Showing 12001 words to 15000 words out of 39065 words
ta kurawa ido tana cewa a ranta inama tana ganin sa tar-tar, domin ta ji dadin abinda ya cewa Inna.
Haka ta cigaba da kallon saitin fuskarsa kamar tana ganin sa sosai, alhalin inuwar sa da karshen tsayin sa kawai take iya gani, bata san me yasa take son sanin yaya kamannin sa na halitta suke ba, ko don tausasan kalaman bakin sa ne da yadda yake lallaba mata rikitacciyar Innar ta, domin a lokacin bata ganin komai dadai ama dai tana ganin haske cikin idanun ta.
Murmushin da Dr. Sarham yayi mata a lokacin kamar ya san me take ciki da zuciyarta ne, taji sautin murmushinsa a kunnen ta, ji tayi kamar ya fahimci ba abinda take son gani a lokacin sai hakikanin kamannin fuskar sa, ba don komai ba sai don ta kwatanta su da kyawun kalaman bakin sa.
Ta kasa manta sautin murmushin nasa. Haka kalaman karfafawa marar lafiya zuciya cikin mutumtawa wadanda Dr. Sarham ya yi mata a lokacin, bata jin har abada zata manta su. Ya bata hope na cewa zata rayu, kuma zata warke cikin yarda da amincewar Ubangiji; wanda ya saukar da cuta kowacce iri tare da maganin ta.
Tsananin tsoron da Dr. Sarham ya gani cikin idanun Hauwa-Kulu, da karkarwar da jikin ta ya fara lokacin da zaa yi mata allurar anaesthesia, ita ta saka shi dakatawa daga abinda yake yi wato saka safar hannu, ya sake matsowa daidai kanta har tana iya jin kamshin balaraben turaren sa, cikin taushin murya da lallashi Dr. Sarham yake cewa,
Relax Hauwau. Zamu yi aikin nan lafiya da iznin Ubangiji kinji, kuma zaki samu lafiya Insha Allahu, zaki warke, saki ranki kin ji ko Hauwau?
Daga haka aka soka mata allurar ‘tafi-da-ran ka wanda hakan yasa Hauwa runtse idanun ta, kuma ta tafi cikin barcin ne da mafarkan kamannin LIKITA SARHAM! Da fatan ko a lahira Allah ya hada fuskokinsu.
Don gani take kamar ta tafi kenan, duk kuwa da hope din da ya bata, har abada ba zata farka ba.
Wato dai Hauwa ta tafi barcin ne da kintacen fuskar Likita Sarham a zuciya da kwakwalwar ta, na wani irin kintace, da dakace, da kuma hasashen ko shin yaya kamannin sa na zahiri suke?
Idan aka yi laakari da irin kyawawan furucinsa/kalaman sa???
Dr. Sarham na iya ganin yadda Hauwa ta runtse marassa lafiyan idanun ta masu cike da ciwon hakiya a kan saitin fuskar sa… (with utmost curiosity) na son ganin hakikanin kamannin sa..
Lokacin da ya dora hannnu akan idanun Hauwa-Kulu domin fara aikinsa da bisimillah dauke a bakin sa, sai ya ji wani sako na kwakwalwar sa kamar yana yi masa amsa kuwwa akan kada yayi, yana janye shi daga yi wa Hauwa aikin ido, yana ce masa kada yayi wannan aikin, don 10% ne tsammanin waraka wato nasarar wannan aikin kashi goma ne cikin dari. Amma aka ce kaddara ta riga fata!!!
Ya ci gaba da aikin sa cike da fargaba don ji yake tamkar wani dabaibayi ya zo ya dabaibaye hannayen sa ya rikita shi, ya hanashi yin komai daidai, don wannan itace tiyatar hakiyar ido (cataract surgery) ta farko da zai yi a rayuwar likitacinsa. Amma wannan bai isa ya zama dalilin kwacewar azancinsa da kwarewarsa ba ai.
Lokacin da yayi nisa da yi mata aikin, sai ya ji hannun sa da jikinsa sun karasa rikice masa da karkarwa gabadaya, zazzabi na shigarsa, zuciyar sa ta hau raurawa, ilmi da fasaha da training din abun duk suka kwace daga kwakwalwarsa ga wani gumi da ya hau yanko masa ta koina, zazzabin da wani irin ciwon kai na kara karfi, ji yayi ya koma tamkar wani dan koyo anan take, ya nemi iyawarsa da jajircewar sa a aikin tiyata da jaruntar sa wajen yin ta duk ya rasa.
A karshe ma Sarham ji yayi ya koma dalibin ajin farko da ko sakandire bai gama ba, exactly dai yadda maaikatan jinyar nan masu gulmar sa su Nos Saratu suka suffanta shi, har daya daga cikin su ta ce tsautsayi kadai zai sa ta bashi idon ta.
