Showing 9001 words to 12000 words out of 35955 words
ana yi a cikin gida ba su sanin ana masu siyan, sai dai in je talla, kuma Innarmu da Babanmu basa son in je yawon talla.”
Ya ce, “Gaskiya ne. To ki dan kara ja baya kadan ko?” Ta ce, “To na gode.” Ya ce, “Ina zuwa nan unguwar layin can na sama shi ne gidan Kakana.”
Ta kai kallonta inda ya nuna. Ta ce, “Layin Shatima ko?” Ya ce, “Ai nan ne gidan Kakana.” Ta dan zaro ido “Laahh! Nasan gidan, muna zuwa ranar Juma’a karɓar sadakar waina, ko shinkafa da wake.”
Ya tsura mata ido, ta ce “Yanzun dai bana zuwa sai kannena.” Ya ce, “To ya jikin Babanku?”
Ta dan fadada fara’arta “Ya samu sauki, har ma yana tashi zaune tunda aka yi mishi gashin kashi sau biyu. Kuma naku mara lafiyar ya samu sauki?”Ya ce, “Ai mu ba a kwance ta ke ba, Maman abokina ce muna kai ta gashin Kashi ne.” Ta ce, “Allah Sarki! Allah Ya bata lafiya.”
Munnir ya leko, “Abokina zo mu tafi mana.” “To, Ya dubi Munnir, sannan ya dubeta. “Sai an jima, amma don Allah ki matsa a titin.” Ta ce, yanzun zan matsa.”
Tana tsaye suka ja motar suka wuce, sannan ta zo ta kara komawa baya da kayanta.
Shatima yana harba motar kan titi, Munnir ya kalle shi rai a hade.
“Wai me yasa ká ke son shiga harkar yarinyar nan ne? ka tsaya kana magana da ita kamar wata sa’ar yin zancenka.”
Ya kalli Munnir, “Laifi ne kenan don nayi mata
magana ta tashi a titi?” Munnir ya ja tsaki. “Mene
ne to na fada mata kana zuwa nan ga gidan
Kakanninka, ga waye-waye?”
Shatima ya yi murmushi, “Ni kaina ban san dalilin da yasa ni ke son shiga lamarin yarinyar ba, amma dai nasan ina tsananin jin tausayinta.
Aliya tana tsifar kai da yamma ranar Lahadi, misalin karfe hudu. So take yi taje wankin kai don rana irin ta yau ne take samu tayi abubuwan da ba ta samu tayi ba saboda aiki.Wayarta ta soma ringing, ta dauka ta kalli fuskar wayar, gabanta ya fadi don ganin (My love) da ta yi. Ta jima tana jiran wannan kiran amma dole ta hakura don tuntuni ta san halin Shatima, ba ya daga cikin maza masu nacin kiran wayar budurwa ko mai son da yake mata.
Ta daga tasa a kunne tayi sallama. Ya ce, “My love fatan kina lafiya?” Ta ce, “Lafiya lau, ina
fatan kai ma haka?” “Hakan ne. Zan shigo bayan sallar Isha’i mu gaisa koda minti goma ne.”
Ta ce, “Sai ka shigo, amma ina neman alfarmar
a kara min yawan mintuna.” Ya ce, “To zan duba in gani.
Kafin takwas na daren, Aliya ta sha wanka sai kamshi take yi, tana son in ya zo ta ce ya shigo ya gaida su Mamanta, don bata basu labarin shi ba kar su karya tata, tunda ko yaushe tsiya suke yi mata, wai ta tsaya jiran Shatiman da bata san duniyar da yake ba, bai ma san tana nan ba.
Kannenta biyu suka yi aure bayan tafiyar Shatima, don haka tana shan gori a dangi.
Lokacin da take shirinta, matar wanta da Mamansu sai zancenta suke wai wane ne kuma ya samu shiga haka? Ta lura amma sai ta share tamkar bata san suna yi ba, ta dai tsara zata basu mamaki ne. Wani yaro yayo sallama. ‘Yar Yayansu ta amsa. Ya ce, “Wai ana kiran Aliya in ji wani mutum a waje.”
Yarinyar ta ce, “Kai Anti Aliya ake cewa.” Mamanta da ke bakin kofarta tana jinsu ta ce, “Ke Yusra ko! In ke Antynki ce shi Antynshi ce? Kije ki kira ta.” Aliya tana jin su.
