Showing 3001 words to 6000 words out of 35955 words

Chapter 2 - Rana Daya Book 1 Hausa Novel Complete

na Katsina ya ce su bar ni in zabi miji da kaina.To sai Yayanmu Aliyu ya kawo min form din School of Nursing, shi ne ma na maida hankalina a kan karatu.Ya ce, “Yanzun kin gama kenan?” Ta ce, “Eh,
har na gama Practical dina, kuma na fara aiki a
wani asibitin kudi da ke nan unguwar.
Ya ce, “Shekarunmu nawa da rabuwa ne har da ki ka yi karatu ki ka gama?” Ta ce, “Shekaru uku fa da watanni kenan.”.
“Hmm! Haka ne. Za ki iya tuna rabuwarmu ta
karshe?” Ta daga kai kamar mai son tayi tunani. Ta ce, “Mun rabu ne wata ranar Asabar wadda ba zan taɓa mancewa da ita ba.Mun rabu kafin Asabar din a kan magabatanka
zasu zo, amma maimakon haka sai na ganka da
labarin wai Mahaifanka sun ce za ka tafi Dubai don kayo Degree na biyu. Ta lumshe ido kafin ta ci gaba da magana. “Ba zan iya misalta bakin cikin da na tsinci kaina a wannan ranar ba, domin a cikin gida ina fuskantar
matsin lamba a kan in fitar da mijin aure. Na ce to, ka sa a zo a fadawa iyayena ko za su amince in jira ka. Washegari Lahadi ku ka zo kai da abokinka Munnir don neman yardar iyayena su bar ni in jira ka dawo, sai Mahaifana suka ce sam! Ba zan jira ka ba, aure za su yi min.” Ta sake yin shiru tare da sauke ajiyar zuciya, sannan ta kalle shi. “Haka ne?” Ya ce, “Ashe dai
ba ki manta ba. Ni Yayanku Aliyu ma ce min yayi
dama wani abokinsa yana sonki, shi yasa na yanke
hukunci cewa yanzun kin yi ‘ya’ya biyu.”
Tayi ‘yar dariya, “Duk sun zo na ce ban son Ya ce, “Ashe rabona ce, amma kina da su. kishiyoyi fa!”
Ta zaro ido, sannan ta dube shi “Kayi aure ne?”
Ya ce “Rana daya za a sa ku a lalle.” Ta ce, “Nasan kana zolayata ne.” “Zancen gaskiya kenan Aliya, ku uku ne. Bayan na tafi Makaranta cike da bakin cikin
rabuwa da ke, sai Allah Ya hadamu da Amna, ‘yar
asalin jihar Kano ce, tana da dangantaka da
Masarautar Kano., Babanta mai kudi ne sosai.
Amna ta birge ni da halayanta na kamun kai, da nutsuwa, haka yasa wasu dalibai ke surutun tana da girman kai. Gidan da take kusa da namu ne mu kan hadu lokuta da dama in Makaranta, ko in mun je sallah. zamu shiga
Ni dai tana birge ni, kuma ina son mu ke magana. Sai wata rana nayi mata sallama ta amsa muka gaisa, na ce ita ‘yar Nijeriya ce a wacce jihar? Ta ce Kuno. Tun daga lokacin muka soma magana har
soyayya ta shiga tsakaninmu, sai ma na gane son
da take min ko kwatanshi bana yi mata. Har mun
shirya batun aure da ita.
Kasancewar zan rigata dawowa sai muka shirya zan jirata. Na rasa sadarwa tsakaninmu da ita sakamakon wayoyina da Laptop da barayi suka sace. Yau din nan ta kira ni ta ke sanar min dawowarta kasar.”
Aliya ta danne kishinta ta ce, “To ka ce mu uku ne dayar fa?” Ya ce, “Nafisa jikar Kaka ce, ina ce kin santa ma?”
Aliya ta ce “Dama kuna soyayya da Nafisa ne? nasan ta mana.” Ya ce, “Kafin in dawo iyaye suka kulla, yanzun su ba su san ma da batun Amna ba bare naki. Yanzu dai za mu gyarota da Kaka, saboda in ta yarda dole Baba ya yarda, shi kuma in ya cije dole Hajiya ta saki.”
Aliya ta ce, “Tab!” Ya ce “Ba za ki iya ba ko?” Ta ce “A’a in ana auren mata dari Shatima ka aura ba zan ki ba, na dai tausaya maka ne.” “In kuma na samu ta hudu sai in cike kawai.”
Ya fada cik zolaya. Aliya ta ce, “Ni dai yanzun
ka fada min wa ka fi so?””Wadda ta fi sona.” Ya bata amsa a takaice tare da mikewa. “Bari in tafi ko, amma kafin nan ki tashi kije gida zamu yi magana da Kaka.” Ya mika mata wayarshi karama.”Sa min lambarki, ki ajiye da sunan da ki ka ga
ya dace.” Ta saka lambar tayi shiru tana tunanin
sunan da zai dace.
Ya ce, “Ki zabi duk sunan da ki ka sa shi ne sunanki a bakina.” Cikin sauri ta rubuta (My Love) ta mika mishi. Ya amsa ya kalleta.My love?”
Tasa hannu ta rufe fuska cikin jin kunya. Ya ce, “Zan kira ki da wannan sunan a gaban kowa ma, kuma ina son ke ma ki kira ni da shi a gaban kowa.
Ya nuna mata hanya da hannunshi, “Je ki
sallami Kaka.” Ta tsugunna a gaban Kaka ta ce,
“Zan tafi gida.” Kaka ta ce, “Har kun gama hirar?
To Allah Ya tabbatar muku da alkairi.” Har bakin falo ya rakata, sannan ya dawo gurin Kaka. Ya ce, “Kin ga abin Allah ko Kaka!”
Ta ce, “Ai ni na zaci ita ce ta biyun.” Nan ya bata labarin Amna. Ya ce, “Goyon bayankı kawai ni ke nema.” Ta ce, “Shatima nemi komai gurin Allah. ni ai in hudu za ka yi ina murna, don bana son ragon namiji.



*Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*

```ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925```

*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427*_____
*🏚️RANA DAYA 🏚️*

CHAPTER 3

*BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*

*Wannan littafin na kudi ne akan farashin 300,idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*

```ACT<<0700549935
Halima Abdullahi Access bank sai ku turo shidar biya ta wannan number 09028485925```

*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427*

*Masu bukatar a tallata masu hajar su ko link din group din su na kasuwanci suyi magana ta wannan number 09068032427 zamuyi maku akan farashi me sauki*


Mun tsaya

Ya nuna mata hanya da hannunshi, “Je ki
sallami Kaka.” Ta tsugunna a gaban Kaka ta ce,
“Zan tafi gida.” Kaka ta ce, “Har kun gama hirar?
To Allah Ya tabbatar muku da alkairi.” Har bakin falo ya rakata, sannan ya dawo gurin Kaka. Ya ce, “Kin ga abin Allah ko Kaka!”
Ta ce, “Ai ni na zaci ita ce ta biyun.” Nan ya bata labarin Amna. Ya ce, “Goyon bayankı kawai ni ke nema.” Ta ce, “Shatima nemi komai gurin Allah. ni ai in hudu za ka yi ina murna, don bana son ragon namiji.

Shatima mai sunanka gwarzo ne, mu hudu ya aje, ba dai rana daya ba. Amma tsakaninmu babu nisa. Duk ciki ni ce kararmu, yau ina abokan zaman nawa? Ina shi Maigidan namu? Duk sun amsa kiran Ubangijinmu.
Mun zauna da dadi-ba-dadi, kuma an yi zaman mutunci, kullum ina yi musu addu’ar samun rahamar Allah, kuma. Allah Yasa tawa tayi kyau irin tasu. The de jah manch slara ar Tilb 2
Ya ce, “Amin Kaka.” Ta ci gaba da fadin, “Mata hudu ba matsala ba ne matsalar tana tasowa ne daga gurin namiji in ya kasa adalci a gidansa.”
Ya ce, “Kaka ni ai renonki ne ko? In sha Allah zan yi ba zata.” Ta ce, “In dai sunanka Muhammad Ja’afar, kuma ka amsa lakabin ka na Shatima, to kuwa nasan kai gwarzo ne.”

*******
Tun da aka soma yi wa Malam Adamu gashin kashi sai jikin ya soma sauki. Dubu ishirin da suka samu a gurin Alhajin nan ta taimaka musu sosai.
Ummu Salma ta sauka daga cikin Adaidaita dauke da kwanukan samira tuwo da miya. Ta shiga cikin asıbitin da hanzarinta don kaiwa Mahaifanta tuwon da ta yo bayan ta gama suyar Wara, ta samu riba tayo cefane ta girko.


