Showing 6001 words to 9000 words out of 27521 words
damu ba ta koma inda take zaune da ta cigaba da aikinta.
Zamanta ke da wuya ta ji an hayaniya da kururuwar Hajara a babban falon tare da sallallami da M.J ke yi, take ta gane cewa wasu sun shigo cikin gidan, da sauri ta miƙe ta ɗauki jacket ɗinta ta saka sannan ta zari ƙaramar bindigarta ta nufi falon. Ai kuwa kamar yadda ta zata mutane ne a falon su tara kowanne da shiga mai kyau fuska a rufe, uku daga cikinsu ne kawai maza amma duk sauran mata ne, ganin fitowarta ne yasa wasu mata su huɗu suka nufeta da nufin rikota, wani wawan naushi ta kaiwa waɗanda ke da nufin riƙe mata hannu da duka hannuwanta biyu sannan ta sunkuya ta kaiwa wacce take gabanta naushi a ciki take ta durƙushe saboda zafin da taji. Sai dai kafin ta kuma wani yunƙuri wasu suka tura ta ta faɗi ta gaba kafin ta ɗago suka yi nasarar ɗaure mata hannaye. Ɗaya daga cikinsu ne yayi maganar su ƙyale Zarah haka sannan ya juya ya kalli M.J ya ce
"Ran matan ka ko kuma dukiya.?"
Cikin kauda kai M.J dake riƙe a hannun ƙarti biyu da mace ɗaya yace
"Malam ni matata ɗaya ce kuma gata nan" ya nuna Hajara sannan ya cigaba da cewa" Ku kama wacce ta muku laifi ku rabu da mu."
Dariya yayi sannan yace
"Ya za'ayi mu yarda da hakan bayan a mun shaida ɗaurin auren ku."
Shiru yayi na wasu mintuna sannan yace
"Idan kuna so ma zaku iya shaida warwarewarsa."
Cike da dariya mugunta ya kuma cewa
"Mai zai hana kuwa."
Cike da takaici Zarah tace
"Yaya Jawwad kada kayi abinda zaka zo kana da na sani, ina da rauni sosai sannan ni marainiyace. Kada ka lalatamin rayuwa ta hanyar maida ni ƙaramar bazawara."
Bai kula da maganganunta ba ya ce
"Na sake ki saki ɗaya Zarah."
Tabbas mutuwar aure babu daɗi ko da babu soyayya wannan dalilin ne yasa Zarah taji zuciyarta tayi mata zafi sosai lokacin da ɗan'uwanta ya furta kalmar saki a gareta.
"Kinsan abinda ya kawo mu dan haka ki bamu salin alin saboda yau zamu yi ta mukare tsakanin mu da ke." Mutumin ya kuma faɗa batare da ya kula da halin da take ciki ba, kauda kai tayi gefe tana addu'ar Allah ya bata nasarar kunce kanta duk da suna da yawa tasan zata iya musu mugun lahani ba tare da makami ba ma. Saura ƙiris ta fasa ƙara saboda wani gigitaccen zafi daya ziyarce ta a gefen cinyarta, kallonta ta maida gurin taga ashe ɗaya daga cikin matan nan ne ta yi mata muguwar yanka a cinyarta take kuwa jini ya ce dama hanya nake nema nan ya fara zuba tamkar kwararo shi ake yi, raɗaɗi take ji sosai amma hakan bai sa ta amsa tambayar da ya kuma mata ba, ya ce
"Ba zakiyi magana ba ke wace iriyar yarinyace mai taurin kai ne, mtsssw ku shiga ku bincika min ko ina a cikin gidan nan."
Dukkansu suka nufi hanyar da suka ga Zarah ta fito mutum uku kaɗai suka bari biyu na tsare da M.J da Hajara sun saka musu bindiga akai sai babban dake gefen inda Zarah ke ɗaure yana wasa da wuƙar hannunshi yayinda ɗaya hannu ke rike da bindiga. Kusan mintuna arba'in suna dube-dube a cikin gidan amma basu ko ga wata alamar da zata nuna musu cewa Diamonds ɗin suna cikin gidan ba, cike da rashin kwarin gwiwa suka dawo suka sanar da shi, bai ce komai ba ya zaro waya ya daddanna sannan ya kara a kunnenshi jim kaɗan ya fara magana yace
"Yallaɓai jiya i yau fa, taurin kan yarinyar yayi yawa ta tushe kowace hanya bata bamu damar sanin komai ba."
