Showing 21001 words to 24000 words out of 27521 words
yi dan haka ne take jinta tamkar ta sauke wani icce mai nauyi akanta.
A matuƙar gajiye ta isa gidan nasu, falon shiru kamar ba kowa a gidan sai dai ta jiyo motsi a kitchen wanda ke tabbatar mata Mama Jamila ce dake sunan da take kiranta dashi kenan.
Jakar hannunta ta wurga kan kujera sannan ta zauna ta tsiyayi ruwan da ta gani a center table ta kafa kai tana sha, ƙarar da wayarta keyi ne yasa ta ajiye kofin ta ɗaga kiran cikin mamakin wanda ke kiran.
A zabure ta mike jin abinda aka faɗa cikin wayar....✍🏻
*BY*
*JASMINE🌸🌸*
*ASP ZARAH*
*BOOK 2*
_About to end_🥰
Wani irin tsalle ta daka tare da ihu sannan ta tsagaita ta ce
"Wayyo Allah na zama uwa Sa-Jid me muka samu ne."
Daga ɗaya ɓangaren Saleem yayi dariya kana ya ce
"An samu baby girl"
"Masha Allah, a gaida Baby da mamanta. Allah ya raya mana ita bisa tafarkin addini. Zan taho zuwa jibi insha Allah."
"Ahh har kin gama jarabawar ne."
"Wallahi na gama ɗazu, idan ta tashi kace zan kirata."
"Tom sai anjima."
Wani daɗi take ji a ranta tana yiwa Allah godiya daya sauki Jiddah lafiya, inda tayi farinciki ma ta gama jarabawarta dan haka tafiya Nigeria bazai mata wuya ba.
Lambar Sadiq ta kira ta shaida mishi aikuwa shima yayi murna sosai dan cewa yayi kafin ya dawo gida zaije ya fara nema musu visa zuwa gida.
Sanda Safwan yaji labarin tafiyarta kuma cewa yayi sam baisan zancen ba dole shima ya bisu su koma tare.
Kwanaki biyu a tsakani suna ta shirye-shirye zuwa Nigeria, duk abinda Zarah ta fita ta gani indai na yara ne sai ta siyawa Baby gefe guda Safwan na taya ta, tun Sadiq na tsokanarsu yana faɗin na marmari har abin ya wuce ƙarfin tunaninshi dan Safwan ko ƴar sa ce iya siyayyar da zaiyi mata kenan.
Ana saura kwana biyu suna suka iso Nigeria,a Gombe jirginsu ya sauka har Safwan dan yace sai angama shagalin suna zai wuce Yola(Kome ya haɗashi da shagalin suna oho). Tarba ta musamman Momi ta musu da ƙayatattun abinci, sosai taji daɗi ganin yadda ƴarta tayi kyau sosai alamun kwanciyar hankali ya bayyana a jikinta, gefe guda kuma ga irin soyayyar da Safwan ke nuna mata dan har a gaban su Momi ba ya kunya musamman da suke mutane ne masu barkwanci.
Sai da suka huta sannan aka haɗu a dinning dan cin abinci. Duk wannan wainar da ake toyawa M.J baisani ba saboda ba shi da labarin Zarah zata dawo don ba'a gaya mishi ba, yaushe ma ya zauna har da za'a faɗa mishi.
Kullum da safe idan ya shigo ya gaishesu Office yake wucewa bayan ya ɗan tsakuri abinci kaɗan wani lokacinma baya iya ci, da Yamma ma idan ya dawo zai shigo yakan jima wani lokacin dan watarana harda shi ake yi dinner.
Kasancewar su Zarah tafiyar safe suka yi yasa baisan da isowarsu ba.
Sosai Baaba ke tsokanar Safwan tana mishi hira lokaci guda. Suka saba tamkar dama sun shekara a tare kodayake haɗuwar fuska ce kawai ba su yi ba.
Bayan Sallar la'asar ne suka shirya zuwa gidan Jiddah harda Sadiq wanda sai da ya gama ƙorafi kafin Momi ta lallaɓashi su tafi tare.
Shiga me kyau suka yi dukkansu, daga nesa idan mutum yaga yadda Zarah da Safwan suka jero ko maƙiyine sai ya yaba da yadda suka dace da juna.
