Showing 27001 words to 30000 words out of 33950 words
ne indai kace Zaka shigo gona ta Ni Maleek, a da baya ina tunanin kasan Ni waye ,ashe jahili ne kai har duniya ta tashi ba zaka taɓa sanin Waye Maleek ba.......yanzu za'a fara . Yana furta haka ya juya cikin takon sa na tijara yana fucewa daga falon zuciyar sa na masa suya da tafasa . A hankali kalaman Daddyn sa ke dawo masa . Maleek ka lura da wanda ke zagaye da kai . Da yawa mutane baa zama don wani saboda Allah sai don wani dalili nasu.
Lumshe idanun sa yayi wanda suka kaɗa sukayi jahhhh , Ji yake zuciyar sa na masa wani irin kuka mai gunji , a haka ya shige moton sa yana tahowa gidan mahaifin nasa , wanda kamin ya iso kiran Rayyan ya shigo masa babu iyaka amma kuma bai ɗaga ba ,don baya cikin natsuwar yin hakan . Part ɗin Ammie ya nufa Amaryar Daddy Wanda da shigar sa ya tadda ita kaman ko yaushe zaune tana aikin istigfari da counter a hannun ta . Ammie Barka da gida . Ɗagowa tayi tana bin sa da kallo tare da kankance idanun ta tana son fahimtar damuwar sa amma kuma ta gagara ganin yanda ya sauya fuskar sa lokaci guda tamkar babu damuwa a tare dashi . Barka" maleek yau dai hutu ake jin yi ,ai yafi hakan ma ,aikin yawa yake maka . Hummm . Murmushi yayi yana magana kai tsaye tare da cewa " Ina Daddy yana sama ne? . Eh yana falon sa...........................!
[11/30, 7:40 PM] 🙂🙂🙂🙂: *Littafin na kudi ne ,don Allah kar ki karanta in baki biya ba . Regular payment ₦500 vip payment ₦1000 Zaki tura kudin ki ta wannan account number 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank shaidar biya ta wannan number 08081202932 https://youtube.com/@mamanteddy4123?si=1cwxAAGsGEzYkelS*
#Hasile#maleek#taufiq#labyoufans.#mr.romantic
Hannun sa yasa yana ƙara kama pennis din sa yana jijjiga ta tare da furta Ohhhh Ashhhh. Ɓangare guda kuma yana ƙara kame nonuwan Hasile yana matsa su tare da furzar da iska mai huci . Really lab you baby . Ya furta cikin yaudararriyar Muryar sa . Wani irin guuuurrrrr yaji tamkar shocking ya Jah sa ,wannan yasa shi ware Lulun idanun nasa yana kallon fuskar ta . Gani yayi idanun ta sunyi sama , sun koma tamkar garwashin wuta babu baƙi ko fari sai jahhhh . Innalillahi wa'inna ilaihir raji'una . Ya furta yana saurin ɗauke hannun sa daga jikin ta yana matsawa baya. Kaman wanda aka yi ruwa aka dauke yaga tamkar ba itace idanun nata suke a rufe ba . Don a yanzu barcin yaga tana yi . Humm". Sauke Numfashi yayi yana miƙa daga tsaye tare da fara kaiwa da komowa .
Sam bai san tsawon lokacin da ya dauka a haka ba , don inda zai duba ga lokaci Tom ya dauki yafi awa guda yana kaiwa da komowa a tsakiyar bedroom din .
Ina son Sanin Waye munafukina na ɓoye me son ganin baya na ? Dole mutum ɗaya ne zan tattauna dashi akan wannan lamarin ...Ruslaan . Ya furta yana juyowa tare da kallon inda Hasile ke kwance , shine kadai zai iya binciko mun domin I know he's Sharp, yana da matuƙar basira . A yanzu Ni bana da wannan sukunin,dole nasan gaskiyar komai .
Yaya!
