Showing 1 words to 3000 words out of 23415 words
[12/27/2019, 17:59] Takori: RAYUWAR RAYHANAH 4
Duk da rashin barcin da ta samu jiya a tsayin daren baki dayansa, hakan bai hanata yin wanka karfe bakwai na safe ba, ta yi sallah ta kintsa, ta zo wajen saka kaya ta rasa wadanda ya dace ta saka. Sai ta tuna da maganar Inna jiya cewa ta yi kwalliyarta da atamfa.
Idanunta duk sun tasa sunyi ja cike da nauyin barci, domin dai shi ba a cin bashinsa a zauna lafiya.
A ranar ma test za ta yi, amma ko Alifun ba ta karanta ba, inda Allah ya taimaketa ma practical test ce (gwaji na aikace).
Karfe goma na safe suka gama ta nufo gida. Daga informatics institute zuwa gidansu babu nisa da kafarta take takowa kullum. Atamfa ce exclusive fara tas a jikinta mai ratsin shudi da ruwan goro, ta yafa mayafi ruwan goro mai girma da ka ganta ka ga cikakkiyar Nigerian.
Ganin motar su ya tabbatar mata sun shigo gidan. Sai ta rage sauri cike da jin nauyin, da wace fuska za ta dubi Daddy a yau, Ibrahim da ya haifa yana aiwatar da wadannan al’amura masu tsaurin fada a gareta? Wato sumbatar ko’ina a tareda ita? Wannan babban tashin hankaline a gareta.
Ba Daddy kadai ba, shi kansa Ibraheem din ba ta jin za ta iya hada ido da shi. Don haka take tafiya sannu-sannu, kafafunta babu kwari. Da ta iso kofar shiga gidan, sai ta kasa danna bell ta yi zamanta a kan wani ginannen verse din fulawa dake bakin kofar shiga falon nata, tana tauna gefen mayafinta da fararen hakoranta.
Wajen mintina ashirin da zamanta kofar ta bude. Inna ta fito da katuwar jakar kayanta za ta sanya a mota.
Gaban Rayhanah ya yi mugun faduwa, kar dai Ibrahim da gaske yake rabata zai yi da Singapore? After one year and a half of dedication, struggle and endeavor?
Inna ta ankara da ita a zaune ta yi salati ta yi sallallami.
“Yanzu daman kin dawo tun dazu kika zauna a nan? Rahane yaushe za ki bar kauyancin ki? Ko ni tsohuwa ba zan yiwa mijina abin da kikewa Ibraheemu ba. To kai Ibrahim fito ka dauke ta ka shiga da ita gidan.... tunda bazata iya shiga ba.”
Ai da jin haka ta zabura ta mike ta danna kai falon, idanunta basu sauka a ko’ina ba sai cikin lumsassun idon Ibraheem, wanda ke nutse cikin kushin, kafafunshi mike a kan tebirin glass mai garai-garai dake tsakiyar falon. Yana sanye da wasu shudayen Tommy hilfiger, masu ratsin ruwan toka da ruwan tokar safa a kafafunsa.
Kallon ta ya yi na minti biyu, sai ya mai da kansa a jaridar dake hannunsa. Sai ta shige bayan labule wai tana gaida Baba Dacta shi ba ma ya jiyowa sosai.
Yasa dariya ga dukkan alamu yau cikin matsanancin nishadi yake, da tabbataccen kwanciyar hankali, ya ce,
“An Rahanen Inna yau sai Chicago, Inna sai TAKAI!”
Ai ba ta san lokacin da ta fito daga labulen ba ta zazzaro ido. Ya girgiza kai yana dariya.
“Ni dai Ibraheem ka warware wannan firraqun da ka yi min da ‘yata, tunda ka zo ban ga hakorinta ba sai razana cikin fararen idanunta. Zo nan Rayhanah, daure ki zo kada ki sa in yi fushi da zuwan Ibraheem.....’’
Ta lallabo da rarrafe ta zauna gefen kujerar da yake zaune. Ya ce,
“Yaushe za ki kare test kuma yaushe zaku fara exams?”
A hankali ta ce,
“Mun gama test..... 1st April zamu fara exams ”.
Ya ce, “Masha Allahu, mu zamu wuce gida Inna za ta Takai da Albasu ta ga dangi sannan ta dawo gidanku (Farm Center) kafin ku dawo.
Za ku wuce Chicago, Ibrahim ya gama kammale-kammalen sa ya dawo gida baki daya.
Kafin nan za a san yadda za a yi a kan karatun ki, ai za ki raka shi ko?”
