Showing 6001 words to 9000 words out of 35955 words

Chapter 3 - Rana Daya Book 1 Hausa Novel Complete

akwai kus-kus, ga kuma faten acca.” Kaka ta ce, “To fa! Duk a cikina? To zubo min
faten sai ki sa farfesun kafar Sa din a ciki.”_____
*🏚️RANA DAYA 🏚️*

CHAPTER 4

*BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*

*Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*

```ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925```

*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427*



*08146017245 hohoho wani Kaya Sai amale shin kunsan kayatattun magungunan Mata na maman haidar*
*Kayan maman haidar basuda matsala domin traditional medicine ne Kuma anahadasu da ingantattun itatuwa masu karfi da Basu da illah*

🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀

*1 Gumbar kankana da ayu* 🍀🍀3 *Gumbar Madara da kwakwa*🍀🍀
4 *Kaza mekwai* 🍀🍀
5 *Zabo me zuma*🍀🍀
6 *Kaza me allurai🍀🍀 sahihiyar mallaka ba boka ba malam*🍀🍀
7 *Kwallin idonka inadona*🍀🍀🍀
8 *Tauwadar mata*🍀🍀🍀
9 *ketar larabawa magani me kankarowa mace kima da daraja*
10 *Maganin sanyi me fatattakarsa duk kuwa nacinsa Koda bakya haihuwa indai matsalar sanyice gwada wnnn*
11 *Maganin nono. Sahihi*
12 *Maganin hips and bobbs*
13 *hodar. Ni I'ma koramar mata*
14 *nakasan Mara babban sirri*
15 *kafi jijjibi*
16 *daga Sha Sai wanka kasaitacce magani*
17 *Dan kwankwalati namata da mazajensu Kevin Mata*
18 *matsin kinfi budurwa dubu ko haihuwa nawa kikai Babu magana*


🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
*Maman haidar Bata tsaya anan ba*
*Tana Saida hijabai dayadikan su akan darashin sari yadika dila dilahijaban. Yan gayu sannan*
*takawomuku hadaddan sabulun gyaran jiki da hadin dilka Mesa sheki da laushin fata gaman kitso Wanda laraba ke amfani dashi inkin gwada saikin dawo kudai kunemeni awannan number* 08146017245
🍀🍀🍀🍀🍀


Mun tsaya

wannan mashirmancin ya zo da zancen zai auri mata uku rana daya, wannan ai labari yake yi. Dubi masu mace daya ma yanda suke fama a wannan zamani, ni dai na ce masa a’a ya dai zabi
daya, in ma karin ne sai ya bari ya ga kamun
ludayin zaman, in yaso can gaba ya kara.” Kaka dai ba ta ce kala ba, har Hajiya Halima ta kai karshe. Kaka ta ce, “Zubo min abin da ki ka zo da shi in lasa ko nafi samun abin fadi.”
Dariya suka yi su duka sannan ta ce, “Farfesun kajin zan zubo miki, ko na kafar Sa? Sannan akwai kus-kus, ga kuma faten acca.” Kaka ta ce, “To fa! Duk a cikina? To zubo min
faten sai ki sa farfesun kafar Sa din a ciki.”


zubo mata ta bata sannan ta kwala ma Badi’atu kira, suka fito. Ta ce, “Ku je ku kawo ma Hajiya ruwa, sannan
ku zo ku kwashe kulolin nan zuwa kicin.” Suka ce, “To.”
Sai da Kaka tayi nak! Ta koshi, sannan ta kalli Hajiya Halima.
“Zancen Shatima, ina son ki cire rashin yardarki da kin amincewarki, ki aje su a gefe. Ki bi da ido, sannan ki hada da addu’a.
Shatima gwarzo ne ba irin mazanku ba, mutum ya zauna da mace daya kamar fasto.” Ta gyara zama sannan ta ci gaba, “Yanzu bari in yi miki wani lissafi, mata nawa Maigidanmu ya aura? Nasan kin samu labari mu hudu ne ko?”
Hajiya Halima ta daga kai alamun “Eh.” Ta ci gaba da cewa, “Kowace mace ta haifi ‘ya’ya da yawa, babbarmu tana da goma sha daya, mai bin ta na da takwas, wadda ni ke bi tana da goma, cikinmu ni ce kadai me ‘ya’ya hudu.
Babbanṣu ya kwanta ya mutu shekara biyu kenan, matarsa na nan a Kaduna da ‘ya’ya biyar. Ke naki mijin ‘ya’yanku uku daga shi Shatima sai Mustapha, sai ko Badi’atu, sai dan uwansa Baban Nafisa.
Suma su uku ‘ya’yansu duka mata, Nafisa da
kannenta biyu. Saude ce ma me ‘ya’ya shida har
na samu aka bani Maryama. Tattara ki kirga min
jikokin nawa duk guda nawa ne?
Ta dafa kirjinta tare da fadin “Ni fa nan da ki
ka ganni yanda Allah Ya halicce ni ina son zuri’a,
naso a ce cikin ‘ya’ya mazan nan guda uku da
Allah Ya bani naso in samu wanda zai gaji
Babansu a ‘ya’ya, don sai da ya bar talatin da
uku a duniya.


Kuma Alhamdulillahi kin dai san komai ba sai
na fada miki ba, cikin ‘ya’yan nan babu mai irin
mukamin da babu. Akwai Soja, akwai Dansanda,
ga yan kasuwa, ga Malamai na duka bangare
biyun boko da Islamiya.
Ga Sarakuna duk da dai wannan gado ne, don
haka ina son ki bi Shatima da addu’a don ina ga
