Showing 30001 words to 33000 words out of 39065 words

Chapter 11 - Hauwa Kulu Book 1 Hausa Novel Complete

Takori   

30 Dec 2024

251

nake gani akan fuskarki a duk lokacin da kika ji sallamata a gidan ku. Me nayi miki haka? Meye dalili? Na rantse gaisuwa ma akan dole kike yi min ita. Kulu baki dauke ni dan uwa kamar yadda na dauke ki ba..
Hauwa-Kulu sai ta fara hawayen babu gaira babu dalili, ko da yake dama sun cika idon tuntuni suna so su zubo ne, tana fin karfin su. Mai neman kuka ne aka jefe shi da kashin awaki. Ta ce dama kullace kake da ni haka duk tsayin lokacinnan ban sani ba?. Nake kullace da ke? Ko kike kullace da ni?.
Inna bata san me yasa ta kasa sauraron takaddamar tasu ba, ko don cikin zafin rai kowanne yake furucinsa, sai ta tashi salin alin ta saka takalmanta ta dau buta da niyyar ta zagaya bayan gida, ba tare da tana jin fitsari ko kashi ba, kawai ta kasa jure ganin hawayen Hauwa shi kuma ta kasa jure ganin bacin ran sa karara yau, don bata taba ganin sa cikin bacin rai ba, shi Sarham ta fahimci kullum mai kirki ne, mai fara ne, mai walwala ne kuma mai farin-ciki da kowanne yanayi (jovial person).
Kasancewar bai taba nuna bacin rai a kan share shin da halin koin kulan da Hauwa-Kulu ke nuna masa ba sai yau, wanda itama ta sha yi mata fada a kan bata kula shi, bata kyautata muamala da shi, bata masa fara kamar bata so yake zuwa gidan su, amma Hauwa sai ta ce,
to Inna me kike so in dinga ce masa? Magana ba sai ta dauro ake yin ta ba? To ni ban da wata magana da shi banda gaisuwar da ta zame min dole, kuma ina gaida shi”.
Rannan da Inna ta hau ta da fadan ya zo har ya fita ranar ko gaisuwar ma bata yi masa ba, Hauwa ta zaro manyan idanunta waje (ta manta da wa take magana) ta ce,
Inna! Idan kin manta ni ban manta ba, daga gyaran ido ya karasa makanta ni, ni duk wannan kirkin nasa gare mu ta baya ta raggo, ido fa na rasa a hannun sa, Inna! Wani abu zai min ya biya ni?”
A ranar Inna ta sha mamaki ta kuma tsorata, ta ce au, dama dalilin ki na kin girmama alamarin likita kenan?. Hauwa ta yi shiru, sai can ta kama hawaye. Tace Inna dalili na kenan, amma ba wai na rike shi a raina bane na san kaddara ta ce, amma kullum na tuna shi yasa idon ya karasa macewa saboda careless na aikin sa sai naji tsanar sa ta darsu min, tunda Inna ba abinda zai yi ya biya ni ido na, ba kuma abinda zai min da zan yi farin ciki da shi idan ba idanuna ne suka dawo min ba!”.
Inna ta kai hannu zata mari Hauwa, ko me ta tuna? Malam Bilyaminu! Ya taba rokonta ko me Hauwa zata yi nasiha ta kasance tsakaninsu ba duka ko zagi ba, duka baya biyar da yaro yayi abinda kake so saidai ya kara kangarar da shi musamman mautum mai riko irin Hauwa-Kulu.
Sai Inna ta rike hannun nata da daya hannun, ta hana shi isa ga fuskar Hauwa. Cikin tashin hankali tace mata na rasa me zan ce miki, Baban ki ya sha gaya min kina da kullata ban taba yarda ba sai yau, amma ina so ki sani Allah ne ya dora miki makanta ba Likita Sarhamu ba, su kawai masu taimakawa ne a samu lafiya amma suma basu hada sani da Allah ba, lalube suke cikin abinda suka karanta don su taimaki alumma kawai.
Inaso ki sani Hauwa-Kulu, komai na rayuwar dan adam a rubuce yake a Lauhul Mahfuz, tun kafin halittar sa balle haihuwar sa.
Ban so kika saka wannan mummunan tunanin a ranki ba Hauwa-Kulu, domin ya zama rashin yarda da kaddara, ya nuna baki dauki kaddararki da kyakyawar zuciya ba kenan, wanda yana cikin sharuddan imanin mumini.
Yi maza ki ce “astagfirullah domin wani Likita duk kwarewarsa ko akasinta, bai isa yayi abinda Allah bai yi ba, kuma shi ba Allah bane da zai bayar da lafiya ko ya hana.
