Showing 24001 words to 27000 words out of 34512 words

Chapter 9 - Rana Daya Book 2 Hausa Novel Complete

19 Nov 2024

216

Ya ce, “Bari in kira Auwal ya kai ma Inna ku gaisa, shi kenan?”
Ta ce, “Allah Sarki, ka ce min zan je.” Ya ce”Ban ce haka ba fa, na ce ne in na dawo zamu yi maganar. Ta ce, “To yaushe za ni?” Cikin shagwaba take yin maganar. Ya ce “Sai kin yi kiba tukuna.” Ta ce, “Don Allah Yaya ina son ganin Yaya Hadiza ma.” Ya ce, “To ki bari sai kin kara kyau.
Ta ce, “Ya za ka gane na kara kyau?” Ya ce, “Ai ina kallonki kullum.” Ta ce, “Me na kara?” Yace “Haske kadai ki ka kara, sai fatar ki da ta soma murjewa, Ta tashi ta dauko dari biyun ta ce, “Gashi canjin ka na tuwon.” Ya ce “Har da canji?” Ta ce, “Eh.” Ya ce, “To ki aje min.” Ta ce, “To.” Ta tashi taje ta aje.
Baccin Amna ya soma damun Shatima, domin yau da ya ke dakinta ma baccin take kwasa babu alamun zasu yi wata hira, shi kuma yana da bukatarta.
Yayi ta tashinta da kyar ta tashi zaune tana zuga hamma. Ya ce, “Amna!” Ta dube shi idanu lumshe, ta ce “Umm, don Allah Honey bacci nake ji.” Ya ce, “Amna, ki tashi don Allah.”
Ta kara cewa “Please, ka bar ni mana.” Ya ce, “Allah sai kin tashi.” Ya girgizata. Ta tashi, “Honey kaina ciwo yake yi, in ban yi bacci ba.” Ya ce, “To kin ci abinci?” Ta ce, “Bana jin yunwa, sai bacci.”
Ya ce, “Kai ki tashi muje asibiti.” Ta ce, “Ni
lafiyata lau, bacci ne kawai matsalata.” Ya bar ta
yazo ya gama duk abin da zai yi kafin ya kwanta.
Sannan yaje ya jata jikinshi ya kwantar suka ci
gaba da bacci.
Da kyar yasa ta tayi sallar Asubahi, don haka ya soma tunanin lallai babu lafiya. Ya kira Aliya a waya da safen yana tambayarta me yake saka mace yawan bacci? Aliya ta ce, “Dalilai da dama, ciki har da shigar ciki.”
Ta ce “Wacece?” Ya ce, “Amna ce, yanzun ya za ayi a gane?” Ta ce, “Gwajin fitsari, tayi a wani abu ka kawo in gwada.”
Da yake ranar Asabar ce ba shi da aiki, bai ko fito gaida saura ba, yana dakin ya sata gaba yana kallo “An ce tana da ciki.” Sha daya ta farka da yunwa, ya ce tayi wanka taji karfin jikinta. Ya ce”Me za ta ci?” Kafin ta fito yasa me aikin ta tanadar mata. tana ci zuba mata ido yayi. Ta ce, “In za ka ci muci mana.” Ya ce, “A’a ki ba babyna ya koshi.” Ta saki dariyar da ta sa ta ta kusan kwarewa.
Ta cc, “In ji wa?” Ya ce, “In ji masu ilimin abin. Yanzun ma fitsari za ki bani in kai a gwada. Ta ce, “Wa zai gwada?” Ya ce, “Aliya kin san Nurse ce. Ta ce, “Wace ce Aliya kuma?” Ya ce, “Ta dakin farko.”
Ta tabe baki “Oh, dama a nan gidan take? Ya ce, “Eh.” Ta ce, “Cikin matanka?” Ya ce, “Eh.” Ta girgiza kai “Ba wadda zan ba fitsarina, don ni ba tsararsu ba ce. Kuma bana dauke da wani ciki domin lokacin al’adata bai yi ba bare in tabbatar. Abin da na sani bacci lafiya ce, ina rama baccin da ban yi ba ne a baya lokacin ina Makaranta, da kuma lokacin biki.”
