Showing 21001 words to 24000 words out of 35955 words

Chapter 8 - Rana Daya Book 1 Hausa Novel Complete

ne shi yasa, sai na isa Kaduna zan kira ta.” Ta ce, “To shi kenan bari in fada mata.”
Momiyo karamar kanwar su Hajiya ce. Ita ce kuma za tayo masa odar akwatunan lefe. Sai da ya isa sannan ya kirata.
“Anty Mamiyo kina ta kirana ina hanya, ka’idata in ina tuki kiran Alhaji ko na Hajiya kawai ni ke dagawa.” Tayi dariya, “Za ka fara daga na matanka kwanan nan.”
Ya ce, “Su a wa? Za dai su san ka’idata a kwanannan.” Ta ce,
“Maganar akwatuna ce zan tura maka online sai ka zaba, saboda gobe zan yi odar.” Ya ce, “Kowace a dauko mata kalar da tafi so.
Ta ce, “Wace kala ce suka fi so?” Ya cc, “Ita dai Amna tun muna Makaranta tana son Lemon green, Aliya kuma na san tana son ja, Nafisa ce dai bari in kirata yanzun, sai kuma daya yarinya
Kin san na samu ta hudu a kawo mata baby
pink.” Ta ce, “Bana son wasa.” Ya ce, “Antywallahi babu wasa. Ke ce ta farko da ki ka san zancan nan, Ta ce, “Ka san me ka ke yi kuwa?” Ya ce
“Don Allah Anty kiyi yanda na ce, kar ki manta
baby pink, bari in kira Nafisa din.”
Take ya kira Nafisa ya tambaye ta best color dinta ta ce purple Ya kira Anty Momiyo ya fada mata.
Salma tana shiga gida ta samu su Innarsu tamkar ita suke jira, ta fada musu komai yanda suka yi ita da Shatima. Su Yaya Hadiza sun hau murna.
Inna kuwa ta dira ta ce “Ba ta yarda ba, ko dai mutumin nan da biyu ya zo?” Salma ta ce, “Inna biyu kamar ya ya?” Inna ta ce, “To ni ban gane ba, daga taimako sai kuma ya ce zai samo mata miji?”
Yaya Hadiza ta ce, “Haba Inna, ki kyautata zatonki a kansa.” Auwal ya ce, “Inna jikan gidan Alhaji Shatima ne fa, sanannu ne
“Shi kenan, Allah dai ya zaba mana mafi alheri.” In ji Inna. Suka ce “Haka za ki fada Inna.” Momiyo ta daga wayarta ta kira Hajiya. Tana dauka ta ce, “Momiyo ki bari zai kira ki.” Ta cc, “Ai ya kira ni Hajiya, wai seti hudu za a kawo masa, wai ya samu ta hudun. Haka ne?”
Hajiya cikin daga murya ta ce, “Abin hauka ne za a ce ya samu ta hudu! Kila dai ita Amna. za a kai wa saiti biyu, tunda kin ga tuwon girma miyarsa nama, a ce komai daya za’ayi?”
Momiyo ta ce, “Ni fa ya nuna min da gaske yake amma dai kyaji in ya dawo daga bakinsa. Ai ni tunda a ka ce flat hudu ya gina na san da wata a kasa.”
Hajiya cikin damuwa ta ce, “To maji-magani.” Suka yi sallama.