Tana taka matakalar da zata hau sama in da dakin maza yake, sai ko kafarta ta zame, takalmin kafarta silifa mai soso ya taimaka gurin zamar da
ita har ta kai kasa.
Ba damuwarta faduwar da zata yi ba, damuwarta kawai kar abincin Mahaifanta ya zube. Sai dai ta makaro, domin tuni abincin ya tarwatse a kan siminti.
Wata ma aikaciyar gurin ta soma yi wa Salma fada. “Ke da Allah can! Kin zo kin bata wa mutane guri da wannan kazamin tuwon naku, da Allah zo ki share shi.”
Ta mike tana kukan bakin cikin asarar abincin
iyayenta. Daidai lokacin da wata mai sharar asibiti
ta iso. Wannan ma’aikaciyar tana ci gaba da yi wa
Salma sababi. Mai sharar ta ce, “Irin kazantar da ku ke yi a gidanku shi ne kin zo kina yi mana a nan guri din?” Ta tambayi Salma cikin hausarta mara dadi.
Salma dai sai kallon su take yi. Ma’aikaciyar ta ce, “Ba za ki kwashe mana warman kazantar a nan gurin ba? kalli wai wannan ne abincin da za’a ba mara lafiya. Ta ya ya zai warke yana cin irin wannan kazanta?”Cikin mutanen da suka taru a gurin suna kallo sai wata daga ciki ta ce, “Gaskiya bai kamata ku saka yarinya karama a gaba kuna mata ihu ba, ita ma ai ba za ta so ba tayi asarar abincin da Allah ne kadai yasan yanda suka samo shi
Nan suka dawo kan matar, hayaniya ta soma yin sama. Tasa hannu zata dauki tuwo, sai ta ji an ce”Bari kar ki taba.” Tana dagowa sai taga Alhajin nan shi da wani a cikin jerin mutanan da suka taru a gurin.
Ya ce, “Ina ma su yin sharar asibitin?” Matar ta ce, “Mu ne muke shara, amma ita ne ta kwashe wannan din da ta zubar.”
Ya ce, “Zo ki wuce, ku ku bar shi in ba za ku
kwashe ba.” har ta nufi sama ya ce, “Zo nan.” Ta
nufo gurinshi, ya ce “Bimu daina kukan.” Ta ce,”To.”
Tasa kasan hijabinta tana share hawaye. Ya ce.. “Kin gane ni kuwa?” Bayan sun je gurin mota. Ta ce, “Eh, na gane ka. Kai ne wanda ka taimake mu shekaranjiya.”
Ya ce. “Sunana fa?” Ta sake kallonshi, sannan ta girgiza kai “Ban san sunanka ba.” Yayi murmushi, sannan ya ciro kudi a aljihunshi ya nuna mata wata hanya.”Ki bi nan ki dan mike za ki ga shagunan saida abinci, su wanke miki kwanukan sai ki sai musu abinci.”
Hannu biyu tasa ta amshi kudin, tana ta godiya. Shima abokin yana cikin mota lokacin, ya ciro dubu daya ya ce, “Kara mata.”
Salma tayi godiya, sannan ta mike hanyar da ya
nuna mata cikin murna tana kirga kudin, dubu
hudu ne cas! Duk da dubun abokin.
Sakwara ta sai musu da miyar agushi, ta sai musu lemon roba da ruwan sanyi. Tana isa Innarsu ta idar da sallar La’asar. Ta ce, “Yau ba kasuwa ne hala muka ji ki shiru
Ummu Salma?” Ta ce, “Ai nazo tun dazu ɓarewa
ya yi. Nan ta basu labarin komai, sannan ta kawo
sauran kudin ta ba Innarsu. Inna ta ce, “Ba na amsa duka ba Salma, bani dai dubu guda sai ki rike dubu biyun, ke da ki ke dawainiya da mu. Shi kuma Allah Ya shi masa albarka, ya saka mishi da alheri, ya biya masa bukatunsa shima.” Salma ta ce, “Amin Inna.
Sai bayan Isha’i sannan Innarsu ta ce, “Maza ki zo Salma ki wuce dare yana yi.” Ta ce, “To Innarmu, bari in zo in je.”
A bakin titi tana jiran mota, wata ma’aikaciyar jinya ta fito itama tana jiran mota. Salma ta dube ta cikin faduwar gaba, don tana zaton matar dazu ce da ta yi mata cin mutunci.
Ta saci kallon matar duk da akwai duhu ta gane ba fuskar waccan ba ce. Dan Adaidaita ya zo wucewa, tare suka hada baki gurin fadin. “Tudun Wada.”
Ya tsaya ya dauke su, ma’aikaciyar ta ce, “Ashe unguwa daya za mu?” Salma ta ce, “Eh, nan za ni.” Ta sake cewa, “Kin zo duba mara lafiya ne?”
Salma ta ce, “Eh, Babana aka kwantar.”
Ma’aikaciyar ta ce, “Allah Ya ba shi lafiya.”
Salma ta ce, “Amin.” A zuciyarta ta ce, ‘Ashe dai
ba duka Nurses din nan ba ne suke da wulakanci, da ko har na tsane su.” Alhaji Isa Shatima yana zaune a falonsa da
misalin karfe tara da rabi, labaran kasa suke kallo
