Showing 48001 words to 49771 words out of 49771 words

Chapter 17 - Alwashi Book 1 Complete Hausa Novel

01 Oct 2025

448

girke girken da aka wuni anayi saboda shi, akusa da mami ya zauna yana kallon hafsa wacce ke tsugunne tana hada salad wanda zasu ci abincin dashi,sai lokacin wai ya lura da kunshin dake hannunta duk hidimar dazu idonshi bai kai kan kunshin ba,

Tashi mami tayi zuwa kan dining domin debo wasu kwanuka,

Hannunshi yakai kan na hafsa,

"Ya akayi dazu banga kunshin nan ba sai yanzu? Koda yake ai ni yau dinne gaba daya amaryar tawa tagama rudani, ta dauke hankalina"

Murmushi hafsat tayi saboda jin abinda yace, janye hannunta tayi daga jikin nashi saboda taga mami na kokarin fitowa ganin haka shikuma ya wayance da lakuto salad din yakai bakinsa,

Kamar koda yaushe a cikin babban faranti yauma suka zuba abincin suka hadu suna ci, idan yusleem yafaki idon mami sai ya kwace abincin hafsa ya kai bakinsa,

Tun daga yanayin cin abincinsa mami da hafsa suka gane cewar lafiya ta samu domin yau yaci abinci sosai wanda rabon da yaci irinshi har anmanta,

Komai da suka girka saida yaci, kallonshi kurum hafsa keyi saboda ganin yanda ya bude ciki ya narki abinci,

Kan kujera yaje ya mike, mami na zaune kusa dashi suna dan yar hira dangane da tafiyarsa da dawowar tashi yana sanar da ita abubuwan da suka wakana,

Hafsa kam wurin da suka gama cin abinci tashiga gyarawa tana kwashe na kwashewa tana kaiwa kitchen ba zuwa tayi tasasu agaba ba domin tasan tsakanin d'a da mahaifi dole akwai abubuwan da zasu tattauna atsakaninsu,

Saida ta kalkale wurin tass sannan ta kunna turaren wuta lokacin har 6 tayi, tashar zee world ta kunna tazauna tana kallo bayan ta dora dan karamin pillow din kujera akan cinyarta,

Tana ta kallonta sam hankalinta baya kansu mami, pillown taji anzare an kwanto akan cinyarta,

Saurin kallon wurin dasu mami ke zaune tayi nan taga mamin bata nan, kallonshi tayi lokacin da yake kara gyara kwanciyar kanshi akan cinyarta,

"Wai yaya yusleem yau da me kazo ne? So kake sai mami tafito ta ganmu?"

"Mami bazata fito yanzu ba ai, tashiga bedroom dinta kuma kin san idan tashiga bata fitowa sai bayan tayi salla"

Shiru tayi, hannunta ya kamo ya hada da nashi yana gani,

"Kinyi kyau..."

Shiru tasake yi domin sai tana ganin kamar gatse yake yi mata, shikuma tsakaninshi da Allah har cikin zuciyarshi yake fada,

"Yanaji kinyi shiru? Uhm"


"Babu komai"

"Ban yarda ba" yafada yana murza babban dan yatsanta,

"Lokacin salla yayi fa.."

Tashi zaune yayi yana kallonta,

"Tashi muje to muyi"

Tashi tayi tabi bayanshi zuwa cikin bedroom din,

"Kishiga ki fara yin alwalar"

"Nifa inada alwalata"

Murmushi yayi ya matsa kusa da ita,

"Allah karya kike, infada miki gaskiya? Wallahi ko tsarki bakida shi garama kije ki sake kiyi alwala.."

Tamkar kasa ta tsage ta shige haka taji dan kunya, ganin yana kokarin sake yimata wata tabargazar yasata juyawa da sauri ta fada cikin bathroom din ta turo kofa, murmushi yayi ya cusa hannuwanshi cikin aljihun wandon jeans din dake jikinsa......



_Fans aci gaba da yimin uzuri domin har yanzu ban gama warwarewa ba, fatan alkhairi agareku all..._




_*Ummi Shatu*_👌🏻

© *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_




*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_




*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_



_DEDICATED TO MISS XOXO_


*Kina ina Hawwa Jidda Aliyu? Page din yau nakine tawan, Allah yakara miki basira da hangen nesa...ina yinki hawwa kulu..!*



*47*




***Yana tsaye ya bawa kofar bathroom din baya hafsat ta fito hannunta rikeda dan kwalinta tana kokarin daurawa,

Juyowa yayi yana kallonta, ganin gashin kanta wanda yasha gyara da yayi yasashi karasawa gabanta ya rike dan kwalin,

"Yanmata harda su gyaran gashi shine ba anuna min tuntuni ba?"