**

Biki saura kwana ashirin da tara, ko ina kansu ya dau zafi, gobe yake son yaje gidan su Aliya da Nafisa ya kai musu makullan gida, don kowa yaje ya ga gida. Haka kuma yana son ya kai musu Amna, amma abin da yafi daga masa hankali yanda zai ga ya shigar da lamarin Salma ga danginsa, dole ya je gurin Munnir yanzun don ya fara samun goyon bayansa. Suna cin abinci a falon Munnir yana gefen fada masa abin da ke tafe da shi. Munnir ya aje cokali, ya ce “Ka ga abokina fada min kawai abin da ka ke son fada min.
Shatima ya ce, “Kai tsaye ina son yin ta hudu da yarinyar nan Salma wadda Mahaifinta ya rasu.
Da karfi Munnir ya ce, “Me ka ce?” Har sai da faisal danshi da ke bacci a kan kujerar da ke kusa da shi ya tsorata ya farka.
Munnir ya dauki yaron tare da kwalana uwarshi kira. Fatima zo ki dauki wannan.” Ta shigo ta amshe shi tana cewa “Ya tsorata ne?” Munnir ya ce, “Magana ce nayi me karfi, shi ne ya fırgita.’
Ta ce, “Kana tunanin mata ukun sun yi maka kadan ne da har sai ka kara da wannan ‘yar babyn da bata fi ka haife ta ba, da a ce kayi aure da wuri. Wai me ke damunka?”
Ya ce, “Lafiyata lau, kuma ba wai wadancan ba za su ishe ni ba ne, taimako zan yi ina jin Tausayin yarinyar.” Ya fada mishi duk yanda suka yi da ita.Munnir ya ce, “Ban ga wata matsala a cikin bukatar tata ba. Ka sai mata kayan daki ka aura mata wancan shi kenan.”
Shatima ya ce “To karatunta fa?” Munnir ya ce “Kayi magana da mijin ya barta kai ka dauki nauyin karatun nata, kaga shi kenan ka huta da wasu surutai da zasu taso daga danginka, da kuma matanka.”
Shatima ya ce, “Ban yi wannan tunanin ba, amma na riga da na fada mata cewa zan kawo mata miji wanda zai barta tayi karatu, kuma tayi
murna. Munnir ya ce, “Ka ce mata kai ne?” Shatima ya ce, “A’a.” Munnir ya ce, “To kawai ka dauko batun wancan ka cire kanka.”
Shatima yayi shiru tamkar mai nazari, har
Munnir ya soma zaton shawararshi ta shiga har yana cewa kayi nazari da kyau abokina.” Sai yaga Shatima ya bude ido sannan ya kalle shi, ba wai na gamsu da shawarar ka ba ne, ina tunanin yanda za ayi fadan karshe ne tsakanina da su Hajiya.
Don tabbatar da yarinyar nan tana cikin mata hudun nan da na gani a cikin baccina. Sai yanzu na luna ban fada maka ba, akwai wata a mafi Kankanta a cikin matan mafarkina, babu shakka
Salma ce Tsaki Munnir yaja sannan ya ce, “Allah Ya taimaka.” Shatima ya ce, “Dama haka ka ce, tun dazu da yanzun mun kusa gidan Kaka.”
Munnir cikin jin haushi ya ce, “Ni babu inda zan fita, bacci ma nike ji.” Shatima ya ce, “Gurin Kaka dole ka zo muje, In na samu goyon bayanta kowa dole ya lafa min.
Sai dai ina ji a jikina, ba za ta ba da hadin kai ba itama. Munnir ya ce, “Allah Ya sa kar ta amince.” Shatima ya mike.
“Don Allah tashi muje koda zugata kayi ka
ji?” Abokina haka sai ya gaji da matsin Shatima ya tashi suka fita.
Allah yasa bata kai ga shiga cikin daki ba, lokacin da suka yi sallama a falonta. Bayan sun gaisa Shattima ya shiga kame kame ya rasa ta inda zai bullo ma al’amarin.
Ya ce, “Kaka nasan dai muna tare ko me nazo da shi, ba za ki kware min baya ba.” Hajiya ta ce, “Kayi magana kai tsaye ni bacci nike ji in shiga ciki, don ka taki sa’a yau a nan nayi sallah.”_____
*🏚️RANA DAYA 🏚️*


CHAPTER 11


*BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*


*Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*

```ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925```

*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 Ga masu son Audio na littafin RANA DAYA shima muna dashi cmplt ku turo kudin ku ta account number din da muka bada can sama👆🏻👆🏻ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana*

*Masu son tallata masu hajar su suyi magana ta wannan number 09068032427 zamuyi maku cikin sauki*


```🧕🏻🧕🏻Ina kuke kasaitattun mata, Hajiyata kada ki bari ki zama bora agidan auren ki yi kokari ki tsuma kanki da ingantattun magunguna na gyaran jiki 07032895551🍉🍉🥥🥥```

```Mun zo maku da ingantattun magunguna masu kyau da inganci akwai TABAJE mai kyau gangariya 5litres 5k 07032895551```

