Showing 15001 words to 18000 words out of 75868 words
Chapter 6 - Dubu Jikar Mai Carbi Book 1 Complete Hausa Novel
Furai sai gani ta yi baya luuu!
Lantan ta zuba kabbara haɗe da cewa, "Innalillahi yau me nake gani haka jama'a ku taimaka mana wallahi sun fara ta kan Furaira." Nan fa suka ƙara ruɗewa sai Mardiyya ce ta yi ƙarfin halin yayyafa mata ruwa don ta fi zargin Inna Furai suma ta yi. Inna Furai na farfaɗowa suka fara jero mata sannu sai ji suka yi tana amsawa da,
"Ashhadu'anlla'ilaha'illallahu, wa'anna Muhammadarrasulillahi."
Lantan ta yi sauri ta ce, "Furaira me kike faɗa ne?"
Inna Furai da bata cikin hayyacinta ta ce, "Wa saumu ramadana. Amma Hajji kam sau ɗaya na taɓa ziyarta." Lantan rasa abin yi ta yi sai kawai ta fashe da matsanancin kuka tana yi tana fatar majina ta ce, "Tun da Uwata Mai carbin Malam ta haife ni ban taɓa ganin ƙadaddararrun ranaku kamar waɗannan ba kai jama'a yanzu Furaira daga suma sai hauka." Inna Furai bata san me ake yi ba don haka suka ƙarasa ganin daren har zuwa asuba Inna Furai na yi musu sumbatu.
Washegari.
Tun asuba da mazan gidan suka fito aka sanar da su abin da yake faruwa, don tun da suka wayi gari da ganin gororin ƴan bijilanti da fitilar Duna sai kuma takalmin ɗaya daga cikinsu, suka tabbatar da babu lafiya. Da aka sanar da su abin da yake faruwa wasu daga cikin mazan zuciyarsu ta fara aminta fa zancen fatalwar, saboda dama da Auwalu da Baba Sule tuni suka aminta da abin da aka sanar da su. Ba shiri aka ɗauki Inna Furai aka wuce da ita asibiti, saboda jikinta wani irin zafi da ya yi ga sumbatu ta take yi ba kai ba fasali.
Kaso casa'in da tara na mutanen da suka halarci gidan mutuwar a wayewar garin duk suka ɗaɗe kowa ya kama gabansa. Lantan dama ko sallama ba ta yi musu ba tana idar da sallar asuba ta fice ko jakar kayanta bata ɗauka. Ta so ta yi wa Autalliyarta magana ta ɗauko Salihu su tafi amma gani take ko ya ta ƙara ƴan sakanni komai zai iya faruwa. Wannan lamarin ba ƙaramin daɗi ya yi wa Dubu, don gabaɗaya gidan abin da ya rage daga ƴaƴa sai jikokin gidan. Wasu daga cikinsu har sun yi niyyar tafiya aka ce su bari a ga yanda jikin Inna Furai zai yi. Yaya Babba ta sake jaddadawa ƴaƴanta tana son zama da su idan komai ya daidaita akwai maganar da za su tattauna mai muhimmanci.
Wannan zaman da aka ce za su yi ba ƙaramim ɓata ran Hajiya Nafisa da Hajiya Fauziya ya yi ba. Ita kuwa Hajiya Rahama ko a jikinta damuwarta ɗaya fargabar da suke ciki ta rashin kwanciyar hankali.
Asalin Zuri'ar Mai Carbi.
Asalinsu mutanen garin Kano ne cikin ƙaramin ƙauyen Ɗangwaro dake jihar Kano. Mai carbi Su biyar ne a wurin Mahaifi da Mahaifiyarsu. Maza uku mata biyu amma acikinsu saura Mutum Uku rayayyun. Yaya Idi, Malam Munzali sai Lantan wacce dama ita ce ƴar autarsu. Sunan Yaya Babba Aisha wacce aka fi yi wa laƙabi da Indo. Ƴar uwar Marigayi Mai carbi ce ta fannin Mahaifinsa ƴar maza zar suke, an yi musu auren zumunci suka zauna anan cikin garin Ɗangwauro.
Inna Furaira ita ce matarsa ta biyu ita ma ƴar uwarsa ce ta ɓangaren Mahaifiya, ita ma auren zumunci aka yi musu sakamakon Mahaifiyar Mai carbi ta nuna itama dole ya auri ƴar ƙaninta tun da ya auro ƴar ƙanwar Mahaifinsa. Wannan dalilin ya sa aka sake yi masa aure bayan yin aurensa da shekara biyu a lokacin Yaya Babba tana goyon Baba Abubakar.
