Showing 6001 words to 9000 words out of 75868 words

Chapter 3 - Dubu Jikar Mai Carbi Book 1 Complete Hausa Novel

24 Sep 2025

956

ta zo ƙarshe.

Ba baka sai kunne. Baba sule ban da hawaye babu abin da yake yi. Wannan shirun da Baba Sule ya yi ba ƙaramin ɓata ran Yaya Babba ya yi ba, don haka ta dube shi ta ce, "Bana son iya shege kai Sule idan ba za ka yi magana ba, ka fice mini daga ɗaki ko na kwashe maka albarkar da ta yi saura a kanka." Baba Sule ya sake matsar ƙwalla ya ce, "Inna wallahi Fatalwar Baba ce za ta tafi da ni matukar na saki hannun Sahuwa ƴan sama jannati ne za su tafi da ni." Ku san mutuwar zaune Yaya Babba ta yi saboda labari ya risketa daga wurin kishiyarta ga shi Ɗan cikinta ma ya sanar da ita.

Nan fa gida ya hautsine hantar cikin kowa ta kaɗa saboda fargaba, Sai da Yaya babba ta yi da gaske sannan Baba Sule ya saki hannun sahura. Ai kuwa yana sakin hannunta ta ranta ana kare. Baba Sule na ganin haka ya rufa mata baya. Sai da ƙyar aka samu aka tsayar da su a soron gidan tare da tura Baba sule cikin ɗaki don Yayan Mahaifinsu gani yake kamar gamo ne suka yi. Dubu ban da dariyar mugunta ƙasa-ƙasa babu abin da take yi.

Sai daga baya aka farga da su Auwalu da suke ɗaki don haka da sauri Yayan Mahaifinsu ya je ya sa suka buɗe ƙofar da ƙyar, Auwalu yana maƙale da Yahanasu don gani yake idan ya sake ta kamar Fatalwar Mahaifinsa za ta yi awon gaba da ita.

Malam Idi shi ne yayan Mai Carbi, tara mutane gidan ya yi gabaɗaya yana yi musu nasiha da nusar da su illar yarda da amincewa abin da suka yi tozali da shi. Sai da ya gama wa'azin sannan ya bawa Inna Furai damar ta yi magana.

Inna Fuarai ta karkace ta ce, "Yaya Idi yadda na ga Fatalwar Malam na ga Annabi. Ganin idona na ganshi kuma har umarnin shayar da su Auwalu ya yi." Sai da suka gama jin jawabinta tsaf sannan aka ce Yahanasu ta yi faɗi abin da ta sani, Yahanasu da ta buɗe ido da kyar tana sunne kai ƙasa don duk yanda hankalinta ya ɗan kwanta har Yaya Idi ya sa ta buɗe ido bata gama sakewa ba. Ta fara yi musu bayani dalla-dalla sanna ta ɗora da cewa, "Kuma da bakinsa ya sanar da ni duk wanda ya wayi gari da likkafani a ɗakinsa to gaba shi za su ɗauka. Shi ya sa na ce tawa ta ƙare." Auwalu ya rumgumota yana cewa, "Ba za ki mutu ba Yahanasuna" Yaya Idi ya yi jim sannan ya ce, "Idan na fahimta wani ne kawai yake son razanar da mutanen gidan amma babu damuwa ku bar mini komai a hannuna zan san yanda zan ɓullowa lamarin.

Dubu tana gefe tana jin duk wainar da ake toyawa don haka ta saci jiki babu wanda ya lura da ita, kuma babu wanda ya taɓa kawo ita za ta aikata wannan abin. Dubu na tafiya ta wuce ɗakin Marigayi ta zaro wasu kayansa da yake zuwa sallar juma'a da su. A wanke suke a goge fari ƙal da su, sai da ta bubbuɗa su ta je bakin katangar banɗaki wacce mutum zai iya haurawa ta wurin ta ajiye, hularsa ta saƙale a jikin wata itaciyar tunfafiya sai kuwa ta kwaso a guje ta shiga wurin taron da suke gabda kammalawa. Ihu take kwarawa kamar wacce ake ɗanawa wuta tana cewa, "Wayyo Allah na ga Fatalwar Baffa na gani zai tafi da ni. Kafin ka ce wani abu tuni wurin ya watse sai takalma da ɗankwalaye da aka barsu suna cin karen su babu babbaka. Yaya Idi sai da ya yi kusan adungure biyu sannan ya samu ya shige ɗakin Inna Furaira. Hularsa kuwa ta yi tsalle ya fi sau biyar kafin ta samu sukuni faɗuwa can bakin ƙofa.
[7/1, 6:03 PM] My Data sim number: *DUBU JIKAR MAI CARBI*


©AMEERA ADAM

FIRST CLASS WRITER'S ASSO...

