Showing 51001 words to 54000 words out of 64985 words
Chapter 18 - Abban Sojojin Bokk 3 Hausa Novel Complete
abun yaso ya bashi dariya,lallai Ammi ta kimtsu tunda har ta fara jin kunyar jikokinta su ganta tana zuqar sigari,
A saman carpet,kowannansu ya zauna tare da lankwashe ƙafa,Abusufyan ne ya fara gaisar da ita"Ina kwana Ammi,kun tashi lafiya?Ya gajiyar tafiya"?
"Lafiya lou Alhamdulillah,"ta amsa mashi,Sannan su Jahad suka haɗa baki wurin miƙa gaisuwarsu,da murmushi a fuskarta ta shiga amsa masu ɗaya bayan ɗaya,a ƙarshe ta tsayar da idanunta kan Hosana tace"Kin tashi lafiya"?
Murmushi hosana ta saki tana faman noƙe kai tace"lafiya lou,"
Janye idonta tayi daga kan hosana ta mayar dashi kan junaid tace"Sarkin Murmushi,Angona nakaina naga kayi kyau sosai ka kuma ƙara haske,faɗamun menene sirrin"?
"Kishiya zanyi maki ne"yayi maganar yana murmura mata ido,ɗan waro ido waje tayi tare da cewa"Wacece ita"?
ɗagowa yayi yana kallonsu,Sehrish har sai da ya gano jahad sannan ya nuna ta da hannu yace"Gatanan,"
Ammi tace"Kin shirya yin kishi dani ko"?
Girgiza kai jahad ta shiga yi alamar a'a,
"To kaji bazata iya kishi dani ba,sai ka haƙura da auren gaba ɗaya,don ni bazan zauna da kishiya ba,"
"A'a wlh Ammi sai dai ki haƙura dani in aurota,"
Yadda yayi maganar ba ƙaramin dariya ya basu ba,don har saida suka dara,
Ammi tace"wato Ni zaka juya ma baya ko?saboda ka samu zankaɗeɗiyar budurwa sabuwa gal cikin leda,Ni kuma nayi maka tsufa,"gyaɗa kai tayi tare da cewa"bakomai na haƙura,"
Murmushi suka saki gaba ɗayansu,mayar da idonta tayi kan Abusufyan"Yanzu ya ake ciki game da zancen Mahaifiyar yaran nan"?
Jin an sako zancen abu yasa shi gyara zama,sannan yace"Muna nan muna shirya waɗanda zasu je kano domin binciko gidan da suka zauna acikinsa,saboda muna sa ran zamu samu wasu muhimman bayanai a wurin makwabtansu,"
Jinjina kai Ammi tayi"hakan yayi kyau,banason a tsaya 6ata lokaci nafi son ayi komai tun da wuri don ba'a san halin da take ciki ba,"
"In sha Allah zamuyi hakan,daga nan suka miƙe tare da yi mata sallama suka wuce ɗakin Modibbo,ba ƙaramin daɗi yaji ba daya gansu,sun jima a wurinshi,kafin daga bisani suka wuce ɗakin gwaggon katsina,sun sha barkwanci a wurinta,daƙyar suka samu tabarsu suka fito,ɗakin hajiya azeema suka wuce,sun jima a wurinta suna shan fira,ɗaya bayan ɗaya haka suka dinga bin ɗakunansu kafin daga bisani,Lokacin yin breakfast yayi suka hallara gaba ɗayansu a dining,kowa saida yazo banda Sgr,saboda yasa ma ranshi cewar za'a kawo mashi ne har part ɗinsa,Azmee ce takai mashi,saboda Sehrish ta sanar da ita cewar,bazata samu damar kai mashi ba,tana so tabi Umarnin mahaifinta ne,
Lokacin da Azmee ta shiga part ɗinsa,yana daga kishingiɗe saman Sofa mai mazaunin mutun ukku,jikinshi na sanye da jallabiya,shigowa ciki tayi gabanta na faɗuwa don tasan cewa dole ya tuhumeta akan me ya hana sehrish zuwa,lalla6awa tayi ta ajiye masa tray ɗin a asaman table,gudun karya tuhumeta yasa tayi saurin ja da baya zata gudu tabar ɗakin,har takai baƙin ƙopar ɗakin tajiyo muryarshi yana fadin"ke zo nan,"dakatawa tayi da tafiyar hannunta dafe da saitin zuciyarta,jiki asanyaye ta dawo ta tsaya agabanshi,kwata kwata idanunshi na a lumshe,wayarshi na ajiye asaman wide chest ɗinsa,
dakyar ta iya cewa gani yalla6ai,
"Bana ce kar na sake ganinki a part ɗina ba da sunan aiki?ko bata faɗa maki bane"?