Yayi murmushi, “Shi kenan muje asibiti.” Ta ce, “Wane irin asibiti, ba zan je ba.” Ya ce “Shi ke nan.
Aliya tayi ta damuwa tana son jin me ake ciki da batun cikin Amna, ga na Nafisa. Koda ta kira Shatima cewa taji shiru bai kawo fitsari ba. Ya ce, “Ashe babu komai ta bar shi kawai.”
Suna cikin hira ta gama cin abinci, sai taji zuciyarta na tashi. Ta ce, “Honey zuciya tana tashi, naci abinci da yawa.” Ya ce, “To kin taba jin haka?”
Ta ce, “A’a sai a ‘yan kwanakin nan. Abin kamar wasa Amna ta shiga bandakinta tana sheka amai. Nan fa Shatima ya ce sai sun je asibiti. Ita kuma ta dage ai taji daidai da ta yi amai din.
Yayi ta lallashinta amma ta ki. Ya kira Hajiayrshi ya kai mata kara. Nan take ta kira layin Amna, cikin sigar lallashi ta ce, “Amna ta yarda taje a dubata.” Ta ce, “To Hajiya.” Ta dube shi, “Ka ci albarkacin Hajiya.”
Sai da suka yi sallar Azahar sannan suka shirya zuwa asibiti, doguwar riga ta saka da dan mayafinta, shi kuma yasha kananan kaya. Sun yi kyau abin su sosai
A kan idon Nafisa da Aliya suka wuce. Kowaccansu da abin da ta kisima a zuciyarta. Cikin gari suka shiga, in da ya kaita wani asibitin kudi gwajin nan take kala biyu suka yi mata.
Cikin sati uku da kwanaki ya bayyana. A gaban Likitan Shatima ya rungume Amna. A nan ya kira Hajiyarshi ya fesa mata. suna hanyar dawowa a mota Hajiyar ta kira shi.
Ta nuna matukar murnarta da samun cikin, kuma ta ba ta shawarwari matsayinta na uwa. Amnar tayi godiya, suka yi sallama. Har suka kai gida Shatima na yiwa Amna sannu da zaran sun hada ido.
Da ya tsaya da mota kuma bayan sun kawo gida, cikin shagwaɓa ta ce sai dai ya dauke ta. Ya ce, “In kullum ki ke son in dauke ki wannan abu ne mai sauki.” Kafin ta ce da wasa take yi har ta ji ta caraf a hannunshi ya yi sama da ita, yasa kafa ya rufe motar.
Bai dire ta ko’ina ba sai a kan gadonta. Ya kira Aliya a waya ya fesa mata. Tayi murna sosai a wayar amma a can kasan zuciyarta takaici ne da damuwa.
Ranar yana dakin har bayan Isha’i, sai da suka yi sallah yaga ta dan ci wani abu sannan ya
lallabata tayi bacci, sannan ya fita bayan ya fada ma mai aikinta cewa ta kula da ita saboda dare.
Dakin Nafisa ya nufa dama can yake, in san
ranshi ne yaje ya duba Salma don bata da wayar da
zai ji laifiyarta, amma baya son mitar Nafisa. Lokacin da ya shiga gurinta ba ta falo, dakin shi ya shige don ya yi wanka, bai neme ta ba ne don yasan yanda suka rabu.
Haka ko ya shigo dubata a ranakun da ba ya dakinta gaisuwa ke hada su. To bai san irin tarbar da zata yi masa ba yau. Ya fito daure da Tawul ya ganta cikin kwalliya ta aje masa goran ruwa da kofi a gefen gado kamar yanda aka saba.
Ya kalle ta cikin murmushi, a ransa ya ce, “Yau da akwai abin arziki.” Ta miko masa kayan baccinsa yasa, ya dube ta. “Turarenki yayi min kamshi sosai.” Ta fadada fara’arta. “Haba?” Ya ce, “Sosai ma, za ki sammin?”
Ta ce, “A’a, za dai ka dinga shakar sa a jikina.” Yayi ‘yar dariya. “Hakan ma na gode.” Ta ce, “Muje ka ci abinci ko? Kus-kus ne nayi maka da fa-dukan shi, yayi dadi.” Ya ce, “Lallai kuwa kin ce yau in ci har in kasa tashi.” Suka yi dariya gaba daya.