shi ne zai zama magajin Kakanshi, dama sunansu
daya. Ina so ki sa masa albarka a cikin duk
lamuranki.”
Ba ta da zabin da ya wuce mika wuya don
tasan ma babu wani abu da zata fada har ya yi
tasiri. Don haka ta ce “To Hajiya, Allah Ya shi
albarka, ya zaba abin da yafi zama alkairi.
Kaka ta ce, “Yauwa hali dubu rubutun dutse,
dama ni nasan ke komai naki cikin sauki ne da
fahimta, Allah Yayi miki albarka.
Hajiya Halima ta ce, “Amin. To amma Hajiya
an bincika sauran da ya ke son an ji ya’yan asali
ne ko? Ta ce, “Ke dai ki kwantar da hankalinki,
komai na jan namiji daban ne, burinmu dai ki bishi da
addu a.Nafisa tana zaune a cikin lambun gidansu kan
kujera irin mai lilon nan, sanyi da kamshin lambun
yana kara ma zuciyarta nishadi.
Ta lumshe ido tana kallon surar Shatima a
idonta, cikin shiga ta kasaita da kamshi. Gaskiya
tana matukar son Shatima har ma ba za ta iya
misalta son ba.
Tasa hannu ta dauki wayarta da ke kan cinyarta
ta bankado hotonsa wanda tasa Badi’atu ta turo
mata. Zuciyarta tana dadi in ta kalli fuskarshi.
Lallai za ta tura mishi sakon gaisuwar Juma’a
yanzun nan tun da yau take babbar rana. Message
ta shiga ta soma tura masa sako kamar haka:
Ya Allah Ya tsareka, Allah Ya tsare gabanka
da bayanka, ya daukaki rayuwarka. Ya sa ka
Cimma duk abin da ka ke nema.
Allah tsare idonka, da kunnenka, da ji da ganin
haram. Allah Yasa Aljanna ce makomarka.
Barka da Juma ‘a.
Ta karanta ya kai sau goma kafin ta runtse ido,
gabanta kuma yana faduwa ta tura masa.
A fili ta ce, “Allah kasa kar in yi da na sanin
tura sakon nan. Abin da ya bata mamaki kuma
bata yi tsammani ba shi ne, jin karar sako ya shigo
wayarta.
Bata ba tunaninta wahala ba, kawai ta yanke
hukunci cewa sakon daga shi ne Cikin nutsuwa ta
duba ga abin da ya ce:
Zan shigo misalin karfe biyar ni da Aminina,
zan kasance cikin farin ciki in na same ki a gida.
Sannan abincin gidan Babana shi ne zai zama
abincin rana na a yau.
Ki húta lafiya.
Tayi ta maimaita karanta rubutun. Ta dai
fahimci yana nufin zai zo yau shi da abokinshi,
amma ba ta gane batun cin abinci ba. Ta ce a fili,
Bari in je gun Mama tayi min fassara.”
Uwar ta gama karanta sakon sannan ta saki
murmushi.
To in ba ki gane ba yau a nan gidan zai ci
abincin rana, nan ba gidan Babanshi ba ne? Nafisa ta ce, Har nayi tunanin haka, sai kuma
na ce kila in yaci abincin rana a gidansu sannan
zai zo. To Mama yanzun me za’ayi masa kenan?
Ta ce, Ki binciko irin abincin da ya fi so mana
koda gurin Badi’atu ne.” Da sauri ta dauki wayarta
ta nufi dakinta. Badi’atu ta kira tana tambayarta
irin abincin da Yaya Shatima yafi so. Kusan duk
abincin gargajiya yana so, amma babu kamar
burabisko.
Sosai tayi kwalliya ta fesa kalolin turaruka, ta
kame tana yawaita kallon agogo. Tsinken agogon
ya sauka kan digon da ke nunas biyar daidai,
kararrawar kofar falo tana bugawa.
Cikin dakinta ta shige da sauri kar ya soma
karo da kwalliyarta, ba birgewa ba ne. Hamida ta
ce, Yaya Nafisa in ba su ba nefa ki ka boye?
Ta ce, “Ke dai kije ki gani. Kunnenta na gurin
taji Hamida na fadin “Sannun ku da zuwa. Sai da
Suka gaisa da Mama sannan ta ce Hamida ta kai su
lambu inda aka yi musu shimfida.
Ta ce, “Mami zo ki cema Yayarku ga su
Yayanku sun iso, sai ki je ki taimaka ma Hamida
ku kai musu abinci.Cikin shadda doguwar riga mai ruwan goro ta nufi inda aka sauki bakinta. Tayi musu sallama
suka amsa, ita da shi suka kalli juna cikin ido. Tayi
murmushi tare da jan dan mayafinta ta rufe
fuskarta alamun kunya Sannan ta zauna a kusa da dayan tuntun wanda
ba a jingina da shi ba. tuntu uku aka saka a kan
kafet din da aka shimfida. Cikin girmamawa ta gaishe su. Ya ce, “Sunana
Muhammad Jafar Isa, lakabina Shatima. Wannan
abokina ne sunanshi Munnir Khamis, dukkanmu
muna aiki ne a karkashin Gwamnati. Nazo gurinki
ne don ina son ki zama daya daga cikin matana. Da sauri ta dago ta dube shi, suka hada ido ya
sakar mata murmushi. Bakinki da magana amma ki fara gabatar
mana da kanki tukunna. Cikin’ son taja ra’ayinsa
da muryarta ta ce, “Sunana Nafisa Musa Shátima
kuma ni daliba ce a Jami ar Ahmadu Bello da ke
nan Zariya.Ina cikin shekarata ta biyu. Sai dai abin da ban
fahimta ba shi ne, ka ce zan zama daya daga cikin