Shiru azmee tayi,tana faman zazzare ido,ranta ne ya bata cewar kawai ta sanar dashi gaskiyar zance,
Don haka tace"Sehrish ta sanar dani cewar bazata ƙara aiki a part ɗin ka ba...."tunkan ta ƙarasa maganar ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu,nan take azmee tasha jinin jikinta,
"Ita da bakin ta,ta faɗi hakan"?
Muryarta na kerma tace"Eh,
Ya kuma cewa"ta faɗa maki dalilin yin hakan"?
"Eh,tace tana son bin Umarnin mahaifinta ne,"
ɗan ciza gefen la66ansa yayi tare da cewa"its Okey,just leave........" da sauri azmee ta juya tare da kama hanya ta fuce daga part ɗin nasa,
Wuraren ƙarfe goma sha biyu modibbo ya shirya tafiya,Kanal yousouf ne tare dasu Irfan suka kai shi har Airpot ya hau jirgi,
Yinin Ranar Aunty babba na ƙumshe a cikin ɗakin Hayaam,tsoro ya hanata fitowa waje,da yunwa ta addabe ta Hayaam ce ta ɗebo mata abinci ta kawo mata a ɗakin,hosana kuwa kar take dasu,don taci alwashin sai ta tona masu asiri wurin daddynsu,da kuma Ya omar,
Hankalin sehrish ba ƙaramin kwanciya yayi ba,jin Cewa sgr bai nemeta ba,duk da ta damu akan son ganinshi,jurewa kawai takeyi,
A ranar Talal Da captain najeeb suka ƙaraso,murna a wurin ƴan uwansu kamar zasu haɗiye su don farin ciki,musamman junaid daya kasance rival ɗinsa ne ya dawo wato Talal,da yake shima autane a ɗakinsu Omar,
After 1 day
*Boss Bature*
Around 2:00 pm,
Zaune take a hakimce saman 2 seater,jikinta na sanye da turkish dress Riga da wando,a launin fata fara ce amma hasken nata hada na bleaching tayi 6au sosai,babbar mace ce a ƙalla zata kai shekara 35,gaba ɗaya idanunta na akan plasma tv din da take kallo aciki,yayin da hannunta ke ɗauke da cup na coffee,lokaci bayan lokaci take kur6asa,ta aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,wuyan kafarta na sanye da ziririyar sarƙa,sai faman karkaɗa kafar takeyi,Tana da manyan idanu dara dara,ga dogon hanci wanda ke manne da nose ring,kai kana ganinta zaka san cewar cikakkiyar ƴar bariki ce,
Jin ringing din wayarta dake ajiye asaman hannun kujerar da take ne yasa ta Ajiye cup din hannunta asaman madaidaicin table din dake a kusa da ita,sannan tasa hannu ta dauki wayar,hidden number ce aka kirata da ita,picking call ɗin tayi ta kanga wayar a kunnanta,cikin harshen fulatanci take magana,
Tana cikin yin wayar taga inuwar mutun tsaye akanta,ɗagowa tayi a hankali don taga wanene,sauke ajiyar zuciya tayi ganin Amrish ce,jikinta na sanye da uniform,ta goya school bag dinta a abayanta,dawowarta kenan daga school,fuskarta a ɗaure kwata kwata babu annuri acikinta,
Rejecting call ɗin tayi tare da ajiye wayar asaman sofa din,sannan ta mayar da hankalinta sosai akan Amrish,
"Welcome back my daughter,Am really glad to see u,"
Tayi maganar tana buɗe mata hannunwanta don tazo ta rungume ta,rai a6ace tace"Mommy na tsani ganinki wlh,banason ki,saboda baki da halin kirki,so kike ki kashe mun rayuwata da hannunki,"tana maganar hawaye na gangarowa akan fuskarta,
Maimakon ta nuna damuwarta akan hakan sai ma ɗan ta6e la66anta tare da cewa"Kamar yadda baki so na,Nima haka bana son ki,donni a tsarin rayuwata ban shirya haihuwa ba saboda bana son ƴa'ƴa don su takura ne,na samu cikinki batare dana shirya ba,babu yadda banyi ba don na zubar da cikin,amma ya liƙe ya nace sai ya zauna a mahaifata,a ƙarshe nayi deciding zuwa ƙasar waje a markaɗe mun shi,mahaifinki ya hana hakan,nayi takaici a wannan lokacin kamar nayi suicide,"
Hankalin Amrish ba ƙaramin tashi yayi ba,jin abunda mahaifiyarta ke faɗi da bakinta,tuni wasu zafafan hawaye suka shiga wankowa a saman fuskarta,cikin shessheƙar kuka tace"ki faɗamun!Su wanene iyaye na!don ina da tabbacin cewar bake kika haife ni ba,"
Fashewa da dariya matar tayi yayin da take karkaɗa kafafunta,
Jin tayi banza da ita yasa ta daka mata tsawa tare da cewa"Mommy ki faɗamun su wanene iyaye na?In ba haka ba zan je na kashe kaina!"
