Showing 9001 words to 12000 words out of 75868 words

Chapter 4 - Dubu Jikar Mai Carbi Book 1 Complete Hausa Novel

24 Sep 2025

954

ko a baƙar zuciyar Munkaila kina ga zai kaini ɗaki?" Hadiza ta girgiza kai tana murmushi, Yaya babba ta ci gaba da cewa, "Don Allah ki ce Garba ya matsa daga gabana ko na fice na bashi wuri." Gefe Baba Abubakar ya matsa Dije ta samu ta lallaɓata suka shige da Yaya Babba ɗaki. Suna niyyar tafiya daga wurin suka ji ƙarar abu tim! Daga bayansu. Da sauri suka waiga sai gani suka yi Inna Furai ce da ƙaton buhunta tana ja Auwalu shima yana ja wai dole a barta ta fita ta yafewa zaman cikin gidan. Ita ma sai da suka sha fama da ita sosai sannan suka samu ta koma ɗaki. Baba Abubakar ya dubi Dubu yace,

"Dubu ince idan muka je da ke za ki iya nuna mana ta wurin da kika ga fatalwar?" Dubu ta gyaɗa kai suna haɗa ido da Baba Munkaila ya watsa mata harara. Shi kansa Baba Abubakar zuciyarsa raya masa take tabbas akwai wanda yake son tsoratar da mutanen cikin gidan tun da wanda ya mutu ya mutu kenan har abada baya ƙara tashi. Dubu suka tasa a gaba tana gaba suna biye da ita a baya, sai wani ɗari-ɗari take ita Allah dole tsoro take ji.

Zu-gar mutane ne suka yi dafifi don ganin ta wurin da Dubu ta ga Fatalwa da idonta. Ita kuwa hakimar kanta sai ƙara girma yake musamman yanda ta ga mutane kowa ambatarta yake ana jinjina mata bisa ga ƙoƙarinta na tunkarar wurin. Daga can hanyar banɗaki suka hango wasu fararan kaya, daga nan wasu suka fara cin burki, sai kuma hular Marigayi Mai carbi da iska take kaɗa ta sama-sama. Mamaki da ta'ajibi ne ya kama su hatta Baba Munkaila sai da ya zubawa kayan ido, ɗaya tsagin na zuciyarsa na son aminta da abin da Dubu ta faɗa sakamakon kayan da ya gani. Amma yana tuna wace ce Dubu zai ji ya ƙi aminta da komai.

Baba Abubakar ne ya yi bismillah ya ɗebo kayan yana ƙare musu kallo zuwa can ya kalli Dubu yana shirin yi mata magana, sai kuwa ta zabura tamkar wacce aka ɗanawa wuta. Can bayan Zulfa'u ta maƙale tana cewa, "Baba Habu wallahi tsoro nake ji." Baba Munkaila ya karɓi kayan yana jujjuyawa sannan ya ce, "Amma gaskiya ana raina wa mutane hankali." Baba Abubakar ya yi gaba yana cewa, "Dole mu san abin yi amma tabbas akwai wata a ƙasa. Da alama wani ne yake son kawo yamutsi amma kowa ya kwantar da hankalinsa komai ya zo ƙarshe." Baba Munkaila ya hau muzurai yana zare idanu ya ce, "Koma wane ne ni da hannuna zan ci ubansa don na san na gida ne yake aikata wannan abubuwan. Amma duk wanda yake da hannu cikin wannan tafiyar sai na kusa tsinka shi gida uku." Ya ƙarasa maganar yana yi wa Dubu kallon idan ma ke ce za mu gauraya da ke.

Kafin wani lokaci tuni maganar fatalwa ta fara zaga cikin garin Ɗangwauro, har da masu isar da labarin abin da bai faru ba. Kasancewar kowa da abin da yake ji shi yake idarwa.

************

"Dubu ki kwantar da hankalinki idan ma don wannan ne kamar an yi an gama a wurina. Ba dai ni na haifi Garba ba?" Yaya babba ta ƙarasa maganar tana kallon Dubu cikin sigar lallashi.