[8/18, 17:54] Ummi Tandama😇: _____
*🏚️RANA DAYA BOOK 2🏚️*


CHAPTER 12



*BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*


*Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*

```ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925```

*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 Ga masu son Audio na littafin RANA DAYA shima muna dashi cmplt ku turo kudin ku ta account number din da muka bada can sama👆🏻👆🏻ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana*

*Masu son tallata masu hajar su suyi magana ta wannan number 09068032427 zamuyi maku cikin sauki*


Mun tsaya

Haka ko ya shigo dubata a ranakun da ba ya dakinta gaisuwa ke hada su. To bai san irin tarbar da zata yi masa ba yau. Ya fito daure da Tawul ya ganta cikin kwalliya ta aje masa goran ruwa da kofi a gefen gado kamar yanda aka saba.
Ya kalle ta cikin murmushi, a ransa ya ce, “Yau da akwai abin arziki.” Ta miko masa kayan baccinsa yasa, ya dube ta. “Turarenki yayi min kamshi sosai.” Ta fadada fara’arta. “Haba?” Ya ce, “Sosai ma, za ki sammin?”
Ta ce, “A’a, za dai ka dinga shakar sa a jikina.” Yayi ‘yar dariya. “Hakan ma na gode.” Ta ce, “Muje ka ci abinci ko? Kus-kus ne nayi maka da fa-dukan shi, yayi dadi.” Ya ce, “Lallai kuwa kin ce yau in ci har in kasa tashi.” Suka yi dariya gaba daya.


Bayan ya gama da abincin kuma ya jinjina mata. Nafisa ta sha mamaki a kwanciyarsu, yanda ya tara da ita sau biyu a daran. Sannan da safe da yake Lahadi ce yana makale da ita sai gurin tara sannan ya tashi ya yi wanka.
Tayi ta tabara wai ya gaji da ita ba za ta iya tashi ta shiga kicin ba. Ya ce “Zauna in shigar miki.” Shi ne ya hada musu abin kari, tayi wanka, tayi kwalliya suka karya. Ya ce, “To bari ya je ya duba lafiyar sauran Jama’ar gidan.
Nan ne ta ɓata rai, wai haka jiya ai ita bai zo ya duba ta ba, kuma ta fito taga ya dauki Amna. Nan take ya dauke ta da yake Nafisa irin matan nan ne marasa kiba, sai dai tana da dan tsawo. Amma sanfurin jikinta, sanfuri ne irin wanda zai yi wuya tayi kiba ko me zata ci.


Ya ce, “To dauka dai gashi na dauke ki ina zan kai ki? Ranta yayi dadi ta ce, “Ka kai ni dakina.” Ya dire ta kan gado, a kunne ya rada mata wata magana da ta sata fashewa da dariya, tare da saka kanta cikin filo. Yayi mata cakulkuli ya fita ya barta tana dariya.
Sha biyu ya gani lokacın da ya kalli agogon falon Amina. Lallai yau hira tayi dadi tsakanin shi da Nafisa. Ya samu Amna zaune tsakiyar gado
tana waya da ‘yan gidansu. A yanayin maganarta ya gane cewa ‘yan gidansu sun sani, ta fada musu kenan.
Ya zauna suyi da wannan, wannan ya kira. Bayan ta gama ta dubi Shatima, “Su Mom suna gaida ka.” Ya ce, “Ina amsawa. Ya jikinki?” Ta ce, “Naji sauki.” Ya ce, “To kin yi karin kumallo?” Ta ce, “Eh, su fa suka tashe ni da kiran waya. Yanzu kam dole in tashi in yi wanka in karya don Direba yana hanya zai zo mu tafi.”
Cikin mamaki ya ce, “Ina?” Ta ce, “Gida mana! Dad zai sa a duba ni na musamman. Shatima ya ce, “Ba ki fada musu cewa an duba ki a nan ba?” Ta ce, “Na fada musu, ka san Dad baya son wasa da lafiya.” Ta fadi tare da sauka ta nufi bayi.
Shatima yayi shiru kanshi a daure, lallai wata
sabuwar matsala kuma zata kunno kai a gidan shi.