Ƴaƴan Yaya babba Shida Maza biyar Mace ɗaya. Akwai: Baba Abubakar, Baba Munkaila, Baba Sule, Baba Shehu, Baba Aminu, Baba Adamu sai Hadiza. Inna Furai tana da ƴaƴa biyar akwai: Larai, Baba Sabi'u, Baba Musa, Baba Sha'aibu sai Baba Auwalu.
Gabaɗaya waɗannan ƴaƴayen kowanne yana da tashi zuri'ar, daga cikin waɗanda ba sa cikin gidan gandun, akwai Baba Abubakar Mazaunin unguwar Na'ibawa, kuma lakcara (Lectural) ne kwalejin Sa'adatu rimi. Sai Baba Adamu.
Baba Abubakar yana da mace ɗaya Hajiya Nafisa da yara Huɗu: Aseem, Nabila, Husna da Humaira. Aseem da Humaira sunan Mai carbi da Yaya babba suka ci amma ana kiran Humaira da Ummi. Baba Adamu yana zaune a unguwar Gyaɗi-gyaɗi likitane yana aiki a asibitin Aminu Kano. Yana da mata biyu Hajiya Rahama ita ce Uwar gida tana da ƴaƴa biyu Fahad da Fatima sai Hajiya Fauziyya mai ƴaƴa uku Halifa mai sunan Marigayi Mai carbi, Zainab sai Hafsa. Sai Hadiza da Larai da suke aure a wasu gidajen.
Tsayawa zayyano wannan ahalin Marugayi mai carbi ba ƙaramin ɓata lokacin mai karatu bane.
Dawowa Labari.
Kimanin sha biyun rana da ƴan mintuna, zaune yake a cikin motarsa yana ƴan danne-dannensa. Ya kai kimanin mintuna ashirin da faka motar amma yana ciki bai fito ba. Ɗaiɗaikun yara ne suka fara zagaye motar suna kallo wasu daga cikinsu har da masu shafawa. Tsirarin ƴan mata sa'annin Dubu har da masu kallon fuskarsu a jikin mudubin motar, ganin suna niyyar yi masa ɓarna ya sa ya zuge galashin motar. Wani sihirtaccen ƙamshi ne ya fito daga cikin motar nai sanyin ƙamshi. Ƙamshinsa ne ya ankarar da su akwai mutumin da ke cikin motar. Kallon su ya fara yi kowa ya shiga taitayinsa sakamakon ganin fuskarsa ko ɗigon murmushi babu. Mugun kallon da ya wurga musu ne ya sa kowacce daga cikinsu ta kama kanta, sum sum sum suka wuce. Gajiya ya fara yi da zaman motar sannu a hankali ya zuro ƙafarsa waje tare da fitowa ya jingina da jikin motar yana ƴan danne-danne a wayarsa. Kakin sojan ba ƙaramin ƙarɓarsa ya yi ba, ya yi kyau matuƙa ga wani kwarjini da yake da shi.
Kasancear mutanen ƙofar gidan sun watse sakamakon ruɗanin da yake faruwa wasu daga ciki kuma sun tafi asibiti wurin Inna Furai.
Lambar mahaifiyarsa ya kira sai da ta kusa katsewa sannan ta ɗauka. Kamar zai yi kuka ya fara yi mata magana: "Momma don Allah ki zo ki shigo da ni banga su Daddy ba kuma na san gidan cike yake da mutane..." Bai ƙarasa magana ba Baba Munkaila ya ƙarasa wurinsa yana washe baki ya ce, "Wa nake gani kamar Soja? Soja mazan fama saukar yaushe." Zame wayar ya yi yana sosa kai ya ce, "Yanzu na ƙaraso Baba."
"Bismillah mu je ciki mana" Baba Munkaila ya nuna masa hanya. Sai da ya kulle motar sannan suka ƙarasa cikin gida.
