Showing 6001 words to 9000 words out of 94091 words

Chapter 3 - Saran Boye Hausa Novel Complete

13 Dec 2024

244

amma Adawiya tazo ta tsare ko ina.

           Ɗakinsu dake a sashen su Nu'aymah suka nufa, inda ƙawayensu suke. Wasu sunyi barci, wasu ko na hira a waya da samarinsu, wasu kuma cheating, ƙalilanne ke hira a tsakaninsu.
        Yusrah data fito daga bayi tace,  “Aymah wai ina kika shiga Hajjo nata nemanki? Sai masifa takeyi tun ɗazun, dan tazo ɗakin nan yafi sau goma”.
            “Yah ilahi, dan ALLAH da gaske Yusrah?”. “Wlhy karkiji wasa, tambayi su Nanah ma kiji, har Addah ma sai da tazo nemanki. Ina kikaje to ke?”.
            “Muna tare da Yah Ab ne fa da Adawiya”.
   “Ohhh! Kice soyayya ce ta lula dake sama. Aiko daga ke har Yah Ab ɗin kunga banu da jaraban Hajjo da safe idan ALLAH ya kaimu, ga ruwan turare can Addah tace idan kin dawo ki shiga ciki”.
         A sanyaye ta amsa da “to”, sauran kuma suka sanya mata dariyar tsokana.
      Bata kulasuba ta nufi toilet ɗin, Adawiya kuma taja tsaki ta fice daga ɗakin batare dasu sunma lura da itaba.

_______________________
ZAFAFA BIYAR 2021
__________________________

         Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

Muna godiya da zaɓin zafafa biyar😍😘👌🏼🤗

________________________________

         Har Nu'aymah ta cire kaya zata shiga bahon da Addah ke haɗa mata ruwan turare saita tuna da tabar wayarta a sashen Abbah, gashi Yah Ab yace mata zasuyi magana ta Cat. Towel ɗin wankanta babba ta cira daga ƴar durowar da suke sakawa, ta ɗaura sannan ta fito ɗakin ta ɗauki babban hijjabi dogo ta zumbula. Batace ma kowa komaiba ta fice daga ɗakin zuwa sashen Abbah.
       Sai da tai sallama a ƙofar ɗakin aka bata iznin shiga sannan ta shiga, Abbah ta iske shi da Abban Abuja suna shan shayi, ta gaida Abban Abuja kanta a ƙasa dan haka kawai yau kunyarsa takeji fiye da kullum shi Da Mamah. Shikam fuskarsa ɗauke da murmushi yake kallonta, “Mamana ai tun ɗazun nake baza idon ta ina zan ganki amma kin ɓoyemin gaba ɗaya”..
        “Lah Abba ba ɓoyewa nayiba, ALLAH bammasan ka iso ba”. Ƴar dariya yayi irin ta kamilan mutane, yace, “To shikenan na amince mamana, kina lafiya ko?”. “Eh Abba lafiya lau”. “To Alhmdllh Mamanmu”.
      Juyawa tai batare da tayi zancen wayarba, dan da anan ta barta tasan Abbah zaiyi magana. Tunanin zuwa inda suka zauna da Yah Ab tayi danta duba ko acan ta yadda bata saniba.
         Gidan yayi shiru, dan mafi yawan mutane ƴan biki sunyi barci kasancewar har 12 ta gota, sai ɗai-ɗaiku marasa barcin wuri. Duddubawa ta farayi kasancewar akwai wutar Gen da aka tada, kamar wasa saita jiyo ring ɗin wayar acan gaba da inda take. Cikin mamaki da kila wakala ta nufi inda takejin, sai dai a ranta tana son ƙin gaskata wayartace, tafi tunanin wanine mai irinsa dai.
     Tana tafiya Ring ɗin wayar na sake gaba, da kuma ya yanke zataji an sake kira, saita fara tunanin ko Yah Ab ne keta jera mata kiran? Ƙila ya hau online bai gantaba. To amma miyasa kamar ana tafiya da wayarne?. Babu mai bata amasa, ƙuruciyarta baisa ta fahimtar da ita akwai matsalaba kuma ta cigaba da bin sautin ring ɗin wayar har ta iso ƙaramar ƙofar da akai daga cikin gidan ta ɓulla massallacin ƙofar gidansu, inda su Abbah kebi da asuba yin sallar asuba dasu ma kansu idan suna buƙata ko zasu shiga islamiyya.
       Anan ne ta tsaya cak tana waige-waige. Sai kawai taji an jeho mata abu akan fuska. Saurin saka hannu tayi ta janye guntun handkerchief ɗin da aka jeho mata fari tas. Kafin ta samu damar yin wani tunani akan hakan ko neman taimako taji duk jikinta ya saki idanunta na wani lumshewa kamar wadda hankalinta ke neman gushewa daga gareta.
      Daga haka bata sake sanin mike faruwaba kuma...............✍

Tashin hankali, to wanene kuma ya da wannan aiki😲🤦🏻🚶🏻?.