Siririyar Muryar ta ya katse shi , wanda bai san lokacin da ta tashi ba sai dai tsinkayar Muryar ta da yayi yaji ta kirasa da sunan da babu wanda ya taba kiransa da hakan . Cikin sauri ya juya yana kallon inda take zaune a tsakiyar gadon itama idanun ta na akan shi . Ƙurrrr yayi mata yayin da itama take kallon sa . Kawai sai gani yayi hawaye na fara bin Kuncin ta tana motsa laɓɓan ta tare da cewa " Yaya na don Allah Ka koma dani Ruga ka kaini gun Umma ta . Na fasa Karatun ,na fasaaa Rugar mu zan koma .
Kallon ta yayi yana saurin isowa inda take , tare da kai hannun sa yana ƙoƙarin riƙo ta , gani tayi yayi saurin janye hannun sa tuno da Duk indan ya taɓa ta abin da ke faruwa dashi . Hafsat kin tuna dani? Kin tuna Ni? . Ƙallon sa Hasilen tayi tana kai hannun ta tare da goge Hawayen fuskar ta tana Girgiza masa kai alamun a'a . Jaaan numfashi yayi yana Girgiza kai tare da furta "Ya ALLAH".
Yaya na bana son karatun bana son zama mai ilimin ka koma Dani Ruga .
Karatu Hasile? Yayi maganan yana kallon ƙwayar idanun ta. Waye yace zaki karatu? . Adda Bilkisu ce . Eh Rugar mu ta taho tayi mun alkawarin zan yi ilimi,sai kuma na ganni anan. Yanzu wurin umma ta zani. Shiru Maleek yayi don ya rasa fahimtar komai daga gare ta ma .
Humm ok yanzu taho muje ki watsa ruwa sai kici abinci , Idan na dawo zan maida ke rugar ku . Amma sai kin mun alƙawari daya!
Kallon sa Hasile tayi kana cike da gurɓataciyar Hausan ta tace " wacce Alƙawari ce ? Faɗa mun zan yarda indai zaka maida Ni gurin Umma ta da su Baffa Harɗo .
Hum". Ok Ina zuwa . Ya furta yana sakar mata sihirtaccen murmushin sa kana ya fice daga bedroom din ba tare da hasile tasan inda zai tafi ba .
Tana Zaune kusan mintuna sha biyar sai gashi ya shigo shi da Wata mata mai ɗan shekaru . Inda Hasile take suka iso . Yayin da Maleek ya kalli Hasile yana sakin mata murmushi tare da cewa " Hafsat ga Hanne , ita zata yi Miki wanka ta gyara ki sai ta baki abinci kamin na dawo yanzu .
A'a Ni ba zata yi min wanka ba , hakan bashi da kyau , Taɓa mun jiki zata yi tayi, haka Adda Bilkisu suke yi da watannan da ta kai ni wurin Hajiyar nan......!
[11/30, 7:40 PM] 🙂🙂🙂🙂: Mr.Romantic
#Mamanteddy
Komai sai dai muce Alhmdlh domin kuwa Umma ta yarda da kalmar da aka ce komai yayi tsanani sauƙin ta na gab . Gaba ɗaya rugar Daala ya hargitse da Fulanin cikin rugar dana maƙotan su , dawowan hasile yayi matuƙar faran ta ran wannan mutanen har da masu kukun farin ciki su Yadikko kenan. A ɓangare guda ne Daddy da Alhaji Aminu suka yi masu liman da Baffa Harɗo duk wani bayani akan dalilin zuwan Bilkisu da kuma yanda ta shirya sharrin ta don ganin ta tarwatsa Rayuwar Ɗan nasu ɗaya tilo . Daga karshe kuma ga yanda Al'amuran suka ƙare da ita. Ya Allah kayi mana tsari da hali da kuma san abin duniya da zai haifar mana da nadama irin na Billy da tawagarta. a wannan yammaci ne Su Daddy suka kuma sanar da Abin da suke buƙata na neman Auren Abdool Maleek da Hasile , Wanda hakan ba su ja ta da tsawo ba . anan ne Baffa Harɗo yayi masu bayanin Matsalar da Hasile ke fama dashi , Wanda tabbas ba zai yiwu a basu Aure ba tare da anyi mata magani ba an rabata da baƙaƙen iskan da take tare su . Shikam Maleek bai yi mamakin jin haka ba ,don dama tuni yayi nazarin ta kuma yayi tunanin hakan a zuciyar sa. Hakuri Liman ya ba Su Daddy tare da ce masa " Su dawo bayan sati biyu , kamin nan komai inshallah an yi an gama. Da fari Maleek yaso turjiya don baya tsammanin zai iya yin nesa da Ita a lokacin da yake buƙatar ta na iya tsawon karshen rayuwar sa. Amma haka Mommy da Ammie suka lallaɓa shi daƙyar ya amince su ka taho .
