Showing 6001 words to 9000 words out of 39065 words

Chapter 3 - Hauwa Kulu Book 1 Hausa Novel Complete

Takori   

30 Dec 2024

245

da ko kirgen dangi ban fara ba. Komai nawa dai-dai misali ne na asalin hausawa gaba da baya, kuma na halitta wanda babu kirkirarre. Zaku iya kiran ni Hauwa Kulu da (natural black African beauty) ta zamanin da na taso.
A wannan shekarar da aka shiga na samu kammala makarantar firamare, na zana jarrabawar kwamen intarans, watakila don na fara karatun da wuri ne na gama firamare da wuri, inda ba da jimawa ba sakamako ya fito, Hauwa sarkin himma (ta bakin Inna), na ci makarantar yammata ta gwamnati ta jeka ka dawo wai ita Shekara (GGSS Shekara).
Asalin iyayena kanawa ne na usul, wadanda ake kira Kanawan cikin Badala.
Wane tudu wande gangare duk aka bi za a fahimci daga Inna har Malam yan asalin cikin kofofin Kano ne, basu da wani kauye da zaa ce daga can suka fito ban da kwaryar cikin birnin Kanon.
Inna iyayen ta sun jima da kwantawa dama yan cikin Kofar Kansakali ne, kusan yanzu ita kadai ta rage a raye cikin jamaar gidan su babu wanda zata kira nata da ya saura, ta haifeni a shekaru na girma tana da kusan shekaru arbain sanda ta haife ni, shi yasa wasu ke dauka Kaka ta ce, babu wanda Inna zata kira nata a halin yanzu duk sun gushe, banda makwabta da abokan arziki da suke rayuwa a lungu guda.
Shi kuwa Malam Bilyaminu yana da dan uwan sa na jini Zakari mai wankin hula, yana nan a raye da nasa iyalin a unguwar kofar Dan agundi wadda ke daura da kofar Naisa.
Sabanin Malam Bilyaminu shi Zakari Allah ya bashi haihuwa da yawa maza da mata sun kai goma, sabida yana da yawan aure-aure, mata biyar ya aura, uku ne a gidan yanzu, don haka yayan iyaye daban daban suka haife su, sai dai ka samu biyu a daki daya ko uku a daki daya, amma kowa ya san babu jituwa ko kankani tsakanin Malam Bilyaminu da kanin sa malam Zakari sai yan ubanci na gani kashe ni, wanda a kan sa suka rayu tun suna kanana har gashi sun cimma furfurar su basu daina ba.
Bayan batan Malam, Inna na yawan korafi gareni, “tun batan dan uwan sa bai taba zuwa ya ga halin da muke ciki ba, bai kuma taba tuna wai dan uwan nasa ya bar diya mace guda daya, yayi tunanin kula da lafiyarmu ko da bai taimaka mana da komai ba”.
Sai in ce Inna kenan. Ai bai ma kamata ki damu ba Inna, don dama kin kwana da sanin ba batan sa ba damuwar sa bane, da kin yi shawara da ni ma bazaki je cigiyar Baba gidan sa ba Inna.
Amma a cewar Innar Hauwa, lalurar batan mutum ta wuce komai, don gara a ce mutuwa yayi a kan ta, a ganin ta sun cancanci kulawar sa ko yaya ne a bayan ido dan uwan nasa. Wannan shine cikar zumunci.
Wani abun mamaki shine bai fi shekaru biyu da batan Malam Bilyaminu ba, aka wayi gari aka ga Baba Zakari ya kudance, ya rushe gidan sa ya zabga ginin katon gida mai dakali biyu irin na masu kudin da, anan kofar dan agundi, ya sayi motar yayi ta zamani da ake kira Marsandi, ya kuma bude katon shagon sayar da atamfofi a Singa. Sunansa ma ya koma Zakari mai atamfa.
Ba irin maganganun da mutane basa yi akan arzikin Zakari na rana daya, wanda babu wanda ya san inda ya samo shi. Shikuwa ya kame bakin sa daga tambayoyin jamaa da an yi magana Baba Zakari zai ce DARE DAYA Allah kan yi Bature.
Wannan ba shi ne a gaban Innar Hauwa da ni kaina Hauwan ba, sai shirin fara karatuna a makarantar yammata ta Shekara, abinda Zakari bai yarda yaran sa maza da mata ko daya cikin su ya yi ba hana rantsuwa in ka dauke babban cikin su da ya saki uwarsa ta fita dashi shikadai yake yi a boye, wato Jamil Zakari, da kannen sa ke kira “Yaya Jamilu”.
**** **** ****