Banda son zuciya irin naki, in ma tuhumar ne ni ya kamata ki tuhuma, ni da tun farko ban kai ki asibiti ba tun ciwon yana apolonsa, sai da idanun suka kusa tashi aiki.
Haka Inna tayi ta mata waazi mai shiga jiki a lokacin, amma Hauwa-Kulu bata kara tankawa ba saboda miskilancin ta, don haka yanzun ma da Inna ta shige bayi ta bar su a nufin su gama fadan sannan ta dawo, Sarham ya ce wai ta fadi abinda ke ranta yau, kada ta bar shi a ranta ya kashe ta, sai taji kuka ya kwace mata ba kakkautawa a gaban sa.
Sarham sai gashi jabar! Ya koma ya zauna dabas a kasa, akan rairayin tsakar gidan su Hauwa. Taja gefen hijabinta ta rufe fuska cikin kakabi da fushi da muryar kuka ta ce, babu komai a raina, sai fatan alkhairi ga kowa”. Sarham ya ce karya kike yi, kuma ni bana shiri da mai karya. Ko amon muryarki ya karyata ki, ya karyata abinda kika fada.
Fatan Alkhairi ne a ranki game da kowa? Amma banda a kaina ni Sarham ko? Wa na kashe miki? Ko me nayi miki haka da zafi da kika kullace ni?. Hauwa ta rasa yadda zata yi da shi, don ba zata iya ce masa tana jin maqaqin sa a ranta ba, da cewa bai iya aiki bane ko kuma carelessness dinsa ga aikin sa ne yasa ta makance gabadaya.
Sai ta samu bakin ta ya bige da cewa cikin rawar murya da rishin kuka.
Ina dakace ne na cewa, inama ina gani! Inama in ga fuskar ka a zahiri in san kamannunka! Rashin idona yana hanani farin ciki da kowa da komai”.
Mamaki ya kashe Sarham daga zaunen da yake na yadda nan da nan ta kirkiri karya don kaucewa tunanin ta na hakika, ya dube ta sosai cikin manayan idanun ta kamar tana ganin sa, zai so ace a lokacin da zai fadi abinda zai fada yanzu sun hada ido, yace cikin wata irin murya mai rauni.
Maijidda you are accusing me for being the cause of your blindness, (Maijidda kina tuhumata da zamowa sanadin makancewar ki), hakane ko ba haka ne ba?!”
Hauwa ta cira ido a firgice, zuwa inda take jin tashin sautin sa, ya daga gira yace Yes, ba wani son ganina da kike yi, karewa ma ba kya son gani na, you are just accusing me.
Ni kuma na san bani na makanta ki ba ALLAH ne ya tsara miki wannan jarrabawa domin ya jarrabi imanin ki Maijidda. Nakaa ba komai bace face jarrabawar Ubangiji ga wasu kebabbun bayinsa.
Unfortunately, kina neman faduwa jarrabawar ki Maijiddah, domin a zuciyar ki babu TAUHIDI babu IKHLASI. So ya rage naki kiyi maza ki gyara, kiyi istgfari, ki yi kokarin cin jarrabawar ki, ko ki bari shaidan ya ci nasara da galaba akan jarrabawar ki ya barki da biyu babu; ba ido ba imani. Don ni, da ke duka mun san yarda da kaddara yana cikin cikar imani.
Hauwa ta dan tsorata da bayanin nan da Sarham yayi mata, amma dai ko ta gamsu da bayanin Sarham bazaka taba gane hakan akan Bakanuwar fuskar ta ba, mai iya boye abubuwa iri-iri da ki-fadi, tace,
ta yaya zaka fadi abinda baka shiga zuciya ta ka gani ba? Saidai in dama kana tuhumar kanka ne”. Sarham yayi dan murmushinsa mai ban shaawa domin yanzu ya gama gane manufar ta, da abinda ke cikin ranta a kansa tuntuni da yake saka shi ganin sad expression akan fuskarta, yace.
Nayi laakari da maganar hausawa ne da suka ce labarin zuciya ai fuska ake tambaya, kuma dai ‘Im older than you, and Im good at reading minds. Da babbar murya zan iya kiran kaina ‘behavioural analyst’, amma mu barshi a abinda kika fada din, watau kina son ganin fuskata ne, me kike kissimawa akan fuskar tawa?
Idan kuma ni din mummuna ne fa Maijidda? Irin munin da in an gani sai an rufe ido don muninsa?
Hauwa bata san sanda tayi murmushi ba, alhalin ga hawaye face-face a fuskarta, ta ce mummunan mutum ba mutum bane? Ai mummuna da kyan hali irin naka, sai yafi kyakkyawan gaske nagarta da shiga ran mutum, bayan haka ma a hakikanin gaskiya ni ba wannan nake kissimawa ba, ina kissima yadda fuskar zata yi dai-dai da irin kyawawan kalaman ka ne, koyaushe kana magana wadda ta dace da muhallin ta, kana da tunani na ilmi (with abstract reasoning)”.