Watakila kwacewar azancin da ya same shi a take, yana da nasaba da gulmar su Nos Saratu dasu Metron Maria, da ya saka a ran sa ya dameshi tun ranar, da suka saka shi cikin wani hali na rashin yarda da kansa.
Gulmar tasu ta dade tana yawo a cikin kwanyar sa, domin a zahiri sun ci fuskar sa, sun kuma raina matsayin iyawarsa da darajar kwalayen sa kamar yadda suka raina shekarunsa.
Bai san ta ina zancen nasu mara dadi ya samu halartowa cikin kwanyar kan sa ya hargitsa shi irin haka ba, musamman a daidai yanzu yayin gudanar da aikin nasa da ya kamata ya samu nutsuwa fiyeda kowanne lokaci, ya ji ya koma tamkar lokacin da yake cikin ajin sakandire a Science College Dawakin Tofa, ko kuwa sanda yake dan koyo na matakin farko a MBBS, inda ya koyo aikin likita a jamiar Sarki Abdul Aziz.
**** **** ****
HAUWA _ KULU
A
n yi aikin Hauwa lafiya an basu gado domin su yi jinyar idon kafin lokacin da likita zai kwance mata shi, a duba nasarar aikin ko akasin ta.
Makwabtan su Inna da yawa sun zo har asibitin domin duba Hauwa. Tun ranar da ya yiwa Hauwa aikin nan Dr. Sarham bai dawo asibitin ba yana gida ya killace kan sa a dakin sa yana fama da zazzabi da masassara da ciwon kai na damuwa da zullumi, domin kaso 80% na zuciyarsa na gaya masa cewa yayi kuskure a cikin aikin tiyatar da ya yi wa Hauwa.
Ilai kuwa ranar kwance idanun Hauwa ta zo, sai ranar ne Dr. Sarham ya shigo asibitin Murtala Muhammed. Bayan ya gama abinda zai yi a ofishin sa cikin rashin fara da rashin walwala kamar da (wanda ba halin sa ba kasancewar shi mutum ne mai yawan sakin fuska ga maaikata, mai fara da faram-faram da mutane musamman marassa lafiyan da suka zo gare shi) amma yau bai tsaya ganin kowa ba yana gama abinda zai yi a ofishin sa sai ya nufi dakin kwantar da mata domin ya duba aikin da ya yiwa Hauwa Bilyaminu.
Tun daga bakin kofa marassa lafiya da masu jinyar su ke gaisar da Dr. Sarham A. Shanono, shi Sarham, an yarda likitan kowa ne, sannan marasa lafiya na son shi saboda kirkin sa da farar sa, yana dakatawa a gaban kowanne gado yana amsawa cikin mutuntawa da tambayar kufan jiki, saidai fuskar nan ba murmushi kamar na kullum, murmushin nan da baya rabo da kyakkyawar fuskar sa ta fulanin Shanono yau babu shi. Haka yayi ta bin su daya bayan daya yana jin lafiyar su. Kusan kowa ya gane cewa shi din mutum ne mai mutunta jamaa ba Innar Hauwa kadai ba.
Har ya iso ga gadon Hauwa, wadda itace a gadon karshen dakin, suka gaisa da Inna da ke zaune a gefen gadon kan Hauwa bisa cinyar ta, ya tambaye ta ko yaya jikin na Hauwa, ta ce tun jiya take min korafin ciwon kai, amma Nos dinnan ta zo ta bata magani. Ta nuna daga cikin Nosis din da ke bayan sa, wadanda suke take masa baya su biyu suna gatsine mata fuska na kin zama ba yadda zamuyi dake.
Bai kula da zancen Inna ba don hankalin sa kusan baya jikin sa. Bakidaya ya tafi ga son sanin aikin sa yayi nasara ko aah. Ya dauki file din Hauwa ya duba yayi rubutu a ciki sannan ya karasa gaban gadonta, yace cikin murmushin fatar baki wanda bai je koina ba.
Kululu-Kuluwa, Kuluwa yar gidan Innarta, yau zaa kwance ido, ina fatan kin shirya? Daga kwance ta amsa na shirya mana Dr, yau sati guda ban ga hasken rana ba, ka bi ka kunshemin ido da bandeji.
Ta bashi dariya amma sabida yana cikin fargaba murmushi kawai yayi, ya fara kuncewa. Da adduoI a bakin sa. Nos din da ke bayan sa ce ta taimaka masa, suka soma warware bandejin da aka nannade idanun Hauwa da shi da dan almakashin da ke hannun su.