Huci ya furzar mai zafi kana yace
"Wannan karon inaso ku taɓa Zarah, ina so taji a lafiyarta cewa ba'a gardama dani, ina so taji lallai cewa bazata iya cigaba da ajiyar Diamonds ɗin nan ba, lallai ku yi mata mummunan lahani kamar yadda zuwa yanzu na tabbatar idan Raliya tana raye to tana cikin mawuyacin hali."
"Angama ranka ya daɗe." daga haka ya katse wayar ya kalli matan dake tsaye ya ce
"Ku cika aiki" tamkar suna jira haka suka ruftu su biyar akan Zarah kowa da irin dukan da yake kai mata amma duk da haka ko tari bata yi ba bare ayi tunanin zatayi kuka.
Karo na farko Hajara taji mugun tausayi da dana sani sun baibayeta, ciwon ƴa mace na ƴa mace ne, sosai taji da na sanin haɗa kai da ita da akayi tun farko har zuwa yau da suka shigo cikin gidan nasu. Shikuwa M.J ba yadda za'ayi ka gane yanayin da yake ciki domin fuskarsa tana nan yadda take.
Cikin mintuna ƙalilan farin tiles ɗin dake falon ya fara rinewa yana yin ja saboda jinin dake gangarowa daka jikin Zarah sakamakon bugu da yanka da suke jikinta, ganin kamar ta daina numfashi ne yasa ya dakatar da su sannan suka fice a gidan.
Da hanzari Hajara ta rarrafa ta isa kanta hawaye na biyowa a idanunta ta juya ta kalli M.J ta ce
"Hubby ɗauki key da sauri mu kaita asibiti."
"Ni? Asibiti? Babu inda zan fita da daren nan, ita ta jawo wa kanta."
"Ka dubi halin da take ciki mana dan Allah ka taimaka."
"Yaya Jawwad dan Allah ka kiramin Daddy ko da bazaka kai ni asibitin ba." Zarah ta faɗa a galabaice, numfashinta na fita ɗaiɗai.
Bai kula ta ba ya zo yaja hannun Hajara suka nufi ƙofar part ɗin shi, tsayawa yayi cak! Sannan ya dawo ya tsugunna a gabanta yana ƙare mata kallo shi kansa yasan tana buƙatar taimako na gaggawa amma yana jin zafinta sosai a ƙasan zuciyarsa, gyaran murya yayi sannan yace
"Kinsan yanzu babu igiyar aure tsakanina dake, dan haka zan taimaka miki ne kaɗai a matsayin karuwar da nakeso ta tuba ga Allah kafin ta mutu, wannan ne kaɗai gatan da zan miki, kin amince na taimaka miki.?"
"Zan fi ƙaunar na mutu a haka matukar da wannan ƙudurin zaka taimake ni, na tsane ka, baka da tausayi ko kaɗan, kai mara imani ne."
Kafaɗa ya kaɗa ya mike sannan yace
"Duk yadda kika gani sai ki kira wanda kike jin shi zai iya taimakonki ko a cikin abokan watsewarki ne." daga haka yaja matarsa suka shige suka barta a nan kwance.
Cikin dakiya da juriya ta miƙe zaune tana jan jiki harta isa ƙofar da zata sada ta da farfajiyar gidan cikin tsananin azaba da ciwo.
A firgice ta miƙe daga baccin da take yi, juyawa tayi ta kalli agogo 2:05am kallonta ta maida kan Saleem dake sharar baccinsa hankali kwance, a hankali ta fara bubbuga bayansa har ya farka ya buɗe idanunsa ganinta a zaune ne yasa shima ya zauna yana miƙa ya kalleta yace
"Lafiya kuwa me ya same ki.?"
"Sa-Jid nayi mafarki Zarah na ta kirana tana faɗin na taimaka mata, zuciyata da jikina sun amsa bana jin daɗi sam ina da tabbacin cewa akwai abinda ke faruwa da ita."
"Me zai faru da ita da wannan daren haba dan Allah mafarki fa ba gaskiya bane."
"Na sani amma dai wannan yayi kama da gaskiya, miƙomin wayar can na kirata."