Ɓangaren Gidan jibo kuwa babu wanda yasan Al'amarin dake kai da kawowa , sai dai matasan gidan da kullum suke ganin Annuri bayyane fuskar Maleek ,har wani chanjawa yayi hasken sa ya kara fitowa yana aje wani irin ƙasumba da suka rasa fahimtar wannan sauyi Na mene haka ? Sai a ranan ta goma sha uku ne Alhaji Aminu jibo yasa mu Yayyun sa da ƙannin nasa iyaye duka da maganan neman Aure Maleek,wanda jin inda zasu tafi nemo auren yasa nan take suka fara gutsiri tsoma , a cewar su ga ya'yan su nan ya rasa inda zai Auro yarinya sai a kauye , kauyen ma ta fulani........? ganin shaiɗan na kokarin sawo kai a bisa Al'amuran yasa Hajiya kaka cewa Allah ya zaba mana mafi alheri Allah yasa Abokiyar arziki ne kowa ya watse . Da wannan yasa ka kowa hakura duk da wasun su da yawa ba haka suka so ba . Musamman mahaifin Nihla wanda yake ganin Sam auren Maleek da Hasile ba zai yi karko ba don basu dace ba ,sai kace wanda aka gama dashi? Ko aka masa sihiri ace Maleek ne zai Auri yar jeji yar ƙauye? Da haka A washe gari iyayen Maleek suka koma rugar Hasile,wanda abun ya firgita Nihila da duk wani magoyin bayan ta , daga tambayar Aure basu dawo ba sai da daddadan labarin auren daka daura shi cikin aminci .
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'una.
Kalmar da Nihila tayi kenan tana fitowa daga saman gadon. Mommm.....momy me kike fadi? Aure Maleek yayi Aure fa kika ce ?. Kallon ta Hajiya Suwaiba tayi kana tace " Kwarai yayi aure an daura masa Aure yau ,kuma sannan yanzu haka suna hanya da dangin Amarya duk da ba yawa ne dasu ba , kasantuwar ba iyayen Amaryar sun shirya ba n........Ya isa don Allah momy? Ya isa ,Nihila ta katse ta cikin nuna zafi da takaici . Yanzu kin zo ne ki faɗa mun rai na ya ɓaci ko kuwa mene? Kin zo ne ki sanar mun duk soyayyar dana dade ina yi ma Maleek ya tashi a banza ,yo har da kike cewa basu shirya Auren ba ,idan za'a sanya masu lokacin auren koda shaikaru dari ne ai basa da Arzikin da zasu iya shigo da ɗiyar su cikin zuri'ar mu . Don ........ Nihila zaki mun shiru ko sai na buge bakin ki? Bude idanun ki dakyau kisan da Wanda kike magana , Suwaiba ce a gaban ki ba wata ba . Ban san Shashancin Banza da wofi . A lokacin da kin kama kan ki da maleek ya isa yaki Auren ki , ko da namiji baya yaji ,duk iskan sa shi burin shi ya samu ta ƙwarai baya taɓa son yar iska irin sa .
Momy Ni kenan bata gari bace? .
