Showing 33001 words to 36000 words out of 39065 words

Chapter 12 - Hauwa Kulu Book 1 Hausa Novel Complete

Takori   

30 Dec 2024

252

ne Jamilu ya matsa gaban ta ya tsugunna, ya sadda kan sa kasa cikin kaduwa da mamaki da tsoron kada Inna tace da gayya ya kade Hauwa, yace Inna Safiya kiyi hakuri, ni na kade ta ban sani ba, ashe Hauwa-Kulu ce ma, kanwata.
Wallahi ina cikin tafiya kawai na ganta a gabana a tsakiyar titi, nayi kokari in kauce ta sake dawowa daya barin da ba yadda zan iya kauce mata.
Inna ta kai duban ta ga saurayin, nan da nan ta gane shi duk da girma da cika idon da yayi, Jamilu ne dan wajen Zakari, Inna ta ce.
Jamilu dan wajen Rumanatu? Yace ni ne Inna Inna tayi kwafa ta ce to babu komai, kana iya tafiya, mun gode.
Jamilu ya ji babu dadi a ransa, yace Inna Safiya wallahi tsautsayi ne, ba inda zani sai taji sauki, zan kasance tare da ku har Allah ya bata lafiya.
Inna bata sake komawa ta kansa ba, ta maida hankali kan gyarawa Hauwa kwanciya, har ya karaci durkuson sa ya tashi, ya tafi cikin damuwa.
Bayan fitarsa Inna ta tambayi Salele yadda aka yi ma ya rabu da Hauwa har ta hau titi bisa ita kadai, cikin kokarin boye bacin ran ta, Salele duk rashin gaskiya ya bayyana a fuskar sa ya ce Inna daga nace ta tsaya in je ni tsallake in dawo Inna tace ka dai fadi gaskiya, kai dai wallahi a kan kalle-kalle ko bakauye nan ya ganka ya barka. Allah ya kiyaye gaba”. Can kuma tace. “Oh ni Safiya, Hauwa-Kulu harda karaya? Idon ta ya kawo ruwa, tasa habar zaninta ta share tana sake gyarawa Hauwa kwanciya, an sakale hannun da aka gyara a jikin karfen gadon.
Ba jimawa da fitarsa Jamilu ya sake dawowa niki-niki da ledoji a hannayensa, yayi sallama akan su, dakin irin dogon dakin nan ne na kwantar da marasa lafiya mata zallah, suna daga gadon tsakiya da wasu a gefeda gefen su, Inna ta juya ta dube shi ta amsa sallamar sa, fuska kadaran-kadahan ta ce wani abu ka manta ne kuma? Ya ce aah Inna, ai na dinga zuwa kenan har sai an sallame ku, in sha Allah. Ya ajiye mata ledojin da ya shigo dasu a gaban ta cikin matsanancin ladabi, sai Inna ta rasa me zata ce, yaushe yayan Zakari suke da hankali balle su yi halin da yake yi a gabanta yanzu?
Koda yake ko dama can shi daban yake a cikin su ta san wannan, saboda uwarsa ta masa tarbiyya daidai gwargwado, bayan Zakari ya saketa da shi ta tafi tayi aure a wani gidan, ba laifi yana gaida mutane duk inda ya gan su ba kamar kannen sa ba da sau dubu zasu wuce ta ko kallo bata ishe su ba. In zata iya tunawa rabon ta da Zakari da wani da ya shafe shi tun batan Malam Bilyaminu, shekaru hudu baya da ta je neman sa yayi mata korar kare. Wani cikin su shi ko yayan sa bai kara neman su ba, yau kuma sai ga Jamilu ya kade Hauwa.
Inna ta nisa, ta kasa ce masa ya kwashe tsiyar sa, don sosai taga damuwa a tare da shi na irin karbar da take masa. Haka suka zauna shi da ita zugum-zugum, ba mai iya ce da kowa uffan, daga baya yayi mata sallama ya tafi. Yace sai gobe in sha Allah kafin ya tafi wajen aiki zai leko ya ga jikin Kulun.
