kunma yi sa'a da Allah ya haɗata da Rimsha, da yanzu wani labari ake yi, da Mr Emmanuel ya jima da buɗe maku aiki, idan da rabo sai dai ku kanta da ciki ba tare da kun san ya aka yi ba, Allah ya baku amanar ƴaƴa, amma kun sake su kun tafi neman duniya, kun barwa masu aiki ragamar kula da su, tamkar ba ku aka bawa amana ba, tamkar ƴan aiki aka bawa amanarsu, ga duniyar yanzu yanda amana ta yi ƙaranci, baku san su masu aikin ya halinsu yake ba, yanda lesbian ya yawaita a duniyar nan, ku dai kawai kun sakar masu komai ba tare da dogon tunani da kuma yin aiki da faɗar Manzon Allah manzon tsira ba, wayewanku dai bai amfaneku ba! Wlh idan baku tuba ba, sai Allah ya kamaku, dan duk wani ɗa a duniyar nan, sai Allah ya tambayi iyayensa ta yanda suka kula da shi, hakki ne da kuma amana ya basu, dan haka sai ku kara zage dantse, Allah ka bamu dacewa. Daddyn yana karɓar Anayar, Mark ya yi saurin shigewa cikin motar, shi ma zuciyarsa tana yi mashi zafi da kuna, Alex ya so ya rakasu, Lion ne ya hana shi, haka motocinsu ya tashi ya bar gidan, suka nufi airport, sai dai kafin su bar gidan, sai da Lion ya ja kunnan gataman a kan kada ya bari wani ya shiga gidan ko kuma wani ya fita ba tare da ya basu izini ba. A gabaɗaya sojoji goma sha biyu da suke gidan, sojoji uku Lion ya barsu a kan su cigaba da kula da family, ya tafi da guda tara. Da yake motocin suna sharara uban gudu sosai, cikin ƙanƙanin lokaci suka isa airport ɗin, an gama shirya masu komai, dama tun jiya Lion ya shirya wasu abubuwa da zai buƙata, dan haka suna zuwa kawai suka ɗauki hanya, ba ɓata lokacin jirginsu ya ɗaga zuwa Enugu state........... TO FATAN MU DAI ALLAH YA TSARE HANYA, YA KUMA KAREKU DAGA SHARRIN QUEEN!!. A gida kuma, komawa cikin gida gabaɗaya family suka yi. A palon sama suka zauna, rarrashin Rimsha da Anaya suka hau yi, da kyar suka samu suka yi masu shiru, ita Rimsha ta tada kai da laps ɗin gwaggo, barcin wahala da kewar mijinta ya ɗauketa, ita kuma Anaya ta tada kai da laps ɗin Brr Naurat, sai tunanin Mark nata take yi, tana bin jama'ar palon da kallo, ita dama Jehan already tana barin wajen bedroom nasu ta koma, saman bed ta haye, haka ita ma ta murji kuka tamkar babu gobe, daga haka barci ya yi awon gaba da ita cike da tunanin mijinta kuma abokin diramarta, yau ina zata sanya ranta? Ya tafi ya barta, yau babu tsokana, yau babu rigima, Allah sarki, dukkansu gwanin ban tausayi. Bayan ƴan kuka sun yi shiru ne Brr Naurat ta sami damar nuna masu Abba Alex, cike da murna suka rungumi ɗan uwansu, duk da cewa daddyn Rimsha da daddyn Anaya suna kama sosai da Brr Naurat, amma Alex ya fisu kama da Turawa sosai, shi ba zaka taɓa cewa Dr Salman bane ma mahaifinsa, saboda shi da su Trump wato kakan Mark ya yi kama, da su yake muguwar kama, duk cikin ƴaƴan Brr babu mai wani irin launin idanu irin na ƴan uwanta, sai shi Alex ɗin, shi kaɗai ne mai blue eyes irin nasu Trump, sai kuma a cikin jikokinta, kanwar Anaya Zaira, idanunta ash color ne, sune kawai masu wani launin idanu ta ɓangaren Brr. Daddyn Anaya ne ya katse masu hiran da cewa "Daughter a ina kika san wannan mutumi da kika rike yanzu kina kuka?". Tana daga kwance, babu kunya ko ɗigo a idanunta, cikin tsantsar shagwaɓa ta fara magana. "Daddy Mark ne fa, kuma shi nake so, kuma shi ma yana sona, kullum ma yana yawan ce mani na gaya maka yana son kawo maka ziyara". Cikin nuna ko in kula, bai ɗauki zafi ko kaɗan ba, dan wayayyun mutane na wuce misali, sun kwankwaɗi boko, dan haka sai ya ce "To kin san shi ne? Su waye iyayensa? Kuma a ina yake?". Turo baki ta yi tana faɗin "Daddy dukka wannan shi zaka tambaya mana, ni ban san kowa nasa ba bayan mijin Rimsha da yake ogansa, shikenan". Salatin mummynta ta sanya tana faɗin "Yanzu daughter baki san iyayensa ba, baki san halinsa ba, kawai ke ƴar soyayya sai kika fara son shi ko? Wai ni yaushe ma kika girma ne? Yau ga ikon Allah, ko secondary school fa yanzu kika fara, amma kike zancen son wani?". Kuka ta saka masu tana faɗin "Daddy baka ga mummy ba, yanzu zaki fara ko mummy? To ai shi yana da kirki, kuma ai kinga idan bashi da kirki ba zai zauna a gidan nan ba, ni mummy dan Allah ki bari mana, ke komai mutun ya yi sai kin yi complain, sai ki rinƙa cewa mutun yarinya, kullum ba'a kara girma a wajenki, kullum sai naci marking sosai a school, amma sai kice bana ƙoƙari, daddy ne kawai yake cewa ina ƙoƙari, shiyasa fa yanzu zan dai'na nuna maki papers ɗina, daddy da Yah Feroz kawai zan rinƙa nunawa". Ta kai karshen maganar tare da mikewa daga kwanciyar da ta yi, tana turo baki ta sa kai zata wuce izuwa ɗakinsu Rimsha. Daddyn nata ne ya dakatar da ita ta hanyar cewa "Zo nan abinki my daughter, rabu da mummy, ni nasan yana da kirki sosai, yanzu dai zo ki gaya mani a ina yake aiki dan na binciko wanene shi?". Ba musu ta nufi daddyn nata, a jikinsa ta kwanta tana tura baki tana faɗin "Daddy kai'na yana yi mani ciwo, ni ba zan iya jure Mark ya je wannan waje ba". Dafa kan nata ya yi tare da fara ce mata sorry, Zaira ƴar auta tana zaune shiru kusa da daddyn Jelly, baiwar Allah sam bata da rigima, tamkar ba ƴar auta bace ita, Anayar da take babba ta fita yawan rigima da shagwaɓa. Brr Naurat ce ta katse masu zancen da cewa "Mark dai jika ne ga babban yayanmu, haka jika yake a wajena kamar yanda kuke jikokina, so bana tunanin mutumin banza ne, tunda har yana tare da su Saif, to a gaskiya shi ɗin ba mutumin banza bane, a gabaɗaya su Saif babu na banza a cikinsu, kuma sai hali yazo ɗaya ake abota, dan haka ina kyautata mashi zato, kuma ina farinciki da Allah yasa jinin babban yayana zai auri nawa jinin, duk da sun gujeni, sun koreni a cikinsu, to ga shi Allah zai sake haɗa ni zumunci da su ta kan jikokinmu kuma, mu zamu aurawa Mark Anaya in har tana son shi yana sonta, shikenan sai ya karɓi musulci ayi masu aure". Kusan a tare dayawa daga cikin jama'ar palon suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya, daddyn Anayar ya ji daɗi sosai, ita kuwa Anaya cool murmushi ta saki tana faɗin "Good ƴar tsohuwa that's why i like you, ashe gwara da baki mutu bama, ga shi kin yi amfani". Ita dai mummyn Rimsha baiwar Allah, duk kunya ya rufeta, kunyar Brr Naurat ma take ji sosai, ga su Abban Imran dukka surakananta ne, hakan yasa duk ta takure waje guda,. A duk cikin palo ita da aunty matar Abbi ne kawai suka san menene kunya, sune kawai masu kunya, ita ma Ammien su Imran ba kunya ke gareta ba, kowa yasan kabilar igbo dai ba kunya ce da su ba. Duk Anaya ta san mummyn Rimsha ta ji wani irin kunya, ta kuma ga laifin mummyn Anayar sosai, dan kome Anaya zata yi a yanzu, to laifin mummynta ne, saboda Anaya yarinya ce, kuruciya na a kanta sosai, tun farko ya kamata mummyn nata ta koya mata kunya, kamun kai, kamala, da dai sauransu, amma ji yanda Anaya take magana abu sam babu tsari, iyayenta ne a cike a cikin palon nan, amma ita babu ruwanta, tamkar da sa'aninta ko kannanta or kawayenta take hira, abin sam bai yi wa mummyn Rimsha daɗi ba, bayan ita da Aunty kowa a cikin palon babu wanda ya ga aibin abin da Anayar ta yi, shi ma daddyn Rimshar bai ga aibin hakan ba, dan a cewarsa, ai yarinta ce kawai tasa Anayar yin hakan, idan ta girma zata dai'na........Babban magana girma kuma na nawa?. Haka suka cigaba da zuba hirarsu har zuwa rana ta ɗago, Anayar ma tuni ta yi barci a kwance a saman laps na daddynta, sai sauke nauyayyar ajiyar zuciya suke yi a cikin barci, sun sha kuka sun ƙoshi, ita ma Jehan barci ne ya ɗauketa, ta ci kuka kamar ba gobe. After 2 days. A cikin wannan kwana biyu da suka wuce, abubuwa da dama sun faru, bari mu fara da ɓangaren su Lion, sun isa Enugu state lafiya, kamar yanda Ammie ta basu address ɗin gidansu, haka suka yi amfani da shi, sai dai ko da suka je, gidan babu kowa, gate ɗin gidan ma a rufe yake ruf, da alama an ɗauki lokaci babu mutane a cikin gidan. Zubawa gidan idanu sosai Lion ya yi, kai daga ganin gidan kasan ba iya kuɗin nema ne kawai ya gina shi ba, wannan uban kuɗi da aka narka wajen gina gidan, ai dole sai da kuɗin TSAFI, dama already Ammien ta gaya masu Queen bata zama a gidan, bata nan a cikin gidan, kuma gidan babu kowa, dan haka ko sun je, wahala za su sha, shi kuma Lion abin da kuka sani ne, a duk lokacin da ake magana, to yana nutsuwa ne ya saurari maganar da kyau, dan tattare zancen mai maganar a cikin ƙwaƙwalwarsa yake yi, saboda samun mafita, yana aiki ne da kaifin basirarsa sosai da sosai, a lokacin da Ammien take bada labarin Daular Mutuwa, a lokacin ya nutsu sosai yana jinta, a maganarta ta ce a baya tana shiga har cikin Daular Mutuwar, which means da akwai hanyar da zai sadaka da Daular Mutuwa daga ta cikin gidan kenan, kuma dama ai da kamar wuya ace babu wata hanya daga cikin gidan Queen da zai sadaka da Daular, tun da ita ce shugaban Daular, to dole akwai hanyoyi ma ba hanya ɗaya ba ta cikin gidanta, hakan tasa ya ce da Ammien ta bashi address na gidan Queen ɗin, kun ji masu hikima da basira, ita kuma Ammien sam bata kawo cewa da haka zai yi amfani ba, dan ita bata taɓa shiga Daular Mutuwa daga ta cikin gidansu ba, ta waje take shiga, Queen ta ɓoye masu hanyar cikin gidan, hanyar sirrice wanda babu wanda ta yarda ya sani, sai ita kaɗanta. Duk sojojin sun tsaya suna jiran su ji me Lion ɗin zai ce, basu ankara ba sai ganinsa suka yi ya yi bismilah ya kama gate ɗin gidan ya haye, dan ba mutane a cikin gidan. Wani abin da basu sani ba shi ne, tun da suka baro garin Kaduna a kan idanun Queen suke tafiya, har suka iso Enugu, duk motsinsu tana ganinsu, ta barsu ne kawai su iso, dan a cewarta a cikin satin nan, suna da liyafa a gidan nata, dodan tsafinsu na bukatar jini sosai, akwai wasu sabbin ma'aikata da suka karu, dama idan baku manta ba, duk waɗan da suka jima a Daular Mutuwa, in dai Queen ta kasa kashe su, to tana mayar da su mutanenta ne, sai ta juyar da su izuwa irinsu barbushi, to akwai wasu mutane guda biyu ciki har da Mustapha da wani, a satin nan za'ayi liyafar mayar da su mukarraban Queen, wato su zama magicians suma. BABBAR MAGANA, shi ne yasa Queen ɗin ta bar su Lion ɗin su iso kawai ta bawa dodan tsafinsu su, asha jininsu a ji daɗin yin liyafa da kyau, har shiga cikin gidanta da suka yi a yanzu, duk tana kallonsu, dariya ma suke bata. Su kuwa bayan sun dira a cikin gidan, kai tsaye kofar da zata sadasu da babbar palon gidan Lion ya nema, babu tsoro ko ɗarɗar a tattare da shi, kai tsaye ya shige cikin gidan, kamar gidansa ne, yana shiga har da kunna wutar palon, dan ya gani ko suna aiki, sai dai a ganin sojojinsa ne suke ganin ya kunna wutar ne dan yaga ko suna aiki, shi kuma akwai dalilin da ya sanya ya kunna wutar, kunsan baya abu haka kawai, sai da dalili. Yana kunna wutar ya nufi wata ɗaki da take fuskantar kugu maso gabas, tsohowar ɗaki ce sosai, dan da alama a kaf cikin gidan, ɗakin ce kawai ba'a buɗe kofarta, saboda kofar ta kama sosai. Har lokacin idanun Queen na'a kansu, ta kuma cire duk wasu matakan tsaro na koforin dake gidanta wanda zai sadasu da cikin Daular Mutuwar, ma'ana ta buɗe masu hanya kenan, jira kawai take yi su shigo. Su kuma bayin Allah, sam basu sani ba, babu wanda ya kawo wa ransa cewa Queen ɗin tana kallonsa, ɗan gara Lion ɗin ma, shi dama yasan matsafan nan babu abin da ba za su iya yi ba. Yana isa wajen kofar, babu tsoro bai yi wata wata ba ya kai hannu ya murɗa handle ɗin kofar, nan take kofar ta buɗu, ganin ta buɗe ne yasa ya gane cewa lallai akwai wata a kasa, dan wannan kofa ta jima a rufe, bai kamata ace daga ya ɗan taɓata ta buɗe ba, dole da akwai wata a kasa, ga shi kuma gidan babu mutane ma, tun daga nan ya fara zargin wani abin a ransa, sai dai bai nunawa sojojinsa da alamar matsala ba, saboda kada ya sare masu gwiwa, ita kuma Queen bata taɓa tunanin cire makullan kofofin da ta yi zai iya sanya Lion ya fara zargi ba, bata kawo haka a ranta ba ,dan bata san kaifin basirarsa da kwakwalwarsa ba, sai dai hakika ta jinjinawa jarumtarsa, musamman yanda ya shigo mata gida kai tsaye, ya kuma nufi wannan kofa babu ko tsoro a ransa, yana acting tamkar shi ya gina mata gidan.......... (ni kuwa na ce in dai lion ne fin haka ma zai yi, shi gida nawa ma ya shiga ya nuna masu izza tamkar shi ya gina masu gidan? ya kuma aikata abin da zai aikata ya fito lafiya lou, ya shiga gidan Abba tamkar gidansa, ya je ya ɗauki Akila, ya kuma ɗaura mata aure da Aseef, sannan ya taka kafarsa har kasar Russia, ya je ya ɗauko Brr Naurat, su ma ya shiga gidansu tamkar shi ya gina masu, har ma da ɗaure gabadaya ƴan gidan ya yi, haka kuma ya fito kasar Russia lafiya lou, saboda tsantsar karfin hali da nuna isa, haka ya shiga gidansu Rimsha kamar gidansa, ya ɗaukota ya fito, ai shi Lion dama dai'dai yake da kowa, ko ya kuka ce READERS? Yanzu kuma ga shi a gidan Queen of Daular Mutuwa, kamar gidansa ya shige😂 Queen taga iko da nuna isa😂) Cikin ɗakin suka shiga, gabaɗaya cikin ɗakin babu komai, wayam yake, sai lallausan carpet na alfarma dake sumfuɗe a cikinta. Zuba masu shegun idanunta Queen ɗin ta yi ta cikin ruwan tsafinta dake kwance a tsakiyar faɗarta kamar pool, sai kallonsu take yi, tana son ganin gudun ruwansu. Areef dai yana goye da uban jaka a bayansa, sai Allah yasan me ya lodo a cikinta!. Sai bin ɗakin da kallo sojojin suke yi. Wani irin sihirtatcen kamshi ne ya fara tashi a cikin ɗakin, shi dai Lion har cikin ransa bai yarda da wannan kamshi ba, dan haka sai ya ce da sojojinsa su sanya face mask a face nasu dan kada su shaki kamshin. Bai kai ga rufe baki ba, nan take sojojin nasa suka fara zubewa kasa kamar gawarwaki, dama wannan kamshi wani tuggune da Queen ɗin ta haɗa masu, ta ha kance kawai zata ɗaukesu izuwa cikin Daular Mutuwar. Lion kafin ya yi wani yunkuri shima sai ya ji gabaɗaya jijiyoyin jikinsa sun tsaya, nan take ya ji tamkar an sare mashi ƙafafuwansa, dole shi ma ya zube kasa, dan already dukkansu sun shaki wannan kamshin turaren. Areef yana ƙoƙarin yin kan Lion ɗin, shima sai ji ya yi tamkar an raba kafafunsa da jikinsa ne, nan take ya zube kasa, duk suka zama kamar gawarwaki, ga dai idanuwansu a buɗe, amma sam jikinsu babu karfi, babu mai iya motsa ko da ɗan yatsansa. Haka suka cigaba da shaƙar wannan daddaɗar hamshin duk wasu gaɓɓai na jikinsu suna mutuwa, har idanunsu ma ya rufe ruf, kamar babu rai a tattare da su. An ɗauki tsawon lokaci suna a haka, har sai da yamma ta yi, rana ta faɗi, sannan ne Queen ɗin ta fara ɗaukar mataki a kansu. Wasu zaratan mazaje jarumai masu ji da lafiya da karfi Queen ɗin ta aiko, zu ashirin cif, haka ta aikosu aka kwashi su Lion ɗin gabaɗaya, ɗakin dai babu wata kofa bayan wanda su Lion suka bi suka shigo, daga ta sama waɗan nan zaratan maza suka ɓullo, haka kuma da suka ɗauki su Lion ɗin, suka bi da su ta saman suka fita, ɓacewa suke yi ɓat........ KAI QUEEN SHEGIYA CE, TA WUCI TUNANIN MAI TUNANI TUNKARARTA SAI AN SHIRYA. Kai tsaye sai cikin Daular Mutuwar aka wuce da su Lion, basu san ta hanyar da aka bi da su ba, dan Daular Mutuwa fa a yanzu bata da hanyar shiga sam sam. BABBAR MAGANA TASHIN HANKALI DA BA'A SAKA MASHI DATE, SU LION ZA SU FITO KUWA?. A takaice dai a wani killatatcen waje Queen tasa suka kulle su Lion ɗin, waje ne mai cike da abubuwan ban tsoro da juya kwakwale, ashe ita Rimsha a cikin kaso ɗari ko kaso ɗaya na bala'in da kuma ɓangarorin dake a cikin Daular Mutuwar bata gani ba, akwai abubuwa da dama sosai. Gabaɗaya su Lion ɗin an kasasu ɗakuna daban daban, ba'a haɗasu waje guda ba, da alama Queen ta fi tsanar Lion a cikin tawagar, shi wani waje na daban mai cike da tsaro na bala'i ta kai shi, babu wani abin da idanu zai iya gani a wajen, saboda tsananin duhu dake a cikin ɗakin, ta sanya sarka ta ɗaure shi, ko motsi baya iya yi. Su kuma sauran sojojin ɗakunan da aka kai'su da akwai haske, suna iya ganin komai, kuma bata ɗaure su ba, kawai an zubasu a saman tiles ne aka barsu. Tsawon kwana biyu suna a sume, Queen kuwa tana ta harkar gabanta, bata bi ta kansu ba tukun nan. A can gida kuwa, sai adduo'i ake ta yi masu babu kama hannun yaro, kowa hankalinsa a tsananin tashe sosai, Rimsha kam har da zazzaɓi take fama da shi, ko sallar dare bata iya tashi ta yi, saboda rashin lafiya, abin kamar ba lafiya ba, sam ta kasa yi wa Noorish ɗin nata addu'a, ta zama tamkar kurma, ciwon nata ma akwai ayar tambaya a kansa, dan fa ko kallonta mutun ya yi sai ta daka mashi tsawa, ta zama tamkar ba ita ba........ Wannan shi ne abin da ya faru a cikin kwanaki biyun da suka wuce, dan haka mu koma kan story. Yau shi ne kwana na uku na kasancewar su Lion a Daular Mutuwa, sai a yau kuma Queen ta waiwayesu, a in da ta fara yi masu ɗauki ɗai'ɗai tana bawa dodan tsafinta, wayewar garin yau, ta kashe sojoji biyu daga cikinsu, kafin ta kashe su kuma, sai da ta dawo masu da hankulansu jikinsu cif, a kan idanunsu tasa aka ɗauresu, suna ji suna gani ta sanya aka fasa cikinsu, ta ɗebi abin da zata ɗeba, jininsu kuma kamar yanda kuka sani ne, an kaiwa dodan tsafi, sauran sassan jikinsu kuma tasa aka wuce da shi izuwa wajen da suke kulla harkokinsu da sauran gidajen matsafa dake a duniya, dan ta sayar masu da abubuwan da suke buƙata daga ciki....... Innallilahi wa Inna ilahirrajiun, ya ilahi ya lillahi, wannan musifa dame ta yi kama?. Mutun na uku a yanzu shi ne a kan layi da za'a kashe, ba kowa bane kuma face Areef na Jehan, shi Lion ma sai Allah ne kaɗai yasan halin da yake a ciki, shin yana raye ne ko ya mutu?. Ɗakin da Areef ɗin yake kwance yana sume suka nufa, babu Queen ɗin a cikinsu, waɗan nan zaratan kyawawan matasan igbo ɗin ne, sune masu aiwatar da komai, ita Queen idan an gama fasa cikin mutun, da tsafinta take ɗaukar abin da take so dan gane da sassan jikin wanda aka kashe, a takaice dai, ita bata fitowa, komai tana daga cikin faɗarta take aiwatarwa. Kamar yanda suka kwantar da Areef ɗin tun ranar da suka kawo su, haka suka zo suka same shi, bawan Allah, ko motsawa bai yi ba. Turo wannan gadon da suke yanka mutun a kai ɗin suka yi izuwa tsakiyar ɗakin. Zaratan maza biyu ne suka ɗauko Areef ɗin, suka kwantar da shi flat a saman bed ɗin, sannan suka zura hannayensa a cikin lock na bed ɗin, suka rufe, ta yanda ko an dawo mashi da hankalinsa, ba zai iya yin yunkurin komai ba, haka kafafunsa ma suka zurata a cikin lock suka datse gam. Sannan ɗaya daga cikinsu ya fito da wata sharɓeɓiyar wuka, sai kyalli take yi, har wani ɗaukar idanu take yi, ga kaifin bala'i, dama su shidda ne zaratan mazan, da mai rike da wukar sun haɗu bakwai dai'dai kenan. Tsayuwa suka yi shiru a kan Areef ɗin suna jiran Queen ta dawo mashi da tunaninsa, dan bakar zalinci da mugunta, sai mutun yana cikin hayyacinsa ma suke yin duk abin da za su yi, yana ji yana gani babu yadda ya iya da su, a da can baya, sai sun gusarwa da mutun hankali suke yanka shi, yanzu kuma tun bayan fitar su Rimsha suka kawo sabbin tsare tsare da wasu abubuwa na tsubbace tsubbacensu. Cikin ƴan sakannin da basu fi 30 ba, sai ga Areef ɗin ya buɗe ash eyes nasa, tamkar wanda aka tasa daga barci, idanuwansa sun kumbura sosai, saboda kwana biyu yana sume. Dishi dishi ya fara gani, saman ɗakin yake ta kallo, su kuwa waɗan nan maza, suna tsaye a kansa, suna jiran ya gama dawowa dai'dai su yanka shi, dukkansu kyawawan gaske ne, farare tas da su, sai dai shi mai ruke da wukar nan, haskensa na daban ne, ba hasken Nigeria ba ne, haka zalika kyansa na daban ne, ya sanya wata bakar handkerchief ya ɗaure daga hancinsa izuwa bakinsa, dan kada jini ta yi mashi fallatse, kuma yafi gabaɗaya matasan wajen tsawo, ya fisu cikar halitta ta kasance cikakken namiji. A hankali kallon Areef ɗin ta washe. Ya sha ruwan mamakin ganinsa a cikin wannan ɗakin, a hankali ya fara juya kallonsa, ya fara bin ɗakin da kallo. Cak ya tsayar da idanuwansa a kan waɗan nan matasan, da mamaki yake ganinsu, ya san dai sojojin Lion ba haka suke ba, fararen Turawa ne, waɗan nan kuma hasken Nigeria ke garesu, bakake ne ma a idanun Areef ɗin. To suwaye su kuma? Ya tambayi kansa da kansa. Yunkurawa ya yi zai mike, sai ya ji ko motsi ba zai iya yi ba, kokarin juyar da kansa ya yi dan ya kalli abin da ya hana shi tashi, ina shi ma kan nasa ba zata iya motsawa daga in da suka kwantar da shi ba, abin ba ƙaramin ɗaure mashi kai ya yi ba, ya yi yunkurin yin magana, nan ma abin ya ci tura, tamkar an ɗaure mashi harshensa ne, ya gagara ambatar sunan Allah, ga shi yana son ya tambayi mutanen su waye su, amma ba hali, Queen ta rufe mashi baki. Sake juya idanuwansa ya yi, dan idanun ne kawai suke motsawa a gabaɗaya jikinsa, sake fara bin waɗan nan zaratan mazan da kallo ya yi. Cak ya tsayar da kallonsa a kan wanda yake ruke da wukar, sosai ya zaro idanuwansa waje yana kallon matashin, shi ma matashin shi yake kallo. A dai'dai wannan lokaci Queen ta turo masu da sakon ta bada umarni a datse kan Areef ɗin. Hannu wanda yake rufe da wukar ya kai saman face nasa, a hankali ya janye wannan handkerchief ɗin daga face nasa, ya buɗe fuskar tasa kenan, sannan ya ɗaga wukar sama dan ya aiwatar da umarnin Queen. Tsabar shiga tashin hankali da ruɗu Areef bai san lokaci da waje baki da iya karfinsa ba, nan take harshensa ta sake, da iya karfinsa na karshe ya furta sunan Aseef, ya yi maganar yana kallon matashin dake ruke da wukar yana ƙoƙarin cire mashi kai. Ba shakka Aseef ne, ko mutuwa ya yi ya dawo, ba zai taɓa mance Aseef ba, idan zai kasa gane kowa a duniya, to banda TRIPLETS nasa, meya kawo Aseef Daular Mutuwa? Yanzu kenan Aseef kashe mutane yake yi? Me haɗinsa da su Queen? Menene gaskiya? Shin ma wanenen Aseef ɗin?!!! Idan baku manta ba Josephine sun canza ɗaya daga cikin TRIPLETS, kuma Lion yana zargin Aseef ne, hakan na nufin Aseef ɗin ne da gaske? Kenan shi ba mutun bane? Kada fa ku manta a gida suka baro shi yana kukan rabuwa da su! Kenan dama Aseef zai iya kashe TRIPLETS nasa? Ko dai yaya ne, wai wanenen shi!!!!!!!!!!!!!!, Ko dai ba shi bane? Amma dai Areef ba zai taɓa iya kasa gane Aseef ba gaskiya, tun da ya ambaci sunansa, to ba makawa shi ɗin ne!!!! Tirkashi, yau ake yinta, wata sabuwar cakwakiya mai ƙulle kai🧠. Na barku lafiya, har kullum taku ce PRINCESS TEEMA ta amana mai salon ban mamaki da ruɗa kwakwalwa!. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E13 Date: 23/4/2024 "Aseef what are you doing here?". Ya yi maganar cikin tsananin fitar hayyaci, da ruɗu, dan ko a mafarki bai taɓa tunanin zai ga Aseef a Daular Mutuwa ba, kuma a nan ɗin ma yana ƙoƙarin kashe shi, wlh zai iya rantsuwa har ga Allah wannan Aseef ne ba gizo ba. Shiru Aseef ɗin ya yi bai amsa mashi ba, sai ma sanya hannu da ya yi ya mayar da handkerchief ɗin face nasa, sannan ya ɗaga wukar da gaske zai datse mashi wuyar, cikin kwanciyar hankali da kwarin gwiwa yake aikwatar da komai nasa, ga kuma tsantsar nutsuwa a tattare da shi, ba zaka taɓa cewa Heartbeat na TRIPLETS da ya kasance rago mai shagwaɓar tsiya bane, a nan ya zama mai taurin zuciya, mara imani da tausayi. "Aseef before you kill me, talk to me fist pls, duk da nasan cewa kai ne, amma ka kara share mani tantama kafin ka yi abin da zaka yi". In a cool voice ya ce "Yeah Areef, it's me, what's next that you want me to tell you before the time of your death". Cikin kwarin gwiwa, jarumta, da nuna isa ya yi maganar, sam babu shagwaɓa ko ɗigo a muryarsa. Tashin hankali, ai shi Areef ganin Aseef ɗin da kuma tabbatarwa da shi ɗin ne yafi kashe shi ɗin da za'ayi ɗaga mashi hankali, yanzu dai da gaske Aseef ɗin me babu tantama, kuma da kansa zai kashesu? Innallilahi wa inna ilahirrajiun, ya ilali ya lillahi. Godiya ga Allah Areef ɗin ya fara yi da Allah yasa shi ne ya kalli Aseef ɗin ba Lion ba, da Lion ne zuciyarsa zata buga, yanda yake tsananin kaunar Aseef ɗin fiye da kansa, sai dai bai san cewa Lion ɗin ma yana a kan hanya ba. "Babu wani abin kuma da nake son sake sani face na ce maka kada ka cutar da Lion, kome zaka yi mana ni ka yi mani ni kaɗai, please ka bar Lion ya huta, ya wahala a kanmu ɗan tahalikin nan, tun muna yara, a kanmu ya koyi faɗa, a kanmu ya koyi zafin zuciya, ka fi kowa sanin cewa saboda kai Lion ya koyi faɗa, a primary school shi yake tare mana faɗa, komai muka kwaso shi yake tare mana, ya tsaya mana a kan maraicinmu na rashin uwa, ya bamu farinciki fiye da kansa, ya kula da mu fiye da rayuwarsa, burinsa kawai ace muna yin yanda muke so, please Aseef ka kashe iya ni kaɗai, ka bar Lion, ka barshi ya huta, kada ka ci amanarsa". Ya kai karshen maganar idanunsa sun yi jajir tamkar jini. Cool murmushi Aseef ɗin ya saki, daga bisani kuma ya ɗaure fuska tamau, cikin muryar shagwaɓa tamkar yanda yake magana a gida ya fara magana yana turo baki "I can't kill you my Areef, i can't do anything to you my TRIPLETS, ku ne ni, kune bugawar zuciyata, kune farincikina, haka zalika ba zan iya bari ko kuda ya taɓaku ba, kamar yanda Lion ya tsaya mana tun muna yara har izuwa yanzu, bai yarda ko kuda ya taɓamu a rashin son ranmu ba, to nima a yanzu Allah ya ara mani lokaci da dama na taimake ku, na ceceku my TRIPLETS!" Ya kai karshen maganar tare da juya wukar hannun nasa ya datse kan ɗaya daga cikin matasan dake tsaye a gefe da gefensa, nan take matashin ya zube kasa bai shura ba, sai jini dake malala a kasa kamar an buɗe bakin fanfo. Kafin sauran su yi wani yunkuri, ya sake datse kan ɗaya. Cikin zafin nama sauran suka yi kansa, ita kuwa Queen dake kallonsu, a zabure ta mike tsaye, dan bata taɓa tunanin cewa ba mutuminta dake yanka mutane bane, tambayar kanta take yi ina wancan mutumin nata mai yanka mutanen kenan? Tashin hankali, wato gaba ma da gabanta, wai aljani ya taka wuta, Queen ta iya bibiyar su Lion tun da suka baro Kaduna, har suka shiga Enugu, har izuwa Daular Mutuwa, amma bata iya gane ya aka yi mutuminta mai datse kan mutane ya sauya ba, bata iya gane shi ɗin ina yake ba, bata iya bibiyar Aseef ba, shin ta yaya aka yi Aseef ma har ya shigo cikin Daular Mutuwar ba tare da ta sani ba? Ya aka yi har ya kashe ainahin mutuminta mai kashe mutane ba tare da saninta ba? Ya akayi har ya shiga cikin tawagar mutanenta ba tare da saninta ba? Wanenen shi ɗin to? Wai wanenene Aseef?!!!!!!. Idan kuwa da gaske Aseef ya zo taimaka masu ne, to kenan hakan yana nufin da wata manufa na daban Josephine ta sanya shi a cikinsu? Ke nan ba ta canza ɗayan TRIPLET'S ɗin bane dan ta cutar da su? Ko dai yaya abin yake ne? Amma to tun farko ma menene makasudin canza TRIPLETS ɗin? Manene yasa suka kawo Aseef suka ɗauki na ainahi? Ina na ainahin yake? Shi Aseef ɗin su waye iyayensa? Dole dai akwai wani dalili mai mugu mugun karfi na yin hakan, akwai babbar cakwakiya da kulla kulla a wannan lamarin, wanene mai gaskiya a cikinsu Josephine? Alkalamin PRINCESS TEEMA ce kawai zai warware maku gaskiya, dan haka ku kasance da ni taku PRINCESS TEEMA mai abin ban mamaki. Babbar magana, a tsananin razane Queen ta mike daga saman kujerar mulkin nata, sai dai kafin ta yi yunkurin yi wa mutanenta dake faɗa da Aseef ɗin wani tsafi, tuni Aseef ɗin ya kashe su dukka, babu imani babu tausayi ko ɗigo a tattare da shi, haka ya yi masu kisan kiyashi, tamkar ba Heartbeat namu ba. Babban abin da ya girgizata ya kuma jijjiga tunaninta, bai wuce yanda ta ga Aseef ɗin ya buɗe Areef daga lock da suka sanya shi ba, ita dai tasan cewa bayan ita babu wanda ya isa ya buɗe waɗan nan locks ɗin, to ya aka yi Aseef ya buɗe shi? Kuma dai da tsafi ake buɗewa, hakan na nufin shima yana da tsafi kenan?. Ta saki baki tana mamaki, bata ankara ba sai gani ta yi dukkansu biyun sun miƙe tsaye, Areef sai tambaya yake yi ina Aseef ya samu karfi haka? Shi kuma Aseef ɗin sai tambayarsa yake yi ina Lion nasu yake? Wannan shi ne cakwakiya....... JAMA'A NI KAI'NA INA SON SANIN WANENE ASEEF FA? DAN A GASKIYA WANNAN ABIN AKWAI ƊAURE KAI. Ganin Areef ɗin zai ɓata masu lokaci wajen tambayarsa wanene shi, sai ya riko hannunsa tare da jansa suka fita, har sun fita ɗakin, sai kuma Aseef ɗin ya dawo ya ɗauki jakar da Areef ya zo da ita. Ita kuwa Queen sai kallonsu take yi ta cikin ruwan tsafin, bata ɗaga hankalinta dan sun fito daga ɗakin ba, dan a cewarta, ai tana da zararan mukarrabanta da za su yi gunduwa gunduwa da su, su cinye namarsu ɗanya, dan haka sam bata wani damu ba, bata san cewa abin ba haka yake ba, ko a tsafin ma ai akwai iyayenka wajen yin shi, gaba ne da gabanta, ita har yanzu a iya Africa take tsafinta, su kuma tsafinsu bugawa suke yi da manyan kasashen duniya masu faɗa aji, su ba kananan kwari irinta bane, iyayenta ne a iskanci da bala'i. E KAM BABU SHAKKA IYAYENTA NE, GA ALAMA TA FARKO, ASEEF YA IYA SHIGOWA HAR YA KASHE MUTUMINTA MAI YANKA MUTANE, YA KUMA SHIGA CIKIN JAMA'ARTA DUK BATA IYA GANEWA BA, BABBAN ABIN TAMBAYAR MA SHI NE, TA YAYA YA SHIGO CIKIN DAULAR?. Suna fitowa harabar wajen, wasu jiga jigan maza masu kama da su barbushi ne suka kewayesu, zaratan maza ne majiya karfin gaske, yanayin nunfashinsu ma kawai abin tsoro ne, dan suna numfashi yana fitar da hayaki tamkar waɗan da aka ɗaurasu a saman garwashin wuta mai tsananin zafi, wasu jibga jibga da su, ga gashin kansu kamar jijiyar bishiya, a tsai tsai kamar kawon shaiɗan, idanunsu kawai abin tsoro ne, tamkar ba idanun bil adama ba, wasu jajir dawu tamkar sun zuwa jini ne a ciki, hannunsu kawai abin kallo ne, wasu dama dama da su, kirjin nan nasu a tsaye tamkar bishiyar kuka, sam yanayin halittarsu ya fita daban da ta mutane, kai daga gani kasan da tsafi suke amfani, da tsafi suka mayar da halittarsu hakan, jikkunansu babu riga, sai dai ta kasa ne kawai suka rufe, sun kasance su goma ne cif. Hakika Areef ya tsorata da ganin waɗan nan halittu, ya girgiza na ganin munin halittarsu, sai dai bai sare ba, bai ji sanyin gwiwa ba, dan hukumar C.I.A idan ba gani suka yi an kashe su ba, to wlh basu taɓa tsarewa a kan abu, komai gani suke yi za su iya, haka Areef yake ganin kamar zai iya faɗa da su, yana ganin mutane tamkar gunguma gungumar kumaka da aka sassaka da dafaffiyar karfe, amma hakan bai sa ya ji ba zai iya yakarsu ba. A tare waɗan nan gunguma gungumar mutane suka nufesu, suna taku kasa na amsawa da dib, dib, dib. Su kuwa suna tsaye suna kare masu kallo. Sai da suka isa wajen ne Aseef ya ciro da wata sharɓeɓiyar wuka daga kugunsa, shi kuma Areef ya yi bismillah dan su fara yaki, sai kuma me? Yana ambatar wannan bismillahi gabaɗaya dakarun Queen ɗin suka ja baya da su, tamkar waɗan da aka janye da tsafi. Ita dai Queen tana cikin faɗarta har wa yau, sai kallon abin al'ajabi da mamaki take yi, wani irin zaro shegun idanun tan nan ta yi na ganin yanda mukarraban nata suka ja baya daga tunkarar su Areef ɗin, irin wannan jan baya kamar an janyesu haka? Abin ya ɗaure mata kai. Amma bata sare ba, sai ta sake yin amfani da tsafinta ta sake turasu suka tunkari su Areef ɗin. A karo na biyuma bismillahi Areef ya yi, dan su TRIPLETS komai za su aikata, to fa da bismillah suke farawa, sunan Allah shi ne a farko kafin su yi komai, kun tuna lokacin da Lion zai shiga gidan Queen? Sai da ya yi bismillah, ko zama za su yi a saman sofa, sai sun yi bismillah, ta yanda koda akwai wani abin da aka kullah masu, to wannan sunan Allah da suka kira, zai zama sanadiyar warwarewar komai, idan suka yi bismillah za su zauna a waje, to duk wasu shaiɗanun dake zaune a wajen za su watse, kowa zai kama kansa, hakan zai sa da wuya su zauna a waje kuma kuga sun yi faɗa ko makamancinsa, saboda da sunan Allah suka fara zama, babu wani shaiɗani a wajen da zai iya zugasu su yi faɗa, shiyasa kuke ganin kullum cikin Kaunar juna suke, babu faɗa babu kyaran juna. A karo na biyu da ya yi bismillah ma, a dubu ɗari jakarun suka sake ja da baya, abin ya yi matuƙar girgiza Queen ba kaɗan ba, dan haka sai ta miƙe tsaye, cikin nuna isa da izza ta sanya hannu a saman ruwan tsafin nata, tare kuma da fara surutansu irin na matsafa, nan take ruwan nata ya fara juyawa kamar fanka. Shi ma Aseef ya yi mamakin ganin yadda mukarraban Queen ɗin suka kasa iso su, sai dai bai nuna ba, kuma already shi ma kun san musulmi ne, akwai dai wata a kasa, amma ban da haka, duk wata addu'ar da Areef zai yi, shima zai iya yinta, so dama kunsan already shi bai yi nisa a karatun addini bane, bai san ma'anonin wasu adduo'i ba, ya dai iya karantawa ne kawai, ita kanta bismillahi bai san me ma'anar yinta ba, ya dai san sunan Allah ne. Wannan surutai da Queen take yi ba komai bane face karawa jama'ar tata karfi, da kuma dakiya. Haka kuwa aka yi, bayan ta gama surutanta, sai ta sake turasu ga su Areef ɗin, bayin Allan, su kuma suna tsaye gam, babu alamar tsoro ko sarewa a tattare da su, sai ma kwarin gwiwar da suka sake ji mai karfi yana kara ratsasu. Da wani irin mahaukacin zafi mukarraban Queen ɗin suka nufosu a karo na uku, dafe kai Areef ya yi yana faɗin "La ilahaillah anta subahanaka inni kuntunminazzalumin, wai ku idan za ku zo mu kashe juna kawai kuzo mana, amma saboda walaƙanci sai ku tinkaro mu, sai mun shirya kuma ku sake ja da baya, wannan abin fa ya fara kona mani rai, wani irin abu ne wannan? Ku yi maza ku karisu in ma kashe juna ne sai ayi komai a wuce wajen, ban son jan rai, zuciyata ta fara hasala".......faka faka kenan. Bai kai karshen surutan nashi ba ya ji an taɓa shi, da sauri ya ɗago kansa, Aseef ne ya taɓa shi, yana ɗagowa ya ce mashi "To ai sai ka dai'na surutun haka ko? Mutanen da sun ɓace kamar haske, kai katsaya sai wani zuba magana kake yi kai kaɗai". Zaro idanu ya yi yana faɗin "Ban gane sun ɓace ba? Ina kuma suka je? Ba kashe mu suka zo yi ba wai? Yaushe suka ɓace?". Duk waɗan nan tambayoyi ya jerosu ne da mamaki a saman face nasa. Shiru Aseef ɗin ya yi na ƴan sakanni kafin ya ce "Oho time da ka fara surutanka mana, ni muje hai". Shiru Areef ɗin ma ya yi yana tunanin to a kan me za su ɓace kuma?. Bai san cewa wannan kalma ta lailahaillah anta subahanaka inni kuntuminazzalumin da ya faɗa bane yasa gabaɗaya suka yi wani irin ɓacewa ɓat, ita kanta Queen ɗin sai da kalmar ta sanyata ta yi wani irin baya baya ta faɗa a sama kujerarta na mulkin, karo na farko a rayuwarta da har wani jiri jiri take gani, kanta har wani sara mata yake yi........... My peoples, wannan shi ne banbancin duk wata shirka da kuma sunan Allah, idan mutun zai yi shirka, ko wani saɓon Allah, to ba makawa sai ya ɗauki lokaci yana haɗa abubuwa, sai ya sha wahala kafin ma ya iya aiwatarwa, kuma ko da ya yi bata taɓa ɗorewa, misali, mushiriki, sai ya haɗa abubuwa da dama ya sha bakar wahala kafin ya iya yin tsafin nan nasa, ya azabtar da kansa ta hanyar shan jini da sauransu, kuma koda sun yi tsafin, baya taɓa tabbata, haka za su yi ta shan wahala, amma ba zai tabbata a jikin wanda suka yi wa ɗin ba, domin annabi ya ce tabbas tsafi bata tabbata a jikin bawa, dole akwai time da zai warware, lokaci gare shi, ɓarawo, sai ya sha wahala wajen yin sata, yana yi zuciyarsa tana bugawa da karfi karfi, saboda yana tsananin tsoron kada a kama shi, idan rana ta ɓacin mashi, to fa har kashe shi ana iya yi, idan kuma ya tsira, to abin da ya sata ɗin ba zata taɓa yin albarka ba, kamar iska haka zata wuce, kunga a nan ya sha bakar wahala sosai a banza, mazinaci, yana yin zina zuciyarsa na dukan uku uku, tsoron kada a kama shi, ko kuma wani abin ya faru yake yi, sannan idan har ya yi zina sau ɗaya, to kofa ce ta wahala da talauci a rayuwarsa take buɗe mashi, mashayin giya, idan ya sha giya, ya shiga cikin maye, ya fita a hayyacinsa, zai iya zuwa ya hau babban titi mota ta take banza ma ba tare da ya sani ba, babban musiface mutun ya gusar da hankalinsa daga jikinsa, masu yin luwaɗi, su maɗigo da sauransu, duk suna kasancewa cikin mufisa da wahala, masu yin lesbian a hankali hankali za su fara wari, ana tafiya ana tafiya har gabansu ta lalace, saboda sun kauce hanyar yadda Allah ya ce ayi, masu bada bayansu ayi zina da su ta wajen, su lalacewarsu ma tafi munin gani, dan har tsutsa suna yi, Allah ai ba abin wasa bane, Allah yana son bayinsa fiye da yanda suke son kansu, dan haka ba zai taɓa hana bayinsa wani abin na jin daɗin rayuwa ba, duk abin da kuka ji Allah ya haramta, to ba makawa wannan abin cutarwa ce ga bayinsa, masu yin bleaching wlh har wani irin wari suke yi, suyi ta zuba turare a jiki, amma kamshin perfume ɗin daban, warin jikin nasu daban, komai za su yi wa jikinsu, wlh ba za su dai'na wannan wari ba, saboda me? Saboda sun kauce hanyar Allah, Ubangiji ya fi kowa sanin abin da zai dace da bawansa, bai yi ki a bakar fata haka kawai ba, haka zalika bai halicci fararen fata haka kawai ba, yasan da cewa shi ne yafi dacewa da kowa daga cikinmu, amma ku ƴan iya, ƴan bani na iya, fit kin daka tsalle kina baka kice sai kin dawo fara, Allah yasan da farar fatar, amma ya baki baka, sai ki gode mashi ba wai ki ra'ina yanda ya yi maki har kina ƙoƙarin canzawa ba, a takaice dai duk masu aikata aikin saɓon Allah, to wlh a wahale suke, su kuma waɗan da suka ce Allah ya isar masu akan komai, wlh ko barci suke yi Allah yana isa masu ɗin, nafi jin daɗi a koda yaushe na yi maku misali a aikace ba wai da baki ba, dan ta hakan ce kawai za su fi ganewa, yanzu misali, ita dai Queen kunsan ba karamar wahala ta sha wajen gina waɗan nan dakarun nata ba, ko da ido ku kunsan dakare ɗaya ya isa ya kashe TRIPLET'S gabaɗayansu, ya isa ya cinyesu gabaɗaya, amma su TRIPLETS ɗin kuma sun ce Allah ya isa masu a kan komai, kuma ga shi ya isa masu ɗin, ƴar ƙaramar kalma ce a baki wajen faɗa, amma babbace a aikace, wato bismillahi munfara da sunan Allah kenan, ga shi su basu sha wahala ba, da iya bismillahi suka ruguje dakarun, ku sani bawai kankantar kalmarce abin dubawa ba, girman abin da ta kuntsa ce abin dubawa, bismillahi, mun fara da sunan Allah, tun da kuwa suka fara da sunan Allah, to ba makawa Allah zai tsaya masu, dan shi suka sako a gaba, shi ne kuma zai shige masu gaban a komai, abin da nake son nuna maku a nan shi ne, duk wani mai aikata saɓon Allah, to wlh a wahale yake har karshe raywuarsa idan bai tuba ba, idan ka ruke Allah, ka gama komai, ba zaka taɓa shan wahala ba, babu wanda zai iya kareka a kan komai a duniyar nan sama da Allah, to ni dai PRINCESS TEEMA na ce Allah ya isa mani akan komai da na saka a gaba a duniyar nan, kuma shi ne a kan gaba a komai nawa, shi na ruke babu wani ja in ja, saura ku kuma my READERS?. STORY. Wucewa gaba Aseef ɗin ya yi yana faɗin "Kai Areef ka cika tambaya". Ya yi maganar a tsananin shagwaɓe, yadda dai yake yi masu magana a gida. Harararsa Areef ɗin ya yi yana faɗin "Kai ni kazo ka gaya mani ta yaya aka yi kazo nan wajen, ba zan yi mamaki da wannan karfin da ka samu ba, dan nasan kai jininmu ne, dole dama kana da karfi, shagwaɓa ce kawai ta cinye karfin, amma ya aka yi kazo nan? Shi nake son sani". Miƙa mashi jakarsa Aseef ɗin ya yi, ba tare da ya dakata daga tafiyar da yake yi ba ya ce "Kai kanka fa baka san ta yaya ka zo nan ba, amma kake tambayar wani ta yaya ya zo? To ta sama na faɗo, ni ka ruke jakarka na gaji ba zan iya ba, ya fi karfina". Ya kai karshen maganar tamkar zai saka kuka. Duka Areef ɗin ya kai mashi a dantsen hannunsa. "Ba wani nan sai ka gaya mani ta ya aka yi kazo nan". Kukan shagwaɓa ya sanyawa Areef ɗin yana faɗin "Kai fa mugu ne, to nima na san tayaya na zo ne? Kawai na ganni ne a kusa da kai, daga haka kuma sai ban sake ganina ba". Jinjina kai Areef ɗin ya yi yana faɗin "Sarkin rainin wayo na duniya ba, yanzu Aseef ni zaka kalla ka yi wa wannan tatsuniyar na cewa kawai ka ganka ne, sai kuma daga baya baka sake ganinka ba, to yanzu kuma da waye nake magana kenan?". Turo baki ya yi kamar zai sa kuka ya ce "Da Heartbeat na TRIPLETS kake magana mana, ni ka karɓi jakarka ya yi mani nauyi, ba zan iya rukewa ba". "Amma kuma ai ka iya kashe mutane rai shidda ko? Jaka ce ba zaka iya rukewa ba?". Kuka ya saka yana ƙoƙarin fara bubbuga kafa a kasa, da sauri Areef ɗin ya karɓi jakar yana faɗin "Rigimamme kawai, ni bani kayana". Ya karɓi jakarsa tare da wucewa gaba abinsa. Haka suka cigaba da tafiya, Areef yana gaba, shi kuma Aseef yana baya, sai wuce ɗakuna suke yi suna neman sojojinsu da kuma Lion. "Aseef wai ina Lion ne?". Areef ne ya tambaya. Shiru Aseef ɗin bai amsa mashi ba, ko da ya juyo dan ya ga meyasa ɗan uwan nasa bai amsa mashi ba, sai ya kalli wajen wayam, babu Aseef babu dalilinsa. Da mamaki ya juyo da kyau yana kallon hanyar, babu wata kofa dai da za'ace Aseef ya bi ya tafi, hanya ce doguwa, sai ɗakunan mutane da suke a rufe ruf. Shiru ya yi yana al'ajabin ina Heartbeat nasun kuma ya yi?. Ina da tantanma a kan Aseef sosai wlh!!. Ya jima a tsaye a wajen ya kasa motsawa, tamkar wanda ruwa ta cinye. Almost 20 mins yana tsaye yana ta tunanin abin yi, kwatsam sai ji ya yi daga ta bayansa an taɓa shi. A razane ya juyo. Cool murmushi Aseef ɗin ya sakar mashi yana faɗin "Muje". "Aseef ta ina kabi ka bar nan wajen?". Ya yi maganar on a serious note. Turo baki Aseef ɗin ya yi tare da wucewa gaba ba tare da ya bashi amsa ba. Kamar ba lafiya ba Areef ɗin ya ji ya mance da tambayar da ya yi wa Aseef ɗin a yanzu, kuma ya mance da tambayar da zai sake yi mashi, haka ya sake bin bayansa suka cigaba da tafiya a wannan shegiyar doguwar hanyar, suna tafiya Areef yana ambaton sunan Allah a cikin zuciyarsa, dan shi dama baya rabuwa da yin tasbihi, wannan tasbihi da yake yi kuma shi ne ya yi mugu mugun taimaka masu wajen kubcewa daga kan idanun Queen, kwata kwata ta dai'na ganinsu a yanzu, gabaɗaya sun fita daga idanun tsafinta, dan haka sai ta tashi ta fara gagarumin sabuwar shiri, dan ta lura abin da take gani ƙaramin abu, to yana neman ya zama babban abu, gara ta miƙe tsaye. A takaice dai sun yi tafiya mai nisa kafin su samu su fita daga cikin wannan waje, suna fita kuma wata duniya suka sake gani, dan faɗawa wani ɓangare na gidan suka yi, gani suke yi tamkar a wata sabuwar duniya suke, Daular Mutuwa gidan akwai girman gaske, babu abin da basu da shi a ciki, Daular ce ta gasken gaske kuwa. "Areef yana da kyau mu raba hanya a yanzu, zan je neman fadar wancan tsinanniya, dan ita ce kawai zata nunamana gidan uwar da ta kai Lion, kai kuma ka nemo su kaka, Heartbeat da sauransu". Cewar Aseef. Ya kai karshen maganar tare da matsowa sosai kusa da Areef ɗin, a kunne ya raɗa mashi "Ka nemomini Heartbeat tawa da wuri, dan ko a yau muka koma gida sai na yi dis virgin nata, bafa zan kyaleta ba". Ya kai karshen maganar tare da juyawa ya nufi ɓangaren hagunsa. Areef ɗin yana son ya yi mashi magana, amma ya kasa, yana son yi mashi tambayoyi sosai, amma sai ya ji ya kasa, harshensa ta yi nauyi, hakan na nufin kenan shi Aseef bada tsafi yake amfani ba? Ko dai yaya ne? Wannan abin akwai ruɗu da ɗaure kai. Areef bawan Allah ya jima tsaye a wajen kafin daga bisani ya nufi nasa hanyar, dan su aiwatar da abin da ya kawosu da sauri su fita a cikin gidan, sai dai kuma zuciyarsa cike take fal da tunanin irin jarumtar Aseef ɗin, tashi ɗaya ya zama jarumi na gasken gaske, kuma ga dai shagwaɓar bai barta ba, idan ta motso mashi yana yi, ga kuma karfin bala'i da yake da shi tamkar wani shararren sadaukin mayaki. Haka dai suka rabu kowa ya yi hanyarsa, suka bazama neman ƴan uwansu, ita kuma Queen tana can tana shirya masu gagarumin shiri ta yadda za ta kashesu gabadaya lokaci guda, tana ta ƙoƙarin taga ta haɗesu waje guda ta konesu ta huta...... Mu leka gida kuma muga me yake faruwa. KADUNA. Wasa wasa Rimsha rashin lafiya sai karuwa yake yi, da mummynta da gwaggo dai kamar yanda kuka sani ne, sun ɗauka laulayin ciki ne, saboda kusan duk abin da take yi a yanzu, ya yi kama da mai ƙaramin ciki, a koda yaushe tana zaune shiru tamkar gunki, bata son hayaniya, kuma ga masifar tsiya idan ka yi mata abu, duk zafi da tsiwa irin na Jehan, to fa yanzu ta shafawa Rimsha lafiya, dan yanzu Rimshar ta fita iya bala'i, jiya ma saura kaɗan su buga dambe, dan Jehan ɗin ta kalleta da ido kawai. Gwaggo da daddy kuma sun hana ayi wa Rimshar abin da bata so, dan gwaggo ta gayawa daddyn wai ciki ne da Rimshar, so dole a kula da ita a lallaɓata. (Kai jama'a ana al'amura a littafinTRIPLETS, wai Rimsha ce mai ciki?🤔 Ita da ko...... Ba ayi ba🤔) Daddy kam murna a wajensa ba'a magana, sai wani ririta suke yi, Jehan kuwa kamar zata fashe saboda haushi, sai Rimsha ta yi mata laifi, amma haka tana ji tana gani su gwaggo za su hanata ɗaukar mataki, abin yana bakanta mata zuciya ba kaɗan ba. A ɓangaren ita kuma Aafia, ta farfaɗo, ko da ta farfaɗo sai ta farfaɗo masu a kurma mara magana, sam sam bata cewa komai, da idanu kawai take bin mutane baiwar Allah, kome aka ce mata, da idanu kawai take kallon mutu, ba um bare umm. Daddyn su Lion ma ya sami lafiya sosai, sai dai har yanzu yana a kan bakarsa na cewa shi wlh bai san gwaggo ba, yana fitowa har palo ya zauna da su Uncle Herry, amma baya ko ɗaga idanu ya kalli gwaggon, ita ma bata bi ta kansa, dan Lion ya gaya mata kada ta kula kowa, ya ce mata kusan kowa da take kallo a gidan, to fa ba yin kansa ne yasa yake yin wasu abubuwa ba, akwai wata gagarumar matsala a kasa, dan haka ba ruwanta da kowa, shi idan ya dawo, zai binciko koma mecece ainahin wannan matsala bakiɗaga. Hakan tasa sam bata ko ɗaga idanu ta kalli Dr William ɗin, ita ma ta nuna kamar bata san shi ba, uncle T kuma Lion ya aike shi Usa, ba da shi suka tafi Daular Mutuwa ba, Jay ya koma Washington abinsa, yanzu saura John kawai, suna rayuwarsu iya su uku, Dr William uncle Herry, sai John, sam basu shiga harkar su gwaggo, suma su gwaggon, basu shi ga harkarsu. Jehan ce kwance a saman bed ɗin gwaggo, dama idan baku manta ba, ɗakin da daddynta ya zauna, shi ne ɗakin gwaggon a yanzu, ta lafe shiru a saman bed ɗin tana tunanin duniya da kuma mijinta. Kamar daga sama tunanin gidan Hjyr daɗi ya faɗo mata cikin ƙwaƙwalwarta, a hanzarce ta miƙe zaune, cikin sauri ta fara leke leke a bayan gadon gwaggon. Jim kaɗan tasa hannu ta fito da wayoyi guda biyu da ta taɓa ajiyewa a wajen tun lokacin da ta zo gidan kafin ta ta fi prison. Ɗaya wayar Abubakar Salahuddeen ne, ɗayar kuma wayar Adiva. Ganin wayar Adivan nan ya sanya idanunta sun ciko tab da kwallah, tunaninsu ya dawo mata cikin ƙwaƙwalwarta, addu'a take yi Allah Ubangiji hasa Hjyr daɗi bata lalata masu rayuwa ba, Allah sarki Maryam baiwar Allah, yanda ta sha fama da wahalar rayuwa, idan dai Hjyr daɗi ta lalata mata rayuwa wlh sun gama zaluntarta, kuma da izinin Allah sanadiyar wannan marainiyar Allah Maryam, in dai suka cutar da ita duk da whalar da ta sha, wlh Allah ba zai barsu ba, zai yi mata sakayya cikin gaggawa. Ƙoƙarin kunna wayoyin ta fara yi, sai dai dukka sun ki kawowa, dan haka sai ta nufi waje da su, bedroom nasu ta nufa, chaji ta je ta sanya wayar tare da zama a gefen bed ta buga uban tagumi tana tunanin mafita. A haka Jelly ta shigo cikin ɗakin ta sameta, kusa da ita ta zauna tana faɗin "Aunty Jehan ina kwana?". A lallai Ammie ta gyara Jelly, har da su Aunty Jehan, duniya sabuwa, wato rashin mahaifiya babbar musifa ce kuma babbar barazace ga tarbiya da kuma rayuwar yaro gabaɗaya, yanzu dai daga ɗan zamanta da Ammie har ta koyi wasu abubuwa masu amfani, ta nutsu sosai, Allah Ubangiji ka karawa mahaifanmu daraja, ka kara masu lafiya, ka kuma kara masu nisan kwana, waɗan da suka rigamu gidan gaskiya, Allah ka jikansu da Rahman. "Lafiya lou Jalila fatan kun zo lafiya?". Ta bata amsa tare da mikewa ta nufi waje, dan ta je wajen daddynta, yau ta tuna da rayuwarta ta baya gabaɗaya, tana son ta je ta gayawa daddynta labarin su Sadiq ɗin Katsina, bata san cewa mum ta riga da ta gaya mashi ba, ya kuma ce idan su Lion suka dawo, komai ya dai'dai ta, zai taka kafarsa har izuwa Katsinar da kansa, zai je ya gaishe su, ya kuma yi masu godiya. A garden ta isko daddynta, daddyn Anaya Abba da kuma Abbi, sai gwaggo da Brr Naurat da daddyn Jelly, suna tattaunawa a kan abin da ya wuce a baya, Brr Naurat ne ta ce daddyn Rimsha ya basu labarin yanda ya yi bayan ya baro gida, da kuma yanda ya yi rayuwa, yanda ya haɗu da mummyn Rimsha da dai sauransu, to bai kai ga fara basu labarin ba Jehan ɗin ta shigo baki ɗauke da sallama, a tare suka amsa mata, sosai Brr Naurat ta zuba mata idanu, tana tsananin Kaunar Jehan ɗin, saboda kamanceceniya da daddynta da take yi. Kuma a duk cikin surukanta Brr Naurat ɗin ta fi kaunar mummyn Rimsha da kuma Aunty matar Abbi, saboda sun fi girmamata, sunfi ɗaukarta da daraja, musammanma mummyn Rimsha, ta ɗauki Brr Naurat ɗin tamkar mahaifiyarta, hakan yasa ita ma tafi kaunarta sosai ita da ƴaƴanta Rimsha da Jehan, dama kuma kunsan already shi daddyn Rimsha shi ne shalelen Brr. A duniya kowa yana son na gari, kowa yana son mutumin kirki, mai kyautata masa, ya Ubangiji kasa mu zama na kirki a koma wani irin hali muke ciki. Kusa da daddyn nata ta zo ta zauna tana faɗin "Daddy yau fa na tuna da rayuwarmu ta baya ne, ina son naje Katsina wajen maman Sadiq, wlh tana da kirki over daddy, ta taimakemu sosai, ina son nima na taimaka mata, ina son ka bani kuɗi dayawa in kai mata". Da yake daddyn nata yana zaune kusa da Brr Naurat ne, sai Brr ɗin ta kai hannu tana shafa kanta, a nutsu ta ce "Haka ake so Jehan, idan mutun ya yi maka alkhairi kada ka taɓa mantawa da shi, Allah ya yi maki albarka". A tare suka amsa da Amin, sannan daddyn nata ya ce "To shikenan my baby, jeki cikin gida muna tattaunawa ne a yanzu, idan Allah ya dawo mana da su Areef lafiya, mun huta, komai ya lafa, zamu je Katsina ɗin ni da ke". Okey ta amsa mashi da shi, sannan ta miƙe ta bar wajen, cikin bedroom nata ta koma, a in da ta ɗauki wayar Rimsha ta zauna a bakin bed kusa da Jellyn tana mai cigaba da kiran number Areef tamkar yanda ta saba a koda yaushe, sai dai kash a koda yaushe number tasa a rufe take, babu network sam sam. Su kuwa su Brr Naurat, daddyn Rimsha ne ya fara basu labarin yanda ya yi rayuwa bayan barowarsa gida, cikin nutsuwa ya fara magana kamar haka............. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E14 Date: 24/4/2024 Su kuwa su Brr Naurat, daddyn Rimsha ne ya fara basu labarin yanda ya yi rayuwa bayan barowarsa gida, cikin nutsuwa ya fara magana kamar haka. "A lokacin da na fita gida, hotel na fara kamawa, ina shiga ɗakin nawa, na zauna na ci kuka na son ra'ina, a wannan rana na kwana ban yi barci ba, sai dai kuma na kudurci niyar duk wuya duk daɗi ba zan koma gida ba, ba zan sake waiwayar kowa ba, na kudurta a zuciyata zan yi rayuwata ni kaɗai'na, zan kuma tsaya tsayin daka na nemi ilimi, zan shiga siyasa, daga karshe kuma ina rokon Allah da ya bani iko da dama na samu na taimaki ƴan uwana a duk in da za su kasance, yin wannan tunani yasa ya sami karfin gwiwa, dan haka sai na tashi na yi wanka, na daura towel ɗin hotel ɗin na ɗan kwanta na huta, sai dai tunanin mummy da cikinta ya hanani sukunin, haka dai a daure ina yi mata addu'a. A washegarin ranar na nemi gida na saya, kuɗin da Mommy ta bani suna da mugun yawa sosai, da su na cigaba da yin rayuwata, na koma makaranta, na kuma fara sana'a, ko kaɗan bana tunanin komawa gida, a duk abubuwan nan da na saya kuma ko rabin kuɗin da mum ta bani ban taɓa ba, saboda kuɗin dollars ne, idan na canza kaɗan suna da yawa a kuɗin Nigeria, haka na cigaba da rayuwata ni kaɗai tsawon lokaci, ina zuwa makaranta, kuma ina juya kuɗina, akwai lokacin da ta kama dole na je gida, haka na shirya na je gidan, sai dai ban bari kunsan naje ba, takardun makarantata na je na ɗauka, a lokacin na sami mum tana zaune a garden, na tsaya tsawon lokaci ina laɓe ina ganinta, sai dai ita bata ganni ba, daga karshe na ɗauki abin da zan ɗauka na fita gidan, haka na kammala karatuna ni kaɗai na, ina kuma bibiyar ƴan uwana, ranar da aka ce daddy ya rasu, har gida nazo dan na tabbatar, amma babu wanda ya ganni, komai da yake wakana a gida ina sane da shi, har auren yaya babba duk ina sane da komai, kuma na tura mashi da gudumawata, sai dai bai san cewa ni ne na bashi ba, auren yaya Deen duk ina sane da su, har haihuwar Imran da matar yaya babba ta yi, duk ina sane, kafin haihuwar Imran ma korin Aunty Aisha da babban yaya ya yi daga gidansa duk ina sane, shi ne na je na ɗauketa, amma fa kafin na yi rayuwa da Aunty Aisha, na ruke Maik tukun nan, lokacin da naje gida dan tabbatar da mutuwar daddy, a lokacin na samu labarin cewa har da mum suka rasu, maganganun mutane ya kasu kashi biyu ne a lokacin, wasu sun ce ban da ita, wasu kuma sun ce har da ita, to ni dai da ban ganta a gidan ba, sai na ɗauko Maik muka dawo da shi gidana, ya yi rayuwa mai ɗan tsawo a wajena, ina ganin su baban yaya suka rinƙa nemansa, amma naki bayyana masu yana wajena, sai da ya ɗauki tsawon lokaci a wajena, sai tafiya ta kamani zuwa Dubai a kan harkar kasuwancina, bani da zaɓi dole na mayar da Maik gidan yaya babba, haka na shirya na ɗauke shi zuwa gidan, na bawa mai gadi shi, sannan na juya na koma, sam ban so rabuwa da Maik ba, na so na rene shi ne ya taso a hannuna, amma ba hali, da na tafi Dubai na ɗauki tsawon shekaru uku a can, a lokacin ne kuma Allah ya kara bunkasa mani arzikina, komai na taɓa kuɗi, har mamaki nake yi, abubuwa suka kara haɓaka, lokacin da Aunty Aisha ta baro gidan yaya babba ta suma a kan hanya, a lokacin ina Dubai, amma na sami labari ta hanyar security dana sanya yana yi mani gadin gidajen ƴan uwan nawa, dan ya gaya mani me yake faruwa, ina daga can nasa aka kai mani ita asibiti, satin ta ɗaya a asibiti na diro Nigeria, ni na cigaba da kula da ita na tsawon shekara ɗaya, bayan ta sami lafiya, sai na ɗauketa muka je har Washington, dan ta bani labarin abin da ya faru da ita, da muka je bamu sami waɗan da muke nema ba, sai na wuce da ita Dubai, a nan muka cigaba da rayuwarmu, ina sane da duk irin nemana da ƴan uwana suke yi, amma ko kaɗan ban ji cewa zan koma cikinsu ba, mun yi rayuwa mai tsawo a Dubai da Aunty Aisha, rabon auren Maryam ya dawo damu Nigeria, kafin mu dawo na sa an shifiɗa mana shinfiɗaɗɗen gini na alfarma, gini na gani na faɗa, muna dawowa na cewa Aunty Aisha zan je Niger in duba yanayin yanda ƙasar take, dan ina son buɗe company a can, a lokacin ina da wani aboki ɗan Niger ɗin, shi ne yake yawan bani labarin kasarsu, a makaranta muka haɗu, shi ne nace to bari naje ziyara na duba mu gani, ashe rabon auren Maryam ne ya kai ni, a hanyata muka haɗu da Shitu wanda ya kasance ɗan uwane ga ita Maryam ɗin, in takaice maku labari da na je ƙasar Niger, na so mu sauka a hotel, amma abokina ya nuna baya son hakan, ya nuna ba zai ji daɗi ba idan har ban sauka a gidansu ba, dan yana bawa ƴan uwansa labarina, iyayensa duk suna son ganina, yin hakan yasa na ce mashi to shikenan mu je gidan nasu, haka kuwa aka yi, lokacin kankanin na yi sabo da Shitu, muka zama kamar ƴan uwa, yana da kirki sosai, har muka karɓi number juna. Saukata a gidansu abokina naga karamci, suna da karamci sosai, mutanen Niger adilan mutane ne masu kirki sosai da sosai, suna da karamci over, haka suka karramani, suka mutuntani, a tare da abokina muka kwana, washegari da safe, bayan na yi wanka na shirya zamu je yawace gari da motar abokin nawa, muka shiga wajen mahaifiyarsa dan mu gaisheta, a nan na fara ganin Maryam, tana zaune kusa da mahaifiyar abokin nawa, da alama aikota aka yi, tana sanye da hijabinta har kasa, duk da cewa hijabin da kuma kayan jikinta duk a koɗe suke, amma ta yi shiga ta mutunci wanda duk wani ɗa namiji mai hankali zai sota, kuma zai yi sha'awar ta zama matarsa. Muna shigowa ta ɗaga mana gaisuwa cikin sanyin murya tana sunkuyar da kai kasa, kyakkyawar gaske ce sosai da sosai, sai dai alama akwai wahala sosai a tattare da ita, dan duk fatar jikinta a koɗe. A gaban idanunmu maman abokina ta bata sakon da ta zo karɓa a leda, ta tashi ta tafi abinta, mu kuma muka gaisa da maman abokin nawa, sannan ta zuba mana adduo'i tare da fatan alkhairi, daga nan muka fito, muna shiga cikin mota abokina ya kai mani duka yana faɗin malam ya naga sai kallon Maryam kake yi? Dariya na yi ina cewa kai kuma sarkin sa ido ba, dan Allah ƴar wacece? Ko kanwarka ce?. Bai yi kasa a gwiwa ba wajen gaya mani cewa ita marainiya ce, kuma ga in da take rayuwa, ya bani labarin komai da irin wahalar da take sha a hannun ƴan uwan mahaifiyarta da sauransu, na ji babu daɗi sosai, kuma na tausaya mata sosai, dan haka sai nace to muje gidansu, ko da muka je sai muka tarar da Shitu a gidan, shi ma ashe ya je dubata ne, ɗan uwanta ne ta gefen mahaifinta daga Nigeria kenan, na ji daɗi sosai na ganinsa, a lokacin yarinya ce sosai, dan ba zata wuci irin 13 to 14 years ba, hakan ce ta bani kwarin gwiwar naji cewa ina son na aureta, dan na tsamota daga wahalar da take ciki, kuma bata wuce shiga school ba, in takaice maku labari zuwana Niger dai shi ne silar aurena da Maryam, Aunty Aisha da kuma abokan arziki sune suka tsaya mani akan komai, da yake a lokacin ba wani ɗaukar Maryam ɗin da muhimmanci ƴan uwan nata suka yi ba, saboda rashin iyayenta, sai suka bani aurenta ba tare da bincike ko bin diddigin wanene ni ba, na auri Maryam, bayan ganina da ita na farko da wata biyar dai'dai, sannan na dawo da ita Nigeria, na kuma kaita har garin Maiduguri wajen ƴan uwan mahaifinta, dan naji labarin komai a kansa daga bakin Shitu, daga nan muka sake komawa Dubai da zama, ban yi zaman Nigeria sosai ba, mun yi rayuwa cikin tsananin farinciki, na sanya Maryam a makaranta, ta yi karatu sosai, dan tana da kaifin kwakwalwa da basira, kuma nima ina kara koya mata karatu sosai, Aunty Aisha ma tana kara mata wani duk da cewa ita ma tana zuwa ismaliya sosai a lokacin, aurena da Maryam ya ɗauki tsawon lokaci kafin mu sami haihuwa, cikin mu na farko yaron bai zo da rai ba, mun ji tsananin rashin daɗi, amma mun fawwalawa Allah komai, haka muka cigaba da rayuwar farinciki, cikinmu na biyu yana da wata bakwai ta haife shi, shima ɗa namiji ne, ya zo da rai, an saka shi a kwalba kasancewar bakwaini ne, kwanansa uku a duniya ya koma ga mahaliccinmu, munji babu daɗi, saboda mun ɗauki son duniyar nan mun ɗaura mashi, amma ba yadda zamu yi tun da haka Allah ya ƙaddaro mana, a cikin Maryam na uku ma yana da wata uku cikin ya zube, daga nan na fara shiga damuwa sosai a kan hakan, na ce sai dai muje asibiti, ko da muka je ma babu wata matsala, kawai dai Allah ne bai kawo mai tsayuwa ba, haka Aunty Aisha ta rinƙa kwantar mani da hankali, da har na fara tunanin shikenan ni ba zan sami magaji ba, a lokacin fa Hassan na ma ya yi aure, ɗansa Feroz har yana gudu ko'ina, ya girma, ga su Imran ɗin yaya babba duk sun girma, amma ni kuma shiru, abin kullum da shi nake kwana da shi nake tashi, ita ma Maryam tana cikin tsananin damuwa a kan hakan, sai dai bata bari na gane ba, kullum sai ta yi kuka, bata san ina sane da komai ba, damuwar da take shiga ne ma yake kara tsananta mani tawa damuwar, haka na cigaba da ƙoƙarin faranta mata rai ko dan maraicinta, in takaice maku sai da muka sami ciki har sau biyar dukka basu zama, wasu ta haifesu da rai su koma, wasu babu rai, a ciki na shidda ne muka haifi ƴan biyu dukka maza, kuma dukka Allah ya barɓi abinsa, shi na farkon, wato Hassan ɗin satinsa ɗaya a duniya ya rasu, na biyun kuma sai da ya yi wata biyar a tare da mu, sannan Allah ya karɓi abinsa, ni nasan mumini baya rabuwa da jarabawa ta Ubangiji, amma wlh wannan jarabawa ta ƴaƴa ya yi matuƙar girgiza mu, badan Aunty Aisha da take tare da mu ba, wlh da mun tabbaka babban kuskure, dan har cewa muka yi zamu sami wata mata mu biyata maƙudan kuɗaɗe, sai a sanya mata kwan haihuwata ta haifa mana yara ko uku ne, Aunty Aisha ce ta tsawatar mana sosai a kan hakan, a lokacin dai na bi umarninta ne kawai matsayinta na babba a kai'na, kuma ko ba komai Aunty Aisha ta nuna mana so da kauna nida Hassan fiye da tunanin kowa a lokacin da muke ƙasar Russia, amma banda haka wlh da a lokacin sam ba zan ɗauki maganarta ba, haka dai muka jure, ina ji ina gani dukka ƴan uwana daga mai yara uku sai mai yara biyu, shi babban yaya har matarsa ta haifi Imran, Akil, da kuma Akila, shi kuma yaya Deen, matarsa ta haifi Irfan, Aafia, and Umaisha har ma matar ta bar gidan a lokacin, ta bar Umaisha tana karama, Hassan matarsa ta haifi Feroz tana da cikin na biya, autanmu Maik dana rena da hannuna ma matarsa tana da ciki a lokaci, abin fa ba ƙaramin ɗaga mani hankali ya yi ba, Maryam da kanta ta ce na kara yin wani auren ko zamu sami ƴaƴan, naki yarda da zancenta, saboda bana son nayi mata kishiya, bana son kowa yazo ya takura mata, ina so ne ta yi rayuwar farinciki, ita kaɗai a cikin gidana, saboda mace ce ta gari, macece ƴar albarka, ta bani farincikin da ban taɓa tunani ba, tana da hankali da nutsuwa, ina tausayawa maraicinta, yanzu kuma ga rashin haihuwa, mun binne yara almost 7, amma shiru, a ƴan tsakanin nan muka sake samun ciki, a lokacin cikin matar Maik bai wani girma sosai ba, dan bai wuce 3 months ba, ita ma matar Hassan haka nata cikin bai fi wata uku ba, shiyasa ƴaƴan namu suka kasance shekarunsu ɗaya, sai dai ratan watanni, wato da Jalila, Anaya, da kuma Jehan kenan, sai dai fa ko da muka haifi Jehan ɗin, bamu wani jata a jiki sosai ba, dan muna ganin kamar ita ma mutuwa zata yi, amma da yake uwa da ƴa ba mai shiga tsakani, ita Maryam ta jata a jiki sosai, ni kam baya baya nake yi da ita, dan rasuwar Hussainin namu ya girgizani, na saba da shi sosai, ko ina zanje muna tare, yaro ɗan wata biyar amma ya san yawo, saboda fita da nake yi da shi, lokacin da ya rasu nasha wahala, har firgita nake yi a cikin barci ina kiran sunansa, to shi ne yasa na ki yarda na ja Jehan sosai a jikina, dan kada na sake shan wata wahala, sai da na ga Jehan ta cika shekara guda bata mutu ba, sannan ne na jata a jiki sosai, na fara nuna mata soyayya, mun so Jehan fiye da kanmu, baki ma ba zata iya faɗar adaddin soyayyar ba, haka muka cigaba da bata kulawa tamkar kwai a saman bajajjen faranti, Aunty Aisha ta fi mu nuna kula a kan Jehan, daga karshe ma haka muka hakura muka bar mata Jehan ɗin tana kwana a ɗakinta, dan ta kwace mana ita, shiyasa kuke gani a yanzu sun fi shakuwa, shakuwa ce da suka yi ta tun tile tile, ba ta yanzu bace ba, tun daga kan Jehan ɗin kuma bamu sake samun haihuwa ba har matar Hassan ta haifi Zaira, bayan haihuwar Zaira da wata ɗaya muma muka sami ciki, nan muka fara tattalin kayanmu, har Allah ya sauketa lafiya muka sake samun ƴa mace, a baya duk ƴaƴan da muka binne maza ne, yanzu kuma mata muka samu, ƴarmu ta biyu wato Rimsha, kama take da Maryam sak, while ita kuma Jehan kama take yi da ni sak, haka muka ɗauki son duniya muka ɗaurawa ƴaƴan nan namu guda biyu, muka cigaba da basu kulawa na wuce misali, sai dai sun fi shakuwa da Aunty Aisha, dan sun fi zama a wajenta, ni kuma ina kyale mata su ne dan su ɗebe mata kewar TRIPLETS nata da ta rasa, kullum maganar Aunty Aisha ɗaya idan tana yi wa su Jehan wasa, shi ne idan ta ga TRIPLETS nata, to sune mazajensu Jehan ba makawa, kuma zata yi ta addu'a a kan hakan, in dai tana raye ta gane ƴaƴan nata, to wlh ko sun yi aure sai sun auri su Jehan, kullum shi ne zancenta, a hankali hankali har ta zo ta fara dai'na zancen TRIPLETS ɗin nata, kamar wasa duk zancen ya bar bakinta baiwar Allah, haka muka rayu cikin farinciki, kullum muna waya da Shitu, shi ma ya jima da yin aure, suna da ƴarsu ɗaya Adiva, sa'ar Jehan ce yarinyar. Bamu tashi dawowa Nigeria ba har sai da su Jehan suka yi wayo, sai da Jehan ta kai primary 4 a school, wannan dalilin yasa sam basu jin Hausa, daga larabci, sai English da kuma yaren mamansu wato shuwa Arab, sai kuma kanuri da take yi masu kaɗan kaɗan, nima time to time ina yi masu fullanci, dan na koya wajen daddyna, sai dai Rimsha ce kawai ta ɗan iya fullanci, ita Jehan ko yaren mummyn nasu ma taki ta koya sosai, ita dai a barta da English, da shi kawai take magana, larabcinma sai taga daman yi, ga kafiyar bala'i, ga zafin rai, akwaita da iya tsare gida sosai, kuma dukka Aunty Aisha take zugata, ni dai bani da ta cewa, idan nayi magana Aunty Aisha ta hau surfa mani masifa, haka na zuba masu idanu, sai da muka dawo Nigeria ne na shiga harkar siyasa, da farko ina tsananin son siyasar, daga baya dana shiga cikinta, naga kazantar dake cikinta, sai naji ba zan iya ba, naso na barta, amma Maryam ta hanani, ta kuma kara mani kwarin gwiwa a kan lalllai na yi siyasa, lallai siyasa tana da bukatar mutun irina, zai tallafawa kasa ba kaɗan ba, ta dai nuna mani alfanonta sosai, na kuma gamsu, dan haka sai na sake zage dantse sosai, ina da abokan hamayya sosai, amma ban taɓa mayar da hankali nabi ta kansu ba, kawai harkar gabana nake yi, a lokacin ne Allah ya haɗani da Abubakar Salahuddeen, muka fara takun saka da shi, in takaice maku labari shi ne ya zama sanadiyar rugujewar farincikina da ni da familyna bakiɗaya, saboda na kama shi yana dillanci kayan maye da kuma mata izuwa kasashen waje, ya yi ya yi na rufa mashi asiri, dan takarar da zai tsaya, naki yarda na rufa mashi asiri, sai ya bukaci da na shigo cikin tafiyar tasu, nan ma naki yarda, to shi ne ya nemi salwantar mani da rayuwata da ta familyna, a lokacin da na shiga siyasa sunana ya fito, kamar hauka haka su yaya Deen suka yi ta nemana, har gida sun zo wajena, amma sai nece masu ni ban sansu ba, bani da wata alaƙa da su, dan haka su kama kansu, shi ma Hassan yazo har gida, naki yarda da shi, kuma sarai na san komai ma da yake tafiya a rayuwarsu, dan ina aika masu da makudan kuɗaɗe tun ina Dubai, har na dawo Nigeria ban dai'na idan suna cikin matsala ta kuɗi na taimaka masu ba, wannan shi ne labarina da abin da ya faru da ni a takaice kenan, kun san komai ba zai faɗu lokaci guda ba, amma ku ruke wannan ɗin kawai". Ya kai karshen maganar yana mai gyarawa ya kwanta, tare kuma da tada kansa da laps na Brr Naurat. Ajiyar zuciya kowa dake cikin wajen suka sauke, Brr Naurat ce ta ce "Sannu ɗana, kasha gwagwarmaya kai ma". Tana magana tana shafa kansa. Abbi ne ya kai mashi duka yana faɗin "Kana ji muna nemanka a lokacin, amma sai ka sheremu ko?". Jinjina masu kai ya yi alamar e ɗin ya share. Nan fa kowa ya fara tofa albarkacin bakinsa, shiru ya yi masu kamar baya wajen. Haka suka kasance cikin tsantsar farinciki da kuma yi wa ƴaƴansu dake Daular Mutuwa addu'a. After some minutes gwaggo ce ta ce "Ni kam wai Aseef bai dawo daga shopping ɗin da ya ce mani zai je bane?". Daddyn jelly ne ya amsa mata da "Gaskiya fa kamar bai dawo ba, wata kila ya wuce wani wajen ne". Da mamaki Abban Imran ya ce "Kai ba Saif ya ce kada kowa ya fita daga cikin gidan nan ba? Ya za'ayi A'isha ki barshi ya fita? Suma sojojin ya za'ayi su karya maganar Saif? Ko da yake sun fi kusa da shi, kila ya ce masu idan Aseef zai fita su bashi hanya ne" "Hmmm yaya babba kenan, Aseef ɗan rigimar ne za'a hana fita, ai idan suka hana shi fita,to wlh gidan nan babu zaman lafiya, ni kai'na idan na ce ba zai je ko'ina ba, to babu ni babu zaman lafiya, shi ne yasa kawai na ce mashi sai ya dawo". Cewar gwaggo. "Gaskiya kam Aseef ɗan rigima ne wlh". Cewar Abbi. Abba ne ya tari nunfashinsu da cewa "Ni ne nan zan baku labarin rigimarsa, yaron da ya je ya tasani a gaba ya rinƙa kuka lokacin da na ce ba zan bashi auren AKILA ba, Irfan ya riga shi, hmmmm ni zan gaya maku rigimar Aseef wlh". Murmushi gwaggon ta yi, ita kaɗai tasan me take tunawa take sakin wannan murmushi. Haka dai suka cigaba da hirarsu na tsawon mintocin kafin nan a kira sallar azzahar kowa ya watse, dan suje su yi sallah. After some days. Abubuwa da yawa sun faru a cikin kwanakin nan da suka shuɗe, ciki harda neman Aseef da su gwaggo suka rinƙa yi, amma shiru babu shi babu labarinsa, hakan yasa hankulansu ya kara mummunar tashi, nan fa suka dukufa wajen addu'a babu kama hannun yaro, suma fa sauran sojojin da suke a bakin gate, hankulansu ya yi mummunar tashi ba kaɗan ba, dan idan har Aseef baya gidan, to ba shakka sun shiga uku da Lion idan ya dawo, dan sun karya mashi doka na barin wani daga cikin family ya fita, su kuma wlh sam basu ga fitar Aseef ɗin ba, ba su san time da ya fita ba, Allah ya gani, bayin Allan sun shiga tsananin damuwa na wuce misali. Daular Mutuwa. Sun shafe kwanaki a cikinta suna neman ƴan uwansu, amma san basu gansu ba, duk wani part da zasu faɗa a cikin Daular, sai su ga kamar sun bar duniya, ga shi su da suke rayenma sun raba hanya, Aseef ya yi gabas, Areef ya yi yamma, sun sha matukar bakar wahala, har shi kansa Aseef ɗin ya wahala, kuma bai gane ina Fadar Queen ɗin take ba. Areef ne ke a kan wata hanya yana tafiya, sai wuce ɗakuna da abubuwa na ban tsoro da tsafe tsafe yake yi, tunanin ina Lion yake kawai yake yi, wani irin azababben yunwa yake ji, akwai snacks and drinks a cikin jakar dake goye a bayansa, amma ya kasa saukewa ya samu waje ya nutsu ya ci ya ƙoshi, shi burinsa kawai yaga ƴan uwansa. Duk wannan wahala da yake sha, bai dai'na ambato sunan Allah ba, hakan yasa Queen ta kasa ganin wai shin a ina ma yake, ya ɓace daga idanun tsafinta, sai nemansu take yi shi da Aseef, amma ko alamar mai kama da su bata gani ba. Ya zo dai'dai wata mararraba, hanyoyi ne suka rabu gida biyu, ɗaya ta yi gabas ɗaya ta yi yamma. A dai'dai wajen ya tsaya yana tunane tunane ya zai yi a yanzu? Shi dai ko mutuwa zai yi wlh sai dai ya mutu, amma ba zai taɓa yarda ya bar cikin Daular nan ba tare da ƴan uwansa ba. Idan ma ya ce zai bar cikin Daular ta ina ne hanyar fita?. A hankali ya fara jin motsi ta hanyar dake kallon yamma, shiru ya surara yana son tantance motsin menene?. Jin kamar sautin numfashin mutane ne yasa ya nufi hanyar babu tsoro ko miskala zarratin a tattare da shi. Ko da ya isa wajen sai ganin su Mark ya yi gabaɗayansu da sauran sojojin a ɗaure da sarkoki masu karfin gaske, sai dai babu Lion a cikinsu. Hamdala ya yi ga Allah, ko ba komai ya ga wasu daga cikin tawagarsu, saura su Ayla da kuma Lion, sai Heartbeat nasu, wato Aseef shalele ɗan rigima. Ba tare da ɓata lokaci ba, cikin kwarin gwiwa ya fara ƙoƙarin buɗe kofar karfen, a rufe kofar take ruf da matakan tsaron Queen. Sai kuma me? Yana ƙoƙarin sakawa kofar karfi ya buɗe ta, kamar daga sama ya ji wani uban jijjiga da ginin ya fara yi, kafin nan ya yi wata yunkuri ginin ta rufta, kofar ɗakin ya toshe. Hakika a wannan karon ba ƙaramar tashin hankali ya shiga ba, ya shiga ruɗu ta yadda kwata kwata baya iya gane ina ya dosa. Da sauri ya bar wajen saboda wani irin turnukin kura da ya taso, dan ma Allah yasa kofofin ɗakunan irin na karafunan nan ne masu kama da prison, so kofar ta tare ginin bai ruguzo a kansa ba. Da sauri ya fito daga hanyar idanuwansa sun yi jajir tamkar wuta, sai wani huci yake yi, Hakika ya ji takaicin mutuwarsu Mark, har wani pat, pat, pat zuciyarsa take harba mashi, wani irin tukukin bakin ciki ne ya tokare mashi maƙoshi, da kyar yake haɗiyar wahalallen yawu, kansa sara mashi take yi tamkar zata fashi, har wani irin jiri ya fara gani. Yana fitowa daga wannan hanya ya faɗa cikin wata tapkekiyar waje, wannan waje kuma ba ko'ina bane face wajen da su Rimsha suka taɓa zama, already dama kunsan ya yanayin wajen yake, ga faɗi da girma, ga kuma ɗakuna da yawa a cikinsu. Zubawa wajen idanu ya yi yana kallon yanda yake, kamar daga sama ya ga dirowan mutane a gabansa. Jiga jigan matsafane masu ji da karfi, dama Queen ta turosu ne su nemo shi, tasbihi da yake yi ne yasa basu iya ganinsa ba, to a yanzu kuma ya dai'na ambaton Allah, saboda bala'in da ya shiga na ganin abin da ya faru da su Mark, a lokacin ne ma ya kamata ya ambaci sunan Allah da kyau, sai kuma tashin hankali ta hana shi, ya shiga ruɗu na ganin yanda wannan gini ta ruguzo. Ganin mutanen yasa ya kara shiga tashin hankali, dama already bai dawo dai'dai ba. Kafin ya yi wani yunkuri waɗan nan jiga jigan matsafa, ɗaya daga cikinsu ya sanya hannu ya sunkuce shi sama, wurgi ya yi da shi can gefe, ta fiya ya yi zai bugu da jikin wannan gunki na karfe mai kifiyoyin tsafi a jikinsa. Tamkar wani walkiya haka Aseef ya bayyana a wajen ya tare shi, a tare suka faɗi kasa ba tare da sun isa ga wannan gunki ba. Ash suka furta a tare. Shi Aseef da Areef ya faɗo a kansa ma yana a cikin hayyacinsa sosai, shi kuma Areef ɗin saboda already yana cikin ruɗani, sai hakan ta kara gusar mashi da hankalinsa daga jikinsa, hakan yasa ya kasa koda motsawa. Kwantar da shi a gefe Aseef ɗin ya yi tare da mikewa tsaye, a hankali ya ɗago da dara daran brown eyes nasa izuwa kan waɗan nan matsafa, sun kasance su biyarne cif, jibga jibga da su madaka karti. Kallon up and down ya yi masu kafin ya mai do da kallonsa a kan Areef dake motsi yana ƙoƙarin dawowa dai'dai. Wani irin taunan hakwara waɗan nan matsafan suka fara yi, tare kuma da wani lankwashe kasusuwan jikkunansu, tamkar wasu macizai. Shiru Aseef ɗin ya zuba masu idanu yana kallonsu, har suka gama duk abin da za su yi, sannan suka tunkare shi da nufin su yi kutsi kutsi da su, su cinyesu ɗanye. Dai'dai lokacin shi ma Areef ya mike tsaye, ya dawo cikin hayyacinsa bawan Allah, ga uban yunwa da yake ji. Wucewa gaba Aseef ɗin ya yi, ya tari waɗan nan matsafa gadan gadan suka fara faɗa babu kama hannun yaro. Areef ya so ya taimaka mashi, sai dai kuma faɗar tafi karfinsa, ta wuce tunaninsa, daga karshe sai ya rabu da su suna faɗar, shi kuma ya fara duba ɗakunan da suke wajen, a cikin zuciyarsa yana ta mamaki tare da tunanin a ina Aseef ya samu wannan karfi har haka, sai dai kuma a baki ya kasa furta hakan, ya kasa iya tambayar Aseef ɗin komai, sai dai kawai ya bishi da idanu, komai zai yi ba zai iya tambayarsa menene yasa ya yi ba....... E lallai da akwai cakwakiyar gaske kenan. Binciken ɗaku nan da ya fara yi ne, a nan ne ya cikaro da Dr Salman da kuma Ayla a ɗaki ɗaya suna zauna, sun buga uban tagumi, dama idan baku manta ba, Ayla mutuniyar Dr Salman ce sosai, sun saba tun zamanta a Daular a shekarun baya, dan haka ko da ta sake dawowa a yanzu, sai kawai ta koma ɗakinsa ma da zama tun da bata da abokan hira. Bayin Allan, da kallo ɗaya zaka yi masu kasan suna cikin tsananin firgici da tashin hankali, sun wahala over, duk sun yi wani tsuru tsuru da su. Da kallo ɗaya ya yi wa Dr Salman duk da tsufan da ya yi, ya gane cewa shi ne kakansu, dan babu in da Abbi ya baro shi a kamanni, akwai kaman ƴaƴansa a tattare da fuskarsa. Bai ɓata lokacin ba ya faɗa cikin ɗakin tare da yi masu bayani a tsaitsaye na cewa sun zo fitar da su ne, sannan ya ce su je ba ɓata lokaci, suma basu ɓata lokaci ba wajen mikewa su bi bayansa, saboda Allah ya gani sun gaji da wannan bakar gida ta bakaken azzaluman. Kafin su fito Aseef ya kashe waɗan nan mutane dukka, yana tsaye a harabar wajen yana aikin gyara agogon hannunsa da suka kwance mashi a wajen faɗa, ko a jikinsa, bai sha wahalar faɗa da su ba sam sam. Nunawa su Dr Salman Aseef ɗin Areef ya yi yana faɗa masu su je wajensa, shi kuma bari ya nemo sauran jama'ar da suka zo ɗauka. Ba musu suka amsa da to, suka wuce izuwa wajen Aseef ɗin, shi kuma Areef ya sake komawa yana leƙa ɗakunan. Suna zuwa Aseef ya rungumi Dr Salman yana faɗin "Welcome ɗan tsoho". Duk da cewa Dr Salman bai san su waye su ba a gare shi, bai hana ya rungumi Aseef ɗin ba shi ma. Yana ƙoƙarin yiwa Aseef ɗin magana ne suka jiyo muryar Areef daga ɗaya daga cikin ɗakunan dake wajen yana faɗin "Aseef come and see something". Kallon Dr Salman Aseef ɗin ya yi. "Ɗan tsoho ku jirani a nan kada ku motsa ina zuwa". Ya kai karshen maganar tare da sakin Dr Salman ɗin, da sauri ya nufi in da suka jiyo muryar Areef ɗin. Yana zuwa ya faɗa cikin ɗakin, sai kallonsa Dr Salman yake yi har ya kurewa ganinsa, ɗan tsoho yaga rayuwa iya ganin idanunsa, baki ma ba zai iya faɗar irin abin da Dr Salman ya fuskanta na kalubalen rayuwa ba, sai dai muce Allah ya kuɓutar da su. Aseef yana faɗawa cikin wannan ɗaki me zai gani? Heartbeat nasa ne a ɗaure cikin wasu sarkoki. Wani irin sanyi ya ji a ransa, da sauri ya karisa gareta, Areef yana ta ƙoƙarin yanda zai yi ya kwance waɗan nan sarkokin, shi kuwa Aseef ɗin yana zuwa ya rungumota yana faɗin ya yi missing nata over. Ita kuwa tana ganinsa ta sa mashi kuka, yi take yi babu kama hannu yaro, haka ya hau rarrashi, sai gaya mashi abin da ta gani da abin da suka yi mata take yi, baya sauraronta ma, shi dai burinsa kawai ta yi shiru, amma ta kiyi sam sam, shi kuma Areef yana ta ƙoƙarin yanke waɗan nan sarkoki. Can kuma ko me ya tuna, sai ya fara karantawa sarkokin karatun Alqur'ani mai girma, nan take suka fara kwancewa suna zubawa kasa, kan kace me sarkokin duk sun zama gari, hakan kuma tasa ɗakin ya yi wani irin haske, sannan kuma ya fara wani irin rugugi tare da surutai da wasu irin muryoyi marasa daɗin ji. Cikin hanzari Areef ɗin ya ce "Kai Aseef da matsala fa a dakin nan, ku wuce da wuri mu fita". Sam Aseef ɗin bai kula shi ba, ya rungume Heartbeat tasa suna kashe juna da shagwaɓa, su gabaɗaya ma sun mance a ina suke, har lokacin sai kuka take zuba mashi, shi ma ya biye mata suna wannan aiki dai da suka saba, wanda already kun san halinsu idan suka haɗu, shagwaɓa babu kama hannun yaro. "Aseef wai ba zaka barta sai mun fita daga ɗakin ba?". Ko ajikinsa, babu tsoro ko ɗigo a tattare da shi, cikin kwanciyar hankali ya ce "Kai Areef kasan tun yaushe ban yi kissing nata bane? Kai ba zaka bar mutun ya sakata ya wala ba, Allah ba zanzo ba sai na gama kissing nata har na ƙoshi". Girgiza kai Areef ɗin ya yi tare da nufarsu, Aseef sai ya sa an yi masu kisan walaƙanci sannan hankalinsa zai kwanta, ban da iskanci ma irin tasa, ana ta rai waye kuma yake ta wani kiss? Ya bari su rayu mana, daga baya ayi komai, yana ganin yanda komai yake ƙoƙarin lalace masu, ga shi har yanzu basu ma san ina Lion yake ba tukunna. Yana zuwa ya ja hannun Akilar yana faɗin "Idan kika biyewa Aseef duk sai mun mutu kamar dabbobi a nan, ke daɗi masoyi ko?". Janyota Aseef ɗin ya sake yi yana faɗin "Wai kai ka bari mana, ka sani ne ko kiss na karshe zan yi mata, idan bamu kai ga fita ba aka kashe mu kamar yanda aka kashe sauran fa? Ni ka barni na yi abinda zan yi Hai........" Bai rufe baki ba suka fara jin jijjigar ginin ɗakin, alamar suma ruguje ɗakin ake son yi da su a ciki, tamkar yanda aka yi wa su Mark kenan. Ihu Aseef ɗin ya kurma tare da shagwaɓe murya yana faɗin "Wayyo Areef mun shiga uku, shikenan zamu mutu ba tare da Heartbeat ta haifa mani baby's ba, wayyo ni Aseef naga ta kai'na". Wani irin harara Areef ɗin ya wurga mashi. Aseef ɗin nan mugun ɗan rainin wayo ne wlh, ji yanda yake kukan shagwaɓa kamar ba yanzu ya gama jibgan karti maza a waje ba!. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E15 Date: 25/4/2024 Wani irin harara Areef ɗin ya wurga mashi. Aseef ɗin nan mugun ɗan rainin wayo ne wlh, ji yanda yake kukan shagwaɓa kamar ba yanzu ya gama jibgan karti maza a waje ba!. "Areef yanzu me abin yi, ni fa wlh bana son na mutu". Ko kallon arziki Areef ɗin bai yi mashi ba, bare ya sa ran zai amsa mashi, hannun Akilar kawai ya ja suka nufi kofar fita da gudun gaske, da ya ga ba zata iya gudun bama, sai ya ɗauketa cak, shi kuma Aseef ɗin yana tsaye yana zuba kukan shagwaɓa. Bayan Areef ya fita da Akila sun tsaya a waje ne, sai ya sauketa tare da dafa kansa yana faɗin "Dama na sani ai, Aseef our heartbeat kuma our headache, wato da gaske yana tsaye a cikin ɗakin kenan? Ya zan yi dole naje na lallaɓa shi ya fito, Heartbeat ki jirani a nan". Ya kai karshen maganar tare da juyawa da sauri ya koma cikin ɗakin. Gabaɗaya bangon ɗakin sai ruguzowa yake yi, amma Aseef yana tsaye yana zuba kukan shagwaɓa, shi dole sai Areef ya zo ya rike hannunsa shi ma, a kan me zai kama hannun Akila kawai, wato yanzu sun fi son Akila a kan shi kenan? Shi ne fushin da yake yi. Da sauri Areef ɗin ya dawo cikin ɗakin, hannunsa ya zo ya riko yana faɗin "Shikenan muje to". Bubbuga kafa ya fara yi yana faɗin "Yanzu ka dai'na sona, sai da ka fitar da Heartbeat shi ne ni zaka ce nazo daga baya, Allah ba zan yarda ba, ni babu in da zanje, kawai ka barni na mutu tun da kun dai'na sona........". Bai kai karshen maganar ba bangon ɓangaren hagu ta ruguzo. A dubu ɗari ya rungumi Areef ɗin yana faɗin "Wayyo daddyna, wayyo my Lion, na shiga uku zamu mutu, Areef ka ceceni bana son mutuwa". Gabaɗaya kan Areef ya kulle, wai shin Aseef ɗin nan wani irin mutun ne? Yanzu ka ganshi cikakken jarumi, anjuma kuma ya koma shagwaɓaɓɓe na kin karawa, ji yanda yake kukan baya son ya mutu, ya zo su fita kuma ya ce bai san wannan ba, shi ya yi fushi saboda an fara fitar da AKILA, yanzu kenan an daina son shi. Shi ma Areef ɗin rungume shi ya yi yana rarrashinsa a kan ya yi hakuri su tafi to. Bai kai ga rufe baki ba kamar daga sama ya ji Aseef ɗin ya sunkuce shi, ya ɗaga shi sama sun yi waje a guje. Suna fita ɗakin ya rufta mai gabaɗaya. Bai sauke ɗan uwan nasa a ko'ina ba sai a kusa da Akila dake tsaye tana faman sharar kwallah. Mamaki ya hana Areef ɗin yin wani kataɓus, yau kuma ko a ina Aseef ya samo karfin ɗaukarsa kamar ɗan baby kuma oho? Abin mamaki baya karewa. Shi kuwa Aseef ɗin yana sauke Areef ɗin sai ya faɗa jikinsa yana mai cigaba da kukan shagwaɓarsa kamar ba shi ne yanzun nan ya gwada wata zazzafar jarumta ba. Ture shi Areef ɗin ya yi ya nufi wajen su Dr Salman yana faɗin "Heartbeat dama kayanki ne, kin fi kowa sanin halinsa a yanzu, sai ku fama, ki rarrashe shi, ni bari na nemo maku hanyar fita daga wannan bakin kazamin gidan, ku fita, idan ya so zamu biyoku daga baya". Ya kai karshen maganar dai'dai lokacin da ya karisa wajen Dr Salman. Matsowa Akilar ta yi ta faɗa jikin Aseef ɗin tana mai cigaba da zuba mashi kuka babu kakkautawa. Rungumeta sosai ya yi tare da dai'na nashi kukan ya hau rarrashinta, ta tsorata sosai baiwar Allah, ta sha wahala, duk ta fita a hayyacinta, a haka ma fa dan tana matsayin jika ga Queen ɗin kenan, ba dan haka ba, da sai yaya? Taga kaɗan daga cikin abubuwan da Rimsha ta gani, a gaban idanunta aka fasa cikin wasu mutane biyu aka ɗebi wasu abubuwa, a gaban idanunta aka shanya gawa kamar busasshen kifi, a gaban idanunta aka yi abubuwa da dama, ita ma dan Allah yasa tana da tsawon kwana ne, da ita ce a kan layi yanzu, ba dan zuwansu Aseef ba, to da ba makawa ba zata kai gobe ba. Areef kuwa magana ya fara yi da Dr Salman a kan ko ya san wani abin dangane da gidan nan. Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Na shafe shakaru sama da talatin da uku a nan, amma har yau ba zan iya ce maka ga takamaimen abin da suke yi ba bayan kashe mutane da ɗibar jini da wasu sassa na jikin ɗan adam, sannan har yau ban taɓa ganin gini na farko ko kuma na karshe na wannan gida ba, sai dai kuma, na san da akwai wata hanya da Duna ya taɓa gaya mani, ya ce ko bayan sun ɗauke shi, idan zan iya na bi wannan hanya zan tsira daga wannan gida, sai dai kuma hanyar tana da haɗari, sannan tana da nisa sosai, kuma a karshen hanyar da kawai kofa da zata fitar da kai waje gabaɗaya, bayan hanyar da su Rimsha suka fita, wannan ita ce hanya ta biyu ta sirri a cikin gidan, sannan ya ce mani idan har ina tafiya a kan wannan hanya, to kada na juya baya, komai zan ji na tafi kawai, abin da yasa ban fita ba, saboda komai ya kare mani, ina jin ko nafita bani da kowa a duniya, kuma ya ce hanyar tana da tsawo sosai, so ba zan iya doguwar tafiya ba, ni kaɗai ne kuma, dan a lokacin, sun ɗauki mai taimaka mani ɗin, wato Mustapha, shi ne mai taimakona dama, to sun rabani da shi, sun mayar da shi cikinsu, suna can suna ƙoƙarin juyar da shi izuwa nasu, a halin yanzu ma ina ga sun mayar da shi ɗaya daga cikinsu ɗin, wannan dalili yasa na ce gara na cigaba da zama a nan ɗin kawai har ranar da rai zata yi halinta". Shiru Areef ɗin ya yi yana jinjina wannan al'amari na Dr Salman, abin gwanin ban tausayi, shekara ɗai ɗai har talatin da uku a cikin wannan bakin azzalumin gidan? Gaskiya Queen ta azabar da bawan Allah nan, ko da ace iya ajiye shi kawai ta yi, bata yi mashi komai ba, wlh masifar da yake gani wanda suke aikatawa kawai ya isa ya kashe shi idan da kwanansa ta kare, Allah sarki, da Allah ya ƙaddara kwanansa na gaba, shi ne har ya kawo iyanzu duk da irin masifu da yake gani, Allah ne kawai zai bi masu hakkinsu, dan kome aka yi wa Queen a yanzu, wlh ba'a biya ko mutun ɗaya abin da ta yi mashi ba, yanzu a kalla ba'a akasaraba wannan Daular Mutuwar ta haura shekaru hamsin da kafata, sai Allah ne kaɗai zai iya kiyaste rayukan da aka salwantar a cikinta, ya ilahi ya lillahi. Rugujewar sauran ɗakunan dake gefe da gefensu ne ya dawo da Areef ɗin daga duniyar tunanin da ya afka, da mamaki ya ɗago kai yana bin ɗakunan da kallo, sai rugujewa suke yi tamkar waɗan da ake jijjigewa. Anya lafiya kuwa? Areef ɗin ya tambayi kansa. Aseef kuwa kara kankame Akila dake kankame da shi gam ya yi, saboda tsoro, ta tsorata ne da ganin yanda gine ginen suke jijjigowa da kansu, sai ruguzowa suke yi, tamkar katafila ce take watsi da su. "Aseef let's go, saboda ina ganin gabaɗaya ruguje arean nan ake son yi, so tsayawarmu a nan babban haɗari ne, ka kawo Heartbeat ta tafi da su baba ta hanyar da ya gaya mani yanzu, zamu cin masu a hanya idan mun gane a in da Lion yake". Cewar Areef kenan. Kankameta ya kara yi yana faɗin "No Areef su baba ɗin su je kawai, ita Heartbeat tana nan tare da ni". "Aseef ba da wasa nake yi ba, kada ka yi ka salwantarwa da yarinyar nan rayuwa, ka barta ta bisu". "Nima ai Areef bada wasa nake yi ba, babu in da zata je, muna tare da ita". Dr Salman ne ya sa baki ta hanyar cewa "Jikana da ka bari mun yi abin da ɗan uwanka ya ce, dan wannan gida ya wuci tunaninka". "Baba ni fa ba zan rabu da Heartbeat ba, ai dama ta ce zata soni komai wuya komai daɗi, kuma idan ma aka bata zaɓi a kan mutuwa, to zata zaɓi mu mutu a tare, dan haka kunga ita already a shirye take da ta mutu a tare da ni, please kada ku dame mu, ko ba haka ba Heartbeat?". Tana daga kwance a saman kirjinsa ta amsa mashi da cewa "Haka ne, a tare zamu mutu". Girgiza kai kawai Areef ya yi, waɗan nan sun yi nisa, sam ba zasu ji kira ba, idan ka biyewa Aseef sai ya sanyaka hawan ruwa ba na jini ba. Tsananin jijjigar da gine ginen wajen suke yi ne yasa suka dawo cikin hayyacinsu, da sauri Aseef ɗin ya riko hannunta tare da raba jikinsu, cikin hanzari ya nufi su Dr Salman ɗin yana faɗin "Wayyo Areef menake ji da gani haka? Kada fa waɗan nan gine gine dukka su faɗo mana a kanmu, ya kamata mu gudu, dan ni dai gaskiya ban shirya mutuwa a yanzu ba, sai na sami magaji tukun nan........" Bai gama rufe baki ba gine ginen suka fara ruguzowa tamkar waɗan da karapila take jijjigewa. Cikin hanzari da zafin nama suka yi maza suka fara ƙoƙarin barin wajen. Dr Salman ne ya nuna masu hanya, a in da suka bi ta wata kofa dake ta yamma. Suna tafiya da sauri sauri, gine ginen ɗakunan bayansu na rugujewa kamar ba lafiya ba. Ganin Ayla zata basu matsala ne yasa Areef ya sauke jakar bayansa, a in da ya dawo da jakar ta gaba, sannan ya goya Aylar a bayansa, dan ba karya ta galabaita iya galabaita, ta sha bakar wahala, da kyar baiwar Allah take iya jan kafafunta, hakan kuma zai sanya har gine ginen su ruguzo a kansu ba tare da sun fita daga wajen ba, shi ne yasa Areef ɗin ya goyata, shi ma Aseef goya Akila a bayansa ya yi. Sun yi tafiya mai nisa kafin su cikaro da wani ɗaki, ƴan mata guda uku ne rufe a cikin ɗakin, buɗe masu kofa Aseef ya yi, duk da basu san su ba, amma sun taimaka masu. Haka suka cigaba da tafiya, duk wani ɗaki da zasu gani, in dai da akwai mutane a ciki, to sai sun buɗewa mutanen, su ce su biyo bayansu, tun suna su kaɗan, har suka kai kusan su 40 a wannan tafiya tasu, har a lokacin kuma basu cinma wannan hanya da Dr Salman yake son nuna masu ba, wanda kuma ta nan ne kawai za su bi su fita. A can gida kuma, abubuwa sai ƙoƙarin rikece masu yake yi, yau da wani irin azababben zazzaɓi Rimsha ta tashi, ga tsananin ciwon kai, tun safe take zuba barcin wahala, har misalin karfe 4, shi ma sai da gwaggo ta ga barcin ya yi yawa, sannan ne ta tasheta. Tana tashinta sai kuma me? Wani sabon tashin hankali suka afka, dan kuwa Rimshar tana tashi ta fara tambayar gwaggon wacece ita? Babbar magana. Zaro idanu waje sosai gwaggon ta yi, idanuwan nata tamkar za su faɗi kasa, cike da mamaki a samar fuskanta ta ce "Rimsha ni yau kuma kike tambaya wacece ni?". Wani irin harara ta watsawa gwaggon da waɗan nan dara daran fararen Sleeping eyes ɗin nata, ta ɗauki tsawon a kallah minti biyar kafin ta amsa mata da "E mana wacece ke? Kin wani zo ki zaunawa mutane a waje". Shiru gwaggon ta yi, ta rasa me zata sake ce da Rimshar. A haka Brr Naurat ta shigo ta samesu. Da mamaki take tambayarsu lafiya suka yi wani cirko cirko da idanu haka. Nisawa gwaggo ta yi tare da gyara zamanta, sannan ta ce "Mummy wai Rimsha ce take cewa bata sanni ba yau kuma". Murmushi kaɗan Brr ta saki tana faɗin "To kin dai san halin masu ciki, wata kila yau kuma da irin halin da ta tashi kenan, ai sai ki rabu da ita ki kama wani abin ko? Idan lokacin da ta dawo dai'dai ya yi, sai ki zo ki yi mata maganar da dama zaki yi mata ɗin". Ta kai karshen maganar tare da zama a gefen bed ɗin. Hakika dukkansu basu ɗauki zancen Rimsha na cewa da ta yi bata sannu ba da mahimmanci, gani suke yi dukka shirmene da kuma laulayin ciki, ita kuma ba wani shirme, har ga Allah da gaske take yi, bata sansu ba, gabaɗaya ƙwaƙwalwarta an ɗauke shi ne aka kifa shi, ta mance da komai na rayuwarta, da kuma kowa, ita kanta ma ta mance da ita wacece. Tashin sense!!. Komawa ta yi ta kwanta tana wani irin ɓata rai tare da ɗaure fuska sosai. Daga gwaggon har Brr Naurat ɗin babu wanda ya sake kulata a cikin ɗakin, da haka barci ya sake yin awon gaba da ita, yau tun da ta yi sallar asuba, bata sake yin wani sallah ba, dan ita kanta bata san wacece ita ba bare ta san cewa ita musulmace ko Kristar, wannan shi ne tashin hankali, to meyasameta kuma? Wanene ya juyar mata da tunani? Meyasa aka yi mata hakan?. Ku kasance da Alkalamin FATEEMA ZAHRA MUSA, PRINCESS TEEMA, alkalamina ne kawai zai iya warware maku wannan cankwakiyar. Hira Brr Naurat da gwaggo suka fara zubawa, ita kuma Rimsha ta mayar da barci. Baki ɗauke da sallama Jehan ta shigo cikin ɗakin. Saman bed ɗin ta haye tare da tada kai da laps na gwaggo, da kallo ɗaya zaka yi mata kasan cewa tana cikin tsananin damuwa, har ƴar rama ta yi, ta yi wani fiki fiki da ita, tamkar ba Jehan D.P.O kuma jarumarmu ba. Shafa kanta gwaggon ta fara yi tana faɗin "Babyn daddynta waye kuma ya taɓo mani ke?". Tamkar jira take yi a yi mata tambaya, sai kawai ta sa kuka, hawaye wani na bin wani, Allah mai iko, yai Jehan ce take kuka da hawayenta? A lallai abu ya yi tsamari. "Subhanallahi, Jehan lafiya kike kuka?". Cewar gwaggon. Brr Naurat ma dai abin da ta tambaya kenan, lafiya take kuka?. Cikin kuka ta fara magana kamar haka "Gwaggo ko na kira number Yah Areef bata shiga, kuma yau tsawon kwanaki fa basu dawo ba, babu wani zancensu ma, ni na rasa ya zan yi, wlh kirjina ciwo yake yi mani, please gwaggo ki ce ya dawo, ba zan iya ba..........." Kasa karisa maganar ta yi, saboda wani kuka daya kubce mata. Soyayya muguwar wasa, ta yi mata mummunar kamu, Allah sarki baiwar Allah, ba zata iya jurar rashin shi a kusa da ita ba. Rarrashinta gwaggo ta fara yi, yau ga uwar miji tana rarrashin matan ɗanta a kan matar tana kewar ɗan, Allah mai iko, abin mamaki dai baya karewa, sam babu kunyar gwaggo a tattare da Jehan, babu wani abin da ya sauya a yadda suke da, ita bata yi mata ma kamar gwaggonce ta haifi TRIPLETS ɗin ba, ita dai iya abin da ta sani shi ne, Gwaggo, gwaggonta ce, kuma abokiyar rigimarta, ta zuba mata shagwaɓa san ranta, ita kuma gwaggon ta biye mata, bayan haka ita bata wani san da cewa ana jin kunyar uwar miji ba. Da kyar da suɗin goshi gwaggon ta samu ta shawo kanta, da kyar ta yi shiru, ta hakura ta dai'na kukan, sai dai fa na ciki na ciki, kewar dai babu abin da ya ragu, har wani zazzaɓi take ji. Haka suka kasance har Anaya ma ta shigo ta same su, ita ma nata sabon babin kukan ta zo ta buɗe masu, yau dai suna ganin ikon Allah, haka suka fara rarrashinta ita ma, har sai da ta hakura ta yi shiru, daga haka kuma barci ne ya yi awon gaba da ita. Ba su suka farka ba har sai da gwaggo ta tashe su a kan lokacin sallar mangariba ta yi, su tashi su yi sallah su yi wa mazan nasu a addu'a. A nan ne Gwaggo ta ga abin mamaki abin al'ajabi. Wannan abin mamaki ba komai bane face Rimsha, tana tashi ta barci da aka ce ta je ta yi sallah, buɗar bakinta sai cewa ta yi menene kuma Sallah? Babbar magana. Zaro idanu suka yi, gwaggon zata daka mata tsawa, Brr Naurat ta yi saurin dakatar da ita, saboda ta lura tamkar da kawai matsala a tattare da Rimshar, abin ku da manya, ƙwaƙwalwarsu da tunaninsu ba irin na yara bane, har ta harbo da akwai gagarumin matsala a tattare da jikar tata, wanda su gwaggon kuma basu gane ba. Dan haka sai ta ce kowa ya je ya yi sallah, ita kuma Rimsha ta kwanta ta cigaba da yin barcinta, su kyaleta kada su sake yi mata magana. Da mamaki cike fal a fuskar gwaggon ta ce "Mummy sallah fa zata yi, kuma kice a barta kada ta yi? Ya haka kuma? Ai Rimsha yanzu idan ta ce ba zata yi sallah ba, to wlh da itace zamu karya mata kafa, dan ai ba yarinya bace tun da har da ciki a jikinta, uwa fa take shirin zama". Jama'a ina ganin ikon Allah, karfi da ya ji gwaggo ta mayar da Rimsha mai ciki, ko me ta gani a jikinta da har ta dage a kan lallai ciki ne da ita? Ku tayani dubawa my readers, ita dai Rimsha bata taɓa yin sunna da Lion ba, har yanzu virgin ce ita, amma an zage a kan tana da ciki, to koma me dalilinsu na cewa hakan, lokaci zai nuna mana komai. "Aisha tun da na ce ku bar Rimsha, to ku kyaleta kawai, idan kika cika matsawa, to ba makawa zaki tabka danasani mai girma, dan haka ku kyaleta ki je ki yi sallarki". Cewar Brr Naurat. Okey kawai gwaggon ta amsa mata da shi, sannan ta miƙe tsaye tare da nufar toilet, ita kuma Brr Naurat ta karisa tashin su Jehan a kan su je su yi sallah. In takaice maku wannan labari, Rimsha dai bayan wannan uban barci, to bata iya aikata komai, ko wanka bata yi, baiwar Allah, sai Allah ne kaɗan yasan menene matsalarta!. Haka Brr Naurat ta rinƙa lallaɓata tana ririta ta, sai dai kuma ba abin da take cewa face su gaya mata su waye su? Bata sansu ba. Abin ya ƙullewa gwaggo kai, ita kuwa Brr Naurat sam bata damu ba, dan izuwa yanzu ta gama yardanwa kanta cewa jikar tata ba lafiya take ba, da akwai gagarumin matsala a kasa, hakan yasa bata wani damuwa. Su Abba kuwa, suna can hankalinsu a tashe, sai adduo'i suke yi tare da bincikar ina Aseef, securitynsa Abban Imran ya kira a waya, ya sanyasu suka je suka shigar da report a kan ɓatar na Aseef, su kuma suna gida Lion ya hana fita. A ɓangaren Aafia dai babu wani sauki, sai ma abin da ya cigaba na rashin lafiya, duk ta kara ramewa, ta bushe sosai, ta yi wani irin duhu mai munin gaske, abin gwanin ban tausayi, kuma har yanzu bata amsawa kowa komai, daga ido sai ido. Akil, Imran da Irfan gabaɗaya tarewa suka yi a masallaci suna zubawa TRIPLETS addu'ar fatan nasara a tafiyarsu, Allah ya karesu ya dawo da su lafiya. A ɓangaren Katsina gidansu Sadiq kuwa, Allah mai iko, shagon Yusuf dai sai kara bunƙasa take yi, yanzu har da fridge ya sanya a ciki, yana sayar da kayan sanyi, abubuwa sun cigaba, shi ma Sadiq Alhamdulillah, abubuwa suna tafiya mashi yadda ya kamata, sai dai kuma kullum yana cikin tunanin Jehan, bawan Allah, yana tsananin sonta, bai san cewa matar wani ce a yanzu ba. Maman Sadiq a yanzu abubuwa sun saukaka mata, girkinta har da nama da kifi, sau uku take girki a rana, gabaɗaya ta fita daga harkar baban Sadiq ɗin, dan dama baya tsinana mata komai, yanzu Allah yasa ƴaƴanta sun fara tsayuwa gam da kafafunsu, abu dai sai dai muce Alhamdulillah, wani lokaci har kaji biyu Sadiq yake sayo mata, ya yanka mata, ta gyara masu, ta zuba mashi miya mai shegen daɗi, Allah ya taimaketa ya bata ƴaƴan masu zuciyar nema da kuma zuciyar taimaka mata dukka biyu, dan wani yaron yana da zuciyar nema, amma kuma kuɗinsa bata ciwuwa, ba zai taimaka ba, ita dai ta yi sa'a, daga Sadiq ɗin har Yusuf ɗin burinsu kawai suga sun yi mata abu, su ganta a cikin tsananin fariniki suna kyautata mata, shi ne muradinsu, kuma hakan ce tasa Allah yake taimaka masu, komai suka saka a gaba, sai sunga dai'dai, dan uwa ba wasa ba!!! Uwa ba wasa ba!!! Uwa ba wasa ba!!! Ku ruke wannan da kyau, duk mai son yaga dai'dai, to ya sanya mahaifiyarsa farinciki, ko da iya murmushi kawai kasanya mahaifiyarka a rana, to ba makawa wannan rana ba zata wuce ba har sai wani abin alkhairi da zai sanyaka farinciki ya wanzu a gareka, bare kuma ace ka yi wa mahaifiyarka abin da har zata buɗe baki ta zuba maka albarka da ruwan adduo'i, haba ai ranar abin alkhairi da zaka fuskanta sai Allah ne kawai zai san adadinsa, ina mai kara jan hankulanku ƴan uwa, a kula da uwa, abi umarninta koda babu daɗi matuƙar bai kaucewa dokar Allah ba, hakan zai sanya muga dai'dai a dukkan al'amuranmu, mu jikanta, mu tausaya mata, iyayenmu sun yi mana komai a duniyarnan, komai muka yi ba zamu taɓa biyansu ba! Sai dai mu kwatanta iya abin da zamu iya sanyasu farinciki kawai. To haka dai rayuwar su Sadiq take a yanzu, shi kuma baban nasu, gaula wanda ya rako maza duniya, yana can har iyanzu yana tare a gindin amarya, sai yadda ta ce haka za'ayi, yadda ta dama haka zai sha, naira na aiki, duk zaginsa da ƴan unguwa suke yi, wlh ko a jikinsa, haka Amarya zata yi mashi ɗinki, ko kunya baya ji zai saka kayan a jikinsa yana washe baki, Sadiq bakinciki kamar ya haɗiyi zuciya ya mutu, yana ji yana gani idan baban nasa ya yi wa Amaryar ba dai'dai ba, a tsakar gida zata kwashe mashi duk wasu albarka dake a tattare da shi, ta tsine mashi, ta yi mashi zagin kare dangi, amma dan rashin zuciya, zuciya ta mutu, haka zai yi ta bata hakuri, kuma bata hana shi ya sake komawa gindinta ya tare, abin dai ba'a cewa komai, Sadiq dai ba dan mamansa ba, da yaronnan ya haɗiyi zuciya ya mutu, saboda kunci da bakin cikin irin wannan hali na babansa, yarinya karama kamar amaryar nan da bata wuce sa'arsa a wajen shekaru ba, ta tsaya tana cin mutuncin mahaifinsa, ai kunsan dole zai ji zafi, dan fa uba uba ne komai lalacewarsa, Allah Ubangiji ka bawa kowa iyaye masu zuciya, masu sanin yakamata, masu sanin darajar kansu, masu sanin mutuncin kansu, ba masu kwaɗayin duniya ba, Allah ka karawa namu muku iyayen lafiya, ka kuma saka masu da mafificin alkhairi. Wannan shi ne rayuwar su Sadiq kuma. Idan muka dawo Kaduna kuwa, bayan sallar issha, Brr Naurat ce ta taka da kanta har izuwa part nasu daddyn Rimsha. A lokacin suna tare da mum suna hirar duniya. A palo ta zauna tare da yi masu sallama. Jin cewa ita ce yasa dukkansu har su Abba basu ɓata lokaci ba wajen fitowa. Da mamaki suke kallonta har suka kariso izuwa in da take, a saman sofa kowannansu ya zauna, sai binta da idanu suke yi, suna jiran karin bayani. Ta ɗan ɗauki mintina da a kallah za su kai biyar tana tunani ba tare da ta yi magana ba. Can kuma sai ta fara magana a nutse. "Nawazuddeen a gaskiya Rimsha tana cikin gagarumin matsala, kuma ga halin da muke ciki a yanzu, babu wanda aka yarjewa ya shiga gidan nan ko ya fita sai su Imran, Akil da kuma Irfan, suma dan tarewa da suka yi a masallaci ne, amma yana da kyau mu san matakin da zamu ɗauka, ba zai yi wu mu barta a cikin ciwo har haka ba, babban tashin hankalin ma shi ne rashin sallah, ba zai taɓa yiwuwa mu barta bata sallah ba har zuwa su Saif su dawo, dole kafin su dawo mu san abin yi". Ta kai karshen maganar tana jan doguwar numfashi tare da saukewa a hankali. Har suna haɗa baki wajen cewa "Me kuma yake damunta?". Nan ma shiru Brr ɗin ta ɗan yi, sai jinjina al'amarin a ranta take yi, abin ya bata mamaki kuma ya ɗaure mata kai. "To bana ce ba, amma yanzu abin da za'ayi kuzo muje ku yi mata karatun Alqur'ani mai girma, ko Allah zai sa a samu sassauci, dan fa ikirari take yi ma na cewa ita bata sanmu ba, mun ce mata to shikenan mun ji bata sanmu ɗin ba, kuma mun yarda, amma ta tashi ta yi sallah, shi ne ta ce bata san shi ba, kunga kuwa ai akwai gagarumin matsala, da farko ma na ɗauka dukka laulayin cikin nata ne yasa ta ce bata sanmu ba, amma da ta ce bata san menene sallah ba, sai na fahimci ba batun laulayin ciki bane, wata matsa ce ta daban". Shiru daddynta ya yi yana tauna zantukan na Brr, shi kuma Abban Imran cewa ya yi. "Gaskiya wannan matsala ce babba, bata san me sallah ba kuma? A dole mu nemi mafita, yanzu dai ina take? Muje sai muga me yakamata mu yi mata". Haka suka rankaya izuwa ɗakin gwaggon, suka baro su mum ko wacce a ɗakin mijinta, bama su san me yake faruwa ba. Har lokacin barci Rimshar take yi, tun abincin safe da ta ci, ƴar tahalikan nan bata sake sanya komai a cikinta ba, ko ruwa, da alama ciwon bayan ta yi breakfast ne ya bugeta, dan ba shakka ta yi sallar asuba lafiya lou. Tana barci basu tasheta ba, dan Brr ta ce kada a tashe ta, su yi mata addu'ar a haka, dan haka sai suka fara yi mata topi ta ko'ina, duk suka haɗu a kanta. Ko motsawa bata yi ba, tamkar wadda babu rai a jikinta, ba dan sauƙar numfashi kaɗan kaɗan da suke ji nata ba, to da sai su ce babu rai a tattare da ita. Sun ɗauki tsawon lokaci suna tofa mata addu'a, amma ko motsawa bata yi ba. Abin ya ɗan bawa daddynta mamaki, sai dai bai bayyana hakan ba, ya dai cigaba da yi mata topin kawai. Daga karshe Brr Naurat ta ce su barta kawai, zuwa gobe da safe In Sha Allah sai a kirawo su Imran a waya, su dawo gida a san abin yi. Okey suka amsa mata, shi dai daddynta ya amsa ne kawai saboda mahaifiya ba wasa ba, basu ja da maganarta, amma ba dan haka ba, a daren nan ya so ya ɗauketa su je neman magani, dan abin ya ɗaga mashi hankali!!, Barema yanda ya ga fuskarta ta kara wani irin haske, ita da take chocolate color, to ta kusa kai Jehan haske a yau, ga face ɗin nata ya ɗan kunbura kaɗan, abin dai ba'a cewa komai, tana a cikin matsala ainun. Da haka suka koma ɗakunansu, ita kuwa Brr Naurat ta gyarawa Rimshar kwanciya tare da rufa mata bargo, sannan ta ce gwaggo ta koma ɗakinsu Rimshar ta kwana da Jehan, su barta da Rimshar a nan. Okey gwaggon ta amsa tare da cewa "Zan je ɗakin Saif na kwana kawai, kyale Jehan ɗin nan, ba zan iya rigimarta ba yau ɗin nan, dan sam yau bana jin daɗi". Ta kai karshen maganar tare da nufar kofar fita. Kiranta Brr ɗin ta yi a kan ta dawo. Ba musu ta koma ta zauna, nasiha mai ratsa jiki Brr ɗin ta yi mata, dan tasan cewa ba wani rashin jin daɗin jikinta da take ji, kawai tunanin TRIPLETS nata ne ya sakata a gaba, ba dan Brr ɗin ma tana yi mata faɗa da nasiha a kullum ba, ai da abin sai ya fi haka. Sosai ta ji nasihar mahaifiyartata, ta kuma yi alkawarin In Sha Allah zata cire damuwar a ranta, za kuma ta kara tsananta masu addu'a sosai. Da haka suka yi sallama, ta wuce ɗakin Lion dan ta kwanta, ita kuma Brr Naurat ta gyara ta kwanta a kusa da Rimshar, baiwar Allah sai barci kawai take ta zubawa ba ci ba sha. A ɓangaren Daular Mutuwa kuwa. Sunci bakar wahala na kin karawa, sun azabtu kafin nan su kai wajen da Dr Salman ya ce masu hanyar take. Sai dai kuma ko da suka je wajen babu wata hanya a wajen, wayam wajen take. Jugum jugum suka tsaya suna mayar da numfashi, ga kuma gine ginen gidan cigaba da rugujewa yake yi, idan har basu hanzarta nemo hanya ba, to har in da suke ma sai ya ruguje ya rufta da su. Sauke Ayla daga bayansa Areef ya yi, sannan ya fara kewaye a wajen yana nema masu ko da akwai wata makama da zata nuna da alamar hanya ta sama ko ta kasa a wajen. Ita kuwa Aylar, yana sauketa ta zube kasa a saman gwiwowinta, cikinta ne yake wani irin murɗa mata, tamkar cikin yana son fita daga jikinta ne, ta wahala ne aihun. Sauke Akila shi ma Aseef ya yi, ita ma yana sauketa ta zuba kasa a saman gwiwowinta, tana mai da numfashi. Shi ma Dr Salman zama a wajen ya yi, saboda wajen tiles ne fari tas da shi, babu alamar kazanta a wajen. Ganin hakan yasa duk sauran jama'ar da suka biyusu, suma sai suka zauna a kasa a wajen ɗin kawai. Wasa wasa cikin Ayla na kara tsananta mata ciwo, tun tana dannewa har ta fara ruwan hawaye, sam Areef ko Aseef babu wanda ya lura da halin da take a ciki, sun tafi dubawa ko za su ga hanya a wajen. Da AKILA ta ga yanda ta dafe cikin nata tana murkusoso, sai ta daure ta matso kusa da ita, cike da kulawa ta rungumota, daman kunsan ita Akila akwaita da son ƴan uwanta da dangi, tana da tausayi sosai. Haka ta rungumo Aylar tana tambayarta meyake damunta take kuka. Kasa yin magana ta yi, Dr Salman ma matsowa kusa da ita ya yi, sun zaci wahalar hanya ce, sai suka fara ƙoƙarin rarrashinta. Sai kuma me, jini suka fara gani ya fara bin kafafunta. Sosai Akila ta tsorata, hakan yasa ta zunduma ihu tana faɗin "Heartbeat jini, jini matar bappa Maik take zubarwa sosai". A tsananin rikice ta yi maganar, saboda bata taɓa ganin jini na fita dayawa daga jikin mace har haka ba, shi ne abin ya tsoratata. A tare Aseef ɗin da Areef ɗin suka juyo da kallonsu a kansu, da yake shi Areef ya fi su tausayi, a dubu ɗari ya nufo in da suke, dan ya duba me matsalar. Sai dai kuma bai kai ga karisowa ba, a dai'dai tsakiyar wajen, filin ta ɓurma da shi ya zurma kasa. Tashin sense, shikenan Areef ya rufta!. Kafin Aseef ɗin ya yi wani yunkuri, ilahirin wajen gabaɗaya ya fara wani irin jijjiga yana ƙoƙarin ruftawa da su......... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E16 Date: 26/4/2024 Kafin Aseef ɗin ya yi wani yunkuri, ilahirin wajen gabaɗaya ya fara wani irin jijjiga yana ƙoƙarin ruftawa da su. Da Aseef ɗin ya ga haka, sai ya yi amfani da nasa tunanin, cikin ƙanƙanin lokaci ya binciko ƴar hanyar da take a wajen, a hanzarce yasa karfi ya buɗe kofar hanyar, ta cikin kasa take. Ya sha bakar wahala kafin ya buɗe masu, sannan ya ce su zo su fita ta wajen. Ayla ba zata iya miƙewa ba, dan haka sai ya kamata ita da Akila da Dr Salman, ya ce da sauran mutane kuma su bi ta hanyar su tafi. Da sauri suka fara dira a hanyar, shi kuma sam bai ji kyamar jinin dake jikin Ayla ɗin ba, ya ɗauketa cak, ya goyata a bayansa, da kyar ta iya ruke wuyarsa, saboda tsananin azabar da take ji. Haka ya riko hannun Heartbeat tasa, sannan ya ce da Dr Salman ma ruke ɗayar hannun Heartbeat, komai zai faru kada su yarda su sake hannun juna. To suka amsa mashi da shi. Da ɗan ɗaga murya ya ce duk su rufe idanunsu, dan yasan halin AKILA sarai, yanzu idan taga ta in da zasu faɗa, to haukace masu zata yi, ga shi ba damar ya goyata, saboda Ayla tafita bugatar taimako a halin yanzu. Suna rufe idanunsu, ya jasu da karfi, gabaɗaya suka tafi suka faɗa ta in da Areef ya faɗa. Suna faɗawa bai fi da minti biyu ba, gabaɗaya ginin dake wajen ya ruguje ruguzum. Suna faɗawa basu sauka a ko'ina ba sai a ainahin cikin fadar Queen da suka kwashe tsawon kwanaki suna ne ma, ashe su suna a sama da fadar ne ma, fadar tata tana a cikin kasa. Suna dira a tsakiyar fadar, cikin hanzari ya sauke Ayla dan su dubata, su ceci rayuwarta, bai ma lura da cewa a fadar Queen suke ba. Sai bayan ya sauke Ayla ɗin ne ya ɗago kansa da nufin ya ce da Akila ta bashi ɗankwalin kanta. Yana ɗago idanu suka yi ido huɗu da Lion da yake zaune a saman kujerar mulkin Queen ɗin. A dubu ɗari ya ɗago kan nasa da kyau, dan ya kalli shin abin da yake gani gaskiya ce. Ba shakka Lion ɗin ne yake zaune kamar yanda ya gani tun farko, gabaɗaya jikinsa duk jini, da alama ya sha gwagwarmaya ba kaɗan ba, ya jingina kansa da jikin head na sofar, sai sauke numfashi yake yi a hankali hankali, yana wani irin nishi, alamar ya gaji over, daga hannunsa, kirjinsa, fuskarsa wajen kumatu, dukka jini ne ya ɓata shi, babu riga a jikinsa, ainahin kakkarfa kuma kyakkyawan surar jikinsa na cikakkun jaruman maza a bayyane, sai binsu da blue eyes nasa kawai yake yi abinsa. A dubu Aseef ɗin ya miƙe tsaye yana kallonsa da kyau, a hankali ya fara bin cikin fadar da kallo. Can ya hango ƴar Queen ɗin a ɗaure da sarka, Lion ya yi mata ɗaurin goro, ita kuma Queen ɗin tana kwance flat a tsakiyar fadar, tamkar gawa, ko motsawa bata yi, da alama rai ya yi halinsa ne, ga kuma hannunta ɗaya babu shi, da alama Lion ya sare mata hannu ɗaya ne, alamu sun nuna ba karamar faɗa suka gwabza a tsakaninsu ba, dan kuwa sun ruguje komai na cikin fadar, babu abin da ya rage mai amfani a cikin fadar. A hanzarce ya nufi Lion ɗin, tsabar a galabaice Lion ɗin yake ya kasa tambayarsa meya kawo shi nan? Ya aka yi kuma ya zo? Ya sha mamakin ganinsa sosai, sai dai ba zai iya yin wani magana ba. Bai kai ga karisawa wajen Lion ɗin ba, sai ga Areef ya fito daga wata ɗaki dake a cikin fadar, hannunsa na ruke da wasu kyallaye farare guda biyu. Wajen Lion ɗin ya kariso yana faɗin "Saif bari na ɗaure maka hannun nan naka dake zubar da jini da wannan tsummar, sai na ɗaukeka mu fita daga wajen nan, idan ba haka ba, duk zamu mutu, kasan dai gabaɗaya gidan nan rugujewa zai yi ko? Tun da dama mafiya yawan ɓangarorin gidan ba ginasu aka yi ba, da tsafi aka yi su, to yanzu mai tsafin ma ta mutu, kaga suma dole ne su mutu, dan haka ka yi sauri muje". Ya kai karshen maganar yana karisowa kusa da Lion ɗin sosai. Ɗaga mashi hannu Lion ɗin ya yi, alamar baya da bukatar a ɗaure mashi hannun nasa, ya bar mashi abinsa. Bai yi ja in ja da shi ba, sai ya bar mashi, dan yasan ba zai ce a bar mashi hannunsa jininsa na zuba haka kawai a banza ba. Da kyar Lion ɗin ya yunkura ya miƙe, wani irin jiri yake kallo, yau tsawon kwanaki bai ci komai ba, sai gwabza yaki yake yi da mukarraban Queen har ya iso gareta, shi ne yasa ya galabaita sosai, kuma ko da ya iso gareta, ba ƙaramin yaki suka yi da ita ba, ta wahala shi ma ya wahala kafin ya samu ya kasheta. Na san zaku so jin ya akayi hakan ta faru, to ku saurara. Shi Lion already ko da ya shaki kamshin turaren da Queen ɗin ta shaka masu a gidanta, to shi bai suma ba, saboda askar na safe da ya yi, askar na safe idan ka nutsu ka yi shi, Ubangiji ya yi alkawarin Mala'iku ne zasu kula da kai, babu abin cutarwa da zai sameka har izuwa maraice, idan ka yi na maraice, to Mala'ikun zasu sake kulawa da kai har izuwa gobe da asuba, wannan faɗar Allah da manzonsa ne, kuma ya yi karatun Alkur'ani mai girma sosai kafin ya baro gida, sannan ya yi adduo'i ba kaɗan ba, dan yanda yaga Rimsha ta rikice, sai ya ɗauki abin serious, shi kuma Areef da yake bai san ya Daular Mutuwa take ba, tun da Rimsha ba matarsa bace, bai san halinta ba, sai bai ɗauki abin serious ba, bai yi wani addu'a ba, shi dai ya saɓi jaka kawai, ya lodi kaya kamar wanda zai je honey moon da matarsa, to a takaice dai shi Lion ko da ya shaki kamshin turaren, bata yi mashi komai ba, ya kwanta ne shiru kawai tamkar ya suma, dan yana son shigowa cikin Daular Mutuwar ta kowace hali, a tunanin Queen, ita ce ta yi wasa da kwakwalwarsu, ta kuma kafa masu tarko, ta yi nasara suka faɗa, bata san cewa ita ta faɗa tarkon ba, ba ita ta kamasu kamar yadda take tunani ba, Lion ne ya kamata a cikin tarkon nata da ta kafa masu da kanta, wasa da tunaninta sosai ya buga, bata taɓa tunanin hakan zai faru ba. Lokacin da ta rufe shi a ɗakin duhu, ta kuma daure shi, duk yana jinsu, yana a cikin hayyacinsa, ya yi masu abin da zaki yake yi idan zai farauci abinci ne, kwanciyar ɗaukar rai ya yi masu, abin da basu taɓa zata ba. Waɗan nan sarkokin da suka ɗaure shi dai, already kun san sarkokin tsafi ne, dan haka yana karanta masu Alqur'ani mai girma, duk suka ruguje, suka zama gari, sai dai ya sha bakar wahala sosai kafin ya fita daga cikin ɗakin duhun. Yana fita kuma bai nemi kowa ba, sai ita Queen ɗin, sam bai nemi ina su Areef suke ba, dan yasan idan ya kamata to tamkar ya gano dukkan in da ƴan uwansa suke ne, saɓanin shi Areef da ya tashi sai ya fara neman Lion ɗin, da yake kowa da irin kaifin kwakwalwarsa da tunaninsa, kuma babba kam ko da minti ɗaya ya fika, to ko yaya babba ne, ya fika, shi ne yasa Lion ɗin ya fisu hangen nesa, dan ya fisu a komai. Yasha bakar wahala sosai a wajen neman Queen ɗin, ya yi faɗa da mukarrabanta sosai. Tsawon kwanaki yana nemanta, a hanyarsa na neman nata ne ya kashe su barbushi, ya yi nasarar kashesu ne da taimakon Allah. Haka ya yi ta fama har ya gano in da shegiyar fadar tata take. Time da ya shigo fadar, babu kowa a ciki sai ita da ƴarta, duk ta tura mukarrabanta domin su kamo mata su Areef, bata san shi ma Lion ɗin ya fito ba, da taimakon sunan Allah ya ɓacewa idanuwan tsafinta, hakan tasa bata ga fitowarsa ba. Tana ganinsa ta miƙe, da tsafinta ta yi ƙoƙarin damko wuyarsa ta janyo shi, dan ta hallaka shi. Already kafin ya shigo cikin fadar tata da bismillah ɗauke a bakinsa ya shigo, dan haka sai ta kasa kama shi ɗin, ta yi ta faman gwadawa, amma ina takasa. Shi kuma yana tsaye gam, kamar wani jarumin sadaukin yaki. Ganin ta kasa saka hannunta a jikinsa ne yasa ta fara ƙoƙarin tura mashi kayan tsafe tsafenta, dan su illatar da shi, to a nan ne aka samu wannan fashe fashen kaya da suka rinƙa yi a cikin fadar, sai da ta fasa komai nata da kanta. Da ƴarta ta ga haka, sai ta yi ƙoƙarin tayata yakin, shi kuma Lion ya ɗauko wani wuka dake a wajen ajiye wukakensu, wuka ce mai tsananin kaifin gaske, ya yi amfani da ita ya sarewa Queen ɗin hannunta na dama ba tare da ta ankara ba, ya cire mata hannun tun daga sama wajen shoulder ta. Yana datse hannun nata ya kai hannunsa ya cire zobben dake a jikin babbar yatsarta, wannan zobbe ba komai bane face karfin tsafinta, shi ne karfinta da komai nata, idan babu shi, to ita ba koman komai bace, already dama yasan da irin wannan zobbe, duk wasu cikakkun matsafa suna amfani da wannan zobbe, duk matsafan da basu da shi, to da sauransu, har yanzu basu kai shegu ba, akwai wata kungiyar matsafa da ya taɓa tarwatsawa a New York, suma haka ya datsewa shugabansu hannu, ya ɗauki wannan zobbe ya jefata a cikin wuta, daga nan alkadarin tsafin ta karye. To ita ma Queen haka ya yi mata, yana cire zobben ya zura a aljihunsa, da ta ga haka, sai ta fara ƙoƙarin yin faɗar hannu da shi da hannu ɗaya, ga bakar azaba tana ji a hannun nata, amma saboda karfin hali, sai bata karaya ba, ta fara faɗa da shi, dan ta kwaci zobben. Bugu ɗaya ya yi mata a bayan kunne ta wajen wuyarta, daga haka bai kara na biyu ba rai ya yi halinsa, dama kunsan ta tsufa, ta kai shekaru 45 zuwa 50 a duniya, to bugu ɗaya mai lafiya Lion ya yi mata, shikenan ta ce ga duniyarku. Already dama shi Lion kun sani, zaratan maza ma ya suka kare da shi? Da duka ɗaya yake kai mutun in da zai yi danasani har ƙarshen rayuwarsa, bare kuma ita Queen da take mace, macen ma tsohuwa, ai dukansa ɗaya ma ya yi mata yawa. Ita kuma ƴarta Lion ɗin ya kamata ya ɗaureta, a cewarsa, bai yi tunanin irin hukuncin da yakamata ya yi mata bama tukun nan. Yana kashe Queen ɗin kuma wasu zaratan maza suka shigo cikin fadar, matasan igbo ne, kyawawa da su majiya karfi, su goma sha biyu cif. Ganin abin da yake faruwa ne yasa suka fara ƙoƙarin kashe Lion ɗin, to da sune ya yi faɗar nan da suka ji mashi ciwo, jikinsa duk jini, sun ji mashi ciwon ne kuma ta hanyar dogayen faratunan yatsun hannunsu da suke da shi, kun san soft skin nasa kuma, tana da laushi tamkar fatar jariri, ya ji hutu ya ƙoshi, to shi ne idan suka yagushe shi sai wajen ta yi jini, hakan yasa suka sami kalaba ta ji mashi ciwo sosai a jiki. A garin dukansu kuma ya yanke da wuka sosai a hannu, shi ne wajen da Areef ya ce zai ɗaure mashi yaki yarda. Wannan shi ne a takaice abin da ya faru, abin da yasa gine ginen wajen kuma suke ruguzowa da kansu, saboda already da tsafi aka yi su, to kuma tsafin dake a cikin gidan a halin yanzu ya karye, komai ya lalace, dole gidan ta ruguje.......... To kun ji yadda aka yi, har kullum PRINCESS TEEMA ce taku ta amana mai abin ban mamaki🤙. STORY. Cikin wata iriyar kasalalliyar murya, can kasa kasa Lion ɗin ya ce "Areef ka ɗauko Mark mu tafi, ya sami karaya a kafa, he can't walk by himself". Zaro idanu sosai Areef ɗin ya yi yana faɗin "Lion what are you saying? Mark fa ka ce?". Jinjina mashi kai kawai ya yi ba tare da ya sake yin magana ba, saboda idan ma ba dan yana da taurin zuciya ba, Allah ko mikewa ba zai iya yi ba, dan tsananin yunwa, kuma dama already kun san shi baya da jumuriyar yunwa sosai, Areef ya fishi jure yunwa, amma shi da Aseef, sam basu shiri da zancen yunwa sam sam, sai dai kuma, basu cin abinci dayawa, idan sun ci kaɗan Alhamdulillah sun ƙoshi. "I think Mark he already dead?". Ya faɗa fuskarsa ɗauke da mamaki ƙarara a bayyane. Ko sannu Lion ɗin bai sake ce masu ba. "Where is he?". Cewar Areef ɗin. Da kyar Lion ɗin ya iya nuna mashi wata hanya da take a cikin fadar. Da sauri ya nufi hanyar, shi kuma Lion ɗin ya fara takowa a hankali yana nufo su Aseef. Ganin yanda yake tafiya da kyar da kyar ne yasa Aseef ɗin ya kariso wajensa da sauri. Yana zuwa ya taimaka mashi suka karisa wajen da su Dr Salman suke tsaye. Ayla baiwar Allah azaba tasa ta sume, har lokacin kuma jini take zubarwa. Kallo ɗaya Lion ɗin ya yi mata ya kawar da kansa gefe guda, wani iri yake ji a cikin zuciyarsa, ga tunanin Meeshansa, ga bakincikin da yake ciki na cewar Aseef ba ɗan uwansu bane, ga bakin cikin abin da su Josephine suka yi masu na cin amanar mahaifinsu, sannan suka ci amanarsu suma, abubuwa sun taru sun yi mashi yawa a cikin zuciyarsa, ba dan yana da dakiya da juriya ba, da ya jima da faɗuwa kasa, da makiya sun yi galaba a kansa, sai dai ya rigasu ya ce Allah, dan haka Allah yake dafa mashi a koda yaushe, hakan tasa a kullum sai dai ya kara tsayuwa da kafafunsa gam, ba dai ya je kasa ba. Areef ne ya fito daga wannan ƴar siririyar hanyar ɗauke da Mark ɗin a saman kafaɗarsa, baya ko motsi, da alama a sume yake. A kusa da Dr Salman ya kwantar da Mark ɗin yana faɗin "Ina sauran sojojin kuma?". "The already dead, remain 2". Lion ɗin ya bashi amsa a takaice tare da wucewa ya nufi kofar fita daga fadar, dan fadar dab take da ta ruguje. Sake ɗaukar Mark ɗin Areef ɗin ya yi, shi kuma Aseef ya ɗauki Ayla dake sume gwanin ban tausayi, duk sun jigata na kin karawa, duk wanda ya gansu a wannan hali, babu shakka sai ya tausaya masu, yau Lion da kansa da kyar yake tafiya, ko daga nan kun san bala'in Daular Mutuwa ta wuce tunanin mai tunani. Sun ɗan yi tafiya mai ɗan nisa kafin su kai wata kofa dake fuskantar gabas. A tab bakin kofar Lion ya tsaya ba tare da ya buɗeta ba. Sai kuma ya duƙa kasa a wajen, a hankali ya buɗe wata kofar kasa dake a wajen, sannan ya miƙe tsaye. In a cool voice ya ce masu su zo su shiga, nan ne kawai kofar da ta rage ta fita a gidan, duk saura sun ruguje, su yi sauri dan in da suke ɗin ma, dab yake da rugujewa, abu kaɗan ya rage. Da sauri suka karisa wajen, ɗaya bayan ɗaya suka shi ga. Lion ɗin ne ya sake ce da Areef ya koma ya ɗauko sojoji biyu da suka saura da ransu. A tare suka koma da Aseef, bayan Aseef ɗin ya sauke Ayla a cikin wannan hanyar kenan. Da sauri suka ɗauko su. Suna fita daga cikin fadar ginin ta ruguzo a kan ƴar Queen ɗin da ita kanta Queen ɗin. Daga in da suke suna jiyo sautin ihun ƴar Queen ɗin, amma babu wanda ma ya ji cewa tamkar mutunce take ihun neman taimako, ga shi ba halin ta gudu, dan Lion ya ɗaureta, haka gini ya ruguzo a kanta, da haka ta mutu. Sai dai fa sun sha ruwan mamakin jin ihun mutane sosai a lokacin da ginin yake rugujewa, hakan na nufin da akwai sauran mutane a cikin gidan, Allah sarkin ginin nata rugujewa a kansu, dan kofofin ɗakunan duk a rufe suke, ba halin su gudu, sai dai wasu daga cikinsu, sun samu sun iya buɗe kofar sun gudu, sun nufi sauran ɓangarori na cikin gidan, fatan mu dai Allah yasa su sami hanyar fita, suma su tsira, ko ina Mustapha da Kausar?. Bayan sun shiga cikin wannan hanyar dukkansu, Lion ne na karshe da ya shiga, sai da ya tabbatar dukkansu sun shiga, bayan ya shiga, sai ya janyo kofar ya rufe. Bayan ya Rufe ne ya tsaya ya tsare Aseef da dara daran idanuwan nan nasa. Ƴan kame kame Aseef ɗin ya fara yi, dan wlh idanun Lion mugun rikita mutun suke yi, musamman idan ya tsareka da su ba tare da ya yi magana ba, duk sai ka ji ka tsargu, ko da kuwa baka yi laifi ba, sai yasa ka rasa nutsuwarka, haka shi ma Aseef ɗin ya yi, duk sai ya rasa nutsuwarsa, ya kama ƴan kame kame kamar wani tsohon munafuki. Ko sannu Lion ɗin bai ce mashi ba, ya sa kai ya nufi wajen da Ayla take kwance, ɗan duƙawa ya yi a kusa da ita, a hankali ya kai hannunsa ya saɓeta a saman kafaɗarsa, sannan ya ruke hannun Dr Salman da hannunsa ɗaya, bai ce da kowa komai ba ya kama hanyar fita. Ganin haka yasa Aseef ya ɗauki soja guda ɗaya, shi kuma Areef ya ɗauki Mark, suka bar soja ɗaya a wajen. Kasancewar tafiyar Lion yana da sauri, hakan yasa ya yi masu nisa sosai. Can saman wani dutse ya kwantar da Aylar, sannan ya juyo ya dawo dan ya ɗauki sojansa ɗayan da yake a bakin kofar shiga hanyar. Duk sojojin suna a sume, kuma babu ruwan da za'a zuba masu su farfaɗo. Duk da ciwon da yake jikinsa, da wahalar da yasha, hakan bai sa ya ji cewa zai iya barin wannan sojan nasa a wajen ba, saboda amana da kuma sanin darajar rai irin nasa. Har cikin ransa yana jin zafin jikinsa, amma haka ya ciza laɓɓansa gam ya saɓi sojan nan a saman shoulder ɗinsa. A hanya bai kai ga karisawa wajen da ya kwantar da Aylar ba, ya ci karo da Areef, karɓa mashi sojan Areef ɗin ya yi, ba musu ya miƙa mashi sojan suka cigaba da tafiya. A takaice a haka sai da suka yi tafiyar kwana ɗaya da wuni ɗaya cur a cikin wannan hanyar, ba dan Allah ba, da ba zasu taɓa kai labari ba, sun sha wahalar da ko makiyinka ba zaka yi mashi fatar ko makamancin irin hakan ta faru da shi ba. Da yake hanyar yana da faɗi, kuma yana da reshuna, ma'ana hanyar ta rabu kashi kashi. Kun tuna hanyar da su Rimsha suka bi suka fita? To ɗaya ne daga cikin reshen wannan hanyar, ta kasu ne kashi kashi, to suma haka suka cigaba da tafiya a cikin wannan dutse, har Allah yasa suka fita. A wajen fita ma ba karamar gwagwarmaya suka sha ba, dan an rasa wanda zai iya jijjige masu kofar ya buɗeta su fita, duk sun galabaita fiye da tunanin mai tunani, shi kansa Aseef ɗan dirama, yanzu ya yi laushi, bare Heartbeat nasa da Dr Salman, ai ba'a magana bayin Allah. Daga karshe dai Lion ɗin ne ya daure ya cije ya buge masu kofar tare da taimakon Aseef, shi kam AREEF ya zama tamkar Aseef a baya yau, ya yi laushi over, ga bala'i yunwa. Suna buge kofar wani irin hasken rana ne ya haske masu idanu, dukkansu sai da suka datse idanuwansu, kafin daga baya su sake buɗewa a hankali. Lion ne ya fara sako kafafunsa waje, dan shi ne babba, shi ne yakamata ya fara fita, dan yaga ya yanayin hanyar take. Kungurmin dajin nan ne da su Rimsha suka fita ta wajen, sai dai su Rimsha ta baya suka fito, su kuma ta gaba suka fito, dama kunsan hanyar tana da reshuna. Ganin wannan dajin ne yasa ya ce su fito kawai su tafi, zasu cinma gari a gaba ai. Wahalar dai su fita gari ne, suna fita gari koma ina ne komai zai saukaka masu, dan su ko'ina suka je, to dole masu ruke da mulkin garin su tarbesu hannu bibbiyu, dan ko a kasar America da kanta moryiyinsu tana da matuƙar kaifi fiye da tunanin mai tunani, ga shi kuma su taurari ne na faɗin Washington DC da kewayenta, ta ko'ina ana ji da su fiye da tunanin mai tunani, so wahalar ta dai a yanzu su fita gari ne. Cigaba da tafiya suka yi ta yamma maso arewa, bama su iya gane gabas ba bare yamma, su dai in da ya fi yi masu, in da suke ganin zai fi masu sauki, nan suka bi. Da yake rani ya shigo, damuna ta tafi, sai ya zamana ƴaƴan itatuwan dake a dajin sun fara ƙarewa, haka dai suka cigaba da tafiya. Sun yi tafiya mai nisa sosai daga in da suka fito, sannan ne Lion ya zauna a kasar wata bishiyar mangoro mai matukar girma, kusan kamar bishiyar kuka. Abin mamaki a kasar wannan bishiyar su Rimsha suka fara zama time da suka fito, dan hanyar da su Lion ɗin suka biyo, ya zo ya haɗu da hanyar da su Rimsha suka biyo, dan idan baku manta ba, ta yamma su Lion ɗin suka juya suka bi, hankan ce ta mayar da su ta wancan hanyar. Dukkansu zama suka zo suka yi a kusa da Lion ɗin, sauke Mark Areef ya yi, sannan ya shiga cikin dajin, dan ya nemo ruwa, su samu su yayyafawa sojojin nan su faffaɗo, idan suka farfaɗo, komai zai zo masu da sauki, zasu rage wahala ta ɗaukarsu. Jingina kansa da jikin itacen Lion ɗin ya yi, a hankali ya lumshe idanuwansa, wani barcin wahala ce ta ɗan ɗaukesa a wajen, ita ma Akila kwanciya ta yi a kasar, tare da tada kai da laps na Heartbeat nata, tana kwanciya sai barci, shi ma Dr Salman kwanciya ya yi, ya yi barci bawan Allah, ita Ayla, dama already a sume take. Kafin Areef ya dawo, duk sun yi barci, ya ɗebo ruwa a cikin wata gora da ya gani a wajen, sai a lokacin ya tuna da jakarsa da ya barota a fadar Queen, har ruwa da akwai a cikin jakar. Ajiye ruwan ya yi, sannan ya zauna dan ya mike kafafunsa ya ɗan huta, shi ma ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi. After some hours. Can cikin barci Lion ya ji motsi a kusa da su, duk da ya san suna da yawa a wajen, amma wannan ba motsin mutun bane, mutsin wata dabba ce, kunsan shi dama already bashi da nauyin barci, dan haka sai ya farka. A hankali ya buɗe idanuwansa. Wata zabgegiyar kunama ce a kusa da Aseef dake jingine da jikin itacen yana barci shi ma, ga Heartbeat ta yi barci a saman cinyarsa, shi Lion already dama ya saba da irin wajen nan, wanda ya fi haka haɗari ma sun zauna a ciki kafin ya taka matsayin da yake a kai yanzu, ai dama soja bai kamata ya ji tsoro ko kuma ace waje irin wannan ta zamar mashi bakuwar waje ba, musamman ma sojoji irinsu na Usa. Dan haka sai ya kai hannunsa ya kama kunamar, tana ƙoƙarin kai mashi harbi, ya yi maza ya damki karin nata, da karfi ya tsige daga jikinta ya gefar gefe guda. Yana gefarwa sai ya ji wani motsi daga ɗan nesa da su, alamar tafiyar mutane ne. Lumshe idanuwansa ya yi yana mamaki mutane kuma a wannan dajin?. Bai buɗe idanu ba har sai da ya ji isowar mutanen kansu. A hankali ya waro idanuwansa a kansu. Mutanene sun kai su 10, kaɗan ne daga cikin mutanen da su Areef suka taimaka a cikin Daular Mutuwar, su ne waɗan da Aseef ya buɗewa kofa suka fita. Sannu suka yi wa Lion ɗin cikin harshen yarabanci. Mayar da idanuwansa ya yi ya lumshe, a cewarsa basu ishe shi kallo ba, ba zai ɓata idanuwansa wajen ganinsu ba. Wata daga cikinsu ne ta yi magana cikin harshen turanci, a in da ta ce "Laaa kuga abin mamaki, ga shi yana zaune a wajen, ga kuma zanen face nasa a jikin itacen da yake zaune ɗin! Ko dai shi ne ya zana? Amma kuma kamar zanen ya jima!". Jin sun ambaci sunan zane ne yasa ya waro idanuwansa, dan shi dai yasan Meeshansa ce kawai ta iya zana shi, kuma ba shakka ya ga tulin zanensa da ta yi a cikin Daular Mutuwar, a hanyarsa ta zuwa neman Queen, a lokacin ya ci karo da wani ɗaki, yana shiga ya tatda zanen face nasa da yawa a ciki, duk tabi jikin bango ta zana, wannan ɗakin kuma ba ko'ina bane face ɗakin da Rimshar ta zauna, idan baku manta ba dama ta yi zanensa sosai a wajen. A hankali ya juyar da kallonsa izuwa kan in da matar take nunawa, dan ya kalli zanen da idanunsa. Bai yi mamaki ba, kuma da kallo ɗaya ya yi wa zanen ya gane tabbas zanen Rimsha ce, saboda zanenta baya ɓuya mashi, tana barin alama guda ɗaya a jikin zanenta idan ta yi, wannan alama kuma ba komai bane face a duk in da ta zana face nasa, to sai ta zana mashi lips nata a saman kumatunsa, alamar ta yi kissing na zanen, so a dukka zanensa da ta yi a rayuwarta, da akwai wannan alamar ta kiss ɗin. Mai da idanuwansa ya yi ya lumshe yana tunani yanzu duk irin wannan wahala ta wannan hanya haka Meeshansa ta biyo? Yanzu haka ta keta wannan kungurmin daji haka? A gaskiya Queen ta cuce shi dayawa, ta wahalar mashi da pleasurensa, dole Rimsha ta ce ba zata dawo Daular Mutuwa ba, ashe azaba ta sha na kin karawa baiwar Allah, ya zama dole idan ya koma gida ya kula da ita sosai....... Yana tsaka da tunanin ne mutanen suka katse mashi tunanin da cewa sun zo su taimaka masu ne, da akwai abinci da ruwan sha a masaukinsu, su zo suje sai su ci.................Lallai rashin sani yafi dare duhu, basu san wanenen Lion ba, da sam bama za su zo in da yake ba bare suce ya zo ya ci abincinsu da suka girka da ita ce duk hayaki, abincin ma a dajin suka samo shi, sai Allah ne yasan menene ma, sai kuma su da suka girka, to shi Lion da ma bai iya cin abincin Nigeria ba! Ai ko sau ɗaya bai taɓa gwada cin abincin Naija ba, bai iya ba, baya ma son kamshinta, ina da tabbacin ko yunwa zata kashe shi ba ci zai yi ba, komai haɗin da za'ayi wa abincin Naija da wuya ya iya ɗanɗanawa, abinci mai rai da lafiya wadda ta amsa sunanta abinci ma kenan, ina ga kuma wannan abincin nasu na ƴan gudun hijira? Ai ko kallo ma ba zai yi ba bare ci, zai ce datti ce, kuma kun san shi da bala'in kyankyani, ai idan ya gani da ido ma, ya rinƙa sheka masu amai kenan har sai abin da hali ya yi kuma. Ko kallon in da suke bai sake yi ba, tamkar ma babu shi a wajen, da suka ga bai amsa ba, sai suka yi tunanin bai ji su bane, sai suka sake yi mashi magana. Wani irin tsawa ya daka masu na su tashi su bashi waje, dan sun ishe shi. Bayin Allah har wani firgita suka yi, su da suka zo taimako, dama sun ga cewa Areef da Aseef sun taimaka masu ne, shi ne suma suna ganin a yanzu sun sami dama, bari suma su taimaka masu, basu san waɗan nan ba'ayi masu goninta ba, ai TRIPLETS barsu kawai a yanda ka gansu, dan sun wuce tunaninka, sai kana tunanin yau zaka gansu a fari, sai ka gansu a ja, haka suke, baka gane ina suka dosa, sam su ba'a yi masu goninta, kuma ba'a burgesu, idan ba yanzu ma da suka sami mata bane abin ya ragu, da a baya ne ai ba'a ma magana. Tsawar nan da ya daka masu ne yasa su Areef suka farka daga barcin da suke yi. Kallon sama da kasa Areef ya watsawa mutanen, a lokacin kuma already sun juya zasu koma wajensu. Miƙewa ya yi ya ɗauko robar ruwan da ya ajiye, a gaban sojojin ya dawo ya tsugunna, a hannunsa ya tarbo ruwan tare da fara yayyafa masu a face nasu. Kusan a tare bayin Allah suka farka, ganin sun farka ne yasa ya ajiye ragowar ruwan, ya koma kusa da Ayla dake kwance bata ko motsi. Shiru ya ɗan yi yana tunanin, shin ya dubata ne? Ko dai ya barta kawai sai sun isa gida? Dan ko ya ce zai dubata ma, sam babu kayan aiki, babu komai a tattare da su, ga shi kuma cikin jikinta ne ya fita, aiki take bukata na musamman. Daurewa dai ya yi ya kyaleta ba dan ya so ba, bawan Allah yana da tausayi sosai. Mikewa Lion ya yi ya nufi cikin dajin, dan ya duba ya wajen yake, bayan ya karɓi Jacket ɗin dake jikin Aseef. Shi kuma Areef ya fara ƙoƙarin tattare kansu, dan su tafi, ya yayyafawa Mark ma ruwa, bayan ya farfaɗo, sai ya saɓesa a saman kafaɗarsa, kasancewar ya sami karaya a kafar tasa, da haka suka mike suka fara tafiya, Lion kuma ya shige cikin daji, Areef ya ce su je Lion ɗin zai samesu a gaba ai, ya san halinsa sarai, ga sauri a wajen tafiya, zai yi saurin cin masu. Haka suka cigaba da tafiya, Lion bai sake haɗuwa da su ba har sai da rana ta kusa faɗuwa, a can gaba da nisa sosai ya cin masu, ya wanke jikin dake jikinsa, ya wanke face nasa sosai, ya yi salloli dake a kansa da sauran abubuwa, ya saki dark black cuirly hair nan nasa, ga shin ma yanzu ta kara tsawo sosai, ya jima bai rage tsawonta ba. Ya sha ruwan mamaki yanda ya rinƙa ganin zanen face nasa a wannan daji, abin ya yi matuƙar burge shi, wani irin azababben kaunar Meeshantasa ya kara ji a ransa, burinsa kawai ya je gida ya ganta, yana tsananin kewarta, ji yake yi kamar a kan kaya yake da bata nan a kusa da shi, baiwar Allah, duk ta bi ta zane face nasa abinta, ba shi kaɗai ya yi mamaki ba, har da sauran abokan tafiyar tasa, kowa ya yi matuƙar mamaki na ganin zanensa a jikin itatuwan dake a dajin, ga zanen ya fito ɓaro ɓaro gwanin birgewa, kamar ka kira shi ya amsa, sai dai babu wanda ya yi gigin yi mashi magana a kan zanen, ko Areef bai yi mashi maganar ba, dan bai ga fuska ba, ya bari sai sun je gida, idan suka huta zai yi mashi tsiya a kan zanukan, sojojinsa sai kallon zanen suke yi suna satar kallonsa, Meesha ta ja mashi, Allah ma yasa sojojin kwara biyu ne kawai suka gani, sai Mark wanda already ya san komai. A haka suka kwashe kwanaki suna tafiya a cikin wannan dajin, banda ƴaƴan itatuwa babu wani abin da suke ci. Da kyar suka iya kaiwa cikin wani ɗan ƙaramin kauye dake kusa da dajin. Tun da suka sako kafafuwansu a cikin wannan kauye, kowa dake cikin kauyen ya zuba masu idanu, sai kallonsu suke yi tamkar sun ga bakin halittu daga wata duniya ta daban, su kuwa ko kallon mutanen kauyen basu yi ba, suka cigaba da tafiya a galabaice. Duk cikinsu babu mai ko raina biyar, haka suka cigaba da tafiya har suka fito cikin babban gari. Kai tsaye shagon sai da wayoyi Lion ya fara nufa, dan already dama basu zo da wayoyinsu ba, sun barosu kashe a gida. Sai ya ce su Areef ɗin zauna su jirasa, kada su bisa wahalar zata yi yawa, bari shi ya je, daga baya zai zo ya ɗaukesu. Abin hawa ya tara, wato mai mashi, ya hau ya ce da mai mashin ɗin ya kai shi katafaren shop na sai da wayoyi, su kuma suka zauna a wajen wani babban masallacin suna jiransa. Sun yi tafiya mai nisa kafin su kai challenge, wani kasuwar waya ce a cikin Ilorin state ɗin. A tare da mai mashin ɗin suka shiga cikin wani katafaren shagon sai da wayoyi. Kun san yarabawa da shegen son kyawawan kuma fararen mutane, sai kallon shi suke yi kamar zasu cinye shi, haushi tamkar ya kwakwale masu idanu yake ji, dan ya tsani kallon nan da suke yi mashi. Amma ba yadda zai yi, dole ya yi abin da yake a gabansa kawai. Yana zuwa ya zaɓi irin wayar da yake da bukata, sannan ya tambayi mai shagon suna karɓar transfer? E guy ɗin ya amsa mashi, da yake katafaren shago ne, akwai yaran gida dayawa a ciki, idan ka zo sayan abu, to za'a sami ɗaya daga cikin yaran shagon ya kula da kai, ainahin Managernsu kuma yana zaune a ciki, gabansa da tarin computers. Tambayarsa Lion ɗin ya yi a kan zai tura masu 2 million Naira, sai su ɗauki kuɗin wayarsu, su bashi sauran kuɗin, sun yarda za su karɓar?. Kasancewar babban shop ne, akwai kuɗi sosai a ciki, sai Manager ya ce ba damuwa ya tura kuɗin. Kum san eƴamurai da bala'in son kuɗi, da kuma daraja costumers, sun iya business over, to shagon na eƴamuri ne bana yarabawa ba, shiyasa suka yarda cikin aminci. Shi ma Lion ɗin cikin mutunci ya ce da guy ɗin da ya yi attending ɗin nasa, ya ɗan ara mashi wayarsa na minti biyar bari ya yi kira. Kun sansu akwai daraja costumers, dan haka ba musu guy ɗin ya ara mashi wayar. Karɓa ya yi, number Imran ya saka ya kira, dan ya haddace number a kansa, sama da shekarun 8 suna a tare da Imran ɗin, kunga kuwa dole ya haddace numbersa, bare ma shi da yake da kaifin kwakwalwa sosai, duk wata number da take a wayarsa idan ka tambayesa zai zayyano maka ita. Bugu ɗaya Imran ɗin ya ɗauka, a tsananin kasale ya ce da Imran ɗin zai turo mashi wata account number ya saka mashi 2m a ciki yanzu. Jin muryarsa yasa Imran ɗin bai san time ɗin da ya miƙe tsaye zubur ba, a hanzarce ya fara tambayarsa suna lafiya? A ina suke yanzu? Kuma yaushe za su dawo?. Cikin ƙaguwa ya rinƙa jefo mashi tambayoyi. Kasancewar a galabaice over yake, sai kawai ya katse kiran, dan ba zai iya biyewa Imran ɗin ya tsaya amsa mashi tambayoyin ba. Yana katse kiran ya ce da guy ɗin ya bashi account number shop ɗin nasu. A hanzarce ya kira mashi, ya yi typing ya turawa Imran ɗin. Ko minti biyu ba'ayi ba sai ga kuɗin Imran ɗin ya turo. A takaice haka suka gama ya biyasu kuɗin wayar ya karɓi saura chanjinsa, daga nan ya tambayi mai mashin ɗin ina hotel nasu mai tsananin kyau take. Mai mashin da kuɗi yake so, sai ya ce su je ya kai shi, ba ɓata lokaci suka nufi hotel ɗin. Katafaren hotel ne mai matukar kyau da kawatuwa, sai da suka tsaya a hanya ya sayi kayan sakawa a wani katafaren super market, sannan suka karisa hotel ɗin. Duk rana ɗaya ra'ina dubu ɗari biyu za su biya kowani ɗaki ɗaya. Ɗaki biyar ya kama masu, 1 million a rana kenan, Imran ya sake kira da number ɗaya daga cikin ma'aikatan wajen, sannan ya saka shi ya tura masu kuɗin ɗakunan. Daga nan ya karɓi keyas dan ya shiga ciki, mai mashin ɗin zai tafi, sai ya ce a'a ya jira shi bari ya zo zasu koma wajen da su Areef suke a tare, daga nan sai ya sallame shi. Okey mai mashin ɗin ya amsa mashi. Sama wajen ɗakunan da ya kama ya nufa, ɗaki ɗaya ya zaɓa ya buɗe ya shiga. Ɗaki ne aljannar duniya, tamkar ɗakinsa na gidan nasa na Kaduna, haka ɗakin take, sai tashin kamshi air freshener mai daɗi take yi, komai very clear. Wayar da ya saya ya sanya a charji kasancewar da akwai wutar nepa, yana so ya yi charjinta dan ya saka sim card ya kira his excellence a turo masu jirgi su bar garin nan. A hanzarce ya yi wanka, sannan ya shirya sosai cikin ƴan mintocin da basu fi 30 ba, ya fito suka tafi da mai mashin ɗin, dan ya je ya taho da su Areef. A hanya sai da ya tsaya ya saya masu ruwar roba mai bala'in sanyi da yawa, dan yasan suna jin kishin ruwa. Ganin yanda yake pacaka da kuɗi ba karamin mamaki ya bawa mai mashin ɗin ba, kasancewar shi ba wani sanin kan kuɗin Naija ya yi ba, ida zai sayi abu, ɗibar kuɗin kawai yake yi ya basu, ko sun bashi canji kuma baya karɓa, ko kallon canjin ma baya yi, hakan ce ta yi mugu mugun bawa mai mashin ɗin mamaki, duk da ya gan shi Bature jajir da shi, amma dole ya sha mamaki, dan akwai Turawa mazauna Nigeria sosai, so a tunaninsa irinsu ne, bai san Lion kam wannan karon ce zuwansa Naija ta farko ba, sai kuma ya haɗu da jarabawa, in ba haka ba ai before bai ma san Naija ba, bare kuma ya san ya take ko ya kuɗinta yake da sauransu! Shi ne yasa yake kashe kuɗin tamkar bai san ta yaya ake nemosu ba. Kai tsaye wajensu Aseef ɗin mai mashin ɗin ya mayar da shi, shi kansa mai mashin ɗin sai satar kallonsa ta cikin mirror gaban mashin ɗin yake yi, saboda ba karya Lion fa duk wanda ya gan shi, in ma mace ko na miji, to sai ya saki baki ya yi ta kallon shi babu gajiyawa, saboda tsananin kyan da Allah ya yi mashi! Ga uban farinjini da kwarjini, bugu da kari ga waɗan nan dara daran idanuwan nasa masu rikitar da mutun idan ya kallesu. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E17 Date: 27/4/2024 Kamar yanda ya baro su Areef ɗin, haka ya dawo ya samesu. Ruwan ya fara basu, a hanzarce suka karɓa, Areef shi kaɗai sai da ya shanye roba biyu na ruwan, sannan ya kama mayar da numfashi, shi ma Aseef roba biyu ya sha, Akila rabin roba, Dr Salman ya shanye sauran rabin nata, sojojin Lion guda biyun nan kowannansu sai da ya sha roba ɗaya da rabi rabi, shi ma Mark roba biyu ya sha. Daga haka Lion ya ce su tashi su karisa hotel ɗin, daga nan su yi wanka su huta kafin ya kira His excellence. Ya kai karshen maganarsa tare da juyawa ya hau bayan mashin ɗin da suka zo, sanna ya ce da mai mashin ɗin ya tara masu taxi su hau, ba musu ya tara masu taxi guda biyu, da yake a bakin babban hanya suke, sai aka yi saurin samun taxi ɗin. Rayuwa kenan, ba ta yanda bata juyawa mutun, wai yau TRIPLETS ne da shiga taxi? Idan ba ƙaddara ba, babu abin da zai kawo su Naija ma da kanta bare har wata Ilorin state, amma da yake kana naka Allah na nashi, sai ga su har ma Daular Mutuwa ba iya Naija kawai ba. Haka suka shiga taxi ɗin, Mark da sojojin nan taxi ɗaya, Areef da Akila da Ayla suka shiga ɗayar taxi ɗin a gidan baya, Aseef kuma ya shiga gidan gaba na taxi ɗin su Areef, Dr Salman ya shiga gidan gaba na taxi ɗin su Mark, haka suka kama hanya. Gaba mai mashin ɗin Lion ya yi, masu taxi ɗin suka rufa mashi baya, bayan su Areef ɗin sun gama shiga kenan, har lokacin Areef ne yake ruke da Ayla baiwar Allah, ko motsawa bata yi ba har izuwa yanzu, ba dan zuciyarta na bugawa ba, to da sai ma su ce rai ya yi halinsa. Suna isa hotel ɗin Lion ya ɗebo makudan kuɗaɗe da a kallah za su kai 200k, ya bawa mai mashin ɗin nasa, shi fa bai san nawa ya bawa mai mashin ɗin ba, dan ko da ya bashi ma sai da ya tambaye shi ya isa haka? Ya biya shi hakkinsa ko dai sai ya kara mashi?. Bawan Allah bai san kan kuɗin Naija ba, mai mashin ɗin da yake yana da tsoron Allah, sai ya ce "Sir this money is too much, is pass my, I think this money pass 200k, my own money is only 5k, so I will going to carry my own and return the remaining change to you". Ya kai karshen maganar yana ƙoƙarin cire 5k nasa. A takaice Lion ɗin ya ce mashi kada ya damu, ya tafi kawai, dan shi bai ma san 5k a kuɗin Nigeria ya take ba, da ma dai dollars ce, ya santa a ido, ya santa a baki dukka. Kun san yarabawa da iya zuba godiya, ai kuwa wannan mai mashin ɗin yana jin Lion ya ce ya bashi kuɗin, a dubu ɗari ya diro kasa daga saman bashin ɗin nasa, cikin hanzari ya zube gwiwowinsa a kasa a gaban Lion ɗin, nan take ya fara zuba ruwan godiya, adduo'i, tare da zallar ruwan albarka da fatan alkhairi. Ko sannu Lion ɗin bai sake ce mashi ba, ya wuce ya je ya bawa masu taxi ma makudan kuɗaɗe da a kallah za su kai 100k ke. Haka suma suka fito daga cikin taxi ɗin tare da zube gwiwowinsu a kasa, suka hau engine zuba godiya. Sam bai kula su ba, bai ma bi ta kansu ba ya sa kai ya wuce cikin hotel ɗin, Areef ya ɗauko Mark ya rufa mashi baya, shi kuma Aseef yana ɗauke da Ayla, haka suka shige ciki, suka bar masu taxi zube a saman gwiwowinsu suna zuba godiya. Suna shiga Lion ya wuce bedroom nasa abinsa. Da Ayla da Akila bedroom ɗaya, Aseef da Areef bedroom ɗaya, Dr Salman shi kaɗai, su kuma sojoji da Mark nasu ɗaya. Haka suka kasa ɗakunan nasu, amma fa sun sha gwagwarmaya wajen diramar Aseef, dan ya ce babu mai raba shi da Heartbeat nasa, a tare za su kwana, Areef kuma saboda mugunta, saboda shi matarsa bata kusa, sai ya kafe a kan lallai Akila da Ayla za'a barta, dan ciwon ƴa mace ta ƴa macece, dan haka Akila zata kuka da Ayla. Kuka sosai Aseef ɗin ya rinƙa zuba masu, amma suka ki kula shi. Daga karshe dai sai ya hakura ya wuce bedroom nasu shi da Areef ɗin. Lion yana shiga cikin bedroom nasa, wanka ya sake yi, saboda tsananin zafi da rana da ake narkawa. Bayan ya shirya cikin ɗaya daga cikin kayan da ya saya, sai ya ɗebi baya kala biyu ya kaiwa su Aseef ɗakinsu, sannan ya wuce ya fita daga hotel ɗin. Su kuwa, wanka suka yi, kowa ya tsabtace jikinsa, suka sanya kayan da Lion ɗin ya kawo masu. Suna gama shiri sai ga masu karɓar order abinci sun shigo. Kasancewar su sun saba cin abincin Naija, sun ci shi a wajen Rimsha, sai suka bada order fried rice, and pepper chickens, sai ruwa da Maltina. Mai karɓar order ya amsa da okey sannan ya fita, yana fita ya faɗa ɗakinsu Mark, bayin Allah su basu taɓa cin abincin Naija ba, amma a yau basu da zaɓin da ya wuce dole su ci, kada yuwa ta illatar da su, haka suka bada order pepper cikin, dan suka ganin kamar shi ne zai fi masu. A ɓangaren Akila kuwa, order jolof rice and chips ta bada. Haka mai karɓar order ya tattara kan order tasu ya koma abinsa. Cikin ƙanƙanin lokaci ya kawo masu duk abin da suka saka order. Dukkansu babu daɗi bakunasu, amma haka suka daure suka tsakuri abincin, dan kada yunwa ta kayar da su. After some minutes, Areef ne ya fito daga bedroom nasu, ɗakinsu Akila ya shiga bakinsa ɗauke da sallama, da yake shi ya fisu tausayi, Ayla tana a cikin ransa, yana ta tunanin halin da take a ciki, ya kasa samun sukuni, burinsa kawai ya zo ya dubata, ya kuma sa Lion ya nemo likitar da zai bata taimakon gaggawa da zai taimaki rayuwarta kada ta mutu kafin su karisa gida. Kamar yanda ya kwantar da ita, haka ya shigo ya sameta. Yana shigowa bai kai ga karisawa cikin bedroom ɗin ba, Aseef ya shigo shima bakinsa ɗauke da sallama, hannunsa ruke da wata jibgegiyar leda da Lion ya sayowa su Akilar kayan sakawa a ciki. A bakin bed ɗin dukkansu biyu suka zauna, Areef ya kai hannu ya taɓa Ayla, dan ya ji har yanzu akwai sauran rai a jikinta ne. Shi kuma Aseef ya miƙawa Akila ledar kayan yana faɗin "Yanzu Lion ya dawo ya kawo maku, ya ce ku shirya da wuri, helicopter zata zo ta ɗauke mu zuwa gida". Ya kai karshen maganar tare da miƙa mata ledar. Karɓa ta yi tare da fara buɗe kayan, Abays ne a ciki, sai takalma. "Heartbeat zaki iya yi wa matar uncle wanka idan na kai maki ita cikin toilet?". Cewar Areef. Da sauri ta gyaɗa mashi kai alamar e zata iya, dan tun ɗazun take yi wa Ayalar kuka, Allah sarki, ba shakka Akila tana da tsananin tausayi kamar Areef ɗin, halinsu kusan ɗaya, dukkansu, kuma babu in da suka baro daddyn Rimsha a kamannin hali, kunga shi ma duk abin da ƴan uwansa suka yi mashi a duniyar nan bai sa ya ji cewa ba zai iya taimaka masu ba, to haka Areef da Akilar ma suke, shi Aseef yana da zuciya gaskiya, idan ka yi mashi abu ya taɓa mashi zuciya, to yana wahala ya mance da wannan abin, kuma shi ruwa biyu ne, wani lokaci yana da zafi sosai, wani lokaci kuma yana da sanyi, kun tuna time da suke Washington? Har su Uncle T bai kyale ba, to haka yake, idan ka yi mashi laifi, to ba zai yafe ba sai ya rama, ko kuma ya fita harkarka, ya zubaka a kwandon shara, shi kuma Lion ai ba wata zancen fita harka, hukunci zai baka mai kyau, daga nan kuma shikenan komai zai wuce, bashi da riko kamar Aseef. Ɗaukar Aylar Areef ɗin ya yi ya kaita cikin toilet ɗin, already Akila ta haɗa ruwa mai zafi a cikin jacuzzi, yana zuwa ya sanyata a cikin jacuzzin, sannan ya fito ya fice daga ɗakinma gabaɗaya. Yana fita wajen Lion ya nufa. Bakinsa ɗauke da sallama ya shiga bedroom ɗin, Lion ɗin yana zaune a bakin bed nasa yana aikin latsa waya. Kusa da shi ya zo ya zauna yana faɗin "Ka yi magana da su momma ne?". Bai amsa ba, kuma bai ɗago ba, ya cigaba da abin da yake yi na tsawon lokaci, kafin nan ya ɗago kansa tare da kai kallonsa a kan Areef ɗin. "Where is your phone?". Yana gida ya bashi amsa. Shiru ya ɗan sake shi kafin ya ce "A wajen waye wayar take? Momma or your wife?". Girgiza kai ya yi yana faɗin "In my room, kuma switch off nata ma na yi". Okey ya amsa mashi da shi, sannan ya mayar da hankalinsa a kan wayar tasa, tun ɗazun number Rimsha yake kira, amma taki ɗauka, hasalima wayar tana a cikin bedroom nasa, ita kuma tana tare da Brr Naurat, dan taki yarda kowa a gidan ya taɓata sai Brr Naurat, ƙwaƙwalwarta sai kara birkice masu yake yi, abu kamar wasa yana neman ya zama babbar case, sam yanzu ta dai'na magana ma, idan ka tambayeta abu, sai dai ta zuba maka idanu kawai taka kallonka, Allah mai iko yau harta daddynta da mummynta bata sansu ba, abin ya yi mugun ɗaga masu hankali ba kaɗan ba, sun shiga damuwa na wuce misali, dan ma Brr Naurat tana kwanta masu da hankali ne, da abin sai ya fi haka, a takaice dai Rimsha bata leƙawa ko palo, ko da yaushe tana kwance a saman bed ɗin Brr Naurat, wanka ma Brr Naurat ɗin ce take yi mata, yanzu ta zama tamkar jaririya, wanka ma bata iya ba, in short ba wani abin da Rimsha ta iya a yanzu, common abinci Brr Naurat ce take bata a baki, duk taurin zuciya irin ta Jehan, sai da ta zubarwa da kanwar tata kwallah ba kaɗan ba, ta sha kuka sosai, saboda Rimsha dai ita kaɗai ke gareta, ita ce kawai kanwarta, duk wannan dirama da suke yi suna tsananin kaunar junansu na wuce misali, kawai Jehan ɗin ce dama da shegen iya tsare gida yasa Rimshar bata kusantar ta sosai, amma suna kaunar juna over. Lion ya kira wayarta har ya gaji ya hakura. Hakika yana son yin magana da ita, saboda a jikinsa yana jin cewa bata da lafiya, ba lafiya take ba, dan duk lokacin da ya tuna sunanta, sai zuciyarsa ta harba, abin ya ɗan ɗaga mashi hankali, hakance ma tasa ya ce da His excellence ya sanya a turo masu jirgin helicopter kawai su koma gida da wuri, sannan da akwai abubuwansu da suka bari a airport na Enugu state, dan haka his excellence yasa ya mayar masu da shi gida. Burinsa kawai ya koma gida, da gwaggo da Rimsha sun tsaya mashi a cikin tunaninsa fiye da tunanin mai tunani. A ɓangaren su Akila kuwa, Areef yana fita daga toilet ɗin Aylar ta farfaɗo, saboda ruwa da aka sanyata a ciki. Tana farfaɗowa ta fara zuba kuka babu kakkautawa, rarrashinta Akilar ta rinƙa yi, amma taki ta yi shiru, hakan tasa Akilar ta kyaleta ta yi mata wankar kawai, bayan ta gama ta tallafa mata ta fito, sannan ta ɗaura mata towel daga kirjinta, da kyar Aylar take iya jan kafarta har suka fito izuwa cikin bedroom ɗin. Ko da suka fito basu sami Aseef a ɗakin ba, ya fice abinsa. A bakin bed ta zaunar da Aylar, ta ciro kayan da Lion ya saya masu, tare da tallafa mata ta sanya a jikinta, sannan ita ma ta wuce toilet ɗin dan ta je ta yi nata wankar. Baiwar Allah Ayla, har kumbura face nata ya yi, ta yi wani iri da ita, gwanin ban tausayi. A takaice dai sai misalin karfe 3 na yamma, sannan jirgin helicopter ya iso, basu ɓata lokaci ba wajen tafiya, Ayla dai sai ruwan hawaye take yi, cikinta tsananin ciwo yake yi mata, baiwar Allah bata taɓa jin azaba irin haka ba, dan cikin nata ba ƙaramin ciwo yake yi mata ba, shiyasa ma ta kasa daurewa har take kuka. Areef bawan Allah shi ya yi ta fama da ita, ya yi ta rarrashinta har suka dira a cikin Kaduna. Already su Imran suna airport suna jiransu. Basu ɓata lokaci ba suka fito suka nufi gida, dan akwai majinyata sosai a tattare da su, shi kansa Lion ɗin kamata ya yi ace yana kwance a gadon asibiti, amma saboda dakiya da taurin zuciya tare da karfin imani, yasa ya dake, ya ki yarda ma kowa ya duba shi, ya ce sai ya dawo gida kawai. Gabaɗaya family suna tsaye a harabar gidan suna jiran isowarsu, Rimsha, Jehan, Anaya, su ne kawai basu a cikinsu, suna ɗaki suna barci, Jehan da Anaya sun ci kuka sun ƙoshi ne har barci ya yi awon gaba da su, ita kuma Rimsha already kun san matsalar da take a ciki, an yi mata ruƙiya ma, amma shiru, farko sun ɗauka aljanu ne suka shafeta, sai da aka yi ta yin ruƙiya aka ji shirune yasa suka fahimci ba aljanu bane, wata matsala ce dai ta daban, dan haka sai suka kyaleta sai Lion ɗin ya dawo, dan sun san halinsa, kada su kira malami ko a kaita wajen magani ya dawo ya sauke masu kwandon aradu a kansu, dan ba ƙaramin aikinsa bane ya ce uban waye ya ce a taɓa mashi matarsa? Waye ya ce wani ko wata ya zo ya dubata? To gudun kwandon bala'insa ne yasa suka bar mashi kayarsa, ya zo ya san yanda zai yi da ita. Suna dira a gida, Lion ne farkon da ya fara fita daga cikin motar, tun motar bata gama tsayawa a parking space bama ya fice abinsa. Sam bai bi ta kan kowa dake tsaye a wajen ba, cikin gida ya wuce abinsa, kai tsaye bedroom nasa ya wuce. Yana shiga ya nufi toilet, wanka ya yi a gurguje, sannan ya fito ya shirya cikin three cuter sky blue da singlet, singlet ɗin fara ce tas, tamkar yanzu ya cirota daga ledarta, abin da ya sanya ya saka singlet ɗin kuma, saboda ciwukan dake a kirjinsa. A box ya ɗauko tare da zama a gefen bed nasa, dan hannunsa in da wuka ta yankar nan ba ƙaramar ciwo take yi mashi ba, hannun ta kumbura, kun san wuka da akwai dafi a jikinta, hakance tasa hannun ta kumbura sosai. Family kuwa, cikin tsananin murna suka fara rungumar juna, kowa baki ya ki rufuwa, saboda tsantsar farinciki. Areef yana ɗauke da Ayla a saman kafaɗarsa, bai wani tsaya a wajensu ba, sai ya wuce izuwa cikin gida kawai, dan ya kwantar da ita, ta huta. Gabaɗaya family sun sha matukar mamakin ganin Aseef a tare da su, sai dai kuma sun kasa iya tambayarsa ya aka yi hakan? Ga tambayar a cikin ransu, amma ta kasa fitowa fili, abin ya ɗaure masu kai, amma haka suka hakura suka daure. Sai rungumar Dr Salman suke yi tamkar za su mayar da shi cikinsu, Brr Naurat har da ruwan hawaye, sai tsiya su Imran suke yi mata. Shi ma Dr Salman ɗin ya sha kuka ba kaɗan ba, dan bai taɓa tunanin familynsa suna a raye ba, ya yi zaton komai ya kare ya lalace masu, ashe dai sunanan, sun zama taurari zakarun gwajin dafi ma a cikin al'umma, wannan abin ya yi mugun sanya shi farinciki wanda baki ba zai iya furtata ba. Haƙiƙa farincikin da wannan family suke ciki a yau, sam baki ba zai iya furtata ba, ya wuce misali. Haka Dr Salman ya rinƙa yin kuka yana faɗin kowa ya yafe mashi, ina Nawazuddeen ɗinsa? Dan Allah Nawazuddeen ya yafe mashi. Anyi anyi ya yi shiru yaki yi, ya ce har sai Nawazuddeen ya yafe mashi. Haka daddyn Rimsha ya rungume shi yana faɗin. "Daddy ni baka yi mani laifin komai ba, idan ma kayi, to ni na yafe maka, ban taɓa ji a ra'ina kamar ka taɓa yi mani laifi ba, kullum cikin yi maka addu'a da fatan alkhairi nake yi, dan Allah ka dai'na kukannan kada ka saka muma muyi kukan". Sosai Dr Salman ɗin ya rubgume shi yana mai cigaba da matsar kwallah. Da kyar suka samu suka lallaɓa shi ya yi shiru, a tare suka rankaya izuwa cikin gida, kai tsaye bedroom na Lion suka nufa, while shi kuma Areef ya kai Ayla ɗakin gwaggo ya kwantar da ita a kusa da Rimsha, sannan shi ma ya fito izuwa bedroom ɗin na Lion ɗin. Lion yana zama a bakin bed ɗin nasa yana ƙoƙarin fara duba hannunsa, sai ga family gabaɗaya sun shigo cikin ɗakin, duk sun biyoshi, gabaɗaya fuskokinsu ɗauke yake da tsantsan annuri da farinciki, yau Dr Salman ya dawo cikinsu, ga shi ba su rasa ko mutun ɗaya ba a cikin ƴaƴan nasu, abin ba karamar daɗi ta yi masu ba. Sun shigo ne dan su duba lafiyar Lion ɗin, dan kunga shi bai tsaya a wajen nasu ba, suna sauka ya wucu bedroom nasa kawai. Kallo ɗaya Lion ɗin ya yi masu ya kawar da kallonsa gefe guda, ya cigaba da aikin da yake yi. Ganin abin da yake ƙoƙarin yi na yiwa kansa magani ne yasa gwaggo da Areef suka kariso kusa da shi da sauri. A tare suka zauna a gefe da fefensa, suka sanya shi a tsakiya kenan. Gwaggo ce ta fara karɓar A box ɗin tare da kama hannunsan tana dubawa, ba shakka ya ji ciwo sosai. A hankali ta ɗago da kallonta a kansa, hannu ta kai ta shafa lallausan kumatunsa kafin ta ce "Let me do something". Shiru ya yi bai yi mata magana ba, ya dai zuba mata idanu, shi ya mance da cewa ita ma babbar likita ce kamar daddynsu, sai da ta ce bari ta yi mashi wani abin ne yasa ya tuna ashe ita ma babbar likita ce sosai, dan haka sai ya miƙa mata hannun ya bita da idanu kawai. Cikin ƙanƙanin lokaci ta fara yi mashi aiki, duk wani magani da zata zuba mashi sai ta ɗago kai ta ce mashi sannu, dan tasan da akwai bala'in zafi ba kaɗan ba, bare kuma yanda hannun ta ɗauki lokaci, ta jiƙa sosai ciwon, dole zai sha zafi, sai dai kuma shi wayarsa ma ya ɗauko yana latsawa da hannu ɗaya, a cewarsa duk zafinta bata kai harbin bullet zafi ba, dan haka shi bai ga abin cewa da zafi a nan ba. Haka gwaggo ta yi mashi treatment na wajen da kyau da kyau, sannan ta ce ya kwanta bari ta duba lafiyar jikinsa gabaɗaya. Sai sannu family suke yi mashi, sam bai ɗaga idanu ya kalli ko mutun ɗaya daga cikinsu ba, dan yana cikin wani irin yanayi wanda shi kaɗai yasan me yake ji bawan Allah, da yake shi kullum a siffa ɗaya yake ne yasa sam sam ba wanda ya gane cewa yana cikin tsananin damuwa, kullum face nasa a haɗe take, baka gane farincikinsa bare bakin ciki, harta TRIPLETS nasa ma basu iya rabe yana cikin farinciki ko bakin ciki, saboda kullum dai yanda yake a haka yake babu canji. Bai yi wa gwaggo musu ba, ya miƙe ya kwanta a saman bed ɗin da kyau, dan a agajiye sosai yake. Duba lafiyar jikinsa ta fara yi ita da Areef, ya rufe idanuwansa yana tunanin duniya. "Momma where is Meesha?". Kamar daga sama su gwaggo suka ji sanyayyar muryarsa ya gefo masu wannan tambayar, ya yita kuma idanuwansa a lumshe. Kallon kallo jama'ar cikin bedroom ɗin suka fara yi, ita kanta gwaggon sai da gabanta ya faɗi na jin tambayar nan tasa. Ganin yanda suke kallon kallo a tsakaninsu ne yasa Aseef da Areef har suna haɗa baki wajen cewa "What is happening? Where is our Rimsha? Ya naga kuna ta kallon juna, is there any problem?". Kamar abin haɗin baki suka jera masu tambayoyin, Areef kam har da mikewa tsaye yana binsu da kallo, dan wlh idan wani abin ne ya sameta yau za'ayi yaki ba kaɗan ba, saboda ita ɗin tamkar bugawar zuciyar TRIPLETS ɗin take, dukkansu ukun suna tsananin sonta fiye da tunanin mai tunani, akwaita da mugu mugun shiga rai na wuce misali ne. Kara datse idanuwansa gam Lion ɗin ya yi, kansa na yi mashi ciwo sosai, yana jin duk abin da suke faɗa, amma ya kasa buɗe idanuwansa, dan ƙwaƙwalwarsa ba zata iya ɗaukar wani abin ya sami Rimsha ba, shiyasa ma ba zai buɗe idanu ba bare ya ga fuskokin family su kara jefa shi cikin wani raɗaɗin. "Areef nothing happened to her, just she is not feeling well, tana ma cikin bedroomna tana kwance, she is sleeping now". Cewar gwaggon kenan. Kusan a tare Aseef da Areef ɗin suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya, da sauri Aseef ya ce bari ya je ya ganta ya tabbatar. A tare suka fita da Areef ɗin dan su je su dubata. Ita kuma gwaggo, sai ta cigaba da duba ɗan nata, Dr Salman ne ya ce su fita su bar Lion ɗin ya huta, dan ya gaji matuƙa. Haka kuwa aka yi, duk suka fita, ita ma gwaggon da ta gama yi mashi duk abin da ya dace, sai ta fita ta kyale shi, yana jin fitarta, amma bai ce mata komai ba, saboda yana da bukatar ya huta ɗin ne, ga salloli na la'asar da mangariba a kansa bai samu ya yi ba. Ransa cike da tunani barci ya yi awon gaba da shi, bawan Allah ya yi matuƙar gajiya na wuce misali, dole ne ma barci ta ɗauke shi. A ɓangaren Aseef da Areef kuwa, da suka je suka tabbatar yes Rimsha tana nan tana zuba barci, sai suka ji wani irin sanyi da salama ya lulluɓesu. Hakan tasa suka zauna a bakin bed ɗin na gwaggon suna ɗan tattaunawa a tsakaninsu. A gabaɗaya cikin family an rasa wanda zai iya tambayar Aseef ya aka yi ya je shi Daular Mutuwa? Ga dai tambayar a cikin ran kowa, amma sun kasa fito da ita fili. To meye dalili? Alƙalamin PRINCESS TEEMA ce kawai zai iya rubuta maku dalilai, dan haka ku biyoni!! A nan family suka shigo suka samesu. Da mamaki ɗauke a fuskar gwaggo take tambayar Areef ɗin me ya sami Ayla kuma?. Kallon daddyn Jelly Areef ɗin ya yi tare da miƙewa tsaye, cike da tausayi ya ce "Sorry uncle, ta yi loosing pregnant nata ne, momma ki bata taimakon gaggawa, dan babu abin da muka yi mata, babu wani drugs or injection da yake a tare da mu, so tana cikin mawuyacin halin, help her". Ya kai karshen maganar tare da sa kai ya fice daga ɗakin, a lokacin ita ma Jehan ita da Anaya duk suna bedroom nasu suna barci, sun ci kuka ne sun ƙoshi, har barcin wahala ta yi awon gaba da su bayin Allah. Haƙiƙa gwaggo ta tausayawa Aylar na ganin halin da take a ciki, dan haka sai ta ce Aseef ya kawo mata kayan aikinsu bari ta dubata, daga nan kuma ta yi wa daddyn Jelly ban hakuri. Kowa daga cikinsu Abba sai da ya bashi hakuri. Ba shakka ya ji zafin fitar cikin na Ayla, dan yana tsananin son yara, Jelly kaɗai gare shi, ita ma ta yi aure, so yana tsananin kaunar yaga ya sake samun yara, amma kuma farincikin dawowar Aylar ta fi yawa a cikin zuciyarsa sama da zubewar cikin, kuma shi dama mutun ne mai yarda da ƙaddara, dan haka ya yarda da ƙaddararsa, ya kuma rungumeta hannu bibbiyu, ya ce babu komai, haka Allah ya ƙaddara, dama ai ba su suka bawa kansu cikin ba, Allah ne ya basu, dan ya karɓi abinsa ba zasu ji babu dadi ba, shi ya godewa Allah ma da yasa ta dawo gida da ranta, iya wannan ma ya ishe shi murna, kuma dole ya godewa Allah da yadawo mashi da ita da ranta. Da haka Brr Naurat ta ce kowa ya je ya yi sallar issha, tun ɗazun aka yi sallah su suna nan suna zaune. Haka suka watse kowa ya nufi bedroom nasa, dan su je su yi sallah, Dr Salman kuma suka tafi tare da Akil, ita kuma gwaggo Aseef ya kawo mata kayan aiki ta fara duba lafiyar Aylar, dan ta lura sai anyi mata wankin ciki ma. Bayan ta gama sai ta yi mata alluran barci dan ta sami hutu. Daga nan ita ma ta mike ta fita izuwa bedroom nasu Jehan dan ta yi sallah, ta bar Brr Naurat tare da Aylar da Rimshar. Tana shiga bedroom ɗin ta tarar da Areef zaune a saman bedside drawer kusa da Jehan, ya zuba mata idanu yana ta kallonta, ita kuma tana zuba barci, ya yi wanka ya canza kayan jikinsa izuwa na barci, da alama ya yi sallah ya ci abinci. "In tasan maka ita ne Areef?." Cewar gwaggon, ta yi maganar tana nufar hanyar toilet dan ta yi alwala. "A'a momma ki barta, i want to see her ne ma kawai yasa na zo dubata, na yi missed nata over, yau ina gajiye sosai, ba zan iya da rigimarta ba, dan haka kyaleta sai da safe". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa, ko kunyar gwaggon bai ji ba ya ɗan duka ya sumbaci Jehan ɗin a kumatu, sannan ya juya ya fice, ita ma gwaggon ko a jikinta ta shige cikin toilet abinta. After some hours, gabaɗayansu sun yi barci, dan a tsananin gajiye suke, family kowa yana cikin bedroom nasa yana zuba barci, masu aikin dare suna yi, yau suma family za su yi barci a cikin salama, dan tun da TRIPLETS suka tafi basu samun barci mai kyau, a kaikaice suke yin barcin, to yau za su sami barci mai cike da daɗi. Misalin karfe biyu yunwa ta farkar da Jehan, dan bata ci abincin dare ba ta yi barci, fitowa ta yi izuwa palon kasa, abinci ta ɗebo a plate, sam bata da labarin mijin nata ya dawo, komawa palon sama ta yi ta zauna a saman sofa, cikin nutsuwa ta fara cin abincinta tana yamutse fuska tamkar mai cin magani, ita kuwa Anaya sai zuba barci take yi, ita bata farka ba. Kamar daga sama ta ga Lion ya fito daga cikin bedroom nasa sanye da farar jallabiya a jikinsa, sai yanzu ya samu ya biya bashin sallolin dake a kansa, tun da ya yi barci sai karfe 1 ya farka, wanka ya yi tare da ɗauro alwala ya zo ya fara biyan bashin sallolin dake a kansa, bayan ya kammala ne ya fito dan ya je ɗakin gwaggo wajen Meesha. Ba karamar tsorata Jehan ɗin ta yi da ganinsa ba, da farko ma ta ɗauka aljani ne, saboda dare ne kuma ga shi da farar jallabiya, bugu da kari bata san sun dawo suna gidanba, sannan ya saki dark black cuirly hair nan nasa bai ɗaure ba, ga shi da tsawo sosai dama, ai dole ya bata tsoro. A dubu ɗari ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin kurma ihu, sai gani ta yi ya shige ɗakin gwaggo bai ko kalli in da take bama, hakan yasa ta fahimci lallai sune suka dawo, dan haka sai ta ajiye plate ɗin abincin nata, da sauri ta sauka kasa izuwa bedroom na Areef. Babu ko sallama ta faɗa cikin ɗakin, wani irin duhu ne a cikin ɗakin, kun san shi baya shiri da haske dama, idan zai yi barci a duhu yake yi, hakan tasa bata iya ganin komai, lallaɓawa ta yi a hankali ta nufi wajen switch, da kyar ta gano switch ɗin ta kunna wutar, nan take haske ya gauraye ko'ina a cikin bedroom ɗin. Cike da tsohon abin da zata iya cin karo da shi a saman gadon ta ɗago kanta, a hankali ta kai kallonta wajen. Yana kwance cikin kyawawan kayan barcinsa yana zuba barci abinsa, ya rungumi pillow a kirjinsa, ya kuma ɗaura kafafunsa a saman pillow ɗaya. Wani irin nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke, ta kasa motsawa daga wajen, ta zuba mashi idanu sai kallonsa take yi. Saboda wannan haske da ta kunna mashi ne yasa ya ɗan fara motsawa yana son farkawa, ganin hakan yasa ta yi maza ta kashe wutar tare da juyawa ta fice daga ɗakin da sauri tana hamdala ga Allah. Shi ma Aseef duk rigimarsa na son ya yi dis virgin ɗin Akila, to yau dai ya shafa mata lafiya, dan dukkansu a tsananin gajiye suke, sai barci suke zubawa babu kakkautawa, sun wahala ne over. Jehan na fita ta koma palon saman, abincinta ta ɗauka ta cigaba da ci, tsabar murna na ganin mijin nata, sai ta ji abincin ma ya kara daɗi, haka yasa ta ci sosai ta ƙoshi, tun ranar da suka tafi rabonta da ta ci abinci dayawa haka, bayan ta ƙoshi ne ta ɗaura plate ɗin a saman dining table dake a cikin palon, sannan ta wuce cikin bedroom nasu, yau barcin nishaɗi zata yi, ranta fes mijinta ya dawo. Shi kuma Lion bakinsa ɗauke da sallama ya shiga ɗakin gwaggon. Gwaggo na a saman dadduma tana sallah, Brr Naurat tana kwance saman bed tana barci, ga Rimshar a kusa da ita tana barci. Ɗakin nasu da akawai hasken wuta sky blue. Saman bedside drawer ta ɓangaren da Rimshar ke kwance ya je ya zauna. Hannu ya kai ya ɗan janye bargon da Brr Naurat ta rufa mata. Da kallo ɗaya ya yi mata ya fahimci bata da lafiya, dan ta yi muguwar rama sosai. Shiru ya zuba mata idanu yana tunanin to me yake damunta?. A hankali ta fara motsawa, alamar tana son farkawa, hannu ya kai ya shafi face nata, hakan yasa ta farka mai gabaɗaya. Tana waro idanunta kai tsaye sai cikin nasa idanun. Turo baki ta yi tare da kawar da kallonta tana faɗin "Kai kuma waye? Daga ina da zaka zo ka tashe ni, kuma ka wani tsareni da wasu shegun idanu kamar na wancan mutumin da yake zama a palon kasan nan (Dr William)". Dama kunsan ciwon nata yasa tana ji da bala'in masifa, duk zafin Jehan sai da ta sarara mata, to yanzu ma tana tashi ta hau surfa masifa, ba gaira ba dalili. Da farko Lion ɗin ya zaci magagin barci ne, sai daga baya ya fahimci babu magagin barci a tattare da ita, tana nan normal, hakan yasa ya fahimci wannan shi ne rashin lafiyar da take fama da shi kenan. Ko kaɗan bai ɗaga hankalinsa ba, dan shi ya fahimci menene matsalar tata, dama kuma already ya dawo da nufin ya yaki wancan matsalar, dan haka sai bai damu ba, godiya ga Allah ma ya yi da ya sanya ya dawo ya sameta ba'a dauketa ba, dan haka sai ya riko hannunta ɗaya, kasa kasa ya ce "Zo muje ki rakani to, sai na gaya mani wanene ni da kuma abin da yasa na tsareki da idona". Kallon sama da kasa ta yi mashi kafin ta ce "Ni ka sake mani hannu hai, babu in da zanje, kuma ka bar mana ɗakinmu". Dama kunsan bata yarda kowa ya raɓeta sai Brr Naurat, duk wanda ya zo kusa da ita bala'i ne yake tashi ya tsaya gam, to shima surfa mashi bala'i ta rinƙa yi a kan ya bar masu ɗakinsu. Nisawa ya yi tare da kai ɗan bakinsa ya sumbaci lallausan kumatunta, sannan ya miƙe ya nufi hanyar fita, yana jiyo muryarta tana faɗin "Mugu da zaka wani taɓani, ina ruwanka da ni?". Bai kulata ba ya fice abinsa, duk abin da suke yi gwaggo dake saman dadduma tana jinsu, hakan yasa ta kara tsananta masu addu'a na samun lafiyar Rimshar. Shi kuma Lion yana fita ya koma bedroom nasa, ainahin wayarsa ya ɗauko, ba wanda ya saya a Ilorin ba, na ainahin ya ɗauko tare da kunnata. Duba time ya yi, karfe 2:40am dai'dai. Number his excellence ya kira, wayar ta yi ringin har ta kusa yanka sannan ya ɗaga. A takaice Lion ɗin ya ce mashi "Zan shigo Usa gobe, ina da bukatar lokacinka at least 1 hour, so sai ka shirya". Yana gama faɗar hakan ya katse kiran, duk da ciwon dake a jikinsa, hakan bai hana shi ya tashi ta fara shirin tafiya ba, acewarsa, gara kawai ayita ta kare. Duk wani abin da zai buƙata ya shirya a cikin trolleynsa, sannan ya fito ya nufi bedroom na gwaggo, ita kaɗai ya gayawa zai tafi yanzu ba sai anjuma da safe ba, ta so ta dakatar da shi, ta so ya bari ya huta, amma ya nuna mata yana sauri, dole ne ya isa Washington gobe goben nan, dan haka kawai ta bishi da addu'a. Ko TRIPLETS nasa bai gayawa ba, a cikin wannan dare ya fita daga gidan tare da Donal, a hanyarsu ta zuwa airport ne ya sanar da Donal ɗin cewa zai turo likita dan a ɗaura kafar Mark, so ya kula da shi sosai, bawan Allah ya azabtu matuka, baki ma ba zata iya faɗar azabar da Mark yake a ciki ba, kowa dai yasan yanda karaya take, idan baka taɓa karyewa ba, to an taɓa yi a kusa da kai, tana da matuƙar raɗaɗi na azaba. A takaice dai Lion da private jet nasa ya bar Nigeria, dama tun da su TGA suka zo jirgin tana airport babu wanda ya taɓata, to da yake yanzu tafiya ce ta ujila, sauri yake yi, sai bai tsaya yin booking na jirgin kasuwa sun ɓata mashi lokaci ba, kawai ya yi amfani da nasa. Ya bar Nigeria karfe 4:30 na asuba, sai addu'a gwaggo take zuba mashi sosai da sosai, su kuma TRIPLETS sai barci suke zubawa a tsananin gajiye, basu da labarin Lion ya bar kasar!. Yana dira Washington Tga ya zo ya ɗaukesa, kamar yanda babu wanda ya san ya bar Nigeria sai gwaggo, haka babu wanda ya san ya dira a cikin Washington sai his excellence, ko Tga ma sai da ya kusa sauka ne ya kira shi a kan ya zo airport ya ɗaukesa, so babu wanda ya sani. Kai tsaye gida suka wuce da Tga ɗin, yana zuwa ya yi wanka tare da shiryawa, sannan ya samu ya zauna ya nutsu ya ci abincin mai yawa sosai, tun daren jiya yake jin yunwa, amma wannan matsala ta tsaya mashi a rai da har ta hana shi cin abincin, ji yake yi idan bai dira a cikin Washington ba, to ba zai iya samun sukuni ba, shi ne yasa bai iya zama ya ci abinci a gida Nigeria ba, ya daure sai da ya dawo nan, amma fa ya wahala matuƙa a cikin jirgin, dan ma dai ya yi ta shan Maltina ne. Bayan ya ci abinci ya ɗan huta na ƴan mintoci, sai ya sake shiri tare da sanya face mask a fuskarsa ya fito, Tga ya so ya raka shi, amma ya hana kowa binsa, ya ce shi kaɗai zai tafi, basu da zaɓi, dole su hakura su kyale shi, amma sam basu so hakan ba, sojojin dake jibge a gidan nasu ba ƙaramin mamakin ganinsa suka yi ba, sun jima rabonsu da shi, sun yi kawarsa. Da kansa ya ja mota, bai tsaya ko'ina ba sai white house wajen His excellence. Abu ne da kuka riga da kuka sani, baya neman permission a wajen kowa idan zai ga his excellence, kai tsaye ma yau palon gidan ya nufa, sam bai je fadar shugaban kasa ba, da yake already his excellence ɗin ya san da zuwansa, sai ya bar duk abin da yake yi, ya tashi ya je ya samesa a cikin babbar palon nasa kawai. Sannu da zuwa His excellence ɗin ya yi mashi tare da fara tambayarsa ina su Michael nasa? Dakatar da shi Lion ɗin ya yi, a takaice ya ce mashi "Where is Anderson?" A tsananin razane his excellence ɗin ya ce "Romeo what... What... What are you saying? Anderson is already died you know that... And now.......". Yana magana yana samun sarkewar word. Dakatar da shi Lion ɗin ya yi ta hanyar ɗaga mashi hannu ba tare da ya barshi ya kammala maganarsa ba, ya sake cewa mashi "Uncle i said where is Anderson?." Tashin hankali!. "Romeo i told and you already know that Anderson is d......" Katse shi Lion ɗin ya yi ta hanyar ɗaga mashi hannu a karo na uku tare da miƙewa tsaye. Bai sake cewa da shi komai ba ya nufi waje abinsa. A tsananin firgice his excellence ɗin ya miƙe tsaye, kana ganinsa kaga zallar mara gaskiya, nan take wata zufar wahala da shiga ruɗu ta fara tsastsafo mashi daga gefe da gefen fuskarsa, idanuwansa duk sun raina fata, ya yi wani wiki wiki da shi, duk wata alama ta rashin gaskiya tare da shiga tsananin tashin hankali sun bayyana a tattare da shi, a kiɗime ya nufi saman bene dan ya kai ga isa bedroom nasa. Shi kuma Lion yana fita daga gidan bai zame ko'ina ba sai gidan kanin his excellence ɗin, mai sunan Michael kenan. Yana shiga palon bai sami kowa ba, kai tsaye ya haura sama izuwa bedroom ɗin na kakan nasu, rabonsa da ya taka kafa ya zo wannan gida yau ya kai tsawon shekaru takwas zuwa goma, yanzu ma ko da yazo securityn gidan basu gane shi ba, har sun nemi su ɓata mashi lokaci ta hanyar dakatar da shi, sai da ya cire masu face mask na face na shi sannan suka gane shi, cikin girmamawa suka barshi ya wuce, ya cire masu face mask ɗin ne kuma saboda baya son hayaniya, aikin da ya kawo shi kawai yake da bukatar yi ya fita. Kamar yanda kuka sanine, dukka ilahirin familyn Roshan shahrarrun masu kuɗaɗene ta duniya, duniya na damawa da su, suna da karfin faɗa a ji a duniya bakiɗaya, ko'ina ka je ka ambaci sunansu an sansu, dan haka shima wannan kakan nasu shahrarren biloniya ne ta duniya, tsayawa zayyana maku kyan gidansa ma ba zai yiwu ba, saboda baki ba zata iya zayyana adadin dukiyar familyn Roshan ba, sai daidai kawai ku ƙawata a ranku. Lion yana hayewa sama kai tsaye ya nufi bedroom ɗin na kakan nasu, yana shigowa ya fara jin sautin karar tapi rap, rap, rap, tamkar jiransa ake yi ya shigo dama. Ba kowa ne yake wannan tapi ba face kakan nasa, da alama yasan da zuwan nasa, sam Lion ɗin bai yi mamaki ba, sai ma karisa shigo cikin bedroom ɗin da ya yi ba tare da ya jira an yi mashi izini ba. A bakin katafaren bed na kakan nasa ya zauna tare da zubawa kakan nasa idanu yana yi mashi wani irin kallo wanda babu wani mahaluƙi da ya isa ya fassara ma'anarta sai shi da kansa, kallo ne mai cike da abubuwa da dama a cikinta. Dama daga ganin idanuwan Lion ɗin a halin yanzu kasan da akwai gagarumar abu a kasa. "Romeo' Romeo Romeo' you are so special our Lion, you really try". Cewar kakan nasa. Mai da kallonsa a saman yatsun hannunsa ya yi, sannan ya yi kasa da kansa, cikin sanyin murya ya ce "Why uncle? Why? Why you people did all that to us? Ina cikon TRIPLETS na? What happened to him?" And lastly where's Anderson?". Cike da izza kakan nasa ya fara magana. "Romeo the time is out! And the game is over! Bari ka ji mu bamu ɗauki ɗaya daga cikin TRIPLETS naka haka kawai bisa raɗin kanmu ba, ina son ka sani mahaifiyarku ita ce da kanta ta sadaukar mana da cikonku, ita da kanta ta ɗauke shi ta bayar, meyasa baka tambayeta ba? Ai ita zaku zarga! Mu a tsarin mu bamu amfani da yaron da ba iyayensa ne suka ɗauke shi da kansu suka bamu ba, idan ma mun ɗauki yaron da iyayensa basu bamu ba, to yaron ba zai yi mana amfani ba, dole sai wanda iyayensa suka bamu ne yake yin amfani a wajenmu, kamar yanda William ya gaya maku tun farko na cewa mahaifiyarku ta badaku, to hakan ce gaskiya! Mahaifiyarku ta bada guda ɗaya ne daga cikinku, William ɗin ma bai faɗi dai'dai ba, guda ɗaya ta bada ba dukkanku ba, shi ne yasa Anderson ya ɗauki wanda ta badan, dan haka ka dai'na neman Anderson, dan bashi da laifi, idan kuma kana ganin ba haka bane, ka koma Nigeriar ka je ka tambayi mahaifiyar taka, zata gaya maka ai, kada ka matsa a cikin wannan al'amari, idan ka matsa to ba shakka zaka fara danasanin zuwanka duniya, ka koma wajen mahaifiyarku ta gaya maka gaskiya!!".................... Tashin hankali, wannan wani irin azababben cakwakiya ce? Gwaggo ce da kanta ta sadaukar da cikon TRIPLETS kenan? Kenan kila shiyasa bata yi maganar yaro ɗaya mai blue eyes ɗin ba tun da ta ganesu? Kenan dama tasan baya nan? Meyasa to zata yi hakan? In dai haka ne kenan tana da sa hannu a ciwon Rimsha? To wai meyasa? Menene dukka wannan abin? Wanene shi wannan Anderson ɗin? Abin da ɗaure kai! Ya ake son Lion ya yi da ransa? Kashe shi suke son yi ne? Wannan bala'i ai sai ta sa zuciyarsa ta buga, uwa fa! Ya ilahi ya lillahi. Ni kai'na PRINCESS TEEMA a wannan gaɓar ka'ina ya yi wani mummunar bugawa, zazzaɓi nake ji my peoples 🥺🥲💔 littafin TRIPLETS wan kill me with more cakwakiya and sarkakiyar. HAR WA YAU TAKUCE FATEEMAH ZAHRA MUSA PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA MAI ABIN BAN MAMAKI🤙❤️ ASHA KARATU LAFIYA🥲💔 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E18 Date: 28/4/2024 *Page na yau ban samu na yi editing nasa yanda ya kamata ba, saboda rashin chaji, so zaku iya samun typing errors, amin afuwa.* Nisawa Lion ɗin ya yi ba tare da ya ce komai ba, dan yana tattauna maganganun ne ma tukunnan. "Haƙiƙa babu wasa a wannan al'amari, tun kuna cikin cikinta, tun cikinta yana da wata biyar aduniya ta bayar da ɗa ɗaya daga cikinku, wannan dalilin yasa da aka haifeku muka ɗauki guda ɗayan, wannan zance haka take, kuma duk in da zaka je ka zo hakan ce! Babu makawa kuma babu tantama a cikinta, muna da shaidu a kan hakan, na san dama zaka zo, zaka zo garemu Romeo, saboda tun da ka fara girma muka fahimci ka ci sunanka da WILLIAM ya sanya maka wato Lion, so our Lion already we know that you're special! Hakan yasa muka ajiye maka tarin hujjoji da zaka gansu a aikace, sai dai bamu yi tunanin zaka zo garemu da wuri haka ba, bamu yi tunanin zaka gane mu da wuri haka ba, anywhere mu bamu cutar da ku ba, ku tuhumi mahaifiyarku da kuma Josephine, sune suka yi komai!!". Haƙiƙa a maganar kakan nasa babu karya a cikinsu, tabbas duk abinda ya faɗa gaskiya ce, gwaggo da bakinta tun cikinta yana da wata biyar, tun bata ma san me zata haifaba, ta bada guda ɗaya, to su kuma basu mantuwa, shiyasa da ta haihu suka ɗauki ɗayan, sai dai da akwai abin da ya saɓa a cikin maganar, wanda kuma dole a wajen Josephine da Cherish ne kawai za'a san ainahin menene wannan!. Wannan shi ne cakwakiya, Lion dai yana tsaka mai matuƙa wuya wanda fitarta sai Allah ya ƙaddara. Nan ma dai shiru ya yi mashi bai yi magana ba. Gabaɗaya kakan nasa ya shiga ruɗu, saboda yin shiru Lion ba alkhairi bane, sun san shi tun yana ƙarami, idan ya yi shiru, to wani abin yake ƙullawa a cikin ransa, so haka har ya girma, shirunsa musiface a wajen marasa gaskiya masu cin amana da tauye haƙƙin ƴan adam. Ganin yanda ya yi shirun ba ƙaramar ɗaga mashi hankali ya yi ba, dan haka sai ya sake cewa "Ni zan je office ana jirana". Ya ɗauki tsawon lokacin da a kallah zai kai 10mins kafin ya sake nisawa tare da ɗago idanuwansa ya sauke a kan kakan nasa, cikin tsananin nutsuwa ya fara magana. "Ni ban tambayeka waye ya baku cikon TRIPLETS da kuka ɗauka ba, ni kawai na ce maka ne ina yake? Me kuka yi da shi? And lastly where's Anderson? Wanda ya baku wannan duk daga baya ne, zamu zo kan zance, for now dai amsa this two questions that i asked you! Where is my TRIPLETS? And where is Anderson?". "Anderson is already died, you know that, so i don't know what do you want us to tell you again kuma". Jinjina kai ya yi tare da faɗin "Okey Anderson is already died, wow this is so nice, agreed, amsa me da remaining question, where's my brother?". Ya kai karshen maganar yana miƙewa tsaye. "Romeo your brother has gone since that time". Sake jinjina mashi kai ya yi kafin nan ya fara takawa a hankali ya nufe shi, dama yana tsaye ne ta wajen mirror, ba halin yin baya baya, bashi da zaɓin da ya wuce ya tsaya kawai har Lion ɗin ya iso gare shi. A hankali ya iso in da yake, hannu ya ɗaga cikin nutsuwa ya shafi lallausa kuma jajir ɗin kumatun kakan nasa, cikin sanyin murya ya ce "Okey let me try something, let me send you to the place that you send my brother!". Ya kai karshen maganar yana gangaro da hannunsa izuwa wuyar kakan nasa. Da karfi sosai ya shake ɗan tsohon, ransa a tsananin ɓace over, amma saboda ya gane suna neman hassala shi ne, sai ya ki bari ɓacin ran nasa ta yi tasiri, sai ya danne kawai. Cikin kwanciyar hankali kakan nasa ya sanya hannu a saman hannun Lion ɗin, tamkar wanda ya kama hannun ƴar baby haka ya ɓanɓaro hannun Lion ɗin daga jikin wuyarsa tare kuma da murɗe ta baya da karfi, nan take yanayin kakan nasa ya fara sauyawa, cikin tsawa da wata iriyar murya wadda da ka ji ta kasan ba nasa bane, dan murya ce ta irin kartin mazan nan, da ita ya dakawa Lion ɗin tsawa, sam Muryar bata da daɗin ji, tamkar an tada injin jiƙa lalatatce. Ba shakka abin mamaki ne canzawar kaka nasa da kuma irin karfin da yake da shi a matsayinsa na dattijo, sai dai kuma ko kaɗan Lion ɗin bai yi mamakin hakan ba, dan ya san fin hakan ma zasu aikata. Kasancewar yana da ciwo a hannun, sai murɗe mashi hannun da kakan nasa ya yi ta yi mashi muguwar zafi, hanan tasa ya kai ɗayar hannunsa yana ƙoƙarin sake shako wuyar kakan nasa, dan tsananin zafi da yake ji. Sam kakan nasa bai bari hannunsa ya sake taɓa jikinsa ba, sai ya yi ƙoƙarin haɗe hannayen nasa dukka biyu ya ruke da hannu ɗaya. Da Lion ɗin ya fahimci wannan karfi fa ba na kakansa bane, dan haka yana da kyau su yi fito na fito, idan ba haka ba, idan ya zuba masu idanu to zasu yi mashi illa mai girma. Tuna hakan ne yasa bai bari kakan nasa ya kama ɗayar hannun nasa, sai ya yi ƙoƙarin kaucewa, hakan ya bawa kakan haushi ba kaɗan ba, sai ya yi wani irin kurma kururuwa kamar kukan giwa a dawa, nan take ya canza halittarsa izuwa wata halitta mai matuƙar girman, tana kama da ɓauna, wato saniyar dawa, ga wasu kawo guda biyu a kai. Ko kaɗan Lion bai ji tsoro ba, sai ma nishaɗi da abin ya bashi, shi da ya yi faɗa da su barbushi jibga jibga mutane masu kama da samudawa, dan haka sai ya gyara tsayuwa tare da dakewa, shi hakan ma ta fi mashi, ya fi jin daɗi su yi fito na fito da su, ya ci ubansu Roshan babu sirki, ya kuma sanyasu su duka su gaya mashi gaskiya!!. Gadan gadan wannan halitta da kakan nasa ya koma ya tunkarosa. Yana zuwa Lion ɗin ya furta kalmar bismillahi tare da fara kokawa da shi. Sai dai ina ya riga da ya ambaci sunan Allah, babu wata tsafi da zata yi amfani a wajen, haka yasa suna fara yin faɗa kakan nasa ya koma ainahin halittarsa, sarai Lion ɗin yasan da hakan, amma sai bai kyale shi ba, ya jibge shi da kyau da kyau, wani irin wawan mari ya kai mashi a kumatunsa wanda har sai da ya sanya shi ganin wani haske ya gilma mashi ta cikin idanuwansa, bai barshi ya dawo dai'dai ba ya kwashe kafafunsa, sai ga ɗan tsoho ya zube kasa wargajam. Guntun tsaki Lion ɗin ya ja, ya so ace da matashin mai jini a jika zasu gwabza, dan ya ci ubansa, ya sauke mashi duk wata haushi da yake ji a kansa, ya jibgi banza, amma sai ya zamana da tsoho ne ba matashi ba, wannan tsohon idan ma ya ce zai dake shi, ai sai dai ya karisa gawar da ba tasa ba, dan wannan idan ya yi mashi duka ɗaya lafiyayyiya ba makawa sai dai a ɗauki gawarsa. Wayar makekiyar Tv dake a ɗakin Lion ɗin ya tsinko, da karfi ya ja har sai da Tv ta faɗo kasa ta tarwatse, ko a jikinsa ya zo ya ɗaure kakan nasa ɗaurin goro, ta baya ya ɗaure hannayen nasa, sannan ya ɗaga shi cancak, bai sauke shi a ko'ina ba sai a saman tsakiyar bed nasa. Ya sauke shi tare da zama a saman bedside drawer, kasa ya ɗan yi da kansa yana ɗan murza ƴatsun hannunsa, ya ɗan ɗauki lokaci da a kallah zasu kai 10mins kafin ya ɗago kai tare da kai kallonsa izuwa kan ɗan tsohon, a takaice ya ce "Are you ready to tell me the truth or not?". Murya a tsarke, cike da tsoro ya ce "Zan faɗa maka komai". Yana magana yana zare ash eyes nasa, haƙiƙa ya tsorata na ganin tsafinsa taki yin aiki a kan Lion ɗin, ya ji matuƙar rashin daɗi, sam ba haka ya so ba, ya so ne ya jibgi Lion ɗin har sai ya yi laushi, sannan ya ɗaure shi kansa a kasa kafafuwansa a sama, sai dai bai san cewa ta Allah ba tasa ba, bai san cewa shi Lion ya rigada ya ruke Allah hannu bibbiyu ba, wanda kuma ya ruke Allah, tabbas babu shi babu taɓewa, wanda ya ce Allah shi ne komai nasa, to babu shakka Allah ba zai taɓa bashi kunya ba, Allah zai kula da lamuransa ba zai taɓa bashi kunya ba, ya Allah ka iya mana da iyawarka!. Jinjina mashi kai Lion ɗin ya yi tare da yi mashi alamar ya yi maganarsa yana jinsa. "Magana ta gaskiya dai, na farko a nan shi ne, da gaske mahaifiyarku ce ta bamu yaro ɗaya, babu wasa a cikin wannan maganar, shi kuma maganar Anderson, ba shakka Anderson yana raye kamar yanda ka yi hasashe, maganar ɗan uwanka cikon TRIPLETS naka kuma, i don't know har yanzu yana raye or not, wannan shi ne iya gaskiyar da na sani". Shiru Lion ɗin ya ɗan yi na ɗan lokaci kafin ya sake cewa "Tun ainahi menene matsalar, and meyasa kuka karɓi cikon TRIPLETS nawa?". A tsananin razane tare da kiɗima kakan nasa ya fara magana "Please Romeo don't ask me this questions! I don't want to die, i have alot of things da nake son cinmawa, idan har na gaya maka gaskiya, to ba shakka zan mutu a yau, please save my life, leave me like that!". Ya kai karshen maganar yana zare idanu kamar an tare ɓera a tarko. Nisawa ya yi nafin a takaice ya ce "I don't want all this miscellaneous excuse, just amsa me, meyasa suka ɗauki cikon TRIPLETS nawa? Me kuka yi da shi?". Allah sarki Lion bawan Allah, yasan cewa baba shakka gwaggo da bakinta ta bada ɗaya daga cikinsu, amma shi ba hakan ce a gabansa ba, dan ya san wlh gwaggo ba zata bayar da su haka kawai ba, dole da kawai kwakkwaran dalili, shi yanzu so yake yasan menene yasa aka yi hakan dukka, ba damuwarsa wanda ya bayarba, a gaskiya sai mai karfin Imani mai kuma tawakkali da yarda da ƙaddara ne kawai zai iya ɗaukar abin da Lion yake ɗauka, bugu da kari shi duk abin da zaka gaya mashi sai ya yi doguwar nazari a kan maganar, shiyasa yana da matuƙar wahala kaga ya yanke kuhunci ba dai'dai ba, saboda aiki da kwakwalwa da basira, a yanzu da wani ne ya ji abin da kakan nan nasu ya ce, to ba shakka da ba zai yi wani dogon tunani ba, kawai zai ɗauki karan tsana ne ya ɗaurawa gwaggo ɗin, alhalin kuma dole da akwai dalilinta na yin hakan, Allah ka bamu ikon yin amfani da kwakwalwarmu wajen yin tunani a koda yaushe. "Romeo it's a long story, please and please let me go........" Kasa karisa maganar ya yi saboda wani irin kallo da Lion ɗin ya wurga mashi, hakance tasa ya haɗiye maganar. "Uncle you know that bana repeating na word ko? And them bana cancel na magana idan nayi ko?". Jinjina mashi kai kakan nasa ya yi, ba shakka yasan da cewa Lion ba zai canza maganar nan ba, ya gaya mashi gaskiya shi ne kawai zai zama mafi a'ala a garesa, idan ba haka ba, wlh Lion zai gana mashi azabar da sai ya gwammaci mutuwa a kanta, dan haka sai ya fara magana cike da iya gaskiyar da ya sani kamar haka. "Romeo ainahin wannan matsala ta samo farko ne daga kan kakanku Jacob mahaifin William, shi ne makasudin shigarku dukka wannan matsala, Jacob wato mahaifin William shi ma member ne na kungiyarmu, kuma shi ne mataimakin shugaban kungiyarmu wanda ya kasance shi ne Anderson, Anderson shi ne shugaba, Jacob mai take mashi baya, to dama a ƙa'ida ta kungiyarmu kowa dole zai kawo yaro daga cikin yaransa wanda ko ya mutu wannan yaro zai gajesa, hakan ce kawai zata sanya kungiyar ta cigaba da haɓaka, so shi Jacob sai ya bada yaronsa Herry, daga baya sai ya sake bada Josephine, saboda yana son zama shugaba, a ƙa'idarmu dama hakance, wanda ya fi sadaukarwa uwargijiyarmu, shi ne zai zama shugaba, kai baka yi mamakin meyasa Jacob ya fi kaunar William a cikin ƴaƴansa ba? Saboda yasan cewa William ɗin shi ne kawai ɗansa, a lokacin sam ba'a san za'a haifi Tga ba, to a takaice dai da Herry da Josephine Jacob ya bayar da su, ya rage saura mashi William kawai, shiyasa ya fifita William ɗin sama da su, ya kaunace shi sosai, dan yasan shi ne kawai zai gajesa a duniyar mutane, su Josephine ba nasa bane, nan da ɗan lokaci za'a ɗaukesu, haka muka cigaba da tafiya a kan tsarukanmu, nima na bada yaro ɗaya daga cikin yarana, dan ya zama magajina a kungiyar, kowannanmu dai ya bada na shi, kwatsam sai William ya zo da batun auren mahaifiyarku wadda ta kasance musulma, shigowar musulma gidan Jacob zai iya zama barazana ga gariyarsa a kungiya, dan haka sai ya tsaneta, na nuna baya goyan bayan tarayyar ɗansa da ita, to da yake abin ya zo da karar kwana, shi William kaifi ɗaya ne, ba'a isa a tankwara shi ba, ai kaga yadda suka kare, William ya zama sanadiyar mutuwar Jacob ɗin, to mukuma abu ne da ka rigada ka sani cewa bamu yafe jininmu, dan haka ba zamu iya yafewa William wannan laifi da ya yi na kashe mana ɗaya daga cikin member kungiyarmu mai karfin faɗa aji ba, bugu da kari kuma yayanmu na jini, hakan yasa muka fara shirye shiryen yadda zamu ɗauki fansa a kan William, a dai'dai lokacin ne kuma muka fuskanci babban barazana da ya yi ƙoƙarin rugujemu, wannan barazana kuma ba komai bane face musuluntar William da su Josephine, mun shiga tsananin tashin hankali na wuce misali, saboda Josephine da Herry namu ne ba naku ba, idan aka ce sun musulunta mun shiga uku, zamu iya rasa rayukansu a kan hakan, ga shi lokacin ya zo a dai'dai Herry zai maye gurbin Jacob tun da ya mutu, kuma suna matsayin musulmai ba ta yadda za'ayi su kasance a cikinmu, saboda suna yin sallah da sauransu, duk musulman da zaka gani a ire iren kungiyarmu, to basu yin sallah da sauran ibadunsu ne, dan tsafi baya haɗuwa da sunan Allah, to su Josephine bayan sun musulunta suna sallah har da karatu, hakan ba ƙaramar ɗaga mana hankali da jefamu cikin bala'i ya yi ba, a wannan lokacin ne Anderson ya fuskanci mummunar ukuba daga wajen uwargijiyarmu, dan shi ne shugaba a wajen, komai ya faru za'a ga laifinsa a matsayinsa na shugabanmu, dan haka sai uwargijiyarmu ta hukunta shi a kan musuluntar su Josephine, wanda hakance tasa duniya take ganin kamar ya mutu, dan ya sha bakar wahalar da kowa ya bashi mutuwa, bayan ya dawo cikin hayyacinsa, uwargijiyarmu ta saukaka mashi ne sai ya koma cikin kungiya da zama mai gabaɗaya, kuma a lokacin ne uwargijiyarmu ta ce ta bamu lokaci ƙanƙani mu ɗauki mataki a kan abin da yake faruwa, kuma mu san yanda zamu yi mu dawo da Josephine da Herry cikin sauri, a takaice hakan tasa muka yi ƙoƙarin dawo da su cikinmu, hakan kuma ba zai taɓa yiwuwa ba har sai mun rabasu da mahaifiyarku, dan tana koya masu abubuwan addini, (Addu'a da karatun Alqur'ani mai girma) idan kuma suka karanta wani abin ma (addu'a) da mu bamu san menene bane suna iya ɓace mana daga idanun tsafinmu, hanan tasa muka fara ƙoƙarin rabasu, sai muka fara da WILLIAM, dan munfi jin haushinsa sama da kowa, shi ne sanadiyyar komai da ya faru, shi ya kawo mahaifiyarku a cikinmu, ya yi mana laifi dayawa, shi ne ya zama sanadiyar mutuwar Jacob, sannan ya janye su Josephine daga garemu, ya kuma kawo mana mahaifiyarku ta zo da addininta tana ƙoƙarin ruguzamu, wannan dalilin yasa muka yi iyaka bakin ƙoƙarinmu wajen cusawa William tsanarta, kuma a lokacin sai muka yi sa'a yazo dai'dai tana da ciki, sai muka cusa mashi tsanar cikin da ita kanta, to hakan ce tasa muka yi nasarar nesanta ta da William ɗin, ta koma gefe guda tana rayuwa, sai mukuma kuka kama William ɗin muka ɗaure shi, sai muka kawo wani mai kama da shi muka yi replacing, a takaice dai William da kuke tare da shi a yanzu ba naku bane, ba shi ne mahaifinku na gaskiya ba, namu ne, naku har wa yau yana ɗaure a kungiyarmu, dan ya yi mana laifi dayawa, Anderson ya ce kada a kashe shi, a barshi a ɗaure har ya mutu, to har yanzu dai bai mutu ba, yana dai shan bakar wahala, sai dai babu wanda ya san da cewa William da yake tare da ku ba naku bane namu ne. Bayan mun ɗauki William na ainahi, sai muka koma kan Josephine, munyi munyi mu juyar da tunaninta, amma da yake ita ta yi sabo sosai da mahaifiyarku, tana tare da ita kullum, sai muka kasa, hakan ba ƙaramin ɓatawa Anderson rai ya yi ba, sai ya yanke shawarar dole ita ma mahaifiyarku mu hukuntata, dan ita ma ta kawo mana barazana a cikin harkokinmu, hakan yasa muka yanke shawarar karɓar ɗanta idan ta haifa, wannan shawara da muka yanke yasa sai muka barta a tare da Josephine ɗin, shi kuma Herry muka juya mashi tunani, muka kife ƙwaƙwalwarsa ma gabaɗaya, sai ya zama bai ma san menene addinin musulunci ko kuma mahaifiyarku ba, muka mantar da shi komai kamar yanda muka yi wa Rimsha a yanzu, haka muka cigaba da saka idanu a kan mahaifiyarku da Josephine, cikin dabara muka fara controlling na Josephine ɗin ita ma, mun sami nasarar yin hakan ne kuma a lokacin da take jinin haila, babu tsarki a tattare da ita, shiyasa muka yi nasarar aikata hakan, daga nan sai muka cigaba da amfani da ita dan muna son mahaifiyarku ta aihu mu ɗauki yaron, ita Josephine ita ce ta sanya mahaifiyarku ta bada yaro guda ɗaya, da bakinta ta ce ta bamu ɗaya, ban dai san ya suka yi da Josephine ɗin har ta yarda ta bada yaron ba, abin da na sani shi ne ta yarda ta bada babban ɗanta, so ba kai bane babba, wanda muka ɗauka shi ne yayanku, shi ne aka fara haifa, tun cikinta yana da wata biyar a duniya ta yarda ta bada ɗan da zata fara haifa, wanda zai fara faɗowa duniya, to shi ne yasa bayan ta haihu muka turo Herry ya karɓi yaron, a lokacin ita ma Josephine ɗin bata isa ta yi mana musu ba, ba a cikin hayyacinta ta bada yaron ba, sai dai abin mamakin shi ne, Bayan Josephine ɗin ta bada yaron, lokacin da mahaifiyarku ta koma gidanta tana kuka, idan baku manta ba Josephine ɗin ta bita ai, a lokacin sun sake zama na ƴan kwana biyu a tare, wannan zama da suka yi ne yasa Josephine ta sake kubce mana, dan mahaifiyarku ta sake ɗaurata a kan turbar musulunci sosai, kuma time da mahaifiyar taku zata bar kasar nan, akwai wani littafin adduo'i da ta bawa Josephine ɗin, ta ce kada ta yi wasa da shi, ta rinƙa karantawa, hakan yasa Josephine ta kubce mana mai gabaɗaya, dama ita sau biyu ta taɓa halaktar kungiyarmu, a lokacin muna controlling nata ne, to tun da mahaifiyarku ta bata wannan littafin, sai muka rasata, wannan dalilin kuma yasa da William namu dake wajen ku, da kuma Herry basu kaunarta, sun tsaneta sosai, saboda idan ta kusancesu, za su iya konewa, William dake wajenku mun sanya shi ya reneku kamar uba, sai dai mun sanya shi ya cusa maku tsanar Josephine ɗin, dan saboda kada ku kusanceta ta gaya maku gaskiya, bamu son ku zama Musulmai, idan kuka zama hakan za'a sami gagarumin matsala, kuma ita Josephine musulmace, to kusantarta a gareku babban haɗari ne a garemu, hakan yasa muka shiryawa William abin da zai gaya maku yasa ku tsaneta, da Josephine ɗin ta fahimci hakan, sai ta yi amfani da wasu abubuwa nata na tsafi da ta koya daga wajen wata kawar mamanku mai su na Cherish yar kasar China, kasan chinawa da iya tsafi, to ita ma Cherish ɗin ta iya, sai ta koyawa su Josephine, mahaifiyarku dai ta ce bata son koya a lokacin, dan babu kyau, ita kuma Josephine ta ce zata koya dan zai yi mata amfani, ai kuwa ya yi mata amfani, dan lokacin da ta farga muna son cutar da rayuwarku, mu tauye ku, bamu son gaya maku gaskiya, sai ta yi ƙoƙarin zuwa ta yi magana da kai, a lokacin kana da 15 years a duniya, amma saboda already William ya cusa maku tsanarta, sai kaki ka saurareta, har ma kayi yunkurin kasheta, to data ga hakan, sai ta fahimci me matsalar, shi ne sai ta yi amfani da ɗaya daga cikinku, wanda kuma mun rigada mun fara yin tsafi da shi a baya, wato Michael, sai ta yi amfani da shi da nata tsafin da ta koya a waje Cherish, sai tana baku kariya sosai, abin ya ɗaga mana hankali matuka, sai muka yi ƙoƙarin kasheta kawai mu huta, amma muka gagara, da muka matsa ma, sai kungiyarmu ta jijjiga tana neman rugujewa, bamu da zaɓi dole muka hakura muka kyaleta, muka kuma fita harkarku, dan mun lura idan muka matsa zamu iya jawowa kanmu gagarumin matsala, Josephine tana shirya maku abubuwa da dama da zai sanya ku zo in da take, dan ta gaya maku gaskiya, amma sai abin ya ci tura, kun rigada kun tsaneta tun farko, shi ne yasa komai zata yi ba zaku je in da take ba, sai dai kai Romeo mutun ne mai sa'a, duk shirin da muka yi wa William namu, duk kula da ya yi daku, kaki ka yarda ka ɗauke shi a matsayin uba, ka fi son Josephine sama da shi, tun daga nan muka gane cewa kai ɗan baiwa ne, kuma idan bamu yi da gaske ba, zaka iya kawo mana gagarumin matsala, mun yi niyar juyar maka da tunani sosai, sai wani gagarumin aiki ya taso mana a kungiya, hakan yasa muka mai da hankulanmu a kan aikin, kafin mu dawo shi ne muka tarar ka musulunta, abin ya yi mummunar ɗaga mana hankali, mun shirya maku abubuwa da dama da baki ba zai faɗe shi ba a kan kada ku kusanci musuluncin nan, amma mun rasa ya aka yi ka musulunta, abin fa ya jijjigamu ba kaɗan ba, daga nan muka fara neman ta yanda za'ayi mu kaika kasa koma ta yaya ne, dole mu kasheka dan zaka iya zama mana babban baraza wanda baki ba zai iya fadarta ba, Amma mun kasa yi maka komai, saboda taimako da kuke samu daga wajen Josephine da kuma mahaifiyarku, duk da bata a tare da ku, amma kullum sai ta yi maku addu'a, wani lokaci muna ganinta tana rabawa al'umma kuɗi sosai, duk a cewarta Allah ya kare ku a duk in da kuke, sau ba adadi muna kawo maku hari dan mu kasheka, amma Josephine tana shiga tsakaninmu da ku ta hanyar Michael, to a yanzu ne muke ganin mun sami dama da zamu kaika kasa ta hanyar matarka da ta kasance ita ce rauninka, a baya bamu iya gane menene rauninka ba, amma a yanzu ya fito karara matarka ita ce rauninka, munsan idan wani abin ya sameta dolenka ka shiga damuwa na wuce misali, idan ka shiga damuwa kuma, hankalin kowa zai karkata a kanka, hakan ne zai bamu damar kasheka cikin sauki ba tare da Josephine ko mahaifiyarka sun shiga tsakaninmu ba, sai dai kuma abin da ya bamu mamaki, duk halin da muka jefa matar taka a ciki, hakan bai sa ka ɗaga hankalinka ba ma bare har ka shiga damuwa, yanzu dai halin da ake ciki Anderson ya ce mu kashe matar taka, yin hakan shi zai sa dole ka shiga damuwar da zai sa hankalin kowa ya dawo kanka, kai Romeo ka bamu ciwon kai na wuce misali, ka sanya mu cikin bala'i ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba, shi ne yasa Anderson ya ce mu kasheka kawai, wannan shi ne ɗan takaitaccen abubuwan da suka faru, saura amsa zaka samu a wajen Anderson.........". Ya kai karshen maganar yana mayar da numfashi....... Nasan ko a iya haka my readers kun fahimci in da aka dosa, tsayawa nace zan yi dogon jawabi na bada labarin komai dallah dallah ba zai yiwu ba, dan haka ga shi nan a takaice na baku ta yanda zaku gane in da aka dosa. Nisawa Lion ɗin ya yi kafin ya fara magana a nutse "Ni babu wanda ya kare ni face Allah da ya halicce ni, addu'a kuma bata faɗuwa kasa banza, koda kun sanya na faɗi kasa, to ba zaku iya yi mani komai ba, koda hankalin su Josephine ya bar kanmu, ba zaku iya yi mani komai ba, saboda Allah ne yake kareni ba kowa ba, Allah kuma baku isa ku karkatar da hankalinsa ba, kunsan meyasa cutar Meesha bai ɗaga mani hankali ba? Saboda already nasan Allah yana sane da komai, and them nasa evil eyes suna kewaye da mu, sannan na san so kuke ku ga na shiga ɓacin rai da har zata iya sanya zuciyata ta buga, already na san shirinku, shiyasa ban bari na ɗaga hankalinna ba, kai baka yi mamakin ya aka yi ban tunkari Josephine da wannan magana ba na tunkareku kai tsaye? Saboda already na jima da sanin cewa Josephine musulma ce ba krista ba, kuma a duk lokacin da zan yi addu'a a tsakanin iyayena, a kan Josephine ne kawai nake samun kwanciyar hankali ba William ba, tun daga nan na fahimci William ba shi ne ubanmu ba, shiyasa kaga ni ban kula shi ba, saboda bani da time nasa, yanzu duk ba ma wannan ba, ina son ka gaya mani wani yaro ne kuka sanya a cikinmu time da kuka ɗauki cikon TRIPLETS nawa?!". "Yaron da muka sanya a cikinku muka ɗauki wancan ai ɗayan ku ne!". Ya bashi amsa yana wani irin jan numfashi tamkar wanda aka shake yake ƙoƙarin fito da numfashin nasa. "How comes zai zamana ɗayanmu? Ban gane ba". "Romeo kamar yanda na gaya maku ɗayanku ne, hakan yake, ku ba TRIPLETS bane, QUADRUPLE (Ƴan huɗu) ne Aisha ta haifa, to dama kasan ɗanta na fari ta ce ta bamu, kuma na gaya maka uwargijiyarmu bata karɓar ɗan da ba a bayar da shi ba, a lokacin da mahaifiyarku ta haifeku, sam bata a cikin hayyacinta, kuma a gida ta haihu ba a asibiti ba, dan ta ce ba zata je asibiti ba, sai dai a ɗebo mata likitoci a gida, Cherish ce ta jagoranci likitocin da suka karɓi haihuwar tata, so a lokacin mun yi amfani da Cherish ɗin da Josephine ne muka ɗauki yaro ɗaya, dama kasan idan aka haifi TWINS, TRIPLETS or QUADRUPLE ana ɗaurawa wanda ya fara faɗowa duniya wata ƴar agogo launin fara a hannu, alama ce da take nuna shi ne babba, shi ma na biyu haka, har dukkansu, to a lokacin Josephine ɗin sun kiɗime, sai suka bamu ɗan autanku a maimaƙon ɗan farin, har mun fara yin tsafi da shi, sai Uwargijiyarmu ta ce ai wannan iyayensa basu bada shi ba, ba shi ne aka bada ba, dan haka ba zai yi aiki ba, already kuma mun fara taɓa ƙwaƙwalwarsa, hakan yasa muka dawo da shi muka ɗauki babban yayanku wanda har lokacin yana ɗaure da white agogonsa na nuna cewa shi ne babba, yaro na farko da muka ɗauka Mahaifiyarku bata cikin hayyacinta, da zamu dawo da shi kuma tana a cikin hayyacinta, tun ɗaukarsa da kwana biyu muka so mu dawo da shi, amma ba dama, dan kullum tana a tare da ku, ganin hakan ne yasa muka ɗan hakura muna jiran wata dama da zata zo sai mu ɗauke shi. A lokacin da ta kaiwa William yaran, mune nan muka sanya William ɗin ya daki JAMES da sanda a kai, hakan ne ya bamu damar ɗaukar babban yayanku, muka dawo maku da ɗan autanku da muka ɗauka da farko wato Michael, so mu ba wani canza ku da muka yi, ita ma Josephine da wannan taɓa ƙwaƙwalwar Michael ɗin da muka fara yi ne ya bata damar samun hanyar baku kariya ai, so a takaice Michael shi ne wanda muka fara ɗauka, daga baya muka dawo da shi muka ɗauki yayanku, wannan dalilin yasa kaga Michael ƙwaƙwalwarsa ba'a dai'dai take ba, mun rigada mun birkita kwakwalwar mun fara yin tsafi da shi ne, kai baka yi mamakin idan kun tambayi William menene ainahin musabbabin ciwon Michael sai ya ce maku haka aka haife shi ba? Ai shi yasan komai, a gabansa aka yi komai, kawai yaki gaya maku ne, dan ma kada ku gane ba shi ne ainahin mahaifinku ba, William na ainahi yana kungiyarmu! Shiyasa ko wani asibiti da kuka je suka kasa gane me matsalar kwakwalwar ta Michael ɗin...........". Shiru Lion ɗin ya yi yana mamakin yanda waɗan nan tsofaffi suka zauna suka shirya abu tiryan tiryan babu mistake a ciki, lallai sun cika shahararrun ƴan duniya, musamman shi Jacob Uban William ɗin da ya mutu, ya fi kowa iya tantiranci da haɗama, har da bada yaransa guda biyu, Allah mai iko, yanzu wani irin hukunci ne ma ya dace da waɗan nan azzaluman? A kan neman duniya kawai?.........Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba, shi Lion yana nan, su gwaggo kuma suna gida Nigeria, kada kuma ku manta suna a tare da Uncle Herry da William na karya wanda kuma dukka sun kasance mambobine na kungiyar su His excellence ɗin, kuma ga Lion ya tirke kakansa a nan ya tonawa kungiyar tasu asiri, kuna ganin ƴan kungiyar za su barsu kuwa? Kuna ganin ba za su yi amfani da William da Uncle Herry su cutar da su gwaggo ɗin da suke gida ba kuwa? Kun dai ji Anderson ya yi umarnin a kashe Rimsha! Ga kuma garkuwanta Lion a nan ya taho ya barta, ga shi sun juya mata kwakwalwa ko sallah ma bata sani ba bare ace zata yo askar Allah ya kareta. My peoples PRINCESS TEEMA naku ta amana yau bana jin daɗi, saboda cakwakiyar TRIPLETS har wani zazzaɓi zazzaɓi nake ji! Na barku lafiya❤️ ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E19 Date: 29/4/2024 Jinjina kai Lion ɗin ya yi, har cikin ransa ya ji tsananin farinciki na wuce misali, dama shi damuwarsa shi ne ace Aseef ba ɗan uwansa bane, ya fi kaunar Aseef fiye da kansa, Aseef ɗan lelensu ne, to yanzu tun da Aseef ya tabbata pleasure su ne jininsu ne Alhamdulillah, har ya ji ya kara samin karfin gwiwa sosai da sosai, ya kara samun nutsuwa. A hankali ya ɗago da dara daran idanuwansa, kai tsaye sai kan face ɗin kakan nasa ya sauke kallonsa. Shiru ya zuba mashi idanuwa yana kallon yadda yake yi, tamkar wanda aka shake haka kakan nasa yake yin acting. Ko sannu Lion ɗin bai ce mashi ba, ya bishi da kallo kawai yana ganin ikon Allah. Shakesa suka yi da karfin gaske, idanuwansa har suka firfito waje, suka yi jajir kamar jini, wasu jijiyoyi sirara a saman idanun nasa suka bayyana, sai fafutukan neman numfashi yake yi, ko da sunan wasa Lion bai yi yunkurin taimaka mashi ba, saboda ya ce dama duk kashe shegu zai yi, sai ya kashesu kamar dabbobi, shi ne yasa ko da sunan wasa bai yi ƙoƙarin taimaka mashi ba. Da gurnanin kakan nasa ɗin ma ya isha shi, sai ya miƙe ya nufi waje abinsa, dan yana toshe mashi kunne da wani irin gurnani na mai fafutuka tsakanin mutuwa da rayuwa. Lion ɗin yana fita bai fi da minti biyu ba suka kashe kakan nasa har lahira, sun kashe shi kuma kamar wanda aka bawa guba, bakinsa duk kumfa fari tas yake fitarwa, haka suka yi mashi. Lion kuwa yana fita gida ya wuce abinsa. Yana komawa ba ɓata lokacin ya kira Areef a waya, wayar ta yi ringing na farko har ta katse bai ɗauka ba, yana can yana ta zuba barcin gajiya, almost karfe 12:30 yanzu, amma basu farka ba, sallar asuba ma da kyar suka iya tashi suka yi, dan fa ba karya sun wahala ne, kwanaki sosai suka ɗauka basu sami barci ba, shiyasa yanzu suke biya bayin Allah. Sake kiransa a karo na biyu ya yi, cikin magagin barci ya kai hannu ya laluɓo wayar, ba tare da ya duba number wanene bane ya yi picking tare da kara wayar a kunnansa, yana mai kara jawo pillow ya matse a saman kirjinsa. "Hello". Ya furta cikin murya irin na mai magagin barci. "What is the time now?". Shi ne abin da Lion ɗin ya gaya mashi. Da sauri ya ɗan waro idanuwansa waje, sai kuma ya sake mayar da su ya rufe. A kasale ya furta "Why Lion? Why are you disturbing me ne? Me zan yi maka to idan na tashi?". Yana magana tamkar Aseef, kasancewar cikin kasale da kuma muryar barci, sai ya zamana kamar mai shagwaɓa. "Go and kill William now". Shi ne abin da ya ce mashi. A wani irin dubu ɗari ya mike zaune a saman bed ɗin, hannu ɗaya ya kai saman face nasa yana murje idanuwansa dan ya tabbatar a duniya yake ko dai a cikin mafarki, ya je ya kashe daddynsu kuma? Wannan wace iriyar lukutar bala'i ce da sassafen nan? Anya Lion yana cikin hayyacinsa kuwa? Ko ma dai ba Lion ɗin bane? Ko dai kunnensa bata ji da kyau bane? Sune tambayoyin da yake jerawa kansa, tuni ya nemi magagin barcin nasa ma ya rasa, cikin kiɗima ya ce "Lion is it you?". Shiru Lion ɗin ya ɗan yi na ƴan mintoci kafin ya sake cewa "Areef i said go and kill William now, sannan Shaikh Sultan is coming, i think ma jirginsu ya kusa sauka, dan tun safe ya taso, zai zo ya yi wa Meesha abin da ya dace, so take care of all those things". Ya kai karshen maganar dai'dai lokacin da yake kunna makekiyar Tv dake a palonsa. Bayan ya kunna Tv ya koma saman luntsumemiyar sofarsa mai zaman mutun uku ya lume a cikinta, saboda laushi, suna mai cigaba da magana da Areef ɗin. "Lion are you hard what you said kuwa? I should go and kill daddy?! For what reason? Are you out of your sense?". "Done talk! Go and do what i said". Ya kai karshen maganar tare da katse kiransa. Shiru Areef ɗin ya yi, hankalinsa ya tashi matuƙa, ya za'ayi ace mashi ya je ya kashe daddynsu? Wannan ai ba magana ce da hankali zata ɗauka ba, shi dai a iya saninsa yasan Lion baya shan komai da ya danganci shaye shaye, ko lokacin da suke ji da zafin kansu, lokacin da suka taso jininsu na tafasa, Lion bai yi shaye shaye ba, ɗan gara shi ma ya sha sau ɗaya, yana farawa kuma ya ji ba zai iya ba ya dai'na, Aseef ne yake shan su wine a da can can ɗin ma, shi ma bai wani sha sosai ba ya dai'na, to yanzu ko Aseef zai ce a je a kashe daddynsu ne? Amma kuma da ya tuna cewa Lion baya yanke hukunci haka kawai, dole sai da wata ƙwaƙkwaran dalili, sai ya ji cewa zai iya kashe daddyn nasu. Yunkurawa ya yi jikinsa duk a tsananin mace, sai zafi gaɓɓansa suke yi mashi. A hankali ya zuro da kyawawan fararen kafafunsa kasan bed ɗin, sai hamma yake yi yana yamutse fuska kamar wanda ya ga wani abin kyama, sam bai so tashi daga barcin nan a yanzu ba, kawai Lion ya zo ya wani tashesa ba gaira babu dalili. Har zai mike sai kuma tunanin number da aka kirashi da shi ɗin ta faɗo mashi. A hanzarce ya jawo wayar tasa tare da sake dubawa, ba shakka ainahin number Lion ɗin ta Washington ne, da shi ya kira shi, sake waro idanu ya yi yana tunanin yaushe Lion kuma ya tafi Washington? Allah mai iko. Ƙoƙarin sake kiran number ya yi, sai dai babu network, wurgi da wayar gefe guda ya yi tare da miƙewa dan ya nufi toilet. A hankali yake ɗaga kyawawan kafafunsa, haka ya shiga cikin toilet ɗin. After some minutes ya fito ɗaure da farar towel a ƙugunsa mai shegen kyau, ga wani ɗan ƙaramin kyakkyawar towel ɗin nan a hannunsa yana goge gashin kansa. A gaban mirror ya tsaya yana ƙoƙarin shafa lotions nasa, sai zuba hamma yake yi alamar yunwa yake ji. Yana ɗago ash eyes nasa ta cikin mirror suka yi ido huɗu da ita, tana tsaye a bakin kofar shigowa ɗakin, ta rungumo hannaye a kirjinta, jikinta na a sanye da wandon jeans baki da T-shirt fara kal, kayan sun zauna a jikinta da kyau da kyau, sun fito mata da ainahin kyakkyawar dirin da Allah ya yi mata, ta ɗan ɗaura ƙaramin veil a kanta, sai zuba kamshi take yi, kyawawan kafafunta na a sanye da flat shoe mai matuƙar kyau da tsada, face nata babu make up sam sam, ainahin natural beautynta ne ya bayyana, kyakkyawace ta gasken gaske, ita da Rimsha idan ma suka yi kwalliyar basu kyau, dan kwalliyar rage masu natural kyansu take yi. A ɗari ya juyo da kyau, dan ya kalli shin ita ce da gaske?. Ba shakka ita ce, ta zuba mashi idanu tana ta kallon shi. Kasa magana ya yi, saboda wani irin abu da yake fusgarsa a kanta, ta tafi da imaninsa, sai ji ya yi gabaɗaya ya nemi gajiyar da kasalar dake a jikin nasa ma ya rasa, har wani sanyi ya ji a cikin zuciyarsa, tamkar wanda aka jefawa dutsen kankara a ciki. "Yah Areef gwaggo tana kiranka". Shi ne abin da ta faɗa, ta yi maganar cikin sanyin murya, ta kai karshen maganar tare da juyawa da nufin ta fita daga ɗaki. "Ji mana ƴan mata". Ya faɗa cikin harshen Hausa, sai dai kana ji kasan bai iya hausa ba, iya word ɗin kawai ya iya faɗa, ita ma ba dai'dai da kyau ya faɗeta ba, sai Allah ya san mashi daga ina ya jiyo wannan kalmar kuma. A hanzarce ta juyo tana kallon shi, cike da mamaki ta ce "Dama ka iya hausa ne?". Shiru ya ɗan yi kafin daga bisani ya ce "What is the meaning of the word? I don't the meaning, and i didn't understand what you're saying". (Kai amma Areef ɗan duniya ne!😂 Ashe ma bai san ma'anar abin da ya faɗa ɗin ba😂 yaran gwaggo nan sai dai Allah ya shirya😂) Harara ta wurga mashi da waɗan nan dara daran fararen idanun nata, ashe ma ko manar kalmar bai sani ba, shi dai kawai ya faɗi abinsa, yanzu da zagi ne kuma fa? Kai Areef akwai neman magana, haka take faɗa a cikin zuciyarta. Shi kuwa wannan harara da ta wurga mashi ɗin ba ƙaramar kara nutsar da shi cikin kogin kaunarta ya yi ba, alama ya yi mata da hannu a kan ta zo. Make mashi kafaɗa ta yi tana faɗin "Iya kiranka kawai gwaggo ta ce nayi, bata ce na zo na zauna ba". Ta kai karshen maganar tare da ɗan murguɗa mashi ɗan ƙaramin bakin nan nata. Cool murmushi ya saki yana faɗin "Haba mana, wai baki missing nawa ne? Please come now, idan baki zo ba Allah zan zo har gaban momma ɗin na kamaki". A takaice ta ce mashi "To sai ka zo kamani ɗin". Ta kai karshen maganar tare da juyawa abinta, har cikin ranta tana tsananin kewarsa, tana son ta je ta rungume shi, amma sai shegen jiji da kai da shegen jan aji, tun da ta shigo ɗakin kuma ta kasa kawar da kallonta a kansa, dan ya tafi da imaninta, dukkansu TRIPLETS suna da surar jiki mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali sosai, a duk lokacin da ta kalle shi, yana matuƙar tafiya da imaninta sosai, kawai dannewa take yi ta ja ajinta. "Please my Jehan don't go, come to me my wife, ina kewarki sosai". Ya kai karshen maganar yana kama kunnuwansa da hannayensa dukka biyu, alamar ta yi hakuri ta zo gare shi. Juyowa ta yi tana faɗin "Ni ba zanzo ba, dan baka yi kewata ba, idan da ka yi kewata ai da kana dawowa wajena zaka fara zuwa, amma baka je ba, ka zo kana ta barcinka kawai baka nemeni ba, dan haka mun ɓata". Kara ruke kunnuwan nasa da kyau ya yi, cikin sanyin murya ya ce "Sorry Queen of my heart, na fa je na dubaki kina barci, kema dai kinsan cewa i can't sleep without seeing your beautiful face my baby, please come now". Ya kai karshen maganar kamar zai yi mata kuka. Harara ta wurga mashi kafin ta ce "To close your eyes". Ba musu ya rufe idanun nasa. Cikin sanɗo ta lallaɓo ta kariso gabansa, daddaɗar kamshi perfume nata ne yasa ya fahimci ta iso wajen nasa, sai dai bai buɗe idanun nasa ba, yana jiran sai ta ce ya buɗe, saboda baya son ya ɓata mata rai, ya san halin kayassa sarai, sarkin rigimace number ɗaya, yanzu idan ya buɗe idanun ba tare da izininta bama, sai ya zama wata sabuwar rigima. (Mata mu ɗin na daban ne, yanzu dai ku dubi shekarun Jehan da Areef, yana da 32 years, namiji cikakke mai jini a jika, ga kyau iya kyau, kuɗi iya kuɗi, mulki, isa da taƙama, taurarone shi mai tsananin haske a duniya, ita kuma tana da 17 years, amma take juya shi san ranta, ta sanya shi ya yi mata abu kamar karamin yaro, ji ta ce ya rufe idanu, kuma ya rufe yana ma jiran sai ta ce ya buɗe, Allah mai iko, waye ya taɓa tunanin TRIPLETS zasu biyewa mace har haka?🤔 Macen ma kananan yara, ji dai Rimsha, 14 years ke gareta fa, amma haka Lion yake biye mata, duk wata izzarsa yanzu a waje yake nunata, idan ya dawo cikin bedroom nasa, kamar baby haka yake biyewa Rimsha suna wasa!!! Abin mamaki abin al'ajabi) Tana karisowa wajen ta faɗa saman kirjinsa tana ɓoye fuska na rashin kunya. A tare suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya. Cikin sanyin murya ya ce "Can i open my eyes now?". Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a kada ya buɗe. Hannu ya sanya ya rikota da kyau a jikinsa, kasa kasa ya furta mata why. Ita ma kasa kasa ta ce bata son sa ido ne kawai, ya bari sai ta tafi sai ya buɗe idanun. Jinjina mata kai ya yi alamar okey ba damuwa, sannan ya fara shafa mazaunanta yana faɗin "I really missed over my baby". Da murya kamar mai raɗa ita ma ta ce "I miss you too my husband". Wani irin sanyi ya ji tana ratsa shi, da kyar ya iya cewa "Please my Jehan ki barni na kalleki mana, please mana my baby". Jinjina mashi kai kawai ta yi alamar to, ta yi hakan tana mai kai hannunta saman kyakkyawar gashinsa dake kwance a saman kirjin nasa. Da sauri ya buɗe idanun nasa, kai tsaye sai a kanta ya saukesu, ta lafe shiru a saman kirjin nasa. Kara kankameta sosai ya yi tare da rankwafowa kanta, a hankali ya ambaci sunanta. Amsawa ta yi ba tare da ta ɗago kai ba. "Look at me". Ya faɗa yana kai hannunsa ya ɗan ɗago haɓarta. Ajiyar zuciya suka sauke a tare kafin ya sake matso da face nasa kusa da ita sosai. Yana son ya yi missing nata, sai kuma maganar Lion ta faɗo mashi a cikin tunaninsa, ya ce ya kashe William. Tuna hakan yasa ya saki haɓar tata tare da rungumeta sosai a jikinsa yana faɗin "My baby zauna ki jirani a saman bed ɗin nan ina zuwa ko?". Okey ta amsa mashi tare da wucewa izuwa saman bed ɗin. Binta da kallo ya yi har ta haye ta kwanta, ta kwanta ta yadda suna fuskantar juna, kusan a tare suka sakarwa juna cool murmushi, suna tsananin kaunar juna sosai, amma sai dirama tamkar wasu ƴan wasa. A hanzarce ya juya izuwa ga mirror, sauri sauri ya fara shafa lotions nasa, yana yi yana kallonta ta cikin mirror, ita ma ta tsare shi da idanu tana ta kallon shi, sai ɗaga mata gera ɗaya yake yi time to time idan sun haɗa idanu, abin gwanin birgewa. Bayan ya kammala ya wuce dressing room nasa. Jim kaɗan ya fito shirye cikin wandon jeans baki kalar ta jikinta, da kuma T-shirt sky blue, ya yi matukar kyau ba ɗan kaɗan ba, sai dai bai samu dama ya busar da gashin kansa ba, da akwai ɗan danshin ruwa, amma haka ya wuce ya nufi waje yana ce mata bari ya zo yana magana yana ɗaure gashin kan nasa. Okey kawai ta amsa mashi da shi tare da binshi da kallo har ya fuce, sannan ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya tare da gyara kwanciyarta ta rungumo pillow da ya runguma ɗazun. Shi kuwa yana fita bedroom na Lion ɗin ya nufa, bakinsa a ɗauke da sallama ya shiga, sai dai babu kowa a ciki. Shiru ya ɗan yi yana mamakin yaushe Lion kuma ya tafi Washington? Ya dai san wancan number da Lion ɗin ya kirasa na Washington ne, to ko yaushe ya tafi?. Ya ɗan jima a cikin bedroom ɗin kafin ya fito ya nufi bedroom ɗin daddyn nasu, wato fake William. Bakinsa ɗauke da excuse ya shiga cikin ɗakin. Turus ya tsaya ganin cewa babu kowa a cikin ɗakin, ya sha ruwan mamaki, dan kuwa shi dai yasan daddynsa baya fita waje, idan ma ya fito to a palon kasan suke zama shi da Uncle Herry su yi hira. Duddubasu ya fara yi yana neman a ina suke, sai dai shiru, babu su babu labarinsu. Fitowa ya yi ya fara kewaye gidan yana nemansu, amma shiru babu su babu labarinsu, tambayar gateman ya yi a kan ko ya kalli su daddynsa? Ko sun fita ne. A'a basu fita ba gateman ya bashi amsa. Wucewa ya yi izuwa cikin gida, zuciyarsa cike da mamakin ina suka tafi, da kuma tunanin meyasa Lion zai ce a kashe daddyn nasu?. Haka dai ya nufi bedroom nasa. Yana shigowa kiran Lion tana shigowa wayarsa, a hanzarce ya kariso ya ɗauki wayar tare da yin picking na call ɗin. "Lion I didn't see dad and uncle Herry". Shiru Lion ɗin ya ɗan yi kafin ya ce mashi "Tun yaushe na sanyaka aikin? Anywhere now dai ka tura aje airport a ɗauki Shaikh Sultan, su William kuma sun koma in da suka fito". "Lion like how sun koma in da suka fito? Wai ma what is happening ne?". "Areef go and send someone to airport i said, shi ma kuma ka ɓata mani lokaci irin na ɗazun!". Ya kai karshen maganar tare da katse kiran. Sam Areef ɗin bai ji daɗi ba da bai yi wa Lion ɗin abin da ya sanya shi ba, ga shi yanzu da alama Lion ɗin ya ji babu daɗi, dan daga voice nasa zaka fahimci bai so hakan ba. "My baby am coming". Ya faɗa tare da wucewa ya nufi waje again. After some minutes ya dawo cikin ɗakin, kusa da ita ya zo ya tsaya tare da miƙa mata hannu a kan ta zo su tafi. Ba musu ta miƙa mashi hannunta, rikota ya yi tare da jawota jikinsa, a haka suka nufi waje. Kai tsaye ɗakin gwaggo suka nufa, yana rungume da ita, ita ma da yake ba kunya ke gareta ba, sai bata wani damu ba. Bakinsu a ɗauke da sallama suka shiga cikin ɗakin. Gwaggo na zaune a bakin bed, Rimsha na kwance ta tada kai da cinyar Brr Naurat, baiwar Allah ta yi shiru kamar mai tunanin wani abin, ita kaɗai tasan me take ji, sai kallon Malika dake tsaye a kusa da mirror take yi, ita ma Malikar ita take ta kallo, sai dai dukka ɗakin babu mai iya ganin Malikar sai ita kaɗai, ita kuma Rimshar bata iya buɗe baki ma bare ta yi wata magana, Allah sarki sarai Malika tana sane da duk abin da ya faru da Rimshar, sai dai kuma bata yi wani yunkurin taimaka mata ba, saboda tana son Lion ya gane gaskiya, shi ne yasa bata taimaki Rimshar ba, ta san cewa idan ta bar Rimsha da wannan ciwon, to ba shakka Lion zai nemi sanin gaskiya, kun ga kuma kamar yanda ta yi hasashen hanance ta faru, Lion ɗin ya tafi neman sanin gaskiya, da ta taimaki Rimshar ta samu lafiya, to da Lion ba zai mayar da hankalinsa ya binciko gaskiya ba, sai dai ayi ta tafiya a haka har ƴaƴa da jikokinsu, shi ne yasa wani lokaci bata tanka abu a kan Rimshar idan ya faru, saboda tana son wani abin ne ya bayyana. Kusa da gwaggo Areef ya zauna, ita kuma Jehan ta koma saman bedside drawer ta zauna, dan bata son hawa saman bed ɗin, tana hawa zasu fara yin faɗa da Rimshar, yanzu kamar wuta da audiga haka suka zama, basu haɗuwa waje guda, ba komai ne yasa hakan ba face ita ma Jehan tauraronta yana da nisa, ba'a banza ta cika faɗa da zafin ran nan irin na Lion ba, su ƴan baiwa ne, taurarinsu yana da nisa sosai, wanda taɓasu a wajen matsafa abu ne mai matuƙar wahala, ita ma Rimshar sai da suka ci bakar wahala tsawon watanni suna bibiyarta kafin su sami galaba a kanta, sun wahala fa fiye da tunaninku kafin su cinwa Rimshar. Kun tuna lokacin da Jehan ta gayawa fake William magana a palo? Kuma babu abin da ya iya yi mata, to hakan ce, ita sam sam bata taɓuwa, duk bala'i haka za'a ganta kuma a barta, kamar Lion take, shi ma dai nan gani nan bari, Rimsha ce dai mai ɗan rauni baiwar Allah, kuma duk wata gaskiya ta wajenta yake fara bankaɗowa, ita take zama sanadiyar bayyanar abubuwa da dama, baiwarta ya wuci tunanin mai tunani, ita ta je Daular Mutuwa, ita ta zama sanadiyar bayyanar Dr Salman, yanzu kuma kusan ita ce ta zama sanadiyar bayyanuwar wannan lukutar matsalar da suke a ciki!!. "Good morning momma". Ya faɗa yana kallon Rimsha dake ta faman kallon wajen mirror. "Good morning or good afternoon?". Brr Naurat ce ta tambayeshi. Ɗan murmushi ya yi yana faɗin "Kai ƴar tsohuwarnan, kin iya sa ido, to ai ni yanzu garina ya waye". "E ba shakka yanzu garinka ya waye kam, ga alama nan na gani". Ɗan zaro idanu ya yi yana faɗin "Ina alamar kuma?". Shiru ta yi bata yi mashi magana ba. Gwaggo ce ta ce "Areef ina Aseef? Ina autana? Ko dai bai tashi daga barcin bane?". "I think bai tashi ba, our Rimsha what are you thinking? Naga hankalinki gabaɗaya baya a kanmu ne". Ya kai karshen maganar yana ƙoƙarin kai hannu zai taɓa face nata. Dakatar da shi gwaggo ta yi ta hanyar cewa "Kaga ne wlh ka rufa mana asiri, yadda take kwance shirun nan barta a haka, idan ka taɓota, kamar ka kwanto bana gidan rina ne! Idan ta fara bala'i sai mun rasa me yake yi mana daɗi". "Momma like how? I didn't understand anything, yi mani bayani, Rimshar ce mai faɗa? Ita da take so silent". Cike da mamaki ya yi maganar. Ba ɓoye ɓoye gwaggon ta bashi labarin duk abin da yake faruwa, da tafiyar Lion, har kiran da Lion ɗin ya yi mata ɗazun ya ce mata ga abin da yake faruwa, dan haka sai su kara taka tsantsan, dama wannan dalilin yasa ta ce Jehan ta kira mata shi, dan ta gaya mashi halin da ake ciki. Shiru ya yi yana tunanin wasu abubuwa, maganganun Josephine ne kawai suka fara dawo mashi cikin kansa, a koda yaushe idan ya je wajenta kai mata ziyara, maganarta ɗaya shi ne tana taya su da addu'ar samun gane gaskiya cikin ƙanƙanin lokaci tun kafin komai ya kure masu, to shi a lokacin yana ɗauka ko gaskiya tsakaninta da Dr William ne take son su gane, bai san cewa ba haka abin yake ba, ga gaskiyar da take magana a kai yau sun fara ganewa, Allah sarki kullum baya taɓa sauraronta idan ya je, da ta fara kawo mashi labarin baya zai dakatar da ita, ya ce mata shi gaisheta ya zo yi ya kuma tambayeta me take da buƙata, dan ya saya mata, idan kuɗi take so ya bata, shi baya son wani dogon magana, bai san cewa ga abin da ta jima take son sanar da shi ba. Duk sai ya ji jikinsa ya yi muguwar sanyi, ya shiga damuwa sosai, tunaninsa ɗaya yanzu ina ɗan uwan nasu, cikon QUADRUPLE nasu yake? Yana raye ko ya mutu? Ina ainahin daddynsu yake? Hakika ya tausayawa daddyn nasu da kuma momman nasu, sun sha wahala, an cutar da su, uncle Herry da Josephine suma an cutar da su matuƙa, ga Tga a gefe, wannan wani irin rayuwa ne?, Ga Rimsha baiwar Allah da bata san komai ba ita ma an jefata cikin bala'i. Gwaggon ce ta katse shi da cewa "Saif ya ce kada kowa ya ɗaga hankalinsa, kada mu yi kamar akwai wata matsala, mu yi rayuwa kamar kullum, nan da lokaci ƙanƙani komai zai zo karshe, dan haka kada ka ɗaga hankalinka kai ma". Nisawa ya yi tare da miƙewa, zuciyarsa na yi mashi kuna na rashin kashe William ɗin da bai yi ba, abin ya baƙanta mashi rai, ji yake yi kamar ya yi ta buga kansa da jikin bango ko zai sami sukuni, hanyar fita daga cikin ɗakin ya nufa yana faɗin "Momma am coming". Ya kai karshen maganar tare da ficewa. Bin shi da kallo suka yi har ya fita, sannan gwaggo ta ce da Jehan "Jeki ki kai mashi abinci, nasan bai yi breakfast ba". Okey ta amsa tare da miƙewa ta bi bayansa. A ɓangaren Lion kuwa, yana zaune a wajen da yake zaune tun ɗazun, bai motsa daga wajen ba, yana aikin latsa waya ga Tv tana magana, kamar daga sama ya fara jin wani ɗan jarida daga cikin Tvn yana bada rahoton wai GENERAL OF THE ARMY'S ROMEO ya kashe wani babban ƙusa a gwamnati babu gaira babu dalili, wanda kuma ya kasance kakansa ne, har gida ya shiga ya yi poisoning nashi, yanzu ƴan'sanda sun sami damar garzayawa gidan, suna kuma bincike a kan gawar, su kasance kusa da Tvnsu dan jin yanda komai zai na wakana. A hankali ya ɗago idanuwansa izuwa kan makeken Tvn nasa, gawar kakan nasu ne aka hasko tare da hotonsa a zaune a saman bedside drawer kakan yana ta kallon kakan nasa. Sam bai yi mamakin ganin hakan ba, dan yasan da akwai CCTV camera a cikin ɗakin, tun time da ya shiga ya gani, kuma da gangan ya bar camerar a kunne ta naɗi komai, dan dama yasan ba zasu faɗi gaskiyar komai ba, zasu yanke video ne ba zasu nunawa duniya ainahin abin da ya faru a tsakaninsa da kakan nasa ba, sai dai su nuna iya in da kakan nasa ya fara fafutukan mutuwa, shi kuma ya fice daga gidan, su suna jin daɗi sun kafa mashi tarko, basu san cewa ya jefawa kifi namane a cikin bakin ruwa idan ta zo kamawa shi kuma sai ya capkota ba, sun shirya hakan suna son ruguje shi ta kowace hali, shi kuma ya shirya yi masu rubdugu, yasan cewa kakansa His excellence zai ma iya shiga ya fita ya sanya a cire mashi kayan aikinsa, ma'ana a karɓi mukaminsa na wajen aiki, saboda yanzu ya yi fito na fito da su, amma sam hakan ko a jikinsa bata damesa ba, saboda shi kaɗai yasan abin da ya ƙulla masu, shi kaɗai yasan abin da zai jijjigo, sai ya tashi kansu. BABBAR MAGANA, YAU AKE YINTA, YANZU WASAN ZAI FARA A TSAKANIN TSOFAFFIN NAN GUDA UKU, WATO HIS EXCELLENCE, ANDERSON, UWARGIJIYARSU, DA KUMA LION SHI KAƊAI, ZAMU GA WAYE YA IYA BUGA WASAN A CIKINSU, ZAMU GA WAYE ZAI ZAMA ZAKARAR GWAJIN DAFI A CIKINSU, SU UKU SHI KAƊAI! BA SHAKKA AKWAI YAKI BA KAƊAN BA, YANZU DAI GA SHI SUN YI MASHI SHARRIN YA KASHE BABBAN ƘUSAR GWAMNATI, SANNAN GA SHAIDA ƁARO ƁARO JAMA'A KOWA YA GANI, KUNGA KUWA DOLE LION YA FITO YA YI WA DUNIYA BAYANIN MEYASA YA KASHE BABBAN ƊAN SIYAYSA KAMAR WANNAN, DUK DA YAKE KAKANSA DOLE YA YI WA DUNIYA BAYANI, DUK DA YAKE GENERAL OF THE ARMY'S DOLE YA YI BAYANI, DAN BA ZAUNA GARI BANZA AKA KASHE BA, BARE ACE KILA ƁARAWO NE KO WANI MAI LAIFIN, BABBAN MUTUN MAI MURYAR FAƊA AJI AKA KASHE, AKWAI KALLO!! YANZU WASAN ZAI ƊAUKI ZAFI. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E20 Date: 30/4/2024 Mikewa ya yi tare da ɗaukar wayarsa ya nufi cikin bedroom nasa. Ko'ina a cikin ɗakin a gyare fes fes, tamkar ba'a taɓa taɓa komai na cikin ɗakin ba, makekekiyar katafen gadonsa a shumfuɗe da white bed sheet na alfarma, mai matuƙar kyau da tsada, sai tashin daddaɗar kamshi air freshener mai kwantar da hankali tare da sanyayya zuciya bedroom ɗin nasa yake yi. Toilet ya nufa, wanka ya yi tare da fitowa ya shirya cikin wata kyakkywar farar jallabiya tas da ita, ya zo ya shumfuɗa dadduma ya tada sallar azzahar. Bayan ya idar ya jima yana addu'a tare da kaiwa Allah kukansa, bayan ya shafa addu'ar ya mike ya nufi saman shumfuɗaɗɗiyar bed nasa. Mikewa ya yi ya kwanta, yana tsananin kewar Meeshansa, a hankali ya lumshe idanuwansa, ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi. A gida Nigeria kuwa, Areef yana fita harabar gidan ya ci karo da motar Donal ya dawo daga airport, ya je ya ɗauko Sheikh Sultan, wato limamin masallacinsu na Washington. Iso ya yi wa Sultan ɗin izuwa cikin gida. Kai tsaye bedroom na Lion ya kai shi, sannan ya fita ya je ya sanar da su gwaggon zuwan Sultan ɗin, daga nan ya fito ya nufi waje, mota ya je ya shiga ya bar gidan mai gabaɗaya. A ɓangaren Mark kuwa, an yi nasarar ɗaura mashi kafafun nasa, sai dai anci bakar wahala, sai da ma aka wuce da shi babban asibiti, a gida abin ya ci tura, Lion ya ce su shirya shi ya dawo Washington ya yi jinya a can, dan sun fi kwararrun likitoci da zasu kula da shi sosai, so yanzu ana shirye-shiryen ne, Brr Naurat ta ce yakamata kafin Mark ya koma Washington, to a ɗaura aurensa da Anaya, ya karɓi kalmar shahada, sai a ɗaura auren kawai su wuce tare da ita, wannan shawara da ta yanke kowa ya yi na'am da ita, dan ita ma Anayar ta damesu da kukan ciwon Mark ɗin, kukan yanzu daban na anjuma daban, ga shi daddynta ya hanata zuwa asibiti wajen Mark ɗin, sau ɗaya ta je ta rinƙa yi mashi kuka, yana fama da ciwo kuma ga kukanta, da wanne zai ji? Shi ne suka hanata zuwa kawai, sai dai ta yi ta takura masu da kukan a gida. Abba, Abbi, daddyn Anayar, daddyn Jelly yau dukkansu za su koma gidajensu, sai dai za su bar Anaya a wajen Brr Naurat, Lion ya ce su bar Brr Naurat da Dr Salman a gidan nasa, shi ne yasa suka barsu, an bar Anaya, Aafia kuma zata tafi da Abbinta, baiwar Allah har yanzu dai sauki bai samu ba, yanzu haka asibiti zasu fitar da ita waje, tana jin duk abin da za su faɗa, bata manta kowa ba, magana ne dai bata yi masu, shiru shiru ta koma. Sai misalin karfe 1:20 Aseef ya farka daga barcin da suke ta zubawa tun bayan sallar asuba. A hankali ya waro idanuwansa, idanun nasa sun yi jajir da su, har sun ɗan kumbura, saboda barcin da ya rinƙa zubawa kamar ba gobe. A hankali ya kai kallonsa gefensa, har lokacin Akila tana zuba barci bata tashi ba. Nisawa ya yi tare da yunkurawa ya mike zaune, cikin wani irin kasala jikinsa duk zafi yake yi mashi, a hankali ya zuro kyawawan fararen kafafunsa kasan bed ɗin. Da kyar ya iya mikewa tsaye, a hankali ya fara jan kafafun nasa ya nufi toilet, sai aikin turo baki yake yi kamar wanda aka yi wa dole ya tashi. Ita kuwa Akila barci sai abin da ya ci gaba, dan ita ta fi shi gajiya. Wanka ya yi tare da fitowa ya shirya cikin pajama launin maroon color, sannan ya shunfuɗa dadduma ya gabatar da sallar azzahar, bayan ya idar ya fito dan ya je wajen gwaggo. A nan ya isko Sheikh Sultan yana yi wa Rimsha addu'a, ta kwanta shiru kamar bata a wajen, a zahirin gaskiya ba shiru ta kwanta ba, Malika ce ta danneta, dan bata son ta ɗaga masu hankali, amma banda haka wannan tofin da ake yi mata ɗin ba karamar haukata matsafan da suke tattare ita ya yi ba, da Malika ta kyaleta, tsab zata shake Sultan ɗin ma da kansa, amma ta ruketa gam, ta ki barinta ta yi borin. Bakinsa ɗauke da sallama ya shigo cikin ɗakin. A tare suka amsa mashi da gwaggo da Brr Naurat. Waro idanu ya yi yana kallon Sultan dake ta faman yin tofi. Cike da mamaki ya ce "Shaikh is it you?" Ya yi maganar yana kara waro idanu waje. Sultan ɗin bai amsa mashi ba sakamakon yana addu'a, sai bai amsa ba. Kusa da gwaggo ya zo ya zauna yana faɗin "Momma am feeling hungry". Hannu ta kai ta ɗan shafi kansa, cikin sanyin murya ta ce "Sannu da tashi, let me bring food for you ko?". "No momma just leave it, I can't eat anything without my heartbeat, bari ta tashi sai muci a tare, zan jirara". Jinjina kai ta yi, rigimar Aseef tana da yawa, shi fa ya ce yana jin yunwa, za'a kawo mashi abinci kuma ya ce sai da Akila zasu ci a tare, ya iya rigima kala kala. "Momma what happened to Rimsha?". Ya yi maganar yana kallon Sultan da ya dafa kanta yana yi mata karatu a fuska. "She isn't feeling fine". Ɗan zaro idanu ya yi tare da cewa "What? Momma kuma shi ne ba'a gaya mani ba? What is wrong with her?". A takaice gwaggon ta ce mashi aljanune suka taɓata. Shiru ya ɗan yi yana maimaita kalmar aljanu, shi sai yau ma ya taɓa jin wannan suna, wai aljanu, abin ma dariya ya bashi, ko meye aljanun? Ya tambayi kansa. Da yaga dai shi ba wani ganewa zai yi ba, sai ya miƙe yana faɗin "Let me go and see uncles". A takaice gwaggon ta ce mashi "Is good, suna ma shirye shiryen wucewa gidajensu yanzu ne". "Why zasu koma gidansu?". Ya tambaya da mamaki a saman face nasa. Brr Naurat ce ta ce "E mana zasu koma gidansu, shi ne dai'dai, a nan sun takura sosai ne". Turo baki ya yi yana faɗin "Amma without uncle Hossain ko? Dan ni Allah ba zan yarda ya je ko'ina ba, dole duk in da zamu je mu tafi da shi tare, i don't want him to stay out of us". Ya kai karshen maganar kamar zai yi kuka. Da sauri gwaggo ma ta ce "You are right! Nima gaskiya ba zan iya yin nisa da Nawazuddeen ba, dan haka shi dole ya zauna a tare da mu, dole na gayawa Saif, ina son mu kasance a tare da Nawazuddeen". Juyowa ya yi ya dawo ya sumbaci gwaggon a kumatunta yana faɗin "That's my momma, that's why I love you, uncle babu in da zai je, we are together with him". Ya kai karshen maganar tare da wucewa ya fice daga ɗakin. Ita dai Brr Naurat da idanu kawai take binsu, Aseef ɗan rigima. A takaice sai da Sheikh Sultan ya shafi kwana uku yana yi wa Rimsha addu'a tare da magunguna irin na addinin musulunci, sannan ne suka sami nasarar cetota ta dawo dai'dai, amma fa anci kwakwa, an wahala ba kaɗan ba, tsayuwa zayyana maku irin wahalar da aka sha ma sai mu cike wannan book 4 ɗin fam, da akwai sauran story a gaba, so ba zan tsaya ɓata lokaci na sosai a wajen zayyano maku ba, just ku yi imagine ya bakar wahala take a ranku, akwai abubuwa da yawa a gabana, ba zan tsaya ɓata lokacina ba!. A cikin waɗan nan kwanaki ukun fa abubuwa da dama sun faru, wanda suka haɗa da dawowar Tga Nigeria, dan Lion ya ce mashi ya dawo Nigeria zai biyo shi, sannan su Abba kowa ya koma gidansa lafiya lou, yanzu gidan ya rage daga gwaggon, Brr Naurat da Dr Salman, sai Jehan, Rimsha and Akila, matan TRIPLETS kenan, sai Sheikh Sultan mai yi wa Rimsha magani, ita kuma Anaya sun wuce Washington da Mark ɗinta, Lion yasa an mayar da shi can, dama already kunsan Brr ta ce ya karɓi kalmar shahada sai a aura mashi Anayar su tafi a tare, to hakan aka yi, su Abba ne suka ɗaura auren a cikin palo bayan ya musulunta, yanzu sun wuce Washington yana asibiti bawan Allah, yana shan wahala sosai da sosai, sai daddyn Rimsha, shi ma yana nan a gidan bai koma gidansa ba, dan gwaggo ta ce babu in da zai je ya barta gaskiya, shi ne Lion ya ce to ya zauna sai ya dawo kawai, Aylar daddyn Jelly kuwa tana asibiti a kwance, saboda ta samu matsala a cikinta har sai da aka yi mata aiki, ta sha wahala ne, cikinta ya zube, ta zubar da jini, sannan ta ɗauki tsawon kwanaki a sume, ga kuma wahala da jijjiga da cikin nata ya sha, abin dai ba'a cewa komai, Allah ne ma ya kaddara tana da sauran numfashi a gaba, ai da ta jima da mutuwa, yanzu dai shi ne yasa sai da aka yi mata aiki, yanzu haka tana gadon asibiti tare da Aunty matar Abbi, dama kunsan sun koma gidansu. A ɓangaren su Aafia kuma, Abbo ya dawo, ya sakata a gaba, tun da ya dawo ya makale yana zarya a tsakanin gidansa da gidan Abbi, Ummi tana Katsina wajen ƴan uwanta, bata san ya dawo ba baiwar Allah, kuma bai bari ta san ya dawo ɗin ba, dan ba ta ita yake yi ba a halin yanzu, hankalinsa ya karkata a kan Aafia, dan ita ya dawo dama, ana buƙatar ta a wajen tsafin nasu, shi ne ya dawo ɗaukarta, sai safa da marwa yake yi a tsakanin gidajen biyu, sai dai Allah da ikonsa, duk zuwa gidan Abbi ɗin da yake yi baya samun ganinta, ko sau ɗaya bai haɗa idanu da ita ba, shi kuma burinsa kawai su haɗa idanu, suna haɗa ido shikenan ya sami kaso 60 a cikin ɗari na abin da yake so, Allah sarki, so suke yi su hallakata kamar yanda suka hallakar da Dr Nawid, Abbo shi ya bada Dr Nawid, sai dai ba'a son ransa ya bada shi ba, dole suka tilasta mashi, da farko ma ya ce ba zai bayar ba, sai da ya ji matsa da wahala ne ya yarda ya bayar, abin da yasa suka ce sai ya bada Dr Nawid ɗin kuma shi ne, idan baku manta ba Dr Nawid ɗin ya hana shi yin amfani da Jelly, to shi ne abin ya ɓata masu rai, suka ce tun da ya rushe masu shirinsu a kan jelly, to za su yi amfani da shi a madadinta, shi ne yasa suka kashe shi. To a takaice dai Abbo ya dawo, yana neman ta yadda zai yi ya ɗauki Aafia ido rufe. A ɓangaren Lion kuwa, a cikin waɗan nan kwanaki uku da suka wuce, ya aikata abubuwa da dama, ciki kuma har da rubuta takardar ajiye aikinsa na soja da ya yi, wannan abin ya yi mugu mugun ɗagawa jama'ar kasar hankali, saboda Lion soja ne wanda kowace kasa take buƙatar jarumi kuma jajirtartce irinsa, tsayayye namiji ne kuma jajirtartce a kan aikinsa, yana da adalci da gaskiya, ga rikon amana, babu zancen cin hanci a lamuransa, kuma babu ɗaga kafa a wajen yanke hukunci, ko kai ɗan uban waye idan ya kamaka da laifi, ba shakka sai ya hukuntaka, babu uban da ya isa ya taka mashi burki, ko his excellence baya ɗagawa kafa, kaifi ɗaya ne shi, babu mai iya tankwara shi, rashinsa a hukumar soja babbar ci baya ne ga kasar U.s gabaɗaya, yana da matuƙar farinjini, al'umma suna tsananin kaunarsa saboda gaskiyarsa, da sama masu kwanciyar hankali da cigaba da yake yi, kowa begensa yake yi, jin cewa ya ajiye aiki yasa wasu har suma sai da suka yi, saboda shiga tashin hankali, wasu kuwa har da rashin lafiya, kowa sai tambayar dalilinsa na ajiye aiki yake yi, amma sam yaki yarda ya fito daga gida ma bare ya yi hira da wasu, duk sojojin dake gidansu ya tarkatasu ya mayar da su headquartersu, sannan ya ɗauko wasu jibga jibgan bodyguards lafiyayyu masu jini a jika ya jibge a cikin gidan nasu, bodyguards ne masu lafiya karfafa masu kiran samudawa, abin ya ɗaurewa jama'a kai, his excellence ya shiga ruɗe sosai, yasan Lion sarai, shi mutun ne da baya yin abu haka kawai, dolen dole sai da kwaƙkwaran dalili, to menene dalilinsa na ajiye aiki? Meyasa? Wannan shi ne tambayar da His excellence ɗin yake ta yi wa kansa, ya haɗa taron gaggawa a white house, ya kuma turawa Lion ɗin saƙon gayyata, amma ya ki zuwa, ko kallon takardar gayyatar ma bai yi ba, dan ya ce bata da amfani a wajensa, his excellence yana tsoron ya sanya karfin mulki ya tursasa Lion ɗin a kan yazo taron dole, dan shi dai yasan waye jikansa, idan ya gwada mashi karfin mulki, to shi kuma ba shakka zai gwada mashi karfin jini, dan Lion baya barin ko ta kwana, dan haka sai His excellence ɗin ya haɗa malaman jikinsa, bai tursasawa Lion ɗin zuwa taron dole ba, haka suka ɗan yi maganganunsu suka watse, anyi anyi da Lion ɗin ya fito ya yi magana a kan meyasa ya kashe kakansa, nan ma yaki buɗe bakinsa, da his excellence ya ga dai Lion fa wani abin yake shirya masu, sai ya lallaɓa ya wankesa a kan zagin kashe kakan nasa da ake yi mashi, duk Lion ɗin yana ganin komai da yake faruwa, amma sam bai yi yunkurin saka baki ba, ya tada kura, a jijiiga gari ya koma gefe ya lafe shiru kamar babu shi, daga shekaran jiya zuwa yau ko'ina idan ka zaga a cikin birnin Washington da kewayenta, maganar Lion ake yi, ko ta ina zancensa ne kawai yake tashi, gidan jaridu kafafen yaɗa labarai, da ko'ina, ya tada tarzoma ba kaɗan ba. Ya koma gefe guda ya yi shiru kamar ba shi ba, abin da ya sanya ya ajiye aikin soja, saboda ya san ta hakan ne kawai his excellence zai yi ƙoƙarin horar da shi, yasan cewa zasu yi ta ce mashi zasu tuɓe mashi kaki, ko kuma su saka shi yin wani abin a gwammatance, to shi ne yasa kafin ma su fara wannan diramar ya ajiye aikin, yanzu ba kaki da gwamnati ce zasu yi faɗar ba, farar hula ce da gwamnati. Wannan shi ne cakwakiya, shi ne ake kira da ainahin game. Tsafinsu ba zai iya kama shi ba, babu abin da suka isa su yi mashi, dole ne sai sun ajiye tsafi sun yi ta kulla mashi manakisa, shiyasa shi kuma ya biyo masu ta karkashin kasa, Allah ne kaɗai yasan shirin da yake shirya masu!!. His excellence ya so haɗuwa da Lion ɗin a koma ina ne, sai dai ina bai samu damar haɗuwa ba, hasali ma Lion ɗin ko waje baya fita, yana cikin gida abinsa, gabaɗaya faɗin U.s ta ɗauka a kan ajiye aikin nan nasa, ta girgiza kasar girgiza mafi girma, amma shi ko a jikinsa, sai ma barci da yake shararawa, yana hutawa, har wata ƴar kiba ya kara abinsa, ban da tunanin gwaggo, TRIPLETS nasa da kuma Meeshansa, to baya tunanin komai a rayuwarsa, hankalinsa a matuƙar kwance, kai daga gani kasan ba karamar abu yake shiryawa ba, komawa da baya ga zaki ba tsoro bane, shirin yaki ne, his excellence ya san da hakan, shi ne yasa hankalinsa ya yi mummunar tashi, shi kansa Anderson a tsorace yake. Wannan shi ne kaɗan daga cikin abubuwan da suka faru a cikin wannan kwana uku da suka wuce, yau ta kama kwana na huɗu, Sheikh Sultan ya kammala aikinsa, Rimsha ta samu lafiya sumul, tamkar bata taɓa yin ciwo ba, yau ta dawo cikin hayyacinta fes, tana dawo dai'dai kuma abinci ta tasa a gaba, ci take yi babu kama hannun yaro, sai kallonta su gwaggo suke yi, baiwar Allah ciki ya buɗe, a kallah yau ta ci abincin da ya kai kusan ukun wanda take ci a baya, sai kallonta Dr Salman da Sheikh Sultan suke yi. Bayan ta kammala ɗirkar abincin ne ta ɗago idanuwanta tana faɗin "Gwaggo ina yaya Saif? Ko basu dawo daga Daular Mutuwar bane?". Shiru gwaggo ta ɗan yi kafin ta ce "Sun dawo, amma shi baya nan, sai dai ki kirashi a waya". Shiru ta ɗan yi tana ji tamkar wadda ta yi tafiya ta je ta yi kwana biyu a wata duniyar. "Gwaggo ina wayata? Jiya da daddare na barta a nan, bani bari na kirashi". Ta kai karshen maganar tare da miƙewa tsaye ta nufi saman bed ɗin, ta bar kayan abincin da ta ci a wajen. Mikewa Dr Salman da kuma Sheikh Sultan suka yi, suka fita suka basu waje, sai Hamdala suke yi ga Allah an samu nasara Rimsha ta dawo dai'dai. Ɗakin ya rage daga gwaggo sai Brr Naurat da kuma Jehan dake ta zuba barci ta tada kai da cinyar gwaggon, ita kuma Akila tana can tana gyaran bedroom nasu, Aseef da Areef basu nan, kwana biyun nan ma sam basu zama a gidan, da alama wani aiki Lion yake saka su, dan a tare da Tga suke fita, idan suka fita tun safe, sai dare suke dawowa, da sun dawo kuma zasu yi barci, dan zasu sake fita da sassafe, mummynsu Rimsha kuma tana can boys quarters tana barci, daddynta baya nan, ya fita zuwa gidansu Abban Imran. Kusa da gwaggo ta zo ta zauna tana faɗin "Gwaggo ina wayar tawa take? Ina so ne na ɗan yi abu da ita". Miƙa mata sabuwar wayarta da Areef ya saya mata gwaggon ta yi, tana faɗin "Nasan Saif zaki kira, to ki kirashi da wayata, numbersa ita ce a farko, dan ba jimawa muka yi waya da shi". Okey ta amsa tare da karɓar wayar tana wani sunkuyar da kai na rashin kunya. Miƙewa ta yi ta nufi waje, da idanu suka bita suna mamakin yadda ta dawo dai'dai cikin hukuncin Ubangiji. Kai tsaye bedroom na Lion ɗin ta nufa, ko'ina a gyare tsab tamkar yana nan. Saman bed nasa ta haye tare da rungumo pillow a kirjinta tana danna mashi kira. Wayar tana fara ringing ya katseta, dan ya ɗauka gwaggoce, shi bai san Meesharsa ta dawo dai'dai ba, yana kwance a saman katafaren bed nasa, daga shi sai singlet fara kal and short, sai wani lumshe idanu yake yi tamkar mai jin sha'awar wani abin, ya kara yin fresh da shi over, bin kiran ya yi tare da manna wayar a kunnansa........... Kiran na shigowa ta ɗauka cikin zumuɗi, a nutse ta ce......... *KADA KU MANTA BABU POSTING A WEEKEND, NA YI CANCEL NASA, IYA MONDAY TO FRIDAY ZAN RINƘA YI KAWAI YANZU.* ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E21 Date: 1/5/2024 Kiran na shigowa ta ɗauka cikin zumuɗi, a nutse ta ce "Hello Noorish". Yana kwance bai san time da ya mike zaune ba, kasa yarda da abin da ya ji kunnuwansa suka ji ya yi, anya ba gizo kunnuwansa suke yi mashi ba kuwa? Anya ita ce kuwa?. Katse mashi tunanin nasa ta yi da cewa "Noorish ka fara ko? Sai mutun ya yi magana kaki amsa mashi da wuri ko?". Ta yi maganar a tsananin shagwaɓe sosai. Calmly ya furta "My Meesha". Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke, jin voice nasa ta yi tamkar an zuba mata zuma a baki, saboda daɗi, wani irin sanyi ne ya ratse zuciyarta, kara kankame pillow hannunta ya yi, cikin sanyin murya ta fara magana a shagwaɓe. "Noorish ka dawo daga Daular Mutuwa kuma ka fita baka tasheni daga barci ba, to ni yanzu kawai ka dawo gida ina son ganinka". Tana magana tamkar zata sanya mashi kuka. "Meesha bana kasar ne, amma zamu rinƙa yin waya kin ji?". Jin abin da ya ce yasa ta fashe mashi da kukan shagwaɓa tana faɗin "Shi ne ka tafi ka barni ko? Allah ni ban yarda ba, koma ina kake ka dawo na ganka, kewarka nake yi sosai". Tana magana tana kuka hawaye bibbiyu. "My Meesha why kike son yin kuka ne? Do you know how sad am feeling idan kina kuka kuwa?". Girgiza mashi kai ta yi. "Sorry Noorish, amma ai ina son ganinka ne". Nisawa ya yi kafin ya ce "Same here, nima ina kewarki sosai my wife". "To Noorish ka dawo mana kawai". Shiru ya ɗan yi mata kafin ya ce "My Meesha, dawowata yanzu ba zai yiwu ba, kuma zamanki a Nigeria yafi mani sauki da samun kwanciyar hankali, ina son kasancewar ki kusadani matuƙa, amma dole na barki a can". Hawayen da suka cika mata idanu ne suka cigaba da gangaro mata a saman face nata, yanzu ta yaya zata iya yin barci ita kaɗai a wannan ɗakin? Ta tambayi kanta da kanta. Jin ta yi shiru ne yasa ya ce "Meesha kuka kike yi ko?". Da sauri ta kai hannunta tana ɗan goge hawayen nata, cikin shagwaɓa da sanyin murya ta fara yi mashi magana a nutse, cike da so da tsantsar kauna. "Noorish ba kuka fa nake yi ba, kawai ina kewarka ne, amma shikenan zan tayaka da addu'a sosai, Allah ya tsare mana kai a duk in da kake, Allah Ubangijin ya dawo mana da kai lafiya, ka kula sosai ka ji?". Yanda ta yi maganar tamkar wata babbar mace mai yawan shekaru. Har cikin ransa ya ji sanyi da daɗi matuƙa, nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da komawa ya kwanta yana jawo pillow izuwa kirjinsa ya rungume, tamkar ita ya ƙanƙame, Allah ya gani yana tsananin kewarta, yana son ganinta a kusa da shi, amma dole ya barta a in da take tukunna, dan shi kansa wannan masifa da yake ƙoƙarin jijjigowa kansa ba ƙaramar wahala zai sha wajen iya tsaida ta ba, bugu da kari kuma idan tana a kusa da shi zata hana shi yin wasu abubuwa, zata sanya mashi tausayi a ransa, kuma dole zai rage wasu abubuwa da ya yi niyar yi saboda ita, shi ne yasa gara mashi suna nesa da juna ɗin, sai su rinƙa yin waya kawai suna jin muryar juna, hakan zai fi sama mashi kwanciyar hankali, zai kuma sanya ya yi aikinsa a yadda ya tsara yin komai ba tare da wata matsala ba. "I really love you my Meesha, pray for me sosai, because nafi bukatarsa sama da komai a yanzu". Tana goge hawayen face nata wasu suna gangarowa, Rimsha sarkin soyayya, tattabara uwar soyayya kuma uwar ruke alkawari, tana tsananin kaunar Lion ta yadda baki ma bai isa ya zayyano irin wannan kauna ba. "Amma Noorish kafin ka tafi ka sumbace ni ko?". Shiru ya yi na ƴan sakanni kafin ya amsa mata. "Yeah my Meesha, i kissed your lips". Cool murmushi ta saki ga guntun hawaye a fuska. "I really like your smile, you're looking so beautiful idan kina yi". Ya faɗa yana ɗago idanuwansa, dan ya duba time, akwai in da zai je da misalin karfe 4 na yamma, fita ce ta sirri!. "Kai Noorish waye ya ce maka nayi murmushi to? Ko dai ka saka mani camera ne?". "Ba wani camera da na saka mani, just na san halin kaya na ne, nasan sai kinyi murmushi a wannan time ɗin da nace nayi kissed naki, that's why na ce hakan". Sake sakin cool murmushi ta yi tana mamakin kwakwalwa irin na Lion, wato shi har ya kammala haddace halinta tsab, yasan duk wani abin da zata aikata da wanda ba zata iya aikatawa ba, ko a bayan idanuwansa, lallai ya cancanci a jinjina mashi. "Noorish ka ci abinci?". Ta tambaya tana lumshe idanu tare da kara lumewa a saman bed ɗin, dan sanyin A.cn dake a ɗakin ya fara yi mata yawa. "Yeah na ci, what of you?". A hanzarce ta ce mashi "Nima na ci, sai dai kuma yanzu ma wani yunwar nake ji". "Okey go and eat another one now, bana son ki rinƙa zama da yunwa, because bana son ki rame, I want to see you the way you are now, ƴar dai'dai". Ɗan turo baki ta yi, a shagwaɓe ta ce "To Noorish kenan baka son na kara yin ƙiba?". Jinjina mata kai ya yi tamkar yana a gabanta, sannan ya amsa mata da Yeah. "To Noorish idan na kara ƙiba fa komai zai kara girma a jikina, ni ina son na kamo Jehan gaskiya". Ta kai karshen maganar tamkar zata yi kuka. Lumshe idanuwansa ya yi, har cikin farfajiyar zuciyarsa ya ji wannan muryar shagwaɓar da ta yi mashi, da tana kusa da shi ai da ya rungumota ya bata hot kiss, abin ya ratsa zuciyarsa da kyau da kyau, Meeshansa nan ta iya zuba shagwaɓa mai tsayawa a rai, a kowani lokaci da irin sabon salon shagwaɓa da take zuba mashi, bata yarda ta rinƙa yi mashi salo ɗaya kullum, na yanzu daban na anjuma daban, tana ratsashi sosai. Calmly ya ce "Wato kin sakawa matar Areef idanu ko?". Murmushi ta yi tana faɗin "Kai Noorish bafa idanu na saka mata ba, just kawai tafi ni girma ne baya yi mani daɗi hakan". Girgiza kai kawai ya yi, Rimsha akwai rigima, idan ya biye mata ba zai je ya yi abin da yake a gabansa ba, wannan yana ɗaya daga cikin abin da yasa sam sam baya son ta dawo Washington a yanzu, sai ya kammala abin da zai yi, idan ta dawo kusa da shi a yanzu, ta rinƙa ɓata mashi lokaci da shiririntanta kenan, ta hana shi yin komai. "Meesha zamu yi waya da daddare, ki kula mani da kanki sosai ko?". Turo baki ta yi tana faɗin "To shikenan, kai ma ka kula sosai". Okey ya amsa mata da shi tare da mannawa wayar tasa sumbata sannan ya katse kiran ya miƙe, a gurguje ya nufi toilet dan ya yi wanka, yanzu ta sami lafiya, hankalinsa ya kara kwanciya. Ita kuma gyara kwanciyarta a saman bed ɗin nasa ta yi, ta lumshe idanunta tana tunaninsa. After some hours, da misalin karfe 9 na dare Aseef da Areef suka dawo gidan, a tare da Tga suke, gaisawa da Alex suka yi a harabar gidan kafin su nufi ciki. Areef da Tga ne suka nufi ciki, shi kuma Aseef ya wuce wajensu Brady a in da suke kulle. Dubasu ya je ya yi ya tabbatar suna cikin ƙoshin lafiya, sannan ya fito ya nufi cikin gida, Lion bai tafi da Brady ba, ya baro shi a nan Naija, so Aseef ya haɗesu da su copper ya rufesu, dan kada su takurawa ƴan gidan, yasan halin matan nan sarai da tsoro, ga shi basu nan, sai su kusa haukatasu a cikin gidan, shi ne yasa ya rufesu. A palon kasa ya isko Tga da Areef suna magana, wucewa ya yi izuwa nasa bedroom ɗin yana faɗin "Am really tied, bari naje na huta, good night". Ya kai karshen maganar tare da wucewa cikin ɗakinsa, Areef yana tambayarsa ba zai je ya gaishe da momma bane?. E ya amsa da shi, dan ya gaji, ya ce sai da safe kawai zai dubata. Jinjina kai kawai Areef ɗin ya yi. Bakinsa ɗauke da sallama ya shigo cikin bedroom ɗin nasa, dai'dai lokacin ita kuma Akila ta fito daga cikin toilet ɗaure da towel a kirjinta, wanka ta yi. Ko sannu bata ce mashi ba, da alama faɗa suke yi, shi kuma ya tsaya ya zubawa santala santalan cinyoyinta da suke jajir da su idanu. Kallon up and down ta yi mashi da waɗan nan dara daran idanuwan nata kafin ta wuce ta nufi dressing room nasa, lotion ɗin ma ta fasa shafawa, saboda yana tsaye a cikin ɗakin, sai ta wuce dressing room kawai zata sanya kaya, da alama fa Heartbeat ranta a ɓace yake sosai. Pajamarsa launin sky blue ta ɗauko, a saman show glass na jera watchs nasa ta ɗaura wandon pajamar tana ƙoƙarin warware rigar ta sanya a jikinta. Kamar daga sama ta ji saukar hannunsa a saman shafaffen cikinta, ya kwanto da kansa a saman shoulder ɗinta, a hankali ya kai ɗayan hannunsa ya karɓi rigar dake hannunta take ƙoƙarin sanyawa, ya ɗaurata a saman show glass ɗin. Ƙoƙarin ture hannunsa daga jikinta ta yi, tana turo baki. Kara kankameta ya yi, a hankali ya ɗan matso da ɗan bakinsa kusa da kunnenta, calmly ya fara yi mata magana a tsananin shagwaɓe. "Why my heartbeat? Ba nace maki sorry yau da safe ba, daga yau fa ba zan ma sake fita ba bare har naje na kai dare, please my pleasure kada kiyi fushi dani, idan kika yi fushi zan iya kamuwa da ciwo, nasan nayi laifi sosai, amma kiyi hakuri". Ture hannunsa ta yi tana faɗin "Ni ka barni, mun yi hannun riga da kai, wai ma meyasa baka kwana a wajen ba kawai". Ta kai karshen maganar tana ture hannunsa tare da janye jikinta dan ta bar wajen. Jawota ya yi mai gabaɗaya ta faɗa jikinsa, ɗaukarta cak ya yi suka fito daga cikin room ɗin. Kai tsaye sai saman bed ya sauketa. Tana ƙoƙarin mikewa ta diro kasa, ya yi maza ya rikota tare da kai hannunsa ya kashe wutar ɗakin. Kwanciya ya yi tare da rungumota sosai a jikinsa tamkar wani ya ce zai kwace mashi ita. Sai ƙoƙarin kwace kanta take yi, amma ina ya kankameta sosai. Da yaga ba zata nutsu ba, sai ya laluɓi lips nata ya haɗe bakinsu waje guda tare kuma da kara kankameta. Ba shiri ta nutsu tsit, dan ita kanta kewarsa take yi, idan ya fita tun da sassafe baya dawowa sai dare, da ya dawo kuma zai yi wanka ya kwanta, ko abinci basu ci a gida, yana kwanciya sai barci, haka gobema zai sake fita, abin yana matuƙar taɓata, kunsan turawa da shegen iya soyayya, ya riga ya narkar da ita da salon soyayyarsa, bata iya jure rashinsa, hakan ma ba karamar jurewa ta yi ba, ta wahala fa. Kissing nata yake yi sosai da sosai, tuni ita ma ta fara mayar mashi da martani. Cikin dabara ya zame towel ɗin da yake a jikin nata, yau ranarsa ce ta sa'a, babu komai a jikinta, ya yi wasa da ita son ransa, yau dai ba zata ce kada ya cire mata pant or bra ba, a dusul nata ya sameta, hannu ya kai ya fara aikin matsa tula tulan, yana yi yana zuba mata shagwaɓa. A hankali ya zame bakinsa daga nata tare da haɗe fuskokinsu waje guda, kuka ya fara yi mata a kan ya yi missing nata sosai, hawayensa ne suke sauka mata a saman face nata, saboda ya haɗe fuskokinsu waje guda. Kara shigewa jikinsa ta yi tare da kai hannu tana goge mashi hawayen, while ita ma kukan take yi hawaye bobbiyu a kan sun yi kewar juna, tun ranar da suka je gidansu Ammienta ziyara, daga nan abubuwa suka runƙa faruwa, sun shafe kwanaki a Daular Mutuwa, ga shi da suka dawo kuma Lion ya sake sanyasu aiki, almost 1 month yanzu rabonsu da mannewa juna haka, dole Akila ta ɓata rai na nisa da ita da ya yi, dan ya riga ya koya mata sabo da shi, dole yau su yi kukan missed na juna. Sosai ta goge mashi hawayen nasa, sannan ta sake mayar da bakinta saman nasa tana bashi kiss mai zafi. Cigaba da wasa da breast nata ya yi yana mai sauke numfashi a hankali hankali. Sun ɗan ɗauki lokaci a haka kafin ya ɗan zame bakinsa daga cikin nata, ya mayar saman nipples nata. Ita kuma botirin rigarsa ta hau cire mashi cikin dabara. Haka suka narkewa juna sosai, sai da suka biya bashin wannan 1 month da basu a taren, sai dai abin mamakin shi ne, duk yanda yake zancen son yin dis virgin nata nan bai yi ba, ga shi yau dai ya samu damar da zai yi ɗin, amma bai yi ba, hakan kuma ya samo asaline na shirye shiryen komawa Washington da suke yi, dan Lion ya ce da shi da Areef duk su shirya su je, sai dai bai gaya masu ga ranar da zasu taho ba, ya dai ce su shirya, kuma ya ce su bar matansu a Nigeria, hakan ce tasa ya daure bai yi abin da yake da burin ya yi ɗin ba, saboda baya son ya tafi ya barta a wahala, duk da Lion ya ce masu bari ya gani wata kila zasu iya zuwa da matan nasu, amma babu tabbas a kan hakan, dan baya son ya jefa rayuwar kowa a haɗari, wannan faɗar na iya TRIPLETS ne da familyn Dr William kawai. Sai da ya samu gamsuwa a wasan nasu, sannan ya rabu da ita tare da miƙewa ya ɗauketa cak suka wuce cikin toilet. Wanka suka yi tare da fitowa, suka shirya cikin kayan barci mai matuƙar kyau da tsada, sannan suka haye saman bed nasu bayan Akilar ta sake gyara bed ɗin da kyau, ta canza bed sheet, sai zuba uban kamshi suke yi, a manne da juna suka yi barci. A ɓangaren Areef kuwa, sam bai nemi Jehan ba, bawai dan baya kewarta ba, sai dai abubuwa da suka taru suka yi mashi yawa, kun san cewa shi ne mai bin Lion, ya yi karatu, yana da ilimi sosai, kuma shi jami'in hukumar sirrice, yana da kaifin ƙwaƙwalwa da basira, so dole shi ne zai iya taimakawa Lion a wannan aikin, dan shi yana da sani sosai a kan sirrin kasarsu, babu wani abu na sirri na karkashin kasa da U.s take yi wan da bai sani ba, shiga da fita ta sirrinsu duk ya sani, ba ƙaramin jami'i bane. To shi ne Lion ya jibge mashi kaso 40 cikin ɗari na aikin, sai fama yake yi bawan Allah, shi ko da sun dawo da daddare ɗin ma, baya samun ya yi barci, bincike yake sake afkawa, dan su kama his excellence da mukarrabanta a cikin ruwan sanyi, su kama shi kuma tare da hujjoji, kasancewar Jehan a kusa da shi, zata sanya ba zai yi abin da ya kamata a kan lokaci ba, kunsan Turawa da son soyayya, tuni zai ajiye aikin ya rumgumeta, sanin halinsa yasa sam baya nemanta, dan su yi abin da ya dace a kan lokaci. A ɓangaren Lion da Rimsha kuwa, sosai suka zuba hira a waya da daddaren, tun Lion ɗin baya amsa mata, har ya dawo bata amsa sama sama, Rimsha akwai iya soyayya da sanya mutun magana ko bai yi niya ba, haka ta rinƙa sanya bawan Allah nan yin magana ba tare da son ransa ba. Da yake suna magana yana latsa laptop ne, hankalinsa na rabuwa gida biyu, idan ta yi magana yana ɗan ɗaukar lokaci kafin ya bata amsa, sai ta saka mashi kuka tana faɗin ya dai'na kulata, daga karshe dai sai ya ajiye laptop ɗin da aikin da yake yi ɗin ya tattara mata hankalinsa gabaɗaya a kanta yana sauraronta, haka zata yi ta zuba mashi shagwaɓa da shiririta, sai dai ya bita da Okey, nan ma ta saka mashi kuka ta ce ko dai ya dai'na sonta ne yasa baya amsa mata magana bayan Okey, dole dai ba dan yaso ba ya buɗe baki ya biye mata suka rinƙa hira, wani abin ma shi bai san ta ya akayi ya iya faɗa ba, duk dan ya sanyata farinciki, wani abin ma idan ta faɗa sam bai san ma'anarsa ba, kawai zai amsa mata ne, dan kada ta fara yi mashi kuka, haka suka yi hira har zuwa karfe 2, a haka barci ya ɗauketa manne da waya a kunne, shiru ya yi yana sauraron saukar numfashinta na mai barci ta cikin wayar. "Rigimammiya kawai". Ya faɗa a fili tare da katse kiran ya ɗaura wayar a saman bedside drawer, sannan ya jawo laptop nasa ya cigaba da abin da yake yi, shirye yake a cikin kyawawan tsadaddun kayan barcinsa farare kal da su. Haka suka cigaba da irin wannan rayuwa a tsakaninsu, har Areef da Aseef ma suka koma Washington ɗin, gidan ya rage daga su gwaggo sai su Rimshar, sai sojojin da suke nan already. Gwaggo da mummyn Rimsha sun zage sai gyara su Rimshar suke yi, gyara na musamman suke yi masu, gyaran larabawar Dubai, kun san a can su gwaggo suka zauna first, su dilka da halawa, ga ingantattun magunguna masu tsananin kyau na larabawan Dubai da suke haɗa masu suna basu. A tunanin su gwaggon fa su Rimsha ba virgin bane, shi ne yasa suke yi masu wanna uban gyara haka...... (E LALAI AKWAI KALLO, NI PRINCESS TEEMA INA GEFE BABU RUWANA, SHI ASEEF MA BA'AYI WA HEARTBEAT GYARA BA YA AKA CIKA? BARE AN GYARA TA?