Bakya kaɗai ba ai duka cikin gidan nan ban ga Ɗa na gari ba , sai dai Allah ya shirya ku tun da ɗaya ya fara shiriya,fatan mu shine kuma Allah ya baku maza na gari . Sannan abun da ya kawo Ni shine ki kimtsa nan da Mintuna arba'in moton amare zai sauka a gidan Maleek na Zarafa street. Ki yi sauri ku shirya don taryar Amarya tare da masu Alheri sai a koma dasu . Wani irin duba Nihla tayi ma Hajiya Suwaiba kamin ta koma tana zama bisa gadon ta tare da caɓe baki tana furta " Allah ya kyauta .!
Nidai Nihla naje gidan Maleek ai har duniya ta ƙare babu abin da zai kaini tayi maganan tana juya mawa Mom Suwaiba baya . Mtswwwww ....dogon tsaki Momy taja kana tace " Allah ya kyauta kya kuma ji dashi . Tana furta haka ta juya tana barin mata wurin.
Tom komai sai dai muce Alhamdulillah, Daya daga cikin tanfatsetsen gidan sa na Zarafa street sabon layi ne na matasa masu fama da Tashen kudi ,duk wani matashin da ya isa anan yake gidan sa da iyalan sa , duka yaran matasa ne a wannan layi. Sosai su Yadikko suka ga tago mashi na arziki . A haka suka ƙara masu addu'ar zama lafiya tare da kauda duk wani masifa da zata Kunno Allah Ubangiji ya kawar. Ɓangaren Hasile kuwa al'amarin ganin sa take tamkar a mafarki . Sam ta rasa gane yo itace wai matsayin matan Aure bayan tasan artabon da ake sha da iskar jikin ta akan lamarin Auren ,amma a yanzu anyi komai sun rabu da ita tare da mata sallama . Sosai take son ta tuno al'amarin da suka faru a baya da yanda ta shigo Rayuwar Maleek da kuma yanda Billy ta dauke ta amma abubuwan da yake ba'a kan ta suke ba ta gaza tuna komai . Shi kan sa wannan auren gani take kaman irin auren su na Fulani aka yi mata don fuskar mijin nata ta bata sani ba ,a Wancen karon Iskar Hasile suke mu'amala da ita ba itace ta asalin ba..........tirƙashi !
Sanye take cikin shigar ta ta Fulani kaman yanda su yagwalgwal suka yi mata ado irin nasu ta amaren Fulani. Sosai tayi kyau sai ƙamshin nono take yi ,gashinn nan har kusan Duwawu. Bin Bedroom din take da kallo kana ta kura ma Agogon bangon ido wanda bata san ma karfe nawa ne ba yanzu. Niko bin lokacin nayi da kallo wanda yake alamta mun karfe 8:50pm na dare.
Wasu irin motoci ne suka fara shigowa farfajiyar gidan , wanda sun fi guda goma sha duka angwaye ne ciki , harda su Taufiq yayyu gyefe kuma babban Abokin ango Rayyan . A lamarin dai ba Ruslaan don kunya ma da bakin ciki tuni kwana ki bakwai kenan da barin sa gida Nigeria ya koma ƙasar japan da zama na dan wani lokaci. Sam Maleek bai sanar da kowa abun da Ruslaan yayi mashi ba ,sai dai sunyi mamaki rashin ganin shi a wannan biki na abokin shi amini ace muna babu shi tabbas da mamaki . Dukan su ƙamshin su ya gama cika gidan ,yayin da sauri mai gadi ya kai jiki zai rufe gare ne , Taufiq ya dakatar da shi a cewan sa ba jimawa zasu yi ba a ciki ,ango sukayo rakiya ...........!