Inna tayi masa godiya, amma sai ta ce “don Allah ba sai ka dawo ba Jamilu, taimakon da kayi mata ma an gode sosai, madallah. Allah yayi albarka.
Jamilu bai ce komai ba ya juya ya fita don ya san tabbas Inna ta kullace su duka ahalin gidansu daga su har mahaifin su, don ma dai tana da kai zuciya nesa.
To bayan fitar sa kuma ta samu kanta da bude ledojin da ya aje musu, ta farko kayan shayi ne a ciki, da katon biredi (Laziz) sabon gashi, sai kayan marmari shake a daya ledar harda Tuffa da Inabi, daya ledar kuma gasashshen naman rago ne mai zafi sosai a ciki.
A lokacin Hauwa ta farka tun bayan kawo ta asibitin da kyar ta iya ta dan motsa, sai ta ji ta kamar a daddaure, koina na jikin ta ciwo, bata san me ya faru da ita ba, ta kai hannun ta da baa daure ba kan goshin ta tace wash! Inna tace sannu Kulu kin ji, tsautsayi ne da baya wuce ranar sa, mota ta buge ki, Allah dai ya dada kiyaye gaba.
Nosis suka zo suka bata magungunan ta, suka ce a bata shayi mai zafi ta sha, kuma zata iya cin wani abu, Inna tace basu zo da ruwan zafi ba, sai suka bata aron karamar heater ta jona ta hada mata shayi mai kauri da kayan shayin da Jamilu ya kawo.
Ta taimaka mata ta zauna a jikin filo tana bata shayin a baki har ta koshi, ta debo naman da zafin sa a faranti irin gasashshen naman nan ne na babbar tukuba mai ruwa-ruwa wanda da kasa a bakin ka ka tauna zaka ji ya baje tsabar laushin sa, wanda yaji yajin citta, Hauwa duk da jikin ta na ciwo taji dadin cin naman nan, don baza ta iya tuna yaushe rabon ta da cin nama ba, tun zamanin Likita Sarham na zuwa gidan su! Balle mai dadi da laushi irin wannnan ai sai zamanin Dr. Sarham.
Daga nan ta koma barci har dare bata tashi ba, Inna ta sallami Salele ya tafi gida bayan ta masa sautun abubuwan bukata da zai zo musu da su washegari har da filas din ruwan zafin su da hita.
Washegari yan dubiya fululu daga kofar Naisa, Salele ya barabada musu mota ta kade Hauwar Inna. Hauwar Inna mai jamaa kowa na son ta, koda makanta ta same ta jamaar unguwar su kowa kokari yake ya kyautata musu, musamman da aka san mahaifin ta ya bata, kuma Innar ta bata da matallafi sai Allah.
Makwabta na ta tururuwar zuwa duba Hauwa kullum, koda Inna ta aika Salele don ya fada a makarantar su Hauwa kada aga bata zuwa, sai ga Malaman su Hauwa sun yo kungiya a motar makarantar su a washegari daga ‘special school Kano’, suka zo suka duba ta da kayan dubiya niki-niki, kasan yaro mai kokari da shiga ran malamai. Don haka a wannan jinya su Hauwa sun samu alheri sosai, don Jamilu ma kullum yana tafe, abin arzikin da zai kawo na yau daban na gobe daban.
Tun Inna na daure masa fuska tana korar sa a wayance, har ta fara gane Jamilu neman shiri yake yi sosai dasu, rannan ya kawo dafaffen abinci yace mata inji Hajiyar sa, da yake bata gidan mahaifin sa ita kuma tare suka yi yanmatanci da Inna, kusan lokaci daya Bilyaminu da Zakari suka aure su.