Dubu ta tura baki gaba tana cewa, "To ai ke sai an gama magana da ke lafiya ƙalau sai kawai daga baya ki sake shawara, gaskiya ni dai ko ki sa mu koma birni gidansa ko kuma ki ce su dawo garin nan wallahi sai mun fi cin daɗi tun da anan me muke ci kamar ba ke kika haifeshi ba." Yaya Babba ta yi jim sannan ta ce, "Ba zan koma birni ba domin Malam har wasiyya ya bari akan kar mu kuskura mu bar gidan nan to kin ga saɓawa miji haramin ne amma Garba ko ya ƙi ko ya so dole ya dawo gidan nan da zama."

Baba Munkaila ne ya kawo kai zai shiga ɗakin Mahaifiyarsu amma ya ga mutane sun yi carko-carko a ƙofar ɗaki ya tambaya ko lafiya.

Hadiza ta taɓe baki ta ce, "Inno ce suke shawara da Dubu shi ne ta koro mu waje." Haushi ne ya ƙara kamashi don ya san duk iskancin da Dubu take yi Mahaifiyarsu ce take ɗaure mata. Ɗaga labulen ɗakin ya yi suna haɗa ido da Yaya Babba ta ce, "Kai Munkaila ka tara mini ƴan uwanka yanzun nan ina son magana da ku!" Kallon Dubu ya yi ya ga ta yi ɗai-ɗai a cinyar Yaya Babba, gudun neman magana ya sa bai tanka ba ya amsa ya fice. Don baya raba ɗayan biyu Dubu ce ta kitsa mata wata maganar.

Ba a ɗauki lokaci ba Iyalan Yaya Babba suka cika a ɗakin kowa da abin da yake ƙissimamawa zuciyarsa. Dubu na ganin haka ta saci jiki ta tafi haɗa kayan aikinta domin da alama tana ganin wankin hula zai iya kaita dare, don ta ga mutanen gidan ba su da alamar tafiya.

"Na san za ku yi mamakin ganin wannan taron amma ba wata doguwar magana bace. Gabaɗayanku so nake idan an yi sadakar bakwai kar wanda ya sa ƙafarsa ya fita daga gidan nan akwai babban taron da za mu yi gabaɗaya gidan nan. Musamman kai Garba tun da kaine babba." Yaya Babba ta yi maganar tana ɓata fuska don kar wani ya nemi kawo mata wargi. Suma ganin haka ya sa babu wanda ya musa mata sai dai cikin ladabi ɗayan bayan ɗaya suka ta shi suka fita kowa yana wani lissafi daban a zuciyarsa.

Baba Munkaila yana lura da duk wani shige da ficen Dubu sai dai kamar yanda ya sa mata ido ita ma tana ankare da shi. Yi ta yi kamar babu wani shiri da take haɗawa don shi kansa a wannan lokaci ya fara rage zarginsa a kanta.

Tun da yamma ta kawo kai doshin magriba ƙafafuwa suka fara janyewa daga cikin gidan kowa daga alwalar magriba ya riƙe abarsa don kowa a tsorace yake. Wannan dalilin ya sa zaman cikin gidan ya gunduri Hajiya Nafisa Matar Baba Abubakar da iyalanta. Allah ya sani ita dama ba ma'abociyar son zaman ƙauye ba ce, don ta kusa shekara biyar ba ta kwana a garin ba sai dai taje ta dawo a ranar, haka ma daga ɓangaren ƴaƴanta shi ya sa basu cika wani sakin jiki da mutanen gidan ba.

Bayan Sallar Isha'i.

Daga cen bayan ɗakin Marigayi suka fara jin kiran sallah da muryar Marigayi mai carbi. Kasaƙe mutane gidan suka yi aka rasa mai zuwa kiran Mazan da ke ƙofar gida don sanar musu da abin da yake faruwa. Don kowa hantar ciki ta kaɗa saboda lokacin dare ma bai gama yi ba don ko tara na dare bata yi ba.

Tana gama kiran sallar ta fara wasa wuƙa ji kake , "Kuyat! Kuyat" Sai da ta ƙara matsowa hanyar cikin gidan ta fara wani irin kuka mai kamar haniniyar doki. Gidan tsit ya yi kamar an yi ruwa an ɗauke tun da Dubu ta ji haka cikin muryar marigayin Kakanta ta fara cewa, "Da alama yau za mu ɗebi mutanen gidan nan da yawa. Amma duk wanda ya cinye tuwon daren yau ya tsira ba za mu taɓa ko ta fatarsa ba."