*Littafin kuɗi ne 200 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin Mtn, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.*

https://chat.whatsapp.com/KQd6gkViAXfKDTv7iWLJpV

FREE PAGE 3

Ƙananan yaran da aka bari a ƙofar ɗakuna ban da kiran sunayen iyayensu babu abin da suke yi, ƴan madaidaitan cikinsu waɗanda suka fara sanin ciwon kansu ne suka samawa kansu mafita suka nemi maɓoya. Sauran marasa wayo sai ihu suke suna buga ƙofar ɗakin da iyayensu suka shiga. Yaya Idi saboda firgita bai san lokacin da ya wuce can ƙarshen gadon Inna Furai ba, mutumin da ko falon Inna Furai baya iya ƙwaƙwaron tsayuwa, a cewarsa yana Yayan miji haka sam bai kamace shi ba. Rabon shi da shiga ɗakin Inna Furai tun wata doguwar rashin lafiya da ta yi sama da shekara goma, lokacin da ya je dubata amma a wannan ranar shi ne har tsakiyar gadonta. Ban da ɗigar da gumi babu abin da gemunsa yake yi saboda tashin hankali. Lantan can ƙarƙashin gado ta shige ban da ƴan idanuwanta babu abin da kake iya hangowa, ta ƙwale kai a jikin ƙarfe gado ya fi sau biyar duk don ganin ta ɓoye kanta ba tare da an hangota ba bare tawagar fatale su kawo mata farmaki.

Inna Furai zaman ƴan bori ta yi zanin jikinta ya jiƙe sharkaf da fitsari don gani take wannan zuwan da Fatalwar nan ta yi zuwanta ne, don a ganinta saɓawa umarnin fatalwar da tayi na sake shayar da ƴaƴanta ne ya sa, fatalwar nan ta yi dirar mikiya domin ƴan sama jannati su tafi da ita. Badariya tuni ta ƙwaƙume Yaya Idi da ke gefenta, duk yanda Badariyya ta kai ga jin ƙyanƙyamin gemun namiji sai ga gumin gemun Yaya Idi na ɗiga a sai tin fuskarta. Gabaɗaya mutanen cikin ɗakin ba ƙaramin tsorata suka yi ba. Ita ma Dubu tuni ta bi yarima don kar wani ya yi saurin gano shirinta saboda ko kaɗan bata son ta samu matsala, ta tabbata muddin ta ci gaba da razana su babu wanda zai ƙara koda nan da kwana biyu ne.

Bayan wasu ƴan mintuna Yaya Idi ya ɗago sai a lokacin ya lura da wacce take gefensa a maƙale da shi suna haɗa ido ya watsa mata harara, da sauri ya matsa gefe yana cewa, "Subhanallah! Astagafirullahi wa'atubu'ialhi ke matsa gefe matsa-matsa" A razane ita ma ta ja baya tana yamutsa fuska alamar ƙyanƙyami, don ita kanta bata san lokacin da ta ƙwaƙume Yaya Idi ba don ta san kowane ne shi. Ya kalli Dubu da ke can bakin ƙofa da yake ita ce ƙarshen shiga sannan ya ce, "Ke Dubu wai da gaske kike kin ga Fatalwar Mamman?" Dubu ta yi wani fakare sai kawai ji suka yi ta rushe da wani irin kuka har tana wani furjin yawu kamar wata ƙaramar yarinya." Yaya Idi ya yi zuru yana kallonta a zuciyarsa yana fatan kada Allah ya sa ta tabbatar da abin da ta faɗa da farko. A ƙagauce Yaya Idi ya sake cewa kamar zai yi kuka, "Ke Dubu wannan kukan ba ke kaɗai za ki yi shi ba ki sanar da mu musan halin da mu kanmu muke ciki."