matanka, shin kana da wasu matan ne ko ko ya ya
abin yake?
Sallamar su Hamida ce ta sa shi yin shiru. Suka
Aje kuloli da kofuna. Hamida ta dauki plate biyu
ta soma zuba musu burabisko.
Yace, Kanwata sa plate daya wa abokina, ni
matata ce zata sa min in gani ko ta san cikin
mijinta.
Nafisa ta amsa ta zuba mishi komai ta jere a
gabanshi. Bayan tafiyar su Hamida ne, Shatima
suka soma cin abinci.
Matso ki ci tare da ni. Ya fada cikin
murmushi. Ta ce, “Ni naci tun lokacin da aka
gama. Ya ce, “Ba ke ki ka girka ba ke nan? Ta
ce, “Ni nayi, bai yi dadi ba ko?
Ya ce, Bari in gama tunda babu kyau magana
in ana cin abinci.” Ta dafa hannuwanta “Bari in
tashi ku gama. Ya ce, “A’a zauna ina son ina cin
abinci ina kallonki.” Ta zauna tare da jan mayafi ta
dan rufe gefen fuska.
Sai da suka gama ci da sha, sannan suka koma
hira.
Ya ce. Meki ka ce dazu? ta ce, “Batun
matanka da ka ce zan zama daya daga ciki.” Ya
ce, “Eh gaskiya ke ce ta uku.
Ta zata zolayarta yake yi, don haka bata ji
Komai ba sai ma ta ce, Ban san lokacin da ka auri
Biyun ba, ko kuma mu ne ba a gayyata ba.
Ai rana daya za’a daura da naki, kuma ina
zaton ma hudu za’a daura duk da ban san wace ce
dayar ba.”
Ta ce, “Zan fi son mu aje batun wasa, ni da kai
muyi zance na gaskiya.” Ya ce, Ai ke ce ki ke
ganin wasa ne, amma babu wasa cikin zancena.
Fuskar Nafisa ta canza launi daga fara’a zuwa
kalar damuwa, shi kan shi ya lura da haka amma
bai bi ta kan haka ba, sai ma ya mika mata
karamar wayarsa.
Ban yi saving din lambar ki ba da na amsa a
hannun Badi’atu, ki saka sunan da ya dace, don da
shi zan kira ki a gaban kowa.
Ta amsa ta saka tayi saving da (Sweety). Ya
kalla sannan ya dube ta. “Sweety! Har a gaban
Mama da Hajiya, da Kaka, da su Baba?
Tayi dan murmushi “Eh. Ya ce “To kema
hakan za ki kira ni.
Sun dauki lokaci suna dan tattaunawa, kafin a
kira Magriba. Suka mike da zummar tafiya. Ya aje
mata kudi ‘yan dubu dai-dai guda goma.
Ki sai omo ki wanke kwanuka, abinci ya yi
dadi.” Ta dube shi, “Haba dai, ka bar shi kawai.”
Ya ce, “Ai ba ki tambaye ni ba. Tayi musu rakiya
har gurin mota.
Bayan tafiyar su tazo a rude gurin Mama. Ta
ce, “Mama Yaya Shatima ya yi min wata magana
da ta sa naji komai na duniya ya ishe ni, wai mu
uku zai aura rana daya!
Mama tayi ‘yar dariya, “Ina ga ba ki san
tsokana ba ko? Wasa ya ke miki.” Hawaye suka
soma zubowa daga idanunta.
“Wallahi Mama babu alamun wasa a tare da shi
sam-sam! Ta ce, “To bari Babanku ya shigo mu
Ji, in dai zai auri wasu ai shi ne waliyyin shi.
Yana Yana daga kwance ya kalli agogon wayarshi,
sha daya ta gota. Ya danna lambar Amna, sai da
tayi ruri ta katsee. Yayi murmushi, ya san kadan
daga cikin jan ajin Amna.
Ya sake kira, can ta daga muryarta can kasa ta
ce, “Hello!” Ya ce, “Ba ki yi bacci ba Amna?” Ta
cc, “Eh, ban yi ba tukunna, sai yau ka ke kirana?
“Kiyi hakuri zan shigo gobe.”
Ta ce, “Sai kuma ka daga zuwan, don gobe
duka gidan ba mu nan.” Ya ce, To fa? Ina za ku
haka har da ba za ku amshi bakuncina ba?”
“Ni dai Umra zamu je da Mom, da Dad sai
Sisters dina guda biyu. Amaryar Dad da sauran
yara za su je (London) hutu.
Ya sauke ajiyar zuciya, “Sai yaushe za. ku
dawo? Ta ce, “Sati biyu zamu yi, ba dadewa
zamu yi ba.” Ya ce, “Shi kenan. Don Allah ki sani
cikin addu’arki.”
Insha Allahu, amma dai zamu yi waya in mun
sauka ko?
Dole na, ina son wannan muryar taki sosai
Amna. Ya fada cikin murmushi.
Muryata kawai ka ke so ban da ni?
Ke ma kin san fada bata baki, ina matukar
sonki.
Nima ina sonka da yawa, sai dai ina ja baya ne
don ina ganin kamar ba ka damu da ni ba.
Ya ce, Me yasa ki ke ganin kamar ban damu
da ke ba?”
Tayi yar dariya tare da sake matse wayar a
kunncnta don dadin hira da shi. Ta ce Tun ranar
da na kira ka ka ce zaka kira ni in ka samu sukuni,
sai yau ka samu sukuni din?
Ya canza kunne da ya manna wayar zuwa
dayan kunnen don ya ji SOsai, saboda Amna bata
magana da karfi ko. kuma ba ta
son hayaniya. Wannan tsarin nata yana matukar
birge Shatima.
Ya ce, “Ba za ki gane ba, amma lokaci ya kusa
da zamu zama tare. Ta ce, “Wane lokaci kenan?_____
*🏚️RANA DAYA🏚️*

CHAPTER 5

*BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*

*Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*

```ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925```

*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427*



*08146017245 hohoho wani Kaya Sai amale shin kunsan kayatattun magungunan Mata na maman haidar*
*Kayan maman haidar basuda matsala domin traditional medicine ne Kuma anahadasu da ingantattun itatuwa masu karfi da Basu da illah*

🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀

*1 Gumbar kankana da ayu* 🍀🍀3 *Gumbar Madara da kwakwa*🍀🍀
4 *Kaza mekwai* 🍀🍀
5 *Zabo me zuma*🍀🍀
6 *Kaza me allurai🍀🍀 sahihiyar mallaka ba boka ba malam*🍀🍀
7 *Kwallin idonka inadona*🍀🍀🍀
8 *Tauwadar mata*🍀🍀🍀
9 *ketar larabawa magani me kankarowa mace kima da daraja*
10 *Maganin sanyi me fatattakarsa duk kuwa nacinsa Koda bakya haihuwa indai matsalar sanyice gwada wnnn*
11 *Maganin nono. Sahihi*
12 *Maganin hips and bobbs*
13 *hodar. Ni I'ma koramar mata*
14 *nakasan Mara babban sirri*
15 *kafi jijjibi*
16 *daga Sha Sai wanka kasaitacce magani*
17 *Dan kwankwalati namata da mazajensu Kevin Mata*
18 *matsin kinfi budurwa dubu ko haihuwa nawa kikai Babu magana*


🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
*Maman haidar Bata tsaya anan ba*
*Tana Saida hijabai dayadikan su akan darashin sari yadika dila dilahijaban. Yan gayu sannan*
*takawomuku hadaddan sabulun gyaran jiki da hadin dilka Mesa sheki da laushin fata gaman kitso Wanda laraba ke amfani dashi inkin gwada saikin dawo kudai kunemeni awannan number* 08146017245
🍀🍀🍀🍀🍀


Mun tsaya

Tayi yar dariya tare da sake matse wayar a
kunncnta don dadin hira da shi. Ta ce Tun ranar
da na kira ka ka ce zaka kira ni in ka samu sukuni,
sai yau ka samu sukuni din?
Ya canza kunne da ya manna wayar zuwa
dayan kunnen don ya ji SOsai, saboda Amna bata
magana da karfi ko. kuma ba ta
son hayaniya. Wannan tsarin nata yana matukar
birge Shatima.
Ya ce, “Ba za ki gane ba, amma lokaci ya kusa
da zamu zama tare. Ta ce, “Wane lokaci kenan?


“Idan mun yi aure mana, kin san fa bana son a
dauki lokaci me yawa nan gaba.”
Ta ce, “Ban san ya zan ji ba in aka ce yau gashi na aure ka, ina tsananin sonka Shatima.” Sun jima suna hira kafin suka yi sallama da
alkawarin zai kira ta gobe kamar yanzun.
Lamo ya yi a kwance yana tunanin cikin su ukun nan bai fi son Amna ba kuwa? Wata zuciyar ta ce, ‘Ina ka bar Aliya mai hankali da sanin ya
kamata, ga kuma Nafisa itama ba baya ba…?” Da wadannan tunanikan bacci ya yi awon gaba da shi.

********

Tana tsaka da tuyar Awarar ta ga yara sun zagaye ta tana son ta sallame su gashi itacen duk danye ne, sai faman hayaki yake yi. Idanunta sun yi jajir, zuciyarta tana can gurin
Mahaifanta tana kokarin ta kammala tayi abinci ta
kai musu, sai taji Horn din mota a kanta.
Da sauri ta dago ta kalli motar, ranta ya dan sosu, don ita dai tasan ba a kan hanya take tuyarta ba bare ta ce, amma masu motar nan sun nufo ta.


Tasan dai ba siyan Awara zasu yi ba tunda bata taba ganin wani mai mota ya tsaya da sunan siyan Awara ba.Yaran suka kauce motar ta tsaya daf da kaskonta. Cikin tsananin tsoro ta mike tsaye tayi baya. Motar taja baya taje gefe tayi parking, ita kuma cikin sauri taje tana tsame Awarar da ke cikin man don kar ta kone.
Tana ta sauri jikinta yana ɓari, tana yi tana kallon inda motar ta tsaya. Yaran da suka dare suka dawo don ta kunsa Awarar. Sai da ta zuba dayan a mai sannan ta shiga kunsa musu.
Tana sallamar su ana bude motar, ta tsura ma gurin ido gabanta yana wata irin faduwa. Sai kawai taga Alhajin nan. Ba ta san lokacin da ta sauke ajiyar zuciya ba tare da hadiye miyau, sai ta ji ta dan samu nutsuwa.
Ta mike tsaye ta dan risina ta dafa gwiwarta alamun girmamawa ta ce, “Ina yini Alhaji?” Ya ce, “Ba sunana kenan ba, lafiya lau.” Ya kalli kayan “Dama nan ku ke?” Ta. ce, “Eh.” Ta nuna wani ribabban gidan sama na kasa, ginin tamkar ya zubo in ya ji kwakkwarar iska.
Ya kalli gidan na tsawon minti biyu, sannan ya dubi kayan suyar tata, sannan ya yi magana. “Salma me ki ke saidawa a nan?”
Itama ta kalli kayan sannan ta dube shi da ‘yar fara’a.
“Awara ce ni ke saidawa.”Ya ce, “Shi ne ki ke zama a nan gab da titi? Ba kya gudun mota ta kwace ta nufo kanki ta taka kamar yanda na kwatanta din nan?”
Ta sake kallon gurin, kamar zata yi magana sai kuma ta fasa. Ya ce, “Nasan za ki ce ba ki hau titi ba, amma mota tana kwacewa, me zai sa ba za ki yi a cikin gida ba?”
Ta ce, “Ai in

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login