Idanunta narai-narai da hawaye ba tareda kwana ba ko sakayawa kai tsaye ta ce,
“A’ah”.
Hatta Inna ranta bai yi mata dadi ba da amsar Rayhanah, balle Ibraheem. Shi kuwa Dr. murmushi ya,
“Why?” (Me yasa).
Ba ta kalli inda Ibraheem din yake ba wanda ta tabbata idonshi na kanta, kunnensa na sauraron amsar da za ta bada.
A sanyaya tace.
“Na fi son na kammala karatun gaba daya mu koma gida kwata-kwata, ina son karatun Daddy, kuma na sha wahala a kansa, sannan na ci karfinsa”.
Inna ta yi tsagal cikin takaici ta ce,
“Amma ke kadai za ki zauna ko, ki auri karatu? Wallahi ba zan zauna ba, na gaji da zama cikin jajayen kunnen nan da basu san Allah basu san Annabi ba, ko kiran sallah babu, sai dai a duba agogo. Ban da wuyanki ya fara kauri yau Babanki ne zai yi umarni ki ce masa a’ah?”
Ran Inna Juma ya baci sosai, sai fada take ta inda take shiga ba ta nan take fita ba. Babu wanda ya ce uffan sai da Rahanen ta fara kuka.
Daddy ya ce,
“Inna yi hakuri, tana da ‘yar gaskiyarta.......”
“Ina wata gaskiya a nan? Boko ya fi aure? To ba dani ba, kinga tafiyata, wallahi ko kwana daya ba zan kara a garin nan ba”.
Ta kinkimi sauran kayan ta yi waje. Ibrahim ya mike ya ajiye jaridar a kujerar, ya shiga bed room din Rahanen ya bude cupboard ya soma diban wasu daga cikin kayanta.
Karfe daya na rana za su tashi zuwa Chicago a ‘American Airlines’ daga ‘Changi Airport,’ yayin da Inna da Baba Dacta za su wuce gida Nigeria.
Daddy ke lallshinta ba da fada ba,
“Ki gane Rayhanatu aure yana gaba da komai, wannan karatun ma da kike yi ai na debe kewa ne kawai saboda rashin sanin ranar da Allah zai kawo mijinki.
Don haka bai ma da amfani yanzu, ko da can da nake yin kan gaban kaina a kanki, a bisa rashin mijinki ne.
To ga shi ya zo, ragamar al’amuran rayuwarki ta fita daga hannuna tana gareshi, shi ya ce zai tafi dake ba zai barki a nan ba, don ba shi da abin yi a nan, bai ma taba zuwa ba. Rahane ke kinga dacewar ke kina wata kasa mijinki yana wata kasa babu wani kwakkwaran dalili?”
Ta girgiza kai tana share hawaye jikinta ya soma sanyi. Ya cigaba.
“To kin gani. Wani hanin ga Allah baiwa ne, da kanshi in kin kwantar da hankalinki zai nema miki makaranta a duk inda kuke, Ibraheem is a nice person.... Allah ba kwarzanta shi nake yi ba. Wata rana ke da kanki za ki gaya min hakan, lokacin da zai sunkuya yana yi muku ‘doki-sukutum’ ke da yaran ku!”.
Ta boye fuskarta cikin gyalenta tana dariya. Dai-dai lokacin da ya fito yana tura dirkekiyar troller dinta, kaya da yawa ya barsu duk da amfaninsu sabida ba zai iya kwasar duka ba sai wadanda suka zama dole.
Haka ya wuce su bai san me sukewa dariya ba. A ransa yana fadin
“Daddy ke dada sangarta yarinyar nan”.
Karfe sha daya da rabi dai-dai na safe suka kullo gidan. Landlord din ya karbi mukallansa da basu kudinsu da suka ragu a hannunsa, da yake na shekara biyu cif Daddyn ya biya, yau kuma shekara daya da watanni biyu kenan, amma Daddy ya ce ba zai karba ba ya bar masa.
Zuwa sha biyu da rabi suna kan layin screening. Karfe daya dai-dai jirgin ‘American-Airways’ ya soma tafiya a kan kwaltarshi. Yana wani irin kartar kasa. Rahane na share hawaye tana kallon dogayen gine-ginen kasar Singapore da suka soma kankancewa yanzun a idonta, a sabili da daidaito da jirgin ya soma a kan gajimare duk da bai keta hazo ba, tana fadi cikin ranta,
“Bye-bye Singapore...... Bye-bye Informatics!!!”.
Karfe biyu na cika suma su Daddy KLM ya lodosu zuwa Nigeria bayan yayi transit dasu a India.
