Showing 27001 words to 30000 words out of 39065 words
four years muna tare cikin kauna da fahitar juna, mun yi wa juna alkawura masu yawa amma Madinah ta saka kafa ta take su tayi fatali dasu rana daya, don haka daga kanta na daina bata lokaci na a kan yammata wallahi. Duk marasa amana ne.
Madinah ta dusar da hasken sauran mata daga idanuna Mama, ba wadda nake ganin farin ta. In fact, Mama bani da niyyar aure nan kusa.
Ban san me kaddara ta tanadar min gobe ba!.
Mama ta ce in uban Madina baya son ka sabida ya raina ajin uban ka, su wadannan uwa da uban duka sun zo da kan su sun ce ka yi musu, suna son hada jini da ni, saboda sun san darajar mu da martabar mu, ni kuwa bana tulawa masoyi na kasa a ido. Amma ban isa in maka dole ba.
Duk abinda uban Madina ke takama da shi na tarin arziki da ilmi da har yake ganin baka isa auren diyar sa ba, uban Sadiya ya mallaki goman sa,
Da sauri Sarham yace ko ita Madinah ba dalilin da yasa na so ta ba kenan Mama, na rantse ban taba sanin waye ubanta ba har sai bayan ya yanke alaqar mu.
Na so Madinah ne akan wani dalili Mama. dalilin kuma shine. kokarin ta a karatu. zai fara bata labarin irin kokarin Madinah da yadda take ‘excelling with high grades a kowacce jarrabawa Mama ta katse shi da karfi, inda tace bana bukatar ji, na gaji da zancen Madinah Attahiru Sarham tunda ba itace autar mata ba.
Ka karbi masu son ka, ka rabu da tsammanin warabbuka.
In dai labarin nan ne ka bani shi yafi sau shurin masaki, yafi cikin carbi, har na riga na haddace shi, kana son Madina saboda kokarin ta akan karatu, na gaji da jin wannan, abinda baka sani ba, Madina ba itace karshen masu kokari ba, Sadiya ma tana da irin nata domin kuwa Quantity Surveyor ce. Kuma uwarta ta tabbatar min tana son ka sosai, ba wai ita ta ga dacewar abin ba Sadiyar ce da kanta tace tana son ka.
“Ahap! Anzo wurin. Mama ta bare ta gabadaya. Sarham ya fada kasa kasa su Mama an kara bare ta, to ai ni Mama bazan taba auren macen da ta ganni wai ta ce na yi mata ba, komai lalacewar zamani akwai mata masu aji, wadda ba ni na ce ina son ta ba in the first place hankalina bazai taba kwanciya da ita ba”.
Duk ta inda Mama ta bullo don Sarham ya karbi tayin yar aminiyar ta Sadiya Sarham sai ya zuqe, amma fa cikin lallami da dabara yake bin Mama don su yi rabuwar salama. Ya san kan Maman sa sarai, yana yi yana dariya da hilatar ta yadda bazai bata mata rai ba.
A karshe Mama ta gaji da jainjar, ta sakar masa inda ta ce Sarham! Na baka shekara daya ka kawo min matar da kake so ka aura, mai kokari irin Madinah wadda hankalin ka zai kwanta da ita din, tunda kai dai a kan Madina kowa dakiki ne, to ka nemo mai kokari irin nata, kafin shekara daya, amma ni wannan Madinar ko zancenta bana son ji.
Sarham idan shekara ta zagayo baka kawomin mata ba na rantse Sadiya zan aura maka, kana so ko baka so, in kuma dauketa in bika da ita har inda kake.
Sarham ya ce to Mama addua zaki yi min Allah ya kawo mai kama da Madinah, fara kamar balarabiya, doguwa siririya mai gashi yala-yala har gadon baya, sannan mai asalin kwanya a karatu irin ta Madinah Sorondinki. Tsaki Mama tayi ta tashi ta bar masa dakin don haushi. Ta sani daga Madina har iyayen ta babu wanda ya damu da shi shi, kadai yake kidan sa yake rawar sa a kan ta.
Ita kuma bazata taba maraba da inda baa son nata ba.
Washegarin ranar Sarham ya ga cewa ya kamata ya je wa su Inna sallama, kai zai yi kewar kawar sa Inna Safiyya… yadda baa zato, tsakanin itada Sumayyah bai san wa zai fi kewa ba.