Yusra ta leka dakinta ta ce, “Anti wai ki zo in ji wani.” Ta ce, “Ki ce ina zuwa.” Ba ta tsaya ɓata lokaci ba tun da ta san cikin lokutanta ne zata bata. Yana jingine a gaban motarshi, ta zaci su biyu ne sai taga shi kadai ne. Ta jingina itama sannan ta
gaishe shi.
Fitilar kofar gidan ta haska su, don haka ta lura da kallon da yake mata, tunda ta fito.
Ya ce, “Kin ganni sai yau ko?” Ta ce, “Ai nasan kana cike da tarin ayyuka da uzurori, sannan dole in koyi hakuri tunda nasan bani kadai ba ce ina da kannai.”
Kalaman Aliya suka yi masa dadi, da alamu ita ce zata fahimce shi fiye da sauran, don ya lura Nafisa tana da kishi sosai. Ita ko Amna har zuwa yanzun shakkar fada mata yake, don baisan yanda za ta dauki abin ba.Yayi murmushi, “Tun-tuni shi yasa ni ke ganin ki daban a ‘cikin mata, haka ma sonki daban ne a zuciyata.
Ta gyara tsayuwa, “Nima a gare ni daban ka ke
a cikin maza, don haka da ba ka nan duk namijin
da ya zo sai in ga tamkar mace ‘yar’uwata.”
Ya ce, “Na yarda da ke tunda ki ka jira ni. Ke na fara so, ke ce za ki zama uwargidana.” Ta ce, “Kana ganin zan girme su?” Ya ce, “Za ki girme su, amma Amna kila kuyi sa’a, ko ki fi ta kadan.”
Ta ce, “Kuma suma duk Sun san cewa a rana daya zamu yi aure?” Ya ce, “Nafisa ce ta sani, amma na lura ta damu. Ina ganin tana da kishi sosai. Aliya ta ce, “Sai lallashi tunda yarinya ce. To
ita fa dayar?” Ya ce “Ita kamma na kasa fada
mata, yanzun haka suna Umra da ‘yan gidansu, ina
son sai ta dawo zan je mata da žancen. Aliya ta sauke ajiyar zuciya, “Amma sai in ga da za ka dan tuntuba mata ko a waya, ba wai ka fito mata da zancen ba, ka nuna mata akwai fa wata muhimmiyar magana da za ku yi in ta dawo, kaga zata yi ta lissafin wace magana ce?
To in ka zo mata da zancen ba za ta ji komai
ba, don kila ta hasashi abin da yafi haka.”Ya ce”To zan gwada haka. Ya su Mama? Ya kamata in shiga in gaishe su ko?” Ta ce “To bari in fada musu.
Suna gama gaisawa da Maman su Aliya, Yayansu Aliyu yana shigowa, shi ne ma ya gane Shatima. Suka gaisa, da zai tafi ya aje musu dubu goma ya fito. Sun dan yi ‘yar hira sannan suka yi bankwana ya tafi.
Shatima da Mahaifinsa sun dawo daga sallar Juma’a, Mahaifin ya ce, “Mu wuce gidan su Hajiya in ba ka da wani uziri, don ban samu damar zuwa da safe ba.”
Shatima ya ce, “Babu uzuri Alhaji, ko ma akwai naka yana gaban nawa. Cikin jin dadi Alhaji ya ce, “Sai dai goron da na sai mata yana motata a gida.” Shatima ya ce, “Sai a sai mata wani yanzun da izinin Allah.”
Sun samu gidan cike da jikoki ‘ya’yan Marigayi babban wansu sun zo daga Kaduna su uku, biyun na gida. Sai kannan Nafisa Hamida da Momi, ga ‘ya’yan Anty Saude.
Shatima ya ce”Masha Allah, duk ‘yan hutun
satin ne haka fal a gida?” Ta ce, “Eh, ga su nan har gidan ya yi dadi, da ko shiru daga ni sai Maryama.”
Suka zauna suka gaisheta. Shatima ya bata goronta da Zuma. Ta dinga zuba musu godiya da sa albarka. Sannan ta ce, “Dama ina son ganinka, dazu da su Hannatu suka zo sai suke fada min wai saurayin Rahma zai zo gaishe ku gobe Asabar.”
Alhaji ya ce, “Allah Ya kai mu. A can Kaduna ta samu saurayin ita ‘Rahmar?” Ta ce, “Ban tambaye su ba, amma in ya zo ai ku za ku ji komai daga bakinsa.