🤔 LALLAI SUNA SO NE KAWAI SU HANA SU AREEF FITA WAJE KWATA KWATA IDAN SUKA DAWO, SAI DAI SU MAKALE A ƊAKI DA MATANSU, GASKIYA I PITY YOU GUYS, AKILA, RIMSHA, JEHAN!! DAMA YA LAFIYAR KURA? ASEEF KAWAI NAKE TUNAWA😂 IDAN YAGA HEARTBEAT TA YI KYAU MY PEOPLE'S KUNA TUNANIN ZAI BARTA KUWA? RIMSHA AND JEHAN ALLAH YA KWACEKU A HANNUN MAZANKU, AMMA ZAKU YABAWA AYA ZAƘINTA, NI DAI INA DA MALTINA MAI SANYI, IDAN NA JI YANE SAI NA KORA KAYATA, KO YA KUKA CE MY READERS?😂.) Cikin ƙanƙanin lokacin suka yi wani irin azababben kyau, fatar jikinsu ya kara yin wani irin luwai luwai kamar ka taɓa jini ya zubo, ga maganin karin girman breast mai inganci irin na larabawan Dubai da gwaggo ta haɗa masu, ga shi ya haɗu da suna da halittar abin, ai kan kace me kirjinsu ya ciwo fam, sun zama kamar basu ba, tamkar wasu taurari haka suke haskawa, irin kyau da fresh da suka yi baki ba zai iya faɗen ta ba, kyau iya kyau, haka daga ta ciki, su da kansu abin damunsu yake yi a yanzu, saboda a rana sai su canza pant sai ya fi a kirga, saboda zubar da uban ruwan ni'ima da suke yi, ga shi su ba za su iya fitowa su gayawa su gwaggon halin da suke ciki ba, ga mazan nasu duk basu nan, sai waya kawai suke yi da su, sai kawai suka daure suka cigaba da karɓar tsumin karin ni'ima suna sha, ita Rimsha ma da yake tsumin akwai daɗi, akwai zuma a ciki, idan aka ce ta sha kofi ɗaya da safe ɗaya da yamma, to kofi biyu take sha abinta, dan bata ma san maganin menene bane, ita dai abu ya yi mata daɗi, kuma ta ganshi available a cikin fridge, ai sai abin da hali ya yi, kamar sha zumami take a fagen shan zaki, shiyasa ta makalewa wanan tsumi babu kama hannun yaro...... E TO I PITY YOU OUR MEESHA😂🥺 (A karshen littafin nan zan rubuta maku kayan haɗin wannan tsumin mai matukar muhimmanci da zai kara maku abubuwa sosai In Sha Allah) Tsawon good 3 weeks su gwaggo suka ɗauka suna yi wa su Rimshar gyara na musamman, su kuwa su Lion abubuwa sun ɗauki zafi, ta ko'ina sun jijjiga faɗin Washington da kewaye. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E22 Date: 2/5/2024 Yanzu da komawar Lion almost 1 month suke nema kenan, abubuwa sai kara gaba suke yi, duk yanda kuka zaci abin ya wuci nan, dan fa har yanzu Lion ya ki fitowa ya yi maganar menene dalilinsa na ajiye aiki, hankulan jama'a a tsananin tashe yake, shi kansa his excellence yana cikin damuwa, ga zaɓe ta kusa zuwa, lokaci sai kara matsowa yake yi, ko Aseef his excellence ya kasa samun damar gani bare Lion, sun tare a gida sun yi shiru tamkar wasu malamai masu ɗaukar karatu, tsit babu wani motsinsu, sai dai suci abinci su yi wanka, su kama yin barci, idan suka tashi, su yi sallah su yi waya da matansu, ko fita daga gidan zasu yi, to fitar sirri suke yi, basu taɓa yarda su bari a san ma sun fita. A safiyar yau ne jama'a faɗin U.s suka tashi da maganar da ta jijjiga faɗin ƙasar bakiɗaya, maganar ya ɗagawa marasa gaskiya dayawa hankali, ya kuma kayatar da masu son gaskiya da kuma son samin cigaba da kwanciyar hankali ga kasarsu, his excellence ya shiga tsakanin tashin hankali da bai taɓa shiga ba a tsawon rayuwarsa, wannan magana ta tashin kan al'umma fiye da tunanin mai tunani, abin ya yi mugun jijjigasu. Wannan magana kuma ba ko wace magana bace face Lion ya cike Nominations form, kuma har ya yi screening, komai ta tafi mashi dai'dai saboda already shi ɗin sannanne ne a faɗin ƙasar, already kowa yasan halinsa, ya san abin da zai yi da wanda ba zai yi ba, sun san adalcinsa, hakan yasa party bata yi kasa a gwiwa ba wajen bashi form ɗin, kuma da ya cike basu yi kasa a gwiwa ba wajen yi mashi screening, yin hakan da suka yi ne ma ya kara tabbatarwa da Lion ɗin suma basu son mulkin his excellence, da alama da biyu yasa suka yi saurin karɓarsa, sai dai bai wani damu ba, matsalarsu ce, shi dai abin da yake gabansa kawai zai yi, kuma babu uban da ya isa ya ce mashi ga abin da yakamata ya yi, kun san shi ba'a tsara mashi abin da zai yi, idan kuma ya tsarawa kansa, to babu uban da ya isa ya kawo mashi shamaki, koma wanene bi ta kansa zai yi ya wuce. Nasan dayawa daga cikinku baku san menene nominations form ba ko? To form ce ta shiga siyasa, takarar shugaban ƙasa Lion yake son tsayawa, kuma har party ta yi screening nasa bayan ya cike form ɗin ya mayar masu, dama shi ba ɓoyayyen mutun bane, already sun san duk wasu bayanai a kansa, dan haka party ta bashi tikitin tsayawa tarar shugaban ƙasa a wannan zaɓe mai zuwa. Hakika Lion ya lura idan ba a president ya fito ba, akwai wasu abubuwa da zasu taka mashi burki wajen ruguje duk wasu azzalumai, president ne yake da Power sama da General of the army's, kuma shi Lion already kun san halinsa, baya yarda wani ya ɗaga mashi murya, baya yarda wani ya nuna mashi iko a duk in da yake, shi ji yake yi tamkar yafi kowa, hakan yasa ya nemi tsayawa takarar neman kujerar shugaban ƙasa mai gabaɗaya, kuma ya yi gagarumin nasara na bashi tikiti da party suka yi, nan take U.s ta ɗauka, kaka da jika zasu buga takara a tare, kuma kaso 80 cikin ɗari na jama'a sun fi supporting na Lion ɗin, dan kamar yadda kuka sani ne, kowa yasan shi ɗin mai adalci ne. Wannan abin yasa his excellence haɗa taron gaggawa a fadar shugaban kasa. Manyan manyan jiga jigan ƙusoshin gwamnati marasa gaskiya duk hankalinsu ya yi mummunar tashi, kama daga kan President, Governor, Chairman, Secretary to government of federation, Attorney general of the federation, Chief of staff, Senate president, Speaker of the house of assembly, Majority leader, Minister of agric, Minister of petroleum, Minister of power, Minister of work & housing, Minister of health, Minister of water and environmental protection, generals nasu na sojoji, irinsu lieutenant general, Brigadier general, major general, general da dai sauransu, duk wasu marasa gaskiya daga cikinsu sai da hankulansu ya yi matuƙar tashi, dan fa sun san Lion sarai ba da wasa yake yin abuba, in dai ya kafa kai a kan abu, ya furta kalmar e a kan abu, to ba shakka sai ya yi wannan abin, kuma muddin suka yi sake ya hau kan mulki, to wlh sun shiga uku, dan duk sai ya yi kaca kaca da su ya jasu a kan hanya, baya shiri da rashin adalci, kamar yanda na gaya maku shi kaifi ɗaya ne, baya tankwaruwa, dan haka yau saboda shi ƴan majalisun tarayya suka ɗauki tsawon 30mins suna tattaunawa a majalisan dokoki, kowa yana ta faɗar albarkacin bakinsa, har da masu cewa ai Lion ya yi yaro da matsayin kujerar shugaban kasa, shugaban ƴan majalisun ne, ya ce ba zancen yaro ake yi ba, zancen al'umma ake yi a yanzu, idan al'umma suna supporting nasa ai shikenan kuma, kuma abin da kowa ya sani ne, kaso 80 cikin ɗari na jama'ar faɗin U.s shi suke supporting, wannan abin tasa har gadon asibitin cikin white house sai da aka kwantar da His excellence and vice president, da sauran kananan ministocin masu rashin gaskiya..... Lion ya yi bala'in ƴamutsa hazo sosai a safiyar yau. Shi kuwa Lion ɗin, duk wannan tarzoma da kuma hazo da ya haɗa a cikin kasar, yana gida yana kwance abinsa, wayarsa ma yake yi da Meeshansa, sai kuka take yi mashi a kan ita wlh ya dawo tana kewarsa, idan ba haka ba yau ba zata ci abinci ba, daga yau har ranar da zai dawo babu ita babu cin abinci, ya zage sai rarrashinta yake yi, can waje ya tada tarzoma, ya sanya jiga jigan gwamnati zuwa gadon asibiti, nan kuma yazo ya zage yana ta rarrashin mace, macen ma ƴar under 15 years, 14 years ɗin ma bata jima da cikawa ba, amma saboda ita soyayya babu ruwanta da shekaru, shi da yake shirin zama president, shi da kasa gabaɗaya take jin tsoron kallon cikin idanuwansa, manya manyan sojoji ƴan'sanda ƴan siyasa da sauransu suna tsananin tsoron tunkararsa, saboda kwarjininsa, shi da hantar manyan maza take kaɗawa da jin sunansa, shi ne yazo ya kwanta ya ƙanƙame pillow yana biyewa shiriritar ƴar babynsa, kome zata yi shi dai'dai ne a wajensa, kome zata yi shi burgesa take yi, soyayya kenan......... Yanzu ba sojoji ba, idan gabaɗaya headquarter yake son a kawo mashi, yana zama president shikenan, yanzu yafi karfin soja, kowa dole ya yi mashi mubaya'a. Areef sai fama yake yi da amsa wayar manya manyan jiga jigan gwamnati a kan wannan case ɗin na Lion, shi kuma Lion ɗin ya ma ajiye normal sim card nasa da aka san shi da shi a kasa, ya sayi sabo dal, saboda Meeshansa da mommansa kawai, su kawai yake kira, kuma su kaɗai ne suke iya kiransa su same shi, bayan su, duk wanda zai kirashi, a kashe zai samu number, ya ce baya son hayaniya, kuma har yanzu lokacin da zai buɗe baki ya bawa jama'a amsa bata yi ba, idan suka cika matsa mashi ma, barin masu kasar zai yi sai lokaci primary election ya dawo........ Babbar magana, yau ake yinta a cikin littafin TRIPLETS, wasan yanzu za'a bugata ta gasken gaske kuwa, Lion president of United States! Waye ya taɓa tsammanin haka daga gareshi? Abin dai akwai show, akwai kuma kallo, yanzu ne ma dole kowa ya dawo karkashin ƙafarsa, karfin iko, isa da izza zata karu, su kansu sojoji yanzu ne zai juyasu son ranshi, dama yaya aka cika da wannan uban izzar tasa? Bare kuma ace ya zama president? Abin dai ba'a cewa komai, dan baki ma bai isa ya zayyano kalar abin da Lion zai yi ba! Sai dai wani hanzari ba gudu ba, kuna tunanin His Excellence zai yarda ya kyale shi kuwa? Kada ku manta da akwai marasa gaskiya da yawan gaske da basu son ya hau kan kujerar mulkin, shin kuna ganin zasu yi shiru su zuba mashi idanu ya hau kan wannan kujerar kuwa? Anya hakan zata yiwu kuwa? Akwai bala'i ba kaɗan ba, dan su turawa basu iya takun saka ba, sun iya zagon kasa da munafurci tamkar a kansu aka sauketa! Sai dai muce Allah ya kare Lion daga sharrinsu da makircinsu kawai, amma faɗa da waɗan nan shegu no be small thing!!. Kwance yake daga shi sai ƴar short wadda bata kai rabin tsala tsalan jajir ɗin cinyoyinsa ba, short ɗin ta ɗameshi sosai, irin wandunan nan ne masu kama jikin mutum, banda kasancewar kalar short ɗin white, da sai ace bai sanya komai ba, amma da yake white ce, sai ya zama za'a iya ganewa, daga ta sama babu riga a jikin nasa, ainahin kyakkyawa kuma kakkarfar surar jikinsa ta bayyana, ya yi wani haske na musamman, dama zuwansa Nigeria rana ta buga shi ya ɗan yi duhu, amma yanzu ya kara haske, ya zama normal colornsa, skin nasa ta kara wani irin fresh na musamman, har wani sheki na daban yake yi, da alama yasamu kwanciyar hankali over, dark black curly hairnsa har wani tsawo suka kara, sun kara wani uban curly alamar yana samun hutu sosai, sai kyallin gashin yake yi sosai, idanuwan nan nasa sun koma normal, ainahin kyan fuskarsa ya kara bayyana, laɓɓansa sun wani kara uban ja sosai, tamkar ya yi coloring nasu ne, ga wani laushi na musamman da soft lips ɗin nasa suka kara, farin cikin idanuwansa sun kara haske sosai tamkar madara, kwayar idanuwansa sun kara fito da ainahin blue nasu sosai, gashin gerarsa kuwa, har haɗewa suka yi, saboda yawa, sai dai suna kwance luf, sajen nan nasa ya wani kara kwanciya, kai tsayawa zayyana maku irin kyan da Lion ya kara yi cikin wannan wata guda ɗin da ya yi a Washington ma ba zai yi wu ba, ya koma ainahin Lion ɗinsa, baki ya yi kaɗan ya iya zayyano kyansa, sai dai ku kawata a ranku, amma fa tamkar yadda ya kara wannan kyau ɗin, haka ita ma Meeshan nasa ta kara tsantsar kyau, dan suna shan gyara, skin nata ma kawai ya isa ya sanya Lion ya susuce mata idan ya ganta, ta zama tamkar wata tauraruwa mai matuƙar hasken gaske. Kwance yake a saman katafaren bed nasa na alfarma, banda daɗɗaɗar kamshi da yake tashi a bedroom ɗin, babu wani abin da zaka ji kuma, A.c ma kaɗan kaɗan take futa, saboda garin da akwai sanyi sosai, so gudu kaɗan ya sanya mata, kamar yanda kuka sani ne, komai na cikin bedroom nasa white color ne, to hakan suke, sai wani sheki suke yi, tamkar ba'a taɓa taɓasu ba, bed sheet dake shunfuɗe a saman bed nasa ma kawai abin kallo ne, fari kal da shi, ga wasu kyawawan throw pillows different design na bed sheet ɗin dake a saman bed ɗin, ya tada kansa da guda ɗaya, ya ɗaura hannunsa a saman ɗaya, ya kuma ɗaura ɗaya a saman Lion chest nasa, yau wani irin fresh face nasa ta yi, kamar wanda ya wuni yana barci yanzu ya tashi. Tsadaddiyar wayarsa na'a mannne a kunnansa, kamar yadda kuka sani ne, waya yake yi da Meeshansa, sai binta da okey yake yi, ya ce su yi video call, taki yarda, dan ba zata iya jure ganin cikin kwanciyar idanuwansa ba, shi kuma baya son ya yi mata dole, lallaɓata kawai yake yi, dan kwana biyun nan rigima sosai take yi mashi a kan ya dawo, kuma baya ganin laifinta, dan shi ma kewar tata yake yi over, shiyasa yake biye mata. Lumshe idanuwansa ya yi, a hankali ya motsa laɓɓansa tamkar baya son yin magana ya furta "Baki gajiya da yin kuka ne?". Already kunsan yadda yake magana, sai ka rantse da Allah bai motsa laɓɓansa, saboda kasa kasa yake furta kalamai, cikin sanyin murya, nutsuwa da kuma kamala. Kuka mai sauti ta sanya mashi dan ya ji cewa ita fa yanzu ba kukan shagwaɓa take yi ba, da gaske take yi, ita ma tana kwance ne a saman bed nasa dake bedroom nasa na gida Nigeria, tana rungume da pillow kamar kullum, kayan barci ne wando da riga kaunin pink a jikinta, yanzu ba jimawa ta tashi daga barci, ko breakfast bata ci ba, tana tashi ta kirashi, ta hau zuba mashi rigimar sai dai ya dawo, yanzu almost 1 month yana can yaki dawowa, ita gaskiya ta gaji, shi ne kalar rigimar da take zuba mashi yau. "Shikenan ya isa kukan haka, zan zo to". Ya bata amsa yana maido da kallonsa izuwa bakin kofar bedroom ɗin nasa, dan ya ji motsi a wajen. Areef ne ya shigo bakinsa ɗauke da sallama, daga shi sai short shi ma, sai dai shi nashi short ɗin ba mai kama jini bane ba, daga ta sama babu riga a jikinsa, shi ma ya kara tsantsar kyau sosai, hasken fatarsa ta kara fitowa sosai, ba shakka zamansu a Naija sun ɗan yi duhu, yanzu tamkar ba su ba, sun koma ainahin kalarsu. Yana zuwa ya haye saman bed ɗin tare da kwanto da kansa a saman pillown dake a saman kirjin Lion ɗin. Hannu Lion ɗin ya kai yana shafa face ɗin Areef ɗin yana mai cigaba da magana da ita, shi kuma Aseef Sarkin rigima, yana can suna aikin yin video call da Heartbeat, suna faman kashe juna da kukan sun yi kewar juna. "Da gaske Noorish zaka zo?". Ta faɗa cikin zumuɗi tare da murmushi a saman face nata, tamkar ba ita ce take zuba kuka yanzun nan ba. "Yeah my Meesha ba dai kina so na zo ba?". Ya yi maganar yana jan dogon hanci Areef. "E ina son kazo, yaushe to zaka zo?". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Nan da one week ya yi ko?". E ya yi ta amsa mashi da shi cikin zumuɗi. Abin da bata sani ba shi ne, already dama yana da plan na barin U.s a yanzu, dan ya je ya ɗan huta, ya gaji da jin surutan jama'a, ya hargitsa ko'ina, lungu da saƙo na kasar dukka zancensa ake yi, ya yamutsa hazo, so yana da buƙatar ya ɗan fita kasar ya sarara, shi ne yasa ya ce mata zai zo, zai je ne ya ɗan huta, ya yi kamar 1 week, sai ya dawo ya ɗaura daga in da aka tsaya, dan zaɓe nata kara matsowa, time na primary election ta kusa. "Noorish mekakeson na tanada maka kafin kazo?". Shiru ya yi na ƴan mintoci kafin ya bata amsa "Ke kaɗai kin fi mani komai, ganinki ma is okey". Wani irin mugu mugun daɗi ta ji ya rufeta, tana ƙoƙarin sake yin magana gwaggo ta shigo ɗakin bakinta ɗauke da sallama tana faɗin "Zoki wuce sarkin yin waya, tun yaushe na zuba maku ruwan nan a cikin baff, ga su Jehan nan duk sun shiga nasu saura ke, naki har ya fara yin sanyi, maza ajiye wayar nan kizo ki wuce, idan kin gama sai ki zo ki cigaba da yin wayar". Turo baki ta yi tana faɗin "Kai gwaggo wlh ke kincika sa ido, ni Allah kawai ku barni". Harara ta wurga mata tana faɗin "Kafa dai na cika sanyawa ba ido ba, zaki zo ki wuce ne ko sai na iso wajen na sameki?". Turo baki ta kara yi tare da mikewa ta sauke kasa daga saman bed ɗin. Duk abin da suke yi yana jinsu, wani irin daɗi yake ji idan yana sauraron diramar mommansa da Meeshansa, ya lura akwai kauna mai tsananin zafi na wuce musali a tsakaninsu, mommansa tana sun Rimsha da Jehan fiye da tunanin mai tunani. Haka ta wuce gaba gwaggon ta rufa mata baya, katse kiran ya yi dan ya barta ta yi abin da momman tasa take son ta yi, bai san tsuma mashi ita ake yi ba. A sama bedside drawer ya ɗaura wayar yana mai dawo da kallonsa a kan face ɗin Areef da ya tsare shi da idanu. Harara ya wurga mashi kafin ya tambayi meyasa yake kallonsa har haka. Duka Areef ɗin ya kai mashi a damtsen hannunsa yana faɗin "Amma Lion ka cika ɗan duniya, dama kana son Rimsha ne? Dama waya ma kake yi da ita ko? No wonder mana naga kana kara kiɓa, haba Rimsha tana rage maka zafi, nasan kullum sai ta sanya ka ka samu gamsuwa kafin ku yi good night, shiyasa ko a jikinka kake wani zaune a nan hankalinka a kwance, mu ka rabamu da namu baby's ɗin, kai kananan kana shan love naka, ni wayar ma bata rage mani zafin komai, sai na sha.........." Bai kai karshen maganar ba Lion ɗin ya kai mashi duka a baki. Cap ya capke hannunsa bai bari ta kai bakin nasa ba, mikewa daga kwanciyar da yake ya yi yana faɗin "Allah Lion bazaka dakeni ba, karya na yi ne? Ka samu ƴar mutane sai zuba mata kalaman love kake yi, a can gari duk sai maganarka suke yi, kowa tsoron tunkararka yake yi, amma a nan kazo ƴar baby tana zautar mana da kai, ita ce kwanciyar hankali da kuma farincikinka". Kwace hannunsa Lion ɗin ya yi, da gaske ya sake ƙoƙarin kai mashi duka. Rike hannunsa a karo na biyu Areef ɗin ya sake yi yana faɗin "To baga maganata ta tabbata ba, dubi yadda heronka ta miƙe tsaye gam kamar zata fasa wando, saboda ka yi magana da Rimsha". Yana magana yana dariyar iyashege. Aseef ne ya faɗo masu ɗakin bakinsa ɗauke da sallama, sai turo baki yake yi, ya zo sanar da Lion ɗin ne shi fa yana kewar matarsa, a barshi ya je wajenta, ita ma kewarsa take yi. Saman bed ɗin shima ya haye, still dai shi ma short zallah ce a jikinsa. Yana hayewa saman bed ɗin ya ce "Lion kaima fa kana kewar matarka, ga penis naka ya miƙe tsaye". Ya yi maganar yana ƙoƙarin kwanciya. Dariya sosai Areef ya tuntsure da shi, cikin dariyar yake faɗin "Kagani ko? Aseef ma ya gaya maka gaskiya, kawai ka dai'na wani yi mana kauce kauce, ka je ka rungumo ƴan babynka ku dawo nan, amma dan girman Allah ka bita a hankali, wlh bata girma ba". Yana magana yana dariyar mugunta. Da sauri Aseef ya ce "Tab wai waye yaga Lion da Meesha on the bed? A first night nasu, Lion kada ka kashe mana our Rimsha fa, dan ka kalleta kwata kwata bata wuce mu goyata ba, duba penis naka fa, yafi karfinta gaskiya, ka bari kawai ta girma". Ya kai karshen maganar yana ɗaura wayarsa a saman bedside drawer. Su da yake sam sam basu da kunya, shiyasa suke zuba maganganunsu son ransu ba tare da jin kunyar juna ba. Shi dai Lion ya rasa me zai ce masu ma, dan bashi da bakin magana, sun fi karfinsa a wannan fanni, duk abin da suka faɗa gaskiya ne, yana tsananin kauna da kuma sha'awar Meeshansa, a duk time da ya ji voice nasa sai Heronsa ta niƙe gam, tamkar zata fasa mashi short nasa, dannewa kawai yake yi, wani lokaci kafin su gama hira sai ya jiƙa short nasa da abin, shi kaɗai yasan me yake ji a ransa, ba yadda zai yi ne, ko kusa ko alama baya kawowa a ransa cewa zai kusanceta a nan kusa, dan yasan ba zata iya ba, tayi ƙanƙanta, amma da suna tare, zata rage mashi raɗaɗin da yake ji ta hanyar wasannin da ita, zai samu sassauci sosai ta wannan hanya, amma ina ta yi mashi nisa sosai, haka yake fama bawan Allah. "Lion bari na baka shawara, kawai ka ɗaukota, zata rage maka raɗaɗi". Cewar Aseef. Komawa ya yi ya kwanta tare da lumshe idanu ya jawo bargo abinsa, dan maganganun da suke yi mashi ɗin nan ma kara jaza mashi raɗaɗi suke yi. Su kuwa, haka suka cigaba da tsokanarsa har barci ya ɗaukesu dukkansu a saman bed ɗin. Basu suka farka ba sai azzahar, bedroom nasu Areef da Aseef suka koma, shi kuma Lion wanka ya shiga toilet zai yi, suma suna zuwa wanka suka shiga yi. Bayan sun gama ne suka shirya cikin jallabiyas farare masu kyau, suka zo suka fara gabatar da sallar azzahar a tare gwanin birgewa da ban sha'awa. Bayan sun idar, addu'a sosai suka yi, kafin su shafa su miƙe izuwa saman dining table. Kamar yadda suka saba cin abinci, haka suka haɗu dan suci. Dukkansu sai da suka bawa Aseef first spoon nasu, sannan suka fara ci, duk wanda ya kallesu, sai sun yi matuƙar burge shi, suna da tsananin ɗaukar hankali, musamman yanda suke tsananin kaunar junansu, abin ba'a cewa komai. Haka suka cigaba da rayuwa su uku kawai a cikin gidan Tga yana Nigeria, su uku suke rayuwa cike da kulawa da kaunar juna, haka suka sake kara sati guda a cikin gidan, idan suna tare suna tsokanar juna sai sun yi mugun burgeka, mafiya yawan lokuta Lion suka fi yawan sakawa a gaba suna tsokana, musamman idan ya yi waya da Rimsha, sai sun takura mashi a kan bananarsa ta miƙe tsaye gam, su saka shi a gaba suna zuba mashi tsiya. Yau dai da Lion ɗin ya gaji, sai ya danne Areef wai zai duba yaga shin ko dai shi bananar tasa ta dai'na harbawa ne da idan ya yi waya da Jehan bata miƙewa, ko kuma Jehan ɗin ce bata iya romance word ba? To idan bananar ce bata harbawa, zai yi mashi maganinta yau, sai dariyar mugunta Aseef yake yi yana kallonsu. Da yaga kallon ma ta yi mashi kaɗan, sai ya masto ya dannewa Lion ɗin kafafun Areef ɗin da kyau yana faɗin wlh kada Lion ya kyale shi, ya tuɓe masu shi su duba, dan kada azo ya kasa dis virgin na Jehan. TRIPLETS BASU DA KUNYA KO MISKALA ZARRATIN WLH😂 NAYI NAN NI DAI, SAI MUN HAƊU GOBE, YAU DAI ZA'AYIWA AREEF ZINDIR ADUBA BANANARSA, ASEEF AKWAI IYA MUGUNTA, HARDA SU RUKE KAFAFUNSA, DAN LION YA SAMU DAMAR TUƁE SHI DA KYAU😂 JEHAN ZA'AYIWA MIJINKI ZINDIR😂 WLH LION MA YA IYA TSIYA BA KAƊAN BA WANI LOKACI. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E23 Date: 3/5/2024 Da dai Areef ya ga da gaske tuɓe shi Lion ɗin zai yi, sai ya sanya karfi zai kwaci kansa, aikuwa Aseef sai ya yi maza ya kara danne shi, sai dariyar mugunta yake yi, shi kuma Lion ya ruke hannayensa dukka biyu tare da hayewa saman kansa da kyau, sannan ya kai hannu zai zame mashi wando kasa. Ihu Areef ɗin ya zunduma yana faɗin "Please ka bari mana, Allah nima dai haka nake fama, to ni ku tsaya na cire maku short ɗin da kai'na ba sai kun cire mani ba, me a ciki dan na tuɓe maku? Naga dai duk abu iri ɗaya muke da shi, kuma dukka girmansu ɗaya, dan haka ni ku bari na cire da kai'na kada ma kuyi ku ji mani ciwo". Aseef kam me zai yi, dariya kamar zai mutu, har da kyakyatawa. Kallon Aseef ɗin Lion ya yi, calmly ya ce "Heartbeat in kyale shi?". Girgiza kai ya yi. "A'a kada ka kyale shi, kafin Jehan ta gani mu rigata gani, mu duba shi da kyau kada ya zamana bashi da lafiya aka aura mashi ƴar mutane, ya je ya cuceta a banza......." Yana magana yana dariyar mugunta. Areef ɗin ne ya katse shi da cewa "Allah Heartbeat idan na kamaka zaka yi bayani ne". "Ka bari mu rabu da kai before kayi zancen taɓa mana pleasure". Cewar Lion ɗin. "Good my Lion, yanzu fa a hannu yake, amma yana zancen idan ya kamani zan yi bayani, ya bari ma na kuɓuta tukunnan". Cewar Aseef ɗin. Hannu Lion ya kai ya zame short ɗin kasa abinsa, dan su fa ba kunya garesu ba. Dariya sosai Aseef yake yi yana faɗin "Lion ruke shi da kyau bari na duba tun yaushe rabon bananar da ta miƙe". "Okey come and check". Lion ɗin ya bashi amsa. Areef ɗin kuwa ya kwanta shiru ya zuba masu idanu, yau wani irin farinciki ma na daban yake ji, koba komai yau Lion ya biye masu sun yi wasa tun bayan shekaru 12 da suka wuce, tun shigar Lion aikin soja ya dai'na biye masu suna irin wannan wasan a tsakaninsu, sai dai kalaman da suke nuna suna kaunar juna, amma a da can baya time da suke 15 to 20 years, wasanni kala kala suna yi a tsakaninsu, idan ta kwaɓe masu su daki juna, su yi faɗa kamar ba gobe, duk su jiwa kansu ciwo, idan kuma ta yi kyau, sai sun baka sha'awa, to sun jima rabon da Lion ya biye masu irin na yau, hakan tasa Areef cikin farinciki ba kaɗan ba, sai ya kwanta shiru yana bin fuskokinsu da kallo, duk da cewa shi Lion kullum a suffa ɗaya yake, baya dariya ko murmushi, kullum fuska a ɗaure, amma a yau ba zai hana ka gane yana cikin farinciki ba, duk da bai yi dariya or murmushi ba, amma alamun farinciki ta bayyana a saman face nasa, shi kam Aseef ai nasa farincikin ma na daban ne, dan dariyarsa har da kyakyatawa, abin da bayayi, yau shi ma ya yi. Kiran wayar Lion da aka yi ne tasa Lion ɗin ya sauka daga kan Areef ɗin yana faɗin "Check him for me our heartbeat, am coming, let me pick this call, I knew it's momma or Meesha". Ya kai karshen maganar tare da ɗauko wayar. Shi kuma Aseef matsowa ya yi da gaske zai duba bananar ta Areef ɗin, a ɗari da sittin Areef ɗin ya miƙe ya damko gashin kansa yana faɗin "Dubawa zaka yi ko? Okey check it mana". Ihu Aseef ɗin ya zunduma yana faɗin mugu kawai. Haka suka cigaba da tsokanar juna, Areef ya mayar da short nasa ya haurar sama yana cin zalin Aseef ɗin suna dariya. Shi kuma Lion picking call ɗin ya yi tare da dirowa kasa daga saman bed ɗin ya nufi balconynsa. Kamar yanda ya yi tunani hakance ta kasance, Meeshansa ce take kiransa. Yana manna wayar a kunne ta sanya mashi kuka, shiru ya yi yana sauraron kukan nata, sai da ta rera shi kaɗan, da ya ji ta fara yawa kukan, sai ya ce "Is okay my rigimammiya, yau kuma me aka yi?". Cikin muryar kuka ta fara magana "Noorish you said that you're coming yesterday, amma shiru baka zo ba, and today ma baka taso ba, what do you want me to do idan ba kuka ba?". Lumshe idanuwansa ya yi tare da zama a saman ɗaya daga cikin lumtsuma luntsumar tsadaddun Chinese chair dake kusa da small pool nasa dake wajen, nisawa ya yi kafin ya bata amsa da "Is okey, tomorrow In Sha Allah by this time around we are together, you sleep on my chest, shikenan?". Cool murmushi ta saki tare da rufe fuska da tafin hannunta tana faɗin "E shikenan". Jinjina mata kai ya yi tare da faɗin "Yesterday momma was told me that zaku je wani wajen, kun je ne? I told Tga to take you to the place, ya kai ku ne?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "No we didn't go anywhere today, amma ban sani ba maybe tomorrow". Ciro wayar daga kunnensa ya yi, a in da ya duba time 9:30pm, dare ta fara yi. Calmly ya ce "Where are you now?". Ya yi maganar muryarsa cike da kishi tab, dan kada ace yanzu tana waje harabar gidan, duk da ya hanata fita, amma ya san halinta sarai, yanzu ba ƙaramin aikinta bane ta fita tsakar gida suna waya. "Am inside your bedroom holding your pillow after i sleep on your bed". Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya yi kasa da murya sosai kamar wani yana yi masu laɓe. "Muyi video call?". Ya faɗa yana mai da kallonsa a kan Aseef da Areef dake a saman bed nasa suna kwance, sun haɗe kai waje guda, da alama wani abin Aseef yake nuwa Areef a wayarsa da ya sanya suka haɗe kan nan nasu waje guda. "Allah Noorish ni kunyarka nake ji, ba zan iya yin video call ɗin nan ba, ina kewar face naka over, amma ni ba zan iya watching naka kana watching nawa like film ba". Ta yi maganar a tsananin shagwaɓe. Shiru ya yi yana tunanin irin tsananin kewarta da yake yi, abin ba'a magana. Jin ya yi shiru ne yasa ta ce "Sorry Noorish tom mu yi video call ɗin". "No just leave it kawai, bana son abin da baki so, gobe zan zo na ganki ai". Cool murmushi ta saki kafin ta cigaba da zuba mashi shagwaɓa yana biye mata shi kuma, sai karfe 2 dai'dai barci ya ɗauketa, sannan ne ya katse kiran tare da miƙewa ya komo cikin bedroom ɗin. Aseef da Areef already sun yi barci tun karfe 1, suma hira da matansu suke yi a waya har barci ya ɗaukesu ruke da wayoyi a hannu. Saman bed ɗin ya haye tare da tattare wayoyin nasu ya ɗaura a saman bedside drawer, sannan ya gyrawa Aseef kwanciya ta hanyar sauke hannunsa da ya ɗaurawa Areef a fuska, sun wani jeru a saman bed ɗin tamkar sun san barci zai ɗaukesu. Ɗan bakinsa Lion ɗin ya kai ya bawa kowannansu sumbata a goshi, a hankali ya motsa laɓɓansa ya fara tofa masu addu'ar barci, dan yasan barci babu shiri ne ya ɗauke su, ko addu'a basu yi ba, dan haka bawan Allah sai shi ya yi masu addu'ar tare da shafa masu bayan ya kammala. Rayuwarsu idan suka haɗu su uku waje guda ko makiyinsu ne sai sun burge shi, rayuwarsu yaruwa ce mai cike da darusa da dama a cikinta, shi kansa kaunar juna da suke yi babban darasi ne mai matuƙar girma a rayuwar ƴan uwa, bugu da kari ga matuƙar fahimtar juna dake a tsakaninsu, ga hakura da abin da ɗaya baya so, ba wai dan basu so ba, duk yanda suka kai ga son abu, idan ɗayansu baya so, to suna iya hakura, dan su girmama ra'ayin juna, suna respecting na juna, ba su nuna kamar ma shekarunsu ɗaya, idan Lion ya ce su bar abu, to suna bari, idan Areef ya ce su bar abu baya so, to suna bari, haka shi ma Aseef ɗin, idan ya ce su bari, suna bari koda basu so, dan kawai su girmama ra'ayin juna, kuma ta hakance kawai zasu samawa kansu shakuwa da kaunar juna, rashin girmama ra'ayin juna babban barazana ce ga shakuwa da kuma zaman tare da mutane, so su suna kiyaye wannan sosai a tsakaninsu, ga shi idan sun haɗu suna zuba wasa son ransu, su yi ta zolayar juna, abin gwanin birgewa, baki ma ba zai iya zayyano irin birgewar ba, ace mutane su taso lokaci guda, a haifesu tare TRIPLETS kamar haka, shekarunsu ɗaya, amma suna irin wannan rayuwa mai cike da kawa da ɗaukar hankali tare da ɗaukar darusa, ai abin dole ya burge, shekarunsu fa ɗaya, ya zaki ji idan aka ce ƴaƴanki ne hakan? Ƴaƴanki ne suke tsanani kaunar juna tare da haɗin kai da son farantawa juna irin haka? Ranar da kika mallaki kamarsu ya zaki ji? A yanzu shakuwa tsakanin ƴan uwa ta yi karanta a zamanin nan, sai kiga yarinya budurwa tana da yayarta mace a gida, amma ta fito neman shawara wajen kawaye, to menene amfanin sister taki ko mahaifiyarki? Abin yana yi mani ciwo sosai, bana son naga ƴan uwa suna koda faɗa ne haka, ina kaunar naga ƴan uwa masu son juna koda kamar rabin yanda TRIPLETS suke son junansu ne, su yi komai a tare, su yi shawara a tare, su yi abinsu su rufe su binne kayansu ba tare da kowa ya ji ba, su yi wasa da dariya, su kaunaci farincikin juna, su girmama ra'ayin juna, akwai tsananin daɗi haka, dan Allah my peoples kowa ya kaunaci ƴan uwansa, babu abin da hakan zai rageku da shi face ma wani kara samun kusanci da Ubangiji da zaku yi, saboda idan kuka shaku sosai, zaku runƙa ƙoƙarin ganin kun zauna kunyi tunanin abin da zai taimaki rayuwarku, zaku yi ƙoƙarin gina kanku a kullum, ku gwada ko da rabin soyayyar dake a tsakanin TRIPLETS wa ƴan uwanku, zaku ji daɗi, kuma zaku sanyawa PRINCESS TEEMA taku ta amana ruwan albarka!!!. Bayan ya kammala tofa masu addu'ar ma sai da ya sake basu hot sumbata, sannan ya miƙe ya sauko kasa daga saman bed ɗin. Jibgegiyar duv nasa ya jango ya rufesu zuwa iya cikinsu, sannan ya ɗan kara masu gudun A.c kaɗan kafin ya wuce ya nufi cikin katafaren dressing room nasa, kada ku mance yanzu fa ya dawo ɗaularsa na Washington, ba irin gidansa na Naija bane, wannan dressing room nasa na nan ma kawai ta fi girman palournsu na Naija, Already kun san komai. Kayansa ya fara shiryawa, sam bai gayawa Aseef a kan gobe zai wuce Nigeria ba, shammatarsu yake son yi ya tafi abinsa, idan ba hakan ya yi masu ba, ba zasu taɓa shiryawa da Aseef ba, dan sai Aseef ɗin ya ce zai bisa, shi kuma baya son hakan, a nan yake son barinsu, dan akwai gagarumin aikin da Areef yake yi mashi, aikine na sirri, kun san Areef fa sune sirri, to aiki ya haɗa shi da shi, yasan idan ya ce su je Naija a tare, to ba zai yi mashi aikin a kan lokaci kuma yanda ya kamata ba, saboda Jehan da Momma, zai biye masu su yi ta shirirta, shi ne yasa gara ya barsu a nan, shi kuma Aseef abin da yasa baya son su koma Naija a tare, dan baya son su baro Areef ɗin shi kaɗai a cikin gidan, ba zai ji daɗi ba, shi ne yasa zai bar mashi Aseef ya ɗebe mashi kewa kafin ya dawo. Tsab ya shirya duk wani abin da zai buƙata, ya haɗa komai kafin ya fito izuwa saman bed ɗin, sun zo sun cika mashi bed, yau a bedroom nasa za su kwana, haka ya kwanta a kusa da su bayan ya yi addu'ar barci, tun bai kai ga tafiya ba har ya fara kewarsu, su ɗin jini ne da hanta bayin Allan, ko ina cikon QUADRUPLE ɗin nasu yake? Ya mutu ne ko yana raye? Allah masani sai kuma alƙalamina Ni PRINCESS TEEMA taku ta amana, dan haka mu kasance a tare kawai dan jin komai. Yana kwanciya ba jimawa ya yi barci abinsa. A gida Nigeria kuwa, washegari gwaggo ta gayawa Tga da akwai in da zai kai'su. Cikin girmamawa ya ce mata Lion ya gaya mashi tun jiya. Tun da Tga yake a rayuwarsa bai taɓa girmama wani in ma mace ko namiji bayan Lion da yake ogansa ba, sai a kan gwaggo, har cikin ransa yake jin Kaunar gwaggon, tun da ya ji cewa ita ce ainahin mahaifiyarsu Lion, daga nan ya ji yana mugu mugun respecting nata. Shiryawa suka yi, gwaggo, mummyn Rimsha, Jehan, Akila, and Rimsha, TGA ya ɗaukesu a mota suka bar gidan, shi kuma daddyn Rimsha a yau ya bar kasar, dan Lion ya ce mashi ya zo Washington ya samu Areef da akwai abin da zasu yi a tare. (Sai shiryawa su his excellence kitimurmura Lion yake yi fa, kome su Areef suke sake shiryawa kuma?🤔 Namu ido ko my peoples?.) Kai tsaye wani katafaren shop na gyaran gashi, lalle da kuma kitso gwaggo tasa Tga ya wuce da su. Ko da suka isa wajen yaki yarda ya jiransu a mota, har cikin wajen ya rakasu, dan ya tabbatar suna cikin lafiya da tsaro, ya tabbatar babu abin da ya samesu, dan haka sai ya bisu har ciki, sai kallon shi tsala tsalan ƴan matan da suka zo wanke kai suke yi, manyan mata ne masu ji da class, ƴaƴan manya, dan shop ɗin bana yara bane, na manyan mata ne. Shi kuwa Tga abin da kuka sani ne, kallo wannan ma babu wacce ta samu ya ɗaga idanu ya kalleta, dan shi bai ma san suna yi ba, ga fuskarsa tamkar ta shanu, ya wani murtuketa gam, babu alamar ya taɓa sanin menene murmushi ma, sak face ɗin Lion haka yake shi ma, abu ne da kuka rigada kuka sani. Duk waɗan nan awannan da su Rimsha suka kwashe ana zuba masu zanen flowers na lalle mai bala'in kyau tare da gyaran gashi, duk yana tsaye bai ko motsa ba, kuma sam bai zauna ba, yana tsaye a matsayinsa na cikakken soja mai jini a jika, yana ta kula da su, dan Lion ya jaddada mashi a kan ya kula da su over, shi ne yasa yake ƙoƙarin jaddada hakan. Sam Rimsha ta mance da cewa Lion baya son lalle, haka ta bari aka zuba mata zanensa ya fito reras, ya yi matukar kyau na wuce misali. Ita gwaggo a tunaninta gabaɗaya TRIPLETS zasu zo a tare, shiyasa ta tattaro har da su Jehan ɗin dukka dan ayi masu gyaran kai, bata san iya Lion ne kawai yake hanya ba. Haka suka gama abin da za su yi, suka je shopping suka yi sayayya, Lion yasa Imran ya biya kuɗi ta hanyar yi wa masu shops ɗin transfer, sannan suka nufi gida, sai murna Rimsha take zabawa, baki yaki rufuwa, an zuba mata lalle kam kamar ba gobe. Sai da suka koma gida ta shiga bedroom ɗin na Noorish ɗin nata dan ta yi wanka ta yi sallar azzahar, a nan ne ta tuna cewa Noorish baya son lalle, nan take hankalinta ya yi mummunar tashi na wuce misali, wani irin tukukin bakin ciki ta ji ya taso mata, kullum tana damunshi a waya akan yazo ta yi kewarsa, ya taso yana zuwa kuma ta je ta yi abin da zai bakanta mashi rai, sam bata ji daɗin hakan ba. Zama ta yi a saman bed ta murji kukanta iya son ranta, sai da ta ji kanta ya fara yi mata ciwo ne ta hakura, ga kan nata ya sha gyara na gasken gaske kuwa, sai wani kyalli curly hair nata yake zubawa, kamar ka sace ta ku gudu, ta yi kyau ne har ta gaji da kyau, dole ma Noorish ya ruɗe idan ya zo ya ganta. Bayan ta gama murzan kukan ne ta miƙe ta nufi toilet, wanka ta yi tare da fitowa ta shirya, sannan ta yi sallah kafin ta fita zuwa kitchen ta ɗebo abinci, ta dawo cikin bedroom ɗin nasa ta zauna ta fara cin abincin nata, suma su Jehan abincin suke ci a bedroom na gwaggo. Bayan ta ci ta yi nak, sai ta hau gyara mashi bedroom ɗin babu kama hannun yaro, da ta kammala sai ta rufe ko'ina tare da zuba mashi air freshener irin wanda yafi kauna, ta bulbula son ranta, tana kammalawa ta wuce bedroom ɗin mummynta. Babu kowa a cikin ɗakin, dan haka sai ta dawo bedroom na gwaggo. A nan ta samesu dukkansu, mummynta da gwaggo suna a zaune a saman bedside drawers dake gefe da gefen bed ɗin, ita kuma Brr Naurat tana zaune a saman bed ɗin, Jehan ta tada kai da cinyar Brr Naurat, ita kuma Akila tana kwance a gefe guda tana aikin latsa waya, sai sakin uban murmushi take yi, da alama ita da Heartbeat nata suke chatting, dan minti minti sai kuga ta turo baki alamar kalmar shagwaɓa ya turo mata, sai magana Brr Naurat take yi mata, amma ina hankalinta na'a kan wayar, sai da mummyn Rimsha ta miƙe ta kwace wayar, sannan ne ta farga ashe ma a cikin mutane take. Rufe fuska da hannunta ta yi tana dariya kasa kasa. "Akila sarkin soyayya ba". Cewar mummyn Rimsha, ta yi maganar cikin zolaya........ Hmmm Mummyn Rimsha fa bata san cewa Rimshar tattabara ce uwar soyayya ba, dan bata san yanda take birkitawa General of the army's kuma ɗan takarar shugaban kasa a yanzu lissafi ba ne, duk ta susutar da bawan Allah, ya fita waje ya yi wa mutane zarra, idan ya dawo gida kuma ya cigaba da biyewa Rimsha ya zama kamar wani ƙaramin yaro, oh Rimsha duniya ne wlh, mum tana cewa Akila sarkin soyayya, ai ga sarkin soyayya kam nan ta fito daga cikinta. "Ku bani hankulanku waje guda". Cewar Brr Naurat. Nutsuwa suka yi tare da tattare mata hankulansu, Rimsha dake a tsaye ma Brr ta ce tazo ta zauna, dama magana za'ayi a kanta ai, dan ita ce mijinta yake hanyar dawowa yau, ita za'ayiwa nasiha, su Jehan dai zasu ji nata ne kawai kafin azo yi masu nasu idan mazansu zasu dawo. Shiru suka nutsu kamar ba su ba, da Brr Naurat da gwaggo ne suka fara yi masu nasiha mai ratsa zuciya ta sanya zuciya yin laushi, sai da suka gaya masu girman Allah, suka tausasa masu zuciya, sannan suka fara gaya masu menene miji ma first, kafin suka gaya masu hakkokin miji da yake a kansu, daga karshe suka ɗaura da zancen biyayya, kada su kuskura su ɗaga muryoyinsu ya fi na mazajensu sauti, yin hakan ya kansa mace ta shiga tsinuwar Mala'ikun Allah ta'ala, kome zai yi masu su daure kada su ɗaga mashi murya, Allah baya barci yana ganin komai da yake faruwa, su kula sosai da mazajensu, su kasance masu sanyasu farinciki na wuce misali, su yi masu duk abin da suke so matuƙar bai saɓawa Allah ba, koda su basu so, to su daure su yi mashi biyayya, ranar gobe kiya zasu samu kaso mai tsoka a wajen Allah, zasu shiga rahmar Ubangiji a lokacin da ubangijin al'arshi ya sauko da rana dai'dai kawunan mutane, to a wannan lokaci Allah zai sanyasu cikin karkashin inuwar al'arshinsa, dan haka su dage sosai, su jure su yi hakuri, duniya ba madawwama bace, lahira ita ce madawwamiya, dan haka su nemi madawwamiyarsu ta yi kyau, kada su biyewa duniya lokaci kaɗan yake a gareta. Sun sha kuka sosai, barema Rimsha, tafi kowa yin kuka a cikinsu, ita kuwa Jehan hawayenma bai gama barin kusa da idanunta ba, da alama ƙaƙalo kukan ma ta yi (ni ko wai menene zai sanya zuciyar Jehan da Lion yin laushi sosai ne?🤔 Wai duk wannan abin Jehan bata yi laushi ba?🤔 Kukan ma ƙaƙalo shi ta yi dan kada ace bata yi ba😂 kai jama'a Jehan dai har gobe da sauranta, shi dama Lion ba'a sanya shi a lissafi, dan ni na juya na juyo banga abin da zai sa zuciyarsa ta yi laushi ba, dan ko yanzu Rimsha ta yi mashi ba dai'dai ba zai bata a jikinta ne, sai dai daga baya ya yi dana sani, amma zuciyar nan tana nan babu abin da ya ragu a jikinta) Akila ma ta sha kuka sosai, daga haka har barci ya ɗaukesu. After some hours. Bayan sun yi sallar mangariba da issha ne Rimsha ta je wajen mummynta, dan dama mum ɗin ta ce mata ta sameta a ɗakinta. Tana zuwa mum ta zaunar da ita a bakin bed ta hau yi mata tata nasihar, ta ɗaura daga kan nasu Brr Naurat, duk wata kunya ajiyeta a gefe mum ta yi, ta rungumi ƴarta ta koya mata yadda zata zauna da mijinta lafiya, harta abin da yafi sanya namiji farinciki sai da mum ta gaya mata, ta ce ba zata tsaya nuna jin kunya ta cuci ƴaƴanta a banza ba, su je gidan miji basu san yanda zasu kula da mijinsu ba, aure ya zo ya yi ta tangal tangal, gara mata ta ajiye kunya, ta jasu a jiki, ta gaya masu komai dallah dallah, hakan ne kawai zai bata daman samun kwanciyar hankalin kasancewarsu a gidan miji, barema Rimsha da take ƴar yarinya, ga mijin nata ba irin sauran maza bane ba, ai dole sai an koya mata abubuwa dallah dallah, ɗan gara Jehan ma ta ɗan girma. Haka ta rinƙa yi mata nasiha sosai har sai da gwaggo ta zo ɗakin ta samesu, sai kuka Rimshar take yi sosai, gwaggon ce ta rarrasheta sannan ta ce tazo su tafi bari ta shiryata dan mijin nata ya iso. Wani irin daɗi ta ji Noorish nata ya iso, kamar zata tambayi gwaggon ina yake, sai kuma ta danne ta fasa dan ganin idon mummynta, da gwaggo ce kawai sai ta tambayeta ina yake, amma tun da mum tana nan, sai ta danne bata tambaya ba. Riko hannunta gwaggon ta yi tare da mikar da ita suka nufi waje suna yi wa mum sai da safe. Fitowa suka yi daga side na boys quarters ɗin suka nufi cikin gidan. Sosai Rimsha ta yi mamakin ganin tsadaddun sabbin motoci dal dal har guda uku a parking space na gidan, motoci ne da suka amsa sunansu motoci masu numfashi, ko ba'a gaya mata ba, tasan dole su ne suka ɗauko Noorish nata daga airport. Wucewa suka yi izuwa cikin gida, tana sanya kafarta a palourn kasa kamshin perfume nasa ne ya fara dukan kofofin hancinta, sai ka rantse da Allah yanzu ya wuce a wajen, amma kuma ya jima da wucewa zuwa sama, dan Rimshar tana fita zuwa wajen mummynta, shi kuma yana shigowa, kasancewar tana part na boys quarters ne yasa bata ji diran motocin nasu ba, dan boys quarters ɗin ta baya yake, kuma motocin sabbi ne dal masu matuƙar tsada, kukansu a hankali yake fitowa, shi ne yasa basu ji ba. Haurawa sama suka yi, kai tsaye bedroom na gwaggo gwaggon ta wuce da ita, shi kuma Lion yana cikin nasa bedroom ɗin, ya yi wanka yana sanye cikin kayan barcinsa tsadaddu masu kyan gaske, launin white color, ya zauna a balcony yana amsa waya nasu Aseef, sai kuka Aseef yake yi mashi a kan ya shammacesu ya tafi, shi dai Areef ya sani tun time da Lion ɗin ya bar gidan, Aseef ɗin suka ɓoyewa, sai yanzu ya sani, shi ne yake cewa shi wlh ba zai yarda ba, to rigimar da suke yi da Lion ɗin kenan. Wanka gwaggo tasa Rimsha ta yi, bayan ta fito, gwaggon da kanta ta shiryata cikin wata dankareriyar doguwar riga mai matuƙar kyau, da suka fita da Tga ne gwaggon ta saya masu su ukun dukka iri ɗaya, da yake du Jehan mazajensu basu zo ba, sai ta ajiye masu nasu, ita kuma Rimsha suka hau shiryata, sai ta fito cas kamar wata ƴar tsana a cikin kayan, ta haɗu iya haɗuwa, gwaggo bata yi mata make up ba, ta ce su bar mata natural beautynta tafi kyau a haka. Sai tsiya Akila take yi mata, sai kus, kus suke yi na munafurci, Akila tana gaya mata wasu zantukar a kunne, ita kuwa Jehan tuni ta fice zuwa bedroom nasu dan ta yi waya da Areef nata, ita kuma Akila ta tsaya ganin gulma, sai da aka yi wa Rimsha komai a gaban idanuwanta, gwaggo ta rufawa Rimshar wani haɗaɗɗen kuma tsadadden mayafi wanda ta feshe shi da tsadaddun Dubai perfume, ta rufa mata a kai ya sauko har saman face nata, tamkar za'a kai amarya, sai tsokanarta Akila take yi wai ta zama sabuwar amarya, gwaggo ta mai da ita sabuwar amarya. A kule ta ce "Aunty Akila dama can ni sabuwar amarya ce, kuma kullum a sabuwa nake, ni ba zan zama tsohuwa ba bare yaya Saif ya auri wata". Dariya sosai Brr Naurat ta kwashe da shi, Rimsha manya iyayen soyayya, wato dai bazata tsufa ba bare yaya Saif ya kara wani aure. Kuka ta saka masu, saboda Brr Naurat tana yi mata dariya. Rungumota gwaggon ta yi tana faɗin "Babu wadda ta isa ta shigo maki gidanki, ko kin tsufa Saif ba zai kara aure ba, ki sha kuruminki abinki, ai ke Saif ne ma zai tsufa ya barki, dan ya ninka shekarunki sau biyu a yanzu, dan haka rabu da su, ke kaɗai zaki yi zamanki a gidansa, ki ci karenki babu babbaka, ke da kike da Ni? Ai kawai kyalesu". Brr Naurat ma cewa ta yi "A'a mayar da wukar sarkin raki, ai kishiya bana yi maki fatanta, ita ce musabbabin ruguje mana farincikinmu, amma kuma ke kin gudu baki tsira ba, dan already ni Saif ya fara aura kafin ke". Buɗe nayafin da gwaggon ta rufa mata ta ɗan yi, ta fito da face nata tare da wurgawa Brr Naurat ɗin harara tana faɗin "Yaya Saif ɗin ne ya aure ki kafin Ni?". Yadda ta yi maganar sai da ta sanya su gwaggo wani irin mugun dariya sosai, Akila har da rike ciki, kai Rimsha duniya, ita fa idan akan Noorish nata ne zasu ɓata da kowa, kamar ba yanzu gwaggo ta gama gaya mata ita kaɗai ce a wajen Saif ba. Rarrashinta gwaggon ta sake yi tare da riko hannunta tana faɗin "Zo mu tafi na kai ki wajen mijinki hai, yana can yana kewarki, daga shigowarsa ya tambayeni ina kike, na ce mashi zan kawo mashi ke, rabu da su Brr, so kawai suke yi ki ɓata kwalliyarki dan kada Noorish naki ya ga kyanki". Da sauri ta ɗago daga cikin mayafin tana kallon gwaggon, tambayar kanta ta fara yi a kan a ina kuma gwaggo ta jiyo sunan Noorish? Ita Brr Naurat ta ruke sunan Meesha, ita kuma gwaggo ta ruke Noorish, wai yane suka sanyawa masoyan nan ido haka ne?. Tana can tana tunani har suka shiga bedroom ɗin bakin gwaggo ɗauke da sallama. Har lokacin yana zaune a balcony suna hira da TRIPLETS nasa a waya, kewarsu sosai yake yi, Allah ya gani sune bugun numfashinsa, yana sonsu fiye da baki ya musulta. Jin sallamar gwaggo yasa ya miƙe ya dawo cikin bedroom ɗin. Kallonta ya fara yi daga sama har kasa, shi baya iya ganin face nata, saboda tana cikin mayafi, ita kuma tana iya ganin face nasa, saboda mayafin bashi da wani kauri sosai, shara shara ne. A hankali ya zane wayar daga kunnensa tare da katse kiran yana mai cigaba da kallonsu har suka isa wajen bed nasa. Karisowa cikin ɗakin shima ya yi. A bakin bed gwaggo ta zaunar da Rimshar, ita kuma ta zauna a saman bedside drawer. Da ya zo shi ma sai ya zauna a bakin bed ɗin kusa da Meeshan nasa. A hankali ya shaki kamshin perfume nata tare da lumshe idanuwansa, har cikin farfajiyar zuciyarsa ya ji wani irin sanyi na daban. Calmly ya furta "Good evening momma". Cool murmushi ta sakar mashi kafin ta ce "Ɗazun mun gaisa ai, yanzu dai ka Rimshar taka na kawo maka ita, amana na baka yarinyar nan Saif, kamar yanda na gaya maka ɗazun, yanzu ma zan sake gaya maka, ka kula da ita tamkar yanda kake kula da su Aseef, zamu yi magana dai da safe yanzu zan je na kwanta". Ta kai karshen maganar tare da miƙewa. Good night ya yi mata yana mai kallonta, wucewa ta yi ta fice ta basu waje. Tana fita ya fara latsa wayarsa, jim kaɗan ya kara wayar a kunne tare da mikewa tsaye, balcony ya sake komawa, Areef ya kira, bayan ya ɗauka ne sai ya ce mashi da safe ya tabbatar bai manta ba ya kai Aseef wajen Sheikh Sultan, dama ya gaya mashi yau da safe, to sake tuna mashi ya yi, dan kada su mance, yana son Aseef ya sami lafiya sosai, yanzu ne ya gane menene matsalar ciwon na Aseef, tun da abu ne na tsafi, to babu maganinsa sai ayar Allah, shi ne yasa ya ce su kai shi wajen Sheikh Sultan ya yi koda sati ɗaya ne, In Sha Allah za su sami sauki komai. Bayan ya gama jaddadawa Areef ɗin, sai ya yi mashi sallama tare da dawowa cikin bedroom ɗin. Tana zaune tamkar yadda gwaggo ta ajiyeta, ta kudundune a cikin mayafi ta wani sunkuyar da kai. Kusa da ita ya zo ya zauna tare da zuba mata idanu. Calmly ya ce "Yau kuma kamar bake ba, duk kewata da kike cewa kin yi ba zaki iya rungumata ki yi mani oyoyo ba? Kin dameni a waya mazo ki ganni, ina zuwa ke na fara tambaya, amma ke kuma baki nemeni ba, since nake gidan nan, amma bama ki sani ba". Ya kai karshen maganar tare da kai hannu zai cire mata mayafin nata, dan ya samu damar ganin face nata da kyau. A hanzarce ta ɓoye hannayenta da suka ji kunshi suka yi maroon color sosai flowers ɗin, bata son ya gani, dan bata son ta ɓata mashi rai ko kaɗan. Bata san cewa tun shigowarsu ya kalli kunshin a kyawawan kafafunta ba, magana ce kawai bai yi ba, amma ya gani, ba yadda zai yi ne kawai, ba shi da zaɓi da ya wuce ya yi shiru. Zame mayafin ya yi tare da ajiye shi a gefe guda. Kirjinsa sai da ya bada wani irin dum dum a lokacin da ya sauke idanuwansa a saman face nata, tamkar wata tauraruwa haka ta zama. Lumshe idanuwansa ya yi tare da sake buɗesu, a cikin zuciyarsa yana faɗin wow, ba karya ta haɗu iya haɗu, haɗuwa ta karshe. Ita kuma sai faman ɓoye hannunta take yi, bata son ya gani, taki yarda kuma ta juyo su kalli juna, tana son rungumarsa, amma ta kasa. "Meeesha". Ya ambaci sunata can kasan maƙoshinsa, yadda ya furta sunan tamkar mai yin mata raɗa, cikin sanyin muryar nan tasa. Ɗan ɗago kanta kaɗan ta yi tare da ɗan juyo da face nata gare shi tana amsawa da na'am. Gabaɗaya ya rasa ma me zai ce mata, gani yake tamkar ba ita ba, ya kasa kawar da kallonsa daga kanta, tuni idanuwansa suka nuna mashi babbar mace ce ba yarinya ba, ga kirjin nan nata a cike fam sosai, sai yaga ta kara yi mashi girma a cikin idanuwansa, fatar jikin nan nata har wani irin sheki na musamman yake yi. Kan kace me Heronsa ta miƙe tsaye kyam, duk wani nutsuwarsa ya nemeta ya rasa, wani irin azababben sha'awarta ne kawai take wani taso mashi, tun daga tafin kafarsa har izuwa tsakiyar kansa yake jin tamkar alluran sojansa ce ta motsa, idanuwansa nan take suka sauya suka yi jajir da su, gabaɗaya ilahirin jikinsa har wani tsuma yake yi, tsikar jikinsa yana wani miƙewa. Kasa jurewa ya yi sai da ya kai hannu ya jawota jikinsa. Tana faɗawa jikin nasa ta yi maza ta rungume shi sosai, saboda tsananin kewarsa da take yi, shi kuwa tamkar kara hura wa kansa wutar azababben sha'awarta ya yi na wannan rungumar tata da ya yi, har wani zafi Heronsa take yi mashi over, saboda irin mikewa kyam da ta yi, sai wani zir zir kawai take yi mashi. Cikin wani irin yanayi da ba zai iya faɗar ga halin da yake ciki ba, ya kai hannu ya ɗago haɓarta, datse idanunta gam ta yi, dan kada su haɗa ido. Yana ɗago face nata ya sake jin kansa a wata duniya ta daban. A hanzarce ya kai ɗan bakinsa saman tata, kissing nata ya fara yi babu kama hannun yaro. Yana kissing nata tamkar kara hura wutar abin yake yi. Kankame shi ita ma ta yi tana mayar mashi da martanin kiss ɗin. Sam bai san time ɗin da ya zame bakinsa daga nata ya mayar saman wuyarta ba, lasheta ya fara yi ta ko'ina, duk ta birkita mashi lissafin ƙwaƙwalwa, ya fita a cikin hayyacinsa, bai taɓa tunanin zai dawo ya sameta ta yi irin wannan azababben kyau har haka ba, dole duk wani lafiyayyen namiji idan ya ganta zai nemi nutsuwarsa ya rasa, dan ta haɗu, ta sha gyara iya gyara. Cancak ya miƙe da ita suka karisa hayewa saman bed ɗin, rabata da wannan doguwar rigar ya yi, ya rage daga ita sai under wears, ƴar karamar farar vest ce da wata kyakkywar pant fara tas. Da kyar ya iya kashe wutar ɗakin tare da dawowa ya yi mata rumfa da faffaɗar kirjinsa, hannu ya kai saman wuyar vest ɗin tata, kasa ya yi da shi, nan take tula tulanta suka bayyana tamkar an hura balo balo, a tunaninsa idan ya yi wasa da su kamar kullum zai sami nutsuwa, sai yaga akasin haka, dan ganinsu da idanu ma kawai kara birkita mashi lissafin ƙwaƙwalwarsa suka yi, saboda ba yadda ya tafi ya barsu bane, sun kara kyau da girma na banmamaki tare da ɗaukar hankali matuka. Nan take ya ji kai ina ko da sunan wasa bafa zai iya controlling na kansa ba a yau, dama da kyar yake iya dannewa, to yau dai komai ya kwance mashi, sai dai meesha ta yi hakuri, amma yau shi nasa hakurin ta kare wlh. Murzan tula tulan nata ya fara yi babu kama hannun yaro, kara rankwafowa kanta ya yi tare da gyara kwanciyarsa ya zame ɗan vest ɗin daga jikinta, ta kugunta ya bi da shi, yana zuwa dai'dai kugun nata ya haɗa da pant nata gabaɗaya ya yi kasa da su. Ɗan bakinsa ya kai saman nipples nata, capko ɗaya ya yi ya fara aikin tsotsa kamar ya samu sweet, yana yi yana shafa shafaffen cikinta da ɗayan hannunsa, sai wani irin numfashi yake fitarwa wanda baki ma ba zai iya musulta shi ba, before ta zo yunwa yake ji, yana ƙoƙarin sanyawa a kawo mashi abinci ne, yanzu kuma ya mance ma da menene yunwa a duniya bakiɗaya. Kuka ta fara yi mashi dan ta ji abin nasa ya fara yi mata yawa, yana tsotsar mata tula tulanta sosai. Ko kusa ko alama bai iya jinta ba, ya yi nisa, sai ma zame bakinsa daga saman nipples ɗin nata ya yi tare da fara zuba mata sambatu yana gaya mata hakika ya yi kewarta sosai, ya zama kamar ba shi ba, duk ya susuce ya birkice mata. Rungumota ya yi tare da ɗaga ta da hannu ɗaya ya juya da ita, sai ya zamata ta dawo saman Lion chest nasa, sai kuka kasa kasa take yi mashi, shi kuma ya yi mata hakan ne dan ya karisa zame pant nata dake wajen cinyoyinta, dan ya sami damar juyata son ransa. Yana cire pant ɗin gabaɗaya, sai ya sake juyowa da ita, sam bata kawo wa ranta cewa wani abin zai yi mata ba, kukan shagwaɓa kawai take zuba mashi. Wani irin ɗaukewa numfashinta ya yi na wucin gadin lokacin da ta ji saukar hannunsa a saman shimfiɗaɗɗiyar gurasarta, ko da sunan wasa bai taɓa kai hannunsa wajen ba sai yau, hakan yasa ta ɗan tsorata har ta fara ambatar Noorish, Noorish, a hankali cikin kukan shagwaɓa. Shi kuwa yana kai hannunsa jin wajen a jike cakop ba karamar kara tayar mashi da hankalinsa ya yi ba, wajen a jike yake sosai, sai aman ruwan ni'ima over take yi, ta tsumu ba karya. Jin yadda take jike ga kuma wani ruwan na bulbulowa ne yasa ya fara wasa da wajen sosai. Tamkar jira take yi ya sanya hannunsa a wajen, aikuwa ta cigaba da bulbular da ruwan ni'ima kamar wadda aka buɗe famfo. Kasa jurewa ya yi, dan kamar yadda ruwan ni'imarta yake bul bula, haka shi ma nasa yake yi, har wani irin zir zir Heronsa take yi mashi, ba zai iya cigaba da gwada yin wasa da ita ko zai samu sauki ba, abin ya wuce tunaninsa, wasa babu abin da zai yi mashi face ya kara mashi azaba da raɗaɗi, dan haka sai ya sanya hannu ya yage rigar jikinsa da karfin gaske cikin tafasasshiyar nama, dan wannan yafi karfin zafin mama, sai dai tafasa, tsayawa cire rigarma ɓata mashi lokaci zai yi, shiyasa ya yaje ta, jikinsa sai wani irin tsuma yake yi na wuce misali, duk ya fita a hayyacinsa, duk sunansa da take ambata bai ji ko sau ɗaya ba. Bayan ya raba kansa da kayan jikinsa, a tsananin yanayi na tsananin sha'awarta ya kai hannunsa wajen kafafun nata, cikin fitar hayyaci ya buɗesu sosai tare da kara yi mata rumfa kafin ya fara laluɓar hanyar da zai shigeta. A gaskiya hanyar ta yi mashi kankanta over, ba zata shigun mashi ba, amma bashi da zaɓin da ya wuce ya shiga koda da karfi ne, dan idan ba haka ba, zai cutu matuka. Bananarsa ya kawo saitin wajen, shiru ya ɗan tsaya na ƴan mintoci da basu wuce biyu ba. Can kuma kamar wanda aka yi wa wani alluran ya fara ƙoƙarin zura bananar tasa kawai, sosai kofar take rufe gam saboda kankantarta, ba shakka Meesha ta yi mashi karama over, Heronsa ta yi mata girma matuƙa, sai ya yi mata ta karfi sosai zai iya samun hanyar da zai ɗan wuce, sai ya sanya karfi zai iya kawar da budurcinta. Wani irin azababben ihu ta zunduma mashi tana ambatar sunansa, ina baya a cikin hanyacinsa sam sam, sai ma kara kai hannayensa dukka biyu da ya yi ya buɗe kafafunta da kyau, dan ya samu hanyar da zai shigeta da kyau, yana gani kamar kafafunta ne suka hana bananar tasa shiga ciki. Da kyar da kyar ya iya buɗe bakinsa cikin fitar hayyaci yana faɗin "My Meesha you're special, you're so sweet...." Kalaman ma da yake faɗa a sambatun nasa sam sam baki ba zai iya faɗarsu ba, ya yi wani irin birkice mata ne, tun bai yi nisa bama ya kasa cigaba da iya zuba sambatun, dan abin ya wuce tunaninsa, sai kara bulbulowa ruwan ni'imarta yake yi sosai da sosai, har yanzu kuma ya kasa iya shigarta gabaɗaya, sai wahala yake sha, bai taɓa tunanin haka abin yake ba bawan Allah. Ita kuwa tun ihun da ta zunduma ta farko farko bata kara yin wani ba, tsit kake ji kamar babu ita a wajen.............(NIMA NA YI TSIT KAMAR BABU NI A WAJEN, DAN YAU DA IDO ƊAYA NAYI MAKU TYPING, MA'ASSALAM.) ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 5/5/2024 E24 Ita kuwa tun ihun da ta zunduma ta farko farko bata kara yin wani ba, tsit kake ji kamar babu ita a wajen, tuni ta sume mashi, dan wannan bala'i ya sha gaban tunaninta. Sosai ya buɗe mata kafafunta tare da shigarta da karfin gaske, shi kansa a wannan lokaci sai da ya ji wani irin zafi ya ziyarcesa bare kuma ita da ya fasata da karfin gaske, ai abin ma ba'a magana. Lokaci guda ya kara fita daga hayyacinsa, duk ya bi ya duburburce, socking nata ya fara yi cikin tsananin azababben sha'awarta, ji yake yi ma tamkar yanzu wani azababben sha'awar tata take kara taso mashi, mararsa har murɗa mashi take yi sosai, hakan yasa ya kara karfin yin socking ɗin nata da yake yi, duk ya bi ya buɗe mata kafafu kamar zai ɓallata, dan yana ganin kamar su ne suke hana shi shigarta yadda yakamata, hankalinsa baya a jikinsa bare ya iya gane cewa kofar ce ta yi mashi kaɗan sosai. Ba shi ya kyaleta ba sai da ya yi mata fata fata, sau biyu yana realizing a jikinta, saboda tsananin daɗinta da ya kwashe shi, ya yi na farko, ya sake jin ina ai yanzu ne ma ya fara jin sabuwar sha'awarta, sai ya cigaba, har sai da ya yi sau biyu, sam bai yi tunanin tana raye ko ta mutu ba, ko da yake, sai hankalin mutun yana a jikinsa zai yi wannan tunani. Sai da ya ji ya ɗan sami sassauci na abin da yake ji dangane da sha'awarta, sannan ya kyaleta tare da zame bananarsa daga jikinta, duk da ya yi socking nata over, amma bananar tasa bata fita lokacin guda ba, sai da ya ɗan janyeta tukun nan, wani irin sara mashi kansa take yi tamkar zata fashe, gabaɗaya jijiyoyin kan nasa sun miƙe, kyawawan gashin dake kwance a hannayensa duk sai da suka miƙe, wasu jijiyoyi ne suka fito mashi ɓaro ɓaro a hannayen nasa gabaɗaya, saboda yanayin da yake a ciki. Sai a lokacin ne ya dawo cikin hayyacinsa da kyau. Kallo ɗaya ya yi wa ɓarnar da ya yi ɗin ya kawar da kallonsa izuwa saman face nata, sam bai yi mamaki ba, dan dama already yasan confirm sai hakan ta faru idan ya kusanceta, ya san kansa sarai, fatansa dai shi ne Allah yasa bata mutu ba, kuma Allah yasa hakan kada ya taɓa mata ƙwaƙwalwa, gaskiya akwai matsala, azabtuwa ta karshe a duniyar nan ta yi shi a yau. Wandonsa ya ɗauka ya mayar jikinsa, sannan ya diro kasa daga saman bed ɗin, shi kansa bananarsa zafi take yi mashi bare kuma ita, ai baki ya yi kaɗan ya faɗi halin da take a ciki, sai Allah nema kaɗai yasan tana raye ko ta mutu. Shiru ya tsaya na ƴan mintoci yana tunanin meyakamata ya fara yi mata first, kun san shi tun ainahinsa komai nasa a nutse yake yi, baya yin abu gar, gar, gar kamar mahaukaci, cikin nutsuwa da class tare da izza yake abinsa, baya yanke hukunci cikin sauri, sai ya yi tunani. Sai zubar da jini take yi tamkar rago aka yanka, ga bed sheet ɗin nasa white color ne sosai, hakan yasa jinin ya fito sosai, shi kam ai ba bakon jini bane, sojoji ba bakin jini bane ba, sun saba. Ya rasa ta ina zai fara, ya rasa me zai yi mata nema first, ya yi iya tunanin da zai yi, a yau dai ƙwaƙwalwarsa bata iya bashi amsar abin da yakamata ya yi wa Meeshan nan nasa ba, dan fa ya yi mata kaca kaca, ko ɗaukarta ya ce zai yi zuwa toilet ba zai yiwu ba, saboda a yanda take ɗin nan kamata ya yi ace sai an fara yi mata ɗinki an bata agajin gaggawa kafin a motsata daga wajen, ba zata ɗauku ba sam sam, abin ya wuce yadda kuke tunani, idan aka ce kaca kaca ana nufin ya yi mata kaca kacan over, dan ya fi karfinta nesa ba kusa ba, tamkar ratar sama da kasa ne suke. Ganin tana zubar da jini sosai zata iya rasa ranta idan ma tana rayen kenan ne yasa ya nufi waje, babu riga a jikinsa, kuma kunsan halinsu ba kunya ne ke garesu ba, haka ya nufi bedroom na gwaggo. Kasa kasa ya yi sallama cikin nutsuwa tare da shiga ciki. Gwaggo na kwance a saman bed ɗinta, Brr Naurat tana ɗakin mijinta Dr Salman a ɗaya daga cikin ɗakunan kasan benen, kusa da bedroom na Aseef kenan, nan ne ɗakinsu, so yanzu gwaggo ita kaɗai ce a cikin ɗakin nata, Akila da Jehan suna bedroom nasu. Allah yasa bata yi barci ba, lokacin ma ta yi shirin barci cikin kayan barcinta masu kyau, dan an ɗauko mata kayanta daga gidan Azharuddin, ta gama shiri ta kwanta kenan ya shigo. Jin sallamarsa yasa ta ɗago idanuwanta tana kallon kofar, dan tana fuskantar kofar shigowar ne, kuma wutar ɗakin a kunne. Ganinsa cikin wani irin yanayi ga shi babu riga a jikinsa ne yasa ta raza ta miƙe zaune babu shiri. Zuba mashi idanu ta yi tana kallonsa har ya karisa shigowa cikin ɗakin. Sai dukan uku uku kirjinta yake yi, ko kaɗan bata kawowa ranta dis virgin na Rimsha ya yi ba, dan idan baku manta ba, su already kallon mai ƙaramin ciki ma suke yi wa Rimshar, to ita ta ɗauka ma wani abin ne ya faru da Aseef ko Areef yasa ya shigo mata ɗaki ko riga babu a cikin wani irin yanayi da baki ba zai fassara shi ba. "Saif lafiya kuwa?". Ta tambaya a ruɗe. "Momma come and help me, I think I killed Meesha by myself". Zaro idanuwa waje sosai ta yi, tare da zabura ta zuro kafafunta kasan gadon, a ruɗe ta ce "What did you do to her? Dukkanta ka je yi ne ka illatata? What crime did she do to you da har zaka yi mata hukuncin da kake tunanin ka kasheta?!". Murya a ɗan kausashe ta yi maganar, kuma ta yi maganar cikin ruɗu sosai. Riko hannunta ya kariso wajen ya yi, tare da miƙar da ita tsaye yana faɗin "Momma Meesha didn't do anything wrong to me, and even if she do me wrong, I will not do anything to her, bana dukan mata, dis virgin nata na yi, shi ne aka samu matsala tana zubar da jini sosai, please momma come and help me, kada Meesha ta mutu". Ai gwaggo bata san lokacin da a dubu ɗari ta dafe kirjinta tare da zame hannunta daga cikin nasa ta nufi waje ba, sam bata taɓa kawowa a ranta cewa Rimsha virgin ba ce, shiyasa ta yi ta ɗirka mata tsumin nan, yau sun shiga uku!. Da sauri ya bi bayanta shi ma. Tana shiga ɗakin kai tsaye bakin bed ɗin ta nufo da nufin ta hau gadon, ai bata san lokacin da ta ci wata uwar burki ba lokacin da idanuwanta suka sauka a kan Rimshar. Kara zaro idanuwan nata waje sosai ta yi dan ta tabbatarwa da kanta shin abin da take gani gaske ne ko mafarki. Dai'dai lokacin shi kuma ya shigo cikin ɗakin. Jin motsin shigowarsa yasa ta daure ta haye saman bed ɗin, ba tare da ta kalli in da yake ba ta ce mashi ina kayan aikinsu yake? Dan gwaggo kwararriyar likitar mata ce na kin karawa, a kallah ta karanci fannin likita daban daban har kala uku a rayuwarta, ta yi biyu a Washington, ta yi ɗaya a Dubai, so ita ta ma fi Dr William sani a fannin aikin nasu, dan ta fishi research a kan abubuwa sosai. A hanzarce ya kwaso mata waɗan da suke a cikin drawersa, ya kawo mata saman bed ɗin, sannan ya fita daga bedroom ɗin cikin sauri ya nufi bedroom na Areef, suna da kayan aiki wasu a can, idan baku mance ba Areef ya taɓa yin jinya a ɗakin, har likitoci daga Washington suka zo suka yi jinyarsa, to suna da kayan aiki sosai a ɗakin. Cikin fitar hayyaci ya kwaso mata komai da komai. A saman bed nasa ya jibge mata komai, duk ya shiga tashi hankali, duk yanda ya kai ga nuna dakiya da karfin hali a kan abu, a wannan karon ya gagara dakewa ya danne, abu zata iya faruwa ya jure ya dake ya yi kamar bai san ta faru ba, amma a cikin ransa yana jin ciwon wannan abin, wannan dai ya kasa dakewa, sai da tashin hankalin ta bayyana karara a saman face nasa, da farko tamkar zai iya dakewa ya ɓoye tashin hankali nasa, amma ina tafikarfin ta ɓoyu har sai da ta fito fili, kana ganinsa kasan a cikin tsananin tashin hankali da damuwa yake, duk yana birkice bawan Allah. Audiga gwaggo ta fara sanyawa a dai'dai gaban Rimshar, dan ta ɗan goge wannan uban jini da yake zuba, saboda ta samu damar fara yin aikinta. Hawaye bibbiyu ne yake fita daga idanunta, ta yi matuƙar tausayawa Rimshar ba kaɗan ba, ko makiyinta ya ganta a cikin wannan hali sai ya tausaya mata, saboda fa ta azabtu azaba ta karshe ma kuwa. Yau dai Lion jikinsa har kerma yake yi, saboda tsananin damuwa da tashin hankali da yake a ciki, saman bedside drawer ya zo ya zauna, duk jikinsa ta yi mugu mugun sanyi, ya rasa menene yake yi mashi daɗi a duniyar nan, ya yi nadamar meyasa bai daure ya yi control na sha'awarsa ba? Da ya hakura ya barta sai ta kara girma kamar yanda su Areef suka bashi shawara. (Ni kuwa nace daga baya kenan, bayan ka gama abin da zaka yi?🤔🥺) Ɗago idanu gwaggo ta yi da nufin ta ce mashi ya fita ya bata waje bata son ganin shi, amma sai ta kasa gaya mashi hakan, saboda yadda ta ga tsananin tashin hankali da damuwa a bayyane karara a saman face nasa, ga jikinsa har kerma yake yi, bata taɓa kallon idanuwansa sun ɗan tara ruwa ba sai yau, dan fa ya tausayawa Meeshar tasa ba ɗan kaɗan ba, tun da yake a rayuwarsa idanuwansa basu taɓa ɗan tara ruwa a kan wani abin na tashin hankali ba sai yau, ga idanuwan nasa sun yi jajir da su kamar wuta, sai dai ya ki bari ruwar ta taru dayawa, ya daure ya shanye. Wani irin tausayinsa ne Gwaggon ta ji ya lulluɓeta, sai ta ji ita ma duk jikinta ya yi sanyi, tasan koma menene ya faru da Rimshar su ne nan suka ja mata, dan su ne nan suka yi ta ɗura mata kayan mata, ga shi yanzu sun jawa yarinya bala'i. Gabaɗaya sai ta ji ba zata iya yi wa Lion ɗin magana mara daɗi ba, ta tausaya mashi, cikin sanyin murya ta ce "Saif ka je bedroom nawa ka kwanta ko?". Shiru ya ɗan yi tare da sunkuyar da kansa kasa, karo na farko a rayuwarsa da ya fara jin nauyin ya haɗa idanuwa da mutun, ya ji ba zai iya kallon cikin idanuwan momman tasa ba. Kasa kasa calmly ya ce "Momma i can't sleep today, na yi wa Meesha abin da bai kamata ba, i can't go anywhere na barta, ki dubata ina nan". Allah sarki uwa da ɗa, sai gabaɗaya gwaggon ta ji wasu zafafan hawaye sun gangaro mata a saman kuncinta, ta tausaya mashi sosai, tasan wlh ba laifinsa bane, kowa ya samu rana zai yi shanya, kuma dole a yanda Rimsha ta tsumunnan dole zata birkita shi, zata sanya ya fita hayyacinsa, dole dama ya yi mata irin hakan, yama yi ƙoƙari ba kaɗan ba da ya iya hakuri ya barta a iya haka. (Kaji mani gwaggo da wani zance, idan bai barta a iya haka ba ya kuke son ya yi da ita? Ai idan ya wuce haka sai dai ya yi chaskale da gawa😒) "Saif ba zan iya yi mata aiki a gabanka ba, ka je bedroom nawa ka ji?". Ta faɗa cikin sanyin murya tana ruwan hawaye. Shiru ya ɗan yi kafin ya miƙe yana faɗin "Please momma take good care of her kin ji?". Jinjina mashi kai ta yi alamar e ta ji. Ficewa daga ɗakin ya yi, yana tafiya cikin nutsuwa, zuciyarsa tana yi mashi wani irin raɗaɗi, sai tambayar kansa yake yi a kan wai shin menene ma ya shiga kansa da har ya kasa iya rike kansa sai da ya yi dis virgin na under 15 years girl, abin kamar a mafarki yake yi mashi, ta wani ɓangare kuma idan ya tuna yadda ya ji ta, idan ya tuna irin zazzaƙar zumarta da ya ɗan ɗana, sai ya furta Alhamdulillah. Yana fitowa daga bedroom nasa ya zauna a saman sofa mai zaman mutun ɗaya na cikin palon saman, jingina kansa da jikin head na sofar ya yi yana tunanin irin zazzaƙar zumarta da ya ɗanɗana, gata kankana uwar ruwa, ta wani fanni kuma yana tuna irin kaca kaca da ita da ya yi, sai Allah ne kaɗai yasan ɗinki kala nawa zata sha, baiwar Allah. Gwaggo kuwa yana fita ta bishi da kallo, duk tausayinsa ya lulluɓeta, sai da ya fice sannan ta maido da hankalinta a kan Rimshar, aiki ta farayi cikin hanzari, tana yi tana faɗin "Kiyi hakuri Rimsha, koma menene ni da mummynki muka ja maki da muka kasa buɗar baki mu tambayeki are you a virgin or not, kawai muka hau ɗirka maku abubuwan da mun san mace virgin bata isa ta sha ko kwatarsa ba, ga shi yanzu mun ja maki kina tsakanin mutuwa da rayuwa, Allah yasa ma abin ya tsaya maki a iya gaban naki da cikin kawai, Allah yasa kada ya taɓa maki kwakwalwa, amma kam ba shakka kin sha wahalar da bana jin akwai wata macen da ta taɓa shan ko rabinsa a duniya". (E gaskiya nima kam na shaida, bana jin da kawai wadda ta taɓa shan kwatan wannan azaban da ta sha, dan wlh kin azabtu, ace Heronsa ya kasa shigarki sai da ya fasaki da karfi?🥺 Allah sarki idan kina da sauran rai ma kin yi ƙoƙari.) (Wlh Lion ɗan duniya ne🤔 kun ji wai tunanin daɗin ni'imarta da ya ji ma yake yi?🤔😂 Ya azabtar da baiwar Allah, a haka ma shi baya allura baya shan komai🤔 kuma cikin soyayya da kauna aka fara chaskalen kafin ayi dis virgin ɗin, da ace yana shan wani abin sai yaya?🤔 Da ace gardama ta yi mashi ya yi mata ta karfi sai yaya? Ina ga ko gawarta bazata ɗaukunwa mutane ba, wannan da bai yi romancing nata ba ya shiga kawai da sai mutu zata yi wlh🥺 a haka ma ya yi romancing nata sosai, ya yi wasa da ita cikin so da kauna ma ta ji irin wannan bakin azaba ta karshe har haka, tab akwai aiki justice for Meesha 🥺🌚.) Sai surutai barkate gwaggon take yi har ta samu ta dakatar da jinin da yake zuba, a nan ne taga ainahin tashin hankali ma kuwa, dan fa wannan buɗe hanyar da karfi da ya yi, sai da ya fasa wajen mai gabaɗaya sosai, kun san ainahin fatar wajen bata da karfin sosai, hakan yasa ta tsage sosai, shi ne yasa ma jinin ya yawaita matuƙa, ga shi da ya shigeta santin daɗi ya ɗebesa ya yi ta socking nata da karfi karfi, hakan yasa wajen ta kara tsagewa sosai, idan fa baku manta ba shi ma ya sha raɗaɗi wajen bakin kan bananarsa bare kuma ita, ai sai shiru kawai, dan yafi karfin baki ya faɗeta. Sosai ruwan hawayen dake a face ɗin gwaggon ya tsananta gudu, ba ƙaramar tausaya mata ta yi ba, haka ta cigaba da bata taimakon gaggawa. A daren ta yi mata ɗinki sosai a wajen, sannan ta rubuto magunguna da alluran da za'a saya mata, da kuma duk abin da ya dace a yi mata, har kusan asuba misalin karfe 4 ta kammala, duk tasha kuka har mura ya kamata, kun san idan mutun ya yi kuka sosai har mura ce take kama shi, sai ya yi ta faman jan hanci, to haka ita ma gwaggon ta yi ta fama. Ko motsawa Rimsha bata yi ba, tamkar babu rai a jikinta, miƙewa gwaggon ta yi tare da dirowa kasa daga saman bed ɗin ta nufi dressing room nasa. Kayan barcinsa ta duba ta ɗauko, saman bed ɗin ta dawo ta haye. Cikin dabara ta matsar da ita gefe guda daga wajen da ya yi dama dama da jinin. Kayan ta sanya mata, sannan ta jawo bargo ta lulluɓeta, saboda akwai zazzaɓi mai tsananin zafin gaske a jikinta, taso ta cire masu bed sheet ɗin ta canza masu, sai dai bazata iya ɗaga Rimshar ba, saboda ba ma zai yiwu a motsata daga in da take ba, dan motsata zai iya zama barazana ga lafiyarta da ma rayuwarta bakiɗaya, dan haka sai ta kyale masu kayansu a haka, ta diro kasa ta nufi waje. Har lokacin yana zaune a saman sofa, ko alamar barci babu a idanuwansa, sai tunanin wani hali Rimsha take a ciki kawai yake yi. Yana jin motsin gwaggo ya ɗago da kansa a hanzarce. Sosai gwaggon ta yi mamakin ganinsa a palon, bata yi tunanin yana wajen ba, ta ɗauka yana cikin bedroom nata, ta dai san mawuyacin abune ya iya yin barci a wannan dare, abu ne wanda ba zai yi wu ba, sai dai ta zaci zata same shi a kwance ko da a saman sofar dake a cikin bedroom nata ne. Miƙewa ya yi ya kariso wajenta a in da take tsaye wajen bakin kofar fitowa daga bedroom ɗin nasa. Kasa ya yi da kansa dan har ga Allah baya son haɗa idanu da ita, can kasan maƙoshinsa ya furta "Momma how is her body?". Duk tausayinsa ya cika mata zuciya, bata taɓa tunanin da akwai ranar da zata zo jinin Dr William su ji kunyar wani abin ba, sai ga shi yau babban ɗa ga Dr William yana jin nauyin haɗa idanu da ita, wannan abin ya yi mugu mugun bata mamaki, har sai da ta ji ita ma kunya ya kamata. "Saif zamu yi magana da safe, yanzu dai bari naje ɗaki kaga lokacin sallar asuba ta kusa, da safe zan gaya maka allurai da magunguna da sauran abin da zaka sayo mata". Ta kai karshen maganar tare da wucewa, dan bata san me zata ce mashi a kan Rimshar ba, hakika babu wani sauki a jikin Rimsha, an dai samu an yi mata ɗinki, bayan haka babu wani cigaba sai tsayar da jinin da ta yi nasarar yi. Shiru ya ɗan zubawa mommar tasa idanu har ta shiga cikin bedroom nata, nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya sa kai ya shiga cikin bedroom ɗin nasa. Har lokacin jikinsa kerma yake yi, yau karo na farko a rayuwarsa da ya ji tsoron wani abin, wannan kuma ba komai bane face tsoron ganin halin da Meeshar tasa take a ciki, yana jin tsoron ɗaura idanuwansa a kanta. Saman bed ɗin ya haye, kallo ɗaya ya yi wa jinin dake malale a saman bed ɗin ya kawar da kansa gefe, cike da zulumi ya kai kallonsa a saman face nata, gwaggo ta lulluɓe mata jikinta da bargo, wlh har wani kumbura face nata ya yi cikin ƙanƙanin lokaci, duk ta sauya, idan ba ka yi mata farin sani ba, ba zaka taɓa cewa ita ɗin bace ba, ta sauya over, face nata ya kumbura sossi. A hankali ya kai hannunsa ya yaye bargon dake a jikin nata, nisawa ya yi kafin ya miƙe, cikin dabara ya ɗauketa cak, dan motsata daga in da take ma babban haɗari ne ga lafiyarta, barinta a haka shi ne mafi a'ala a garesu, idan suka kuskura suka motsata har jikinta ya jijjiga, to ba shakka zasu ɓaro mata wani babban matsale ga lafiyarta da rayuwarta, yanzu haka ma basu san a iya ina matsalar ta tsaya ba, sai ta farfaɗo zasu iya ganewa. Wannan shi ne tashin hankali. Cikin dabara ya ɗagata kamar wanda ya ɗaga jaririn kwai irin wanda bai yi ɓawon nan ba, wanda yake iya ledar ciki ne kawai, kun san idan za'a ɗauki irin wannan kwan dole abi a hankula, saboda kada ya fashe, to a hana Lion ɗin ya ɗagata zuwa saman sofa mai zaman mutum uku da yake a cikin bedroom ɗin, ya kwantar da ita, sannan ya dawo ya cire bed sheet ɗin gabaɗaya tare da ajiyewa a gefe guda. Da kyar ya iya ɗauko wani bed sheet ya shunfuɗa, dan har ga Allah shi bai iya shunfuɗa gado ba, ba aikin da ya iya dangane da aikin gida, haka ya shunfuɗa bed ɗin ko kyau bai yi ba, bed sheet ɗin ma ba'a dai'dai ya sanya ta ba, ya dai sakata ne kawai, shi dai ba ya samu ya cire wannan na jinin ba? Ai shikenan kuma, koma a yaya ya shunfuɗa wannan haka zasu kwanta. Komawa ya yi ya ɗaukota a hankula, a saman bed ɗin ya shumfuɗeta, sai kara kumbura face nata yake yi tamkar ba lafiya ba. Duv na bed sheet ɗin ya jawo ya rufa mata, sannan ya sauko ya ɗauki bed sheet ɗin da ya cire ya kai wajen kayan wanki, ya nufi toilet dan ya yi wanka. Bayan ya fito ya shirya cikin jallabiya fara tas, dan an fara kiraye kirayen sallar asuba. Dadduma ya shunfuɗa tare da fara gabatar da nafilfilu, daga karshe ya yi shafi'e da witiri kafin alfijir ta keto, bayan ta keto sai ya yi rakatainil fajir ya fito zuwa masallaci, har lokacin da kallo ɗaya zaka yi mashi kasan cewa yana cikin tsananin tashin hankali na wuce misali, yau dai ya canza daga suffa ɗaya da aka san shi, dan tashin hankali ta bayyana mashi a saman face nasa. Ko da ya dawo daga masallaci bai zame ko'ina ba face bedroom ɗin nasa, bai kalli in da take ba, dan ya san ko motsawa ba ta yi ba, ta shiga doguwar suma ne. Wanka ya kara yi tare da shiryawa cikin kananan kaya masu matuƙar kyau da tsada, sannan ya fito tare da ɗaukar wayarsa. Saman bed ɗin ya haye, sai zuba uban kamshi perfume nasa yake yi, kusa da ita ya kariso. Tamkar gawa haka take kwance baiwar Allah. Ranƙwafowa kanta ya yi, a dai'dai saitin kunnenta ya kawo ɗan bakinsa, kasa kasa ya fara yi mata raɗa, bai bawa kowa damar jin abin da yake faɗa mata ba, shi kaɗai yasan me yake faɗa, ita da take sume ba jinsa take yi ba, amma ya zage sai yi mata raɗa yake yi, da kallo ɗaya zaka yi mashi kasan har yanzu a birkice yake, har yanzu akwai tashin hankali sosai a tattare da shi. Ya ɗan ɗauki lokaci yana yi mata radar kafin ya ɗago ya sumbaci lallausan lips nata da suke a bushe sosai yanzu, saboda bakar azabar da ta sha ne yasa har suka yi wani irin bushewa tamkar babu ruwa da jini a jikinta. A hankali ya diro kasa daga saman bed ɗin ya nufi waje, har ya kai bakin kofa ya sake juyowa ya kalleta, sannan ya sa kai ya fice daga ɗakin. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 6/5/2024 E25 A hankali ya diro kasa daga saman bed ɗin ya nufi waje, har ya kai bakin kofa ya sake juyowa ya kalleta, sannan ya sa kai ya fice daga ɗakin. Yana fita ya nufi bedroom na gwaggo, ya zo zai shiga dai'dai lokacin ita kuma zata fito daga cikin ɗakin, saura kaɗan su yi karo. Baya ya ɗan yi yana faɗin "Good morning morning". Tsare shi ta yi da idunuwa tana mai faɗin "Morning where are you going in this early morning?". Shiru ya ɗan yi na ƴan sakanni kafin ya amsa mata da "Yesternight you said da akwai wasu drugs and injection da zan sayawa Meesha, that's what i came for, ki bani list ɗin". Allah sarki bawan Allah duk a ruɗe yake, hakika yana tsananin kaunar Rimsha, kauna mara misaltuwa, hankalinsa a tashe yake sosai. "Saif what is the time now?". Ta tambaye shi har lokacin bata kawar da kallonta daga kansa ba, tsananin tausayinsa ne cike fal a ranta. "6:05". Ya bata amsa yana duba dankareriyar watch dake ɗaure a hannunsa. Ba shakka Lion ya shiga tashin hankali da damuwa na wuce misali, kuma dai kun san abin da zai sanya Lion ya canza daga wannan suffa guda ɗayar, abin da zai sanya shi har a iya gane yana cikin bakinciki da tashin hankali wanda ko TRIPLETS nasa duniyar farincikinsa basa iya ganewa, amma yau ga tashin hankali karara bayyane a face nasa har ya kasa hakura gari ta waye sosai ya je ya sayo mata magani, ko daga nan kun san abin ya kai mashi intaha, abin ya wuce misali a wajensa, kofa TRIPLETS nasa basa iya ganewa idan yana cikin damuwa or ɓacin rai ko kuma farinciki, saboda dakiya da juriya irin nasa, amma yau shi ne yake birkice haka, babu shakka abin ya wuce misali, soyayya tabarmar kaya, idan ka iya zama ka ji daɗi, akasinta kama? Kun san sauran. "Saif nan fa ba U.s bane ba, they didn't open their shop's at this time around, sai irin 8 haka, now is to early ai". Ta kai karshen maganar tana mai kara yin kasa da muryarta sosai, tana yi mashi magana cikin sigar rarrashi da nuna tausayawa tare da tausasawa, dan ya ɗan ji sanyi a ransa, duk da ba ita ta renesu suka girma ba, bata san halinsu sosai ba, amma ta san cewa ba ƙaramin abu bane zai iya sanya jinin Dr William shiga damuwa har haka, bare kuma shi Lion da kusan komai irin na daddyn nasa ya ɗauko, Dr William akwai taurin zuciya na bala'i, to haka Lion ɗin ma yake, sun iya shanye abu. Shiru ya ɗan yi yana mai cigaba da kallon kasa, kwata kwata baya son su haɗa idanu, duk wani irin yanayi yake ji a jikinsa. "Kanaji ko Saif? In Sha Allah Meesharka zata samu lafiya, babu abin da zai sameta, yanzu abin da nake so da kai ka nutsu ka kwantar da hankalinka, ka yi mata addu'a, zan je na dubata ne dama yanzu, kada ka damu zata warke kamar ba'ayi ba cikin ƙanƙanin lokaci In Sha Allah". Tana magana tana kallon jikinsa yadda yake wani irin tsuma alamar still dai yana cikin tashin hankali. Rumgumeta ya yi tare da fara magana kasa kasa kamar mai raɗa "Momma i know kawai kin gaya mani hakan ne dan naji daɗi, i already knew that ko da Meesha zata samu sauki not now, ban taɓa jin daɗi cikin bakinciki ba sai yau momma, ko ba komai yau for the first time a rayuwata bayan TRIPLETS na an gaya mani magana da zai kwantar mani da hankali, a ko da yaushe ina yawan jin Sheikh Sultan yana faɗin duk wanda ya rasa uwa, to tamkar ya rasa komai na duniya ne, komai kuɗinsa komai mulkinsa ba zai taɓa jin daɗi ba idan babu mahaifiya a gefensa, kasancewar ban ma san ya uwar take ba, ban taso da ita ba, sai ina ganin kamar dukka shirmensa kawai yake faɗa, ban taɓa jin ciwon rashinki a tattare damu ba sai yau, am really happy da jin kalamanki masu sanyi a gareni, a kodayaushe idan abin bakinciki ya sameni, sai dai na barshi a cikin zuciyata, dan babu mai iya fahimtarta a duniyar nan, even su Areef ba kasafai suke iya fahimtata ba bare har su gaya mani magana mai daɗi da zai sanya ɓacin ra'ina na wuce, kullum ni kaɗai nake faɗa da zuciyata, a yau ne na gane cewa Sheikh Sultan ya yi gaskiya da ya ce rashin uwa musifa ce, i really love our momma". Ya kai karshen maganar yana kara kwantar da kansa a saman kafaɗunta. Ko da sunan wasa bai taɓa yin magana mai tsawon haka ba, bai kuma taɓa yin magana makamancin irin haka da wani ba, lallai uwa uwa ce ko da kuwa a kan bola take yawo, Allah sarki bawan Allah dole ma ya zamana yana da zafin zuciya, dole ya zamana yana da taurin rai, dole ya zamana mafaɗaci, a koda yaushe shi kaɗai yake shanye ɓacin rai, bakinciki, damuwa, da komai da komai nasa shi da TRIPLETS nasa, ya shanye bakincikinsa ya kuma shanye nasu Areef, bashi da wanda zai gayawa damuwarsa, already kun sani tun farko shi baya magana, bai saba da kowa ba, TRIPLETS nasa ma iya wasanni na nishaɗi suke yi idan sun haɗu, ga ciwon Aseef, kunsan ba yadda za'ayi ya zauna yana gayawa Aseef damuwarsa, Areef kuma ba zama ma yake yi a gidan ba time ɗin bare ya fahimci shi, kusan za'a ce shi kaɗai yake rayuwarsa ta baɗini, baya shigo da kowa, bawan Allah. Sosai gwaggon ta ji wani irin mugu mugun tausayinsu ya kara kamata, duk abin da ya faɗa gaskiya ne, ba shakka ya yi ƙoƙarin da sai a tara zaratan maza 100 ba'a sami biyu da zasu iya kamanta abin da ya shanye na tsawon shekaru 25 ba, tun da suka fara girma keman har zuwa yanzu, dama ance babba juji ne, komai a kansa take karewa shi kaɗai, damuwar ciwon Aseef na shawon shakaru shi ya shanyeta a ransa, sau da dama Areef yana jefa shi cikin damuwa, amma haka yake shanyewa kamar ba'ayi ba, ba shakka ya cancaci a yi mashi babbar jinjina. "Saif bawai kawai ina gaya maka Rimsha zata samu lafiya dan na maka daɗin baki ko kuma na kwantar maka da hankali bane, da iya gaskiyata nake gaya maka In Sha Allah bazata jima ba zata samu lafiya, keep praying for her ka ji my son?". Ta kai karshen maganar tare da ɗaura hannunta a saman lallausan dark black curly hairnsa tana ɗan shafawa. Shiru ya kwanta, ban da tunanin Rimsha babu wani abin da yake a cikin zuciyarsa, shi kaɗai yasan meyake ji. Cigaba da shafa kan nasa ta yi tana kara gaya mashi kalaman da zasu kwantar mashi da hankali, dan ta lura idan bata yi da gaske ba, to zata zama mai jinyar majinyata biyu, saboda ba shakka idan bata bada himma ta kwantar mashi da hankali sosai ba, zai iya faɗuwa, dan Rimsha ta zama jinin jikinsa, ba zai iya jurar ganinta a cikin wani hali ba, kamar yanda ba zai iya jure gani Aseef ko Areef a cikin wani hali ba, to ita ma hakance a wajensa, ta zama wani ɓari na rayuwarsa, so dole gwaggo ta mayar da hankali sosai, dan kada ta yi jinya biyu. Ba ita ta kyale shi ba sai da ta ji ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya har sau biyu, alamar ya ɗan samu nutsuwa kaɗan, sannan ne ta raba jikinta da nasa tana mai kara jaddada mashi Rimsha zata samu lafiya nan bada jimawa ba, dan haka ya je ya kwanta ya huta, ya yi barci, saboda daren jiya bai yi ba. "Momman i can't sleep, bana ma jin barci, zan je garden na ɗan samu hutu ni kaɗai". Ya yi maganar cikin wannan nutsuwa tasa, har gobe akwai zallar madarar izza a voice nasa, da alama hakan a cikin jininsa take. "Tom shikenan bari ni kuma na kara duba Rimshar, by 8:00 dai'dai sai ka zo ka saya mata abubuwan da ake buƙata ko?". Jinjina mata kai kawai ya yi tare da wucewa ya nufi stair case dan ya sauka kasa. Ita kuma ta wuce ta nufi bedroom nasa dan ta duba jikin Rimshar. Yana shiga garden ya zauna a saman sofa mai zaman mutun uku, shiru ya jingina kansa da jikin sofar yana tunanin yanda ya yi wa Meeshansa kaca kaca, abin ya ɗaga mashi hankali. Wayarsa ce ta fara ruri alamar shigowar kira, ko bai duba ba yasan su Areef ne, dan haka suke, idan basu a tare, da gari na waye zasu kira juna video call dan suka ga juna, tun suna ƴan samari 12 to 13 haka suke. Nisawa ya yi kafin ya fito da wayar daga aljihunsa. Su ɗin ne kuwa suke kiransa, kuma video call ne. Shiru ya ɗan yi, ba dan TRIPLETS nasa bane, da ba abin da zai sanya ya ɗauki kiran wani a wannan halin da yake a ciki, amma su sun kasance bugawar zuciyarsa ce, dole ya ɗauka dan ya kalli kyawawan face nasu, yana kewarsu shi ma. Picking na call ɗin ya yi cikin nutsuwa. Areef ne kaɗai kwance a saman tampatsetsiyar lallausan bed nasa, ya tada kai da lallasan pillow, daga shi sai short, babu riga a jikinsa, ya sakarwa Jehan wannan Lion chest nata da zata rinƙa kwanciyar a buɗe, ko singlet bai saka ya rufe mata kayanta ba, ya saki gashi har tsakiyar bayansa, dama kunsan shi a cikinsu dukka ya fisu tara gashi, nasa ta kai har tsakiyar baya, while na Lion a iya bayan wuya take, shi kam Aseef ma ai dukka yake datse kayansa, baya son takura ya ce. "Good morning our Lion". Ya yi maganar voice nasa cike da zolaya. Lumshe idanuwa Lion ɗin ya ɗan yi tare da buɗesu a kan wayar tasa. "Where is Heartbeat?". Ya faɗa a sanyaye. "Kai da ka sani, yana barci mana, time na tashinsa bai yi ba". Jinjina kai kawai ya yi, yau ji yake yi ma magana ta zame mashi tamkar maɗaci, sam bai son motsa laɓɓansa, dama shi ba gonin yin magana bane, sai ta kuke mashi yake buɗe baki ya yi magana, da ido ma ya isa ya amsawa mutun, bare yau da yake cikin wannan hali, ai sai a slow kawai. "Ka je wajen Sheikh Sultan ɗin ne?". Cewar Lion ɗin. "Wlh Lion baka da gaskiya, ji idanunka kamar na momma a yau, duk sai wani kawar da kallonka kake yi, ni nasan dole akwai wani abin da ka aikata, faɗa mani me kayi?". Cikin zolaya ya yi maganar, dama already kun san halinsa sarai da iya zolaya da neman tsokana. "Areef zaka bani amsa nane ko kuma dai you're asking me this silly silly questions marasa amfani?". "I can't amsa you har sai nima ka gaya mani me ka aikata, where is Rimsha and momma ma first? I asked Jehan about Rimsha, she said she don't know where is she, to kai faɗa mani ina take, dole kai ka sani". Areef akwai neman magana ta karshe, daga kansa an rufe kofa in dai wajen neman tsokana ne, har da yi wa Jehan karya, duk dan ya sanya Lion yin magana, Jehan ɗin da ko tashi daga barci bata yi ba, amma dan neman tsonana wai ya tambayeta ina Rimsha? Neman tsonace kawai, ai yasan tun da Lion ɗin yana gari tare zasu kwana da Rimshar, ba da Jehan zata kwana ba, sai ya yi kamar bai san hakan ba, dan shegen iya tsokana "Areef wai ni kam am i play with you? Am I your mate?". "Yeah you're my mate, and we're playing together mana, what's next?". Ji Lion yake yi tamkar ya damko shi ya makure shi, amma ba hali, da'a tare suke, da ba abin da zai hana shi yau bai shake shi ba, a kage yake da ya ji amsa, amma tsabar iskanci irin na Areef yaki bashi amsar abin da yake son ji, yana son jin ya suka yi da Shaikh Sultan ne, amma ya tsaya sai tsiya yake yi mashi. "Lion do you now something?". Ko kallon in da yake Lion ɗin bai yi ba, bai kuma da niyar sake tanka mashi. "Am seeing your face like wanda ya kwana da mace suna chaskalen ma'aurata, anya kana da gaskiya kuwa? Tell me the truth ba dai chaskale mana our Rimsha ka yi ba?". Ya kai karshen maganar yana karewa face ɗin Lion ɗin kallo. Areef akwai kwakwalwa sosai, sarai ya gane matsalar Lion ɗin, kada ku manta shi ya zauna da mutane daban daban, kuma ya zauna a wajaje daban daban, tun kallon farko da ya yi wa ɗan uwan nasa ya fahimci dole akwai wani abin da ya aikata, musamman yanda damuwa ta bayyana a saman face nasa, ai dole kowama a wannan gaɓar ya gane cewa e lallai Lion yana a cikin damuwa. Ɗago idanuwansa ya yi izuwa saman screenshot ɗin wayar, calmly ya ce "Ka kammala aikin da na baka ne?". Gabaɗaya Lion so yake yi ya canzawa Areef ɗin topic na hiran, dan baya jin kamar zai iya gaya mashi ga abin da ya faru, sai dai shi kuma Areef ɗin ya matsa mashi da tambayar sai ya gaya mashi meyafaru da shi haka. Bashi da zaɓi dole ya gaya mashi ga abin da ya faru kawai. A wani irin dubu ɗari Areef ɗin ya miƙe zaune, wani irin zaro idanu waje ya yi, ya rasa me ma zai ce da Lion ɗin. Wani irin kallo Lion ɗin ya wurga mashi, irin kallon nan na lafiya kake wani gani na haka? Irinsa ya wurga mashi da waɗan nan dara daran idanuwan nasa. Marairaice murya Areef ɗin ya yi tamkar wani maraya yana cikin tsaka mai wuya ya ce "Allah sarki our Rimsha". Abin ma gwanin ban dariya, dan da iskanci Areef ya faɗi wannan kalmar. Ganin serious ɗan uwan nasa yana a cikin damuwa ne yasa ya kawar da duk wata shiririta tare da gyara nutsuwarsa ya tattare hankalinsa wajen guda, cikin sanyin murya ya ce "Sorry our Lion, ba laifinka bane, kuma ba laifin Rimsha bane, dama kowace mace sai ta fuskanci makamancin haka, amma ba irin naka ba, naka ai ya wuce tunani, fatana dai yanzu Allah ya bata lafiya yasa kuma mun samu baby's, yasa kwallo uku kamar mu ka zura a raga........" Kasa karisa maganar ya yi sakamaƙon wani irin kallo wanda ya fi harara kuna Lion ɗin ya wurga mashi, dan kawai ya yi maganar babys, idan baku manta ba shi fa Lion baya son yara, sam sam baya son hayaniyarsu ko kaɗan, so baya shiri da duk wanda zai yi mashi addu'ar samun yara, a tunanin Areef tun da yanzu sun kai ga yin aure, wata kila Lion ɗin ya sauya yana son yaran a yanzu, bai san cewa babu abin da ta sauya ba, har yanzu yana a kan bakarsa na baya son yara. Tashin sense lallai akwai kura ba kaɗan ba. "Sorry our Lion ba baby's nake son cewa ba, mantawa na yi, sai ya yi mani kamar da Aseef muke hira ne". Shiru ya yi bai sake tanka mashi ba, dan shi kaɗai yasan me yake ji. Sosai Areef ɗin ya yi ta rarrashinsa tare da kwantar mashi da hankali, har karfe 8 ya cika, sannan ne ya miƙe tare da yi wa Areef ɗin sallama, ya katse kiransa ya nufi cikin gida. Kai tsaye bedroom nasa ya nufa. Bakinsa ɗauke da sallama ya shiga, a nan ya isko gwaggon a zaune kusa da Rimshar, har yanzu dai Rimsha ko motsawa bata yi ba. Wajen bed ɗin ya kariso, barka da safiya ya yi wa gwaggo, yana magana yana kallon face ɗin Meeshan tasa, har yanzu dai tana nan yadda take ba sauyi. Miƙa mashi takardan duk abin da zai sayo mata ta yi, tana mai karfafa mashi gwiwa tare da kwantar mashi da hankali, ta lura zai iya jure komai na rayuwa, amma banda damuwar TRIPLETS and Rimsha, daga kanta ita gwaggon, TRIPLETS nasa da kuma Rimshar sune rauninsa a rayuwa. Karɓa kawai ya yi ya fito waje, kai tsaye bedroom na uncle T ya nufa, dan su tafi a tare. Ita kuma gwaggon mikewa ta yi ta fita izuwa nata bedroom ɗin, saboda gari ya waye tasan yanzu Jehan zata zo ta fara zuba mata shagwaɓa, so bata son su san abin da ya faru da Rimshar ma bare su kuma su tsorata. Tana shiga bedroom nata Jehan ɗin ta shigo bakinta ɗauke da sallama tana aikun turo baki, kayan barci riga da wando dogaye ne a jikinta, launin pink color masu matuƙar kyau, ga cup mai bala'in kyau a hannunta, A dubu ɗari gwaggon ta ce "Jehan mekike sha?". Ba tare da ta kalli in da gwaggon take ba ta bata amsa da "Abin da kuka haɗa mana nan ne, ba dama kafin mu ci komai da safe shi muke fara sha ba? Wai gwaggo ko dai kin fara tsufane waɗan nan idanun naki manya manyan kamar na Dr Salman ɗin nan sun dai'na gani? Ka gansu manya manyan da su kuma ace baki gani sosai, sai na kai ki asibiti". Ta kai karshen maganar tare da hayewa bakin bed ta zauna tana ƙoƙarin kai cup ɗin ɗan bakinta. "Ke dakata tukun nan". Gwaggo ta faɗa a hanzarce. Ɗago fararen idanuwanta ta yi tare da saukesu a kan face ɗin gwaggon, fuskarta cike da mamakin meyasa ta dakatar da ita daga sha kuma. Zama a gefenta gwaggon ta zo ta yi, cikin sanyin murya ta ce "Jehan kada ki ɓoye mani, faɗa mani gaskiya, shin kun taɓa kwanciya ta sunnah da Areef ne?". A ɗari ta zaro ido tana kallon gwaggon, kafin kuma ta tuntsure da dariya tana faɗin "E lallai yau dai gwaggo bake bace, Queen ta canzo mana ke, au ashe Queen ɗin ta mutu ma, yanzu gwaggo kawai sai ki tambaye ni?". Harara gwaggon ta wurga mata kafin ta fara magana "Ke bada wasa nake yi ba, faɗa mani gaskiya yanzun nan". Girgiza mata kai ta yi tana bata amsa da "A'a bamu taɓa ba......." Ai tun bata kai karshen maganar ba gwaggon ta kwace cup ɗin daga hannunta tana faɗin "Daga yau kada ki kara shan wannan abin, komai ma da muka haɗa kada ki sake sha, maza jeki duba idan Akila ta tashi daga barci ki kira mani ita". Mamaki sosai ne ya bayyana a saman face nata, tambayar kanta take yi shin meyasa gwaggo zata hanata sha? Ita da kullum take takura masu a kan su sha maganin nan sosai, kada su tsallake kona minti ɗaya, shi ne yau kuma zata hanata? Abin da mamaki. "Akila nace ki kira mani ne ko kuma tunani na ce ki shiga yi?". Turo baki ta yi kafin ta ce "Gwaggo Akila fa bata tashi daga barci ba, kin sani sai almost 12 take tashi fa". Da Akila da Aseef dai sarakan barci ne, su ne last na tashi barci a gidan, da daddare kwana suke yi manne da waya suna kashe juna da kalaman love, duk iya soyayya na Areef ya basu hanya, dan fa su macewa juna suke yi, sai su kwana makale da waya, sai anyi sallar asuba suke samu su kwanta, shi ne idan suka fara barci sai 12 na rana, suna tashi kuma ko abinci basu nema suke sake makale waya, wani lokaci ma suna wayar video call suna breakfast, Aseef and Akil halinsu babu wani banbanci, duk zani ne ta tattada muje, shagwaɓaɓɓune na gasken gaske, na kin karawa, haka zasu yi ta zubawa juna kukan shagwaɓa kamar ba gobe, kuma haka zasu rarrashi juna, da yake sun saba ma abin ya zamto masu jiki. "Gwaggo ina son muje shopping, za'a saya mani kaya da kuma waya, mafiya yawan kayan da nake sanyawa a gidan nan fa kayan Rimsha ce, to ni gaskiya na gaji da saka kayanta". Tana magana tana haɗe gerar sama da kasa. "Dama basu yi maku lefe bako?". Cewar gwaggon. "Menene kuma lefe?". Ta tambaya tana bin wayar gwaggon dake ringing da kallo. "Lefe kayan da maza suke sayawa mata kafin aure mana". Ta bata amsa tare da jawo wayar tata dan ta ga wanenen yake kiranta?. "Mu babu wani lefe da suka yi mana, kawai ni gwaggo ki kira daddy a waya muje shopping hai, ina ruwana da wani lefe? Mu ba muna da kuɗin sayan kayan ba? Dole sai su ne zasu saya mana?". Ta kai karshen maganar tana turo baki tare da ɗaure fuska. Duk abin da ta faɗa Areef ɗin yana jinta, saboda shi ne ya kira gwaggon a wayar, kuma already ta yi picking call ɗin, ga shi da English suke magana, so ya ji komai. Jehan sarkin iyayi da nuna isa, wato ita lefenma bata ce Areef ya yi mata ba, daddynta yana da kuɗi, dan haka su sun wuce ayi masu lefe. (Ni ko nace ba shakka duk wannan izzar da isar tata tana taka bakin gate na farko na gidan Lion na Washington zata zama ƴar kauye, dan gidansa ginine da babu kwatankwacinsa a Nigeria, maƙudan dukiya aka narka na kin karawa, Daula ce guda, idan kana cikinta sai ka yi tunanin ba'a duniya kake ba, Allah ka yi mana arziki mai albarka mai amfani da zamu taimaki Al'ummar musulmi Al'ummar manzon rahma manzon tsira.) "Good morning momma". Ya faɗa cikin sanyin murya, duk da lokaci time na agogo namu da nasu daban daban, amma ratar bata da yawa sosai, kuma ya san safiya ce yanzu a Nigeria, shiyasa kawai ya ce mata good morning. "Morning how are you and my auta?". Nisawa ya yi kafin ya amsa mata da "Autanki yana can yana aikin barci da ya saba, Momma please help me give my baby this phone, jiya taki yin magana da ni, fushi take yi da ni, dan banzo ba". Kallonta gwaggon ta yi da mamaki a saman face nata, wato Jehan ta cika ƴar duniya, sai tazo ta nuna masu tamkar bata damu da Areef ɗin ba, tamkar bata son shi, ashe ma saboda bai zo ba har da yin fushi da shi ta ɓata rai, kai Jehan ba'a iya mata, kuma baka gane mata sam sam, ta sanya bawan Allah a cikin tunani, kuma sarai ita ma abin yana damunta, kawai dakiya ce, ita ma jiya ta ji a jikinta na rashin wayar da basu yi da daddare ba, ta dake ne ta nuna kamar ba komai, dan ma kada a ra'inata. (Allah mai iko, Jehan duniya, ta iya dakewa ta shanye abu kamar Lion, sai ta yi kamar bata san komai ba, alhalin tana azabtuwa daga ta cikin zuciyarta 😂) Miƙa mata wayar gwaggon ta yi tana faɗin "Karɓi za'ayi magana dake". Harara ta wurga wa wayar tana faɗin "No need". Nisawa ya yi kafin ya ce "Please my baby, ya isa haka wahalar da ni ɗin kin ji, i can't agree irin wannan avoiding nawan da kike yi, ina shan wahala sosai fa, wai baki jin tausayi nane?". Wani irin sanyi ta ji a ranta na jin muryarsa, har da sauke nauyayyar ajiyar zuciya, amma saboda taurin kai sai ta ce ita fa ta gama magana kenan ba zata karɓi waya ta yi magana da shi ba. Gwaggo baiwar Allah tana ganin rayuwa wajen ƴaƴan nan nata da matansu, kowa da kalar tasa rashin kunyar. Katse kiran gwaggon ta yi tare da fara yi wa Jehan ɗin nasiha a kan ba'a yiwa miji haka, ta sani Allah zai kamata, tun jiya ta sanya mijinta cikin damuwa, ya kwana cikin ɓacin rai, sannan yau da safe ma ta tashi ta kara mashi wani? Bata da hankali ne? To wlh ta bi duniya a hannu. Hararar gwaggon ta yi kafin ta ce "Kawai dan ke baki jawa Dr William aji ba shi ne ni zaki hanani jan ajina? Dake da mummy duk naji tarihinku ai, ba wani jan aji da kuka yi, ita mummy tana gani daddyna kyakkywa ta ce shikenan zata bishi ita kam, kema Dr William yana ɗan zuba maki kallon soyayya da waɗan nan blue eyes ɗin nasa kawai kika ruɗe, ba wani jan aji kike biye mashi, to ni wlh a'a, sai na ja ajina dan ma kada ya renani, dole ya kalleni da daraja, sai na wahalar da shi". Ta kai karshen maganar zata mike ta fice daga ɗakin, ko kunya bata ji ba, a gaban mahaifiyarsa take cewa sai ta wahalar da shi, duk wahalar da take bashi a yanzu bai isheta ba, ikirarin kara mashi wani ma take yi. Rikota gwaggon ta yi tana salati, wai shin ya zasu yi da Jehan ne sukam? Yarinya ta ra'ina mutane? Wai jan aji take yi, lallai ma yarinyar nan. Duk abin da ta faɗa a kunnuwar mummynta ta faɗa, dan mum ɗin ta shigo gaishe da gwaggo kenan ta ji suna maganar, shi ne ta tsaya a bakin kofa tana sauraronsu. Jin abin da Jehan ɗin ta faɗa ne yasa mum ɗin ta juya ta fasa shiga ɗakin, dan tasan mutun ɗaya ne a yanzu zai saita mata Jehan ɗin nan, tun farko gwaggon ce ta shagwaɓa ta, ta ɓatata, ta kuma sangarta, dan haka yazu basu isa su ce zasu tankwarata ba, Areef dai shi ne zai gyara mata zama ya dawo da ita a kan hanya tun da tana son shi, dan haka sai mum ɗin ta koma bedroom nata dan ta kira daddynsu ya haɗa ta Areef ɗin a waya tun da suna a tare, zata gaya mashi yadda zai yi mata magain Jehan ɗin ne, dan idan ba haka suka yi ba, Jehan fa ba zata gane me ake nufi da miji ba, already gwaggon ta ɓata komai. (Gaskiya akwai cakwakiya kam, dole Areef ya saitata a kan hanya, idan ba haka ba zasu sha wahala.) Sai misalin karfe 9:30 Lion da Tga suka dawo cikin gidan. Tga na yin parking a parking space babu ɓata lokaci Lion ɗin ya fito hannunsa na ruke da ledoji manya manya, Tga ɗin yaso ya karɓa mashi kayan, amma ya ce ya bar mashi abinsa, a haka suka nufi cikin gida. Kai tsaye bedroom nasa ya nufa, bakinsa ɗauke da sallama ya shiga, gwaggo na bedroom nata, a saman bedside drawer ya ɗaura ledojin tare da zagayowa ya dawo ta ɗayar ɓangaren gadon, kusa da Rimshar kenan. Zama ya zo ya yi tare da zubawa face nata idanu yana kallon yadda ta kara uban haske kamar ba lafiya ba. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 7/5/2024 E26 A haka Gwaggon ta shigo ta same shi, magunguna da alluran ta fara ɗauka dan ta yi aikinta, tun bata yi mashi magana ba ya tashi ya fice daga ɗakin, dan yasan zata ce mashi ya fita ne, so is better for him da ya fita ɗin ma. Yana fita garden ya koma, dan ya zauna ya huta. Saman sofa mai zaman mutun uku ya kwanta tare da miƙe dogayen kyawawan fararen kafafunsa, a hankali ya lumshe dara daran idanuwansa, sai tariyo mashi komai ƙwaƙwalwarsa take yi mashi, wani irin yanayi yake jinsa a ciki, da haka barci ta ɗan sace shi, dama kunsan ita barci ba'a cin bashinta, idan ma kaci sai ka biya, so gara ma kawai lokacin yinta ka yi ta sai ya fimaka. After 15 days. (Bayan kwanaki shabiyar) A tsawon kwanakin nan gabaɗaya ko motsawa Rimsha bata yi ba, sai dai duk da tana sume tana samun sauki dai'dai gwargwado, a yanzu jikin nata ya koma normal, temperature jikinta ya dai'dai ta, wannan uban haske da ta yi ma a yanzu ta ɗan koma normal colornta, duk da ba gabaɗaya ba. Shi ma Lion a yanzu hankalinsa ya ɗan kwanta, sai dai fa har ƴar rama ya yi, kyakkywar jajir ɗin skin nasa ta ɗan yi duhu, saboda ana zuba rana a Naija ba karya, damuna ta jima da tafiya, yanzu shirye shiryen azumi suke yi, saura watanni biyu a kama azumin, so fatarsa ta ɗan yi duhu, ya rame saboda ciwon na Rimsha, ga shi har tsawon waɗan nan kwanaki 15 ɗin bata ko motsa ba, a halin yanzu mummynta tasan me yake faruwa, sai dai bata ɗaga hankalinta ba, dan tasan already dama da akwai wannan rana a rayuwar ƴaƴan nata, Aseef yana wajen Sheikh Sultan, kullum suna manne da waya suna aikin da suka saba shi da Akila, kamar wasu chewing gum basu rabuwa. Har wa yau abubuwa sai kara zafafa suke yi har suna tafasa a Washington, shi kuma Lion da ya tada tarzomar, hankalinsa a kwance yana Naija abinsa, ya baro su Areef da shan aiki, daddyn Rimsha ma yana can Washington ɗin already kun sani, takardan ɗan kasa Lion ya sanya ayi mashi, da kuma sauran abubuwa da suka shafi kasar, sam Lion yaki yarda ya haɗa hanya ko da ta waya ce da su His Excellence, sun buga sun raya, amma ina ya ce bashi da lokacinsu a yanzu, lokacin zama ya yi magana da su ta wuce, a yanzu primary election sai kara matsowa take yi, saura ƴan kwanaki, kun san yanayi na juyawa, haka shi ma watannin namu suke juyawa, so a yanzu kasar U.s tana shirye shiryen yin primary election ne, kuma Lion sai kara samun goyan bayan al'umma yake yi, shi kaɗai yasan kudurinsa idan ya ci wannan zaɓen, shi kaɗai yasan me yake shirya masu. A waɗan nan kwanaki sha biyar ɗin dukka Jehan tana ta fama da rashin lafiya, ba komai ne ya haddasa mata hakan ba kuma face shareta da Areef ya yi, sai dai babu wanda yasan da dalilin rashin lafiyar tata, saboda dakiya irin nata, ta jure ta ɓoye abin a cikin zuciyarta, shi kuma Areef ɗin ya shareta ne bisa umarnin mummynta, ita ta gaya mashi ya jure ya daure ya shareta ko da na wata guda ne, dan idan ba haka ya yi ba, tabbas zaman aurensu zai bashi wahala, Jehan ba zata san mahimmancinsa ba, ba zata ɗauke shi da daraja ba duk da tana son shi, so yana da kyau ya fara koya mata hankali tun yanzu, a cewar mummyn nata kenan. Ita kuwa Gwaggon duk hankalinta a tashe, ga Rimsha kwance kamar gawa tsawon kwanaki, ga Jehan ba lafiya, zazzaɓi mai zafi ne kamar zata mutu, ita gwaggo baiwar Allah bata san cewa ciwon Jehan Areef ne musabbabi ba, da ta sani ai da tuni ta sanya shi ya kira Jehan ɗin, dan kun dai san Jehan ta gidan ta ne, so yana da kyau ku fahimci duk abin da Jehan take yi ba fa laifinta bane, horon gwaggonce ita, komai ta yi dai'dai ne a wajen gwaggon nata, bata laifi, so kunga kuwa ai dole a samu matsala, idan baku manta ba tun farko, tun suna Abuja ita Rimsha ta fi shakuwa ne da mummynta, shiyasa ma tafi Jehan samun ilimin addini sosai, ita kuma Jehan tana manne ne da gwaggo, shiyasa ta fi Rimsha ilimin boko sosai, to idan baku manta ba tun ainahi suna da banbanci, dan gwaggo dai kowa yasan ƴar bokoce ta gasken gaske ma kuwa, kunga kuwa dole Jehan ta so boko sama da ilimin addini, dan ma dai an yi sa'a ita ma gwaggon akwai ilimin addinin ne, sai dai na bokon yafi yawa. A takaice dai gwaggo bata san menene yake damun Jehan ba, sai faman tambayarta take yi menene matsalar, domin kuwa da ta yi mata test, results ɗin ya nuna mata cewa wannan zazzaɓi fa ba daga kwayar cuta Jehan ɗin ta same shi ba, zazzaɓi ne na damuwa da pressure ya yi mata yawa, anyi mata tambayar duniyar nan taki gaya masu menene yake damunta, dan a cewarta idan ta ce tana kewar mijinta ne ai ta zubar da mutuncinta. (E lallai baki dawo kan hanya ba Jehan, da sauranki.) Mummynta kuwa ta san komai sarai, ta kyaleta ne sai ta yi laushi, sai ta buɗe baki da kanta ta ce da Areef ya yi hakuri ta tuba bazata kara ba, sai ta yi hankali ta koyi sanin darajar mutane. A koda yaushe idan gwaggon tana hira da Areef ɗin, idan ta tambayesa ya yi magana da Jehan ya ji ya jikinta yake kuwa? Sai dai ya ce mata e sun yi magana ta wayar Rimsha ko wayar Lion, yaki gayawa gwaggon gaskiyar basu magana, saboda mum ta ce mashi in dai ya sake ya bari gwaggo ta sani, to wlh daga shi har ita kanta mum ɗin gwaggo ba kyalesu zata yi ba, dan a kan Jehan fa ita bata ji bata gani, duk wanda zai taɓa mata Jehan zasu yi dirama daga nan har kotun bangon duniya, dan haka ya kiyaye kada ya yarda ya sake ya bari gwaggon ta san cewa basu waya kuma sanadiyyar hakance ta kwantar da Jehan ɗin rashin lafiya, shi dai ya san yadda zai yi kawai. To shiyasa sam yaki yarda gwaggon tasan halin da ake ciki, amma fa shi ma yana azabtuwa matuƙa, yana ji a jikinsa, dan har zazzaɓi na kwana biyu sai da ya yi, kun san su dama basu iya so ba, idan suka fara son mutun, to wlh har ga Allah da gabaɗaya zuciyarsu suke son shi, babu wasa a ciki, hakan cema tasa su basu yin mata biyu, Baturen mutun mace ɗaya yake aura, dan su sunce ba zasu iya raba zuciyarsu gida biyu su bawa mata biyu ba, ɗaya ta ishesu, to wannan ɗayar gabaɗaya zuciyar tasu suke ɗauka su miƙa mata, shiyasa idan mace ta yi breaking heart nasu a soyayya har kashe kansu suna yi, ko kuma zuciyar ta buga su mutu, dan ba zasu iya jura ba. To dai shi ma Areef sai da ya yi zazzaɓi, gabaɗaya a daddafe yake yin duk wasu ayyuka na Lion, dan ma dai mumnyn Jehan ɗin ce ta ce ya yi hakan, da wlh ko kwatantawa ba zai taɓa iya yi ba, ba zai iya fitowa ya ce wa mum ɗin ba zai iya bane, kun san shi daban yake a cikin TRIPLETS, da Lion ne ko Aseef wlh ba mum ba ko uban mum ne ɓaro ɓaro zasu ce mata ba zasu yi ba, amma da yake shi Areef zuciyarsa daban da tasu, sai ya hakura ya daure ya bi abin da ta ce, dan ya ɗauki mum ɗin tamkar uwa tun da uwa ce ga matarsa farincikinsa, kuma mata ce ga uncle nasa da ya fi kauna, dole ya jure ya yi mata biyayya, banda haka wlh komai wahalar da shi da Jehan zata yi zai iya jurewa ya biye mata, dan yana sonta da gabaɗaya zuciyarsa. A ɓangaren Aseef kuwa, har wa yau dai yana a wajen Sheikh Sultan abinsa, sai kwarara mashi ruwan adduo'i ake yi, saukar Alqur'ani mai girma babu kama hannun yaro, kullum yana hira da Heartbeat nasa sosai bawan Allah, suna faranta ran juna. Har wa yau Akila da Jehan basu san menene ya faru da Rimsha ba, su dai an ce masu bata da lafiya ne kawai, so sun ɗauka zazzaɓi ne ita ma, da yake kuma Lion yana gari, sai basu nemi ganinta ba, dan suna tsoron shiga bedroom nasa, kuma already kunga a cikin bedroom na mijin nata take jinya, a in da ya yi dis virgin ɗin nata a wajen ake jinyarta baiwar Allah. ❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷ Lion ne tsaye a harabar gidan nasu, sanye yake da wando three cuter da riga mai karamar hannu, ƴar ramar da face nasa ta yi ta fito ɓaro ɓaro, ya ɗan rage tsawon gashin kansa, ya kuma ɗaureta a bayan wuya, face nasa ta yi fayau da ita kamar wanda ya tashi daga zazzaɓi, sai tashin daddaɗar kamshi perfume nasa yake yi, ya harɗe hannayensa a saman Lion chest nasa, duniya duk ta yi mashi wani iri. Donal ne ya kariso wajen da yake a tsaye ɗin, sara mashi ya ɗaga hannu ya yi cikin girmamawa kafin ya ce "Sir Alex said you're call me". Shiru ya ɗan yi na ƴan mintoci da a kallah zasu kai uku zuwa biyar kafin calmly ya fara magana "There's some cases da suke a hannun Mark before ya koma U.s, akwai wani mutumi da ɗauko shi daga Abuja da na bashi a kan ya horar mani da shi before na buƙace shi, to ina bukatar mutumin a yanzu". Wani irin kamewa Donal ɗin ya yi tare da kara ɗaga hannu ya sara mashi, sannan ya wuce izuwa ɗakin da Mark yake kulle mutane. Jim kaɗan ya dawo, Lion ɗin yana tsaye a wajen bai motsa ba, cikin girmamawa ya sanar da shi babu kowa a cikin ɗakin. Jinjinawa Donal ɗin kai kawai ya yi, alamar ya ji ya tafi to. Da sauri ya juya ya bar wajen. Shiru Lion ɗin ya yi yana tunani, tabbas in dai babu kowa a wajen, to ba shakka Areef ne ya yanke masu hukunci. Kamar yanda ya yi hasashen kuwa hakan ce, Areef ne yasa aka kashe mutumin, dan dayaga Lion ɗin ya shiga busy, sai ya bibiyi case ɗin kawai ya yanke masu hukunci, su kuma malaman makarantarsu Rimsha ya sanya sojojin dake gidan suka basu horo mai tsanani, sannan ya sallamesu. Time da ya sallamesu ko takawa da kafafunsu basu iya yi, da rarrafe suka bar gidan, shi ma Areef oga ne wajen iya bada punishment idan ka shiga hannunsa. Ya ɗan ɗauki lokaci a tsaye a harabar gidan kafin ya wuce izuwa garden, dan ya kwanta ya ɗan huta, tun da wannan abin ya faru, bashi da wajen zama sai wannan garden ɗin, ita ma ba dan daɗi yake zama a cikinta ba, kawai dan bashi da yadda zai yi ne, garden ɗin yanzu duhu take yi mashi, Rimsha ita ce dama fitilar dake haske duk in da yake, so yanzu bata nan, ko'ina duhu yake yi mashi, sai dai ya runtse idanuwansa ya zauna a waje kawai, amma ba dan daɗi ba. A ɓangaren gidan Abbi kuwa, A'A Salahuddeen ya turo yayyunsa dan a tambaya mashi auren Hanan, dan shi da gaske yana sonta, sai dai baya zuwa wajenta, a waya kawai suke yin hira, saboda yana jin zafin su haɗa idanu da maman Ayla, kun san kuma tana gidan Abbin, so ita kanta Aylar baya son haɗa idanu da ita, yanzu kunyar mutanen gidan ma yake ji, saboda abin da mahaifinsa ya yi, da farko ma kamar zai hakura da neman auren Hanan ɗin, sai da Imran ya karfafa mashi gwiwa, sannan ya turo yayyunsa. Abbi ne ya yi masu jagora izuwa garin Katsina, dan su nemi auren Hanan ɗin daga hannun mahaifinta, shi kuma daddyn Jelly ya ce ba zai sami zuwa ba, saboda rashin lafiyar Ayla, almost wajen 3 months a yanzu kenan da kwanciya ciwon nata, amma bata warke garau ba, sai kuka abu kaɗan, duk ta zama wata birkitaciya baiwar Allah, so daddyn baya son ya matsa ko nan da can daga kusa da ita, duk da cewa mamarta tana kusa, amma ya fi son ya zauna ya kula da ita. Yau ɗaukarta ma ya yi suka tafi gidan Azharuddin Bature, saboda gidan babu kowa, Abbi da su Aunty sun tafi Katsina, maman Aylar ma ta bisu, dan su yi wa Hanan ɗin kara, Aunty ta ce tana son zuwa taga iyayen Hanan ɗin, shi ne Abbi ya ce to su je a tare, sun baro Aafia sai Hjy Hadiza da ba zama a gidan take yi ba, yanzu ma bata gidan, su Abbi suna fita ita ma ta fita, yanzu yawon bin malamai take yi, duk dan ta shawo kan Abbin, sai wahal take yi buƙata ta gagara biya, a matsayinta na uwa ta kasa zama ta yi jinyar Aafiar, sai gantali take yi a kan namijin da bai san ta yi ba, dan shi Abbi yanzu idan ba Aunty ba, baya ganin kowa a gabansa. Shi kuwa Irfan ya koma school abinsa, dama bai kammala master nasa ba, shi ma Akil sun koma Madina shi da Umaishansa, cikinta ya girma sosai har ya shiga watannin haihuwa, a yanzu kula na musamman Akil yake bata. Saura Imran da Jelly ne kawai a tare da Hjy Umaiya, shi ma Imran ɗin zai koma U.s, dama a can yafiye yawan zama, soyayyar jelly take dawo da shi Naija dama, so yanzu yana so ne ya ɗauketa su koma can mai gabaɗaya, ya zama Naija sai dai su kawo ziyara, Ammie ce ta dakatar da su yasa bai tafi ba, ta ce bata yarda ba, ya zauna a nan tare da su, Akil ya tafi shi ma yana son ya tafi ya barsu da kewa, sai rarrashinta yake yi yana neman shawo kanta dan ta yarda, so har yanzu dai bata amsa mashi da to ba, amsar kawai yake jira jirginsu ya ɗaga. ❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷ Su Abbi sun dira garin Katsina lafiya, kai tsaye gidansu baban Sadiq suka nufa, sam Abbi bai manta hanyar ba, motoci biyu suka yi dama, na familyn A'A Salahuddeen ɗaya, na Abbi, Aunty, Hanan ɗin, sai mana Ayla, su kuma mota ɗaya, . A kofar gidan daga can ɗan nesa suka yi parking na motocin nasu, sannan suka fito suka nufi gidan. A kofar gida suka tsaya, Hanan ta ce bari ta shiga ta duba baban nata, su Aunty su zo su karisa ciki tun da mata ne. Ba musu suka bita izuwa ciki, su Abbin kuwa suka gyara tsayuwa a wajen, sai kallon kaskanci ƴan uwan A'A ɗin suke yi wa gidansu Hanan ɗin, basu yi zaton a irin wannan lakar gidan za su wanko kafa su zo nemawa A'A mata ba, su duk a zatonsu a gidan Abbin matar take, sun ɗauka ƴarsa cema, dama idan baku manta ba gabaɗaya familyn A'A akwaisu da jiji da kai da alfahari, hakan yasa suka fara surutai a kan su fa a gaskiya sun fi karfin su nemi aure a irin wannan gidan. Sai hakuri Abbi yake basu, kin yarda suka yi, suka ce wlh A'A ba zai kawo masu wannan gayyar tsiya, gayyar talauci gidansu ba, dan haka ya nemi mata ƴar gidan mutunci, ƴar gidan mutane ba muna mutane ba. Surutai dai marasa daɗin ji suke ta jefar Hanan baiwar Allah da shi, sun ki tsayawa kuma baban Sadiq ɗin ma ya fito, sun ce sun fi karfin haɗa idanu da shi ma, sai da Abbi ya kira A'A a waya, suka haɗu suka rinƙa basu hakuri, sannan suka yarda zasu haɗu da baban Sadiq ɗin, amma su daga yau sun zame hannunsu a kan batun auren A'A, sun yarda zasu tambaya mashi auren, amma ya sani idan ya aureta kada ma ya ce zai kawo masu ita gidansu, su je can gidansa ya zauna da ita, basu bukatar ganin ƴar matsiyata a cikinsu, haka ba dan ya so ba ya ce ya yarda da sharaɗinsu, sannan ne suka ce to baban Sadiq ɗin ya fito su yi komai a wuce wajen. Ko da baban Sadiq ɗin ya leƙo ya ga manyan mutane masu ji da Naira, sai ya yi maza ya koma ya ɗauko tabarmar amarya mai kyau, kunsan shi da son abin duniya dama, tuni ya fara yi masu mubaya'a tare da zubar da girma da mutunci, abin ma har sai da ya bawa Abbi kunya, sai da ya yi danasanin rakosu da ya yi, dama tun farko basu ɗauki Hanan ɗin da daraja ba, ga shi babanta ya zo ya kara zubar mata da mutunci, duk sai Abbin ya ji wani iri, ya ji dama ya zo shi kaɗai ya gayawa baban ga abin da ake ci, daga nan ya sanar da shi zai yi mata miji ya bashi izini, idan ya bashi izinin sai ya aurar da ita cikin mutunci kawai, idan ya so bayan auren sai Hanan ɗin ta kawo A'A ɗin ya gaida baban nata, amma yanzu komai ya riga na kwaɓe, sai dai Allah ya ceceta kawai daga hannun familyn A'A, dan zata wahala, zata sha kyara, gori da kuma walaƙanci tare da cin mutunci, marainiyar Allah, sai dai daɗin abin ma dai A'A ba mazauni Nigeria bane ba, bai cika zama a cikin ƴan uwan nasa ba, so zai ɗauketa ne su tafi, shi ne sauki da zata samu, ba dan haka ba tana a tsaka mai wuya. A ɓangaren su Hanan ɗin kuwa, hannu bibbiyu maman Sadiq mace mai kirki da mutunci ta tarbesu, da yake yanzu ɗakinta Sadiq ya gyara mata shi, sai ya zamana fes gwanin birgewa, dama ita ba mace mai kazanta bace, tana da tsabta sosai, dan haka ko'ina fes a cikin ɗakinta, ga ɗan lafiyayyiyar bed nata mai matuƙar kyau da Sadiq ya saya mata, ta shimfiɗe shi da bed sheet mai kyau dai'dai talakawa, sai kamshin turaren wuta ƴar icce ɗakin nata yake. A saman tabarma suka zauna, cikin mutunci ta kawo masu ruwa a randar tulunta mai sanyi. Karɓa suka yi a mutunce suka sha, sannan suka fara gaggaisawa dan sanin juna. Hanan ce ta gabatarwa da Maman Sadiq ɗin su waye su, tare da yi masu karin bayani. Kara faɗaɗa murmushinta Maman Sadiq ɗin ta yi tana mai kara yi masu sannu da hanya tare da zuba masu ruwan godiya a kan ruke Hanan ɗin da suka yi. A can waje kuwa, baban Sadiq yana jin cewa neman auren Hanan suka zo yi, tun bai san su waye su ba ya ce ai ya basu ita duniya da lahira, ko bata so dole ayi auren, dan haka kada su damu. Ji Abbi ya yi tamkar ya kifa mashi mari, wannan wani irin uba ne? Abin ya yi matuƙar kona ran Abbi sosai da sosai. Shi wato baban Sadiq idan dai ya ga ƴar maiƙo maiƙon kuɗi duk sai hankalinsa ya tashi, duk sai ya ruɗe ya fita a hayyacinsa ya rasa tunaninsa, abin takaice, ya Allah ka rabamu da mataciyar zuciya. A can gida Kaduna kuwa, da misalin karfe 8 na dare, su Abbi basu kai ga isowa gida ba, suna a kan hanyar dawowa. Aafia ita kaɗai ce a gidan, baiwar Allah a yanzu saura ƴan kwanaki ta kammala iddarta, amma bata sani ba, Abbi ya bar Hjy Hadiza a gidan ne dan ta kula da ita, bai san suna fita ita ma ta yi nata ficewar ba, dama kun san daddyn Jelly da Aylarsa basu nan, so basu dawo ba har yanzu, shi ma Irfan baya nan, so ya rage saura ita kaɗai a gidan. Fitowa palo ta yi ta zauna a saman sofa, daga ita sai ƴar doguwar riga mara nauyi a jikinta, kanta na sanye da turban cap white color, ta yi wata iriyar ramar da idan ka kalleta sai ka tsorata, sai ka zubar mata da kwallah, dama kun san ita bata da ƙiba sosai, bata kai su Umaisha ba, so ta kara figewa kamar figaggiyar kaza kwaila, abin dai gwanin ban tausayi, ta yi duhu sosai, sai wannan dara daran idanuwan nasu na gado zaka gani a face nata, hancinta ya gara tsawo sosai, saboda ramar, ba laifi tana samun sauki, duk abin da mutun yake yi tana sane, ta koma normal kamar da, sai dai magana ce da bata buɗe baki ta yi, amma tana jin komai, da alama a yanzu babu wata cuta a tattare da ita face jimamin mutuwar Dr Nawid, shi ne yasa bata magana sam sam. Ta yi shiru ta zubawa Tv idanu kamar mai kallon Film, a zahiri ba kallon take yi ba, ta lula duniyar tunani ne kawai. Sallama ta ji daga bakin kofar shigowa, a hanzarce ta kai kallonta a wajen. Abbo ne ya shigo bakinsa ɗauke da sallama. A razane ta miƙe tsaye, dan kuwa ba zata taɓa mantawa da fuskarsa ba, a lokacin da Dr Nawid ya zo mutuwa, tabbas fuskantar Abbon ya bayyana a saman face nasa, shi ne ya kara jefata cikin tashin hankali da ya juyar mata da ƙwaƙwalwa, saboda yanda da ga fuskar Dr Nawid ɗin ya canza a lokacin, kun san dama ita already bata san Abbo ba, time da aka yi aurenta da Dr Nawid Abbo baya gidan, idan baku manta ba ya tafi wajen tsafinsu, so baya nan, ita a Man na school nasu wanda ya kashe Amal ta san Abbo, bata san ainahin face nasa ba, farkon ganinta da face nasa dai ranar da Dr Nawid zai mutu, kuma bata manta da shi ba!!. "Aafia lafiya kika razana kika mike haka?". Ya faɗa cikin nuna kulawa, tamkar bai san me ta razananwa ɗin ba. Baya ta ɗan ja kaɗan tana girgiza mashi kai tare da fara ruwan hawaye. "Aafia lafiya kike kuwa? Meyake faruwa? Kullum ina zuwa dubaki bana samun damar ganinki sai yau, kullum idan nazo sai na samu kina barci a ɗaki". Ya yi maganar yana nufota. Baya baya ta fara ja tana girgiza mashi kai ta kasa yin magana. Nufota ya cigaba da yi yana ta wasu surutai da bata gane me yake faɗa ba. Har suka kewayo ta wajen kujerar dake kusa da kofar fita, hakan ne ya bata damar ta zunduma ihu tare da juyawa a guje ta fita daga cikin palon, da gudu ya bi bayanta. Mai gadi yana zaune a saman chair nasa bai ankara ba sai ganin Aafiar ya yi ta buɗe gate ta yi waje a guje. Kafin ya mike ya zo ya bi bayanta dan ya ga ko lafiya, sai ganin Abbo ya yi ya zo ya wucesa fiw kamar wani fanka ya yi wajen shi ma, ai a dubu ɗari mai gadin ma ya nufi waje, dan a tunaninsa irin wannan fitowa da suka yi da gudu kamar wasu iskar fanka to ba lafiya ba cikin gidan yake, gara mashi shi ma ya gudu waje, koma me zata faru a ciki ya tsaya daga ta waje yana kallah. (Wayyo cikina, jama'a mai gadin nan zai kasheni da dariya, a'a yana da gaskiya fa😂 gara mashi ya tsaya ta waje, yaga sai fitowa suke yi kamar iskar fanka, tamkar waɗan da ake gefowa daga sama, kunga kuwa dole ya yi ta kansa shi ma😂) Kasancewar unguwar ta manyan mutane ne, babu kofa a wajen, duk suna cikin gidajensu, kuma Aafiar tun da ta yi wannan ihun sau ɗaya bata sake yin wani ba, dama kun san ba magana take yi ba, yanzu ma Allah ne kawai ya ƙaddara ta iya zunduma wannan ihu ta farkon, daga shi kuma bata sake yin wani ba, tana ta ƙoƙarin ta yi ihu dan a kawo mata ɗauki, amma tamkar an shake mata wuya, ta kasa iya buɗe bakin nata, haka ta cigaba da gudu da iya karfinta na karshe, dan ta ceci kanta daga sharrinsa. Shi ma Abbon da gudu ya biyo bayanta, ga shi dare ne ba rana ba. Tana haurowa ainahin babban titin fita daga unguwar tasu wata dankareriyar mota ta kwasheta, saboda ta shigo kan titin ne babu excuse, a guje kamar mahaukaciya. Shi kuwa Abbo buƙata ta biya, dama shi burinsa kawai ya kamata, ko tana raye ko tana mace, koma yaya dai ya kamata kawai. Dan haka ko kaɗan bai damu dan mota ta bugeta ba, sai ma wani daɗi da ya ji, ya nufi in da take kwance cikin jini malale a gefen hanyar dan ya ɗauketa............... ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 8/5/2024 E27 Da kyar mai motar ya iya taka birki, saboda yanda kan motar ta so ta kwace mashi. Bai tsaya dai'dai ta nutsuwarsa ba ya fito a hanzarce, dan ya duba ko tana raye ko ta mutu. Dai'dai lokacin shi kuma Abbo ya karisa wajenta da nufin ya ɗauketa. "Hi guy, where will you take her to?". Ya yi maganar cikin ƙwararriyar harshen turancinsa, kuma ya yi maganar yana nufosu, sanye yake da wandon jeans baka mai shegen kyau, sai army's T-shirt daga ta sama, kafafunsa na sanye cikin wasu kyawawan tsadaddun Booth mai matuƙar kyau, launin black color, ya saki gashi har bayan wuya, sai kamshi yake zubawa. "She is my daughter, i want to take her to hospital". Ya bashi masa shi ma cikin harshen turanci ba tare kuma da ya ɗago ya kalli wanene bane, shi dai burinsa kawai ya ɗauketa su bar wajen. Jin hakan yasa Tga ɗin ya juya ya nufi wajen motarsa ba tare da ya sake yi masu magana ba, dama idan baku manta ba shi baya son bakaken fata, yanzu ma abin da yasa ya fito dan yaga wanene ya buge ne, saboda a matsayinsa a soja bai kamata ya taka dokar kowace kasa ba, hakan ce ma kawai tasa ya fito, to tun da ya ji mahaifinta yana wajen, sai ya koma cikin motarsa da nufin ya bar wajen kawai. Kunna motar ya yi tare da ɗan yin reverse, dan ya samu damar wucewa. Kamar wanda aka yi wa allura, sai wani tunani ya faɗo mashi a cikin ransa, idan har da gaske wannan mutumin mahaifin yarinyar nan ne meyasa baya kuka da ya ga an bugeta? Meyasa bai nuna damuwa da tashin hankali ba? Ko dai su mutanen Nigeria haka suke basu damu da ƴaƴan su ba ne?. Waɗan nan sune tunani da tambayoyin da suka faɗo mashi a cikin ƙwaƙwalwarsa kamar wadda aka yi wa allura. Shiru ya ɗan yi kafin ya ce yes maybe mutanen Nigeria haka suke, basu damuwa da ƴaƴan su ne. Tuna hakan yasa ya ja motarsa ya bar wajen. Shi kuwa Abbo hannu ya kai da nufin ya ɗauketa, sai ya ji a yanda yake ɗin nan fa ba zai iya ɗaukarta ba, dole sai ya canza zuwa matashi mai jini a jika idan yana son ɗaukarta. Dan haka sai ya fara ƙoƙarin canzawa izuwa matashi. Cikin ƙanƙanin lokaci ya canza izuwa santalelen matashi, da yake dare ne, jama'a sam babu kowa a saman titin, dama kuma kunsan irin waɗan nan manyan unguwanni ba kasafai ka cika ganin mutane a waje ba, sai dai jefi jefi kaga giftawarsu, hakan tasa babu wanda ya nufi in da suke. Yana ƙoƙarin ɗaukarta wasu matasa su biyu daga bayansa suka yi mashi sallama tare da tambayarsa ko lafiya? Accident aka yi ne?. "Mota ce ta buge mani yarinya ta, kuma mai motar ya gudu, shi ne zan ɗauketa zuwa gida, daga nan sai mu wuce asibiti". A hanzarce matasan suka ce "Innallilahi wa inna ilahirrajiun, wannan ai gaggawar kaita asibiti zamu yi, idan ba haka ba tana iya rasa ranta, bakaga yadda take zubar da jini bane? Ameer mu taimaka mashi". Jin haka yasa Abbon ya juya idanun tsafin nasa tare da juyowa ya kallesu, nan take suka juya suka kama kansu, da alama shi ne nan ya kawar wa da mutanen arean gabaɗaya hankalinsu daga kansu, haka su Ameer dai suka juya salamun salamun suka bar wajen, tun da suka juya kuma basu sake waigo shi ba, da haka suka tafi. Santalelen matashi mai jini a jika ya rikiɗa ya koma, hannu ya kai a karo na uku zai ɗauketa, kamar daga sama ya ji daga bayansa an ce "Am doubting about what you said, this girl isn't your daughter, am a soldier, you look like a criminal in my eyes, so i have to be come back and check you very well, that's why am here!". Cikin nustuwa ya yi maganar, kamar Lion idan yana magana. A razane ya juyo, dan ya ga wanene, kun san ɗazun dama bai ɗago ya kalli Tga ɗin ba. Yana juyowa kuma ya jefa kwakwalwar Tga ɗin a cikin tunani, saboda a iya saninsa dai ɗazun babban mutun ya gani ba matashi ba, ya aka yi yanzu kuma ya dawo yaga mata shi? Shi ne abin da ya ɗan juyar mashi da tunani kenan. Shi kuwa Abbon, ganin Tga ɗin ba karamar razana shi ya yi ba, saboda abin da kuka sani ne, Tga tsayayyen namiji ne mai jini a jika, lafiyayye kuma horarre, ga kirar karfi, idan ka ganshi kamar TRIPLETS yake, basu da banbanci sai ɗan abin da ba'a rasa ba, so dole duk wani mutun idan ya gansu sai ya ji gabansa ya faɗi, musamman ma wannan Lion face ɗin nasu, da yake cike da kwarjini na wuce misali, ga kuma hasken fitillu a kan hanyar ko'ina, so suna iya ganin juna sosai. Ƙoƙarin juyarwa da Tga ɗin hankali Abbon ya yi, amma ina ya kasa, tsafinsa taki yin aiki a kansa, abin ya razana shi, ya kuma yi mugu mugun ɗaure mashi kai, meyasa tsafinsa ta ƙi kama Tga? Ya tambayi kansa. (Ni kuma nace saboda Josephine tana kula da su😒🤧 ba zata taɓa bari a cutar da su ba, sai dai idan an shanmaceta) Shi kuma Tga ganin cewa wanda ya gani ɗazun da wanda ya gani yanzu ba mutun ɗaya bane yasa ya nufe shi gadan gadan, yana taku cikin nuna jarumta tare da nuna cewa shi ɗin tsantsar lafiyayye ne. Yana zuwa bai yi wata wata ba ya damko wuyar Abbon tare da shakesa da karfin, calmly ya ce "Who are you? What do you want to do for her? Where's that man that i saw in the first place?". Ya kai karshen maganar tare da ɗaga Abbon da hannu ɗaya kuma da wuyarsa da ya damke, ya raba shi da kasa sannan ya yi wurgi da shi gefe guda. Dama kunsan halin uncle T da iya mugunta, baka yi mashi laifi bama ya iya zalunci bare kuma yana zarginka, ai sai abin da hali ya yi kawai, sai ya baka a jikinka kafin ya baka damar ka yi mashi bayani. Gadan gadan ya sake nufarsa, sai dai abin al'ajabi kafin ya kai in da yake yashe a kasar ya yi amfani da tsafinsa ya ɓace ɓat ya bar wajen. Dakatawa da nufar wajen Tga ɗin ya yi, da mamaki yake kallon wajen, da gaske ya ɓace, babu shi babu labarinsa, abin mamaki. Abin ya ɗan ɗaure mashi kai, sai dai ko kaɗan bai bashi tsoro ba, babu tsoro ko ɗigo a jinin familyn Roshan, haka suke tun ainahi, daga manyansu har kananansu basu da tsoro, bare kuma shi Tga da yake horon Lion, ai dama tsoro ma bataga wajen zama a wajensu ba. Juyawa ya yi ya nufi wajen da take kwance cikin jini, da farko kamar ba zai ɗauketa ba, amma da ya tuna yanda Abbon ya ɓace, sai ya sawa ransa cewa cutar da ita zasu yi, dan haka bari ya taimaka mata. A gabanta ya zo ya tsugunna, dan ya duba ta ina zai fara ɗaukar tata. Zubawa face nata idanu ya yi, sosai ya ga kamanninta da su Imran, kun san an ce jini ba wasa ba, a zahirin gaskiya bata wani kama da su Imran, amma da yake jini ya wuce wasa, akwai kaman jini a jikkunansu, kuma kowa da yanayin yanda yake kallon mutun, sai kaga mutun ya yi maka kama da wani, idan ka tambayi jama'a kuma sai su ce maka a'a babu kamar da kai kake gani, so kowa da yanayin yanda yake ganin mutun, shi dai Uncle T ta yi mashi mugu mugun kama da su Imran, sai dai kuma fa ba iya kamar kawai ya tsaya gani a face ɗin nata ba, tsintar kansa ya yi da jin sha'awar kallon face ɗin nata duk da baya son bakaken fata kuma bashi da wata ra'ayi a kan mace, amma ba shakka face ɗin Aafia ta tafi da tunaninsa a kallon farko. Ya ɗan ɗauki lokaci yana kallonta kafin nan ya tsinci kansa da kai hannu ya taɓa kumatunta. Wani irin sanyi kamar daskararren ƙanƙara da ya ji a tattare da face ɗin nata ne yasa ya ɗauke hannunsa da wuri tare da miƙewa ya saɓeta da hannu ɗaya a saman kafaɗarsa, alama ta nuna babu jini a jikinta, baiwar Allah dama ba isshasshen lafiya yake gareta ba. Anya basu Abbon bane suka zuƙe mata jinin⁉️ Gidan baya na motar ya buɗe tare da shumfuɗeta a saman lallausan kujerar motar, sannan ya koma mazaunin driver da sauri, saboda tana zubar da jini kuma alama ta nuna babu jini a jikinta sosai. Da gudun gaske ya figi motar ya bar wajen, dama fitowa ya yi zai je shopping, saboda akwai abubun amfaninsa da suka kare, dama shi already kun sani kamar Areef yake, akwai shi da yawace yawace idan ya zo waje, kun tuna farkon zuwansa Naija wani lokaci ma baya kwana a gida? Kun tuna lokacin? Yawonsa yake tafiya dan ya ga gari, hakan tasa ya san wajaje da dama a cikin garin Kaduna. Kai tsaye gida ya koma da ita. A haukace yake taka motar, dan su isa da wuri. Wani irin horn mai sauti ya fara dakarawa gateman tun bai kariso bakin gate ɗin ba. A hanzarce suka wangale mashi gate ɗin. A guje ya danna hancin motar ciki, yana kashe motar a parking space ya fito tare da buɗe gidan bayan, babu ɓata lokaci ya saɓeta a kafadarsa zuwa cikin gidan. Kai tsaye bed nasa ya wuce da ita, sai zubar da jini kanta yake yi, a iya kai ne kawai ta samu buguwa, kuma fashewar ba dayawa bane, amma da yake shi jini kofa kaɗan idan aka yi mashi ya samu hanya, to zuba kawai zai yi ta yi, buguwar da kan nata ya yi ne kuma yasa ta sumewa. Katafaren bed nasa na'a shunfuɗe da white bed sheet, a haka ya kwantar da ita a kai da jinin nata, bai wani damu ba. (Abin mamaki, Uncle T da ya tsani bakar fata yau shi ne da taimakon bakar fata? Kuma har ya ɗaga hankalinsa haka?🤔 Abin da mamaki) Fitowa ya yi tare da haurawa saman benen. A bakin kofar bedroom na Lion ya tsaya tare da yi mashi excuse, dan Lion ɗin ya shata masu layi da shiga ɗakinsa a yanzu, ya ce kada su rinƙa shiga mashi kai tsaye, dan matarsa tana kwance a ciki, baya da bukatar kowa ya kallah mashi ita a kwance, idan ta fito da kafafunta, wannan suna iya kallon face nata, amma tana a kwance a cikin bedroom nasa kam bai lamunta wani ya ganta ba, hakan yasa suke yi mashi excuse su kuma tsaya sai ya fito. Ya ɗauki tsawon a kallah minti 10 a tsaye a wajen lafin Lion ɗin ya fito, jikinsa na sanye da kayan barcin masu matukar kyau, launin milk color, sai tashin kamshi yake yi kamar anyi ɓarin perfume a jikin nasa. Ko da ya fito ma bai yi magana ba, sannan kuma tun da ya ɗaura idanuwansa a kan uncle T ɗin nasu, kallo ɗaya ya yi mashi yasan ba lafiya ba, ga jini a hannunsa da jikinsa, sai dai bai tambaye shi meyake faruwa ba, ya tsaya shiru dai ya zuba mashi idanu. "Lion I need A box and the rest". Ya faɗa cikin nutsuwa. Shiru Lion ɗin ya yi mashi na tsawon mintoci kafin calmly ya ce "What is going on?". Ba tare da ɓata lokaci ba ya bashi labarin abin da ya faru sama sama, daga karshe ya gaya mashi cewa yarinyar da ya buge ɗin tana dakinsa a sume, shi ne yake son dubata. Jinjina mashi kai Lion ɗin ya yi, saboda yasan uncle T ɗin ma ba baya ba wajen sani da kuma karantar aikin likita daga wajen daddynsu na karya, ko ace photocopy, an cucesu aka sanya mashi komai na ainahin Dr William, harta ilimi da komai, da yake abu ne na tsafi, sai dai ko ba komai sun karu da shi, ga shi yanzu suna iya treating na kawunansu idan basu da lafiya, sam basu zuwa hospital sai idan abu ya zama mai matuƙar zafin gaske, amma ciwo irin na yau da kullum tsab suke duba kawunansu. Ciki ɗakin Lion ɗin ya koma, jim kaɗan ya fito mashi da duk abubuwan da yake buƙata ɗin, dan su a wajensu dan Tga ya kawo mace wanda ya buge da mota, dan zai dubata ba su ɗauki hakan a bakin komai ba. A hanzarce ya karɓa tare da juyawa ya nufi bedroom ɗin nasa. Shi kuma Lion ya koma ciki, har yanzu dai Rimsha shiru shiru bata farfaɗo ba, kusa da ita ya kwanta yana ta kallon face nata, ta kara wani irin azababben kyau, saboda karin ruwa da ake ta yi mata, tana kwance a sume, babu ci babu sha, drip kawai ake ta loda mata, dan ya taimakawa jikinta kada ta nakasa, hakance tasa ta kara kyau, kun san dama fa shi drip yana sanya mutun ya yi ƙiba ya kuma kara haske da kyau, duk wanda aka yi wa karin ruwa a hospital, zaku gan shi ya kara ƙiba, sai dai idan dama ba mai jikin ƙibar bane ba, amma koma yaya zai ɗan murmure. Sosai ya zuba mata idanu babu ko kyaftawa, idan ya kalleta sosai, sai ya kai kyawawan lips nasa saman nata ya sumbata, sannan ya cigaba da kallonta kamar wani ya ce zai kwace mashi ita, ko ance za'a rabasu. Shi kuwa uncle T, yana shiga bedroom ɗin nasa ya fara dubata cikin hanzari. Da yake bata ji wani ciwo sosai ba, a iya kai ne kawai, cikin ƙanƙanin lokaci ya kammala komai tare da yi mata alkuran barci, sannan ya nufi toilet dan ya yi wanka, sai tunanin face nata yake yi, ta tsaya mashi a ransa, sai dai bai ɗauki hakan a matsayin wani abin ba, ya mayar kawai taimako ne. Bayan ya yi wanka ya fito, shiryawa ya yi cikin kayan barcinsa masu kyau da tsada, kusan irin na jikin Lion. Saman bed ɗin nasa ya haye abinsa, tana gefe guda, shi ma ya kwanta a gefe guda tare da ɗan rage gudun A.c, dan kada sanyi ya daketa. A hankali ya lumshe idanuwansa, ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi. A ɓangaren su Abbi kuwa, time da suka dawo gida, ba ƙaramar tashin hankali suka shi ga ba ganin Aafia bata a gidan, kasancewar dare ne, sai basu kira su Abba sun tayar masu da hankali ba, suka fara nemanta a cikin unguwar, ita kuwa Hjy Hadiza tana can wani kauye wajen wani malami, a can zata kwana, Aunty baiwar Allah ta shiga damuwa na wuce misali. Sun sha yawo kamar ba gobe, amma babu Aafia babu dalilinta, haka suka dawo gida har wuraren 12 na dare, ga gajiyar hanyar Katsina, ga wahalar yawo a cikin unguwa, mai gadi dai ya shaida masu Aafia da kafarta ta fita gidan da gudu, ga shi babu waya a hannunta bare su kirata, haka suka kwanta jugum jugum, a wannan dare dai barci ya gagaresu, dan suna cikin tsaka mai wuya, Allah Allah suke yi kawai gari ya waye su shiga nemanta babu kakkautawa, baiwar Allah ga shi ba lafiya yake gareta ba. Ita kuma Hanan sun barta a Katsina, dan next week za'a ɗaura auren nasu, A'A ya ce baya son ɓata lokaci, ayi komai da wuri a wuce wajen, to shi ne yasa suka barota a can zata yi kwana biyu, dan ta bi ƴan uwa su yi ban kwana, daga nan sai ta dawo gidan Abbin, dan a nan za'ayi komai na bikin, Abbin ya ce ba zasu sake zuwa wajen babanta ba, gara ayi komai a gidansa cikin mutunci tun da baban ya amince. Washegari tafiya ce ta kama Lion cikin gaggawa, bashi da zaɓin da ya wuce ya koma U.s, sam baya jin kamar zai iya tafiya ya bar Rimsha ba tare da ta farfaɗo a gabansa ba, amma dole ce tasa sai ya tafi ɗin, saboda primary election da sauran abubuwa, ba zai yi wu ya tafi da ita ba, dole zai barta a nan. Gwaggo ce ta yi ta kara mashi kwarin gwiwa a kan ya je kawai zata kula da Rimshar sosai, kada ya damu. Shiru ya yi bai amsa mata ba, dan shi gani yake yi ma ita fa gwaggo sam bata san me yake ji ba, ba zata gane halin da yake a ciki bane, da zata shiga cikin zuciyarsa ta ga irin azababben son da yake yi wa Rimsha, da sam ba zata taɓa yin gigin ce mashi ya yi hakuri ya tafi ya barta ba. Karfe 7 na safe ya kamata jirginsa ya ɗaga, amma sai ya ɗaga tafiyar zuwa da yamma, duk saboda Rimsha, duk da baya jin cewa zata iya farfaɗowa a cikin wannan satin ma gabaɗaya ba yau ba, amma ya jinkirta tafiyar tasa zuwa yamma, dan ya kara kula da ita sosai kafin ya tafi. A ɓangaren Jehan kuwa, duk ta yi laushi, ta rame sosai, amma har yanzu taki yarda ta kira Areef ɗin a waya ma bare ta bashi hakurin. Sam Areef baya son wannan rama da take yi, abin yana kona mashi rai, sai dai bashi da zaɓin da ya wuce ya bi maganar mum, a koda yaushe yake son ganinta, zai ganta, amma ita ba zata gan shi ba, saboda bata san cewa yana da hanyar ganinta ɗin ba, sai dai fa shi ganinta bai wadatar da shi ba, ba iya ganinta da ido yake da buƙata ba, yana bukatar jin voice nata, duk da kullum dama cikin dirama suke, ba wasu kamai da take gaya mashi, amma yana son diramar, yana son jin muryarta tana yi mashi diramar, ba wai ya ji muryarta tana magana da su gwaggo ba, in takaice maku shi fa komai Jehan ta yi burgesa take yi, pure love na kin karawa yake yi mata, tsayawa zayyana irin son da yake yi mata ma ɓata baki ne, dan bakin ya yi kaɗan wajen iya zayyana shi. A takaice sai misalin karfe 5 jirgin Lion ya ɗaga zuwa U.s, zuciyarsa sam babu daɗi na rabuwa da Meesharsa, babban abin da ya fi ɓata mashi rai ma shi ne, yanda tafiyar ya kama shi ba tare da Meeshar tasa ta farfaɗo a gaban idanunsa ba, shi ne ya ɓata mashi rai a game da tafiyar kawai. A ɓangaren Tga kuwa, washegari da safe da ya tashi, wanka ya fara yi tare da shiryawa cikin tsadaddun kayansa, ya fito ya nufi motarsa ta jiya, bai bi ta kan Aafia ba, duk da tana kwance a saman bed nasa, kuma ya ganta sarai, sai dai wani abin ya sha gabansa, akwai in da zai je. Da ya je shiga motar ne ya ga kujerar duk jini, hakan tasa ya ɗauki motar Aseef ya fice daga gidan, ya barta sume a saman bed nasa, ga shi babu wanda yasan tana ɗakin bare a sanar da su Abbi dake ta faman yawon nemanta a gari, duk sun karaɗe gari da nemanta, police station ne, gidajen Radios duk sun baza bayananta ana cikiya, shi kuma ya kai ta ɗaki ya kwantar ya kama kansa abinsa, dama kun san daren jiya ya fita zai ke shopping ne, dan gaskiya yana da bukatar abubuwa dayawa, har da mayukan goge baki, shi ne yasa ya fita da wuri dan ya je ya yi shopping nasa, saboda abubuwa ne na amfaninsa mafi muhimmanci zai saya. Su gwaggo sam basu san da Aafiar a gidan ba, ga shi su ba shiga ɗakinsa suke yi ba, bare ace idan sun shiga za su ganta har su ganeta su kira su Abbi, to bama su san tana gidan ba. Shi kuma Lion da yasan cewa Tga ɗin ya buge wata yarinya da mota, ai kun san halinsa, baya shiga abin da bata shafe shi ba, dan haka babu ruwansa da zuwa ya duba waye Tga ya buge, hakan ma sam ba zai yiwu ba. Duk hankulan family ya tashi ana neman Aafia, izuwa yanzu su gwaggo duk sun sami labarin halin da ake ciki, sai kiraye kirayen waya suke yi wa ƴan uwa, dan su ji ko dai an samu wani labari, amma shiru. Sai dai sunki gayawa Dr Salman da Brr Naurat halin da ake ciki, dan kada su shiga tashin hankali sosai, dama har yanzu basu gama warkewa daga azabar da Queen ta ɗanɗana masu ba, sai jinyar Dr Salman ake yi, ya sha allurai da karin ruwa tare da magunguna, shi ne yasa sam suka ki sanar da su halin da ake ciki. ❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉✷❉ Lion ya isa Washington lafiya lou masha Allah, gabaɗaya airport ɗin cike yake da jami'ai, ƴan jaridu da kuma ƴan siyasa, dan kowa so yake yi ya yi magana da Lion ɗin, a ƙage suke, dama idan baku manta ba, a yanzu almost tsawon 2 month kenan jama'a suna neman ganinsa ruwa a jallo ko da da ido ne kawai, ƴan jaridu suna haukar nemansa, dan su yi mashi tambayoyi, amma babu wanda ya iya samun damar ganinsa, sai yau da ya shigo kasar, da yake ba tafiyar sirri ya yi ba, shi ne yasa suka sami masaniya a kan dawowarsa tasa. Shi kuwa ko a jikinsa, dan bai ga uban da ya isa ya sanya shi ya buɗe bakinsa ya yi magana bai yi niya ba, haka ya fito daga cikin jirgin yana takunsa na nuna isa da izza, duk ƴan jaridun babu wanda ya iya tunkararsa, saboda basu ga fuska ba, dama already fuskarsa a ɗaure tamau take kun sani, yau kuma ya kara tamketa babu alamar wasa a tattare da shi, hakan yasa kowa ya ji matukar tsoro da shakkar tunkararsa da wata magana. Duk sun tsaya cirko cirko kamar masu jiran sadaka. Suna ji suna gani har ya je ya shiga motar Areef dake jiransa su wuce. Ga Generals nasu na sojoji duk nemansa suke yi, yau ga shi sun gan shi ido da ido amma sun kasa iya tunkararsa. Suna ji suna gani ya bar airport ɗin suka wuce gida, sai tsokanarsa Areef yake yi a kan wai ya je Nigeriar ya ci angwancinsa, ya tura yarinya doguwar suma ya dawo ya barta a wahale ko farfaɗowa bata yi ba. Ko sannu bai ce mashi ba, ya bar shi ne sai sun je gida ya shake shi da kyau, dan Areef yana takura mashi ba kaɗan ba, dole ya yi mashi koda shaƙa ɗaya ne wata kila zai bar shi ya sarara, tun da ya yi dis virgin ɗin Rimsha ya saka shi a gaba da tsokana, idan suka yi waya maganar kenan, dama da abin a ransa ya dawo, sai ya wahalar da Areef ɗin nan sosai wannan karon kam. (Ni ma dai na ce ya shake shi da kyau, Allah Areef akwai tsonana, ya saka mana Lion a gaba😂) "Lion kaki ka bani labarin ya kaji ko? Serious dole na ɗauko my baby ni ma, dan naji me ka ji, saboda naga ka yi wani kyau ne". Yana magana yana kara gudun A.cn motar, cikin zolaya kuma ya yi maganar. Banza da shi dai Lion ɗin ya yi bai tanka ba. Har suka isa gida sai tsokanarsa yake yi bai kula shi ba. Yana yin parking na motar a parking space na gidan, ya fito ya nufi ciki abinsa, dan aikin da ya kawosa ba karamar aiki bace ba, so baya bukatar ɓata lokaci koda second ɗaya ne. Yana shiga palon sama suka yi four eyes da daddyn Rimsha dake zaune a saman sofa mai zaman mutun uku yana latsa waya. Already kunsan basu shiri kamar wuta da audiga, amma kuma ya iya zubawa ƴarsa soyayya ya ce kuma baya son ubanta. (Wlh Lion ɗan duniya ne, baya shiri da uba, amma kuma yana son ƴa, anya hakan zata yi wu kuwa?🤔) ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 9/5/2024 Kallo ɗaya ya yi wa daddyn ya kawar da kansa tare da wucewa ya nufi bedroom nasa. Shi ma daddyn bin shi da kallo kawai ya yi, Lion halisna sai shi, ba dai abin da ya canza a tattare da shi, Rimsha kawai ya canzawa, bayan ita kowa a yanda ya san shi yake ganinsa. Yana shiga bedroom nasa wanka ya yi, kayan shan iska ya sanya a jikinsa tare da hayewa saman bed nasa ya kwanta, dan a tsananin gajiye yake sosai, ga uban tunanin Meesharsa da ya sako shi a gaba. Shi kuwa Areef juya kan motar ya yi izuwa gidan Sheikh Sultan, dan dama ya ce yau zai je ya ɗauki Aseef ɗin, da izinin Allah ya sami lafiya sosai da sosai. A ɓangaren Tga kuma, shopping nasa ya je ya yi abinsa, ba shi ya dawo gidan ba sai misalin karfe 11 na rana. Yana shigowa ya nufi bedroom nasa, har lokacin still Aafia bata motsa ba, shi sam ya mance ma da tana a cikin bedroom ɗin. Da ya ganta sai da ya ɗan yi mamakin mantawa da ita da ya yi, bai bi ta kanta ba ya wuce izuwa toilet, dan ya shirya abubuwan da ya sawo a mazauninsu. Daya kammala wanka ya sake yi tare da shiryawa cikin wandon jeans three cuter baka, da T-shirt mai ɗan shara shara. Fita ya yi daga bedroom ɗin ya nufi saman benen, ɗakin gwaggo ya nufa, a bakin kofa ya tsaya tare da yi mata excuse. Jim kaɗan ta fito. Cikin girmamawa ya gaishe da ita kafin ya faɗa mata abin da ya kawosa na ya buge wata yarinya da mota ne a daren jiya, kuma yaga yarinyar tana kama da su Imran, ta zo ta ganta ko ƴar uwarsu ce. Da yake tasan da batun ɓacewar Aafia ɗin, sai bata ɓata lokaci ba wajen ce mashi "Tabbas Aafia ce ma In Sha Allah, mu je bari na ganta". Wucewa gaba ya yi ya sauke kasa. A hanzarce ta bi bayansa, kai tsaye bedroom ɗin nasa suka nufa. Tana ɗaura idanu a kanta ta ce "Dama na ce ita ce, tun daren jiya muke nemanta, bari na kira su Deen ɗin a waya mun sameta, sai wahala suke ta sha, ashe gata a gida ma". Ta kai karshen maganar tare da kai hannunta a saman kumatun Aafia ɗin. "Meyasa me ta? Suma ta yi ne?". Ta tambaye shi. "Na yi mata alluran barci ne tun daren jiya ɗin, amma kuma yakamata ace alluran ya saketa izuwa yanzu ai". Kai kallonta a kan in da ya sanya mata bandeji da plaster bayan ya wanke wajen ta yi, kamar zata yi magana, sai kuma ta fasa tare da juyawa ta nufi waje. Bedroom nata ta koma ta ɗauko wayarta. Number Abbi ta kira, bugu ɗaya ya ɗauka, a hanzarce ta sanar da shi cewa ga Aafia nan a gida Tga ya bugeta da mota. Murna sosai suka yi da Allah yasa tana gidan, sai dai kuma sun shiga damuwa ta wani ɓangaren a kan bugeta da motar da aka yi, ba ɓata lokacin Abbin ya tambaya ta ji ciwo ne?. "E ta ji ciwo amma kaɗan ne, kuma a iya kai ne kawai". Gwaggon ta bashi amsa. "Okey tom bari na sanar da su Abba, gani nan zuwa gidan yanzu". Okey ta amsa mashi da shi, sannan suka yi sallama. Fitowa ta sake yi ta koma bedroom ɗin na Tga. Tana zuwa ta ce mashi ya kai mata Aafiar ɗakinta, iyayenta suna zuwa yanzu, zata cigaba da jinyarta a can, sun gode da taimakon da ya yi mata. Gwaggo ta tara majinyata kam, ga Rimsha, ga Jehan, yanzu kuma Aafia, ɗakinta ya koma kamar clinic. Ba ɓata lokaci ya ɗauketa zuwa ɗakin gwaggon kamar yanda ta buƙata, sannan ya dawo ya cire bed sheet dake shunfuɗe a saman bed ɗin nasa, ya canza wata. Ita kuma gwaggo kula da Aafiar ta cigaba da yi har Abbi da Abba suka ƙariso cikin gidan. Sai a lokacin ne Brr Naurat ta sami labarin abin da ya faru, jajanta masu ta yi, sannan ta ce to a bar Aafia ɗin a wajen gwaggon ta cigaba da kula da ita. Haka kuwa aka yi, duk suka amince, sannan suka koma gidajensu, kwananta biyu a wannan suma da ta yi Allah yasa ta farfaɗo tare da taimakon gwaggon, sun kuma yi sa'a ta farfaɗo lafiya lou ba tare da buguwar da ta yi a kai ya taɓa mata ƙwaƙwalwa ba, sun yi sa'a sosai. Sai kula da su gwaggon take yi, bata da wata nutsuwa sosai a tattare da ita, Rimsha kam har yanzu tana a bedroom na mijinta. After some days. Washington. Sun yi primary election lafiya ba tare da wata tangarɗa ba, Lion shi ne na farkon ma, shi ne a sahun gaba na cin primary election ɗin, dan jama'a suna yinsa ba karya, kowa yana son mutumin kirki mai adalci ai dama, abin ya kara razana mutane sosai, ya tada tarzoma a majalisan dattawa, tashin hankalin da His excellence ya shiga ma baki ba zai iya faɗarta ba, shi kuwa Lion tamkar bai san meyake faruwa bama, yana gida tare da ƴan uwansa hankalinsu a kwance, sai tunanin Meesharsa da yake yi, yana tsananin kewarta sosai, ji yake yi ba zai iya zama ba tare da ita a kusa da shi ba, ga wani azababben sha'awarta da take takura mashi kwana biyun nan, komai yake yi ita ce a cikin tunaninsa, zazzaƙar zumarta ya tsaya mashi a rai over. Da yake Areef ya san komai, sai ya yi ta tsokanarsa. Yau ma dai yana zaune a saman luntsumemiyar sofarsa mai zaman mutun uku dake wajen balcony, sanye yake da pajama launin milk color mai matuƙar kyau da tsada, tsadaddiyar sabuwar laptop nasa ne a gabansa, aiki yake yi a azahiri, amma a baɗini ba aikin yake yi ba, ya yi shiru yana tunaninta ne kawai, hankalinsa sam baya a kan laptop ɗin, da kallo ɗaya zaka yi mashi kasan yana cikin matsananciyar azababbiyar sha'awa, waɗan nan fararen idanuwan nasa sun sauya launi izuwa jajir, kwayar idanuwansa har wani kara blue suka yi, sai kyalli idanun nasa suke yi, alama ce dake nuna a hannu yake, ga shi kuma yau tsawon kwana 29 kenan Rimshar bata farka bama bare kuma su san tana lafiya ko dai kwakwalwarta ta taɓu, tun abin baya damun gwaggo sosai har ya zo ya fara damunta, har ƴar rama ta yi, ita kanta mummyn Rimshar ta rame sosai, bata fito ta nuna damuwarta a fili ba, amma kullum ta shiga cikin ɗaki sai ta yi wa ƴar tata kuka, abin ya tsaya mata a rai, ta tausayawa ƴaƴan nan nata kamar me, babban damuwarta ɗaya shi ne, kada ace Rimsha mutuwa ta yi, ƴaƴa biyu kawai Allah ya bar mata, ya karɓi sauran dukka, tana son ƴaƴan nan kamar ta yi masu numfashi, musamman Rimsha da suka fi shakuwa da ita, idan ta mutu ya zata yi? Ina zata sanya ranta? Ga shi bata zuwa duba Rimshar sosai, a rana sau ɗaya take zuwa, saboda Rimshar tana bedroom na Lion ɗin ne, ita mummyn bata son shiga bedroom na sirikin nata, kuma bugu da kari bata son ganin ƴar tata cikin halin doguwar sumar ne, hankalinta yana tashi matuƙa, ga shi daddy baya nan bare ya rinƙa kwantar mata da hankali, abin ya yi mata yawa sosai, shiyasa har rama sai da ta yi, da Allah yasa ma ciwo bai kayar da ita ba, haka ita ma gwaggon, tsoronta ɗaya kada ace Rimsha mutuwa zata yi, ba zata iya jurar hakan ba, abin ya ɗaga mata hankali da har ta sa a ranta idan su Areef suka dawo a gaskiya sai ta ja masu kunne sosai a kan su Jehan, su bi komai a sannu, su Jehan yarana, dan Allah su rufa mata asiri su taimaketa su taimaki mum su yi masu komai a sannu. (Gwaggo ta ji papper😂 dole baiwar Allah ta ce su Areef subi komai a sannu😂 waye ya ce mata Borno a gabas take?) Baki ɗauke da sallama Areef ya shigo cikin balcony ɗin, jikinsa na sanye da three cuter sky blue, daga ta sama kuma farar singlet ce a jikin nasa, sai zuba uban kamshi yake yi, hannunsa na ruke da wani kyakkyawan cup mai ɗauke da green tea, sai tiririn hayaki yake yi, ya saki gashi har baya, kyawawan fararen kafafunsa na sanye cikin bedroom slippers masu matuƙar laushi kamar audiga, ga kyau farare tas da su, kusan iri ɗaya ne da na kafar Lion ɗin, sai dai na Lion up white ce. Kusa da shi ya zo ya zauna yana faɗin "Our Lion good evening". Yadda ya yi maganar cike da nuna tsantsar so da kauna. Sam Lion ɗin bai kula shi ba, dan shi kaɗai yasan meyake ji. Areef ɗin zai sake yin magana sai ga Aseef ya shigo hannunsa rike da waya ya manna a kunne, ɗayar hannunsa na ruke da cup irin na hannun Areef, jikinsa na sanye da short zuwa iya santala santalan cinyoyinsa, daga ta sama babu riga, dukkansu sun kara wani irin kyau na musamman, bare ma shi Aseef da dama ya fisu samun hutu, su suna ta busy game da Election, shi kuwa kome za'ayi yana kwance a gida manne da waya, baya leƙa ko palon kasa, hakan tasa ya fisu hutu, jikinsa ya fi nasu fito da wata sihirtatcen kyau na daban. (Yo dama Aseef ai sai dai ya kwanta ya mannewa wayar😂 ina zai iya yin minti 30 bai ji muryar Heartbeat ba? Ai ko sun saka shi aiki ma ba zai yi ba😂 jibge masu kayansu zai yi, dan shi dai iya wuya Heartbeat kawai😂) A ɗayar gefen Lion ɗin ya zo ya zauna, ya zama sun saka Lion ɗin a tsakiya. "Heartbeat Allah ni ba zan yarda ba, kawai video call nake so". Cewar Aseef. Ya faɗa yana ajiye cup ɗin hannun nasa a saman table dake gaban Lion wanda ya ɗaura laptop nasa. Harararsa Areef ya yi yana faɗin "Allah ya nuna mani ranar da Aseef da Akila zasu canza hali". (Ni kuwa na ce nima ina jiran wannan rana,😂 su sam basu da wani aikin yi sai kashe juna da love da shagwaɓa, ko gajiya ma basu yi?🤔😂) Da yake ya saba da abin ta bi jininsa, ko da aka yi mashi magani ƙwaƙwalwarsa ta warke garau shagwaɓar bata rabu da shi ba, kun san sabo, ya rigada ya saba, kuma haɗuwa da Akila yasa shagwaɓar tasa ta yi yawa, saboda shagwaɓarta da take zuba mashi yana biye mata yasa shi ma nasa ta karu sosai, da ace bata da shagwaɓa, da nasa ba zata kai haka ba, kuma da izuwa yanzu ya dai'na yinta ma, amma da yake ita shugaba ce, sai ta kara shagwaɓa shi kawai abinta. Shi dai Lion ko sannu bai ce masu ba. Akilar ce ta cikin wayar ta ce "Heartbeat yanaji kamar maganar Yah Areef?". "Shi ne mana". Ya bata amsa. "Yanzu a gabansa muke dukka wannan hiran dama?". Ta faɗa tana zaro idanu, tana daga kwance a saman bed na bedroom nasu. "No yanzu na shigo wajensu, to idan ma a gabansu ne sai me? Ina ruwansu da mu?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "A'a ni ina jin kunyarsu". "Ke gara ma ki dai'na wannan shirmen, su basu san wannan ba". Ya faɗa yana kwanto da kansa a jikin Lion. Hannu Lion ɗin ya kai yana shaga face ɗin Aseef ɗin cike da tsantsar so da kauna, waɗan nan bayin Allah baki ya yi kaɗan wajen bayyana yadda suka kaunar junansu. Cigaba da zuba hirarsa Aseef ɗin ya yi, ba ko kunya yake zuba kalaman da ya ga dama, idan ta ce mashi ita yana bata kunya, sai ya ce mata yanzu dai shi mijinta ne, idan a da time da take gida tana taka mashi burki a kan wasu kalai, saboda basu yi aure ba, to yanzu dai hakura zata yi ta barshi ya zuba kalamansa son ransa, dan yanzu mallakinsa ce ita ɗin, ko hoto ba kaya ya ce ta yi mashi dole ta yi ta tura mashi, dan haka shi ta kyale shi ya ji da abin da ma yake ji na kewarta. Areef kam dariya kamar ya mutu, saboda yadda Aseef da Lion ɗin dukka suka zama wasu jugum jugum kamar wasu marayu, duk saboda kewa da kuma sha'awar matansu, yana son ya tsokanesu, amma yana tsoro, dan a yadda suke ɗin nan, idan ya taɓosu lallasa mashi jiki zasu yi son ransu, haɗuwa zasu yi su bashi a jikinsa, so is better for him da ya ja bakinsa ya rufawa kansa asiri ya yi shiru. Sai dai shi ma fa yana jin azababben kewar babyn tasa, abin da yasa shi ta shi tafi yi mashi sauki shi ne, na farko kun dai san bai saba kwana da Jehan ɗaki ɗaya ba, na biyu bai saba wasanni da ita ba, kullum cikin dirama suke, na uku dama ko ya kirata a waya ba wasu kalamai na soyayya take gaya mashi ba, so bai wani saba ba, shiyasa abin bai taɓa shi sosai kamar su ba. Shi kuma Aseef ba sai na faɗa ba, kun san ya fi kowa tsotsewa Heartbeat baki da tula tulanta, ya fi su dukkansu murzar matar tasa son ransa, kullum suna manne da juna, ɗaki ɗaya suke kwana, shi ne yasa abin ya taɓa shi sosai, a daddafe yake iya barci, dan ma dai sai sun yi hira da ita a waya har zuwa asuba ne, shi ne yake samun nutsuwa kaɗan. Shi kuma oga Lion, a yanzu ya kai point ɗin da dede da rana ɗaya ba zai iya raba makwanci da ita ba, yin hakan zai azabar da shi matuƙa, ya riga ya leƙa duniyar sama jannati, ya ɗanɗani zuma mai azababben daɗi, so ba zai iya jurar rashinta ba, shi ne yasa shi ma abin ya taɓa shi sosai, bugu da kari kuma ga shi ba waya suke yi da ita ba, bare ta ɗan ɗebe mashi kewa, tana sume bata san in da kanta yake ba, shi kuma da yake cikin hayyacinsa ɗin, da shi da sumammen babu wani banbanci sosai, saboda baya iya yin komai face tunaninta, ba shi da aikin da ya wuce kallon hotunanta da videos nata da ta rinƙa ɗauka a wayarsa time da ya tafi Daular Mutuwa, kun san dama ya tafi ya bar wayar a gida, so kafin ta fara rashin lafiya ta yi ta hotuna da videos da wayar, a yanzu sune suke rage mashi kewarta, kun fa san su Turawa na faɗa na kara faɗa, idan zasu yi soyayya to da iya gaskiyarsu suke yinta, gabaɗaya zuciyar suke bawa mace, so dole kuga Lion a irin wannan hali, dan ya riga da ya bata gabaɗaya zuciyarsa, sai kuma abin da hali ya yi. (Under 15 years girl da ruke zuciyar Lion, abin da ban mamaki gaskiya, Rimsha ta ciri tutan da babu wata macen da ta taɓa ciran irin sa gaskiya.) Haka Aseef ya kammala rakinsa son ransa kafin su yi sallama da Akilar tasa. Ɗaura wayar a saman table ɗin gaban nasu ya yi tare da kara narkewa a jikin Lion ɗin yana wani tura baki, shi dai gaskiyar magana ya gaji, a barshi ya koma Naija. Areef dai sai guntse dariyar mugunta yake yi, yana tsoron yin dariyar ne, kada ya ja su sauke mashi haushin a kansa. A can gida Nigeria kuwa, da misalin karfe 6 na mangariba, gwaggo na zaune a bakin bed ɗin Lion ɗin tana ƙoƙarin cirewa Rimshar drip ɗin dake makale a hannun nata, dan ya kare, tana son saka mata wani ne. A hankali Rimshar ta fara motsa yatsun kafafunta, babu kowa a cikin ɗakin, Jehan tana ɗakin gwaggon ita da Aafia suna kwance, ita Aafia tana barci, ta kuma samu lafiya masha Allah, ita kuma Jehan tana ruwan hawaye, dan abin ya kai mata kololuwar makura a yanzu. Kafin gwaggon ta yi wani yunkuri Rimshar ta fara ƙoƙarin buɗe idanunta da suka yi mata wani irin nauyi, ji ta yi tamkar an sanya masu super glue an datse mata su, da kyar ta iya ɗan warosu kaɗan, sai kuma ta yi maza ta rufesu, saboda hasken da ya haske mata idanun nata. Sunanta gwaggon ta fara ambata cike da ƙaguwa tare da zumuɗi. "Rimsha! Rimsha". Ga mamakinta sai ta ji ta amsa mata da na'am, sai dai ta amsa ne kasa kasa, muryar tata baya fita, kuma yana a dashe kamar mai yin mura. Wani irin azababben daɗi gwaggon ta ji tamkar ta zunduma ihun murna, tun da Rimshar ta iya gane sunanta har ta amsa da na'am da aka kirata, to ba shakka tana a cikin hayyacinta, da alama kwakwalwar tata da suke zaton ya taɓu, to bai taɓu ba, Allah ya tsare, kuma ta sami tsananin kulawa ce ta musamman daga ƙwararriyar likitan, wato gwaggon, gaskiya babu zancen wasa gwaggon ta kula da ita fiye da tunanin mai tunani, ta yi treated nata fiye da tunaninku, ba dare ba rana tana a kanta kullum, shiyasa abin ma ya zo masu da sauki, Allah ya taimakesu bata sami taɓin kwakwalwa ko kuma wani ciwo daga ta ciki ba, amma batun azabtu ba'a maganarsa shi kam, baki ya yi kaɗan ya faɗi kalar wanda ta sha. "Rimsha kina jina?". Gwaggon ta faɗa cike da zumuɗi da kuma ƙaguwa. Can kasan maƙoshinta ta yi magana a kasale "E gwaggo ina jinki". Rimsha akwai kwakwalwa, bata buɗe ido ta ga wacece ke magana ba, duk da yanzu ta tashi daga ciwo na tsawon kwanaki 29 a sume, amma ta ɗauki muryar gwaggon, bai shige mata ba voice ɗin. Matsowa gwaggon ta yi tare da ɗago kanta ta ɗaura a saman laps ɗinta tana faɗin "Buɗe idanunki ki kalleni ko?". Da kyar take iya motsa laɓɓanta baiwar Allah, saboda sun yi mata nauyi sosai, kasa kasa ta yi magana "Gwaggo hasken ɗakin ne yana kashe mani idanuna". Allah sarki, yanda ta yi maganar gwanin ban tausayi. "Ki buɗe su a hankali hankali ba zai kashe maki ba, dan kin jima baki buɗe idanun bane shiyasa, amma yanzu dai gwada buɗesu a hankali ko?". Okey kawai ta ce tare da fata ɗan buɗe idanun nata, tana yi tana sake mayar da su ta rufe, a haka har ta buɗesu gabaɗaya. Idanun nata sun yi jajir kamar jini, saboda sun jima a datse. Hamdala ga Allah gwaggon ta yi, ita kuma Rimshar fara bin ɗakin da kallo ta yi, shiru ta yi tana tunanin abin da ya faru da ita, a iya saninta dai tasan cewa ita da Noorish nata ne kawai a cikin ɗakin nan, kuma soyayya suke zubawa juna tare da nuna tsantsar kewar juna, abu ɗaya zata iya tunawa kuma ta rike a ranta shi ne, tabbas lokacin da ya shigeta ta ji wani azababben zafi, bayan wannan zafin ita bata sake sanin komai ba, duk bidirin da Lion ya yi bata sani ba, dan tana sume baiwar Allah. "Gwaggo ina Yah Saif ɗin?". Ta faɗa murya can kasa kasa. Da mamaki gwaggon take kallonta, saboda bata taɓa tunanin cewa Rimshar zata tashi kuma ta nemi Lion ba, ta yi tunanin sai an kai ruwa rana da ita kafin ma ta sake yarda su haɗa ido da shi, sai kuma ta ga akasin haka. Abin da gwaggon bata sani ba shi ne, ita fa Rimsha bata san aika aikan da Lion ya yi mata ba, idan da ta sani ne wata kila ta guje shi, amma sam ita bayan buɗe hanyar shigarta da ya yi, bata sake sanin komai ba, kuma in da Allah ya kara taimakonta shi ne, kafin ta farfaɗo daga doguwar sumar, ta sami lafiya, dan har ɗinkin da aka yi mata ma gwaggon ta kwance shi tun last two weeks ago, so babu wani sauran ciwo a jikinta da zai iya sanyawa ta gane ga abin da ya faru, sai dai idan ta zo miƙewa ne zata ji jikinta ya yi mata nauyi, kuma kunga ita yarinya ce sosai, ba zata iya fahimtar halin da ake a ciki cikin sauki haka ba, misali koda ta je toilet yin wani uzuri nata, idan ta ji gabanta yana zafi, bazata taɓa tunani kwatankwacin abin da ya faru kenan ba, zata dai ce ko saboda shigarta da Lion ɗin ya yi ne yasa hakan, shekarunta sun yi ƙanƙanta na sanin wannan karatu a yanzu, ko zama aka yi aka bata labarin abin da ya faru da halin da ta shiga caf, kananun shakarunta ba zai kai ta hango wahalar da ta sha ɗin ta kai ko kwatan hakan ba. Shiru gwaggon ta yi, tana tsoron ta gaya mata Lion ya koma, saboda bazata ji daɗi ba, ya dawo ne fa suna tsaka da rungumar juna na kewar juna da suka yi, ko fuskarsa mai kyau bata samu ta gani ba ta shiga doguwar suma, sannan yanzu daga farfaɗowarta a sake ce mata ya koma, ai zasu sanyata ta sake suma, tana tsananin son Lion sosai baiwar Allah, shi ma yana tsananin kaunarta over. Dan haka sai gwaggon ta kasa iya samun dakiya da kwarin zuciyar iya gaya mata ya koma, kawai sai ta ce mata ya fita yana zuwa. "Amma gwaggo ki faɗa mani me Noorish ya yi mani? Ina jin jikina yana ɗan yi mani zafi, kuma ni dai nasan tabbas ya........." Kasa karisa maganar ta yi, dan sai da ta fara maganar ne ainahin abin ya yi mata ɗin ya faɗo mata a cikin tunaninta, ba wai ta tuna abin da ya faru bane, no, ta tuna cewa mumynta ta gaya mata haka ake mu'amala ta auratayya, so abin da Noorish ya yi mata shi ne aure, hakan yasa ta kasa iya karisa gayawa gwaggon maganar, saboda wani irin azababben kunyar gwaggon da ta ji ya dira mata a ranta lokaci guda, duk sai ta ji ta takure waje guda, sai ta ji ba zata iya cigaba da yin magana da gwaggon ba, tana buƙatar matsawa daga kusa da ita, saboda kunya. Ita kanta gwaggon ta ji matuƙar daɗin yaddan Rimshar ta yanke maganar ta kasa karisa tambayar tata, abin ya yi mata daɗi, dan dama bata san wani amsa zata bata ba idan da ta idasa maganar. "Gwaggo ina Jehan da mumyna?". "Jehan tana ɗakina, mumynki ma tana ɗakinta, ƴar gidan mummy". Murmushi kaɗan ta yi, kafin ta yunkura zata miƙe, amma ina gaɓɓanta sun ki bata haɗin kan ta miƙe, ta kasa iya miƙewar. Komawa ta yi ta lafe shiru, kamar zata sake tambayar gwaggo meyake faruwa da ita ne ta kasa miƙewa? Sai kuma ta sake tuna last abin da ya faru a tsakaninta da shi, hakan yasa ta yi tunanin to ko abin da ya yi mata ɗin ne yasakata ciwon jiki? In kuwa haka ne ba zata iya tambayar gwaggon ba, dan ita tana da kunya sosai. Ganin haka yasa gwaggo ta ce "Ina zaki je dama?". "Wajen mumy". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "To bari na kira maki mumyn naki ko?". Ta kai karshen maganar tare da mayar mata da kanta a hankali ta kwantar mata, sannan ta miƙe ta nufi wajen. Da kallo Rimshar ta bita har sai da ta fice, sannan ta dawo da kallonta izuwa saman kayan magunguna da alluran dake ɗaure daman table da yake a kusa da gadon. Sai mamaki take yi a kan waye aka zandumawa waɗan nan uban alluran dukka, bata san dukka a jikinta suka kare ba, baiwar Allah bata san komai ba. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 10/5/2024 E29 Sai mamaki take yi a kan waye aka zankaɗawa waɗan nan uban alluran dukka, bata san dukka a jikinta suka kare ba, baiwar Allah bata san komai ba. Gwaggon tana fita ta so ta kira Lion a waya ta sanar da shi Rimshar ta farfaɗo, kuma sun yi sa'a bata gane komai da ya faru da ita ba, saboda suman da ta yi. Da ta duba time a wayarta, sai ta kalli lokacin yin sallar issha ne a Washington yanzu, dan haka sai ta ce bari ta kyale shi sai anjuma ta sanar mashi, kamar tasan yana cikin yanayi mara daɗi. Bedroom na mum ta nufa, ba ɓata lokaci ba ta gaya mata halin da ake ciki. Murna tamkar mum ta zuba ruwa a kasa ta sha, babban abin da ya fi sanyata murna ma shi ne yanda Rimsha bata gane komai da ya faru ba, da idanunta biyu aka yi komai ta sha wannan bakar azaba, da wlh ba zata koma wajen Lion ta daɗin rai ba, amma Alhdulimmahi da Allah yasa bata san komai ba, yanzu zata yi begen mijin nata, zata koma wajensa cikin so da kauna, ba za kuma ta ji tsoronsa ko ta rinƙa gudun shi ba, abin ya yi masu daɗi sosai, su wannan suma da ta yi ma taimaka masu sosai da sosai ya yi. A tare suka nufo ɗakin Lion ɗin, sai godiya ga Allah subhanahu wata'ala suke yi. Bakinsu ɗauke da sallama suka shiga cikin ɗakin, tana kwance kamar yadda gwaggon ta barta. Kusa da ita mum ɗin ta zo ta zauna tana tambayarta ya jiki?. Hannun mum ɗin ta riko tana faɗin. "Alhamdulillah mum". Sannu ta cigaba da yi mata, ita kuma gwaggo alwala ta ɗauro dan ta yi sallar mangariba ta godewa Ubangiji da ya tashin masu Rimshar cikin ƙoshin lafiya. Sosai Rimshar ta sha mamakin irin yanda suke ta ce mata sannu, abin ya ɗan dameta, ta ji sannun yaki karewa, ita yanzu duk ba sannunsu bane a gabanta, Noorish nata kawai take son ya dawo su ga juna. A ɓangaren shi kuma Lion ɗin, bayan sun yi sallar mangariba da issha, saman table suka haye dan su ci abinci, sam Lion baya jin ra'ayin cin abincin, saboda yanayi na sha'awa da yake a ciki, ga kuma damuwa na rashin farfaɗowar Meeshar tasa. Sai dai yunwarce ta yi mashi yawa over da har tasa ya haye saman table ɗin zai ci abincin. Shi ma Areef ba dan daɗi zai ci abincin ba, dan kawar da yunwa kawai zai ci, banda haka yanayin da yake a ciki na kewar Jehan ya hana shi sukuni. Shi kuwa Aseef suna zama a saman table ya kira Akila video call tare da ajiye wayar a yadda zasu ga juna, haka yake yi kullum, dan ya ce ba zai iya cin abinci ba tare da suna kallon juna ba. (Aseef ɗan dirama ne wlh😂 iskanci kala kala ya iya.) Kamar dai kullum, sai da ya karɓi first spoon na ƴan uwan nasa, yana yi yana karewa Akila dake kwance a saman bed kallo, daga ita sai kayan barci riga da wando a jikinta, ta lafe a saman bed tare da rungume pillow a kirjinta tana kallonsa, Jehan dai har wa yau tana bedroom na gwaggo, ita kuma Akilar a normal bedroom nasu ita da su Jehan ɗin take, ba'a bedroom na mijin nata ba, tun da ya bar kasar ita ma ta baro bedroom ɗin. Sai kallon shi take yi, ya kara kyau, ji take yi kamar ta zuro hannu ta shafi wannan lallausan kumatun nasa mai matuƙar ɗaukar hankali, ga sajensa ta kara kwanciya luf, duk sai ta shiga santin kyau ɗin da ya kara yi. A nashi ɓangaren shi ma santin kyau ɗin gyaran da ta sha yake yi, ta yi fresh, ji yake yi kamar ya jawota ya rungume, sai zubawa juna shagwaɓa suke yi, ko kunyar su Lion basu ji, su kuwa su Lion ɗin ko a jikinsu, tamkar babu su a wajen, abincinsu sama sama kawai suke ci. Kaɗan Lion ya tsakuri abincin ya miƙe bayan ya goge bakinsa, bedroom nasa ya nufa dan ya yi wanka ya fito ya duba ya jikin Mark yake, dan yau sam bai leƙa shi ba. Mark ɗin yana part dake kusa da na Aseef, a nan yake jinya, an ɗaura mashi kafar tasa, yana samun lafiya Alhamdulillah, likitoci har huɗu Lion ya sanya suka zo suna kula da shi, dan already kun riga kun sani cewa Lion yana Kaunar Mark sosai, shi ne ma yasa ya ce a dawo mashi da shi gida ya yi jinya a gabansu, dan su rinƙa kallon halin da yake a ciki. Bawan Allah yana shan wahala ba kaɗan ba, duk ya rame, kunsan yadda karaya take da azaba!. Kullum Anaya tana gefensa, bata taɓa yin nesa da shi, idan kuka ga ta fita daga bedroom ɗin, to sai dai idan likitoci ne suka zo zasu yi aikinsu, shi ne zata fita ta koma ɗayar ɗakin, dan a cikin part ɗin ɗakuna uku ne da palo guda, so ɗaya nata ne ɗaya na Mark ɗin, ɗayan babu kowa a ciki, idan likitoci sun zo, sai ta koma nata ɗakin, dan ta basu waje. Mark yana kaunarta sosai, ita ma ba sai na sake faɗa ba kun sani, ita ce ma ta fara son shi kafin shi ya faɗa mata. Duk da yana a halin ciwo, amma hakan baya hanashi ya rinƙa kula da ita tare da gaya mata kalamai masu daɗi, dan ya rinƙa kwantar mata da hankali, saboda tana cikin damuwa sosai wlh, dayawan lokuta idan ta zauna bata da aikin yi sai yi mashi kuka, shiyasa yake iyaka bakin kokarinsa dan ya ga ta dai'na shiga damuwa tana farinciki. A yanzu dai kafar tasa ta kai matakin da za'a kwance mashi ita ya ɗan fara takawa, umarnin Lion kawai likitocin suke jira, dan su kwance mashi ya ɗan fara takawa. Bayan ya yi wankar ya shirya cikin kayan barcinsa masu bala'in kyau da tsada, sai zuba kamshi yake yi tamkar a jikinsa ake kera perfume. Bedroom na Mark ɗin ya nufa, yana tafiya cikin wannan nutsuwa tasa. Kasa kasa ya yi sallama tare da shiga cikin ɗakin. Anaya tana zaune a saman bed ɗin kusa da mijin nata, hannunta na a ruke da cup mai ɗauke da coffee, sai tiririn zafi yake yi, shi kuma Mark ɗin yana ɗan gefenta, yana zaune, daga bayansa ta sanya mashi pillow, da alama ma coffee ɗin take ba shi a baki, ga ɗaya daga cikin Drs dake kula da shi yana zaune a saman bedside drawer, da alama ita Anayar ita ta ce zata bashi coffee ɗin a baki, hakan yasa Dr ya kyale mata ta bashi, dan duk abin da ta ce zata yi mashi, sai Mark ɗin ya ce masu su kyale mashi ita ta yi mashi. Kusa da bed ɗin ya ƙariso, a takaice ya tambayi Mark ɗin ya yake jin jikin nasa a yanzu?. "Alhamdulillah sir". Ya bashi amsa cikin girmamawa. Anaya ta koya mashi faɗin Alhamdulillah. Jinjina kai Lion ɗin ya yi tare da tambayar Dr ba wata matsala. Babu ya amsa mashi da shi cikin gaggawa shi ma. Sallama ya yi masu tare da ficewa ya koma bedroom nasa. Saman bed ya haye ya kwanta, shiru ya lumshe idanuwansa tamkar mai yin barci, a haka Areef ya shigo ya same shi, saman bed ɗin ya nufa yana faɗin "His Excellence what is wrong with you? Since in the evening naga like you're not in a good mood". Ɗan waro idanunsa waje ya yi, in a cool voice ya fara magana "Areef am in too much of missing Meesha, abin ya kai ni makurar da i can't control myself, I can't stop myself daga kai kai'na gareta". Shiru Areef ɗin ya ɗan yi. Hakika ya yi mugu mugun tausayawa Lion ɗin, dan yasan wanene ɗan uwan nasa, abin da zai sanya shi ya buɗe baki ya ce ya yi missing na wani abin, this thing is not be small thing ooo, duk sai ya ji ya shiga damuwa sosai, ya tausayawa Lion ɗin sosai da sosai. "Do you know something our Lion?". Shiru ya zuba mashi idanu ba tare da ya amsa ba. "Ka sanya a ɗauko maka ita, this is the only solution we have, zaman ta a kusa da kai ma zai taimaka maka sosai a kan duk wani abin da zaka yi, and then lastly Rimsha she is so special, she is very very smart, sometimes idan ta faɗi wani magana, zaka yi tunanin mace mai 30 years old ne ta faɗe shi, tana da hankali, nutsuwa and bata da yawan magana bare ka ce zata dameka da surutu ta hanaka yin aiki, so just ka ɗauki kayarka kawai, ta dawo kusa da kai, now she is your power and she is your weakness". Harara ya wurgawa Areef ɗin kafin ya ce "Meeshar ce so silent?". "Yeah Lion, Meesha she is so silent girl, ga hankali, ko da baka yi sex da ita ba, zaku yi wasa, zata na rage maka abin da kake ji sosai, ni bana goyon bayan ka sake kusantarta a yanzu, because idan ka sake kusantarta nan kusa zaka kasheta ne kawai, amma ka ɗaukota dan ta rage maka feeling da kake ji ta hanyar wasa". Har lokacin harararsa ya sake yi, sannan ya ɗan yi shiru na tsawon mintoci kafin ya ce "Meesha she isn't like you're thinking, she isn't silent at all, and them I can't control myself idan na ganta a kusa da ni, you can't understand anything Areef, you can't understand who is Meesha, even if i explain to you, you can't understand anything, what i know dai shi ne Meesha ce kawai zata iya kashe mani abin da nake ji that's all". "Lion why are you saying I can't understand who is Rimsha? I think na fika ma sanin wacece ita, kai fa baku jima da fara shiri ba, bata jima da fara zama kusa da kai ba, she is so silent, very very cute and smart girl". Girgiza kai kawai Lion ɗin ya yi, Areef fa ba zai gane komai ba, she a wajensa Rimsha ba shiru shiru bace, su ne take yi wa shiru shiru, shi a wajensa banda kuka da shagwaɓa babu abin da take yi mashi, and then yadda ya ɗanɗani zumar nan tata ba zai iya hakura ya kyaleta kamar yadda Areef ɗin ya faɗa ba, ba zasu gane me yaji ba, kawai su kyale shi da abin da yake ji, shi kaɗai yasan wace duniya ya shiga, shi kaɗai yasan wacece Rimsha, a yanzu ko iyayenta sai dai ya kallesu da ido, amma ba dai su gaya mashi sanin wacece Rimsha ba, saboda Areef bai san komai bane yake wani cewa ya fishi sanin Rimsha, to abin da bai sani ba ita dai Rimsha kamar mutun biyu ce a jikin mutun ɗaya, saboda acting biyu take yi, a wajensu Areef tana nuna masu true colornta, shi kuwa Lion ko magana zata yi mashi na serious a kan abu, ba zaka taɓa jin ta buɗe murya ko kuma ta yi magana da asalin voice nata ba, cikin shagwaɓa take yi mashi magana, yanzu da za'a cewa Areef tana da saurin kuka, ba zai taɓa yarda ba, saboda bata taɓa yi masu ba, amma shi kuma Lion, da ya yi mata abu kaɗan zata sa mashi kuka, sai ya yi ta aikin rarrashi, so sanin da Areef ya yi mata ya mata ne a kan Rimshar ta na ainahi, shi kuma Lion Meesha uwar shagwaɓa da soyayya ya sani, suna da banbanci sosai. "Areef you don't know who's Rimsha, that's all kawai". Ya faɗa tare da jawo wayarsa dake ɗaure a saman bedside drawer tana ringing. Shiru Areef ɗin ya yi yana tunanin halayen Rimshar, shi dai yasan shiru shiru ce Rimsha, ga shiga hankali sosai. Ganin kiran mommansa ne yasa ya katse kiran tare da gyara kwanciyarsa haɗe da jawo pillow izuwa saman Lion chest nasa, sannan ya bi kiran. Bugu ɗaya suka ɗauka. Cikin sanyin murya ya ce "Assalamu alaikum, good evening Momma". Daga ɗaukar ɓangaren ta amsa mashi da "It's not Momma, it's Meesha, wai Noorish ina ka tafi ne? Tun ɗazun gwaggo ta ce ka fita, kuma baka dawo ba, ni fa gaskiya........" Dakatawa da yin maganar ta yi sakamakon jin yanda ya ambaci sunanta da ɗan sauti kuma cikin sarkewar murya, yana daga kwance bai san time da ya miƙe zaune ba, kwata kwata bai kawowa ransa cewa ta farfaɗo ko zata farfaɗo a yanzu ba, kuma dole ya shiga mamaki na jin yadda ta kirashi babu wata alama da take nuna cewa ya yi mata laifi, ko tana fushi da shi, bai san ita bata san komai da ya faru ba, bai taɓa tunanin zata farfaɗo ta yarda da shi ba, bai taɓa tunanin zata yarda ko a waya su yi magana ba, abin ya yi matuƙar bashi mamaki. Love period ❤️🥲😌 "Noorish lafiya kuwa?". Ta faɗa a ɗan tsorace. A hankali ya koma ya kwanta tare da kara jawo pillown nasa ya rungume yana faɗin "My Meesha is it you?". Ya faɗa cikin wata iriyar murya da take nuna tsantsar kaunarta da yake yi. Mamaki ne ya kamata, ita tarasa wannan abin da me ya yi kama, su mummynta sai su rinƙa lallaɓata suna ta ce mata sannu, sannu yaki karewa, ga maganganun da zasu kwantar mata da hankali wanda gwaggo da mum ɗin suke gaya mata, sannan ga kula na musamman da suke bata, sun hanata zuwa ta je ta yi wanka, da ta motsa za su ce mata sannu tana bukatar wani abin ne? Yanzu ta ce zata yi magana da Noorish gwaggo ta kira mata shi a waya, shi ma yana ɗaukar kiran ya ruɗe daga jin voice nata, tunani ta fara yi anya wani gagarumin abu bai faru ba kuwa? Anya babu wani abin da suka ɓoye mata kuwa? Tasan cewa gwaggon da mum ɗinta duk tun fil azart suna nuna masu kauna da kulawa, amma ta yau ɗin nan ta yi yawa over, sun saka mata kai a duhu, sun kuma saka mata kwakwalwa a cikin tunani. "Meesha meyasa kika yi shiru?". Ya faɗa yana kallon Areef da ya tsare shi da ido. Sai mamakinsa Areef ɗin yake yi, bai taɓa tunanin ko da sunan wasa zai ga Lion cikin zumuɗin jin muryar mace irin haka ba. Hannu ya kai ya kyastawa Areef ɗin kyawawan yatsunsa a dai'dai saitin face nasa yana sauraron abin da Meeshar tasa take faɗa. Kasa sosai ta yi da murya, dan gwaggo tana a cikin ɗakin nata, mum ta koma nata ɗakin zata je ta yi sallah, so bata son gwaggon ta ji hiranta da mijin nata, dan wani azababben kunyar gwaggon take ji a yanzu. "Noorish kafaɗa mani me kayi mani please? Naga su mum sai sona suke kara yi". (Rimsha zata kashe mutun da dariya, wai su mum sai kara sonta suke yi😂) Shiru ya ɗan yi, sai yanzu ya gane dalilin da ya sanya ta yarda ta kira shi a waya, wato bata san abin da ya faru ba? No wonder mana, da ta sani ai da sun yi hannun riga kenan. Nisawa ya yi tare da sauke nauyayyar ajiyar zuciya kafin ya fara magana in a cool voice. "Meesha babu abin da na yi maki face soyayya kawai, know lest do a video call, I want to see your beautiful face my life". Shi kam Areef ai gabaɗaya Lion ya kwance mashi lissafin ƙwaƙwalwa, ko da sunan wasa bai taɓa tunani Lion ya iya kalamai masu daɗi haka ba, basu taɓa jin sa ko da sunan wasa ya furta makamantansu ba, ko a mafarki basu taɓa zaton ganin irin wannan rana ba. "Noorish Allah kunyarka nake ji, ni kawai ka dawo gida sai muga juna". A shagwaɓe sosai ta yi maganar. Kamar zai ce mata baya kasar, amma sai ya tuna da cewa ta ce mashi gwaggo ta ce mata ya fita yana zuwa, hakan na nufin sun ɓoye mata baya nan kenan, tuna hakan yasa ya ce mata "Meesha ba zaki yi mani abin da nake so ba? Ina son kallon face naki fa na ce? Before na dawo ɗin ne nake son ganinki, do you know how much i love? Do you know what am feeling about you now danaji voice naki kuwa?". Kwace wayar Areef ya yi tare da sanyata a hand-free, dan ya tabbatar wa da kansa Rimshar da ya sani ce, ko dai wata ce, so yake ya ji yau dai ya suke magana, me Rimsha take gayawa Lion da har shi ma yake gaya mata kalamai irin haka. (Areef akwai shegen son jin gulma, ga sa ido, ko ina ruwansa da su?🤔 😂 Amma dai gara ya jiyo mana me suke faɗa da kyau 😂) "Noorish kome kake so zan yi maka mana, in dai bai saɓawa Allah, ka manta cewa kai ne farincikina? Amma dai ni gaskiya sai ka rufe ido, idan na kalli kyakkywar face ɗin nan naka da kyau da kyau, sai na kawar da kallo na, sai ka buɗe idon, dan ina jin kunyar ganin cikin idonka ne fa". Ta yi maganar a shagwaɓe sosai. Salati Areef ɗin ya fara yi a cikin zuciyarsa, yana mamakin yaushe Rimsha ta zama haka shi bai da labari? E lallai dole Lion ya rinƙa zuba mata kalamai ba tare da ya san yana zuba su ba, irin wannan zallar madarar shagwaɓa da kalamai da take zuba mashi, ga muryarta a kwance kasa kasa, idan ba ka yi mata farin sani bama, ba zaka taɓa cewa ita bace, gaskiya bai ga laifin Lion ba, dole ne ma ya shiga zuba kalamai ba dan ya shirya ba. Daga kasan zuciyarsa kuma tunani yake yi ko yaushe shi kuma zai sami irin wannan soyayya haka? Yaushe Jehan zata fara nuna mashi soyayya haka?. Bawan Allah duk sai ya ji babu daɗ, Rimsha dai har da wani sunan soyayya mai azababben daɗi tasakawa mijinta, wai Noorish, Noorish ɗin ma idan zata kira da salo mai matuƙar jan hankali take kira, amma shi ƴar diramar nan tasa tasan komai, kuma ta iya komai sai wahalar da shi take yi, kuma a haka saboda rashin adalci irin na zuciyarsa kara sonta ma yake yi, baya son ya ji an faɗi laifinta, bawan Allah. Karɓar wayar tasa daga hannun Areef ɗin ya yi tare da katse kiran ya kirata video call. Bugu ɗaya ta ɗauka. Wani irin doguwar numfashi ya ja lokacin da idanuwansa suka sauka a kanta, a hankali ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya. Ita ma tana ɗaukar kiran ta sauke idanunta a saman face nasa, wani irin daddaɗar ajiyar zuciya ta sauke, sai dai kuma ta canza fuska sosai na ganin shi kwance a saman bed, ina yake to? Ta tambayi kanta. Ganin ta ɗaure fuska sosai ne yasa ya ɗaga mata gera ɗaya alamar lafiya?. "Yah Saif ina kake yanzu haka?". Ta faɗa kamar zata saka mashi kuka. Shiru ya ɗan yi, ya lura da ita sosai, idan ya yi mata abin da bai yi mata daɗi ba, zai ji ta kirashi da Yah Saif saɓanin Noorish, hakan na nufin ranta ya sosu kenan, yarinya mai hankalin manya. "Meesha i want you to understand me, and ki yi mani uzuri, I'm not around, I'm not in Nigeria now, ina U.s, but zanzo ba da jimawa ba kin ji?". Kuka mai sauti ta saka mashi tare da kifa wayar a saman bed, da gaske take kukan, hawaye zafafa ne suka fara bin kuncinta. Da sauri gwaggo dake zaune a saman dadduma ta miƙe ta nufota tana tanbayarta lafiya, shi ma Lion ɗin sai hello, hello yake ce mata, amma ina ta kifa wayarma a saman bed ɗin, baya iya ganinta bare yasan ta yadda zai shawo kanta, yana dai jin voice nata tana kuka, yana kuma jin voice na gwaggo tana magana a kusa da ita, shiru kawai ya yi yana sauraronsu. Tari ta fara yi mai sauti sosai tamkar makoshinta zai fashe, tana mai cigaba da yin kukan nata da iya gaskiyarta. Matsowa gwaggon ta yi ta rungumota tana tambayarta lafiya?. Kasa yin magana ta yi, saboda kukan ya ci karfinta, ga kuma tarin da take yi sosai da sosai. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 13/5/2024 E30 Kasa yin magana ta yi, saboda kukan ya ci karfinta, ga kuma tarin da take yi sosai da sosai. Hankalin gwaggo idan ya yi dubu to ya tashi a wannan lokaci, kiran sunanta take yi, amma ina ko kulata Rimsha taki yi. Shi kuwa Lion ganin ba zasu ji shi bane yasa ya katsi kiran ya sake kira, dan wayar ta yi ringing ta sa su dawo da hankalinsu a kanta, duk hankalinsa a tashe bawan Allah, a yanzu a duniya, idan akwai abin da ya tsana, to bai wuce yaga ɓacin ran matarsa ba, sam baya son yaga antaɓa mashi ita, zai iya yin komai a kanta. Yana sake kira gwaggo ta kai hannu ta ɗauki wayar, ganin shi ne yasa ta yi picking da wuri, dan dama ko bai kirata ba, tana da niyar ta kira shi, dan ta ji me ya yi wa Rimsha da har take irin wannan kuka da tari haka. Ita kuwa Rimshar, kwanciya ta yi tare da rungume pillow tana mai cigaba da yin kuka kasa kasa, hawaye bibbiyu take zubarwa. "Assalamu alaikum". Ya faɗa cikin sanyin murya. "Wa'alaikumussalam". "Good evening momma". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Firstly me ka yi wa Rimsha take irin wannan kuka haka?". "Nothing momma, kawai dai dan na ce mata am not around ne yasa ta yi fushi, please Momma ki rarrasheta ta yi shiru, kinga bata da lafiya, and if that's the case ki yi mani izini na sa a ɗauko mani ita kawai, because ba zata iya zama babu ni ba, nima kuma haka". Ya kai karshen maganar yana jan dogon gashin kan Areef da yake ta yi mashi dariyar mugunta, saboda Rimshar tana fushi da shi, duk ya bi ya rikice, shi ne Areef ɗin yake yi mashi dariya dan neman tsokana. "Meyasa zaka gaya mata baka kusa? Kasan wahalar da muka sha kafin ta farfaɗo kuwa? Ka san wahalar da ƴar tahaliƙar nan ta sha? A yanzu Rimsha farinciki take so ba wai a kara ɓata mata rai ba, ba zan ji daɗi ba idan har ka sake yi mata abin da ba daɗi, ka yi magana da ita, idan har tana son zuwa wajenka shikenan ka tura a ɗauka maka ita ɗin". Ta kai karshen maganar tare da sanyawa Rimshar wayar a kunne, sannan ta juya ta fice abinta. Shiru ya ɗan yi yana sauraron kukan nata da take rerawa, yana kuma tunani a cikin zuciyarsa, lallai uwa uwace, tun da yake babu wanda ya iya tunkararsa ya ce mashi Saif abin da ka yin nan baka kyauta ba, ba'a taɓa samun wanda ya kwatanta kwantankwacin haka ba, wasu ma da yin magana da shi kawai tsoro yake basu, yana yi masu kwarjinin da ba zasu iya ba, amma yau kai tsaye gwaggo ta ce ya yi laifi, kuma bai ji zafin faɗar hakan da ta yi ba, sai ma daɗi da ya ji da ta yi mashi faɗa, to gaskiya dai uwa ta wuce abin wasa, dole ya kara jinjinawa duk wasu iyaye jajirtattu a kan ƴaƴansu. "Meeshana". Ya faɗa a sanyayye. Tana jinsa ta ki amsawa, cigaba da kukanta ma ta yi. "Am so sorry, please stop crying mana, kina nema ki sanya zuciyata ta ɗau zafi ba? Ni nasan ke mai hakuri ce kuma mai yi wa mutane uzuri, amma meyasa kika kasa yi wa mijinki uzuri?". Cikin kuka a ƙule ta ce "Saboda ina sonka mana, babu wani uzuri da zan yi maka, kuma dan kaga ina son kane yasa kake bani wahala ko? Dama ni nasan ni kaɗai nake sonka, kai baka so na". "Meesha why you said that? You know i really love you, amma kike cewa bana sonki?". Mikewa zaune ta yi tare da ɗaukar wayar tana faɗin "Yah Saif baka sona, da kana sona ba zaka taɓa yarda ka tafi ba tare da munga juna ba, kasan kewarka da nake yi kuwa? Kasan......". Wani irin burki ta ja a maganar tata, kasa cigaba da yin magana ta yi, saboda wani irin tsawa da ya daka mata ta cikin wayar. "Do you know how many times i take together with you?! Meyasa kike son kureni ne Meesha? Kinsan da ya na iya danne zuciyata har nake iya sauraron maganarki na cewa bana sonki kuwa? Idan kika sake gaya mani irin haka sai na fasa maki baki, am i your mate?!". Kuka mai sauti sosai ta kara rushe mashi da shi tana faɗin "Shikenan tom ka yi zamanka a in da kake, nima zan yi zama da iyayena, dama can da su nake zaune". Ta kai karshen maganar tare da yin wurgi da wayar a jikin bangon ɗakin, ji kake tarrr wayar ta tarwatse, ta zuciyane baiwar Allah, ta fusata, yau Lion ya kureta iya karshen kurewa, ba abin da ya fi bata haushi ma irin tsawar da ya daka mata, wannan shi ne a daki mutun a hana shi kuka, dama kun san idan mutun yana a irin wannan hali da take a ciki na ɓacin rai babu abin da ba zai iya faɗa ba, tana son shi kamar ta mutu ne yasa dukka hakan take faruwa. Shi ma dai a nashi ɓangaren jin kalamanta na karshe yasa ya cire wayar daga kunnensa yana bin screenshot ɗin da kallo, nan take shaiɗan ya yi mashi raɗa da cewa yarinya under 15 years ce yau ta tsaya take yi mashi magana son ranta haka, kamar shi ɗin nan, shi da zaratan maza masu ji da jini a jika ma tsoron tinkararsa suke yi dan su yi magana da shi, amma yau under 15 years ce ta samu damar yi mashi irin wannan rashin kunya, lallai kuwa soyayya bata yi mashi adalci ba, kuma dole a yau soyayyarta ta fita mashi a cikin zuciya, dan bai ga wata ƴa mace da ta isa ta gaya mashi magana makamanciyar wanda Rimsha ta gaya mashi ba, wai ya yi zamansa a can, dama can ai ita da iyayenta suke zaune, kuma dama ba sonta yake yi ba, wannan abin ya kona mashi rai da har yasa shi ma ya yi wurgi da wayar tasa, ya kuma sanya a ransa daga yau ba ya cireta a ransa, dole ya rabu da ita tun da har abin ya zamana haka!!. Lallai akwai cakwakiya!. Duk abin da suke yi Areef yana ganinsu, tausayin Lion ɗin ma kawai yake ji, dan yasan yariga da ya bawa Rimshar zuciyarsa, so ba zai iya rabuwa da ita ba, kuma idan tana cikin damuwa shi ma Lion ɗin zuciyarsa ba zata taɓa samun sukuni ba, kawai wahalar da kansu zasu yi, dan ba zasu taɓa iya hakura da juna ba, zasu wahalar da kansu ne a banza, kuma zasu sha wahala in dai fushi da juna zasu yi. (To mu dai bari mu gani, shin zasu iya yin fushi da junan ne ko dai zasu kasa🥲 namu ido😂) Kwanciya ya yi tare da rumtse idanuwansa gam, tamkar zai fasasu, sai ka ce su ne suka yi mashi laifi, zuciyarsa wani irin zafi take yi mashi, tun ainahi kunsan su TRIPLETS basu son raini ko kaɗan, hakan yasa Lion ɗin yake ƙoƙarin kawar da Rimsha daga cikin zuciyarsa, saboda a cewarsa ta ra'ina shi. (Wani irin raini kuma ya rage tun da har ka iya kwanciya da ita, kana wasa da tula tulanta, ai daga nan ma kawai His Excellence Saif ka manta da batun ta rai'naka🥺😌 kun rigada kun zama ɗaya, kawai ka jawota ku rarrashi juna) Kamar Areef zai yi mashi magana, sai kuma ya fasa, saboda ya lura ran Lion ɗin ya ɓaci sosai, idan ya kuskura ya yi mashi wata magana a yanzu, to suna iya dakuwa da juna, mafi a'ala kawai ya kyale shi sai ya yi barci ya farka, idan zuciyar ta sauka, sai ya gaya mashi ita fa Rimsha yarinya ce, kuma son shi da take yi ne yasa har ta damu da tana son ganinsa, idan bata son shi ba zata ko kula shi ba, a cikinsu dukka TRIPLETS ɗin waye ta kira ta ce sai dai ya dawo idan ba shi ɗin ba? Ai ko iya haka ya kamata ya san cewa ba wai dan rashin kunya ko raini yasa ta faɗa mashi magana haka ba, so ne ya jawo hakan, kuma su mata fa sai ya yi hakuri da su, dan annabi ya ce a karkace suke, ba zasu taɓa miƙewa ba, so dole ka bisu a yadda suke idan kana son zama da lafiyarka ba sai ka rinƙa ziyartar asibiti ba, bugu da kari kada ya manta da abin da ya yi mata kwanaki ashirin da tara da suka wuce, dan ma Allah ya taimake shi bata san me ya faru ba, ai ta cancanci ya ɗaga jirgi ne ma musamman ya je ya dubata ya dawo, ba wai ya kara ɓata mata rai ba, amma dukkansu zuciya da kuma shaiɗan sun ɗebesu, sun zuciya a banza, wanda hakan kuma sam ba shi ne solution a garesu ba, dan ba hanya mai ɓullewa suka bi ba, hanyar da zata jefasu cikin ukuba suka sake afkawa, zasu yi bayani ne dukkansu biyu! Dan dukkansu suna matuƙar kaunar juna na wuce misali!. Miƙewa Areef ɗin ya yi ya diro kasa daga saman gadon, bedroom nasa ya nufa yana mai addu'ar Allah ya shirya mashi Lion ɗin nan, mutun sai bala'in zuciya, yana da tabbacin da'a gabansa Rimsha ta yi wannan magana, da ba abin da zai hana bai yi mata dukar mutuwa ba, dan duk cikinsu ma Lion ɗin ya fi tsanar kalmar raini, da sai ya yi mata ɗan banza duka, sai dai daga baya ya yi danasani, amma zata daku kam. Lion a haka ya runtse idanuwansa yana mai jin zuciyarsa tana yi mashi zogi har barci ɓarawo ya yi awon gaba da shi. Shi ma Areef ɗin bedroom nasa ya koma ya kwanta, dama shi Aseef already yana can bedroom nasa suna aikin da suka saba shi da Heartbeat a waya. Asuba ta gari. KASAR CHINA. Babban birnin Beijing, Capital Cityn kasar China kenan, birni ne mai matuƙar girma tare da cike da abubuwan more rayuwa da kawa, yana da matuƙar ɗaukar hankali, akwai guraren yawon buɗe idanu kala kala, kun san China da uban technology, akwaisu da iya ƙere ƙeren abubuwa, ga wajajen hutawa na more rayuwa, ko'ina a cikin birnin tsab yake babu datti, al'adunsu dayawa daga ciki gwanin birgewa, ga su da karrama bako, suna da son mutane, tsayawa zayyana maku yaɗuwar birnin Beijing ma ɓata lokaci ne, dan baki ya yi kaɗan wajen zayyano shi, dan fa kowa yasan China karshe ce, sun haɗu iya haɗawa, dan haka mu shige kai tsaye cikin storyn dan jin yadda zata kaya. Ministry of defence, wato Ma'aikatar tsaro ta kasa bakiɗaya. Wani tampatsetsen office ne a cikin Ministry of defence ɗin, a dukka ofisoshin dake a wajen wannan ya fisu girma da kawatuwa, ya tsaru iya tsaruwa na wuce misali, kai daga gani ko ba'a faɗa maka ba kasan cewa office ɗin Defence minister ne, wato Ministan tsaro, yanayin tsarin office ɗin nasa ma na daban ne, ya tsaru iya tsaruwa, gabaɗaya fentin office ɗin fari kal ne mai matuƙar kyau da tsada. Daga cikin parlour na office ɗin, wato wajen meeting nasu kenan, wasu lumtsuma luntsumar tsadaddun Chinese sofas ne masu numfashi jere a wajen, set biyu ne dai'dai sofas ɗin, sun tsaru iya tsaruwa, gasu da laushi tamkar audiga, kana zama zasu lume da kai, launin ash color ne, lallausa kuma tsadadden Chinese carpet dake shumfuɗe a tsakiyarsu ma launin ash ɗin ne, daddaɗar kamshi tare da sanyin A.c mai ratsa zuciya tare da kwantar da hankali sai tashi yake yi a cikin parlour, kai kace parlourn wani hamshakin sarki mai ji da karfin mulki ne, amma kuma office na mutun ɗaya ne, common dustbin dake a cikin parlourn office ɗin nan abin kallo ne, dan ba kuɗin wasa aka zuba mashi wajen sayansa ba, na manyan kai ne, ko'ina tsab kamar yanzu aka zuba sabbin kayan cikin. Akwai wani kyakkyawan table mai ɗauke da table chair da yake a gefe guda, wata farar tattabara ce, wato wata farar budurwa kyakkyawar gaske ce zaune a saman chair ɗin, da alama Secretariya ce, ƴar Chinance, tana cikin shiga irin na ma'aikata, mining sket black color and long sleeve fara, ta ɗaure gashin kanta a tsakiyar kai, ta saki jelar har gadon bayanta, kunsan yanda gashin Chinawa yake ai? Ba sai na taya zuba maku dogon bayani ba. Kana shigowa zaka yi ido huɗu da tampatsetsen frame na president, governor and Defence minister a manne a bango suna fuskantar kofar shigowa. Wani haɗaɗen Chinese door ne daga gefen dama, irin tsadaddun nan ne da suka amsa sunansu, cikin wannan door ɗin, nan ne ainahin cikin office ɗin, duk wanan kawatuwa da na zayyano maku a iya parlour ne kawai, cikin ya wuce tunaninku, idan ka shiga sai ka yi zaton kabar duniya, saboda wani irin ni'ima da zai ziyarceka lokaci guda, wani irin sanyin A.c mai bala'in daɗi ga kuma daddaɗar kamshi air freshener mai matukar kwantar da hankali, su kansu luntsuma luntsumar sofas dake a cikin office ɗin ya isa ya sanya mutun ya saki baki yana kallonsu, office chair ne mai bala'in kyan gaske a wajen wani katafaren table wanda ya haɗu ya gaji da haɗuwa, wannan office chair ya wuce baki ya zayyano kyansa, shi kansa table ɗin ya wuci misali, tiles na kasar floor white color ne mai matuƙar kyau, ga shi fari kal, hakan zai tabbatar maka da cewa mamallakin wannan office ɗin tsabta tana yi mashi mubaya'a, tiles dake a jikin bango light ash ne, sai kyalli suke yi, alamar ko wace rana sai an gogesu tsab, tamkar hannu bai taɓa taɓasu ba, gabaɗaya Curtain dake a cikin office ɗin white color ne masu bala'in tsada. Wasu tsadaddun desktop computers ne a ɗaure a saman wannan tsararriyar table ɗin, tulin files ne a gabansa kusa da computers ɗin. Wani santalelen matashi mai jini a jikka ne zaune a saman wannan dankareriyar office chair ɗin nan, tsalelen matashi dogo da shi, daga kafafunsa dake sanye da wasu shegun black covers masu matuƙar kyau da tsada har izuwa kyakkywar dark black curly hairnsa dake kwance mashi har bayan wuya dukka tsadaddun kaya ne da suka amsa sunansu tsadaddun, komai na jikinsa kuɗi aka narka ba kaɗan ba, watch ɗin hannunsa kawai ma abin kallo, danƙareriyar diamond watch mai matuƙar ɗaukar idanu saboda kyalli ne, ɗayar hannunsa na sanye da wata ƴar siririyar diamond hand chain, akwai wani tsadadden diamond ring a ɗaya daga cikin kyawawan fararen ƴatsun hannunsa, baka iya ganin face nasa, saboda ya duƙar da kai ya kurawa wata hoto dake jikin jarida idanu. Black suit ce a jikinsa, ta yi matuƙar yi mashi tsantsar kyau, duba da yanayin fatar jikinsa kamar madara, hakan tasa ya yi wa suit ɗin matuƙar kyau sosai. Gashin kansa sai wani kyalli yake yi tamkar gashin kan Lion namu na Meesha. Shiru ya zubawa wata hoto idanu yana kallo, idanuwansa na sanye da black glass mai matuƙar kyau wadda ta kara fito mashi da hasken face nasa, soft skin nasa tamkar madara, a kwance luwai luwai, ga wasu chains na zallar zinari masu bala'in kyau a wuyarsa wadda suka sauko mashi har saman chest nasa, fuskarsa a ɗaure tamau kamar hadari, alamar babu wasa a tattare da shi, tamkar yadda face ɗin Lion take a ɗaure kullum, haka nasa face ɗin ma take. Ba komai ya kurawa idanu ba face hoton Lion, bai taɓa sanin Lion ba sai a yanzu da Lion ɗin ya fito takarar neman shugaban kasa, a nan ne ya ga hotunansa a kafafen yaɗa labarai suna yawo, a news sai maganarsa suke yi tare da ɗaura ainahin hotonansa, ga postoci da aka yi mashi, kun san a da can baya ba kowa ya san ainahin face nasa ba, saboda da face mask yake yawo, so a yanzu babu face mask ake buga postocin siyasar tasa, ta hakan wannan matashi ya samu hotonsa na ainahi, abin ya yi matuƙar girgiza shi time da ya fara ɗaura idanunsa a kan hoton Lion ɗin, saboda babu wata banbanci dake a tsakanin face nasa tsawonsa komai nasa da ta Lion ɗin, time da abokinsa ya turo mashi hoton, lokacin da ya buɗe sakon abokin nasa, yana ɗaura idanunsa a kan hoton bai san time da ya miƙe tsaye a razane ba, da farko ya ɗauka hotonsa ne, sai daga baya da ya kalli na jikin hoton da kyau, sai ya lura Lion ya fishi murɗewar jiki, sannan ya fishi cika, kuma a jaridar an rubuta cewa ɗan takarar shugaban kasa na ƙasar America da ya lashe zaɓen primary election a halin yanzu, hakan tasa ya fahimci ba shi ne a jikin hoton ba, kama ce kawai da ta yi over, tun da gari ya waye ya zo office nasa ya fara aiki, tun da abokinsa ya turo mashi jaridar nan ya dakata da yin aikin komai, ya dakatar da kowa da samun damar ganinsa, ya zauna ya zubawa wannan hoto ido yana mamaki tare da al'ajabin irin wannan muguwar kamanni da take a tsakaninsu. Abin ya yi matuƙar girgiza shi, ya aka suka yi irin wannan kama tamkar mutun guda haka? Abin ya yi mugu mugun tashin kansa ba kaɗan ba. Tsadaddiyar wayarsa da take a gefensa ne ta fara ringing, har ta katse bai ɗaga ba, kira ta biyu ta sake shigowa, ita ma har ta katse bai ɗaga ba, sai a na uku ne ya ɗauki kiran. Kara wayar ya yi a kunnensa ba tare da ya ce uppan ba, sai a lokacin ne kuma ya ɗago kansa tare da ajiye jaridar hannun nasa mai ɗauke da hoton Lion, sannan ya koma ya jingina da jikin chair ɗin yana sauraron abin da ake faɗa mashi a cikin wayar. Haƙiƙa babu wata banbanci dake a tsakanin fuskarsa da ta Lion, duk da idanuwansa suna a cikin black glass, baka iya gane wani irin kalace da su, amma hakan ba zai hana ka ga tsantsar kamanninsa da Lion ba. Ya ɗan jima yana sauraron abin da ake faɗa ta cikin wayar ba tare da ya amsa ba, sai ya ɗago hannu yana duba time a jikin dankareriyar watch dake a hannunsa. Calmly ya furta "Am coming". Da zazzaƙar muryarsa mai muguwar kama da ta Lion, Iya abin da ya furta kenan tare da katse kiran. Nisawa ya yi tare da ɗan ɗago da kansa da nufin ya miƙe tsaye. Turo kofar office ɗin Secretariyarsa ta yi tare da shigowa tana faɗin "Sir ARVIN you have some visitors from West Building, Zhongnanhai". Shiru ya yi mata bai amsa ba, ganin haka yasa ta juya ta fita, da alama ta yi mashi farinsani, hakan yasa ta san fassarar shirunsa. Wanene ARVIN. ARVIN dai shi ne Defence minister na kasar China bakiɗaya, wato ministar tsaro ta kasa, duk wani mai kaki a karkashinsa yake, idan ana maganar duk wani mai kaki kuma mai muƙami, to fa gaɓaɗaya ake magana, duk wasu jiga jigan Generals na sojoji, ƴan'sanda da dai duk wasu masu muƙami, harta General of the army's a karkashinsa yake, shi ne Minister tsaro gabaɗaya, mutun ne mai matuƙar girman kai, jiji da kai, isa, izza da kuma taƙama, mahaifinsa shi ne Senate president na ƙasar, yana da kanne biyu, namiji ɗaya sai mace ɗaya, namijin yana da shekaru 27 a halin yanzu, ita kuma macen tana da 13 to 14 years old, mutun ne miskili, ga kuma ɗan banzan farinjini kamar ba gobe, jama'a kowa son shi yake yi, yana tare da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa, bashi da aure, ko budurwa bashi da ita, saboda shi gani yake yi ɓata lokaci ne ma ya tsaya sauraton mata, haka zalika kanin nasa ma bashi da mata. Wannan shi ne ɗan takaitaccen tarihin Sir ARVIN. Miƙewa ya yi tsaye, dogo da shi tamkar Lion ne yake tsaye a wajen. Hannu ya kai ya rufe laptop dake a gabansa, kafin ya ɗauki tsadaddun wayoyinsa har biyu ya nufi waje cikin takun nuna isa, tsantsar lafiya da kuma izza. Yana fitowa gabaɗaya kananan ma'aikatan dake wajen suka fara duƙawa suna yi mashi mubaya'a, kun san halin Chinawa da iya duƙawa kasa su gaishe da mutum, ko sannu zasu cewa mutun sai sun ɗan dukar da kansu kasa, so yana fitowa haka suka fara duka mashi cikin girma da girmamawa, ko kaɗan bai ɗago idanu ya kalli ko mutun ɗaya ba, dama na gaya maku yana da bala'in girman kai. Sai da ya fito harabar wajen ne wasu jiga jigan bodyguards masu ji da lafiya da karfi, su goma sha biyu ciff suka take mashi baya har zuwa wajen wani haɗaɗɗen parking space dake a wajen, gabakiɗaya bodyguards ɗin Chinawa ne, jajir da su kamar tsada, ga su da faɗi, basu da tsawo sosai, kamar yanda kuka sani ne, bodyguards ɗin suna sanye cikin black suit kamar yanda kowasu bodyguards suke sanyawa. A hanzarce wani ƙosasshe kuma lafiyayyen bodyguard ya kai hannu ya buɗe mashi wata dankareriyar mota kirar *ROLLS-ROYCE* Fara tas da ita tana wani ɗaukar ido, sai ka rantse da Allah yanzu aka fito da ita daga laida, wasu luntsuma luntsumar sofas ne a cikin wannan mota masu matuƙar laushi, kun san idan aka ce luntsuma luntsuma, ana nufin masu lumewa da mutun saboda laushi da tsantsar kyau, wani irin azababben daddaɗar kamshin car perfume ne yake tashi daga cikinta, ga wani irin sanyi A.c dake tasowa, kai tsayawa zayyana maku haɗuwar wannan mota ma ɓata lokaci ne, dan ya wuce misali. Cikin nutsuwa tamkar Lion haka ya shiga cikin motar ya zauna, zuciyarsa cike taf da tunanin wanene Lion? Meyasa suke muguwar kama haka? Why Lion ya yi kama ba da iya shi kawai ba, har da kanwarsa Pinky? Shi Lion da yake Americans, shi kuma da yake Chinese me haɗinsu? Ga ita ma Pinky da take nan. Abin ya dame shi sosai, haka bodyguards nasa suka shiga ciki sauran tsala tsalan motocinsa guda shidda dake a wajen. A jere kai guda motocin suka tashi gwanin birgewa, kai daga gani kasan babba ne zai bar wajen, dan motocin nasu ma kawai abin kallo ne, a haka suka nufi tampatsetsen gate na ma'aikatar. Tun kafin su iso jiga jigan masu gadi sun wangale masu gate ɗin, da gudun gaske suka danna hancin motocin waje, motar ƴan'sanda mai lode da jam'ai har guda uku ne suka rufa masu baya tare da sakin jiniya tamkar filin yaki zasu tafi. Kai tsaye.............. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 14/5/2024 E31 Kai tsaye Zhongguncu motocin suka nufa, katafaren unguwa ce wadda ta ji manya manyan tsara tsaran gine gine na zamani har ta ƙoshi, ko'ina ka ɗaga idanu ka kallah sai ka ji baka son kawar da kanka daga wannan wajen, tsaruwa iya tsurwa, haɗuwa iya haɗuwa, shunfuɗaɗɗiyar titin da ta keta cikin unguwar ma kawai ya isa mutun ya saki baki daga safe har yamma yana kalle kalle kayan alatun da aka shunfuɗawa wannan titi, abubuwa ne kala kala, wajen tafiyar mutun a kafa daban, wajen tafiyar keke daban, wajen tafiyar mota daban, haka titin nan yake, gwanin birgewa, baki ma ya yi kaɗan ya zayyano yadda haɗuwar titin take, sai dai ku kawata a ranku. Tun da motocin Sir Arvin suka hau saman wannan titi babu wata mota da ta gifta har suka nufi wata dankareriyar gini na alfarma, wadda ake yi wa yaƙabi na karshen burin ɗan adam, kunsan ɗan adam da shegen buri over, to duk wani burinka idan ka sanya kafarka a cikin irin wannan gida fa shikenan angama, sai ka ji tamkar bama a duniya kake ba, bene ne hawa biyar, gini ne na tiles da glass, abin dai ba'a magana, gate ɗin gidan ma kawai abin kallo ne. Tun kafin jerin gwanon motocin su iso an wangale masu tampatsetsen gate ɗin, da alama gate ɗin da na'ura take amfani, dan babu gateman a wajen sam. Kai tsaye suka danna hancin motocin nasu cikin gidan a jere, wani tampatsetsen parking space suka nufa, ya haɗu ya gaji da haɗuwa, wasu shegun tsadaddun motoci ne maƙare a parking space ɗin, tamkar companyn kera motoci suka shiga, kowani mota ka ɗaga idanu ka kallah sai ka sake kallah, saboda tsabar kyau. A jere waje guda motocin nasu suka dakata, tamkar abin haɗin baki haka suka kashe motocin gwanin birgewa, tare da fitowa lokaci guda, da alama already sun saba yin hakan ne. Wannan bodyguard na ɗazun da ya buɗewa Sir Arvin kofar mota a office, shi ne nan ya sake zuwa ya buɗe mashi a yanzu ma. Yana buɗe mashi ya fito da sauri ya nufi tsadaddiya kuma haɗaɗiyar elevator su, cikin sauri yake tafiya tamkar wanda ya ƙosa da su iso gidan, kamar wani abin yana jiransa a ciki. Haƙiƙa gidansu Sir Arvin ya wuce baki ya zayyano kyansa, kun fa san yadda ginin Chinawa yake, ba wasa ba! Sun iya tsara gini sosai. A harabar gidan waɗan nan jiga jigan bodyguards ɗin nasa suka dakata cirko cirko kamar masu jiran umurnin su aiwatar da wani abin, su kuma ƴan'sandan nan sun wuce wajen wasu tsadaddun kujeru dake wajen wani tsalelen pili da aka kewaye da glass dan hutawa. Hawa na biyu Sir Arvin ya wuce kai tsaye. Wani irin haɗaɗɗen parlour ne mai girma wadda ya haɗiye luntsuma luntsuman sofas set har kala uku, komai na more rayuwa wadda ɗan adam mai bala'in buri zai buƙata da akwai a cikin wannan gida, dukiya ta yi masu mubaya'a ainun, wani irin azababben daddaɗar kamshi air freshener ne mai bala'in daɗi ne yake tashi a cikin parlourn, tsayawa zayyana maku kyan parlour ma ba zai yiwu ba, dan duk iya misalin mai misali ba zai iya misilta haɗuwar wannan parlour ba. Yana sanya kafarsa a cikin parlourn wata kyakkywar yarinya mai matukar kyan gaske ta miƙe daga saman sofar da gudu ta nufo shi, jikinta na sanye da gown white color, iya cinyoyinta gown ɗin ya tsaya, ga gashin kanta tamkar na Arvin ɗin, babu wata banbanci dake a tsakanin fuskarsa da ta wannan yarinya, harta launin kwayar idanunsu da ya kasance sky blue shi ma iri ɗaya ne, sak dai shi ɗin take, tana rike da ƙatuwar chocolate a hannunta, sha take yi ta ji kararrawar kofar parlourn ta yi kara, alamar za'a shigo kenan, dama haka kofar take, kun fa san China karshe ce wajen kera abubuwa, to kofar shiga parlournsu ma idan aka taɓa za'a shigo sai ya sanar da waɗan da suke ciki cewa za'a shigo, duk da cewa kofar tana amfani ne da card or fingerprint, amma da zarar an taɓata sai ta sanar da na ciki ana shigowa. Da gudu yarinyar ta tafi ta faɗa jikinsa tana yi mashi oyoyo. Tamkar ƴar baby haka ya ɗagata sama yana kallon face nata, sai sakin uban murmushi take yi baki duk chocolate. "Pinky where's mum?". Ya faɗa can kasa kasa. "She's inside her bedroom". Bai sake ce mata ko uppan ba ya wuce da ita zuwa wani katafaren haɗaɗen stair case, wanda yake amfani da remote, sai ka danna remote zai fito, idan ka hau zai koma ya naɗe kansa ya haɗe da p.o.p tamkar babu shi, ba zaka taɓa cewa da akwai stair case a wajen ba. Yana hayewa wata katafaren parlour ya sake shiga, parlourn sak na kasar nan, sai dai shi wannan komai na cikinsa light ash ne na kasan kuma golden brown. Cikin bed nasa ya wuce da ita a saman kafaɗarsa. Ya ilahi ya lillahi, wannan bedroom shi ake kira da karshen haɗuwa, katafaren king bed nasa ma kawai abin kallo ne, bare kuma sauran kayan more rayuwa da suke a ciki, Chinese carpet dake gaban bed ɗin tamkar audiga haka yake, duk in ka taka sai kafarka ta lume, wajen mirrornsa kawai ya ci rabin bango guda na ɗakin, dressing room nasa da glass aka yi ta tamkar na Lion, bedside drawers ɗinsa kusan irin na Lion, haka zalika lamp dake a saman bedside drawers ɗin suma haka, sai dai nasa milk color ne na Lion white, wani shegen bed sheet ne wanda ya amsa sunansa bed sheet na alfarma, shi ne shumfuɗe a saman bed ɗin, ga wasu kyawawan pillow masu matukar kyau da ɗaukar hankali. Saman bed ɗin ya ɗaura Pinky tare da zama a gefenta ya fara cire tsadaddun covers ɗin da suke a ƙafarsa. Bayan ya kammala ya miƙe ya nufi toilet ya barta a wajen. Karisa hayewa saman bed ɗin ta yi tare da jawo pillow ta rungume, sannan ta cigaba da shan chocolate ɗinta. After some minutes ya fito cikin wasu tsadaddun pajamas launin blue color, sai tashin wani fitinannen kamshi yake yi, har lokacin Pinky na kwance mashi a saman bed. "Let's go and eat Pinky". Ya kai karshen maganar tare da nufar hanyar fita bayan ya sanya bedroom slippers a kyawawan kafafunsa, har lokacin babu alamar dariya a tattare da shi. Da sauri ta diro kasa daga saman bed ɗin, da gudu ta tafi ta rungume shi ta baya, duƙa mata ya yi, a hanzarce ta haye saman bayan nasa, ya fita tsawo sosai ne yasa bata iya hayewa saman bayan nasa ba sai da ya duƙa mata, goyata ya yi tare da miƙewa tsaye suka nufi waje. Kai tsaye dining room ya nufa, rayuwarsu sak kusan irin na gidansu Lion. Yana zuwa ya sauketa, dining room ɗin nasu ma duniya ne, kusan kamar na gidansu Lion, sai dai banbancin colors kawai, saman katafaren dining table ɗin shaƙe yake da abinci kala kala, kun san su suma basu girki kala ɗaya, sai su yi wajen kala goma ko sama da haka lokaci guda, ga kuma fruits a jere makil a wajen. Wasu bodyguards guda uku ne suke tsaitsaye a wajen dining table ɗin, jiran umarni kawai suke yi su fara zuba abinci, sanye suke cikin suit bakake, fuskokinsu a ɗaure tamau alamar aikin gabansu kawai suke yi, babu wasa a tattare da su. Saman haɗaɗiyar table chair ɗaya ya ɗaura Pinky kafin shi ma ya zauna a nasa chair ɗin kusa da ita. Ko da ya zauna sai da ya ɗauki 10mins kafin ya bawa bodyguards ɗin umarnin da su zuba mashi kalar abincin da yake buƙata, har a lokacin kuma tunanin Lion ne fal a cike a cikin ransa, yarasa dalilin da ya sanya ya ji yana matuƙar kaunar Lion ɗin, da kallon farko ya ji tamkar ya ɗaga jirgi zuwa U.s suka ga juna ido da ido, dan ya kara tabbatar da wannan kamannin nasu shin da gaske ne ko dai a hoto ne? Haƙiƙa zuciyarsa ta kamu da kaunar Lion, burinsa kawai ya je wajensa koma ta halin yaya. BABBAR MAGANA TAB!!!!. Abincin kawai yake ci, amma hankalinsa kwata kwata baya wajen, yana kan tunanin Lion, barema da ya dawo gida ya kalli Pinky, sai abin ya kara tsaya mashi a rai sosai, dan sai ya kalleta tamkar Lion ɗin ya kallah. Wani kyakkyawan matashi ne ya shigo dining room ɗin, shi ma sanye yake da pajama launin black color, sai tashin kamshi yake yi, yana kama da su, sai dai ba sosai ba, kuma shi launin idanuwansa brawn color ne. Saman table chair ɗin ya zauna yana faɗin "Good afternoon bro". Da kallo sir Arvin ya bishi ba tare da ya amsa ba, Pinky ce ta ce "Good afternoon brother Handsome". Da yake yana a kusa da ita sai ya kai hannu ya shafa kanta kafin ya bawa bodyguards ɗin umarnin da su zuba mashi abinci. "Where's mum?". Handsome ya tambaya yana ɗaura wayarsa a saman table ɗin ta gefe. "Mum she's inside her bedroom". Pinky ta bashi amsa. Abinci suka cigaba da ci cikin nutsuwa da kula, babu wanda ya sake yin magana daga cikinsu. After some minutes wata ƴar caras cas ɗin mata ta shigo cikin room ɗin, tana sanye da doguwar riga mara nauyi mai matukar kyau da tsada, launin pink color, ƴar kyakkywa da ita, ga kyan jiki, da ganinta kasan ƴar China ce, sam bata yi kama da Arvin ɗin ba, ta dai yi kama kaɗan da Handsome. Handsome da Pinky har suna haɗa baki wajen cewa "Welcome mummy". Idanuwanta na'a a kan Arvin da yake ta faman tura abinci tamkar wadda aka yi wa dole, sai faman yamutse fuska yake yi. "Son what's going on? What's wrong with you?". Cewar mum ɗin, ta yi maganar tare da zama a saman chair dake kusa da Handsome. "Nothing" ya amsa mata da shi tare da miƙewa yana mai ɗaukar tissue daga wajen ajiyewa, hannunsa da ɗan ƙaramin kyakkywar bakinsa ya goge, sannan ya nufi barin wajen. Binshi da kallo ta yi har sai da ya fice, sannan ne ta dawo da kallonta a kansu Handsome tana faɗin "What's going on here Handsome?". Girgiza kai ya yi yana faɗin "Mum i don't know anything, yanzu na dawo nima". Miƙewa ita ma Pinky ta yi tare da ɗaukar tissue ɗin ta goge ɗan bakinta, sannan ta jefa tissue a cikin kyakkyawan dustbin dake wajen, da sauri ta bi bayan sir Arvin, su kuma suka cigaba da cin nasu abincin. Da alama Pinky ta yi muguwar sabo da sir Arvin sama da kowa a cikin gidan. A bedroom nasa ta isko shi kwance yana rike da tsadaddiyar wayarsa, hoton Lion yake kallo a news. Tana zuwa ta kwanta kusa da shi tana ɗauko ɗayar wayar tasa dake saman bedside drawer. "Pinky come and see something" ya faɗa tare da buɗe hoton Lion ɗin sosai. Da sauri ta kara matsowa kusa da shi tare da kwantar da kanta a saman kirjinsa. Hoton Lion ɗin ya nuna mata yana faɗin "See this pic". Zaro dara daran blue eyes nata ta yi tana faɗin "Is it not you?". Girgiza mata kai ya yi alamar ba shi bane. Kara zaro idanu ta yi sosai, da wata ƴar muryarta ta yara a wajen ta ce "Who's he? He look like you over". Fita daga kan hoton ya yi yana mai kara tabbatar da kamanin nasu tun da har Pinky ƴar karamar yarinya ma ta iya gane cewa sunyi kama over, to ba shakka ba gizo idanuwansa suke yi mashi ba, gaskiya ce wannan hoton tana muguwar kama da shi. Sake tambayarsa wanene a jikin hoton Pinky ta yi, hannu ya kai yana shafa gashin kanta zuwa bayanta yana gaya mata shi ma bai san shi ba. Da sauri ya miƙe zaune tana mamakin ya aka yi suke kamata to kuma basu san shi ba?. Hannunta ya jawo ta koma ta kwanta kawai, wayar tasa ya kunna yana gaya mata tazo su yi game, dan ya mantar da ita zancen Lion, yasanta sarai zata je ta gayawa su Handsome abin da ta gani, idan ta gaya mashi kuma zai zo ya takura mashi da tambayar wanene Lion ɗin, so gara ya ɗauke mata hankali da buga game. Murmushi ta fara yi kyawawan farare hakwaranta tas suna bayyana, sai ka rantse da Allah bata taɓa cin abinci ba, saboda hasken hakwaran nata. Game ɗin suka fara bugawa na wasu baloon a cikin ruwa har barci ya ɗauketa. Ganin ta yi barci ne yasa ya ajiye wayar a saman bedside drawer tare da gyara mata kwanciya da kyau da kyau a kusa da shi, sannan shi ma ya jawo pillow ya gyara kwanciyarsa da kyau, ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi. A ɓangaren su mum da Handsome kuma, sai da suka ci suka ƙoshi sannan suka bar dining room ɗin, ita mum ta wuce nata bedroom ɗin, shi kuma Handsome ya wuce parlourn kasa. A ɓangaren su Lion kuwa, a wannan dare dai sun yi barci cikin rashin daɗi daga shi har Rimshar, washegari da safe misalin karfe 9 na safe, shirye cikin tsadaddun kaya iri ɗaya Lion da Areef suka fito, komai na jikinsu iri ɗaya ne, sai suka fito a ainahin TRIPLETS nasu, harta black glass da yake a face nasu iri ɗaya ne, idan ba ka lura da kyau ka ga gashin kansu ba, to ba zaka iya banbantasu ba, saboda jini ya wuce wasa, sai kuma Lion ya fi tsawo da cika. Sun yi matukar kyau na wuce misali, bedroom na daddyn Rimsha suka fara shiga. Jim kaɗan suka fito suka nufi bedroom ɗin Aseef. Yana ta zuba barcinsa, zuba mashi idanu suka ɗan yi suna kallonsa, bawan Allah yana sanye cikin tsadaddun kayan barcinsa, riga ce da wando launin ash color, ya yi matuƙar kyau, yana rungume da pillow a kirjinsa, da alama dai hira da Heartbeat suke yi barci ta yi awon gaba da shi. Saman bed ɗin suka hau kusan a tare, sumbata Lion ya fara kai mashi a saman lallausan kumatunsa kafin ya kai hannu ya ɗaga mashi wayarsa da take a kusa da kirjinsa, juyo da screen ɗin wayar ya yi izuwa face nasa, har lokacin call ɗin bata yanke ba, da alama ita ma Akilar ta yi barci ne suka bar wayar a kan call. Katse kiran ya yi tare da ɗaura wayar a saman bedside drawer yana mamakin halin Aseef, shi dai soyayya kawai abinsa, bashi da wata damuwa a rayuwarsa, baya tunanin matsalar kowa da komai, baya ajiye wata damuwa a cikin ransa, kawai harkar gabansa na hira da Akila su kashe juna da love shi ya sa a gaba.........(😂 Allah ya yafewa Aseef ya shirya mana shi😂) Sumbatarsa Areef ɗin ma ya yi a saman jajir ɗin kumatunsa dai'dai in da Lion ya sumbacesa, sannan suka diro kasa daga saman bed ɗin a tare. Fitowa suka yi suka nufi harabar gidan mai gabaɗaya. Already anfitar masu da motoci anjerasu layi biyu dan zuwa airport, tsayuwa suka yi a harabar gidan, sannan suka juyo suna fuskantar juna gwanin birgewa. Areef ne ya fara magana cikin nutsuwa. "Please Lion idan ka sauka ka kira Rimsha a waya, ina son ka san abu guda, Rimsha tana sonka ne yasa ta damu da kazo in da take, idan ba tana sonka ba wlh ba zama ta damu da tafiyarka ba, kayi tunani da kyau, she love you over and then su mata ƴan a lallaɓa ne, ita fa Rimsha ma ka yi sa'a tana da hankalin manya, banda haka da wlh yarinya under 15 ba zata iya ɗaukar abin da Rimsha ta ɗauka ba, wata ma mai 30 years idan ta zuba maka wata shirme Allah sai ka ji kamar ka kasheta dan haushi, kuma serious ka sani ko mace mai 30 years ba zata iya ɗaukarka ba, amma duk zafin zuciyarka Rimsha ta danne, tsawon shekaru tana azabtuwa a kan sonka! Kasan da haka, and then ka duba abin da ya faru a tsakaninku 30 days back, a gaskiya ta yi mugu mugun ƙoƙarin da baki ba zai iya faɗa ba, now kaga bata da lafiya, please kada ka kara mata ciwo a kan ciwo, wannan mu zaka yi wa ba kanka ba, idan wani abin ya sameta ba zamu iya jurewa ba, please ka yi tunani a kan maganar". Ya kai karshen maganar yana ƙoƙarin ciro wayarsa daga aljihunsa. Matsowa Lion ɗin ya yi suka rungumi juna kawai ba tare da ya yi magana ba, sumbata Areef ɗin ya kai mashi a kumatu kafin shi ma Lion ɗin ya sumbacesa. "Take care". Shi ne kawai abin da Lion ɗin ya furta tare da sakinsa ya wuce izuwa wajen nasa jerin motocin. Juyawa shi ma Areef ɗin ya yi ya nufi nasa motocin. A tare motocin suka fice daga gidan. After some minutes suka sauka a airport, jirgi daban daban suka shiga, Lion ya shiga jirgin kasar China, shi kuma Areef Nigeria zai je, amma da yake jirgin kasuwa ya bi, sai ya bi jirgin Spain, daga can zai hau jirgin Nigeria, shi kuma Lion da yake da nasa jirgin zai tafi, sai ya zama direct kawai zai nufi China, dama idan baku manta ba ya taɓa cewa Rimsha zasu je kasar China da ita, so yanzu yanayi yasa ba zai tafi da ita ba, kun ga dai halin da take a ciki, tafiya da ita ba zai yiwu ba, suna ma wajen daban daban da ba zai yiwu su tafi a tare ba, shi ne yasa ya wuce shi kaɗai. Shi kuma Areef zai je ya ɗauko su gwaggo ne gabaɗaya, Lion ya ce duk su tattara su dawo, shi ya sallami Nigeria kenan, ba zai sake komawa ba, so Areef ya je ya tattarosu su haɗu a U.s kawai nan da kwana uku zuwa biyar......... Babbar magana, akwai aiki kam!!. After some hours. Lafiya lou Lion ya yi landing a Daxing international airport Beijing dake a South Beijing ɗin. Da yake shi da wasu daga cikin bodyguards nasa kawai suka zo, sai ya ce da bodyguards ɗin su fita su nemi hotel su zauna a ciki yana zuwa, idan ya kammala abin da yake yi zai nemesu, ya yi maganar tare da sanya face mask a face nasa, sannan ya fito daga cikin jirgin bayan. Yana fita kai tsaye wajen masu taxi ya nufa da yake a wajen airport ɗin, kun san kasar China da abin hawa kala kala, wata ma sai ka saki baki ka ɓata lokaci kana kallonta, sam su basu gajiya da kere kere, Allah ya yi masu fikira da basira ne over. Wata kyakkyawar taxi ya hau, kai tsaye address na *GOLD CROSS HOSPITAL (GCH)* ya ce a kaisa. Su kuma bodyguards ɗin nasa suka fito tare da trolleynsa suka nufi waje dan su je su aiwatar da umarnin da ya ce masu su yi na neman hotel. Lion baka gane gabansa baka gane ina ya dosa, yanzu duk rikicin da tarzomar da ya haɗa a U.s ya tashi kura, hakan bai hana shi ya shiryawa kansa zuwa kasar China kamar yanda ya yi niya a baya ba, yana da karfin hali sosai, komai zai aikata yana aikatawa ne cike da kwarin gwiwa ɗari bisa ɗari tare da yakiyi da kuma sanyawa a ransa tabbas zai yi nasara, ba komai ne yasa hakan ba kuma face rike Allah a zuciyarsa da ya yi, komai zai yi Allah yake fara sakawa a gaba, shi ne yasa yake samun kwarin gwiwar na cewa zai yi nasara a komai, kuma ya yi gaskiya, duk wanda ya saka Allah a gaba, to babu abin da zai hana shi yin nasara, babu wata barazana da zata tsorata shi, babu wata shamaki da zata gifta a tsakaninsa da nasararsa, shiyasa a koda yaushe TRIPLETS namu suka zamana masu yin nasara a rayuwarsu!! Allah ka bamu dacewa. Kafin ya tako kafarsa a cikin ƙasar China, sai da ya shiryawa kansa komai da komai, harta in da zai je sai da ya nemo address, ya jima yana bincike a kan Cherish, tun lokacin da ya gano cewa an canza ɗaya daga cikinsu, idan baku manta ba tun bai zo U.s ya ji gaskiya a wajen kakansa ba ya yi maganar zuwansa kasar China ya nemo Cherish, so tun a lokacin ya fara bincike a kanta, duk wata hukunci da ya yanke har da shiga siyasa da ya yi, duk basu hana shi yin binciken nasa ba, dama after primary election ya tsara zai shiga ƙasar ta China, to shi ne ya cika abin da ya tsara a yau. Yau dai ga mai kama da Arvin a cikin Beijing, ga kuma shi ma Arvin ɗin a nan, dama yana cewa zai je U.s ya haɗu da mai kama da shi, za su haɗu ko ba za su haɗu ba? Idan sun haɗu ya haɗuwar zata kasance?..... PRINCESS TEEMA ce kawai zata iya gaya maku wannan amsa!!. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 15/5/2024 E32 Dedicated to Halimatus Sadiya ƴar amanar Jehan ❤️ yau dai amanar Jehan page ɗin naki ne😂 A ɓangaren shi ma Areef ya sauka Nigeria lafiya lou, Tga ne ya zo airport ya ɗauke shi zuwa gida. Sam Jehan bata san da zai zo ba, bata da labari, tana can tana fama da zazzabin sonsa kamar zai kasheta, amma taki sauƙa daga kan bakarta. Yana zuwa bedroom nasa ya wuce, duk da bashi da burin da ya wuce ya kalleta ɗin, amma kuma bai je in da take ba, sai ya wuce bedroom nasa. A ɓangaren ita kuma Rimsha, sosai ta kara jin haushin Lion, saboda yadda suka kwana suka tashi bai nemeta ba, bata yi zaton haka daga gare shi ba, hakan yasa ta kara ji a ranta da gaske cewa baya sonta, kowa ya sani tana bala'in sonsa na kin karawa, baki ma ya yi kaɗan ya iya zayyana yadda take son shi. Hakan yasa abin ya yi mugun taɓata sosai, har wani irin zazzaɓi mai zafi gaske take ji, idan baku manta ba ita fa time da daddynta ya hana ta kallon shi a Tv tun suna Abuja bata kai haka ba ma, sai da ta kwanta a gadon asibiti, a lokacin ma bata san menene matsayarsa a wajenta ba, bata san cewa tana son shi ne ko dai iya burgewa ɗin bace ba, bare kuma yanzu da ya zama mijinta, suka zama abu guda, ta saba da shi, soyayyarsa ya karu a zuciyarta na wuce misali. Sai abin ya yi muguwar jijjigata, sai dai fa wani abu guda game da ita wanda nasan tabbas kun manta da shi, duk daɗi duk wuya, duk yadda Rimsha ta kai ga son abu, to fa bata jurar walaƙanci a kan wannan abin, nasan dayawanku kun manta zamanta a Ilorin kwara State, to PRINCESS TEEMA dai ban manta ba ni, kuma bari na tuna maku, time da kausar ta yi mata walaƙanci a kan abinci, a haka ta zauna da yunwa duk da Iya Kausar ɗin ta ce tayi hakuri ta ci, amma taki ci sai dai suka sayi drinks ita da Ayla, time da Kausar still ta sake yi mata rigima a kan kayan sakawarta, kun tuna ta ce ba zata sanya kayar ba, har ta ɗauko tsohon nata ta saka, kun tuna? Bugu da kari kunsan saboda ba zata iya jurar walaƙanci bane ba yasa suka baro gidansu Kausar, duk da abin ya haɗu da yi mata fyaɗen da Borda Jami'u ya so ya yi, so haka zuciyarta take, ba zata iya jurar walaƙanci ba, wasu abubuwa da kuke gani take yi wa Lion, sau da dama Malika ce take sanyata yi, amma banda haka ko shi ɗin ba bazata ɗauki walaƙanci daga wajensa ba, haka ƴaƴan Nawazuddeen suke, Malika tasan cewa shi Lion tamkar bugun zuciyar Rimshar ne, already ta yi saurin kamuwa da sonsa tun kananun shekarunta, so hakan yasa ta tayata yakin neman soyayyarsa, badon taimaka mata da ta yi ba, da ko kusa ko alama Lion ba zai so ta ba, Malika tana kaunarta sosai yasa take kaunar duk abin da take so, idan baku manta ba Rimsha bata sanya kananan kaya, bata sanya irinsu wandunan Jeans da sauransu, har Kausar tana mata horo da su idan bata son ta sanya mata kaya, amma baku yi mamakin meyasa take sanya kananan kaya a gidan Lion ba? Tun kuma basu fara soyayya ba, to Malika ce take sanyata sakawa saboda wasu dalilai guda biyu, na farko shi Lion bai ma san irin dressing na Hausawa ba, kuma ba kyau zata yi mashi ba ko da ya gani, saboda su a al'adarsu kowa ya sani mace ta bayyanar da surar jikinta shi ne kyau da birgewa, so idan mace bata yi hakan bama su ganin mahaukaciya mara sanin abin da take yi suke yi mata, kada ku ga laifinsu haka al'adar duk wani Bature yake, in ma musulmi ko Kristen, duk tafiyarsu kusan ɗaya ce, banbancin kawai ibada ne, wani Baturen ma idan ya kalli mace da common doguwar riga ce har kasa, tambayarta zai yi anya yau kanta lafiya kuwa? Ko dai mijinta ne ya mutu? Yasa ta sanya buyagin haukar da ta sanya a jikinta nan? So haka suke rayuwarsu tun iyaye da kakanin, na tabbata koda baku taɓa zama a cikinsu ba, to kuna kallonsu a Tv, yadda kuke ganinsu a Tv ma abin wasa ne, rayuwarsu ta zahiri ta fi hakan, a Tv ai sai sun kawata shi yadda zai ja ra'ayin ƴan kallo, kuma wani lokaci a film suna yin abin da zai ja ra'ayin jama'a ce kawai dan su cigaba da samawa kasarsu kuɗin shiga, banda haka rayuwarsu ta zahiriya ma ai ya ninninka haka, wannan dalilin yasa Malika take sanyata yin dressing irin nasu, dan kada ya ganta da shigar hausawa ya yi mata kallon wata mahaukaciya mai tsummokarai a jiki. Abu na biyu kuma Malikar ta yi amfani da rauninsa ne a wajen, tasan dayawan Turawa suna bala'in son mace mai shape, baya da kuma breast tula tula, abin yana tashin kansu sosai, so idan Rimsha tana sanya irinsu a baya ba zasu fitar mata da shape nata ba, hakan yasa ta sanyata rinƙa saka irin waɗan nan kaya, kuma ta dalilin hakan ne ya ja ra'ayin Lion ɗin, yana tsananin kaunar shape na Rimsha sosai, tudun mazaunanta ba ma sai na yi magana ba, kunsan yana bala'i sonsu, barema kuma tula tulanta, kunga kuwa Malika ta kafa mashi tarko ne kuma ya afka ba tare da sanin shi ba, Malika ta yi abubuwa da dama wa Rimsha wanda baki ba zai faɗesu ba, wasu lokuta idan Rimshar ta yi wani abin da bata saba yi ba, ko kuma ba'a al'adarmu ta Hausa Fulani ba, to idan kuka bincika da sa hannun Malika, ba komai yasa Malikar ta taimaka mata ba a lokacin face dalilai guda biyu, na farko tasan Rimshar ta yi shigar sauri wa soyayyar Lion ɗin, kuma tabbas a kansa tana iya mutuwa, dan idan baku manta ba ta sha suma a kansa sosai, na biyu kuma a time ɗin tana da matsala a ƙwaƙwalwarta na razana da birkicewa da ta samu daga Daular Mutuwa, abu kaɗan yana razanata ta suma, sai abin ya zo ya haɗe mata da soyayyarsa, wanda idan ba'ayi dace ba tsab zai kasheta har lahira, hakan yasa Malikar ta taimaka mata sosai dan tana kaunarta da iya gaskiya, ita ɗin aljanace mai mutunci kuma bata manta halacci, dama dayawan al'janu basu manta halacci a rayuwa, nasan kowa tana son sanin wacece Malika, lokacin sanin hakan ya kusa zuwa, zata gaya maku wacece ita da kanta. So a wannan karon fushin da Rimshar ta yi ma da sa hannun Malika, ba wai kuma ta tayata yin fushin bane, a'a, dama kun san ita Malika a koda yaushe ita take ƙoƙarin ɓoyewa Rimshar duk wasu laifuka da Lion ya yi mata a baya, sai ta rufe mata idanu ba zata taɓa damuwa da laifin ba, ita dai soyayyrsa kawai ta sani, a lokacin tana yi mata hakan ce saboda ta ceci rayuwarta, sannan kuma su danne komai su hakura dan su sami soyayyarsa, banda haka da wlh Rimsha ba zata ɗauki wasu abubuwa da ya yi mata a bayaba, saboda bata da zuciyar jurar walaƙanci ko kaɗan, ba zata iya ɗauka ba. So a yanzu da Malikar ta fahimci Lion fa ko zai mutu ba zai dai'na son Rimshar ba, ta rigada ta zama jinin jikinsa, shi ne yasa sai ta tsame hannunta daga lamarinsu ta koma gefe guda tana kallon masoyan tana jin daɗi abinta, shiyasa Rimsha ta kalli laifinsa a wannan karon, shiyasa ta kalli kamar walaƙanci ya yi mata, hakan yasa ta ce ko zata mutu ba zata ɗauki hakan ba, shiyasa ta ɗauki fushi mai zafi da shi, dama mai hakuri bai iya fushi ba, idan ka kure mai hakuri to wlh ka kuka da kanka, dan sai ka ɗanɗani bakinciki, ga shi kuma ya kara ɓata mata rai yadda ya kwana ya tashi bai kirata ya rarrasheta ba, abin ya kara baƙanta mata rai, sai take ganin ai walakancin ya yi yawa over. Shi kuma har ga Allah ba wai baya son kiranta ɗin bane, dannewa kawai ya yi bai kira ɗin ba, saboda abin da ya sanya a gabansa, a wannan point da yake a ciki sam baya son ya biye mata, dan zata caza mashi kai sosai bayan wanda yake ciki, shi ne dalilin da yasa ya danne ya jure ya kyaleta ɗin, amma shi da kansa yana ji a jikinsa, har wani zazzaɓi shi ma yake ji na barinta a cikin damuwa da ya yi, tun daren jiyan yasan bai kyauta ba, bayan abin ya faru da ya kwanta zai yi barci, zuciyarsa ta ɗan yi sanyi, shi da kansa yasan bai yi mata adalci ba duba da yanayin karantar shekarunta, bai kamata ya haɗa hankalinsa da nata ba, kuma gaskiya Areef ya gaya mashi, son shi yasa take damuwa da shi, idan da bata son shi ko zai shekara miliyan bai zo in da take ba, ba zata taɓa damuwa ba, bugu da kari kuma ga abin da ya yi mata 30 days back, ta bakin mommar tasu yanzu ne yakamata ya lallaɓata ya biyata dakon soyayyarsa da ta yi na tsawon shekaru, so a takaice dai shi da kansa yasan sam bai kyauta mata ba, ya danne zuciyarsa ce kawai ya kyaleta sai ya kammala aikin da yake gabansa, idan sun haɗu a U.s sai ya ɗauki kayansa ya lallaɓata, sai dai fa bai sawa ransa cewa zai bata hakuri ba, babu wannan tunanin a ransa, tunaninsa dai shi ne idan sun haɗu a U.s ba shikenan sun ga juna ba? A tunaninsa daga haka zata sauko su koma normal, abin da bai sani ba shi ne ita fa a wannan karon da gasken gaske take yin fushin nata, babu alamar zata sauko ma, dan ta zo har wuya, ga Malika ta zame hannunta, ta bar Rimshar ta ɗan wanashi kaɗan, wata kila daga haka ya fara sanin darajar mum da dad ɗinta, dan abin yana bakantawa Malikar rai yadda Lion ɗin yake yi wa mum da dad ɗin, sam bata so, to ita ma kenan, bare kuma Rimsha da take ƴar cikinsu, ai idan ta sani zasu yi yaki da shi ba kaɗan ba, dan wlh zata iya rabuwa da shi tsab akan iyayenta, barema mum ɗinta, bazata iya jurar wani ya yi masu walakanci ba. Shi kuma Lion a zahirin gaskiya sam ba wai walaƙanci yake yi masu ba, a haka yanayinsa yake, idan zaku yi wa kanku adalci, ai ba iya mum da dad yake yi wa hakan ba, harta Dr William a time ɗin bai bari ba, ya yi wa Abbansu Imran, kuma ai Imran babban abokinsa ne wanda ma bashi da biyunsa a duniya, bugu da kari kuma ta dalilin Imran ɗin suka musulta, amma ya yi iyayen Imran ɗin hakan tun kafin ya yi wa iyayen Rimsha, ya yi wa Uncles nasu da kakanninsa na kasar Russia, su Uncle T da uncle Herry kam ma ai ba'a maganar irin walaƙanci da ya yi masu, shi fa bai bar kowa ba, taka kowa yake yi ya wuce, so su daddy dan sun bashi auren Rimsha ne yasa nasu yafi damun mutane, banda haka ai shi Lion haka halinsa yake tun ainahi, kuma ai ba shi kaɗai bane ba, harta Aseef idan kuka lura haka halinsa yake, baya damuwa da mutane, kuma baya ɗaga idanu ya kalli mutane, soyayyar Akila ta koya mashi sanin darajar wasu daga cikin mutane, a hakan ma ba kowa yake gani da daraja ba, so shi Aseef idan kuka nutsu zaku fahimci babu in da ya baro Lion ɗin a wasu ɗabi'u, shi dai kawai soyayya ce ta yi saurin canza shi, amma shi ma me bai yi wa su Uncle T ba? Ai shi ma ya yi abubuwa son ransa, so haka ƴaƴan Dr William suke, Areef ne ya fita zakka saboda yanayin aikinsa shi ma, banda wannan aiki da shi ma ai irinsu zai taso, dan kusan kaso 80 cikin ɗari na ƴaƴan turawa haka suke tasowa babu sanin darajar nagaba da su, hakan ba laifin TRIPLETS bane, laifin daga kakannin tile tile ne, amma abin da baku sani ba shi Lion yana bala'i son daddyn Rimsha na wuce misali, baku yi mamakin yanda ya ce daddyn Rimsha ya zo U.s su zauna ba? Haka kawai ai ba zai saka shi ya taso ya zo ba, yana bala'in sonsa, a duk duniya waƴan da ya fi so a yanzu, daga mommansa, TRIPLETS nasa sai Rimsha da iyayenta, kamar yadda yake sonta haka yake son parents nata, yana son ganin daddynta a kusa da su, tun kafin ya san cewa daddynta ne ma yake Kaunar Nawazuddeen har cikin ransa, kawai dai shi dai ba zai girmama kowa bane, wannan ita ce matsalarsa da yasa ake ganin kamar baya son parents ɗin nata, amma yana kaunarsu ta yanda baya son sam sam ma su yi nisa da daddyn nata, saboda daddyn nata yana gaya masu gaskiya, idan Areef ko Aseef suka yi ba dai'dai ba, baya ɓoye masu, yana gaya masu sun yi kuskure su gyara, so Lion ɗin yana sane da komai, hakan yasa ma yake kara son daddyn, shi ne dai bai bawa dad ɗin fuskar da zai gaya mashi gaskiya ba, da har shi dad ɗin ba zai bari ba sai ya gaya mashi, dan kowa yasan daddyn Rimsha mutun ne mai gaskiya, zuciya da kuma sanin yakamata, kuma zuciyar ce ma tasa basu shiri da Lion ɗin, in dai suka zauna inuwa guda sai sun yi faɗa, dan dad shi ma akwai izza, ga zuciyar bala'i, kunaga tun da ya yi fushi ya bar gidansu sai da ya haura sama da shekaru 30 bai sake leƙa in da suke ba, bai kula kowa daga cikinsu ba, ai daga nan ma ya isa ayi shiru a kan zancen zuciyar Nawazuddeen, dole Jehan da Rimsha su yi gado, dole Jehan ta zama haka, ga kari daga wajen gwaggon ta samu, ai abin ba'a magana. AREEF Misalin karfe 9 na dare, sanye cikin kayan barcinsa masu kyau da tsada launin black color, ya fito daga cikin bedroom nasa, sai zuba uban kamshi yake yi. Kai tsaye ɗakin mommansu ya nufa. Bakinsa ɗauke da sallama ya shiga cikin ɗakin, tun da ya zo bai leƙota ba, yana zuwa ya hau yin barci, sai bayan mangariba ya tashi ya yi wanka tare da yin sallah, ya shirya cikin kayan barci, sannan ne ya fito ya dan ya je ya gaisheta. Rimsha, Jehan, Aafia, duk suna kwance a saman gadon gwaggon, Akila tana ɗakinsu suna aikin da suka saba na waya da Heartbeat ɗinta. Duk cikinsu Aafia ce kawai mai ƙoshin lafiya, Jehan kam ba'a magana, ta yi wani uban rama sai kwala kwalan idanu farare tas zaka gani a face nata, ita ma Rimsha abin ya ɗan taɓata, sai dai ta danne, hakan yasa ma ta baro ɗakin Lion ɗin ta dawo na gwaggo abinta, dan ma kada ta tuna shi. (Rimsha manya, wai dan ma kada ta tuna shi😂 kaji dayawa a wajen Meeshan Noorish 😂 waɗan nan masoya suna yin son ransu ni kuma ina shan Maltina mai sanyi 🥱) Gwaggo na zaune a saman bed ɗin ta gefe tana shafa kan Rimsha tana kuma tambayarta meyake damunta a yanzu, sam taki gaya mata abin da yake faruwa, sai ta ce mata babu komai, ita kuma gwaggon ta yi masu farin sani dukkansu, tana ganin damuwa karara a kwance a fuskarta amma zata ce mata babu komai, shi ne take lallaɓata tana nuna mata fifikon shekaru dan ta sanyata ta gaya mata meyake damunta. Jin sallamarsa yasa suka ɗago kai dukkansu, ai Jehan bata san time ɗin da ta miƙe zaune ba, har wani kyafta idanuwanta ta yi, dan ta tabbatar da shi ɗin ne ko dai mafarkinsa da ta saba yi ne?. Shi ma satar kallonta yake yi ta kasar ido, amma da yake ya iya duniyanci, sai ya yi kamar gwaggo yake kallo ba ita ba, dan suna kusa da juna, ji yake yi kamar ya je ya rungumeta, yana kewarta over. Tsare shi da idanu ta yi har ya ƙariso ya zauna a saman bedside drawer, a nan ne gwaggon ta fahimci da matsala kenan a tsakaninsu, wato ɓoye mata suka yi, duba da yanayin irin miƙewar da Jehan ɗin ta yi daga jin voice nasa, da kuma irin kallonsa da ta yi har ya ƙariso cikin ɗakin, sannan shi ma gwaggon ta ga yana satar kallon Jehan ɗin, hakan yasa ta gano akwai wata aka sa. Ɗan kawar da kanta gefe guda Rimsha ta yi, dan ita ko su Areef ɗin ma yanzu bata son gani, saboda dukkansu abu guda ne da Lion ɗin. Sarai Areef ɗin ya ganta abin da ta yi, sai dai kuma ko kaɗan bai ga laifinta ba, ai tama yi ƙoƙari sosai, ta cancanci a jinjina mata. "Good evening momma". Ya faɗa cikin sanyin murya yana mai cigaba da satar kallon ƴar diramar tasa. Jin voice nasa yasa ta sauke nauyayyar ajiyar zuciyar da har sai da ya sanya su gwaggon zuba mata idanu, hakan ya kara tabbatarwa da gwaggon tabbas akwai matsala a tsakaninsu, amma sai bata nuna masu ta gane ba, ta amsa mashi da "Ya hanya? Ya ka baro mani autana da kuma Nawazuddeen?". "They are all fine ya yaranki". Ya faɗa cikin zolaya yana mai ɗago da idanuwansa gabaɗaya ya saukesu a kan Jehan ɗin, dan ya kallin face nata da kyau, satar kallonta da yake yi nan bata wadace shi ba, ta yi mashi kaɗan. "Yarana ina fama dasu mana, bagasu nan a kewaye dani ba". Ta bashi amsa. Sai dai a lokacin sam bai ji amsar tata ba, dan ya afka tekun soyayya, ya tsare babynsa da dara daran idanuwan nan nasa, ita ma kuma kallonsa take yi, ta kasa kawar da kanta kamar yadda shi ma ya kasa, tamkar wasu magnet haka suka ji wata iriyar soyayyar juna yana fisgarsu da karfi. Kawar da kallonta daga kansu gwaggon ta yi tana mamakin meyahaɗasu faɗa ne dama?. Ita kuma Rimsha lumsshe idanuwanta ta yi, dan ma kada su haɗa idanu da shi. Aafia kuma miƙewa ta yi ta nufi waje tana faɗin tana zuwa, dukkansu kayan barci ne a jikkunansu, dan sun yi shirin kwanciya ne. Sun ɗauki saman da 10mins suna kallon juna ba tare da sun furta ko uppan wa juna ba, wani irin abu ne yake fisgarsu dukkansu biyu, ji suke yi idan basu rungumi juna ba ba zasu sami sukuni ba. Can kamar wanda aka yi wa allura zancen mum ya dawo mashi cikin ƙwaƙwalwarsa, ajiyar zuciya ya sauke tare da kawar da kallonsa daga kanta izuwa kan gwaggon yana faɗin "Momma let me go and eat, am feeling hungry, maybe zan dawo, maybe kuma sai da safe, dan a gajiye sosai nake". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa yana mai do da kallonsa a kan Rimsha, sam baya son ya yi mata magana a daren nan, yasan a kule da haushi take har wuya. Binshi da kallo Jehan ɗin ta yi har ya fice, ji ta yi sam ba zata iya jurewa ba, a halin yanzu zuciyarta ta kai makura, ba zata iya jure dannewa ba, ga wani irin azababben kyau da ya kara yi abinsa, sai dai shi ma akwai rama kaɗan a face nasa. Miƙewa ta yi ta diro kasa daga saman gadon, ba tare da ta ce da gwaggo komai ba ta nufi waje abinta. Binta da kallo kawai gwaggon ta yi tana mamakin su dukkansu biyun, tama rasa a wani mataki zata ajiyesu. Tana fita kasa ta sauƙa, bedroom nasa ta nufa, babu ko shayi a ranta, saboda ita kaɗai tasan me ta shirya mashi, dama wuyarta basu haɗu bane, tun da sun haɗu zai san waye ake cewa mace, bare ma ita da idonta yake a buɗe, wayayyiya ce sosai, ta fi Rimsha sanin komai, kawai yi ne ba zata yi ba, amma duk wani duniyanci ta iya shi. Bata yi sallama ba ta faɗa cikin ɗakin, yana zaune a bakin bed nasa ga abinci a gabansa kasan carpet, amma ya kasa saukowa kasa ya ci, saboda hankalinsa yana a kanta ne, tun da ya ɗaura idanuwansa a kanta ya ji ya kasa nutsuwa, komai kuma ya dawo mashi saboda, ya wani haɗe hannu ya zuba uban tagumi. Tsayuwa ta ɗan yi daga ta bakin kofa tare da harɗe hannayenta a saman kirjinta tana kallon shi, sam bai ji shigowarta ba. Sun ɗauki 10mins a haka kafin ta tako a hankali cikin sanɗo ta shigo cikin ɗakin. Wajen switch ta nufa, bai ankara ba sai ganin duhu a ɗakin ya yi, ta kashe wutar yana can duniyar tunani bai sani ba. Ɗago kai ya yi yana mamakin meyasa wutar ta ɗauke? Dan bai ji time da ta kashe wutar ba, sai dai kuma wannan ɗago kan da ya yi tasa ya fahimci ta shigo mashi ɗaki, dan ga kamshin perfume nata ya kai mashi karo a hanci. Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali, lumshe idanuwansa ya yi tare da gyara zamansa yana jiran ya ji dalilinta na kashe mashi wutar ɗaki. A hankali ta lallaɓo ta zo ta haye saman bed ɗin nasa, sai dai kuma ya jita, ya ji hayewar da ta yi, amma bai nuna kamar ya jita ba, ya zauna shiru yadda yake. Matsowa ta yi dab da shi, a hankali ta kwantar da kanta a saman bayansa tare da zuro hannayenta ta ƙugunsa izuwa plat tummynsa, harɗe hannayen nata a saman cikin nasa ta yi. Can kasa kasa kamar mai raɗa ta ce "Am so sorry Yah Areef, ka yi hakuri". Yadda ta yi mashi maganar bata taɓa yi wa wani ɗan adam magana da irin wannan muryar ba, cikin shagwaɓa sosai yau ta yi mashi magana, ga wani irin kwantar da murya da ta yi. Haƙiƙa har cikin ransa ya ji saƙon nata, muryar ta ratsa shi over, sai dai kuma bai nuna mata hakan ba, ya daure ya ce "Laifin me kika yi mani da kike bani hakuri kuma Jehan?". Kukar makirci da kisisina ta saka mashi tana faɗin "Ai ka sani, laifi dayawa mana, ka ce gwaggo ta bani waya nace ba zan karɓa ba, kuma naki kiranka daga baya". Tana magana tana kara karfafa kukan nata ta yadda zata karyar mashi da zuciya ta kuma rufe mashi baki. "Kin yarda hakan da kika yi laifi ne kenan?". Ya tambaya yana jin kukan nata har cikin ransa. Kara ƙanƙame shi sosai ta yi dan munafurci da sanin duniyanci kafin ta ce "E na yarda kuma shi ne nake baka hakuri, ba zan sake ba". Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce "To ki bawa mum ma hakuri kin ji?". Gyaɗa mashi kai ta yi tare da cewa "Tom yanzu ta yi barci, amma da safe zan bata". Sam bai ce mata promise me ko makamancin hakan ba, dan yasan ita mutun ce mai magana ɗaya kamar daddynta. "Kukan me kuma kike yi rigimammiya". Ya faɗa yana ƙoƙarin juyowa gareta. Kamar jira take yi ya juyo ta faɗa saman Lion chest nasa tana kara sakin kuka mai ɗan sauti. Rungumeta sosai da sosai ya yi a jikinsa, ya kasa magana saboda tsantsar farinciki, ita kuma kara shigewa jikin nasa sosai ta yi tana goga kanta a saman Lion chest nasa. Kansa ya rankwafo da shi dai'dai sai tin tata, kasa kasa kamar mai raɗa ya furta "I really missed you my baby". Ɗan ɗago kan nata ta yi, sai yazamana suna fuskantar juna. "Missed you more my husband". Ta faɗa cikin kuka da kuma shagwaɓa sosai. Nisawa ya yi kafin ya haɗe fuskokinsu waje guda, calmly ya ce "Is okey my baby, kukan ya isa haka mana". Ya kai karshen maganar tare da fito da harshensa ya fara lashe hawayen nata. Yana lashe mata su tana sake fito da wasu dan ta bashi wahala. (Jehan dai ba zata canza hali ba kamar yanda su Aseef da Akila suka ƙi canza hali😂) "Baby stop crying mana, ko so kike yi ki saka mani ciwon kai ne?". Ya faɗa murya cike da soyayya. Cikin kuka ta ce "To ai bani zan tsayar da kukan ba, dan dama bani na fito da shi ba, kai kasa hawayen suka fara fitowa, dan haka kai zaka dakatar da su". "Are you sure?". Gyaɗa mashi kai kawai ta yi. Jinjina mata kai ya yi tare da mayar da tongue ɗin nasa cikin ɗan bakinsa, sannan ya ɗan juya ya kwantar da ita a saman bed ɗin, ɗaura wayar dake hannunsa a saman bedside drawer ya yi kafin ya matso ya yi mata rumfa da faffaɗar kirjinsa. Cikin wani irin salo na daban ya fito da tongue nasa ya fara lashe kyawawan lips nata, sai ya yi kamar zai fara shansu, sai kuma ya fasa, haka zai ɗan zura mata harshensa kaɗan a cikin baki, sai zata kama sai ya janye abarsa. Shammatarsa ta yi ta kama hatshen nasa, cikin salo na musamman ta fara shan lips nasa, har ta mance ma da cewa kuka take yi. Tamkar jira yake yi ya fara bata hot kiss babu kama hannun yaro. Hannu ta kai tana cire botiran rigar barcin jikinsa, dan ta samu damar yin wasa da abin da ya fi burgeta a jikinsa. Cigaba da kissing nata ya yi cikin tsantsar kewa da fita hayyacinsa. Ita kuma tsab ta cire mashi riga tare da kai hannunta saman ɓul ɓul ɗin breast nasa, saboda suna burgeta sosai. Wash ya furta da karfi time da ya ji saukar hannunta a kansu, da sauri ya zame bakinsa daga nata dan ya samu damar faɗin wash ɗin da kyau. "Baby you want to kill me with your love ko?". Ya faɗa cikin muryar mayen soyayya. Matsa mashi ɓul ɓul ɗin nasa ta ɗan yi da ɗan karfi kafin ta tsuke fuska tana kafin "Daɗin taɓawa suke yi mani kawai". Wani irin duniya ya ji ya tsinci kansa a ciki, abin da bata taɓa yi mashi ba ko da sunan wasa, yau ga shi tana yi mashi, tana yi kuma tana zuba mashi shagwaɓa kamar ba ita ba, da ɗan karfi ya runtse idanuwansa tare da ciza kyawawan lips nasa na ƙasa yana fitar da wata iriyar numfashi mai ɗan sauti da sauri sauri. Ko kaɗan bata ji tsoro ko ɗar ɗar ba, sai ma kara matsa mashisu da ta cigaba da yi da ɗan karfi kafin. Wani irin azababben daɗi da ya ɗebesa sam bai san lokacin da ya.................... GASKIYA DAI JEHAN TA NUNA MASHI MATA DAI SUN WUCE TUNANINSA😂 GA SHI YANZU HAR DA SAMBATU YAKE SHIRIN FARA ZUBA MATA, A HAKA KUMA WAI FUSHI YA YI DA ITA NA TSAWON KWANAKI, AMMA CIKIN MINTI BIYU TASA YA SAUKO😂 MATA DUNIYA 🥱 ALLAH YA YAFE MANA ZUNUBANMU ❤️😂 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 16/5/2024 E33 Ko kaɗan bata ji tsoro ko ɗar ɗar ba, sai ma kara matsa mashisu da ta cigaba da yi da ɗan karfi kafin. Wani irin azababben daɗi da ya ɗebesa sam bai san lokacin da ya damko tula tulanta da karfi ba. "Yah Areef ka yi a hankali mana, ko so kake ka ji mani ciwo ne?". Ta faɗa can kasa kasa a shagwaɓe. Kasa amsa mata maganar ya yi, ya dai ji abin da ta faɗa, dan bai fita a hayyacinsa ba, so ya ji me ta ce, magana ce ba zai iya yi ba. Cigaba da wasa da ɓul ɓul ɗin nasa ta yi tana zuba mashi ruwan shagwaɓa a kan suna yi mata daɗi taɓawa. Kara birkita bawan Allah nan ta yi, Jehan akwai iya tsiya sosai, duk wasu lagon maza ta sani sarai, dama tsiya ce kawai tasa bata kula shi. Tun yana dannewa har ya kasa hakuri sai da ya fara zuba mata sambatu babu kakkautawa, biye mashi ta yi wajen zuba sambatun nasa, idan ya yi magana sai ta kai hannu ta matse mashi ɗan bakin nan nasa tana maimaita mashi abin da ya ce cikin shagwaɓa, ba karamin kara kwance mashi lissafin ƙwaƙwalwa take yi ba hakan da take yi mashi, duk ya susuce mata, bai ma san time ɗin da ya fara zuba mata shagwaɓa tamkar Aseef ba. Tuni ya rabata da dukka kayan jikinta, ko kaɗan bata yi ƙoƙarin hana shi ba, dan tasan babu abin da zai yi mata da ya wuce wasa, hakan yasa ta biye mashi, idan ya cika sambatun sosai ma sai ta matse mashi lallausan lips nasa har sai ya furta wash, sannan sai ta kai ɗan bakinta ta tsotsi lips ɗin nasa tana ce mashi. "Sorry na shanye zafin to". Da ya lura in bai yi da gaske ba sai ta saka shi yin ihu a cikin ɗakin nan, sai ya miƙe ya ce bari dai ya sakata yin ihun kafin ita ta saka shi, dan ya fahimci yau kure shi take da niyar yi, dan haka bari ya gwada mata kaɗan daga cikin kwarewarsa. Hakan yasa ya miƙe ya yi mata rumfa da faffaɗar kirjinsa, hannu ɗaya ya sanya ya kama tula tulanta guda ɗaya, cikin salo na musamman ya fara murzawa, yana yi yana kallon face nata duk da a cikin duhu suke. Tana jin murzansu da yake yi a jikinta, amma ta danne ta ki nuna mashi hakan, dan ta sanya a ranta yau ba zai sakata kuka or suma ba, sai dai yau ta sanya shi kuka. Abin da bata sani ba shi ne, shi fa Areef ya fita iya tsiya, duk tsiyarta ko kwatan kafarsa bata kama ba, shi fa a gabaɗaya cikin TRIPLETS ma ya fisu iya tsiya, ya fisu sanin wacece mace, sai dai idan bai yi niyar yi ɗin ba, amma idan ya yi niya ko motsawa ba zata iya yi ba sai dai kuka a iya wasa kawai, so yau abin ya bashi mamaki ne sosai, bai taɓa tunanin ta iya soyayya har haka ba, saboda kowa kallon irin bosawan nan yake yi mata, bata magana bare azo ga murmushi or dariya, shi ne yasa suke yi mata kallon sam babu abin da ta sani dangane da soyayya. Hannunsa ɗaya ya kai gabanta. Ai bata san time ɗin da ta furta ash da karfi ba. Lumshe idanuwansa ya yi lokacin da ya jita a jike sosai tare da fara wasa da gaban nata da kuma breast nata. Tun tana ɗan jujjuya mashi a hankali tana dannewa, har ta fara faɗin "Yah Areef ka bari to". Matsowa ma ya yi ya kara mata wata saukin ta hanyar kama lips nata, kissing nata ya fara yi kafin ya zame bakin nasa ya mai do shi saman cibiyarta, still hannunsa ɗaya na'a saman tula tulanta dake kara kwance mashi lissafin ƙwaƙwalwa, ɗayar kuma tana a gabanta, ban da aman ruwan ni'ima babu abin da take yi mashi, ba dan gobe da safe akwai in da zai je da ita kuma jibi zasu wuce U.s ba, da ba abin da zai hana shi shigarta, saboda uban ruwan da take bulbularwa, ta gigita shi sosai, hakan yasa yake wasa da wajen sosai, saboda yadda yake jin wani zir zir a jikinsa haka yake kara sanya yatsarta a wajen yana wasansa son ransa. A hankali ta fara yi mashi kuka tana kara kankame shi, sai faɗin "Yah Areef ka bari hakanan, please ya isa, wayyo gwaggona". Amma ina sam yaki kulata, kuma yana jin duk abin da take faɗa, ramawa shi ma yake yi, ɗazun ta sanya shi zuba sambatu, shi ma bari ya sanyata a yanzu, sai dai kuma ita ba zata iya ɗaukar ko rabin wasanninsa ba a yanzu, sun fi karfinta over. Ganin yadda take mashi kuka ta ƙanƙanme shi ne yasa ya zame hannunsa daga gaban nata tare da sake tula tulan nata, kamar wadda ya hakura zai kyaleta, tana ƙoƙarin yi mashi magana sai jinsa ta yi ya buɗe mata kafafu da kyau ya zira harshensa a gaban nata. Ai bata san time da ta zunduma mashi ihu ba, ya cika ɗan duniya, ita bata san cewa sambatun da take zuba mashi ne ya yi mashi kaɗan a wajen saurara ba, shi ne yasa ya ce bari ya yi mata abin da zai sanyata yin surutun duk abin da yake cikin zuciyarta ba tare da ta shirya faɗarsu ba. Ai kuwa yaga surutai kala kala, duk kuma yana jinta, sai ma kara sanya harshen nasa a gabanta ta saman ya yi, wasa sosai yake yi da wajen, duk ya rinkita baiwar Allah, kuka hawaye bibbiyu take yi mashi, sai ambatar sunansa da na gwaggo take yi, kuma wlh tsab yana jin duk abin da take faɗa, dan shi ba kasafai ya cika fita daga hanyacinsa wajen wasa da mace ko wani abin ba, zai ji duk abin da ta ce, magana ce dai ba zai iya yi ba, sai dai idan daɗin ta yi mashi yawa ya fara sambatu a hankali hankali, so yana jinta sarai, amsa mata ne ba zai iya ba. "Wayyo Yah Areef zaka kasheni, please ka bari ka ji? Ba zan sake ba, wayyo gwaggo na kice Yah Areef ya kyaleni haka, ba zan iya ɗauka". Kaɗan daga cikin surutan da take yi mashi kenan. Sai da ya yi wasa da ita son ransa, yana yi tana zubar da ruwan ni'ima, hakan kara tsuma shi yake yi, ya juyata son ransa, har sai da ya ji ya ɗan sami saukin abin da yake ji, sannan ne ya zame ɗan bakin nasa daga wajen, ya kai saman mararta ta kasa ya sumbata tare da komawa kusa da ita ya kwanta. Sai kuka take yi mashi hawaye bibbiyu. Jawota jikinsa ya yi yana faɗin "Sorry my baby, ke ɗin ce kin cika zaki dayawa, taɓa penis nawa ki ji fa, ko kaɗan bai ji kamar ma mun fara wasa ba, shi kawai so yake yi ya shiga cikin jikinki, ni kuma na hana shi, kinsan kalar wahalar da zan sha a kan hakan kuwa?". Ya kai karshen maganar tare da riko hannunta ya ɗaura a saman Heronsa dake tsaye kyam kamar muciya. Ƙoƙarin zame hannunta daga wajen ta yi tana faɗin "Ni Yah Areef ba zan iya taɓawa ba". Ƙanƙame hannun nata ya yi, a kunne ya raɗa mata "Amma zaki iya gani kuma ki yi mani wasa da shi dan na sami sauki ko? Duk fa wasan da na yi da ke tamkar bai ma san ina yi ba, shi dai kawai abinci yake so na bashi". Yadda ya yi maganar sai ya baka tausayi, cikin raunin murya ya yi ta, yana cikin azababben sha'awarta ne. "Yah Areef ba zan iya wasa da ita ba, tsoronta ma nake ji". Kara ɗaura hannun nata a wajen da kyau ya yi, kasa kasa ya ce "Idan baki yi mani wasa da ita ba wakike son ya yi mani? Ko so kike yi na fara neman wanda zata yi mani ne?". Hannunta ɗaya ta kai ta matse ɗan bakin nan nasa har sai da ya ce "Oh my god" "Gobe ka kara zancen zaka nemo mai maka wasa da ita". Ta faɗa cikin sanyin murya tare da yunkurawa zata tashi. Jawota ya yi ta faɗa saman Lion chest nasa, a kunne ya raɗa mata "To please ko kaɗan ne ki ɗan yi mani wasa da ita, ko kin fi son ki ganni cikin wahala na kasa barci ne?". Girgiza kai ta yi tana faɗa mashi ba zata iya ba gaskiya. Saketa ya yi tare da juyawa ya kifa a saman mattress ɗin, har wani irin azababben ciwo yake jin mararsa tana yi mashi, ji yake yi tana yi mashi wani irin murɗa mai zafi. A hankali ya fara juyi a saman bed ɗin dan ya nemawa kansa saukin abin da yake ji, saboda idan yana wasa da ita ma kara miƙewa kyam Heron tasa take yi tana yi mashi wani irin zafi, so gara dai ya kyaleta. Ita kuma ganin haka yasa ta matso ta kwanta a saman bayansa tana mai bashi hakuri tare da yi mashi alkawarin zata yi mashi wasa da ita, dan Allah ya yi hakuri ba zata sake ba. Bai iya amsa mata maganar ba, sai dai kawai ya juyo ya rungumeta a saman chest nasa, matseta sosai ya yi yana wani irin lumshe idanuwansa da suke jajir kamar wuta. Hannu ta kai saman Heronsa nasa kamar yadda ta yi alkawari, a hankali ta fara matsa mashi ita tana wasa da ita, ban da wash babu abin da yake ita furta mata. Sai a lokacin ne ta fahimci ashe ga in da zata taɓa mashi tasa ya fita daga hayyacinsa shi ma, tasa ya zuba sambatu sosai, wato kowa da abin da ya fiso a yi mashi wasa da shi kenan? Sai a yanzu ta gane hakan, dan haka sai ta kudurta a ranta Allah sai ta sanya shi fita a cikin hayyacinsa watarana, ba yau ba, dan yau already ya gama kashe mata jiki, ya luguigui tata son ransa, so bata da wani karfin kirkin da zata yi mashi abin da ta yi niya. "My baby keep doing it, is so sweet". Ya faɗa ba tare da ya san time ɗin da maganar ma ta fito daga cikin ɗan bakin nasa ba. Kara shigewa jikinsa ta yi tare da fara yin kissing na lips nasa, ta kara matsa mashi heron nasa da ɗan karfi. "Wash my baby you will going to kill me with your love, it's very very sweet, oh my god". Ya sake faɗa cikin wata iriyar murya wadda kunnuwar mutane daga waje ba zasu iya ɗauka ba, sai dai matar tasa kawai, saboda yadda ya kwantar da muryar, idan ƴan mata suka ji ta sai su ruɗe su birkice. Cikin fitar hayyaci ya kai hannu ya zame wandon jikin nasa, dan ya bata damar yi mashi wasar da kyau, sai dai kuma a lokacin tsoro ya hanata taɓawa, dan kuwa yadda take jinsa a ciki daban da yadda ta jisa a waje. Da ya fitar da ita sai ta jita ta wani irin kara uban girma sosai, dama saboda tana ciki ne yasa bata iya taɓata dukka, to yanzu gata a waje, sai ta jita wata zabgegiya da ita, ga kauri. Har wani kerma jikinta ya fara yi, saboda tsoro, da sauri ta ɗan ja baya daga jikin nasa. Shi kuwa cikin duhu ya laluɓo hannun nata, kai tsaye sai saman Heron nasa dake ta aman madara ya ɗaura hannun nata. Kasa motsa hannun ta yi, jikinta na kermar tsoro sosai. A ruɗe ta ce "Yah Areef ba zan iya ba, Allah ba zan iya taɓata a fili ba, tsoro take bani, narasa meyasa har jikina yake kerma". Ta faɗa tana hawaye. Sake hannun nata ya yi tare da matseta a jikinsa, cikin zafin nama ya haɗe bakinsu waje guda. Kissing nata yake yi da zafa zafansa, saboda wani irin azababben yanayi da yake ji a jikinsa, sannan ya kara matseta sosai a jikinsa, a hankali ya ɗago heron nasa ya sanyata a tsakanin cinyoyinta, da yake kafafunta suna a manne da juna, sai ya fara wasa da gabanta ta hanyar ɗaura heron nasa a wajen. Da kyar ya iya furta cewa "Zaki barni na shiga ciki my baby? Ba zan iya jurewa ba". Har ya manta da cewa jibi zasu tafi, gobe kuma zai fita da ita unguwa. A tsorace ta fara girgiza mashi kai tana faɗin "Dan Allah Yah Areef ka yi hakuri, please kada ka shiga, wlh ina jin tsoro sosai". Jin yadda ta yi maganar ya fahimci ta rigada ta tsorata, idan ya ce zai yi dis virgin nata a yanzu, to tabbas zai lalatawa kansa jin daɗin rayuwa ne, saboda yadda ta tsoratan nan idan ya shigeta to har abada a tsoronsa zata kasance, koda sun saba, a haka zata ɗauke abin da zafi, so is better ya shammaceta ne bata yi zaton hakan ba, sai ya fi mashi a kan tasan da hakan. Wannan dalilin yasa ya hakura ya rabu da ita, ya cigaba da wasa da ita dan ya nemawa kansa salama da saukin abin da yake ji. A ɓangaren Aafia kuwa, tana fitowa daga bedroom na gwaggo waje ta nufa, a harabar gidan ta ɗan tsaya shiru tana tunanin duniya. Ta ɗan jima a haka kafin ta nufin garden na gidan zuciyarta cike taf da matsananciyar damuwa na rashin Dr Nawid, yanzu ya tabbata da gaske ya mutu? Abin da take ta tunawa kenan, almost wata 5 kenan a yanzu basu a tare, ya tafi ya barta, kullum da tunaninsa take kwana take tashi, kullum sai ta kira Umminsa a waya, dan su gaisa, idan kuma suka gama wayar to sai ta sha kuka sosai, saboda tausayin Ummin, ita kaɗai tasan irin son da Ummin take yi wa Dr, ita kaɗai tasan shakuwar da take a tsakanin wannan uwa da ɗanta, Allah mai iko mai yin yanda yaso. Zuciyarta cike taf da tunani ta shiga cikin garden ɗin, saman sofa ta zauna tare da buga uban tagumi wasu siraran hawaye suna bin kuncinta, har ga Allah tana tsananin son Dr ba kaɗan ba. "Why are you crying". Tamkar daga sama haka ta ji voice nasa. A hanzarce ta ɗago kanta dan ta ga wanenen. Yana zaune a saman sofar dake fuskantar, hannunsa na rike da wayarsa, ɗayan hannunsa na rike da cup mai ɗauke da coffee, jikinsa na sanye da sleeping dressing launin ash color mai haske, ya saki gashin kansa mai kama dana Areef sak, shi ma dai irin Areef ɗin ne, baya datse kashin nasa, hakan tasa take da tsawo har gadon bayansa kamar mace, sai tashin daddaɗar kamshi perfume nasa yake yi, ya fito shan iskansa abinsa. Ɗan kawar da kanta gefe guda ta yi tana faɗin "Nothing". Sai dai zuciyarta na a cike da mamakin abin da ta kalla ɗin, duk da tana cikin yanayi mara daɗi hakan bai hana ta shiga wani irin ruɗani da ganin face nasa ba, daurewa kawai ta yi ta kawar da kanta gefe dan kada ta cika kallonsa. Tsareta da ash eyes ɗin nan nasa irin na Areef ya yi, kamar ba zai sake ce mata komai ba, sai kuma ya sake cewa "Ba'a kuka babu dalili, just tell me the season kawai". Miƙewa ta yi da nufin ta bar wajen, dan bata san cewa da mutun a garden ɗin ba, da ta sani sam ba zata shigo ba, saboda ita kwata kwata bata son ma ayi mata magana, bata son hayaniya, shiyasa ta baro ɗakin gwaggon ma, dan Areef ya shigo zasu yi ta yin hira, ita kuma bata son jin magana a kusa da ita. "Where are you going?". Ya tambaya tare da miƙewa tsaye, wani dogo da shi, sai ta zama ƴar gajera a gabansa, dan ba karya Tga yana da tsawo sosai, da kaɗan Lion ya fishi tsawo, shi kuma ya fi su Areef tsawo. Bata kula shi ba, dan bata jin kamar ma zata yi magana, nufar hanyar fita kawai ta yi. Zura wayarsa a cikin aljikun wandon barcin jikin nasa ya yi tare da riko hannunta ɗaya cikin sauri yana faɗin "Ina zaki je? I think kin fito shan iska ne?". Juyowa ta yi da sauri saboda ta kwace hannunta da ya rike, sai dai kuma ganin face nasa yasa ta kasa yunkurin kwace hannun nata, saboda kowa dai yasan ya fuskan Tga take, a ɗaure tamau kamar ta Lion, ba shi da wasa, so ganin yadda face ɗin nasa take ne tasa ta ji wasu Mala'ikun nutsuwa sun diro mata a jikinta, tsit ta yi, jikinta har ya fara kerma, saboda tsantsar tsoron ganin face ɗin nasa da ta yi, ga shi kuma bata taɓa tunani a rayuwarta ko da sunan wasa zata gan shi ba. Shi kuwa tsareta da idanu ya yi yana kallonta from head to toe, lokaci guda ya ji wani irin sauyi a tattare da shi, ga shi kuma kayan barci ne ita ma a jikinta. Shiru ya yi, ya kasa ce mata ko uppan. Ganin yadda yake ta binta da kallo ne yasa ta yi ta maza ta zame hannunta daga cikin nashi, da gudu ta bar wajen. Binta da kallo ya yi har sai da ta fice daga wajen, ji ya yi tamkar ya bita ya kamota, amma kuma sai ya kasa, komawa saman sofarsa da ya tashi ya yi ya zauna, jingina kansa da jikin head na sofar ya yi tare da lumshe idanuwansa. Ita kuma tana barin wajen ɗakinsu ta koma, nan ta isko Akila tana wannan aikin dai da suka saba na waya da habibinta sahibinta. (Nace ba wai su ko rasa abin faɗawa junansu ma basu yi ne?😂 Kullum suna maƙale da waya, kai Aseef ɗan soyayya ne😂 jinin Dr William ɗin ne da gaske yake gudu a jikinsa🥳 dan Dr da gwaggo sun zuba love ba karya) Kusa da ita ta kwanta zuciyarta na harbawa da karfi karfi, bata taɓa tunanin zata ga Tga a zahiri ba, idan baku manta ba tana kallonsa a news sosai, shi ne mutun na farko da ta fara so a rayuwarta kafin Dr Nawid, tasan cewa ba zata sami Tga ɗin ba ko a mafarki baiwar Allah shi ne yasa kawai ta fara son Dr Nawid ta cire Tga a ranta, yau sai ga shi sun yi ido huɗu da shi, tun da ta zauna a gidan bata taɓa cin karo da shi ba sai yau, time da ya taimaketa daga hannun Abbo tana a sume ne, bata sani ba, so yaune karonta na farko da ganinsa da ta yi a gidan, wani irin bugu kirjinta yake yi da sauri da sauri. A ɓangaren Lion kuwa, yana isa *GOLD CROSS HOSPITAL (GCH)* fitowa ya yi daga cikin taxi ɗin tare da gayawa mai taxi ɗin yana zuwa. Kai tsaye cikin hospital ɗin ya nufa. Abin ya yi matukar bashi mamaki yadda securityn wajen suka yi matuƙar girmama shi har da duka mashi kasa, sam basu hana shi shiga ba, sai ma ƙoƙarin raka shi ciki da suka yi, abin ya bashi mamaki sosai, shi dai yasan basu san shi ba, dan sau ɗaya ya taɓa zuwa kasar China yin wani aiki, kuma sam bai taɓa zuwa wannan hospital ɗin ba, to ya akayi suke girmama shi haka?. Abin da bai sani ba shi ne, a matsayin Sir Arvin suke kallonsa, duk da ya sanya face mask, sun san Sir Arvin ɗin sosai, shi ma ba mutun ne da ya cika yawo haka ba face mask ba, mafiya yawan lokuta da face mask zaka ganshi, hakan yasa suka bawa Lion ɗin hanya shi ma, dan kallon sir Arvin kawai suke yi a wajen. Katafaren hospital ne wanda yake cike taf da manya manyan jiga jigan security's a ta ko'ina, shi ne hospital ta biyu a girma, kyau da tsada a kasar China, an narka maƙudan kuɗaɗe sosai wajen gina shi, idan aka ce maku shi ne hospital na biyu a gabaɗaya faɗin kasar China, ai kunsa ba asibiti bane na wasa, so tsayawa zayyana maku haɗuwarsa ma sam ba zai yiwu ba, dan baki ba zai iya zayyano haduwarsa ba, ga uban ma'aikata dayawa sosai, sai ɗan wane da wane ne suke iya kwanciya jinya a cikinsa, saboda tsada da kyau, kwararrun likitoci ta duniya ne ke aiki a cikinsa. Kai tsaye kyakkywar elevatornsu Lion ya nufa, hawa na 10 ya nufa kai tsaye, da alama yasan address na in da zai je ɗin tun kafin ya tako kafarsa izuwa cikin kasar. Sai wani girmama shi suke yi, ko da ya isa hawa na gomar ya fito daga cikin elevator, duk wata likita da zai wuce sai ta duƙar da kai ta girmama shi, tun abin yana bashi mamaki har ya dai'na. Kai tsaye office na babbar likita wato Dr Cherish ya nufa, yana taku cikin nuna isa da ƙasaita, sak yadda Sir Arvin yake tafiya, dan shi ma akwai shi da nuna isa da izza, ga ɗan banzan girman kai kamar me, yana kallon mutane kamar kashi, abin nasu a jini yake!! Babu in da Sir Arvin ya baro Lion, tamkar a waje guda suka yi rayuwa, tamkar a tare suka girma, suna kasashe daban daban, amma komai nasu kusan iri ɗaya ne, kama daga halayya ɗabi'u, komai dai, sak TRIPLETS sir Arvin yake!!. Babu ko excuse ya danna ciki office na Dr Cherish abinsa, manya manyan security's uku dake tsaron kofar office ɗin babu wanda ya yi yunkurin hana shi, saboda a tunaninsu sir Arvin ne, dan yana zuwa hospital ɗin time to time, so sun san shi, basu isa su hana shi ganin Dr Cherish ba. Tana hakimce a saman dankareriyar office chair ɗinta, A.c na bugata ta ko'ina, idanuwanta na sanye da wani shegen tsadadden farin glass, ga wani tsadadden laptop a gabanta saman table, daga gefe uban tulin files ne na majinyata, kyau iya kyau ta yi, kayan jikinta dukka masu uban tsada ne, watch dake ɗaure a hannunta sak irin watch dake ɗaure a hannun Lion ɗin, tamkar daga company guda suka saya, da yake yau ba watch nasu na TRIPLETS na sanya ba, wata ce daban, sai aka yi sa'a ta yi iri ɗaya sak dana Dr Cherish ɗin, ta dake tare da hakincewa a saman chair, ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya, ga wasu tsadaddun waya har biyu a gefenta, daga dukkan alamu tana cikin kwanciyar hankali na wuce misali. Kowa dai yasan yadda office na babban Dr yake da haɗuwa da tsantsar kyau, ba sai na tsaya ɓata lokacina wajen zayyano maku haɗuwarsaba. Tana ganinsa ta cire glass ɗin face nata tana faɗin "Arvin what are you doing here? Is there any problem? Kai da na bari a gida kana barci, ka ce mani fa yau ba zaka fita ba, ba zaka je office ba, to me kazo yi a nan?". Saman chair ya zauna ba tare da ya amsa mata maganar tata ba. Lion akwai nuna tsantsar isa, ya shigo mata kai tsaye kawai, ya samu waje ya yi zamansa ba tare da izini ba, yanzu kuma me next our Lion?........... Alkalamin PRINCESS TEEMA taku ta amana ce kawai zata gaya maku me next...❤️ Kallonsa ta fara yi from head to toe, yanayin kayan jikinsa sam ba irin dressing na Sir Arvin bane ba, Sir Arvin bai cika sanya jeans and t-shirt ba, ya fi yawan sanya suit kullum, sai kuma kayan ƴan kwallo da kuma pajamas, saboda shi tun safe yana office sai yamma yake dawowa gida, idan kuma ya dawo ya yi wanka kayan shan iska yake sanyawa, shiyasa kullum yake a cikin shigar suit kala kala masu tsada, bugu da kari sai yanzu ta lura da Lion ya fi Sir Arvin cika, sannan dark black curly hairnsa ya fi na sir Arvin yawa, kuma sir Arvin bai taɓa shigowa har ya zauna ba tare da ya yi mata magana ba, amma Lion har ta yi mashi magana ma bai amsa ba, daga haka sai ta fahimci wannan kamar ba sir Arvin bane, suna da banbanci, amma sai mutun ya tsaya ya lura sosai ne zai gane banbancin nasu. "Who are you?". Ta faɗa a ruɗe tana zaro idanuwanta sosai a kansa. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 17/5/2024 E34 "Who are you?". Ta faɗa a ruɗe tana zaro idanuwanta sosai a kansa. Shiru ya yi mata almost na 10mins, sannan ya ɗago kai a nutse tare da cire face mask dake a face nasa, a saman table nata ya ɗaura face mask ɗin. Wani ruɗewa ta kara yi, saboda kara kamanceceniya da sir Arvin da ya yi, da ya cire face mask ɗin ma sai ainahin kamar tasu ta bayyana, in dai ba wai ka yi wa sir Arvin or Lion ɗin farin sani sosai ba, to bazaka taɓa iya banbantasu ba, ita kuma ita ce mahaifiyar sir Arvin, ita ta rene shi, ta san shi ciki da waje, so dole ne ta iya banbantasu da Lion, dole ta gano banbanci a tsakaninsu, dan ba ta yadda za'ayi ace sun fita abu ɗaya sak, dole da akwai banbanci, saboda duk duniya babu dai'dai sai Allah, Allah shi kaɗai ne dai'dai!!. Jikinta har kerma ya fara yi, saboda tun da take a duniya bata taɓa kallon irin wannan tsananin kamanni a zahiri ba, sai dai a film, ashe akwaisu da gaske a zahiri? Abin ya ruɗar mata da ƙwaƙwalwa sosai, hakan yasa cikin hanzari ta ɗauko wayarta, number sir Arvin ta fara kira jikinta na wani kerma sosai. Yana gida yana ta zuba barcinsa abinsa, hankalinsa a kwance, banda tunanin Lion da ta kutso mashi cikin rayuwarsa, da babu komai da yake damunsa. Bugu ɗaya ya ɗauka, idanuwansa duk barci, a tsananin tashin hankali ta ce "Son where are you now?!". Shiru kaɗan ya ɗan yi mata kafin ya ce "Mum am sleeping you know that, amma sai da kika tasheni, what do you want again? Before ki bar gidan nan sai da kika tashe ni fa, yanzu ma kika sake". Cikin muryar barci sosai ya yi maganar. "Son come to our hospital now!". Ta faɗa words ɗin ta basu fita sosai, sai haɗesu take yi. "Mum are you okey? Why are you talking like that? Is there any problem?". Ya yi maganar yana miƙewa zaune, saboda yadda ya ji tana magana sam bai yi kama da wadda take a cikin hayyacinta ba, ya fi kama da wadda aka sanyawa bindiga a kai aka sanyata yin magana dole, bai san cewa bama bindiga ce aka sanya mata ba, nuclear makamin kare dangi ce mai gabaɗaya zaune a gabanta, dan Lion shi kaɗai gayyace mai tarwatsa tawagar azzalumai, tamkar nuclear yake, idan ya shiga gungun azzalumai komai yawansu sai ya tarwatsasu, ga karfin halin bala'i, ga dakiya na wuce misali, ga kwarin gwiwa full a tattare da shi, baya sarewa kuma baya ja da baya idan zai dimfari waje, so abin da yake a gabanta yanzu yaci uwar bindiga, dole ta yi in'ina a magana, dole ta kasa fitar da words yanda ya kamata, a hakan ma bata san wanene a gabanta ɗin ba, ita dai kwarjinin dake a saman face nasa ne kawai ya razanata, bata riga ta ji waye shi? Kuma meya kawo shi ba?. "Arvin i said come to our Hospital now!". Ta faɗa cikin ɗaga murya, tana kai karshen maganar ta katse kiran jikinta na ɓari, duk kuma maganar da take yi tana yin shi ne idanuwanta na a kan Lion ɗin, ko kyaftawa ta kasa yi. Shi kuwa tun da ya shigo kallo ɗaya ya yi mata ma ya kawar da kansa gefe guda, dan baya da buƙatar sake kallonta, idan baku manta ba, shi baya ɗaga idanu ya kalli abu, tama yi sa'a ne da ya yi mata kallo gudan. Tana son kiran security's su shigo dan tsoron kada Lion ɗin ya cutar da ita, amma ta kasa iya kiran nasu, saboda azababben tsoro da kuma kwarjininsa da take gani, ta kasa kiransu, dan a yadda take kallon Lion ɗin nan babu wani securitynta da zai iya ɗaga mashi yatsa ma bare har ya iya dakatar da shi idan ma zai cutar da ita ɗin ne, saboda shi a tsaye yake, kuma Lion irin mutanen nan ne da suke a buɗe sosai, hakan ma tana ɗaya daga cikin abin da yasa mutane suke tsoronsa, saboda Lion chest nasa a buɗe take sosai, zakin ne da gaske, ya ci sunansa na Lion ɗin. Tamkar wata marainiyar biranya haka Dr Cherish ta koma saman chair nata ta zauna, duk da sanyin A.c dake dukanta, to zufa take haɗawa, ta yi wani fiki fiki da ita, ga idanuwan nata na ƴan China kanana da su, sai suka kara ƙanƙancewa. Shi dai Lion saboda karfin hali ko sannu dai har yanzu bai ce mata ba, kuma yaki sake ɗago idanu ya kalleta. Almost 30 mins suna a haka shiru kafin sir Arvin ya turo kofar office ɗin ya shigo bakinsa ɗauke da excuse, tun daga kan wannan excuse ɗin ta gane shi ne ɗanta, dan shi baya shigo mata babu excuse, saboda ya girmama mahaifiyar tasa, shi kuma Lion mai gayya mai aiki, bata kai ya ce mata excuse ba........... 😂 Wlh idan kana neman ƴan duniya idan ka samu Lion da Areef to shikenan ka gama komai. Cikin tashin hankali sir Arvin yake faɗin "Mum what's happening?". Subhallahi, ai sai a yanzu ne ma Dr Cherish ta shiga ainahin tashin hankali, saboda yadda mutane biyu suka haɗe suka zama mutun ɗaya saboda kamanni, sai dai fa shi Sir Arvin ɗan siririr ne kamar Aseef namu ɗan soyayya, dama na gaya maku Lion ya fishi cika. Kasa magana ta yi sai dai ta nuna mashi Lion da yake zaune da hannunta. Karisowa cikin office ɗin ya yi yana cikin shigar suit ash color masu bala'in kyau da tsada, sai tashin kamshi yake yi. Wani irin uban jan birki ya yi lokacin da idanuwansa suka sauƙa a kan Lion ɗin, duk da cewa tun jiya ya ga hotonsa, amma ya tsorata da ganinsa a zahiri, saboda hoto ma ta ɓoye wasu abubuwa, a zahiri ainahin kamar tafi fitowa sak. Ganin yadda ya ja birki ne yasa Lion ɗin ya ɗago idanuwansa tare da saukesu a kansa. Kara waro idanuwan nasa waje shi ma ya yi, wani irin mamaki ne ta kama shi, sai dai bai bayyanar da mamakin tasa ba, saboda abin da ya kawo shi ba karamar abu bace, so ba zai bari su fahimci ya yanayinsa ma yake ba bare har su kawo mashi wata wargi, ya yi bincike a kan Dr Cherish sosai kafin ya zo, so ya yi mata farin sani, makira ce ajin karshe. Kawar da kallonsa daga kan sir Arvin ɗin ya yi tare da mayar da shi izuwa kan Dr Cherish ɗin, calmly cikin wata iriyar nutsuwa ya ce "Where's Dr William?". Shi ne kalma ta farko da ta furta tun shigowarsa cikin office ɗin kenan. A zabure ta miƙe tsaye tana kallonsa. Kara ja da baya sir Arvin ya yi, saboda jin harta voice ɗin Lion sak irin tasa take, yadda suke magana a hankali sak iri ɗaya, yadda suke magana cike da class da nuna isa da tsantsar izza, shi ma sak iri guda, abin ya kara bashi mamaki. Kallon kallo suka fara yi a tsakaninsu wato sir Arvin da Dr Cherish ɗin. "Bana magana biyu, idan nayi na farko shikenan, in aka matsa sai na yi na biyu, to sai dai hannuna ya sake maimaitawa mutun, so is better for you da ki bani amsa ba ɓata lokaci, because i have a lot of things to do, time nawa yana da mahimmanci a gareni!". Cewar Lion, cikin wannan sexy voice ɗin nasa dai ya sake yin magana, hankalinsa a kwance. "Who are you? And what do you want?!". Sir Arvin ya tambaye shi cikin ɗaga murya. Tamkar bai san da tsayuwarsa a wajen ba, dan bada shi yake magana ba, kuma kunsan halin Lion, idan ba da kai yake abu ba to ko kai uban waye baya bi ta kanka, bama ka ishe shi kallo ba, so yanzu dai da uwarsa Cherish yake yi ba da sir Arvin ɗin ba, saboda haka bai ga dalilin da zai sa ya kula sir Arvin ɗin ba!! Babbar magana. Ganin kamar bata da niyar yin magana ne yasa ya miƙe tsaye tare da harɗe tafukan hannayensa ɗaya cikin ɗaya yana ɗan shafe juna, kafin ya saci kallon sir Arvin ɗin dake ta gefensa ta wutsiyar idanu, sannan ya ɗauke Dr Cherish ɗin da wata iriyar mari wadda ta sanyata komawa saman chair ɗinta ta yi wani irin zaman ƴan bori. Nan take ta fara ganin wani irin duhu duhu da wasu yana suna gifta mata ta cikin idanuwanta, kunnenta ta gefen da ya mara dai ya tashi a aiki, dan ta dai'na jin sautin komai ta gefen yana tashi, duk da tana zaune sai da ta kalli wani irin ajijiya mai karfi yana wani kwasan chair ɗin nata, da alama ta leƙa lahira ne ta dawo, tama yi ƙoƙari da bata suma ba, saboda zaratan maza ma basu iya shanye marin Lion bare ita mace, ko da yake dama ba zai mareta kamar yanda yake marin maza ba, zai sassauta mata, dan kada ta mutu bai sami amsar da yake so ba!!. (Oh ni PRINCESS FATEEMA ya zan yi da karfin hali irin na Lion ne?🤔 Kasamu mata ka bata lafiyayyen mari a cikin office nata dake kewaye da security's babu ko ɗar ɗar? Bugu da kari a cikin kasarsu? Sannan a gaban ɗanta? Tana matsayin babban likita uwa ga jama'a?😒 Dole mu nemawa Lion sauki wajen Ubangiji, in dai karfin hali da nuna isa da izza ne daga kansa an rufe kofa, wato shi ko shakkar shiga cikin kasar tasu ma bai yi ba?🤔 Kai lamarin Lion sai shi wlh, sai kuma Rimsharsa ƴar baiwa, dan idan baka da baiwa ba zaka iya ɗaukar zama na minti goma da shi bama) A fusace sir Arvin ɗin ya yi kansa, dama kuma yasan za'ayi hakan, shiyasa ma ya saki kallonsa kafin ya mari Dr Cherish ɗin, ya kalle shi ne dan ya ga a yadda yake, saboda ya ji daɗin bashi nashi marin da kyau idan ya nufo shi, dan yasan ɗan nata ba bari zai yi ba. Sai da ya bari sir Arvin ɗin ya iso gare shi da nufin ya bashi mari shi ma, sai ya rike hannun nasa tare da ɗauke shi da marin shi ma, dan idan ba hakan ya yi masu ba, ba zasu yi mashi abin da yake so ba. Babban magana Lion da marin sir Arvin. Bayan ya mare shi ɗin ma sai da ya haɗe hannayensa dukka biyu ta baya ya rike da hannunsa ɗaya, dama na gaya maku shi sir Arvin kamar Aseef yake, bashi da cika sosai, hakan yasa Lion ɗin ya rike hannayensa da hannunsa guda, cikin wata iriyar murya a kwance cikin nutsuwa ya ce "Ka nutsun mani, idan ba haka ba zan turaka in da ba'a dawowa, da uwarka nazo yin magana ba kai ba, so be careful!". Turo kofar office ɗin da aka yi ne yasa Dr Cherish ta dawo cikin hayyacinta, shi kuma Lion hannu ya kai ya ɗauko wani kyalle fari da yake kusa da Dr Cherish ɗin ya ɗaure hannun sir Arvin ɗin ta baya, har lokacin sir Arvin ɗin bai dawo dai'dai na marin da ya sha ba, jiri ma yake gani, sai ya ji kamar ba shi ba, kamar ba'a duniya yake ba, ya maru ba karya, bawan Allah wannan jajir ɗin kumatun nasa bata taɓa shan mari ba sai yau, yau ɗin ma kuma marin Lion, ai dole ya faɗa wani yanayi na fita cikin hayyaci. Bayan ya kammala ɗaure shi ta wutsiyar idanu ya kalli wanda yake shigowa ɗin. A dubu ɗari ya saki sir Arvin ɗin tare da juyowa da kyau ya kalli mutumin da ya shigo ɗin, shi kuma sir Arvin saboda yana ɗaure zubewa kasa ya yi a saman gwiwowinsa da Lion ɗin ya sake shi. Cikakken Dr ne, kyakkyawan Bature tas da shi, yana sanye da suit masu tsada launin white color, ya ɗaura rigar aikinsa a sama, idanuwansa na sanye cikin white Medicated glass mai shegen tsada, hannunsa na ruke da wasu files dayawa, dark black curly hairnsa a ɗaure a bayan wuyarsa, sai sheƙi yake yi. From head to toe Lion ya fara kare mashi kallo, bai tsayar da kallon nasa a ko'ina ba sai a cikin dara daran blue eyes na wannan Drn, ɗan ciza lips nasa ya ɗan yi kafin ya dukar da kansa kasa yana wani irin sauke numfashi mai wuyar fassaruwa. "Cherish what's happening here?". Cewar wannan Dr da ya shigo yanzu, ya yi tambayar yana mai do da kallonsa a kan Lion, cikin hanzari ya sake kai kallonsa a kan Arvin da yake durkushe a saman gwiwowinsa. Zaro idanuwa waje sosai ya yi, cikin sauri ya ce "Cherish who is this guy that look like our Arvin over?". Kasa magana ta yi, sai zare idanuwa take yi. Matsowa kusa da table ɗin nata Lion ya yi, cikin tafasar jini ya ɗago da idanuwansa da suka yi jajir, ya saukesu a kanta, fuskarsa tamkar wanda aka aikowa da sakon mahaifiyarsa ta mutu, jikinsa har wani irin tsuma yake yi, kansa na wani irin sara mashi, yanzu ko ba'a bashi amsa ba ya sami amsarsa, domin wannan likitan da ya shigo yanzu ba kowa bane face ainahin Dr William, kuma ga dukkan alamu mijin Cherish ne, a yanzu komai ya bayyana, abu ɗaya Lion yake son sani, tayaya aka yi hakan?!! Shi dai yasan Dr William a wajen matsafan can yake, to ya aka yi ya dawo wajen su Cherish? Shi fa Lion dama ya zo bincike ne a kan Cherish ta gaya mashi ina ne gidan tsafin kakan nasu, dan a binciken da ya yi tana da masaniyar in da gidan yake, kuma tabbas before ta taɓa aiki da su, bai taɓa kawowa ransa Dr William yana tare da ita ba, to ya aka yi hakan?!!. "How!!! How you did all this?!! How Cherish?!!!" Cewar Lion ɗin, ya faɗa cikin ɗaga murya. Tsawa Dr William ɗin ya daka mashi a kan waye shi? Kuma waye ya bashi dama ya shigo cikin office na matarsa ya yi magana da ita? Har kuma ya ɗaure mashi yaro da kyalle?. Wani irin mahaukacin tsawa Lion ɗin ya dakawa Cherish ɗin har sai da ya sanyata ta buɗe baki babu shi, sam bai bi ta kan Dr William ɗin ba, yanzu daga bakin Cherish yake son jin magana, shi kuma sir Arvin yana ta ƙoƙarin kwance hannunsa dan ya yi faɗa da Lion ɗin a kan iyayen nasa da yake ƙoƙarin cinwa zarafi, duk cikinsu an rasa wanda zai iya kiran security's, da alama duk jini ne yake fusgarsu yasa suka kasa kiranwa Lion ɗin security's. Murya na kerma Cherish ɗin ta ce zata gaya mashi gaskiyar abin da ya faru, ya zauna. Cikin tsawa ya ce mata ba zai zauna ba, babu ruwanta da shi, kawai ta gaya mashi gaskiya ko kuma yanzu ba sai anjuma ba ya kasheta har lahira!!. Cikin sauri Dr William ya tambayeta wai wanene Lion ɗin nan? Daga ina ta san shi?. Ɗaga wa Dr ɗin hannu ta yi, alamar ya yi shiru kawai su saurareta su ji. Shirun suka yi, suna sauranta, ita kuma zama ta gyara tare da fara yin magana kamar haka. "A takaice dai tun muna one hundred level a school namu Harvard university Washington DC nake tsananin son Dr William, sai dai shi baya kula kowa, tsoronsa ma nake ji, because he is a dangerous boss, ba shi da sauki ga zafin rai, duk wanda ya bi ta hanyarsa ma take shi yake yi ya wuce, ina tsananin tsoronsa da yasa ban iya bayyana mashi soyayyata ba, muka cigaba da tafiya a haka har na haɗu da wata friend ɗina ƴar kasar Russia mai suna A'isha (gwaggo kenan, dan su ainahi basu san gwaggo tana da alaƙa da Nigeria ba, dan duk takardun makarantarta ya nuna daga kasar Russia ta fito, idan baku mance ba bata yi zaman Nigeria ba, so takardan ɗan kasa da komai nata na Russia ne, shiyasa suka san ita ƴar Russia ce kasarsu Naurat kenan, idan baku manta ba ita ma gwaggo ta faɗa lokacin da suka haɗu da fake William, ta ce mashi dama baka san ni ƴar Nigeria ba ce ko? So basu san tana da alaƙa da Nigeria ba sam, haka zalika a yanzu Cherish bata san Lion ɗan gwaggon bane, yanzu labari take basu ba tare da tasan waye shi ba, fatan kun gane?.) Mun yi ƙawance mai nisa tare da A'isha, ina sonta sosai, saboda tana da kirki, kuma in the first place da gaske muke ƙawancen namu, da gaske nake sonta har cikin ra'ina, shigowar Dr William rayuwarta ne yasa na tsaneta, saboda ina son Dr William tun kafin A'isha ta san shi, shi kuma sai ya zo ya fara sonta, amma haka na danne na jure muka cigaba da tarayya da A'isha ba tare da na nuna mata cewa ina son Dr ba, na yi ƙoƙarin cire Dr a ra'ina, amma abin ya ci tura, na kasa, saboda ina son shi da gaskiya, wani abin haushinma shi ne, son nashi karuwa mani yake yi a kullum, hakan yasa na fara tunanin kashe A'isha, sai dai ban kai ga aiwatar da hakan ba suka yi aure da Dr kuma iyayen Dr suka mutu, wannan dalilin yasa na ɗan dakata da shirin kasheta da nake yi, muka yi zama a haka tsawon watanni kafin na zo nan kasarmu hutu, to a nan ne na sanar da auntyna halin da ake ciki, sai ta ce to na juyarwa da Dr ɗin tunani ta yadda zai tsani Aishar mana kawai, ba sai na kasheta ba tun da nace ina sonta, hakan tasa na ɗauki shawarar aunty na cusawa Dr tsanar A'isha, time da na koma hutu na sami A'ishan da Dr sun yi faɗa har sun raba gida, a lokacin har A'isha ta ce ba zata kyale shi ba sai ta kashe shi, saboda ya ci amanarta, ga ciki a jikinta ya barta da shi, na rinƙa bata hakuri tamkar ban san komai ba, alhalin kuma nasan komai, so in takaice maku labari ban san ya aka yi uncles ɗin Dr suka san cewa na tsani A'isha ba, ina zaune a gidana uncle na Dr wani wai Anderson ya zo gidana a daddare, to a nan ne suka bani aikin na ɗaukewa Josephine hankali ta dai'na ibada ita da A'ishan na tsawon awanni, saboda zasu yi amfani da hakan su juyarwa da Josephine tunani, ita kuma A'isha zasu sanyata ta amsa da bakinta ta bada ɗan da zata haifa domin su ɗauki fansar jinin Roshan da Dr William ya salwantar, suka yi mani alkawarin zasu bani Dr William idan na yi masu hakan, ni kuma ina son Dr sosai, dan haka sai na yi iya kan ƙoƙarina na aikata abin da suka ce, bayan sun juyarwa da Josephine kwakwalwa, suka sanyata ta sa A'isha ta bada ɗan da zata haifa da kanta, (Kunsan labarin yadda gwaggo ta kare da Dr William, so ba sai na sake maimaita shi ba, dan haka zan tsallake.) So a takaice bayan A'isha ta haihu sun ɗauki yaron, sai suka ki cika mani alkawarina da suka ɗauka mani na bani Dr William, sai suka ce mani ai shi ma mai laifi ne, dan haka kashe shi zasu yi, shi ne ni kuma na gwada masu cewa duk duniya babu in da ya kai ƙasar China iya tsafi da makirci, na yi wasa da hankalinsu na ra'ina masu wayon da har yanzu basu iya gane gaskiya ba, na yi amfani da tsafin kanana ni ma na shiga har cikin Daular tasu na ɗauki ainahin Dr William na sanya masu na karya, har zan tafi sai na kalli ɗan A'isha suna ƙoƙarin yin tsafi da shi, shi ne shi ma na ɗauke shi na yi amsani da tsafina na basu wani yaro na karya, abin da yasa na ɗauki yaron kuma, saboda da iya gaskiyata ina son A'isha, kawai soyayyar Dr William ce ta rufe mani idanu yasa na tsaneta, amma da na san na sami Dr, sai na ɗauko ɗan nata na rike, daga nan muka dawo ƙasar nan China da zama, na shafewa Dr William tunanin kowa a rayuwarsa sai ni da ɗansa kuma ɗan A'isha wato Arvin, mu biyu kawai yake tunani, dama already mun gama karatu, sai na buɗe mana karamar hospital kafin muzo mu boɗe babban nan da kuɗi ta zauna, mun yi aure da Dr William kuma mun haifi yara biyu, da Handsome da Pinky, su ne yaranmu, shi kuma Arvin ɗan A'isha ne, amma bai taɓa sanin cewa shi ba ɗana bane, saboda na rike shi da amana, a kullum ina jin zafin cin amanar mahaifiyarsa da nayi hakan yasa na rike shi da amana ko zan goge zunubina dana aikata, su Pinky basu san shi ba ɗana bane, kuma tun daga lokacin ban sake jin labarin A'isha ba, su Josephine duk na rufe babinsu, muna rayuwarmu cikin tsantsar farinciki da kaunar juna, Dr William ma ba ya iya tuna kowa sai mu, saboda na juyar mashi da kwakwalwa, har yau yanzu da nake yi maka magana su His Excellence basu iya gane cewa na ɗauki Dr William da kuma Arvin na gaskiya na sanya masu na karya ba, dan tsafinsu karami ne, mune iyayensu a tsafi, wannan shi ne a takaice labarin abin da ya faru, amma kai kuma da kake kama da Arvin nawa waye kai?!!". BABBAR MAGANA WANNAN SHI NE GABA DA GABANTA WAI ALJANI YA TAKA WUTA, GA IYAYEN SU HIS EXCELLENCE A IYA TANTIRANCI. Ta kai karshen maganar cikin raunin murya. Haƙiƙa Cherish ta cuci gwaggo, babban cuta mafi muni da ta yi mata ma shi ne yadda ta bar Arvin ya taso a Kriste, kenan daman musulcin karya ita ta yi? Duk dan ta ci amanar gwaggon, duk dan ta sami kusanci da su ta cutar da su, yanzu Arvin yana da 32 years, amma yana Kristen, ta cuci Dr William ta bar shi a Kristen tsawon shekaru bayan ya musulunta a da can baya, ko iya wannan cuta aka barta da shi ta gama cutar gwaggo sosai. Shiru Lion ɗin ya yi yana tunanin me ya dace ya yi wa wannan shaiɗaniyar? Bawan Allah kullum yana cikin jin bala'in da karamar kwakwalwa ba zata iya ɗauka ba, ya gama jin nasu His Excellence, yanzu kuma ga wani sabo na Cherish, sai kuma waye next? Dole Malika ta ce suna da ciwo a cikin rayuwarsu, ciwo kam babba kuma ba karama ba, bayin Allah, ga uban makudan dukiya, ga mulki, ga isa da izza, komai sun tara, amma suna cikin matsanancin ciwo da tarin tarihi marasa kyau da rashin daɗin ji!! Shi kuwa Dr William ko kaɗai ma bai iya tuna komai ba, duk wannan labari da Cherish ɗin ta bada, bai iya tunano komai ba, saboda ta juya mashi ƙwaƙwalwar ne, amma shi Arvin ya ji komai, saboda shi babu abin da ta yi mashi, bata juya mashi ƙwaƙwalwa ba, kawai dan yana jariri ta ɗauke shi ta rike shi har ya girma ne yasa yake ɗaukarta a uwa, amma ba abin da ta taɓa daga jikinsa. Dan haka ya ji komai, a yanzu ya ji ba ita ta haife shi ba, saura Dr William...... Yau ake yinta gaskiya, TRIPLETS gidan surprise, yau kuma kun ji ta in da muka juya, gidan cakwakiya gidan ruɗani, waye ya taɓa tunanin Dr William yana ƙasar China? Waye ya taɓa tunanin su Lion suna da wasu ƴan uwa, Arvin, Handsome da kuma Pinky? Tun da kuka fara karatun littafin TRIPLETS waye ya taɓa wannan tunani? To dai ga shi yau gaskiya ta fito cewa su Pinky dai ubansu ɗaya da su Lion, tashin hankali da ba'a sanya mashi date! Wannan shiri rikici da cakwakiya!! Kada dai daɗin labari yasa ku manta da cewa kuna karanta wannan daddaɗar labarin ne daga Alkalamin FATEEMA ZAHRA MUSA, A.K.A PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA MAI ABIN BAN MAMAKI 🤙, zan fa tashi kanku a next book na ina kara gaya maku, ku shirya da kyau, dan TRIPLETS dai remain few pages mu kai karshensa In Sha Allah ❤️ ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 20/5/2024 E35 Dan haka ya ji komai, a yanzu ya ji ba ita ta haife shi ba, saura Dr William. Ya jima shiru yana tunanin kalar hukuncin da zai yi mata kafin ya ɗago kai ya kalleta. "Let's go". Shi ne abin da ya furta mata a sanyaye. Ya kai karshen maganar kuma tare da juyawa ya kwance wa sir Arvin hannayensa da ya ɗaure mashi, sannan ya juyo da kallonsa a kan Dr William da yake tsaye yake binsu da kallon kawai. "Before we go, I want to know who are you?". Ta faɗa tana mai dafe sai tin zuciyarta, dan a tsananin tsorace take, tana tsoron ta ji cewa Lion ɗan gwaggo ne, duba da yanayin uban kamanin nan da yake a tsakaninsa da sir Arvin, idan har ya zamana da gaske ɗan gwaggo ne kamar yadda take tunani, to ta san ba makawa sai ya hukuntata. Ko kallon in da take bai sake yi ba, dan wani haushinta ma na musamman yake ji, yadda ta bar mashi ɗan uwa ya taso a Kristen, ta mayar mashi da mahaifi Kristen, bugu da kari ta raba zuciyar masoya, ta raba gwaggo da mijinta, sannan ta rabasu da iyayensu, basu ta so da ko guda ɗaya daga cikin iyayen nasu ba, ba uwar ba ba uban ba, kuma kaso tamani cikin ɗari na laifin ita ta aikata shi, domin da bata shiga tsakanin Dr William da gwaggo ba, wlh su Anderson basu isa su rabasu ba, basu isa su shiga tsakaninsu ba, saboda idan suna haɗe da kai, suna ibada sosai, to fa babu abin da ya isa ya rabasu sai mutuwa, shiga tsakanin nasu da ta yi ne, yasa suka rabu, bayan sun rabu kuma hankalin kowannansu a tashe, saboda suna son juna, dole damuwar da suke ciki ta rabuwar tasa ba zasu rinƙa ibada yadda ya kamata ba, da wannan dama su Anderson kuma suka fara yin amfani, so idan kuka duba abin kaso tamanin cikin ɗari laifin Cherish ɗin ce, hakan yasa Lion ɗin ya ji sam baya son sake ganin face nata ma a rayuwarsa!!. Yana kwance sir Arvin ya miƙe tsaye tare da fara bin Cherish ɗin da kallo, yana mamakin yadda ta zauna ta zayyano waɗan nan bayanai dallah dallah kamar wadda ta aikatasu a yanzu, tsawon shekaru 32 bata mance komai ba, tsabar ita da kanta ta san ta zalinci mutane dayawa, wannan akwai mai bakar zuciya!. Kasa ce mata ko uppan ya yi, saboda wani irin jiri ma da yake gani, kansa yana sara mashi, jin abin yake yi tamkar a mafarki. A hankali ya dawo da kallonsa a kan Lion dake ta faman latsa wayarsa kamar mai tura wata saƙon. Kyawawan laɓɓansa irin na TRIPLETS ya motsa yana son ya wa Lion ɗin magana, sai dai ina, bai kai ga yin maganar ba numfashinsa ta ɗauke diff. Sulalewa ya yi zai zube ƙasa, tamkar Lion ɗin yana ganinsa, bai bari ya kai ƙasar ba ya taro shi da sauri, sir Arvin ɗin ya faɗa a saman Lion chest nasa. Hankali a tashe Dr William ya nufo wajen yana ambatar ARVIN!!! ARVIN!!! Yana magana ne da ɗaga murya. Ita ma Dr Cherish cikin ɗaga murya ta fara ambatar sunansa tare da baro in da take da nufin ta kariso wajen. Wani irin gigitaccen tsawa da Lion ya daka masu ne yasa daga Dr William har Dr Cherish ɗin suka kasa karisowa in da yake, ya ce baya bukatar ganin Dr Cherish a kusa da su. Mayar da wayarsa cikin aljihunsa ya yi tare da gyara tsayuwarsa ya saɓi sir Arvin ɗin a saman kafaɗunsa, kai tsaye waje ya nufa da shi ba tare da ya bi ta kansu ba. Da sauri suka rufa mashi baya, a haka suka fito harabar katafaren hospital ɗin. Ganinsu a haka yasa jiga jigan bodyguards ɗin sir Arvin ɗin suka yi sauri fara buɗe masu gidan baya na motocin nasu, a gidan baya na motar sir Arvin ɗin ya kwantar da shi, sannan ya ciro kuɗi dollars in his pocket ya bawa ɗaya daga cikin bodyguards ɗin a kan ya kaiwa mai taxi ɗin da ya kawosa. Lion yana da adalci sosai, baya taɓa tauye haƙƙin wani, baya taɓa tauye wani, a koma ina yake yana ƙoƙarin saukewa kowa hakkinsa da ya rataya a wuyarsa, ya ci sunansa na shi kaɗai ma gayyace mai zaman kanta, yana da tarin abubuwar da kwakwalwar zaratan maza dayawa ba zasu iya ɗauka ba, amma duk da haka baya barin wani abin nasa ta taɓa haƙƙin wani, a kowani hali yana ƙoƙarin yaga dai bai tauye wani ba, shiyasa mutanen U.s suke bala'in son shi, duk da bala'in zuciya, turin kai, zafin rai da kafiya da yake da shi, to yana da adalci sosai na wuce misali. A haka su Cherish suka shiga wannan motocin, saboda sir Arvin, kai tsaye airport Lion ya ce da drivers ɗin su wuce, dan ya kammala aikinsa, so bai ga abin da zai tsaya jira ba. Abin mamaki kuma abin al'ajabi shi ne, suna isa airport suka isko gabaɗaya bodyguards na Lion ɗin a tare da su Handsome and Pinky. Sosai Dr Cherish ta yi mamakin ya aka yi su Pinky suka zo airport?. (Ni kuwa na ce mata an gaya maki Lion ɗin wasa ne? Ai bai fito ba sai da ya shirya, kuma kafin ya kai muƙamin da yake kai ya take irinku dayawa, ya takeku kamar ƙuda a gabansa🥱🧐) Suna isa airport ɗin ya fito tare da sake saɓar sir Arvin ɗin a kafaɗarsa, cikin jet nasa ya nufa da shi, da mamaki su Cherish suka tsaya a baya suna kallon ikon Allah. Jim kaɗan ya fito daga cikin jet ɗin bayan ya kwantar da sir Arvin a saman luntsuma luntsuman sofas dake a ciki. A kofar shiga jet ɗin ya tsaya tare da yi wa Handsome alama da hannu a kan yazo. Gabaɗaya Handsome ɗin yana ruɗe, sai wani kallon Lion ɗin yake yi, saboda tsananin kamar da ya gani na sir Arvin, ita kuwa Pinky tana ganinsa ta taho da gudu ta rungume shi tana ambatar sunan sir Arvin, dan a tunaninta sir Arvin ne. Hannu Lion ɗin ya kai ya ɗauketa cancak tamkar yadda sir Arvin ɗin yake yi mata, a saman Lion chest nasa ya ɗaurata, ba tare da ya kallin face nata ba ya juya tare da yi wa su Dr William dake tsaye alama da hannu a kan su zo, dai'dai lokacin kuma Handsome ɗin ya kariso wajen hannunsa ɗauke da password nasu shi da iyayen nasa, dan Lion ɗin da ya tura a ɗauko mashi su, sai ya ce bodyguards ɗin nasa su sanyasu su taho da password ɗin su gabaɗaya, dan U.s zasu wuce, bai ga dalilin zamansu a ƙasar China ba, ya gama aikin da zai yi, ba mai sake dakatar da shi kuma. Sumbata Pinky ta kai mashi a kumatu tana tambayarsa yau ma yawo zasu je wata kasar kamar ranar? Duk a tunaninta sir Arvin ne, sai da Lion ɗin ya juyo da face nasa tare da kallonsa a kanta da kyau, sannan ne ta zaro blue eyes nata waje sosai, dan ta ga ba sir Arvin bane, dama na gaya maku in dai ka yi wa ɗaya daga cikinsu farin sani, to zaka iya banbantasu, dan suna da banbanci, ita kuma Pinky ai bama wanda ya kaita sanin sir Arvin, dole ta gane ba shi bane. Ƙoƙarin sauka daga jikinsa ta yi, ta tsorata sosai har jikinta ya fara kerma, shiru Lion ɗin ya ɗan zuba mata idanu ba tare da ya ce mata ko uppan ba, sannan kuma bai sauketa ba, sai mutsu mutsu take yi tana son sauka daga jikin nasa, dan ta tsorata, kallon yadda jikinta yake kerma ya yi kafin ya mayar da kallonsa a kansu Dr William da suka iso wajen a yanzu, hanya ya basu a kan su wuce su shiga cikin jet ɗin da sauri kada su ɓata mashi lokaci. Hannu Pinky ta kai ta ƙanƙame Handsome dake a kusa da Lion ɗin, kuka ta fara yi tana faɗin "Please Yah Handsome who's this man? Where's my baby?". Dama mafiya yawan lokuta baby take cewa sir Arvin. Kasa bata amsa Handsome ɗin ya yi, saboda shi ma dai bai san wanene bane, abin da zai iya cewa kawai shi ne yana jin Lion ɗin tamkar ɗan uwansa sir Arvin, shi ne kawai. Ganin tana kuka ne yasa Lion ɗin ya ɗaura yatsarsa ɗaya a saman kyawawan lips nasa yana yi mata alama da ta yi mashi shiru, ya yi hakan kuma ba tare da ya sauketa daga ɗaukarta da ya yi ba. Tsananin tsoronsa yasa ta nutsu tsit ta dai'na kukan da take yi, bata da zaɓin da ya wuce ta kwantar da kanta a saman kafaɗunsa duk da tana tsoronsa. Hannu ya sa ya nunawa Handsome ɗin ma cikin jet ɗin a kan ya wuce ciki su tafi. Ba musu ya shiga ciki tun da ya ga su Dr William ma sun shiga. A takaice sai da duk suka gama shi, Lion ɗin shi ne na ƙarshen da ya shiga, sannan aka rufe jet ɗin. Zama ya yi a saman nasa luntsumemiyar sofar ba tare da ya sauke Pinky ɗin daga jikinsa ba, duk da mahaifiyarta ta cuce su, hakan bai hana ya ji yana kaunar Pinky ɗin da Handsome ba, saboda ba laifinsu bane, laifin wani baya shafar wani, bare kuma Pinky yarinyar akwai shiga rai ita ma kamar Rimsha. Daga Dr William har Dr Cherish ɗin sun kasa iya nufar in da sir Arvin yake a kwance a sume, saboda tsoron Lion suke ji sosai, suna son duba lafiyar ɗan nasu su ga menene yasa ya suma? Amma sun kasa iya koda ƙwaƙƙwarar motsi, haka zalika shi ma Handsome, yana son tambayar menene ya sami yayan nasa? Amma kuma ruɗani da tsoro sun hana shi, yana cikin ruɗanin ganin mai kama da yayan nasa da kuma daddynsu over, ga Pinky a gefe, sannan yana tsoron tambayar me ya sami sir Arvin ɗin, dan bai ga fuskar da za'a kawowa wargi ba a tattare da Lion!!. A takaice dai a haka jirginsu ya ɗaga, tafiyar dole, tafiyar da bada son ransu ba, tafiyar da basu shirya mata ba, dan ma dai Lion ɗin ya shirya masu tafiyar ce tun kafin ya zo, dama ya shirya a kan idan ya zo dole ya koma da Cherish U.s, sai dai shi kansa bai san da su Pinky ba sai da ya zo, dole ya sake shirya tafiyar har da su, dan ba barinsu zai yi ba, dole ya ɗaukesu ko dan su karɓi kalmar shahada, ba yadda suka iya tun da ubansu ɗaya, dole kawai su rikesu hannu biyu. To tun da jirginsu ya ɗaga bari mu koma Nigeria muga me ake ciki, wata kila kafin mu dawo sun sauka a U.s lafiya. NIGERIA❤️ Areef dai bai kyale Jehan ba sai da ya sami nutsuwa, ta yi kukanta har ta gaji, ya yi ta juyata son ransa, bayan ya sami nutsuwa kuma sai ya hau rarrashinta a kan ta yi hakuri ba zai sake ba, ƙin kula shi ta yi, ta ki yi mashi magana, sai da ta ga ya miƙe zai kunna wutar ɗakin ne ta yi maza ta rike hannunsa, a kule ta ce "Ni ka mayar mani da kayana jikina kafin ka kunna wutar". Kamar zai yi dariya, sai kuma ya fasa, saboda yanzu ma ya yi laifi sosai, idan ya yi dariya kara yin wani laifin zai yi, dan haka sai ya rufawa kansa asiri kada ya kara takalo faɗa, yasan halin kayarsa sarai. Ita kuma Jehan abin da baku sani ba shi ne, ba dan Allah ta kawo kanta gare shi ba, ba dan Allah ta biye mashi ba, abu take nema a wajensa, kuma kunsan Jehan haka kawai wlh ba zata durkusar da kanta kasa ba, taurin kanta ya wuce tunaninku, duk da yes tana son shi, amma ba zata zo ta bashi hakuri cikin sauki haka ba, kawai tana so ne ta yi amfani da shi ta fito da su Adiva daga gidan Hjyr daɗi, tasan dai shi kaɗai ne zai iya taimaka mata da gaskiya, tana ganin hukuma ba zasu yi gaskiya a kan al'amarin ba, ta yarda da shi sama da kowa, ko daddynta bata yardanwa da zuciyarta ta gaya mashi ba, saboda idan ta gayawa daddyn nata ma bai wuce ya ce su shigar da kara ga hukuma ba, kunga ta gudu ne bata tsira ba, ita kuma tasan da cewa Hjyr daɗi tana da manya manyan mutanen da hukuma ba zasu iya yi mata komai ba, maganinta kawai sai dai a sami tantiri irinta, wannan shi ne dalilin dayasa Jehan ta bada kai lokaci guda, saboda kullum da tunanin su Adiva take kwana take kuma tashi, abin yana ranta sosai, shiyasa ta yi wa Areef kwanciyar ɗaukar rai. Sai dai abin da bata sani ba, shi ne sarai Areef yasan dole da akwai abin da take so yasa ta yarda ta bashi hakuri, ya san halinta sarai fiye da kowa, saboda yasanta a ɓaɗini, idan kasan mutun a baɗini to shi ne kasan shi ba'a zahiri ba, yadda aka yi ya santa a baɗininta kuma shi ne, yana ganin duk abin da take yi a lokacin da take ita kaɗai, a lokacin da kake kai kaɗai shi ne ainahin halayyarka take bayyana, ainahin wanenen kai yake bayyana, so yasan ta a wannan lokaci, yana ganinta ta Camera, ita ce dai bata sani ba, so a takaice ya yi mata sanin da su mummynta ma basu sani ba, dan su zahirinta suka sani ba baɗini ba, yasan abin da zai sanya Jehan ta karya maganarta ta duƙar da kai ba ƙaramin abu bane, dan ta faɗa wa kanta sai dai Yah Areef ya nemeta ba dai ta neme shi ba koda zata mutu, so abin da zai sa ta karya wannan magana ba ƙaramin abu bane, koda kuwa zata mutu, haka take tamkar kanwar Lion a shegen taurin kai. Kayan nata ya ɗauko ya mayar mata a jikinta, yana yi yana ce mata sorry, kin kula shi ta yi, ta ce dai fushi take yi da shi. "Zaki yi wanka a tare da ni?" Ya raɗa mata hakan ne a kunne. Girgiza mashi kai ta yi alamar a'a ba zata yi ba. Why ya tambaya, mikewa zaune ta yi tana faɗa mashi babu wani dalili, kawai ba zata yi bane. Kara jawota jikinsa ya yi yana faɗin "Please mana my Jehan". Ɗan ture shi ta yi. "Ni karabu da ni mun ɓata". Ɗan bakinsa ya sake mayarwa saitin kunnenta ya fara yi mata raɗa "Haba nana my baby, na ce fa na tuba ba zan sake ba, please mana, mu yi wanka a tare, zan kashe wutar toilet ɗin sai na kunna blue light, kinga shi babu haske sosai". "Kana son mu yi wanka a tare? Kuma kana son na dai'na fushi?". Ta tambaya tana ɗaura hannunta a saman ɓul ɓul ɗin breast nasa, dan ma kada ya yi mata musu a maganar da zata gaya mashi. (Ba shakka Jehan ta cika ƴar duniya 😂 bafa abin da bata sani ba yarinyar nan😂 harda fara matsa mashi ɓul ɓul nasa dan kada ya yi mata musu idan ta faɗi bukatarta 😂 Maman Yasmin come forward, irin tarbiyar da kika bata kenan ba?🤔😂 Yaudara kiri kiri😂 zata cuci bawan Allah bai ji bai gani ba🧐😂) "Yeah my baby, ina son muyi wanka a tare". "Okey promise me that duk abin da nace kayi mani zaka yi?". Shiru ya ɗan yi, dan yasan halinta sarai, yanzu sai ta jefa shi cikin wata cakwakiyar, amma tun da yana sonta, sai ya ce "I promised you in dai abin bai kaucewa Shari'a ba, bai kuma saɓawa Allah ba, to tabbas zan yi maki my baby". Kara matsa mashi ɓul ɓul ɗin breast ɗin nasa da ɗan ƙarfi ta yi har sai da ya ce "Wash my baby, so kike na koma ruwa ko?". Hannu ta kai ta ɗaura a saman kyakkyawar lips nasa tana faɗin "To ai ko ka koma ruwan ma kayan ka ne, ni taka ce, yanzu dai muje mu yi wankar, sai kazo na baka abinci a baki kafin na gaya maka abin da nake son ka yi mani, nasan kana jin yunwa sosai, ka bari can cikin dare sai ka koma ruwan". Haƙiƙa ya yi mamaki sosai da jin maganar nan tata, saboda bai taɓa tunanin ta iya magana har haka ba, wai zata bashi abinci a baki dan tasan yana jin yunwa, kuma da tsakar dare ya koma ruwa, wato cikin dare zasu yi wasa, bai taɓa tunanin ta iya waɗan nan abubuwa dukka ba, yarinyar nan ba shakka idan aka barta da namiji sai ta kwance mashi notikan kwakwalwa, dama an ce ka guji mutun mai shiru shiru, dan ya wuce tunaninka, wannan shiru shirun da yake ɗin ka barshi a haka, idan ka sake ka bari ya buɗe baki, to sai ka zama wawa a gabansa, kuma ba shakka hakance, idan namiji ya kuskura ya shiga hannun Jehan, wlh sai Allah ne kawai zai kwacesa, dan ta iya duk wani duniyanci, barema idan tana da bukatar ayi mata abu, tamkar mage mai kwanciyar ɗaukar rai take zama, sa'ar Areef ɗin dai ɗaya da Allah yasa da iya gaskiyarta take son shi, tsakani da Allah take son shi, banda haka da zata wahalar da zuciyar bawan Allah'n nan ba kaɗan ba, sai dai Allah ba azzalumin bawansa bane, sai dai bawa ya zalinci kansa, da Allah ya tashi kamata sai ya cusa mata son mijin nata kamar hauka, ba zata iya rayuwa babu shi a gefenta ba. Ganin ya yi shiru ya faɗa duniyar tunani ne yasa ta shige cikin Lion chest nasa tana saka mashi kukan shagwaɓa tare da fara shafa ɓul ɓul nasa. Rungumeta sosai ya yi yana faɗin "Menene kuma?". "Katashi muje mu yi wanka mana, amma ka zauna kana wani tunani, yanzu tunanin me ma kake yi? Ba dai na wata macen ba ne?". Nisawa ya yi kafin ya miƙe tare da ɗaukarta cak, duk kaifin ƙwaƙwalwa irin nasa yau Jehan tana neman sanya shi ya ji duk tunaninsa ta tsaya cak, tana neman kwance mashi lissafin ƙwaƙwalwa, ya rasa a wani point zai ajiyeta, ga shi ma taki yarda ya kunna wutar ɗakin bare ya ganta ido da ido, bai san cewa gara mashi ma da bai kunna wutar ba, dan idan ya kunna waɗan nan shegun sexy eyes ɗin nata kara birkita shi zasu yi, dama can yana kaunar idanuwan nata, shiyasa yake ce mata da idanunta kamar ball, to idan ya kunna wuta suna ganin juna, idan ta juta mashi fararen idanun nan sama cikin kisisina ai sai ya kara ruɗewa ya birkice ya rasa ina zai sa kansa. (Akwai ƴan duniya kala kala a TRIPLETS, amma bana jin akwai biyun Lion da Jehan 😂 kamar dukkansu nonon gwaggo suka sha😂) Bai sauketa a ko'ina ba sai a cikin tsakiyar toilet, da yake da akwai haske wuta a toilet ɗin, sai ya zubawa face nata idanu yana kallonta cike da tsantsar so da kauna. Wani irin kallon soyayya ta wurga mashi tare da ɗan turo baki a shagwaɓe ta ce "To me kake wani kallona kuma? Kafa ce zaka kashe wutar toilet ɗin". "Ina, ina my baby, ba zan iya kashe wannan wutar ba, barni na kalli matata". Ya kai karshen maganar tare da jawota jikinsa sosai, sai a lokacin ta lura da babu kaya a jikinsa, tamkar zata zunduma mashi ihu, sai kuma ta daure ta cije ta kwantar da kanta a saman Lion chest nasa tare da runtse idanuwanta gam. "Jehan". Ya ambaci sunanta cikin sanyin murya. "Na'am my baby". Ta amsa mashi. Shiru ya ɗan yi yana jin sautin sunan my baby da ta faɗa, ko da sunan wasa bata taɓa kiransa da hakan ba, wani irin daɗi na musamman ya ji tana ratsa shi. "Muje nayi wa matata wanka ko?". Ya kai karshen maganar yana shafa kanta izuwa tsakiyar bayanta. Kai kawai ta gyaɗa mashi kafin ta ɗan raba jikinta da na shi, sai dai taki buɗe idanuwanta, dan tsoron ganinsa babu kaya take ji. Wucewa ya yi ya je ya haɗa masu ruwan wanka, tana tsaye idanu a rufe har ya dawo wajen nata, cancak ya ɗauketa sai cikin jacuzzin. Wash ta ɗan furta saboda yadda ruwan yake da zafi sosai, su kuma TRIPLETS sun saba yin wanka da ruwa mai zafi sosai, saboda sanyin kasarsu, so abin sai ya zamar masu jiki. A takaice a cikin ruwan ma bai kyaleta ba, sai da ya yi ta wasa da ita son ransa, sannan ya yi mata wanka, ya yi ya yi a kan ta yi mashi wankar shi ma, amma taki yarda ta yi mashi, haka ya hakura ya yi wa kansa, ya naɗota a towel suka koma cikin ɗakin, a saman bakin bed ya sauketa tare da wucewa ya kunna wutar ɗakin, sannan ne ya wuce izuwa dressing room nasa. Kayan barcinsa masu kyau da tsada ya sanya a jikinsa, sannan ya ɗauko mata kala ɗaya, da kansa ya sanya mata, bata hana shi ba. Bayan sun kammala ta sauko kasa ta fara zuba mashi abinci, kusa da ita ya zo ya zauna, sai kallon face nata yake yi cike da so da tsananin kaunarta tamkar wani ya ce zai kwace mashi ita. "Baby gobe zaki rakani wani waje fa". Ya faɗa yana tara mata gashin kanta dake zubo mata a wuyarta idan ta sunkuyar da kai kasa tana zuba abincin, kayan barcin nasa babu hula, hakan yasa kanta yake a buɗe, ga gashin da danshin ruwa a jikinsa, basu busar da kan nasu ba, saboda Areef ɗin yana jin yunwa sosai, sai ta ce ya fara cin abinci kafin su kammala komai daga baya. "Okey tom". Ta faɗa tana dago da kallonta a kansa. A duk lokacin da ta sauke idanuwanta a kansa, sai ta ji tamkar ta shige cikin jikinsa su cure su zamo abu guda kawai, saboda tsananin son da take yi mashi. "You are so very very beautiful my baby". Ya faɗa yana kai hannunsa ya ɗan shafi gefen face nata. Wani irin kallon ta wurga mashi da waɗan nan dara daran idanuwan nata masu rikita shi. "Ban kai ka kyau ba ai my baby, yanzu dai ka ci abinci". Ta kai karshen maganar tare da ɗebo abincin a spoon ta kawo mashi saitin ɗan bakinsa. (Idan ba wani abin Jehan ta shirya ba yaushe zata tsaya zuba waɗan nan kalamai fisabilillahi 🤌😂 kun ji fa har da nuna damuwa da ya ci abinci yana jin yunwa 😂 har da bashi a baki yau🤌 innallilahi Jehan wan kill me with laugh 🤌😂 harda kiransa da baby, dan ma Allah yasa shi ma Areef ɗin ba tayan baya bane, da ai ba mai kwatarsa a hannun wannan yarinya ta maman Yasmin 😂) A hankali ya buɗe ɗan bakin ta zuba mashi, lumshe idanuwansa ya yi yana mai matuƙar jin wani irin daɗi yana ratsa shi kai, kai, kai nima haka nake jin daɗi idan ina shan Maltina mai sanyi 🧐 haba mana, ni masoyan nan sun fara isata🥲 dan haka zan dakata a nan sai gobe kawai in Allah ya kai mu, ina dalili? Kowa sai love yake sha sun barni da kayan takaici🤌😂 na fara kishi🥱😂 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 21/5/2024 E36 A hankali ya buɗe ɗan bakin ta zuba mashi, lumshe idanuwansa ya yi yana mai matuƙar jin wani irin daɗi yana ratsa shi. "Did you eat yours?". Ya faɗa yana kallon cikin kwayar idanuwanta, ita ma kallonsa take a cikin idanu. Gera ɗaya ta ɗaga mashi tare da kashe mashi ido ɗaya kafin ta ce "Yeah, amma kuma idan zaka bani abaki zan kara ci". Ta kai karshen maganar tare da sake ɗebo mashi wani abincin ta kai mashi saitin ɗan bakinsa. Karɓa ya yi yana faɗin "Dole zan baki a baki mana, because gobe da sassafe zamu fita da ke, ba zamu yi breakfast a gida ba, yanzu zan kara baki ki ci sosai, dan ba ma lallai mu yi breakfast on time ba". Ya kai karshen maganar yana kai ɗan yatsarta ya shafi lallausar lips nata. Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce "Wai Yah Areef ina zamu je ne?". Tana magana tana kara ɗebo mashi abincin. "Gidar Hjyr daɗi". Ya bata amsa cikin halin ko in kula, sannan ya yi maganar like bai ma san me ya faɗa ba. Zaro dara daran idanuwanta waje ta yi, sam bata san lokacin da a dubu ɗari ta ajiye spoon na hannunta tana kallonsa ba, a lokacin shi kuma ya mayar da kallonsa a saman abincin, ganin ta ajiye spoon ɗin ne yasa ya ɗago da idanuwansa a kanta. "Lafiya?". Ya tambayeta yana tsareta da idanu. "Who told you the story about Hjyr daɗi? Ya aka yi ka sani? And them yaushe kasan da hakan?". Ta yi maganar ba tare da ta kyafta idanuwanta ko sau ɗaya daga kallon da take yi mashi ba. "Maso tsuntsu ai shi yake binsa da jifa, do you think that soyayyar da nake yi maki is a joke? Do you think that kawai kalmar i love you ɗin ce take yi mani daɗi nake furta maki ita?". Girgiza mashi kai ta yi ta kasa yin magana, fuskarta ɗauke da mamaki ƙarara. Ganin haka yasa ya ture abincin gefe guda tare da jawota jikinsa, calmly ya fara magana. "You are so very very special my baby, ke ɗin mai zuciyar zinari ce, ban taɓa ganin mace mai jarumta irin taki ba, a dai waɗan nan kananan shekarun naki, abin ya yi matuƙar bani mamaki, tun time da kika rabu da su uncle har izuwa time da muka haɗu dake kullum cikin jefa rayuwarki a cikin haɗari kike yi, duk dan ki taimaki wasu, tun time da Rimsha ta yi magana a kan Daular Mutuwa, sai naga yakamata nima na yi binciken a ina matata ta yi rayuwa bayan rabuwarta da su Rimshar, nasan dole yadda Rimshar ta yi rayuwa a wani waje har da Daular Mutuwa, kema ɗin hakance, dama kuma already na fara bincike a kan dalilin da yasa kika kashe Abubakar Salahuddeen da kuma in da kika kashe shi, sai zancen Rimsha na Daular Mutuwa ya zo ya dakatar da ni, da na dawo muka koma U.s sai na faro bincike daga farko tun ranar da kuka je Katsina, tun farkon rikicinki da Farooq Salahuddeen wanda kuma dama shi ne Lion ya kawo shi gidan nan a matsayin yayansa, hakan tasa nasa aka kashe shi, amma fa my baby kin iya dirama, waye ya baki idean da kika shirya wa baban Sadiq wancan muguntar?". Shiru ta lafe a jikinsa tana ruwan hawaye tana sauraronsa, bata taɓa tunanin yana bincike a kan rayuwarta ta baya ba, ya tuna mata da abubuwa dayawa a yanzu, ya tuno mata da su Sadiq, da irin tsiyar da ta sanya suka yi wa babansu shi da amarya, ga kuma rayuwar da ta yi a gidan na Hjyr daɗin, komai ya dawo mata sabo. Jin ta yi mashi shiru ne yasa ya ɗago haɓarta. "Sure my baby, for sure dole ki yi kuka, amma idan bananan ne zaki yi kukar, ina nan babu kukan da zaki yi, you are the best, kin shiga haɗari sosai saboda ki taimaki wasu, i really love, baki barin rashin adalci a wajen da kike zaune, ya isa kukan haka, su friends naki da suke a gidan Hjyr daɗin duk gobe zamu je mu ɗauko su kin ji ko?". Ya kai karshen maganar yana matso da face nasa izuwa saman tata. A hankali ya fito da tongue nasa ya fara aikin lasar hawayen nata. Rungumarsa sosai ta yi a jikinta tare da cusa kanta a cikin kirjinsa tana sakar mashi kuka mai sauti. Sosai ya rikota tare da fara rarrashinta, da iya gaskiyarta yau take kuka, babu makirci ko kuma tsiya, iya gaskiya yau take yin kukan, wani irin azababben sonsa ne ya ninkun mata a cikin zuciyarta. Rarrashinta ya rinƙa yi har sai da ya samu ta yi shiru, sannan ne ya jawo plate na abincin suka cigaba da ci a tare. Sai da suka ƙoshi tab, sannan ta tattare komai ta fitar waje, da kallon so da kauna ya bita har ta fita ta dawo. A kusa da shi ta zo ta zauna, cikin nutsuwa ta ce mashi "Yah Areef am coming, zan je bedroom namu ne". Murmushi kaɗan ya sakar mata kafin ya gyaɗa mata kai alamar to, mikewa ta yi ta nufi waje, sai dai kafin ta fita sai da ta kashe wutar ɗakin, bai damu ba ya miƙe ya haye saman bed ya kwanta yana jiranta. 30 mins a tsakani, yana kwance shiru cikin duhu, sai jinta ya yi a saman jikinsa tana tashin wani fitinannen kamshi mai sanyayya zuciya. Wani irin nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya kai hannu ya rungumota sosai a jikin nasa, kasa kasa ya furta "Dama na ce your special my baby". Face nata ta matso da shi dab da tasa, kasa kasa kamar mai raɗa ta fara magana "Like the way you're special ba? Kai makura ne my husband, I really love you more than your expectations". Tsabar daɗi wani irin juyawa da ita ya yi, ya zamana ya yi mata rumfa da faffaɗar kirjinsa, lips nata ya fara tsotsa cikin salo, cike da kwarin gwiwa ta fara taya shi ita ɗin ma. Haka suka raba dare suna aiki ɗaya, sai wuraren karfe 2, sannan ya rabu da ita, ya je ya yi wanka, ya fito ya fara sallar dare, ita kuma duk ya gama kashe mata jiki da wasanninsa, ya wahalar da ita son ransa, hakan yasa yana kyaleta ta jawo bargo ta shige, ba jimawa barci ya yi awon gaba da ita. Ba shi ya kwanta ba sai wuraren karfi biyar da ya yi sallar asuba, sannan ne ya ɗan kwanta dan ya ɗan yi barcin awa ɗaya kafin su wuce gidan Hjyr daɗi. Da misalin karfe 6 suka shirya shi da ita, ita ta koma bedroom nasu ta shirya a can, shi kuma ya shirya a nasa, bayan sun kammala shiri dukkansu suna fitowa suka haɗu da juna a parlourn sama. Cool murmushi ta sakar mashi tana sunkuyar da kai kasa, abubuwan da suka faru daren jiya na sambatun da ya rinƙa yi mata ne ya dawo mata cikin ƙwaƙwalwarta, duk sai ta ji kunyarsa ya kamata, ga shi ita ma tai ta yi mashi kuka a kan ya bari ba zata iya jurewa ba. Tsayuwa suka yi shiru a tsakiyar parlourn, ya tsareta da idanu babu ko kyaftawa, ita kuma ta sunkuyar da kanta kasa tana ɗan murmushi. From head to toe yake kare mata kallo, atamfar Rimsha ce ɗinki riga da sket a jikinta, kasancewar kayan Rimsha ce, sai kayan suka kamata sosai, duk wasu shape nata yana bayyana ne, a Duniya Areef yana tsananin son yaga ta sanya atamfa, kyau yake yi mashi sosai, yana son mace ta yi dressing na Hausa Fulani, hakan yasa idan ta sanya zai ɓata lokaci mai tsawo yana kallonta. Jin bai ce komai ba kamar babu shi a wajen ne yasa ta ɗan ɗago idanuwanta dan ta saci kallonsa, yana a cikin dressing nasu kamar kullum, wato shigar kananar kaya, ya ɗaure gashin kansa a baya. Tana ɗago idanuwa suka yi 4 eyes da shi, da sauri ta yi kasa da kanta tana mai kara faɗaɗa murmushin dake a saman face nata. A hankali ya tako kafafunsa ya matso kusa da ita, kafin ta ɗago ta kalle shi ya jawota jikinsa. A tare suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya, haɓarta ya ɗago suna fuskantar juna, ɗan bakinsa ya kai saman tata, ya shanye mata lips balm data sanyawa lips nata dikka, sannan ya saketa yana wurga mata kallon waye ya ce ta sanya lips balm ɗin?. Juya fararen idanuwanta ta yi tare da kwace hannunta ta wuce gaba bata ce mashi komai ba, da kallo ya bita har sai da ta shige bedroom na gwaggo tukun nan ya bi bayanta. Gwaggo na zaune a saman bed suna hira da Aafia da kuma Rimsha, magana suke yi a kan zasu je wajen gyaran jiki kafin gobe su wuce U.s, Rimsha ta ce tana son ayi mata kunshin flowers masu kyau, daga hannunta har wuyarta, da alama da gangan ta buƙaci yin haka. (Rimsha anya kuwa?🤔 Na dai yi shiru babu ruwana, amma dai kada a mance our Lion baya son ƙunshi🥲🧐) Saman bedside drawer ya zauna, ita kuma Jehan gefen bed ta haye ta zauna. Cikin girmamawa ya ɗagawa gwaggo gaisuwa. Wani irin tsananin farinciki gwaggon ta ji na ganinsu a tare da ta yi, wani sanyi ta ji zuciyarta yana yi mata, hakan yasa ta amsa gaisuwar tasa tana farinciki, sannan ta ɗaura da tambayarsa ko ya yi magana da Lion? Dan tana ta kiran numbersa a kashe. A takaice ya amsa mata da cewa kafin Lion ɗin ya baro kasar China ya yi mashi massage a kan jirginsu zai ɗaga zuwa U.s, so wata kila basu sauka bane yasa numbersa a kashe, amma dai babu damuwar komai ta kwantar da hankalinta. Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Ka yi magana da Auta na ne?". Ɗan kawar da kansa ya yi yana faɗin "Ai idan kina son yin magana da autanki sai kin nemo Heartbeat ta baki wayarta, idan ba haka ba ko kin kira shi ba zaki same shi ba! Wayarsa bata zaman banza, kullum a kan call yake, kawai ki nemo Heartbeat ta haɗaku". Murmushi ta yi tana faɗin "A'a in dai yana lafiya kyale su suyi ta yi, ba ma sai kun nemo mani Akila ba, barshi ya ji daɗinsa abinsa". Ta kai karshen maganar tare da shafa kan Jehan dake zaune tana ta faman satar kallon mijin nata, tamkar wani ya ce zai kwace mata shi. Miƙewa ya yi tare da miƙawa Jehan ɗin hannunsa ɗaya a kan ta kama ta miƙe yana faɗin "Momma bari mu je, take good care of yourself, zamu dawo anjima". Miƙa mashi hannu Jehan ɗin ta yi, rikota ya yi tare da jawota jikinsa, ko kunyar gwaggon basu ji ba a haka suka fice gwaggon tana yi masu Allah ya kiyaye su dawo lafiya. Da harara Rimsha ta bisu kamar su ne suka yi mata laifi, ita kuwa Aafia miƙewa ta yi tare da cewa da gwaggon tana zuwa. Waje ta fito, ba komai ne ya fito da ita waje ba kuma face ta duba ko zata ci karo da Tga, dan da tunaninsa ta kwana, ya tsaya mata a rai, dama shi ne first love ɗinta kafin Dr Nawid. Garden ta nufa, a hankali ta lallaɓa ta shiga, tamkar wani zata leƙa. Babu kowa a ciki, zama a saman sofa ta yi tana tunanin rayuwa. 30 mins a tsakani tana zaune tana tunani, kamar daga sama ta ji an taɓata. A hanzarce ta ɗago kai, daga shi sai pajama launin milk color a jikinsa, fuskar nan dai kamar kullum, a ɗaure kamar hadari, sai tashin daddaɗar kamshi perfume yake yi. Ganinsa yasa ta miƙe tsaye da sauri, cike da tsantsar tsoronsa ta raɓa gefensa zata wuce, tana tsananin sonsa, kuma tana tsoronsa, dan dama da face ɗin Lion dana Tga da kuma Mark idan kaci karo dasu dole ka ji tsoronsu, saboda babu alamar wasa ko kaɗan a tattare da su, yanzun nan zaka nemi nutsuwarka ka rasa! Saboda kwarjini. Hannunta ya riko tare da juyowa gareta da kyau "Where are you going?". Ya faɗa a sanyaye. Girgiza mashi kai cikin tsoro ta fara yi, ta kasa iya buɗe baki ta yi magana. Binta da kallo ya fara yi from head to toe, wani irin yanayi ya tsinci kansa a ciki. Sun jima a haka, sai ƙoƙarin kwatar hannunta take yi, amma ta kasa, daga karshe ma jawota jikinsa mai gabaɗaya ya yi. Fargaba da faɗuwar gaba tare da tsorata yasa numfashinta ya ɗauke diff ta sume mashi a jiki. Sai a lokacin kuma ya dawo cikin hayyacinsa. Rikota da kyau ya yi tare da ɗaukarta cak zuwa saman sofa ya kwantar da ita, mamaki kansa yake yi a kan meya haɗa shi da wannan yarinya bakar fatar kuma? (Ni kuwa nace mashi ai dama mu bakaken fata muguwar shiga rai gare mu😒 wlh duk in da muka shiga dai sai an zauna da mu, kuma ko ba'a so sai an kaunace mu, kalar baiwar ƴan Nigeria kenan!!😏😌) Zama ya yi a gefenta yana ta kallonta kawai. A ɓangaren su Areef kuwa, suna fita Abuja suka nufa, kai tsaye gidan Hjyr daɗi ya nufa, tamkar ya san hanya, sai mamakinsa Jehan take yi, ita da farko a tunaninta ta yi mashi wayo, zata sanya shi yazo gidan ya fitar da su Adiva, bata san cewa already Areef kam ya wuci nan ba, ya wuce tunaninta. Sam ba da niyar tarwatsa gidan na Hjyr daɗin ya zo ba, su Adiva kawai yazo ɗauka, saboda a binciken da ya yi tarwatsa wannan gida sai an shirya, dan haka sai sun koma U.s, idan suka gama da case ɗin zaɓen nan nasu Lion, daga baya zai shirya yadda za'a ruguje wannan tsinannen bakin kazamin gidan. Kai tsaye ya danna motarsa har cikin gidan abinsa, a tare suka fito da shi da ita bayan ya yi parking. Jehan bata karasa tsinkewa da mamaki ba sai da ta kalli yasan hanyar shiga har can cikin in da suka yi rayuwa a baya, tafiya yake yi cikin nutsuwa tamkar wanda zai shiga cikin gidansu, ko a jikinsa. Kai tsaye office na Hjyr daɗin suka nufa, sun kuma yi sa'a tana nan, ta hakimce a saman office chairta, ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya, sai wani taunar chewing gum take yi. Ko sallama bai yi mata ba, kawai ya afka abinsa, dan sallama ta masu daraja ce, ita kuma kazamar kadangariyar bariki ina ta ga wani daraja?. Ita ma Jehan ɗin ciki ta bi shi. Ba tare da ɓata lokaci ba ya ce da ita ina su Adiva?. Tun daga yanayinsa da ta kallah yasa ta sha jinin jikinta, dan bata ga wajen wasa a tattare da shi ba, sai dai kuma da yake ƴar duniya ce, sai ta nuna ita bata san akan me yake magana ba, ta nuna ita fa sam bata san su waye kuma Adiva ba, hasali ma ita dillaliyace mai fitar da ma'aikata masu yin aikatau izuwa kasashen waje, bayan haka ita bata da wata sana'a. Kallon Areef ɗin Jehan ta yi tana faɗin "Yah Areef ka bani izini ni zan tuna mata da su waye ne su Adiva". Jinjina mata kai ya yi. "Na baki izini my D.P.O". Cool murmushi ta sakar mashi kafin ta tako izuwa gaban Hjyr daɗin, kallon sama da kasa ta yi mata kafin ta sanya hannu ta ɗauketa da wani gigitaccen mari. Wani irin ihu Hjyr daɗin ta kurma. "Weeeee hooooooo ni zaki mara Jehan?!". Kallon Areef Jehan ɗin ta yi ta ce "Yah Areef kaga yanzu ta tuna sunana, saura nasu Adiva, in kara saitata a kan hanya ne?". Jehan ba dai karfin hali ba, shi mamakin jajircewarta a kan gaskiyarta ma yake yi, ko zaka kashe Jehan sai dai ka kashe ta, amma ba zata taɓa kaucewa gaskiyarta ba, bata da tsoro a zahiri, ga karfin halin, yanzu da wata ce ko kusa ko alama ba zata iya marin mace babba kamar Hjyr daɗin nan ba, koda kuwa ace bata da kirki, wlh ba zata iya marinta ba, duk da tasan akwai mai tsaya mata a wajen, amma Jehan with her full confidence ta ɗauke ta da mari, kuma har tana ikirarin kara mata wani. A tare su Zinariya da ƴar gold suka shigo cikin office ɗin, jin Hjyr ta yi ihu ne yasa suka shigo da gudu, sun warke daga dukan haukar da Jehan ɗin ta yi masu before ta fita daga gidan. Ganin su Jehan ɗin yasa suka tsaya cirko cirko suna kare mata kallo, ko kallon in da suke bata yi ba ta ce "Ke Hjyr daɗi kike ko waye? Zaki gaya mana in da su Adiva suke ne ko sai na kara maki wani marin?". Yadda ta yi maganar tamkar wata hamshakiyar hukuma mai doka a hannu, cike da confidence abinta. Zinariya ce ta ce "Au Jehan kin dawo kenan? To kuwa yau zaki ci ubanki ne, babu mai karbarki shegiya!". Sam basu lura da Areef ɗin a wajen ba, duk hankulansu na'a kan Jehan da Hjyr kawai. Wani kallon walaƙanci Jehan ɗin ta wurgawa Zinariyar kafin ta ce "Keeeeee ni bance zaki ci ubanki ba sai kece zaki ce zan ci ubana? Kin manta karon mu ta farko kenan? To a da can baya ma kenan, bare kuma yanzu da ke ko da ido kika ganni kin san na wuce dukan kato ko katuwa, sai dai dukan ruwan sama da kuma iyaye wanda suma nasan ba zasu ɗaura hannunsu mai albarka a jikina da nufin duka ba, sai dai su ɗaura hannunsu a jikina dan su samin albarka, ke yanzu kinsan zaren ba kalar yadin bane, ni yanzu bani da lokacinku, kawai ku bani su Adiva nake so, banzaye kazaman banza, sai warin bleaching kuke yi, kamar mutun ya yi amai, shashasshu, karyoyi, kadangarun bariki masu bakin iyaye kawai!!". Hannu Zinariyar ta cire zata zabga mata mari, cikin hanzari Jehan ɗin ta yi ƙoƙarin kai hannunta ta tare mari, sai dai bata kai ga yin hakan ba Areef dake tsaye a gefe yana binsu da kallo yana mamakin confidence irin ta matar tasa ya rigata, damke hannun Zinariyar ya yi tare da ɗauketa da wani gigitaccen mari da ɗayan hannunsa, kafin kuma ya sauke hannun nasa daga marin da ya yi mata ɗin, tuni numfashinta ya ɗauke diff ta sume, dama kunsan ita Zinariya ƴar a lallaɓace, duk duniya ya cinyeta, ta zama ragwaɓaɓɓiya, maza sun yi bidirinsu a kanta ba iyaka, babu wani abin azo a gani da ya saura a jikinta, sai uban talauci, ga muni da bleaching kamar ya kashesu, shegu sai wari suke yi, sun sayar da duk wasu albarkatun da ni'imar da Allah ya yi wa jikinsu, amma har yau sun kasa yin dukiya, kullum suna cikin talauci, dama in dai ta hanyar saɓon Allah ne ba zaka taɓa yin arziki ba, sai dai ka rasa komai naka, daga karshe ka faɗa cikin musifa, ga tsinuwar Mala'iku ga kuma fushin Ubangiji, bugu da kari ga azabar da Allah zai maka, me ribarka na saɓawa Allah to? Tun farkon duniya har kashenta babu wanda ya taɓa cin riba a saɓon Allah, hakan ma ta isa bawa ishara da kuma aya mai girman gaske, duk wanda ya saɓawa Allah tasa bata kyau, Allah ka iya mana ka mana mai kyau, su dai su Zinariya tasu bata yi kyau ba sam sam. Ganin ta sume ne yasa ya saki hannun nata ta zube kasa wanwar kamar wata kayan wanki, guntun tsaki ya ja tare da ɗago da kallonsa a kan Hjyr daɗin. Duk sun yi wani tsuru tsuru da su, tsantsar tsoro ya bayyana a saman face nasu. Jiki na rawa Hjyr ta fara ƙoƙarin kiran waya dan mutanenta masu ɗaure mata gindi su kawo mata agaji. Shiru Areef ɗin ya yi mata, ko a jikinsa, dan yasan call ba zata tafi ba a wannan gida dai, bai shigo ba sai da ya shirya, tsawon watanni huɗu yana bincike a kansu, ya sha aiki kafin ya iya gane komai a kansu, har waɗan da suke ɗaure mata gindi a kasar duk ya sansu, sai dai a yanzu bashi da isasshen lokacin da zai tsaya ya ce zai bisu ɗai ɗai ya kashesu, saboda kurar da suka tayar a U.s ma kawai ta ishesu, ga zaɓe na gabatowa, bugu da kari a yanzu basu da goyan bayan His Excellence, hasalima faɗa suke yi da shi, kuma wasu manya ne daga cikin manyan kasar suke tallafawa Hjyr, so dole sai a gwamnatance za'ayi maganinsu, hakan yasa kawai ya bar batun rushe gidan sai bayan zaɓen U.s, su Adiva ɗin ma abin da yasa ya zo ɗaukarsu shi ne, Jehan tana damuwa sosai a kansu kullum, yasan da hakan, sannan Adiva ƴar uncle ɗin su Jehan ɗin ce, ba zai so wani abin ya sameta ba, ko dan amanar da mahaifinta ya rike wa daddyn Rimshar, shi ne yasa yazo ɗaukarsu kawai. Sam call yaki tafiya, ganin haka yasa Hjyr ta fara ƙoƙarin gudu ta fita daga cikin office ɗin, ita ma ƴar gold ƙoƙarin guduwa ta fara yi dan ta fita. Tsawa ya daka masu wanda yasa dole suka dakata, cikin fusata ya ce ko ta gaya mashi a in da su Adiva suke, ko kuma ya kasheta a nan ya kashe banza! Shi su Adiva kawai ya zo ɗauka, babu ruwansa da su. Bata da zaɓin da ya wuce ta gaya mashi, murya na rawa ta gaya mashi cewa Maryam tana cikin ɗakinsu bata da lafiya, ita kuma Adiva jiya a daddare an fita da ita. Idan ransa ya yi dubu to ya ɓaci a wannan lokaci, sam bai san time da ya ɗauke Hjyr da wani ɗan iskar matsiyacin mari ba. Wani irin ihun azaba ta saki, tsabar azaba bata ma san time da bakinta ya furta masu address ɗin in da aka kai Adiva ɗin ba, sake kara mata wani matsiyacin lafiyayyen marin ya yi, sai gata a kasa ta zube kamar kayan wanki, kamar wata mushen doki. Ita kuwa Jehan tana jin abin da ta ce ta juya a guje ta nufi ɗakin nasu tun da already ta san hanya. Ƴar gold kuwa, tuni idanu ya rai'na fata, jiki sai kerma yake yi, tana jiran ta ji nata saukar marin. Sai dai bai bi ta kanta ba, juyawa ya yi ya bi bayan Jehan ɗin. A kwance rai a hannun Allah suka isko Maryam, sam bata a cikin hayyacinta, bata iya gane su waye ne ma a kanta, ga dai idanuwanta a buɗe, ta yi wani uban rama tamkar wata figaggiyar kaza mai kwanci, harta gashin kanta sai da ya sauya launi, sai Allah ne kaɗai yasan me wannan tsinanniyar Hjyr ta yi mata, ko da Jehan ta ambaci sunanta ma, sam bata iya amsawa, bata iya magana, kusan irin ciwon da A'isha ta yi suka je suka jefar da ita, to kusan hakance ita ma Maryam ɗin take fama da shi. A hanzarce Areef ɗin ya ɗauketa cak, dan gani suke tamkar zata mutu kafin ma su fita da ita daga cikin gida, dan idan baku manta ba a tsakanin ginin farko ba gidan da kuma in da su Jehan ɗin suke da akwai tazara mai yawa, hope baku manta yadda tsarin ginin gidan yake ba?. A hanzarce suka fito da ita, bai sake bi ta kan kowa da yake a gidan ba suka fice. A gidan baya na motarsu suka sanyata, da gudu Jehan ta shiga gidan gaba, shi ma ya shiga mazaunin driver, a haukace ya tashi motar suka bar gidan. Ita kuma Hjyr daɗi tana baje a kasa kamar mushen doki, sai Allah ne ma kaɗai yasan tana raye ko ta mutu, haka zalika ita ma Zinariya, sun ji hannun maza, ƴar gold kuwa, gabaɗaya a tsorace take, sai mamaki take yi ta yaya aka yi su Areef suka iya shigowa wannan gidan nasu da mutane basu iya ganinsa sai wanda Hjyr ta zaɓa zai shigo mata? Abin ya ɗaure mata kai, basu san cewa a shirye da addu'a sosai Areef ɗin ya zo ba. Hospital mafi kusa da gari suka fara kai Maryam ɗin, idan baku mance ba gidan Hjyr daɗi yana ɗan bayan gari ne. Sai da suka tabbatar da likitoci sun dukufa a kanta, sannan ne ya ce su je su ɗauko Adiva kuma a wannan address ɗin da Hjyr daɗin ta gaya masu, haka kuwa aka yi, suka baro asibitin, sun baro likitoci a kan Maryam ɗin sunata fama, a haka suka nufi in da Hjyr ta gaya masu. Bayan sun fito daga cikin hospital ɗin, tambayar Jehan ɗin ya yi a kan ko tasan wannan address ɗin da Hjyr daɗin ta faɗa?. "A'a Yah Areef ban sani ba, amma mu tambayi mutanen da suke wucewar nan mana, kila zasu sani". Jinjina mata kai ya yi tare da yin parking na motar a gefen hanya ya sauke glass ɗinta kasa. Can wani matashi yazo zai wuce, dakatar da shi ya yi tare da yi mashi sannu, sannan ya gaya mashi abin da suke nema. Ɗan zaro idanu matashin ya yi kafin ya basu amsa da cewa "Kai wannan waje fa ba wajen zuwa bane, yana da uban nisa sosai daga nan, sannan kuma............ ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 22/5/2024 E37 Ɗan zaro idanu matashin ya yi kafin ya basu amsa da cewa "Kai wannan waje fa ba wajen zuwa bane! Yana da uban nisa sosai daga nan, sannan kuma kungurmin daji ne sosai, zaku sha tafiya". Kallon Jehan Areef ya yi, saboda da Hausa matashin ya yi magana, su kuma TRIPLETS kun san basa jin hausa ko kaɗan, so bai ji me guy ɗin ya ce ba. Mayar mashi da abin da guy ɗin ya faɗa da turanci ta yi, sannan ta ɗaura da cewa guy ɗin ta ina ne hanyar da zasu je wannan waje?. Kwatance ya yi masu ta hanyar, sai ka fita daga cikin Abujar, sannan ka sauka daga titi ka fara kutsawa cikin daji, sai sun yi tafiyar sama da awa guda kafin su kai wajen, a wajen akwai wani katon dutse mai aman ruwa, daga wajen wannan dutse nen wannan address ɗin yake, tashin hankali!!. Sake gayawa Areef ɗin abin da guy ɗin ya faɗa Jehan ɗin ta yi. Shiru ya ɗan zubawa guy ɗin idanu yana tunanin to ya akayi guy ɗin ya san da wannan waje kenan?. Kamar zai tambaye shi, sai kuma ya share, saboda mugaye a duniya dai ba zasu kare ba, sai dai kawai Allah ya yi mana tsari da su!. Kunna motar ya yi bayan sun yi wa guy ɗin godiya, ɗaukar hanya suka yi babu kama hannun yaro, gudu sosai Areef yake shararawa kamar babu gobe, ita kuwa Hjy D.P.O lefewa ta yi a jikin kujerar motar tare da lumshe idanuwanta tana jin sanyin A.c na ratsa ta. A ɓangaren su Lion kuwa, sun isha Washington DC lafiya, kasancewar ba tafiyar sirri bace, kamar yadda kuka sani ne airport ɗin a cike take tab da manya manyan jiga jigan masu faɗa a ji a kasar, ga jiga jigan sojoji ta ko'ina rike da jiga jigan bindigu masu aika sako babu saɓa saiti, suma ƴan'sanda ba'a barsu a baya ba, sun cike ko'ina suna shawagi, sannan ga ƴan jaridu rirrike da cameras a hannunsu ta ko'ina, jira kawai ake yi ya fito su fara aikin ɗaukarsa a hoto. Sai dai kuma fitowarsa ta tada hazo mai matuƙar kurar gaske, dan kuwa ya fito ne ɗauke da sir Arvin a saman kafaɗunsa, wadda kuma kunsani kamansu ɗaya sak, wasu daga cikin mutanen dake a airport ɗin ma sun kasa banbance Lion na gaskiya, wasu su ce shi aka ɗauko a saman kafaɗa, wasu kuma su ce shi ne ya ɗauko wani mai kama da shi. Kan kace me magana ta karaɗe kasa bakiɗaya, kowa so yake yi yasan wanene ɗayan? Sai dai kuma an rasa mai iya tunkararsa ya tambayesa wanene sir Arvin? Abin da kuka sani ne, kowa tsoronsa yake ji. Aseef dake cikin mota yana jiransu ma bai san time da ya fito waje daga cikin motar ba, saboda sir Arvin, sam Lion bai gaya masu zancen sir Arvin ba, ko Areef yaki sanarwa, kai har gwaggo bata sani ba, ya barsu ne sai ya dawo gidan kawai suga zahiriya da idanuwansu, so abin ya girgiza Aseef sosai, ya kasa hakuri ma har sai da ya tambayi Lion ɗin wanene sir Arvin?. Jama'a duk sun kasa kunne dan su ji amsar da Lion ɗin zai bada, duk wasu ƴan siyasa dake a wajen burinsu kenan su ji amsar da zai bada. Sai dai kuma kamar yadda kuka sani ne ko kallon Aseef ɗin ma bai yi ba bare ya amsa mashi, ya wuce kawai ya kwantar da sir Arvin a cikin mota, sannan ya shiga gidan gaba. Da dai Aseef ɗin yaga da gaske ba zai amsa mashi ba, sai ya daure ya juya ya nufi motar, sai dai bai kai ga shiga ba su Handsome suka fito daga cikin jet ɗin, bodyguards na Lion ɗin suna a biye da su a baya. Da sauri Aseef ya kara zaro idanuwa yana kallon Handsome mai kama da shi, ba shakka Handsome ya yi kama da shi, sai dai ba cancan sosai ba, kama ce dai ta jini, amma Handsome ya fi kama da jinin Chinawa, bai yi zubin Americawa sosai ba. Gabaɗaya jama'a haɗe da Aseef ɗin basu gama tsinkewa ba sai da suka ɗaura idanuwansu a kan Pinky dake rike da hannun Handsome gam, yarinya kyakkyawar gaske kamar ita ta yi kanta, ga shegen shiga rai kamar Rimshar Lion, sannan babbar abin rikitarwa shi ne kama da su Lion ɗin da take yi, kunga kuwa dole ta yi kyau iya kyau ai, saboda wannan kama, ga idanuwanta dara dara kamar nasu, kuma idanuwan blue eyes, ya kuke tunanin kyanta zai kasance? Kama da Lion fa aka ce maku, ai dole nema kowa idan ya kalleta sai ya sake kallonta, mummynta ta ɗaure mata kyakkyawar gashin kanta gida biyu, an zuba mata rebons masu flowers, sai gashin ya yi matuƙar kyau, ga shi dark black, sai kyalli yake yi, sai dai bai kai nasu Lion curly ba. Kai tsaye wajen sauran motocin dake a bayan na Aseef ɗin suka nufa. Sai da suka shiga ciki, sannan ne Aseef ɗin ya iya shiga cikin motarsa shi ma, banda haka ya tsaya ne yana kare masu kallo, ga Dr William a tare da su, sai ya ji tamkar ya je ya tambayi Dr William ɗin cewa shi ne na gaske ko? Kada a sake ra'ina masu hankali, amma ganin yadda airport ɗin yake cike da mutane, kuma kowa jiran kiris yake yi a saki magana wa duniya, hakan tasa ya ja bakinsa ya yi shiru tare da komawa cikin mota zuciyarsa cike tab da mamakin wannan al'amari. Bayan sun kammala shiga ne motocin suka tashi a tare, jama'a kowa bakinciki yake yi na rashin buɗe bakin Lion ya yi magana ko da word ɗaya ne, kowa so yake yi ya sami abin faɗa, sai dai Lion ya wuce tunaninsu, shi ko a gida ma yaushe yake buɗe baki ya yi magana balantana a wajen, wajen ma a airport, a airport ɗin ma wajen da yasan abokan hamayyarsa suna wajen, bugu da kari ga siyasar da yake a gabansa, ai dole ma su datse bakunansu dan samun zaman lafiya, in ba haka ba yanzu sai a canza masu magana idan suka yi, saboda mutun ɗan adam ya wuce tunanin mai tunani!!. Su Cherish sun ga duniya a lokacin da suka sauke idanuwansu a gidan Lion, sai suka ga nasu gidan ma ashe kurkuku ne, su suna jin cewa su masu kuɗi ne, ashe ga nan in da kuɗin kam yake, su nasu ma duk wasan yara ne! Gidansu ko kwatan na Lion ɗin bai kai ba a girma, kyau da kuma tsaruwa, komai ma basu haɗa hanya ba, Lion ya yi masu nisa, dan ma sun yi sa'a sun zo a time da ya kwashe gabaɗaya sojojin an mayar da su barack, ai da sai sun san cewa yes nan fa gidan General of the Army's suka zo, a yanzu kuma His Excellence mai jiran gado, kai gaskiya Lion duniya ne, His Excellence ne mai jiran gado da kansa!. Kauyanci ne karara ya bayyana a fuskokinsu, dan wasu abubuwa da suke cikin gidan Lion sam basu taɓa ganinsu ba, tun daga kan tsarin ginin gidan sun san Daula ce mai zaman kanta, sun san ba wajen wasan yara bane, Handsome dai sai kalle kalle yake yi abinsa, ba zai bari kansa ta kulle ba, duk abin da ya yi mashi kyau sai ya kallah ya sake kallah, ita ma Pinky sai kallo ko'ina take yi, idan ta ga wani abin da bata taɓa gani ba, sai ta tambayi Handsome menene wannan? Shi ma sai dai ya ce mata bai sani ba ta bari anjima zai tanbaya mata sir Arvin idan ya tashi daga barci, Okey kawai take amsa mashi da shi. Basu kara tsinkewa da lamarin wannan Daula ta Lion ba har sai da suka shiga parlourn kasa, a nan ne suka zama ainahin ƴan kauye. Shi kuwa Lion kai tsaye saman doguwar sofa ya wuce ya kwantar da sir Arvin ɗin, sannan ya buƙaci Aseef da ya bashi ruwa. Cike da mamaki Aseef ya wuce ya ɗauko mashi ruwa roba guda, kawo mashi ya zo ya yi, bayan ya karɓa sai ya tsaya a gefensa yana kallon wannan iko na Allah. Su Pinky kuwa har tsoron zama a saman sofas ɗin suke yi, saboda yanayin yadda tsaruwan sofas ɗin suke, sun sha banban da sofas da kuka sani, idan ka gansu ma kai kace wasu jiragene, saboda wasu irin luntsuma luntsuma ne masu numfashi, sun ƙoshi ainun. Shafawa sir Arvin ruwan ya yi. Ajiyar zuciya bawan Allah ya sauke, sannan ya fara ɗan motsa idanuwansa da suke a rufe a hankali hankali. Ganin ya farfaɗo ne yasa Lion ɗin ya mike daga kusa da shi ya koma saman wata sofar, zama ya yi tare da ciro wayarsa ya kunnata, dama ya yi off nata ne, saboda tafiya. Sam bai bi ta kansu Cherish ba, cikin nutsuwa ya ce da Dr William da yake a tsaye yana bin parlourn da kallo. "Dad have a seat". Ya yi maganar kuma idanuwansa na'a kan screen ɗin wayar tasa, ya kunnata yana ƙoƙarin kiran number Areef, dan ya sanar da shi sun isa lafiya, saboda yasan halin ƴan uwan nasa, idan ɗaya daga cikinsu baya nan, to basu samun nutsuwa, bare kuma ace basu yi waya ba, duk suna shiga damuwa sosai, shiyasa duk in da zasu je a duniya, in dai sun sami dama to dole sai sun kira juna, hakance kawai yake samar masu da kwanciyar hankali. Sam Dr William bai yi wa Lion musu ba, saboda duk da baya a cikin hayyacinsa, bai san ma wanenen shi ba, amma yana jin cewa Lion ɗansa ne, saboda kamanceceniya da suke yi da shi kansa, ga kuma kamanceceniya da sir Arvin da suke yi, hakan tasa ya ji cewa lallai Lion ɗansa ne, har cikin ransa yake jin kaunar Lion ɗin sosai, ji yake yi ma kamar yaje ya rungumesa, amma haka ya daure dai, ya sami waje a saman sofa set dake set ɗin kusa da su ya zauna, ya kasa kawar da blue eyes nasa daga kallon Lion ɗin, ya kalli Lion ya kalli Aseef, duk sai ya ji kamar ya je ya rungumi Aseef, yana jin kamar Aseef wani ɓangarene na zuciyar tasa, dama shi Aseef kun san shi da shiga rai kamar Rimshar Lion ɗin, so tun daddynsu bai dawo cikin hayyacinsa bama yake jin wani irin zazzafar kaunar Aseef ɗin. Shi ma Aseef ɗin sai kallon daddyn nasu yake yi, yana son ya yi magana, amma ya yi shiru, saboda yasan ko ya yi magana ma Lion ba kula shi zai yi ba, sai time da yaga damar amsawa zai amsa masu, dan haka sai ya ja bakinsa ya yi shiru tare da zama kusa da Lion ɗin. Sau biyu Lion ɗin yana gwada kiran number Areef, amma bata shiga, hakura ya yi sannan ya kira number gwaggo, a lokacin Rimsha ta tada kanta da cinyar gwaggon tana zuba shagwaɓarta son ranta, ita kuma gwaggon tana biye mata. Sabuwar waya Areef yasa Tga ya sayawa gwaggon tun kafin yazo Nigeriar, tun time da Rimsha ta yi fushi ta fasa mata wayar tata. Bugu ɗaya gwaggon ta ɗauka, dan dama sai neman numbersa take yi a kashe. "Good afternoon momma". Ya faɗa a sanyaye "Afternoon my son, how was your journey?". "Alhamdulillah how are you and my wife?". Bawan Allah komai yake yi yana tunanin Rimsha sosai, tana ransa, bai san cewa ma fushi take yi da shi ba. "Alhamdulillah, your wife gata nan tana zuba mani rigima". Jin abin da gwaggon ta faɗa ne yasa Rimshar ta miƙe tare da saukowa kasa daga saman bed ɗin, tana ɗingisa kafa ta fice daga ɗakin, dan kada gwaggon ta ce zata haɗata da Lion ɗin, a cewarta fushi take yi da shi, baiwar Allah har yanzu bata iya tafiya da kyau, sai dai ta yi ta ɗingisa kafafu, kuma har yanzu tana ɗan jin zafi, barema idan tana tafiya wajen yana ɗan yi mata zafi, dan ma kullum gwaggo bata barinta sai ta shiga ruwan zafi ta gasu, hakan ce ma tasa abin ya yi mata sauki. Da kallon mamaki gwaggon ta bita har ta fice daga ɗakin, dai'dai lokacin kuma Lion ɗin ya ce "Momma please give her the phone, i really missed her, i want to hear her voice". Ya yi maganar kasa kasa sosai, dan ko Aseef da yake a zaune kusa da shi saman sofa ɗaya ma bai ji me ya faɗa ba, dama can kullum maganarsa a kasa kasa take, amma fa idan zai yi magana da Rimsha ko zai yi magana a kanta, yana kara yin kasa sosai da muryarsa, ko kai da kake waya da shi idan ba kana da lafiyayyen kunne ba, bazaka taɓa jin abin da ya faɗa ba. Thank God gwaggon dai ta ji abin da ya ce, sai dai ta rasa amsar da zata bashi, tun farko tarigada ta ce mashi ga Rimshar a kwance a kusa da ita, yanzu kuma ta ce mashi bata nan? Anya kuwa hakan zai yi wu? Ga shi yadda ta ji voice nasa duk a gajiye yake, uwa da ɗa, har tana iya fahimtar halin da yake a ciki ko da waya suke yi, Allahu Akbar, wani abin sai uwa! Allah dai ka kara masu lafiya da nisan kwana, waɗan da suka rigamu gidan gaskiya kuma Allah ya jikansu ya rahamcesu, ya kai haske cikin kabarinsu, daga karshe ya saka masu da gidan Aljannartul firdaus. "Yanzu ta shiga toilet, sai ta fito". Ta bashi amsa da haka ba dan ta so ba!. Shiru ya ɗan yi, duk da mommarsa ce, a wannan magana tata ya fahimci ba dai'dai ta gaya mashi ba, dan shi akwai shi da fahimta over, kuma gwaggon bata saba yin karya ba, dama haka ne, idan baka saba yin karya ba, in kayi sai an gane, duk sai ya ji jikinsa ya yi sanyi, zuciyarsa tana gaya mashi cewa akwai wani abin a kasa, ko Rimsha bata da lafiya, ko kuma dai fushin da ta yi da shi ne har yau bata sauko ba, tabbas akwai wani abin da aka ɓoye mashi, duk sai ya ji ya damu, sai ya ji zuciyarsa babu daɗi, haka dai ya daure ya ce mata "Okey momma let me go and take a bath, daga nan zan yi barci kaɗan, sai dare zamu yi waya, and kada ki manta gobe zaku taso fa kuma, because i really missed you over, and then there's important thing that's waiting for you here". "Okey my son, take good care of yourself, and ka kula mani da my autana sosai, komai yake so ku tabbatar kun bashi". (Bala'i lallai gwaggo, wai komai Aseef yake so a bashi? Dama yaya lafiyar kura bare kuma ta yi zawo?😂) Nisawa ya yi a cikin zuciyarsa yana godiya ga Allah dayasa ba'a gaban gwaggo Aseef ya taso ba, da iskancin nasa sai ta wuce haka, yanzu ma ya suka kare da shi? Amma a haka Gwaggon take cewa ayi mashi komai da yake so? Lallai kuwa da ita ta rene shi lalacewarsa sai tafi haka. Jin ya yi shiru ne yasa ta ce "Son are you okey? What are you thinking?". "Nothing momma, see you later". Ya kai karshen maganar cikin kasalalliyar murya tare da katse kiran. Sai bayan ya katse kiran ne ya ɗago da kallonsa izuwa kan su Handsome dake tsai tsaye cirko cirko, sun kasa zama, ganin parlourn suke yi tamkar ba'a duniya suke ba. Miƙewa tsaye ya yi tare da nufar saman bene yana sanar da Aseef a kan ya kula dasu Handsome ɗin, ya basu wajen zama da ruwan sha tare da abinci, shi bari ya yi wanka ya kwanta ya yi barci. Okey kawai Aseef ɗin ya bishi da shi, sannan ya ce su samu waje su zauna mana, sai a lokacin kuma ya sauke idanuwansa a kan Cherish, ɗan zuba mata idanu ya yi, yanzu kam ko ba'a gaya mashi meyake faruwa ba ya gane, dan gabaɗaya ƴaƴan Dr William shegen kaifin kwakwalwar bala'i ke garesu, yanzu ya fahimci in da komai ya dosa, saboda yasan Cherish a hoto, kuma yaji labarinta, ya san alaƙar dake a tsakaninta da gwaggon, kallon ɗai ɗai ya fara yi wa su Handsome ɗin, dan ya kara tabbatarwa da kansa abin da yake zargi. Alama ya yi wa Pinky da hannu a kan tazo. Da farko kamar zataki zuwa, sai kuma ta tuna cewa ai gidansu suka zo, dan haka bata isa ta yi mashi musu ba, kuma taga su ba masu mugunta bane, tun da sun zubawa sir Arvin ruwa ya farfaɗo daga suma ya faɗa barci bawan Allah. A hankali ta nufesa tana ɗan ɗari ɗari. Kusa da shi ya zaunar da ita yana mai cigaba da kallon face nata. Suma su Cherish zama a saman sofa guda ɗaya mai zaman mutun uku suka yi ita da Handsome ɗin. Welcome Aseef ɗin ya yi masu kafin nan yasa bodyguards su kawo masu ruwa da kayan cima. Bayan ya tabbatar ankawo masu, sannan ya miƙe tare da haurawa sama yana faɗa masu yana zuwa. Okey handsome ha amsa mashi da shi, sannan suka fara cin abubuwan da aka zube masu a gabansu a saman carpet, yunwa suke ji yasa dole suka ci. Sun ɗan yi nisa a ci abinci, miƙewa Cherish ta yi tare da nufar in da take zaton shi ne kitchen, tambayarta lafiya ina zata je? Handsome ya yi, "Am coming i want to check some type of their food". Ta bashi amsa. Shiru ya yi bai sake yin magana ba. Cikin kitchen ɗin ta shiga. Babu kowa a cikin kitchen ɗin, duk sun kammala aikinsu sun fita waje. Su kuwa su Pinky sai cin abinsu suke yi, dole tasa suke cin abincin ma ba dan yayi masu ba, sai dan yunwa da kuma basu da zaɓi, basu isa su ce bai yi masu ɗin ba. After some minutes, bayan sun kammala cin abincin nasu, shiru shiru Dr Cherish bata dawo cikin parlourn ba, miƙewa Handsome ya yi domin ya je ya dubata lafiya bata dawo ba tun ɗazun, da kallo suka bishi har ya shige cikin kitchen ɗin. Wani iri razababben ihu ya kurma tare da fitowa daga kitchen ɗin da gudu, a tare Dr William da Pinky suka miƙe tsaye suna tambayarsa lafiya?. Da gudu Aseef ya sauko kasa daga sama shi ma yana tambayar lafiya kuwa suke yin ihu?. A tsananin ruɗe Handsome ɗin ya gaya masu abin da ya gani a cikin kitchen ɗin. A dubu ɗari kusan a tare Aseef da Dr William suka nufi cikin kitchen ɗin. Cherish ce kwance cikin jini malala a kasa, ta daɓawa kanta wuƙa a ciki, da alama ma ta ɗan ɗauki ƴan mintoci da mutuwa. Zaro idanuwa waje sosai Aseef ya yi, cikin tashin hankali yake tambayar waye ya yi mata hakan? Waye ya kasheta?. Tamkar daga sama ta bayansu wajen kofar shigowa cikin kitchen ɗin suka ji voice irin na Lion yana faɗin "Babu wanda ya yi mata hakan, ita ta yi wa kanta da kanta, nasan halinta sama da kowa a cikinmu, tana tunanin wancan mai kama da ni ɗin ba zai kyaleta ba, zai kasheta ne, shiyasa ta riga shi aiwatar da hakan, kowa dai yasan yadda dokar kasar China take a kan cin amana irin haka, so ita ta yi amfani da dokar in da ta baro ne ba in da take ba, dan haka babu wanda ya yi mata hakan, ita ce nan ta yi wa kanta". A tare suka juyo da kallonsu dan su ga mai yin wannan magana, Sir Arvin ne a tsaye a bakin kofar shigowar, ihun da Handsome ya kurma ne ya farkar da shi daga barcin da ya ɗaukesa tun bayan farfaɗowarsa daga suma. Da gudu Pinky ta tafi ta faɗa jikinsa tare da sakin kuka mai sauti. Hannu yasa ya ɗauketa cak, da sauri ya juya da ita suka bar wajen, da yake shi ma ɗan zafin kai ne, sai ya nufi saman benen dan yana son ya yi magana da Lion, tun da kuma yaga Lion ɗin baya a nan to yasan bai wuce yana sama ba. Su Aseef kuwa, sun tsaya cirko cirko a kan gawar sun rasa abin yi. Handsome hawaye bibbiyu ne yake zuba daga idanuwansa, shi bai san menene ya faru ba! Bai san kan magana ba, yana da buƙatar karin bayani bawan Allah, dan yasan meyasa mumynsu zata kashe kanta?!. Yana haurawa parlourn sama ya ɗan fara ƴan waige waige yana neman ina ne ɗakin Lion ɗin? Akwai parts sosai a saman, akwai na Lion ɗin, Aseef, Areef da kuma wasu da babu kowa a ciki, so daddyn Rimsha yana a ɗaya daga ciki, sai kuma sama wato hawa ta uku, shi kuma akwai part na daddynsu na fake, sai part na uncle Herry, John da kuma Jay, shi kuma sama gabaɗaya wajen hutawa ne kawai da shan iska, sai kayan gym nasu a wajen, so a wannan hawa ta farkon dai parts na TRIPLETS ɗin ne a wajen sai daddyn Rimsha da yake a tare da su yanzu. "What are you looking for?". Aseef da ya hauro saman yanzu ne yake tambayarsa. Ɗan zubawa Aseef ɗin idanuwa ya yi, lokaci guda ya ji wani irin kaunar Aseef ɗin tana ratsa zuciyarsa. "Am looking for that man that we looked alike". Da hannu Aseef ɗin ya nuna mashi part na Lion ɗin ba tare da ya kyafta idanuwansa daga kan kallon da yake yi mashi ba, yana son sanin wanenen shi? Shi ma sir Arvin ɗin yana son sanin wanenen Aseef ɗin? Sai dai shi a jikinsa ya ji cewa lalllai Aseef yana ɗaya daga cikin QUADRUPLE nasa kenan kamar yadda Dr Cherish ta bada labari jiya a kasar China. Gaba Aseef ɗin ya yi ya shige cikin part ɗin na Lion ɗin dan ya gaya mashi abin da yake faruwa a parlourn kasa. Bayansa sir Arvin ɗin ya bi, sai kalle kallen wajen Pinky take yi, ga hawaye a fuskarta jaga jaga, harda majina. Ko da suka shiga parlourn Lion ɗin sai da sir Arvin ya ɗan tsorata, saboda ya ga abin fa ba na wasa bane, ya wuci tunaninsa, irin wannan dukiya da aka narka tamkar baza'a mutu ba?. Lokacin da suka shiga cikin bedroom ɗin a lokacin Lion ya fito daga dressing room nasa, jikinsa na sanye da kayan barci masu bala'in kyau da tsada, kamar dai kullum launin up white mai haske sosai, sai dai ya ɗaura Jacket a saman kayan, saboda wani irin azababben sanyi da ake yi, duk da ya kunna na'urar ɗumama ɗaki, amma akwai sanyi, kun san kasarsu dama da bala'in sanyi. Yana ƙoƙarin hayewa saman bed nasa suka shigo mashi, Aseef bakinsa a ɗauke da sallama, shi kuma sir Arvin excuse ya yi mashi. Ɗago blue eyes nasa ya yi tare da fara binsu da kallo. Cike da tashin hankali Aseef ya kora mashi jawabin abin da yake faruwa. Tamkar bai ji me Aseef ɗin ya faɗa ba, idanuwansa suna a kan sir Arvin da yake ta faman kallonsa shi ma, ita ma Pinky ta kalli sir Arvin ɗin ta kuma sake juyowa ta kalli Lion ɗin, sun ɗaure mata kai baiwar Allah. Fasa hayewa saman bed ɗin ya yi, wajen mirrornsa ya nufa, tissue mai bala'in kyau da tsada ya ɗauko, a gaban sir Arvin ɗin ya kariso cikin nutsuwa yake tafiya, yana zuwa ya fara gogewa Pinky hawaye da kuma majinar da yake a face nata ya yi jaga jaga, sannan ya kalli Aseef ɗin ya ce mashi zai zo ya duba gawar, amma sai ya tashi daga barci, dan haka kada su taɓata, su kyaleta. Sir Arvin ne ya ce mashi "I want to talk to you". Ɗauke hannunsa daga saman fuskar Pinky ya yi tare da wucewa ya koma saman bed nasa ya zauna bayan ya miƙawa Aseef dake a tsaye tissue ɗin. "I don't have time for talk now, because am feeling sleeping too much, and ni ina da tsari! Bana haɗa two things one time, everything has his on time!". Ya kai karshen maganar tare da kwanciya abinsa. Shiru kaɗan sir Arvin ɗin ya yi yana mamakin yadda aka yi halayyarsa da ta Lion ɗin iri guda, shi ma haka yake yi, sai ya ce baya haɗa abubuwa biyu lokaci guda, sannan komai da lokacinsa, to yau ga wanda ya fishi iya furta wannan kalmar!. Yana tsaka da tunani zazzaƙar muryar Lion ɗin ta daki dodan kunnuwansu. "Come and have a seat". Ya faɗa tare da lumshe idanuwansa. "No zan je kasa, idan ka tashi barci sai mu yi magana". Shiru bai amsa mashi ba, wucewa sir Arvin ɗin ya yi, ya nufi waje, shi kuma ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi. Da sauri Aseef ya bi bayan sir Arvin ɗin suka koma parlourn kasa A ɓangaren su Jehan kuwa, tamkar yadda wannan matashi ya yi masu kwatance haka suka nufa, sun yi tafiya tun da daɗin rai har ya zamana babu daɗi, Jehan ta sha barci ta tashi, sai dai ta tashi a dai'dai, dan a lokacin suka isa wajen wannan dutsen, motarsu dai ta ji jiki ba kaɗan ba, duk da zama duk taɓo jikinta, ga hawa da sauka da suka rinƙa hawa, wata hanyar ma da kyar suka iya kutsawa suka wuce. Yana isa wajen ya kashe motar tasa, juyo da kallonsa ya yi a kan Jehan ɗin, sai faman turo baki take yi, ta sha barci kamar ba gobe. "Sorry my baby, na wahalar dake ko? Dama na barki a hospital ai". Ya faɗa yana kara tsareta da idanuwa. Matsowa ta yi ta kwantar da kanta a saman shoulder ɗinsa, a hankali ta motsa laɓɓanta da suke yi mata zafi saboda wahala, ga yunwa tana ji. "Yah Areef yunwa fa nake ji". Hannunsa ɗaya ya ɗaura a saman flat tummy ɗin nata, kasa kasa ya ce "Sorry yanzu zamu koma gida In Sha Allah, amma kafin nan bari na rage maki yunwar kin ji ko?". Ya kai karshen maganar tare da juyowa gareta sosai, hakan ya bata damar shigewa Lion chest nasa da kyau ta lafe. Da alama sun mance a in da suke. "My baby". Ya ambaci sunanta a hankali. A hankali ita ma ta ɗago da kanta, haɗe fuskokinsu ya yi tare da fara kissing nata. Narke mashi ta yi a jiki tana ɗan matsa mashi ɓul ɓul ɗinsa. Ƙoƙarin wuce gona da iri ya yi, cikin sauri ta riko hannunsa da yake ƙoƙarin tura mata a cikin riga, a hankali ta zame bakinta daga nasa tana faɗin "Kai my baby ka bari mana, wai ka manta a in da muke ne?". Lumshe idanuwansa da suka yi jajir kamar wuta ya yi, a hankali ya furta "Yunwa zamu ragewa juna fa, please ki barni na ɗan more mana". "Uhm ni ka bari sai mun koma gida". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "You're right, gobe muna da tafiya zuwa U.s a gabanmu, yakamata muyi komai a yau ne, dan haka let's go". Ya kai karshen maganar tare da buɗe kofar motar tasa. Raba jikinta da nasa ta yi ita ma ta buɗe kofar nata side ɗin ta fito. Kallon wajen suka fara yi, sun rasa ta ina zasu fara tinkarar wajen, abin mamakin ma a nan shi ne, ya aka yi mutane suke rayuwa a irin wannan wajen? Anya wajen nan babu wata ayar tambaya a kanta kuwa? Dan waje ne mai haɗari, bil adama mai gaskiya ba zai taɓa zuwa ko kwatan wannan waje ba!. "Baby waiting for me inside the car am coming". Ya faɗa tare da wucewa gaba ya nufi dutsen, babu ko tsoro a ransa, cikin jarumta yake tafiya, tamkar ba'a kungurmin daji suke ba. "No Yah Areef, ni zan bika, ba zan iya zama ba". Ta kai karshen maganar tare da bin bayansa da sauri, tana zuwa kuma ta riko hannunsa dan ma kada ya hanata binsa ɗin. Shi kuwa tun daga kan yanayin hanyar da suka biyo suna zo wannan waje ya fahimci ba waje ne na lafiya ba, tun daga lokacin yake danasanin zuwa da ita da ya yi. Bashi da zaɓin da ya wuce ya kama hannunta su nufi wajen dutsen, dan baya son ɓacin ranta kuma baya son barinta a cikin motar ita kaɗai, bai san me zai iya faruwa ba, gara mashi suna a tare. Tsit kake jin wajen babu motsin kowa, sai kukan tsuntsaye da suke ta faman shawagi daga can nesa da wajen. Kamar zasu shiga cikin wannan kogwan dutsen, sai kuma suka fasa ya ce da ita su fara duba kewayen dutsen su gani, dan su tabbatar da ya haɗarin wajen yake kafin su afka. Ita dai da to kawai ta bishi. Bayan dutsen suka nufa, tafiya suna rinƙa yi mai ɗan nisa kafin su isko wani abin da zukatansu suka kasa yarda da abin da idanuwansu suke gani, kallon juna suka yi kafin su sake mayar da kallonsu a wajen. Wani katafaren gida na alfarma ne a wajen, gini ne wanda ya amsa sunansa gini, tsabar kyan wannan gida sai ka ɗauka aljanu ne suka kera shi ba mutane ba. Tashin sense!! Waye zai zo cikin wannan kungurmin daji ya yi wanna tampatsetsen gida haka? Shin gidan mutane ne ma ko na al'janu? Dan dai wannan gini tsarinsa bai yi kama da tsarin gine ginen gida nan Nigeria ba. Buɗe baki ta yi zata yi magana, cikin sauri ya rufe mata bakin da tafin hannunsa, a kunne ya raɗa mata ta yi shiru kawai su je. Ba musu ta ja bakinta ta yi shiru, hannunta ya riko cikin nasa, sannan suka nufi cikin gidan babu ko alamar tsoro a tattare da shi. Tamkar wani jarumin sadaukin yaki ya sa hannu ya buɗe tampatsetsen gate ɗin wannan gida. Gida ne dai tamkar gidan sarauta, komai na more rayuwa da akwai a cikinsa, sai dai kuma a tsakiyar dokar daji yake!!. Ciki suka shiga, tsorata iya tsorata Jehan ta yi, sai dai bata nuna mashi ta tsorata ba, ta daure tare da dakewa suka kutsa har can cikin gidan. Katafaren parlourn ya ji komai na more rayuwa. Fasa shiga can cikin parlourn Areef ɗin ya yi, saboda ya hango wata ɗaki mai matuƙar abin tambaya a tattare da ita daga ɗan can gefe a harabar gidan ta wajen flowers, ko'ina a gidan fentin yellow da fari ne, amma shi wannan ɗakin fentinsa baki ne da jajir kamar jini, daga ta sama rabin ginin ɗakin fentin jajir ne kamar jini, daga ta kasa kuma bakin kirin kamar zunubi. Hakan yasa Aseef ɗin ya dasa ayar zargi a kan wannan ɗakin, shi ne yasa ya fasa shiga cikin parlourn ya juyo suka nufi wajen ɗakin. Yana zuwa babu ko shakka bare tsoro yasa hannu ya wangale tampatsetsiyar kofar ɗakin wadda take baka kirin kamar zunubi. Saman ɗakin ma dakin ne ba kwano bane ba, hakan yasa ɗakin yake da duhu sosai, ga kuma babu Windows a cikinsa. Suna buɗe kofar wani irin haske ne ya kauraye cikin ɗakin. Ɗakin empty yake babu komai, floor nasa ma siminti ne ba tiles ba, tamkar irin waɗan nan gingima gingiman storys na manyan kasuwanni da ake yi dan ajiyar kayan hatsi kada su lalace. Can suka hango mace a kwance zindir babu kaya a jikinta a kasar floor ɗin, gashin kanta a barbaje kamar wata mahaukaciya, ko motsi bata yi, ga jini dake zuba ta karkashinta, kamar wadda aka yi wa fyaɗe, jikinta ya yi wani irin green color tamkar wadda ta jima da mutuwa ta fara ruɓewa, kafafunta duk a kumbure tamkar ruɓaɓɓen alala, sam babu numfashi a tattare da ita. Ihu Jehan ta kurma tana faɗin "Adiva!! Adiva!! Wlh she's.........". Bata kai karshen maganar ba ta kwasa a guje ta afka cikin ɗakin, ba tare da yin wata tunani ba. A dubu ɗari Areef ɗin ya yi ƙoƙarin dakatar da ita, sai dai ina ta rigada ta shige ciki da gudun gaske. Nan take ɗakin kuma ya fara wani irin kururuwa tamkar kukan zaki a lokacin da yake jin yinwa, wani irin kura mai haɗe da hayaki ne ya bule gabaɗaya cikin ɗakin, daga ita Adivar har Jehan ɗin da ta afka cikin ɗakin Areef ɗin ya dai'na ganinsu, saboda wannan turnukin hayaki da kuma kura, ga kurar da shiga hanci da ido, shi kansa a haukace ya ja da baya, saboda wani irin azababben tari da yafara yi, kan kace me jini ya fara fitowa daga cikin bakinsa da hancinsa na wannan tari da yake yi. Daga ina wannan hayaki da kura suka fito⁉️bayan kuma kasar ɗakin siminti ne ba kasa ba bare ace dama akwai kasa za'a iya samun kura! Gidan wanenen a dokar dajin nan⁉️ ina su Jehan ɗin suka yi da suka bacewa Areef ⁉️ meyasami Adivan⁉️ ta mutu ne ko tana a raye⁉️. Kai, kai, kai TRIPLETS dai ba zai dai'na cazamun kai ba sai ranar da na ajiye alkamanina, ma'ana na dasa aya a littafin kenan, ina ga a ranar ne zan huta da cakwakiyarsa🥲 irin wannan cakwakiya haka?! Duk fa wannan daɗi, sugar da karɗi tare kuma da cakwakiya na littafin TRIPLETS wasa ne a kan next book nawa da zan sakar maku! Kada kuma fa ku manta na gaya maku shi littafin TRIPLETS tamkar ina barci haka na rubuta shi, shi kuma next book nawa da zai zo maku idan Allah ya kaimu na kammala littafin TRIPLETS, shi sai da na waro idanuna,👀 na nutsar da kwakwalwata🧠 na taushi zuciyata🫀 sannan na iya fara typing nasa, saboda na daban ne, idan nace maku na daban ne, to fa ina nufin na daban ɗin ne, salonsa ya sha banban da kowani story, tafiyar ta manyan kai ce,🔥 dan za'ayi ɓarin wuta🔥dan haka kada ki yarda baki karanta wannan book ɗin ba, ayi babu ke, idan littafin TRIPLETS yazo da zafinsa, to shi kuma wancan da tafasa yake tafe, tafasa yake yi bul bul bul!🙃 Yana hayaki mai tashin kai!!🔥 Ba zan gaya maku sunansa a yanzu ba😂 sai a karshe littafin TRIPLETS sunansa da ɗan takaitaccen bayani a kansa zai zo maku❤️🔥 MA'ASSALAMA, TAKU HAR KULLUM FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA ZERO TENSION❤️🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 23/5/2024 E38 Tari sosai Areef ɗin yake yi tamkar maƙoshinsa zai fashe, wannan kura da kuma hayakin sai kara yawaita a wajen yake yi. Sun ɗauki a kallah 5 mins a haka kafin wannan kura da kuma wannan hayaki ya dakata cak, haka zalika shi ma Areef ɗin tarin nasa ya tsaya cak, abin mamakin kuma jinin dake fita daga bakin nasa shi ma sai ya ɓace ɓat, nan take ya koma normal kamar babu komai. A wani irin zafafe ya nufi ɗakin gadan gadan. A sume ya isko Jehan ɗin, ta sume kwance kusa da Adiva ɗin. A zafafe ya karisa cikin, kai tsaye kanta ya nufa, cikin zafin nama ya kai hannu yana ƙoƙarin taɓata, tamkar daga sama wata halitta mai kama da shanuwa ta bayyana a gabansu. "Hasbunallahu wani'imal wakil ". Ya furta tare da ɗago da kallonsa izuwa kan wannan halitta. Nan tane wannan Halitta ta kurma wani irin kururwa mai matuƙar doɗar da kunnuwar mai sauraro, kururuwar sai da ta amsa a gabaɗaya ilahirin dajin, wani irin amon sauti mai bala'i kara mara daɗin ji take fitarwa, bakinta na fitar da wata iriyar bakar hayaki, ko kaɗan wannan halinta bata da kyan gani, tsabar muninta ma sai idan kana da karfin imani ne zaka iya ganinta, ga wani ɗan iskan kaho a tsakiyar hancinta tamkar kawon shaiɗan, hancin nata kam sai dai mu ce subhanallahi, saboda wani irin bala'i muni, ga wasu garman hakwara tamkar kopaton doki. Duk wannan hayaki da kurafa kenan alama ce ta bayyanar wannan halitta. Sake furta hasbunallahu wani'imal wakil Areef ɗin ya yi tare da miƙewa tsaye suna fuskantar juna da wannan halitta, ko kaɗan bata bashi tsoro ba, saboda yasan abu ne na tsafi, shi kuma ya riki Allah, yana da kwarin gwiwa, sannan yana jin zai iya karawa da kowa da komai, dan haka ko a jikinsa. Wani irin kururuwa wannan halittar ta sake zunduma tare da durkushewa kasa a saman gwiwowinta. Kafin Areef ɗin ya yi wani yunkuri halittar ta daka uban tsalle! Ta haye kansa. Kokawa suka fara yi da gasken gaske, cikin ikon Allah, Allah ya bawa Areef ɗin dama ya samu ya murɗe wuyar halittar, nan take ta kurma wani ihu wanda sai da ya sanya Jehan ta farfaɗo daga sumar da ta yi, shi kuma Areef ya yi maza ya toshe kunnuwarsa da hannayensa, saboda bala'in karar wannan halitta. Kasa wanwar halintar ta zube, nan take ta rikiɗa ta koma ainahin halittar mutun. Cikakken namiji ne kuma babban mutun, ba kowa bane kuma face Abbon Nawid!! Tashin sense, dama kenan nan ne wajen tsafinsa kenan? Meyake yi da ƴan matan idan ya kawosu nan? Ga dai Adiva ko me ya yi mata? Ta mutu ne ma ko tana raye?. Kawar da kallonsa daga kan Abbon Areef ɗin ya yi, ya mayar da kallon nasa a kan Jehan da ta miƙe tsaye cikin fitar hayyaci, gabaɗaya a birkice take, waje ta nufa da gudu. A hanzarce ya rikota tare da jawota jikinsa yana ambatar sunanta kasa kasa. Baiwar Allah wannan kururuwar da Abbon ya kurma lokacin da yake wannan halintar ne ya birkita mata kwakwalwa. Jin ya ambaci sunanta yasa ta dawo dai'dai, ƙanƙanme shi ta yi tare da sakar mashi kuka mai tsuna zuciyar mai sauraro, rarrashinta ya fara yi cikin nutsuwa yana mai da numfashi. Wani irin jijjiga ɗakin da suke ɗin ya fara yi, almace na yana son rugujewa. Saketa ya yi a hanzarce tare da cire mayafin jikinta duk da babu girma ya rufe Adiva ɗin da shi, sannan ya ɗauketa cak ya ce da Jehan ɗin zu je, su yi sauri su fita gidan zai ruguje, domin Abbon ya mutu duk wasu kambun tsafi ya karye, so dole gidan ya ruguje. A takaice dai da kyar suka iya sha daga cikin wannan gida, saura kaɗan ginin ya ruguje da su, Allah ya taimaka suka fito. A gidan baya na motar ya kwantar da Adiva ɗin, sannan suka shiga gidan gaba, a guje ya figi motar suka ɗauki hanyar da suka bi suka zo. Gidan tsafin Abbo kuwa ya ruguje gabaɗaya da gawarsa a ciki. A can gida kuwa, gwaggo, Rimsha, Akila da kuma Aafia, sun shirya tsab suka nufi wajen gyaran jiki tare da kunshi haɗe da wankin kai. Tga ne zai kai'su, sai kallon Aafia yake yi, yana tuna sumar da ta yi a jikinsa a garden, bayan farfaɗowarta da yadda ta zaro mashi idanu da ta farfaɗo ta gan shi a gabanta, ta tsorata sosai shi ne ta tashi ta gudu cikin gida, bai hanata ba dan kada ta sake sume mashi. Yau sun ci kwalliyar Abayas, sun yi matuƙar kyau da su, Rimsha dai sai ɗingisa kafa take yi, tun da suka fito Tga ɗin ya tsare Aafiar da idanu, sun zo zasu shiga cikin motar a gidan baya, ya yi maza ya buɗewa gwaggo karfin motar yana faɗin Aafia ta shiga gaba ba sai sun yi mota biyu ba, su tafi a ɗayar ma ya wadatar. Cikin hanzari Aafiar ta ce "A'a ni ba zan shiga gaba ba gaskiya, sai dai Akila ko Rimsha su shiga gabar, ni a baya zan zauna". Why ya tambayeta yana tsareta da idanu. Kawar da kanta daga kallonsa ta yi tana jin zuciyarta na bugawa da sauri sauri. "Ni matar mutun ce, dan haka ba zan shiga gabar mota da mijin wata ba, dan Heartbeat bai yarda da hakan ba". Cewar Akila, ta kai karshen maganar tare da wucewa ta shiga gidan baya abinta, tana ta aikin latsa waya. Guntun tsaki Rimsha ta ja kafin ta ce "Uncle T gaya masu ni haramun ce ma shiga gabar mota idan ba motar yaya Saif ba, kuma ko motarsa ɗin ma sai dai idan shi zai tuƙa ne zan shiga gaba". Cikin masifa ta yi maganar, kamar mai jin haushin wani. Me gwaggo zata yi idan ba dariya ba? Su Rimsha manya, akwaita da iyayi idan ya gameta, barema yanzu da take jin haushin Lion, sai abin ya shafi kowa, kowa masifa take yi mashi, yanzu shi dai Uncle T uncle nata ne fa, tun da Uncle ɗin Lion ne, amma har da shi yau ya sha masifar, dan hawai tana jin haushin Lion.............😂 "A'a Rimsha ai dama ko da kowa zai shiga gabar motar wani ai banda ke". Cewar Tga ɗin, dan ya san halin Lion sarai, ya san shi da bakar kishi, dan haka shi ko da sunan wasa ma baya fatan Rimsha ta shiga mashi gabar mota, yana da tabbacin yanzu ma ba dan gwaggo ba, da wlh Rimsha ba zata tako ko tsakar gidan nan ba, saboda Lion fa karshe ne a ɗan banzan bakin kishi. "Aafia to ki shiga gaban mana kawai". Cewar gwaggo, ta yi maganar ita ma tana shiga cikin motar gidan baya kenan. Ɗan turo baki kaɗan ta yi. "A'a gwaggo ni nafi son baya ne". "Meyasa to?". Gwaggon ta tambaya. "Saboda ni uncle T tsoro yake bani". "Meyasa nake baki tsoro?". Ta tambaya yana rufe Kofar motar gidan bayan, dan su gwaggon sun kammala shiga, saura ita kaɗai suka bari a waje tsaye kamar mara gaskiya. Tsareta da ido ya yi yana jiran amsa, ƴan kame kame ta fara yi mashi. "Okey now sai ki shiga kawai tun da baki da wani sauran option". Ya faɗa tare da buɗe mazaunin driver zai shiga. Turo baki ta yi kamar ta ce ta fasa zuwa, amma saboda tana son ayi mata gyaran jiki da kuma kunshi, sai ta hakura ta shiga, tun da Dr Nawid ya rasu bata sake yin kunshi ba, har ta gama takaba da jimawa, kafin Dr Nawid ya rasu kullum cikin yin kunshi da gyaran jiki take, Allah sarki rayuwa kenan. Tun da ya fara tukin motar yake aikin kallonta ta cikin mirror motar, jefi jefi ita ma tana satar kallonsa ta gefen idanu, sai dai tafi mayar da hankalinta a saman titi. Wajen gyaran jikin da suka je last time, nan suka je yauma, har cikin wajen ya bisu, gwaggo tana ganin yadda yake ta aikin kallon Aafia kamar wadda aka bashi gadinta, daga nan ta ce tafiya da Aafia U.s ya kamasu, dan ko basu tafi da ita ba sai Tga ya dawo ya ɗauketa, gara ma kawai su sassautawa bawan Allah kawai su wuce tare da ita, idan sun je komai ya dai'dai ta sai ya musulta kawai a ɗaura masu aure a can, dama bai kamata su bar Aafiar a Nigeria ba, duba da abubuwan da suka rinƙa faruwa da ita a baya, bare kuma yanzu da ta yi aure mijinta ya rasu, ai tana bukatar kulawa ne fiye da can baya, kowa kuma yasan Aunty dai ba zata iya rike Aafia ba, saboda suna ganin bata yi wani karatun kirki ba, so bata waye ba a ganinsu, ita kuma Hjy Hadiza ai bama sai na sake faɗa ba, kun sani tana can tana yawon ta zubar ɗinta, so bazata bi ta kan Aafiar ba, Abbi ba zama yake yi ba, shi ma daddyn Jelly zai koma Kano abinsa, dama a can ya fi wayo, Irfan ya koma school, gidan yanzu babu kowa, dama solution dai kawai gwaggon ta ɗauketa ko kuma su mayar da ita gidan Abba wajen Ammie, tun da ita ma Ammien ba baya ba, ta iya bada tarbiya kuma tana da zafin sosai, ita ce zata iya zama da Aafiar duk da ba ita ta haifeta ba, amma yanzu tafiya da ita U.s ma ai dole ne, dole ayi mata password da komai da komai duk a yau ɗin nan!. Yau ma dai kamar ranar, kusan wuni zumbur suka yi a wajen gyaran jikin, sai dai fa sun sha gyara, Rimsha dai bata fasa ba, sai dai aka yi mata flowers na zane har wuya abinta, a tafin hannunta ma ta bada kalar zanen da take so ayi mata, ta yi wani irin fitinannen kyau, amma wa ƴan Nigeria ta yi wa kyan, dan su dai TRIPLETS basu son kunshi, ita ma Akila ta biyewa Rimsha aka zana mata har wuya, da yake ita bata san da cewa Aseef baya son ƙunshin ba. (Ni kuwa nace lallai U.s zata kama da wuta, dan duk son da Aseef yake yi mata sai ya goge ƙunshin nan da chemical 😂 yo ni ina ruwana? Ina da Maltina mai sanyi a fridge ai😏) Wlh kamar ka sace Rimsha saboda tsananin kyau, an kara tsatso mata kyan fatarta da gyara, sun yi wani luwai luwai da su, gwaggo dai bata daddara ba, a karo na biyu ta sake bari an yi wa Rimsha gyara na musamman, ita ma Akilar haka, ita fa gwaggon bata san da cewa kyan da Rimshar ta yi wancan karin ne ya fara ruɗar da Lion ba a wancan ranar ma, ita ta ɗauka sai da ya shigeta ne ya gigice, bata san daga kallonta ma da ya yi bane ya gigice ɗin, sai ta bari aka sake zuba masu gyara na musamman, sun yi kyau kam, Akila ba'a magana, sai tashin wani fitinannen kamshi suke yi, dan anyi masu wankar turare. Da yake Tga yana zaune a parlourn wajen ne bai bisu can ciki ba, saboda gyaran jikin da za'ayi masu sai a can cikin bedroom, dan sai an shafe dukkan jikinsu da kayan gyara da sauransu, shi ne yasa ya zauna a parlourn saman sofa yana jiransu. Time da suka fito shi da kansa sai da ya miƙe tsaye yana kallonsu, sun zama kamar wasu taurari masu matuƙar hasken gaske, sai dai kuma shi ma baya son ƙunshi, da alama hakan a jininsu yake, ko kuma saboda Lion baya so ne ya dasa masu tsanar abin suma, saboda kada ma su kawo mashi a arear da yake. Sai kallon Aafia yake yi tamkar wani ya ce zai ɗauketa, ita kuma sai faman ɓoyewa take yi kada su haɗa ido, dan ita tsoron ash eyes nasan nan ma a zahiri take yi, gara a Tv tana iya kallonsa sosai, a zahiri sai idanun suna bata tsoro, tana ganinsu suna wani haske, a haka ma dan bai taɓa zaro mata su ba. (Ni kuma nace dan bata taɓa yin 4 eyes da blue eyes na Lion bane, ai da sai ta kusa fitsari a wando, musamman ma ace da daddare, kuma ya zarosu😂 ya kuke gani?😂) Gaba ya yi suka rufa mashi baya, gidan baya na motar ya je ya buɗewa gwaggo. Kamar yadda suka zo haka suka shiga a komawar ma, wajen shopping suka nufa. Abubuwa sosai suka saya, komai da suka yi Tga ne yake ta aikin biyan kuɗi, sai da suka kammala komai suka dawo gida. Suna dawowa kuma suka hau shirin tafiyar da zasu yi gobe, sam ba zama. Su kuwa Areef da Jehan da kyar motar nan tasu ta iya mayar da su wajen asibitin da Maryam take a kwance, suna zuwa suka miƙawa likitocin Adiva ɗin ma, dan a ɗan yi mata dressing su sami ta yadda zasu wuce Kd da ita, daga nan suma ya yi masu password and visa, dan ya ce ciwon nan nasu sai kwararrun likitoci, Allah ma yasa da jet ɗin Lion zasu tafi, dan yana isa U.s ya sake sanyawa aka tashi jet ɗin dan ya zo Nigeria ya ɗaukesu, ba jirgin kasuwa zasu bi ba, saboda tafiya mai gabaɗaya zasu yi, sun sallami Nigeria kenan. Ko da suka koma asibitin ba laifi, jikin Maryam ɗin da ɗan dama dama, ba kamar yadda suka ɗauko ta ba, sai dai har yanzu ba'a iya gane menene ainahin abin da yake damunta ba. Karbar Adiva ɗin ma suka yi, duk da basu da tabbacin tana raye ko ta mutu, fitowa Areef da Jehan ɗin suka yi daga cikin hospital ɗin, dan su je su nemi abin da zasu ci, almost 12 na rana yanzu basu karya ba, gara shi Areef zai iya jurewa, ita kam Jehan ba zata iya ba, sai kukar yunwa take yi mashi, ga uban gajiya, duk a galabaice suke. A takaice. After some hours. Sun koma Kaduna lafiya, a lokacin Tga ya yi wa su gwaggo jagoranci sun gama duk wasu shirye shiryen da zasu yi, suna isa gida ya bawa Tga ragamar yi wa su Maryam ɗin shirye shiryen tafiya, ya yi masu na majinyata ya ce mashi, dan komai ya tafi normal cikin sauri. A bedroom na Aseef dake a kasa Areef ɗin ya kwantar da Maryam da kuma Adivar, sannan ya sanar da gwaggo da ta ɗan kula da su, ta cigaba da duba lafiyarsu zuwa gobe su tafi. Haƙiƙa gwaggon ta tausaya masu, har kwallah sai da ta matsa masu duk da bata san meyafaru da su ba, ta yi masu kwallah sosai, a haka ma dan dai bata gansu tun ɗaukosu da aka yi ba, yanzu ai sun ɗan yi kyan gani. Bedroom nasa Areef ya wuce, wanka ya yi tare da fitowa ya shirya, sannan ya biya bashin sallar azabar da kuma la'asar da ake binsa. Bayan ya idar sai ya zauna a bakin bed nasa tare da ɗauko wayarsa da ya fita ya barta a saman bedside drawer, ba da ita ya tafi ba. Number Lion ya fara kira bayan ya kunna wayar, a lokacin kuma Lion ya tashi daga barci ya baro wayar a cikin bedroom nasa, ya fita zuwa parlourn kasa dan ya sanya a fitar da gawar Dr Cherish zuwa mortuary, so baya tare da wayar tasa, two miss call Areef ɗin ya yi mashi, ganin bai ɗauka bane yasa ya kyale shi tare da yunkurawa zai mike. Kasa miƙewar ya yi, bai san time da ya koma ya zauna ba yana mai binta da kallo, tsaye take a bakin kofar shigowa cikin bedroom ɗin, hannunta ɗauke da kayan abinci, ta yi wanka ta canza kaya izuwa kananan kaya, wandon jeans fari tas da T-shirt maroon color, ta yi matuƙar kyau sosai da sosai, ta gyara gashin kanta, sai kai mashi karo daddaɗar kamshi perfume nata yake yi. Duba time ya yi karfe 5 saura ƴan mintoci, wani irin murɗa mashi cikinsa ya yi, saboda yunwa, dama abincin zai tashi ya je ya ce ta kawo mashi, sai kuma gata ta zo. Karisowa cikin ɗakin ta yi bakinta ɗauke da sallama, har ƴar rama sai da ta yi, saboda shiga damuwa na halin da su Adiva ɗin suke a ciki. Sam basu ɓata lokaci ba wajen cin abincin a tare, dan suna jin bakar yunwa over. Bayan sun kammala sai suka zauna hirar yadda aka yi ta tsinci kanta a gidan na Hjyr daɗin. Da daddare misalin karfe 8 bayan sallar isha kenan, gabaɗaya family sun zo yi masu sallama, su Abban Imran duk sun zo, a nan ne gwaggo ta sanar da Abbi cewa zasu tafi da Aafia, bai ce komai ba, saboda gwaggo yayarsa ce, ba zai iya ja da hukuncinta ba idan ta yanke, dan haka sai ya ce Allah ya kaisu lafiya kawai. Sun sha hira da family kamar ba gobe, Akila sai kuka take yi akan wai ba zata iya rabuwa da Ammienta ba, har da cewa ita gaskiya ba zata bi su gwaggo ba, zata zauna da Ammienta ya fi mata daɗi. (Ni kuwa nace iskancin kawai, anjuma kaɗan zaku ganta da waya tana faɗawa Heartbeat ta ƙosa ta ganshi😂 mu da mun san komai😏 yo Aseef da Akila ai sai Allah, halinsu sai su😌) Sai aikin rarrashinta Ammien take yi, haka shi ma Abba, sai rarrashinta suke yi. Suna a tare cikin farinciki Akil ya kirasu a waya ya sanar dasu Umaisha ta haifi ɗa namiji yanzu, murna a wajensu ba'a magana, Ammien tafiya ya kamata zuwa Madina kenan, su Umaisha anzama maman baby, Akil kuma za'a dawo sabon aiki.............