Sarham wani irin kallon bakinta dake motsi a hankali yake yi, da murmushi yace ikon Allah. Ya akayi ni ban sani ba? Kamar wadanne iri ne kalamai na masu kunshe da abstract reasoning? Irin dai wadanda kake yawan yi cikin surutun ku kai da Inna, wani lokacin ina saurara, nafi zama mai sauraro a hirar mutane fiye da mai contributing, ta nan nake fahimtar yanayin zancen kowa, na fahimci maganganun naka duka a muhallin su kake yin su, kuma a takaice, amma cike da tarin maanoni da alfanu, sannan duk wani cukurkudadden alamari ka san ta yadda zaka bi ka warwareshi cikin hikima irin taka”. Sarham ya zura takalman sa, ya mike idonsa akan Hauwa, yana sakin dariyar da bai shirya zuwanta ba, ya lura yau in zasu kwana a haka, bazai gaji da sauraron dadadan furucin Maijidda gareshi ba, ya ce SAI WATARANA Maijidda sai watarana, ina rokon ki, duk runtsi kada ki bar zuwa makaranta, koda kin rasa dan jagora! Ina nufin against all odds, koda da rarrafe ne ki jure ki nemi ilmi, duk da nasan ba zai zamo abu mai sauki gareki ba, dama duk masu lalura irin taki, amma ki sani Allah ne gatan ki sai kuma shi (ilmin)”.
Idan na rasa dan jagora da wanne idon zani makarantar? Misali, idan Salele ya daina kaini ko ya mutu?”
Hauwa bata san sanda ta jefe shi da wannan tambayar ba, a lokacin har ya saka kai zai bar tsakar gidan su. Amma jin yadda muryarta ke rawa da karkarwa kamar kuka zai kwace mata yayin fadar hakan, a lokacin da take fadin hakan ma tuni hawaye ya ciko idonta, sai Sarham ya juyo yana kallon Hauwa da wani irin expression a idanunsa, cikin wata irin karaya da kewa, hasken farin wata ya haske masa fararen idanun ta suna jujjuyawa a cikin lalurar rashin gani. Ya kamata ya bata amsar wannan tambayar ta yadda zata dade tana tuna ta, wato tayi ta shawagi a kwakwalwarta, har ta zame mata tsani a rayuwa.
Ta hanyar sakawa ran ki cewa zaki iya komai da mai lafiyar ido zai iya, hankali ke gani ido gululu ne, ki tuna kullum da karin maganar da Bahaushe ke cewa “ba nakasashshe sai kasashshe”. Bature kuma yace
“theres ability in disability!”.
Sannan kullum kisa a ranki “nakasa ba komai bace face wata kankanuwar jarrabawar imani ga wasu kebabbun bayin Allah na kwarai daga Azza wa Jallah”.

Wadannan kalaman nasa su suka zamewa Hauwa-Kulu a food for thought, har bayan tafiyar Dr. Sarham daga rayuwar su, bata bar mayar dasu madubin ta na rayuwa ba, fitilar dake haska mata duhun koina dake cikin nakasar ta, sannan jagoran ta a duk lokacin da ta rasa dan jagora, wato kalaman sa ta saka a gaba suke saita mata hanya a duk inda ta nufa, don cimma rayuwa mai amfani a cikin halin data ke ciki na nakasar idanu.
Watanni masu dama suka biyo baya suna cikin kewar sa mai yawa itada Inna. Cikin tuno ‘precious moments’ din su tare dashi. Ko na rana guda sun kasa mantawa da shi.
Sun kasa mantawa da tarin gudunmuwarsa ga rayuwar su, da lokutan da suka kasance tare da shi cikin yanayi na zumunci da yan uwantaka. Zaman sa na dan lokaci cikin rayuwar su ya dauke musu kewar Baban ta watau Malam Bilyaminu kaso 50% data dan uwanta mai rasuwa wato Zulkifl, duk da a sanda yake zuwa wajen su din bata wani damu da shi ba, sai ma kullata data biyo baya, duk da repentance dinsa gare su akan laifin da ba lallai a kira shi nashi ba, amma bayan tafiyar sa, da irin emotional sallamar da suka yi mai zaunawa a rai, hakan yasa ta yin kewar sa bad an kadan ba.
Guzurin kudi da ya bar musu har naira dubu daya sun dade suna cin moriyar su, kafin bayan wasu watanni masu yawa su kare, duk da haka Inna bata bar sanaar ta ba ta sayar da wake da shinkafa da juyen dabbobi a kasuwa duk shekarar sallahr layya.