Ta manta rabon ta da Rumanatu don tun Jamilu na yaro Zakari ya aunata gaba.
Daga baya ma ya dauko Innar tasa ya kawo dubiya, nan suka baje ita da Inna a kan tabarma ana labarin yaushe gamo da tuna baya. A bakin Hajiya Rumanatu Inna ta ji cewa Jamilu yayi karatun shi mai zurfi har digiri a hannun ita mahaifiyar shi a boye, ba tareda Baabnsa ya san yana yi ba, tace yanzu haka Jamilu aikin Banki yake da bankin Afrika (United Bank of Africa) da akafi sani da UBA. Kuma da wannan aikin har yana taimakawa kannensa sosai da suke garari da gararramba a gari, matan yawanci an sako su suna gidan uban suna zawarci, tace yayan Zakari mata basa jimawa a gidan miji zaki ji an sako su, uban duk kudin da ya tara baya iya saya musu ko gasarar koko, sai dai ya je tukubar mai shayi a lafta masa kwai da shayi mai kauri, ta ce ai ita kam Allah ya cece ta da ya raba ta da gidan su Jamilu.
Ta shiga lissafo wa Inna yawan matan da Zakari ya aura bayan ita yana shika musamman bayan yayi kudi abun babu ko dadin ji.
Tace bayan rabuwar ta da Zakari ta yi aure ta haifi wasu yayan mata guda biyu Hansatu da Lami, duk ta aurar dasu. Shekarar baya Allah ya yiwa mijin ta rasuwa wanda ya rike mata Jamilu kaamr shi ya haife shi.
Har yamma kafin Jamilu ya zo daukar Hajiyar sa, suna tafe a hanya Hajiyarsa na bashi labarin irin mutuncin Inna Safiya tun suna yammata. Jamilu ya sosa kai, da damuwa yace.
Hajiyata ina da magana, tuntuni, amma ina shakka, kin ga ba don halin Baban mu ba da illar da ya yiwa mutuncin mu gun Inna Safiya ba, me zai hana na auri Hauwa? Da ba sai kawai a yi yar gida ba ni da Hauwau? Rai kwance hankali kwance?”
Hajiya Rumana ta ce cikin mamaki wai kana nufin kana son Hauwa din ne? Jamilu ya koma sosa keya da hannun sa daya yace gaskiyar maganar kenan, Hajiyarmu tun ranar da na buge ta, nake fama da zuciyata a kanta, zuciyata bata kara zama lafiya ba a kan tunanin yadda zan yi na mallake ta, kullum tunani na shine yadda alamarin zai yiwu cikin sauki, amma na hanga na duba ta bangaren Babanmu na tabbatar zan samu matsala sosai da shi.
Jiya na je gaishe shi, na same shi na gaya masa tsautsayin da ya gifta na kade Hauwa, cewa yayi tun da na kaita asibiti na biya magani kada ya kara jin na koma inda suke.
Haj. Rumanatu ta ce umh, ni na rasa irin wannnan yan ubanci da yake yi wa dan uwan sa, shikadai ya rage masa amma ya kasa kaunarsa, wallahi shi bai dauke shi haka ba Bilyaminun, baka ga irin cin kashin da yake masa ba, haka yake masa tun suna yara saboda bakin cikin ya fi shi samu a sanaar sa ta gwanjo.
Kaima dai Yayan Hansatu banda kana son taro aradu da ka, ba zaka kaiwa mahaifin ka wannan maganar ba.
Jamilu ya ce (with boldness) idan har Hauwa ta amince min in sha Allahu zan yi nasara a kansa. Hakan ne kadai zai gyara wannangurbataccen zumuncin ya rage kiyayyar idan mun haihu nida Hauwa. Ta ce “to idon ta fa? Zaka iya zama da makauniya Jamilu?
Ba wai ina kin Hauwa bane saboda lalurar ta, tunda kuwa yar uwar kace jininka ce, amma akwai abun dubawa.