Aka warware bandejin tsaf. Sai ga kyawawan idanun Hauwa tsaf da su garai-garai dasu kamar a wanke babu hakiya, aiki yayi kyau kenan. Amma me?
Dr. Sarham ya tambayi Hauwa su nawa ne a tsaye a gaban ta? Hauwa ta shafa idanun ta ta kyafta su, ta sake kyaftawa kafin ta girgiza kai tace,
LIKITA AI BANA GANIN KOMAI A GABANA SAI DUHU!
In kin ji faduwar gaba da tashin hankali a wurin su su duka dake wurin abin baa cewa komai. Amma shi Dr. Sarham ba faduwa kawai gaban sa ya yi ba, yankowa yayi daga zuciyar sa ya tsinko daga kirjin sa ya fado kasa yana majaujawa a dandaryar kasa..
Ko dama ya dade cikin wannan zullumin tun ranar da ya yi wa Hauwa aikin. Jikin say a gama bashi bai yi nasara ba. Ya tabbata yayi kuskure a cikin aikin domin a lokacin da yake mata aikin ya samu kansa cikin wani bakon yanayi na rashin yarda da kai, wanda zai iya cewa ya gusar da consciousness din sa (hayyacin sa) na dan wani lokaci.
Yanayi ne da bai taba samun sa ba a yayin ‘surgery’, ya sha yin aikin da yafi wannan hatsari na glaucoma amma bai taba sarewa ba sai a kan wannan, yafi danganta abinda ya same shi a lokacin da fargaba da tsoron rashin yin nasara sakamakon abinda ya tsinkaya ana cewa a kan sa, wanda ya jefa shi a halin rashin yarda da kwarewar sa akan karan kansa, amma ba don bai iya ba din, dadin dadawa bai taba yin aikin hakiya ba sai wannan karon akan idon Hauwa, ya kuma ga yadda hakiyar tayi zurfi sosai taci idanun ta lalata maganan ta, wannan ya jefa shi a fargaba mai yawa ta aikin bazai yi nasara ba wadda bai kamata ta zo masa a lokacin ba a matsayin sa na likita.
Tunda ya koma gida kuma da wannan tunanin ya kasa dawowa asibiti, don ya tabbatar bai yi aikin yadda ya kamata ba, ko yace yayi kuskure a aikin da ya yiwa Hauwa, ko yace kamar hakiyar da ragowa a ciki bai cireta duka ba, a sakamakon gushewar hayyaci da ya samu na dan wani lokaci (at the said moment).
A karshe ya tabbata garesu dai bakidayan su babu ko tantama Hauwa ta makance a dalilin aikin da Dr. Sarham Abbas Shanono yayi mata ba daidai ba, iyakar maganar kenan. Gulmar su ta tabbata aka bai iya di ba. Ga idanun nan tarr a bude, amma Hauwa bata iya ganin ko dan yatsan ta balle inuwar mutum ko hasken rana da take iya gani kafin ayi aikin.
**** **** *****
GULMA AJALI
A
wannan yammacin a Nurses station na sashen ido a asibitin Murtala baa komai sai gulamammaki masu lasisi, na abinda ya faru a kan aikin da sabon likitan ya yiwa maras lafiyar tasa. Su Nos Saratu da Metron Maria an samu abinda ake so, aka maida abin topic of discussion na wannan ranar.
Ko aikin su na ranar sun kasa yi yau, tsabar saboda yadda gulmar Sarham ke cin su.
Metron Maria wadda ita ta halarci aikin warware idanun Hauwa tare da likitan, ta ce hey! In baku labari dai, kunnen ku nawa?
Suka hada baki (in chorused) wajen cewa kunnen mu biyu, to ku kara biyu ku sha labari.
Dr. Sarham dai ya karasa makantar da yarinyar nan mai hakiya da yake mana balbali akan su, aikin da yayi mata was not successful at all.
Kuma ya kama bakin sa salin-alin bai ce komai akai ba ya bar asibiti, ba tareda kowa ya san taasar da yayi ba, ya ja bakinsa ya tsuke ko sum utu ko suyi rai oho musu.
Nos Gambo tace ki bari don Allah?
Saratu ta yi rantsuwa ta labarta musu abinda ya faru, ta ce yo dama idon ya gama rubewa fa, maganin su kenan suma, da sun lallaba sun tafi da muka kore su da ta ci gaba da morar dan wani abun a idon, aa su ga sarakan naci dambun kuturu, ni dama na san idon kiris yake jira a taba shi, shikuma karambanin sa kenan, an ce musu sawun su a likkafa su koma gida su cigaba da barbada farin kwallin su da suke barbadawa suka ki ji, wanda bai ji bari ba ai ya ji hoho, yanzu da ya maidata totally blind ai sa hakura.