APOLO”
W
ani ciwon ido ne na yayi (eye flu) da aka yi annobar sa a wasu shekarun can baya. Wanda daukacin yara da manya dai-dai ne suka tsallake shi.
A wani wata na Junairu da muka shiga, bazan manta ba aka wayi gari da annobar cutar ciwon ido na apolo a garin Kano, yaya aka yi yaya aka yi? Ko wane tudu wane gangare aka bi aka samo? Sai gani nima Hauwa na samo nawa rabon na apolo, daga makarantar bokonmu ta Shekara. Amma Inna ta gagara dauka sabida karfin jinin ta da shaye-shayen magungunan gargajiyanta yana bata immunity iri- iri.
Da farko Innar Hauwa bata dauki abun nawa da muhimmanci sosai ba, don haka bata damu ba, duk da idon yayi jajawur ya kuma kankance kamar gauta, abinda yasa bata damu ba shine kusan kowanne yaro ya samu rabon sa na apolo a wancan lokacin, kai har manya ma, don in yaro daya ya samo duk gidan su sai sun raba (dauka). Amma in aka kwana biyu ko uku da kan sa sai kaga yana washewa. Daga nan kuma sai labari ko ba a saka masa maganin komai ba.
Don haka babu wani mataki da Innar Hauwa ta dauka baya ga tunanin cewa in an kwana biyu idon zai washe dan kan sa, kamar yadda yake yiwa 'ya'yan kowa.
Ciwon idon ya ritsa dani Hauwa-Kulu ina yar shekaru goma sha biyu da haihuwa. Aji biyu na karamar sakandire a GGSS Shekara.
Wasa-wasa abin da ake zaton kwana biyu ko uku zai washe sai gashi ya dauki wata biyu ba abinda ya canza, sai ma idon ya koma ya cabalbale da kwantsa ba kyawun gani, ko buduwa baya yi idan gari ya waye wato na tashi daga barci, in kai mai kyankyami ne kaga idona a lokacin bazaka iya cin abinci ba, kullum kuma ciwon karuwa yake ta yi kamar ana rura shi maimakon ya ragu ko yayi sauki, na kan cewa Innata idan na yi sujjadah ji take kamar kwayan idon zata zazzago (fado kasa).
Daga baya idon ya koma tsiyayar da ruwa da hawaye ko buduwa ya daina yi sosai, yayi jawur yayi luhu-luhu gwanin ban tausayi.
Innata, wato Innar Hauwa na daga cikin mutanennan yan gargajiya da a rayuwar su basu bada yarda da maganin asibiti ba, kai ita ko sunan likita ta ji an ambata sai ta yi tsaki, don haka kullum saidai ta gasa min idon da ruwan zafi da dan gishiri, ta rambade min shi da farin kwalli, in yi ta kuka don azaba, wanda hakan yasa ciwon idon kullum sai karuwa da cigaba da taazzara yake ta kara yi.
Watanni uku da fara ciwon, idon ya rikide ya koma min wata kebantacciyar cutar idanu da ake kira hakiya’ (cataract) ta fito ta kwanta tayi babakere a tsakiyar duka idanun guda biyu.

Lokacin ne hankalin Innata ya fara tashi, ganin wadannan Hakiya cikin kwayar idona sun fara girma, kowa ya ganni sai yayi fadan don me Inna ta ki kai ni asibiti? Meyasa ta bar idon ya zama haka? Ayi ta mata fada kamar a ari baki. A kuma gaya mata ai Innar Hauwa hakiya baa wasa da ita fa”.

Amma Inna tayi funfurus. Sai da ta kai na daina fita don zuwa makaranta don fadan da malamai ke yi akan a kaini asibiti amma Inna ta ki ji, sai cewa take ai tana saka min farin kwalli shine babban maganin ciwon ido, a hankali zai tsotse hakiyar gabadaya, amma ina! Abu kullum kamar ana kara iza shi. Har sai da ta kai ta kawo idanuwan nawa gabadaya sun yi fari tas, sabida yadda hakiya ta mamaye su.

Yau muna tsakar gida ina zaune bisa tabarma da littafin makaranta a hannuna, ba tun yau ba na fahimci na daina ganin abubuwa da kyau, yadda suke a zahirin kamanninsu, amma duk da haka na dage ni a dole karatu zan yi wanda ya wuce ni a makaranta, duk da idanuna dake neman zagwanyewa yau don zafi, amma me?
Ko da na bude cikin shafukan takardar sai na ga bana banbance duk wani rubutu dake cikin littafin sai hasken takardar kadai. Sai wasu taurari suna gilmawa ta gaban idona. Wannan ya tabbatar min, kodai ganina ya tafi, ko yana gab da tafiya ya barni.
Cikin tsorata da alamarin na kwalawa Innata dake madafi tana kwashe tuwo kira, nace, Inna ki zo, watakila fa Inna NA MAKANCE!!!
Inna na daina ganin komai a cikin littafi na komai ma bana ganewa.