Shi ne mijinta shi ya kamata a nemi izininsa kafin a fada mata, shi ne ya kamata ya fada mata cewa Dad ya ce za ki je Kano a sake duba lafiyarki, amma sai gashi ita ce take bashi labari, babu wani neman izini. Jiki babu karfi, ya shige zuwa gurin Aliya. Yanayin da ta ganshi taso taji ko menene, amma ta

san ba zai fada ba. Haka Salma duk shirmenta sai da ta lura cewa yau din yana cikin damuwa.
Domin taga be tsokane ta ba. Ya dai miko mata kudin nama. Ta ce, “Me zata dafa?” Ya ce, “Tayi abinda take so. Gaba daya sai ya ji gidan yayi masa kunci. Dakin Nafisa ya nufa ya dauki makullin mota ya fita.
Shi kanshi bai san ina ya dosa ba don yana bukatar shawara. Titin da zai kai ka filin bajakoli nan yasha kwana ya tsaya, saboda akwai karancin zirga-zirga a titin. Ya kifa kanshi a kan sitiyarin motar.
Kamar minti daya ya dago, ya dauki waya ya shiga kiran layin Munnir. Babu jimawa Munnir ya daga, tun daga gaisuwa Munnir ya fahimci akwai matsala. Ya ce, “Ya ya abokina, naji muryarka wata
kala?” Ya ce, “Akwai matsala.” Ya karanto mishi
komai. Munnir ya ce, “Tabdi! To ai tun da wuri
zaka yi maganin wannan matsalar ba sai ka bari
tayi girman da zaka kasa magance ta ba.”
Shatima ya ce. “Ta ya ya? Ni bana son ne a ce daga aure dududu ko wata biyu ba mu cike ba amma na soma kuno da matsala.”
Munnir ya ce, “Kai da ka ke da basira ma, kayi kokari sosai fa, da harka tara mata guda hudu zuwa yanzun babu wata matsala ko wani korafi.
Mace daya ma in ka aje in ba a yi sa’a ba kafin kuyi wata daya makota sun soma jin ku.” Shatima ya ce, “Ai kaina ya kulle, basirar tawa duk ta toshe, ka riga ni aure dai, ka san kuma yanda kowane Maigida yake takama da ikon gidansa.”
Munnir ya ce, “Haka ne.” Shatima ya ce, “To sai a ce an tauye maka wannan ikon.” Munnir ya ce, “Abin da yafi kawai ka cije ka hana, ka ce ba ka bada izini ba, nasan dai za a dan samu fushi da sauransu kayi lallashi daga baya. In ko ba haka kayi ba, tabbaci hakika matsalar ta samu gindin zama.
Shatima ya ce, “Haka ne, bari in koma gidan kawai da na fito ne nayi fushi a kan in sun tafi suma wuce Kano don ni.” Munnir yayi dariya. “Ai ka tsaya a namijinka nawa.”
Shatima ya ce, “Har ina son in kira Hajiya itama in ji ta bakinta.” Munnir ya ce, “Kar ka sake kayi wannan kuskuren, domin zaka yi da na sani a gaba. Bari in fada maka wata magana abokina, duk rintsi kar ka sake ka sako iyayenka a cikin abin da ya shafi matsalar gidanka.
Na farko zaka jona raini tsakanin Mahaifiyarka
da matarka, domin ka san suma iyayenmu sai a hankali, basa so a ce kaza laifinmu ne, don haka sai kaga sun dora mu kan shawarar da mu zamu fitamma zamu cutar da iyalanmu.
kuma kayi rashin sa’a a goyi bayan matar kai kuma kiri-kiri ka dinga cutuwa. Don haka kar ka sake ka zama mai kai matsalar cikin gidanka ga Mabaifiyarka, shi ke haddasa irin rikicin nan na tsakanin sirika da sarakuwa, wanda har yanzun an kasa cimna nasarar kawo karshen wannan lamarin shekaru masu yawa.
Kawei abokina ka zama wanda kullum iyalansa suke ganin girman darajar iyayensa. Su kuma iyayenka kullum kana fada musu labari mai kyau, mai faranta rai daga iyalansa.
Kai ko wata ce cikinsu ta kai kararka gurin Mahaifiyarka, in kaje kar ka ce ita ce ta min kaza da kaza, ka ce ayi hakuri zaka gyara.”
