Showing 18001 words to 21000 words out of 39065 words

Chapter 7 - Hauwa Kulu Book 1 Hausa Novel Complete

Takori   

30 Dec 2024

247

yasa take tausaya mata wannan lalura data sameta yanzu, yadda Hauwa ke taimaka mata da ayyukan gida bata da kiwa (bata da ganda), ga son karatu kamar tsuntsun alhuda-huda.
Inna ta ce cikin mutuwar jiki da yanke tsammani, babbar damuwar ta a yanzu da makancewar Hauwa-Kulun ta, ba makantar bane ba kai tsaye, ko kiranta makauniya da mutane zaa ke yi, damuwar tata shine; ta yaya Hauwa zata yi ta cigaba da karatu?
Wannan magana da Inna ta yi, ba Hauwa kadai ta saka a tunani da damuwa ba har da shi kan sa Dr. Sarham. Kamar wani assignment na lissafi (mathematics) mai wuya yaji Innar Hauwa ta bashi shima. Wanda zai tafi gida dashi domin yayi solving ta hanyar tunani. Don haka koda suka yi sallama da Inna jikin sa duk a sanyaye yake shima, ya fito lokon ya shiga motar sa ya tayar, amma sai ya kasa tafiya, sai ya kifa kansa a kan sityarin motar na tsayin lokaci yana tunanin ta inda zai iya taimaka musu da rage musu.
Ya shiga cikin tunanin ta wace hanya zai bi ya taimaki rayuwar wadannan bayin Allah da yarinyar su tilo, ta nakasa a hannun sa? Yo a hannun sa mana! Da yayi aikin nan da kula yadda ya dace da Hauwa bata makance ba (a tunanin sa).
Iyaka tunanin sa bai ga da me zai iya taimaka musu ba banda a kan shaanin karatun Hauwa din, don haka ya yanke shawarar baiwa Abban sa labarin su, da neman shawarar sa da karin haske akan ilmin da bai sani ba wato special education. Kasancewar Abban sa mutum mai hangen nesa da yalwar ilmi a bangare daban-daban fiye da shi, ya san a nan ma bazai rasa sani ba.
Shi da Abban sa (are more than father and Son, they are very close and best friends) na junan su tun yana karami. Haka kanwar sa Sumayyah ita ce babbar abokiyar sa a rayuwa, Sumayyah is nice and easy going sannan (talkative like her Bhaiya) yadda take kiran sa kenan, shiyasa tasu ta zo matukar daya, su yi hira suyi dariya kasancewar sa very jovial likita abokin kowa, ba kamar sakuwarsa ba wato Surayyah, wadda ta dauki rayuwar sababbin yan jamia (JJC) mai tsauri ta sanyawa kanta.
Duk da kasancewar Sumayyah mai karancin shekaru to fa ya shaida ta fi Surayya hankali da hangen nesa, kai dai bar Surayya wajen iya ado, da iya daukar wanka da kuma son kyale-kyalen da zaa ce tafi kowa cikin tsararrakin ta aji. Halayen da ke hadata fada da Bhaiya din kenan a matsayin ta na sakuwarsa a haihuwa, kusan kullum sai an ji kansu, don shi ta rage wuni a gidan su sai gidan Hajiya Kulu kakar su.
Dr. Sarham, in ka cire abokan karatun sa da har gobe in an hadu akan gaisa, bashi da wani shaqiqin aboki da zaa kira aminin sa, duk da surutun sa da sakin fuskar sa to fa ya san a inda yake yin su, baida abokai sam saboda training din da mahaifin sa yayi masa kenan na ya zamo shine babban abokin sa (Abban), saboda gudun kada abokai su bata masa shi. Abba Prof. akwai saka ido akan tarbiyyar yaransa kamar baida wani aiki a duniya sai kula da su, sai ko abokanan aikinsa a Murtala, wadanda yanayin aiki kan hada su akan dole.
Maman sa kan ce he is very anti-social, yet a parrot”, bashi da saurin yarda da sakin jiki da kowa, sai ko autar su Sumayyah, ko ita kan ta Maman ba komai yake iya gaya mata ba, da ya shafi sirrikan shi, amma tsaf zai iya gayawa kanwar sa Sumayyah komai su kashe su rufe ba tare da iyayensu sun sani ba.
Babu shakuwa mai yawa tsakanin Barr. Maimuna da daukacin yaranta, wannan ya faru kasancewar gabadaya rayuwarta ta sadaukar da ita ga aikin ta na Lauya da zurfafa karatu, don haka su Sarham sun taso kusan a gaban Kakar su ne Hajiya Kulu. Sun fi shakuwa da Hajiyar Gadon Kaya fiye da Maman su, wadda a can baya a gidan su take zaune.
Lokacin da aka maido Prof. cikin gidajen malamai na sabuwar jamiar Bayero sai Hajiyar Gadon Kaya tace ba zata biyo su ba, domin bazata iya zaman wajen gari ba, a cewar ta a cikin Badala aka haifeta don haka a kwaryar badala take so ta mutu a binneta, don haka Prof. ya samar mata mai aiki mai suna Gambo, ta zame mata abokiyar zama suke zaune tare a gidan sa na Gadon Kaya wanda mallakin sa ne da ya gina da gumin sa. Lokaci-lokaci yana sabunta shi zuwa ginin zamani irin na wancan lokacin daidai da yawan iyalin sa.
Har yanzu Hajiyar gadon kaya na can amma ta tsufa ainun, sun yi sun yi ta dawo ta zauna tare da su ta ki, don haka kusan koyaushe kafar su bata rabo da gidan Hajiya musamman Surayyah, saboda yadda Hajiya ta shagwaba ta, kuma tafi jan ta a jiki duk cikin su.
Wannan ya samo asali ne daga sanda aka haife ta bada jimawa ba Mama tayi wani dogon rashin lafiya mai tsanani na lokaci mai tsaho wanda yasa dole aka dauke Surayyah a nono ba tare da ta isa yaye ba, Hajiya ce ta cigaba da rainon ta a dakin ta da madarar yara har ta yaye ta, sai ta cigaba da zama a wurin ta har bayan da Maman ta samu sauki, aka zo aka haifi auta Sumayyah, amma Hajiya ta rike Surayyah, bata kara bari ta dawo wajen Maman su ba, saidai ta zo da yawo har girma.
Ita kuma Sumayya dalilin shakuwar su itada Sarham ya samo asali da cewa kusan Sarham shi yayi rainon ta, domin akwai rata ta kusan shekaru goma sha biyu a tsakanin su.
In Mama na wajen aiki shi yake kula da Sumayya su tafi makarantar islamiyyar sa tare, har zuwa sanda itama ta isa shiga makaranta, malamai na hanawa azo da kananan yara amma Sarham ba ya jin Magana, gobe sai ya dawo tare da kanwar sa, in har ba za’a bar shi ya shiga aji da Sumayyah ba tofa zai koma bayan tagar ajin su ne shi da ita su make su yi ta leke, korar duniya malamai zasu yi masa ba zai tafi ba, har suka gaji suka kyale shi yake zuwa aji tare da ita, don Mama bata da lokacin kula da ita.
Inda Mama ta zama akasin Prof. Kenan, shi kam yanada lokacin yaran sa no matter what, yana jan yaran uku a jiki, daga yamma zuwa lokacin barci idan ya dawo daga cikin makaranta suma suka dawo makarantar islamiyya zai kasance tare da su.
Ita Mama zaka samu ko ta dawo aiki zata ce ta dawo da muhimmin (case) a hannunta zata yi nazari, tace su zauna a falo kada su dame ta. A haka Sarham da kannen sa biyu mata suka rayu tsakanin yan bokon iyayen su. Sai ya zama cewa a girman su ma Surayya ta fi shakuwa da Kakar su, itada Sarham basa ga maciji, sai fadan sako da sakuwa, yayin da Sumayyah kuma tafi shakuwa da shiri da shi fiyeda Mama.