A daidai wannan lokacin kuma M.J na zaune a office yana aikin tunanin daya saba yi na Zarah, lokaci guda yaji ƙirjinsa ya buga da ƙarfi har sai sa ya durƙusa ya dafe gurin, jin kamar ciwonshi zai tashi ne yasa ya mike ya lalubi key ya fita dan zuwa gida saboda magungunan shi duk a gida ya ajiye.
A hankali yake tuƙi har ya iso gaban wawakeken gate din gidan nasu, me gadi ya buɗe masa ya kunno kan motar cikin gidan.
Ai kuwa idanunshi suka yi mugun gani.
Zarah ce tsaye sanye da doguwar riga ba atamfa me kyau, kanta na yane da wani gyale me duwatsu a jiki, gefenta kuwa Safwan ne cikin wank tsadadden yadi kalar fari da hula ɓaka a kansa. Sun yi kyau sosai Sadiq na tsaye a gabansu yana ɗaukarsu hoto duk suna dariya.
Duk da sun ganshi amma sai suka yi biris suka gama abinda suke yi Sadiq ya jasu suka fice daga gidan, jiki ba laka haka ya shige sashin sa a lokacin har jiri ya fara ɗebarsa aikuwa yana shiga ya zube akan doguwar kujera lokaci guda kuma tari me karfi ya turneƙeshi sai kuwa aman jini ya biyo baya.
Ya daɗe cikin wannan yanayin kafin ya samu lafawar ciwon ya mike dakyar ya watsa ruwa sannan ya fito ya sha magani ya fara gyaran gurin da ya ɓaci bayan ya gama ne ya jona ruwan zafi a ƙaramin kofi ya haɗa tea me kauri yasha. Sannan ya kwanta da niyyar hutawa sai dai abu ya gagara domin daya runtse ido hoton Zarah da Safwan ne ke mishi yawo a kwakwalwa.
Ajiyar zuciya me karfi ya sauke dan ya tabbar indai Safwan shine mijin da Zarah zata aura tayi sa'a don hatta shi da yake kyakkyawa babu abinda zai nunawa Safwan din indai wajen kyau ne ko kuma cikar sura, gashi kuma an faɗa mai ɗan gidan Sarauta ne dan haka dole ya koyi yadda zai rarrashi zuciyarsa akan Zarah dan tun farko shi ya jama kanshi.
A haka har wani wahalallen bacci ya ɗaukeshi.
Ɓangaren su Zarah kuwa sosai Jiddah tayi farin cikin ganinsu musamman aminiyarta, sai koɗa yadda Zarah ta koma take yi har tana faɗin itama za'a haɗa da ita a musu gyaran amarcin, sun yi godiya sosai da irin kayan da suka narka musu. Nan su Sadiq suka bar Zarah ta ƙarasa yininta sai dare suka dawo suka ɗauke ta nan suka dawo gida.
Sai dare kafin Daddy ya samu ganawa da ƴaƴan shi da kuma sirikinshi, yayi murna sosai da zuwansu musamman da ya fahimci hankalinsu kwance ya ke babu alamar damuwa a tattare da su.
Sun jima suna hira kafin kowa ya nufi makwancinsa.
Kwanciyarta kenan a kan gado taji ana kwankwasa ƙofar ɗakinta, a tunaninta Momi ko Baaba ne amma tana buɗewa taga M.J tsaye cikin farar jallabiya, ƙofar tayi nufin rufewa amma yasa hannu ya dafe sannan ya tura da ƙarfi ya shiga ɗakin ya maida ƙofar ya rufe, kallon tuhuma take binshi da shi bai ko kula da yanayinta ba ya durƙusa a gabanta ya haɗe hannayenshi guri guda ya fara magana
"Bansan dame zan fara ba, nasan nayi miki kuskuren da ban cacanci ki yafemin, amma gani a gabanki na cire duk wani girman kai ina roƙonki dan Allah ki yafemin abubuwan da na aikata a gareki bansan da wasu irin kalmomi zanyi amfani da su wajen baki haƙuri ba. Ki taimaka ki yafemin ko zanga haske a rayuwata. Dan Allah wallahi nayi nadamar komai dana aikata miki."
Tsaki tayi a fili sannan ta ce.
"Malam tashi ka ficemin a ɗakina dan Allah ba zan yafe ba ɗin."
Ƙafar ta ya riƙo hawaye na bin fuskarsa ya ce
"Nasan laifukana a gareki masu girmane ki taimaka badan halina ba ki yafemin."