Dubu ta tsagaita da kukan sannan ta fara cewa, "Na ga fatalawar Baffa ido da ido don har cewa suka yi za su fara ɗaukan Innarmu da Innar su Sabi'u. Kuma wai sun ci alwashin duk wanda ya haure shekara Arba'in a gidan nan sai sun naɗe masa ƙafafuwa kamar alkaki."

Tashin hankali wanda ba a samasa rana. Inna Furai na jin ance za a tafi da ita da Yaya Babba hantar cikinta ta sake kaɗawa gumi ta ko'ina sai keto mata yake yi. Don har kusan suman zaune ta yi saboda waɗansu irin taurari ta rinƙa gani suna yi mata gizo a tsakar idonta. Tun daga abin da Dubu ta faɗa babu wani abu da Inna Furai ta sake fahimta a ƙwaƙwalwarta, don sama-sama ta rinƙa jin wani yuuuuuu a zatonta wannan abin da ta fara ji ƴan sama jannatin ne suka fara kawo mata farmaki. Cikin fitar hayyaci Inna Furai ta fara cewa, "Ikon Allah Ikon gaske! Kai Auwalu kana ina ne? Ke Larai don Allah a cikinku wani ya ɗauke ni ko a kafaɗe ya fice da ni tun fatalwa bata tafi da ni. Auwaluna! Auwaluna na ci burin ganin Ɗanka amma da ƙyar idan zan samu wannan damar ka kawo mini Yahanasu idan ya so mu tafi da ita ko da Fatalwar sun tafi da mu na yi mata raino a cen barzahun idan ta haihu." Dubu juyawa ta yi ta rinƙa ɓaɓɓaka dariya ƙasa-ƙasa saboda ta lura tuni Inna Furai ta riga da ta fita hayyacinta, don fitsari ma ta yi ya kai sau uku daga shigarsu ɗakin.

Lantan tun da ta ji labarin naɗe ƙafafuwansu kamar Alkaki, ta sake firgicewa wani buhu da ke gefenta ta fisgo wanda yake ɗauke da dawa kusan kwano biyu, bata bi ta kan dawar ba ta watsar da ita a gefe ta fara tura kanta a ciki. Don yanda Lantan take ji da ace akwai hanyar da za ta fitar da ita daga cikin ƙarƙashin gado ta tuni ta fice ta yi hanyar zariya. Babban abin da ya fi ɗaga mata hankali shi ne zancen naɗe ƙafafuwansu da ta ji ance Fatalwa za ta yi mayar da su kamar alkaki. A duniya babu abin da ta fi so da ƙauna a jikinta kamar santala-santalan ƙafafuwanta, wannan ya samo asali ne sakamakon kirarin da marigayin mijinta yake yi mata akan Doguwa mai tsawon alheri tsawo rabin kyau ƴar fillo.Wannan kirari ba ƙaramin baƙanta zuciyar Lami kishiyar Lantan yake ba saboda ita gajeriya ce, kuma hatta bayan rasuwar mijinsu idan wani abu ya haɗo Lantan da Lami haka za ta yi ta hura hanci tana yi wa Lami habaici. To kuwa idan aka mayar da ƙafafuwanta kamar Alkaki ai ta shiga-uku don ta tabbata idan aka naɗe mata ƙafafuwa, ta san ko tsahon turmin gidansu ba za ta kai tsayi ba.

Lantan bata gama tunani ba ta riski maganar Dubu cikin kuka tana sake cewa, "Kuma har ce mini ya yi a cikin ƴan uwan sa zai aiko a tsotsewa wani ko wata roman da ke cikin Ƙwaƙwalwarsu. Saboda gonar Mahaifinsu da suka taɓa danne masa."

Lantan na jin haka ta ci gaba da karanto duk wata addu'a da ta san ta taɓa biyata a bakinta. Saboda ta san badaƙalar da suka shuka akan gonar Mahaifinsu. Hatta kalmar larabci indai Lantan ta santa a baki haka za ka ji tana maimaitata ya fi sau goma. Ta yi kiran sallah da tayar da iƙama ya fi sau biyar, idan ta biya addu'ar shiga banɗaki sai ka ji ta fara, "Labbaikallahumma Labaik" Idan ta dire sai ka ji ta sake cewa, "Hayya'alal salah" haka ta rinƙa yin addu'a don neman kariyar Ubangiji, amma addu'a har da ta shiga abin hawa haka ta rinƙa maimaitawa. Tana gamawa sai ka ji ta sake cewa, "Walaƙadkarramna bani adama..." Bata iya direwa sai ta ƙara kamo wata kalmar hatta sunayen Annabawa da Sahabai waɗanda ta san sunansu haka ta rinƙa biyawa.