Ya iso gida wajen karfe tara na dare. Jamaar gidan su dama ga aladar su karfe tara na dare na yi sun baje daga falo kowa ya nufi makwancin sa. Amma Abba na nan bai tashi ba, yana nan zaune a kujerar da yake zama a falon yana jiran ganin dawowar sa, yana sauraron labaran kasa da ake yi a gidan talbijin na NTA yana kuma duba tangamemen agogon dake like a bango.
Sarham yayi sallama a babban falon mahaifin sa, inda Abba Prof. ya amsa masa, ya shigo ya zauna daga kasan kafafun Abban, ya ce Abba sannu da gida Abba yace yawwa, kai kuma sannu da yawon dare, daga ina kake haka? Ka bar yan kannen ka cikin damuwa, ka birkice musu wuni guda, me ke faruwa da kai yau?
Sarham ya yi ajiyar zuciya ya ce Abba ina kofar Naisa, wata marainiyar yarinya na yi wa aikin ido, Abba cikin rashin saa zan ce ko kaddara ko tsautsayi ko gangancina ne ban sani ba, ta makance gabadaya, maimakon a samu lafiyar da ake nema.
Muryar Sarham kamar zai fashe da kuka don damuwa, zaka iya karantar tsantsar karaya da sarewar da yake ciki a cikin sautin nasa.