Tarbiyyar yaya, dawainiyar cikin gida, abubuwa ne da sai mai ido zai iya yin su. Da aikin banki zaka ji, ko da kula da nakasassar mata a cikin gida musamman in ta fara haihuwa? Kaida in ka fita tun sassafe wani zubin sai dare kake tasowa?
Don kuwa Hauwa, kasa a ranka in ka aure ta duk kai zaka yi mata wadannan abubuwan dana fada a can baya tana daga zaune tana fama da kanta.
Jamilu ya nisa cikin jin karin kauna da soyayya da tausayin Hauwa, sannan ya ce Hajiyata, a irin son da na samu raina yana yi mata, sam ban hango wadannan kalubalen ba, amma ni Jamil Zakari naji na gani, na yarda in har zan samu auren Hauwa, zan hadasu duka ita da yayanta in raine su in kula dasu har aikin bankin duka bazan kasa ko daya ba. Hajiya Rumanatu tausayi ya cika ta, ta dade da sanin dan ta Jamilu mutum ne har mutum, mai kyakkyawar zuciya akasin ta mahaifinsa, ta dade tana dakacen dama ace Bilyaminu ne ya haife shi, saboda halinsa na yawan kirki da nagarta shiyasa ma mahaifin sa sam bai cika shiri da shi ba don komai nasu Allah daya ne gari banban.
Sai ta ce Allah ya tabbatar da alkhari a tsakanin ku idan akwai, ya huwwace maka lamunin mahaifin ka cikin sauki. Auren Hauwa hakika Jihadi ne babba zaka yi, na gyaran zumunci da kuma na taimakon miskinin da baida maraba da maraya.
**** **** ****

An sallami su Inna daga gadon asibiti bayan an kwance karayar hannun Hauwa ranar wata lahadi, ta dauka shikenan sun rabu da jelen Jamilu. Amma ina! Ashe wasa farin girki, lokacin nema Jamilu ya maida gidan su wajen zuwansa. Aka ce in kaga kare na sunsunar takalmi.
Wani babban abinda yafi bata mata rai, duk shiru-shirun Hauwa da miskilancinta in da Jamilu suke hira kaji ta har tana kyakyatawa tun daga soro, tana hira rai-rai-rai kamar kanari ita da shi, ta sake da shi sosai abin ki da jini! Asabar da lahadi da baya zuwa aiki a gidan su yake wuni, makale da Hauwa, Inna ta rasa yadda zata yi da Jamilu. Daga baya ya fito fili ya gaya mata shi fa kamun kanwarsa yake yi, da zarar ta kare sakandire zai kawo sadakinsa.
Inna kam bata yi kasa a gwiwa ba ta ce Jamilu kana wasa! Kaima ka san wannna abu ne da ba zai taba yuwuwa ba, don haka na roke ka daga yau kada ka kara tada wannan maganar mara yuwuwa.
Ni bazan raba ka zumunci da yar uwarka ba, amma bana bayan wannan maganar wai auren zumunci kai da ita.
Jikin sa a sanyaye ya koma gida ranar, kuma kai tsaye ya yanke shawarar tunkarar mahaifin sa a kan maganar, a yi ta ta kare. Komai ta fanjama-fanjam.
Malam Zakari sai da ya bari Jamilu ya gama bayani kaf cikin kankan da kai, da tsananin ladabi ga mahaifin nasa, sai ya ce masa, kai kai kai! Kai kuma ta nan ka bullo?
Auren makauniya? Diyar BILYAMINU jafai a cikin zuria ta? Toh ban shirya haifar jikan da zai zo ya zama dan jagora ba. Ko ya gado makanta ya saka min a cikin zurria, ko babu makanta haihata-haihata jinina ya gogi na Bilya jafai, jinin jaraba jinin masifa jinin tsiya da rashin arziki.