Yunkurawa mommyn tayi tare da mikewa tsaye ta daddage ta kifa ma Amrish mari tare da cewa"Sai me idan kin kashe kanki!?wa kikayi ma asara!shashasha kawai,"
Fashewa da kuka Amrish tayi yayin da zuciyarta ke tafarfasa tace"Mommy yau ke da kanki kika mare ni"?
Dogon tsoki taja tare da cewa"Har kashe ki ma zan iyayi,Saboda kinyi mun tsawa,ko iyayena da suka haife ni basu ta6a gigin daka mun tsawa ba,balle ke ƴar dana haifa,idiot"
Ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta ɗauki wayarta,sannan tabar falon tana fadin"kafin gobe in samu gawarki dan Allah,"tayi maganar cikin halin ko in kula,
Da gudu Amrish ta watsa,izuwa bedroom dinta dake a upstairs,datse ƙopar ɗakin tayi,bayan tayi wurgi da school bag dinta,ta shiga neman igiyar da zata shaƙe kanta don ta mutu,ganin bata samu ba yasa ta buɗe kopar ɗakin,ta fita,bada jimawa ba sai gata ta dawo cikin ɗakin hannunta dauke da insect powder,buɗe murfin tayi da sauri sauri ta daga robar tare da zazzagawa acikin bakinta,
Mommyn na acikin bedroom ɗinta,ta jiyo wata irin razananniyar ƙara mai rikitarwa,sakin wayar dake hannunta tayi,da gudun gaske ta fito daga bedroom ɗinta dake a downstairs,tamkar za tayi tuntu6e ta fadi kasa haka take gudun,lokacin da ta ƙarasa bedroom din Amrish,hannu tasa ta dinga bubbuga ƙopar tana faɗin"AMRISH!AMRISH!!baki da hankali ne,bakisan wasa ba,me kika aikatawa kanki!ba zaki zo ki buɗe mun ƙopa ba!!Amrish gaba daya duk tabi ta rikice,
Shiru amrish bata buɗe mata ƙopar ba,hakan yasa ta dawowa wurin window ɗin ɗakin ta buɗe ta don ta gane ma idonta,
A gigice ta fasa uwar ƙara tare da aza hannyenta asaman kanta tana fadin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!na shiga uku!!!!zubewa tayi ƙasa saman guiwowinta tana faman zabga kuka,hawaye jaga jaga a fuskarta,tana cikin wannan yanayin,taji shigowarsu Zeenat da sofia ƙawayen Amrish cikin falon gidan,mikewa tayi da sauri har tana tuntu6e ta saukko downstairs,tunkararsu tayi tana fadin"Nashiga uku!!Amrish ta kashe kanta!!bansan ya zanyi da rayuwata ba!!
Kallon juna sukayi hankalinsu a matukar tashe suka haɗa baki wurin cewa"Am...Amrish!!meya faru da ita!taya akai ta kashe kanta!!!