😂 A takaice dai family basu bar gidan ba har karfe 10 na dare, sannan suka yi masu sallama a kan da safe zasu zo su rakasu zuwa airport, sai bankwana ake yi kamar antafi kenan, Rimsha har da rungumar Ayla tana kuka, Malika ma tana wajen, sai dai babu mai ganinta, harta Rimshar ma bata san da zamanta a wajen ba, dan bata bayyanar masu yadda zasu ganta ba. Ammien dai baki har kunne ta sami jika, ga shi Akil ya turo masu hoton babyn, yaron kamarsa ɗaya sak da Akil ɗin......... Ni dai nace Allah yasa ta tsaya a iya kamar ta fuska, kufa my readers?. Bayan kowa ya wuce gida, yanzu gidan ya rage daga Areef and Jehan wadda suke cikin ɗakinsu, sai Dr Salman da Brr Naurat suma suna ɗakinsu, Adiva da Maryam suna a kwance a ɗakin Aseef, ko motsi basa yi dukkansu biyu, sai dai jikin ba laifi ya ɗan yi kyau. Gwaggo da Aafia suna ɗakin gwaggon, Akila tana bedroom nasu manne da waya tana yi wa Aseef kuka a kan ita fa wlh gobe ma ya yi mata nisa, ta ƙosa da gan shi, kamar ba yanzu ta gama cewa ita ba zata je U.s ba, zata zauna da su Ammienta, sai rarrashinta yake yi, suna nan dai suna aikin da suka saba, ita kuma Rimsha yau ɗakin mummynta ta tafi, saboda ta san Lion ya zai kira gwaggo a waya, sai ta gudu ta koma wajen mum ɗinta, dan ma kada gwaggon ta ce ta karɓi wayar su gaisa, ga shi ba zata iya ce da gwaggon a'a ba, shi ne yasa kawai ta gudu abinta. Ta je kuma ta sami mum idanunta biyu, zama ta yi a saman bed suna hira, sai nasiha mum ɗin take kara yi mata, tana kara tunantar da ita mahimmancin miji da kuma hakkokinsa a kanta, sannan tana kara koyar da ita dabarun zaman gidan miji, tana ta koya mata abubuwa dai kala kala, haka suka raba dare har wuraren karfe 2 suna hira na tsakanin uwa da ƴa, sai da mum ɗin ta ce yanzu kam su yi barci, tun da da asuba jirginsu zai ɗaga. A gado ɗaya suka kwanta, sai dai ita dai Rimsha bata yi barci ba, saboda tunanin Lion, haka zalika shi ma bai yi barci ba, ya kasa iya yin barcin ba tare da ya ji muryarta ba, ya kira gwaggo kuma ya kasa iya tambayar ina take a bata su yi waya, saboda jikinsa yana bashi cewa fushi take yi da shi, so yasan ba lallai ta yarda ta yi waya da shi ba, shiyasa ya daure bai tambayi ina take ɗin ba, ya bari kawai gobe ai zata zo har in da yake. A takaice dai dukkansu haka suka kwana cikin kunci, sun kasa yin barci har aka kira sallar asuba. Suna yin sallah kuma su Abban Imran suka zo rakasu zuwa airport, ansha koke koke kam kamar babu gobe, shi dai Areef sai binsu da kallo kawai yake yi, wani maganar ma da Hausa suke yi, shi kuma baya ji, dan haka sai ya zama ɗan kallo shi da Tga. An jima ana koke koke da sallama da juna tun daga gida har airport kafin su wuce zuwa cikin jirgin, Abban Imran ɗin Areef ya dankawa makullan gidan Lion ɗin, suna tsaye suna kallonsu har sai da jirgin ya ɗaga, sai Allah ne kuma yasan yaushe zasu sake ganin juna, Dr Salman da Brr Naurat ma da su aka wuce, dan Lion ya ce lallai dole su dawo U.s, dan yana da bukatar ganin kakanninsa a kusa da shi, hakan yasa suka wuce da su, Abban Imran ya so a bar mashi iyayensan a nan ya kula da su, amma ba yadda ya iya, dole ya hakura aka tafi da su. Tun da jirginsu ya tashi Rimsha ta gyara kwanciya a jikin gwaggo ta hau zuba barci abinta, kamar wata mai ƙaramin ciki, ita kuwa Jehan babu kunyar kowa ta zauna kusa da mijinta, har da kwantowa a jikinsa tana shaƙar kamshin perfume nasa, Akila sarkin waya, dole dai ta hakura ta kashe wayar tata sai sun isa, Tga sai kallon Aafia yake yi tamkar wadda aka bashi gadinta, sauran sojoji biyu da suka rage a gidan wanda da su za'a koma kuma, suna kujerun can baya suna zaune abinsu, shi ma Alex yana a tare da su, mummyn Rimsha tana zaune kusa da Brr Naurat, ta sunkuyar da kanta kasa shiru, ita kuma Aafia sai satar kallon Tga time to time take yi, Maryam da Adiva suna a kujerun da yake a kusa da sojojin nan, kasancewar suna sume, sai aka ɗan kwantar masu da kujerun kaɗan, akwai wani part na rufe karnika a cikin jirgin, so a ciki aka rufe su copper, wayyo sun yi wa Nigeria bye bye suma, Aafia bata yi sallama da Ummin Dr Nawid ba, basu ga juna ba, saboda idan baku mance ba Ummin tana Katsina baiwar Allah, bata san zasu tafi ba, da alama kuma su Abbi sun sha'afa ne basu sanar da ita ba..................... To fatan mu dai Allah ya sauki wannan ahali lafiya a cikin garin Washington, Akwai sauran rina a kaba fa! Mun gama ɗan kwantar da tarzomar Nigeria, saura Washington DC, Cherish ta kashe kanta, waye zai nunawa su Lion in da Daular tsafin su Anderson yake? Ina uncle Herry na gaskiya? Yana raye ne ko shi ma ya mutu? Shin His Excellence wannan shiru da ya yi ya zubawa Lion idanu baku tunanin akwai wata a kasa? Kuna tunanin zai yi shiru ya zuba masu idanu suna ƙoƙarin kwace mashi kujerarsa ne? Anya ba mage mai kwanciyar ɗaukar rai ya yi masu ba kuwa? Wai shin wanenen Anderson? Ina kuma yake? Anya komawar su gwaggo Washington a yanzu babu wata a kasa kuwa? Anya ba shirya hakan aka yi ba? Anya Basu cikin gagarumin haɗari kuwa? Ku kai dubanku a kan yadda suka tafi, duk abin da ya faru sun ki yarda su ɗaga tafiyar, Kada kuma ku manta aradun da Lion ya jinjigowa kansa na tsayawa takara! Kun dai san wlh His Excellence ba zai taɓa yin shiru yana gani a kwace mashi kujerarsa ba! Wani karin tambayar ina Duna na Daular Mutuwa yake? Kun dai san ba'a ce ya mutu ba ko? Dole kuma tun da bai mutu ba yana wani wajen, to ina yake? Ina mahaifiyar Adiva? Ga shi yanzu an ɗaukota sun wuce U.s ba tare da daddynta ya ganta ba, meyasa su gwaggo basu haɗata da daddynta ba? Ina mahaifiyarta take? Ai tana da uwa! Ya makamor mutanen Katsina wato su Sadiq? Jehan ta tafi ba tare da ta je wajensu ba! Wacece Malika? Meyasa kuma take taimakon su Rimsha? Ina wannan tsinannen mahaifin Maryam ɗin? Shin yana raye ne ko ya mutu, gwaggo zata karɓi su Handsome a matsayin ƴaƴan kuwa? Anya zata yafewa Cherish ta rike mata ƴaƴanta kuwa? Ya makomar Dr William da yake a cikin duhun kai a yanzu? Ya makomar Hjy Hadiza? Ga dai Aafia a hanyar U.s, ina Rufee da kidnappers suka kama. Kai na barku haka nan, amma dai da akwai sauran bambayoyin da yakamata nayi maku, muna da sauran aiki, amma dai TRIPLETS ya zo gangara, ku shiryawa cakwakiyar! Ku shirya tarar aradu da ka! Dan za'ayita ta kare ne!!! Akwai gagarumin rugugin jijjigar aradu dake dimfarowa😌😏 KADA DAI KU MANTA, WANNAN CAKWAKIYAR A LITTAFIN TRIPLETS KUKE KARANTA SHI WADDA ALKALAMINA NI FATIMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU ZERO TENSION NA RUBUTA...✍️ MA'ASSALAMA!!.🥱 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* Date: 24/5/2024 E39 *Da Cherish da Arvin dukka sunan kristars ne, masu tambayata a kan sunan ga amsarku, ba sunan musulmai bane ba, fatan kun gane?.* WASHINGTON🌹🔥 bayan an kawar da gawar Dr Cherish daga cikin gidan, zuwa mortuary. Zaune suke gabaɗayansu a cikin parlourn kasa, da Lion da Aseef suna a zaune a saman sofa guda mai zaman mutun uku, shi kuma sir Arvin shi da Handsome suna zaune a nasu sofar ita ma mai zaman mutun uku, Pinky tana a kwance a jikin sir Arvin, har lokacin sai shasshekar kuka take yi, da alama ita ma dai ta gaji zuciyar Dr William ɗin kaɗan, saboda yadda take shasshekar kukar a zuciye take yinsa. Dr William yana kwance a sume saman sofa, tun lokacin da ya ga Dr Cherish ta kashe kanta, tun lokacin ya yanke jiki ya faɗi, sir Arvin ne ya ɗauke shi ya kwantar da shi a saman doguwar sofa, a lokacin Lion yana barci. Daddyn Rimsha ne ya sauko kasa daga sama zuwa in da suke, sai kallonsu yake yi da mamaki, dan shi duk bidirin da aka yi a gidan yana sama ta uku bai da labari, dama idan ka tsallake hawar farko, to ba zaka iya jin me yake faruwa a parlourn kasa ba, so shi yana hawa ta uku yana wani aikin nasa na daba, kuma ba wai barci yake yi ba, no idanunsa biyu, bai ma san sun yi baki a gidan ba. Da Jay da John suna a zaune saman nasu sofar, kowa dai Lion yake jira ya yi magana. Kusa da Lion ɗin daddyn Rimshar ya zo ya zauna yana faɗin "Saif lafiya? Who are they?". Ya yi maganar idanuwansa na'a kan sir Arvin mai kama da Lion ɗin, sai kallonsa yake yi da mamaki cike fal a face nasa. Nisawa Lion ɗin ya yi kafin ya ce "I can't talk to much uncle, but Arvin ka basu labarin abin da yake faruwa from A to Z, mu bamu bukatar jin yadda kuka yi rayuwa, just tell them who are you people's and what's going on here". Ya kai karshen maganar yana duba sakon da ta shigo wayarsa a yanzu. "Kazo yanzun nan". Shi ne sakon da aka rubuta mashi tare da address. Wani siririn tsaki ya ja tare da duba time kafin ya kashe wayar mai gabaɗaya ya ajiyeta a gefensa, saboda ya lura su His Excellence ba zasu taɓa rabuwa da shi ba, shi kuma ba zai taɓa yarda ya haɗa hanya da su ba, saboda ya tsanesu fiye da tunanin mai tunani, duk da suke kakanninsa, sam baya son ganinsu, shi da ace Jacob Roshan yana raye ma, ai da da kansa zai kashe ɗan banza, kawai ya tashi ya ɗauki yara ya sadaukarwa da matsafa wai sune magadan kujerar tsafin nasa, tsabar iskanci ba zai sanyasu su gaje shi a abin arziki ba sai a na tsiya, ya cutar da rayuwarsu a banza da wofi, yanzu ga uncle Herry dai bama su san a in da yake ba, ya mutu ko yana raye Allah masani, ji yake yi kamar ya je ya tono kabarin Jacob ɗin ya gana mashi azaba ta musamman kafin ya mayar da shi (Wlh Lion zai kashe ni da dariya 😂 shekaru talatin da uku da mutuwarsa idan ka tono kabarin me zaka gani banda farin kashi? Kawai hakuri zaku yi kakanku dai ya cuceku a banza) Nauyayyar ajiyar zuciya sir Arvin ya sauke kafin ya fara basu labarin duk abin da yake faruwa dallah dallah. Mamaki iya mamakin Dr Cherish sun sha, sai dai kuma daddyn Rimsha da yake yana da zuciya mai kyau sosai, sai ya ce. "Allah sarki ai da bata kashe kanta ba, yanzu dai wuta zata tafi kai tsaye, da ta bari ko musulta ne sai ta yi, ai Aunty A'isha tana da tawakkali, zata yafe mata duk da nasan zata surfa masifa ba kaɗan ba, amma tabbas zata yafe mata" "Uncle kana nufin mommarmu mafaɗaciya ce?". Cewar Aseef. Guntun murmushi daddyn Rimsha ya yi tare da faɗin "Bazaka san hakan ba sai ranar da ka yi wa Akila ba dai'dai ba, ai ina ga duk cikin yaran babanmu ba wanda ya kaita iya faɗa da surfa ruwan bala'i, ga zuciyar bala'i da rashin tsoro, kai faɗe ma ɓatawa, wani lokaci ka yi wa Akila zalinci ka ga ikon god, mantawa zata yi da kai autanta ne, saboda ba'a zalinci a gabanta, baka ga Jehan bace? Ai Jehan goyonta ne, shiyasa take a haka, Aunty Aisha karshe ce". Shiru Aseef ɗin ya ɗan yi kafin ya ce "Wayyo i really love my momma, ai gara ta zama haka, idan ba haka ba mutanen duniya sai su rinƙa ɓata mata rai, amma idan tana da faɗa kowa zai ji tsoronta". Shi dai Lion abin da kuka sani ne, binsu da ido kawai yake yi, sai hira suke yi. Handsome bawan Allah ya yi shiru, akace uwa da ɗa sai Allah, tunanin Dr Cherish kawai yake yi ɗan tahalikin nan, duk da ya ji abin da ta yi bata kyauta ba, amma kuma uwarsa ce, yana kaunarta over sama da kowa, dole ya shiga damuwa sosai na rashinta, babban abin tausayin ma shi ne, idan aka yi sa'a Dr William ya dawo cikin hayyacinsa to fa ba shakka bai san su ba, zai ce bai sansu ba, dan shi rayuwar da suka yi a China duk sun yi ta ne cikin shi baya a cikin hayyacinsa. Gyaran murya sir Arvin ya yi tare da fara magana a nutse. "Now where is our real mom? I want to see her, i want to see this strong woman that give birth to QUADRUPLE, Lions and Kings! I want to see her more than your expectations, an cutar da ita ba karya, kuma ta sha wahala ba karya". Kallon Aseef Lion ya yi kafin ya ce "Ka basu labari a kan momma". Cike da mamaki tare da al'ajabin abin da Dr Cherish ta aikata ya fara magana a nutse, labari ya ɗauko masu tun kan soyayyarta da Dr William har kawancenta da Cherish ɗin, komarta Nigeria da duk abubuwan da suka faru, daga karshe ya rufe masu da mommar tasu tana hanyar zuwa ai. Shiru sir Arvin ya yi yana mai kara jinjinawa mahaifiyar tasu, ba shakka ta cika jarumar uwa, gaskiya duk ita aka fi cuta a cikin wannan al'amari. A wannan rana dai haka suka wuni cikin farinciki, Sir Arvin yaki yarda ya rabu da Lion da kuma Aseef, sun sake komawa TRIPLETS tun da Areef baya nan, duk ya ƙosa su Areef su iso ya ga cikon ɗayansu, yau a bedroom na Lion suka wuni, shi kuma Handsome a tare da daddyn Rimsha ya zauna, sai tunanin Dr Cherish yake yi, ita kam Pinky abin da kuka sani ne, tana manne da Sir Arvin, dan shi ta sani, da shi ta saba, ta saba da shi sama da mummynta, shiyasa ko'ina suna a tare. Da daddare ma sir Arvin ya ce shi a bedroom na Lion zai kwana, dama shi Aseef ai already sun saba in dai kwana a bedroom na Lion ne, sai su zo su haye mashi bed nasa shi da Areef, su haye su kwanta, su bar nasu part ɗin, to yau shi ma Sir Arvin ya ce babu in da zai je, Lion ya ce mashi da akwai almost parts empty da babu kowa wajen guda uku a wannan hawa da suke, ya ɗauki ɗaya, ya ce sai wani lokaci zai ɗauki ɗayan, yanzu dai a nan zai kwana tare da su. Aseef kuwa ya ce mashi "Ai bed ɗin tana ɗaukarmu mu dukka TRIPLETS dama, dan haka ga toilet ka yi wanka ya sanya kayan barcin Lion kazo mu kwanta, ni bari na kira matata". Ɗan zaro dara daran blue eyes nasa sir Arvin ɗin ya yi tare da faɗin "Wow kana da mata?". Jinjina mashi kai Aseef ɗin ya yi tare da fito da hoton Heartbeat ɗin tasa yana nuna masa. Karɓar wayar ya yi yana kallonta. "She's so beautiful, amma bata sanya maka ciwon kai ko?". Lion ne ya amsa mashi da cewa "Ƴar aljanna ce in ji Aseef ɗin, ƴar aljanna kuma ai kaga ba zata sanya mashi ciwon kai ba". Kallon Lion ɗin da kyau sir Arvin ɗin ya yi kafin ya ce "Okey we can see ai, ni dai nasan mata koya kake dasu sai sun sanyaka ciwon kai, haka Dr Cherish da daddy, kullum cikin sanya shi ciwon kai take yi, ya yi ta faman shan magani, kuma wai a haka tana son shi". Karɓar wayarsa Aseef ɗin ya yi yana faɗin "No my heartbeat dai daban take da kowace mace, wai baka ji Lion ya ce maka ƴar aljanna bace? Ai ƴar aljannarce da gaske, bata laifi, kuma bata son ɓacin ra'ina, ni ku bar damuna bari na kirata mu sha love ɗin mu". Jinjina mashi kai kawai sir Arvin ɗin ya yi, dama shi Lion baya kula shi in dai a kan Heartbeat ce, dan fa shi Aseef bai yarda Heartbeat zata yi mashi laifi a duniya ba, ƴar aljannarsa ce. Nufar toilet sir Arvin ɗin ya yi, ita dai Pinky tana zaune kusa da Lion saman bed, ta yi shiru abinta, wannan ita ce Queen amount the Kings, ita kaɗai ce mace a cikinsu, gata ƴar karama, zata sha gata kam, daga wajen Lion sai wajen sir Arvin abinta. Har sir Arvin ya je zai shiga toilet ɗin, sai kuma ya dakata tare da juyowa, a kan Lion ya sauke idanuwansa, while shima Lion ɗin shi yake kallo. "Kai fa? Kana da mata?". Sir Arvin ɗin ya tambaya. Jinjina mashi kai ya yi, calmly ya ce "I have a Queen amount the Queens, one in million". Duk da sir Arvin baya dariya, a wannan gaɓar sai da ya ɗan yi siririn murmushi kaɗan, sannan ya ce "Oh ashe ba laifin Aseef bane, kai ma hakance, ƴar aljana wadda bata laifi kai ma ke gareka ba?". Shiru Lion ɗin ya yi bai amsa mashi ba. "Will you show me her pic's?". Cewar sir Arvin ɗin. Girgiza mashi kai Lion ɗin ya yi. "No". Ya faɗa tare da kwanciya da kyau a saman bed ɗin. Kamar zai tambaye shi meyasa ba zai nuna mashi ita ba, sai kuma ya fasa ya wuce cikin toilet ɗin kawai, sai dai zuciyarsa cike tab da mamakin ya aka yi matar Aseef take bakar fata? A haka ma bai san Akilar fara ce tas a Nigeria ba, in da Rimsha ya gani ne sai ya ce mata baka kai tsaye, saboda ita ce chocolate color, su Akila da Jehan ai fararen tattabaru ne, amma da yake shi mai jan kunne ne sai yake masu kallon bakaken fata. A takaice dai a tare suka kwana a saman bed guda su ukun, Pinky dai tana manne da Sir Arvin, taki rabuwa da shi, a saman kirjinsa ta kwanta, kuma Lion bai rabasu ba, dan ya lura sun yi muguwar sabo fiye da tunanin mutun, so ba zai so a rabasu a kaita wani bedroom ɗin ba, sai dai da suka yi barci shi ya tashi ya bar masu bedroom ɗin, ya koma part ɗin Areef ya yi kwanciyarsa kayansa. Washegari da safe suka rinƙa damunsa da tambayar meyasa ya gudu ya barsu da suka yi barci?. Shiru ya yi masu bai amsa masu ba, haka suka gama takura mashi da tambayar, da dai suka ga ba zai amsa masu ba, sai suka kama kansu suka nufi dining room, dan su yi breakfast. Dr William kuwa tun wannan suma da ya yi jiya, har yau bai farfaɗo ba, kuma Lion ya hana a zuba mashi ruwa, ya ce su kyale shi na ɗan lokaci, dan da alama kullin da Dr Cherish ta yi mashi ne yake son kwancewa, shi ne ma yasa ya shiga doguwar suma bawan Allah. Sai da suka yi breakfast a tare cikin farinciki, kowa yana farinciki amma banda Handsome, yana cikin damuwa bawan Allah. Yau Lion ma a tare da su ya yi breakfast, duk da baya karyawa da wuri, yau saboda su ya karya da wuri. Bayan sun kammala ne suka ɗugunzuma izuwa bedroom na Dr William da yake kwance, yana kwance kamar yadda Lion ɗin ya kwantar da shi jiya, sai dai ko da suka shiga sai suka tarar da ya fara motsi, a hankali yake motsawa yana sambatu kasa kasa, basu iya jin me yake faɗa, saboda kasa kasa sosai yake magana. Sai da suka matso kusa da shi ne suka fara jiyo abin da yake faɗa kasa kasa. Ba komai yake faɗa ba kuma face sunan gwaggo. A'ish, A'ish, yake ta kira. Tsawon shekaru talatin da uku zuwa da huɗu kenan yau, tun kafin a haifi TRIPLETS ya rabu da gwaggo, amma yau sai ga shi anwayi gari bayan tsawon waɗan nan shekaru dukka ya farfaɗo da ambatar sunanta, Allah Akbar. Da alama ya dawo cikin hayyacinsa ne. Sosai sambatun nasa yake kara yawaita, zuba mashi idanuwa suka yi suna kallonsa, Lion da daddyn Rimsha ne suka yi karfin halin fara tofa mashi adduo'i, dan kada ya tashi a birkice, suna tofa mashi adduo'in ne dan Allah ya taimakesu ya tashi a cikin nutsuwarsa. Sir Arvin kuwa tuni idanuwansa suka ciko da kwallah tab, hakika ya ji tausayin daddyn nasu da kuma mommar tasu, tsawon waɗan nan shekaru masu uban yawa haka! Shin gwaggon ma zata yarda da shi kuwa? Idan fa aka karyawa mutun zuciya a karon farko, mawuyacin abu ne ya sake yarda da koma me! Allah sarki Dr William, rayuwarsa da akwai ciwo ainun. Sun jima a haka kafin nan su samu ya farfaɗo mai gabaɗaya, ko da ya farfaɗo kuma da sunan gwaggo a bakinsa ya farka, ya tashi ne da tambayar ina take? Sai dai sun yi sa'a ya farfaɗo cikin hayyacinsa, ya farfaɗo a cikin nutsuwarsa, wannan adduo'i da suka rinƙa yi mashi ta taimaka mashi sosai. Sai dai fa kamar yadda Dr William ya dawo normal sanadiyyar mutuwar Cherish, haka suma su Anderson suka sami damar gane cewa ba Dr William na gaskiya bane a hannunsu, saboda Cherish ta mutu komai ya karye, gaskiya ta bayyana, akwai kura ba kaɗan ba, kada ku manta shi Sir Arvin ba musulmi bane ba, zasu iya ganinsa a duk in da yake tun da shi ne nasu, shi ne aka basu, shi suka ɗauka Cherish ta ra'ina masu wayo, ta kwace shi, tab ga rai'inin wayon da ta yi masu, hakan zai kara bakanta masu rai, akwai badakala!!. Dr William yana ɗaura idanuwansa a kan su Lion ɗin ya dakata daga ambatar sunan gwaggo da yake yi, zaro idanuwansa ya yi yana kallonsu da mamaki, ga shi Lion da sir Arvin ya fara sauke idanuwansa a kansu, su ne masu kama da shi kuma. Cike da mamaki ya kai hannu ya shafi face nasa, dan ya ji wai nasa face ɗin tana nan ne ko dai ita ce aka cire aka sanyawa waɗan nan masu kama da shi ɗin? Tambayar kansa yake yi su waye su? Sam bai san cewa yaransa bane, bai ma kawo a ransa cewa yanzu shakaru 32 sun wuce ba, shi dai yasan tabbas gwaggo tana da ciki, kuma cikin nata bai wuce wata 3 ba a lokacin da ya sani, to suwaye waɗan nan masu kama da shi ɗin kuma?. Tambayar da yake ta faman jefawa kansa cikin ruɗani kenan, ya shiga ruɗani, ya kalli Lion ya kalli sir Arvin....... Allah sarki Dr William bawan Allah. Ganin haka yasa daddyn Rimsha da yake ya fisu girma, ya kuma fisu sanin yakamata, sai ya ce masu bari ya bawa daddyn nan nasu labarin abin da ya faru, idan ba haka ba ƙwaƙwalwarsa tana a cikin ruɗani over, dan haka kowa ya zauna za'a sake dawo da labari daga farko. Dukkansu babu wanda ya musawa daddyn Rimshar, waje suka samu suka zauna. Cikin nutsuwa daddyn Rimsha ya fara yi wa Dr William bayanin komai, tun daga farko har karshe izuwa yau yanzu da suke zaune, tashin hankali. Dr William ya yi shekaru 32 zuwa da uku bai san in da kansa take ba! Bai ma san wanene shi ba, anyi ta wasa da kwakwalwarsa tamkar yadda ake buga ball, bawan Allah, Allah ne kaɗai zai saka mashi wannan cuta da suka yi mashi, amma hakika ancuce shi ba kaɗan ba!!. Ɗago idanuwansa ya yi ya sauke a kan yaran nasa, yanzu su dukka biyar ɗin nan ƴaƴansa ne bai sani ba, iya cikin su QUADRUPLE kawai ya sani, bayansu bai san komai ba, suma QUADRUPLE ɗin bai san su huɗun bane a cikin gwaggon, saboda a lokacin cikin nata karami ne, so ya ɗauka ma yaro ɗaya ne. Suma kallon shi suke yi, alama ya yi masu da hannu a kan su zo gare shi, dukkansu suka miƙe amma banda Lion, dan shi da aka sake bada wannan labari ma an sake ɓata mashi rai ne, ji yake yi meyasa suka yi sakaci har Cherish ta kashe kanta? Ai da hukunci mai tsauri zata fuskanta, sannan wlh ba zai bar su His Excellence ba, sai sun ɗanɗani kuɗarsu, dan haka ya kasa tashi ya karisa wajen Dr William ɗin ma, ya zauna yana ta binsu da idanu kawai. Rungume juna suka yi da Dr William ɗin, a gefensa suka zazzauna, sai shafa fuskokinsu yake yi kamar ance za'a kwace mashi su, sam bai nuna cewa baya son ko ɗaya daga cikinsu ba, harta ƴaƴan Cherish ɗin ma, dan idan baku manta ba ai ya musulunta kafin su juyar mashi da kwakwalwa, so yana da ilimin addini ai, yasan laifin wani baya shafan wani, dan haka sai ya haɗasu ya rungume, yana shafa fuskokinsu yana kallon Lion da yake zaune yana binsu da kallo. Alama ya yi mashi da hannu a kan yazo mana shi ma. Nisawa ya yi tare da miƙewa a hankali, yana isa wajen bed ɗin Aseef ya tashi ya bashi waje, kusa da Dr William ɗin ya zauna tare da ɗan sunkuyar da kansa kasa kaɗa, bawan Allah ƙoƙarin dannar zuciyarsa kawai yake yi, dan yazo har wuya, gaskiya an cucesu da yawa, jikinsa har tsuma yake yi a kan su His Excellence, barema wannan tsinanne Anderson ɗin, ji yake yi tamkar ya yi mashi gashin kazar Hausa, kun san kazar Hausa ce sai ta ji wuta sosai take gasuwa, to haka Lion yake ji zai yi wa Anderson idan ya kama shi............. Lallai Anderson zai gasu ba karya😂 A takaice yau dai sun yi wunin farinciki, duk bayan ƴan mintina sai Dr William ya tambayi Lion yasu gwaggo, sai dai Lion ɗin ya ce mashi suna hanya, sun kusa sauka, duk ya damu yana son ganinta bawan Allah, shin zata yarda ta karɓe shi kuwa?. Sai can rana ta yi sanyi jirgin su gwaggo ya sauka a cikin Washington, sam Lion yaki sanar da Dr William cewa sun sauka lafiya, yana son kawai suzo gida su haɗu, baya son su tada mashi da tarzoma a airport, dan yasan wlh gwaggo ba zata karɓi Dr William a cikin sauki ba, ko da ta ji meyafaru, shi kuma Dr William ba zai iya ganinta ya daure har sai sun dawo gida ba tare da ya yi mata magana ba, so zasu iya tada masu da rigima a cikin airport ɗin, shiyasa sai ya boye mashi, suka barshi a gida suka tafi airport shi da sir Arvin da kuma daddyn Rimsha, shi ma Aseef yana wajen daddynsa ai, bai ma san su gwaggon sun iso ba, Pinky ma tana wajen Dr William, saboda ita ta saba da shi a rayuwar da suka yi a kasar China, dan haka sai ta sake jiki ta manne mashi. Kafin su Lion su isa airport ma airport ɗin ta cika makil da jama'a, saboda kowa ya ji labarin jet ɗin Lion ta sauka a airport ɗin, so kowa zai so ya san daga ina jet ɗin ta fito? Su waye kuma a cikinta? Dan haka manya manyan mutane masu faɗa a ji, sojoji da kuma ƴan'sanda sun cika airport ɗin tab, ga kuma ƴan jaridu kala kala makil a cikinta. Sai dai su gwaggo basu fito daga cikin jet ɗin ba har sai da motocin su Lion suka danno hancinsu a cikin airport ɗin, sannan ne Areef ya yi umarnin da a boɗe masu jet ɗin su fita. Sojoji biyun nan ne suka fara fitowa, sannan Alex ya rufa masu baya, sai Dr Salman and Brr Naurat da suka biyo bayansu suna shawagi kamar wasu taurari, kun san hasken Brr Naurat ba irin nasu bace, ta fi su Aseef haske sosai da sosai, duk da suke Turawa dukkansu, amma ta fisu haske, tayi fari over har haske ya so ya yi mata yawa, shiyasa gwaggo take sajewa da Turawar ai, saboda hasken Brr Naurat ke gareta, dama ita gwaggo ai Baturiya ce ba bakar fata ba, duba da yanayin yanda take ga ta girman kasar Russia. Gwaggo da ƴan matanta tare da Areef sune a karshen fitowa, mummyn Rimsha ma ta rigasu fita, sun bar su Adiva a cikin jet ɗin, daga baya za'a ɗaukesu. Gabaɗaya wajen motocinsu Lion ɗin suka nufa, ƴan jaridu da shegen gulma duk da basu san su waye bane, sai ɗaukarsu a hoto suke yi, saboda sun gansu daga cikin jet ɗin Lion suka fito. Wani irin birki gwaggo ta ja a dai'dai tsakiyar airport ɗin lokacin da idanuwanta suka sauka a kan Lion da sir Arvin da suke tsaye a jikin motar Lion ɗin suna ɗan tattaunawa. Sam sam bata san da zancen sir Arvin ɗin ba, sun ruɗar mata da ƙwaƙwalwa, ta kalli Lion ta sake kallon sir Arvin, ga shi sun yi shigar kaya iri guda, Lion yasa nasa shi kuma sir Arvin ya sanya kayan Areef, so kayan iri ɗaya ne sak, dama haka kayan TRIPLETS suke, abin da ɗaya yake da shi sauran ma suna da shi, so sun fito tamkar mutun ɗaya ne, mai iya rabe su sai Rimsha da Pinky, dan Rimsha idan Lion goma masu kama ɗaya za'a kawo mata, to ba shakka zata fitar da nata Lion ɗin daga cikinsu........... Haƙiƙa ta yi wa masoyinta farin sani🤌😂 Sam gwaggo bata san time ɗin da ta saki hannun Rimsha ba, dama ta rike hannunta ɗin ne saboda ɗingisa kafa da Rimshar take yi, shi ne yasa ta rike hannunta dan ta taimaka mata, amma ganin sir Arvin da Lion yasa ta saki hannun nata tana binsu da kallo, ta kasa iya cigaba da tafiya. Ganin hakan yasa Lion da sir Arvin ɗin suka nufota a tare, a lokacin kuma tuni su Brr Naurat sun shiga cikin motocin da suke jiransu, shi kansa Areef kasa cigaba da tafiya ya yi, duk wanda yasan cewa TRIPLETS mutun uku ne ba huɗu ba, sai da ya dakata da tafiya a lokacin, Rimsha ma ta sha ruwan mamaki sosai, amma Akila da Jehan basu wani sha mamaki ba, wucewa ma suka yi izuwa cikin motocin, dan su dama can ba wani sanin Lion suka yi ba, bare su sha mamaki dan an sami mai kama da shi, dama basu gama sanin su waye TRIPLETS ɗin ba. Tga ma dai tsayawa ya yi yana kallon ikon God. A tare suka iso wajen gwaggon, welcome suka yi mata, sir Arvin ya riga Lion rungumeta, dan Lion ɗin ya gaya mashi ita ce mommansu, kuma shi ma ya ga hakan a face nata, saboda tana kama da Aseef idan ka ganta a fisge, kuma ita gwaggo na gaya maku farar baturiya ce, bata da banbanci da su. Shi kuma Lion a ɗan gefe guda ya tsaya yana karewa Rimsha kallo, ƙunshin jikinta kawai yake kallo, sam baya so, amma a yanzu dai bashi da zaɓin da ta wuce ya kawar da kallonsa daga kan ƙunshin nan, shi ne zamansa lafiya, dan haushinsa ake ji..........😂 Sam gwaggo bata san wanenen ya rungumeta ba, bata san sir Arvin ne ko Lion ba, ita dai ta shiga ruɗani, kanta ya kulle, sai kawai ta rungume shi ita ma. Areef ne ya matso kusa da su yana tambayar Lion wanene wanda ya rungumi mommansun nan. Harararsa Lion ɗin ya yi kafin ya ce "Saif ne mana". Siririn dariya Areef ɗin ya yi yana faɗin "Sai dai biyunin Saif, wai kai Lion kana tunanin ko mutuwa nayi na dawo ba zai iya tsamoka daga cikin dubu irinka bane? To idan ma haka kake tunani ka makara, ni dai nasan TRIPLETS nawa TRIPLETS nawa ne babu in da zasu je su ɓuya mani ban iya gane su ba, yanzu dai gaya mani wanene ya rungumi momma? Dan brain nawa tana dab ta tarwatsewa, irin wannan kama haka". Kin kara tanka mashi Lion ɗin ya yi, saboda bai son buɗe baki a cikin taron wannan uban jama'a haka. Ko'ina hasken ɗaukar hoto ne kawai yake tashi a airport ɗin, daga masu cameras har masu wayoyi, abin ya girgiza jama'a, sun rasa wannan baki da gidan The General of the Army's yake yi na menene? Suna son jin su wanenen suke ta zuwa gidan, jiya wasu sun je, yau kuma ga wasu, anya lafiya kuwa? Babban abin da yafi damun jama'a ma shi ne, yadda yau suka ga Lion a cikin bakaken fata, shi da kowa ya sani a baya sam baya son bakaken fata, dan ma dai Allah yasa yawancin familyn gwaggon turawan ne ita ma, saboda kal kal suke kamar ka taɓa jini ya zuba, musamman daddyn Rimsha da Azharuddin Bature, so mix nasu da bakaken fata dai kaɗan ne, iya gefen Dr Salman ne, wanda kuma mutun biyu ne kawai daga cikin ƴaƴan nasa suka fito chocolate colors irinsa, sauran duk brr Naurat suka yo, shi kam Alex ma ai ba'a magana, harta blue eyes ke gare shi, sak su yake. Waɗan da basu ganin abu su yi shiru har sun fara tofa albarkacin bakinsu a kan su waye ne su gwaggo?. Kasa hakuri gwaggon ta yi har sai da ta tambaya ya aka yi suka zama su biyu masu kama ɗaya? Ta manta da cewa jariranta biyu ne masu blue eyes kuma kamanninsu ɗaya sak, sannan Lion bai sanar da ita abin da ya je yi a kasar China ba, ya dai ce mata ya je yin wani aiki, so bata san da zancen komai a kan su Cherish ba. Kasa kasa Lion ya ce mata "Idan mun je gida kun huta zuwa gobe zan gaya maki". Jinjina mashi kai ta yi, sai da ya yi magana ta iya gane shi ne Lion, dan haka sai ta dawo da kallonta a kan sir Arvin, ko ba'a gaya mata komai ba ta ji a jikinta cewa ɗanta ne shi ma, sai dai ta rasa ya akayi ya zama ɗanta, ita dai tasan TRIPLETS ta haifa, kuma duk suna tare da ita, gaskiya kanta ya kulle a wannan gaɓar, bata san cewa tun time da ya faɗo duniya aka ɗauke ɗayan ba, tun time da bata a cikin hayyacinta aka rabasu, so lokacin da ta dawo cikin hayyacinta sai ta kalli su uku ne, anrigada an ɗauki ɗayan, dan haka bata san da shi ba baiwar Allah. "Let's go momma". Lion ya faɗa har lokacin idanunsa suna a kan Rimsha, ta ɗaure fuska sosai, ita a dole da gaske fushi take yi dashi, taki yarda su haɗa ido kuma. (Rimsha want to kill me with laugh🤌😂) Hannun gwaggon sir Arvin ya riko tare da wucewa gaba yana faɗin "Let's go momma". Gaba suka yi, Rimsha ta rufa masu baya tana ɗingisa kafa. Zuba mata idanu Lion ɗin ya yi yana kallon yadda take ɗingisa kafafun nata tana aikin wani turo baki, alamar tana jin zafi. Sai da ta ɗan yi tafiya kaɗan, sannan ya bi bayanta, ya tako izuwa in da take, bai yi mata magana ba ta baya ya sa hannu ya sunkuceta sai saman shoulder ɗinsa. Habawa nan take jama'a suka fara yi masu hotuna na musamman, kowa sai tambayar kansa yake yi wacece ita? Yau Lion da ɗaukar mace, macen ma kuma gata bakar fata, sai dai kyakkyawar gaske ce, kuma a baynar nasi ya ɗauki kayarsa, ko a jikinsa? Lallai kam. Kuka ta sa mashi tana faɗin "Ni Yah Saif ka sauke ni........" Wani irin harara daya dalla mata ne yasa ta kasa iya cigaba da yi mashi magana, nan take ta haɗiye kukan nata cif, saboda tsoronsa, kuma ita ma dama bata son ta yi ja in ja da shi a cikin mutane, koda kuwa a cikin family ne bare kuma mutanen garin, hakan ma yasa ta yi shiru sai sun isa gida. Tun da ya ɗauketa har ya kaita cikin motarsa karewa face nata kallo yake yi, ya yi tsananin kewarta sosai, ga shi ta sha gyara ta sha kyau over. Tun da ya ɗauketa kuma jama'a suka aikin kashe masu hotona babu kakkautawa. Sir Arvin cikin motar da yazo suka wuce da gwaggo, shi kuma Lion cikin motarsa ya wuce da Meesha, Areef da Jehan suna nasu motar, Akila ta yi mamakin rashin ganin Aseef a wajen, bata san cewa bai ma san sun iso ba, Lion ya ɓoye mashi, dan kada Dr William ya ga dukkansu basu nan ya damu, shi ne yasa ya bar mashi Aseef ɗin. Sai da suka shiga cikin motocinsu, sannan ne Areef yasa bodyguards na Lion da su fito da Maryam da Adiva, su kuma fito dasu copper. Haka kuwa aka yi, suka fito da su. Daga nan motocin suka tashi izuwa gida. Kan kace me labari ya baza gari, wasu su ce Lion ya yi aure ya auri bakar fata, wasu kuma su ce budurwarsa ce, wasu ma cewa suke yi yarinyarsa ce, dan sun ganta ƴar karama, basu san wannan under 15 years ɗin ita take cazawa His Excellence Lion ɗin nasu kai ba, wasu kuma su ce sai dai ko idan ya fara neman mata, dan su basu taɓa jin yana da aure ba, ko da sunan wasa ma basu taɓa jin yana da alaƙa da wata mace ba, a iya saninsu ma shi mutun ne da ya tsani mata a rayuwarsa, so dan haka wannan yarinya da ya ɗauka a airport karuwarsa ce, haka gidan wasu jaridun suka rubuta, abin ku da siyasa, tuni magana ta bazu har kunnan His Excellence. Yanzu wasan zai fara kenan....🔥 Kuma da idanunsa Lion ɗin ya ga jaridar da aka buga wai The General of the Army's ya ɗauko karuwarsa daga airport, ga shi kuma yadda aka ɗauki hoton nasu da aka sanya a jaridar, sun fita sosai, ya tsareta da idanu tamkar zai cinyeta, shi da kowa yasan mawuyacin abu ne ya ɗaga ido ya kalli abu na second biyu ma a rayuwarsa, amma ita ya tsareta da idanu sosai, ai dole dama ace wani abu a kan hakan, dan irin wannan kallo haka ya wuce na ƴan uwantaka ko kanwa ma, kallon tsantsar madarar soyayya ce tare da kewa ya rinƙa zuba mata. Ganin wannan labari da aka buga a jaridar a wayarsa yasa ya kashe wayar ma gabaɗaya, yazama mashi dole ya fito ya gayawa duniya wacece Rimsha, ko yana so ko baya so, idan ba haka ba wannan magana ta karuwarsa ce ita zata iya sa ya kashe mutane dayawa, dan Rimsha ta fi karfin su dangantata da karuwarsa, zuciyarsa ba zata ɗauki hakan ba, bugu da kari hakan zai taɓa mashi siyasarsa sosai, so yana da kyau ya yi wani abin a kai koda ba yau ba ba gobe ba. Ita kuwa Rimshar sai aikin turo baki take yi ta kawar da kai gefe guda, ita a dole bata son su haɗa idanu, sam bai kulata ba, dan baya son hayanayi a yanzu, wannan kalma ta karuwarsa ce da aka dangantata da shi ta tsaya mashi a rai, ta ɓata mashi rai, dan haka shi ma bai sake bi ta kanta ba har suka isa gida. Sun isa gida lafiya, ita dai gwaggo bin sir Arvin kawai take yi, saboda tana jin a jikinta ɗan tane, amma duk ta ƙosa ta ji gaskiyar wanene shi?. Ana kashe motocin a parking space na gidan suka fara fitowa, nan suka zama cikakkun ƴan kauye, dan gidan Lion fa ko mai mulki idan ya zo sai ya zama ɗan kauye, saboda ya tsaru ne iya tsaru, Daula ce guda. Lion dai bai bi ta kansu ba, yana fitowa ya wuce cikin gida, ɗaukarta ya yi cak suka nufi parlourn, sai kalle kalle take yi, taga abin da ya sha gaban tunaninta. A saman sofa mai zaman mutun uku ya zaunar da ita, sannan ya haura sama ya kira su Dr William. Lokacin da ya sauko kasa su gwaggo duk sun shigo cikin parlourn. Koda gwaggo ta ga Dr William bata nuna kamar ma ta san shi ba, sai ta ɗauke kanta kawai, ta cigaba da kallon su Pinky da Handsome. Shi kuwa Dr William yana ganinta ya furta A'isha, dan ko mutuwa zai yi ya dawo ba zai manta da face nata ba. Sam bata ɗaga idanu ta kalle shi ba, saboda bata san menene yake faruwa ba. Cikin sanyin murya Lion ɗin ya ce da daddyn Rimsha "Uncle ka kai Dr Salman and brr Naurat ɗaya daga cikin part dake a hawa na uku, su Areef kowa already yasan part nasa, kai kuma Uncle sai ka ɗauki part ɗaya a hawa na biyu, daddy da momma ma part nasu yana hawan da kake......" Kasa karisa maganar ya yi saboda wani irin kallo da gwaggon ta wurga mashi, dan kawai ya ce daddy da momma part nasu na hawa na biyu, tasan da ita yake yi, kenan ita da Dr William? Tab akwai ƙura, sam bata ma san time da ta harare shi ɗin ba, sai da ta ga ya dakata da maganar da yake yi ne ta fahimci ashe ta harare shi ne........... (Gwaggo duniya😂) Ganin ta banka mashi wannan harara yasa ya ja bakinsa ya yi shiru tare da wucewa yana faɗin "Momma ki zaɓi duk part ɗin da ya yi maki, ku je ku yi wanka ku huta, yamma ta yi yanzu, sai mun haɗu a dinner". Ya kai karshen maganar tare da wucewa sama abinsa, ba zai iya da masifar gwaggo ba, irin wannan harara da ta wurga mashi tasa bai san time da ya dakata da magana ba, to tun wuri gara ya kama kansa kada ya sami rabon mari. (Tab waye yaga an mari His Excellence Lion?😂 Akwai show🔥😂) Ganin yadda ya ja bakinsa ya yi shiru ba ƙaramin dariya ya bawa gwaggon ba, dariya ta ɗan yi kafin ta wuce ta haura saman ita ma. Ambatar sunan Dr William ɗin ya fara yi, ko kallon in da yake bata yi ba, ta haye sama dan ta duba ɗakin da ya yi mata ta zauna a ciki, shi kuma daddyn Rimsha ya yi wa su brr Naurat jagora dan cika umarnin Lion. Jehan ta bi bayan mijinta, Aafia ta bi bayan gwaggo, parlourn ya rage saura Dr William da ya yi mutuwar tsaye yana mamakin menene yasa gwaggo taki kula shi? Ko dai bata san gaskiyar abin da ya faru bane? Sai kuma Handsome da shi dama bashi da kowa, sai kuma sir Arvin da bai wuce saman ba, Rimsha ma ta miƙe tana ɗingisa kafa ta bi bayan gwaggon. Aseef kuwa ya tsaya ne yana karewa ƙunshin dake a hannun Akila kallo, akwai ƙura, dan wlh ya tsani ƙunshin nan, dole ta goge shi idan tana son zaman lafiya. (Da alama Aseef ya manta ita ƴar aljannace bata laifi🤌😂😂) Tausar Dr William ɗin sir Arvin ya yi, ya sanar da shi cewa a yanzu gwaggo ba zata saurare shi ba har sai ta ji gaskiyar abin da ya faru, idan ta ji gaskiya zata saurare shi, ya yi hakuri dan Allah. Da kyar dai ya samu ya shawo kansa ya yarda ya wuce part nasa, zuciyarsa cike da tunanin gwaggon.............. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* Date: 27/5/2024 E40 Juyawa sir Arvin ɗin ya yi da nufin ya haura sama shi ma, sai yaga Aseef a tsaye ya zubawa Akila idanu yana kare mata kallo, ita kuma ta yi kasa da kai tana wasa da ƴan yatsun hannunta da suka ji ƙunshi suka yi jajir da su. "Aseef lafiya kuwa? What are doing here? Kowa ya wuce bedroom nasa dan ya je ya huta kai kuma ka tsayar da ita a nan! Shin ita bata gaji bane?". Tsabar bakinciki kamar ba zai amsawa sir Arvin ɗin ba, amma sai ya daure ya buɗe baki cike da tsananin ɓacin rai zai fara magana. Bai kai ga fara maganar ba wani irin amai mai karfin gaske ta kwace mashi, kafin ma ya yi yunkurin motsawa daga in da yake har ya wanke ko'ina a arear wajen da amai ɗin, ga shi ya kasa dukawa kasa bare aman ta ɗan yi mashi sauki, a tsaye yake kwararata. A dubu ɗari sir Arvin ɗin ya yi kansa yana yi mashi sannu, ita ma Akilar da sauri ta matso kusa da shi tana yi mashi sannu. Tamkar kara injiza aman ta yi da ta matso kusa da shi, kara yawaita aman ya yi sosai, bata san cewa shi ƙunshin ne baya son gani ba, shi ne dalilin aman nasa, ga shi ta sake matsowa kusa da shi, ai dole aman ta karu, kuma babu halin yin magana bare ya ce mata ta tashi a kusa da shi, shi kuma sir Arvin bai san menene dalilin yin aman nasa ba, bare ya ce da Akilar ta matsa daga kusa da shi. A wani irin dubu ɗari Lion da Areef suka sauko kasan, saboda aman da suka ji, kuma ko ba'a faɗa masu ba sun san Aseef ɗin ne, saboda yana aman ne tare da wani irin tari mai sanya bawa fita daga cikin hayyacinsa. Sam aman yaki tsayawa, yi yake yi tamkar zai amayar da ƴaƴan hanjinsa, ga wani wahalallen tari da yake yi tamkar maƙoshinsa zai ɓalle. Rirrike shi suka yi suka tsugunnar da shi kasa, daga Lion har Areef ɗin basu lura da Akilar a wajen ba, da sun ganta zasu gane dalilin yin aman, dan shi kansa Lion ɗin tun daga airport daya ga ƙunshin Rimsha yake jin zuciyarsa tana tashi, daurewa kawai ya yi dan babu yadda zai yi, amma shi kaɗai yasan me yaji dayaga ƙunshin, shiyasa ma bai kaita bedroom nasa ba, ya barta a parlourn, dan zata iya saka shi amai over. Shi dama Areef bai zafafa a kan tsanar ƙunshin ba, tabbas dukka TRIPLETS suna da kyankyani over, amma na Lion da Aseef sune suka zafafa over, shi ma Areef ɗin da farko ya zafafa, amma yanayin aikinsa yasa ya saba da wasu abubuwa, hakan tasa kyankyanin nasa ta ragu ba kamar nasu ba, so shi zai iya zama da mace idan ta yi ƙunshi, abin hannunta ne kawai ba zai iya ci ba idan ta bashi, amma dan zama waje guda, lafiya lou zasu zauna saɓanin Lion da Aseef da ko gani suka yi sai sun yi ta amai kamar su mutu. Da sauri su gwaggo ma dukka suka sauko kasa, dan Aseef kamar zai mutu haka yake tari, kuma da sauti mai karfin tarin take fita, hakan ne ya bawa family da suke kusa damar jin abin da yake faruwa, ga aman taki tsayawa. Ganin abin da yake faruwa yasa gwaggo, daddyn Rimsha and Dr William har suna rige rigen karisowa wajen nasu. Sai dai kuma shi kansa Dr William ɗin yana zuwa ya yi ido biyu da ƙunshin hannun Akilar, kan kace me shi ma ya fara sharara nasa aman, hakan na nufin abin nasu ma na gado ne. Sai a lokacin kuma Lion ya lura da Akilar, dafe kansa ya yi tare da sanya hannusa dukka biyu ya ɗauki Aseef ɗin cak dan su bar wajen, idan ba haka ba suna iya rasa shi ma mai gabaɗaya, dan irin wannan tari da yake yi ai zai iya kashe mutu har lahira. Duk Aseef ɗin ya bata mashi jiki da amai, amma sam bai damu ba, ya wuce da shi kai tsaye cikin part nasa, kai tsaye toilet ya wuce da shi, bai sauke shi a ko'ina ba sai a cikin jacuzzi mai cike tab da ruwan wanka da ya haɗa, dama wanka zai yi ya jiyo tarin Aseef ɗin. Sai a lokacin kuma aman ta tsaya sak, hannu bibbiyu Aseef ɗin ya dafe saitin kirjinsa da shi, saboda wani irin azababben ciwo da yake yi mashi, duk kuma wannan tari ita ce sila, ita ta ja mashi wannan ciwon kirjin. Zuba mashi idanu kawai Lion ɗin ya yi yana kallonsa, shi ma dai aman nan yake ji ba kaɗan ba, bare ma da ya sake ganin ƙunshin Akila, sai abin ta kara tada mashi da zuciya, gara mashi ƙunshin Rimsha ma, saboda nata ja ne yafi yawa a jiki, na Akila kuma a iya yatsu kawai aka sanya mata ja, sauran dukka bakin kirin ne, hakan yasa nata ya fi basu kyama. A parlour kuwa, tamkar gwaggo bazata kula su ba, sai kuma ta ce da Akilar. "Akila zo mu tafi, ƙunshin hannun nan naki ne basu so, haka Dr William yake tun bai kai haka ba, ina ga shi ne yasa autana ma yake amai, sun yi gado kenan, Areef sai ku san yadda zaku yi da shi ya dai'na yin aman ai". Guntun murmushi sir Arvin ya yi, gwaggo duniya, har cikin ranta take jin ciwon wannan aman da Dr William yake yi, amma taki bayyana hakan, sai dai ta fake da su Areef su san yadda zasu dakatar da aman, dan tana tsoron kada mijin nata ya mutu..............(Kai ana duniyanci a TRIPLETS, soyayya ba karya bace😂) Tana kai karshen maganarta ta ja hannun Akilar suka nufi sama, sai dai zuciyarta a cike yake tab da damuwa, shap ta manta da cewa Dr William baya son ƙunshi, kuma bata kawo a ranta cewa a cikin ƴaƴan nasa akwai wanda ya gaje shi ba, shiyasa ma ta bari su Rimshar suka yi lallen, to yanzu meyakamata ta yi kenan? Ta tambayi kanta. Tamkar mummyn Rimsha ta shiga cikin tunaninta sai ta ce mata "Aunty Aisha meyakamata ayi kenan? Tun da ya zama Aseef baya son wannan lalle, to ba shakka dukkansu haka suke! Ga shi kuma dukka yaran sun yi ƙunshin". Gwaggon tana zama a bakin bed a cikin bedroom nata ta amsa mata da "Gaskiya kam kuma ba'a kyauta masu ba, ni wlh na mance da cewa mahaifinsu baya so ne, kuma tunanin na tambayesu ko na tambayi matan nasu sam bai zo mani ba". Zama ita ma mummyn Rimshar ta yi a saman bedside drawer tana faɗin "Amma kuma dakamar wuya ace matan nasu basu san basu so ba". Ɗago idanu gwaggon ta yi ta sauke su a kan Rimsha dake kwance a saman bed ɗin, ta basu baya, jin abin da suke faɗa yasa ta rufe idanuwa kamar mai yin barci, dan kada mummynta ta tambayeta ta san Lion na son ƙunshi ko bata sani ba, idan ta ce ta sani wlh mum ba zata kyaleta ba, idan ta yi wasa ma sai ta sha lafiyayyen mari, shi ne yasa ta yi kamar ta yi barcin karya dan kada a tuhumeta. Ambatar sunanta gwaggon ta yi, shiru bata amsa ba, saboda ta yi barcin karya. "Rimsha fa barci ya ɗauketa, ke Akila kin san da cewa Auta baya son lalle ko baki sani ba?". Cewar gwaggon. Shiru ta ɗan yi kamar mai tunani wani abin, sai can kuma ta ce "Kamar dai na sani ne Kamar kuma ban sani ba, na manta, amma dai a tsakanin Jehan da Rimsha akwai wadda ta taɓa ce mani mijinta baya son ƙunshi ya hanata yi". Ta kai karshen maganar tana ɗan sunkuyar da kanta kasa. Mummyn Rimsha ce ta ce "Au kinma taɓa ji kenan? Akila shin kun san me kuke yi kuwa? Yanzu dai kinga halin da kika jefa shi a ciki, ba tare kuma da ya yi maki laifin komai ba, kin ɗauki alhakinsa, kinsan kalar tsinuwar Mala'iku da zaki samu kuwa? Ace ma baki san yana so ko baya so ba, meyasa da zaki je yin lallen baki tambaye shi yana so ko baya so ba? Kin san da cewa komai zaki yi a yanzu sai idan yana so ko baki sani ba? Ki sani fa in dai mijinki bai yi maki laifin komai ba kika azabtar da shi, wlh babu in da zaki je sai Allah ya kamaki, koda ma ace ya yi maki wani laifin bai kamata ki rama da sharri ba, ki kyale shi ai Allah yana ganinku, kada ki yarda kiyi abu da gangan dan ki kuntatawa wani ma bare mijinki, kowa ya biki da sharri ki bishi da alkhairi, sai kiga Allah ya kareki daga wannan sharri da yake nufarki da shi, duk lokacin da kika yi abu da gangan dan ki cutar da wani, ki sani Mala'ikun Allah ta'ala suna tsine maki albarka, tsinuwar mutun ɗan adam ma kawai idan aka barki da shi ya zaki kare bare kuma tsinuwar Mala'iku? Common bakin mutane yana lalata mutun bare shinuwa bare kuma na Mala'iku, tun wuri na gaya maku ku shiga hankalinku ku san menene miji a gareku, ba abin wasa bane shi ɗin, yana da kyau ku kula sosai". Da yake Rimsha da gangan ta yi ƙunshin nata, sai ta ji kamar da ita mum take yi, duk sai ta damu sosai, jikinta duk sai ya yi sanin, yanzu ace ita ma Lion idan ya ganta zai yi ta zuba amai kamar yadda Aseef ya yi ai ba kamar cutar da shi ta yi ba, meya yi mata da zata cutar da shi haka? Koda ma ace ya yi mata wani laifin meyasa zata cutar da shi ta abin da tasan baya so? Meyasa ba zata tsaya a iya fushin da ta yi da shi ɗin kawai ba? Meya yi mata har haka da ya cancanci hukuncin cutarwa daga gareta?. Sosai ta rinƙa tunani tare da danasanin yin wannan ƙunshi da ta yi, sai dai kuma bata jan ye fushin da take yi da shi ɗin ba, ta ce dai fushi kam ba zata fasa ba tun da ya nuna baya sonta... Ƙasa da kai sosai Akilar ta yi tana sauraron nasihar ta mum, ya ratsata sosai da sosai, duk sai ta ji babu daɗi, ta ji ta matuƙar damu sosai. Ita kuwa mum sosai ta yi masu nasiha mai ratsa jiki, sannan ta miƙe ta nufi nata part ɗin wanda yake a kusa dana gwaggon. Tana shiga ta isko daddyn Rimsha yana tsaye a wajen mirror. "Kin tafi wajen ƴaƴanki kin manta da ni ko? Kefa ko kewata ma baki yi ba ko?". Ya faɗa yana juyo da kallonsa a kanta. A gefen bed ta zauna tana mai bashi hakuri. Toilet ya nufa yana faɗa mata ba zai hakura ba, bari ya fito wanka zai ɗauki mataki...........🙄🙃 A ɓangaren Aseef kuwa, ya ci bakar wahala kafin ya samu ya dawo dai'dai, har wani firgicewa fuskarsa ta yi, bawan Allah ba laifinsa bane, a jininsu abin yake, gado aka ce ba karambani ba. Shi ma dai Dr William ya ci bakar wahala kafin ya samu ya dawo dai'dai, bedroom nasa Areef ya wuce da shi, suka bar masu aiki da aikin gyaran parlourn, kowa ya wuce part nasa, dan su yi wanka su huta zuwa dare. After some hours. Lion da sir Arvin zaune suke a saman bed ɗin na Lion da yake a cikin bedroom nasa, ita kuma Pinky tana a tare da Dr William, daga shi sai sir Arvin suka saba a gidan, sai kuma Lion tana ɗan yarda da shi, albarkacin kamar da yake yi da sir Arvin yasa take yarda da shi idan zai ɗauketa ko ya bata abu, tana yarda. Sai hira suka yi gwanin ban sha'awa, da yake dukkansu ba sarakan yawan magana bane, sai ya zamana hiran nasu sama sama suke yinsa. Areef ne ya shigo cikin bedroom ɗin bakinsa ɗauke da sallama, kayan barci masu bala'in kyau irin na jikinsu Lion ɗin ne a jikinsa, sai dai nasa ash color ne, Lion da sir Arvin kuma nasu white colors ne, da alama shi ma sir Arvin sarkin son farin abu ne, dan ko kayan Lion zai sanya farare kal kal yake ɗaukowa, son farin abin nan a jininsu yake. (Nima a jinina yake, fav color na kenan a duniya🥱 kusan komai idan zan saya in dai akwai fari, to shi zan ɗauka, kuma kun shaida😂) Saman bed ɗin ya haye yana faɗin "Our Lion what's wrong with you? And meyasa baku fito mun je dining room dan yin dinner ba?". Ya yi maganar yana mai karewa Lion ɗin kallo, nazari face nasa yake yi, da yake shi ya san ɗan uwan nasa fiye da sir Arvin, shiyasa yana shigowa ya fahimci akwai abin da yake damunsa, dan damuwar ta fito karara a saman face nasa, shi kuma sir Arvin sam bai gane ba, saboda dama bai san halinsu ba, da saura tukun nan. "Areef Meesha fushi take yi da ni fa, taki zuwa in da nake, kuma she knew that i hate this thing that she did on her legs and hands, amma ta je ta yi har da wuyarta, because of tana fushi da ni". Ya faɗa yana mai ɗauko wayarsa dake a saman bedside drawer. Da yake shi Areef yasan menene matsalar da take a tsakaninsa da Rimshar, sai ya ce "Ok yanzu dai muje muyi dinner, daga baya zamu yi maganar Rimshar, dama shiyasa nace maka idan ka sauka a kasar China ka kirata a waya, saboda mata sai ana lallaɓasu". "Yau kowa a bedroom nasa zai yi dinner, saboda rashin jituwa da yake a tsakanin momma da dad, bana son mu haɗu a dining room ba tare da na gayawa mum abin da yake faruwa ba, idan ba haka ba za'a samu matsala, dan dad ba zai ganta ya yi shiru ba, ita kuma ba zata saurare shi ba, so the solution kawai kowa ya yi dinner a bedroom nasa, zuwa gobe da safe ko anjima zan sameta na gaya mata abin da yake faruwa". Cewar Lion kenan. Baki ɗauke da sallama Aseef ya shigo cikin ɗakin, duk ya yi wani iri da shi bawan Allah, wannan aman da ya rinƙa yi ta galabaitar da shi sosai, har ya ɗan yi rama, sai dara daran idanuwan nan nasa kamar ball. A saman bed ɗin shi ma ya haye yana faɗin "Ni Areef ka matsa bari na yi barci". Fuska a ɗauke da mamaki sir Arvin ya ce "What? Ina ƴar aljannarka take da zaka zo nan kace zaka yi barci? Ina ka barota?". Areef ne ya capki zancen da cewa "Shi ne nima abin da zan tambaya kenan, ina ka baro Heartbeat da zaka zo nan ka ce mana bari ka kwanta, Heartbeat taka da kake ta kukan ta dawo ne fa! Ko ka manta ne?". Ya kai karshen maganar yana dariya, dan yasan me matsalar, da gangan ya yi mashi wannan tambayar. Shi dai Lion ko a jikinsa, ƙoƙarin mikewa ma yake yi ya je wajen gwaggo, dan ya kalli Meesharsa, yana kewarta sosai, yana son ganin face nata ko zai sami saukin abin da yake ji. "Ni Areef ku rabu dani, su fa mata idan ka biye masu wlh sai ka mutu bama kasan ka mutu ɗin ba, sai ka ji ka kabari zaka gane". Dariya kamar Areef zai mutu, shi dai yana burin daman yaga Aseef da Akila sun yi faɗa kamar yanda Lion da Rimsha suka yi a yanzu, dama sun ishesa, ji yake kamar duk ya shakesu, bini bini suna manne da matan nasu, to yau dai Allah ya kamasu dukkansu, matan nasu yau ji da sabon iskanci suke yi, ita kam Rimsha ai sai dua'i, wai fushi ma take da Lion, ita kuwa Akila ƙunshi, dole Aseef ya daka yaji sai ƙunshin nan ta goge............😂 Damko Areef ɗin Lion ya yi tare da haɗe hannayensa dukka biyu, dan Areef yana kule su har wuya, suna fama da zafi zai kara masu wani ta hanyar yi masu dariya, a maimaƙon ya tayasu shawo kan matsalarsu, amma saboda neman tsokana sai ya kama dariya, yau kam ba zasu barshi ba. Da sauri Aseef ya sauka kasa daga saman bed ɗin ya je ya ɗauko igiya dan tsabar mugunta, so yake yi Lion ya ɗaure Areef ɗin, ɗaurin goro su jibge shi, saboda Areef ɗin yana kara masu zafi a kan zafi na abin da suke ji, idan ba iskanci ba yazo ya tasasu a gaba yana masu tambayoyi, idan sun gaya mashi ga yadda aka yi, sai ya zauna ya yi ta dariya har yana shakewa tare da yin tari tsabar mugunta, wlh dole yau su yi maganinsa. (Rifat yau Allah ya kama Areef ɗinki, kuma ba mai kwatarsa😂 dama tara mashi suke yi tun tuni, sai yau dubunsa ya cika) Karɓar igiyar Lion ɗin ya yi tare da fara ƙoƙarin ɗaure hannayen Areef ɗin. Da sauri sir Arvin ya ce "A'a meyayi maku zaku ci zalinsa?." Kin kula shi Lion ɗin ya yi, Aseef sai faman dukan Areef ɗin da pillow yake yi yana faɗin "Kai ma Allah yau ba zaka je wajen matarka ba, a nan zamu zauna kamar masu takaba a tare". "Wannan ne kuma baku isa ba" Cewar sir Arvin, ya yi maganar tare da kai hannunsa zai kwaci igiyar da Lion ɗin yake ƙoƙarin ɗaure hannayen Areef ɗin da shi. Da sauri Aseef ya yi ƙoƙarin hana shi, amma ina tuni ya kwace igiyar yana faɗin "Areef jeka wajen matarka hai, shi Saif waye ya ce ya yi wa tasa Queen ɗin laifi? Kai kuma Aseef me kayi mata nema da har ta yi fushi da kai ɗin ma?". Har lokacin Areef bai dai'na dariya ba ya ce "Lion fa sai da nace mashi idan ya je kasar China ya kirata a waya ya rarrasheta, dan shi ya yi mata laifi, ya ɗauka mata wasa ne, to ai ga shi yanzu zai karɓi ga shi a zuciyarsa". Ya kai karshen maganar tare da sake kwashewa da dariya. A kule Lion ɗin ya haɗesu daga Areef ɗin har sir Arvin ɗin ya murɗe masu hannu ɗai ɗai ta baya, sai da sir Arvin ya furta wash da karfi. Aseef kuma tsabar mugunta har da sake ɗauko wata igiyar dan Lion ya ɗauresu. Ƙoƙarin kwace kansu suka farayi, da Aseef ya ga haka sai ya matso ya fara taya Lion ɗin dannesu da kyau, kamar wasu ƴaƴan mage, abin dariya gwanin ban sha'awa. Shigowar Tga da Mark cikin ɗakin ne yasa Lion ɗin ya sake su, dan idan baku manta ba baya wasa da TRIPLETS nasa a idanun kowa, dan baya son ra'ini, so baya son su Mark suga ashe yana wasa da ƴan uwan nasa har haka, shi ne yasa ya sakesu tare da miƙewa ya ɗauki wayarsa ya nufi waje. Mark bawan Allah har yanzu yana ɗan ɗingisa kafa, bai gama samun sauki ba, sai dai ya kara wani irin azababben kyau, ya ɗan yi ƙiba kaɗan, ga shi kuma ya tara gashin kansa saboda jinyar da yake yi, sai ta kara mashi kyau sosai, a yanzu ya ce tun da ya musulunta a rinƙa kiransa da sunan Abdurrahman Sudais, so wannan ita ce sunansa ta musulci, idan baku manata ba dama shi ma Tga time da yake karami yake tare da su Josephine, sunansa Sudais, kafin su Anderson da Cherish su ruguje komai ya koma Tyson ɗinsa. Zama a saman bedside drawers Abdurrahman wato Mark da kuma Tga ɗin suka yi, sun zo duba sir Arvin ne daman, dan haka sai suka fara gaisawa cikin girmama juna da mutunta juna. Shi kuwa Lion yana fita bedroom na gwaggo ya nufa. Bakinsa ɗauke da sallama ya shiga ciki, daga ita sai Rimsha ce kawai a cikin bedroom ɗin, ga abincin da Lion yasa aka kawo masu an jere masu a dining na parlourn part ɗin nasu, basu je sun ci ba, suna zaune a saman bed, kuka Rimshar take yi, gwaggo na aikin rarrashinta tare da tambayarta me yake damunta, ta tada kai da laps na gwaggon, kayan barci wando guntu zuwa iya santala santalan cinyoyinta ta sanya, sai kuma ƴar karamar riga mai hannun vest zuwa iya kugunta, Kasancewar kayan launin pink color ne sai suka yi mata kyau sosai, babu ɗankwali a kanta, ta saki wannan dark black curly hair nan nata har baya, sai aikin kuka take yi, an tambayeta dalili kuma taki faɗa. Jin zazzaƙar muryarsa ya yi sallama ne yasa gwaggo ta kai kallonta a kansa, ita kuma Rimsha runtse idanuwanta gam ta yi, wai dan ma kada ta kalle shi su haɗa idanu, dan duk da bata ji sallamar tasa da kyau ba, kamshin daddaɗar perfume nasa ya kai mata saƙon ya shigo a cikin hancinta. Saman bedside drawer ya zauna, gabaɗaya bedroom ɗin ta bule da kamshin perfume nasa, ga ɗumi mai daɗi yana tashi a cikin ɗakin, tun da ya shigo idanuwansa suke a kanta, ya kasa kawar da kallonsa, ga hawaye a saman face nata na kukan iyashege da take yi wa gwaggo. "Good evening momma". Ya faɗa cikin sanyin murya. Kasa jurewa Rimshar ta yi, hakan yasa ta miƙe daga kwanciyar da ta yi a saman laps na gwaggon, ba tare da ta kalli in da yake ba ta sauƙo kasa daga saman bed ɗin ta nufi hanyar fita abinta. Tana dab da fita sexy voice nasa ya daki dodan kunnuwanta wanda ya sanyata jan birki babu shiri, dan da tsawa ya yi maganar. "Are you out of your sense? Kin manta kayan da yake a jikinki ne da zaki fita waje da su?!". Ya yi maganar yana kara ɗaure fuska sosai da sosai. Turus ta tsaya ta kasa gaba, ta kuma kasa juyowa, ta san in ta sake ta fita a haka, wlh tsab Lion zai iya karyata a wannan zafin kishin nasa, ba za kuma ta iya juyowa su yi ido huɗu da shi ba, saboda tsoronsa da take ji kuma tana fushi da shi. Ganin haka yasa gwaggo ta miƙe tare da nufar in da take a tsaye, hannunta ta riko da nufin su dawo cikin bedroom ɗin. Kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro ta sakarwa gwaggo tana tirjewa a kan ita ba zata dawo cikin ɗakin ba, ita ba zata zauna waje guda da Yah Saif ba. Babbar magana. Sai a yanzu gwaggon ta gane menene yake faruwa, wato dai suma faɗa suka yi kamar Jehan da Areef, lallaima. Jin hakan yasa gwaggon ta ɗauko hijabinta da ta yi sallah ta sanyawa Rimshar a jikinta, sannan ta ce mata to ta tafi bedroom na Aafia da yake a cikin part na gwaggo, idan Yah Saif ɗin ya tafi sai ta dawo su kwana a tare. Ai tun gwaggon bata gama magana ba ta yi saurin ficewa tana ɗingisa kafa. Duk abin da suke yi yana jinsu, yaki ɗagowa ya kallesu ne dan tsab zai iya zane Rimshar da bulala sai jikinta ya gaya mata, kuma ba hakan yake so ba, yana so ne su shirya, hakan yasa ya danne zuciyarsa kawai yana jin yadda gwaggo take biye mata, yasan ma idan ya ce zai yi mata wani abin ba zasu yi ta daɗi da gwaggon ba, gara mashi kawai ya rabu da su yadda ya gansu, a tare ya gansu dama....... Dawowa cikin bedroom ɗin gwaggon ta yi, a saman bakin bed ta zauna suna fuskantar juna da Lion ɗin, tun bata yi mashi magana ba ya ce "Momma fushi dani Meesha take yi fa". Yadda ya yi maganar sai da gwaggo ta ji wani iri, saboda ya yi ta ne kamar wani mara lafiya. "Mekayi mata to?". Nisawa ya yi kafin ya gaya mata duk abin da ya faru, dan yaki kiranta a waya kuma dan ya tafi ya barta ne yasa take fushi da shi har take cewa dama tasan baya sonta. Murmushi kaɗan gwaggon ta yi kafin ta ce "Rimsha manya, yarinta ce, amma kuma kai ma baka kyauta ba da baka kirata a wayar ba, yanzu dai sai ka san yadda zaka yi ka shawo kanta, ni babu ruwana da faɗarku, Rimsha tana da saukin kai sosai ba kamar Jehan ba, tana kuma da tausayi, zata saurareka, idan ka bata hakuri komai zai wuce, kamar mummynta take da kyan zuciya". Maimaita kalmar hakuri a cikin zuciyarsa ya yi, a fili kuma sai ya ce "Shikenan momma zan yi abin da kika ce, amma yanzu dai bari muyi magana a kan dad". "Saif bana son wannan maganar". Matsowa ya yi tare da rike hannayenta dukka biyu a cikin nasa, a nutse ya fara yi mata magana ta yadda zata fahimce shi, ya sanar da ita komai ba tare da ya tsawaita bayanin ba, ya yi mata yadda zata fahimta kawai. Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "Dare ya yi, zan je naci abinci na kwanta, sai da safe, ka je kaima ka kwanta". Kallon face nata da kyau ya yi kafin ya ce "Kin yafewa daddyna?". Harara ta watsa mashi kafin ta sake ce mashi "Nace maka dare ya yi, kaje ka kwanta". Sake hannayen nata ya yi tare da ɗan shafa kansa da hannu guda, sannan ya miƙe tsaye tare da nufar hanyar fita daga cikin bedroom ɗin. Da kallo ta bishi da shi tana mai kara godiya ga Allah da ya bata waɗan nan ƴaƴan, taurari waɗan da kowa zai yi fatan samun makamantansu. Yana fitowa parlourn gwaggon ya ci karo da daddyn nasu zai je wajen gwaggon, dan ya kasa hakuri, yana son gwaggo sosai, ba zai iya jurar taki kula shi ba, shi ne ya yanke shawarar bari ya je ya sameta su fahimci juna. Gaishesa Lion ɗin ya yi tare da wucewa abinsa, ya rage nasu, shi dai ya yi abin da zai iya yi, ya yi wa gwaggo bayani, Dr William ya je ya karisa sauran aikinsa. Bedroom nasa ya nufa, yana shiga Areef yana fitowa tare shi da Aseef. "Ina zaku je ba tare da mun yi dinner ba?". Ya tambaya yana kare masu kallo. Wucewa gaba Aseef ya yi yana faɗin "Ni wajen momma zan je, sai anjima zan yi dinner, shi kuma Areef ya ce mani zai je ya ɗauki matarsa ya je ya yi dis virgin nata". Ya kai karshen maganar tare da wucewa abinsa. Aseef manya sun yi sirri shi da Areef amma ya tonawa Areef ɗin asiri.........😂 Harara Areef ɗin ya bishi da shi kafin shi ma ya wuce gaba yana faɗin "Abin da Aseef ya faɗa shi zan je na aikata, idan na gama aikin zan yi dinner, yanzu ba zan iya cin komai ba, dan a gaskiya yau ba zan iya hakura ba". Ya kai karshen maganar tare da wucewa ya nufi part ɗin na gwaggon. Wucewa cikin nasa part ɗin shi ma Lion ɗin ya yi, zuciyarsa a cike tab da tunanin yadda ya kalli Meesharsa sanye da waɗan nan kayan barci, abin ya tsaya mashi a rai, ga wani azababben sha'awarta da yake ji, ga shi ta kara kyau na ban mamaki. Yana zuwa ya haye saman bed nasa kusa da sir Arvin da yake kwance, su Mark sun fita daga cikin ɗakin tun ɗazun. Wani irin azababben sha'awarta ne yake kara taso mashi, duk sai ya ji cewa ba zai iya cin abincin bama shi ma, Meeshansa kawai yake da bukatar ya jita a jikinsa. Sosai sir Arvin ya lura da cazawarsa tun time da ya shigo, dan haka sai ya yi ƙoƙarin tambayarsa meyake faruwa? Dan ga idanuwansa nan duk sun kaɗa sun yi jajir da su, ya je ya gano abin da zai hana shi yin barci. Shi kuma Areef yana zuwa part na gwaggo zai shiga bedroom nata sai ya hango su Jehan ɗin a ɗayar bedroom dake a kusa dana gwaggon, dama na gaya maku bedroom uku ne a cikin kowani part sai parlourn ɗaya, dan haka sai ya fasa shiga wajen gwaggon, dama ba ita yazo gani ba, matarsa ya zo ɗauka ya je ya aikata sirrin da suka yi shi da Aseef........(wlh TRIPLETS ƴan duniya ne, duk abun da ɗaya zai yi sai ya gayawa ɗaya kamar an tambayesa😂 idan baku manta ba shima Aseef ɗin haka ya sanar da Areef ɗin zai yi dis virgin na Akila time da suke Nigeria, amma Allah bai yi ba, to shi ma yanzu ya gayawa Aseef ɗin ga abin da zai je ya yi😂 anya basu gayawa sir Arvin bama kuwa?🤔 Dan sufa sam basu da kunya a rayuwarsu) A bakin kofar bedroom ɗin ya tsaya yana kare mata kallo, daga ita sai kayan barci kusan irin na jikin Rimsha, gwaggo ce ta ce saya masu kayar time da suka je shopping bayan sun je lalle kenan. Akila tana cikin bargo ta ƙudundune, da alama kewar Aseef take yi, shi kuma ya yi yaji har sai ƙunshi ta goge........😂 Ita kuma Aafia tana a saman dadduma ta idar da nafila tana addu'a baiwar Allah, Rimsha na zaune tana latsa wayar Akilar. Duba da cewa basu san ya shigo cikin bedroom ɗin bane yasa ya ɗan yi masu gyaran murya, a tare suka ɗago kai suka kalle shi. Kasa da kai Rimsha ta yi tana ƴan kame kame, ita kuma Aafia sai ta cigaba da yin adduo'inta, Akila dama already ta basu baya ne tana ƙudundune a cikin bargon, so bata juyo ba. Ɗan zaro mashi idanu Jehan ɗin ta yi alamar mamakin me ya kawo shi?. Gera guda ya ɗaga mata alamar tazo. Mikewa ta yi tare da dirowa kasa daga saman bed ɗin, rashin sani yafi dare duhu, bata san meya shirya mata ba. Tana isa gabansa ya ja hannunta suka nufi waje, suna fita ya sunkuceta sai saman shoulder nasa yana faɗin "Shi ne zaki barni ni kaɗai ko? Ke yanzu idan na barki a nan zaki kwana?". Kai ta gyara mashi alamar yeah a nan zata kwana. "Ni kuma in yi yaya idan kin kwana a nan?". Saƙalo wuyarsa da hannunta ta yi tana faɗin "Ka rungumi sorry tare da pillow mana". "Da gaske?". Ya yi maganar yana direta a saman bed nasa. Wani irin laushin da bata taɓa jin irinsa ba ta ji a saman bed ɗin nasa, bedroom ɗin nasa ta fara bi da kallo, daula ce guda, duniya ce guda, ya haɗu iya haɗuwa, ga wani azababben daɗin kamshin air freshener da yake tashi, kasancewar su sanyi ne da kasar tasu, sai ya zama na'urar ɗumama ɗaki suke kunnawa, ɗumi mai daɗin gaske ne yake a cikin bedroom ɗin. Sam bata san lokacin data lumshe idanuwanta ta dake buɗesu a hankali ba, duk dan ta tabbatar da ba mafarki take yi ba, a duniya take. Hayewa saman bed ɗin ya yi tare da jawota jikinsa yana faɗin "Zo ki yi mani tausa kafin mu tashi mu yi dinner kin ji?". Shigewa jikinsa ta yi tana turo ɗan baki. "Ni Yah Areef ban iya tausa ba". "To ni in yi maki?". Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e ya yi mata. Sumbatar lips nata ya yi kafin ya miƙe zaune, kayan jikinta ya fara rabata da su bayan ya kashe wutar ɗakin. "Yah Areef me haɗin tausa kuma da cire mani kaya?". A kunne ya raɗa mata cewa babu kaya sai tausar ta fi yi mata daɗi, kuma shi ma zai fi jin daɗin matsa ko'ina. Shiru ta yi mashi bata sake tankawa ba. Tas ya cire mata kaya kafin ya shiga matsa mata laps nata cikin salo da soyayya. Wani irin daɗi ta rinƙa ji, bata san time da ta fara zuba mashi shagwaɓa ba, hakan ba ƙaramin kara gigita shi ya yi ba, tuni ya matso ya haɗe bakinsu waje guda, hannunsa guda yana a saman cinyarta yana ɗan matsa mata. Kukan shagwaɓa ta sa mashi a kan ita gaskiya bata yarda ba, tausa ya ce zai yi mata ba soyayya ba. Cikin wani irin yanayi na sha'awarta mai wuyar fassaruwa ya ce Please ta barshi haka nan, idan ta cigaba da zuba mashi shagwaɓar nan zata sanya ya zauce, soyayar kaɗan zai yi ba dayawa ba. Juya mashi baya ta yi tana faɗin ta yi fushi. Cikin zafin nama ya juyo da ita tare da kai ɗan bakinsa saman nipples nata, da zafi zafi ya fara shansu babu kakkautawa. Tun bata biye mashi har ta fara mayar mashi da martani ta hanyar fara wasa da ɓul ɓul ɗinsa, nan take ta kara birkita mashi lissafi, bai san time da ya cire rigar barcin jikinsa ba. Sun ɗan murji juna kafin ta kasa iya biye mashi ta sakar mashi ragamar tana yi mashi kuka a kan ya rabu da ita ya isa haka. Sam bata ankara ba, ta yi nisa bata san time da ya shigeta ba, sai dai ta ji wani bakin azaba ya ziyarceta. Ihu ta zunduma mashi tare da fara ƙoƙarin tureshi daga jikinta, amma ina sam ta kasa, ihu take yi da gasken gaske tana kai mashi duka a baya, amma ko kaɗan bai saurara mata ba, sai da ya aiwatar da abin da ya yi niya. Sunci bakar wahala, ita ta suma shi kuma ya wahala, dan shi ma da kyar ya iya shigarta, duk da ta girmi Rimsha, amma ya sha wahala sosai kafin ya sami hanya, kuma ya azabtar da ita matuka. Da ya dawo cikin hayyacinsa ya ga ta suma, sai tsoron abin da ya yi ta kama shi, wanda dama duk yawanci ana samun haka a wajen maza, wannan lokaci tsoro tana shigarsu duk jarumtarsu, duk da yasan da ba makawa hakan zata faru, amma tsoro sosai ya kama shi, ya shiga damuwa sosai ta yadda har ya diro kasa daga saman bed ɗin ba tare da ya sani ba, cikin hanzari ya fara taɓata yana ambatar sunanta, amma ko motsi bata yi, ga kuma uban jininta da ya zuba kamar an yanka rago, abinku da white bedsheet, sai jinin ya fito ɓaro ɓaro, duk da ya saba ganin jini, amma na yau na daban ne, ya rikita shi, ya rasa meyakamata ya yi mata, Allah sarki sai yanzu yake jin tausayin Lion, ashe haka Lion ɗin ya ji wancan ranar, dole ya rikice, ashe abin ba karamar abu kamar yadda ya ɗauka bane, ta wuce tunaninsa. Wandon barcinsa ya sanya a jikinsa tare da fitowa da sauri ya nufi part ɗin gwaggo, dan shi har ga Allah ya rasa meyakamata ya yi mata. (Ni kam nace gwaggo kina ganin rayuwa😂 kinga na Lion yanzu kuma ga Areef nan shi ma, saura autanki da baban yaya sir Arvin😂 sai kuma Anaya ta Mark, kina da sauran aiki Dr gwaggo tamu ta zamani😂) Ko sallama babu ya afka a cikin bedroom ɗin na gwaggon, a lokacin kuma Dr William ya tsugunna kasa a saman gwiwowinsa a gaban gwaggon yana bata hakuri bawan Allah, ya rike kunnuwansa da hannaye bibbiyu yana ce mata sorry, ita kuma tana hakimce a saman bed in da Lion ya barota ɗazun, taki kula shi, sai hakuri yake bata. (Hajiya gwaggo da girman kujerarki👍😂) Ganin Areef ɗin a birkice haka yasa ta mike da sauri tana tambayarsa lafiya meyake faruwa ya shigo masu a birkice?. Mikewa shi ma Dr William ɗin ya yi, kusan a tare suka tari Areef ɗin suna masu haɗe baki wajen sake tambayarsa lafiya yake kuwa?. A birkice ya ce masu "Momma dad my wife, Jehan....Jehan..." Iya abin da yake ta furta masu kenan, saboda a ruɗe yake, ga word ɗin sam basu fita a dai'dai, ya zama mai in'inar dole. Kusan a tare Dr William da gwaggon suka haɗa baki wajen cewa "Meyasami Jehan ɗin? Ina take kuma........" Gwaggo bata karisa tambayar ba ta lura da yanayin da yake a ciki, babu riga a jikinsa, sannan ga shi nan ne dai, abin da ya faru da Lion da Rimsha ne ya dawo mata cikin ƙwaƙwalwarta, hakan na nufin shi ma abin da ya aikata kenan, innallilahi. Dr William kuma ya riko shi sai faman tambayarsa yake yi, sun mance da zancen cewa faɗa ma suke yi shi da gwaggon , sun rungumi ɗan nasu suna tambayarsa me yake faruwa...........(Ni kuma na rungumi Maltinata mai sanyi ina mata wani irin ƙurɓa mai sanyaya zuciya🥱🤨) ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNMATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* Date: 28/5/2024 E41 Dr William kuma ya riko shi sai faman tambayarsa yake yi, sun mance da zancen cewa faɗa ma suke yi shi da gwaggon, sun rungumi ɗan nasu suna tambayarsa me yake faruwa?. Wucewa gwaggo ta yi tana tambayarsa ina Jehan ɗin! A ina ne bedroom ɗin nasa?. Da sauri ya bi bayanta dan ya je ya nuna mata, duk a birkice yake bawan Allah. Rufa masu baya Dr William ɗin ma ya yi. Kamar yadda ya barota haka suka shigo suka sameta, ko motsi bata yi, tana a sume. Saman bed ɗin gwaggon ta haye ba tare da ta sake ɗaga idanuwa ta kalli in da suke ba. Ganin hakan yasa Dr William ɗin ya fahimci abin da ya faru, ƙoƙarin taimakawa gwaggo ya fara yi, dakatar da su ta yi tare da ce masu daga shi har Areef ɗin su fita su bata waje dan Allah, sannan Areef ya kawo mata A box ya kuma nuna nata word room nasu, dan ta je ta ɗauki abubuwan da zata ɓukata. Jikinsa har kerma yake yi bawan Allah, duk a tsorace yake ya wuce ya nufi wajen da yake ajiye A box ɗin nasa, da yake dukkansu suka da A box ɗin a cikin bedroom ɗin nasu, sai ya ɗauko da sauri ya kawo mata. Karɓa ta yi tare da kara gaya masu su fita su bata waje ta yi aikinta. Ba musu Dr William ya ja hannun Areef ɗin dan shi bashi da burin da ya wuce yaga gwaggo a cikin farinciki, baya son ɓata mata rai, shiyasa ya ja Areef ɗin dan su fita wajen kamar yadda ta buƙata. Da farko Areef ɗin ya kafe yaki fita, sai da gwaggo ta yi mashi kalamai masu taushi tare da gaya mashi in dai yana ɗakin ita ba zata iya duba Jehan ba, so idan yana son a ceci ran matarsa sai dai ya fita. Jin hakan ne yasa ya yarda ya bi daddyn nasa suka fice waje. Bedroom na daddyn nasa suka wuce, sai kerma jikinsa yake yi, duk jarumta irin tasa yau ya nemeta ya rasa, wani irin tsoro ne ya shige shi. A saman bed nasa daddyn ya zaunar da shi yana mai tausarsa tare da kara mashi kwarin gwiwa. Murya a raunace ya ce "Daddy ba zata mutu ba ko?". Zama a gefensa daddyn ya yi tare da ɗan rungumo shi yana faɗin "In Sha Allah ba zata mutu ba, babu abin da zai sameta, mommarku ƙwararriyar likita ce, zata yi mata magani, cikin ƙanƙanin lokaci zata sami sauki, be strong my son". Sake jikinsa ya yi ya kwatar da kansa a saman laps na daddyn nasa yana faɗin. "Daddy she's bleeding and kuma bata motsi, please daddy help me kada ta mutu, i really love her more than your expectations". Ya yi maganar da wata iriyar raunataciyar murya. "My son calm down, babu abin da zai faru ka ji ko? Bari na kawo maka ruwa ka sha, sai ka kwanta a saman bed nawa ka huta kaɗan kafin mommarku ta gama aikinta ka ji?". Shiru ya yi ya kasa magana, saboda bai san me zai sake cewa daddyn nasa ba. Ruwa mai sanyi a fridge daddyn ya ɗauko mashi tare da dawowa ya kawo mashi. Tsabar yana cikin damuwa bai san time ɗin da ya ɓalle robar ruwan nan ya fara sha ba, sai da ya shanyeta tas ne ya lura da ma ruwa yake sha ashe. Karɓar robar dad ya yi tare da ce mashi to ya kwanta ya huta, wayo daddyn yake so ya yi mashi, yana so ne ya saka shi yin barci, idan ba haka ba ciwon kai zata kama shi, saboda da alama abin ta taɓa shi sosai, yasan cewa idan ya ce kai tsaye ya kwanta ya yi barci, ba zai taɓa yarda ya kwanta ɗin ba, amma da yake babba kam babba ne, kuma wanda ya haifeka ko bai taɓa zama a class ba to zai iya juyaka ta sigar da baka yi tunani ba koman iliminka kuwa, koda ka kai matsayin professor or Dr, bare kuma shi Dr William da karatun ma da ya yi sam babu wanda ya yi ko rabinsa a cikinsu, da shi da gwaggo ai sun yi karatu bana wasa ba, idan baku manta ba duk soyayyar da suka yi a tsakaninsu, basu taɓa yarda soyayyar ta shafi karatunsu ba, shi ne ribar da suka fara cinmawa kenan, dan haka sai ya lallaɓa shi har ya yarda ya kwanta ba tare ma da yasan ya kwanta ɗin ba, zama a kusa da shi daddyn ya yi yana mai cigaba da lallaɓa shi har sai da burinsa ya cika barci ɓarawo ta ɗauki ɗan nasa. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da miƙewa ya nufi waje, dan ya je ya duba gwaggo da kuma jikin Jehan ɗin, tun da Allah ya taimakesu barci ya ɗauki Areef ɗin, kuma da alamar gajiya sosai a jikinsa, so barcin nasa zata yi nauyi sosai. A ɓangaren Lion da sir Arvin kuwa, ko da sir Arvin ya lura da canzawar ɗan uwan nasa, sai ya yi ƙoƙarin tambayarsa me yake faruwa ya gansa a cikin damuwa har haka?. Sam Lion bai ɓoye mashi komai, ya gaya mashi abin da yake faruwa a tsakaninsa da Rimshar, daga karshe ya rufe mashi da cewa "I can't sleep without her, am in to much of missing her". Matsowa sir Arvin ɗin ya yi tare da dafa kafaɗunsa, cikin nutsuwa ya fara magana. "Ba tana sonka sosai ba?". Jinjina mashi kai ya yi alamar yeah tana son shi sosai. "To in dai tana sonka sosai me ka zauna jira? Go and carry her, duk fushin da take yi da kai na tabbata sai dai idan bata haɗa jiki da kai or baka ɗaukota zuwa nan ba, kuna dawowa cikin bedroom nan shikenan, ka mantar da ita cewa tana yin wani abin wai shi fushi da kai, are you not a man? Ai ba ma sai na gaya maka ba, yakamata kasan abin da zaka yi mata". Nisawa ya yi kafin ya ce "I know that idan na ɗaukota ko kuma na tsaya na yi magana da ita na second biyar kawai zata dai'na yin fushin, dole ma ta sauko ta hakura, tana da zuciya mai kyau, but the problem here is, wannan abin da ta zana a jikinta, i don't want to see it at all, yana sanyani ciwon kai mai tsanani, and then kuma yana sanya zuciyata tashi, ba dan haka ba, zan yi abin da ka ce". Shiru sir Arvin ɗin ya ɗan yi kafin ya ɗaura da cewa. "Ka danne zuciyarka, ka kawar da tunanin abin a ranka, and then kuma ai abin ba wani abin kyama bane ba, is just a flowers ne fa kawai, please Saif kada ka cutar mana da kanka, kawai ka je ka ɗauko ta, ka kalli flowers ɗin da ta yi ɗin a matsayin masoyiyarka da tafi kowa sonka ta yi maka kwalliya, idan ka gan shi ta wannan sigar to tabbas zaka ji kana son flowers ɗin sosai, ka kallah a matsayin kai ta yi wa kwalliya, kuma soyayya ce tasa ta yi maka hakan, you will love it more than your expectations". Shiru ya yi tamkar ba zai sake tankawa ba, sai kuma ya miƙe tsaye tare da sumbatar sir Arvin ɗin a kumatu yana faɗa mashi yana zuwa bari ya je wajenta. Da ɗan guntun murmushi sir Arvin ɗin ya bishi da shi yana mai jin tsananin kaunar ƴan uwan nasa har cikin ransa. Yana fita part na gwaggo ya koma. Babu kowa a cikin bedroom ɗin na gwaggon, kai tsaye sai ya nufi ɗaya daga cikin bedroom da yake a part ɗin wanda yake zaton zai samesu a ciki. Ya kuwa yi sa'a Akila da Aafia suna a cikin bedroom ɗin, Rimshar bata nan. Karo na farko a rayuwarsa tun da ya girma ya yi wayo da ya fara magana da wata mace bayan Rimsha da gwaggo, Aafia ya tambaya ina Rimsha, dan Akila kam har yanzu tana ƙudundune a cikin bargo, da alama zazzaɓi ne yake damunta. Sosai Aafia ta tsorata da ganinsa, tun da take bata taɓa ganinsa ba sai yau, wani irin razana ta yi saboda kwarjininsa, ga shi yana sanye ne da kayan barci ya kuma saki dark black curly hairnsa nan har baya, sai ta kalli kamar aljani ne ba mutun ba, saboda azababben kyansa, ga idanuwansa sun kara kyalli, saboda dare. Bakinta har kerma yake yi wajen bashi amsar Rimsha tana ɗakin mummynta. Bai sake bi ta kansu ba, ya juya ya fito daga part ɗin mai gabaɗaya. Part ɗin daddyn Rimshar ya shiga, bakinsa ɗauke da sallama kasa kasa. Iya daddyn Rimsha ne kaɗai a cikin parlourn, mum da ita Rimshar suna cikin bedroom, yanzu suka kammala cin abincin a tare, shi ne mum da Rimshar suka shiga ciki, ita mum ta wuce bedroom nata, ita kuma Rimsha ta shiga ɗayar bedroom ɗin, dan ta yi wanka ta shirya ta kwanta a cikin bedroom ɗin, ta ce wa mum ɗinta yau a nan zata kwana, da mum ta ce ta je wajen mijinta, sai ta ce ai baya son ƙunshi ya ce sai ƙunshin ta goge, idan ba haka ba zai yi amai, shi ne yasa mum ɗin ta barta a part ɗin nasu ta kwana. A cikin tsakiyar parlourn ya shigo yana mai kara yin sallama, da mamaki daddyn Rimshar yake kallonsa, kasancewar shi ne babba kuma yasan halin Lion ɗin, izuwa yanzu ya fahimci wanene shi, ya fahimci ba wai son shi ne Lion ɗin baya yi ba, kawai shi yanayinsa ne a haka, amma yana tsananin sonsa, a duk cikin ƴan uwan gwaggo ma yafi son shi, hakan tasa ya ce "Saif lafiya kuwa?". Zubawa uncle ɗin nasa idanu na ƴan sakanni ya yi kafin ya ce "Uncle am looking for my wife". Haƙiƙa daddyn ya yi mamakin na jin cewa Rimsha yake nema, saboda ta ce masu wai shi ne ya ce ta tafi sai ƙunshinta ya goge zasu sake haɗuwa, to ya aka yi yanzu kuma yake nemanta? Kenan karya ta yi masu ne ko yaya?. Sexy voice ɗin Lion ɗin ne ya katse mashi tunanin da yake yi da cewa. "Uncle where's she? And what are thinking?". Nisawa daddyn ya yi kafin ya ɗan yi murmushi kaɗan, sannan ya ce mashi. "Am thinking about you and Rimsha, she's inside that bedroom". Kamar zai sake tambayar daddy tunaninsa shi da Rimsha kuma a kan me yake yi? Sai kuma ya fasa ya nufi bedroom ɗin kawai. Da kallo daddyn ya bishi har ya karisa shiga cikin bedroom ɗin. (Asamu wata fisabilillah ta koyawa TRIPLETS kunya 🤌 sam su basu da shi, bama iya TRIPLETS kawai ba, gabaɗaya familyn Dr William zaku taimaka ku koyawa kunya my readers 🤌 dan turawan nan sai a hankali, yanzu dai babu ruwansa ya shige cikin bedroom ɗin abinsa, dan ma dai dukkansu daga su har su daddyn Rimsha jirgi ɗaya ce ta kwaso su, akwai mix na jinin a jikinsu, shiyasa basu damuwa) Yana shiga cikin bedroom ɗin ita kuma ta fito daga wanka kenan, ɗaure take da towel a kirjinta, iya rabin santala santalan cinyoyinta towel ɗin ya tsaya mata, ta saki kyakkyawar gashin kan nan nata, sai ƙoƙarin goge gashin nata da ƙaramin kyakkyawar towel da yake a hannunta take yi. Sam bata ji shigowarsa ba, kuma bata lura da shi a bakin kofar bedroom ɗin ba, sai dai kuma kamshin perfume nasa da ya bulbule ko'ina a cikin ɗakin ne yasa ta fahimci lallai ya shigo ko kuma yana kusa da bedroom ɗin, ta ɗaura wannan ƙaramin towel ɗin a saman kanta ya yin da ta dukar da kai tana goge gashin nata, kasa ɗago kai ta yi ta kalli hanyar shigowa ko kuma ta karewa cikin bedroom ɗin kallo, saboda tana tsoron haɗa idanu da shi, tabbas tasan ya shigo ko yana kusa. Sak ta tsaya a tsakiyar ɗakin ta kasa iya cigaba da nufar gaban mirror da take nufin zuwa, ta kuma kasa iya cire wannan ɗan towel ɗin daga kanta ta ɗago ta kalle shi, tsoro ne duk ya kamata. Shi kuma yana tsaye ya harɗe hannayensa a saman Lion chest nasa yana kare mata kallo cike da sonta da kuma tsantsar kaunarta, sir Arvin ya yi gaskiya da ya ce mashi idan ya kalli ƙunshin nata a matsayin shi ta yi wa kwalliya zai ji abin ya burgesa, karo na farko a rayuwarsa da hakan ta faru, sai ya ga ƙunshin ya yi mata kyau sosai, bare ma ƴan yatsun hannun nan nata da suka ji jan ƙunshin suka yi jajir har wani maroon maroon suka yi, sai abin ya yi matuƙar tafiya da imaninsa. Ganin ta tsaya ta kasa gaba ta kasa baya, ga shi kuma tana fama da ciwon kafa tana aikin ɗingisata, sai ya ce bari ya rage mata wahalar tsayuwar nan da ta yi. A hankali ya tako zuwa in da take. Hannu ya kai ya cire ɗan towel ɗin daga kanta kafin ya ɗauketa cak. Sai a saman mirror chair ya sauketa. Hannunsa dukka biyu ya sanya yana ƙoƙarin tattaro mata gashin kan nata domin ya tara waje guda ta samu ta buɗe idanu su kalli juna. Sai dai ko da ya tara mata gashin nata, sai ta datse idanuwanta gam taki yarda ta buɗesu. "Meeshana". Ya ambaci sunanta kasa kasa cikin wata iriyar murya mai sanyin gaske. Har cikin ranta ta ji wannan zazzaƙar sexy voice ɗin nasa, hakan yasa ta saka mashi kuka idanu a rufe tana faɗin "Ni Yah Saif me ya kawoka gidanmu? Ni ka tafi bana son ganinka, me kazo yi?". Duk zakin sexy voice nasa da kuma kewarsa ne ya ruɗata ta ce ya tafi masu daga gida, wai gidansu, idan ka bibiya ma bata san ta faɗi hakan ba, so mugun wasa. Rage tsawonsa ya yi ta yadda ya ɗan kwanto da kansa a saman shoulder ɗinta, a kunne ya raɗa mata. "Kewarki ne ya kawoni gidanku rigimammiya kawai, kuma ba zan tafi ba sai tare da matata, ko ki bini mu tafi, ko kuma nima na kwana a nan, wai Meesha yanzu kin dai'na jin tausayi nane? Kin dai'na so nane?". Kai ta gyara mashi alamar yeah ta dai'na son shi. "Okey to buɗe idanunki ki kalli cikin nawa idanun ki gaya mani kin dai'na sona, idan kika yi hakan zan tafi". Kuka ta sake saka mashi tana faɗin "Ni wlh ba wani buɗe idon da zan yi, a haka ya isa, ni kawai ka tafi". Nisawa ya yi tare da manna mata sumbata a wuya, ga ruwan dake sauka daga gashin kanta yana jika mashi face nasa, kasa kasa kamar mai raɗa ya fara magana. "Meesha meyasa kike son ki wahalar dani ne? Kin san me nake ji kuwa? Kin san adadin son da nake yi maki kuwa?". Turo ɗan baki ta yi tana faɗin "Yah Saif baka sona, idan da kana sona ba zaka tafi ka barni ba, kuma baka kirani a waya ba, sannan kuma......." Bai bari ta karisa maganar ba ya kai hannunsa ɗaya ya rufe mata ɗan bakin nata, a kunne ya raɗa mata. "Wlh i really love you more than anything in my life my Meesha, kawai aiki ne ta sha gaban tunanina ta yadda bani da zaɓin da ya wuce na yi maki abin da nayi maki, please kada ki horani da fushinki a gareni, ba zan iya jurewa ba kin ji ko? Am so so sorry na rashin kiranki da ban yi ba". Juyowa gare shi ta yi tare da fara kai mashi dukan wasa a kirji tana faɗin. "Ni babu ruwana da kai, kawai ka tafi part naka, ni na dawo wajen daddy na kenan". Riko hannayen nata da take kai mashi dukan ya yi yana faɗin "Da gaske kin dawo wajen uncle?". Kai ta gyaɗa mashi alamar e da gaske tare da cewa. "Kuma ba zan sake zuwa in da kake ba, sannan daddyna abin da nake so shi yake so, shi ma zai ce ba zan bika ba". "Okey bari mu gani da ni da ke waye uncle ɗin yafi so". Ya kai karshen maganar tare da sake hannayen nata ya juya izuwa parlour. Still har lokacin daddyn nata yana zaune a saman table ɗin yana shan green tea mai zafi, mum ma ta fito cikin shigar kayan barci, bata san cewa Lion ɗin yana part ɗin nasu ba, shi kuma daddy ya manta bai sanar da ita ba, Allah ma yasa tana zaune a kusa da daddyn ne, iya wuyarta zuwa face nata zaka gani, da a tsaye take ne sai ta ji kunyar Lion ɗin sosai, shi dai kunsan ba dai ya ji kunyarta ba, sai dai ya barta da jin kunyar ita, to Allah ma yasa a zaune take suna hira da mijin nata ita ma, sai abin bai bata kunya sosai ba, amma dai bata so hakan ba sam sam, dan da ta gan shi ya fito daga bedroom ɗin da Rimshar take a cikima sai da gabanta ya faɗi. Daga ɗan nesa da su ta kusa da bedroom ɗin da Rimshar take ya tsaya. Kallon shi daddyn Rimshar ya yi kafin ya tambaye shi lafiya?. "Uncle Meesha ta ce ba zata bini ba, wai ta dawo wajenka kenan". Ya faɗa yana kallon daddyn a cikin ido. "Ta isa ta ce ba zata bika ba, tun wuri ta fito kafin nazo". Ya bashi amsa tare da miƙewa ya nufi in da yake. "Ina take nema?". Dama da gangan Lion ɗin ya yi mata hakan, da gangan ya haɗata da daddyn nata, da biyu ya yi hakan. Cikin bedroom ɗin suka koma a tare, tana zaune a wajen da Lion ɗin ya barta sai aikin kumbure kumburen kumatu take yi. "Rimsha yau kece kike cewa bazaki bi mijinki ba? Ke da nake yabo kullum ɗin? To tun wuri ki tashi ku tafi, da safe ma zamu haɗu da kene, me kika ce mana ɗazun? Ba kin ce shi ya ce baya son ganin lallen da yake hannunki ba, dan haka ki dawo nan da zama ba?". Ya yi maganar cikin harshen Hausa, dan kada Lion ɗin ya ji abin da za su ce. Kuka ta sakawa daddyn nata tana faɗin. "Daddy Allah Yah Saif ɗin nan shi ne ya ce baya sona, yanzu kuma saboda dare ya yi shi ne zai ce............." Kasa cigaba da maganar ta yi, saboda ta fahimci ta saki layi tun farko a maganar tata, wani irin azababben kunyar daddyn nata ne ma ya kamata, sam bata san ya aka yi ko ta yaya maganar nan ta fara fita daga bakinta ba, ya ilahi ya lillahi. Ganin hakan yasa daddyn ya ce "Tun wuri ki tashi ki bi mijinki, idan ba haka ba ranki zai ɓaci, idan ma shi ya ce baya sonki ɗazun yanzu ba shi ya zo da kansa ɗaukarki ba? To Allah ki yi maza ki wuce ki bishi kafin na sake dawowa na sameki". "Uncle please small small, kada kayi mata faɗa ta yi kuka ka ji?" Cewar Lion ɗin. Bakin daddyn ya saki yana ganin ikon Allah, suna neman su bashi kunya, wato kada ya yi mata faɗa sosai ta yi kuka, lallai ma Lion ya iya iyashege shi ma. Wucewa salin alum daddyn ya yi yana faɗin "To ki tashi ki bi mijinki tun wuri". Daga haka ya fice daga ɗakin abinsa, dan ta lura kunyar da bai taɓa jin irinsa ba Lion da Rimsha zasu saka shi ji a yau idan ya biye masu..........😂 Daddyn yana fita Lion ɗin ya dawo kusa da ita. Ƙoƙarin sauka daga saman chair ɗin ta yi, dan ta bar mashi wajen, ita a dole ya ɓata mata rai, ya kai karanta wajen daddy. "Ina kuma zaki je". Ya faɗa tare da rikota. A kule ta ce "Wajen mummyna zan je, tun da daddy ya dai'na sona, kuma ni da kai baram baram, ka sake ni, ni ba zan bika ba, mun ɓata sosai, kowa ya yi hanyarsa". Saketa ya yi yana faɗin "Ita ma kanta mum ɗin a yanzu ni take so ba ke ba, idan kika je ma zata ce ki dawo waje nane, yanzu da uncle da ita duk sun fi sona a kanki, dan haka kizo kawai mu tafi, baki da sauran mafita". Ya kai karshen maganar yana harɗe hannayensa a saman Lion chest nasa. A tsananin kule ta ce "Amma ai ina da gwaggo, kuma ita ce maganinka daga kai harsu daddyn, wlh wajenta zan tafi yanzu, ba zan bika ba". Ta yi maganar on a serious note, babu wasa a voice nata, shi wasa yake yi mata, ita kuma bai san ta zo har wuya ba, haushi take ji. Jin ta ambaci mommansa, kuma yasan tsab momman nan nasa zata goya mata baya, sannan yasan tabbas idan ta yanke hukunci ko daddyn Rimshar bai isa ya ce gwaggo kiyi hakuri ba, yasan tsab zata hana shi Rimshar a daren nan, dan ita gwaggo ta iya kwatawa kowa ƴancinsa, bare kuma Rimsha da Jehan, ai bazata taɓa bari a ɓata masu rai ba, jin ta ambaci mai gayya mai aiki yasa ya yi saurin rikota yana faɗin. "Is okey my Meesha, let's go and eat, am feeling too much of hungry, since morning ban ci komai ba, please zo ki bawa mijinki abinci a baki". Kin kula shi ta yi, ta sauko daga saman chair ɗin da nufin ta tafi wajen gwaggon abinta. Ta baya ya ɗauketa cak ya nufi waje da ita, a lokacin dad da mum sun shige cikin bedroom nasu, saboda kada Lion ɗin ya fito ya sake samunsu a wajen ne yasa mum ta ce su shiga ciki, ita kunyar Lion take ji baiwar Allah, bata san wahalar da kanta kawai take yi ba, shi Lion sam bai san kunya ba. Bai direta a ko'ina ba sai a saman katafaren bed nasa, sir Arvin baya ɗakin, dan tun da ya fita ya ce bari ya je ya ɗaukota, tun daga nan sir Arvin ɗin shi ma ya fice daga bedroom ɗin zuwa nasa, dan kada Lion ɗin ya dawo da Rimshar ya samesa. Kuka ta fara yi mashi tana ƙoƙarin sauka daga saman bed ɗin nasa. Hayewa ya yi tare da rungumota sosai a jikinsa, kasa kasa ya ce "My Meesha, please kada ki kara wahalar da mijinki kin ji?". Tirje mashi ta fara ƙoƙarin yi taki ta saurare shi, ganin hakan yasa ya haɗe hannayenta dukka biyu ya rike da hannunsa ɗaya, sannan ya matseta sosai a jikinsa bayan ya kwanta ya yi mata rumfa da faffaɗar kirjinsa kenan. Sai ƙoƙarin tirje mashi take yi. Matso da face nasa dab da tata ya yi, cikin sauri ta runtse idanuwanta gam. Haɗe fuskokinsu waje guda ya yi, kasa kasa ya ce "Please ki nutsu". Ya yi maganar tare da fito da harshensa, a hankali ya fara lasar lips nata kafin daga bisani ya fara kissing nata da kyau da kyau. Sai da ya ji ta sauke ajiyar zuciya, sannan ya zame ɗan bakinsa daga nata ya kuma saki hannayen nata. Tsit ta nutsun mashi a saman bed ɗin, ta kasa wani motsin kirki, dan shi salon kiss nasa na daban ne, duk in ya yi mata sai ya kashe mata gaɓɓan jiki, duk sai ta ji wani irin kasala ta musamman ta lulluɓeta. "My Meesha do you know how much I love you? Please ki dai'na wahalar dani kin ji ko my wife? Stay with me, you're my power". Ya yi maganar ne cikin wata iriyar murya mai matuƙar ɗaukar hankali. "Noorish sanyi nake ji sosai". Ta faɗa kamar zata yi mashi kuka, dan duk da ɗakin nasa da akwai ɗumi, ita sanyi sosai take ji, saboda bata saba da sanyin kasar tasu ba, ga shi kuma daga ita sai towel ya ɗaukota. Duv na bed ɗin ya jawo ya rufesu, sannan ya matso da lips nasa kusa da kunnenta, calmly ya furta. "Kin tafewa mijinki?". Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e ta yafe mashi. Wani irin nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da matseta a jikinsa yana jin tsananin farinciki. A ɓangaren Aseef kuwa, zazzaɓi mai zafi ne ta lulluɓe shi, yana kwance a cikin bedroom nasa, ya ƙudundune a cikin tapkekiyar bargonsa, can gefe ita ma Akila gata a ƙudundune a cikin bargo tana kerman sanyi. Can kuma ga gwaggo tana yi wa Jehan aiki tana hawaye, shi kuma Dr William ya sanya Areef yin barcin dole. A gefe guda kuma Tga ya kasa yin barci, dan bai sanya Aafia a idanuwansa ba, while shi ma Mark sai yi wa Anaya magiya yake yi a kan ta barshi ya yi dis virgin nata, amma taki yarda, saboda ya taɓa gwada yi mata hakan, bai shigeta ba ta ji azaba ta rinƙa yi mashi ihun da tasa dole ya hakura ya kyaleta, so sai magiya yake yi mata a kan ta yi hakuri ta bari ya yi, ya yi mata alkawarin ba zai yi mata da zafi ba, sam taki yarda, sai fama da wahalar sha'awarta yake yi bawan Allah. A gefe guda kuma Adiva da Maryam an miƙasu ga babban hospital na fake Dr William tare da sa hannun Lion, sai da ya taimaka ya sa baki aka karɓesu, sai bincike likitoci suke yi a kansu, har yanzu dai result na abin da yake damunsu bai fito ba, ko ɗaya daga cikinsu kuma babu wadda ta farfaɗo daga doguwar sumar da suka yi. A gefen sir Arvin kuma, Pinky ya je ya ɗauko suka haye bed nasa suka kwanta suna zuba barci, shi kuwa Handsome yana tare da Alex, a yanzu gidan Lion ya zama GIDAN FARINCIKI. Sosai brr Naurat da Dr Salman suke jin daɗin rayuwarsu, suna farinciki sosai da sosai. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* Date: 29/5/2024 E42 Sosai brr Naurat da Dr Salman suke jin daɗin rayuwarsu, suna farinciki sosai da sosai. Sai dai kuma gwaggon ta ce a dawo da su kasa, hawa na saman nan sun yi nisa da su, shi dai Lion in dai Gwaggo ce ta yanke hukunci to baya cewa komai, ko a jikinsa, haka su brr Naurat suka dawo kasa. Washegari da safe da misalin ƙarfe 7, Lion yana toilet yana wanka, akwai taron da zai je a office ɗin Ministar's, so yana da buƙatar ya shirya da wuri, baya son African time a lamuransa. Kwance Rimsha take a saman bed ɗin nasa, idanuwanta biyu bata yi barci ba, sai dai kuma ta lumshesu kamar mai yin barci, wani azababben ciwon mara ne yake damunta da har yasa ta kasa waro idanun nata waje. Sai juyi a hankali a saman bed ɗin take yi, duk jikinta a mace, domin Lion kafin ya shiga wanka sai da ya tumurmusheta son ransa, ya yi wasa da ita sosai, duk ya kashe mata jiki, sannan ya wuce toilet ya barta, ya ce tazo su je su yi wanka a tare, amma taki yarda ta bishi, dan ko a wasan da ya yi da ita ɗin ma taki yarda ta barshi ya je kasa, iya tula tulanta kawai ya murza son ransa. Ɗaure da towel a ƙugunsa ya fito, kasancewar idanuwanta a lumshe ne yasa bata ga ainahin kyakkyawar surar jikinsa ba, bata taɓa ganinsa babu riga ba!. Lotions nasa masu tsananin tsada ya zo ya shafa, a hanzarce ya busar da kyakkyawar gashin kansa, tana jin duk abin da yake yi, amma ta kasa buɗe idanuwa ta kalle shi, saboda ji take yi kamar idan ta buɗe idanu fa ciwon zai karu ne ma. Sai da ya kammala dik abinda zai yi, sannan ya nufi cikin katafaren dressing room nasa na alfarma. Cikin wasu shegun tsadaddun kaya ya shirya, wandon jeans ce fara tas tare da polo shirt milk color, kayane masu bala'in tsada, ba ƙaramin kyau ya yi wa kayan ba, ya fita iya fita, kowa da zai je taron suit zai sanya, amma ban da shi, saboda shi already kun sani ba mutun ne da za'a cewa ga abin da zai yi kuma ya yi ɗin ba, sannan kuma shi a ko'ina na daban yake, baya fitowa iri guda da kowa, dole sai ya fita daban, hakan yasa ya yi dressing nasa son ransa. Ya yi wani irin fitinannen kyau na wuce misali, sai tashin daddaɗar kamshi yake yi. Wajen wani katafaren drawer sabo da yake a cikin dressing room ɗin ya nufa, before babu wannan drawer sam, a cikin week ɗin nan aka sanyata. Ko me a cikinta?. Hannu ya kai dai'dai saitin marfin drawer, yana kai hannu ta buɗe kanta da kanta. Ya ilahi, kayane dankare makare a ciki, kaya ne da suka wuce baki ya misilta maku su, da yake drawer tana da girman cin bango guda, sai ya zamana komai da nasa part ɗin, to wannan part ɗin da Lion ya buɗe shake tab yake da always da kuma pants, ma'ana dai kayan ciki na period na mata ne, tun ranar da Rimsha ta fara period time da suke tafiya ƙasar Russia, tun a ranar ya rike date ɗin, kasancewar zasu dawo U.s kuma ya ga date ɗin period ɗin nata ya kusa ne yasa a kayan da ya yi mata oder har da always mai uban yawa kamar wadda zai buɗe shagon sayar da su, su kaɗai sunci side ɗaya na drawer, dan ma dai dama ba kayan fita waje ya saya mata ba, iya su kayan barci ne da nasu shan iska, sai su pant and bra, sune ya saya mata, Josephine yasa ta saya mashi kamar yadda ta saya mashi wancan time ɗin, to wannan time ɗin ma ita ya aika ta sayo mashi, sai dai bai je gidan nata da kansa ba, sako ya tura mata a wayarta, daga karshe ya sanar da ita su gwaggo zasu zo, so zai turo azo a ɗaukota, da okey ta bishi, sannan ta je ta saya mashi duk abin da ya dace mata masu bala'in kyau da tsananin tsada, ya tura aka ɗauko mashi zuwa gidan nasa. Katon ledar always guda ɗaya ya ciro, sannan ya ɗauko kwalin kyakkyawan pant kwali ɗaya. A saman mirrorsa da yake a cikin dressing room ɗin ya ɗaura always da pant ɗin, sannan ya yage ladar ya ciro always ɗaya ya ajiye a gefe, sai ya buɗe kwalin pant ɗin shi ma, irin wanda yake zuwa guda uku a kwali ɗayar nan ne. Ɗaya ya ciro mata tare da mayar da sauran ya mai da su cikin drawer, ya zo ya ɗauki waɗan da ya fitar ɗin ya fito daga room ɗin izuwa cikin bedroom nasa. Har lokacin tana kwance idanu a lumshe, tana jin azaban ciwon mara, dama idan baku manta ba nata period ɗin da azababben ciwon ciki yake zuwa mata. Kusa da ita ya zauna tare da ɗan kai hannu ya yi kasa da bargon da take lulluɓe da shi ɗin. Saman kanta ya ɗaura hannunsa tare da shafawa a hankali yana ambatar sunanta. Tamkar jira take yi ayi mata magana, sai kawai ta sa mashi kuka, ta kuma kasa iya buɗe idanuwanta. Ajiye always and pant ɗin ya yi a gefe guda, hannayensa dukka biyu ya kai ya ɗagota, a saman Lion chest nasa ya mannata yana shafa bayanta a hankali. Ƙanƙameshi ta yi, cikin azaban ciwon take faɗin "Noorish cikina ne yake yi mani ciwo". Tana magana wasu zafafan hawayen suna bin kuncinta da gudu kamar ruwan famfo. Ɗan raba jikinsu ya yi tare da sanya hannunsa a saman shafaffen cikin nata. "Sorry my Meesha, yanzu zai dai'na yi maki ciwon In Sha Allah, nan da ƴan mintuna kaɗan dai period ɗin naki zai zo ki huta, yanzu daure ki tashi ki shirya mashi kin ji?". Kara ƙanƙanme shi ta yi tana kara sautin kukan nata. Rarrashinta ya rinƙa yi tare da lallaɓata har ta hakura ta mike ta shirya kamar yadda ya buƙata, sai da ta miƙe ɗin ne kuma da ta buɗe idanuwa ta kalli irin kyan da ya yi, ya yi shirin fita, sai me? Ai tuni kishinta ya motsa, ji ta yi Allah ba zata iya barinsa ya fita da irin wannan azababben kyan nasa ba, saboda tasan dole sai ya gwara kan ƴan mata, dole za'a tsare mata shi da kallo, zai haɗa accident ba kaɗan ba. Dan haka sai ta sake narkewa a jikin nasa tana mai sake saka mashi kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Nan take ya hau rarrashinta tare da tambayarta meyafaru kuma take sake yin kuka?. Kin bashi amsa ta yi, sai ma kara shigewa jikinsa da ta yi tana mai kara marairaice murya ta yadda kukan nata ma zai taɓa mashi zuciya sosai da sosai. Aikuwa dai ta yi sa'a, dan kuwa wannan kuka ba ƙaramin ɗaga mashi hankali ya yi ba, dik sai ya rasa me yake yi mashi daɗi, ga shi taki yi mashi magana bare ya ji menene yanzu kuma yake damunta. Rarrashinta ya rinƙa yi, dan ba zai iya jurar kukar ba, da kyar ya samu ta buɗe baki cikin kuka ta ce "Ni Noorish bana so ne ka fita, ka zauna da ni tun da bani da lafiya". Shiru ya ɗan yi yana tunanin meeting ɗin da zai je ɗin, tana da mahimmanci, amma kuma hannun Meesharsa guda ɗaya kawai ta fi mashi komai nasu mahimmanci bare ita da kanta. Ganin ya yi shiru ne yasa ta sake cigaba da yin kukanta, shi da yake bai gane tana kishi dan ya yi kyau over bane, saboda shi bai san kalar kishin matan Nigeria ba, na turawan ma bai sani ba bare bakaken fata, kun san shi ba alaƙa da nata take yi ba bare ya sani, sai kawai ya kara rumgumeta a jikinsa yana faɗin. "Do you agree na yi attending meeting ɗin through online?". Tsit ta natsu a jikinsa jin abin da ya ce, kasa kasa ta ce "Amma a wajen meeting ɗin babu mata?". Sai yanzu ya gane dalilin hana shi fita da take son yi, sosai ya ji daɗin hakan, dan su maza a duniya suna bala'in son suga an damu da su har ana nuna kishi a kansu, ko basu fito sun nuna jin daɗinsu a fili ba, amma ba makawa suna jin daɗi over, idan ma baki nuna kishi a kansu wasu har kasa hakura suke yi sai sun tambayeki kekam baki da zuciya ne? Dan kawai baki nuna kishi a kansu ne zasu ce maki baki da zuciya, so wannan ɗabi'a ce ta maza, koda mata biyu suke da su a gida, zasu so ayi zaman lafiya a tsakanin matan, amma kuma suna bala'in son suga ko wacce tana nuna masu tana kishi sosai a kansu, a jininsu yake, dan haka idan ma baki nuna mashi kina kishinsa, tun wuri gara ki fara, zaki ga har wani murmushi yake yi idan kika fito da kishin naki fili ya gani, dan yaji daɗin andamu da shi, maza mutanenmu mu kuma sai Allah.........🤌😂 "Meesha sarkin rigima, to idan ma akwai mata a wajen ni ina ruwana da su?". Ya yi maganar yana kallon face nata, kun san idan mace tana period tana kara wani sihirtatcen kyau, jikinta har wani glowing zai rinƙa yi, to haƙiƙa ta tafi da imaninsa sosai ta yadda ya kafeta da idanu babu ko kyaftawa. Turo baki ta yi kamar zata sa kuka. "Noorish ni gaskiya in dai da akwai mata a wajen bazaka je ba, ko ta online ɗin nema bana so". A shagwaɓe sosai ta yi maganar. Matso da ɗan bakinsa saitin kunnenta ya yi, kasa kasa ya raɗa mata."To ai ke kaɗai kin ishe ni, ni bana ma haɗa hanya da mace, because dukka ina ɗaukarsu a abu guda, keda momma ce kawai kuke daban". "Ni gaskiya duk da haka dai mu zauna tare a nan, ai idan kai baka kulasu su zasu kula mani kai, kaga kyau ɗin da kayi kuwa? Shi ne kuma zaka fita? Tab kana son ka saka mata su yi ta suma a kan hanya ko? Wata ma mayya mai kafar shamuwa nasan sai ta yi maka magana koda ba zaka kulata ba". Ta kai karshen maganar tare da sanya mashi wani irin kuka mai kama da na shagwaɓa, sai dai kuma na soyayya ce. Shiru ya zuba mata idanu har ta gama zuba surutun nata tana aikin turo baki. Shi dai Lion kamar kullum, har yau murmushi sam bata ga gurbin zama a face nasa ba, Rimsha ta yi juyin duniyar nan dukka a kan ya yi mata murmushi ko da sau ɗaya ne a rayuwarsa, amma ya ce sam shi bai iya ba, bai san ya ake yi ba, kullum fuska a ɗaure tamau, bata da zaɓin da ta wuce dole ta hakura ta rabu da shi, dan a yanzu ta fahimci rashin murmushin nan haka yake, ba zai taɓa yi ba, gara kawai ta kyale shi har Allah ya kaita ranar da zata ga murmushinsa koda sau ɗaya ne a rayuwarta. "See your beautiful mouth like mace zata yi mani magana, aww ke yanzu Meesha kina tunanin yadda nake dake a nan haka nake magana da kowa a waje ne?". Gyaɗa mashi kai ta yi alamar e. Nisawa ya yi kafin ya ɗaura da cewa "Ai in dai ni ne yanzu ki fita ki zuba makudan kuɗaɗe ki ce namiji ma ya tinkare ni ya yi mani magana zaki bashi kuɗin, zaki ga ikon Allah, babu wanda zai kulaki ko me zaki basu, namiji ma bare kuma mace, ni ai kowa tsorona yake ji a kasar nan, i don't know the reason why, but wani lokaci zaki gani idan muka fita, yanzu haka idan kika tara mutane ɗari ba lallai biyar daga cikinsu sun san kalar voice nawa ba, yanzu dai jeki shirya kizo mu yi attending meeting ɗin a tare da ke, ba shikenan ba?". Kai ta gyaɗa mashi tare da shigewa jikinsa tana murmushi, ita a dole ta ji kunya, ga wani guntun hawaye na iyashege a face nata. Miƙewa da ita ya yi zuwa toilet, a tsakiyar toilet ɗin ya sauketa, sannan ya juya izuwa waje yana mai gaya mata idan ta gama wanka da akwai kayanta a drawer a cikin dressing room nasa, ta shirya sai ta zo ta same shi a ɗakin computers nasu, ya gama mata kwatance ya fito abinsa. Ya ilahi ya lillahi, ai sake baki ta yi tana kallon toilet ɗin, duniya ne guda, ku dai my readers kun san yadda katafaren Daular Lion take, su Rimsha ce basu sani ba, ai sai tazama ƴar kauye, tun da take a rayuwarta ma bata taɓa ganin jacuzzi irin na Lion ba, ga wasu kyawawan kwan yantarki masu bada hasken blue light a ciki masu matuƙar ɗaukar hankali, duk sai ta rasa ina ma zata bi, girman toilet ɗin kawai ya kai girman ɗakuna da koma na gidan wani, wajen mayukan wanke kansa ma kawai tamkar shop na sai da mayuka mai girman gaske, show glass na jera mayukan goge bakinsa kawai abin kallo ne, bare azo kan sauran abubuwa, duk sai Rimsha ta rasa ma wanne yafi haɗuwa, toilet ɗin ko bedroom ɗin. (Ni kuwa nace dan ma baki shiga dressing room bane, ai da sai kin wuni kina kalle kalle.) Tafi 30 mins tana kalle kalle kafin ta nufi wajen jacuzzin nasa, sam bata san taya zata haɗa ruwan wankar ba, saboda kusan komai na cikin toilet ɗin da remote da kuma madannai suke amfani, show glass ɗin nan ma da na'ura suke amfani, shi kuma Lion shap na mance da bazata iya amfani da abubuwansa ba har sai idan shi ya koya mata, ya mance ne ya sauketa ya fice kawai. Almost 20 mins tana tsaye a wajen jacuzzin ta rasa ta ina zata taɓa ruwan zafi dana sanyi su zubo. Kamar daga sama ta ji kamshin perfume nasa ya daki kofofin hancinta. Da sauri ta kai kallonta izuwa bakin kofar shegowa. Yana tsaye ya goya hannu a Lion chest nasa. Turo mashi ɗan bakin nan ta yi tare da wurga mashi harara da waɗan nan dara daran fararen Sleeping eyes ɗin nata. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da karisowa izuwa cikin toilet ɗin, dama ya jita shiru ne yasa ya tuna cewa da wuya idan zata iya amfani da toilet ɗin nasa, shi ne ya zo dubata, ashe kuwa haka ɗin ne. Sumbata ya manna mata a ɗan bakin da tare turo mashi ɗin kafin ya haɗa mata ruwan, zuba mashi idanuwa ta yi tana kallon abubuwan da yake dannawa a jikin remove ɗin ruwan yana fitowa, sai da ya zuba na zafi mai ɗan yawa kafin ya dakata ya zuba mata na sanyi. Ba tare da ya taɓa ruwan ya ji ta yi dai'dai ne ko bata yi ba ya ajiye remove ɗin a mazauninsa, saboda already haka yake haɗa nasa ruwan kullum, so ita ma a haka zata shiga koda ya yi mata zafi. Wajen brush ya nufa, yana kai hannunsa saitin wajen kofar glass ɗin ta buɗu mashi, brush ne dayawa tamkar a shagon sai da su, dik masu kyau ne da tsada sosai, amma sai da ya tsaya ya zaɓa mata karshen haɗuwa a cikinsu, sannan ya fito mata da mayukan goge baki. Ita dai tana tsaye tana kallo ikon god, ta zama ƴar kauye putuk, wannan abubuwa haka ina zata iya? Komai an wani zuba mashi matakan tsaro an killace, to ina ga kuma ita da take matarsa?.......... Dole ki tambaya kam Rimsha, komai na amfani a cikin toilet ma kawai a killace suke da tsari har haka ina ga ke kuma matarsa? Ai zaman ɗaki ne ya kamaki, dan Lion dai ba zai bari kina fita waje ba, saboda tsananin kishi. Ta shagala da kalle kalle sai ji ta yi ya hura mata iskar bakinsa a face nata. Kara turo baki ta yi kamar zata yi mashi kuka. "Remain 30 mins mu fara meeting, ki yi sauri". Ya faɗa tare da juyawa ya fice abinsa. Da kallo mai cike da tsantsar kaunarsa ta bishi da shi, har sai da ya kurewa ganinta, sannan ne ta juya ta nufi cikin Jacuzzin bayan ta cire kayan jikinta dikka. Sosai ruwan ya yi mata zafi, amma bata da zaɓin da ya wuce ta shiga ciki, dan yana jiranta ne. Bata ɓata lokacin wajen yin wankar ba, ta fito ɗaure da towel a kirjinta, dressing room ɗin nasa ta shiga, nan fa sabon kallo ya ɓalle, nan taga duniya, tamkar super market na sayar da kaya kawai, glass na jera watch's nasa ma kawai ya isa mutun ya wuni yana kallo. Dik da tasan yana jiranta, hakan bai hanata tsayawa ta bawa idanuwanta abinci ba, sosai ta rinƙa bin duk wasu glass tana dubawa, harta na takalmarsa da su nasu glasa ɗin ma kamar fridge aka yi su, dik sai da ta leƙa. Almost 20 mins tana a ciki tana kalle kalle tare da kauyanci kafin ta nufi wajen drawer da ya ce mata kayanta suna a ciki. Cikin sauri ta fara duba wanda zata sanya a jikinta, duk babu kayan kirki a ciki, kaya ne irin nasu na turawa, to dama shi da bai ma san ya dressing na hausawa yake ba ta ina zai samo maki irin namu? Ai dole ne kawai ku koma amfani da irin nasu, ɗan gara ma Areef da ya nuna sha'awarsa a kan Atamfa idan Jehan ta sanya, so shi zai iya sanyawa ɗaya daga cikin family ta yi mashi order Atamfa a yiwa Jehan ɗin ɗinki a can a sako a jirgi, amma shi Lion da Aseef da basu ma san me atamfar ba ta ina matansu zasu gansu har ma su sanya? Ai Akila da Rimsha sun sallami su Atamfa, sai dai idan wajen Jehan zasu rinƙa zuwa suna kwasa. Wasu ƴan kananan kwali ta gani a cikin drawer, guda ɗaya ta ɗauko ta fitar, wani irin shegiyar doguwar riga ce a ciki, ba irin dogayen rigunar da kuka sani bace, a'a wannan tsarinta daban take, tana da tsagu daga cinya har kasa ta gefe guda, ga cof na breast part a jikinta, bata da hannu sam sam rigar, sai dai tana da bala'in kyau na wuce tunanin mai tunani, ta tsaru ga fitinar tsada. Ɗaukar shi ta yi tare da ɗauko wani always and pant ɗin ta fito izuwa cikin ɗakin, da sauri sauri ta shirya cikin kayan. Tamkar dan halittar jikinta aka yi kayan, ta fita sosai, sai kuma zanen sunansa da yake a saman tudun tula tulanta ya bayyana, saboda rigar bata da hannu, cof na breast part ɗin nata ma bashi da girmar da zai rufe har sunan nasa, sai zanen ta fito ɓaro ɓaro sosai. Ta haɗu karshen haɗuwa, ga wani irin shegen high heels da ta zuba a ƴan kyawawan kafafun nan nata, tamkar wadda zata tafi wajen dinner party, gyara gashin kanta da kyau da kyau ta yi, sannan ta bul bula perfume nasa a jikinta, wlh baki ya yi kaɗan ya zayyana irin kyan da ta yi, ga shi launin kalar rigar pink color, abin sai ya yi mugun haɗuwa. Da kyar take iya tafiya, saboda high heels ɗin, ga kuma tiles mai tsantsi, sannan ga kafarta dama yana ciwo. A haka ta fito wajen da kyar tana jan kafafu, ta zuba gashin nan nata a baya kamar wata indiyana. Kai tsaye in da ya kwatanta mata ta nufa, da yake ta hanyar da ya ce tabi ba hanyar kowa bane face nasa shi kaɗai, sai ya zamana bata ci karo da kowa na gidan ba har ta isa ɗakin. Yana zaune a saman wata shegiyar haɗaɗɗiyar sofa mai bala'in laushi, sai aikin latsa wayarsa yake yi. Jin sautin karar takalmarta a tiles ɗin ne yasa shi ya ɗago da kallonsa izuwa hanyar shigowa. Ai bai san time ɗin da ya kawar da wayar tasa daga saitin face nasa dan ya sami damar kallonta da kyau da kyau ba, ta haɗu iya haɗuwa, nan take ya ji wani irin azababben sha'awarta ta kara motsa mashi, dama tun daren jiya yake fama da hakan, dannewa kawai ya yi bai taɓata ba, saboda tsaro, amma yanzu ta sake taso mashi da sabon tsumi. Kusa da shi ta kariso ta zauna tana wani yauki da turo ɗan baki. Tun da ta shigo idanuwansa yake a saman tudun tula tulanta, zanen sunan nan nasa kawai yake kallo, abin yana kayatar da shi a yanzu, tsareta da idanuwa ya yi bai iya ce da ita ko uppan ba. "Noorish kayan sun yi mani kyau?". Zazzaƙar muryarta ne ta katse mashi tunani. Doguwar numfashi ya ja tare da saukewa a hankali, hannu kawai ya kai ya jawota jikinsa ba tare da ya yi magana ba, har wani irin zir zir yake jin Heronsa tana yi mashi, saboda tsananin sha'awarta da yake ji. "Noorish baka gaya mani na yi kyau ko ban yi ba?". Ta faɗa a shagwaɓe sosai. Haɓarta ya ɗago tare da haɗe fuskokinsu waje guda. "Kullum ke mai kyau ce, kuma a haka kike, amma na yau the kyau is too much for me, kin jefani a cikin wahala". Tongue ɗinta ta fitar ta ɗan lashi lips nasa, tana murmushi bata ce komai ba. Ya ilahi, ji ya yi kamar ya tashi ya cireta tsab ya shiga kayarsa, sai dai kuma ina tana period, ba shi da zaɓin da ya wuce ya hakura kawai. Sun ɗauki almost 10 mins a haka kafin nan ya saketa tare da bata wani kwali karami. Karɓa ta yi ta buɗe, ƙaramin hijabi mai matuƙar kyau ne a ciki, sanyawa ta yi a jikinta, a iya dai'dai flat tummynta ya tsaya, dama yasan kalar kayayyakin da suke a cikin drawer tata, shi ne yasa ma ya tanada mata hijabi. Hannunta ya riko suka nufi saman wasu haɗaɗɗun chair dake a gaban tables na desktop computers ɗin, ya zauna a saman chair ɗaya ita ma ta zauna a saman ɗaya, sannan ya kunna computer ya yi setting nata. A lokacin duk waɗan da za'a yi meeting ɗin da su sun hallara saura shi kaɗai suke jira, dama already tun da Rimsha ta ce ita bata so ya je, sai ya sanar masu da zai yi attending meeting ɗin amma ta online, dan haka su shirya, hakan yasa suka san da zancen ta yadda zai yi attending ɗin, sai suka shirya nasu computer kawai suna jiransa. Gabaɗaya jiga jigan ƴan siyasar da suke a cikin wannan katafaren office ɗin babu wanda bai sha ruwan mamaki ya kuma girgiza da ganin Lion a tare da mace ba, duk da wasu daga cikinsu sun gan shi a airport lokacin da ya ɗauketa, basu ɗauka cewa yana tare da ita har a yanzu ba, duk sai suka tsareta da waɗan nan idanuwansu na turawa masu kama da glass ɗin, sai kallonta suke yi, hakan ba ƙaramin ɓata mashi rai ya yi ba, kun san shi da ɗan banzan kishi, duk da cewa dukka waɗan da suke cikin office ɗin sun haura sheƙaru hamsin, ba yara bane, shi ne ma kawai matashi mai jini a jika a cikinsu, amma kishi yasa ya daka masu wata uwar tsawa, wadda ya sanyasu wata uwar firgita, ba su kaɗai suka firgita ba harda ita kanta Rimshar. Sarai yasan sun haife shi, wasu daga cikinsu ma sun yi jika da shi, amma hakan bai hana ya daka masu tsawar ba!. Babu wanda bai razana na jin tsawar tasa ba a cikinsu, cike da izza da nuna isa ya tambayesu meeting suka zo yi ne ko kuma kallon matarsa?. Wani irin mamaki ne ya kama Rimshar na ganin yadda waɗan nan jiga jigan ƙusoshin gwamnati kuma tattijawa suke girmama shi, kuma suke tsoronsa, bugu da kari ta ga ba yadda yake magana da ita ko TRIPLETS nasa haka yake magana da su ba, a nan yana magana ne da kaifi ɗaya da kuma tsantsar madarar isa da izza, magana ɗaya ba sake maimaitawa!!. E yanzu kam ta yarda ita kaɗai Lion ya canzawa, ita kaɗai yake yi wa magana cikin sanyi da tausasawa, a waje shi ɗin zaki ne mai firgita manya da kananan halittu da gaske!!. Kusan gabaɗaya waɗan da suke a cikin office ɗin sai da suka yi kasa da kansu alamar suna bashi hakuri, saboda duk da yake yaro a cikinsu, shi ne shugaba a samansu, shi ne president nasu nan gaba kaɗan In Sha Allah, so basu da zaɓin da ya wuce su bashi hakuri tare da girmamawa. Kara ɗaure fuska tamau kamar hadari ya yi tare da ce masu shi ya fasa attending na meeting ɗin ma, idan akwai wani abin da suka tattauna very important suna iya tura mashi ta massage's, zai duba ya gani idan ta yi mashi. Yana kai karshen maganar bai saurari amsarsu ba ya kashe computer yana wani huci kamar wani zaki, sun ɓata mashi rai na irin kallon da suka tsare Rimsha da shi Areef and sir Arvin ne suka shigo cikin computer room ɗin, bakin Areef ɗauke da sallama. Ganin Lion a tare da Rimsha yasa Areef ɗin ɗan yin murmushi kaɗan, duk da yana cikin matsananciyar damuwa na halin da Jehan take a ciki, hakan bai hana ya ɗan yi murmushin ba, shi ma sir Arvin duk da dama bai san wacece Rimshar ba, bai san face nata ba, sunanta kawai yake ji, ganin ɗan uwan nasa a tare da ita yasa ya ɗan yi murmushi yana faɗin "Kun haɗu kenan?". Wani kallo Lion ɗin ya jefa masu, dan shi ransa a ɓace take basu sani ba, ya yi nadamar meyasa ma bai sanyata ta sa face mask ba da zasu yi attending na meeting ɗin, kawai sun tashi sun kalle mashi face ɗin mata a banza, da wasu shegun idanuwansu kamar ball. "Saif kazo ka duba jikin Aseef fa baya jin daɗi". Cewar sir Arvin. Ɗan zaro idanu Lion ɗin ya yi, no wonder mana yake jinsa duk sai a hankali, ashe da biyu, dole ya ji jikinsa tana yi mashi babu daɗi. "What's wrong with him?". Ya faɗa yana kallonsu. Hannu Areef ya kyastawa Rimshar da ta tsare Lion ɗin da kallo a saman face nata yana faɗin "Zazzaɓi ne yake damunsa, ke kuma Our Queen mu fa ba ɗaukar Lion muka zo yi ba, kin wani tsare shi da idanu kamar mun ce zamu gudun maki da shi". Turo baki ta yi. "Kai Yah Areef ni ba shi nake kallo ba". Ta faɗa kamar zata yi kuka. "To kai Areef ina ruwanka da ita? Kafa cika sa ido, ai gara ta tsare shi da idanu mana, ba nata bane shi ɗin? Mallakinta ne fa, kin ji yi ta kallon abinki, naki ne ke kaɗai". Cewar sir Arvin. "Good morning". Ta faɗa tana satar kallon sir Arvin ɗin, tana son kallon shi kai tsaye, saboda ta kalli mai kama da Noorish nata, amma tana jin kunyar su haɗa idanu. Matsowa kusa da ita ya yi ya ɗan rungumota kaɗan yana faɗin." Morning my sister how was your night?". Kallon Lion Areef ya yi, dan yasan ba zasu shirya da sir Arvin ba, duk da cewa al'adarsu ce rungume mutun idan suna gaisawa, ko kuma su bashi hannu, to wlh shi dai Lion ya yaye wannan al'adar, matarsa da shi kaɗai zata haɗa hannu, sannan shi kaɗai zai rungumi kayarsa, sir Arvin bawan Allah shi bai sani bane, bai san kishin ɗan uwan nasa har ya kai haka ba, da ya sani shi ma ba zai taɓata ba. Lion ɗin kuwa dama can ransa a ɓace na kallonta da waƴan can mutane suka yi, ga kuma su Areef ɗin sun gaya mashi Aseef bashi da lafiya, yanzu kuma sir Arvin ya ɗan rungumo Rimsha, me kuke tunani zai faru? Sai mun haɗe gobe idan mai dikka ya kaimu.🥱 (Dole goben nan na saka Maltinata a cikin fridge ta yi sanyi over, saboda naji daɗin kallon chaskalensu ina korawa🤌😂) PRINCESS FATEEMA taku ta amana ❤️🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* Date: 1/6/2024 E43 Hannu ya kai ya ja gashin sir Arvin ɗin da karfi ba tare da ya yi magana ba. Wash sir Arvin ɗin ya furta tare da sake Rimshar yana faɗin. "Menayi maka kuma?". Areef ne ya amsa da cewa "Ka taɓa nashi one in million nasa mana, kai baka san ba'a taɓata ba ko?". Ɗan zaro idanuwansa waje ya yi, abin mamaki ma ya bashi, sabida shi bai ɗauki hakan kamar wani abin azo a gani ba, kunga na farko shi bai musulta ba, kuma shi bai taɓa zama cikin bakaken fata ƴan Nigeria ba bare ya san da yin hakan da ya yi ba dai'dai bane, sannan bugu da kari shi bai zauna da ƴan uwan nasa ba bare har yasan abin da suke so da wanda basu so, shi ne yasa abin ya bashi mamaki. Sake shi Lion ɗin ya yi tare da miƙewa tsaye, cikin nutsuwa ya miƙa mata hannunsa a kan ta kama ta miƙe su tafi. Ɗan satar kallon sir Arvin ɗin ta yi, duk kunya ya kamata, amma haka ta miƙawa Lion ɗin hannunta. Kamawa ya yi tare da ɗan jawota ta miƙe tsaye, mannata da jikinsa ya yi suka nufi hanyar fita daga cikin room ɗin. Da kallon sir Arvin and Areef ɗin suka bi shi da shi har suka fice. Part na Aseef kai tsaye suka nufa, har lokacin yana kwance bawan Allah. Kasa kasa Lion ya yi sallama a parlourn, babu kowa a ciki, bedroom suka wuce kai tsaye, sai kallon part ɗin Rimshar take yi, taga komai na TRIPLETS iri ɗaya, harta carpet da komai nasu iri ɗaya sak, colors ne kawai ya banbanta, abin ya yi matuƙar burgeta ba kaɗan kaɗan ba. Sallama Lion ɗin ya sake yi kasa kasa kafin ya sa kai ya shige ciki, bawan Allah Aseef yana ƙudundune a cikin bargo. Saman bedside drawer ya ce da Rimshar ta zauna, shi kuma sai ya haye saman bed ɗin mai gabaɗaya. Kasa da bargon kaɗan ya yi izuwa kirjin Aseef ɗin, idanuwansa a lumshe kamar mai yin barci, sai dai kuma ba barcin yake yi ba, zafin zazzaɓi kawai tasa yake jinsa a s sama. "Our heartbeat". Lion ya ambaci sunansa kasa kasa. Da kyar ya iya amsa mashi da na'am. "What's wrong with you?". Duk da yana zazzaɓin hakan bai hana shi turo baki kamar biro ba, a shagwaɓe kamar zai yi kuka ya ce. "Ba Heartbeat bace, ba ita ce ta je ta yi wannan abin ba, kuma ni Allah ba zan iya zama ba tare da ita ba, mutuwa zan yi Lion". Ya kai karshen maganar yana buɗe idanuwansa da suke jajir sabida zazzaɓin. Nisawa Lion ɗin ya yi kafin ya fara magana. "Wannan shi ne kawai abi da ya saka mana kai zazzaɓi?". Gyaɗa kai ya yi alamar e. "Okey tom tashi ka yi wanka muje mu yi breakfast, anjima zan kawo maka Heartbeat ɗin taka". Girgiza kai ya yi yana faɗin. "No Lion, bana son ganin wannan abin da ta yi, kada ka kawota, idan ka kawota zan mutu, kuma ba zan iya rayuwa ba ita a kusa da ni ba, pls ni kasan ya zaka yi". Dogon hancin nan nasa Lion ɗin ya ja kafin ya ce. "Za'a goge abin da ta yi ɗin, yanzu dai je kayi wanka kazo muyi breakfast ko?". Jinjina kai ya yi yana faɗin. "To Lion a goge dukka fa". Sumbata a kumatu kawai Lion ɗin ya kai mashi kafin ya mike ya sauko kasa daga saman bed ɗin, sannan ya riko hannun Rimshar suka nufi waje ba tare da ya bari Aseef ɗin ya kalleta ba, dan idan ya kalleta tabbas amai zai yi ta sake fara kwarara masu. Suna fita bedroom nasu suka koma, shi kuma Aseef ya tashi ya nufi toilet dan ya yi wanka kamar yadda Lion ɗin ya faɗa masa. A ɓangaren gwaggo kuwa, abu ne da kuka sani, wato kwararriyar likita ce, ta yi wa Jehan aiki cikin nasara, sai dai Jehan ɗin bata farfaɗo ba har safiyar yau ɗin, Areef duk hankalinsa a tashe, duk ya yi wani iri da shi, dan ma sir Arvin yana kwantar mashi da hankali ne, da abin sai ya fi haka, da alama sir Arvin da Areef jikinsu yafi haɗuwa sosai kamar yadda Lion yafi kusa da Aseef, idan baku manta ba Lion ya fi kusa da Aseef sosai, shi ne pleasurensa, to shi ma Areef yanzu sun fi kusa da sir Arvin, sai suka zamana kamar twins twins guda biyu kowa da ɗan uwansa da suka fi shakuwa. Lion yana shiga bedroom nasa ya ɗauki wayarsa ya kira Areef a kan ya zo su san abin yi a kan Akila, dan shi gaskiya ba zai iya ganin Aseef a cikin damuwa ba, kuma bai kamata su sanya mata chemical a jiki ba, domin ba ƙaramin aikin Aseef ɗin bane ya zauna ya yi ta yi masu kukar da babu karshe idan suka sanya mata chemical, so gara dai kawai su san abin yi. Ita kuwa Rimsha saman bed ta haye ta kwanta, dan dama har yanzu cikinta yana yi mata ciwo, bata gama komawa dai'dai ba duk da period ɗin nata ya zo, dan haka sai ta koma ta kwanta, luf ta lume a cikin bargo tana tunanin rayuwar da suka yi a gidan su Kausar na Ilorin. A tare sir Arvin da Areef suka shigo cikin ɗakin, Lion yana zaune a gefen bed ɗin kusa da Rimshar tasa yana tambayarta har yanzu tana jin ciwon cikin ne ya yi mata allura?. Make mashi kafaɗa ta yi a kan ita ta ji sauki bata son allura, a haka su sir Arvin suka shigo suka samesu gwanin birgewa. Saman bedside drawers na gefe da gefen bed ɗin suka zauna. Ba ɓata lokaci Lion ɗin ya sanar da su cewa ga abin da yake buƙata a kan Aseef da Akila, koma ta halin yaya ne a goge wannan ƙunshi ba tare da an jimata ciwo ba. Sir Arvin ne ya ce wannan ai mai sauki ne, zasu fita da ita, dole za'a goge shi, tattoo ma aka goge bare lalle?. Areef kuwa guntun murmushi ya saki kafin ya ce da sir Arvin ɗin "A yadda kaga Lion haka Aseef yake da bala'in kishi, sai dai mu fita da ita bai sani ba, amma idan ya sani, to wlh babu zaman lafiya, zai ce ba za'a kaita wasu su kalla mashi ita ba, shi fa yadda kaga Lion haka yake, banbancin kawai shi ya fi Lion saukin kai ne, kuma shi ma sabida abin da ya taɓa faruwa da brain nasa ne, bacin haka wlh da babu in da zai baro Lion a komai da komai, to yanzu dai zamu fita da ita ba da saninsa ba kenan?". Jinjina masu kai Lion ya yi yana faɗin. "Yeah na baku izinin ku ɗauketa a je a goge wannan abin, is better for me da na ga Aseef a cikin ciwo, koma ina zaku kaita lallai a goge wannan abin ba tare da bata lokaci ba, kada a bar komai ƙanƙantarsa a jikinta". Ɗan satar kallon Rimsha da ta basu baya ta lumshe idanu kamar mai yin barci Areef ɗin ya yi, ganin alamar bata yi barci bane yasa ya yi shiru, da yaso ne ya ce da Lion ɗin ya cika son kai dayawa a kan TRIPLETS nasa, wato a kai Akila duk in da za'a kaita, shi dai kawai a goge wannan abin dan Aseef ya samu lafiya, kai Lion duniya, a kan TRIPLETS nasa babu abin da ba zai aikata ba. Shiru ya yi dan kada ya faɗi hakan ya tadawa da Lion ɗin tarzoma, sabida idan Rimsha ta ji hakan dole zata saka shi a gaba da cewa baya sonsu da gaske dama, bazata yi la'akari da cewa Akilar ma causing ɗin su Lion ɗin bace, dama Rimsha ai sarkin rigima ce, shiyasa Areef ɗin ya yi shiru. A kan haka suka tsayar da matsaya Areef and sir Arvin suka wuce suka fita. Suna fita basu zame ko'ina ba sai ɗakin su Akila ɗin, tana ƙudundune a cikin bargo ita ma. Kasancewar su Areef ne suka zo yasa ta miƙe zaune da kyar, kanta na wani sara mata sosai sabida ciwo, ta ɗaga masu gaisuwa cikin girmamawa. Sorry suka yi mata tare da ce mata ta tashi ta shirya su tafi, bata tambayesu ina zasu je ba, kawai ta hau yin shiri abinta, jiki duk babu kwari, su kuma suka fice daga cikin ɗakin zuwa parlourn dan su bata damar shiryawa. After some minutes ta fito cikin shirin doguwar riga, kallo ɗaya zaka yi mata kasan cewa bata da lafiya, duk tana wani firgice, ga idanuwa duk sun faɗa. Sai da Areef ya sake leƙa Jehan kafin ya fito suka tafi. Har lokacin Jehan ɗin bata farfaɗo ba. Bayan sun kaita an goge mata ƙunshin tas, a hanyarsu ta dawowa sai suka biya asibiti suka duba su Adiva. A nan ne Dr yake sanar da su cewa Maryam an cire mata kodarta guda ɗaya ne, shi ne ya hassasa mata wannan ciwon, Allah ma yasa tana da ragowar shan ruwa a gaba, kuma sun yi ƙoƙarin wajen miƙata ga kwararun likitoci cikin lokaci ne, basu bari lokacin ya ƙure masu ba, sannan abin da yasa ta yi ta wannan ciwo da aka cire mata kodar tata, ba'a bata kulawar likitoci ba, ana cirewa aka barta ba wani cimar kirki, dan ma likitan da ya cire mata kodar kwararren likita ne, da wlh mutuwa zata yi. Ita kuma Adiva sai dai su danganata da wajen malamai, dan su dai a asibitin nan sun gama nasu, kuma bawani ciwon kirki wanda ya isa ya sanyata doguwar suma da suka gani a tattare da ita, ɗan crash ne, kuma sun yi treated nata, sai dai har yanzu bata da niyar motsawa ma bare ta farfaɗo, kamar babu rai a jikinta, so wannan sai an haɗa da malamai, dan da alama tsafi aka yi da ita. Areef ɗin ne ya tambaya ba dai dukkansu suna raye ba?. Tabbatar mashi da suna raye likitocin suka yi, sannan suka kara masu da cewa ita Maryam ai zata iya yin rayuwa da koda guda ɗaya, babu wata matsala, sai dai an cucuta ne, duk wanda ya yi sanadiyar cirewar kodar nan tata ya yi mugu mugun cutarta a rayuwarta. Shiru Areef ya yi yana tunanin kalar azabar da zai ganawa Hjyr daɗi idan ya kamata, sai ta gwammaci dama bata zo duniya ba. Sallama suka yi wa Drs ɗin, suka ɗauki Adiva zuwa wajen Shaikh Sultan, suka bar Maryam a hospital ɗin dan a cigaba da bata kulawa ta sami lafiya sosai da sosai. Suna miƙa Adiva ga Sheikh Sultan ya gane menene matsalar tata, dan haka sai ya hau aiki, su kuma suka wuce gida da Akila. A saman table na cin abinci suka isko gabaɗaya familyn ban da Jehan and Aseef, su basu da lafiya, basu fito ba, Jehan ma bata farfaɗo ba har yanzu, Aseef kuma ɗaki Lion yasa aka kai mashi nasa breakfast ɗin, amma kowa yana waje, yau ba'ayi breakfast da wuri ba, almost 10 yanzu, sai lokacin zasu yi breakfast. Saman table ɗin suka haye suma, bodyguards ɗin ne suka fara yin serving nasu ba tare da ɓata lokaci ba. Kaɗan Areef ya ci abincin ya miƙe ya bar wajen, sabida baya jin daɗin jikinsa, hankalinsa yana a kan Jehan, yana barin dining room ɗin ma part nasa wajenta kenan ya nufa, dan ya duba jikinta bawan Allah. Sir Arvin ne ya sanar da daddyn Rimsha halin da ake ciki dan gane da Adiva da kuma Maryam, addu'a sosai jama'ar da suke a saman table ɗin suka yi masu kafin daddyn Rimshar ya ce. "Arvin da kai da Alex tun da yau Friday, zamu wuce masallaci a tare da ku dan ku karɓi kalmar shahada". Okey uncle sir Arvin ya ce, shi kuma Alex ya ce Okey brother, dan idan baku mance ba shi daddyn Rimsha yayansa ne uwa ɗaya uba ɗaya, dan haka da Yaya yake kiransa. Shi dai Lion suna cin abinci ma idanuwansa da hankalinsa yana a kan Rimsharsa, sai faman shan ice cream take yi, sam baya son ya yi mata magana a cikin mutane, amma wannan ice cream ɗin da take sha har cikin ransa yake jin hakan, sabida yasan a wani hali take ciki, tana period ne, ga ƙasarsu da bala'in sanyi sosai, shan abu mai sanyi yana da matuƙar illah a gareta a yanzu, ga shi taki ɗagowa bare su haɗa ido ya hanata sha, daga karshe da ya ga ta shanye zata ɗauki wani, sai ya ce mata "It's okey, kada ki sake ɗaukar wani, momma ku zuba mata tea mai zafi sosai ta sha". Binta da kallo kowa da yake a saman table ɗin ya yi, shi kuwa Lion ya sha kunu ya murtuke kamar ba shi ya yi magana ba, dan baya son ra'ini. Turo baki ta yi, dan tana son kara wani ice cream ɗin, sam bai isheta ba, shegen daɗi ne da shi, amma kuma bata isa ta ce zata kara ba, idan ta yi gigin yin hakan zata ci duka a hannun daddynta ma ba Lion ɗin ba, dan tun da suka ji Lion ya hanata sha, to sun san ba haka kawai ba, akwai dalili. Zuba mata tea ɗin ɗaya daga cikin bodyguard ɗin ya yi, ya tura mata gabanta, a hankali ta ɗago da kallonta izuwa kan face ɗin Lion ɗin, ta yi hakan tana ƙoƙarin ɗaukar cup ɗin tea ɗin tana kuma aikin turo baki. Wani irin harara ya wurga mata wanda ya sanyata dakatawa daga ɗaukar cup ɗin, miƙewa ya yi ya bar saman table ɗin, da kallo sir Arvin ya bishi, dan kuwa yana kallon duk abin da suke yi, Lion sai Rimsharsa, ita ma Rimshar sai Lion ɗin, ba mai iyasu sai junansu. Ganin ya harareta kuma ya tashi ya bar wajen ne yasa ita ma ta mike jiki ba kwari ta bi bayansa, dan tasan ba haka kawai ne yasa ya yi mata irin wannan kallo ba. Kwance a saman bed ta isko shi, a saman jikinsa ta zo ta haye tana faɗin. "To ni yanzu kuma menayi maka ne?". Zuba mata waɗan nan sexy eyes ɗin nasa masu rikitarwan ya yi ba tare da ya yi magana ba. Duk sai ta ji ta nemi nutsuwarta ta rasa, ƙoƙarin sauka daga jikin nasa ta yi, dan ta gudu kada ya zama wani laifin ta yi, ya hukuntata. Capkota ya yi yana mai cigaba da kallonta bai ce ko uppan ba. "Kayi hakuri Noorish". Ta faɗa tana tsuke fuska. Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin calmly ya ce "Waye ya ce ki sha ice cream? And na yi magana kuma kina turomun wannan ɗan bakin naki kamar biro ko?". Kasa kasa ta ce "Oho dai bakin nan dai kyau yake yi maka, kuma haka zaka barmin kayana, kasha iya shanka ba zai kare ba, kullum sai ka tsokani bakin bayan kuma daɗin sha yake yi maka". Gera ɗaya ya ɗaga yana sauraron maganar tata, lallaima Messhan nan tasa, wato yasha iya shansa ba zai shanye ba, ga shi tana maganar tana kara turo mashi bakin nata. Matseta a jikinsa sosai ya yi har sai da ta ce "Wayyo mummyna, kai Noorish me kuma nayi maka?". Kasa kasa ya ce "Dani da ke waye yafi son bakin wani?". "kai mana, kafi son nawa". Ta bashi amsa a hanzarce, tana wani kawar da kai daga kallonsa kamar wata mara gaskiya. "Ni na taɓa satar kallon bakinki ne? Ni nataɓa kissing na lips naki a hoto ne? Ni ina satar hotonki a wayar prof ne? Lokacin da muka je Russia ni ina zuwa in yi ta satar kallon lips naki idan kina barci ne? Bana yin dikka wannan, kece kike yi, kinga kece mai satar kallon lips nawa sabida yafi naki kyau". Kuka ta saka mashi tana faɗin. "Ni wlh sharri kake mun, ni ban saci kallon lips naka ba, kuma ni me zan yi da lips naka?, Allah na ɓata da kai". Ta kai karshen maganar tana ƙoƙarin barin jikin nasa. Da sauri ya kara ƙanƙameta sosai yana faɗin. "Dawo kiji mana sarkin rigima". Ya kai karshen maganar tare da raɗa mata magana a kunne. Cool murmushi ta sakar mashi tare da bashi sumbata a kumatu tana faɗin. "Amma dai nawa lips ɗin yafi naka kyau!". Lumshe idanuwansa ya yi tare da ɗaura hannunsa ɗaya a saman mazaunanta, a hankali ya fara shafasu yana sauke numfashi cikin nutsuwa ba tare da ya sake ce mata komai ba. Kwatar da kanta a saman Lion chest nasa ta gefen wuyarsa ta yi tare da fito da tongue nata tana yi mashi tafiyar maciji a lallalausan wuyar nasa. Cikin wata iriyar murya mai kama da na mai jin barci ya ce. "Zaki fara ko Meesha?". Kasa kasa ta ce "Ai kai ne ka fara ba ni ba". Dogon numfashi ya ja tare da waro idanuwansa a hankali, a take har sun sauya launi izuwa jajir da su, da alama abin ta motsa mashi ne. Ɗan juyo da kansa ya yi ya zamana suna fuskantar juna. "Me na fara ɗin?". Ya yi maganar kamar mai raɗa. Zame tongue nata daga wuyarsa ta yi ta mayar izuwa saman lausasan lips nasa, a hankali ta fara lashesu. Wani irin lumshe idanuwansa ya yi tare da kara matseta a jikinsa. Ta jima kaɗan tana lasar lips ɗin nasa kafin ta zura harshenta mai gabaɗaya a cikin ɗan bakin nasa, kamar jira yake yi ya capko harshen nata ya fara wasa da shi. Hannu ta tura mashi a cikin gashin kansa tana watsawa, kara rikita shi ta yi, hakan yasa ya fara kissing nata da zafa zafa kamar ance za'a kwace mashi ɗan bakin nata. A can dining room kuwa, miƙewa Aafia ta yi ta fice daga wajen tana faɗin "Gwaggo zan je na kwanta, kai'na na ɗan yi mani ciwo". Kusan a tare suka haɗa baki dasu daddyn Rimsha wajen cewa "Subhanallahi, ciwon kai kuma?". E ta basu amsa a kasale. "To kije ganinan zuwa na dubaki". Cewar gwaggon. Da sauri ta wuce ta bar wajen, ba wani ciwon kai da yake damunta, kawai kallon da Tga yake yi mata ne ya isheta, ta kasa samun sukuni, shi ne yasa ta gudu. Sai dai kuwa ta gudu ne bata tsira ba, dan kuwa tana barin wajen shi ma ya tashi ya bi bayanta. Da kallo su gwaggo suka bisu da shi, ga Mark ma shi da Anayarsa suna cin abincin, kowa dai na familyn suna saman table ɗin, da yake table ɗin ma duniya ne guda, dik ya ɗaukesu har da sauran kujeru da suke empty. Kai tsaye part ɗin gwaggon Tga ya nufa, dan kuwa ya hango shigarta wajen. A balcony ɗakinsu ya cimmata tana tsaye, ba tare da jin wani ɗar ba ya shige ciki abinsa. A kusa da ita ya zo ya tsaya. Zaro idanuwa ta yi tana kallonsa, gabanta ne ya bada ras, bata yi tunanin zai biyota ba, da sauri ta yi yunkurin juyawa ta bar wajen. A hanzarce ya riko hannunta yana kare mata kallo bai ce komai ba. "Wai meyasa kake takura mun ne Malam?" Ta faɗa a ruɗe, muryarta cike tab da tsoronsa sosai. Can kasa kasa ya ce "Because I really love". A dubu ɗari ta zaro idanunta waje, bata taɓa tunanin zata sake jin kalmar love a bakin wani ɗan adam na daban ba ma bare kuma shi Tga da ya zamana sam ba class nata bane, yafi karfinta ta ko'ina, bugu da kari mutumin da ta fara so a rayuwarta, ta yi zaton ta yi bankwana da jin wannan kalma ta love a rayuwarta ta duniya, kai ina, ɗaukar abin ma take yi a mafarki, dama akwai wanda zai iya cewa yana sonta a yadda take ɗin nan ne? Komai ya lalace mata, ta kare, ban da dara daran idanu babu abin da zaka gani a face nata, ta yi mummunar rama na kin karawa. Girgiza kai ta fara yi tare da kwace kannunta daga rikon da ya yi mata ta fara ja da baya, dan a mafarki ta ɗauki abin. Biyota ya fara yi, a hankali yake takowa yana mai karewa face nata kallo sosai. Har ta kai karshen balconyn ba tare da ta sani ba, tana ƙoƙarin faɗawa kasa ta baya baya ya yi saurin riƙota yana mamakin meyasa take yin hakan kuma dan ya ce yana sonta? To ko dai tana da wani motsi a kai ne? Anya bata da aljanu kuwa?. Sai tambayoyi yake jefawa kansa. Kwace kanta ta yi tare da juyawa da gudu da nufin ta bar wajen. Wani irin mahaukacin walkiya ta gani ya gifta ta gabanta, nan take ta ga fuskar da ba zata taɓa mancewa da shi ba a duniya ya bayana ta cikin wannan walkiyar. Ihu ta kurma tare da juyawa ta kankame shi tana runtse idanunta. Ba fuskar kowa ta gani ba face fuskar Abbo, kenan Abbo bai mutu bane ko yaya? Menene gaskiyar al'amari?. FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU CE TA AMANA🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* Date: 3/6/2024 E44 Haƙiƙa ba shakka face ɗin Abbo ta gani, ba gizo bane ba, gaskiya ce, hakan na nufin bai mutu ba kenan?. Sosai ta ƙanƙame uncle T tana numfashi sama sama, dab take da ta sume mashi a jiki, dan tana bala'in tsoron Abbo, shi ya kashe mata miji, ba zata taɓa mantawa da shi ba a rayuwarta, kuma ba zata taɓa yafe mashi ba, azzalumi!!. Ganin tana ƙoƙarin sume mashi a jiki ne yasa ya rikota da kyau yana tambayarta lafiya? Dan shi bai ga komai ba, abin da abu na tsafi, ita kaɗai ta ga kayanta. Cusa kanta a cikin faffaɗar kirjinsa ta yi tare da sakin wani marayar kuka mai ratsa zuciyar duk wani mai sauraro, Allah sarki baiwar Allah. Shiru uncle ya ɗan yi, ya rasa me zai yi mata, me zai ce mata, shi ba wani rarrashin mutane ya iya ba, Aseef kawai ya iya rarrashi a rayuwarsa, dama shi Aseef ai dole ma su iya rarrashinsa, dan idan ya tashi zuba tsiyarsa ba'a magana. Jin yadda take kukan yana taɓa mashi zuciya sosai ne yasa ya ɗauketa cak suka fito izuwa cikin bedroom ɗin. A saman bed nasu ya kwantar da ita yana ƙoƙarin komawa saman bedside drawer. A dubu ɗari ta kara ƙanƙame shi tana mai cigaba da kukan nata, jikinta sai wani irin kerma na tsananin tsoro yake yi, duk ta yi wani iri da ita lokaci guda, ta fita a hayyacinta. Dole ba dan yaso ba ya zauna a saman bed ɗin tare da riketa da kyau, shi ba addu'a ya iya ba bare ya tofa mata, shi fa ko addu'ar da pastor yake yi masu ma bai wani rike ba, da yake tun ainahinsa musul ne hakan yasa ma duk abin da pastor zai yi bata shiga kansa, a lokacin yana dai zuwa church ɗin ne saboda Lion yana zuwa, bacin haka da wlh ba zai je ba, ba wani son addinin yake yi ba dama, bawan Allah ashe ma shi musulmi ne bai sani ba, kai su Anderson basu kyauta ba, duk kuma Jacob Roshan shi ne silar komai, ya cuci Dr William da familynsa sosai. Haka ya mannata da jikinsa kawai yana ganin yadda take ta kerman tsoro, ga shi ta kasa yi mashi magana, duk ya shiga ruɗu, yanzu zargin da yake yi a cikin zuciyarsa na cewa tana da wata matsala a ƙwaƙwalwarta ya tabbatarwa da kansa hakan, amma bai nuna mata a fili ba, ya dai riketa kawai yana jiran yaga karshen haukar tata a ina zai tsaya. A can dining room kuwa, duk Akila ta damu, so take yi kawai taga Heartbeat nata, cin abincin kawai take yi, hankalinta da nutsuwarta yana can wajen tinanin Heartbeat nata. Duk cikin dining room ɗin babu wanda ya lura da ita sai gwaggo, da yake ta je wajen Aseef ɗin ɗazun ta san me matsalarsu, sai ta ce "Akila tashi ki je ki yi wanka ki je ku yi breakfast ɗin a tare da autana, nasan da cewa bai yi breakfast ɗin ba, dan ya ce shi dole dole dake zai ci abinci". Kasa da kai ta yi, dan ita tana da kunya sosai, jiki ba kwari ta miƙe ta bar wajen. Tagumi sir Arvin ya buga yana kallonsu, har ta fice daga room ɗin. Daddyn Rimsha ne ya ce "Arvin lafiya kuwa?". Nisawa ya yi kafin ya ce "Uncle wai dukka yanzu sun yi aure sun barni? Gaskiya sun yi mun wayo, kuma ba zan yarda ba". "To waye ya hanaka yin aure dama my son?". Cewar gwaggo. "Momma ni da ban da girlfriend ina ni ina aure? Ai sai kana da ita, amma dai koma menene QUADRUPLE na sun saka mun sha'awar son yin auren, dukkansu sai su ɗauki matansu su wuce dasu cikin bedroom su barni tare da Pinky? To ita ma Pinky aure zamu yi mata da wuri, na koyi darusa sosai zuwana nan, dan haka aurar da Pinky da wuri zamu yi muma Daddy". "Haba Arvin Pinky ai yarinya ce sosai". Cewar Dr William. "Daddy matar Saif fa da kaɗan tafi Pinky, dukkansu mate ne, kuma ga shi ta zauna zaman aure da mijinta lafiya, dan haka ita ma Pinky shagwaɓarta ya isheni a gidan nan, na gaji". "Babu ruwanka da Pinky, kai dai ka nemo mata mai hankali da nutsuwa, ida muka yaba da hankalinta sai mu yi maku aure, Pinky tana nan tare da mu har sai idan ita ta buƙaci yin aure, kawai zaka wani sauke haushin gaurancinka a kanta, a kanka take zaune?". Cewar daddyn Rimsha. Ƙasa kaɗan ya yi da kansa kafin ya ce "Kai uncle, yanzu kuma ni za'a sakawa ido kenan?". "E mana da kai da Alex gaku manya daku, Alex fa ya kai 36 yanzu, amma babu mata, bashi ma da niyar yin aure, dan ko maganar bayayi, baku tunanin gaba, to ni dai ba zan zuba muku ido ba, ba zan barku ku zauna a haka ba, maza ku nemo mata mu san abin yi". Alex ɗin ne ya karɓi zancen da cewa "Kai yaya wato yanzu kai ma ido ka saka mun ko? To daga yau na dai'na zuwa cin abinci dining room ɗin nan, dan ido zaku saka mun, ni ina naga wata girlfriend da har zan yi aure? Nifa seriously ban taɓa tsayuwa na kalli wata yarinya da ido bama, idan kaga na kalli mace to by mistake ne, kunga yanzu babu in da zan samo mata kuma". "Yauwa uncle Alex, tell them, we don't have a girlfriend". Cewar Arvin "Ai su ma su Saif ɗin da kuke gani sai da aka kai ruwa rana suka yi aure, barema shi Saif, ina ga duk kin matanku ko kwatansa baku kai ba, ni tun da Saif ya yi aure to duk wanda yake cewa ba zai yi aure ba a mashirmaci na ɗaukeshi, dan daga kan Saif an rufe kofa in dai a kan tsanar mata ne, amma yanzu ga shi nan tare da matarsa cikin farinciki, duk ya mance da abubuwan da ya yi a baya, har poison ƴan mata sun sha a kansa, ku tambayi Areef zai gaya maku, ku ai kun san Saif a lokacin da ya zama Saif ne, baku san shi a time da yake Romeo or Lion ba!". Cewar daddyn Rimsha, dan shi sarai yasan wanenen Lion. Ita dai gwaggo da ido kawai take binsu da shi, ga idon nata kamar na Jehan da daddynta, dara dara da su, kai familyn Dr Salman akwai dara daran ido kam ba karya. Sai kallonsu take yi, amma hankalinta yana a kan tunanin Jehan, tunaninta kawai take yi, tana so ne ta gama cin abincin nan ta je ta sake dubata. "Uncle do you know something?". Cewar sir Arvin. Girgiza kai daddyn ya yi alamar a'a bai sani ba. "Yanzu kawai ka nemo mana matan da zamu aure, ba shikenan ba?". Kallon Alex daddyn ya yi yana jiran ya ji me zai ce shi kuma. "Yeah I greed, ka nemo mana matan kawai masu hankali, dan mukam bamu da ƴan mata, bamu ma taɓa yinsu ba, yanzu kaga bamu san a ina zamu nemo mai kirki ba, amma kai sai ka nemo mana". Ajiyar zuciya daddyn ya sauke kafin ya ce "Sai na koma Nigeria, dan ƴan Nigeria dukkanku zaku aura, ban yarda da ku sake auran masu jajayen kunnuwar nan ba, gara mana.........." Ƙasa karisa maganar ya yi saboda wani kallo da Brr Naurat ta wurga mashi, wato bai yarda da masu jajayen kunnuwa ba, lallaima daddyn Rimsha yana tsakiyarsu kuma yana ƙoƙarin kauce hanya. "Nawazuddeen ni kuma yaya zaka yi da ni kenan? Nima baka yarda dani ba ko?". Cewar Brr Naurat ɗin. Ƙasa ya yi da kai yana ɗan shafa kan nasa, gwaggo kam me zata yi idan ba dariya ba, shi ma Alex dariya abin ya bashi, da alama daddyn Rimsha ya manta asalinsa ne yasa yake nema kauce hanyarnan, da alama ya manta da suna wajen, da alama ya manta fa a kasarsu kuma cikinsu yake, dan gasu Dr William, Jay, da kuma John duk suna a wajen, yana cikinsu tsundum yake sakin layin. Dr Salman ya ce "Barshi ba laifinsa bane, ƴar Maiduguri ce ta kiɗima shi, shiyasa yake ganin babu kamarsu, amma ni ai nasan babu kamar masu jajayen kunnuwar, ga kuma shaida nan kun gani". Tamkar mummyn Rimsha ta nutse cikin kasa, haka ta ji sabida kunya, daddyn Rimsha ya ja mata. Alex ne ya ce "Gaskiya bro ni ma ƴar Maidugurin nan zan aura, sabida daga jin yadda ka canza akala to fa ba'a banza ba". Daure fuska gwaggo ta yi tana faɗin. "Kai duk ku tashi ku bamu waje tun da kun gama breakfast ɗin, ni zaku sakawa ɗan uwa a gaba? To wlh baku isa ba, ku tashi ku wuce". Ba dan sun so ba Alex da sir Arvin suka miƙe suka bar wajen, sannan Jay da John ma suka rufa masu baya. Miƙewa ita ma gwaggon ta yi tana faɗin "Bari na duba jikin Jehan". Ɗan zaro idanu daddynta ya yi yana faɗin. "Meyasameta?". Ya yi maganar cikin murya mai kama da wanda ya shiga damuwa. Shap gwaggon ta mance da cewa basu san komai ba, da ba zata yi maganar ba, abin ya yi mata ne kamar sun san meyafaru shiyasa ta yi magana. "Ba wani abin bane, ɗan ciwon kai ne". Ta basu amsa. Yadda ta yi maganar yasa Brr Naurat ta zargi cewa ba gaskiya ta faɗa masu ba, bata saba yin karya ba, shiyasa da ta yi ma maganar bata zauna ba. "Jeki abinki A'isha kai kuma Nawazuddeen ina ruwanka ita da ƴarta? Ba ra'inonta bace?". Cewar Brr Naurat. Shiru ya yi yana tunanin meyasami Jehan? Yana kaunarta ne fiye da kansa, sabida idan baku manta ba ya binne yara dayawa kafin ita, dole ya sota sosai fiye da tunanin mai tunani, dan har ya fidda rai da samun yara Allah ya kawo mashi ita. Wucewa gwaggo ta yi ta nufi part ɗin Areef. Tun daga parlourn take jiyo muryar Jehan ɗin tana kuka, abin ya yi mugun bata mamaki, saboda bata yi zaton zata farko a yanzu ba, to amma meya sakata kuka?. Da sauri ta karisa cikin bedroom ɗin. Kwance Jehan ɗin take kamar yadda ta kwantar da ita tun farko, ga Areef kuma ya duka a saman gwiwowinsa ya riko hannunta yana bata hakuri, ta datse idanuwanta gam wai bata son ganinsa, shi kuma ya ce ba zai tafi ba har sai ta hakura ta yafe mashi, ya tuba ba zai sake ba. Sam taki kula shi, ba dan wani azababben tsoronsa da take ji bama kuma ba zata iya tashi ba ai da babu abin da zai hana bata gudu ta bar mashi dakin ba, mugun tsoronsa ne yanzu yake cike fal a ranta, da ta buɗe idanu ta gansa a ɗakin sai da ta ji wani azababben jiri tare da ciwon kai saboda tsoronsa, tsoron nasa ne ma yasa ta kasa yi mashi magana, ta dai datse idanu bata son ganinsa, amma tana tsoron yi mashi magana, karo na farko a rayuwarta da tsoronta ya fito fili ɓaro ɓaro, kana ganin face nata kasan a tsananin tsorace take. Shi kuma dai yaki sakin hannayenta, sai rarrashinta yake yi, ya yi juyin duniyarn nan a kan ta buɗe idanu su kalli juna, amma ina taki yarda, dan tamkar fuskar zaki ko dodo haka take ganin face nasa. "Areef me yake faruwa ne?". Gwaggon ta tambaya. Jin muryar Gwaggo yasa Jehan ɗin ta kara sautin kukan nata idanuwa a datse gam take faɗin "Gwaggo dan Allah ki ce ya tafi, wlh tallahi tsoron shi nake ji, nashiga ukuna, ni bana son ganinsa, ya tafi, ya tafi wayyo daddyna". Gwaggon na ƙoƙarin yin magana Areef ɗin ya rigata da cewa "Momma please help me tell her that am so so sorry, ba zan kara ba, please kada ta yi fushi dani, ta ce bata son ganina, wai na tafi fa momma". Ya yi maganar kamar zai yi kuka, duk jarumta irin tasa yana da rauni sosai a kan Jehan, ta zama tamkar bugun numfashinsa gudun jininsa. Still gwaggo na ƙoƙarin yin magana Jehan ɗin ta tari numfashinta da cewa "Wlh ba zan yafe mashi ba, ni bana son ganinsa, kuma wlh ba zan hakura ba". Tana magana idanu a rufe ruf. Ita dai gwaggo yau taga ikon Allah, sun ma ki barinta ta yi magana, wannan ya faɗa wannan ya faɗa, duk sai ta rasa me zata ce masu, ita Jehan ta rantse bata son ganinsa, shi kuma ya rantse ba zai fita ba har sai ta yafe mashi, kai ana dirama kala kala a gidan Lion. Samun waje saman bedside drawer kawai gwaggon ta yi ta zauna, ta buga uban tagumi tana kallon ikon Allah, ta mayar da su kamar wasu Tv kawai, sai yi suke yi, Jehan ta faɗa shi ma ya faɗa, ga Jehan ɗin taki yarda ko da sunan wasa ta buɗe idanu su yi four eyes da shi, ya yi ya yi ta buɗe idanun nan taki. Areef sai Jehan, ita ma Jehan sai Areef kamar yadda Lion sai Rimsha, ita ma Rimshar sai Lion ɗin, Aseef sai Akila ita ma Akila sai Aseef ɗin, ba mai iya masu sai su yaku yakunsu, to ni dai Princess Teema bari na ɗauki alƙalamina na je na leƙo su Heartbeat, watakila kafin na dawo zasu bawa gwaggon damar ta yi masu sulhu, ta samu ta saka baki a maganar ko za'a samu dai'daito......🥱 Wanka Akila ta tsara tare da shiryawa cikin wani wandon jeans baki da T-shirt sky blue, ta kara gyara gashin kan nan nata da yake ta faman tashin fitinannen kamshi, ita kanta sai zuba uban kamshi kamar anyi ɓarin perfume a jikinta take yi, flat shoe ɗin Jehan ta sanya a kyawawan kafafunta kafin ta ɗauko hijabinta ta sanya a jikinta, ta yi kyau matuƙar kyau. Kai tsaye part ɗin Heartbeat ɗin nata ta nufa, dan tasan part ɗin nasa sarai, a gaban idanunta ya shiga ciki jiya. Bakinta ɗauke da sallama ta shigo cikin parlourn, babu kowa sai daddaɗar kamshi air freshener mai daɗin sanyayya zuciya da yake tashi, ga makekiyar Tvnsa tana magana kasa kasa, sanyi A.c ne yake tashi a maimaƙon ɗumi, duk da wannan uban sanyi na ƙasar hakan bai hana Aseef kunna A.c ba. Shiru ta ɗan tsaya tana zuba kauyanci a parlourn, ta rasa wani bedroom ne daga cikin ukun nan nasa, ita bama bedroom ɗin take nemaba first, parlourn take karewa kauyancinta tukun nan, ya haɗu ne haɗuwar da bata taɓa ganin irinsa ba. Ta jima a tsaye a wajen tana kalle kalle kafin ta tsinci kanta da jin cewa ta tsargu, ta ji kamar wani yana kallonta. A hankali ta ɗago idanuwanta ta fara bin kofofin shiga da fice da yake a cikin parlourn. Tsaye yake a kofar shiga cikin bedroom nasa, ya harɗe hannaye a saman kirjinsa, daga shi sai short, da alama ma daga toilet ya fito, dan jikinsa duk danshin ruwa, babu riga a jikinsa, ya tsareta da ido babu ko kyaftawa. Ƙasa ta yi da kanta tana faɗin "Good afternoon heartbeat". Bai amsa ba kuma bai kawar da kallonsa daga kanta ba. Almost 10 mins a haka, da dai taga bashi da niyar yin mata magana, sai ta fara ƴan kame kame tana son zamewa ta gudu ta bar part ɗin. Yana kallonta tana ɗan motsawa tana ɗan ja da baya kaɗan kaɗan, tana kaiwa tsakiyar parlourn ta juya a guje zata fita. Ina taku biyu ya yi ya rikota. Wage baki ta yi zata zunduma mashi ihu, hannu yasa ya toshe mata bakin nata yana faɗin "Kiyi mun shiru ko kuma na zaneki a nan". Tsit ta nutsu ba dan taso ba. Jawota jikinsa sosai ya yi tare da matseta, kasa kasa ya ce "Waye ya ce ki je kiyi wancan abu baki da kika yi ɗin?". "Kayi hakuri, ban san baka so bane shiyasa nayi, amma ba zan sake ba". Nisawa ya yi tare da cewa "Yanzu da zaki gudu kuma ina zaki je?". Kukan shagwaɓa ta saka mashi tana faɗin "Kai Heartbeat nifa bani da lafiya, amma ka tsayar da ni a nan, zazzaɓi nake yi, bana iya tsayuwa sosai, kuma yunwa nake ji". Ta kai karshen maganar tana kai mashi duka a bayansa. "Muje ciki na baki abinci to". Ya kai karshen maganar tare da ɗaukarta cak suka koma cikin bedroom ɗin. Bai direta a ko'ina ba sai a saman katafaren bed nasa. Hayewa shi ma ya yi yana faɗin "Zo ki fara bani nawa abincin kafin in baki naki". Wani irin tsoronsa ne ya dira mata a cikin zuciyarta, amma sai ta danne ta ce "Kai Heartbeat ni dai ban yarda ba, yunwa nake ji, ka fara bani abinci na ci na ƙoshi kafin ka fara aikin wasan naka". Turo mata ɗan bakin nan nasa ya yi. "Zo to ki ji wata magana". Ya faɗa a shagwaɓe, ya kai karshen maganar kuma tare da jawota ta faɗa saman kirjinsa. "Heartbeat me zaka yi mun?". Ta tambaya a tsorace, saboda tasan me ya faru da Jehan da kuma Rimsha, duk tana sane da komai, shi ne yasa tsoron nasa ma ya kara kamata sosai. A kunne ya raɗa mata cewa "Breast zan sha na ƙoshi kafin na baki abincinki kema". "Iya breast kawai?". Ta faɗa har lokacin muryarta akwai tsoro sosai. "Yeah iya shi kawai zan sha sai kuma lips naki" Guntun murmushi ta sakar mashi kafin ta ce. "My shagwaɓati ba zaka canza ba". Hannu ya ɗaura a saman bayan yana ƙoƙarin ɗage mata T-shirt ɗin jikin nata dan ya rabata da shi ya ce "Kema ai baki canza ba, tunda kinki ki canza nima ba zan canza ba". Sumbata ta kai mashi a lallausan kumatunsa tana faɗin "I really love you my shagwaɓati". Cak ya tsaya da ƙoƙarin cire mata rigar da yake yi, dawo da hannunsa a saman gashin kanta ya yi ta cikin hijabin, a hankali ya juya da ita, ya zamana ya yi mata rumfa da faffaɗar kirjinsa. Hijabin nata ya fara rabata da shi kafin ya cire mata riga. Ganin bata sanya bra ba yasa ya kara waro idanuwansa waje yana kallo kyawawan tula tulan nata kamar an hura balo balo. Rufe idanuwanta gam ta yi tana faɗin "Kai Heartbeat kallon fa?". Nisawa ya yi kafin ya kai hannunsa dukka biyu ya damkosu, tap suka cika mashi hannu, matsa su ya fara yi kamar mai yi masu tausa. Kuka ta saka mashi tana faɗin da zafi fa, shi kuma kuka ya saka mata yana faɗin da daɗi wlh. (Astagfirullah babu ɗan rigima biyun Aseef a duniya🥱 ta yi kukan zafi, shi kuma ya yi kukan daɗi😂 gaskiya Aseef ya fara wuce tunanina, ya iya tsiya 😂🥱) "Heartbeat da zafi nace maka fa". Ta faɗa tamkar zata sanya mashi kuka. Cikin shagwaɓa sosai shi ma ya ce "My heartbeat akwai daɗi wlh, wayyo mommana daɗi". Ai Akila bata san time da ta buɗe idanunta tana ganin yadda yake kiran wayyo momma daɗi sosai ba, mamaki ya bata, bata taɓa jin irin wannan abin ba ko a novels da take karantawa, bata taɓa jin namiji kamar shi yana ihun daɗi kuma yana kiran mommansa ba sai a kan Heartbeat nata, yau dai taga abin da ya sha gaban tunaninta. Bata gama tsinkewa bama sai da ya jita a jike sosai, nan ya hau kira mata sunan momma daɗi zai kashe shi ɗin da kyau da kyau, na ɗazun dukka wasa ne. Baki da ido ta saki tana kallonsa, sam baya a tare da ita, ya luluka duniyar sama jannati yana aikin zuba santi da sambatu, ga shi sai matsa mata su yake yi son ransa, duk ya gigice. Ta shagala da kallonsa bata ankara ba sai ji ta yi ya shigeta. Ihu ta zunduma mashi na azaba, shi kuma ya yi mata ihun daɗi abinsa. (Ni kam Princess Teema dariya kamar ya kasheni😂 Aseef yana ihun daɗi, momma ki kawo ɗauki.😂) Sosai take kuka tana kai mashi duka a kan ya sauka a kanta ya rabu da ita, ina wlh sai ma lumshe idanuwansa da ya yi yana faɗin. "Wayyo mommana, wayyo daɗi zai kasheni, Lion, Areef kuzo daɗi zai kasheni, my heartbeat zata juyar mun da kwakwalwa". Sai zuba sambatun daɗi yake yi abinsa. Har ya sumar da ƴar mutane ba tare da ya sani ba, time da ya zo zai kawo ma wani irin ihu ya yi yana faɗin. "Mommana daɗi zai kasheni, please ki zo, wayyo mommana". Haka ya rinƙa ihu daɗi abinsa, ya yi abin da yake so a kanta, ita kuwa baiwar Allah ta yi kuka har ta sume. Allah ya shirya mana Aseef my peoples 😂 ya sumar da ƴar mutane, amma yana can yana ihun daɗi tare da zuba sambatu FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU CE TA AMANA🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* Date: 4/6/2024 E45 Sai da ya gama ihun daɗinsa son ransa, ya yi bidirinsa son ransa, shi ko wuyar da ya sha ma bai bi ta kai ba, ko zafin da bananarsa take yi mashi ma bai wani damu ba, shi dai ya ji daɗinsa kawai. Sai da ya nutsu ya dawo dai'dai ne ya iya gane cewa ashe ta suma, nan kuma labari ta sauya, nan take ya ruɗe, cikin ruɗun yake ambatar sunanta tare da jijjigata, amma ina ko motsi bata yi. Kuka ya fara yi yana faɗin dan Allah kada ta mutu ta tashi, ba zai iya yin rayuwa idan babu ita ba. Amma shiru. Ganin hakan yasa ya mayar da short nasa jikinsa ya diro kasa daga saman gadon. Kai tsaye part ɗin Lion ya nufa abinsa, idan ba ku manta ba shi kome aka yi mashi Lion yake fara sanarwa kafin kowa, dan haka yanzu ma sai ya nufi part ɗin Lion ɗin kai tsaye. Lokacin da ya shigo Lion ɗin yana rungume da Rimsha a saman Lion chest nasa suna zuba hira kamar ba Lion namu ba, sai biye mata yake yi tana bashi labarin garin Ilorin garinsu Kausar ƴar yarabawa, ta ce idan suka je Nigeria zai kaita ko? Ya ce mata e zai kai ta, sai murmushi take yi tana wasa da kyawawan yatsun hannunsa masu matuƙar ɗaukar hankali, sun kasance gwanin birgewa da ban sha'awa. Jin shigowar mutun yasa dukkansu suka kai kallonsu a wajen kofar shigowar. Ganin Aseef yana kuka ne yasa Lion ɗin bai san time ɗin da ya sauke Rimsha daga jikinsa ya miƙe zaune ba, dan shi fa abin da kuka sani ne, a kan Aseef sai dai ayi yakin duniya ta uku, sai dai kowa ya mutu in dai a kan TRIPLETS nasa, sam bashi da adalci ta ɓangarensu, idan abin da ya shafesu ne to wlh suɗin kawai yake bawa attention nasa. Da sauri Aseef ɗin ya kariso cikin ɗakin yana faɗin. "Lion kazo ka tayarmun da my heartbeat nawa, mutuwa ta yi na shiga uku". Ɗan satar kallon Rimshar Lion ɗin ya yi kafin ya miƙe tsaye, ko ba'a gaya mashi ba yasan me Aseef ɗin ya aikata, duba da yanayin da yake a ciki kuma ga bananarsa a tsaye kyam, so ko Aseef ɗin bai bashi labari ba ya gano menene ya faru. Riko hannunsa ya yi tare da jansa suka fita waje, suka bar Rimsha dake ta faman binsu da kallo kamar ta samu Tv. A parlour suka tsaya yana tambayarsa to meya faru kuma?. Kukan nasa ya karawa Power kafin ya fara bawa Lion ɗin labarin abin da ya faru babu ko kunya a idanuwansa. "Dis virgin nata fa nayi, kuma da nazo yi sai naji da daɗi, na ji daɗi sosai har na manta a ina nake, shi ne na yi ta yi har na jimata ciwo, wlh kuma ba laifina bane, da daɗi ne kawai". Yana magana hawaye suna zuba mashi daga idanuwansa. Girgiza kai kawai Lion ɗin ya yi kafin ya ce "To ina momma?". "Nima ban san in da take ba, ni dai dan Allah Lion kazo ka cececi Heartbeat ɗita ka ji?". Shiru ya ɗan yi kafin ya ce "Okey muje wajen momma, saboda ita kaɗai ce zata iya duba maka me yake damun Heartbeat ɗin, ni ma ba zan iya ba, saboda na Meesha ma bani na yi mata komai ba, momma ce, dan haka ita zamu je mu gayawa". Rungume Lion ɗin ya yi yana faɗin "To muje da wuri, i love you my blood". Raba jikinsu Lion ɗin ya yi kafin ya wuce gaba, da sauri Aseef ɗin ya rufa mashi baya. Part ɗin gwaggon suka nufa. Bata a ciki, tana wajensu Areef bata dawo ba, sai mummyn Rimsha kawai suka samu a cikin bedroom ɗin, tana zaune a saman bedside drawer tana jiran gwaggon, dan gwaggon ta ce mata ta zo su yi magana. Ganin gwaggo bata nan har sun juya zasu tafi sai Lion ya ce da mummyn Rimsha ta zo ta duba masu matar Aseef mana, dan yana da tabbacin gwaggo tana tare da su Dr Salman ko Dr William, dan haka a barta kawai mum Rimshar ta je ta dubata. Ba musu ta amsa mashi da Okey, sannan ta tambaya ina Akilar take?. Aseef ɗin ne ya yi gaba ya je ya nuna mata, shi kuma Lion ya nufi part nasa. A hanya ya haɗu da Areef, kallo ɗaya ya yi mashi ya kawar da kansa gefe guda yana faɗin "What's going on?". Kamar Areef ɗin zai yi kuka ya amsa mashi da "Baby ce ta ce bata son ganina, momma kuma tabi bayanta wai na fita masu daga cikin ɗaki, shi ne duk ra'ina ya ɓaci, wai momma bazata taya ni bata hakuri ba, sai dai ta ce na fice masu a ɗaki, kuma wai har da karawa da cewa baby kada ta kulani, dama baby kam ba'a gaya mata haka ba ma, ba wani kulani take yi ba, bare kuma momma ta goya mata baya". Wani irin kallo Lion ɗin ya wurga mashi da waɗan nan dara daran idanuwan nasa masu kama dana Dr William kafin ya ce "To da can waye ya aikeka ka je kayi abin da ka aikata? Ai sai ka rungumi sorry ka kuma rungumi pillow, kawai ka kyaleta ɗin ko na 1 month haka". Harara ya watsawa Lion ɗin yana faɗin "Aww haka kaima zaka ce? Wai ni ya kuke son nayi da ra'ina ne? Wato kenan da so kake yi na zuba mata idanu ina kallonta kullum bananana tana tsaye kyam ina kwana rungumar pillow ko? Kai to meyasa baka rabu da Rimsha ba? Meyasa ka kasa hakuri ta kara girma? Kai fa Lion kai ya kamata ma acewa meyasa ka je ka aikata abin da kayi wa Rimsha ba ni ba, wato ni na mutu ko?". "A'a ba ka mutu ba, ka dai jure sai gaba". "Kai me ya hanaka jurewa? Meyasa ka kasa hakura har sai da ka fatattaka under 15 years girl, ka jefata doguwar suma for almost 1 month? Yanzu haka nasan ka sake koma mata baka hakura ba". Harara ya watsa mashi kafin ya ce "To idan ma na koma ina ruwanka? Kayanka ko nawa?". Wani irin dariya ce ta kubcewa Areef ɗin, lallai Lion da karfin hali yake, wato ya manta time ɗin da yake kiran mata da halittu, ya manta da cewa Rimsha wannan karamar halittar da yake faɗa ne, yanzu ko a jikinsa yake kwanciya da ita, gaskiya maza basu da kunya musamman kuma irin Lion, wato yanzu yasan daɗin duniya har da cewa kayansa ne, ya ɗan ɗani abin da bai taɓa jin irinsa ba, lallaima. Wucewa ya yi ganin Areef ɗin yana dariya, sai ya wuce abinsa. Da sauri Areef ɗin ya sha gabansa yana faɗin "Dawo mana malam mai kayan daɗi, kai fa Lion wlh mugun ɗan rainin wayo ne, wato kayanka ko? To kada dai ka manta she's under 15, dan Allah ka rinƙa tausaya mata kaji, idan kayi sau ɗaya sai bayan one week sannan ka kara, dan nasan duk time da kayi sau ɗaya sai tasha bakar jinya na koda kwana huɗu ne, kaga sai ta huta na kwana uku sannan ka sake buɗeta ka shiga". Ganin Areef yana ƙoƙarin ya saka shi subutar baki ne yasa ya yi shiru bai ce komai ba ya raɓa gefensa zai wuce abinsa, dan Areef akwai neman tsonana. Da kallo ya bishi da shi, har ya ji damuwar da Jehan ta gefashi a cikin ma ya washe, dan haka sai ya nufi part na daddynsu kawai abinsa, dan idan ya ce zai bi Lion cikin part nasa ma, yasan wahala zai sha, dan kuwa Lion dai ba zai fasa yiwa Rimsha abin da ya yi niyya ba dan Areef ɗin ya shigo, sanna kuma ba zai kula shi ba, so gara mashi kawai yaje wajen daddynsa su ɗan yi hira na tsakanin uba da ɗa. A ɓangaren uncle T kuma, rungumeta sosai ya yi yana ɗan bubbuga mata bayanta ba tare da ya yi magana ba, har sai da ta sami nutsuwa. Sai da hankalinta ya dawo jikinta, a zabure ta miƙe zaune tana ƙoƙarin raba jikin nata da nasa. Riƙota da kyau ya yi tare da sanya hannu ya ɗago haɓarta. Ganin face nasa yasata nutsuwar dole, nan take ta ji wasu malaman nutsuwa sun sauko mata a jikinta. Ƙoƙarin kawar da kanta gefe guda ta yi, dan kada ta cigaba da kallon face nasa, abin da kuka sani ne kullum a ɗaure face ɗin take kamar ta Lion. Hata kawar da kan nata ya yi ta hanyar matso da nasa face ɗin dab da tata, har suna iya jiyo sautin numfashin juna, ga dogayen hancinsu suna gogar na juna. "What's wrong with you Aafia?". Ya faɗa a nutse. Runtse idanuwanta gam ta yi kafin ta iya bashi amsa da Nothing. Haƙiƙa ba zata iya yi mashi musu ba idan ya yi magana, ba zata iya kin amsa mashi ba kuma ko da bata so, saboda abin a jinin familyn Dr William yake, kwarjinin bala'i ga kuma shegen shiga rai garesu kamar me. "Why are you doing something like you have brain problem?". Ya yi maganar yana kara jawota jikinsa sosai, saboda tana ƙoƙarin zille mashi ne, cikin dabara take ƙoƙarin raba jikinta da nashi, to ya ganota, shi ne yasa ya kara riketa gam. "Babu abin da yake damuna, nima dai haka kawai nake jina wani iri". Ta bashi amsa. Kawar da zancen ya yi da cewa. "Do you love me?". Ya tambayeta yana mai dawo da kallonsa a saman wuyarta, da waɗan nan shegun idanuwan nasa irin na Areef. A dubu ɗari ta buɗe idanuwanta babu shiri, jin wannan tambaya tasa ta taɓa mata brain, dan ita fa har yanzu ma bata yarda cewa da Tga take tare ba, ganin abin kawai take yi a mafarkin da ta saba yi nasa tun kafin ta yi aure ne. "Aafia talk to me, do you love me?". Mayar da idanuwanta ta yi ta datsesu tana tunanin iko irin na Ubangiji, wato duk yadda kake a duniyar nan akwai mai sonka a haka, mutun ma mai daraja da kima, Allah mai iko, duk wanda ya riki Allah ya huta. Kara matso da face nasa sosai ya yi har sai da ya haɗe fuskokin nasu, a karo na uku ya sake tambayarta tana son shi?. A wannan karon girgiza mashi kai ta yi alamar a'a. "Why baki Sona?". Ya tambaya a ɗan ruɗe. "Saboda ni ba class taka bace, kafi karfina, kuma ni na taɓa yin aure mijina ya rasu, and kuma nasan koba ma haka ba kafi karfina, ni ban yarda da cewa ma akwai wanda zai sake cewa yana sona ba, ban taɓa.........." Katse mata maganar ya yi ta hanyar sumbatar lips nata da wannan ɗan bakin nasa irin na Areef, yadda take magana ne yasa ya ji ba zai iya ba sai ya sumbaceta. Da sauri ta waro idanuwanta waje, kai tsaye sai cikin nasa idanun, shi ma kallonta yake yi sosai. "Ni ke nake so ai, ba ruwana da kin taɓa yin aure, so stop talking all this miscellaneous excuse, just kawai tell me, do you love me or not?". Shiru ta ɗan yi kafin ta ce "I love you since before, amma kuma for now dai........." Sake katseta ya yi a karo na biyu, nan ma ta hanyar sumbatar lips nata kafin ya ce "You love me that's all, i don't want to hear any excuse, so now get ready, dan zan gayawa momma abin da yake faruwa, bana son ki sake kawo mun wani miscellaneous talk talk kuma". Ya kai karshen maganar tare da zaro mata dara daran idanuwansa yana kara sumbatar lips ɗin nata. Suma kwance kawai ta yi mashi, ta rasa me zata sake ce mashi, ya goge mata hadda. Shi kuwa ganin bata ce da shi komai bane yasa ya kara matseta sosai a jikinsa tare da matso da lips nasa ya haɗe bakinsu waje guda, shi a wajensa hakance soyayya. Da sauri ta sanya hanayenta dukka biyu tana ƙoƙarin ture shi ta raba jikinsu. Ganin haka ne yasa ya zame ɗan bakin nasa daga nata ya kuma raba jikin nasu yana kallonta har cikin ido. Miƙewa ta yi da sauri ta nufi hanyar fita waje. Da ido ya bita ba tare da ya dakatar da ita ba. Sai da ya kalli ficewarta sannan shi ma ya miƙe jiki duk babu kwari, abubuwa sun motsa, a haka ya fito waje ya nufi part nasa. A ɓangaren Akila da mummyn Rimsha kuwa, sai da suka yi da gaske kafin Akilar ta farfaɗo, nan ma sai can rana ta yi sanyi sannan ne ta farfaɗo, hakan ma da taimakon gwaggo, sai da gwaggo ta sa hannu kafin su samu ta farfaɗo, shi kam Aseef sai kuka yake yi musu a kan kada su bari Heartbeat ɗinsa ta mutu, wlh yana sonta, idan ta mutu zai bita. Da kyar gwaggo ta samu ta shawo kansa ya hakura ya nufi bedroom na daddynsa, ya barsu su yi aikinsu, a can ma ko da yaje ya saka daddyn nasu a gaba da kuka a kan lallai shi dai Heartbeat ɗinsa ta tashi, haka daddyn suka haɗu shi da Areef suka yi ta ɗannarsa har suka samu ya yi barci. Sai misalin karfe 4 na yamma ya farka daga barcin, yana farkawa kuma da sunanta ya tashi, a lokacin su daddy basu cikin bedroom ɗin, da sauri ya diro kasa daga saman bed ɗin ya nufi part nasa dan ya duba Heartbeat ɗinsa. Yana shiga cikin bedroom ɗin lokacin ita kuma Akilar ta farfaɗo su gwaggo sun tallabota zasu kaita toilet a gasa mata jiki sosai. A hanzarce ya kariso wajensu yana tambayar lafiya ina zasu Kaita? A gefe guda kuma yana yi wa Allah godiya da Allah yasa bata mutu ba tana da rai. Gwaggon ce ta bashi amsa da cewa zasu je ne su gasa mata jiki, dan sai an gasata sosai, ta sha bakar wahala ita ma, yaran Dr William dukka ba sauki, gado suka yi, dan shi ma daddynsu fa babu sauki. Jin cewa gasata za'a je ayi, nan fa ya saka masu kuka a kan shi ma wlh in dai haka ne sai su Lion sun gasa shi. Dariya kamar gwaggo zata yi yaya, amma ta danne dariyar ta ɓoye bata bari ya kubce mata ba. Aseef ikon Allah, wai sai su Lion sun gasa mashi jiki, duk abin da yake yi fa yana sane yake yi, kawai shagwaɓar ce tabi jikinsa, amma wlh tsayayyen namiji ne shi ma, meyasa bai ce su gwaggon su gasa mashi jiki ba sai ya ce su Lion? Kun ga kuwa sarai yana sane yake zuba tsiyarsa dan yaga suna biye mashi. (Amma kuma fa ni for me yana da gaskiya, gara ya yi musu kafin lokacinsa ta kure, yanzu ai idan suka haifi yara ba zasu rinƙa biye mashi ba, kunga kuwa ya yi abin da yake so yanzu, ni dai PRINCESS TEEMA ina goya mashi baya😂 saura naji wata readers ta yi magana😒 yauwa ina goyon bayansa, ban ga laifinsa ba, ya mori lokacinsa, dan nan gaba kaɗan gwaggo zata fara renon jikoki, su Areef su fara renon yaransu, kunga ba zasu wani biye mashi ba) Da kyar nan ma gwaggon ta lallaɓa shi ta ce ya je su Lion ɗin su gasa mashi jikin nasa to. Haka kuwa aka yi, wajen su Lion ɗin ya wuce abinsa, ya tsayar masu da rigimar sai sun gasa mashi jiki shi ma, saboda ai ya sha wahala ba kaɗan ba shi ma. Areef ne ya ce to su je toilet ya gasa mashi tun da haka yake so, Lion kam ko kallon in da yake ma bai yi ba, sir Arvin ma yana rike da Pinky a saman laps nasa ya ce to su je a gasa mashi mana, abu mai sauki ne ai wannan, ita kuma Rimsha tana cikin bedroom na Lion ɗin tana zuba barcinta abinta, dan kunga bata da lafiya, tana period, ba isshasshen lafiya ke gareta ba, shi ne yasa Lion ɗin ya kyaleta ta yi barci ya fito parlourn part ɗin nasa suna hira da su sir Arvin ɗin. Da gasken gaske kuwa Sir Arvin da Areef suka je suka gasawa Aseef jikinsa a cikin toilet da ruwa mai zafi, harda towel suke matsa mashi jiki, kada ku manta sun iya gashi sosai, saboda suna yi idan sun je wani aikin sun dawo, ko idan suka yi faɗa da wasu, musamman ma shi Areef da ya yi rayuwa da ƴan ta'adda, so suna iya faɗa a tsakaninsu su daki juna da har sai sun gasa jiki, to haka suka gasawa Aseef ɗin ma jikinsa, ko yaya suka gudanar da hakan? Su dai suka sani, yaran gwaggo sai gwaggo, my readers Allah ma ya rufa mana asiri da yaran gwaggo suka tsaya a iya QUADRUPLE ɗin nan, ba dan haka ba da jinin Dr William zamu ga abubuwa kala kala da bamu taɓa ji da gani ba, ga sir Arvin ma ya zamo irinsu, da yake abin nasu a jini yake, dama bai da abokan da za su yi ne yasa yake a haka, amma yanzu ai sai abin da muka gani kawai......😂 Areef kam da karawa abin armashi har da ɗauko wata katuwar towel mai girman gaske ya lulluɓe Aseef ɗin da shi, suka haɗu da sir Arvin suka shafa mashi lotions kala kala masu daɗin kamshi, sannan suka ɗauko mashi kaya masu matuƙar kyau da tsada sosai. Sai dai fa ko da suka bashi kayan sai ya ce shi ba zai sanya da kansa ba, dan Heartbeat ma yasan saka mata kaya su gwaggo zasu yi, dan haka shi ma sai dai su saka mashi. Areef dai ya ce ba zai saka mashi ba, ya gasa mashi jiki ta isa, kaya kuma ya saka wa kansa. Kuka ya fara ƙoƙarin saka masu, da sauri sir Arvin ya karɓi kayar tare da cewa A'a ba sai ya yi kuka ba, bari ya saka mashi, abu mai sauki Areef yake son ɓata mashi a rai a kansa, to ya yi shiru ya kwnatar da hankalinsa, dole shi zai saka mashi kayan. Narkewa ya yi a jikin sir Arvin ɗin yana turo baki, shi a dole an mashi ba dai'dai ba. Wucewa Areef ya yi ya koma parlourn, dan iskancin Aseef sai shi. Sir Arvin kuwa ya saka mashi kayan kamar yadda ya ce, sannan ya ce su koma parlourn. Ko da suka fito Pinky baiwar Allah har ta yi barci kwance kusa da Lion, ta tada kai da laps nasa, shi kuma yana aikin latsar waya. Mu koma baya kaɗan, da sir Arvin da kuma Alex sun karɓi kalmar shahada lokacin da suka je sallar jumma'a, kowa ya zaɓi kalar sunan da yake so, shi Sir Arvin Lion ya ce a saka mashi Safwan, shi kuma Alex daddyn Rimsha ya ce a saka mashi Mahhir, so a yanzu su ba Kristen bane ba, sun shiga addinin Musulunci addini mai ni'ima da tsarki wanda babu biyunsa, Allah ka kashe mu a cikinta, ka karɓi rayukanmu muna masu imani da kai ya, daga karshe ka karɓi rayukanmu muna masu tsananin son manzonka, manzon tsira Manzon rahma ɗan Amina da Abdullahi fiyayyen halitta ɗan gatan Allah, kalmar shahada ta zama abu na karshe da zata fito daga bakunanmu, Amin ya rabbussamawati wal'ardi. After some days. Da Akila da Jehan duk sun tare a ɗakin gwaggo, sam sun ki yarda su koma wajen mazajensu, kuma sarai sun sami lafiya, ita kuma gwaggon bata son ta ce su koma wajen mazajen nasu dan kada ace ta yi son kai, da dai ba yaranta bane suke aure, da sai ta tsaya tsayin daka sai sun koma, amma da yake yaranta suke aure, sai ta yi kara bata ce masu komai ba. Ai kuwa mazajen nasu kamar zasu yi hauka, sam sun kasa hakuri, barema shi Aseef, dan ma gwaggon ta ce mashi Akilar bata da lafiya ne yasa ya yarda ya barta ta ɗan yi kwanaki a wajen gwaggon, ba dan haka ba da ko kwana ɗaya ba zai iya hakuri ba. Shi kuwa Areef bawan Allah, kwata kwata Jehan taki yarda ma ta sake haɗa hanya ɗa shi ne, ko ya shigo wajen gwaggon sai ta yi kamar bata gan shi ba, idan tana kwance ne sai ta juya masu baya ta rufe idanu, idan kuma tana zaune ne sai ta kwanta ta basu baya, haka take yi. Areef ɗin ya yi magiya har ya godewa Allah, amma taki sauraronsa, taki ma ai su haɗa ido, gwaggo kuma ta bi bayanta, dan haka yana cikin damuwa sosai bawan Allah. Rimsha da Lion kuwa soyayyarsu suke zubawa son ransu mai tsabta, kamar zasu cinye juna dan so. Zaɓe yana ta matsowa sosai, sai kara samun nasarori Lion yake yi, su His Excellence dai kamar babu su a duniya, sun yi cif, sai dai Lion duk abin da yake yi yana lura da lamuransu, dan ba shirun lafiya suka yi ba, bare ma yanzu da suka gane cewa Dr William na gaskiya da sir Safwan basu a hannunsu, sai suka kara ɗaura ɗamarar hallaka gabaɗaya familyn Dr William ɗin, sannan kuma suka ce shi ma uncle Herry da yake hannunsu wanda shi ne sarkinsu a yanzu, ya gaji Jacob, ya karɓi karagar mulki, dama idan baku manta ba shi ba wai an sadaukar da shi ne dan a kashe shi ba, a'a shi dan ya gaji karagar mulkin Jacob aka sadaukar da shi, to yanzu shi ne sarkin Daular tasu, shi yake mulkarsu, to shi ma yanzu suna kullah yadda za'ayi su kashe shi, dan sun san idan Lion ya juyo ta kansu ba zasu yi saura ba, shi ne yasa suke hanzari su aiwatar da abubuwansu cikin lokacin kafin komai ya kwaɓe musu, hakan ce ma tasa basu wani bi ta kan siyasar sosai ba, suna ƙoƙarin yadda za su kamo gwaggo ne su kasheta, dan a cewarsu gwaggo ita ce bangon rayuwar gabaɗaya familyn, idan suka kasheta dole kowa ya girgiza ya yi kuka sai idanuwnasa ta kumbura, hakan zai sa Lion ya yi laushi a cewarsu, to shi ne suke shirin yadda za'ayi su ɗaukota ba tare da ɓata lokaci ba, daga ita kuma suka ce sai Rimsha, ita ce ta biyu kafin su ɗauki su Dr Salman and Dr William. E lallai su Anderson sun shirya sanya ilahirin familyn Dr Salman kukan jini ma bana hawaye ba, sai dai muce Allah ya tsare mana familyn Dr Salman ɗin mu kawai, ga shi sai sha'aninsu suke sha basu san me ake shirya masu ba, Allah sarki. To yau dai Aseef yazo har wuya, hakurinsa ta kare, da misalin karfe 9 na dare, shirye yake a cikin kayan barcinsa masu kyau da tsada, kai tsaye part na gwaggon ya nufa. A tare ya sameta da ƴan matan nata suna hira, ita kuma Aafia ta basu baya tana kwance a saman bed tana chatting da Uncle T a Whatsapp ta wayar gwaggon, ya yi ya yi da ita a kan tafito waje suga juna, amma taki fitowa, ta maƙale a saman bed tana zuba mashi tsiya, ya ce idan bata fito ba shi zai zo ai ya ɗauketa, hakuri ta fara bashi tana ce mashi sai zuwa anjuma zata fito, dan tasan halinsa sarai, zai iya shigowa ya ɗauketa ɗin kamar yadda ya faɗa. A bakin bed ɗin Aseef ya tsaya yana faɗin "Momma tazo mu tafi mana tun da dai yanzu komai normal ta ji sauki". Gwaggon na ƙoƙarin yin magana, cikin sauri Akilar ta riga ta da cewa "Wlh ni gwaggo a'a, a nan zan zauna kawai, ni ba zan bishi ba, ya tafi abinsa". Kallon shi gwaggon ta yi kafin ta ce "Shikenan ɗan autan mommansa, jeka ka barta a nan ɗin tun da ta ce ba zata bika ba, ka barmun ita ɗin a nan kamar yadda take so". Ta kai karshen maganar tare da kashe mashi ido ɗaya kamar ba uwa da ɗa ba. Murmushi ya yi tare da manna mata sumbata a goshi kafin ya juya FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU CE TA AMANA🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* Date: 5/6/2024 E46 Murmushi ya yi tare da manna mata sumbata a goshi kafin ya juya ya fice daga cikin ɗakin. Yana fita ita ma Aafia ta miƙe zaune tare da zuro kafafunta kasan bed ɗin tana faɗin. "Gwaggo zan je parlour, uncle T ne yake kirana". Siririn murmushi gwaggon ta yi kafin ta ce "To a dawo lafiya, ke kuma Akila zo mu je bedroom naku mu yi sirri". Ta kai karshen maganar tare da miƙewa ta yi gaba. Sai aikin turo baki Akilar take yi ta miƙe tabi bayanta. Suna fita ba'a fi da minti biyar ba sai ga Areef ya shigo cikin bedroom ɗin bakinsa ɗauke da sallama. Jehan na jinsa ta yi maza ta lumshe idanuwanta gam, dan ma ya ɗauka barci take yi. Saman bedside drawer ya zauna, tun da ya shigo idanuwansa suna a kanta, sanye yake shi ma da kayan barci a jikinsa, ya yi kyau sosai, sai dai ƴar rama da ya yi na rashinta a kusa da shi, yana cikin damuwa sosai, sai tashin fitinannen kamshi yake yi sosai. Yana ƙoƙarin yi mata magana ne wayarsa ta fara ringing, cirota daga aljihun wandon barcin nasa ya yi. Mamaki ne ya bayyana a saman face nasa lokaci da ya kalli saman screen ɗin wayar, new number ce take kiransa. Shiru ya ɗan yi, kamar ba zai ɗauka ba, sai kuma dai ya yi picking tare da sanya wayar a Hand-free. Daga ɗayar ɓangaren muryar mace ce ta ambaci "Hi dear". Jin haka yasa cikin sauri ya cire wayar daga hand-free ɗin yana mai kallon Jehan ɗin da kyau da kyau, dan baya son a kara ɓata mata rai, ya sani sarai ranar ma da mace ta kirasa basu wanye lafiya da ita ba, dan haka sai ya katse kiran ma mai gabaɗaya ya kuma kashe wayar. Cikin aljihu ya mayar da wayar kafin ya miƙe tsaye tare da gyara hannun rigarsa, sannan ya shammaceta ya ɗauketa can cak suka nufi waje. Bugawar da zuciyarta take yi ne yasa bata yi mashi rigima a kan ya sauketa ba, ta ji muryar mace a wayarsa, hakan yasa har wani bada dum dum kirjinta ya yi, shi ne yasa da ya ɗauketa bata iya yi mashi gardama ba, dan tana cikin yanayi mara kyau. Bai direta a ko'ina ba sai a saman bed nasa, yana sauketa kuma ya yi saurin kashe wutar ɗakin tare da kara gudun A.c. tana kwance shiru tamkar mai yin barci, duk abin da yake yi tana jinsa, kawai bata jin ra'ayin yi mashi magana ne. Hayewa saman bed ɗin ya yi tare da jawo masu lallausan bargonsa, sannan ya jawota jikinsa. A tare suka sauke nauyayyar ajiyar zuciya, su dukkansu sun yi kewar juna, amma sai rigimar tsiya su yi ta wahalar da kansu abanza. Cikin nutsuwa ya fara magana kasa kasa kamar mai yin raɗa. "Baby i know baki yi barci ba, kina jin duk abin da nake yi, please ki yafe mun mana, kin san halin da nake a ciki kuwa? Zan iya mutuwa fa, please kin ji?". A kule ta ce mashi. "To wacece kuma ta kira wayarka yanzu?". Wani irin dariya ne ya so kubce mashi, amma sai ya danne, dan kada ya kara laifi a kan laifi, yasan idan ya kuskura ya yi mata dariyar nan to fa sai an jisu a rana, Jehan sarkin rigima, uwar kishi kuma. "Baby i don't know her, kawai new number na gani, kuma ai ga wayar nan ki duba mana ki gani, you should have call her and ask her ma idan kina so, ask her a ina ta sami numberta zata gaya maki". Ya kai karshen maganar yana ɗan shafa bayanta. Shiru ta yi mashi bata sake kula shi ba. Ganin hakan yasa ya fara yi mata raɗa tare da kalamai masu sanyaya zuciya a cikin kunnenta. Sai dai kuma sam taki kula shi. Da yake ɗan yi ne kuma ya iya duniyanci, tuni yasan yadda zai yi ya shawo kanta har ma ta mance da fushin da take yi ta biye mashi, bata ma san lokacin da suka fara wasa da juna ba, sai dai har lokacin da akwai tsoronsa cike tap a ranta, amma ta danne ta biye mashi dan dole ba dan ta so ba. A ɓangaren gwaggo da Akila kuwa, nasiha mai ratsa jiki ta je ta yi mata, sannan ta ce to ta yi wanka ta shirya maza ta wuce wajen mijinta. Haka kuwa aka yi, ta yi wanka tare da shiryawa cikin wasu kayan barcin, sai tashin kamshi take yi ta nufi bedroom nasa. Yana kwance a saman bed yana latsa waya, hira yake yi da Haroon abokin karatunsa. Kasa kasa kamar mai ciwon baki ta yi sallamar tata. Bata jira ya amsa ba kawai ta shigo cikin bedroom ɗin, bata kula shi ba ta nufi saman bed ɗin kawai ta kwanta ta baki bakin gadon, sai aikin turo baki take yi. Ɗaura wayar tasa a saman bedside drawer ya yi tare da matsowa kusa da ita, tamkar zai sa mata kuka ya ce. "Heartbeat yanzu fushi kike yi da ni? Ni ɗin naki? Shagwaɓatinki ne fa!". Kin kula shi ta yi, sai ma runtse idanuwanta gam da ta yi. Hannunsa ya kai ya jawota jikinsa, sannan ya cigaba da cewa. "Please my heartbeat ki dai'na fushin nan kin ji? Please ki yafe mun mana, na tuba fa, kuma ai ba laifina bane, kece nan kika yi daɗi dayawa, shi ne yasa duk na ruɗe". Yana magana yana turo mata baki tare da shafa mazaunanta. Duka ta fata kai mashi a saman kirjinsa tana faɗin. "Wato ma daɗi nayi maka ko? Lallai Heartbeat ka iya mugunta, da na mutu fa?". Hannun nata da take dukan nasa da shi ya riko yana faɗin. "Bazaki mutu ba, kin manta da cewa tare zamu mutu ne? Idan kika mutu ai dole na biki, kin san adadin son da nake yi maki kuwa? Kin san ya nake ji a zuciyata kuwa? Allah Heartbeat ba zan iya jure rashinki ba, please ki yafe mun". Kara shigewa jikinsa da kyau ta yi kafin ta ce. "A'a ba zan yafe maka ba gaskiya, sai ka yi mun tausa to". Da sauri ya ce "Tausar ita kaɗai kike so?". Kai kawai ta gyaɗa mashi alamar e ba tare da ta yi magana ba. Miƙewa ya yi zaune tare da fara yi mata tausar babu kama hannun yaro, yana yi yana kallon face nata. Sai da ta gajiyar da shi sosai, sannan ta ce to ya isa ya zo su kwanta. A hanzarce ya mannata da jikinsa suka fara aikin da suka saba, suna yi suna zubawa juna shagwaɓa kamar ba gobe. A ɓangaren Aafia kuwa, a parlourn kasa ta sami uncle T, daga shi sai kayan barci a jikinsa, hannunsa na rike da cup mai ɗauke da coffee, ya saki kyakkyawar gashin kan nan nasa har baya, sai tashin kamshi yake yi. Tun da ta sako kafarta a saman stair case ɗin ya tsareta da idanu yana kallonta, sanye take a cikin kayan barci ita ma, sai dai ta ɗaura hijabi mai ɗan girma zuwa laps nata a saman, sai tashin daddaɗar kamshi ita ma take yi. A saman sofa ɗan nesa da shi ta zauna tana yi mashi barka da dare. Ɗaura cup ɗin hannunsa a saman table dake a kusa da shi ya yi kafin ya amsa mata tare da ce mata ta dawo kusa da shi mana. Kai ta girgiza mashi alamar a'a a in da take ɗin nan a nan zata zauna. Miƙewa shi ya yi ya koma kusa da ita ya zauna, yana ƙoƙarin fara yi mata magana suka jiyo muryar Dr William ta bayansu yana faɗin. "Sudais baka kwanta ba har yanzu?". Shiru Tga ɗin ya yi yana tunanin sunan Sudais, da alama shi ma an mantar da shi addinin Musulunci, bare kuma yanzu da su Anderson ɗin suka juyo da aiki a kansu, so da wuya ya iya tuna sunan, shi kuma Dr William kunga yanzu ya koma ainahinsa, a yanzu shi cikakken musulmi ne mai ilimin addini dai'dai gwargwado. Ganin ya kasa iya tuna sunan ne yasa kawai ya amsawa yayan nasa da cewa suna hira ne da matarsa, amma yanzu ba jimawa zasu shiga. Kamar Dr William ɗin zai sake yin wata magana, sai kuma ya fasa ya juya izuwa saman kawai. Nisawa uncle T ɗin ya yi, haka suka cigaba da zuba hira cikin nuna tsantsar so da kulawa. A ɓangaren Lion and Rimsha kuwa, abin ba'a magana, idan aka ce shakuwa ma an rage, sun haɗe sun zama chewing gum abinsu, zuba soyayyarsu suke yi son ransu, sam Lion baya jin kunyar kowa, a gaban kowa zai ɗauki matarsa su wuce ɗaki, yanzu ta fara sabawa da Brady, har aikansa tana yi ya kaiwa Jehan ko gwaggo abu, sai dai bata taɓa yarda ya hau mata jiki, ɗan nesa nesa dai ake abotar. After some months. Election time. An yi zaɓe lafiya lou Alhamdulillah, gabaɗaya kasa ta rikice zaɓen da aka yi, kowa burinsa kawai ya ji sakamako, ga shi Lion ya tashi kan al'umma ya jijjiga kowa da kowa a in da ya tsayar da daddyn Rimsha a matsayin mataimakinsa, dama da biyu ya ce ayi wa daddyn Rimshar ktakardan ɗan kasa da komai da ya shafi doka, ashe abin da yake shiryawa kenan, masu cewa baya son daddyn Rimsha yanzu ya rufe masu baki, dama shi wlh yana kaunar daddyn nata kamar yadda yake kaunarta, musamman ma da gwaggo ta ce tafi son daddyn sama da kowa a cikin ƴan uwanta, sai ya kara son shi sosai, rashin jituwa da basu samun nan kuma hakan ta samo asali ne da dukkansu suna jiji da kai, izzar bala'i ke garesu, shiyasa ba zasu shirya ba, ba zasu zauna waje guda ba, dan ba wanda zai yarda ya duƙawa ɗan uwansa a cikinsu. Gabaɗaya faɗin U.s ta girgiza na jin cewa bakin fata Lion ya fitar a matsayin mataimakinsa, sannan kuma a halin yanzu kasa ta dulmuye cikin kura na jiran sakamakon zaɓe, shi kuwa Lion hankalinsa a kwance yana gida tare da rigimammiyarsa, ya sakata a gaba yana ta kallon kayarsa, ta wani kara kyau abinta, ta yi ƙiba dumur mur da ita, komai nata ya kara cikowa, sai aikin zuba mashi shagwaɓa take yi yana biye mata. Kwance suke a saman bed nasa, tana kwance a saman Lion chest nasa tana aikin zuba mashi kukan shagwaɓa a kan lallai ita sai dai su tafi yawo, sai dai ya kaita bakin ruwa su je su huta a can, tana son zuwa bakin teku. Kawai ya zuba mata idanu ne yana kallon ɗan bakin nan nata, sai aikin turo shi take yi, ya kasa iya ce mata ko uppan. Ganin bashi da niyar yi mata magana ne yasa ta yunkura zata bar jikin nasa. Da sauri ya riƙota yana faɗin. "Zaki fara ko?". Kamar zata yi kuka ta ce. "Noorish kai ne fa ka fara, kaki ka canza hali, nafi 30 mins ina yi maka magana amm kaki ka ce mun ko uppan, to ya kake son nayi? Sai dai nayi ta magana ni kaɗai kamar mahaukaciya?". Ta kai karshen maganar idanuwanta sun ciko tab da kwallah. Lumshe idanuwansa a hankali ya yi tare da ɗan sake buɗesu a kanta, sumbata ya fara kaiwa ɗan bakin nata kafin ya fara magana kasa kasa a nutse. "I really like your lips my Meesha, sarkin rigima, kina ji ko? Ni ban iya godon magana bane, amma i will try my best wajen ganin ina amsa maki, and maganar muje yawo kuma zamu je, amma ba yanzu ba, kinga gobe za'a saki sakamakon zaɓe, fitarmu a yanzu babban haɗari ne, ki bari sai komai ya lafa, zamu je duk in da kike so Queen of my heart". Tsananin farinciki ne ya bayyana a saman face nata, wani irin cool murmushi ta sakar mashi tare da bashi hot sumbata a saman lallausan lips nasa. "I really love you my Noorish, king of my heart". Tongue nasa ya fitar tare da fara aikin lasar lips ɗin nata yana mai jin tsananin kaunarta tana kara ratsa shi, a haka manne da juna suka yi barci, tamkar zasu shige cikin jikin juna. Washegari da safe, gabaɗaya kasa sun zuba idanu suna jiran sakamaƙon zaɓe da za'a saki, kowa yana fatan Allah yasa nasa zaɓin ya ci, while su kuma su Anderson suna can suna faman yadda za'ayi ko ta halin ƙaƙa ne su ɗauko Gwaggo, har yanzu sun kasa iya ɗaukarta, saboda yawan zama da alwala da take yi, ga askar na safiya da maraice wanda duk wuya duk daɗi bata bari ya wuceta bata yi ba, haka shi ma zama da alwalar, duk wuya duk daɗi da alwalarta take tare, hakan yasa suka kasa iya ɗaukarta, sai suka koma suna rakuɓe rakuɓe suna neman wanda zasu ɗauka a cikin gidan, wanda yake kusa da zuciyar Lion sosai. Maryam kuwa an sallamota daga aaibiti ta dawo gida, tana part na gwaggo, Areef ya ɗauko masu aiki mata guda biyu suna kula da ita. Ita kuma Adiva har yanzu tana wajen Sheikh Sultan, yana ta fama dan ya ga ya ceto baiwar Allahn nan. Uncle T da Aafia soyayya ta yi nisa, gwaggo ta ce dole su je Nigeria neman aure wajen Abbi, daddyn Rimsha ya ce zai aurar da ita a nan ɗin kawai, ba sai sun je ba, gwaggo ta ce a'a masu son zuwa Nigeria suna dayawa, dan haka a can za'a je a nemi aurenta a kuma ɗaura kafin nan su dawo. Ba yadda zasu yi da ya wuce su yi na'am da zancen gwaggon kawai, yanzu sun shirya a kan cewa dama bayan zaɓe zasu je, daga nan gwaggo da mummyn Rimsha zasu wuce Dubai su yi wa su Rimshar sayayyar kayan lefensu da ba'ayi masu ba. Yau dai gabaɗaya U.s ta yi tsit suna jiran jin sakamakon zaɓe daga wakilan zaɓen, shi kuwa Lion yana kwance a saman sofa ya tada kai da laps na Meesharsa suna kallon news ɗin a Tv, sai sanya mashi chip chop a baki take yi, yana tauna a hankali, tana rike da kwalin chip chop ɗin a hannunta, ita bama news ɗin take kalla ba, face ɗin mijin nata kawai take ta kallah, shi kuma yana kallah Tv. Misalin karfe ɗaya dai'dai wakilan zaɓe suka saki sakamakon zaɓen kamar yadda yake a rubuce, already dama kusan gabaɗaya family suna a gaban Tv suna jiran sakamakon, Areef, sir Arvin da Uncle T ne kawai suke part nasu suna bibiyar news ɗin ta wayoyinsu, sun ki fitowa parlourn, shi Areef saboda Jehan bata jin daɗi, tana fama da zazzaɓi ne yasa bai fito ba, shi kuma Sir Arvin kawai yana kwance ne, duk a gajiye yake, Pinky ta bashi wahala na goyonta da ya rinƙa yi, ta ɗan buge kafafunta ne a jikin stair case, shikenan yarinyar nan wai ba zata iya takawa da kafafunta ba, haka ya wuni goyonta yana yawo da ita a cikin gidan, duk in da zata je shi ne mai kaita. Shi kuma Uncle T soyayya ta hana shi fitowa ya haɗu da family a parlourn su zauna a tare, soyayya suke zubawa da Aafiarsa shi ne yasa. Kamar yadda kowa yake hasashe, kamar yadda gabaɗaya faɗin U.s suke saka rai, hakan ce ta kasance, Lion ne ya yi nasara, saboda ya tara uban masoya na kin karawa. Abin ya tashi kan family dama kasa bakiɗaya, ya jijjiga jiga jigan ƙusoshin gwamnati marasa gaskiya, kowa idanu ya fara raina fata, dan sun san zasu gasu ba karya, sun san Lion zai yi maganin rashin adalci, zai ci uban duk wasu gurɓatattu ba sani ba sabo, shi dai His Excellence bata kan zaɓen suke yi a yanzu ba, a cewarsu idan suka gama da familyn Dr William kwatar kujerarsa abu ne mai sauki, cikin kwana ɗaya zasu yi shi, abin ku da tsafi, shi ne ma yasa sam basu wani damu da batun zaɓen ba. Tsabar farinciki na ganin sakamakon zaɓe Lion bai san time ɗin da ya miƙe zaune ya rungumo Meeshar tasa sosai ba, tamkar zai mayar da ita cikin cikinsa, har sai da ta fasa mashi ƙara tana faɗin. "Noorish zaka kashe ni ne?". Cikin tsantsar farinciki yake faɗin. "My meesha mun yi nasara, burina ya cika, Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah, a yanzu kin zama first lady na gabaɗaya faɗin U.s, Allah na godema, yanzu yaki zai fara". (My readers a cikinku waye ya iya tuna cewa tun farkon book 1 First Lady ake kiran Rimsha? Kun tuna sunan? Dama nace ba zan tuna maku ba sai rana irin ta yau😂 to ga dai ainahin sunan ta fito, First Lady of United States, sunan ta tabbata!!.) "Noorish tun da kaci zaɓe yau please ka yi murmushi mana ko da sau ɗaya ne, ko kaɗan, ina tsananin son in ga murmushinka". Ta yi maganar kamar zata yi mashi kuka, ta kuma yi tana kallon face nasa sosai. Zuba mata waɗan nan kyawawan idanuwan nasa masu rikitarwar ya yi na ƴan sakanni kafin ya ce. "Meesha ban iya ba, da na iya tabbas da yau zan yi maki, amma ban iya ba, ban san ta ya ake yi ba, try to understand me". Ya kai karshen maganar yana shafa lallausan kumatunta. Cool murmushi ta sakar mashi kafin ta kwantar da kanta a saman Lion chest nasa, kasa kasa cikin shagwaɓa ta fara magana. "Noorish idan ni ban fahimceka ba wacece zata fahimceka? Na fahimta, kuma ko kaɗan ban ji babu daɗi ba, ina sonka ko da murmushi ko babu, kai ɗin nawa ne ni kaɗan". Ta karisa maganar tana tura hannunta cikin rigarsa ta kasa. Plat tummynsa ta fara shafawa haɗe da lumshe idanuwanta. "Ash my Meesha, zaki fara rikitani ko?". "A'a tukuicin munci zaɓe kawai zan baka, ba wani rikitarwa". "Da gaske?". Ya faɗa tare da ɗan zaro idanu. "Yeah da gaske, ni bani da wani abin da zan baka da ya wuce wannan, ban da komai sai Allah da manzosa, kai da kuma mummy and dad sai ƴan uwanmu, kuɗi kuma ko na baka me zaka yi dasu? Kai ma kyauta da su kake yi, bani da komai sai wannan ɗin". Tana magana tana cigaba da shafa plat tummyn ɗin nasa tare da zura mashi ɗan yatsanta a cikin ramin cibiyarsa. "Meesha da gaske zaki bani kanki? Yanzu baki tsorona?". Kamar zata yi kuka ta ce. "Ina jin tsoro, amma kuma ba zan iya hanaka ba a yau, tsawon lokaci na yi ta hanaka kuma ka jure, please ka yi mun a hankali ka ji?". Tsananin farinciki tamkar ya zuba ruwa a kasa ya sha. Matseta sosai ya yi a jikinsa yana zuba mata kalaman soyayya tare da nuna mata tsantsar farincikinsa, yau shi ne karo na biyu da zai ɗan ɗani zumarta, a baya kullum idan ya yi yunkurin yin hakan sai ta fara gudunsa tana tsoro, zata tsaya su yi wasa, da zarar ya fara ƙoƙarin kai wa wajen, zata ki yarda, daga kasha ma sai ta kai kwana uku tana gudunsa, hakan yasa ya dai'na kwatanta nufar wajen, sai dai su sha love nasu a iya sama kawai, su kuma yi wasa sosai, amma ban da kasa, yau da bakinta ta ce ta bashi kanta, ai dole ya yi murna, yadda ya ɗanɗani na farkon nan har yau daɗin bata sake shi ba, har yau ya kasa mancewa, abin tana ransa. Cancak ya ɗauketa suka koma saman bed, remote ya sanya ya rufe kofar bedroom ɗin nasa kafin ya fara rabata da kayan jikinta. Datse idanuwanta gam ta yi tare da ɗan kawar da kanta gefe dan ma kada ya fahimci idanun nata sun kawo ruwa, har ga Allah tana tsananin tsoronsa, amma ba yadda zata yi, ya isheta ɗaukar alhakinsa da take yi ne yasa ta ce bari ta jure. Rufesu da bargo ya yi kafin ya kwanta ya jawota jikinsa. Muryarta na rawa ta ce . "Noorish ka yi mun a hankali ka ji ko?". Sumbatar lips nata ya yi tare da fara yi mata raɗa a kunne, cikin dabara ya juya da ita ya zamana ya yi mata rumfa da faffaɗar kirjinsa. Sosai ya ɗauke mata hankali da wasanninsa haɗe da kalamai masu daɗi, sai da ya tabbatar ya mantar da ita zancen sannan ya yi ƙoƙarin shigarta, sai dai kuma me? Yadda yaso ya shiga bai samu hakan ba, ya so ya shigeta farat ɗaya ta yadda ba zai yi mata zafi sosai ba, sai kuma ya ji kofar a rufe kamar ba'a taɓa shiga ba, hakan tasa dole ya shiga da ɗan karfi ko kuma ya hakura. To babbar magana, Lion dai zai mori farinciki biyu lokaci guda, ga murnar ya ci zaɓe, ga kuma lonce amaryarsa a karo na biyu da zai yi, sai dai kuma babu hanyar shiga ta sauki, dole sai....... (Ni kuma zan more Maltinata mai sanyi, yau ta yi sanyi over ma kuwa🥱) ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* E47 Ba shi da zaɓin da ya wuce a karo na biyun ma kawai ya shigeta da karfi, saboda a gaskiya yana sha'awarta sosai da sosai, ba zai iya hakura ba, dama bai ga haka bama ya yake hakura bare kuma ya gani? Ai sai dai ita ta yi hakuri ta jure. A karo na biyu ma bidirinsa ya sha son ransa, ya rinƙa zuba mata sambatun da bata jinsa, dan ta yi nisa a cikin azabar da ya sanyata, kwata kwata bata tare da shi. Sai bayan ya samu nutsuwa ya yi abin da zai yi ne ya lura da cewa ya sake yin ɓarna a karo na biyu, dafe kansa dake sara mashi kamar zata fashe ya yi kafin ya kai hannu ya tallabo kanta izuwa saman Lion chest nasa. Kasa kasa ya fara ambatar sunanta, amma ina shiru diff kake ji. Lallausan kumatunta ya shafa da hannunsa kafin ya ce. "Am so so sorry my Meesha, ke ɗin ce duk sai ki bi kisa mutun ya mance a wata duniya yake". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa tsaye da ita a jikinsa. Toilet ya wuce da ita, a saman shoulder ɗinsa ya kwantar da ita kafin ya kunna ruwan mai zafi a cikin jacuzzi. Sai da ruwan ta yi mashi dai'dai misali, sannan ya kunna na sanyi kaɗan ba dayawa ba, dan baya son ruwan sanyi ko kaɗan, sun fi son mai zafi sosai. Bayan ya kammala haɗa ruwan sai ya shiga tare da ita manne a jikinsa. Saukar ruwan a jikinta yasa ta farfaɗo daga sumar da ta yi. Wani irin marayar kuka ta saka mashi tare da kara ƙanƙame shi sosai. Riƙota da kyau shi ma ya yi yana mai ambatar sunanta, bata iya amsa mashi ba sai dai kuka. Karisa shigewa da ita cikin mai gabaɗaya ya yi tare da kara rungumeta sosai yana yi mata sannu. Sam bata ce mashi ko kala ba, haka ta cigaba da kukanta kala biyu, na farko ga azabar da ta ci a wajen Lion ɗin, na biyu ga azabar zafin ruwa, ita ruwan ya yi mata zafi sosai, amma bata da bakin yin magana a halin yanzu, azabar zafi ma ba zai bari ta iya yin magana ba. Cigaba da kukanta ta yi har na tsawon lokacin da suka ɗauka a cikin ruwan, ya yi rarrashi har ya hakura, amma taki ta yi shiru, sai shafa bayanta kawai yake yi yana ce mata sorry, ta kwantar da kai shiru a saman Lion chest nasa tana hawaye. After some minutes ya naɗota a towel suka dawo cikin ɗakin, a lokacin idanuwanta a datse gam, saboda bata son su haɗa ido. A saman bed ya shimfiɗeta kafin ya juya ya koma cikin toilet ɗin, wanka mai kyau ya yi tare da fitowa, dressing room ya shiga dan ya shirya. Bayan wasu ƴan mintuna ya fito sanye da pajama mai matuƙar kyau launin milk color. Saman bed ɗin ya zo ya haye. A kusa da ita ya kwanta yana kallon face nata. Tamkar mai yin barci haka ta rufe idanu ruf, sai dai ta dai'na ruwan hawayen nata da take yi. "Am so so sorry my Meesha". Ya raɗa mata a kunne. Ɗan turo baki ta yi ba tare da ta ce mashi komai ba. Calmly ya furta. "Meeshana in kara yi kaɗan?". A wani irin dubu ɗari ta buɗe idanuwanta, abin gwanin ban dariya, sai dai ga mutane, amma Lion kam bata bashi dariya ba, sai ma kashe mata ido ɗaya da ya yi kamar wani......... Ganin tana binshi da harara ne yasa ya ɗaga mata gera guda ɗaya yana faɗin. "In zo in kara kaɗan? Ban ƙoshi bafa". Tsuke fuska sosai ta yi tare da juya mashi baya bata ce komai ba, azababben raɗaɗi take ji gabanta yana yi mata, ta daure ne kawai. Ganin ta juya mashi baya ne yasa ya yi maza ya jawota jikinsa yana faɗin. "Rigimammiyata, to me abin fushi da Noorish naki kuma? Kaɗan fa zan kara, kuma ba zan yi maki da karfi ba". Dukan wasa ta fara kai mashi a kirji tana faɗin. "Noorish babu ni babu kai, mun yi hannun riga, wajen gwaggo zan koma tun da mugunta kake mun, kuma ka sakeni na tafi yanzu, kada ka sake rungumata". "Da gaske?". Ya tambaya yana lashe siraran hawayen nata. "Ni bada wasa nake yi ba, babu ruwana da kai, dan nace ka yi mun abu a hankali shi ne kaki, ina ta kiran sunanka ma kaki ka amsani, kaki ka kulani, kayi ta abinka ni kuma ina jin azaba, Allah mun ɓata da kai". Ta kai karshen maganar wasu hawayen suna bin kuncinta, saboda ba karya tasha wahala sosai, kamar bai taɓa yi ba. Kara matseta a jikinsa sosai ya yi, a kunne ya fara raɗa mata. "Ai idan babu Meesha to babu Saif, babu in da zaki je matata, ni dake mutuka raba, wai Meesha laifina ne? Ke ce fa kika cika daɗi dayawa, ga ki kankana uwar ruwa, amma dai am so sorry daɗin ne ya saka ban ji kiran da kike ta yi mun ba my ƴar aljannata, ɗan yi murmushi kaɗan". Bata san lokacin da murmushi ya kubce mata ba, dukan wasa ta kai mashi tana faɗin. "Ba za'a yi murmushin ba" . Tana magana kuma murmushi yana a kan face nata, da alama bata san ma ta yi shi ba. Sumbatar lallalausan wuyarta ya yi kafin ya ce. "Wannan murmushi ma ta wadatar, zo mu je mu shirya zuwa parlourn, kinga tun ɗazun sai danna mun kararrawar suna nemana Areef yake yi, murna zasu tayani, mu je ko?". Make mashi kafaɗa ta yi tana faɗin. "Ni dai zan kwanta a nan, ba zan iya zuwa ko'ina ba, jikina yana yi mun ciwo sosai, kuma wajen shi ma zafi yake yi mun, ni ka je kai kaɗan ɗinka kawai". Fito da tongue nasa ya yi ya lashe lips nata kafin ya bata amsa da. "Idan babu Meesha a waje to baza'a ga Saif ba, kwanta a jikina ki yi barci ki huta gajiya, dan wajen ya dai'na ciwo anjuma na kara yin wani chaskalen, bari na turawa Areef sakon su kyaleni yau ranarki ce". Hararar wasa mai ɗauke da kallon tsantsar so da kauna ta wurga mashi, tsabar farinciki bata san lokacin da ta kai mashi sumbata a kumatu tana bayyanar mashi da irin tsantsar soyayyar da take yi mashi ba, ta ji daɗi sosai da ya ce idan babu Meesha to babu Saif. Mayar mata da martanin sumbatar shi ma ya yi tare da ɗauko wayarsa a saman bedside drawer. Saƙo ya turawa Areef a kan su rabu da shi yau ranar Meesharsa ce, kada wanda ya damesu. Allah mai iko, lokacin da Areef ya ga wannan sakon haƙiƙa ya sha mamaki, bai taɓa tunani ko da a cikin mafarki da akwai wata rana da zata zo cikin rayuwarsu wadda za'a ce Lion ya katse duk wasu abubuwa masu mahimmanci saboda wani namiji bama ba mace ba, sai ga shi yau da bakinsa yake cewa kada wanda ya sake damunsa ya katse komai yau ranar Meesharsa ce, Allah mai iko kenan. Shi kuwa yana tura saƙon ya kashe wayar tare da ɗaurata a saman bedside drawer, sannan ya ja masu bargo tare da gyara mata kwanciya a saman kirjin nasa. Cikin salo ya kai hannunsa saman gabanta, kasa kasa ya ce. "Shi ne mai yi maki zafi ko?". Kai kawai ta gyaɗa mashi tana kara lafewa a jikin nasa. Shafa wajen ya fara yi a hankali yana yi mata sannu har barci ya yi awon gaba da ita. Shi ma ba jimawa barci ya ɗauke shi suna manne da juna. Mu koma baya kaɗan kafin ayi zaɓe, Lion yasa an ɗauko mashi Josephine kamar yadda ya faɗa, a yanzu ta dawo cikin gidan, sun sake haɗewa da gwaggo, rayuwarsu gwanin birgewa da ban sha'awa, waɗan nan family guda biyu wato familyn Dr Salman and Familyn Jacob Roshan suna cikin tsananin farinciki na wuce misali. After some times, bayan wani lokaci. Zaune suka gabaɗayansu a saman dining table suna cin abincin safe, gobe za'a rantsar da Lion kamar yadda doka ta tanada, su gwaggo kuma jibi zasu wuce Nigeria dan neman auren Aafia kamar yadda ta faɗa. Sai hira suke yi wasu daga cikinsu, wasu kuma suna aikin tunani, Adiva ma yanzu ta samu lafiya ta dawo cikin gidan, ga kuma Maryam, sai suka sake haɗewa, suna farinciki sosai. Sir Safwan ne ya ce. "Uncle idan mun je Nigeria zaka nema mun mata ko? Dan na gaji da kwana a tare da Pinky". Ya yi maganar yana kallon daddyn Rimsha. Jinjina kai daddyn ya yi kafin ya amsa mashi da. "Ba sai mun je Nigeria ba, ga mata ma na yi maku a nan, kai Safwan nabaka Maryam duk da bani na haifeta ba, kai kuma Mahhir na bata Adiva, Adiva ƴa ta ce, ita kam ni na haifeta tun da Shitu ne Mahaifinta, ko yau kake so za'a ɗaura maku aure, amma ita Maryam sai mun je mun nemo izini wajen iyayenta. Da mamaki gwaggo take kallon irin wannan karfin hali na daddyn Rimsha, wai ya basu mata, ya bari mana su je Nigeriar ƴaƴan suga iyayensu, kawai ya tashi ya yi masu miji a nan. Sir Safwan ne ya ce. "Wow this is so nice, ni dai na karɓi matar da aka bani, Maryam the name is so sweet". Mahhir ne ya karɓi zancen da cewa. "Okey brother nima na karɓa, kuma ita ma ƴar Maidugurin ce ko?". Harara gwaggo ta wurga mashi ganin yana neman tsokanar mummyn Rimsha, wato wasan kanin miji zai yi mata. Daddyn ne ya amsa mashi da "Yes ita ce ma ai cikakkiyar ƴar Maiduguri, saboda ita da uwa da uba duk ƴan can ne, ita kuma mummynsu Jehan ai ruwa biyu ce, babanmu ne kawai ɗan Maidugurin, mamanmu ƴar Niger ce". Ɗan matsowa saman table ɗin kaɗan Mahhir ɗin ya yi yana faɗin. "Aunty kina ji ko? Ki koyawa matar da Yaya ya banin nan abubuwan mutanen Maiduguri, dan nima na more". Ya yi maganar yana kallon mummyn Rimsha. Ita dai mummyn Rimsha tana ganin rayuwa a wajen waɗan nan masu jajayen kunnuwar, sam basu san me kunya ba, su yi magana son ransu abinsu, Allah mai iko. My readers kun dai ga Alex wato Mahhir cikin hukuncin Allah ya samu Adiva ƴar Maiduguri ko? Nasan baku manta da cewa uncle Shitu ɗan Maiduguri bane ba ko? To kamar dai wasa ga shi yanzu shi ma ya samu mata a familyn mumnyn Rimsha, sai dai mu ce Allah ya bada zaman lafiya. Sai hira suke yi suna dariya, kamar wasa Akila ta fara murkusoson ciwon ciki, tun tana dannewa dan kada kowa ya fahimta a cikin room ɗin, har ta ji ina ba zata iya ba, azaban ya wuce misali, kuka ta fara yi hawaye bobbiyu, sam bata san lokacin da ta sauka daga saman chair ɗin da take ba, sai dai suka ga ta durkushe kasa a saman gwiwowinta tana mai cigaba da dafe cikinta tana kuka. Kusan a tare dukkansu suka miƙe. Ai a dubu Aseef ya duka a gabanta tare da rikota yana tambayarta lafiya me ya faru?. Ban da kuka babu wani abin da take yi mashi. Areef ne ya kariso wajen tare da sa hannu ya ɗauketa cak suka fito parlourn. Da sauri gabaɗaya familyn suka biyo bayansu, Aseef kam kamar zai yi kuka shi ma. A saman doguwar sofa ya shimfiɗeta. Lion ne ya fara karisowa kanta yana kallon yadda take murkusoso kamar zata mutu, ga hawaye bibbiyu yana zuba daga idanuwanta. "Areef kawo mun ita word room bari na dubata". Cewar Lion ɗin, ya kai karshen maganar tare da wucewa gaba, saboda kada ma Aseef ya saka masu kuka, shiyasa zasu yi saurin dubata, dan ba ƙaramin aikinsa bane ya fara kuka kamar yadda take yi. Sake ɗaukarta izuwa room ɗin Areef ɗin ya yi, haka gabaɗaya family suka sake ɗunguma suka rufa masu baya. A saman bed ya shimfiɗeta. Matan QUADRUPLE ƴan gata, ana ji dasu, da Lion da gwaggo haɗe da Dr William ne suka fara ƙoƙarin dubata, duk dan kada Aseef ya tsayar masu da iyashege a wajen, shiyasa suka haɗu gabaɗaya a kanta, dan su shawo kan matsalar da wuri. Duk da haka sun gudu basu tsira ba, dan sai da Aseef ɗin ya rinƙa zuba masu rigima a kan dan Allah kada su bari ta mutu, sai da sir Safwan ya riko shi suka fita waje. Ita gwaggo abin da yake damun tunaninta ma a nan shi ne, ya zasu yi da Aseef idan aka ce ga Akila a labour room? Anya zai iya bari ta haihu ita kaɗai kuwa? Wannan ko za'ayi yaya da shi tare da ita zasu yi wannan haihuwa, tana kuka yana yi, ciwon kai kawai ma idan ta yi shiga tsananin tashin hankali yake yi, duk ya fita daga cikin hayyacinsa, ya bi ya ruɗe ko abinci baya iya ci, ina ga kuma aka ce haihuwa zata yi? Ai shikenan kuma ranar dai sai dai family su runtse idanu, dan zasu ga abubuwa kala kala, shi bai yarda Heartbeat tasa ta sha wahala ba, gara mashi shi ya wahala ita ta ji daɗi bawan Allah. Gwajin farko da su Lion suka yi mata suka tarar da ciki ne ma a jikinta na tsawon watanni almost uku, abin ya yi mugun basu mamaki, ga cikin nata babu laulayi babu komai, yanzu ma ƴar matsala aka samu cikin kamar yana son fita, shi ne yasa yake yi mata ciwo har haka, Allah mai iko, duk babu wanda ya san da ciki, shi kansa uban cikin bai san da zancen ba, kullum dai yana aikin yi mata kukan yana son baby's, ita ma sai dai ta yi ta Maganar har yanzu dukkansu matan QUADRUPLE babu wadda ta samu ciki, kullum cikin yin zancen suke yi, har ita kanta gwaggon kullum sai ta yi maganar da Dr William, ta ce mashi ƴaƴanta dai shiru har yanzu babu wadda ta sami ciki a cikinsu, sai dai ya ce mata ta yi hakuri lokaci ne, komai mai wucewa ne, Allah dai ya basu masu albarka, ashe ma Allah ya basu su ne basu sani ba, ai yau murna a wajensu ba'a magana, ga shi kuma gobe za'a rantsar da Lion, suna da babbbar shagali na walima da Areef and sir Safwan suka shirya, a wani katafaren diamond hall za'a gudanar da walimar, sai dai basu gayawa Lion ɗin ba, bazata suka shirya mashi kawai, sun shirya mashi abubuwa dayawa, kawai jiran goben nan suke yi ta zo, akwai shagali, ga hjy Rimsha First Lady da kanta, sai wani kara kyau ita ma take yi, ta yi wani dumur mur da ita, tana tafiya abubuwa suna juyi, kullum cikin rikita mana our Lion bawan Allah take yi, tasa ya yi ta biye mata kamar ba under 15 years da 32 years ba.........😂 Ganin Akila tana da ciki yasa gwaggo ta ce dukka sauran ma su zo a gwada su, irin wannan ciki na bazata haka, waya sani kila saura ma suna da shi. Da sauri Brr Naurat ta ce haka za'ayi kam, duk su zo a gwadasu. Da Anaya aka fara bayan gwaggon tasa an canzawa Akilar gado, ta ce Dr William ya ceci cikin Akilar kada ya fita, so yana ta fama da ita, shi kuma Lion ya koma gefe ya zauna yana tunani, shi dai har ga Allah baya son yara, bai shirya masu a yanzu ba, a cewarsa kuma babu ranar shirya masu ɗin, dan yara basu a tsarin rayuwarsa, ya kuwa yi sa'a dukka matan da aka gwadasu Rimshar ce kawai babu cikin a jikinta, Jehan and Anaya duk suna da ciki for two two months, cikin Akila yafi girma, ashe ba'a banza Jehan ta rinƙa yin zazzaɓi kwanaki ba, ashe cikin ne ita ma, ita dai Rimsha babu shi babu labarinsa, hakan yasa Lion ya yi farinciki ba kaɗan ba. Gwaggo kuma ta yi bakin ciki ba kaɗan ba, dan tana da burin son ganin yaran Lion and sir Safwan, saboda sune masu kama da masoyinta Dr William, tana son ta sake ganin an haifa mata Dr William again, tana son ganin yarantar mai kama da Dr William, hakan yasa sam bata ji daɗin rashin samun cikin Rimsha ba, bugu da kari tun ranar da ta haifi QUADRUPLE soyayyar Lion da sir Safwan suka fi ninkuwa a cikin zuciyarta, ta fi sonsu sama da kowa, saboda wannan kama dai da suka yi da fist love ɗin nata wato Dr William. Wani irin tattali da kulawa na musamman aka fara bawa Akila, Anaya and Jehan, ta kowani ɓangare samun kulawa na musamman suke yi, Aseef kam nasa ba'a magana, tamkar zai koma cikin cikin Akalar, saboda tsananin son da yake yi wa wannan ciki, kowani bayan ƴan lokuta kaɗan sai ya zo ya kwantar da kansa a saman cikin nata wai ko zai ji motsin babynsa, kowani lokaci aikin kenan, shi ma Areef hakan yake fama. Shi kam Lion ya rungumi Meesharsa sun cigaba da gashi abinsu, sai zuba love kamar wasu tattabaru, basu da damuwar komai. Josephine ta tare a part ɗin Aseef mai gabaɗaya, dan kula da Akila, saboda ita Josephine ta fi kaunar Aseef sama da kowa a cikin gidan, tana bala'in kaunarsa na wuce misali, shiyasa ma ta tare a part nasa, dan ta tabbatar da babu abin da ya samu Akila ko ɗigo. Washegari kamar yadda yake a dokance aka rantsar da Lion a cikin........ ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* E48 Washegari kamar yadda yake a dokance aka rantsar da Lion a cikin fadar shugaban kasa da yake a cikin white house, su ba'a EAGLE SQUARE suke rantsar da shuwagabanninsu ba, saboda they're DEVELOPED COUNTRIES, so komai nasu ba na kanana bane ba, basu wuce su ɗauki 10 mins wajen yin abin da zasu yi a wuce waje, saboda suna ɗaukar lokaci da mahimmanci fiye da komai a Rayuwarsu, basu wasa da lokaci, dan in ya wuce ya wuce kenan ba zai dawo ba, hakan tasa suke daraja lokacin fiye da komai nasu, sai dai kuma sun shirya party a cikin fadar shugaban kasar, wanda iya ƙusoshin gwamnati da iyalansu ne kawai zasu halakta, party ma ta shiryawa Lion ɗin wani shagalin, ga su Areef sun shirya mashi a gefe wanda bai san da shi ba. Dukka wasu masu muƙaman gwammanati sai da suka harci cikin fadar shugaban kasar. Kamar yadda kuka sani ne a bisa ka'idarsu Lion ko in ce shugaban kasar zai je wajen ne tare da matarsa, to hakance ta kasance, tare suka shirya da shi da Meesharsa. Duk da cewa kowa yasan da cewa Lion ya musulta, domin ya yi editing na komai da komai nasa ya cire sunansa na Romeo William Jacob izuwa Saif William, duk da sun san da hakan, dan kafin ya yi hakan sai da sanin ƴan jarudu kamar yadda yake a dokance, amma kuma abin ya yi matuƙar basu mamaki na ganinsa tare da Rimsha kuma cikin shiga irinta addinin musulunci, sun sha mamakin ganinta cikin complete shiga ta rufe komai nata. Sanye take da farar abaya mai bala'in kyau da tsada, sai ɗaukar idanu yake yi tsabar kyansa, ta yi rolling na veil ɗin abayar a kanta, sannan ta sanya face mask mai bala'in kyau irin na mijin nata a face nata, hannayenta da kafafunta dukka suna sanye cikin safa fara kal, ta yi kyau iya kyau duk da tana cikin face mask, watch da Lion ya ɗaura mata a hannunta kawai ya ɗauki idanun duk jama'ar da suke wajen, wani dankareren diamond watch ne wanda sai Allah kaɗai yasan a ina ya sawo mata shi, kuɗin wannan watch ɗin kawai ta isa ta sayawa mutun dankareriyar gida a malali Abuja, ga shi watch ɗin ɗan dai'dai da hannunta, duwatsun da aka yi wa wannan watch ɗin kwalliya ba ƙaramin ɗaukar idanu kyallinsu yake yi ba, daga wuyarta zuwa kunnenta dukka wasu shegun gwala gwalai ne wanda Josephine ta sanya mata, dan ita Josephine ɗin ita ce ta yi mata kwalliya yau, sai tashin kamshin perfume ɗin Lion ɗin take yi, sai dai kuma ta kara zama baka sosai a cikin masu jajayen kunnuwar. Shi kuwa Lion sanye yake cikin wasu shegun tsadaddun suit masu bala'in kyau launin white color irin kalar kayan jikin Rimshar, ya tara kyakkyawar dark black curly hairnsa a baya ya ɗaure, sai face nasa ta fara fitowa sosai, sai dai kuma duk wannan uban kyau da ya yi fa fuska a ɗaure tamau kamar hadari, yau ya sanya siririn glass mai bala'in kyau a face nasa, sannan ya sanya face mask, cover shoes ce a ƙafarsa, kuɗin duwatsun dake jikin cover ɗin nan kawai ya isa ya buɗewa mutun katafaren mall mai cike tab da kaya, kusan takalmar kafarsu iri guda dana Rimsha, ita ma cover ce mai kwalliyar duwatsu masu bala'in kyalli a jiki, sai dai nata na mata ne nasa na maza, komai na jikinsu from up to down farare ne kal kal, tsadarsu kuwa baki bai isa ya faɗi kuɗinsu ba. Tun da suka shigo white house Lion yake ruke da hannunta, ya kuma ɗan mannata da jikinsa dan ma kowa ya sani cewa ba son wasa yake yi mata ba, kuma ita Rimsha ma bata iya tafiya sosai, kafarta yana ciwo, shi ne ma yasa Josephine ta ce ta sanya cover shoe plat wanda Lion ɗin ya saya masu a tare, da ita Rimshar a yarintarta high heels zata saka, ita da kafa yake ciwo, Lion ya ragargajeta jiya, hakan yasa bata iya tafiya sosai, karfin hali ne ma kawai irin nata, da farko ma cewa ta yi ba zata je white house ɗin ba, sai da ya lallaɓata sannan ta yarda da cewa zata je. Ita dai mummyn Rimsha kunya abin yake bata, yadda Lion ya wani rungume matarsa kamar ance za'a kwace mashi ita, gwaggo kam ko a jikinta, hannunta ita ma yana a cikin na Dr William kamar wasu taurari, kusa hasken fatar Dr William dana gwaggon ɗaya, da kaɗan ya fita, sun fito a iyayen QUADRUPLE ɗin da gaske, sai haskawa suke kamar wasu sabbin taurari. Sam mummyn Rimsha taki yarda daddy ya riko hannunta a bainnar nasi, sai dai suka nufi cikin a jere kawai, saboda tana kunyar su brr Naurat. Shi kam Aseef da akwai dama ma ai ɗaukar Heartbeat cancak zai yi ya saɓata a shoulder ɗinsa su shiga ciki, dan baya son ta sha wahala, kada ta jijjiga mashi baby. Areef da Jehan ma haka suka jero gwanin birgewa, yana ƙanƙame da hannunta. Sir Safwan da Maryam haka suka jera rike da hannun juna, duk kuma shirin Josephine ne, Uncle T tare da Aafia, Mahhir tare da Adiva, Dr Salman and Brr Naurat suna rike da hannun Pinky, Mark tare da Anaya, sai aikin turo baki Anaya take yi wai bata son zuwa, da kyar ita ma ya lallaɓata ta yarda ta biyo shi. Tamkar wasu taurari haka familyb Dr Salman and Familyn Dr William suka shigo white house, a kalla dankara dankaran motoci sama da guda hamsin ne suka ɗaukosu daga gida, hakan zai tabbatar maka da Lion ya shirya abubuwa sosai, dan motocin gabakiɗaya sababbi ne gal gal, babu tsoho na gida ko ɗaya a ciki. His Excellence ma yazo taya Lion murna, kuma dama dole ya zo, dole ya kasance yana wajen, dan shi ne zai miƙawa Lion ɗin mulkin. Manyan shuwagabannin kasashe da dama sun halakci taron rantsarwar. An kawata white house ɗin nan na wuce misali, baki ya yi kaɗan ya zayyana yadda kawatuwarsa ya kasance, har shi kansa speaker room dake a cikin fadar shugaban kasar, komai sai dai mu ce masha Allah, billions of dollars aka narka wajen sake kawata white house ɗin, saboda sabon shugaba zai shi ga, tsadaddun motocin da aka zuba na fitar President a cikin white house ɗin ma kawai kuɗin su ya kai kuɗin budget ɗin wata ƙasar, dollars sun yi kuka, sun ci uwarsu a wannan lokaci, ita kanta kujerar da His Excellence Saif William zai zauna kuɗinta ya fi kuɗin budget na state. Dollars da aka kashe wajen shirya kujerun zaman bakin da zasu taya Lion murna ma kawai ta isa wata kasa ta inganta kanta, shegun tsadaddun kujeru aka zuba, bafa wani zama zasu yi su jima ba, amma a haka aka narka waɗan nan shegun dollars ɗin kawai dan a kawata wajen, abin dai baki ya yi kaɗan ya faɗe shi. Wani irin azababben fitinannen daddaɗar kamshin ne yake tashi a gabaɗaya ilahirin white house ɗin, ga wasu jiga jigan security's masu jini a jika dake aikin fesa perfume ta ko'ina. Dubbannin zaratan sojoji masu jini a jikka ne suka kewaye ko'ina a faɗin cikin white house ɗin, ta ko'ina idan ka juya kaki zaka gani rike da jiga jigan bindigu masu rai da lafiya, ƴan'sanda ta ko'ina suna shawagi, ga wasu haɗaɗɗun helicopters da suke shawagi a sararin samaniya dan kara tabbatar da tsaro, apart from helicopters da akwai wasu na'urori da suka tasa sama dan kawai su tattabar da tsaro, ga wasu kananan jirage masu amfani da computers, duk wasu Generals na sojoji sun hallara a wajen, a ɓangaren ƴan'sanda ma I.G da D.I.G na kasa bakiɗaya ma sun bayyana a wajen. Duk wasu Ministers sai da suka zo, ga manya manyan lauyoyi ma dukka a wajen. Kowa daga cikinsu ya samu waje cikin tsadaddun luntsuma luntsuman sofas da aka jeresu a cikin fadar suka zauna, daga gefe guda kuma shuwagabannin kasashen da suka zo taya shi murna ne a wajen. Dukkansu suna saman sofas Lion and Rimsha ne kawai suka hau saman stage ɗin da aka kawata shi da ado mafi tsada a duniya, shi kansa speaker da Lion zai yi magana a wajen da diamond aka yi shi. Meesharsa tana gefensa, ga wasu jiga jigan lauyoyi ta kotun duniya da suke tsaye a gefe da gefensa, sanye suke cikin kayan lauyoyi masu kyau da tsada, ga su jajir dasu kamar ka taɓa jini ya zuba. Ta ko'ina hasken Cameras wanda ƴan jaridu suke ɗaukarsu ne yake tashi, daga ɗan bayansu Lion ɗin kuwa lieutenant General na sojoji ne, sai Major General and Brigadier General, su ne suka tsaya a bayansa ta gefe guda rike da jiga jigan bindigu, ta gefe guda kuma I.G and D.I.G na kasa ne tsaye a wajen. Wani hamshakin shararren lauya ne ya kawo wa Lion wata takarda wanda zai karanta a wajen domin ya sanar da al'umma irin alkawarin da ya yi masu da kuma aikin da zai yi masu, takardar tana kunshe da abubuwa sosai na bayani da zai yi. Sai dai kuma, ko da suka kawo mashi bai karɓa ba, ya ɗaga masu hannu a kan baya buƙata. Rimsha ta ƙanƙame shi sosai saboda tsoron waɗan nan jiga jigan sojoji dake tsaye a bayansu, ga taron jama'a dukka idanu naa kansu, hakan yasa ta kasa sukuni, baiwar Allah bata saba ba, duk sai ta shiga damuwa ta ƙanƙame shi sosai, shi ma ɗin bai saki hannun nata ba duk da sun hau saman stage ɗin, yaki sakinta, dan yasanta da shegen tsoro. Har mamaki jama'a suke yi, waɗan da basu gani su kyale har sun fara tofa albarkacin bakinsu, sai maganarsa ake yi, na farko ga shi sun ra'ina matar tasa, ƴar ƙarama da ita, na biyu ga shi sai biye mata yake yi, ya wani ƙanƙameta kamar sun ce zasu kwace mashi ita, hakan yasa ƴan jaridu suka kara ɗaukarsu hotuna sosai da kyau da kyau dan su sami abin yaɗawa a tashoshinsu. Live aka kunna a fadar, gabaɗaya faɗin ƙasar har ma da na ketare ana kallon me yake gudana, kowa ya sha ruwan mamakin kin karɓar takardar nan da Lion ya yi, hakan tasa kowa ya nutsu domin ya ji menene dalilinsa. Wani hamshakin alkali ne dake tsaye a wajen nasa speaker ne ya fara magana cikin ƙwararriyar turancinsu wadda tamkar a bakinsu aka kerata. Sallama irin tasu ta Kristen ya yi kafin ya fara da karantowa Lion ɗin abubuwan da ya shafi doka da kuma alkawarin da zai yi ma'ana ya fara karanto mashi cewa "Ni Saif William Jacob, a rana irin ta yau, a gaban dubbanin al'umma, na yi alkawarin rike kasa ta da gaskiya da amana, na yi alkawarin kawo mata dukkan wani cigaba, na yi alkawarin tallafawa talakawa da kula da rayukansu". Irin abubuwan da alkalin yake karanto mashi kenan, Lion ɗin yana maimaitawa cikin wannan cool voice ɗin nasa, tamkar baya son yin magana, da alama ma duk jikinsa a mace take, kuma hakan ce, zuciyarsa tana buga mashi, yana jin tamkar wani abin zai faru da shi, hakan ce ta kashe mashi jiki sosai. Gabaɗaya ko'ina ya yi tsit, tamkar babu kowa a cikin wajen, duk sun kasa sunne suna sauraton zazzaƙar muryarsa yana maimaita abin da wannan alkalin yake faɗa. Bayan wannan alkalin ya gama jawabinsa, sai aka buƙaci da Lion ɗin ya faɗa da bakinsa abin da yake so da kuma muradin yi wa kasarsa, wanda kuma dama shi ne a rubuce a jikin takardar da wancan lauya na ɗazun ya bashi yaki karɓa, shi kuma yaki karɓa ne domin ba'a aiki a takarda yake da buƙata ba, baya son kowa ya rubuta mashi abin da zai yi, zai faɗi kayansa da bakinsa, kuma zai jaddada hakan a aikace da izinin Allah, hakan yasa yaki karɓar takardar da lauyan ya bashi, sai kawai ya gyara tsayuwarsa tare da kara matso da Rimsha jikinsa sosai, sannan ya fara magana a daf bakin speaker tasa cikin kwarewa tare da sanyayyar muryarsa. Daga nan ya buƙaci daddyn Rimsha ma ya zo ya yi nasa alkawarin a matsayinsa na vice president. Haka kuwa aka yi, suka iso wajen shi da mummyn Rimsha, duk da cewa face ɗin Rimsha na sanye da face mask, amma tsabar gulma irin na jama'a sai da suka iya gane cewa sir Nawazuddeen da mummy iyayenta ne, dan kuwa duk wanda ya ga kwayar idanun mummyn Rimsha ya ga na Rimsha sai yasan jini guda ne, yanzu duniya an daina kiwon dabbobi, an dawo kiwon mutane, tsabar gulma da sa ido har sun iya gano cewa vice president dai mahaifin First Lady ce, abin ya yi mugu mugun basu mamaki, wasu kuma abin ya burgesu sosai, musamman ƴan mata, sun ji matuƙar daɗi yadda Lion ya kasance a tare da surkunayensa inuwa ɗaya, a haka ma basu san cewa uncle nasa bane, su dai sun gansu kawai, kuma basu isa su tunkari wani daga cikin familyn da nufin su tambaye shi ba, sai kawai suna ta canki canka. Cikin ƙwararriyar turanci daddyn Rimsha ya fara magana, dayawa daga cikin jama'ar wajen sun yi mamakin yadda aka yi harshen daddyn Rimsha bata da banbanci data Lion ɗin wajen magana, turancinsu iri ɗaya, ga shi dai suna yi wa daddyn kallon bakin fata, basu san cewa shi ma daddyn harshen nasa duk irin nasu bane, zaman Nigeria yasa ma harshen ta fara sauyawa, domin zamansa a Nigeria yaruka dayawa sun hau kan harshen, ba dan haka ba ai da duk ɗaya ne. His Excellence ne ya kariwo wajen a in da ya miƙawa Lion ɗin hannu suka gaisa kafin daga bisani ya miƙa mashi takardun gwammati, waɗan nan files ɗin su ne suke nuna cewa ya miƙawa Lion ɗin mulki kenan kamar yadda doka ta tanada!! Sai kallon juna suke yi, His Excellence dai nasa kallon kamar da biyu, kamar ya shirya wani abin, shi kuma Lion nasa kallon tamkar wanda yake isar wa da kakan nasa sakon cewa lokacin wasa ya fara. To babbar magana, kaka da jika ne fa.........🥱 Bayan sun kammala duk wasu alkawaruruka ne manyan manyan shuwagabannin kasashen da suka halarci taron suka fara isowa wajen domin su gaisa da His Excellence Saif William and His vice Sir Nawazuddeen. Wata Prime Minister kasar England ce ta kariso wajen, kyakkyawar macece mai ɗan shekaru da a kallah zasu kai 40 to 45. Tana zuwa ta miƙawa Lion ɗin hannu domin su gaisa, dama kunsan su haka al'adarsu take, hakance taya murna, ƴan jaridu sai kashe masu hotuna ake yi, ga live kowa yana ganin me yake gudana a cikin fadar. Miƙa mata hannunsa Lion ɗin ya yi da nufin su gaisa, kamar a mafarki ya ji Rimsha ta saki ɗayar hannun nasa da ta rike tana ƙoƙarin juyawa ta bar wajen. Ai kuwa wannan Prime Minister ta kawo hannunta kenan zata rike nasa hannun ya yi saurin kaucarwa ya riko hannun Meesharsa dake ƙoƙarin barin wajen, ya bar hannun Prime Minister a saman iska tana kame..........(😂 Gaskiya Lion da Rimsha ƴan duniya ne, ya shanya hannun mata basu gaisa ba🤔😂) Kamo hannun Rimsharsa ya yi tare da jawota jikinsa yana kallon idanunta. Cikin harshen Hausa ya furta mata. "Ina zaki je?". A dubu ɗari ta yi wani irin zaro idanu waje, mamaki ne ya bayyana a saman face nata, ya aka yi ya iya Hausa?. Ba shakka yana jin Hausa tun bai je Nigeria ba, yana jin yaruka da dama waɗan da suka ɗaukaka a duniya, sai dai Hausar ba sosai ba, sama sama yake ji, and kuma duk cikin QUADRUPLE shi ne kawai yake jin Hausar, su Areef basa ji, bai taɓa magana da yaren da wani ba sai yau da ya yi mata. Ganin ta tsare shi da idanu ne yasa ya ɗan yi kasa da face mask nasa ya hura mata iskar bakinsa a idanun nata. Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce. "Noorish shi ne zaka gaisa da wata ina wajen ko? A gabana". Ta yi mashi maganar cikin harshen Hausa ita ma. Mayar da face mask nasa ya yi yana faɗin. "Ki yi mun magana da English, Hausar kaɗan na iya, yanzu haka ban ji me kika ce ba". Ya yi maganar cikin harshen turanci. Hararar wasa ta wurga mashi, dama ba wani kwarewa ya yi a Hausar ba, kawai neman magana ne. Ganin yawan hasken cameras a saman face nasu ne yasa ya ɗan saketa tare da riƙo hannunta suka juya ga jama'a, sai a lokaci ya fahimci ashe wai ya ci mutuncin Prime Minister kasar England daya barta shanye da hannu a saman iska tana jiran su gaisa, kawar da kansa daga kallon jama'a ya yi abinsa, dan shi a kan Rimsharsa sun daɗe basu ce duk abin da suka ga dama ba, matsakarsu ce, dan shi bashi da lokacin shirmensu. After some minutes an kammala taro za'a wuce wajen cin abincin da aka kawata aka shirya shi shiri na musamman a cikin wani katafaren hall dake a cikin fadar, kujerun da aka tanadawa His Excellence da First Lady ya yi bala'in ɗaukar hankali jama'a a wajen, abin ya kawatar. Zama suka yi cikin class da izza suka fara cin abinci, sojoji ne ta ko'ina suke serving nasu abincin. Sai da kowa ya ci ya ƙoshi, abincin da aka shirya masu kawai ya kai kuɗin budget na state, an kashe kuɗi ba karya. Bayan an kammala komai jiga jigan sojoji ne suka raka su Lion zuwa gida, dan ba yau zai dawo white house da familynsa ba, a cewarsa su barshi ya sa rana tukun nan. Bayan motocinsu sun tashi sai motocin jiga jigan sojoji sama da guda goma suka rufa masu baya, a can gaba kuma motocin ƴan'sanda ne suka wuce gaba, ta ko'ina jiniya aka sake tamkar filin yaki zasu tafi. Suna isa gida family suka ɗunguma suka wuce cikin parlourn kamar yadda suka fito, jiga jigan sojojin nan kuwa suka kewaye gidan ta ko'ina, ga jiga jigan bindigu a hannunsu, abin dai ba'a magana. Bayan sun shiga parlourn ne Lion ya ce "Where's uncle? I want us to discuss something". Ya yi maganar yana kallon su Areef da suke ƙoƙarin zama a saman sofas. Nan fa kallo ya koma kallon kallo a cikin parlourn, ina daddyn Rimshar yake to? Babu shi kuma babu mummyn Rimshar ma. A dubu ɗari Lion ɗin ya juyo da kyau tare da sake hannun Rimshar yana bin familyn da kallo, sai juye juye suke yi suna neman daddyn. A hanzarce Areef ya ciro wayarsa, jikinsa har tana kerma wajen kunna hasken screen ɗin wayar, da kyar ya iya laluɓo number daddyn domin ya kira, a tunaninsa ko dai daddyn yana wani waje mafi kusa ne, dan yasan babu familyn da ya rage a waje bai shigo cikin parlourn ba, sai dai idan a white house suka baro daddyn. Sai dai kuma ko da ya kira number daddyn, a kashe wayar take, tamkar zai yi hauka ya sake gwada kira, amma a kashe, shi ma Aseef a dubu ya saki hannun Akila tare da fito da nasa wayar. Shiru Lion ɗin ya ɗan zuba masu idanu yana kallonsu, wani irin azababben sara mashi kansa ta fara yi, ji yake yi ma wani irin jiri tana ɗebarsa, cikin hanzari ya ce su kunna mashi Tv da yake a parlourn bari ya ga lokacin da aka rantsar da su da duk abin da ya faru a wajen, tun da live ce, so tana nan kuma yasan gidan jaridu zasu yi ta maimaitata ne. Uncle T ne ya kunna Tvn, gabaɗayansu sun kasa zama, suna tsaye cirko cirko, kowannansu tashin hankali ne ya fara bayyana a saman face nasa. Sun kuwa yi sa'a, suna kunna Tv suka fara kallo daga in da suke cin abinci a dining hall na white house ɗin, kuma a lokacin daddyn Rimshar yana tare da su, sai bayan sun kammala cin abinci ne wani mutun mai kama da Lion ɗin sak ya zo ya ja daddyn Rimsha gefe suka fita waje, camera ta ɗaukesu, sai daddyn ya tafi tare da Mummyn suka jera a tare, tabbas Lion ɗin ne ko ace da face ɗin Lion ɗin aka yi amfani, kunga kuwa an ɗaure shi ne, saboda koda maganar ɓatar daddyn Rimshar ta bayyana to idan aka duba cameras da komai da komai za'a ga daddyn Rimsha tare da Lion ɗin suka fita cikin fadar suka keɓe waje guda, alhalin kuma ba Lion na gaskiya bane, tsafi ce kawai ta yi aiki a wajen, sai dai abin ban mamakin a nan shi ne ta ya aka yi suka fita da shi daga cikin white house ɗin, duk da abu ne na tsafi kuma Kiristoci ne cike a wajen ma'ana za'a iya rufe masu ido, amma abin da mamaki gaskiya, sannan ya aka yi sam su Lion ɗin basu lura da cewa daddyn baya a tare da su ba har suka dawo gida? Duk da cewa ma jama'a suna cike sosai a wajen, amma da mamaki ace family basu lura daddy da mummy basu a tare da su ba!. Tsabar shiga tashin hankali wani irin azababben sarawa kan Lion ɗin ya yi, shi dai yasan bai kira daddyn Rimsha sun fita gefe ba, ga camera kuma ta nuna shi ne ya kirasa, yau ake yinta kenan, wannan shi ne bala'i, ya zamar masu dole su ɓoye batun ɓatar daddyn, idan ba haka ba Lion ɗin yana cikin tsaka mai wuya, to wai wani shafaffe da mai nema ya ɗauki daddyn? Ina kuma suka kai shi? Me zasu yi mashi? Allah sarki mummy baiwar Allah, bata san komai ba. Nima Princess Teema ban san komai ba, Wayyo Allah na, yau bani ba shan Maltina, family suna cikin wani hali, ai bani ba zaman lafiya.....😭🥲 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* E49 Gabaɗaya jama'ar parlourn sai kallonsu ya koma a kan Lion ɗin. A ruɗe gwaggo ta ce. "Saif ba ga shi nan a tare kuka fita da Nawazuddeen ɗin ba? A ina yake to?". Dr William ne ya sake jefa mashi wata tambayar na cewa "Son ina uncle ɗin naku yake?". Yana rufe baki Aseef ya karɓa da cewa. "Ga shi a tare kuka fito kuma har da mum, to ina yake?". Areef kam shiru ya yi yana kallon ɗan uwan nasa, domin shi ya fahimci komai, ko ba'a gaya mashi ba ya gane matsalar, ya yi amfani da kwakwalwarsa ne wajen karantar yanayin da Lion ɗin yake a ciki, a nan ne ya fahimci cewa tabbas wanda ya fita da daddyn Rimsha dai ba Lion na gaskiya bane, kuma ba sir Safwan bane, to waye ne? Wannan shi ne abin da Areef bawan Allah yake ta ƙoƙarin iya ganewa. Shi kuwa Lion tsabar tambayoyi da suke jefa mashi da ruɗewar da iyayen nasa suka yi tasa bai san lokacin da ya yi karyar da bai taɓa yin irinta ba, bai san lokacin da ya ce masu shi ne ya fita tare da daddyn Rimshar ba, ya ce masu a tare suka fita mantawa ya yi ne, ya aiki daddyn wani waje ne, dan haka su kwantar da hankulansu, kowa ta wuce bedroom nasa. Jikake gabaɗaya parlourn ta ɗauka da sauke nauyayyar ajiyar zuciyoyin family, hankula sun kwanta da jin cewa shi ne ya aiki daddy, Areef ne kawai yanayinsa bata canza ba sai sir Arvin da yake kokwanton akan amsar da ɗan uwan nasa ya bayar. Shi Areef abin da yasa yanayinsa bata sauya ba, saboda ya fahimci gaskiyar al'amarin tun farko, shi kuma sir Safwan duk da cewa ba tare suka taso suka girma da su Lion ɗin ba, amma yana iya karantarsu a wani hali suke ciki, sannan yana iya gane maganarsu ta dai'dai da ba dai'dai ba, bugu da kari bugawar zuciyoyinsu yana tafiya ne a tare, idan baku manta ba su dukkansu idan ɗaya yana cikin damuwa ko wani abin ya same shi, to ba shakka zuciyoyinsu suna bugawa a tare, so tabbas zuciyar sir Safwan tana yi mashi kuna kamar yadda na Lion ɗin take yi mashi, hakan yasa yake tantanma a kan amsar da Lion ɗin ya bayar, ya dai yi shiru ne kawai bai yi magana ba, saboda iyayen nasu su samu nutsuwa da kwanciyar hankali. Haka suka lallaɓasu kowa ya wuce cikin bedroom nasa. Shi kuma Lion sama ya wuce wajen ɗakin bincikensu. Ko da ya je ɗakin ma ya kasa iya taɓuka komai, jikinsa duk a mace, zama kawai ya yi a saman sofa yana tunanin abin da yakamata ya yi, tsabar shiga tension ma bai san lokacin da ya shigo ɗakin binciken nasu ya baro Rimsha a parlourn ba, shap ya mance da ita, ya wuce kawai abinsa, hankalinsa ta yi gaba. A tare sir Safwan da Areef suka shigo cikin room ɗin. A saman sofa dake fuskantar na Lion ɗin suka zauna, ya zamana suna fuskantar juna. Zubawa Lion ɗin idanu sosai suka yi suna kallonsa. Areef ne ya yi karfin halin cewa. "Lion menene gaskiya? Su waye suka sace uncle? Me kuma ya haɗasu da kai? And ya aka yi ya zama kai ne mutun na karshe da ya fita tare da uncle ɗin daga nan ba'a sake ganinsa a wajen taron ba?!!". Nisawa Lion ɗin ya yi, shiru ya yi masu na akallah 10 mins, har sun fidda ran zai yi magana, sai kuma suna ji shi in a low voice yana faɗin. "Abin da na gaya maku shi ne gaskiya, tabbas ni na aiki uncle wani waje, zaku iya tafi ku rabu da ni pls". "No Saif, abin da bakinka yake faɗa daban, abin da zuciyarka yake amsawa daban, tabbas bugawar zuciyarka da amsar da yake a bakinka ba abu guda bane, ka manta da cewa muna jin bugun zuciyar juna ne?". Cewar sir Safwan. Shiru Lion ɗin ya yi bai sake ce masu ko uppan ba, dan bashi da abin da zai sake ce masu kuma. "Lion please tell us the truth, saboda mu samu nutsuwa, kuma mu san a wani mataki muke". Cewar Areef. Aseef ne ya katse masu magana ta hanyar shigowa cikin ɗakin bakinsa a ɗauke da sallama. Saman sofar da Lion ɗin yake shi ma ya zo ya zauna suna fuskantar juna da su Areef Cikin dakiya da jarumta Aseef ɗin ya fara magana. "Lion lallai akwai abin da ya sami uncle, saboda ina jin zuciyata tana bugawa da sauri sauri, da alama kuma zuciyarka ce mai wannan bugawa da tasa nawa take bugawa a haka, kuma nasan babu shakka haka sauran ƴan uwana suke ji ko Areef?". Ya yi maganar ne cikin tsayayyiyar murya da babu shagwaɓa ko kaɗan a cikinta, kallo ɗaya zaka yi mashi kasan yana cikin tsananin damuwa na wuce misali. Kawar da kai Lion ɗin ya yi yana faɗin. "Aseef duk abin da ka faɗa zata iya yiwu kana jin hakan, amma ba shi ne zai sa ka yi tunanin cewa bani ne na aiki uncle ba, yanzu ka je ka kwanta ka huta". Ya kai karshen maganar tare da miƙewa daga samar sofar da yake. "Lion tabbas a wannan karon abin da kake gaya mana ba hakan bane ba, tabbas ina ji a jikina akwai abin da kake ɓoye mana". Cewar Aseef. Lion ɗin yana ƙoƙarin sake yin magana kamar daga sama suka ji voice ɗin Rimsha a bakin kofa tana faɗin. "Yah Aseef yana da gaskiya, wlh Noorish akwai abin da ka ɓoye mana, wanda ya fita tare da daddyna ba kai bane ba, wlh ba kai bane". A tare suka juyo da kallonsu a kanta, abin ya yi matuƙar basu mamaki da al'ajabi, Lion bai taɓa tunanin zata gane ba shi bane ba ya fita a tare da daddyn. Hawaye ne yake bin saman lallausan kumatunta, hawaye bibbiyu take yi, ta tsaya a bakin kofar shigowa tana kallonsu, while suma ita suke kallo. "Rimsha waye ya ce maki ba Lion bane? Shi ne fa, jeki ki kwanta ki huta, yanzu kinga muna magana ne a kan siyasa, daddynki zai dawo anjuma, Lion ne ya aikesa". Cewar Areef. Kara tsananta gudu hawayen da yake a saman kuncinta ya yi, tamkar am buɗe ruwan famfo, gabaɗayanta a firgice take, ta shiga damuwa na wuce misali. "Yah Areef wlh ba Yah Saif bane ya fita tare da daddy, wlh ba shi bane ba, ni ina jin a jikina sace daddyna aka yi". Da kyar take iya yin maganar nata. Sir Safwan zai yi magana Lion ɗin ya ɗaga masu hannu alamar su yi shiru. Tsit suka yi suna kallonsa. Calmly ya fara magana. "Meesha ba zata yarda da abun da zaku ce mata ba, saboda abin da take faɗa shi ne gaskiya, so kune zaku yarda da abin da take gaya maku, tabbas bani bane na fita da daddynta, na faɗawa su momma ni na fita da shi na aikesa ne kawai dan su sami kwanciyar hankali, copy nawa aka yi, ban yi mamaki ba da Meesha ta iya gane bani bane, dan tun da a labarin da momma ta bada a time da take gaya mana meyafaru da ita a baya, kowa na parlourn bai iya gane cewa ƴaƴan momma masu blue eyes biyu bane, Meesha ita kaɗai ta iya gane wa, bugu da kari ita kaɗai ta iya rabeni da Safwan da kallo guda, wanda ko iyayenmu basu iya rabemu da kallo guda ba! Ko ita kanta Cherish da ta rayu da Safwan tsawon shekaru talatin da biyu bata iya rabeni da shi da kallon farko ba, amma Meesha da kallon farko ta banbanta mu, tun daga nan ni kam na yardanwa kai'na Meesha a ko'ina zata iya fitarda ni, koda kuwa masu kama da ni sun kai dubu, to tabbas zata fitar dani daga cikinsu, ban san wani irin shaida ta yi mun a jikin nawa da yasa take iya cireni a cikin miliyoyin mutane ba". Ya kai karshen maganar yana yi mata alama da hannunsa a kan ta zo. Da sauri ta kariso cikin ɗakin izuwa gabansa ta tsaya tana mai cigaba da kukanta. Jawota jikinsa ya yi yana faɗin. "Kukan ya isa haka, zauna ki gaya mun ya aka yi kika san bani bane na fita a tare da daddynki". Yana maganar yana goge mata kwallah. Kwantar da kanta a saman Lion chest nasa ta yi tana wani irin shesshekar kuka mai taɓa zuciyar mai sauraro, ta kasa iya sake buɗe baki ta yi magana, ɗazun ma da kyar ta iya yin maganar. "Is okey my Meesha, kukan ya isa haka, uncle zai dawo gare mu nan bada jimawa ba, keep praying for them". Yana magana yana mai cigaba da goge mata hawayen, duk ta kara ɗaga mashi hankali, ya shiga cikin tsananin damuwa over, wani irin sara mashi kansa take yi na wuce misali, sam baya son ganin damuwarta. "Noorish ina jin kamar wani abin zai faru da mummyna". Ta faɗa cikin shasshekar kuka tare da sarkewar murya. "Babu abin da zai sameta, da ita da Uncle duk suna da riko da addini sosai, kuma waɗan da suka ɗaukesu mutane ne mushirikai, so ki kwantar da hankali, ki sani idan suka yi wasa wannan ɗaukar uncle ɗin da suka yi zai iya zama sanadiyar rugujewarsu, domin ayar Allah ta wuce wasa, ya isa haka kukan nan, jeki ki kwanta a ɗaki ki huta kin ji? Bari mu fara bincikar a ina suke, da ban yi niyar shiga office this week ba, amma saboda uncle yau ba sai gobe ba zan fara aiki, so keep praying for us my pleasure". Yana magana yana shafa kanta izuwa bayanta. Su Areef kam sun mayar dasu tamkar wasu Tv, sai kallonsu suke yi, sir Safwan kam duk sai ya ji wlh ba zai iya hakuri ba, dole shi ma a ɗaura mashi aure da Maryam ɗinsa, dan gaskiya shi ma yanzu a hannu yake, ya gaji da kallon irin wannan madarar soyayya da ƴan uwansa suke zubawa a tare da matansu, ga shi shi ne babba amma har matar Aseef da Areef suna da ciki shi ko auren ma bai yi ba bare ya yi tunanin ko ya zura kwallo a raga. "Noorish ka barni a tare da kai, ka barni kusa da kai, Allah ba zan iya zuwa ɗaki na kwanta ba, ni dai zan zauna da kai". Kasa kasa ya ce "Haka kike so?". Kai kawai ta gyaɗa mashi alamar e haka take so. Ɗan rungumarta da kyau ya yi yana faɗin. "To shikenan ki zauna a tare da ni ɗin, amma ki dai'na kukan nan, promise me that ba zaki sake zubar mun da hawayen nan naki mai tsada ba". Zuro hannayenta ta yi ta bayansa ta ƙanƙame shi da kyau tana faɗin. "I promised you, ba zan sake hawaye ba". Ɗan duƙo da kansa kasa kaɗan ya yi ya sumbaceta a 4head nata. Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke tare da ɗago da kanta, har lokacin yana duke a kanta, hakan ya bata dama ta sumbaci lallausan lips nasa. Kasa hakuri sir Safwan ya yi har sai da ya ce. "Wai ni kam Saif me ka mayar damu ne?". Sai a lokacin Rimshar ma ta tuna da cewa ashe QUADRUPLE nasu suna wajen, wani irin kunya ne ta ji ya kamata, nan take ta hau ɓoye fuska a jikin Noorish ɗin nata. Shi kuwa Lion kallon ina ruwanka ya wurgawa sir Safwan ɗin kafin ya ɗan raba jikinsa da nata, sannan ya riko hannunta suka isa gaban computers da suke a cikin room ɗin. Zama ya yi a saman ɗaya daga cikin chairs dake a gaban computers ɗin, sannan ya ɗaurata a saman laps nasa tare da kwantar da kanta a saman Lion chest nasa, in a low voice ya ce. "Kwanta ki yi barci, kada fa ki tashi, zan yi aiki ne". Hannunta ɗaya ta kai ta saƙalo ta bayan wuyarsa tare da gyara kwanciyar tata tana faɗin. "In kwanta dai in yi ta kallon kyakkyawar fuskar mijina domin na haifi mai kama da kai". Jin ta kawo zancen haihuwa yasa ya kawar da zancen da cewa. "Ta yaya aka yi ne ma kike iya banbanta ni da kowa Meesha?, ya aka yi kika gane bani bane na fita tare da daddynki?". Ɗayar hannunta ta ɗaura a saman lallausan kumatunsa tana shafawa a hankali ta fara magana in a cool voice. "Wanda ya fita a tare da daddyna yana da wani tambari na wani zane a wuyarsa, kai kuma baka da shi, sannan wanda ya fita a tare da daddyna sajensa bai kai naka kwanciya ba kuma bai kai naka baki da yawa ba, sannan kuma fuskarsa bata da kyau duk da yana kama da kai, da kallo ɗaya zaka yi mashi ka fahimci face ɗin sanyata ya yi, dan bata ma zauna dai'dai da jikin wanda aka sakawa face ɗin ba, jikinsa ma bata da kyan gani, kuma yana da wani huji kamar sami a wajen kunnensa ta sama, and kuma a hannunsa na dama akwai wani abin hannu wanda kai sam baka saka ire iren su, iya watch kawai kake ɗaurawa". Tun da ta fara magana ya tsareta da idanu yana kallon ɗan bakin nan nata, ba ƙaramin mamaki ta bashi ba, lallai tana da kaifin ƙwaƙwalwa, yanzu da kallo ɗaya ta yi wa wannan guy ɗin irin wannan sanin haka? Har ta san da akwai wani abu a hannunsa daya ɗaura, sannan har tasan da wani ɓuli ta wajen kunnensa, duk da suit da yake a jikin guy ɗin har ta iya gane akwai zane a wuyarsa, lallai tana da kaifin kwakwalwa, bai kamata ya bar kwakwalwar nan tata ta tafi a banza ba, dole ya mayar da ita school, dan shi kansa zata taimaka mashi a kujerar da yake kai a yanzu, ga shi yanzu ma ta taimaka mashi, domin bai lura da akwai zane a jikin guy ɗin ba, bai kuma lura da akwai wani abu a ɗaure a hannun guy ɗin ba, yanzu ta taimaka masu sosai, dole ya yi bincike a kan wannan zane da abin hannu, yasan ba shakka zasu taimaka mashi. "You're special my Meesha". Ya faɗa tare da kunna computer dake a gabansa. Ganin ya kunna computer ne yasa Areef and sir Safwan suka kariso wajen, shi kuma Aseef ya yi suman tsaye ne ya faɗa duniyar tunani. "Areef ka kawo mun video wajen taron nan yanzu, ina da buƙatar na sake ganin wannan guy ɗin". Cewar Lion ɗin. A hanzarce Areef ɗin ya ciro wayarsa tare da kunnata, data ya kunna dan ya je ya ɗauko videon. Aiki suka hau yi a kan guy ɗin babu kama hannun yaro, a tare suke yin komai, Lion, sir Safwan and Areef, shi kuwa Aseef sai dai ya bisu da ido kawai yana kallonsu, suna cikin damuwa, sosai Aseef ya rage zama a tare da Akila, kullum yana ɗakin bincike suna aiki, computers nasu gabaɗaya sun kasa iya binciko masu ainahin in da daddyn Rimshar yake, ko number daddy suka bi sai ya rinƙa nuna masu wajaje daban daban a kallah sun kai 20, kuma dukka manyan kasashe ne, number guda ɗaya a ƙasashe daban daban har guda 20 ai ku daga ji kunsan tsafi ce kawai take aiki, abin dai ya ci tura, ya sha gaban tunaninsu, duk yadda kuke tunani ya wuci hakan. Wasa wasa har tsawon good three months babu daddyn Rimsha babu mummy babu labarinsu, idan hankalin QUADRUPLE ya yi dubu ɗari to fa ya tashi, sun shiga damuwa, sun rasa mafitar ta ina zasu nemo uncle ɗin nan nasu. Ita kuma Rimsha, da yake baiwar Allah ce mai tawakkali, sai ta ragewa mijin nata zafi a kan zafi, sai ta janye daga jikinsa ta koma zaman cikin bedroom tana aikin yin sallah da yi masu addu'ar samun nasara, komai ya yi zafi maganinsa Allah, har azumi take yi sosai. Tabbas tana cikin damuwa na wuce misali, dan har rama sai da ta yi, amma hakan bai sa ta mance da cewa Allah shi ne maganin komai ba, bai sa ta mance da cewa Allah shi ne ya bata iyayen nata ba, baisa ta mance da cewa Allah ne kaɗai zai iya kawo masu mafita ba, dan haka ta koma ga Allah ta dukufa da azumi, sallolin nafila, karatun Alqur'ani mai girma babu kama hannun yaro. Ba ƙaramin daɗi Lion ɗin ya ji ba, ya kara jinjina mata sosai, a kakanun shakarun nan nata tana da karfin imanin da ba kowani bawa ne yake samun baiwar hakan ba, da wani bawa ne wannan bala'i ta afka mash, rashi uwa da uba lokaci guda, da mantawa zai yi da addu'a ko sallah ya yi ta aikin rusa kuka, amma ita sam bata yi hakan ba, dan tasa babu wata mafita a kukan ma idan ta yi. Yana da kyau muyi koyi da halin Rimsha my peoples, a duk lokacin da wata iftila'i ta afka mana komai girmanta, to muyi ƙoƙari mu tuna cewa babu mai fitar damu daga cikinta face Ubangijin talikai, mu yi ƙoƙarin danne zuciya mu kori shaiɗan mu koma ga Allah, hakan ce kawai zata sa mu rinƙa samu magungunar matsalolinmu, kada ki yarda wani damuwa ya sameki ki zauna kina kuka ko ki tafi kina yayatawa jama'a, babu abin da jama'a zasu iya yi maki wanda Allah bai rubuta maki ba, ko yaya jama'a suka kai ga son taimaka maki in dai Allah bai kaddaro shi a kaddararki ba to wlh a banza ne, gara maki ki koma ga Allah, ko ba komai zaki samu sauki!!. ALLAH KASA MU DACE. Wasa wasa daddyn Rimsha and mum sun doshi wata na huɗu kenan a yanzu, babu su babu labari. Gwaggo ta shiga tashin hankalin da yasa Lion bashi da zaɓin da ya wuce ya sanar da ita gaskiyar abin da yake faruwa, domin suna da buƙatar addu'arta. Jin abin da ya faru da kanin nata ba ƙaramin tayar mata da hankali ya yi ba, hakan yasa har sai da ta kwanta a gadon word room nasu, sai da ta yi jinya na tsawon sati ɗaya. Su brr Naurat kuwa, Lion ɗin ya barsu a matsayin ya aiki daddyn Rimsha yin wani aiki a kasar England, dan haka wata shidda zai yi ya dawo, hakan yasa basu tashi hankalinsu ba, Lion ɗin yana kwantar masu da hankali sosai, ya kuma ce masu ba zasu yi magana da daddyn a waya ba saboda yanayin aiki. Ita kuwa gwaggo bata iya ɓoyewa Dr William nata gaskiyar da Lion ya sanar da ita ba, ta gaya mashi, domin ya shiga damuwa na wuce misali ganinta a cikin damuwa da yake yi, hakan yasa ta gaya mashi gaskiya. Sosai hankalinsa ya tashi, dukufa suka yi a kan addu'a babu kama hannun yaro. Jehan da Akila kuwa suna ta aikin tura cikinsu, cikin Akila wata shidda yanzu ya shiga na bakwai, na Jehan kuma ya shiga na shidda, batun zuwa Nigeria ɗaurin aurensu Aafia kam tuni ya kwanta, dan ba'a sake bi ta kan zancen ba, da dai gwaggo taga Tga ba zai iya hakura bane kawai ta ce gara a ɗaura auren a nan daga baya zasu je Nigeria a sake shagalin biki. Hakan yasa a cikin satin nan Shaikh Sultan ya ɗaura aurarraki guda ukun, Aafia and Sudais, wato Tga, sai Mahhir and Adiva, sai kuma Sir Safwan and Maryam. Sam ƴan Nigeria basu san da zancen bikin ba, gwaggo ta ce a bari sai sun je kawai a sanar dasu, hakan kuwa aka yi. Yau ta kama weekend, Lion bai je office ba, kuma har yau bai koma white house da familynsa ba, ya bari sai ya gano daddyn Rimsha, so har yanzu yana cikin Daularsa ne. Kwance yake a saman katafaren bed nasa, jikinsa na sanye da pajamas launin sky blue, ya yi shiru yana tunani, while ita kuma Rimsha tana zaune a saman sofa tana shan ruwa. Daga ita har Lion ɗin sun yi wani irin rama sosai, duk suna cikin damuwa, sai dai su danne kawai suna ƙoƙarin farantawa juna. Wayarsa da take a saman bedside drawer ne ta yi kara, lumshe idanuwansa ya yi tare da sake buɗesu a hankali kafin ya ɗan juyar da kansa izuwa kan wayar. Hannu ya miƙa ya jawota, dai'dai saitin face nasa ya kawota. Ganin cewa........... FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA CE🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA🔥🌹) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581 ban da kira* E50 Ganin cewa massage ne da ɓoyayyiyar number yasa ya ji kamar ba zai buɗe ba, dan baya da bukatar karin ciwon kai a kan wanda yake fama da shi a yanzu. Har ya mayar da wayar ya ajiye, sai kuma wani tunani ta faɗo mashi a ransa, idan sako ne a kan daddyn Rimsha fa?. Tunawa da hakan ne yasa ya yi sauri sake ɗauko wayar tasa. A hanzarce ya buɗe saƙon dan ya gani. Wani irin miƙewa a dubu ɗari ya yi lokacin da idanuwansa suka sauka a kan sako. To me ya gani haka?. A ɗari ya zaro idanuwansa waje sosai kafin ya miƙe tsaye mai gabaɗaya. Kofar fita daga cikin bedroom ɗin ya nufa ba tare da ya yi magana ba, sai dai da kallo ɗaya zaka yi mashi kasan ya shiga tsananin tashin hankali na wuce misali. "Noorish ina zaka je?". Rimsha ce ta jefa mashi wannan tambayar. Sam bai bi ta kanta ba, bai amsa mata ba, da alama ma bai ji me ta ce ba, baya a tare da ita, hankalinsa ya yi gaba. Waje kawai ya fice abinsa cikin tsananin tashin hankali. Bin shi da kallo kawai ta yi, da farko kamar zata tashi ta bi bayansa, sai kuma ta yi tunanin irin halin da suke a ciki, dan haka sai kawai ta cigaba da zamanta. Yana fita ɗakin bincikensu ya afka, a hanzarce ya dannawa Tga, Mark, sir Safwan and Areef kira. Cikin ƴan mintocin da basu fi uku ba sai ga su nan sun shigo kusan a tare, Uncle T shi ne a gaba. Lion ɗin yana a tsaye a gaban wata makekiyar desktop computer, ya harɗe hannayensa a saman Lion chest nasa yana jiran shigowarsu. Cirko cirko suka tsaya ta bayansa suna kallon shi, dukkansu an rasa mai iya tambayarsa menene yake faruwa? Meyasa ya kirasu? Sun kasa iya tambaya, saboda yanayin yanda suka ga face nasa babu ɗigon annuri ko miskala zarratin. Ganin sun shigo ne yasa ya yi connected na wayarsa da wata desktop computer da yake a gabansa, sannan ya juyo da kallonsa a kansu. "General ka yi waya headquarter Major ya shirya tawaga kamar yadda na gaya maka jiya, tafiyar ta kamaku, Areef sai ka shirya saka kaki a yau, dama ai da gangan ka ce ba zaka shiga office this week ba, to tafiya ta kamaku, kuma dole kai da Tga and Mark ku zaku jagoranci tawagar sojojin". Cewar Lion ɗin. Mu koma baya kaɗan, farkon shigar Lion office, a week da ya shiga ya fara aiki, ya rubuta later wa Chief of Army's Staff nasa, ya bukaci da Tga ya tashi daga matsayin General ya koma tsohuwar muka min Lion ɗin, wato General of The Army's, hakan kuwa aka yi, shi kuma Areef sai aka bashi muƙamin Tga ɗin, wato General, shi ne ya ce ba zai shiga office a yanzu ba, gaskiya shi sai ya sake shiryawa ya karɓi training na musamman daga wajen Uncle T ɗin, shi kuma Mark aka kara mashi matsayi zuwa lieutenant General, Aseef da Handsome sun koma school, Sir Safwan kuwa sun yi cancel na aikinsa da yake a kasar China, abinku da mulki yanzu tana a hannunsu, Lion ya bashi irin wannan aikin a nan U.s ɗin, so a yanzu Sir Safwan ɗin shi ne Defence minister. Wannan shi ne abubuwan da suka faru bayan shigar Lion ɗin office. A zabure dukkansu suka kurawa screen ɗin wanna makekiyar desktop computer ido, da mamaki suka dawo da kallonsu a kan Lion ɗin. "Saif what are we seeing?". Cewar sir Safwan. Areef ne ya karɓi zancen da cewa. "Kenan Lion dama you know in da uncle yake? Kenan kasan komai? Kenan da sa hannunka aka ɗauki uncle ɗin? To meyasa ka yi hakan?" Ya jero mashi tambayoyin ne cikin tsananin tashin hankali, yana magana kuma idanuwansa suka a kan desktop computer, yana kallo babu ko kyaftawa. Ba komai suke kalla a saman screen ɗin wannan computer ba face hoton daddyn Rimsha a ɗaure da sarkoki a cikin wani ƙungurmin daji, ga kuma map na computer tana nuna masu in da location na dajin yake! To ina mummyn Rimshar kuma?. "Saif talk to us, amsa us, kenan kasan da cewa za'a ɗauki uncle? Meyasa ka yi hakan?". Cewar sir Safwan. Mark kam ya kasa yin magana, kallon screen ɗin computer kawai yake yi babu ko kyafta idanu. Areef zai sake yin magana Lion ɗin ya ɗaga masu hannu tare da cewa. "Amsa kuke son na baku ne, ko kuma dai cigaba da jero mun tambayoyi zaku yi?". Shiru suka yi suka zuba mashi idanu. Shiru shima ya yi na a kallah good 10 mins kafin ya yi ɗan gyaran murya, sannan ya fara magana in a cool voice, cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. "Ban san cewa zasu ɗauki uncle ba, abin da na sani kawai shi ne dole zasu so ɗaukar ɗaya daga cikin family, kuma na yi hasashen maza zasu ɗauka ba mata ba, hakan yasa dukkanku na sanya maku na'urar bi diddigi a jikinku ba tare da saninku ba, duk wani namiji da yake a cikin gidan nan to akwai wannan na'urar a jikinsa, na yi mamakin ya aka yi tsawon watanni na'urar dake jikin uncle bata aiki sai yau, i think in da suka kai uncle ɗin da farko suna amfani da software na hana bin diddgi ne, a yanzu kuma sun canzawa uncle ɗin waje, sun fitar da shi zuwa wani wajen, sun yi hakan ne kuma domin su ɗauki hotonsa su turo mun kamar yadda suka yi ɗin, sun yi hakan ne kuma dan hankalina ya tashi, na shiga damuwa, sai dai basu san cewa hakan da suka yi shi ne zai kawo karshensu ba, dan fitar da Uncle ɗin da suka yi daga in da suka kai shi da farko ne yasa na'urar jikinsa ta fara aiki, dan haka ga location da komai da komai a jikin computer nan, sai ku fara aikinku, kada ku kuskura ku bar ko mutun ɗaya da rai face Anderson and His Excellence, su biyun nan kawai nake son ku kawo mun su a raye, saura duk ku kashesu, ku yi bombing na wajen kaca kaca". Cikin sauri Areef ya tari numfashinsa da cewa. "Amma Lion uncle Herry fa? Ka ce mu kashe kowa! Kuma kasan uncle Herry shi ne king nasu a wajen, ya zamu yi da shi". Nisawa ya yi kafin ya ce. "Uncle Herry ai namu ne ba nasu ba, what i mean here is, duk wasu mutanensu ku kashe dabbobi banza, namu kuma ku dawo dasu, Anderson and His Excellence ina da bukatarsu a raye, saboda hukuncin mutuwa ta yi masu kaɗan". Ya kai karshen maganar tare da wucewa ya nufi hanyar fita waje. "Amma Lion yaushe zamu tafi?". Cewar Mark. Ba tare da ya tsaya daga tafiyar da yake yi ba ya basu amsa da. "Now". Ya kai karshen maganar tare da ficewa daga room ɗin. Kallon juna suka fara yi a tsakaninsu. Sir Safwan ne ya katse masu kallon da cewa. "Zan iya rakaku?". "Gidan biki or party ne da zaka rakamu?". Cewar uncle T Girgiza mashi kai Areef ya yi yana faɗin. "Ka kula mana da matanmu kawai, kila mu dawo da wuri, kila aka sin haka, amma daga yanayin wajen akwai haɗari sosai, zamu ɗauki kwanaki ko watanni, anywhere ka kula sosai". Uncle T ɗin ne ya sake karɓar zancen da cewa. "Ba shakka zamu iya ɗaukar watanni muna fama kam, amma dai ina sa ran nasara, ya kamata mu fara aiwatar da abin da ya dace, Safwan kada ka gayawa Dr William ga in da muka tafi, dan hankalinsa zai tashi sosai, kuma bana son hakan". Areef ya ce. "Yeah dama nima abin da zance kenan, kada ku sanar da family ga in da muka nufa, ku barsu a kan mun yi tafiya kawai, let's go uncle T". Ya kai karshen maganar tare da nufar hanyar fita. Rufa mashi baya Mark and Tga ɗin suka yi, sir Safwan kuwa ya tsaya ƙasaƙe yana kallonsu har suka fice, sannan shi ma ya ja dogon numfashi tare da saukewa a hankali ya rufa masu baya. A takaice haka suka shirya rundunar sojoji guda, tamkar waɗan da zasu tashi duniya, a wannan rana suka nufi wannan ƙungurmin bakin dajin, sun yi shahada dan kawar wa da kasarsu ɓata gari bayin Allah. Shi kuwa Lion dukufa ya yi da yi masu addu'a tare da fatan Allah ya dawo mashi da su lafiya, ba halin ya bisu ne da wlh ba zai iya bari su tafi su kaɗai ba, dole ce tasa ya zauna shi, domin kujerar President ba wasa ba, ya sanya Sheikh Sultan sai yi masu addu'a yake yi babu kama hannun yaro. Wasa wasa sai da suka shafe watanni kamar yadda suka faɗa kafin su tafi, ga shi shi Areef ma ko sallama da Jehan bai yi ba, ya barta tana barci, kuma da gangan yaki tashinta, dan yasa zata tsayar da su ne ta hanasu tafiya a kan lokaci, zata yi ta yi mashi kuka tasa ya tafi da tunaninta tare da damuwa a ransa, shi ne yasa kawai ya bawa Lion ɗin amanarta sannan suka wuce. Tun da suka tafi kuma gabaɗaya wayoyinsu bata aiki, ba network a wajen, babu wani connection da suke samu tsakaninsu da ƴan uwa, shiru kake ji tamkar an ɓallawa sama harara. Har Akila ta haifi ƴaƴanta santala santalan guda uku, wato TRIPLETS, dukkansu kuma maza kyawawan gaske, su Areef shiru basu dawo ba. Sai dai fa ranar haihuwar Akila an yi ƙaramin yaki ba kaɗan ba a gidan, dan kuwa sun ga dirama wajen Aseef, likitoci jiga jigai aka ɗebo daga hospital ɗin Dr William, aiki aka yi mata aka cire ƴaƴan, ba zata iya haifarsu da kanta ba, ba yadda ba'ayi da Aseef ba a kan ya tsaya a waje, ya ce wlh ba zai tsaya ba, ɗakin ya shige abinsa, ya je ya zauna kusa da Heartbeat ɗin tasa, ya ɗaura kanta a saman laps nasa tare da ƙanƙame hannunta yana ta kallon duk wahalar da take sha, ya sha kuka kam hawaye bibbiyu, sai faɗi yake kada likitocin nan su yarda su bari ta mutu, idan ta mutu sai ya kashe su ɗaya bayan ɗaya suma, sai kace su ne suka ɗaura mata ciwon, yana neman sauke haushi a kansu. Ai su gwaggo sunga ikon Allah, dan fa Aseef ya yi masu karamar hauka, dan ma Allah yasa aiki aka yi mata, da da kanta zata haifesu ai da ina ga zuciyarsa ce zata buga idan yaga halin da zata shiga, aikin ma ya bi ya wani ƙanƙameta ya takurawa likitoci basu samu su yi aikinsu yadda ya kamata. Sai dai kuma fa abin dariya abin takaici, ana ciro mashi baby's ɗin ya saketa ya koma wajen yaran abinsa, wai ya je ganinsu, har ya manta yanzu ya gama zubar mata da hawaye har yana cewa shi fa baya son baby's ɗin, ya fi sonta, dan haka shi a ceci rayuwarta kawai, ba ruwansa da baby's ɗin, har da cewa ba zasu sake haihuwa ba daga wannan, amma da yake ɗa mai daɗi ne, ana cirosu har ya manta da surutan da ya rinƙa yi a kan nasu, ya wani shige gaba yana ta kallon yaran, sai tsallara ihu suke yi, shi kuma sai masifa yake yi wa likitocin a kan su saka mashi yara su yi shiru ko kuma ya hukuntasu, dan shi ba zai iya hakuri ya ji baby's nasa suna kuka ba. Izuwa yanzu dai kowa na family ya dai'na mamakin halin Aseef, sun zuba mashi ido kawai suna kallon ikon God, dan ya wuce tunaninsu, daga wannan sai wannan, a kan waɗan nan TRIPLETS ɗin nasa zai iya kashe mutun. A gaban idanuwnasa aka yi wa baby's and maman baby's komai, yana tsare da kayansa yana kallonsu. Ko da aka gama gyara su ma ya hana family ɗaukar yaran, wai kada su yi su karya mashi yara, dan kashin yaran ba kwari ne da shi ba. Gwaggo kawai ya yarda ya bari ta ɗauki na farko da aka fara haifa, dukka yaran wlh kama da Aseef ɗin sak suke yi, kamar an tsaga kara, babu wanda ya ɗauko Akilar, harta kwayar idanuwansu da yake brown irin nasa, duk sai suka fito a turawan, babu kalar Akila a cikinsu. Ita kuma Jehan tana nan tana aikin tura uban ciki haihuwa ko yau ko gobe, ga cikin nata ita ma kato da shi, an yi mata scanning, sai dai ta ki yarda kowa yaga result ɗin abin da yake a cikin nata, ta ɓoye kayanta, daga ita sai gwaggo suka sani, ta ce kowa ya barta ta sarara, sai cikin ya fito duniya zasu ga menene a ciki, haka suka hakura suka rabu da ita. Ba yadda gwaggo bata yi da Lion ba a kan ya zo ya ga yaran Aseef, amma ya murje idanuwansa ya ce shi wlh ba zai je ba, kuma kada a kawo mashi su ɗaki baya so, ita kam gwaggo yanzu al'amarin Lion a kan tsanar yara ya fara bata tsoro, ga Maryam matar Sir Safwan har tana da ɗan kara min ciki, amma shi Lion shiru, hakan yasa gwaggon ta fara zarginsa a kan anya ba wani abin yake bawa Rimsha yasa bata ɗaukan ciki ba?. (Nima Princess Teema na yi wannan tunani🤔 gwaggo ki binciko mana gaskiya, ina dalili? Mu muna son muga little Lion) Kowa yasan da cewa Lion ya fi Kaunar Aseef sama da kowa a cikin ƴan uwansa, amma kuma duk wannan uban kauna da take a tsakaninsu Lion ɗin yaki yarda ko da ido ya kalli ƴaƴan Aseef ɗin, da yake Aseef ɗin yasan tun farko Lion baya son yara, sai bai yi gigin kai mashi labarin Akila ta haihu ba, sai ya rabu da shi kawai ya rungumi ƴaƴansa abinsa, sai murna yake yi ya sami TRIPLETS tashi ɗaya. Ita kuma Rimsha Allah ya gani tana son yara, kullum sai ta yi zancen cikin Akila da Jehan ɗin, amma da zarar ta fara yi wa Lion ɗin zancen haihuwar zai canza masu topic na hira, shi zancen yaran ne sam baya so, amma kuma duk da haka yana tsananin bawa Jehan kulawa na wuce misali, a yanzu haka tana a part nasu da zama, saboda yana ganinta tamkar Areef, dan maganarsa ta karshe da Areef ɗin ma kenan a kan Jehan ɗin ne da abin da yake a cikinta, amana ɗan uwan nasa ya bashi na Jehan ɗin, dole ya kula da wannan amanar ta ɗan uwan nasa, saboda bashi da tabbacin Areef ɗin zai dawo a raye ko kuma zai mutu?. Hakan yasa yake kula da Jehan ɗin over, bedroom ɗin da take ma sai da ya saka mata camera, duk da a cikin part ɗaya suke, yana iya jiyo motsinta, amma bai wadacesa ba hakan, sai ya kara mata da camera dan ya rinƙa kallon duk wani abin da take yi. Haka shi ma sir Safwan, ya fi kula da Jehan ɗin sama da yanda yake kula da matarsa Maryam, wani lokaci abin har yana neman ya zamar masu faɗa a tsakaninsa da Maryam ɗin, sai ta rinƙa cewa meyasa ya fi bawa cikin dake jikin Jehan kulawa sama da nata cikin? Ita da cikinta ma karami ne, ita ya kamata ya bawa kula sosai, dan kada a samu matsala, amma sai ya fi kula da cikin Jehan ɗin, kullum yana part ɗin Lion wajenta, da ta yi motsi kaɗan zai tambayeta tana lafiya kuwa? Abin ya fara bawa Maryam ɗin haushi, kun san mata da kishi, kada kuga laifinta, haka muke........