Dubu tun a hanya su Kaltume suka tare ta da zancen baƙon da suka yi. Hura hanci ta yi kanta na ƙara girma sannan ta ce, "Wani dogo mai mota baƙa? Yau ma da kayan sojoji yazo ko?" Har rige-rigen bata amsa suke sannan ta tallaɓi ƙwaryar tsakin da ta karɓo ta fara buɗa kafaɗa tana cewa, "Ai shi ya sa nake gaya muku duk shegen da ya kawo raini wallahi haɗa shi da Yaya Aseem zan yi ya ci ubansa. " Tana gama maganar ta yi gaba. Su kuwa kowa ya yi zuru-zuru don basa manta ranar da suka taɓa ganinsa da bindiga.
Dubu cike da ɗoki ta shiga gidan don ko ba komai so take ta riƙa ƙare masa kallo tana ayyana wai shi ma ɗan uwanta ne a matsayinsa na soja. Ita ba shi yake birgeta ba illa kakinsa na soja da sautari idan zai zo garin da su yake zuwa.
Kamar wacce aka wurga tana shiga gidan ta yi ciki da Nabila ai kuwa suka fara faɗa, juyawar da Dubu za ta yi a zafafe ta sheƙawa Aseem garin tsakin da ta karɓo daga injin niƙa. Sai ga Aseem da ke cikin unifom ɗin sojoji har da hankicin ɗin goge-goge ya fito furu-furu kamar wanda ya yi wanka da toka. Gashin kansa har wani tsinin farin garin masara ya yi.
Ummou Aslam Bint Adam🌚
[7/1, 5:59 PM] My Data sim number: *DUBU JIKAR MAI CARBI*
©AMEERA ADAM
FIRST CLASS WRITER'S ASSO...
*Littafin kuɗi ne 200 idan kina buƙata za ki biya ta wannan Account ɗin Aisha Adam 3090957579 First bank ko katin Mtn, ki turo da shedar biya ta wannan lambar 07062062624.*
FREE PAGE 6
https://youtube.com/c/DuniyarHausaNovels
Ku dannan👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼 subscribe tare da alamar kararrawa domin samun shirye-shirye da sauran littafai.
Duk wannan abin da ya faru sam Dubu bata lura ba, masifa na cin ta bata san da ta sheƙa wa Aseem garin masara a jiki ba, sai ma uban tsalle da ta buga ta cukumi wuyan Nabila tana kai duka tana cewa: "Wallahi ba za ki daki banza, kwarankwasa dubu sai na koya miki hankali, hegiya tsigi-tsila da ƙafa kamar ta tsinken tsintsiya" Ganin ɗankwalin da ke kanta na niyyar kawo mata cikas ya sa ta fisge shi wurga shi ta baya sai kuwa ya sauka a kan fuskar Aseem, ban da tsami da bashi babu abin da yake tashi a cikinsa. Sai ga kitson kanta ya fito duk ya tuje hatta da tsagar kitson ta haɗe sai furu-furun amosani a saman kan.
Warin ɗankwalin ne ya doki fuskar Aseem har ya shaƙa da ƙofofin hancinsa ya sa shi farkowa daga suman tsayen da ya yi na wucin gadi. Aseem tun da ya zo duniya ba a taɓa yi masa abin da ya fusata shi lokaci ɗaya kamar abin da Dubu ta yi masa, dom shi abin daga haushi ma sai ya koma ba shi mamaki. Bakinciki da ganin yadda mutane suka zura masa ido ne ya ɓata masa rai har ya gagara sanin abin da zai aiwatar don ya wanke masa zuciya. Amma tabbas sai ya koya mata hankali don ya lura har lokacin Yaya babba ba ta ɗora ta a hanyar arziƙi ba.
Duk yanda Dubu ta so nunawa Nabila ƙarshen iyawarta abin ya ci tura don a girme Nabila ta girme ta da kusan shekara huɗu. Gudun kar a kunyatata cikin jama'a ya sa Dubu ta tattara ƙarfinta ta fara wani fisge-fisge kamar mai aljanu tana kai duka ta ko'ina, ai kuwa ta ɗaga ƙafa bisa taautsayi ta harbawa Aseem da ke saƙa da warwara akan irin abin da ya dace ya yi mata. A hassale ya ƙarasa wurinta cikin zafin nama ya fisgi hannunta. Cikin tsiwa da rashin sanin wa ya riƙe ta Dubu ta ce, "Wallahi duk wanda ya riƙe ni sai na yi masa jini da majina dalla ku sake ni wallahi ba za ta daki banza ba." Ai kuwa ya sauke mata mari a fuska, kafin wancen marin ya gama ratsa fuskarta ya sake kifa mata wani marin har sa da ta ga wasu irin taurari na gilma mata. A gigice Dubu ta buga tsalle cikin fitar hayyaci ta ce, "Innalillahi wayyo Baba Munkaila zai kashe ni wayyo! Inno fuskata."