Kasa bude baki tayi don tayi masu magana,da hannu ta dinga nuna masu bedroom ɗinta,nan suka gane cewar tana acikin ɗakinta,da gudu suka nufi upstairs ɗin,itama tabi bayansu,nan fa suka shiga ƙoƙarin 6alle ƙopar ɗakin nata,
💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*
*Father of soldiers*
*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*
Wuraren ƙarfe shida na marece,ta fito daga cikin toilet,jikinta na sanye da towel fari ta ɗaure shi a saman ƙirjinta,da alama wanka tayi aciki,jahad ta samu zaune saman gadonsu,hannunta ɗauke da wayarta tana ɗan daddanawa,tsayawa tayi a ƙopar toilet ɗin ta ruqe ƙugunta tare da ɗan ɗaure fuskarta tace"Jahad!bana hanaki ɗaukarmin waya ba?kin manta abunda ya faru ran nan?kika kusa kashe mun waya gaba ɗaya!,yanzu da ace ta lalace dashi kenan wa zai siyamun wata"?
Fuskar jahad ɗauke da murmushi tace"Daddy mana!ae yace zai siya mana Phones gaba ɗayanmu,hada ke ma zai canza maki wata,hada ma laptop xai siya mana,"
Washe baki Sehrish tayi tare da cewa"Wai dagaske"?
"Eh,mana,shi da kanshi ya faɗi hakan,Kuma yace next week zamu koma school da kanshi zai mayar damu,don kada wani ya ɗaga mana yatsa,"ta ƙarasa maganar fuskarta dauke da dariya,sehrish kuwa tunda jahad tayi maganar school ba kowa ya faɗo mata aranta ba,face ƙawarta AMRISH,lokaci guda ta faɗo mata acikin ranta,nan take kuma taji gabanta ya faɗi rass,
Ganin fuskarta da alamun damuwa atattare da ita,yasa jahad kiran sunanta"Sehrish,meya faru ne?maimakon inga kina farin ciki?ko baki son komawa school ne?baki gaji da zaman kashe wando ba acikin gida?
Muryarta asanyaye tace"ba haka bane jahad,kawai na tuna da wata school friend ɗita ne,Nayi missing ɗinta sosai,Yarinyar tana sona sosai,itace take ƙarfafa mun guiwa akan in ringa yin karatu,in daina bacci a class,Gaskiya banyi mata adalci ba,sam na manta da ita,ni nasan cewa amrish ta neme ni har ta gaji,"
Jahad tace"Eyya,gaskiya baki kyauta mata ba,gashi sunan ku shigen iri ɗaya ke da ita,ni tun kafin ma in ganta har naji ina sonta,saboda tana son ƴar uwata sosai,Amma meyasa ba zaki jaraba kiranta ba tunda ga waya ko baki da numbarta ne?
"Ina da numbarta,kinsan kwanakin nan hankali na duk ba'a kwance yake ba,tun lokacin da muka daina zuwa school,ban ƙara bi takan wayar ba,sai ma na ganta a hannunki ne sannan nake tunawa da cewar ina da waya,Allah sarki Amrish ɗina,bansan wani hali take ciki ba,gashi bansan gidansu ba,"
Mikewa jahad tayi ta nufi wurin da Sehrish take tsaye,mika mata wayar tayi tare da cewa"Ki jaraba kiranta mana,sai mu gaisa,"
Kar6ar wayar Sehrish tayi,ta shiga cikin contacts ɗinta,ta lalubo numbar amrish,sae dai kash tana kiran layin taji wayar akashe,ɗayan layinta na Airtel ta kira shima akashe yake,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,
"Bansan meyasa ba'a samun layinta ba,amma mu bari da anjima sae mu jaraba kiranta mu gani kilan ta kunna wayar,"tayi maganar tare da miƙa ma jahad wayar ta kar6a,sannan ta koma gefen gadon ta zauna,ita kuma ta wuce gaban wardrobe tana lalubar kayan da zata sanya,
Turo ƙopar ɗakin nasu hosana tayi,da sallama abakinta,juyowa sehrish tayi tana kallonta haka itama jahad,
Nuna Sehrish tayi da yatsanta manuni,kafin tace"RISHI KIZO INJI DADDYN MU YACE KI SAME SHI A ƊAKIN SHI,KADA KI WUCE MINTI BIYAR"
Rasss!taji gabanta ya faɗi,
"Hosana dagaske ni daddy ke kira?kuma ni kaɗai yace inzo"?