Wata zuciyar a can kasan kirjinsa tayi whisphering a sace, inda tace masa MISKINIYA KULU!” Da sauri Sarham ya kalubalanci zaciyar sa da cewa capital NO! he will never HAUWA_KULU, zai yi kewar kowa tabbas, har Surayyah da basa jituwa, amma ko kadan ba zai yi kewar Maijidda ba, ba don komai ba ko don halin koin kulan ta da miskilancin da take nuna masa, da rashin maganar ta da sakewa da mutane wanda baya bari ayi sabo mai shiga jiki da ita irin wanda har zaayi kewar ta don an daina ganin ta a wuri.
Shin wai kodai shi kadai Maijidda take nunawa halin koin kula, da shariya, da miskilanci, da rashin walwala wani lokacin ma sai ya ga kamar sad face a tare da ita idan taji muryarsa a gidan su???
Ya isa gidan ana kiran sallahr Isha, Inna na alwalah Hauwa na cin tuwo. Yayi sallama Inna ta amsa Kulu ko kamar yadda yayi tsammani a cikin cikinta ta amsa masa sannan bacin ran da yake zargin gani ya dan bayyana kansa a kan fuskar ta. Sai Sarham ya lallaba ya dauke kwanon tuwon daga gaban ta ba tare da yayi magana ba, ta shafa gabanta don kara kai loma sai taji wayam, babu kwanon, amma bai sani ba kamshin turaren sa da ya nashi hancinta (Oud Abyad) ya tabbatar mata shine a wurin ya dauke kwanon.
Baya jan ta da wasa amma yau da yake sallama ya zo, shiyasa ya ke son ko yaya ta kula shi. Dan murmushi tayi, wani basakkwacen murmushi ta share shi, ta janye hannu ta koma gefe, ai kuma ta mike don wanko hannu, tana tafe kanta tsaye zuwa famfo kamar ba mara ido ba, ba tare da ta nemi Inna tayi mata jagora ba. sai data kai bakin famfon ta kunna sannan tace ka hutar ni dauke kwanon, dama na koshi ai. Mamaki yasa Sarham rufe baki yana dariya yace.
Inna ashe idon mu ya bude! Inna tace fata nagari lamiri, me yasa aka ce muyi fatan alkhairi akan komai? Ai don bamu san tasirin bakunan mu ba, mai yuwuwa Allah ya biye bakin ka watarana Likita”.
Sarham ya ce haka yake Inna, amma shi ya san da kamar wuya wai gurguwa da auren nesa, sai dai duk wani mumini yayi amanna da cewa ba abinda ya gagari Allah, suma likitocin lalube suke yi a cikin duhu. Sanin gaibu sai Allah. Ya russuna har kasa ya gaida Inna, ta kawo masa darduma ta shimfida, sai ya ce,
“tunda sallah za kuyi, muyi jami gaba daya kawai, ban taba jan ku sallah ba Inna. Maijidda dauro alwallah.
Daga inda take tsaye a jikin famfo tayi dan sakale! Bata ce toh ko aah ba, don jiya ta fara ganin jinin alada a rayuwar ta, itama bata sani ba, Inna ce ta gani a jikin zanin ta ta gaya mata, ta kuma taimaka mata wajen kunzugu, ta koya mata yadda zata dinga killace kanta da tsaftataccen tsumma, dankwalin sabuwar atamfarta mai tsafta ta dauko ta tsaga shi gida biyar ta koya mata amfani da shi, ta kuma gaya mata baa sallah da komai na ibada sai an samu tsarki, koda yake duk ta sani a makaranta tun kafin ta fara din
Duk da cewa ta tsorata da Inna ta gaya mata ta fara alada, ta kuma tabbatar mata yanzu ta girma dole ta kula da kanta da tsare mutuncin ta daga wannan lokacin, da kuma koyon yadda zata ke muamala da maza daga yanzu.
Inna ta zaunar da ita ta ja kunnen ta sosai, ta gaya mata yanzu da girman nan ya hau kan ta ko hannun ta namiji ya kama cikin shege ne zai shiga jikin ta kuma haramun ne. ta tsoratar da ita sosai akan maza ko yaya take dasu. Yinin jiya zungur laccar da Inna ta wuni tana yi mata kenan. Sarham ya gaji da jiran Kulu ta zo su tada sallah, don tunda ta shige daki ta ki fitowa ya dauka hijabi zata shiga ta dauko amma shiru kake ji. Sai Inna ce ta sadda kai ta ce,
ja mu sallahr ka ji! Kuluwa girma ya zo!.
Sarham cikin rashin fahimta ya tambayeta girma kamar yaya?.
Duk surutun Inna da yadda ta ke sakewa da Sarham wannan karon kasa fada masa Hauwa ta fara alada tayi, ta hau inda-inda, har ya gaji ya tada sallah, amma daga karshe a matsayin sa na likita malamin kiwon lafiya sai ya dago su.