Alhaji ya ce, “Haka ne.” Shatima ya ce, “Rahma ta gama karatun ke nan?” Kaka ta ce, “A’a, sauranta shekara daya. Ai yanzun in an samu miji ba a cewa sai an gama karatu, haka kuma tsakanin karami da babba ba a jira.
Ita Madina ai ta gama karatun yanzun bautar kasa ta ke. Da Allah zai kawo mijin ai sai duk a hada su.”
Alhaji ya ce, “Sosai kuwa. Yaran suka dinga zuwa suna gaida su Shatima.
Maryama ta kawo musu waina da miya, Shatima bai ci ba don yasan ‘yan aiki ne suka yi. Amma Alhaji da ya ke yana son waina ya ci kayansa.Suna ta hira har a ka zo kan batun auran Shatima. Kaka ta ce, “To kai yanzu gida daban daban za ka aje matan naka ko kuwa?”
Alhaji ya ce, “Yauwa, dama nayi wata shawara. Filayen da na raba musu shi da Mustapha da Badi’atu ya yi min ciko ya maido min da nashi sai in ba shi wani babban filina da ke Rigachikun, kawai ya yi ginin guri hudu shi da matansa kawai, ko ya ya ku ka gani?”
Kaka ta ce, “Amma kuwa kayi tunani mai kyau, ko ko kai ya ya ka gani Shatima?”
Shatima ya ce, “Ai ni Alhaji ka gama min komai, don ka ga na sami saukin zuwa Kaduna gurin aiki kullum, don da ina tunanin duk su zauna nan Zariya, ni kuma ina Kaduna sai su ke zuwa.”
Kaka ta ce, “Hakan shi ne daidai.” Ya ce, “Kaka a taya ni godiya gurin Alhaji, sannan a nema min alfarma, a rubuta takarda na yarda zan ba da cikon amma sai nan gaba, don kudin hannuna zan tada ginin da su.”
Ya ce, “Wannan hutun na karshen mako sai muje kaga gurin.” Ya ce, “Allah Ya kara girma da lafiya Alhaji, Allah Ya jikan Mahaifinku, ya raba ku lafiya da Kaka.” Suka ce “Amin.”
Nan suka ci gaba da tattauna al’amuran da suka shafe su.
._____
*🏚️RANA DAYA 🏚️*
CHAPTER 6
*BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*
*Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*
```ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925```
*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427*
*08146017245 hohoho wani Kaya Sai amale shin kunsan kayatattun magungunan Mata na maman haidar*
*Kayan maman haidar basuda matsala domin traditional medicine ne Kuma anahadasu da ingantattun itatuwa masu karfi da Basu da illah*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
*1 Gumbar kankana da ayu* 🍀🍀3 *Gumbar Madara da kwakwa*🍀🍀
4 *Kaza mekwai* 🍀🍀
5 *Zabo me zuma*🍀🍀
6 *Kaza me allurai🍀🍀 sahihiyar mallaka ba boka ba malam*🍀🍀
7 *Kwallin idonka inadona*🍀🍀🍀
8 *Tauwadar mata*🍀🍀🍀
9 *ketar larabawa magani me kankarowa mace kima da daraja*
10 *Maganin sanyi me fatattakarsa duk kuwa nacinsa Koda bakya haihuwa indai matsalar sanyice gwada wnnn*
11 *Maganin nono. Sahihi*
12 *Maganin hips and bobbs*
13 *hodar. Ni I'ma koramar mata*
14 *nakasan Mara babban sirri*
15 *kafi jijjibi*
16 *daga Sha Sai wanka kasaitacce magani*
17 *Dan kwankwalati namata da mazajensu Kevin Mata*
18 *matsin kinfi budurwa dubu ko haihuwa nawa kikai Babu magana*
🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
*Maman haidar Bata tsaya anan ba*
*Tana Saida hijabai dayadikan su akan darashin sari yadika dila dilahijaban. Yan gayu sannan*
*takawomuku hadaddan sabulun gyaran jiki da hadin dilka Mesa sheki da laushin fata gaman kitso Wanda laraba ke amfani dashi inkin gwada saikin dawo kudai kunemeni awannan number* 08146017245
🍀🍀🍀🍀🍀
Mun tsaya
kullum, don da ina tunanin duk su zauna nan Zariya, ni kuma ina Kaduna sai su ke zuwa.”