```Muna da hadin Abulbulo, akwai Dan saudiya Hajiyata kada ki bari wannan hadi ya wuceki,dagajin sunan ABULBULO kinsan akwai aiki 4k ne kudin shi🙈🙈```

```Akwai sa Buzu Kuwwa,muna da kafi Budurwa uku sai angwada akansan na kwarai```

```🗣️🗣️🗣️Ina matan da mazajen su kebin matan banza to matso kusa Hajiyata Muna hadi na musamman duk macen da tayi amfani dashi mijin ta be karajin dadin wata mace, wannan hadi in kinsan kinada kishiya don Allah kada ki siyeshi 8k ne kudin shi🥥🍉```

```Akwai dahuwar kaza gangariya sai kin gwada Hajiyata zaki bani labari🙈🙈 akwai Dan dakarawa ya matseki tsam ya kuma saukar maki da ni'ima, akwai kafi sugar, kwallin mata dan matsi daya tamkar da dubu kenan🍉🥥```
```Akwai hadin Zama daram,munada miski mekyau original, akwai dahuwar kaza ta amare da uwar gida🐓🐓🐓 Akwai Sabulun infection ya matseki ya yi maki maganin infection,yasa wajen yayi sulbi Hajiyata```

```Muna garin katsina Muna aikawa ko ina a fadin Nigeria har ma da makotanmu Niger 07032895551```

```Sai angwada ake sanin na kwarai, amma don Allah idan baki shirya siya ba kada kiman magana 07032895551 muna bada sari game bukata🙏🏻🙏🏻```


Mun tsaya

Don Allah tashi muje koda zugata kayi ka
ji?” Abokina haka sai ya gaji da matsin Shatima ya tashi suka fita.
Allah yasa bata kai ga shiga cikin daki ba, lokacin da suka yi sallama a falonta. Bayan sun gaisa Shattima ya shiga kame kame ya rasa ta inda zai bullo ma al’amarin.
Ya ce, “Kaka nasan dai muna tare ko me nazo da shi, ba za ki kware min baya ba.” Hajiya ta ce, “Kayi magana kai tsaye ni bacci nike ji in shiga ciki, don ka taki sa’a yau a nan nayi sallah.”


Ya ce, “Ko kin shiga sai na bi ki. Dama dai ta hudun ce na samu, shi ne ni ke son ki sa ba ki a jone ta cikin bikin.”
Ta hade fuska, “Kai bana son maida bara bana, an riga an wuce nasan tunda kayi uku ai dole zaka yi ta hudu, amma ka bari sai can gaba.”
Ya ce, “Haba Kaka! Don Allah ni a hada rana daya, dama su hudu na gani a cikin gara kawai mafarkina.” Taja tsaki, “Mafarkin ka na banza tunda kai ba Annabi ba ne ba wani tabi’i ba ko Malami, har wani mafarki ke gare ka?”
Munnir ya ce, “Shi ne nima na gani da anyi magana sai ya ce mafarkin shi.” Shatima ya dubi Munnir, “Haba abokina! Kai fa ka san komai.”
Ya dubi Kaka, “Wallahi yarinyar Marainiya ce, na san ki da tausayi.” Ta ce “Ni har a fada min maraici, ni da ubana ya mutu tun ina ciki, uwata kuma ran da ta haife ni ta rasu?”