Prof. Abbas Shanono, ya dubi babban dan nasa Sarham cikin kulawa, yace haba Muhammad Sarhamu! Be a man mana! Sai kace ba likita ba? Da haka zaka cigaba da aikin likita kana karaya akan rashin nasarar aiki irin haka? Ai dama aikin likita ba a hannun ku yake ba, a hannun Allah yake, sai abinda ya hukunta ga marar lafiya.
Never blame yourself a kan duk wani unsuccessful surgery. Ka sa a ranka ka yi iya yin ka, sauran, wato samun lafiya ko akasin ta, yana hannun Ubangijin halitta.
Maganar mahaifin nasa ta dan kwantar masa da hankali, at least shi bai ce masa bai iya ba, bai ce don shekarunsa ba masu yawa bane, bai kuma ce laifin sa bane this is soothing, a hankali Sarham ya ce.
Abba kuma shikenan idan yaro ya makance wato ya samu nakasar ido ba zai yi karatu ba sai ‘bara?’
Abba Prof. yace in ji wa? Ai akwai cigaba yanzu sosai akan ilmin masu nakasar ido, akwai makarantu na musamman da gwamnati ta bude domin koyar da su kyauta (public special schools) can ya kamata iyayen ta su kai ta, har anan Kano akwai special school dominyara mau nakasa daban-daban.
Sai Sarham ya ji tamkar Abban sa ya bashi amsar ‘assignment’ din da ya baiwa kansa, ko yace Inna ta bashi, na yaya zai yi Hauwa tayi karatu, sannan kuma Abba ya bashi mafita akan damuwar sa kan matsalar Hauwa, at least zai iya taimaka musu da wannan wato ya tsaya a kan karatun ta, nan take ya yi wani kuduri mai girma ga zuciyar sa shi kadai; na daukan nauyi da takalihun alhakin ilmin Hauwa Blyaminu na sakandire har sai ta kammala in har yana raye, in dai da gaske makafi suna iya yin karatu da rubutu su samu ilmi kamar kowa, da yardar Allah zai tsayawa Hauwa, tunda shi ya samu yayi har gashi ya tsaya da kafafun sa yana kuma da albashin sa, to zai tsaya ya ga cewa Hauwa bata tagayyara a fannin ilmin sakandire sanadin makantarta ba.
Wannan wani alkawari ne da Dr. Sarham ya yi wa kan sa a zuciyar sa, da yake fatan Allah ya bashi iko da tsawon ran cika shi.
Sai washegari wajen karin kumallon su akan dining suka hadu da Maman sa da sauran kannen sa biyu wato Sumayyah da Surayyah. Bayan ya gaida iyayen nasu shikuma kannen sun gaishe shi yadda suka saba ya ja kujerar sa ta dindindin a dining din ya zauna. Mama ta tambaye shi me ya faru da shi ne jiya?
Nan yake gaya mata labarin aikin da yayiwa Hauwa da yadda yake blaming kansa kamar yadda ya gayawa Abban sa.
Barr Mama. itama kamar Abban nasa cewa ta yi ba laifin sa bane. Ta kuma kara da cewa kada ya kara sakawa kansa damuwa irin wannan kan aikin sa in har yana son cimma nasara a gaba, don hakan zai iya sawa ya tsani ‘profession’ din nasa da ya tashi da burin sa. Surayya ta gatsine baki ta ce,
dadi na da mutum daurawa kai damuwar wasu, damuwar da Allah bai dora masa ba, to sai me zai faru don aiki bai yi nasara ba da zaka bi ka wuni cikin damuwa har da kulle kofa da yiwa kai horon yunwa ta hanyar kin cin abinci wuni guda haka Yaya Doctor, ina dalili ina dan mafari?
Sarham ya jefe ta da harara, Mama ta ce ke bana son rashin kunya, wa ya saka ki a maganar mu?
Dagagefen sa inda take zaune Sumayya ta ce cikin jimami.
Bhaiya, kayi wa Allah ka kai ni in duba ta, haka kawai naji tausayin ta ya kama ni nima, makancewa fa totally, a hannun ka, ai da tausayi da sanya damuwa, dole ka shiga phobia dinka, dama dai a ce a hannun wani liktan ne ba kai ba bazaka damu har haka ba, Allah sarki Bhaiya na!.
Yace I know you always pity me Summy, and you are with me especially in such a bad situation (nasan koyaushe kina tausayamin Summy, kuma kina tare dani musammman a lokaci mara dadi). Madallah da wannan kanwa tawa. Karamar su-babbarsu!.
Haka suka karya kumallon suka tashi, masu zuwa aiki wato Sarham da iyayen su suka shiga motocin su daban daban suka wuce wajen aikin su, Surayya ta wuce cikin makaranta inda take karatu anan cikin jamiar Bayero, tana aji daya na digiri a tsangayar ilmin lissafi (mathematics).
Sumayya na aji biyu na babbar Sakandire a makarantar Musa Iliyasu College, dake nan daura da sabuwar jamiar Bayeron, suna fitowa ne kullum tare da Yayan ta Dr. Sarham tun bayan fara aikin sa, sai ya sauke ta sannan zai mika zuwa asibitin Murtala inda bai jima da fara aiki ba, bayan yayi aiki na dan lokaci da asibitin Abdullahi Wase da aka fi sani da asibitin Nasarawa, suka maida shi can don an fi bukatar kwararru a asibitin Murtala fiye da kowanne asibitin gwamnati a Kano.
Wannan ya faru ne jim kadan bayan dawowar sa daga kasar Saudi-Arabia da kadan, inda ya karanci fannin likitancin ido a jamiar Sarki Abdul Azeez dake Jeddah.
**** **** ****