"Wai meye haka sakar min ƙafa karka jamin abin kunya ko ka manta mijin da nake shirin aura na cikin gidan nan ne "
Me neman kuka an jefe shi da kashi awaki, nan take yaji zuciyarsa ta masa nauyi saboda ambatar Safwan da tayi aikuwa kamar yadda ya saba idan ranshi ya ɓaci, tari ya fara a hankali har yayi yawa jini ya fara biyowa bayan, hankalin Zarah ne ya tashi ganin yadda yake ta aman kuma najini gashi dare yayi tasan motsi kaɗan za'a iya jinsu. Tsugunawa tayi a gabanshi ta tallabo fuskarsa da hannayenta cikin murya irin na masu raɗa ta fara magana hankali tashe.
"Dan Allah kayi haƙuri ka tafi a ɗakinnan wallahi na yafe maka duniya da lahira duk laifukan da kayimin da wanda nasani da wanda bansani ba wallahi duk na yafe, kaji dan Allah bari na taimaka maka ka tashi."
Idanunshi a lumshe yaji wata irin nutsuwa ta sauka mishi lokaci guda, abu biyu ne sila na farko yafiyar da yaji ta ambata a gare shi abu na biyu kuwa a karo na farko ta taɓa shi da lallausan hannayenta kuma cikin kulawa take maganar.
Wani yanayi ya tsinci kanshi a ciki lokacin da ta dafa kafaɗarshi tanason mikar dashi tsaye, ganin ta kasa ne ya sashi mikewa ya kalleta cikin ido ya buɗe baki da niyyar magana tayi saurin saka hannu ta rufe mishi baki dan a tunaninta zai iya yin wani aman dan haka tace
"Ba sai ka godemin ba ka tafi kawai"
Jiki ba kwari ya fice a ɗakin ya barta tsaye cikin tunanin iri iri, sosai taji tausayinshi ya kamata kasancewarta mace me rauni sosai, wannan wata irin lalura ce ta samu M.J haka gaskiya yana cikin wani hali da ya kamata a tausaya mishi. Har cikin zuciyarta ita kam ta yafe mishi dama can bata rikeshi da komai ba.
A wannan dare kusan kwana tayi idonta biyu da tunanin M.J a ranta.
Washegari kuwa da manyan baƙi suka tashi don Ammi ce da Rahama suka diro ƙasar tun safiya, murna kuwa a gurin Zarah kamar ta shiɗe. A ranar haka suka wuni cikin walwala da yamma kuma suka wuce gidan Jiddah dan acan zasu kwana saboda aikace-aikacen suna da za'ayi washegari.
Mutanen sunyi mamakin karar da Jiddah tawa Zarah kodayake ba mamaki idan aka duba irin shaƙuwar dake tsakaninsu. Yarinya dai taci suna Fatimah Zarah za'a dinga kiranta da Amrish.
Suna ya ƙayatar sosai uwa da ƴa sun samu kyaututtuka na ban mamaki, a haka aka watse taron kowa ya tafi da souvenirs da aka yi.
Saleem bai yarda a tafi da Jidda wankan gida ba dan haka ne aka nemi wata daga cikin danginsu ta zauna da ita.
Kwanaki biyu tsakani Safwan ya shirya tafiya Yola sai dai zai jira Yayanshi da yazo Gombe aiki ya gama su tafi tare. Tun ranar da yazo basu haɗu da Safwan ba sai ranar tafiyarsu gida ya taho gidansu Zarah dan gaisawa da surukan ƙaninshi.
Rabon kwaɗo ko a ruwa zafi yake baya wucewa, Tunda yayi arba da Rahama zuciyarshi a karo na farko ta gamsu da ita yaji yana sha'awar ƙulla taraiya ta har abada da ita.
Bai bayyana hakan ba sai a hanyarsu yake shaidawa Safwan aikuwa yayi murna sosai inda yace zai sanar da mai martaba a haɗa aurensu tare.
Sanda iyayensu suka ji wannan batu sunyi murna matuka musamman da kullum burinsu bai wuce suka Mahmud yayi auren ba, babu wani jan lokaci dan sun yanke shawarar a haɗa auren biyu indai ya tabbata, ko da Mai martaba ya kira Daddy ya tambayeshi ko anyiwa Rahama mijin cewa yayi a'a amma zai tambayeta ko akwai wanda take so, Alhamdulillah bai sha wuya da Rahama ba ta gayamai babu wanda ta tsayar dan haka ya kira Mai martaba ya shaida masa.