Daga can ɗakunan mutanen ɗakin nɓa jin haka suka fara kantamar tuwon da ko minti ashirin ba a yi da kwasarsa ba. Da zafinsa suka rinƙa ci saboda tsira daga kaidin tawagar fatalwa. A ɗakin Inna Furai faɗa ne ya ɓarke tsakanin Lantan da Inna Furai akan suɗin kwano har Lantan ta ji haushi ta kwalawa Inna Furai silba a goshi.

Dubu na daga wurin da take laɓe tana jin hayaniyar mutane sai da ta kintaci lokaci, ta fara wani irin nishi mai ban tsoro tana cewa, "Duk wanda ban ji sautin tusarsa ba shima wallahi babu mai hanamu ɗaukansa a daren nan."
*DUBU JIKAR MAI CARBI*


©AMEERA ADAM

FIRST CLASS WRITER'S ASSO...

*Littafin kuɗi ne 200 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin Mtn, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.*


FREE PAGE 4


Wannan karon gabaɗaya turus suka yi da jin abin da aka faɗa, kallon-kallo aka fara yi a tsakanin juna kowa da abin da yake nazari a zuciyarsa. Suna cikin haka suka sake jin an ce, "Bismillahir rahmanirrahim bari mu fara ɗauka daga kan ta bakin ƙofa." Ai Dubu bata rufe baki ba sai ji ta yi alamar guje-guje, Yahanasun Auwalu tun bayan sallar asuba da ta shiga ɗakin Inna Furai ba ta sake fitowa ba kuma ta ci alwashin ko da fitsari za ta ji sai dai ta matse abin ta, idan ta kama ma sai ta saki abin ta a wurin. To ashe tsugunne bata ƙare mata ba tun da har fatalwar za ta iya kawo musu farmakin dare har cikin ɗakuna, tun da ta ji an ce za a fara ɗauka daga na bakin ƙofa.

Nabila ƴar wurin Hajiya Nafisa, budurwa ce don ta yi sha tara a shekaru. Turo baki ta yi tana cewa, "Maganar gaskiya Mommy ni fa na gaji da wannan abubuwan kullin abu ɗaya wacce irin fatalwa ana zaune ƙalau bayan kowa ya san babu wata fatalwa a musulunci." Cike da ƙosawa Hajiya Nafisa ta ce, "Nabila ya za mu yi kin san dai ba mu da ta cewa tun da zuwan nan na dole ne ya kama mu haka Allah ya ƙaddara mana." Yaya Babba da ke gefe fuskarta ban da gumi da maiƙo babu abin da take yi, ta dubi Hajiya Nafisa da kallon sheƙeƙe ta ce, "Ke Nafi! Zuman ku a gidan na shi ne ƙaddara? Wallahi za ki ga ƙaddara kuwa ganin idonki. Wannan gidan da kike gani kin zo kenan zuwa sojan badaskare." Tana gama faɗa ta yi ƙwafa a zafafe. Dubu daga wurin da take ta jiyo hayaniya na tashi kaɗan-kaɗan ta sake shaƙe murya ta ce, "Ƴan sama jannati basa lamintar kuskure don haka za mu fara bi ta kan dabbobin gidan kafin mu fara taɓa mutanen ciki, ina tawagar Fatale ku fara dirowaaaa." A hankali ta lallaɓa da sauri ta buɗe ɗakin zabbin Baba Munkaila. Hannunta riƙe da muciya ta fara buga ƙyauren langa-langar da ke jikin ƙofar. Nan da nan zabi suka fitowa a tsorace suka fara tsalle da kuka "Ƙurƙet! Ƙurƙet!" Da yake da hasken wutar lantarki tuni zabbi suka fara bazama suna kuka, Dubu ta sa muciya ta riƙa make kawunansu ɗaya bayan ɗaya. Da ta bugawa zabo ɗaya sai ka ji ya yi ƙara ya faɗi ƙasa. Wannan kukan Zabbin ba ƙaramin ɗaga hankulan mutanen da ke cikin ɗakunan ya yi ba. Shiru suka yi suka zurawa sarautar Allah ido. Kowa da abin da yake ayyanawa zuciyarsa. Sai dai a wannan ƙadamin Lantan ta ci alwashin matuƙar tana da rabon ganin wayewar gari, babu wanda zai hanata tafiya don tun da ta zo duniya bata taɓa ganin masifa da tashin hankali irin wannan ba.