Shatima ya ce, “To ni dai kiyi hakuri in Alhajina ya zo ki ce kin yarda. Ta soma yunkurin mikewa. Munnir ya yi saurin mika mata sandarta. Ta amsa tare da fadin “Na gode dan nan kaje gida gurin iyalinka ka fita batun wannan uban wautar. Shatima ya taimaka mata har cikin daki yana kara rokonta amma sam ta ki magana.
Bayan ya sauke Munnir ya nufi gida. Bai zaci zai samu Hajiyarshi a falo ba tun da sha daya ta gota, bai ma lura tana nan ba sai da ya nufi samanshi ya ji ta ce, “Kai zo nan.
Gabanshi ya fadi, don tun jiya ta fada mishi cewa tana son ganinshi. Da safe a gurguje ya gaishe su wai yayi latti, da yamma ma haka ya yi ta goce ma haduwarsu, yanzu kuwa an ritsa shi.”
Ya zauna gabanta, “Gani Hajiya.” Ta ce, “Wai ka manta na ce ina son ganinka ne ka ke ta yi min goce-goce?” Ya ce, “A’a abubuwan ne, kiyi hakuri.”
Ta ce, “Ni ban yi fushi ba amma zan yi “Ai matsawar ka kasa fada min gaskiya.” Ya ce, ” ban taba yi miki karya ba Hajiya.” Ta ce, “Mene ne gaskiyar zancan da Momiyo ta fada min, wai ka samu mace ta hudu, haka ne?”
Ya ce, “Haka ne, dama da safe zan zo muku da batun.” Ya daure ya kau da tsoron shi ya fada. Ta ce, “To wannan karon babu hannuna a ciki, kaji na fada maka.” Ya ce, Hakuri za ki yi Hajiya, in na cike ai ba sauran in da zan saka wata ko?”Ta ce, “Tunda kai naga kamar Namamajo ne sarkin mata ai in ka hango wata zaka iya zuwa ka saki wata ka shigo da wata.
Ya ce, “Haba Hajiya, kar ki yi min fatan haka. Ki daure ki sama abin albarka gaba daya.” Ta mike tare da fadin, “Ba zan sa ba, dama kai ni ke jira in ji tabbaci, in haka ne in ce maka ba da yawuna ba.” ta nufi dakin Maigidanta ta bar shi nan zaune turus ya rasa tunanin da zai yi.
Ya mike yana rangaji ya nufi samanshi, zuciyarshi bata taba mai zafi irin wannan ba, gani yake kamar gara ya fasa auren sauran matan guda uku ya auri Salma kadai, domin ita ce ya dauki alkawari tsakaninshi da MahaliccinShi zai taimake ta.
Ya kalli abincin shi, ya kauda kai. Ya nufi gadon shi ya fada. Ruf da ciki ya kifa kanshi a kan filo, rabin kan shi ya soma ciwo, ya rasa tunanin da zai yi.
A haka bacci ya soma fizgarshi. Can kuma sai ya soma jin sanyi, yaja bargo. Abin kamar wasa sai jiki ya yi zafi.
Haka ya kwana, yana jin agogonshi yana kiran sallah amma ya kasa tashi. Badi’atu tazo kawo mishi abin kari sai ta ganshi a bargo, yana ta rawar sanyi ta ce, “Yaya! Yaya!!”