Abu daya zai hana mace sallah uwarta ta bi bayan ta shine idan tana fashin sallah.
Ikon Allah, har nawa Hauwa-Kulu take? Maiyuwuwa kuma irin jikin ta kenan. Irin su kuma sune masu haihuwar wurwuri. Koda yake kanwarsa Sumayyah ma haka ta fara da wuri, kuma shi ta fara gayawa tana kuka, don ta kasa gayawa Mama da Surayyah, tana ganin wani mugun abu ne ya faru da ita, ba zai manta ba shi ya fara saiwa Sumayya always pad ko Mama sai da Sumayya tayi wajen sau uku kafin ta sani.
Bayan sun idar da sallah shi da Inna, kasa gaya mata tafiyar sa Saudi yayi, saboda sabo, da wata irin kewar su da tazo ta rufe shi, Inna kuwa tana ta hidimar hada masa tuwon masara miyar kuka da manshanu, ga yajin daddawa a gefe, ta kawo ta aje masa da ruwan randar ta mai sanyin dadi. Taga yayi shiru ya kasa cin abincin da doki kamar yadda ya saba, cikin kulawa Inna ta ce, likita ya dai? Jikin ko garin?” Ya nisa, kafin yayi kundumbala ya ce babu ko daya. Inna sallama na zo muku, zan bar kasar nan!.
Ba Inna kadai ba hatta Kulu da ke daki fitowa tayi da sauri daga uwar dakin data je ta boye jin abinda Dr. Sarham yake cewa.
Tafiya ta same ni zuwa kasa mai tsarki, zan tafi karo karatu na akalla shekaru uku, Inna ina fatan zaki cigaba da tayani kula da karatun Maijidda har ta kammala, alkawari ne na dauka tsakanina da Ubangiji sai na ga ta kammala sakandire hankali na zai kwanta, to amma ga yadda Allah ya tsara min.
Ina fatan kafin in dawo Inna zaki tsaya akan karatun ta na sakandire har Allah ya cika min wannan burin nawa”.
Inna gaba dayan jikin ta ya mutu. Bata san ta saba da Sarham ba sai yau da yake maganar barin kasar mu baki daya, bata san dimbin alkhairin sa mai yawa bane a gare su, sai yau da zai bar su. Kokari take ta mai da hawayen da suka kawo mata cafka, don kada ta kara karya masa guiwa da tata karayar, don hatta yadda yake maganar kadai zaka san ya fi ta shiga damuwa da kewa, ya karaya.
Hauwa dai ba tace komai ba, amma a cikin ranta wani irin ‘dakace’ take yi, cewa take inamainama! Inama na ga fuskar sa yau, inama nayi masa kallon karshe yau kafin ya barmu, wanda zai sa kullum nake tuna fuskar sa, in yi ta masa addua!.
Don duk tsayin lokacin nan da suka kasance da Sarham a cikin rayuwar su kusan koda yaushe cikin wannan fatan take, ba don komai Hauwa take son ganin fuskar Sarham a rayuwar ta ba, sai don ta yi quenching curiousity dinta a kan kamannin sa ta kuma yi matching din fuskar da kyawawan kalaman bakin sa na kullum a kan su, wadanda a kullu yaumin masu maana ne wadanda suke kara mata son ganin kamannin halittar sa, shi Sarham mutum ne mai fasahar zance na ilmi, da girmamawa ga mutane, ba tare da laakari da matsayi ko ajin rayuwar su ko nasa matsayin ba, kalaman Sarham har kullum masu tausasawa dan adam ne, a duk halin da yake ciki ya san kalaman da ya dace yayi masa, wato koyaushe kalaman sa na tafiya ne da irin yanayin da ya tarar da kai a ciki.
Alal misali, in ya lura kana cikin farin ciki zai taya ka da zolaya da tsokana yakara maka farin ciki, haka in bakin ciki kake shima zai taya ka har a murya da zuciyarsa, daga yanayin kalaman sa kadai zaka tabbatar (he feels what you are feeling) kuma yana tayaka. Sarham ta kwana da sanin cewa shi din, wani kyautar Ubangiji ne koko tace (dauki) da Ubangiji ya kawo cikin rayuwar su, ya hada su da shi, a lokacin da suke tsananin bukatar tsayawar namiji a rayuwar su.
Ubangiji ya nufe shida shigowa rayuwar su ne don ya zame musu fitila mai haske kuma sanyi daga kuncin da suka samu kan su rana daya na nakasar ta, wanda in ba hadin Allah ba, ba abinda zai sa ya shigo cikin rayuwar su ya tsaya kamar Yayanta na jini. Domin ta kowacce fuska babu ta inda rayuwar su ta zo daya.
