Showing 27001 words to 27521 words out of 27521 words

Chapter 10 - Asp Zarah Book 2 Hausa Novel Complete

Unknown   

01 Jan 2025

114

ta haihu ƴan biyunta macw da namiji kyawawa masu kama da ubansu. Farin ciki kuwa ba'a magana a gurin dangi. Nan aka fara cika gidan ƴan uwa da abokan arziki kowa na zuwa ganin ƴan biyu.

Ranar suna kuwa ansha mamaki kwarai sunan da M.J ya sakawa yaran, macen Fadimatul Zarah namijin kuma Safwan inda za'a kirasu da Amrah da Amran. Mutane da dama sun jinjina wannan abu da ya yi, ita kuwa Zarah tayi farin ciki matuƙa har ta kasa ɓoye hakan.

Mai Martaba da kanshi sai da yazo ya yi godiyar wannan kara, inda yawa yara kyautan manyan filaye guda biyu bayan kuma kaya da aka kawo musu.
Yara sunzo da goshi dan sun samu kyaututtuka da dama na ban mamaki.

Kulawa sosai suke samu daga wajan iyayensu da sauran dangi. Musamman mahaifinsu ma daya ɗaura son duniya akansu.

Haihuwar Zarah ba da dadewa ba aka yi auren Sadiq wanda ya tara manyan mutane sosai sannan an kashe kuɗi sosai.

A haka rayuwa ke tafiya awanni na shudewa su bada kwana daga nan satika har watanni.


Watarana su Zarah sun fita shopping, a hanyar dawowarsu ne suka kusa kaɗe wata almajira, ko da suka fita suka duba ba kowa ba ce face Hajara, ƙafarta ɗaya an guntule sai sanda take amfani dashi. Ko da ta ganesu nan ta durƙusa tana basu hakuri sosai tana basu labarin abubuwan da suka faru da ita dan har prison sai da aka kaita sanadin wannan Alhajin daya mata ciki, gashi iyayenta ma duk basu da lafiya suna kwance ƴar uwarta ce kawai ke taimaka musu itama mijinta ya ɗauke ta sun bar ƙasar.
Sun tausaya mata sosai nan M.J ya mata kyautar maƙudan kuɗaɗe bayan sun yafe mata.

Shekararsu Amran ɗaya da watanni mahaifinsu ya kwanta ciwo zazzabi me zafi ya rufe shi, ba shiri ya ɗauki Zarah suka tafi asibiti aikuwa kamar yadda yayi tsammani tana da shigar ciki na wata biyu murna ce ta kamashi ita kuma Zarah ta nuna sam bataji dadi ba saboda yaranta basuyi girman da za'a yayesu duk da dai babu inda basa zuwa da ƙafarsu sannan kuma suna cin abinci sosai.
Shawarwari likita ya basu na yadda zata kula dasu kafin cikin nata ya girma. Da haka suka dawo gidaa.

Sanda Ammi taji labarin cikin Zarah ta kanta ta shiryo ta taho Nigeria ta ɗauki su Amran ta wuce Egypt da su dama kuma yaran sun santa gashi basa da kiwa ko kadan dan haka ne bata sha wuya da su.

Tabar M.J yana cigaba da rainon cikin matarshi da a yanzu ma yake fatan ta haifo mishi ƴan biyun.


*KARSHE*


*ALHAMDILILLAHI NAN NA KAWO KARSHEN WANNAN LITTAFI NA ASP ZARAH, ABINDA NA FADA DAIDAI ALLAH YA BANI LADARSA INDA NA KUSKURE KUMA INA ROƘON ALLAH YA YAFEMIN.*
*MASOYA INA GODIYA SOSAI DA IRIN ƘAUNARKU A GARENI, ALLAH YA SAKA DA ALKHAIRANSA YABAR ZUMUNCIN DAKE TSAKANINMU. INA GODIYA SOSAI DA HAKURIN DA KUKAYI DANI TSAWON WANNAN LOKACIN. SON SO FISSABILILLAH*


*KU TSUMAYE NI A LITTAFINA NA GABA DA ZAI FARA ZUWA MUKU NAN DA WANI ƘANƘANIN LOKACI ME SUNA AL-MUSTAPHA. FREE BOOK NE NAYI SHI DOMIN KU MASOYA, YAZO DA SALO NA MUSAMMAN KADA KU BARI A LABARTA MUKU*.



*TAKU HAR KULLUM*
*JASMINE🌸🌸*

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login