Kaka ta ce, “Hakan shi ne daidai.” Ya ce, “Kaka a taya ni godiya gurin Alhaji, sannan a nema min alfarma, a rubuta takarda na yarda zan ba da cikon amma sai nan gaba, don kudin hannuna zan tada ginin da su.”
Ya ce, “Wannan hutun na karshen mako sai muje kaga gurin.” Ya ce, “Allah Ya kara girma da lafiya Alhaji, Allah Ya jikan Mahaifinku, ya raba ku lafiya da Kaka.” Suka ce “Amin.”
Nan suka ci gaba da tattauna al’amuran da suka shafe su.
Ya idar da Nafilfilinsa na dare ya zauna yana istigfari, sai ya tuna wannan lokacin a Saudiya tamkar rana ce, zai iya yin magana da Amna. Ya tashi ya ciro wayarsa a chaji ya kunna yana neman lambar da Amna ta kira shi shekaran jiya.
Ya kira sau biyu bata daga ba, ya mata uzuri kila bacci take yi tunda ba kowa ne ya saba da zama har wannan lokacin ba.
Ya sake kira kashi na uku, sai gashi ta daga cikin mayen bacci. Ta ce, “Hello honey!” Ya dan zaro ido, don bata taba kiranshi da wannan sunan ba, ta kan dai ce mishi ‘Dear’.
Ya ce, “Honey kiyi hakuri na tashe ki a bacci ko?” Ta ce, “Ba komai, ya ka ke?” Ya ce, “Ina lafiya. Kina yi mana addu’a kuwa ki ke bacci?” Ta ce, “Ina yi mana.” Ya ce, “Wace iri ki ke
min?” Ta ce, “Ta kara karfin soyayya har gidan
Aljanna.” Ya ce, “Kin kyauta, amma ina son kiyi min wata tawa ta musamman. “Kamar wacce ke nan?” Ta tambaye shi.
“Ki min addu’a in kin dawo duk abin da na zo miki da shi za ki amshe shi.”
“Ban gane ba?” Ta fada da sauri.”Za ki gane in kin dawo, ni dai ina son ki daga hannu ki ce Ya Allah Kasa duk abin da Muhammad Ja’afar ya zo min da shi in amshe shi. Tayi dariya, “In ka zo da abin da ya sha kan tunanina fa?”
“Ba zai sha ba in sha Allah.””Nayi alkawarin zan yi maka.” Ya ce, “Na gode. Yaushe za ki dawo? Na kosa
in gan ki.”Saura kwana biyar mu dawo.””To ni in zo yaushe?” Ya tambayeta.”Ban da ranar da muka dawo, amma ka iya zuwa koyaushe.” Ya ce, “To washegarin ranar zan zo.” Ta ce, “Na gode da kulawa, kaje kayi bacci.” Ya ce, “Ranki ya dade.” Tayi ‘yar dariya sukayi sallama.
Ta shiga kicin ta samu Mama tana girkin abincin rana, taje tá jingina da (Freezer) din da ke bayanta. Ta ce, “Mama da zan tafi Makaranta kin ce min za ku yi magana da Babanmu, wallahi ni fa yau ko a aji ban iya gane komai ba.
Ina son in san gaskiyar abin da Yaya Shatima ya fada, tun ranar da ya kira Baba Alhaji ya ce masa yaje gurin Kaka a can zai ji gaskiyar magana, to wai bai je ba ne?” Mama ta kalli yarta cikin tausayi, “Bari
Babanku ya dawo sai kuje gurin Kaka tare don kiji da kunnenki.”
Ta ce, “Amma dai zance mafi inganci shi ne mu ukun kenan?” Ta ce, “A’a, ni na fada miki ban san komai ba sam-sam!”
Ta ce, “Ai ko yau da dare zan je tare da Baba
din.” Ya zuba ido yana kallon gurin zaman Nafisa, “Ina me wannan kujerar?” Mama ta ce, “Tana dakinta tana kunci.” Ya
tsura ma Mama ido.Wane kunci kuma?”
Ta ce, “Zancan auransu da Shatima mana, bad na fada maka tace ya fada mata su uku ne rana daya ba, ka kira Alhaji ya ce maka kaje gurin Kaka ka ji cikakken zance.”
Ya aje cokalin hannunshi ya kurbi ruwa sannan ya mike. Dakin Nafisa ya nufa saboda duk cikin ‘ya’yansa babu kamar ta a zuciyarshi.
