Showing 12001 words to 12562 words out of 12562 words
Chapter 5 - Binta Yar Jagaliya Book 1 Hausa Novel Complete
yau zan yi komai sai kafin nan da ƙwana sittin mun jefi tsintsu biyu da dutsai daya kaga a idon jama'a ka zama mai aure sai dai mu muka san manufar yinsa
Wannan kenan
Murna take tunda komai ya lafa yau zata kwana a gidan ta kwashe komai nata tayi ta fito ita da rufaida shiga motar ta tayi ta fara tuƙi tace
Wallahi rufaida yau jina nake wani sa kayau nasan de yanzu ya haƙura ya zubar da makamansa
Uhmm Allah yasa
Ameen kin mai da su kahu
"Eh jiya suka koma ,
Gaban makeƙen gidan suka tsaya sosai binta tayi mamakin arahar gidan tayi farinciki sosai sai ma da ta shiga taga an zuba komai yanzu jibi zata fara binkican mahaifinta kahu yayi murna da ganinta sai nan nan suke da ita shi da uwani zama tayi tana ƙarƙada ƙafa tace
"To yanzu kahu komai ya sauya Banda fita bara ,
toto nadena binta
Uwani
gyara zanin ta tayi tace
"Na'am binta,
Banda sana'a ina da kuɗin ciyar da ku
to bazan sake ba
kawata ni zan tafi
Okay muje in raka ki ko
Tashi tayi su ka fita
Tashi yayi shima ya dubi uwani yace
Ni zan fita in zaga gun yan uwa daula ta samu
To me gida sai kadawo
Dariya yayi yace
Rabon kiyimin wannan tarbar tun muna cin amarci
Ae yanzu komai ya huce
Babbar riga ya gyara ya fita tafiya ya fara wata ƙatuwar jeep ce ta tsaya baƙa wasu burɗadɗun mutane ne suka fito suka ce
Tsoho shiga
Ja da baya ya fara ji yayi ya jingina da wani garo juyowa yayi ashe mutum ne yace
"Lafiya ,
Ka yiwa kanka arziki ka shiga tambaya zaka amsa mana
Ba yarda ya iya yace
"To ba yarda ya iya ya bisu tafiya sukai mene sa tu kunna su ka je gidan gona duk bishiyo fitowa sukai suka tisa ƙeyarsa har wani har wani hadaddan floor wanda shi ake kira da aljannar duniya zama yayi a ƙasa suka fita suka jawo ƙofa
Hawaye ne ya fara zubomai ya gashi a fadar aljanu shi daman ya san ba zasu barshi ba tafiya yaji
Zabura yayi ganin mutumin da yake gani a poster
Murmushi ya sakar mai ya zauna yace
Bisimillah zauna cikin aminci
Murza idonsa yayi yace
Nan ma ya isa
Okay wata alfarma nake nema
Anya kuwa ni labahani ba mafarkin da nasa ba naka ba
Ido biyu kake zauna dan Allah
"To to zama yayi ,
Kai haƙuri na sa an dauko ka
Bakomai ka isane
Yauwa Nagode ina nemawa jikana auran yar wajanka ina fatan ba ai mata miji ba
Washe baki yayi me ragaje tayi goshi yace
"A'a ban mata ba Maryam a kwai ƙirkir wallahi tafi Binta komai,
ganin be gane wacce yake nufi ba ya danna wani majigi nan hotan Binta ya bayyana yace
"Wannan nake nufi,
Zaro ido yayi yace
"Binta tafi ƙarfina wallahi ga Maryam nan na baku ita nake da iko a kanta,
Kar ka damu aikai wakilinta ne zamu san yarda za a Kaita gidan a ɓoye sai dai ta farka ta ganta a gidan su zan kai ka Makka sannan zan baka ƙaton gida kai shiru da bakin ka
Zama ya gyara yace
"To to Ni wallahi yanzu a shirye nake na baku ita yanzu muje masallaci a daura,
Murmushi yayi yace
Angon baya ƙasar nan amma nine wakilinsa ga abokin sa zai zo a yau zan baka komai da nayi maka alƙawari za a dauki komai a nuna mata dan ya zama sheda.......✍🏻