Hannu yasa ya ɗauko wayar dake kan bedside drawer ya bata, cikin hanzari ta fara danna lambar Zarah tana kira amma kusan kira 30 babu amsa. Zuwa lokacin ta gama ruɗewa, kuka ta sakawa Saleem akan lallai sai ya kaita gidan Zarah a daren duk yadda yaso ta haƙura amma taƙi, sanin da yayi cewa idan damuwa zata iya jawowa ƙaramin cikin dake jikinta matsala ne yasa dole ya miƙe ya zura jallabiya ya ɗauki key ɗin motar suka fice a gidan, har zuwa lokacin kuma bata daina kuka da sambatu ba...✍🏻
*BY*
*JASMINE*🌸🌸
*ASP ZARAH*
*BOOK 2*
*Page 5*
... Su uku ne zaune a cikin wani ƙayataccen falo da yaji kayan alatu tamkar na shugaban ƙasa Sadiq, Rahma da kuma Zarah, kallo ɗaya zaka musu ka gane suna cikin tsantsar farin ciki da suka daɗe basu samu ba duba da yanayin yadda fuskokinsu suka kasa ɓoye farin cikin da suke ciki. Rahma ce ta ajiye cup ɗin dake hannunta a center table ɗin dake gabanta sannan ta juyo ta dubi Sadiq dake nunawa Zarah abu a waya suna ƙyalƙyala dariya ta ce
"Bazan iya tuna ranar ƙarshe da naga dariyarku haka ba musamman Zarah."
"Ba mu da wata sauran damuwa ne shiyasa ki ka ganmu haka, ke ba abin farin ciki bane a gareki ace yau wanda yayi sanadin da iyayenmu suka bar duniya shima ya mutu ta dalilinmu, baya ga haka ƴar'uwar mu wacce muke tunanin ta zauce yau ta samu lafiya ingantacciya, kinga kuwa dole mu yi farin ciki." Sadiq ne yayi wannan sharhin bayan ya maida hankalinsa kanta.
Gyaɗa kai tayi ciki da gamsuwa tace
"Haka ne amma naku ne kawai ke fitowa fili, nawa na barshi a zuci."
Zarah waccw tun da aka fara maganar bata tanka ba ta ɗago tace
"Meye zai hana ki fito dashi fili mu haɗu mu yi murnar tare."
Cike da zolaya Rahma tace
"Yau kam naci girma na bar muku."
Ɗaya daga cikin ƙananun pillows ɗin dake kan kujerar Sadiq ya ɗauka ya jefeta da shi cikin harara yace
"Ke banson raini fa"
Itama cikin zolaya tace
"Kwanaki ƙalilan a ne tsakaninmu fa."
"Duk da haka dai ya riga ki shaƙar iskar duniya." Cewar Zarah.
"Haka ne toh na baka girman ka, yanzu daga nan ina zaku wuce."
Shiru sukayi na wani lokaci kafin Sadiq yace
"Daga nan Malasia zamu wuce, Little zata fara karatun masters ɗinta acan, ni kuma na cigaba da aikina."
Fuska ta sauya kamar zatayi hawaye tace
"Za mu ƙara yin nisa da juna.?"
"Ki shirya mu tafi tare." fadin Zarah.
Hararar wasa ta mata sannan ta kuma cewa
"Na gaji da kawaici fa, tun ɗazu inaso ku ɗauko min hirar abubuwan da suka faru amma kun share."
Dariya suka yi duka sannan Sadiq yace
"Tun ɗazu na lura dake kawai na yi miki shiru ki furta da bakinki."
"Na tambaya yanzu a gayamin meya faru."
"Labari ne mai tsawo fa ki nemo biro da takarda" Inji Zarah.
"A'a bani wannan baiwar sai dai na kira Sis Jasmine ta mana aikin rubutun."
"Tom shikenan haka za'ayi."
"Ke nake sauraro."
🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸🩸
Ina cikin tsananin azaba a wannan rana da yaran Alpha suka shigo har gida sukamin rauni amma Yaya Jawwad yaƙi ko kula da lamarina bare yayi tunanin kaini asibiti duk da a lokacin babu dangantakar aure a tsakaninmu amma nayi tunanin zai taimakeni a matsayi na na ƴar'uwarsa sai dai hakan bai kai ga ci ba. Ganin sun bare yashe a falo cikin jini ne yasa nayi ƙoƙarin nafara jan jiki domin zuwa na saka Baba Mai gadi ya kiramin Daddy ko Sa-Jid saboda a halin da nake ciki a wannan lokacin nasan komai zai iya faruwa dani sakamakon jinin da ke zuba daga jikina, da jan jiki na fita har farfajiyar gidanmu zuwa ɗakin Mai gadi sai dai nayi rashin sa'a domin shima sun yi mishi duka bai san inda kansa yake ba. A lokacin nafara ficewa daga hayyacina saboda tsananin azaba da zafin raunukan dake jikina, ina cikin wannan halin ne naji ana horn a ƙofar get ta waje amma bani da kuzarin da zan iya xuwa na buɗe, an daɗe anayin horn ɗin daga baya kuma akazo jikin ƙofar ana bugawa, ganin gate ɗin a buɗe ne yasa su shigowa ba kowa bane illa Sa-Jid.