😂 Duk yadda gwaggo ta kai ga son Jehan a wannan karon sai da ta hakura ta barwa Lion da sir Safwan kula da Jehan ɗin, domin kuwa suna ɗaukar Jehan ɗin ne a matsayin Areef ɗinsu, cikon QUADRUPLE nasu, kuma kowa yasan sir Safwan da Areef ɗin sun fi shakuwa sosai, dole kunga ya mayar da hankali wajen kulawa da ɗan uwan nasa kayansa fiye da komai. Wasa wasa har cikin Jehan ya shiga watannin haihuwa, su Areef shiru basu babu labarinsu, Lion yasa an tura wasu runduna na sojoji ma, amma still shiru, suma rundunar sun tafi basu dawo ba, ba wani labari. Kullum cikin kuka a ɓoye Jehan take yi, duk da Lion ya ce mata Areef sun je ƙasar China ne yin wani aiki, zasu dawo bada jimawa ba, amma ta kasa samun nutsuwa, tana jin kamar ma Areef ɗin baya raye a duniya ne, ga rashin iyayeta na tsawon watanni da dama, abin sai ya haɗu ya yi mata yawa, ga uban ciki haihuwa yanzu ko anjuma, duk ta rame, ta yi wani irin duhu sosai. Amma Lion yana iya ka bakin ƙoƙarinsa wajen ganin ya kwantar masu da hankali ita da Rimsha da kuma gwaggo, abin ne yana neman ya fi karfinsu. Ƴanƴan Akila sun fara wayo, ta tare a part ɗin gwaggo abinta, kullum na Allah Aseef yana manne da baban ɗan nan nasa wanda ya fi kama da shi, ba'ayi shagalin suna ba, sun ce sai Jehan da Anaya sun haihu za'a haɗa dukka ayi party, daga nan a shirya zuwa Nigeria, sai dai an sanyawa yaran suna kamar yadda addinin musulunci ta tanada, Aseef ya yi wa Abban Akila takwara, ya kuma yi wa Dr William sai kuma sunan Lion ya sakawa autar cikinsu, baya taɓa yarda wani ya ɗauka yaran nan idan ba gwaggo ba, ko su Anaya ya hanasu, sai dai ka kalli yaran da ido suna kwance a saman bed nasu, gasu gwanin ban sha'awa, ƴan ɓul ɓul da su, amma baka isa ka ɗauka ba, ubansu ya ce kar a karya mashi su, a barsu a kwance a rinƙa kallonsu. Yau ni PRINCESS TEEMA ina ganin ikon god a wajen Aseef, wai kada ayi a karya mashi su, Kai jama'a, yara masu daɗi, Allah mai iko, Allah ka bamu masu albarka Shi kuma fa zai ɗauki yaransa son ransa, kuma koda yaushe idan ya zo ɗauka bai iya ba sai gwaggo ta ɗauka ta miƙa mashi su, amma a haka yake cewa kada wasu su karya mashi yara basu iya ɗaukarsu ba, Aseef duniya. Yau ta kama Monday, tun karfe 7 Lion ya hau shiri. A tunanin Rimsha office zai tafi, sai kuma taga akasin haka, dan ba shirin zuwa office yake yi ba, abin ya yi mugun bata mamaki. Yana gaban mirror yana gyara dark black curly hairnsa ta fito daga cikin toilet ɗaure da towel a kirjinta ta same shi. Karisowa wajensa ta yi tana faɗin. "Noorish ina zaka je da irin wannan shiga haka? Yau kuma me ya haɗaka da Army's shirt?". Yana aiki sauri sauri ya bata amsa a takaice da cewa. "Wajen su Areef". Da yake bata san ina su Areef ɗin suke ba, bata san ina suka tafi ba, sai ta ce. "Amma Noorish tafiya zaka yi ne da irin wannan shiga haka? Kuma naga kamar harda gun ka ɗauka, to dai nima zan bika". Shiru ya yi bai bata amsa ba, domin harshensa ma wani irin azababben nauyi take yi mashi, yau ba zai iya hakuri ba sai ya bi bayansu Areef, sai dai duk abin da zai faru ya faru, tun da ya tashi barci yau da asuba, zuciyarsa take tsananin buga mashi da karfi karfi, kuma already kunsan zuciyar QUADRUPLE tana irin wannan bugawar ne idan wani abin ya sami ɗayansu, so yana kyautata zaton akwai abin da ya sami Areef, hakan yasa ya ji ba zai iya zama ba, duk bala'i yau da izinin Allah sai ya kai in da ɗan uwansa yake!!. To fa babbar magana. FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA CE.....✍️🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E51 "Noorish baka ce komai ba, na ce fa zan bika". Ta yi maganar kamar zata yi mashi kuka. Ta cikin mirror ya zuba mata idanu yana kallonta, ta rame sosai, ga wasu kasusuwa da suka bayyanar mata a wuyarta, tamkar ba Meesharsa ƴar dumur mur da ita ba, yanzu ta dawo sai a slow, sai dara daran fararen Sleeping eyes ɗin nan zaka gani, hakan yana nuni da cewa kullum a cikin damuwa take. Sai ƙoƙarin latsa wayarta take yi tana son kiran number Anaya a kan ta zo su haɗu a part na gwaggo, sam bata lura da yana kare mata kallo ta cikin mirror ba, ga shi daga ita sai ɗan ƙaramin a kirjinta, wanda kuma tsawonsa sam bai gama rufe mata rabin santala santalan cinyoyinta ba. Tun ranar da aka sace daddyta, tun ranar Lion ɗin bai sake kusantarta ba, saboda suna cikin wani hali, sam baya ma jin wata sha'awa face damuwa, daddynta ya zamar mashi wani ɓangare ne na rayuwarsa, hakan tasa baya jin sha'awar komai face tunanin daddyn nata. "Meesha". Ya ambaci sunanta in a cool voice. Ɗago da idanuwa kawai ta yi ba tare da ta ɗago da kanta ba. Juyowa ya yi gareta da kyau tare da buɗe mata hannayensa a kan ta zo gare shi. Cool murmushi ta sakar mashi da ramammiyar kumatun nan nata, da sauri ta taho ta faɗa saman Lion chest nasa. Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya sa hannu ya rungumota da kyau da kyau. Ƙanƙame shi ita ma ta yi, kamar nace zan kwace mata shi......😒 "Meesha kin rame sosai". Ya faɗa can kasan maƙoshi. "Kai ma ai ka rame sosai Noorish". Ta bashi amsa tana ɗan ɗago da kanta. Zai sake yin magana Tvn dake manne a bangon ɗakin nasu wanda yake haɗe da camerar ɗakin Jehan ya fara fitar da sauti mai kama da sautin numfashi. A hanzarce ya ɗago da blue eyes nasa tare da kai kallonsa saman screen ɗin Tvn. Ai bai san lokacin da ya saketa a dubu ɗari ba ganin abin da yake faruwa. Ita kanta bata san lokacin da ta waro idanuwanta waje tana kallon Jehan ɗin ta cikin screen ɗin ba. Kafin ta yi mashi wani magana tuni ya fice daga ɗakin cikin sauri. A hanzarce ta bi bayansa ko mayafi bata ɗauka ba, daga ita sai wannan towel ɗin. Yana saka kafarsa a cikin bedroom ɗin da Jehan ɗin take ciki, baby na faɗowa, ashe tun ɗazun naƙuda take yi, kun san halinta da dakiya tare da juriya, duk azabar nan da take ji ta daure ta kuma jure, sam bata nuna alama ba, sai da abin ya fi karfinta ne haihuwar ta zo gadan gadan, shi ne ta rasa ya zata yi, kuma karfinta duk ya kare, ta rasa mada fa, hakan yasa ta zamo ta sauko kasa daga saman bed ɗin nata, a nan ta cigaba da murkusoso tana fafutuka har sautin numfashinta ya fara fita da karfi karfi, ta so ta lallaɓa ta tafi wajen gwaggo a lokacin da ta sauko kasan gadon, amma ina karfinta duk ya kare, ta jigata sosai, hakan yasa ta kasa iya tafiya koda da ja a kasa ne, ta kasa, shi ne kawai ta hakura ta zauna a kasan tana ta fama ta kuma zubawa sarautar Allah iso. Duk tsananin kin yara da Lion yake yi yau da hannunsa ya ɗauki babyn Jehan a cikin jini, saboda babyn ta haife shi da riga, abin da ake nufi da babyn da aka haifa da riga shi ne, wanda ake haifarsa yana zuwa da wani abu mai kamar yana da yake rufe mashi fuska, wanda idan ba'ayi saurin cirewa ba yana kashe yaro nan take, dan yana tare mashi numfashi ya hanasa yi, hakan ce tasa Lion ɗin ya ɗauke shi cikin jinin ya yi saurin yage abin ya cire. Da gudun gaske Rimsha ta shigo cikin ɗakin, kan Jehan ɗin ta ƙariso tana ambatar sunanta da karfi. "Get out Meesha". Shi ne abin da Lion ɗin ya ce da ita yana ƙoƙarin janyo duv dake saman bed ɗin dan ya kwantar da babyn dake hannunsa. Kasa fita waje ta yi, sai ma kara matsowa da ta yi tana ƙoƙarin riko Jehan ɗin. Wani irin nishi Jehan ɗin ta sake yi tare da riƙo wuyar rigar Lion ɗin, dan ya fi kusa da ita a kan Rimshar, Rimsha tana ta gefenta ne, shi kuma yana tsungunne ne a ta gabanta in da ya ɗauki baby, hakan yasa da azaba ta yi azaba bata san lokacin da ta damko wuyar rigarsa tana sakin wani irin numfashi mai matuƙar razanarwa ba, tamkar mutuwa zata yi, baiwar Allah. Cikin zafin nama Lion ɗin ya janyon duv ɗin a dubu ya kwnatar da babyn tare da kai hannunsa dukka biyu ya riƙo shoulders ɗin Jehan ɗin yana mai dakawa Rimsha tsawa a kan ta fita a ɗakin kamar yadda ya faɗa mata tun farko. Wannan tsawa da ya daka mata ya yi dai'dai da faɗowar baby a karo na biyu, ita kuma Rimshar tsabar tsorata da tsawar, sam bata san lokacin da ta kwasa a guje ta bar room ɗin ba, daga ita sai towel a kirji. Yau dai Lion da baya kaunar yara a rayuwarsa, saboda kaunar Areef da yake yi tasa ya karɓi haihuwar Jehan da kansa, shi da ya ce ko kallon yaran baya son yi, sai ga shi da Allah ya tashi kamasa a hannunsa aka haifo yaran Areef, daga karshe ma gabaɗaya jikinsa ta yi dama dama ta yi wanka da jini, dan kuwa ba ƙaramar damka Jehan ta rinƙa yi mashi ba, saboda azaba, babynta na uku dana huɗu kam ma kusan a jikin Lion ɗin ta haifosu, duk ta fita daga cikin hayyacinta, hasalima bata san waye ne a wajen ba, Allah ya bata haihuwar QUADRUPLE a saukake, dan kuwa a saukake za'a ce, duk wannan azaban da ta sha wlh ya zo mata da sauki, saboda ba kowace mace ba ce zata iya haihuwa ƴan uku da kanta ba ma bare QUADRUPLE, wannan sai ikon Allah da ya bawa gwaggo da Jehan ɗin damar yin hakan, idan baku manta ba, ita ma gwaggon hakan ce, Jehan ƴar ɗakinta ta yi gado sosai sosai, a komai ta gaji gwaggon, bata rage komai ba abinta. Duk taurin zuciya irin ta Lion wlh sai da idanunsa suka ciko da kwallah, ya yi matuƙar tausaya mata, dan daga karshe ma sai da ya bata iskar bakinsa ta iya cigaba da numfashi, a haihuwar na karshe ta kasa samun numfashin da zai riketa ta iya haifar baby, sai da Lion ɗin ya tallafa mata, ga shi su gwaggo basu kusa, dan gwaggo ma tana can sama hawa ta karshe ita da Josephine suna tsara yadda tafiyarsu Nigeria and Dubai zai kasance, sam bata kawo cewa haihu zai zowa Jehan ɗin a satin nan ba, a nata kissafin sai cikin next week, shi ne yasa suka ɗan matsa kusa da ita. A lokacin da Rimsha ta fita daga bedroom ɗin, kai tsaye bedroom na gwaggon ta nufa, sai dai ko da ta je bata sami kowa ba, abin ku da yarinta, a maimaƙon ta fita ta nemi gwaggon a cikin gidan, dan ta gaya mata halin da ake ciki, sai kawai ta haye gado tana kuka tare da addu'ar Allah yasa kada Jehan ta mutu, Allah yasa ba mutuwa zata yi ba. Kada kuga laifin Rimsha, ita bata san menene haihuwa ba, yarinya ce, ko cikin ma bata san ya ake ji idan aka ɗauke shi ba bare kuma tasan zafin haihuwa, ita dai kawai addu'a take yi Allah yasa kada Jehan ɗinta ta mutu. Shi kuwa Lion babu halin ya fita ya bar Jehan ɗin ya je naman gwaggo, duk dakiya irin tasa ya ji ba zai iya matsawa daga kusa da Jehan ɗin ba, dan yana ganin kamar idan ya matsa daga kusa da ita ya karya amanar da ya karɓa daga hannun Areef, yana ganin kamar yana barin wajen zata mutu kafin ya dawo, dan haka sai ya dakata kawai ya kasa tafiya, ya cigaba da riketa har ta haife cikin nata complete QUADRUPLE. Baby na ƙarshe yana faɗowa ta saki jiki ta sume a jikin Lion ɗin, baiwar Allah. Shi kansa Lion ɗin wani irin nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke kafin ya sake shoulders ɗin nata tare da zareta daga jikinsa. A kasa saman duv ɗin kusa da baby's ɗin nata ya kwantar da ita, sannan ya miƙe tsaye, gabaɗaya ya yi wanka da jiki tamkar shi ne ya yi naƙudar. Har zai bar ɗakin idanuwansa suka sauka a kan yaran, complete QUADRUPLE, suna kwance shiru. Lokaci guda ya ji wani irin tsananin son yara ya kama shi, barema yadda ya kalli yaro ɗayan nan mai matuƙar kama da Areef ɗin, sai ya ji ba zai iya tafiya ba, juyowa ya yi tare da sake tsugunnawa a gaban baby's ɗin. Tamkar mai tsoron taɓa abu, haka ya kai hannunsa zai taɓa kumatun wannan baby mai kama da Areef ɗin, ga yaran da cibiya a jikinsu. Ai kuwa yana taɓa fuskar yaron ya fara tsallara mashi ihu, a hanzarce ya miƙe kamar wani mara gaskiya, da sauri ya fice daga cikin ɗakin. Kai tsaye bedroom nasu ya koma. Yana shiga ya hau cire kayan jikinsa, sam bai nemi Rimsha ba, saboda bata kanta yake ba a yanzu. Sai da ya cire kayan ya rage daga shi sai short ne, ya ɗauko wayarsa ya rubutawa Sir Safwan sako a kan ya kira gwaggo Jehan ta haihu. Yana tura sakon ya wuce toilet abinsa, zuciyarsa a cike tab da tunanin baby's ɗin, sun yi matuƙar shiga ransa ba kaɗan ba. Har ya yi wanka ya fito tunanin baby's ɗin yake yi, sake sabon shiryawa ya yi, har lokacin kuma bai nemi Rimsha ba, yama mance da cewa ya daka mata tsawa. Bayan ya kammala shirin nasa ne ya zo ya tsaya a gaban Tv dake manne a bangon yana kallon yadda su gwaggon suke ɗawainiya da baby's ɗin, yaran kawai yake ta kallo, ji yake yi kamar ya je ya sake taɓa yaron nan mai kama da Areef ɗin, tunanin Areef ya dawo mashi sabo gal. Ya jima sosai yana kallon su gwaggon, har suka gama shirya baby's ɗin suka kwantar da su a saman bed, sannan suka hau gyara Jehan ɗin, gwaggon a tare da Josephine suke aikin. Ganin cewa sun kawar da yaran daga idanun Camerar zasu fara gyara Jehan ɗin ne yasa ya kawar da kallonsa tare da juyawa ya bar wajen. Sai a lokacin ne kuma ya tuna da cewa ashe Rimsha bata a cikin ɗakin, dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali kafin ya sa kai ya nufi waje. Kai tsaye bedroom na gwaggo ya nufa, dan yasan a can kawai zai sameta. Akila kuwa tana bedroom na Josephine ne, kada ku manta Aseef dai na Josephine ne, hakan yasa Josephine ɗin ta ce a bedroom nata matar Aseef ɗin zata zauna ta yi jego, dole gwaggo ta bar mata Akilar, Anaya kuma tana wajensu Brr Naurat, a can tafi yawan zama, su Aafia kowa tana part na mijinta. Tana kwance kamar yadda ta shigo ta kwanta, bata motsa daga wajen ba sai ruwan hawaye da take yi. Kasa kasa ya yi sallamar da babu wanda zai iya jinta face shi da ya yi kayansa, sai zuba uban kamshi perfume nasa yake yi tamkar ba daga ɗakin haihuwa ya fito yanzu ba jimawa ba. Tana ganinsa ta miƙe zaune tana mai cigaba da kukanta, hawaye suna gudu a saman face nata kamar ruwan famfo aka buɗe. Ɗan tsura mata idanu ya yi kafin ya ƙariso wajen nata. Kasa ta yi da kanta tana shesshekar kuka. Yana isowa wajen ya miƙa mata hannunsa. Ɗago kai ta yi ba tare da ta yi magana ba, kuma bata iya miƙa mashi nata hannun ba. Ganin hakan yasa shi ya kamo hannun nata tare da jawota a kan ta sauƙo kasa, dan baya jin kamar zai iya hawa saman bed ɗin gwaggon. Ba musu ta sauko kasan. Cak ya ɗauketa ba tare da ya yi magana ba. Bedroom nasu suka koma. Bai direta a ko'ina ba sai a saman katafaren bed nasa. Zama shi ma ya yi a bakin bed ɗin tare da jawota jikinsa yana faɗin. "Ya isa kukan nan haka, calm down sarkin rigima". Cikin dashewar murya ta ce. "Noorish ina Jehan ɗita take? Bata mutu ba ko? Ya take?". "Jehan ɗinki bata mutu ba, sai dai ma haifa mana kyawawan baby's har guda huɗuda ta yi, juya ki ganta a jikin Tv". Ya kai karshen maganar yana shafa kanta. A dubu ɗari ta zaro idanuwanta tana kallon Tv, su gwaggo kawai ta gani suna aikin gyara kasan wajen, Jehan ɗin tana saman bed suka mayar da ita, saboda har lokacin tana sume ne, hakan yasa suka mayar da ita saman suna aikin gyara kasan kafin su koma ta kanta. "Noorish ban ga Jehan ɗin ba, in je bedroom ɗin in dubata?". Ta yi maganar muryarta cike tab da zumuɗi. Kai kawai ya gyaɗa mata tare da sakinta a kan ta je. Da gudu ta miƙe da nufin ta fita. A hanzarce ya riƙota yana faɗin. "Saka kayanki tukun nan mana". Nisawa ta yi tare da nufar dressing room nasa. A gaggauce ta zura abaya a jikinta tare da fitowa da sauri, har tana haɗawa da gudu. Da kallo kawai ya bita da shi har ta fice abinta, sai zumuɗi take yi. Bayan ta fita ne ya miƙe da nufin ya fita waje shi ma, zuciyarsa cike tab da tunanin baby's ɗin nan, da hannunsa yau ya karɓi haihuwa, Allah mai iko, idan ba dan Areef ba yaushe zai yarda ya kusanci mace mai ciki ma, amma sai ga shi ya kusanceta har ya karɓi haihuwa, Allah da ikonsa kuma har soyayyar yara ta dasu mashi a cikin zuciyarsa, dama ance wani sanadi shi yake kawo wani, to shi dai sanadin ya karɓi haihuwa Jehan, ta haihu a hannunsa, wannan sanadi tasa ya fara son yara, Allahu Akbar. Parlourn kasa ya sauko, babu kowa a ciki, dan ƴan gidan nan wasu suna kaiwa 12 na rana basu tashi barci ba wani lokaci, so babu kowa a parlourn. Waje harabar gidan ya nufa. Yana fitowa motocin jiga jigan sojoji masu ɗauke da jini tamkar zasu ruguje garin, tamkar zasu yaki kowa da komai na duniyar ne suka danno hancinsu a cikin gidan, ji kake jiniya ta karaɗe ko'ina a faɗin arear wajen tana tashin kai. Zubawa motocin idanu ya yi yana kallonsu har suka iso cikin tsakiyar harabar gidan. Tun basu gama yin parking ba wasu jiga jigan zaratan sojoji turawa farare kal kal dasu ne suka fara dirowa kasa daga saman bayan motocin. Ji kake dib, dib, dib, suna dirowa, ga wasu shegun jiga jigan bindigu a hannayensu. Suna dirowa kuma suka fara aikin bubbuɗe kofofin motocin. Tga ne ya fara fitowa daga ɗaya daga cikin motocin, cikin zafin nama yake taku izuwa wajen motar dake kusa da wanda ya fito. Yana zuwa ya ɓalle marfin bayanta, hannu ya zura ciki ya saɓo Areef dake kwance kamar gawa a saman shoulder ɗinsa. Ai a dubu ɗari Lion ɗin ya nufosu, sojojin suna ganinsa suka ja da baya, cikin girmamawa suka hau sara mashi. Sam bai bi ta kan kowa ba, bai kalli in da suke ba ya nufi Tga ɗin kawai. Yau idanuwan Uncle T kamar wuta saboda tsananin ja da suka yi, da alama sun ji wuya ba kaɗan ba, fuskar nan tasa kawai idan mai ƙaramar zuciya ya gani sai zuciyar ta buga ya mutu. Lion ɗin yana isa wajensu ya kai hannu ya karɓi Areef ɗin. Saura kaɗan ya sake shi ya faɗi kasa, saboda yadda ya ji jikin ɗan uwan nasa a sake kamar gawa, abin ya yi tsananin girgizasa. Amma sai ya daure ya rikesa da kyau ya wuce da shi cikin gida. Shi kuma Uncle T ya koma ya fito da mummyn Rimsha da ita ma take kwance kamar gawa, shi kuma Mark ya tallafawa daddyn Rimsha da baya iya tafiya a miƙe, saboda ya jima tsawon watanni a ɗaure cikin sarkoki yana tsugunne a saman gwiwowinsa, hakan yasa baya iya miƙewa ya taka kafafun nasa, su Anderson sun kai tsinannu azzalumai wlh. Cikin gida suka wuce su ɗin ma, jinin Uncle T yau a tafashe take over. Waɗan nan jiga jigan sojojin ne suka fito da dattijo Anderson and His Excellence, duk jikkunansu ciwuka ne, sun sha ɗauri kamar wasu huhun goro, daga ganin wannnan azzalumin baƙin ɗaurin na rashin imani uncle T ne ya ɗaure su, da gani babu tambaya shi ne nan ya ɗauresu, dan tsabar sun ɗauru har ta wuyarsu bai bari ba, duk ya kanannaɗesu da wata shegiyar igiya mai kaifin gaske, kamar wasu dabbobi, sai yankar jikinsu igiyar take yi, uncle T babu imani ba tausayi idan ya kamaka da laifi. Da kyar da makyarkyata suke iya yin numfashi, duk sun zama wasu iri da su, shi His Excellence ma har da kumburi a tattare da jikinsa, saboda rashin samun isasshen gudun jini da yake fama da shi, dan sun ɗauru ne over ta yadda yasa har jinin jikin nasu baya ratsa sassan jikinsu da kyau, da alama kuma sun ɗauki tsawon kwanaki suna a cikin wannan hali na ɗaurin, dan kuma ga su nan sun yi fari pat kamar wasu farin fenti, dama yaya lafiyar kura bare kuma ta yi zawo?. Wani shirgegen soja ne ya fito da Uncle Herry wanda shi ma ya samu harbi da bingiga a shoulder ɗinsa ta dama, da alama ya yi ƙoƙarin yi masu gardama ne uncle T ya harbesa, dan da alama uncle T shi ne ya karisa wannan yaƙin duba da yadda Areef yake kamar gawa, Allah ne kaɗai yasan ya mutu ne ko yana raye. Cikin gida wannan shirgegen sojan ya wuce da Uncle Herry ɗin ma, a lokacin tuni Lion ya wuce da Areef word room nasu, a saman sofa ya kwantar da Uncle Herry ɗin, sannan ya juya ya fice abinsa. Yau dai gida suna farinciki kuma suna bakin ciki, farincikin Jehan ta haifo QUADRUPLE ne, bakin ciki kuma na dawo da gawar su Areef da mummyn Rimsha........... NASO NA HAƊE MAKU COMPLETE LAST PAGES YAU, AMMA BAN SAMU DAMA BA, SABODA WANI UZURI, KUMA KUN SAN DAMA BA ISSHASSHEN LAFIYA NE DA NI BA, WLH KAWAI KARFIN HALI NE DA KUMA BANA SON BARINKU A CIKIN KEWA TASA NAKE DAGEWA NA YI MAKU POSTING ƊIN!!. MA'ASSALAMA. FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA CE.....✍️🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E52 Yau dai gida suna farinciki kuma suna bakin ciki, farincikin Jehan ta haifo QUADRUPLE ne, bakinciki kuma na dawo da gawar su Areef da mummyn Rimsha. Saman ɗaya daga cikin bed dake room ɗin Lion ya kwnatar da Areef, su Uncle T gabaɗaya sun biyo bayansa, a saman wata bed ɗin ya kwantar da mummyn Rimsha da ta yi wani irin bala'in haske, tamkar jinin jikinta aka zuƙe, da alama ma hakan ce. "Call dad". Cewar Lion, ya sanar da Uncle T kenan a kan ya kira masu Dr William. Da sauri uncle T ɗin ya fice daga cikin ɗakin. Da Areef da mummyn Rimshar tamkar an zuƙe masu jini ne, dan kuwa ciwo iri guda ne yake damunsu. Ko da Dr William ya zo, kallo ɗaya ya yi masu ya ce ai waɗan nan babu rai a jikinsu, sun mutu, dan kuwa ga shi nan har jinin jikinsu ya dena motsawa. Cikin dakiya tare da kwarin gwiwa Lion ɗin ya ce. "No dad, basu mutu ba, suna raye, idan har da gaske Areef ya mutu, to dole dukkanmu zuciyoyinmu zata tsaya da bugawa na ɗan lokaci, sannan kuma idan har da gaske Areef ya mutu dole zamu ji a jikinmu cewa babu shi, kuma dole wasu abubuwanmu zasu ragu, gaskiya bai mutu ba". Ya kai karshen maganar wani irin zufa tana tsastsafo mashi daga gefe da gefen kunnensa. Shiru Dr William ɗin ya ɗan yi kafin ya ce. "Haka ne, in dai Areef ya mutu to dole zasu ji a jikinku, haka su Anderson suka ji lokacin da daddyna ya mutu". "Kana nufin Jacob suma QUADRUPLE ne?". Cewar uncle T. Wato shi uncle T ba zai ce daddyn bama, sai dai Jacob kai tsaye, dan ya jefasu a cikin bala'i. Jinjina kai Dr William ɗin ya yi tare da tabbatar masu ai ainahin haifar QUADRUPLE ya samo asali ne daga kan su Jacob, da Jacob da su Anderson ƴan huɗu ne masu masifar kaunar junansu, shi ne yasa suka kasa yafe mutuwar Jacob ɗin da Dr William ɗin ya zama sanadi, sun kasa hakuri, amma kuma rashin imaninsu ya yi yawa da har suka iya raba jarirai guda huɗun nan, ai shi Jacob sai da suka girma aka rabasu, dama kuma ko Dr William bai yi mashi abin da ya yi mashi a wancan ranar ba, dole a lokacin zai mutu, dan sai kwana ta kare ake mutuwa. Amma kuma gaskiya in dai haka ne Roshan bai yi masu adalci ba, dan kuwa shi ne nan ya bada Jacob a matsayin magajinsa a kungiyar tsafi, da haka da haka har ya bada ƴaƴansa guda huɗun dukka, ka haifi ƴan huɗu gwanin birgewa, sannan dan tabbatar tsinuwar Allah a kanka ka rasa a me yaran zasu kajeka sai a karagar mulki ta tsafi, kuma sai ka rabar da su dukka? Abin kam ba'a magana, ga can wasu suna neman haihuwa ido rufe, haihuwa abin da ba'a sayarsa da kuɗi, hmmmmm. "Dad wannan abin fa tsafi ne ya taɓasu, shi ne ya daskarar masu da jini, Mark mu je ka kai'ni gidan Shaikh Sultan". Cewar Lion, ya kai karshen maganar tare da wucewa gaba. Binsa da kallo kawai suka yi, dan sun san bafa zasu iya dakatar da shi ba, domin Lion ai yama yi kokarin da ya tsaya a iya haka, TRIPLETS nasa sun wuce tunanin mai tunani a cikin zuciyarsa, zai yi fin ninki ba ninkin haka a kansu. Suna fita gidan shi da Mark tare da shirga shirgar motoci masu numfashi da suka take masu baya, basu zame ko'ina ba sai wajen Sheikh Sultan, suna fita daga gidan kuma ruwan sama tamkar da baƙin kwarya ta fara zuba. Rimsha na zaune kusa da baby's ɗin Jehan tana aikin kallonsu, sai ta ji kamar alamar saukar ruwan sama, kai ta ɗago tana kallon sama, kamar zata iya ganin saman daga cikin ɗaki. Shiru ta kasa kunne tana son ta gane wai da gaske ruwa ake yi ne ko kunnenta na jiyo mata karya ne. Ta jima a haka, amma bata iya ganewa ba, dan idan mutun yana daga ta cikin gidan nasu, ko karan ruwan sama ba zai ji ba, sai dai ɗan alama alama. Hakan yasa ta miƙe da sauri dan ta fito waje ta duba, amma kafin ta tafi, sai da ta bi yaran dukka ta rinƙa manna masu kiss a goshi kamar zata cinye masu goshi, har uwar baby's ɗin ma bata bari ba, sai da ta bita ta sumbata, sannan ta diro kasa daga saman bed ɗin, su gwaggo suna ta aikin bule ɗakin da air freshener masu daɗin kamshi bayan sun kammala tsabtace ko'ina tsab. Waje ta nufa da sauri. A hanzarce ta sauko kasa, ita sam bata yarda ta bi ta elevator, stair case take bi abinta, da wasu ƴan kafafunta na under 15 years ɗin nan. Waje harabar gidan ta fito, sai dai ta kasa iya buɗe kofar parlourn nasu har sai da Aseef ya zo wucewa ne ya buɗe mata. Wani irin siririn murmushi tare da tsantsar farinciki ne ya bayyanar mata a saman face nata, sosai ta ji daɗin ganin wannan ruwan saman. Babu wani tunani bare ƙoƙarin yanke hukunci kawai ta afka cikin ruwan abinta, bata damu da cewa ya yanayin gidan yake ba, bata san cewa akwai manya manya Cameras da suke harabar gidan ba, domin gidan da president yake a ciki ai ya zama dole a bashi tsaro fiye da kowani gida a duniya. Duk abin da take yi ana kallonta, sai magana take yi wa ruwan sama, tana wani irin tsantsar farinciki. "Rimsha wato ba zaki girma ba ko?". Wata zazzaƙar murya ce ta yi mata magana ta bayanta. Ba tare da ta juya ba ta ce. "Malika kema ba zaki canza hali bako? Sai mutun yana tsaka da jin daɗi kike zuwa ne?". Ta kai karshen maganar tare da juyowa. Ido huɗu suka yi da Malikar, sakarwa da juna murmushi suka yi kafin Malikar ta ce. "Ni yanzu ai ba wajenki nazo ba, wajen mummy nazo, munji cewa bata da lafiya, shi ne aka turoni na dubata". Mamaki ne ya bayyana a saman fuskar Rimshar. "Mummy kuma? Waye ya ce maki mummy bata da lafiya? Waye ya ce maki mummy ma tana nan? Mummy bata nan, kuma a ina ma kika san Mummyn?". Nisawa Malikar ta yi kafin ta bata amsa da cewa. "Tun kafin na sanki na san mummy mana, tun kafin a haifeku muke tare da ita, amma ita bata sanni ba". Guntun murmushi Rimshar ta yi kafin ta ce. "Amma gaskiya kekam Malika kin iya maganar banza, wani wai tun kafin a haifemu kike tare da mun, kalleki fa, tsawona ɗaya dake, amma shi ne kike cewa tun kafun a haifeni kike tare da mummy? Hala lokacin kina jaririya ne? Dan wlh ni dai nasan ko kin fini shekaru to da shekara ɗaya ne, amma kike zancen manya, Allah Malika kin iya tsara magana kamar wata babba". Da yake Malikar tasan cewa Rimshar yarinya ce, sai bata ɗauki zafi a kan maganganun Rimshar da ta gaya mata ba. "Amma kema Rimsha kin iya maganar banza fa, wuce nikam ki fita daga cikin ruwan nan kada mura ya kamaki ki kara mana zafi a kan zafi, kuma ga can motocinsu Saif suna kan hanyar dawowa, idan baki fita ba, kin san sauran, sai ya fasa ɗan bakin nan naki". "Nifa Malika ba zan fita daga cikin ruwan nan ba har sai an ɗauke, kawai jeki abinki, Yah Saif kuma ba zai yi mun komai ba, sai dai ya ɗaure fuska ya ce kada na kara". Girgiza kai Malikar ta yi tana faɗin. "Amma ai kin ce mashi kin yi alkawari ba zaki sake shiga cikin ruwan ba, ko kin manta ne?". Kara faɗaɗa murmushin dake a saman face nata ta yi kafin ta ce. "Wannan alkawarin tsoro ne, barazana aka mun na yi shi, dan haka ba zan dai'na ba, ke dai kawai ki tafi abinki". Ganin motocin su Lion ya danno kai cikin gidan ne yasa Malikar ta ɓace daga kan idanun Rimshar, sai dai bata tafi ba, tana wajen, dan tana jin daɗin ganin diramar Lion da Rimshar. Ita kuwa Rimshar bata ma san sun shigo cikin gidan ba, dan harabar gidan gari ne guda, parking space yana ta gefe can, bazaka san mutane sun shigo gidan ba idan kana ta gefen shiga ainahin cikin gidan, dan haka da taga Malika ta tafi, sai kawai ta cigaba da sharholiyar tana juyi kamar wata mai tafiyar maciji. Tana tsaka da juyawa tana rera wakar. Da kai ne zan yi, amma a maimaƙon ta ce da kai ne zan yi wuff, sai dai ta ce da Noorish na zan yi wuff, abin gwanin ban dariya, har yanzu akwai yarinta sosai a kanta. Bata ankara ba sai ji ta yi ta bugi mutun wanda ko bata ɗago ta kalle shi ba tasan wanene, daga yanayin tsayuwar Lion chest nasa da take kyam har izuwa kamshin perfume nasa, hakan ne yasa ta gane wanene. A dubu ɗari ta yi baya baya zata faɗi. In da dai ya saba riƙota idan zata faɗi, wato wuyar rigarta, a yanzu ma nan ya riƙo tare da ɗan daidaita mata tsayuwarta yana kallon face nata. "Ban hanaki shiga cikin ruwa ba?!" Ya yi maganar tamkar mai jin barci, da alama akwai gajiya sosai a tattare da shi. Tsuru tsuru ta yi da idanu tana tunanin me yakamata ta ce mashi, dama idan baku manta ba, time da ya hanata shiga ruwan, a cikin zuciyarta ta ce ba zata dai'na ba, ga shi kuwa bata dai'na ɗin ba. Malika dake laɓe tana kallonsu me zata yi banda dariya, barema da ta ga Rimshar ta yi tsuru tsuru da idanu, abin ba ƙaramin dariya ya bata ba, kamar ba yanzu Rimshar ta gama cika mata baki a kan Lion ɗin ba zai yi mata komai ba. "Ba dake nake magana ba ne?". Ya sake jefo mata wata tambayar. Ɗan satar kallon hanyar guduwa izuwa cikin gida ta yi, dan ta samu ta gudu, sai dai kuma ai jikinta akwai ruwa over, tana guduwa zata zame ta faɗi kasa, ya zata yi kenan?. Ta tambayi kanta da kanta. Kallon gefen ido ya wurgawa Mark dake tsaye a gefensa. Tun bai yi magana ba Mark ɗin ya miƙa mishi jakar Sheikh Sultan ɗin dake a rike a hannunsa tare da sa kai ya wuce abinsa, dama saboda jakar ya tsaya bai wuce ba. Shi kuwa Al Shaikh yana cikin mota ba zai iya fita a cikin ruwan nan ba. Binsu kawai da idanu yake yi babu ko kyaftawa. Ganin bata da mafita ne yasa ta fara ƙoƙarin magana tana in ina. "Kayi hakuri na manta ne, kuma na tuba ba zan sake ba ka ji?!". Tana magana kamar da gaske, alhalin karya take yi, gobe ma taga ruwa sake shiga zata yi. (Wlh Rimsha ƴar dirama ce😂) Sarai ya sani ba wani mantawa da ta yi, iya shege ne kawai, yasan halinta, ba kasafai ta cika mance abu ba, musamman ma da ya kasance maganarsa ce, ba zata taɓa mancewa ba. Dan haka sai ya kara ɗaure fuska sosai na wuce misali, dan ma ta san yanzu ba da wasa yake yi ba, a kan wannan shiga ruwan zai iya zaneta sosai wlh. Yana ƙoƙarin yin magana tamkar daga sama ya ji an ambaci sunansa daga bakin kofar shiga parlourn. Ko bai ɗago ba yasan wacece, dan muryarta ita kaɗai ce ba ta biyunta a zuciyarsa. Kin ɗagowa ya yi su haɗa idanu, sai ma ya yi kamar bai ji ba, dan so yake yi ya hukunta Rimsha. "Saif ka kyaleta ka zo". Cewar gwaggon dake tsaye a kofar parlourn. Ita gwaggo tasan amanar da yake a tsakanin Rimsha da ruwan sama, tun suna Dubai haka take, komai sanyin da ake yi sai ta shiga ruwa idan aka yi, yanzu ku duba mani uban sanyin da yake a U.s ɗin nan, amma hakan bai hanata shiga cikin ruwan sama mai uban sanyi ba. Jin abin da gwaggon ta ce ne yasa ya kama hannun Rimshar kawai suka nufi cikin gida. Sam ba haka Malika ta so ba, ta so ya bata mari ko guda ɗaya ne, dan Rimsha bata ji, basu son tana shiga cikin ruwan sanyin nan, amma sam bata ji. A parlourn ƙasa ya saki hannunta tare da wucewa sama, a lokacin shi kuma Mark ya shigar da Sheikh Sultan, dan ya yi mashi amfani da lema ne suka shige ciki. Shaikh Sultan dattijon arziki dattijon kirki, yana ganin su Areef ya fahimci tsafi ce ta ɗan taɓasu, dan haka sai ya fara aikin zuba masu adduo'i babu kama hannun yaro. A kusa da su Lion, sir Safwan, and Aseef suka zauna, shi kuma Dr William sai ya fara aikin cirewa uncle Herry bullet ɗin da yake jikinsa. Gwaggo kuma ta gama aikin Jehan ta zo ta fara aikin duba daddyn Rimsha, dan kafafunsa suna ciwo sosai. Izuwa yanzu gabaɗaya gidan sun san da cewa su daddyn Rimsha sun dawo, dan haka kan kace me sun cika word room ɗin nan tab. Ita kuma Hjy Rimsha uwar rigima, da farko da Lion ya barta a parlourn ƙasa ya haura sama, ta so ne ta koma wajen ta ɗan kara shiga cikin ruwan saman, saboda tsabar rashin jin magana, shiyasa Malika ta so Lion ɗin ya bata koda mari ɗaya ne, kila zata rinƙa jin magana. Amma kuma da ta sami labarin su mummynta sun dawo, ai kuwa da gudu ta haura sama, a gaggauce ta canza kayan jikinta, ta fasa wanka a ruwan saman. Bayan ta gama canza kayan ne tana ƙoƙarin fitowa waje daga bedroom ɗin nasu, shi kuma Lion yana sako kai, karo suka ɗan yi. Baya kaɗan ta koma tana faɗin. "Noorish wai su mumnyna sun dawo?". Hannu ya kai ya tura kofar bedroom ɗin. Yana turata kuma ta rufe kanta, bai ce da ita komai ba ya wuce ya nufi toilet ya barta tsaye a wajen. Bata damu ba ta nufi hanyar fita, sai dai kuma kofar a rufe, bata iya buɗe kofofin gidan ba, dan dayawansu ma da fingerprint suke aiki, wasu da card, hakan yasa bata iya buɗe kofar ba. Tamkar zata yi kuka ta koma saman bed ta kwanta tana jiransa ya zo ya buɗe mata ta fita. Shi kuwa samun tabbacin su Areef zasu iya tashi ko yanzu daga bakin Sheikh Sultan ne ma yasa ya dawo cikin bedroom nasa dan ya yi wanka, Sheikh Sultan ya ce kowani lokaci tsafin zai iya sakinsu, yana sake su kuma zasu koma normal kamar babu abin da ya taɓa taɓasu. Bayan ya yi wanka, cikin pajamas ya shirya, sannan ya sanar da cewa kada wanda ya dame shi a yau, dan yana da abin yi nasa na kansa. A saman bed ya iskota, sai latsa mashi waya take yi tana jiransa ya zo ya buɗe mata kofa ta fita. Kwanciya ya yi tare da kurawa Tv idanu yana kallon kyawawan baby's ɗin Areef, sai ɗaga hannayensu sama suke yi, ga Jehan ɗin kuma sai zuba barci take yi, su gwaggo sun gasa mata jikinta da ruwa mai zafi, sannan suka yi mata alluran barci, dan ta huta. Ganin yana ta kallon yaran ne yasa Rimshar ta ce. "Noorish mu kuma sai yaushe zamu haifi namu?". Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali kafin ya dawo da kallonsa a kanta. "Ai ina ganin ma yanzu zaki karɓi naki baby's ɗin, ba dai kin shirya ba?". Ya yi maganar yana ɗaga mata gera ɗaya. "Wlh Noorish na shirya, ko yanzu ka bani". "To zo ki karɓa". Ya faɗa tare da jawota jikinsa. "Noorish iya baby's fa kawai zaka bani, irin na Jehan ko Akila nake so". Kasa kasa ya ce mata. "Fin haka ma zan baki, mu our baby's special ne". Ya kai karshen maganar tare da haɗe fuskokinsu, cikin salo ya fara aiwatar da abin da yake da niyya. "Noorish baby fa kawai zaka bani". Ta faɗa a ɗan tsorace. Katseta ya yi ta hanyar zuwa mata tongue nasa a cikin ɗan bakin nata, hakan yasa ta yi shirun dole ta fara karɓar sako. Ai yau ma ba shi ya kyaleta ba har sai da ya fanshe kewarta na tsawon watannin nan da ya yi, sannan ya rabu da ita. Ban da kuka hawaye bibbiyu babu abin da take yi mashi, ta ji a jikinta ne ba karya. Rarrashi ya hauyi babu kama hannun yaro, sam taki kula shi. Ganin haka sai ya ce ta yi shiru bari ya je ya yi mata wanka sai suje wajen mummynta. Jin hakan yasa ta danne ta yi shiru, tana jin raɗaɗin zafi kam, amma a haka ta danne, dan tana son ganin mummynta. Sumbatar lips nata ya yi yana faɗin. "I really love you my Meesha". Turo bakin nan ta yi, kamar zata sa kuka ta ce. "Love you too". Ta yi maganar kamar wadda aka saka dole. Kamar zai sake yin magana, sai kuma ya fasa tare da miƙewa ya ɗauketa sai cikin toilet. Wanka ya yi mata kamar yadda ya faɗa, sannan ya naɗota a towel ya dawo da ita saman bed, ya koma cikin toilet, dan ya yi nasa wankar, taki yarda su yi a tare ne, har wa yau kunyar yin wanka tare da shi take yi, shiyasa yake fara yi mata kafin ya yi nasa. Kafin ya fito daga wanka har ta shirya cikin wata abayar, ta haye saman bed ta kwanta, ta yi shiru tana jin raɗaɗin da gabanta yake yi mata. Har ya fito ya gama shiryawa bata sani ba, ta afka duniyar tunani. Bayan ya kammala ne ya dawo wajen bed ɗin. "Let's go". Ya faɗa yana ɗaure dark black curly hairnsa a bayan wuyarsa. Make mashi kafaɗa ta yi, ta ce sai dai ya ɗauketa cak, dan ita bazata iya tafiya da kafafunta ba. Bashi da zaɓin da ya wuce ya yi hakan, dan shi ne nan ya ja mata ai. Dan haka sai ya ɗauketa cak suka nufi wajen. Sai shafa kyakkyawar bakin gashin sajensa take yi tana sumbatar wuyarsa. Kasa kasa kamar mai raɗa ya ce "Zaki fara ko? Ki cigaba, ai ban yi nisa da bedroom ba, sai na juya na mayar dake ciki, dama ni ban ƙoshi ba, kawai ragwantarki yasa na barki". Ganin sun ɗan yi nisa da part ɗin nasu ne yasa ta ce. "Allah Noorish ni ba raguwa bace ba". Cak ya tsaya da tafiyar yana tambayarta. "Are you sure?". Ganin ya tsaya ne, kuma tasan tsab zai iya juyawa da ita su koma ciki ya bata ajikinta ne yasa ta yi sauri girgiza kai tana faɗin. "Am not sure, wlh yanzu ma wajen ciwo yake yi mu" Ta kai karshen maganar kuma tare da saƙalo wuyarsa ta ɓuye fuskarta a wajen wuyar tasa. Cigaba da tafiya ya yi ba tare da ya sake ce mata komai ba, ƴar rigima kawai. Bai direta a ko'ina ba sai a cikin room ɗin, a lokacin kuma Allah da ikonsa mum ta farfaɗo, ta kuma dawo normal kamar yadda Sheikh Sultan ya faɗa, shi kuma Areef bai dawo normal ba, yes ya farfaɗo, amma kuma bai dawo dai'dai ba, dan lokaci da ya farfaɗo ya farfaɗo ne da karfi tare da fara yunkurin barin cikin ɗakin, su Uncle T ne suka danne shi, sai fisge fisge yake yi. Da kyar suka samu suka dannesa ya nutsu Sheikh Sultan ya cigaba da yi mashi addu'a, daga haka barci ta ɗaukesa bawan Allah. Mummy kuwa, ta dawo dai'dai sai hira da su gwaggo ma take yi, dama tsafin ne ya taɓata, a wajen faɗar tasu ne ma aka samu akasi su Anderson suna ƙoƙarin jefar daddyn Rimsha da abin tsafin, sai ya taɓata ita, shi ne ya kandarar mata da jiki kamar ta mutu. Amma da yake babu abin da yafi karfin Allah, ayar Allah ba wasa ba, sai ga shi cikin hukuncin Ubangiji ta dawo dai'dai normal abinta. Shi kuwa Areef sai washegari suka samu ya dawo dai'dai. Yana dawowa dai'dai kuma Jehan ya fara nema, a nan ne Lion ya gaya mashi tana nan lafiya kuma ta haifa mashi ƴan huɗu jiya, ita ma tun jiyar take ta faman barci kamar me, ta gaji ne over, shiyasa take ta zuba barci kamar ba gobe baiwar Allah. Mummyn Rimsha baki har kunne, ta ji daɗin samun jikoki QUADRUPLE, sai uban murmushi take yi abinta. Cikin zumuɗi Areef ɗin ya ce zai je ya kalli Jehan ɗin. Hana shi Lion da sir Safwan suka yi, suna son ya ɗan huta, Lion ya ce da gwaggo a kawo mashi baby's ɗin nan ya kallesu, sai zuwa dare idan ya kara hutawa, sai ya je ya kalli maman babyn. Haka kuwa aka yi, gwaggo ta je tare da Josephine suka ɗauko baby's ɗin, gwanin ban sha'awa. Ana miƙa mashi ɗaya ya karɓa yana sakin cool murmushi. A fili ya furta "Ga takwaran Saif nan, na hannun momma kuma takwaran Safwan, ɗayan na hannun Josephine takwaran Aseef, ɗayan kuma takwaran uncle ne (daddyn Rimsha)". Ya kai karshen maganar yana ɗago da kallonsa izuwa kan Lion ɗin. "Lion yakamata ka rike takwaran nan naka fa". Ya faɗa yana miƙo mashi babyn. Sam Lion ɗin bai so ɗauka ba, amma kuma saboda babyn yana tsananin kama da Areef ɗin, ga shi kuma takwaransa ne yasa ya kai hannu ya karɓi yaron, sam baya son ya kalli wannan murmushin dake a saman face ɗin Areef ɗin ta kau, shi ne yasa ya karɓi baby, dan in bai karɓaba tabbas wannan murmushin zata kau daga saman face ɗin Areef ɗin. Karɓar yaro na biyu daga hannun Josephine Areef ɗin ya sake yi yana kallon babyn sosai, nan take wasu siraran hawaye suka fara bin kuncinsa. Zuba mash idanu Lion ɗin ya yi yana kallonsa da mamaki. "Areef meyasa kake kuka kuma?". Cewar sir Safwan, ya yi maganar a ɗan ruɗe. Nisawa Areef ɗin ya yi kafin ya goge hawayen nasa yana faɗin. "Dole nayi kuka, Allah mai kyauta mai kari, ya bani ƴaƴa maza har guda huɗu, tamkar fa yadda aka haifemu mu huɗu, kamar yadda Allah ya albarkaci daddynmu da samun mu mu huɗu, haka ya sake kara mana da wasu huɗun, wasu suna can suna haukar neman haihuwa, abin da kuɗi, mulki, isa, taƙama, izza, kai komai bai isa ya bada haihuwa ba, Allah shi kaɗai yake bayarwa, dole na zubar da hawayen farinciki". Gwaggo ce ta ce mashi "Bama iya kai kawai ba, Aseef ma Allah ya bashi TRIPLETS kuma dukka maza". Zaro ash eyes nasa ya yi yana mamaki, abin kamar a mafarki yake jinsa. Haka suka kasance cikin tsananin farinciki har Allah ya sauki Anaya lafiya a cikin wannan sati da Jehan ɗin ta haihu, ratarsu kwana huɗu, ita kuma Anaya ta haifo TWINS kamar daddynta kenan, idan baku manta ba daddynta ai ƴan biyu ne da daddyn Rimsha, so ita ma TWINS ta haifa, ta gado kenan. A nan ne fa gwaggo ta ce yana da kyau su shirya gagarumin walima na murnar samun wannan ni'ima da Allah ya yi masu, dan haka yana da kyau su Abban Imran su Abbi da sauran dangi duk su zo, su zo ayi taron suna tare da wannan walima, idan ya so daga baya sai su koma. Haka kuwa aka yi, Brr Naurat ta buƙaci kowa da ya zo, harda daddyn Anaya da mum nata sun zo, su Irfan harda Ummin Dr Nawid kowa ya zo, daddyn Adiva shi ma yazo, mummynta ne dai shiru ba'a san in da take ba, ta mutu ko tana raye, Allah masani. An shirya walima sosai na wuce misali, amma ba'a gidan za'a gabatar da walimar ba, a wani tapkeken hall za'ayi shi, sai shirye shirye suke yi, gobe ne walimar, sai hidima ake yi tamkar baza'a mutu ba. Su gwaggo anje shopping ya kai sau biyar, sai ta sawowa ƴaƴan nata kuma matan ƴaƴan nata kaya, sai taga bai yi mata ba, haka zata sake tasan jiga jigan motoci ta sake komawa shopping ɗin, sai sharholiyarta take yi, tana so ne matan ƴaƴan nata su tashi kan al'umma da haɗuwa ranar walimar. Da misalin karfe 9 na dare, gabaɗaya familyn sun haɗu a parlourn ƙasa, sai hirar yaushe rabo ake yi. Rimsha ta tada kai da cinyar mummynta, ita kuma Jehan tana kusa da gwaggo, baby suna ɗakin gwaggo tare da Ummin Dr Nawid, ta ce ita ba zata fito parlourn ba, zata zauna a tare da baby's ɗin, uncle Herry ma duk da bai gama samun lafiya ba, ya fito parlourn ana hira da shi, sai tambayar ina matarsa mamansu John yake yi, an rasa wanda zai iya gaya mashi ta mutu bata raye. Jay da su John duk kowa yana nan, Jellyn Yah Imran dai har yanzu shiru babu ciki, ga yaron su Akil har ya yi wayo, amma su shiru har yanzu, sai more duniyarsu suke yi abinsu, ga wani uban kyau da Jellyn ta kara kamar me. Umaisha ce ta kunna masu wakar zuri'a guda tsintsiya guda babu mai rabawa, soyayyar gaske ake in da rai da lafiya ba zaku ganmu a rana ba, a wayarta ta kunna wakar. Sai murna suke yi, shi kuma Lion so yake ya tashi ya ɗauki Rimsha su wuce ɗaki, dan fa shi sun takura mashi, yana jinsa a sama, ga Rimshar taki zuwa wajensa, ta wani maƙale a jikin mummynta kamar wata jaririya. Sai bibiye wakar ƴan matan suke yi. Jin anzo wajen wata baiti yasa Rimshar ta miƙe zaune tare da zuro kyawawan kafafunta kasa ta miƙe tsaye tana bibiye wakar. Wajen Lion ɗin ta nufa tana bibiye baitin da suke cewa. "Innayo tunawa na tuna cewa kai ne mijinawa ba, sai in ji da sanyi zuciyata ta dai'na yin kuna". Ta kai karshen baitin tare da zama a kusa da Lion ɗin babu ko kunya, yanzu sun koya mata rashin kunyarsu ita ma. Dama shi Lion jira yake yi su haɗa ido ya ce ta zo, sai ga shi kuma ta kawo kanta dalilin baitin waka, dan haka sai ya miƙe tare da ɗaukarta cancak ya keta gabaɗaya family ya wuce sama da ita abinsa. Kada ku manta dukka familyn dai jirgi ɗaya ya kwasosu, wato dai jinin turawan ne, dan haka ko a jikinsu, ko kallon Lion ɗin ma basu yi ba, suka cigaba da hiransu. Akila ce ta sake miƙewa tana bin wata baiti da ake cewa. "Inna sake waigawa naga ƴaƴan dake garemu, dani da kai dole mu gobewa wanda ya bamu, shi ne wanda yasa mun haɗa kanmu ana ganinmu, ni na tabbata bazaka mun abin da bazana so shi ba". Ta kai karshen baitin ita ma tare da zama kusa da Aseef. (Yaran nan sun zama ƴan duniya🥱😒 duk sun zama marasa kunya, dama ita gwaggo uwar miji sam ba'a jin kunyarta😂 kaka ma suka mayar da ita, ɗan gara Dr William ma suna raga mashi😂) Ai kuwa Akilar tana zuwa kusa da shi, shima ya capkota, dama tun jiya yake lallaɓata a kan tazo suje bedroom nasu ta ki yarda, ta ce mashi wlh sai ta yi arba'in zata dawo, ya yi ya yi har ya gaji, har kuka sai da ya yi mata, amma ta murje idanu taki yarda ta bishi, ya gaya mata shi fa a gaskiya sha'awarta tana neman kashe shi, sai tace mashi ai tana jini, kuma karya take yi, tun last week ta yi tsarki, kawai binsa ne ba zata yi ba, to ga shi ita ma ta kawo kanta sanadiyar baitin waka, ai kuwa ya capkota, tana ƙoƙarin guduwa ya damketa tare da ɗagata cak yana faɗawa gwaggo sun tafi sai da safe.............(😂 Allah ka shirya mana Aseef, shi harda sai da safe ma ya yi wa family😂) Ganin haka yasa Umaishar ta miƙe tana dariya tana faɗin. "Wakar zuri'a guda dai ta haɗa wata zuri'ar". Akil ne ya ce. "Abba muma mun shiga sai da safe". Ya kai karshen maganar tare da riƙo hannunta suka wuce nasu masaukin, suna tafiya yana gaya mata ita ma yanzu zai bata wani zuri'ar tun da babynsu ya yi wayo. Jelly da ta ga haka, sai ta lallaɓa ta gudu sama wajen Ummin Dr Nawid abinta, dan dama ta gaji da jarabar Yah Imran ɗin nan nata. Allah sarki Ummin Dr Nawid, akwaita da bala'in son yara, Dr Nawid shi kaɗai Allah ya bata kuma ya karɓi abinsa, kunga kuwa dole yanzu da taga yaran Akila da Jehan dole ta ruɗe baiwar Allah, dole ta ce ita zata zauna tare da su a cikin ɗakin. Shi kuma Handsome babu kunya babu komai ya ce da gwaggon shi fa yana son wannan karamar yarinyar, ta burge shi sosai, dan haka ya yi mata. Kallon yarinyar da ya nuna gwaggon ta yi, ita da kanta bata san ƴar wacece bace, amma dai tasan familynsu ne. "Wacece wannan ɗin?". Ta tambaya tana kara karewa yarinyar kallo. Daddyn Rimsha ne ya bata amsa da cewa. "Zaira ce kanwar Anaya ƴar Azharuddin". Kun san halin gwaggo da shegen son fadanci da nuna isa, dan haka sai ta ce. "Ba komai Handsome na baka ita, ko yau kake so sai a ɗaura maku aure". Jama'a kunji karfin hali wajen gwaggo, dan kawai ita ce yayar su daddyn Anayar, wato ko suna so ko basu so ita ta bada Zaira. (Hjy Gwaggo ikon god😂) Wani irin daɗi Handsome ɗin ya ji, cike da murna ya zo ya ɗan rungumi gwaggon yana zuba mata godiya. Ganin haka yasa shi ma Irfan ya ce da gwaggon yana son Pinky. Aikuwa kara ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya gwaggon ta yi tare da shaida mashi cewa shima ta bashi aurenta, ba kuma wanda ya isa ya hana. Hjy Gwaggo sarkin son mulki. Dr William kam da yake yasan halin kayarsa, sai ya ce ai bama wanda ya isa ya hana maganarta, dan haka kamar yadda ta bada aure, to ba mai hana wannan auren sai wani ikon Allah, dan haka shima ya bada Pinky ga Irfan. Miƙewa Irfan ɗin ya yi tare da zuba masu godiya kafin ya wuce nasa masauki, alwala ya je ya yi ya fara sallah tare da rokar Allah da yasa Pinky matarsa ce, kada a fasa bashi kamar yadda aka yi mashi a kan Akila, har ga Allah yana tsananin son Pinky sosai da kallon farko. Gaskiya Irfan ya more mata, kada ku manta Pinky fa kyakkyawar gaske ce, jinin jajayen kunnuwa, kama da su Lion take yi, ai kuwa ya more......😌 Da haka da haka family suka watse kowa ya yi nasa ɓangaren, dan suje su kwanta su huta gobe suna da gagarumin Walima. Asuba ta gari. Washegari🤍 LOVE PERIOD❤️🕊️ Tun karfe 7 Rimsha ta farka, dama sun mayar da barci da suka yi sallar asuba, so da yake tana son zuwa wajen walimar, sai ta tashi tun 7, shi dai Lion ya ce ba zai je walimar ba, hakan yasa ma ita ta yi saurin farkawa dan ta shirya. A hankali ta zame jikinta daga nasa, dan ya rungumeta ne suka yi barci. Cikin dabara a hankali take ƙoƙarin sauka ta bar saman bed ɗin. Sai dai....... FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA CE.....✍️🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E53 A hankali ta zame jikinta daga nasa, dan ya rungumeta ne suka yi barci. Cikin dabara a hankali take ƙoƙarin sauka ta bar saman bed ɗin. Sai dai kuma ta manta da cewa bashi da nauyin barci, dan haka tana ƙoƙarin sauka ya capkota, idanuwnasa a lumshe ya jawota jikinsa. "Where are you going?". Ya faɗa can kasan maƙoshinsa, da wata iriyar murya mai matuƙar shegen daɗi, ga shi a sanyaye fiye da yadda yake magana ya yi ta. "Wanka zan je fa na yi Noorish". Ta bashi amsa a shagwaɓe. "To ni kin sallameni ne?". Ya yi maganar tare da waro idanuwansa a saman face nata. Ta wani tsuke ɗan bakin nan nata kamar ya ce zai yi mata kiss, ita ala dole ta ji haushin ya ganota zata gudu. Gera guda ɗaya ya ɗaga mata yana mai cigaba da kallonta, idanuwansa sai wani kyalli suke yi. Turo mashi bakin nan ta ɗan yi kafin ta matso ta shige jikinsa. Hannunta ya kama tare da ɗaurawa a saman Heronsa dake tsaye kyam. A kunne ya raɗa mata cewa abinci yake son ci. A shagwaɓe ta ce. "Allah Noorish kai ko, wai shi baya ƙoshi ne?". A kunne ya raɗa mata. "Tambaye shi mana, baga hannunki a kansa ba?". Zame hannun nata daga wajen ta yi tare da mayarwa saman mararsa tana shafawa a hankali. Da ɗan karfi ya furta. "Wash my Meesha". Ya yi maganar tare da kara matseta sosai a jikinsa. Tana ƙoƙarin yin magana ya yi saurin haɗe bakinsu waje guda, cikin salo ya fara bata zazzafar kiss mai tashin kai. Cikin so da tsananin kaunarsa ta fara mayar mashi da martani babu kama hannun yaro. Nan take suka shiga farantawa juna rai babu wasa. Ba shi ne ya rabu da ita ba sai karfe 9:30, nan ma sai da ta saka mashi kuka, sannan ne ya kyaleta yana mai ce mata raguwa kawai. Bata ce mashi komai ba, dan tasan idan ta ce mashi wani abin ma sake komar da kanta ruwa zata yi, ita kuma sam ba haka take so ba, so take yi ta je ta hau shirin zuwa wajen walimar da za'a gabatar anjuma, tun daga karfe 12 za'a fara har zuwa lokacin da Allah ya yi za'a gama, ba karya Lion and sir Safwan sun kashe maƙudan kuɗaɗe a wajen wannan walimar, saboda iya kaya da motocin da suka tanada za'a rabawa al'umma ma kawai abin ba'a magana, shugaban kasa guda ace Familynsa zasu yi walima ai kunga dole dollars su ci ubansu, dole dollars su yi kuka. Cigaba da kwanciya shi kuma Lion ɗin ya yi, dan duk jikinsa a mace yake, baya jin kamar zai iya tashi, ita kuma sarkin son zuwa wajen walimar, tuni ta miƙe ta lallaɓa zuwa cikin toilet. Yana jinta ta yi wanka ta fito, shiryawa ta yi cikin wata abaya kafin ta zo ta gaya mashi ta tafi wajen gwaggo. Bai amsa mata ba, bai kuma kawar da kallonsa daga kanta ba, ya tsareta da idanu sosai kamar nace zan rabasu. "Noorish lafiya? Meyasa kake ta kallona haka kaki yin magana? In tafi ne?". Nisawa ya yi ba tare da ya kawar da kallon nasa ba, a hankali ya motsa laɓɓansa tamkar suna yi mashi ciwo, kasa kasa ya ce. "Ban ƙoshi bane". Ya yi maganar yana cigaba da kallonta. Zama ta yi a gefen bed ɗin tare da juyowa gare shi sosai, cool murmushi ta sakar mashi kafin ta ce. "Tom bismillah". Ɗan zaro mata idanu kaɗan ya yi kafin ya jawota jikinsa. A kunne ya raɗa mata ta yarda ya kara?. Sumbatar kumatunsa ta yi tare da cewa. "E mana Noorish, ka yi har iya yadda ya isheka, In Sha Allah Allah zai baki ikon iya jurewa, da na shiga fushin Mala'iku da tsinuwar Allah na ka buƙaceni naki ba gara na jure ko zan mutu na baka hakkinka ba, na san ko na mutu ta haka zan huta, me aka yi aka yi zuwa wajen walima? Meyasa zan yi zumuɗin zuwa wani waje bayan mijina yana buƙatata a kusa da shi? Kawai ka yi abinda kake so". Tabbas abin da take faɗa har cikin zuciyarta take faɗarsa. Daɗi sosai ya ji, sumbata ya kai mata a saman ɗan bakin nan nata kafin ya ce. "I really love you my Meesha, jeki abinki, dama na gwadaki ne naga da gaske zaki iya bani idan na buƙata, da gaske zaki iya daurewa a kowani irin hali kike ciki wanda bai saɓawa Allah ba ki bani, sai kuma ga shi kin bayar ɗin, Allah ya yi maki albarka, jeki ki gaida Momma sai na yi wanka ina zuwa wajen nata nima". Ya kai karshen maganar tare da manna mata sumbata a ɗan bakin nata again. Cool murmushi ta sake sakar mashi kafin ta kai ɗan bakin nata ta capko lips nasa na ƙasa. Kissing nasa ta fara yi cikin tsananin so da kauna. A saman mazaunanta ya ɗaura hannunsa guda ɗaya yana karɓar sakon nata tare da lumshe idanuwansa. A hankali ya fara yawo da hannunsa a saman bayan nata, yana matuƙar kaunar mazaunan nan nata. Sun ɗan jima a haka kafin ya daure ya saketa, dan baya son ɓata mata rai, ta faranta mashi rai sosai yau da safen nan, so ba zai so ya yi mata abin da zata ji babu daɗi a cikin zuciyarta ba. Miƙewa ta yi tana mai gaya mashi da ya kula mata da kansa sosai. Sai ta dawo ya yi mata tare da gaya mata ta kula sosai ita ma. Okey ta amsa da shi tare da nufar kofar fita. Da kallon tsantsar so da kauna ya bita da shi har ta kurewa ganinsa. Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali kafin ya miƙe zaune, wani irin azababben sonta ne yake kara narkuwa mashi a cikin zuciyarsa. Da kyar ya iya miƙewa ya nufi toilet, jikinsa duk a mace yake, ta saukar mashi da kasala. Ita kuwa tana zuwa part na gwaggo ta isko Josephine tana ta cancaɗawa su Jehan make up, ga gwaggo ma ta shirya cikin dandatsesiyar Dubai abaya mai bala'in kyau, ta fito a uwar His Excellence ɗin da kansa, kyau iya kyau, yau sai ta yi kama da Aseef sosai, sai nanata kalmar kamar tasu Josephine take yi. Gabaɗayansu Josephine ta tsara masu kwalliya, har ita kanta Rimshar da gwaggo ta ce ta cire abayar jikintan nan, kayan indiyawa zasu saka yau, sai murna suke yi. Mazajensu suna nasu bedroom ɗin suma suna shiryawa, Lion ne kawai ya ce shi ba zai je taron ba, ba kuma zai je office ba, kwanciya zai yi a gida, su je sai sun dawo. Su sir Safwan kam duk sun shirya cikin wasu shegun suit masu bala'in tsada abinsu, sai tashin fitinannen kamshi suke yi, shiga iri ɗaya suka yi a matsayinsu na QUADRUPLE, haka zalika matan nasu ma gabaɗaya kwalliya iri ɗaya Josephine ta yi masu, dukkansu sari Pink color suka sanya. Rimsha sarkin son ta yi kyau, tuni ta saki dark black curly hair nan nata har baya, ga wani uban sarkar diamond da gwaggo ta ɗaura mata a ƙugunta, abin sai ya tashi kai matuƙa gaya, ta yi wani irin azababben kyau. Dukkansu Josephine ta feshesu da perfume mai bala'in daɗin kamshi. Sai santin kyan da suka yi gwaggo take yi, ta yaba ta sake yabawa. An shirya baby's cikin wasu shegun kaya masu matuƙar kyau, sannan aka jibga masu wasu uban kayan sanyi masu bala'in kyau da tsada a saman kayan nasu, sai wani irin bala'in kamanninsu da iyayensu maza ya bayyana, a cikin baby's ɗin Areef guda ɗaya ya fito mai tsananin kama da gwaggo sosai, ɗayan kuma tamkar Aseef, biyun kuma da shi suke kama, kuma biyu daga cikin baby's ɗin ne suka ɗauki kalar idanuwnasa wato ash color, saura biyun dukka idanunsu irin na Jehan ɗin ne, suma baby's dai sun yi gadon dara daran idanuwan Dr Salman, dattijon nan ya rabar masu gadon idanu kam, akwai su da dara dara ba karya, da wannan idanu ake iya gane cewa jinin Dr Salman ne, dan duk kusan design na idanun nasu iri guda ne, sai dai na wani ya fi na wani girma, amma duk idanun Dr Salman ɗin ne. Har karfe 11 ana ta wannan uban shirye shiryen, baki ma ya yi kaɗan ya zayyano irin shirin da suka yi wa walimar nan, sun yi kyau na wuce misali. A cikin waɗan nan sabbin motocin da aka saiwa His Excellence Saif za su tafi, Lion ɗin ne ya ce a ɗaukesu a cikin motocin, duk da cewa already an sayawa mahaifiyar His Excellence nata motar, haka zalika ita ma matarsa, amma ya ce ina su tafi a nasa motocin. Suna ƙoƙarin fita, wasu ma har sun yi gaba sun sauka parlourn kasa, part ɗin ya rage daga Jehan, Rimsha sai kuma gwaggon, su ne suka yi bayan sauka kasa, ana can kasa an haɗu a parlourn ana jiransu, su kuma sun tsaya jiran Rimsha tana aikin ɗaure igiyar uban high heels da take sanye da su a kyawawan kafafunta. Bakinsa ɗauke da sallama kasa kasa ya shigo cikin bedroom ɗin. Wani irin cool murmushi gwaggon ta sakar mashi tana faɗin. "Sai yanzu ka tashi?". "No sai yanzu dai na iya fitowa, amma tashi kam tun ɗazun na yi shi". Ya faɗa yana ƙarisowa cikin ɗakin. Tun da ya sako kyawawan kafafunsa cikin wannan ɗakin idanuwansa suke a kan babyn tasa, ta tashi kansa over, sai ya ji ina, ai ba zai ma iya barinta ta tafi ba, wani irin zir zir ya ji a jikinsa, sabuwar tsumi ta tashi mashi. Ita ma a nata ɓangaren sai kallon shi take yi kamar nace zan kwace mata shi, ya yi matuƙar kyau cikin shigar three cuter fara kal mai bala'in kyau and shirt sky blue, ya ɗaure kyakkyawar dark black curly hairn nan nasa a baya, sai tashin fitinannen daddaɗar kamshin yake yi. "Good afternoon Momma". Ya faɗa har lokacin ya kasa kawar da idanunsa daga kanta. Fuska a ɗauke da fara'a gwaggon ta amsa mashi gaisuwar tare da tambayarsa ya ya tashi?. "Na tashi cikin farinciki da ban taɓa shiga irinsa ba my Momma". Ya bata amsa yana dawo da kallonsa a kanta. Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce Alhamdulillah ya Allah, sannan ta yi mashi sallama a kan kowa yana parlourn kasa yana jiranta, to sun wuce. Addu'ar Allah ya kiyaye hanya a dawo lafiya ya yi masu. Gaba gwaggon ta yi rike da hannun Jehan, ita ma Rimsha ta rufa masu baya. Cikin sauri ya riƙo kyawawan hannayenta tare da ɗan jawota jikinsa. Bai yi magana ba sai dai ya zubawa gwaggo da Jehan idanu har sai da suka fita, sannan ya dawo da kallonsa a kan matar tasa. Cak ya ɗauketa sai cikin bedroom nasu, ko uppan bai ce mata ba, ita ma bata ce mashi ko uppan ba, kawai ta bishi da kallo ne. Sai saman katafaren bed nasa ya direta. A kusa da ita ya haye ya zauna yana ta kallonta. Kwantowa ta yi a jikinsa, cikin shagwaɓa ta ce. "Noorish lafiya?". Hannunta ɗaya ya riƙo cikin nasa kafin ya fara magana. "Meesha anya zan iya bari ki je wajen walimar nan kuwa? Kin yi kyau over ne". Kyawawan fararen yatsunsa ta riƙo, a shagwaɓe ta ce. "To shikenan Noorish ai sai na fasa zuwa! Dama me zan je nayi a wajen da mijina aljannata baya nan? Me zan je nayi awajen da farincikina baya wajen, na san ma kona je wajen tunaninka kawai zan yi ta yi, dan haka gara mun kawai na zauna a tare da kai king of my heart". Tana magana tana murza mashi ƴan yatsunsa. "Meesha da gaske zaki fasa zuwa ki zauna da ni?". Da sauri ta gyaɗa mashi kai tana faɗin. "Mai zai hana my Noorish, ai bama zan fasa zuwa ba, na rigada na fasa zuwa, zan zauna da mijina". Dogon numfashi ya ja tare da saukewa a hankali. "Me kike so ni kuma na yi maki my wife?". Nisawa ta ɗan yi kafin ta kamo hannunsa ta ɗaura a saman shafaffen cikinta, cikin nutsuwa ta fara magana. "Abu biyu nake so, na farko in samu ciki nima in haifi baby's nawa masu kama da kai, abu na biyu kuma shi ne bakin ruwa, kullum da ina ƙarama idan zan yi mafarkinka ina yinsa ne muna a bakin ruwa muna zuba Love, to wajen nake son ka kai'ni Noorish na". "Iya su kawai?". Da sauri ta gyaɗa mashi kai. Ƙanƙameta ya yi a jikinsa sosai tare da gaya mata cewa tabbas zasu je bakin ruwan nan kamar yadda ta buƙata, maganar ciki kuma yana addu'ar Allah ya basu, Allah yasa wasan da zai buga a yanzu ya samu nasarar zura kwallo a raga. Da amin ta amsa mashi da shi kafin ta gyara kwanciyarta a jikinsa. Hannunsa ya zuro a ta cikin kayan nata ya fara shafa plat tummyn nata. Narke mashi ta fara yi tana kara shigewa jikinsa. Kan ka ce me ya birkice mata, tuni ya cire duk wannan uban kwalliya da Josephine ta zauna ta yi mata ɗin, duk ya rabata da komai kafin ya fara aikin juyata son ransa, tamkar ba ɗazun suka hau network suka sauƙa ba. Ita ma haka ta cigaba da biye mashi babu kama hannun yaro, lamarinsu sai dai mu ce azimun.......🥱 Su kuwa ƴan zuwa walima, sun jima a parlourn ƙasa suna jiran Rimshar ta fito, amma shiru bata fito ba. Da Areef ya ga haka sai ya ce da gwaggon wai ina Rimshar suka barota ne dama?. "Tana tare da Saif a part nawa". Gwaggo ta bashi amsa. Guntun murmushi Areef ɗin ya saki kafin ya ce. "Ku mu tafi abinmu, dan in zaku kwana a nan Rimsha ba zata zo ba, tab Lion fa, ai tun da suka yi wannan kwalliyar suka yi kyau to ita Rimsha sai dai hakuri, kishi ba zai kyale shi ya iya barinta ta fito ba, ai muje kawai". Da farko Gwaggo ta so ta ce su ɗan kara jira ko kuma Aseef ya je ya dubota, daga baya kuma sai ta ce to su tafi ɗin kawai, idan ma zata je shi Lion ɗin ya kawota da kansa. Haka suka tafi abinsu, ita kuma Rimsha tana cikin bedroom tana manne da babynta suna aikin da suka saba. Walima ya yi walima, waje ya yi waje, sun yi rabon kuɗi ba karya, sai dai fa kowa kallon Lion yake yi wa Sir Safwan, saboda ba mai iya banbantasu idan ba Rimsha da kuma su gwaggo ba, su gwaggon ma ba su jima da fara iya banbantasu ba, kunsan idan kana zaune da mutane waje guda, to dole dole a kwana a tashi watarana zaku iya rabesu komai kamanninsu kuwa, to hakan ce tasa su gwaggon ma suke iya rabesu, dan sun zauna da su, shi Areef ma dama already yana iya rabesu, ga kuma Aseef da Mahhir wato Alex, suma kada ku manta kamanninsu ɗaya, banbancin kwayar idanu ne kawai. Kowa idan yazo kallon Sir Safwan a matsayin Lion suke yi, babu wani bare daga waje da ya iya banbanta su ko ya iya gane cewa ba Lion bane a wajen. Anyi bidiri ba karya, gwaggo ita ce ta rinƙa rabon abubuwa, sai hotuna ƴan jaridu suke yi mata, ga shi ta sha kyau sosai da sosai, shi kam Dr William bawan Allah ɗan baruwana, duk abin da gwaggo ta faɗa hakan za'a yi, baya ja da maganarta, kamar wani mijin Hajiya, kuma ba haka bane, kawai tsananin sonta da yake yi ne, da kuma yasan halin kayarsa, tun tana ƴanmata har izuwa yanzu bata canza hali ba, ya santa da shegen son girma ga nuna izza, isa da taƙama, ai ba'a ƙasa su Lion suka ɗauko wannan dabi'u ba, a jiki yake. Hakan yasa Dr William kam yake biye mata, komai ta ce sai ya ce Okey baby. Taro ya yi taro, dan tsayawa zayyana maku irin taron da aka yi sai ya cike mun ɗan filin da ya rage mun dan na kammala book nan, dan haka ku kawata wannan taro a ranku ya zai kasance? Haɗuwa iya haɗuwa ne, iyalan His Excellence Saif da kansa ne a wajen, kunga kuwa ai abin ba'a magana. Suna dawowa daga wajen walimar nan naƙuda ya kama Aylar daddyn Jelly, zata haifo masu ɗan U.s kenan, kamar dai yadda aka saba gwaggo ce ta karɓi haihuwar, yaro namiji kyakkyawar gaske fari tas da shi suka samu. Family sun yi murna, sai samun karuwa suke ta yi, amma kuma kowa so yake yi ya kalli yaron Lion and sir Safwan, kowa a ƙage yake da ya kalli nasu. Abin har ya fara yi wa gwaggo daɗi, yadda taga in dai za'ayi maganar yara to fa yaran Lion da babu su babu alamarsu su ne a farkon magana, sai jinkirin haihuwar na Lion ɗin ya yi mata daɗi, dan ga shi gabaɗaya family har kasa bakiɗaya jiran ƴanƴan nasa suke yi, yaran Lion masu tsada da kuma wuyar gani, su Imran duk zancensu kenan, kowa ƴaƴan Lion, kowa Rimsha shiru har yanzu, gara Sir Safwan basu cika maganar nasa sosai ba, saboda Maryam tana da ciki, ita kuma Rimsha jiya eyau, babu wani canji sai shegen kyau da take karawa tana kara rikita mana Lion ɗin mu........😌 Mummynta da daddynta ma dukka yanzu ƴaƴan nata kawai suke da muradin gani, sun ga na Jehan kam, bare ma mummy da kunsan tafi son Rimshar, sun fi shakuwa, dan haka sai ta fi jin ƙaguwar ganin ƴaƴan Rimshar, shi kansa Dr William ƴaƴan Lion kawai yake jiran ya gani. (Yaran Lion namu masu tsada ne fa, kowa jira yake yi ya gansu?🤔 Sun saka mana ido fa😒😌) Wannan family guda biyu, wato familyn Dr Salman and Dr William za'a ce ne ko kuma Jacob Roshan, to dai waɗan nan two families da suka cure waje gudan ba ƙaramin farinciki suke yi ba, Adiva taga daddynta, ta makale mashi da wani cikinta a gaba. Baki ya yi kaɗan ya iya zayyano maku irin tsantsar farincikin da waɗan nan family suke a ciki. Satinsu Abba biyu suka koma Nigeria abinsu. Ranar da suka koma tamkar sun koma ne da lafiyar Rimsha, tun daga ranar ta fara ciwo, ciwo, zazzaɓi bini bini, shi Lion ya san matsalar kayarsa, domin kuwa ko ciwon kai Rimsha ta yi baya iya barci sai ya binciko dalili ya kuma nema mata lafiya, so a yanzu ma hakance, sarai yasan dalilin rashin lafiyar tata, sai dai yaki sanar da kowa, idan su sir Safwan sun tambaye shi, sai ya ce babu ruwansu. Gwaggo ma ta yi tambayar duniyar nan amma yaki gaya mata menene yake damun matar tasa, ta ce zata duba lafiyarta, nan ma ya ce a'a ta bar mashi matarsa, ai shima Dr ne, dan haka su barsu kawai. Haka gabaɗaya family suka zuba masu idanu suna kallonsu, sai fama da ciwo Rimsha take yi kamar zata mutu, su Areef sun kasa jurewa, hakan yasa suke takura mashi a kan dole su kaita hospital, saboda su ciwon nata yana damunsu. Da dai yaga sun takura masu a gidan, sai ya shirya tsab tare da sanar da tsofaffin sojojinsa wato su Donal kenan, ya ɗauki Mark, Donal, Tyrone da kuma wasu sojoji guda biyu, ya ce su shirya su kaɗai yake da buƙata zasu raka shi wani waje. Bayan ya sanar da su ne ya dawo cikin bedroom nasa, Rimshar tana kwance a saman bed ta yi shiru kamar mai tunanin wani abin, duk ta rame baiwar Allah, kamar ba ita ba, sai gulu gulun idanuwa zaka gani. A kusa da ita ya zo ya zauna bayan ya ɗauko A box, cikin dabara ya lallaɓata ya yi mata alluran barci, sannan ya kira Sir Safwan a waya a kan ya zo bedroom nasa ya same sa. Ba tare da ɓata lokaci ba Sir Safwan ya zo. Cike da so da kauna ya ce mashi. "Zan yi tafiya na ɗan lokaci, dan haka ka shiga office nawa a matsayin kai ne ni, dama babu mai iya banbanta mu, so ka rike mun aikina sai na dawo, tafiyar sirri zan yi shiyasa na yi wa Meesha alluran barci, so ka kula da komai, and lastly jibi zaku koma white house da zama, tun da komai ya dai'dai a yanzu". Ya kai karshen maganar tare da miƙe ya hau shirya duk wani abin da zai buƙata. "Amma ina zaka je haka?". Cewar sir Safwan ɗin. Da mamaki ɗauke a saman face nasa ya jefa mashi wannan tambayar. "In da Meesha ta fi so a rayuwarta, wajen mafarkinta zamu je mu huta, dan kun saka mata idanu sosai a gidan nan, gara na ɗauketa muje ta huta a wani wajen ko ta huta da jin muryoyinku na tambayarta ya jiki, musamman ma kai ɗin nan, kafi kowa takura mata da ya jiki". "Amma akwai waya a wajen ai? What I mean here is zamu iya samunku a waya ko?". FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA CE.....✍️🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E54 "Amma akwai waya a wajen ai? What I mean here is zamu iya samunku a waya ko?". Jinjina mashi kai ya yi alamar e ba tare da ya yi magana ba. "Okey tom Allah ya tsare hanya, ka dai kula mana da our Meeshar mu, dan naga kamar ba ita kaɗai ba ce". Nan ma jinjina mashi kai ya yi ba tare da ya ce komai ba. Juyawa Sir Safwan ɗin ya yi ya fice daga cikin ɗakin, shi kuma Lion ya hau shiri na duk abin da zasu buƙata. Ta kofar sirri wanda yake ta bayan ya fice, gwaggo and Dr William kawai ya sanarwa da ga in da za su je sai sir Safwan ɗin. Addu'a sosai iyayen nasa suka yi mashi tare da sanya mashi albarka, sannan suka ce ya kuka masu da Rimsha sosai. Amin ya rinƙa amsawa da shi kafin ya sa kai ya wuce abinsa. Iya waɗan nan sojoji daya ware ne kawai suka bisa, bayan ya fita ta baya ɗauke da Rimshar tasa dake barci, sai sojojin suka zago suka same shi, da motoci biyu suka tafi. Sun yi tafiya mai ɗan nisa kafin su isa baƙin wata dam, already an shirya masu jirgin ruwa ɗan ma dai'daici, yana zuwa kawai suka kama hanyar tafiya. Gabaɗaya tsallake arear su suka yi, suka nufi ɗayar tsagin, tamkar yadda Rimshar take damunsa tana son rayuwa a irin wannan waje, haka ya kaita yau, a bakin ruwan su Mark suka yi aikin haɗa masu irin wannan ɗakin da take magana a kai ɗin. Da yake ya san in zasu je, sai ya tanaji komai, harta electric katifa dake aiki da wuta, kuma yana aiki da Power bank, to haka su Mark suka sha aikin shirya waɗan nan abubuwa, jirgin ruwansu kuma suka baro shi a can jefe. Sai zuba barci Rimshar take yi, bata san me yake faruwa ba, sai dai ta farka taga surprise. Baya su Mark sun kammala aikin haɗa masu komai, ɗauko Rimshar ya yi daga cikin jirgin ruwan ya kawota cikin ɗakin, suna da komai a cikin jirgin ruwan, har da katafaren bed, amma dan ya cikawa Rimshar mafarkinta, sai yasa aka yi mata irin wannan ɗakin da take so a rayuwarta, suka rufo jirgin ruwan nasu kuma. Kwantar da ita ya yi a saman electric bed ɗin nasu, sannan yasa su Mark su kawo masu trolleynsu. Mark kam mamaki ne kamar zai kashe shi, yarasa dalilin da yasa Lion ya zo nan wajen, me ya kawo shi? Ga shi ba halin tambaya. Bayan sun kawo mashi trolleyn ya karɓa ya koma cikin ɗakin, su kuma suka tsaitsaya a gaba da bayan ɗakin dan bashi tsaro. Kayan jikinta ya cire mata ya sanya mata pajama mara nauyi, dan ya ga duk da sanyin da yake a ƙasar tasu ita zufa take haɗawa, hakan yasa ya canza mata kaya izuwa shara shara mara nauyi. Daya kammala sai ya ɗauki kayan da zai buƙata ya koma cikin jirgin ruwansu dan ya yi wanka ya shirya, ya rufota a cikin ɗakin. Tyrone ne ya bi bayansa dan ya bashi tsaro a wajen jirgin ruwan, ita kuma Rimsha su Mark suka cigaba da tsaron ɗakin da take. Bayan ya yi wanka ya shirya a cikin three cuter, bai sanya riga a jikinsa ba, saboda yanayin weather wajen da akwai ɗan zafi zafi, kasar tasu akwai sanyi sosai, ga shi nan bakin ruwa suke, sai dai kuma wani ikon Allah wajen da ɗumi sosai kamar ba bakin ruwa ba. A dai'dai bakin ruwan ya zo ya zauna bayan su Mark sun kawo mashi wata tsadaddiyar kujera daga cikin jirgin, Mark dai har yanzu mamakin zuwansu wannan waje yake yi, ya baro Anayarsa da baby's nasa, sai kewarsu yake yi Lion ya wani kawosu bakin ruwa ya ajiye, kamar ya yi kuka haka yake ji, to amma ya zasu yi? Dole ne su bi umarni. Aikin latsa wayarsa ya fara yi yana tunanin yakamata ace Rimsha ta farka izuwa yanzu. Bai kammala dawowa daga cikin duniyar tunanin da ya afka ba kamar daga sama ya ji ihunta. A dubu ɗari su Mark ɗin suka juyar da kallonsu izuwa wajen ɗakin da take a ciki ɗin, shi ma Lion ɗin miƙewa ya yi tsaye cikin nutsuwa, dan yasan ba komai yasa ta yi ihu ba face farkawa da ta yi ta ganta a bakon wajen da bata taɓa tunanin zata ziyarci wannan waje ba, hakan yasa ta kurma wannan ihu. Yana ƙoƙarin nufar ɗakin sai gata ta fito da gudu. Dakatawa ya yi daga tafiyar da yake yi, zuba mata waɗan nan dara daran idanuwan nasa ya yi. Ita ma dakatawa ta yi daga tunkarosa da gudun da take yi, ta tsaya cak tare da tsare shi da idanu babu ko kyaftawa. Su kuwa su Mark, ai a dubu suka juya, dan kada su ganta, sai suka juya suka ba su baya tare da sunkuyar da kansu kasa. Kasa karisowa in da yake ta yi, ta yi mutuwar tsaye ne a wajen. Ganin bata da niyar karisowa gare shi ne yasa shi ya tako cikin nutsuwa, kafafunsa suna sanye cikin wasu shegun tsadaddun bedroom slippers, ga su farare tas masu kyan gaske. Yana isa gabanta ya kai hannu ya kyafta mata yatsunsa a dai'dai wajen idanuwanta. Ina ko kyaftawa bata iya yi ba, tamkar wadda ta yi samar tsaye. "Meesha are you okey?". Ya faɗa in a low voice sosai. Kasa amsa mashi maganar ta yi, ta kafe idanuwanta a kansa kawai tana kallonsa. Ba komai yasa ta yi wannan sumar tsaye ba face surar jikinsa, tun da suke bata taɓa ganinsa babu riga ba sai yau, bata taɓa kallon waɗan nan ɓul ɓul ɗin kyawawan breast ɗin nasa ba sai yau, hakan yasa ta yi sumar tsaye, taga abin da ya haura sheƙarunta. Shi kuma bawan Allah sam bai ma san dalilin da yasa ta yi mashi sumar tsaye ba, yaga dai sai kallonshi take yi babu ko kyaftawa. Hakan yasa ya kai hannu ya ɗauketa cancak suka koma saman kujerar da yake zaune ɗin. Ya zauna da ita a manne ajikinsa, sannan ya kai hannu ya ɗebo ruwa daga cikin tekun ya ɗan yarfa mata a fuska. Dogon numfashi ta ja tare da sauke a hankali, sannan ta fara aikin kyafta idanuwanta domin ta tabbatarwa da kanta ba mafarki take yi bada. Kyakkyawar dogon hancinta ya ja kafin ya ce. "Lafiyarki kuwa my Meesha?". Da sauri ta dawo da kallonta a saman face nasa, sai kuma ta fara sauko da idanuwanta izuwa saman Lion chest ɗin nasa domin ta tabbatar da abin da ta gani ɗazun gaskiya ce ko mafarki ne. Ganin gaskiya ce yasa ta fara bin damatsan hannunsa da kallo, duk mamaki ya cika mata rai, anya yah Saif ɗinta ne kuwa? Ta tambayi kanta, dan taga kyakkyawar kakkarfar surar jikin nan nasa ya gigitata. Shi kuwa mamaki ta bashi, ya rasa ma me zai ce mata, ga su Mark kuma can a kame sun juya masu baya, ba halin su juyo bayin Allah. Ta ɗan ɗauki lokaci kafin ta warware ta dawo dai'dai, sai kuma me? Ai sai ta hau yin murna na wuce misali, yau gata a wajen mafarkinta, bakin ruwa tare da mutumin da take mafarkinsa tun tana karama, mutumin da ta fi so sama da komai nata, kuma ya zo mata a sak irin mafarkin nata, ga shi babu riga, ita kuma da ƙananan kaya, abin ya yi mata daɗin da ba zai taɓa yiwuwa ta manta da shi ba. Rungumarsa ta yi cikin tsananin farinciki tana mai manna mashi sumbata ta ko'ina a face nasa saboda jin daɗi da murna. Shi kuwa ya yi shiru ya tsareta da idanun yana ta kallon kyakkyawar fuskar nan tata mai ɗauke da kayatatcen murmushi. Sun ɗauki ɗan lokaci a wajen da a kallah ya kai awa biyu suna zuba love nasu, kafin ta ce "Noorish ka kamo mun kifi, ina son in ci gasasshen kifi". Ɗan zaro mata idanun ya yi. "Meesha me zaki yi da kifin cikin tekun nan? Idan kifi kike so ai sai Mark ya je ya kawo maki fresh ko?". Kukan shagwaɓa ta saka mashi tana faɗin. "Ni bana son wani fresh, na cikin tekun nan nake so". Shafa lallausan kumatunta ya yi kafin ya ce. "To ya isa haka rigimammiyata, yadda kikeso haka za'ayi, bari su Mark su kama maki". Wani sabon kukan ta saka mashi tana faɗin. "Wai Noorish cikin Mark ne a jikina ko naka? Babyna ya ce shi wanda daddynsa ya kamo yake son ci, dan haka kai zaka kamo mun nikam, idan ba haka ba sai dai babynka ya hakura da ci, bana son nasu Mark". Tana magana tana kuka, har da wani ɗan guntun hawaye na iyashege. Ɗan dafe kansa ya yi yana faɗin. "Wannan baby da alama ya fi uwarsa rigima, to tashi mun a jikina bari na je na kamo maki". Make mashi kafaɗa ta yi tana faɗin. "A'a ni dai sai dai ka goyani mu kama a tare". "To tashi bari na miƙe sai ki hau bayan nawa ko?" Ya bata amsa a takaice. Da sauri ta miƙe daga jikin nasa, miƙewa tsaye ya yi tare da ɗan duƙa mata kaɗan ta yi tsalle ta haye bayansa tana dariya. Cikin jirgin ruwansu ya koma da ita, dama kunsan a cikin jirgin ruwa da akwai abubuwan kama kifi, rigar ruwa, da dai sauran abubuwa, so shi abubuwan kamun kifi ya je ya ɗauko, sannan suka fito. Ganin shi da abin kamun kifi a hannu yasa Mark ya ce. "Sir bari na kama maka". Da yake ta gabansu Mark ɗin suka bi, shi ne yasa Mark ɗin ya gani. Ba tare da ya tsaya daga tafiyar da yake yi ba ya ce. "No ka barshi kawai, baby ya ce kifin da daddynsa ya kama zai ci, so bari". Yana magana yana tafiya, ita kuma ta wani kwanta mashi a saman bayansa tana aikin murɗa mashi dark black curly hairnsa ta bayan wuya. Bakin ruwan ya koma ya fara aikin kamun kifi dan dole, idan ba haka ba babynsa dai ba zai ci komai ba. (Wlh Rimsha ta san ta kan tsiya😂 yanzu His Excellence da kansa ta saka kamun kifi🤔 kai wannan yarinya tana yin son ranta, dole na zuga Lion ya kara aure, ya auro baturiya😒🥱) Da kyar ya iya kama mata manya manyan kifi guda biyu, sannan ya ce ta sauka mashi a jiki ga shi ya kama mata bari ya kaiwa Mark ya je cikin jirgi ya gyara ya gasa mata. Nan fa ta saka mashi kuka tana faɗin ita fa ba gashin su gas take so ba, da itace za'a hura wuta a gasa mata, haka babynta yake son ci. "Meesha meyasa kike son saka mun ciwon kai ne? Itace kuma?". Kuka ta sake saka mashi tana faɗin. "To ni Noorish laifi nane? Ba babynka bane yake son ci? Ni fa bana cin kifi, babynka ne nan yake son ci". "To sauka bari su Mark su gasa maki da itacen". Sake make mashi kafaɗa ta yi tana faɗin. "Baby gashin daddynsa yake son ci, ni dai kai nake so ka gasa mun, Allah idan ba kai ba na ƙoshi". Tana magana tana kuka, har da hawayenta bibbiyu dan rigima. Bashi da zaɓin da ya wuce ya gasa mata ɗin, domin kuwa yana tsananin son cikin nan nata, ga cikin watansa ɗaya kenan a duniya, amma sai rigima kala kala ta iya, kuma cikin yazo mata da laulayi tare da zaɓar abinci ne, yasan idan bai gasa mata ba to ba lallai ta ci abinci ba, abin da cikin yake so shi kawai take ci. Babbar magana. Lion akwai shi da wani ra'ayi fa shi ma, ganin cewa dukka family suna ta burin Rimsha ta samu ciki, kowa so yake yaga ɗansa, shi ne fa sai ya ɓoye zancen ciki, yaki bari kowa ya sani, daga ita sai shi, ko gwaggo bai sanarwa ba, wai kada su sakawa matarsa ido, kada su damesu ita da babynsa, shi ne nan ya ɓoye menene yake damunta, ya ki bari gwaggon ta gwadata, ya ki bari kowa ya sani, kunga daga karshe ma ya ɗaukota sun bar gidan abinsa. Ni kam PRINCESS FATEEMA TEEMA ina ganin ra'ayi kala kala a wajen Lion. Sanya su Mark ya yi suka kawo mashi itacuwa busassu, sannan suka hura mashi wuta ta bakin ruwan, dan dole yau ya koyi gasa kifi, amma sai da Mark ya nuna mashi yadda zai haɗa kifin da kayan miya, da yake suna da komai a cikin jirgin Kujera Mark ya kawo mashi ya zauna kusa da wutar yana gasawa. Ba dan tsananin tsoronsa da su Mark ɗin suke yi ba, da yau babu abin da zai hana basu yi mashi video ba, dan ko a mafarki basu taɓa tunanin zasu gansa a kusa da gas na girki bama bare kuma itace, sam basu taɓa yin gigin irin wannan tunani ba, sai ga shi yau saboda babynsa ya zauna a gaban itace mai ci da wuta yana gasa kifi, gaskiya mace duniya ce, duk wanda ya ce maka mace bata isa ba, to wlh bai shiga hannun macen da ta kai mace wadda ake cewa mace ba mun rako mata ba, kun san akwai mace wadda ta amsa sunan mace, sannan kuma akwai mun rako mata, sune zaku gansu sai a hankali, amma cikakkiyar hamshakiyar mace, ai ko namiji baya so sai ta juya shi son ranta. A takaice dai yau ga His Excellence of United States yana aikin gasa kifi a bakin ruwa........😂 Kai mata duniya ne, dole haka ya yi wannan aiki ba dan ya so ba, sai dan yana son farincikin matar tasa da kuma abin da yake cikinta, a can gefe guda kuma Sir Safwan ya ɗake a saman kujerarsa cikin office nasa dake white house, ya haye kujera yana ta aiki tamkar Lion ɗin ne, babu wanda ya iya gane cewa ba Lion ɗin bane, kowa a matsayin Lion yake ɗaukarsa, ba su san ga shugaban kasarsu mai mulkarsu a nan bakin ruwa shi ma ana mulkarsa ba, ya mulki al'umma, ya juya su son ransa, shi ma kuma under 15 years girl ta mulkesa ta juyasa son ranta, wannan abin ni PRINCESS FATEEMA ZAHRA yana mugun yi mun daɗi..................😂(Team Lion kada wanda ta ji haushina kun ji na gaya maku😂 ato daɗi nake ji yadda Rimsha take murza kanbun mulkinta😂 ya gasa mana kifi muci😂 dama ni ina da Maltina mai sanyi 🥱) Haka ya gasa wannan kifi tsab, sannan ya bar wajen tare da komawa ta gefe guda yana turɓune fuska. A saman laps nasa Rimshar ta zo ta zauna tana faɗin ya bata kifin a baki to. Idan baku manta ba tun a book 1 Aseef baya cin namar kifi, hakan yasa dukka TRIPLETS basu damu da shi ba, ya zamana suma basu so, so har yanzu Lion wari kifi take yi mashi, bai iya ci ba, baya son karninta kuma. Amma a haka ya daure ya rinƙa bawa Rimshar a baki, dan ya samu ta ci abinci, yasan ba komai take ci ba sai abin da ta zaɓa. Shi dai Mark izuwa yanzu ya gama sadaukarwa da cewa babu abin da mace ba zata sanya namiji ba, mace zata iya juya namiji son ranta idan ta san menene ciwon kanta. A takaice sun ɗauki tsawon lokaci a wajen wannan bakin ruwan, sun sha soyayya ba karya, Rimsha ta zuba sarautarta son ranta, abin gwanin birgewa, sai da lokacin da zasu tafi Nigeria ya yi ne gwaggo ta kira shi a waya a kan ya dawo zasu je Nigeria. Okey ya amsa mata da shi, amma sai ana gobe zasu tafi sannan ya dawo gidan. Wani irin kyau Rimshar ta kara, jikinta ya samu sauki sosai, dan ta samu hutu, ga kayan marmari da take ci sosai, sai ta kara fresh over. Sai dai kuma har yanzu babu wanda ya iya gane cewa tana da ciki, sam basu gane ba, dan cikin bai fito ba, kwata kwata 3 months ne cikin, domin two months suka yi a bakin ruwan kafin su dawo. Sun shirya zuwa Nigeria gagarumin shiri, dan sun tsara idan suka je zasu yi ziyara sosai. Sai dai fa ko da suka je Nigeriar basu sauka a gidan Lion na Kaduna ba, a villa suka sauka, a fadar shugaban kasa, saboda yanzu in dai ba tafiyar sirri zasu yi ba, to babu in da zasu je su zauna a karamin waje, sun wuce wannan level ɗin, ku kanku kunsan matsayi ta ci uban na da. Daddyn Rimsha bai zo Nigeria ba shi, shi suka tarawa aikin a matsayinsa na vice president, suka tara mashi aiki suka tafi suka bar bawan Allah, mummy ta so zuwa, amma ina ba hali, haka ta hakura ya zauna tare da mijinta. Sun sha yawo a Nigeria sosai da sosai, sun yi ziyara wajen ƴan uwa da abokan arziki, har Bauchi sai da suka je wajen ƴan uwan Dr Salman, sannan suka je Katsina wajen su Maman Sadiq. Jehan ce ta sanya Areef ya yi wa Maman Sadiq da Sadiq ɗin gagarumin kyauta, katafaren dankareriyar gida na alfarma ya saya masu a cikin gari, ya ce su bar kauyen nan, sannan ya biyawa Sadiq da Yusuf school fees na tsawon su kammala karatun a wani katafaren school na ƴaƴan manya, ya bawa Sadiq jari mai tsoka da zai iya isar sa ya rike ahali guda, shi ma baban Sadiq ɗin ya bashi jarin sosai, da farko Jehan ta so hana shi ya bawa baban Sadiq ɗin, ta ce ai munafikin uba ne mugu, sai da Rimsha ta roketa, sannan ne ta yi shiru ta hakura Areef ɗin ya bashi 5m. Daɗi kamar baban Sadiq ba zai mutu ba, nan take ya hau zuba masu godiya tare da godewa Maman Sadiq da ta rike su Jehan mutanen kirki. Ni kuwa nace ɗan banza, sai yanzu kasan da cewa su mutanen kirki ne ba, da yake anji maiko, kai amma wannan hali naka dai tirr da shi. Lion kuma Rimsha ta ce to ya biya masu kuɗi su je Makka su yi ibada, Okey ya amsa mata tare da cika mata abin da take so, su maman Sadiq za'a keta hazo zuwa ƙasa mai tsarki. Bayan sun kammala zasu bar garin Katsina su koma Abuja ne Aafia ta ce da Uncle T zata je wajen Ummin Dr Nawid a gidan sarki kenan. Ba musu suka ɗunguma zuwa can, dan ziyara suka zo, sai dai fa Lion da Rimsha basu bisu ba, sun kama hanyarsu sun bar garin, Rimsha ta tsayar mashi da rigimar sai dai ya kaita garin Ilorin, dan tana son ta je taga Kausar, dama kuma idan baku manta ba ya taɓa yi mata alkawarin zai kaita can, dan haka sai ya ɗauketa suka nufi can. Su Aafia kuma sun je su duba Ummin Dr Nawid tana nan lafiya, a nan ne suka sami labarin Abbo ya dawo bai mutu ba, sai dai ya haukace yana yawo bola bola, ga ciwon kafa da yake fama da shi, kafar ta ruɓe har tana tsutsa, an nemi magani har an gaji babu sauƙi, hakan tasa aka raba auren Ummi da Abbon, da da farko ma an ɗaure shi ne, daga baya da aka ga wannan fa ba samun lafiya zai yi ba, sai aka sake shi ya shiga duniya ɗan banza. Nasan zaku yi mamakin jin cewa Abbo yana raye, to dama bai mutu ba, da ginin tazo ruguzowa a kansa sai ya ɓace, hakan tasa yake raye, sai dai kuma aljanun tsafin nasa sun ce ba zasu yafe mashi ba, dan sun bashi arziki mai tarin yawa, da alkawarin zai basu mata, sau uku kenan yana yi masu alkawarin basu ƴan mata amma yana karyawa, ya yi alkawarin basu Jelly, Allah ya kuɓutar da ita, sanan ya yi alkawarin basu Aafia, nan ma Allah ya kuɓutar da ita, sai Adiva kuma, ita ma Allah ya kuɓutar da ita, hakan ne ya arzuƙa dodannin tsafin nasa suka haukatashi, sannan suka sanya mashi ciwon kafa mai azaban zafi har tana tsutsa. Sosai Aafia ta ji daɗin hakan, amma bata nuna hakan a fili ba, sai ta ɓoye murnarta ta taya Ummin Alhini kawai. Sun samu tarba ta karamci da girmamawa a wajen ƴan uwan Ummi, hakan ya yi masu daɗi sosai. Cikin dabara Aafiar ta tambayi Ummin ina Oummunsu wato hjy Hadiza, nan Ummin take sanar da ita ai ita ma Oummu ƙwaƙwalwarta ya taɓu an kaita gidan mahaukata an ɗaureta. Cikin ruɗu Aafiar ta tambayi me ya sameta, nan fa Ummi ta bata labarin cewa Hjy Hadizar ta yi aure a kan aure ne da wani Balarabe har sun haifi yara biyu, to ashe balaraben kam mugu ne, duk ya lalata mata yara, ba wanda yasan me yake aikatawa har sai da ciwo ya kama yaran suka mutu, to Hjy Hadizar ta zo ta gane gaskiya shi ne kwakwalwa ya taɓu saboda son da take yi wa yaran. Sosai Aafia ta yi kukan jin abin da oummunsu ta yi, abin ya yi mata ciwo sosai, amma ya zata yi? Haka Allah ya ƙaddaro masu nasu kaddarar, dole kuma su rungumeta. Sosai Ummi ta rinƙa rarrashinta tana bata baki tare da nasiha a kan yarda da ƙaddara. Jiki a mace ta rinƙa zubawa Ummin godiya. Haka suka cigaba da yin hira har zuwa karfi 2 na rana, bayan sun yi sallar azahar sai suka ɗauki hanyar komawa Abuja. Amma fa kafin su koma sai da aka ɗaura auren Uncle Herry da Ummin Dr Nawid ɗin, dan ta gama idda, kuma dama tun da ta je Washington time ɗin haihuwar su Jehan ya kamu da sonta da ya ji cewa mamar su John ta mutu, sai ya ji yana sha'awar ya auri ƴar Nigeria kamar yayansa Dr William kenan, duk da cewa shi Dr William kusan za'a ce ba ƴar Nigeria ya aura ba, dan gwaggo dai ƴar Russia ce, bata wani zauna a Nigeria ba koda suka dawo ɗin ma, kada ku manta da ta koma wajen daddyn Rimsha ma a Dubai suka zauna kafin daga baya su dawo gida Nigeria. So a takaice dai sai da aka ɗaura auren Uncle Herry da Ummi kafin so dawo Abuja, kuma ya taho tare da matarsa, Ummi ta baro Katsina kenan, Allah mai kyauta mai kari, mai yin yadda yaso, tana son Aafia sosai, ga shi Allah ya sake haɗasu waje guda da Aafiar, sun sake curewa a family guda abin ya burge matuƙa. A ɓangaren su Lion kuwa, kasancewar da jirgi suka tafi Ilorin ɗin, sai suka isa da wuri, kai tsaye gidan gwamna suka sauka, sai da suka ɗan huta kafin su bada sanarwar zasu je in da suka zo domin shi. Dankara dankaran motoci goma sha biyar gwamna ya fitar dan a kai'su in da za su je ɗin. Har kofar gidansu Kaunar aka kai'su, dan Rimsha bata mance da sunan unguwar ba, suna zuwa unguwar kuma ta gane gidan. Tun da suka dimfaro unguwar jama'a suke ta kallon motocin, domin tsadaddun motoci a jere irin haka basu saba zuwa su wuce ba, ga kuma uban jiniya da motocin sojoji biyun da suka rakosu suka saki, jiniya ta karaɗe ko'ina tamkar filin yaki zasu tafi. Ganin motocin sun yi parking a kofar gidansu Kausar ne yasa jama'a suka fara cincirindo suna fitowa daga gidajensu ne shagunansu ne, dan su kalli me yake faruwa. Rimsha sarkin kauɗi, har ta kai hannu zata buɗe kofar motar ta fita Lion ya riƙota. Da mamaki take binsa da kallo, ɗaure fuska sosai ya yi yana faɗin ina zata je?. Ganin babu alama sauki a tattare da shi ne yasa ta nutsu, cikin sanyin murya ta bashi amsa da cikin gidansu Kausar. Kallon driver da yake tuƙasu ya yi, cikin bada umarni ya ce. "Go and call Kausar for her". A hanzarce bodyguard ɗin ya amsa da okey sir, sannan ya fito da sauri ya nufi cikin gidan. Sojojin da suka rakosu kuwa, suna yin parking na motocinsu suka diro kasa daga saman bayan motocin, cikin ƙanƙanin lokaci suka kewaye arear wajen da bindigunsu dan tabbatar da tsaro, da gwamna ya so a tashi helicopters ne ma dan bawa Lion ɗin tsaro mai inganci, amma sai Lion ɗin ya ce mashi a'a baya bukatar hakan, iya motoci biyu na sojoji sun wadacesa, dan shi ba rago bane ba........😌 FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA CE.....✍️🔥 ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥 *KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*. *KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*. ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S ❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥 TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️ ❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋) *Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581* E55 "Noorish a kirata kuma? Tom ai ba ita kaɗai bane, ina son in ga Iya ma". Jawota jikinsa ya yi yana faɗin. "Koma waye kike son gani za'a kirasa ya zo nan, ba zaki shiga wannan local wajen ba, da na san a irin wannan kazamin wajen suke ma ai da ba zan kawo ki ba, sai dai nasa a ɗauko maki su ki gansu, amma saboda rigima irin taki sai da kika wahalar da ni kika kawoni dirty place ɗin nan". Wai shi Lion bai san cewa ita Kausar ji da kanta take yi a matsayin big girl bane da zai zage masu unguwa?😂 Shiru ta kwanta a jikin nasa har bodyguard ɗin ya fito daga cikin gidan a tare da Kausar da kuma Iya, Kausar ɗin tana rike da wani baby boy mai kama da boda Jami'u, bakin kirin da shi. Ganinsu yasa Lion ɗin yasa aka sauke mata glass ɗin motar ta side ɗinta, sannan ya ce ta tashi su gaisa dan shi ya gaji da kallon wannan kazamin unguwar, yana son su tafi. Cikin zumuɗi ta tashi daga jikin nasa tana ambatar sunan Kausar ɗin. Sam Kausar ɗin bata iya gane ta ba, saboda ba karya Rimsha fa ta canza gabaɗaya, ba zata taɓa cewa ita ɗin bace. Sai da ta yi wa Kausar ɗin bayani, sannan ne ta iya gane ta, abinku da yarabawa, ihu Kausar ɗin ta fara zundumawa tana ambatar Rimsha! Rimsha!. Sai murmushi Rimshar take yi, taso ta fita su gaisa da kyau, amma Lion ya hanata, wai ba zata sauka a cikin dattin nan ba, dole ta hakura suka gaisa tana daga cikin motar. Kausar ɗin taso bata labarin bayan rabuwarsu da komawarta Daular Mutuwa da ruguje Daular Mutuwa da wasu bayin Allah suka yi suka sa ta fito, da cikin shegen da boda Jami'u ya yi mata ya gudu Lagos ya barta da yaro wai ya tafi neman kuɗin da zasu yi aure, da dai sauransu. Amma ina Lion ya ce su wuce, dan shi bashi da lokacin tsayawa shirmen matan nan, Rimsha ta so jin labari, amma ina ba dama, haka dai ta ji labarin sama sama. Ta taya Kausar ɗin alhinin abin da suka faru, sannan ta ce Lion ya basu kuɗi mana, yana ta aikin latsa wayarsa tun lokacin da su Kausar ɗin suka zo, ba tare da ya ɗago kai ba ya ce ta ɗeba ta basu mana. Sai ɗaga mashi gaisuwa Kausar da Iya suke yi, amma ina ko kallo basu isheshi ba, tamkar bai san da sun zo wajen ba, sai ya kama aikin latsa wayarsa kawai, sai kallonsa Kausar take yi, tana son ta yi wa Rimsha gulma ta tambayeta waye shi, amma tana tsoron shi, saboda bata ga fuska ba, kun san yadda face nasa take ai? Babu alamar wasa, ga kwarjini mai rikitar da mutane, hakan yasa Kausar ɗin ta sha jinin jikinta ta haɗa malaman jikinta ta nutsu. Cikin zumuɗi Rimshar ta ɗebo maƙudan dollars daga aljihun Lion ɗin ta miƙawa Iya, sannan ta sake ɗebowa ta miƙawa Kausar ɗin. Abin ku da yarabawa, har kasa iya ta zube gwiwowinta tana zuba uban godiya. Umarnin Lion ya yi wa drivers ɗin a kan su tafi. Ba ɓata lokaci suka tashi motocin a dubu suka bar unguwar. Har suka ɓacewa ganinsu Iya da Kausar suna zube a saman gwiwowinsu suna aikin zuba godiya, iya har da kukanta da hawaye, dan ba kuɗin wasa Rimsha ta basu ba, idan zasu canza wannan kuɗi a kallah zai kai 5m, dan dollars ne, Lion bashi da wani kuɗin da ya wuce dollars, ga shi dama suna cikin halin babu, abinci ma idan sun sami na safe basu sa ran zasu sami na rana, sai ga shi yau Allah ya aiko masu Rimsha ƴar albarka ta zo ta basu kuɗin da basu taɓa tunanin zasu same shi ba a rayuwarsu, ai dole su yi kukan murna. Suna barin unguwarsu Kausar kai tsaye airport suka nufa, dan su koma Abuja. Su Akila kuma sun je Kaduna gidan Abbanta, a nan ne Ammienta take sanar da ita ɗan uwanta Duna ya dawo, ashe dama bai mutu ba, kuma ya musulunta shi ma, ya bar harkar tsafi, sannan ya gaya mata gaskiyar cewa Queen ba Mahaifiyarsu bace, yayarsu ce da suke uwa ɗaya uba ɗaya, dan haka ba Queen ce ta haifesu ba, sosai Ammien ta yi mamaki jin hakan, dama ita ta ra'ina girman Queen ɗin nan a ce uwarsu ce, ashe uwarsu ta mutu tun kanwar Ammien tana jaririya, kwananta uku da haifar kanwar Ammien ta rasu, Queen kuma ita ce babbar yayarsu, shi ne yasa ta rikesu tamkar ita ce uwarsu, dan ta girmesu sosai. Alhaji Mustapha mijin Hjy Zainab ma ya dawo, ashe bawan Allah yana a tare da Duna, tare suka gudu daga Daular Mutuwar lokacin da Queen ta yi ƙoƙarin kashesu, sun samu sun kuɓuta da kyar, sai dai ita Hjy Zainab kam ta mutu, Queen ta kasheta kamar yadda ta kashe Amarya matar Dr Salman, sai dai muce Allah ya sakawa Hjy Zainab kasheta da aka yi bada hakkinta ba, ita kuma Amarya dama mugun iri ce, sai dai muce masu hali irin nata su yi ƙoƙari su tuba su dai'na, ko kuma suma karshensu ta yi irin ta amarya ko fin haka. Sosai Akila ta yi murna da jin cewa dan uwan mamanta Duna ya dawo, kuma ya musulunta, ko ba komai yanzu tana da uncle guda ɗaya musulmi. Sun je gidan Abbin Irfan ma, a nan Abbi ya sanar da Aafia cewa kidnappers sun sako kawarta Rufee ta dawo gida, shi ma last week ya samu labari, amma sun yanke mata kafa guda ɗaya, dan kafar ta ruɓe, da kyar ma suka sakota, dan sun mayar da ita parkarsu ce, bada aure ba suke kwanciya da ita, kuma ba mutun ɗaya ba, wannan ya yi ya bawa wannan, tamkar wata karya haka suka mayar da ita, kawai Allah ya kaddara tana da rabon fitowa daga hannunsu ne ma yasa ta fito, badan haka ba da ai ita kam shikenan tata ta kare, yanzu ma cututtuka kala kala ta ɗauko, sai dai muce Allah ya bata lafiya ya kawo mijin aure, masu hali irin na Rufee ishara gareku, ku tuba ku da'ina. Aafia ko a jikinta da ta ji wannan labari, sai ma cewa da ta yi Allah ya kara. Sosai Aunty ta kara yi mata nasiha a kan ta zauna ta rike mijinta da kyau, ga shi ta samu miji jarumi ɗaya tamkar da dubu, ga kuɗi, mulki, ga shi soja, sannan ba karo mata kishiya zai yi ba, dan su mata ɗaya suke aura, dan haka ta kula da shi sosai su mori kuruciyarsu, ita ma Aunty ta haifi ɗanta namiji ɗaya. Godiya sosai Aafiar ta yi mata. Misalin karfe 1 aka daura auren Irfan da Pinky a kofar gidan Abbin, sannan suka je gidan Azharuddin Bature, a nan aka ɗaura auren Handsome da Zaira, daga nan suka wuce Kano wajen daddyn Jelly, nan suka sami Ayla da babynta kyakkyawan gaske, ita ma Maman Ayla tana gidan, dan dama daddyn Jelly ya mayar da ita wajen iyayenta ta nemi yafiyarsu, ta kuma yi sa'a albarkacin daddyn sun yafe mata, to shi ne ta cigaba da zama a gidan nasu, da Ayla ta haihu ne sai ta zo zama da ita. A hanyarsu ta dawowa Abuja daga Kano ne Jehan ta kalli A'isha ta gidan Hjyr daɗi a kan hanya kamar mahaukaciya tana tafiya, sai tsince tsince take yi, Allah sarki ashe har Kano su Hjy daɗi suka zo suka jefar da ita, ƙwaƙwalwarta ya taɓu. Sosai Jehan ɗin ta ji babu daɗi, sannan ta roki Areef da yasa a kaita asibiti a nema mata lafiya. Hakan kuwa aka yi, yasa sojoji suka ɗauketa dan su kaita asibiti. Akil da Umaisha dai suna Madina hankalinsu a kwance da ɗan babynsu gwanin ban sha'awa. Sun je kauyensu Maryam, a nan suka tarar da babanta ya mutu bayan fama da ya yi da jinya na tsawon lokaci, cutar daji ce ta kashe shi, ɗan banza ko alhakinsu Maryam ɗin ma ai ba zai barshi ba, haka zalika ita ma yayarta Allah ya yi mata rasuwa shekara ɗaya da suka wuce, Maryam ta sha kuka sosai da sosai, sai rarrashinta Sir Safwan yake yi. Masu hali irin na Baban Maryam aya gareku! Tun lokacin bai kure maku ba ku tuba!!. Ita kuma Adiva sun yi sa'a da suka je Maiduguri sun sami mamanta a can, dan haka uncle Shitu ya ɗauko matarsa suka dawo Abuja. Gaskiya ba karya family fa sun yi ziyara sosai, sun leƙe yan uwa da abokan arziki sosai. A takaice dai wata guda suka yi a Nigeria kafin su tattara su koma ƙasarsu. Lion ya cigaba da renon cikin Rimsha yana tarairayar kayarsa har sai da cikin ya bayyana kowa ya gani. Sun sha ruwan mamakin ganin cikin nata, a lokacin cikin nata ya kai almost 7 month, abin da yasa kuma basu gane da wuri ba, kowa dai yasan Rimsha bata fita, ko nan da part ɗin gwaggo Lion baya barinta ta je, kullum zaman ɗaki kamar wata mai takaba, matar kowa daga cikin QUADRUPLE suna yawonsu a cikin gidan, amma ban da ita, sai tafi sati bata fito daga cikin bedroom ba, abin ku da mai ciki, daga barci sai wanka, cin abinci da sallah, to da yake kowa yasan halin Lion da bakar kishi, sai babu wanda ya damu kansa ko ya yi tunanin wani abin a kan rashin fitowar tata, kawai sai suka zuba masu ido, basu ankara ba sai ganin Rimshar suka yi da katon ciki kamar me. Murna iya murna sun yi, Brr Naurat ta rinƙa yi wa Lion tsiya, abinku da Turawa ba kunya ke garesu ba, haka ta rinƙa yi mashi tsiya tana faɗa mashi cewa ashe abin da ya aikatawa ƴar mutane kenan yasa yake ɓoyeta a daki, sai dai ya ce mata ya yi ɗin ba kayarsa bace?. Dukkansu ba mai alamar kunya a idanunsa ko kaɗan, waɗan nan family guda biyu suna sha'aninsu son ransu. Rayuwar farinciki ya wuce baki ya faɗa suke yi, Anderson da His Excellence Lion ya turasu bakin gida, wani gidan kurkuku ne da yake a cikin teku, ba halin gudu daga wannan gida, dan a tsakiyar ruwa yake, ga bakar azabar da ake ganawa prisoners ɗin, abinci sau ɗaya ake basu a rana, kuma abincin ma rabin plat ne, ga uban duka da suke sha na safe daban na yamma daban, wannan gida shi ma Areef yasa aka jefa Hjyr daɗi da kuma Zinariya and Ƴar gwal bayan ya ruguje gidan nasu kenan. Rungunar sojoji ya sa suka dira a Nigeria bisa umarnin shugaban kasa, yasa suka yi pata pata da gidan Hjyr daɗin, aka saki duk yaran da suke a ciki dan su koma gidajen iyayensu, sannan suka kwaso Hjyr daɗin ita da masu goya mata baya, aka zubasu a bakin gida, wannan bakin gida sai mutun ya gwammaci mutuwa da shiga gidan, dan ɗakunan dake a cikin gidan ma a tsaye bawa yake kwana, ba halin kwanciya, kafafu duk su kumbura, idan kunga bawa ya miƙe kafafu ya ɗan kwanta, to sai da safe idan sun fito tsakar gidan, kuma ba kullum ake fito da su tsakar gidan ba, a sati sau biyu suke fitowa, sauran kwanaki duk suna cikin ɗaki a tsaye kamar gumaka, suna ganin izayar rayuwa. To masu hali irin nasu aya gareku, mugu dai karshensa bata kyau!!. Su kuma family yanzu komai zam zam, rayuwa mai tsabta tare da farinciki mai kawa suke yi har izuwa ranar haihuwar Rimsha, a lokacin kuma Maryam ta haifi yaro ɗaya, Adiva ta haifi yarinyarta mace, Aafia ta haifi ƴan biyu dukka mata, Ummin Dr Nawid tuni ta karɓe yaran wai ita zata renesu, Allah sarki tana son yara sosai, ga shi har yanzu Jellynta kuma Jellyn Yah Imran bata haihu ba. Gida ya kara cika sosai da yara da jikoki, yanzu kowa dakon jiran yaran Lion yake yi. Tun safe Rimshar take naƙuda har karfe 2 na rana, amma shiru bata haihuwa, da alama ba zata iya haihuwa da kanta ba, hakan yasa Lion ya ce ayi mata aiki a cire babyn kawai, dan hankalinsa ya kai makura wajen tashi, ya shiga damuwa na wuce misali, ya ji ba zai iya jurewa ba, dole kawai ayi mata aiki a cire yaran nan kada matarsa ta mutu. Dan dole su Dr William suka karɓi maganar Lion ɗin a in da aka shirya tsab aka yi mata aiki, cikin ikon Allah aka ciro mata baby's nata Maza guda uku da mace ɗaya, duk cikin QUADRUPLE ita kaɗai ta haifa masu ɗiya mace, yarinyar tamkar Pinky, ma'ana kamar Lion ɗin, harta kalar idanunta, duk yaran babu wanda ya biyo Rimshar, dukkansu Lion ɗin suka ɗauko, harta kwayar idanuwansu blue eyes ne, sak irin nasa. Gwaggo baki har kunne, dama burinta kenan, ga shi Lion ya samu ɗiya mace, abin ba'a magana, gwaggo kamar baki ba zai rufu ba, kowa idan ya zo ganin baby's macen yake ɗauka, sun fi son macen sama da sauran mazan, dan sun gaji da rike maza, yanzu sun samu canji, harta su Areef da suka zo ganin yaran macen suka ɗauka, kowa santin macen kawai yake yi, daddyn Rimsha ma macen ya ɗauka da ya zo. Abin har sai da yasa gwaggo ta ce, kai lafiya kuwa? Kowa idan ya zo sai ya ɗauki macen yana santinta, dole ta rinƙa yi wa yarinyar nan addu'a, idan ba haka ba ai sai a samu matsala. Yarinyar ne ta ɗauko shegen shiga rai irin na mamanta, kowa sonta yake yi, gata jajir irin babanta, kunsan blue eyes kuma da shiga rai da ɗaukar idanu, musamman a wajen kananan yara, sai hakan tasa yarinyar ta kara shiga ran kowa. Shi kansa Lion ɗin ana ciro yaran bayan an gyarasu macen ya ɗauka, ita ya fara yi wa huɗuba, yau dai bai ce baya son ganin yara ba, wani irin azababben so ma yake yi wa ƴaƴan nasa, sai dai yafi son macen nan, dan wlh ita ce ta fito sak shi sosai tamkar an tsaga kara, ga ɗan bakin nan nata kamar nasa aka cire aka sanya mata, sosai yake jin azababben kaunar yarinyar, hakan yasa da ranar suna ta zago sai ya sanyawa yarinyar sunan gwaggo, hjy gwaggo mulki ta karu......😂 Su kuma mazan ya yi wa daddyn Rimshar takwara, ɗaya kuma Dr William, ɗayan Dr Salman. Wlh baki ya yi kaɗan wajen zayyano maku irin farincikin da waɗan nan familyn suke ciki. Daga kan waɗan nan QUADRUPLE da Rimsha ta haifa, Lion ya dakatar mata da haihuwa, ta hanyar tsari mai kyau, ya ce yaran sun ishe su, huɗu yake da buƙata, kuma ga shi ya yi sa'a ya samu mace da maza uku, kunga yana da kowani jinsi, dan haka sai ya ce su kam sun gama kenan, sun rufe kofa, shi ma Areef hakan ce, ya ce sun gama kenan, amma shi Aseef ya ce zasu kara ɗaya idan ta huta nan da shekara biyar haka, zasu gwada ko zasu sami mace, shi dai Sir Safwan bai ce komai ba, binsu da idanu kawai yake yi abinsa, dan shi bashi da zaɓi a kan yara. After some years. Sanye take da wando three cuter zuwa gwiwa da ƴar vest zuwa cibiyarta, ta kara kyau ta yi ƙiba sosai, tamkar ba ita ta haifo QUADRUPLE ba, ta yi haske komai yana nan cif cif. Hannunta na rike da wasu towels guda huɗu masu matuƙar kyau, launin white color. Tafiya take yi komai na jikinta yana motsawa, kai tsaye wajen katafaren pool da yake cikin gidan ta nufa, ba White house ba, ainahin Daular Lion ɗin, nan suka zo hutu, wani lokaci Lion ɗin yana ɗaukosu su zo gidan su yi two weeks su ɗan huta ba tare da damuwar kowa ba kafin su koma white house. A bakin pool ɗin ta tsaya tana faɗin. "Oya come out, kuzo ku je ku ci abinci". Kyawawan QUADRUPLE nata ne a cikin pool ɗin tare da daddynsu, ya ɗaura takwarar gwaggo wadda suke kira da pretty a saman Lion chest nasa yana tara mata kyakkyawar dark black curly hairnta da yake jike da ruwa. Yaran nan tun suna ƴan wata shidda Lion yake shiga dasu cikin pool, sai ya ɗaura masu robar hana yaro lumewa a wuya, ya jefasu cikin ruwan suna yawo asama ya shiga shima su yi wanka a tare, har ya saba masu, ya koya masu, yanzu kullum suna ninƙaya a ciki abinsu, ita kam Rimsha ko a jikinta. "Mummy we can't eat anything now, ki bari sai anjuma". Cewar ɗaya daga cikin mazan wanda suke kira da little, dan shi ne karami kuma shi ne takwaran Dr William. "Noorish Allah kai ne kake koyawa yaran nan duk wani abin da suke yi, zaku fito ne ko sai na shigo na same ku?". Ɗaya takwaran daddynta ɗin ne ya ce. "Mummy we're soldiers, bamu jin yunwa, daddy ya ce sai muna nuna jarumta zamu zama jarumai irinsa, so we can't eat anything". Harara ta wurgawa Lion ɗin, ya tsareta da idanun yana kare mata kallo bai ce da ita ko uppan ba, shi wani azababben sha'awarta ma yake ji, ta wani kara kyau, komai yana nan cif cif ɓul ɓul kamar bata taɓa haihuwa ba, ga tula tulan nan nata kamar an hura balo balo, sun sha gyara a wajen gwaggo, duk sai ya ji kai ina yana hannu fa. Ita kuma haushinsa ma take ji, duk ya bi ya yi wa yara huɗubar banza wai su zama jarumai, duk ya koya masu halayyarsa, harta macen ma wai sai ta tsaya tana wani cewa daddy ya ce zata zama jaruma idan ta yi kaza ko ta yi kaza. Ganin sai harara take wurga mashi ne yasa ya kashe mata ido ɗaya tare da motsa laɓɓansa a hankali tamkar mai ciwon baki ya ce. "In zo ne ƴan mata?". A kule ta ce. "Allah Noorish ba zan barka ba, wato kai bama kasan ina jin haushi ba ko?". Sake kashe mata ido ɗaya ya yi tare da ɗaga mata gera guda. A kule ta jefa mashi towels da suke hannunta wanda ta ɗauko zata gogewa yaran jiki, ta jefa mashi su a fuska tare da juyawa ta bar wajen tana huci. Dariya Pretty ta yi har sai da dimple nata irin na mamanta suka lotsa, cikin wani ɗan siririn muryarta na yara mai shegen daɗi kamar na babanta ta ce. "Daddy mum want to be a hero ko?". Nisawa ya yi kafin ya ce. "She's a hero since before, now let's go and eat food, kunga mum ɗin ku ta ɓata rai, kada ta yi fushi". Ya kai karshen maganar tare da zame towels ɗin daga saman face nasa, sannan ya ɗaga pretty ɗin sama ya fitar da ita daga cikin ruwan. Da sauri su little suka riga shi fitowa, kamasu ya yi tare da ɗan goge masu jiki, sannan ya ce to su je. Gaba suka yi ya rufa masu baya bayan ya ɗauki pretty cancak kenan, ita duk in da zai je to tana jikinsa, ɗaukarta yake yi. A parlourn sama na part ɗin Lion ɗin suka iskon Rimshar, ta fitar masu da kayan da zasu saka. Ta zauna shiru suna hira da Malika, Malikar ta zo tayata murna ne, shi ne take tambayarta ina ta je tsawon shekaru biyar yanzu rabonta da ta leƙota, nan take gaya mata cewa tana nan tana kusa da su, kawai bayyana ne bata yi, amma tana tare da su, shi ne Rimshar ta ce to dan Allah yau kam ta gaya mata a ina ta sansu?. Yau dai bata ki gaya mata ba, labari ta fara bata na zaman da suka yi a Dubai, da taimakon da daddynta ya yi wa iyayen Malikar a rashin sani, bai san cewa dattijawan da ya taimakawa a kan hanya aljanu bane, shi ne yasa dayawan lokuta ba kyau walaƙanta ɗan adam, musamman ma dattijo, dan baka san waye shi ba, ba kuma kasan a ina zaku sake haɗuwa ba, to su dai iyayen Malika suna yawan zama a suffar mutane ne, basu cika zama a suffar aljanu ba, hakan ya ba daddyn Rimshar nasarar taimaka masu, har gida ya saya masu kyauta, shi duk a tunaninsa bayin Allan ƴan adam talakawa ya taimakawa, dan ya gansu cikin kunci da talauci a gefen titi, a lokacin kuma suna a tare da mummyn Rimshar ne, lokacin Jehan tana karama Rimshar kuma tana ciki ba'a haifeta ba, ita kuma Malikar ta tafi yawonta abinta, to wannan taimako da ya yi masu ne yasa suma suke taimakawa iyalansa babu kakkautawa, dan duk wani aljani na kirki baya manta alkhairi, suna da tuni, sannan suna da rama alkhairi da alkhairi, sai shaiɗanun cikinsu ne basu da kirki sam sam, wannan shi ne a takaice tarihin tarayyar su Malika aljana da su Rimsha, babu wanda yasan da Malikar sai Rimshar, dan a lokacin ita ce a cikin cikin mum, kuma ba tare da Jehan suke tafiyar ba, Jehan tana wajen gwaggo a gida, so Rimshar kawai suka sani a lokacin, shiyasa ita suka fi tallafawa kuma suka bayyanawa ta sansu, fatan kun gane?. STORY🔥 Kusa da ita Lion ɗin ya zauna ya hau tayata sanya masu kayan tare da shafa masu lotions nasu, gwanin ban sha'awa. Su Aseef kuwa suna white house tare da yaransu, yanzu Aseef da Akila an rage shagwaɓa, amma ba wani sosai suka rage ba, sai dai kuma fa sun haifo irinsu, dan kuwa a cikin TRIPLETS nasa akwai mai shegen shagwaɓa irin baban nasa, da an taɓa shi kaɗan sai kuka. Dama aka ce gado ba karambani ba. Bayan sun kammala shirya yaran a tare, sai suka nufi saman table, gwanin ban sha'awa suka ci abinci a tare, sai hira sama sama suke yi har suka kammala, sannan ne Lion ya ce su zo su ne wajen gudun motsa jiki. Gaba yaran suka yi da gudu suna rige rige, rufa masu baya ya yi suka bar Rimshar tana aikin cin fruits salad da ta haɗa. Gudu ya fara sanya yaran suna yi, rige rige yasa su su yi, ya ce duk wanda ya riga shi ne hero, kun san wajen motsa jikinsu already, waje ne mai matuƙar girman gaske. Fara gudun suka yi babu kama hannun yaro, gwanin ban sha'awa, ƴan ɓul ɓul dasu kamanin daddyn nasu, sak kuwa kamar an tsaga kara, da ganinsu ba tambaya kasan cewa ƴaƴansa ne, yana ji da su ne fiye da yanda nake son kansa, ya dai ce daga kansu an rufe kofa a haihuwa, Rimsha ta huta baiwar Allah. Yana tsaye yana kallonsu cike da kaunarsu har suka je suka juyo, pretty ta riga kowa isowa. Tsalle ta fara yi tana faɗin. "I am a hero daddy...." Bata gama rufe baki na boy takwaran Dr Salman ya tsinketa da mari a kumatu. Cikin huci da fushi ya ce. "Baki ji daddy ya ce maza sune a sama da mata ba, so mune hero's ba ke ba!". Ihu ta sanya tare da dafe kuncinta. Tsugunnawa a kusa da ita Lion ɗin ya yi yana faɗin. "Sorry my momma, kyale boy ba zamu je Russia da shi ba........". Katse mashi maganarsa Rimsha dake tsaye a bayansu ta yi da cewa. "Gaya masu zaka yi mata sune a sama da maza ba maza ne hero's ba!!". Tayi maganar tana murtuƙe fuska, irin Boss ɗin nan..........😂 Miƙewa tsaye ya yi yana faɗin. "No maza sune a sama da mata, kada ki ɓata mun tunanin yara". Tsalle little ya yi yana faɗin. "Yes daddy mune a sama". Harara ta wurgawa little ɗin kafin ta ce. "Mata ne a sama da maza, so gara ma ka ji in gaya maka......" Lion bai bari ta karisa maganar tata ba ya ɗauketa cancak yana faɗin. "Boy little yanzu ku gaya mun wanene a sama? Kunga dai yadda na ɗauki mum ɗin taku kamar baby, to waye yafi wani karfi?". Da sauri little ya ce. "You dad, kai ne hero a kan mummy". A kule Rimsha ta buɗe baki zata yi magana, kamar yasan me zata ce ya yi maza ya rufe mata baki tare da nufar cikin gida da ita yana gayawa su Little su je wajen uncle Donal su yi wasa bari ya zo. Okey suka amsa mashi da shi tare da wucewa wajen sojojin suna neman Donal, ita kuma pretty yarinya mai hakuri mai irin halin Areef, sai ta wuce bedroom nasu mai shegen kyau ta haye saman bed ta kwanta, hannunta na'a saman kumatunta in da boy ya mareta barci ya ɗauketa, baiwar Allah, tana da kyan zuciya tamkar uncle nata Areef, sai dai akwai ta da faɗa idan ka kureta. Shi kuma Lion bai sauke Rimsha a ko'ina ba sai a saman katafaren bed nasu. Yana sauketa ta yi saurin yunkurawa zata bar bed ɗin. A hanzarce ya riƙota yana faɗin. "Haba mana rigimammiyata, yanzu me kuma nayi?". "Maza sune suka fi mata jarunta ko? To ni raguwace ba zan iya sake ɗaukarka ba". Ta kai karshen maganar tare da sake yin yunkurin sauka daga saman bed ɗin. Fisgota ya yi ta faɗa saman Lion chest nasa, juyawa da ita ya yi ya mata rumfa da faffaɗar kirjinsa, cikin sanyin murya ya ce. "Am so so sorry my Queen, mata sune a sama to, yanzu dai please a kula dani, tun ɗazun fa nake jin ina hannu, please mana gimbiyata". Harara ta wurga mashi ba tare da ta ce komai ba, shi kuwa hakan ma ya yi mashi, tuni ya kara matseta a jikinsa ya fara aikin matse mata tula tula, dama a hannu yake. "Noorish wai yanzu da gaske ba zaka taɓa yi mun murmushi ba a rayuwarmu? Ban fa taɓa ganin murmushinka ba". "Ba ke kaɗai ba my Meesha, ni babu wanda ya taɓa ganin murmushina, dan bana yi kuma ban iya ba". Yana magana yana matse mata tula tulan nata kamar zai fasa mata su. Shigewa jikinsa da kyau da kyau ta yi tare da kai hannunta a saman Heronsa tana faɗin. "Bari na ji". Wash ya furta da karfi tare da kara matse mata breast ɗin nata tamkar su ne suka taɓa mashi heron nasa, da zafa zafa ya fara kissing nata, tuni ya rabata da kayan jikinta suka hau aikin da suka saba..................... (Da alamun dai zasu samowa su pretty kanne ne😌 Irin wannan zafa haka?) A can white house kuma, Areef ne sundume tsulundum cikin katafaren pool shi da Jehan, sun manne da juna kamar nace zan rabasu, a cikin pool ɗin ma basu hakura ba, sai sun yi kiss, ga kyawawan QUADRUPLE nasa suna wasa a wajen, suma jikinsu na sanye da kayan wanka, amma basu shiga cikin ruwan ba, suna ta aikin guje guje dai a wajen, kyawawa da su masu kama da daddynsu. Shi kuma Aseef yana can wajen basket ball shi da Akila da TRIPLETS nasa, kwallo suke bugawa, dukkansu sanye suke da gajerun wanduna zuwa cinyarsu, har ita kanta Akilar, wando guntu zuwa cinya take sanye da shi, sai ƴar riga da bata wuci cibiya ba, karfi da ya ji dai sun zama turawan suma. A can cikin gida kuma Gwaggo and Dr William suna zaune saman dining table suna cin abinci, sai zuba love nasu suke yi tamkar ba sune iyayen QUADRUPLE ba. Sir Safwan da Maryam nasa da babynsu guda ɗaya sun bi Mahhir wato Alex kasar Russia, kun san shi Alex a kasar Russia ya girma, so ba zai iya juya masu baya kamar Brr Naurat ta yi ba, ita dai ta hakura da su, amma shi yana zuwa kai masu ziyara abinsa, so wannan karon sun tafi a tare da Sir Safwan. Uncle T da Aafia suna zaune a parlournsu, Aafia ta tada kai da saman laps nasa ga wani katon ciki a jikinta, baby's ɗinta kuma suna wajen Ummin Dr Nawid, dan ita ce ma ta renesu. Sai mammatsa mata jiki uncle T yake yi wai yana yi mata tausa. Mark and Anaya sun tafi yawonsu abinsu, dan Anaya akwai ta da shegen son ganin gari, bata zama. Daddyn Rimsha da mummynta ma soyayya babu kama hannun yaro. Ita kuwa Josephine tana tsakiyarsu ne, tana bayan kowa baiwar Allah, babu ruwanta da damuwa, sai son taga farincikin kowa, Allah sarki su Anderson ne dama duk suka sanyawa su Lion tsanarta, sune nan suka bawa su Rimsha chain mai poison lokacin nan, sai suka yi amfani da face ɗin Josephine ɗin, duk dan kada su Lion su so ta har su je wajenta ta gaya masu gaskiyar abin da yake faruwa, yanzu dai komai ya wuce, ta dawo cikin ƴan uwanta baiwar Allah, ta rungumi kowa nata ne. Rayuwa yanzu komai yana tafiya dai'dai, sai farinciki suke yi, komai sai kara haɓaka masu yake yi. A ɓangaren Lion da Rimsha kuwa, haka suka murji juna son ransu, sannan suka kwanta manne da juna, sai shagwaɓa Rimsha take zuba mashi, shi kuma sai biye mata yake yi ya bar su boy a wajen Donal, dama Donal shi ne mai kula da su, yana matuƙar kaunar yaran sosai. "Noorish yaushe zamu je Nigeria?". Ta faɗa tana mai da hannunta a saman Heronsa. "Zaki fara ko?". "Ni me nayi to?". Ta yi maganar tana turo mashi baki. "Okey baki yi komai ba, bari dai ni nayi wani abin". Ya kai karshen maganar tare da yunkurawa zai miƙe ya haye kanta. Da gudu ta sauka daga saman bed ɗin tare da ɗaukar wani towel dake a saman bed ɗin ta nufi waje tana ɗaurawa a jikinta. A dubu ya diro kasa ya bi bayanta. A parlourn ƙasa suka ci karo da su little suna wasa, yanzu suka dawo daga wajen Donal. A dai'dai tsakiyar parlourn ya capkota yana faɗin. "Yaushe kafafunki suka yi kwarin da zaki tsere mun?". Shiru ta yi tana turo baki tare da sauke numfashi, ta sha gudu. "Muje ki kwantar da abin da kika tayar". Kukan shagwaɓa ta saka mashi tana faɗin. "Kai Noorish ka barni haka". "Ai na barki ke ce nan kika taɓani, dan haka tun da kika taɓoni sai kin cikasa ladarki, kawai muje". Ya kai karshen maganar tare da ɗaukarta cancak suka haye sama. Sai dariya su little suke yi suna faɗin. "Daddy ya fi mummy karfi, mummy bata da karfi, kullum daddy shike ɗaukarta sama". Tsawa yayansu babba wato wanda aka fara haifa ya daka masu. Fuska a ɗaure tamau kamar na babansa Lion ɗin, ya ce. "Idan baku yi mun shiru ba sai na ɓallaku, kun ishe mutane tun ɗazun da cewa daddy ya fi mummy karfi, to idan ma haka ne so what? Allah ku bari na sake jin voice na wani a nan ku gani, duk sai na ɓallaku". Hayewa saman sofa boy ya yi ya kwanta yana faɗin. "Ni ina kewar Son wlh". Wato yaron Areef babban kenan. Wani uban harara yayan nasu ya dalla mashi, sam bai san lokacin da malaman nutsuwa suka shige shi ba. "Da kai da son ɗin duk zaku karɓi punishment bari mu koma white house, zaku sani ne". Da sauri little ya ce. "Big bro amma ban da ni ko?". Wani kallon banza ya wurga mashi kafin ya ɗauko iPad nasa ya fara buga game ba tare da ya sake yin magana ba. Duk cikin ƴaƴansu Lion ɗin wannan Big bro ɗin nasu ya fisu iya shege, ga shegen faɗa kamar wani tiger, ga ɗan banzar zuciyar bala'i, baya da yawan magana, amma idan ya yi kuma to umarni ne, kamar dai babansa Lion, Lion ɗin kuwa, kara ɗaure mashi gindi yake yi, dan a cewarsa wai haka yakamata namiji ya kasance, ƴanƴan Aseef da Areef sune manya, amma Big bro ya zama yayansu, dan dole suke ce mashi Big bro, saboda tsoronsa da suke ji, ga waɗan nan shegun dara daran blue eyes ɗin nasa irin na babansa, idan ya zarosu sai sun yi wani irin kyalli mai rikitarwa, hakan yasa yaran suke kara tsoronsa, tun yana karami idan ya yi wa yaro mari ɗaya sai wajen ta bada shatin yatsu. Kuma dan bala'i kowa ya fi sonsa a kan sauran ƴan uwansa, kunsan Hjy Gwaggo da shegen son isa da izza, shi ne yasa ta fi kaunar Big bro ɗin sama da kowa a cikin jikokin nata, dan shi ne mai irin halinta ita da Lion, da Big bro da Pretty sune sanyin idaniyar Familyn Dr William gabaɗaya. KAI WAƊAN NAN AHALI SUNA SHA'ANINSU..🔥 Saman bed Lion ya mayar da Rimsha tare da hayewa ya rungumota yana faɗin sai ta kwantar da abin da ta tayar. Tana turo ɗan bakin nan ta zura hannunta ta fara shafa mashi Heron nasa dake tsaye kyam. Wani irin lumshe idanu ya yi yana faɗin. "My Meesha ke over ce, ke ɗin maƙura ce, kina kasheni da daɗinki, You're so sweet my Queen". Zura harshenta a cikin ɗan bakinsa ta yi ta fara juyawa cikin salo. Jawo masu bargo ya yi ya rufesu har kawunansu..........🌝 NI MA PRINCESS FATEEMA ZAHRA NA JA ALƘALAMINA IZUWA WATA DUNIYAR..😌 TAMMAT BI HAMDULLAH🔥. HAPPY END🕊️❤️🔥💘🤸💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃 A Nan na kawo ƙarshen wannan littafi mai suna TRIPLETS dana ɗauki lokaci mai tsawo sosai ina rubuta shi, kuskuren da yake ciki Allah ya yafe mun, duk wanda na ɓatawa a tarayyata da shi a cikin wannan littafi na TRIPLETS ina mai bashi hakuri, ya yafe mun! Ɗan adam ajizi ne!. Kai amma dai yau zan yi barci har da munshari😌🌝 na huta Wayyo ni daɗi kashe ni!.🤸💃🤸💃🤸💃 And finally my lovely fans that patronized me,🔥 suka jure suka bibiyeni tun daga farkon wannan book na TRIPLETS har izuwa karshe , wallahi ina yin ku, without u all they won't be me FATEEMA ZAHRA MUSA, Allah ya bar Kauna,🤍 Allah subhanahu wata'ala ya dawwamar mun daku a cikin farinciki mai ɗorewa, Allah ya baku arziki from every angle wanda babu talauci a bayansa, Allah ya kara mana son Manzon Allah manzon tsira, Allah yasa mu tashi a cikin bayin da zai yi alfahari da su a ranar gobe kiyama! Nagode! Nagode! Nagode! ina alfahari da ku. My lovely people's,🤍 i mean my ƴan Amana ƴan comments section group. A'isha Baita Jidda, Maman Yasmin, Amirat iliyasu Ladan, Maman sultan, Maman abba, Adama goni, Queen Hassena, Anty rifat, Baby baby, Daughter in law, Hafiza Ayuba, Jiddatulkhair, kareema, Maryam, Oum samha, Reechel, Ruky Anty, Oum Ihsan, Young lady, Zarah, Faty beli, Adama, Ameera, Aysha, Mrs Fruits, Zainab mansur, Fm gombe, Beentu muhd abdullah, Amina niger, Aisha galadima, Fatima Ridwan, Maman Samrah, Mrs deen mom jidda, Mrs Hyder, Official Ameera, Yasmina, Anty Nihal, Aysha musa, Fatima kabir, Hajara Ahmad, Huraira abubakar, Xainab idris muhd, Teema, Sm farida, Ummee, Ummu amatullah, Mom Bilal, Oum ayda, Halima idris Ahmad, Hauwa'u Bala msh, Rukayyah Ahmad, Naja'atu, Hasiya Abdurrahman Ago, Fatima Ado, Princess, Deejarh's collection, Maman Usman, Baby, Meeno, Luvly bee, Safna, Maman Noor, Fatima shamsuddin, Mariya Nasir Hassan, Meenart, Aisha Jahazu, Maman Zaitun, Yusra, Khadija Musa, Maryam, Fa'eeza Yusuf. Kai na rantse da Allah sunayenku ba zai yi ko kwatan kirguwa ba, to da duk sauran masu bani hot comments da ban kira sunansu ba, ina alfahari da ku, kuma kuna ra'ina, a gaskiya na ji daɗin yadda kuka rinƙa bani hot comments ba gajiyawa, Allah ya bar kauna🔥🤍 Fatan zaku cigaba da nuna mun kauna kamar haka ko fin hakan ma. To daga karshe dai sai mun sake haɗuwa da ku a wani zazzafar sakon littafin nawa mai sunan *RAWANIN ZALINCI* shi wannan ba zazzafa bane ba ma, tafasa yake yi yana bada tiriri, salonsa daban ne, ina mai tabbatar maku salonsa daban ne, ku my peoples kun sani already ba sai na sake faɗa ba, PRINCESS TEEMA taku mai abin ban mamaki ce, kun san zaku sha mamaki a wannan karon ma, kun san idan nace salonsa daban ne, to fa daban ɗin ne, trust me ya sha banban da sauran labaran da kuka sani, na tabbata da hakan, kuma ina kara gaya maku yasha banban da kowani irin littafi, dan haka kada ki yarda ki bari a baki labari, da a baki ai gara ki bayar, gani ya kori ji, dan haka ki hanzarta maza ki kasance a cikin tafiyata, dan ki gani ba ki ji labari ba👌 ina kara jaddada maku wlh ba zaku taɓa yin danasanin bibiyar wannan littafi mai suna *RAWANIN ZALINCI* ba, tabbas zaku yi alfahari da ni fiye da tunaninku, kun sani Alkalamin PRINCESS TEEMA alkalamina mai ilmantarwa, fadakarwa, wa'azantarwa, tare da nishaɗantarwa ne, uwa uba ga koyar da ilimin rayuwa, na san kun san da hakan, dan kune ma kuka shaideni da hakan, bani na faɗa da bakina ba, shaidarku ce wannan, kun shaidani bana rubuta shirme da abubuwan banza a labarina, bana rubuta abin da hankali ba zai ɗauka ba! Bana rubutu kamar tatsuniya! Ina rubutu ne kamar gaske, abin da yake kewaye damu!! Kada dai na cikaku da surutu, mu haɗe daku a cikin littafin *RAWANIN ZALINCI* kawai, zaku sha mamaki.🔥🤍 Ku daga jin sunan *RAWANIN ZALINCI* kun san da akwai abubuwa ba kaɗan ba wanda baki ya yi kaɗan ya kwatantasu!! Fatan zaku bani haɗin kai?. HAR KULLUM TAKU CE FATEEMA ZAHRA MUSA🤍 A-K-A PRINCESS TEEMA 🔥 ƳAR AMANARKU🔥🤍 SSG Palace Gujungu