Hancinshi yakai kan gashin wanda har hafsat na iya jin dumin numfashinsa wanda ke sauka akan gashin nata,

Hannunshi tarike tana mai bata fuska,

"Yaya yusleem dan Allah kabari, Allah lokacin salla zai wuce.."

"Da yaushe ma aka kira sallar? Da sauran lokaci ai baby.."

Ribom din dake daure da gashin nata ya warware yasoma baza mata shi akan kafadarta,tamkar mai yimata tafiyar tsutsa haka taji,

Rike hannunshi tasake yi,

"Nikam gaskiya yaya yusleem alwalata..."

Murmushi yafara wanda yakarashe shi da dariya,

"Ta karye?"

Girgiza masa kai tayi alamun a'a,

"A'a dai baby hafsa fada min gaskiya, ta karye?"

Runtse idonta tayi tana rikeda hannunshi,

"Dan Allah kabari kar time din salla yakure mana.."

"To bari naje masallaci..."

Har yasaketa yasake rikota,

"Bari kawai nakarasa karyata inyaso sai kisake sabuwa"

Kafin takai ga yin magana har ya kama lips dinta,

Mintsininshi tayi a hannunshi nan yasaketa yana dariya, fita yayi daga cikin dakin zuwa bathroom din dake cikin falo anan yayi alwala yatafi masallaci.

Koda hafsa ta idar da sallar magrib kin fitowa tayi anan inda tayi salla ta kwanta har saida lokacin sallar isha yayi sannan tatashi ta gabatar da sallar isha da shafa'i da wutri,

Batare da ta cire hijab din da tayi sallar ba tafita falo wurin mami,

Mamin nazaune da carbi a hannunta tana ja sannan kuma tana kallon labarai a tashar BBCW,

Tana zama yusleem yana shigowa, kin kallonshi tayi tamaida idonta kan tv, a kusa da mami ya zauna wato kujerar dake kallon ta hafsa,

"Hafsa akawo abinci ko?" Mami tayi maganar tana kallonta,

"To mami bari nakawo muku nidai nakoshi.."

"Nima gaskiya na koshi amma zansha kunu" yusleem yayi maganar yana zaro wayarshi daga aljihun jeans dinshi,

"To shikenan adama mana kunun gaba daya sai musha" inji mami,

Tashi hafsa tayi zuwa kitchen, mintuna kalilan ta damo kunun ta dawo falo dauke dashi,

A cup ta zuzzuba musu ta dauko sugar da madara tasa musu,da kafarshi ya tabota kasancewar tana zaune akasa kusa da kujerarshi, dagowa tayi ta kalleshi,

"Wannan na waye kike zubawa?"

"Nakane.." Tabashi amsa,

"Yayi yawa ai, rage"

Sauka kasan shima yayi kusa da ita,

"Bar sugar dinnan haka, amma ki kara milk da yawa"

"Duk wannan wadda nasa batayi ba?"

"Nifa ke nake yiwa gata yarinya, ko bakya so indaina?" Yayi maganar cikin rada rada tayadda mami bazata jiyo ba domin tana dan nesa dasu,

Shiru tayi masa saboda tagane abinda yake nufi, ita yau mamaki yake bata domin kamar zuwansa Cairo dinnan rashin kunya yaje ya koyo domin tunda yashigo cikin gidan yau yaketa yimata abubuwa masu nauyi,

Tura masa gwangwanin madarar tayi gaba daya da kunun nashi tadauki na mami takai mata tadawo ta zauna tasoma shan nata kunun,

Tana jinshi yanata dungurinta tarabu dashi daga karshe ma tashi tayi tawuce cikin daki tayi kwanciyarta, wayarta ta jawo nan taga miss called din umminta, kiranta tayi suka gaisa suka dan taba hira daga nan sukayi sallama.


Tana kwance lullube cikin bargo taji shigowarshi, rufe idonta tayi kamar mai yin bacci, akusa da kafarta ya zauna yakama yan yatsun kafar yasoma jansu daya bayan daya suna yin kara, duk da tanajin zafi shiru tayi masa ita adole bacci take yi,

Jin tayi shiru yasashi haurawa saman gadon, abayanta ya kwanta bayan ya dan ture bargon da take ciki,

Kamshin turarenshi da taji shine ya haifar mata da kasala, luf tayi tana jinshi yana baza mata gashin kanta,

Juyo da ita yayi tana fuskantarshi, jikinta ne yabata cewar kallonta yake domin tsawon mintuna biyar zuwa shida tajishi shiru baiyi koda motsi ba kuma tasan ba bacci yake yiba, ahankali ta bude idonta guda daya kadan ta kalleshi ai kuwa kamar yanda ta zarga ganinshi tayi ya zubawa halittar kirjinta manyan idanuwanshi ko kiftawa bayayi, ganin yana kokarin kai hannu yasata saurin juya masa baya kamar mai bacci, juyo da ita yasake yi,

Rike masa hannu tayi tabude idonta,

"Keda kike yin barci ya akayi kikasan abinda ke faruwa?"