Ko da suka shigo da ni suka fara yin arba a kwance cikin jini ai kuwa hankalinsu ya tashi sosai domin saida Jiddah ta suma dakyar ya samu ta nutsu kaɗan sannan ta taimaka mai suka shigar da ni cikin motar ba su ko kula da mai gadi ba bare su ɗauke shi mu tafi asibitin a tare saboda tsananin firgici da suke ciki. A guje Saleem ya ja motar muka bar cikin anguwar muka nufi hanyar asibiti, gudu yake yi tamkar zai tashi sama saboda azalzala da Jiddah ke yi masa, ni dai a lokacin sama-sama nake iya jiyo maganganunsu saboda zafin raunukan dake jikina da kuma jinin da har a lokacin bai daina zuba ba. Cak! Motar ta tsaya taƙi yin gaba ko baya duk yadda Saleem yayi ƙoƙarin ta motsa amma taƙi hakan ne yasa ya fito daga cikin motar cikin tsananin mamaki domin yasan motarsa lafiya lau take sannan akwai mai sosai a ciki, buɗe-buɗe ya fara yi yana dubawa ko zai ga ta inda matsalar take amma bai fahimci komai ba, ganin haka yasa itama Jiddah ta fito a motar tana taya shi dubawa ko zasu gano matsalar motar. Kamar wanda aka umarta haka ya sunkuya ƙasa tare da leƙa ƙasan motar, abinda ya gani a gurin ne ya matuƙar bashi mamaki, bakomai ne ya hana motar tafiya ba illa wani littafi ƙaramin dake ƙasan tayar gaba na hagu, cikin al'ajabi ya sa hannu ya zaro littafin da ƙarfi, cikin zarewar idanu ya nunawa Jiddah littafin wanda a bango cikakken sunana ne a rubuce cikin rubutu mai matuƙar kyau. A wannan lokacin bana tsayawa wasu maganganu bane saboda halin da nake ciki hakan yasa Saleem ya ajiye littafin a gaban motarsa zuwa lokacin da zan samu kaina. Bansan abinda ya faru ba domin a lokacin juriyata ta ƙare tuni na sume, a haka muka isa asibitin cikin gaggawa, ba mu sha wahalar samun likita ba domin a wannan asibitin Jiddah ke aiki sannan ita ke dubani lokuta da dama idan kalar hakan ta faru, a wasu lokutan ma bama zuwa asibiti idan zamana a asibiti na da hatsari.
Emergency room aka shigar dani, nan da nan Jiddah da wasu likitoci biyu tare da nurses suka duƙufa domin ceto rayuwata, sai bayan da aka idar da sallar asuba'i kafin numfashina ya daidaita bayan sun gyaramin raunukan dake jikina sannan nasha ɗinkuna a waɗanda ke buƙatar ɗinki. Daga haka aka yimin alurar bacci sannan Jiddah da kanta ta turani ɗakin hutu. Sai a lokacin ta samu sukunin kiran Daddy ta shaida mishi abinda ke faruwa, ba'ayi mintuna ashirin ba kuwa sai gasu a cikin asibitin gabaɗayan su harda Baaba, ganin yanayina kuwa ta matuƙar ta da musu da hankali nan suka tambayi abinda ya faru, Saleem ne kaɗai ya iya buɗe baki ya musu bayani tun daga kan farkawar Jiddah daga bacci har zuwa lokacin da nake kwance bansan me ke gudana ba.