tare da matarsa Hajiya Halima.
Dukkansu Tea suke sha wanda suka maida shi al’adarsu duk dare Daidai wannan lokacin ya kalli wani daurin auran da aka gama nunawa na ‘yar. wani Minister daga cikin Ministoci.
Ya ce, “Au! Hajiya Halima har na tuna.” Ta ce, “Ka tuna me?” Ya ce, “Da na je duba Hajiya yau da safe take fada min wata magana da na kasa ce mata komai.” Ta maido da hankalinta kanshi sosai. “Meta ce?” Ya ce, “Shatima wai mata uku zai aura…”
Kofin hannunta ya kusan faduwa, sannan ta kware da ruwan zafin da ta kurba. Dan tari ta shiga yi har ta yi zaton asmarta ce zata tashi, sai sannu Alhaji ya ke yi mata.
Kusan minti biyar sannan ta dawo hayyacinta. Idanunta jajir ta ce, “Amma dai wasa ya ke yi ko?” Alhajin ya ce, “Babu alamun wasa a fuskar Hajiya lokacin da take yin maganar.”
Hajiya ta ce, “Hmm! Wannan hira ce ya ke yi. Ban da Shatima ina zai kai mata uku?” Ya ce, “Na fadi hakan sai Hajiya ta min gorin da na gwammace ban yi magana ba sannan ta saki zancen alamun an wuce gurin.
Hajiya Halima tayi shiru tana tunani. Badi’a ta shigo falon zata dauki takardarta wadda tayi home work da rana. Hajiyar ta ce, “Badi’a zo nan, kira min Yayanku a samansa.
Kammala aikinsa ke da wuya ya rufe Laptop din yana hamma, ya sani ba bacci ba ne yunwa ce ke damunsa, don bai ci komai da rana ba.Ya ji an kwankwasa kofa. Ya ce, “Shigo.” Tayi sallama ya amsa, ta ce “Hajiya tana kiranka Yaya.” Ya ce, “To ina zuwa Badi’atu.”
Gabansu ya zauna ya gaishe su, sannan ya ce, “Gani Hajiya.” Ta gyara zama ta hanyar dora kafarta daya a kan daya, duk lokacin da tayi hakan ya san umarni zata ba da na dole, don haka sai ya sake nutsuwa don jin abin da zata zo da shi.
Koda yake tuni ya soma hasashen abin da zata yi magana a kai, zancen auransu da Nafisa…
Ta katse tunanin shi da cewa, “Yanzun Mahaifinku ya ke bani labarin wai za ka auri mata uku rana daya?”
Ya sunkuyar da kai cikin mamakin har zancen
ya riske su da sauri haka! Yana tunanin lallai da
gaggawa lamuran za su ke zuwa masa. Ta ce. “Kayi shiru Shatima?” Ya sake sunkuyar da kai. Ya ce, “Haka ne Hajiya.” Ta ce, “Amma ka fita a tunaninka ko? Ya ya za ka yi da mata uku rana daya? Yaron ka da kai Shatima za ka dora ma kanka matsalar iyali da yawa furfura ta fito maka ko? To ka sani ban amince ba sam-sam!”
ya dan gyara zama. “Hajiya duk al’amarin ya zo ne ba da shirina ba, sai da shirin Ubangiji. Kuma Hajiya shekaruna talatin da shida, ai ko na girmi yaro.Sannan addinina bai hana ni ba, Allah a cikin Alkur’ani mai tsarki ya fada mana cewa, mu auri mata biyu, ko uku, ko hudu. In ba za mu iya adalci ba sai mu auri daya.
To ni kuma ina da tabbacin zan iya adalci, don ina alfahari da irin tarbiyyar da ki ka bani, adalcin da ki ka tsaya a kai ki ke yi ma kowa da shi muka dogara.
Kuma shi ni ke kwatantawa a ko’ina, da shi
kuma zan zauna da mata ko nawa ne. Ina son ki sa albarka a cikin wannan auran, albarkarki ita ce ginshiki Hajiya.” Ta ce, “Ai kai Shatima ko dan siyasa ya fi ka iya zance kuwa? Ni dai kaje kayi tunani a kai, rike
mace ko guda daya ce sai jan namiji. Amma kai ka
ce rana daya guda uku!” Ya ce, “Hajiya ki sa albarka.” Ta ce, “Yanzu dai ba zan saka ba, in kana son in saka sai dai ka duba a cikin ukun ka dauki guda daya, ka zaɓa in ma ba Nafisar ba ce dai wadda kafi so.
Don ka san an ce so daya ne tak! Kuma mace daya ka ke wa a cikin ukun, don haka sai ka cire ta.”
Ya kalli Mahaifin nashi wanda bai ce kala ba tun da suka soma magana. Ya ce, “Alhaji ba ka ce komai ba?” Ya ce, “Ba ni da ta cewa Shatima, duk abin da yafi alkhairi Allah Ya zaba, tunda ka samu daurin gindin Tsohuwa a ta gefena ka kai makura.
Shatima ya yi murmushin nasara a ta wannan gefen. Hajiyar ta ce, “Ka je kayi tunani nan da jibi.” Shatima ya mike cikin rangaji tare da fadin “Badi atu ta kawo min abinci Hajiya.”