RANA DAYA

Da kyar ya ce”Kira min Hajiya.” Da gudu ta sauka, tun daga benen take kwala ma hajiya kira. A falon Alhaji ta same su tana kokarin hada ma Alhajin shayi.
A tsorace ta waiwayo ta ce, “Mene ne?” Ta ce, “Yaya ba shi da lafiya.” Alhaji da ke cikin dakin baccin shi ma ya fito da sauri.
“Ba shi da lafiya kuma?” Badi’atu ta ce, “Eh, yana ta rawar sanyi.” Gaba dayansu suka nufi saman. Sun tsorata da ganin yanayin shi, domin gaskiya ba shi da yawan ciwo.
A tare suka bude bargon, ya kanannade
jikinshi yana ta bari. Alhaji ya kama shi ya
tallafo mishi kai. “Babana me ke damunka?”
Hajiya ta ce, “Badi’atu, maza ki taso Mustapha ya fito da mota, yi sauri.” Ta tafi da gudu.
Uban ne ya tallafe shi suka sauka kasa zuwa mota. Alhaji ya koma ya cire malun-malun yasa jallabiyya ya dauki kudi. Asibiti mafi kusa suka je ana shiga dashi, Likitan baya nan.
Alhaji ya hau fada, yana cewa wane irin Likita ne har yanzun bai zo asibitin shi ba. Nurse ta ce, “Yi hakuri Alhaji, bari a kira shi, gidan shi babu nisa. Sauran Nurses kuma suka sa shi a gado don yi masa taimakon farko. Sun duba shi suka sa
masa ruwa tare da allura.
Iyayan da Mustapha kaninsa suna tsaye a kanshi suna yi masa sannu har lokacin jikinsa yana rawar sanyi, gashi ba su rufe shi ba, kuma sun kunna fanka.
Likitan ya shigo da sauri. Ya ba Alhaji hannu suka gaisa, Alhaji ya ce, “Haba Likita! Bai kamata ace ba ka fitowa da wuri ba, asibiti mai zaman kanshi a ce an zo babu Likita?”
Ya ce, “Kayi hakuri Alhaji, jiya sai kusan karfe uku na dare na bar asibitin nan mutum uku muka yi wa tiyata. Ya isa gaban Shatima ya soma da bude idanunsa yana tambayar abin da ke damunsa.
Alhaji ya ce, “To mu dai lafiya ya kwanta jiya.” Hajiya ta ce, “Ni da har magana mun yi da shi kafin ya kwanta din ma.”
Likitan ya taba jikinshi ya ji rau da zafi. Ya dubi ‘su Alhaji ya ce, “Ku dan zauna a waje.” Suna fita ya cire ma Shatima ruwan sannan ya taimaka mishi ya cire rigar jikinshi. Shatima ya ce, “Sanyi ni ke ji.” Likita ya ce, “Kar ka damu, zaka daina ji yanzun.” Ya kalli Nurse din da ke tsaye ya ce mata ta kawo mishi wata allura, ya fada mata sunan
allurar ta fita. Ya maida masa ruwan yana ci
gaba da yi masa tambayoyi. Bayan an kawo allurar ya yi masa ita a cikin ruwan, sai ya ce “Kar ka damu gajiya ce da zirga-zirga, sai kuma rashin bacci. Yanzun za ka yi bacci ka huta a nan zuwa jibi zaka wartsake sarai.”
Shatima yayi saurin kama hannun Likitan mai kokarin fita. Ya ce, “Likita don Allah ina son kayi wani taimako daya, nima dai taimakon zan yi.
Likitan ya dawo ya tsaya. Shatima ya ce, “Ina son ka ce ma iyayena damuwa ce ke tare da ni, don haka kada suke yawan matsa min, kuma ka ce musu su tambaye ni damuwar don suyi saurin kauda min ita saboda zata iya haifar min da wani ciwo.”
Likitan ya ce, “Amma kai Lauya ne ko?” Shatima ya yi dan yake tare da fadin “A’a.” Likitan ya ce “Ka iya tsara magana. Zan fada
musu haka din tunda ba cewa kayi a ce kana da wani ciwo ba.”
Ya leka ya ce, “Alhaji za ku iya shigowa.” Suka shigo. Allah Sarki, iyaye duk sun damu suji me ke damun dansu har suna hada baki gurin tambayar Likitan “Me ke damunsa?” Ya ce, “Akwai rashin samun ishasshen bacci, zirga zirga da gajiya.
Sannan kuma akwai wata damuwa a tare da shi wadda ya ki fada min ita. Ya kamata ku san ta don kuyi gaggawar raba shi da ita, domin zata iya haifar masa da katuwar matsala.”
Suka ce, “To Likita, zamu bincika.” Yana fita Hajiya ta ce, “Shatima me yake damunka ne ka boye mana?” Alhaji ya ce, “Haba Hajiya, ki bari tukunna ya samu sauki mana. Zai fada mana kuma za a magance ta.”
Shatima na jin su ya yi lamo, a hankali naman jikinshi ya daina rawa, bacci ya kwashe shi.
Labari ya watsu a dangi cewa Shatima yana asibiti. Nafisa ta samu labari, hankalinta ya tashi take ta fasa zuwa Makaranta ta ce “Mama ba zan jira ku ba, bari in je in ganshi.” Ita ce ta fara zuwa a cikin Amaren Shatima.
Lokacin da ta zo Hajiya tana zaune a bencin kofar dakin da wasu kawayenta. Nafisa cikin kunya ta durkusa ta gaida su, ta kuma tambayi jikin nashi. Hajiya ta ce, “Da
sauki, ki shiga yana dai bacci, Mustapha ma yana ciki.”
Tana shiga idanunta na kanshi, yana kwance sambal jikin shi babu riga, tausayinshi yasa idanunta kawo ruwa. Ta kalli Mustapha.yaya me ya ke damunsa?” “Zazzabi ne kawai, kar ki damu. Da ya farka
zai warware.” Muryarta na rawa ta ce, “Allah
yasa haka. Allah dai ya ba shi lafiya.” Mustapha ya tashi daga kan kujerar da yake zaune ya ce, “Ki zauna.” Ta ce, “A’a da ka bar shi.” Ya ce, “Bari in dan fita in mike kafa ma. Ta zauna shi kuma ya fita. Ta tsura ma halittarshi ido, a ranta tana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login