*****
RAYHANAH A CHICAGO
Sanda suka sauka a babban filin jirgin saman Chicago ruwan sama ake yi kamar da bakin kwarya. Kalma wannan bata shiga tsakanin Ibraheem da Rayhanah ba.
Domin dai har zuwa lokacin zuciyar Rayhanah ba ta yi sanyi ba da wannan yankan kauna da Ibraheem ya yiwa karatun ta, karatun da ta sha bakar wuya a kanshi, ta kuma ciwa buri mai yawa. Rahane ta dauki wannan karatun matsayin madafar rayuwarta ta wata rana.
A kullum tana tuna maganganun Babanta ne da ya ce, ta yi kokari ta dinga tunawa a ko’ina ta tsinci kanta, ita ba kowa ba ce.... ba ‘yar kowa ba.... ba ‘yar kowan-kowa ba....face talaka ‘yar talaka. Jikar talaka. Tayi kokari ta tsaya da kafafunta. Kuma kar ta zurfafa buri.
Don haka wannan karatun shikadai ne burinta a rayuwa.
Tana da burin zuzzurfan ilimi domin cin gajiyarsa wata rana, tunda su ma su Daddyn alfarmar ilimin suke ta ci har su ma suka samu suka rabesu ana ci tare da su.
Har yau zuciyarta ta gaza sallamawa zuwa ga karbar Ibraheem matsayin mijinta balle wani matsayi na soyayya ko akasinta a gareshi gaba daya.....domin a ganinta ya fi karfinta, ta dai yi kokari ta cire Yaya Khalipha a ranta, amma ta kasa cike gurbin da Ibraheem.
Rahane ba ta gama firgita da al’amarin Ibrahim din ba sai da ya sanya mukulli ya bude wani American-Villa suka shiga har ciki da motar asibitin (Illinois) wadda ta kwaso su daga airport da chauffeur guda, mota ta alfarma da bata taba shiga irin ta ba ko a Singapore.
Gajiyar dake tare da ita ba ta hanata fara yin sallah ba sannan ne ta ji ta sakayau. Ibrahim na waje da makotansa mutanen Sri Lanka suna yi mishi barka da zuwa, kafin ya sallamesu ya shigo Rayhanah ta yi barci a falon cikin kujera da kayan jikinta ba ta nemi ko da bed-room ba.
Ya dade tsaye a kanta hannunshi cikin aljihun dogon wandon Armani dake jikinsa da bakar rigar sanyi mai kauri, a yadda ta yi kwanciyar, za ka fahimci sanyi take ji, ta cure ta dunkule jikinta cikin gyalenta wanda ba wani kauri ne da shi ba.
Kallon ta kawai yake al’amuran da suka shude shekaru goma sha biyu a baya na dawo mai filla-filla. Yarinya mai yawan jin kan mahaifi, da nuna mishi sadaukarwa. Mai hakuri da Abida, da rashin mutuncin ta. Mai son Azizah da yin biyayya ga Mami.
A saninsa Mami na son yarinyar, amma me yasa ta hana aurenta da Khalipha? Zuciyarshi ta yi saurin halarto da amsa (saboda wani baya auren matar wani). Shi mijin aure tun ranar da aka haifeka aka rubuta maka shi a allon da baya kankaruwa (Lauhul-Mahfuz).
Khalipha fari sol mai kyawun da za a likashi a goshi, me yasa yake son Rayhanah? Baka..... not so much attractive...... Ba kowane namiji ne ya san darajar mata irin Rahane ba, sai su likitoci da suka san amfanin kowacce gaba da aikin kowacce halitta ta dan Adam.
Wannan Rahanen, ya sha matukar wahala kamin ya manta da ita da al’amarinta bayan barowarsa gida.
[12/28/2019, 12:34] Takori: ‘She’s that something which goes far beyond mere or casual assumption!’ Da ya yakice yayi fata-fata da shi daga zuciyarsa a isowar sa Chicago, wato shekaru goma sha biyu a baya kada ya zamo hindrance ko obstacle ga cigaban rayuwar sa da kyakkawan kudurin da ya fito da shi daga gida.
Dadin dadawa a lokacin ya kalubalanci kansa kan damuwa da al’amarin ta da cewa tausayi ne kawai. Me take da shi da za’a so ta akan shi a lokacin banda deficiencies and inefficiencies? (Tarin nakasu).
A tsarin halitta da dabi’a (personality) irinta yake burin samu.
Abin nufi, baya son macen data cika kyau, baya son farar mace, baka yakeso ‘yar uwarsa, baya son mace mai kyale-kyale da artificial beauty, baya son wadda ta waye da yawa, baya son mai budadden ido, baya son wadda suka hada alakar jini, baya son yar masu kudi ko masu mulki duk da baya son ‘yar talakawa likis.