Sauke hannun Aseem ya yi daidai da fitowar Yaya Babba za ta zagaya banɗaki. Da sauri ta saki butar hannunta ta fashe da kuka ta ƙarasa wurinsu, tana shirin riƙe hannun Dubu; Aseem ya sake fisgar Dubu ya nufi hanyar fita da ita. Duk irin kiran da Yaya Babba take yi masa ko waiwayenta bai yi ba bare ta saka ran zai tanka mata.
Duk yanda zuciyar Dubu take a bushe wannan karon sai da hanjin cikin ya kaɗa, tsoro ya mamaye ta musamman ta lura da irin ɓarin makauniyar da ta yi masa da garin masara. Suna zuwa soron ƙarshe ta yi ta maza ta fara ƙoƙarin fisge hannunta tana faɗin:
"Wai ina za ka kaini? Ka sakar mini hannu malam." Idanunsa sun kaɗa jawur saboda ɓacin rai don haka tambayar Dubu ba ƙaramin baƙanta masa rai ta ƙara yi ba. Bai tanka mata ba ya sake fusgarta da ƙarfin tsiya ya buɗe mota ya wurga ta sannan ya buɗe mazaunin direba ya zauna.
Ganin ya tuƙa mota da ya fice da gudun tsiya ya ƙara hargitsa hanjin ciki Dubu, don wannan karon har ta fara bubbuga gilashin motar tana ihu. Can gefen titi ya gangar ya faka motar sai dai uffan bai ce ba. Sai da ya share minti biyar a haka yana jin kukan da Dubu take yi da ɗan ƙarfinta, ya zaro ƴar ƙaramar bindiga ya juya yana ce mata.
"Idan baki rufe mini baki ba zan harbe ki na wurgar da banza a wurin nan." Wata ajiyar zuciya da Dubu ta sauke idan ka ji za ka yi tsammanin numfashinta na ƙarshe ne zai fita. Bata san lokacin da ta haɗiye kukanta ba, ban da raba idanu babu abin da take yi, haɗe da jin wata irin da-na-sanin zuwanta duniya. Saboda ta san da ba'a haifo ta ba babu wata ƙaddara da za ta haɗo ta shi har ya nemi kashe ta da bindiga murus ya wurgar a gefen hanya. Don tun da take bata taɓa ganin bindiga ido da ido ba sai dai ko idan tana daga moto ta hangota a hannun Sojoji ko ƴan sanda. Amma yau har ita ake yi wa iƙirarin harbewa da ita da rana tsaka. Tana son tambayarsa inda zai kaita amma tsoro ya hanata, tana cikin tunani ta ji ya sake fisgar motar da wani irin matsanancin gudu, ai kuwa ta ƙwalla uwar ƙara tare ta ƙanƙame jikin kujera.
A wannan yanayin suka ƙarasa gidan Mahaifinsa da ke unguwar Na'ibawa. Yana zuwa ya ciro mukulli ya buɗe gate ɗin gidan ya shiga da motar sannan ya buɗe murfin motar ya fisgi hannun Dubu, ai kuwa tana ganin zai shiga gidan da ita ta riƙe ƙofar gate ɗin gidan da sauri tana cewa.
"Wallahi ni ba ƴar iska ba ce da za ka kawo ni gidan nan." Maganarta ba ƙaramin dariya ta so bashi amma ya sake tamke fuska ya ce, "Ni ko ɗan iska ne an gaya miki zan yi iskanci da kucaka irinki?" Yana gama maganar ya sake fisgar hannunta aikuwa ta rungume wani ƙarfe tana cewa, "Kwarankwatsa dubu ba zan shiga ba, dama Inna ta ce ƴan iska ne suke bin maza." Tsugunnawa ya yi cikin ɓacin rai zai yi mata magana, ita kuwa Dubu tuni ta shagala da ƙarewa fuskarsa kallo don tun bayan fitowarsu ta lura da abin da yake jikinsa. Ai sai tsoro ya sake kamata saboda bata taɓa zaton haka garin masarar ya yi masara furfurar da bai shirya ba. Ta maza ya yi ya tsugunna a gabanta don wani tsami ne yake bugar hancinsa, saboda tun da aka yi rasuwa Dubu bata ƙara saka ruwa a jikinta ba. Dama wankanma sai Yaya babba ta yi da gaske take yi to rurumar jama'a ya sa ta basar ta ci gaba da harkokinta. Zaro bindigar aljihunsa ya yi ya ɗora mata akan goshinta nan take kuwa ƙirjin Dubu ya fara bugawa da ƙarfi, da hannu ya nuna mata ƙofa alamar ta shiga Dubu ta soma hawaye tana cewa, "Don Allah ka yi haƙuri idan saboda na zuba maka garin masara ne. Wallahi ban kana kusa ba."