Ni ai dama na fada muku tsautsayi ne kadai zai saka ni baiwa wannnan yaron idanuna ya saka musu wuka, har yaushe ya bar sakandire ko ince ya bar shan nono a cinyar uwar sa? Da zan bari ya fede min ido? Ai yafi kama da Romeo (Uban soyayya) fiyeda consultatant.
Ban da ilmi a Najeriya ya zama sabatta-juyatta, ya zama abinda ya zama wajen tabarbarewa, ban taba ganin inda dan kasa da shekaru talatin ya zama surgeon ba” wata bakuwa a cikin su mai hankali ta ce,
ku kuwa ku daina abinda kuke yi bai kamata ba, shi aikin fida ai haka ya gada, ko ayi nasara, ko akasin ta, kafin ayi aikin mara lafiya ya san da haka saboda haka nema ake saka hannu bisa yarjejeniyar amincewar iyaye da makusan ta, so ko mutuwa ta yi bashi da alhakin hakan. Yayi iya kokarin sa Allah ne bai yi ba.
Idan fitsari banza ne kaza ta yi mana? Kuna ta zagin sa da kushe shi alhalin bai ci muku ba bai sha muku ba, ku ku je kuyi karatun fidar idon mana? Shin wai kyawun Dr. Sarham da gayunsa ne ya koma masa abin hassada a bakunan ku ko me?.
Da wannan ta kashe bakin su murus, bayan sun musa da cewa ina abin yake da zasuyiwa hassada abu tsololo kamar karan raken takanda. Wata kuma mara kunya a cikinsu ta kada baki tace ai irinsa sun fi dadin shaani a gado, baa dakin tiyatar ido ba. suka kwashe da dariya. Har suka tashi aikin ranar basu bar wadannan zantukan ba na shegantaka har daya na cewa ya kamata a kwace licence din sa na aikin likitanci tunda daga zuwa ya fara da makantar da yayan mutane, saboda rashin iya aiki. (Ni kuma nace gulma-ajali mai yin ki kadai zaki kashe).
***** ***** *****
DESTINY TORMENTS.”
(DA KARFE SHIDDA NA YAMMA A GIDAN PROF. ABBAS SHANONO)
M
awakin ya sake cewa Destiny torments my heart… cikin baitin wata waka ne da Dr. Sarham yake saurare daga kwancen da yake a yammacin ranar, bayan komawarsa gida daga kwace idon Hauwa.
Yana kwance har kusan magriba a rigingine a tsakiyar matsakaicin gadon dakin sa. Sai ya ji shahararren mawakin zamanin wato R-Kelly kamar dashi yake. Don zuciyar sa duk ta takura. Ya shiga kunci na babu gaira babu dalili. Ya yarda abinda ya faru dashi a kan aikin da ya yiwa Hauwa Bilyaminu kaddara ne, wadda ta rigayi fata, ba don haka ba ai yaji ‘warning alarm’ a cikin kansa, mai cewa ya bari kada yayi aikin nan babu nasara a cikin sa sam, don haka tunanin sa yafi karkata ga cewa sakacin sa ne ko gangancinsa.
Amma kuma da aikin kaddara ai, altogether.
Allah ya riga ya rubuta Hauwa Bilyaminu zata makance a hannun sa. But this written destiny really touched and tormented his heart.
Ace ka zama sanadin nakasar idanun wani dan adam kwata-kwata, duk da cewa dai aikin likita irin wannan (a mutu ko a rayu) ne, sannan ba zaa tuhume shi ba, tunda ya tafiyar da komai a kan kaidar aikin sa ne, amma IDO fa ake zance, wannan kwayar tsokar guda biyu mafi amfani da muhimmanci ga halittar dan adam, sannaan in har kana da zuciyar yan adamtaka a cikin kirjin ka da humanity a tare da kai, dole zuciyar ka ta tabu, da ganin yadda fuskar Innar Hauwa ta shiga tashin hankali a lokacin da Hauwa tace,
bata ganin komai a gabanta sai duhu.
Wanda tayi ta kokarin danne tashin hankalin data shiga din saboda shi. To shi tashi zuciyar ba tabuwa kawai ta yi ba da tausayin su da disappointment akan aikinsa, ta kekkece ne, sannan ta tsatstsage ta yayyage ta yagalgale (into pieces at the same time). Ta yadda a gaban Innar Hauwa duk dauriyar da yake yi sa sai da idonsa ya kada, kwalla ta cika idonnasa, a fakaice ya yi kokari maida kwallar, ta hanyar juya musu baya ya zuba dukkan hannayen shi cikin aljihu yana