A lokacin Hauwa ta shiga babbar sakandire aji biyu, watarana ta dawo daga makaranta tare da Salele kafin su hawo motar bus da zata kawo su kofar Na’isa Salele ya hango ana hawan kilisa a kan dawakai a tsallaken titi. Saleleh mayen dokuna ne na gani kashe ni, yana matukar son wasan Polo da hawan angonci ko hawan sallah na sallah da sarki ke yi a Kano, tuni suka kwashe hankalin sa daga kan Hauwa, ya bata jakar makarantar ta ya ja sandar da suke kamawa shida ita a matsayin jagora tsakanin su, don ba hannun ta yake rikewa ba duk da ta girme shi, yace.
Hauwa, zauna kan bencin can ki dan jira ni in ga wucewar masu kilisar can akan dokuna Hauwa tace toh, amma don Allah kayi sauri Salele, ka san yanzu Inna tana duban hanyar mu, kada ta ga mun dade ta damu.
Salele tunda ya nausa cikin yan kallo ya bace mata bat! Shiru shiru Hauwa na jiran Salele bai dawo ba, karambani irin nata yasa taga cewa bari dai kawai tarabu da shi yau tayi kokarin kai kanta gida kada hankalin Inna ya tashi. “Dr. Sarham” yace ba ido ke gani ba hankali ne ido gululu ne kawai.
Sai ta tashi da zummar ta tsallaka titi ta tari motar kofar Naisa, don daga yadda take jin karar motoci ta san a bakin titi suke, tana tafiya a hankali abunta kanta a kasa ba tare da ta san ina take saka kafa ba ai dai mutum ya gane da kansa bata gani shi ya kauce mata.
Ai kuwa bata jima tana tafiyar ba taji ‘horn’ din mota a tsakar kanta, wanda ya kidimata ta diririce ta kwasa da gudu, motar kuwa bata yi kasa a gwiwa ba wajen kwasheta, ta yi sama da ita sannan ta nana ta da kasa.
Salele dake tsallakowa titi akan idon sa mota ta kwashe Hauwa. Ya dora hannu a ka ya rafsa ihu yayi kanta a tsakiyar titin yana fadin na shiga uku, Hauwa ban ce ki jira ni ba? Hauwa!!!”
Mai motar ya gangara gefen titi ya tsaya, ko kafin ya fito daga motar jamaa sun taru a kan Hauwa ana salati. Da yake na kirki ne sai bai gudu ba, ya taimaka aka saka Hauwa a motarsa, tareda wani dattijo da Salele da ya ce ai Yayar sa ce, suka nufi asibiti da ita jini nata disa a motar, amma mai motar nan bai damu ba ta ran Hauwa yake, yana rokon Allah yasa abun ya zo da sauki kada diyya ta hau kansa.
Hauwa bata san inda kanta yake ba har suka shiga babban asibiti.
Asibitin Malam suka kai Hauwa, a ka karbe ta a imajensi likitoci uku suka rufu akan ta suna kokarin ceto ranta. Sai bayan an samu an yi treating raunukan da ta ji, an kuma daure karayar da ta samu a hannu sannan aka basu daki kwanciya. Wanda ya kade ta duk shi ya biya komai, kuma ya tsaya har aka kai su dakin kwanciya din na mata inda aka basu gado.
A lokacin ne ma ya samu damar da ya kalli Hauwa tana barci, duk da ta kara girma sosai, ta zama budurwa sai yaga kamar ya santa. Ya tambayi Salele gidan su, don aje azo da iyayen ta, Salele ya ce zai je shi kadai ya zo da Innar ta.
Don haka saurayin ya ja kujera gaban gadon Hauwa ya zauna bayan fitar Salele, ya dau wata jarida a kan lokar gadon ta asibitin yana dubawa yana satar kallon Hauwa yana fadi a ransa yau tsautsayi ne ya fito da shi daga wajen aikinsa ba tare da lokacin tashin sa yayi ba, tsautsayi da baya wuce ranar sa, banda haka shi baya wani fita cin abinci har cikin bankin a ke kai musu su biya, daga yaje ya ci abincin rana a restaurant ya koma office zuwa lokacin tashi tsautsayin nan ya ritsa da shi?
Ya sake kai duban sa ga Hauwa a karo na sau ba adadi, sosai take masa kama da wata fuska da ya jima da sani, amma ya kasa tuna inda ya san fuskar ba.
Har saida Inna tayi sallama a gigice ta fado dakin asibitin kamar an turo ta, Salele ya biyo ta a baya da buta da bokiti da tabarma da bargo, nan ne mutumin ya gane ta sarai. A tsorace ya mike tsaye, ita kuwa Inna bata ma lura da shi ba kan Hauwa tayi tana salati tana godewa Ubangiji.
Bayan ta dan nutsu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login