Zabbin nan gabaɗaya haka suka warwatsu suka shiga sauran sashen da ke cikin gidan. Muhsana ita ce ƴar autar Lantan, ta taho daga can sashen Baba Sule ba ta san abin da yake faruwa ba ta hangi Zabbin Baba Munkaila suna guje-guje wanda ya tabbatar mata da alama akwai abin da yake faruwa. Gabanta ne ya faɗi sakamakon ganin gawarwakin Zabbi kusan bakwai a ƙasa jini duk ya ɓata wurin. Sai dai har lokacin bata ga wanda yake aikata wannan abin ba, ɗaya zuciyarta ce take raya mata ko dai da gaske Fatalwar da ake faɗa ce ta fara aikinta, yayin da ta ƙara riƙe hannu Ɗanta Salihu don dama yaron ne ya fito da ita zai yi kashi. Ta bayan ɗakin Marigayi mai carbi ta je wucewa ba ta yi aune ba sai ji ta yi an fisgi hannun Salihu, aikuwa kusan tare suka ƙwalla ƙara daga ita har Salihun da ake ja, jan Salihu ta riƙa yi tana yi tana ihun neman agaji amma ba a daina jansa ba. Dubu na ganin Muhsana ta kusa fin ƙarfinta ta raɗa mata muciyar a baya tana cewa, "Ki taho mu yi rayuwar barzahu da ke. Ko ki bani Ɗanki Salihu na tafi da shi, ko kuma na ɗauke ku gabaɗaga." Muhsana bata gama jin ƙarashen maganar ba ta saki hannun Salihu ta yi cikin gida da gudu tana tafe tana sosa wurin da Dubu ta maka mata muciya. Shi kansa Salihu da ba a yi masa komai ba ya gama tsorata, dama jikinsa babu riga babu wando haka ya zuba a guje da tiƙeƙen cikinsa a daidai lokacin aka ɗauke wuta Salihu ya rasa wurin da zai bi haka ya riƙa gware da bango yana make sauran zabbin da suma ta kansu suke yi.

Ihun da Salihu yake yi ne ya tabbatar musu da lallai Fatalwa ta fara zuwa kan bil'adam, tun da; da farko sun ji kukan zabbi. A wannan lokacin Yaya Babba da ƙaramin tsorata ta yi ba don ko kaɗan Dubu bata faɗo mata a rai ba bare ta ambace ta. Lantan da ke ɗakin Inna Furai ta fara hawaye bibbiyu don saboda firgici ta tuɓe kayan jikinta ta sake saka su ya fi sau bakwai. Lokacin da ta riski muryar Muhsana na ihu, kuka ta riƙa yi wiwi don Mushana ita ce autarta. Da ta daina jin kukan Muhsana sai na Salihu wannan ne ya bata tabbacin tuni Tawagar Fatalen sun gama da Muhsana sun koma kan Salihu. Da ƙyar Salihu ya samu ya isa wurin ɗakuna ya fara lalubawa yana kuka, hannunsa ya ɗora akan ƙofar su Inna Furai yana bugawa yana faɗin, "Innaaaaa! Iyaaaa" Lantan na jin haka ta ɗare saman gadon Inna Furai hannunta riƙe da ɗan kanfen Badariyya tana ta tura kai duk a tunaninta rigarta ce za ta saka. Inna Furai wani farfari ta riƙa yi kamar wacce take kan hanyar suma, sai motsa baki take tana addu'a.

Zabbin da suka tarwatse wasu daga cikin su hanyar waje suka yi, suna kuka a firgice. Dubu tun da ta ga an ɗauke wuta ta haye katanga ta dira ta bayan gidan. Sai ga ta kamar mumina ta wuce shagon Lamarana ta siyo maganin sauro, da sauran wata hamsin ɗinta. Zuwanta ƙofar gidansu ya yi daidai tashin Baba Munkail kenan yana kaɗa Zabbin da ya ga suna tsalle suna fitowa ɗaya bayan ɗaya. Mutanen wurin ne suka fara taya shi, Dubu na zuwa ta zabga uwar sallama, ta yi haka ne saboda Baba Munkaila ya ganta don ta sake cire zarginta da yake daga kanta.