Ana cikin haka suka jiyo muryar Baba Munkaila a bakin ƙofar Inna Furai yana cewa, "Lafiya kuwa mutanen gidan nan tun daga babban zaure nake sallama shiru ga ƙananan yara suna ta kuka." Ya ƙarasa maganar yana bubbuga ƙofar ɗakin, da ƙyar Yaya Idi ya ta so ya fara ƙoƙarin zare sakata.

A can ɗakin Yaya babba dirama ake yi da ita akan dole sai an barta ta fito wai sai dai Fatalwar ta ɗauketa ita da Dubu don ba za ta iya jure rashin Dubu ba. Hadiza da ke riƙe da kubar ɗakin ta ce, "Inno don Allah ki yi haƙuri ki zauna na san Dubu ba za ta zauna a waje ba, kuma ni fa gani nake sharrin shaiɗan ne amma babu wata fatalwa." Yaya Babba ta sake share ƙwalla ta ce, "Kaico rayuwa ban taɓa sanin haka zuciyarki ta ƙeƙashe ba Dije, wannan wacce irin falsafar rashin imani ce? Kowaccenku na riƙe da Ɗanta amma ni kun hanani nemo Marainiyar Allah. An ya kuwa Dije?" Hadiza babu yanda ba ta yi ba amma fir Yaya Babba ta kafe, don ban da ruwan hawaye babu abin da take yi. Hadiza na buɗe ƙofar Yaya babba ta fice da sauri tana ƙwalawa Dubu kira. Da sauri Dubu ta taho aikuwa caraf Baba Munkaila ya damƙi hannunta bayan ya gama jin labarin abin da aka bashi dangane da fatalwa. Yana fisgota ya zuba mata ranƙwashi a ka yana cewa, "Wallahi sam ban yarda da abin da wannan shaiɗaniyar yarinyar nan ta faɗa, ke a gidan uban wa kika ga fatalwa har ta baki saƙo?" Yaya babba na ganin haka ta ƙarasa wurin ƙafar Baba Munkaila ta yi zaman dirshen sai kawai ta fashe da kuka. Gabaɗaya ido ya dawo kanta, Baba Munkaila ya sassauta murya ya ce, "Inno lafiya kuwa?" Yaya Babba ta ɗago ya dubi Mukaila ta janyo hannunsa ta ce, "Ka dake ni kawai Munkaila na ce ka dakeni ka huce takaici. Kaga sai na tabbatar da falsafar rashin mutumcinka yanda ya kamata."

Baba Abubakar da shigowarsa kenan ya hango taron jama'a yana zuwa ya ga Mahaifiyarsa ce mutane ke zagaye da su. Har ƙasa ya russuna yana tambayar Mahaifiyarsa. Yaya Babba ta share hawaye ta ce, "Allah ya yi maka albarka Garba! Don Allah ka ga ya mini me na tsare wa Munkaila da Dije? Munkaila dai ya fi jin haushina. Garba ka gaya mini wacce tsiya suke tsinana mini, bayan Allah da ma'aiki waye gatana wa zai tsunduma ni a aljannah?" Baba Garba ya jinjina kai ya ce, "Inna wai me yake faruwa ne? Me suka yi miki?"

"Tsoronsu kake ji da zan yi magana ka amsa ƙasa-ƙasa. A cikinsu ka gaya mini akwai Malam ko kuma akwai ni. Ban da Allah da Manzonsa wa yake ƙaunata, ya hore mini lafiya da abin da lafiya za ta ci?" Yaya Babba ta yi maganar cikin ƙunan rai. Baba Abubakar ya ce, "Ayi haƙuri Inno"

Yaya Babba ta zuba hannuwa biyu tayi tagumi ta ce, "Garba ni wace ce a wurinku?" Baba Abubakar ya bata amsa, "Ke Mahaifiyarmu ce Inno"

"Idan na tsinewa su Munkaila wa billahi sai ta ka kama su ko ba haka ba?"