Kwance ya same ta tana wasa da rigar wayarta, amma ga dukkan alamu tunaninta ba ya tare da rigar wayar, hankalinta yana can wani gurin.Ya tsaya a gabanta, sannan ya maida hannuwansa baya. Ya ce, “Nafisa!” Ta dago ta dube shi. Ya ce, “Me yasa ba ki zo cin abinci ba?” Ta ce, “Na koshi Babanmu.” Ya ce, “Ina son ki fada min damuwarki.” Ta dago ta kalle shi.
“Babanmu ina son ka binciko min gaske ne Yaya Shatima mu uku zai aura rana daya?” Ya kalli ‘yarshi cikin tausayi, duk da kunya irin ta Nafisa amma sai da ta iya yi masa wannan magana. Ya ce, “Tashi muje gidan Hajiyar yanzun.
Cikin sauri ta saka hijabinta.
Kaka ta idar da sallar Isha’i tana jan carbi kafin tayi shafa’i da wutiri. Sallamar su ta jiyo, duk da bata san ko wane ne ba, ta raya a ranta ba za ta fito ba sai dai in na gida ne su shigo cikin dakin nata.
Maryama ta shigo ta ce, “Kaka ga Kawu Alhaji nan.” Ta ce, “Kamar murya biyu naji.” Ta ce, “Eh, shi da Nafisa ne.” Ta ce, “Su shigo ciki.”
Gabanta suka zauna suka gaisheta. Ta kalli Nafisa, “Dama kina nan?” Ta sunkuyar da kai. Kaka ta ci gaba da yuwa Nafisa fadan rashin son shiga jama’a, da rashin zumunci. Hakuri tayi ta baiwa Kaka.Alhaji Musa ya ce, “Hajiya kiyi hakuri, wannan halinta ne rashin son shiga mutane, kullum tana gida in dai ba Makaranta taje ba.”
Kaka ta ce “Ita dai ta sani, ga shi nan za ki yi aure da kishiyoyi, zama ne za ku yi na wanda ya iya allonsa ya wanke ya sha…”
Nafisa ta dafa kirji. “Dama gaske ne Kaka ba ni kadai Yaya Shatima zai aura ba?” Kaka ta ce, “Au! Dama bai fada miki ba?”
Nafisa ta soma kuka. Alhaji ya ce, “Hajiya bai kamata a bar Shatima yana dan karamin shi ya auri mace sama da daya ba, zai hada ma kanshi damuwar da zata sa shi yayi da na sani.”
Kaka ta ce, “Allah Ya raba shi da aikata da na sani, sunna fa zai yi, ibada ka ke fada min da na sani? Yanzun dai a takaice ka taso ‘yarka ne ka fada min cewa ya fasa auran ‘ya’yan wasu ya auri ‘yarka?”
Ya sunkuyar da kai, sannan ya shiga ba Hajiya hakuri don ba a son ɓacin ranta saboda tana da hawan jini. Duk da haka Hajiya ba ta yi shiru ba sai da tayi masu tatas!
Ta ce, “Ku kun kasa zama jarumai, kun amince ku mutu da mata dai-dai shi yasa kowanne zai zo yana fadin bai kamata ba, amma ba wanda ya kawo min aya ko hadisi da ta haramta masa auran.Ke kuma ko da dayar zai zaba ai ba ki ciki, saboda akwai yarinya Aliya ‘yar makotanmu ce, sama da shekaru uku tana jiransa. Don haka kin ga kema cikin ‘yan kari ki ke.Nafisa ta mike fuuu! Cikin kuka ta ce, “Kaka
sai anjima.” Alhaji ya ce, “Bari mu tafi Hajiya.”Ta ce, “Ku gaida gida.”A mota yana ta lallashinta. Ta ce, “Baba ni dai kawai na fasa, na hakura.” Ya ce, “A ‘a Nafisa, kar ki ce haka, ki bari dai muje gida.
Iyayen sun tasa ta a dakin Maman suna lallashinta, kan cewa tayi hakuri kar ta ce ta fasa, domin Kaka za ta yi fushi.
“Kin san dai fushinta zai janyo babbar matsala.” Mama ta ce, “Ke da yake dan uwanki, Hajiyarsu ke tafi so, kuma kema kin san dole zai fi sonki saboda dangantaka.”
Haka dai suka yi ta lallashinta