"Eh,ke kaɗae yake son gani,"
Cikin sauri ta juya tare da zura hannunta cikin wardrobe ɗin,ta lalubo wasu pakistan riga da wando,rigar fara ce,har guiwa daga ƙasanta kwalliyar duwatsu ne,wandon kuma pink colour ne,bai da kwalliya ajikinsa,irin falazun nan ne burgujeje,mayafin kayan ta yafa Shima pink colour,gaban madubi ta koma ta ɗauki flower bomb ɗinta,ta feshe jikinta dashi,sai da ta fara kallon fuskarta a mirror ta ɗan sakarwa kanta murmushi,sannan ta kama hanyar fita daga ɗakin,
Jahad tace"Allah yasa alkhairi ne!kullum in daddy zai kiramu atare yake kiranmu amma yau ke kaɗae kawai yake son gani,"ta ƙarasa maganar tana nuna bayan sehrish da hannunta,
Murmushi kawai ta saki kafin ta buɗe ƙopar ta fuce,
Da sauri da sauri take tafiya don karta wuce minti biyar ɗin da Hosana tace,tana ƙarasawa baƙin ƙopar ɗakin takai hannu kenan zata buɗe,taga an ja ƙopar daga cikin ɗakin,da alama wani ne zai fito,zubama dogayen yatsun hannunshi ido tayi,farare tass ya ruƙe handle ɗin ƙopar dasu,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga ɗakin,nan take ta gane Cewa BABBAN YAYA NE,mamaki ta shiga yi mai ya kawo babban yaya a ɗakin daddynsu?bayan sa6anin da suka samu a tsakaninsu,ko sun shirya ne,?
Bata ƙarasa zancen zucin nata ba,SGR ya ƙarasa fitowa daga cikin ɗakin Abusufyan,wankan suit ne ajikinshi farare,kyau iya kyau,
Tsayawa yayi cak kamar an dakatar dashi,Sehrish kuwa tuni gabanta ya shiga faɗuwa,tun daga ƙasa har sama yabi ta da kallo,Yarinyar ko ƙafaɗarshi tsayinta bai kai ba,
Daƙyar sehrish ta iya buɗe baki tace mashi"Ina yini"
Tamkar bazai amsa mata ba,don har sai da ya wuceta ya ɗan yi nisa sannan taji yace"Lafiya,"yana faɗin hakan ya ƙara gaba,su babban yaya irin wannan shan ƙamshi haka,
Jiki asanyaye ta shiga cikin ɗakin da sallama abakinta,A zaune ta samu Uncle abusufyan,daga gefen gadonshi,juyowa yayi tare da kallonta fuskar nan tashi ɗauke da murmushi yace"Daughter,"
"Na'am daddy,ta amsa mashi tare da ƙarasawa,ta samu wuri saman sofa ɗin dake fuskantar gadonshi ta zauna,suna facing ɗin juna ita dashi,sannan tace"gani daddy hosana ce ta sanar dani cewa kana nema na,"
"Eh hakane,ni na ce ta kira mun ke,"
Natsuwa tayi tana jiran jin me zaice mata,sae faman wasa takeyi da yatsun hannunta,
"Gobe yaushe"?yayi tambayar yana kallonta,
..fuskarta ɗauke da murmushi tace"Friday," jinjina kanshi yayi tare da cewa"Masha Allah,Juma'a babbar rana,zaifi kyau in aka kafa tarihi aranar juma'a,ina tunanin kamar zai yi wuya a manta dashi,ko ba haka ba daughter?
Dariya sehrish tayi kafin tace"gaskiya ne daddy,juma'a itace babbar rana,duk abunda ya faru a ranar friday,zaiyi wuya a manta dashi,"
Abusufyan yace"Shiyasa nake so gobe na ɗaura maki aure,ko bakya so"?