Cikin masifa ya fara yi mata magana, "Dallah sakarai matsa kina gani zabbina na fitowa sai wani ya ɓace a cikin duhu." Da sauri ta matsa gefe ta ce, "Baba Munkaila don Allah ara min fitila na kaiwa Inna Maganin sauronta tsoron soro nake." Ci kanki bai ce mata ba har suka samu suka kame zabbin, ban da masifa babu abin da Baba Munkaila yake yi, don a duniya idan kana son ganin ɓacin ransa cikin gaggauwa ka taɓa masa zabbinsa ko kuma wani laulawar keken hawansa. Yana gaba Dubu na biye da shi sai mutum uku da suke riƙe da zabbin nasa. Faɗa yake ta saki yana cin alwashi ga duk wanda ya buɗe masa Zabbi sai ya yi masa rashin mutumci. Suna shiga tsakar gida Baba Munkaila ya hasko gawar wasu zabbi biyu daga bakin ƙofa. Nan take cikinsa ya bada sautin ƙululululu! Jikinsa ne ya ɗau tsuma wani gumi na keto masa ta ko'ina, watsar da na hannunsa ya yi; ya kwasa a guje.

Yadda jaruman Indiya suke kwasar gudu idan sun yi tozali da masoyansu haka Baba Munkaila ya watsar da zabbin hannunsa ya kwasa da gudu har da wata uwar ƙara yana zuwa ya zube a wurin ya suri Gawarwakin zabbin ya rungume yana sauke ajiyar zuciya mai zafi, haɗe da haɗiyar wani irin yawu mai ɗacin gaske.

Kamar mai shirin yin kuka haka Baba Munkaila ya rinƙa shafa matattun zabbin yana cewa, "Don Allah wanene ya yi mini wannan ɗanyen aikin. Wallahi duk wanda na kama yana da hannu a ciki sai na ci ubansa." A daidai lokacin Dubu da sauran mutum ukun da ke riƙe da zabbinsa suka ƙaraso. Dubu ta yi tsaye tana kallon yanda gumi ke ɗiga daga jikin Baba Munkaila. Yana ɗagowa ya maka mata duka yana cewa, "Don Ubanki za ki kamo mini sauran ko su ma sai an kashe mini su." Kamar mai jira haka Dubu ta sheƙa da gudu kamar gaske tana dariya ƙasa-ƙasa. Daga can ɗan nesa Baba Munkaila ya fara hango ƙaramin yaro yana tafe yana jan ƙafar wata ƙatuwar zabuwa, wacce da alama ita ce uwar garken ciki. Salihu yana tafe yana murmushi yana zuwa ganin Baba Munkaila na riƙe da sauran zabbin ya sa ya miƙa masa yana sake yaƙe baki yana cewa, "Baba an ci kaza." Kusan suman zaune Baba Munkaila ya yi, ya ƙurawa Salihu ido ya ganshi tik ko wando babu. Cikinsa ya yi kurcici sai sheƙi yake da maiƙon abinci. Baƙin cikin ne ya kama Baba Munkaila ya dubi Salihu murya a daƙile ya ce, "Kai a ina ka gano wannan?" Salihu ya juya bayansa ya nuna ya sake cewa, "Baba an ci kaza"

A fusace Baba Munkaila ya buga masa tsawa ya ce, "A gidan uwarka za a ci kaza?" Salihu ba ƙaramin tsorata ya yi ba don haka ya saki zabon hannunsa jikinsa na rawa. Baba Munkaila ya sake ɓata fuska ya ce, "Waye ya kashe mini zabbi ko kaine?" Tsoro da ganin yanda Baba Munkaila ya ɓata fuska ya sa Salihu bai yi wata-wata ba, ya ce, "Ni ne a cen"

Baba Munkaila zuru ya yi yana kallon Salihu kamar wanda ya yi tozali da sabuwar halitta, ya sake haɗiyar yawu mai ɗaci murya a daƙile ya ce, "Wato kai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login