Kwanaki uku tsakani aka hado lefe da sadakin Rahama aka kawo inda aka tsaida biki rana ɗaya da nasu Zarah wata ɗaya da sati biyu masu zuwa.
Murna kuwa ba'a magana, nan Ammj ta ƙara zagewa ta fara gyara ƴaƴan nata na musamman.
Shidai M.J ya daina jinya a fili sai a zuciya, yana matuƙar galabaita sosai dan ya rame yayi haske kamar wanda ke gargarar mutuwa.
*********************************
Kwanci tashi asarar mai rai, yau gashi har an shiga satin da za'a fara shagalin bikinsu Zarah, duk wasu shirye-shirye da suka kamata anyi. Kuɗi kuwa tamkar ba nemansu ake yi da zafi ba yadda ake fiddasu kamar ba'asu.
Daga masarautar su Safwan kaɗai miliyon goma aka turo na gyaran amare banda manyan akwatuna da aka ciko da kayan fitar biki masu tsadar gaske.
Ɓangaren su Daddy ma shirye-shirye ake yi sosai dan Daddy kwarai yake son nuna su Zarah na da gata duk da ubansu baya raye, shikanshi sai da ya musu akwati bibbiyu ya shake da kaya na fitar biki bayan kayan ɗaki da suka shirya da Momi da Ammi suka je har Italy dan siyowa, hatta cokali abin banza a ƙasar waje aka siyo musu komai nasu daga can ne.
Baaba kuwa tayi faɗan harta gaji amma sunƙi dainawa.
Babban Yaya kuma wani danƙareren Boutique ya gina musu wanda aka cikashi da kayan siyarwa na manyan mutane da ko a ƙasar waje sai haka, inda aka shirya taron buɗeshi ranar da za'ayi bridal shower ɗin amaren, bayan haka sai da ya saka musu makudan kudi a cikin account dinsu.
Tun ranar Monday aka fara gudanar da shagulgula inda akayi Welcoming dinner ranar monday a farfajiyar gidan Daddy an kashe kuɗi sosai amare kuwa sun sha kyau tamkar a sace su a gudu, washegari ranar talata kuma akayi Fulani day mai ban sha'awa dan harta mutanen Yola sai da suka zo a jirgi bayan angama ya kwashe su ya kuma, Ranar laraba kuma akayi shagalin buɗe Boutique ɗinsu Mai suna *RAHAZAR BOUTIQUE* wanda ya samo asali daga farkon sunan kowaccensu.
Washegari Alhamis ne za'a gabatar da Reception kuma a ranar Safwan da abokansu zasu taho Gombe dama shi Mahmud tun ranar Monday yake nan saboda wani taro da suka gabatar shiyasa bayan an kammala yayi zamansa kawai tare da wasu daga cikin abokanansu.
Fitowar Zarah daga wanka kenan saboda bata tashi da wuri ba dan gajiya dama kuma tana fashin Sallah, turo ƙofar akayi a hankali kanta ta maida kan me shigowar Sadiq ne da Daddy suka shigo kallo ɗaya zaka musu ka gane tsantsar damuwa a tattare da su. Hijab ta ɗauka ta zura sannan ta gaida Daddy bai amsa mata ba illa zaunar da ita da yayi a gefen gado ya fara magana kamar....✍🏻
*BY*
*JASMINE🌸🌸*
*ASP ZARAH*
*BOOK 2*
Nasiha sosai Daddy ya fara mata me ratsa jiki, ƙirjinta ne ya fara dukan uku saboda yadda taji yana ambatar karɓar ƙaddara, ko wacce ƙaddarar ce ta kuma samun rayuwarta, tunaninta ya katse sanda taji Daddy na faɗin
"Zarah haƙuri da juriyar da na sanki dashi a wannan karon ma shi nakeso kiyi sannan ki rungumi ƙaddarar da Allah ya ɗora miki da hannu biyu. Kiyi haƙuri Zarah yau da asuba Allah yayiwa Safwan mijin da zaki aura rasuwa sakamakon ciwon ciki da ya kulleshi a jiya da dare."
Tamkar saukar aradu haka taji maganar Daddy a kunnuwanta bata kyma gaskatawa ba sai da taji ɗan uwanta na maimaita batun Daddy ɗin.