Mummunar faduwar gaban da ta samu Innar Hauwa a wannan lokacin bata taba jin irin ta a rayuwar ta ba, ko lokacin data gane batan Baban Hauwa, da sanda aka shigo mata da gawar Zulkiflu daga rafi. Watakila sabida son da take wa Hauwa ne, ko kuma don ta saka buri mai girma a kan Hauwa a ran ta???
Burin ta na Hauwa ta yi maza ta girma ta aurar da ita, burinta na HAUWA ta zamo mai zurfin ilmi a rayuwa, irin wanda basu samu damar yi ba su, itada Malam, kuma basu da wasu yayan da zasu yi shi bayan ita, burin ta na Hauwa ta samu kwakkwaran abun yi da zai rike su a tsufanta nan bada jimawa ba, koda ta zama malamar makaranta ne. Ta kuma yi aure ta hayayyafa, yayan ta su maye mata gurbin yaya masu yawa da Allah bai bata ba a rayuwar ta? Ko kuwa don ita kadai ta rage mata matsayin sanyin idaniya a halin yanzu, amma ace yau idanun ta babu? Ba karamin fadar da gabanta hakan yayi ba.
Sai Inna ta bar abinda take yi, ta taso zani na kwancewa ya kusa faduwa ya barta, ta yo kan Hauwa da gudu, tana ambaton "bana son fatan tsiya HAUWA. INNALILLAHI WAINNA ILAIHI RAJIOUN.
**** **** ****





Wannan shine labarin da Barr. Hauwa Bilyaminu ta bayar a safiyar yau a dakin taron da aka hada mata na 'meet and greet,' tsakanin ta da kungiyoyin da take da alaqa dasu, kungiyoyi ne da suka tsayawa rayuwarta har ta kawo wannan matsayin, da sauran masoyanta mutanen arewa wato masu nakasa iri daban daban maza da mata wanda yau yayi quenching curiousity da jita-jitar kowa cewa HAUWA BILYAMINU IS A PHYSICALLY CHALLENGED PERSON. Kuma a ranar ne Hauwa take murnar cika shekaru hamsin da haihuwa, sannan a ranar ne ta karbi jagorancin Nigerian Bar Association. Wanda yayi daidai da ranar anniversary din aurenta da "HER PACE-SETTER..." shekaru dai-dai har talatin da daya.

Barr. Hauwa Bilyaminu Kofar Naisa, ta bamu labarin asalinta da tushenta ne a wannan muhimmiyar ranar mai tarin achievements a gareta daga hakikanin bakinta, da asalin lalurar ta. Daga nan na kasa hakura da jin me ya faru da sauran rayuwar HAUWA-KULU? Ni Sumayyah Abdulkadir (Takori) na bibiyi labarin Barr. Bilyaminu bayan taron nan, zan kuma labartawa Takorites labarin HAUWA-KULU daga ranar data rasa abu mafi muhimmanci ga rayuwar bil adama har zuwa yau da take bikin murnar zagayowar cikar shekarun haihuwarta hamsin a duniya.