Idan ka ji yanda Dubu take magana a ladabce za ka rantse da Allah mutuniyar kirki ce. Iya nadama Dubu ta shige ta don ta gama tsorata gabaɗaya, amma duk da haka bata jin za ta bi Aseem cikin gidan saboda ba za ta taɓa manta Baraka da ta yi ciki ba aka riƙa tsangwamarta ƙarshe sai sayar da gidansu Mahaifinta ya yi suka bar garin. Ita kuwa idan ta yi ciki ai ta san ko sama da ƙasa za ta haɗe babu wanda zai yarda a sayar da gidan Mai carbi.
"Idan kika bari na ƙirga uku ba ki tashi ba zan baki mamaki." Maganar Aseem ta farkar da ita daga dogon tunanin da ta tafi. Cikin hawaye Dubu ta ce, "Don Allah me za ka yi mini a ciki."
Banza ya yi mata yana buga bakin bindigar a ƙasa a hankali cikin sigar, idan baki tashi ba kin san sauran. Dubu bata yi ƙasa a gwiwa ba ta sake tambayarsa. Bai ɗago ya kalle ta ba ya ce, "Idan kin shiga kya gani."
"Wallahi ko me ka ce zan yi amma ni ba ƴar iska bace." Dubu ta faɗa lokacin da gumi da hawaye ya gama mamaye ilahirin fuskarta zuwa wuyanta.
"Ni ɗan iska ne." Ya bata amsa yana miƙewa a fusace ya fisgi hannun Dubu tana ihu tana fisge-fisge ya wuce da ita ciki. Yana shiga ya datse ƙofar ya wurgar da ita gefe sannan ya faɗa wani ɗaki da ke ɓarin hagu. Dukda gidan ba baƙon Dubu ba ne amma a wannan ranar gabaɗaya bata da nutsuwa. Bai jima da shiga ba ta ga ya fito da wani abu a hannunsa na dama, ɗayan hannun hagun kuma wata ƴar ƙaramar wuƙa ce, ai kuwa ta zabura kamar wacce aka ɗanawa wuta za ta gudu. Fuska a murtuke ya fisgi hannunta ya wuce da ita cikin banɗaki. A wannan karon Dubu duka ta fara kai masa tana cewa.
"Jama'a ku taimaka min zai yanka ni. Kuma ka rabu da ni na ce maka ni ba ƴar iska bace. Wallah idan ka kashe ni na rataya a wuyanka duk zunuban su Inna Furai dana ɗauka kai za a ɗorawa." Suna shiga ya sa hannu ya bige bakinta har sai da ya fashe ai kuwa Dubu ta fashe da wani marayan kuka bai bi ta kanta ba ya sa kilifar aski ya ɗora mata akan gaban goshinta. A zabure ta matsa baya ta ce, "Aski za ka yi..." Idanun da ya zuba mata ne ya sa ta haɗiye maganar ba tare da ta ƙarasa faɗa ba. Ta ci gaba da hawayen baƙinciki da nadama.
"Idan kika sake yi mini magana sai na yanke harshenki da wuƙar nan." Dubu na ji na gani haka Aseem ya sauke mata sumar kanta ban da hawaye babu abin da take yi. Kafin wani lokaci sai ga kan Dubu ya fito ral da shi babu gashi. yana gamawa ya nuna ta wuƙa hannunsa ya ce:
"Wannan da kika gani somin taɓi ne amma matuƙar kika sake shiga hannuna sai na yi miki zanen gobirawa da wuƙar nan a fuskarki." Ganin wuƙar na sheƙi ba ƙaramin razana Dubu ta yi ba, kuma a yanda ta ga babu ɗigon tausayi a fuskarsa ta san zai iya aikatawa don haka ta hau gyaɗa