Yau da yake cewa zai tafi, har tsayin shekaru uku sai taji cewa lallai zasu yi rashin da baa mayarwa, zasu yi kewar da bata karewa, don shekara uku ba kwana uku bace, abu ce ta mai yawan rai.
Inna ta cigaba da hana kanta kuka a gaban Sarham, tana gayawa kanta saboda su ba zai fasa gina rayuwar sa ba. Yo fisabilillah don su aka halicce shi? Daga taimako? Kuma dai duk wani abinda ya dace don kyautata rayuwar mutum Sarham ya gama yi musu shi, tunda yayi wa Hauwa sanadin cigaba da karatu bayan iftilain da ya same ta.
Sun koyi abubuwa da dama daga gare shi, irin su magungunan da ya dace da taimakon farko na cikin gida (first aid), home hygiene, sanitation duk karshen wata, cin balance diet a gargajiyance da irin abincin da suke da shi, sun koyi abubuwa masu yawan gaske da suka shafi kiwon lafiya a bakin sa a dalilin zamansu tareda shi.
Haka kuma ko yau bai yi shiru ba sai da ya ce da Inna ga kudi zai bar musu ta tabbata ta sayawa Hauwa auduga mai yawa a chemist, bai yarda da kunzugun tsumma ba, yace ita ba ido ba, don haka ba iya kula zata yi da kanta ba kada yaje ta dauki kwayoyin cuta.
Kunya duk ta kama Inna. Kulu kuwa da ace a da ne Dr. Sarham ya fadi haka da tuni ta hau shan kunu da fushi da bacin rai na cewa an yi mata gorin ido, watakila harda su kuka, amma da yake yau itama zuciyarta ta tabu da zancen tafiyar tasa ba tace ko uffan ba, saima kunya da taji sosai itama kamar Innar.
Inna har sai da ta kasa rike hawayen nata a wannan karon, da ya ajiye mata kudi masu dama a gabanta, tace. Dan nan shekara uku ba kwana uku ba. Allah yasa ka same ni a raye, rayuwar nan da bata da tabbas. Allah yasa muna da rabon sake ganawa, Allah ya hada fuskokinmu da alkhairi. Allah ya albarkaci rayuwar ka ya baka ilmin da zaka je nema, ya kuma baka dukkanin abinda kake nema a cikin samunsa, ya huwwace maka saukin sa, ya kuma baka albarkar sa.
Amin- amin Inna, nagode kwarai da gaske da wannan addua mai dadi daga bakinki, na ji dadin zama da ke Inna, zan kuma yi kewar ki ba dan kadan ba!.
Sai da ya tashi tafiya yaga Hauwa ba tace masa komai ba, koda kuwa adduar fatar baki ce, ta sunkuyar da kai kawai. Wannan karon kam ya kufula da wannan mugun hali nata, ya ce Kuluwa!!!”. (Sunan da ya san ta tsana, kuma yana kular da ita), ta dago manyan idanun nan tayi harrr! Dasu a saitin da ta jiyo tashin muryar sa, ga mamakinsa hawaye ya gani ya kwanta dankam a cikin su, ya basu wata irin kala kamar na mai jin barcin da ke hamma, ya sake cewa, ko ba da Hauwa-Kulu-AKA-Kuluwa nake magana ba?.
Hauwa ta tsuke baki, sannan ta sosa hanci cikin jin haushi, bata amsa ba, sai can data mula taga damar magana don kanta sannan tace,
amma dai saboda Allah in mutum ya nuna baya son suna, bai kamata a dinga kiran sa da shi ba, har raina bana son suna KULUWA! an ce miki Kuluwar, Kulun Majadun, Hauwa-Kulu, Kululu, da wasu idanuwanki kamar na Kuliya (mage/mussa).
Ke kam baki ji dadin halin ki ba, wallahi ba don Inna ta tabbatar min a gida ta haife ki ba, da na yi rantsuwa an canja mata ke a asibiti.
Don Inna ba sumumu-kasau bace, bakin ta baya shiru don ya cutar da ita, ki fada kar ta kashe ki, mai yuwuwa kafin shekara ukun na mutu! Ko ke kin mutu! Ko dukkan mu mun mutu! Don haka fadi abinda ke ran ki yau da nazo yi muku sallama, ba tare da mun san ranar sake haduwa da juna ba.
Hauwa zan iya rantsuwa kan ban taba jin kin yi min magana da ta wuce sentence biyu ba, a tsayin shekaru biyun da nayi da sanin ki. Ga wani ‘sadness’ da