**
Tunda Kaka taji sallama tare da kamshin kalolin abinci ta tabbatar cewa Hajiya Halima ta diro gidan, domin wannan ita ce shaidar farko da take fara alamta mata cewa Surukar arziki ta shigo gidan.
Ta fito daga cikin dakinta tana dogara ‘yar sandarta mai kyau, wadda ta ke taimaka ma kafafunta wadanda suka yi rauni.
Ta amsa sallamar cikin murna, ta zo ta zauna kan kujera. Hajiya Halima ta zauna kasa kan kafet. Badi’a da Maryama suka shiga jere kulolin da Hajiya Halimar ta zo da su.
Suka sake fita suka shigo da sauran. Kaka ta ce, “Ba ki gajiya Hajiya Halima, kowane lokacin in za’a zo duba ni sai an zo min da abin tabawa. Allah Ubangiji yasa ke ma ‘ya’yanki suyi miki. Ga jarumin namiji nan Shatima, cikin matansa Allah zai sa wata ta miki fiye da abin da ki ke min.
Hajiya Halima tayi murmushi bata amsa ba don nuna kara ga uwar mijin tata.
Bayan sun gaisa ne suka shiga hirar duniya, Badi’atu autar Hajiya Halima, da Maryam yar gidan Hajiya Saude kanwar Baban su Shatima wadda ke gaban Kaka, sun kule a daki suna tasu hirar.
Hajiya Halima ta kalli Kaka ta ce, “Hajiya sai kuma wannan mashirmancin ya zo da zancen zai auri mata uku rana daya, wannan ai labari yake yi. Dubi masu mace daya ma yanda suke fama a wannan zamani, ni dai na ce masa a’a ya dai zabi
daya, in ma karin ne sai ya bari ya ga kamun
ludayin zaman, in yaso can gaba ya kara.” Kaka dai ba ta ce kala ba, har Hajiya Halima ta kai karshe. Kaka ta ce, “Zubo min abin da ki ka zo da shi in lasa ko nafi samun abin fadi.”
Dariya suka yi su duka sannan ta ce, “Farfesun kajin zan zubo miki, ko na kafar Sa? Sannan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login