Shatima ya ce, “Amma dai na gode da wannan shawara, in Allah Ya yarda zan kiyaye. Shi yasa a ka ce me shawara aikin sa baya baci, sai dai asirinsa ne a tone.” Suka sa dariya, sannan suka yi bankwana kowa ya kashe waya.
Ya aje mota ya nufi dakin Amna. Tana zaune a kan Dining tana cin kwai da Tea. Ya kalleta, “Sai yanzun ki ke karyawa?”
Gira ta daga masa alamun “Eh.” Ya ce “Me yasa? Ki daina wasa da abinci ba fa ke daya ba ce yanzu.” Ta ce, “Na gama hada abin da ni ke bukata ne, kar ya zo ya yi tajirana, ban dauki kayan sawa ko daya ba, don ina da kaya a gida a dakina. Ko lefena ma yana can…” Ya katse ta da cewa, “Ina wai za ki je ne kina ta fadin kar ya zo ya yi ta jiranki.”
Ta cc, “Sau nawa zan fada maka cewa Dad ya ce a zo a tafi da ni.” Ya ce, “Amma Dad din bai fada min ba. Ya za ayi ki tafi ba tare da neman izinina ba
Cikin mamaki ta kalle shi ya wani hade rai. Ta ce, “Dad dina fa na ce, ko ba ka ji da kyau ba ne?” Ya ce, “Naji ki sosai, amma tafiyarki kiran Dad din naki ikona ne ba ikonsa ba, don haka bisa ikona babu in da za ki je, ki kira shi direban a waya ki ce masa ya juya.”
Ta mike a fusace, “Shatima kana son ka ce min za ka hada kanka da Dad dina? Shi ne fa ya haife ni ya raine ni, ya sani Makarantu mafi tsada a in da muke, har waje ya kai ni a can ka ganni ka ce,
kana sona. To don Allah ka dawo cikin hankalinka bana son mu samu matsala, don… ihun murna da Summy ta shigo da shi, shi neya katse Amna daga zafafan maganganun da ta
tanada don fesar ma mijin nata. Ta rungume
kanwar tata, tare da nuna murnar ganinta. Sumayya ta kai hannu ta shafi cikin Amna tare da fadin “Na riga Dad taba Baby.” Amna ta saki dariya tare da tambayar ko sun yi muhawara ne? Sumayya ta ce “Ai ba su san na biyo dircba ba, domin Dad yacd babu wanda zai fara shafa Baby.”saishi
Amna cikin dariya ta kalli Shatima, wanda ya harde hannu yana kallonsu. Ta ce, “Honey dubi son kudi irin na Summy. Bai ce komai ba, Sumayya ta dan risina “Ina yini Ya Shatima, ban ganka ba fa.” Ya ce, “Ai ba za ki ganni ba, idonki ya rufe.” Suka yi ciki suka bar shi nan tsaye.malala
Kafın yayi wani tunani har sun fito, me aikinta dauke da dan karamin akwatinta. Sumayya da me aikin suka yi gaba, bayan ta ce “Yaya har da kai zamu?” Ya ce “A ‘a ina da office Summy.” Ta ce, “Yau Sunday.” Ya ce, “Gobe ni ke nufi
nima.” Amna ta kalle shi, “Honey sai mun yi
waya.” Ya ce, “Za ki tafi ba da izinina ba? Za ki tafi cikin fushin Allah da tsinuwar Mala’iku?”
Amna ta ce, “Ni ban gane zantukanka ba, in ka gama fushin zamu yi waya.” Ta fice abinta. Bai fito ba har sai da ya daina jin sautin motarsu. Ya fito ya kulle dakin ya nufi dakin Nafisa.
Kan kujera yaje ya zauna ya zabga tagumi. Nafisa ta zo ta zauna kusa da shi, ta dafa shi. “Lafiya kuwa?” Shatima ya ce, “Kanshi ke ciwo.” Ta ce, “Gashi babu magani a gidan ko za’a aiki direba ne ya siyo?” Ya girgiza kai tare da lumshe
ido. “Gajiya ce da kai-kawo, in ya dan huta zai daina.” Ta rage TV

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login