Ya sani ba wanda ke samun rayuwa ko abokin rayuwa 100%da burinsa. Don haka zai iya cewa ya samu Rayhanah 80% da burin da ya dade yana ciwa abokiyar rayuwar sa.
Da yake Allah ya rubuta matarshi ce ga shi ya biyoshi da ita har inda yake. Ba da yunkurin shi ba, ba da motsin sa ba, ko wani kokarin sa. Sai don kasancewar al’amarin su rubutaccen al’amari.
Sai dai har yanzu ba zai iya sakin jiki da Rahane ba, ba don komai ba sai don cewa.... bai yarda da akwai soyayyarsa a zuciyarta ko da digo daya ba, kawai dai an fi karfinta ne ita kuma ta yi biyayya......
Amma Khalipha take so, tunda har maganar aure ta shiga tsakaninsu. Allah kadai ya san irin soyayyar da suka yi kafin zancen aure ya shigo ciki.
In haka ne ta yi kadan ya mika mata dimbin soyayyar da ya tanadarwa matarsa alhalin ita ba son shi take yi ba. Sai dai ya yi mamakin yadda ya kasa sarrafa kansa a kanta the very first day of their encounter....(rana ta farko da haduwarsu) har kuma yanzu haka abin yake, amma zuciyarshi na ta karyatawa da kalubalantar hakan da gangan.
Haka ya ci gaba da tsayuwa yana kallon ta yana kissima abubuwa da yawa..... zuciyarshi na azabtar da shi a kan tunani mara tushe da makama (kishi akan abinda bai gani ba).
Motsi ta yi don ta gyara rufarta, sai ta ji alamun tsayuwar mutum a kanta, ta bude idanunta a hankali sai cikin na Yayan, idanunta sunyi kalar da ba zai iya jurewa kallon cikinsu ba tare da ya kara karyata kansa ba.
Don haka shi ya fara dauke idonsa da hanzari ya wuce bed room ya sakarwa kanshi shower. Sanda ya fito falon cikin shiri ne na bakaken suit da jibgegiyar rigar sanyi, kanshi babu hula, sumar nan ta yi luf a kanshi har sheki take na alamar ta kara ganin ‘ArganaVita’.
Nan ya taddata inda ya barta a yadda ya barta. Haushi ya tokareshi bai san cewa ita ma haushin nasa take ji ba.
Don haka yana hararar ta ita ma tana dan harararsa da karshen idanunta, ta yi kicin-kicin da fuska duk sai ta bashi dariya.
Ya girgiza kai ya ce,
“Ni kike harara ko Rayhanah?”
Ta zumburo mishi ‘yan tausasan lebbanta gaba, abinda Ibrahim baya iya jurewa gani kenan (those luscious lips) ba tareda ya karya ta kansa ba, don haka ya yi sauri ya kawar da kansa.
“Dube ki da Allah ba wanka ba sallah kina ta shirgar barci, to wallahi ba zan dau wannan ba. Nan ba Inna ba Daddy sai in yi kuli-kulin-kubra dake ba wanda zai cece ki. Mintuna ashirin na baki kafin in dawo in ganki yadda na soma ganinki, in ba haka ba, na rantse..... ni dake ne a gidan nan.......”
Ya sa kai ya fita. Ta bishi da kallo tana mamaki tana harararsa. Mamakin da take yi shine, yadda duk ta zaci al’amarin ba haka ya zo ba, ta dauki Ibrahim din tuntuni a wani mutum mai raini da wulakanci.
Ba za ta taba manta labarin data ji Daddy na baiwa Inna Jumah ba a (farm-center) suna hira ne inda yake gaya mata dalilina na hada auren Rayhanah da Ibrahim shine halayen Ibrahim duk irin na Rayhanah ne wato miskilanci don haka yake da tabbacin zasu ji dadin zama da juna, yana bata labarin ranar data bude idanunta daga hatsarin da sukayi ita da Iya.
Daddy ya ce ya ba ta tea ta sha a AKTH ya yi baya ya buya ya tura Eric Epatobe wani abokin karatunsa baisan cewa Daddy na ganin sa ba.
Tana kuma iya tuna ranar da Abida ta kifa mata pampas na kashin Aziza a fuska ya zo ya gani bai ce komi ba, bai nuna komi ba, bai wa Abida koda fada ba. Sai YAYA KHALIFA ne yayi hakan.
Tun zuwanta gidansu kafin ya bar gidan, kalma wannan koda ta gaisuwa ce bata taba hadasu ba.