"Dan Allah nidai ka kashe hasken nan"

Murmushi yayi ya kalleta,

"Bakya son inganki ahaske? Nikuma da nafi son inkare miki kallo sosai"


Jan bargo tayi ta rufe har kanta, sauka yayi daga kan gadon yaje yakashe hasken yadawo amma abin mamaki koda yahau kan gadon ji yayi babu ita babu alamunta nan yafara shashime amma bai jitaba,

"Hafsa, hafsa, dama wayo zakimin kenan.."

Jin bata amsaba yasashi sauka daga kan gadon yafara bin bangon dakin yana lalubenta domin bai zo da wayarshiba,

Shiru bai jitaba sai can yajiyo kamar motsinta awurin gaban mirror, ahankali yataka yaje wurin, hannayenshi ya mika da niyyar damkota amma sai aka samu akasi suka sauka akan abunda yaketa zumudin samu yanzu,

"Wai wai yaya yusleem..." Tace dashi tana rike hannunshi,

Rikota yayi ya dagata yadorata akan kafadarshi ya lulubi gado ya hau har lokacin tana kan kafadarshi,

"Allah ne yaga zuciyata shiyasa yabani cikin sauki.." Yace da ita yana kokarin kawar da sleeping gown dinta,

"Dan Allah kayi bacci kaga daga tafiya kadawo..."

Murmushi yayi mai sauti wanda har sai da ita kanta taji,

Bata kara jin muryarshi ba har tsawon wani lokaci,

Duk da cewar bacci yacika mata ido amma haka tahakura,

A tsakiyar kirjinta ya kwantar da kanshi ahaka bacci ya daukesu,

Dakyar ta iya tashi da asuba saboda tsabar bacci, komawa tayi ta kwanta bayan ta idar da salla,tana kwanciya yazo ya matseta ya kwanta abayanta.


K'arfe 10 tatashi, wanka tayi ta shirya tasa atamfa blue ta fita, iya mami ce kadai a falon tana duba jaridar daily trust, durkusawa tayi tagaida mami sannan tahau kan dining tahada tea tasha,

"Yafada miki yafita ko?" Mami ta tambayeta,

"A'a mami ai sai yanzu natashi"

"Hakane kuma, can yatafi gidan alh musa mori zasu karasa wannan yawon ganin kadarorin nasu wanda suka fara rannan"

"To Allah yadawo dashi lafiya"

"Amin amin".

Koda yusleem yafarka daga barci bathroom yashiga yayi wanka yafito, ganin hafsat bata tashiba yasashi fita zuwa part dinsu Abdul, acan yashirya cikin farar shadda kal da ita yasa agogon azurfa yafito bayan yashafe jikinsa da turare, sauri sauri yashiga part din mami yasha tea domin alh musa nacan yana jiranshi, wurin hafsa yakoma har lokacin bacci take gagarumi bata da ranar tashi, yan yatsun kafarta yaja, ganin ko motsi batayi ba yasashi yiwa dan madaidaicin bakinta kiss da wuyanta,shi baisan dalilin da yasa baya iya dauke idonshi daga jikinta ba musamman ma kirjinta idan yazuba mata ido shagala yake, saida yakai hannunshi wurin sannan ya iya kwantar da kwalamarshi yafita,

Yana fitowa daga dakin itama mami nafitowa daga nata,

Keyarshi yadan fara sosawa sannan ya durkusa yagaida mami, sallama yayi mata yakarbi key din motarta yafita,

Lokacin da yaje gidan alh musa dake unguwar millionaires estate aharabar gidan ya ajiye motarshi wadda tafito a matsayin bare acikin sauran motocin dake farfajiyar gidan domin duk sunfi tashi aji da matsayi,

Wata zukekiyar budurwace tafito sanye da wata hadaddiyar bakar gown, hannunta rikeda hand bag da key din mota tasha takalmi mai mutukar tsini tasa bakin face afuskarta, ashekaru zata kai 30 sai kamshinta ne ke kai kawo acikin iskar dake kadawa a compound din gidan, hango yusleem tayi yana fitowa lokacin da take kokarin bude motarta sabuwa dal,

Fasa shiga cikin motar tayi ta tsaya tana karewa yusleem kallo domin ko acikin finafinan India tasan ba kasafai aka fiya samun handsome, classic guy kamarshi ba.....



*_Ummi Shatu_*👌🏻


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login