[11/30, 7:40 PM] 🙂🙂🙂🙂: Mr.romantic
#Mamanteddy
Mugu mara imani kome nayi maka sai ka rama da hannun ka ne ba ka bari ana azabtar dani ba , yo ko menene nayi maka Rayyan ban kai matsayin da zaka yafe mun ba a rayuwa ? Rayyan na cuce ka na kuma azabtar da kai amma ina rokon ka da Allah ka yafe mun ,ko baka dawo dani cikin rayuwar ka ba ina rokon afuwan ka da yafiyar ka hakan kaɗai zai wanke zuciya ta daga cikin bakin cikin da take ciki kullum . "bude baki Sakatariyar ta yi tana kallon Yanda ta dage ta falla masa Mari shi kam tamkar ba hannun ta ta sa tayi marin ba ko kwakƙƙwaran motsi baiyi ba bare ya tanka ta ko yayi yunkurin daukar wani matakin. Yallaɓai kika mara? Ke Wacece ke??. Yau ba zaki bar companin ba sai mun saka security sunyi Miki dukan Tsiya sannan , ai ban san mahaukaciya bace ke sai yanzu . Tayi maganan tana nufo inda Sakina ke tsaye. Wani irin kallon ta Sakina tayi kana takai hannun ta tana kama Hannun Rayyan tare da cewa " Wallahi Ni kika yi mun akan shi zan sauke. Shine dai dai Ni ba kya ba . Jin wannan furucin nata yasa Rayyan kallon ta cikin sauri yana mamakin wai dama har yanzu Sakina bata yi hankali ba . Wannan wata irin yarinya ce , wato Nine Marainin wayon ta .
Hannu sakatariyar ta ɗaga tana kokarin janyo Sakina tare da cewa " Tabbas ya tabba mahaukaciya ce banza yar talaka . Keeeeee! Fita Hauwa! Maza fice ki bani wuri . Muryar Rayyan ya katse ta Wanda bata yi zaton jin haka daga gare sa ba . Cike da mamaki ta bude baki tana furta "Sir? " Yes I said you Go! . Wacece wannan? Da wannan tunanin ta juya tana barin Office din . Jan numfashi sakina tayi tana zubewa a wurin , tare da fashewa da wani irin marayan kuka ta nadama da tarin takaici da bakin ciki . Shiru yayi mata bai ce komai ba , haka bai rarrashe ta wai don tayi masa shirun ba .duk da yana jin ciwon kukan nata ,amma kuma idan ya tuno da barin sa da tayi a lokacin da yake tsaka da buƙatar ta sai nan take zuciyar sa tace masa ka barta ka barta bari na har abada. Ka gummaci rayuwar ta ƙare a haka har mutuwa . Rayyan! Muryar ta ya katse ta wanda a yanzu yake a ɗashe . Rayyan! Rayyan ka tsane Ni Ko? Rayyan baka son ganina a Rayuwar ka haka ne ? Tabbas nasan ganina yafi maka ganin bakar kaddarar ka dole wannan haka yake......wani kuka ne ya ciyota wannan yasa maganan nata daukewa . Tana cigaba da kukan ta .
Wani irin hajijiya yake ji na dibar sa ,idanun sa sun kada . A hankali ya fara kiran sunan Allah daga cikin Zuciyar sa koya samu sassauci . Wannan yasa masa dan natsuwa . Hannun sa yakai yana jawo flask din dake gaban sa na coffee a wani mug ya fara tsiyaya Cofee din kana ya mike a hankali yana takawa zuwa inda take. Miƙa mata yayi yana furta " amsa ki sha yanzu". tsayawa tayi tana bin sa da Wani irin kallo , a hankali take fara tuno da zaman su ta baya . Wasu irin Zafafan marayun Hawaye na biyo Kuncin ta . Tabbas yunwa ne a cikin ta don ko ƙaryawa ba tayi ba ,rabon su da daura sanwa yau kwana biyu kenan a cikin gidan .
Sakina! Amsa mana".
A hankali tasa hannun ta tana amsa har kuma a lokacin hawayen bai daina bin kuncinta ba . Kafa kai tayi lokaci daya ta kyankyame saboda bakar yunwar da take ji. Mikewa yayi yana kara hada mata wani yana dawowa dai dai tana sauke cup din sai ya amsa yana ƙara mika mata wani . Amsa ki ƙara.! Bakin ta ne ya hau Rawa tana kokarin masa magana amma sai yayi saurin katse ta ta hanyar daura mata yatsar sa a bisa laɓɓan sa tare da cewa " Shiiiiiii......". Gama sha sai muyi Magana .
**
Tun da suka fara ɗaukar Hanyar Rugar