Bata kuma sanin inda kanta yake ba sai buɗe ido tayi ta ganta kwance a gadon asibiti da ƙarin ruwa a hannunta, a hankali ta fara juya idanunta tana ƙarema inda take kallo da mutanen dake wajen, mutum uku ta gane a cikinsu Baaba, Jiddah sai Rahama da suka yi wujiga-wujiga alamun tashin hankali ya bayyana a garesu, ƙoƙarin mikewa ta farayi da sauri duk suka ƙaraso inda take suna mata sannu bata kula ba ta fara magana tana cewa
"Dan Allah kuce mafarki nayi na zahiri bane dam Allah kada kucemin Safwan ya rasu bazan iya rayuwa batare dashi ba, wayyo Allah shin wani zunubi na aikata a rayuwata da nake ganin irin waɗannan kaddarori." Kuka mi cin rai ta fashe da shi me cin rai.
Gabaɗaya tausayinta ne ya kamasu su kansu rasuwar Safwan ta jijjigasu matuƙa bare ita kuma da kowa ya zauna da su a ɗan ƙanƙalin lokacin nan zai fahimci irin ƙaunar da suke wa juna. Kwananta biyar kenan a kwance batasan wanda yake kanta ba tun ranar da aka faɗa mata batun rasuwar Safwan ɗin. Bayan su Daddy sun kawota asibiti ne suka bi jirgi zuwa garin Yola dan jana'izarsa, kwanansu biyu suka dawo kuma kafin su dawo sai da aka ɗaura auren Rahama da Mahmud sannan Zarah da Jawwad dan Mai martaba ya ce baza'a ɗaga auren ba sannan shi da kanshi ya baiwa Daddy shawarar a ɗaura aurenta da Jawwad ɗin sannan yace shi da kanshi zai zo ya taushi Zarah idan anyi sadakar bakwai sai dai an dakatar da shagulgulan da aka shirya.
Kuka takeyi sosai harda shiɗewa suna bata baki ganin taƙi yin shirune yasa Jiddah ta kira likita yana zuwa kuwa ya mata allurar bacci nan bacci ya ɗauke ta sannan ya cigaba da dubata.
Sai da Zarah ta yi wata guda a asibiti kafin ta fara dawowa daidai tare da sakawa ranta cewa lallai Safwan ya tafi ya barta saidai ya barta da rauni a zuciyarta da bazata taɓa warkewa ba, ta kuma shiru shiru sam bata son hayaniya kullum cikin jan carbi da karatun alqur'ani take yi, a haka likita ya bata sallama bayan nasihohi da aka mata.
A ranar da Safwan ya rasu harda M.J da Abdallah suka shirya zuwa jana'izarsa. Kuma a gabansa aka ɗaura aurensa da Zarah, a ranar ji ya yi tamkar mafarkan da ya saba yi ne yake yi, babu kalar addu'ar alkhairi da bai yima mai martaba ba godiya kuwa har saida ya dakatar da shi, kwana yayi yana sallar godiya ga Allah da kyautar da yayi masa a lokacin da ya cire tsammanin samu.
A haka suka gama kwanaki uku suka baro Yola zuciyar M.J cike da farin ciki sai dai a ɓangare guda yana taraddin yadda zai fuskanci Zarah ko da wani idon zata kalleshi idan taji labarin ya zama mijinta a karo na biyu.
Kullum sai yaje asibitin dan dubata sai dai yafi zuwa lokacin da yasan tana bacci, tana bashi tausayi sosai saidai a ɓangare guda yana kishi idan ya tuna saboda wani take yin wannan jinyar.
Kwanaki biyu da sallamo Zarah Mai martaba da tawagarsa suka zo, da kanshi ya nemi ganawar sirri da Zarah, shima dai nasihar ya mata sosai kafin daga baya ya shaida mata batun aurenta da Jawwad, aikuwa nan hankalinta ya ƙara tashi ta fashe da kuka, roƙonta mai martaba ya shiga yi dakyar ya samu ta sassauta bayan ya shaida mata yau yake so dukkansu a wuce dasu ɗakin mazajensu dan dama Rahama tare da masu ɗaukarta suka zo. Nisawa yayi ganin yadda take risgar kuka yace
"Fadimatu bawai shawararki nake nema ba ina baki umarni ne a matsayina na uba gareki indai kin bani wannan matsayin. Kiyi hakuri da yadda ƙaddara tazo miki mun sani duka cewa kina halin da yakamata