**** ***** *****


M
afarin makancewar Hauwa-Kulu kenan. Makanta mai sunan hakiya da akafi sani da (cataract blindness), ko a ce makanta mai lasisi, tunda kuwa Innar ta ce ta sayo mata da kudin ta.
Don da farko Inna ta dauka Hauwa wasa take yi, amma cikin kwana biyun da Hauwa ta koma lalube da tsakar rana ko da daddare ta fahimci cewa Hauwa da gaske take, tana gab da daina gani, amma dai tana ganin haske da inuwar mutum in ya tsaya a kan ta, dan ko daki sai da lalube take kai kan ta, ko Innar ta kama hannunta ta kai ta don kada ta buge goshi.
Saboda haka ne wannan karon Innar ta tsorata. Dole kanwar na ki, ta tambayi inda zata kai Hauwa aka ce mata ta kaita bangaren ido a Murtala (Murtala Mohammed Specialists Hospital), washe gari tasa ta a gaba sai asibitin Murtala.
Da tambaya suka isa bangaren ido, a kafa suka tako suka taho tun daga kofar Naisa har zuwa bakin asibitin Murtala. Kusan wannan shine karon Inna na uku da zuwa asibiti a rayuwar ta, sauran biyun duk dubiya ta zo, don ita ba mai yawan ciwuwwuka bace sabida yadda ta tsaya da shan magungunan gargajiya da jike-jiken saiwoyi akai-akai bata yarda tayi wasa da su, don ko haihuwar Hauwa data marigayin Yayan ta bata yarda an kaita asibiti ba, don haka hatta yanda ake karbar kati basu sani ba, saida taimakon wata mata da itama ta kawo yar ta ganin likita, suka samu suka karbi kati suka hau dogon layin ganin likitan ido. Don kuwa a makare suka iso.
Suka kuma gamu da dogon layi don ranar ganin likitan ido ce wato Alhamis.
Sune kusan na karshe a kan layin, suka zauna a kan bencin da aka tanadar wa marassa lafiya masu bin layin ganin likita bayan sun mika katin su, maaikatan jinya da yake akwai marassa kirki cikin su, idan suka juya suka kalli idanun Hauwa sai suyi tsaki, su hau maganganu na gugar zana cikin zagin jahilcin mutanen kauye wajen sakaci da zuwa asibiti, sai ciwo ya ci ya cinye a kwaso jiki hajaran majaran wai an zo asibiti, sun dauka daga kauye suke don sun fi musu kama da kauyawa.
Inna na jin su, ta yi shiru ta sadda kai, bata tanka musu ba.
Wata metron zaqaqura a cikin su, ta kasa gugar zanar ma, sai da ta fito fili ta dubi tsakiyar idon Inna ta ce.
To yanzu saboda Allah baiwar Allah me likita zai iya muku a wadannan matattun-rubabbun idanun da hakiya ta riga ta cinye?
Allah wadaran bakauyen mutum wajen wasa da lafiyar sa!.
Da sauri Inna ta dago ta dube ta, kafin ta rufe baki dayar ta amshe.
“Taya ni gani, tun dazu nake kus-kus din hakan a raina kika riga ni furtawa, saboda Allah dubi yarinyar nan sai da Hakiya ta gama cinye idon tas, sannan zasu wani dauko kafa budu-budu dasu su zo asibiti, yo wannan ai ta gama makancewa da lasisi, ko me likita zai iya musu a wannan lokacin ina ce aikin banza ne?.
Inna dai na jin su, amma bata tankawa, duk da ta yarda basu da mutunci kuma basu girmama furfura, amma ita da kanta ta yarda har da sakacin ta wajen lalacewar idon Hauwa-Kulu.
Ta sunkuyar da kai kasa sosai, hawaye fal idon ta, amma bata bar su sun zubo ba. Ta dago ta dube su, su duka basu fi a kira su yayan cikin ta ba amma suke mata wannan tanadin. Kodayake kowa ya san yadda maaikatan jinya na gwamnati suke, daidaiku ne masu jin kai da kirki ga marar lafiya, musamman ga mutanen kauye da talakawan da suka raina wa ajawali kamar yadda suka raina Inna din, don sun ganta da kodaddiyar atamfa mai barewa, kuma tayi abunda a wurin su jahilci ne da gidadanci.
Sanin halin malaman asibiti da sau tari ake bata labari tuntuni, yau da suka gwada mata sai bata yi mamaki ba kuma bata ji zafi sosai ba, shiyasa ta daure taki damuwa da su, fatan ta kawai su mika katin su ko sa samu ganin likita.
In ya so shima ko me zai ce mata yace mata a shirye take da daukan laifin ta. Fada ne dai ta san zata sha shi har a wurin likitan shima, to in dai a karshe zai baiwa Hauwa magani, ganin ta ya gyaru, ta rabu da wannan hakiya, to babu komai, shima zata jure nasa.
Ba abinda malaman jinya basu ce mata ba na raini da wulakanci, da suka tambaye ta ko tun yaushe Hauwa ta fara hakiya? Ta ce an fi wata uku, suka ce to tun yaushe suke ganin likita? Nan kuma ta sunkuyar da kai ta ce basu taba zuwa ba sai yau.
Sai wata maaikaciyar jinyar mara kunyar gaske tayi kamar ta doke ta, yadda ta rufe Innar da fada duk da ta girme ta, ta ce to ba zata mika katin nata ga likita ba, su tattara su tashi su tafi, in yaso su je su karata da farin kwallin da take rambada mata kamar idanun kwatami.
Inna ta kauda kai ta rabu da su. Amma bata yarda ta tafi ba, duk da sun kore ta. sun kuma tabbatar mata bazasu mika katin nata ba. Sai suka rabu da ita suka koma hirar da ta shafe su, suka manta da su a wurin. Lokaci lokaci suna kiran sunan marasa lafiya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login