Sun shiga damuwa sosai musamman Baaba da a lokacin take tunanin na mutu ne ake ɓoyewa, shi kuwa sarkin zuciya Sadiq ya kasa furta ko kalma ɗaya amma kallo zaka yi masa ka gane yana cikin tsananin damuwa da ɓacin rai duba da yadda idanunsa suka sauya kala zuwa jajaye sannan kyakkyawar farar fuskarsa ta rine tana nuna alamun ɓacin rai. Haka suka zauna shiru har ƙarfe goma na safiya amma ban farka ba wannan dalilin ne yasa Momi da Daddy suka nemj komawa gida domin taho da abinda ba'a rasa ba na buƙatar majinyaci domin ita kam Jiddah ta ce babu inda zata motsa sai taga farkawa ta, tana gefen Baaba a zaune acan wata kwanar ɗakin suna sharar kwalla lokaci lokaci.
Duk cikinsu babu wanda yayi tuna M.J bare ayi tunanin abinda ya hanasa zuwa a matsayinshi na mijinta, Sadiq ne kawai ya farga ga haka tun lokacin da yazo baiga M.J a wajen ba yasan akwai wata manaƙisar a ƙasa saidai ya share saboda jiran farfaɗowata amma cikin ranshi ya ɗau alwashin cin zarafin M.J matuƙar ya bincika ya samo da sa hannunshi a cikin abinda ya faru dani.
Wani abu da nafara manta wanzowarsa a cikin shafin rayuwata shi ya sameni a lokacin da nake tsaka da baccin dole da likitoci suka sani yi sakamakon allurar baccin da akamin, duk da daɗewar shekaru amma ko a ina naga wannan fuskar zan ganeta, kinsan wacece?"
Rahama dake sharar kwallar tausayin ƴar'uwar tata ce ta girgiza kai alamun a'a domin ba zata iya bude baki tayi magana ba, tabbas ta daɗe bataji ko a labari ba wacce ke da irin ƙaddarar Zarah, domin da ta fita daga wannan take kuma shiga wata batare da ta warke ƙuncin da ke ranta ba.
Numfasawa Zarah tayi sannan ta cigaba da cewa.
Ba kowa bace face Almajirata wacce na daɗe da fara manta abinda ya gudana a tsakaninmu, ina tsaka da wannan baccin nayi mafarkinta ta zo min tana hawaye tace
"Kamar yadda na ɗaukar miki alƙawarin cewa zan barki a baya amma zan kuma dawowa domin taimakonki, Batula ban taɓa nesa daga inda kike ba saidai kawai ina ɓoye kaina ne saboda alƙawarin da na miki na rashin bayyana a gareki. Sai dai a yau na bayyana gareki ne domin taimaka miki akan abinda kw jefa rayuwarki cikin ƙunci. Ki riƙe wanna littafin duk wasu bayanai da zaki buƙata na Alpha yana ciki baki da buƙatar zuwa wani waje domin samo su." Ta ƙarashe maganar tana mikomin wanj ƙaramin littafi dake hannunta, cike da rauni na miƙa hannu na karɓa ina kallon jikin littafin, ɗagowa nayi da nufin tambayarta saidai kuma banganta ba. A daidai nan na farka daga baccin a firgice ina faɗin "Kin bani littafin.?" a gaggauce Jiddah ta matso kusa da ni ta riƙeni tana ƙoƙarin maida ni na kwanta.
Bansan abubuwan da nake furtawa ba a lokacin sai dai naji Jiddah na faɗin
"Littafin yana cikin motar Saleem bari na kira shi ya shigo miki dashi." daga haka na maida kaina ina sauke numfashi a hankali. Shuɗewar mintuna goma ne ya dawo dani hayyacina, a lokacin ne kuma na fara jin raɗaɗin raunukan dake jikina, haka nayi ta daurewa har zuwa lokacin da wata Nurse ta shigo, ganin idona biyu ne yasa ta kuma suka dawo da likita ya ƙara duddubani tare da tambayata inda kemin ciwo, nan na faɗa mishi ina jin zafin raunukan jikina cikin sanyayyar muryata ta marasa lafiya, take ya haɗa allurai yayi min sannan suka fice a ɗakin suna mai ƙara yimin addu'ar samun sauƙi.
Fitarsu ke da wuya Baaba da Jiddah suka ƙaraso kusa da gadon nawa suna jeramin sannu kamar zasu aro baki, da taimakon Jiddah na samo na miƙe zaune bayan ta saka filo a bayana na jingina da gadon, zafin da nakeji ya ragu sosai sakamakon allurar rage zugi da akamin, wannan ne ya bani damar yi musu ƴan tambayoyi game da mutanen da nake da