Idan ka kuskura ka sake zuwa inda suke, idan na ji labari, sai na tsine maka albarka.
A gigice Jamilu ya bar gaban Baban sa, o ganain gabansa baya yi, shi kuma Zakari Jamilu na tafiya ya saka takalman sa ya fito ya rufo shagon atamfofin sa dake cikin Singa.
Da ya fafuri mota bai tsaya a koina ba sai a Badalar Kofar Na’isa.
Gidan ai ba zai taba bace masa ba, tunda kuwa gidan gadon su ne, Bilyaminu yayi masa karfa-karfa ya raba shi da shi, don haka kai tsaye ya tuna hanya, bayan tsayin shekarun da ba zai iya tuna yawan su ba rabon sa da ko bin hanyar.
Zakari ya yi sallama a zauren Inna, da katotuwar murya mai razana wanda ake yimawa.
Ta na tsakiyar dabbobin ta tana zuba musu dussa, ta ji muryar sa yana kwada sallama kamar zai tada gidan Safiya, ina Safiyar ne? Diyar masu Danjangabo?.
Nan da nan zuciyarta tace mata ZAKARI!. Don shikadai yake kirata diyar masu Danjangabo don sanaar mahaifiyarta kenan. Inna ta dago kai cikin mamaki ta tako ta iso soron ta yi tsaye a gaban sa, bazata iya tuna rana ta farko da ya tako kafar sa gidan su ba tun bayan rigimar mallakar gidan, da a karshe ya sayarwa Malam Bilyaminu.
Ai bai kamata kiyi mamakin gani na yau ba, tunda ke kika takalo ni, kuma kin sanni farin sani kamar kashi nake, sai an kula ni nake doyi”. Zakari ya fada cikin gyara murya da gyara tsayuwa. Inna tace,
dole in yi mamaki mana tunda dai na san banza bata kai zomo kasuwa yo daman ina kuwa zata kai shi? Sai ya ji wuta!
Zuwa nayi in ja kunnen ki, in sake ja, da kwantareriyar murya, in kin ji kin dauka, ki zauna lafiya, in kin ki ji ba kya ki gani ba.
Ki saki kurwar Da na Jamilu ta shakata, don shi ba nakasashshe bane, haka kawai kin ga yaro da maikon sa shine zaki bi dare ki bi rana ki lika masa makauniya ko? Yo Allah na tuba ko Kulu idon ta hudu kinga ta dace da Jamilu yaro son kowa dan gata dan asali, mai ilmi, mai nasaba, Uwar Bilya kuwa ki bincika tarihi kiji inda uban mu ya samo ta, can ne cikin zuriar su barbushe da tsimbirbira.
Inna Safiya ta yi tsaki ta ce kana tunanin ko Hauwa ta rasa miji saboda makanta, ko tana yawo tsirara saboda talauci, zan dauketa na baiwa dan ka ko shugaban kasa ya zama?
Ai ni martabar diyata da kake gani, duk da take marar ido, miskiniya, wallahi tafi karfin gidan ka, wulakantaccen gida na rashin tarbiyyah, gidan da daga yan daba sai yan shaye-shaye, sai sauta ga wawa rututu. Uba daya uwa kowa da tasa, kurwar ya ta kurr da shiga irin wannan laanannen gidan na Allah wadai, in sha Allahu.
Zakari ya kyabe baki duk da ya ji mugun ciwon maganganunta, ya ce ni dai na gaya miki, kuma aure-aure ai arziki ne, idan fitsari banza ne kaza tayi mana, shi bai iya ya kara ko daya ba saboda talaucin da yasa shi barin gida, ke da aka gudu aka bari bakin jini yasa ba wanda ya taba zuwa ya sunsuna ki da sunan aure, a haka zaki mutu gwauruwa, da makauniyar ya a gaban ki kina mata tsarkin kashi.
Daga yau zan zuba C.I.D a kofar gidan nan, aka kara

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login