Bayan ya sauke Sumayyah ta daga masa hannu, ya ja motar sa zuwa asibiti. Koda ya zo ward round na wannan ranar sai idanun sa suka hango masa gadon da “Hauwa-Kulu” ta kwanta jinya. Nan da nan ya tuno su, wadanda dama da su ya kwana ya kuma tashi a ran sa.
Sai ya ji yana son sake zuwa ya duba su, ya ga lafiyar su itada Innar ta.
Haka kawai yake jin Innar Hauwa a ran sa, jinta yake kamar uwa a gare shi, sabida halin kirkin ta da dattaku, da kuma tawakkalin data nuna akan abinda ya samu yar ta a hannun su.
Don haka da ya fito daga asibiti sai ya samu kansa da juya sitiyarin motar sa zuwa unguwar su Inna, da ya isa bayan Badalar kofar Naisa kasa gane gidan yayi, da tambaya ya isa har kofar gidan su Hauwa don ya kasa ganewa da farko, kansa ma juyewa yayi ya rasa direction abode gidan yayi cikin lungu sosai, amma da yake ya rike sunan maigidan da Inna ta gaya masa kamar ta san zai bata din sai baa sha wahalar kai shi har kofar gidan ba.
Dr. Sarham yayi sallama a kofar gidan Mal. Bilyaminu, Inna dake duke tana share tsakar gidan ta amsa sannan ta leko, koda dau taso daukar muryar dama mai kaifi kamar an fike ta anyi sharpening fitar ta gently daga makogaron sa, bakin ta ya koma har kunne da ganin Dr. Sarham, ta dau wankan ta tsaf ta sha wankakkiyar atampa, kodayake dama ta dauki muryar sa, Inna ta bashi iznin shigowa ya sa kai ya rage dogon wuyan sa ya shigo da sallama.
Inna ta amsa cike da faraa ta shiga lale marhabin da shi, sannan ta dauki tabarmar karauninta ta shimfida masa.
Sarham ya tsuguna har kasa ya sake gaishe da Inna, ya kuma tambayi jikin Hauwa. Inna ta ce cikin damuwa,
ai tun bayan tafiyar ka jiya zazzabi ya rufe Kuluwa, ko tashi bata iya yi, sallah ma sai na taimaka mata take iya yi daga zaune, ta dauki damuwar duniya ta dorawa kanta a banza akan abinda Allah ya kaddara mata. Dr. Sarham ya ce,
ashsha! Kakata jiki bai yi dadi ba ashe, ki barta Inna, dole ne ta damu, amma a hankali damuwar zata bi jikin ta in sha Allah, bari to in koma in samo mata magani.
Har ya mike zai saka takalmin sa sai ya dubi Hauwa dake zaune a kan tabarma daga gefe, ta jingina da filo, ga idanuwan tarr a bude kal dasu, amma shi a iya dan ilmin likitancin ido da Allah ya bashi, da abinda ya karanta, ya san wadannan idanun na Hauwa’u in ba wani babban kudurar Allah ba sun tafi kenan, wato sun tashi aiki sai ko wani ikon Allah, wanda ya fi gaban ilminsu su likitocin fidar idon.
Ya matsa gaban tabarmar ya russuna yace sannu Kakus, ina yake miki ciwo? Don in san irin maganin da zan karbo? Ko allura kike so?” Hauwa ta bata rai sosai saboda sunan da ya kira ta da shi kamar wata tsohuwa, haka mafa a asibiti yace mata Kululu bata ce masa don me ba, yanzu kuma yace mata kuskus, ta dan fiddo manyan idanun kamar tana ganin sa irin warning look dinnan, ta yi fuska sosai ta ce masa, sunana Hauwau Bilyaminu ba kuskus sunana ba, kuma ni ai bana tsoron allura inda a hannu za’a yimin, ba sai na kwaye zani ba”, Inna ta ce an ce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login