Da sauri tasa tafukan hannunta tare da rufe fuskarta,tana dariya,
"Na ƙosa na fara ganin ƴan jikoki na," cikin zolaya yayi mata maganar,
"Dan Allah daddy,ka daina faɗin haka wlh kunya nake ji," cikin shagawa6a tayi maganar har lokacin bata zame tafin hannunta daga saman fuskarta ba,
Miƙa hannu Abusufyan yayi tare da janyo drawer chest ɗinsa gida na tsakiya,ya ɗauko wani small box Golden Colour mai shegen kyau,sae faman ƙyalli yake yi yadda kasan da Zallar Zinari akayi shi,
Ruƙo shi yayi a hannunshi yana jujjuya shi,ɗan ɗagowa yayi yana kallon sehrish wadda ta rufe fuskarta,
Gyaran murya yayi mata tare da cewa"Buɗe fuskarki mana," a hankali ta zame hannunta daga kan fuskarta,kai tsaye idanunta suka sauka kan small box ɗin dake hannun Daddynsu,ɗan zaro idanunta tayi tana ƙare mashi kallo,akwatin ya burgeta sosai,jikinshi sae ƙyalli yakeyi mai matuƙar ɗaukar ido,da jan hankali,cike da zumuɗi tace"daddy wannan fa?wlh yayi kyau sosai,ban ta6a ganin irin shi ba,"
Ƴar dariya Abusufyan yayi tare da cewa"koya burge ki ne"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh,
Jujjuya akwatin yayi tare da cewa"Sadakin wata Ne,aka biya da Gold,"
Waro ido waje sehrish tayi cike da mamaki tace"daddy!dagaske ka ke dowry ne aka biya da Gold,but daddy who's she? Dariya abusufyan ya kuma yi ganin yadda tabi ta ruɗe da jin abunda yace,
"Dagaske nake ba wasa ba,sadakin wata Mai sa'a ce,Jinin nasara,"
"Daddy,can i see it pls"?
Miƙa mata small box ɗin yayi hannunta har kerma yake yi wurin kar6arsa,janyewa Abusufyan yayi fuskar nan tashi ɗauke da dariya yace"Da hannun hagu kuma?hannu biyu zaki sa ki kar6a,sannan in zaki kar6a ki tabbatar da kinyi bismillah,don Abun yayi albarka,"
Murmushi sehrish tayi tare da gyara natsuwarta,sannan ta miƙa hannanyenta duka biyun,tayi bismillah kafin ta kar6e shi daga hannun abusufyan,wani irin sanyi ne taji ya ratsata,jujjuya akwatin ta shiga yi tana ƙare mashi kallo,yana da nauyi duk da ƙarantar shi,hakan ya tabbatar mata da cewar,abune mai daraja acikinsa,ƙoƙarin buɗe akwatin ta shiga yi,da sauri Abusufyan ya dakatar da ita"kada ki buɗe shi,ki adana shi a wurinki,bana so kowa ya gani,kuma kada kowa yasan inda kika ajiye shi,"
Abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,
"Amma daddy,sadakin wata ne fa?kuma naji ka ce in ajiye shi a wurina,saboda Me"?
Bai bata amsa ba,sae ma kwantar da bayanshi da yayi saman gadon nashi,ya ɗan kishingiɗa,ya aza kansa saman pillow,yana kallonta,ta zuba mashi ido tana jiran jin amsar da zai bata,
Ƙayataccen murmushi ne ya bayyana akan fuskar Abusufyan,ya jima ahaka suna kallon kallo shi da Ƴar tashi,kafin yace"Zaki samu amsar tambayarki,amma ba yanzu ba,ki bani lokaci zan neme ki,yanzu zaki iya tafiya,"ya ƙarasa maganar yana nuna mata hanyar fita daga ɗakin,
Tamkar wadda aka zarewa lakar jikinta,haka ta miƙe jiki ba kwari,wani irin faɗuwar gaba kawai take ji,daƙyar ta iya ɗaga ƙafarta,tana tafiya tana waiwayen daddyn nasu,daya zuba mata ido yana kallonta,tabbas akwai wani abu da yake 6oye mata,sai da takai bakin ƙopar ɗakin,tana ƙoƙarin buɗe kopar ta fita,taji ya ambaci sunanta
"SEHRISH" da sauri ta juya tana kallonshi,
"Game da abunda ya faru tsakaninki da babban yayanku,Nasan ranshi ya 6aci sosai,ya baki Umarnin kiyi mashi aiki,amma na hanaki a matsayina na mahaifin ki,inaso kije ki bashi haƙuri,'
Waro ido waje sehrish tayi a ɗan tsorace tace"daddy in bashi haƙuri fa ka ce?wlh tsoro nake ji,jiya ranshi ya 6aci sosai,idan na kuskura