"Inno abar maganar tsinuwa don Allah." Baba Abubakar ya faɗa cikin sanyin murya. Yaya babba ta kuma rushewa da kuka sannan ta ci gaba da cewa, "Don Allah mecece tsinuwa da zan tsinewa ƴaƴan cikina. Idan na tsine musu na ɓalɓace duniya da lahira ko ina da wasu ƴaƴan bayan ku?" Baba Abubakar ya yi ƙasa da murya ya ce, "Inna don Allah ki yi haƙuri kin ga duk mutane kallonki ake yi."

Yaya Babba ta yi jim sannan ta ce, "Ka yi mini iyaka da Munkaila ko a hanya ya ganni kar ya nuna ya sanni, balle a lahira ya yi gabas na yi yamma. Haƙƙi ɗaya na san Munkaila yana bina, lokacin da aka yi masa shayi (kaciya) don Allah Garba ka biya shi cinyar kazar da na ci, ko ba za ka biya shi ba Garba?" Baba Abubakar ya rasa abin faɗa sai kawai ya girgiza mata kai. Yaya Babba ta ci gaba da cewa, "Me marainiyar Allah ta yi masa da zai ƙullace ta har ya sheganta mini ita? Don Allah Garba ka tambayar mini shi ta wurin da Dubu ta zama shegiya? Ka tambayi munkaila Ni Indo Kakarta ce shegiya ko matattun iyayenta?"

Baƙin ciki ne ya cika Baba Munkaila domin jikansa ya ba shi abin da Dubu ta faɗa ba gaskiya bane saboda ya san wacece ita, amma gani yake meye laifinsa don yana son hukunta Dubu domin ta faɗi gaskiyar magana. Gani yake idan ya yi haka shi zai kawo musu ƙarshen duk wannan guje-gujen da ake yi. Tun da tun farar safiya ya ji labarin abin da ya faru yake tantama akan Dubu don kowa ya san irin hatsabibancinta.

Wata uwar harara ya watsawa Dubu sannan ya kalli Mahaifiyarsa ya ce, "Yanzu Inno saboda na hukunta Dubu shi ne ya ɓata miki rai? Tun da haka ne na zame hannuna daga cikin sabgarta shi kenan?"

Yaya babba ta wara hannuwa alamun abin ya mata daɗi ta ce, "Sadaƙallahul azeem! Kana jin me ya ke faɗa ko Garba, dama me Munkaila yake yi wa Dubu? Ka gaya mini waye yake shiga lamuran Dubu bayan Allah da manzonsa idan ba ni ba?" Baba Abubakar ya sake ƙasa da murya ya ce, "To duk na ji wannan Inno amma don Allah ki taho mu tafi ɗaki."

Yaya Babba ta yi biris da Baba Abubakar tana cewa, "Don Allah ka yi mini iyaka da Dije saboda tsoro nake ku tafi ku bar ni da ita a ɗaki ɗaya, kar a wayi gari ta maƙure ni na mutu har lahira." Cewar Yaya Babba tana satar kallon Hadiza.

Rass gaban Hadiza ya faɗi da jin kalmar Mahaifiyarta, da sauri ta ce, "Inno ni kuma? Ni ce zan kashe ki?"

"Duk gidan nan babu wanda ya ƙullace ni yake jin haushi kamar Dije dubi irin kallon da take yi mini, haushina take ji saboda na ce ta buɗe mini ƙofa na je wurin Dubu. Don Allah Garba ka gaya mini me na yi mata ko zargina take akan mutuwar mahaifinku?" Sam wannan maganar bata yiwa duka ƴaƴan Yaya Babba daɗi da cikin yanayin rashin jin daɗin maganarta ya ce, "Haba Inno me kike yi haka ne kowa fa a wurin nan ke yake kallo saboda Allah me mutane za su ɗauka jiya-jiya Mahaifinmu ya rasu amma kina wannan abubuwan." Ya ƙarasa maganar yana dafa ƙafarta.

"Sakar mini ƙafata Garba." Yaya Babba ta faɗa a hassale. Ba musu ya sakar mata ƙafa. Sai kawai ta miƙawa Hadiza hannu ta ce, "Allah ya jiƙanki ba don kin mutu ba Dije don Allah taimaka min zan koma ɗaki,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login