Amsarku na a Littafin SARAN ƁOYE dake cikin rukunin littatafai biyar na ZAFAFA 2021 da a yanzu haka sun fara zuwa muku da ɗumi-ɗuminsu, karku bari a baku labari guys, wannan tafiyar tanada banbanci sosai dana baya ina ƙara tabbatar muku😉👌🏼😀😍😍😘💃🏻😋.

           ZAFAFA BIYAR 2021

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
  
          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_*



*_SARAN ƁOYE!!_*


*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


Free page😋.



No. 3

...............Sama-sama takejin motsin mutane na matsota, sai dai bata fahimtar maganar da sukeyi balle ta ɗauki muryar kowa. Ta dafe kanta dake tsananin juya mata tare da jingina jikinta da bangon daya raba gidan nasu da massallaci. A hakanma dai bata tsiraba, garin cigaba da mata hajijiya yakeyi. Tai ƙasa zata zame ta faɗi aka riƙota. Ƙoƙarin buɗe ido take taga wanene? amma ta kasa saboda nauyin da sukai mata, haka ta sake jiki ga koma wanene ya riƙeta sosai, kafin ya fara janta suna takawa a tare batare da tasan ina suka dosa ba.
          Tabbas taji an sakata a mota an kwantar, amma daga haka bata sake sanin komai dake faruwaba a duniyar, dan barci mai nauyin gaske yayi awan gaba da ita.......

★★

            A ɓangaren Abdallah kam yata jiran Nu'aymah ta buɗe data amma sai yaji shiru, sai kusan 12 yaga tazo online ɗin, yay mata magana sai dai ta buɗe saƙon amma bata amsashi ba. Hakan yaso sosa ransa, amma kuma daya tuna ƙuruciya na bala'in ɗawainiya da Nu'aymah sai ya watsar da abin yay kwanciyarsa, a cewarsa ai daga dai gone idan ALLAH ya kaimu duk wani zagaye-zagaye ya ƙare kuma, tunda ta zama tasa. Da wannan tunanin yay barcinsa batare da ya sake bi takan wayarba ma.

______________________________
  
           A firgice ta farka jikinta jiƙe sharkaf da gumi. Baba malam dake saman abin salla ya kalleta da mamaki, sai kuma ya ajiye Al-Qur'anin hannunsa ya miƙe zuwa gareta. Zama yay kusa da ita ya rungumeta dan ya kula sam bata cikin hayyacinta, da alama kuma wani mafarkin tayi mara daɗi. Sai da sukaja kusan mintuna huɗu a haka ya tabbatar numfashinta ya dawo dai-dai sannan ya ɗagota ya bata ruwa ta sha. Sai da tasha kamar rabi ta miƙa masa sauran tana sauke ajiyar zuciya. “Jannat! lafiya kuwa?”. Ya faɗa yana share mata gumin goshinta.
        Umm taɗan dafe kanta tana kallon mijin nata, “Abban Nu'aymah mafarki nayi wlhy, kuma akan Nu'aymah ne. Inaga bara naje na dubata a ɗakinsu” tai maganar tana ƙoƙarin sauka ƙasa.
     Saurin riƙota yay da faɗin, “Ah ah Jannat”. Kallonsa tai tamkar zata fasa kuka, muryarta a sanyaye tace, “Inaji a jikina Nu'aymah tana cikin damuwa  Abbansu”. Murmushi yayi daɗan girgiza kansa. ya kamata ya maida ya kwantar tare da duƙawa ya sumbaci goshinta. “Nasan maganganunta na ɗazun da kika saka a ranki yasa kikejin kamar bata da lafiya, ki kwantar da hankalinki Jannat, ƙuruciyace kawai ke ɗawainiya da Nu'aymah, idan bamu ƙarfafata ba karmu yarda taga gazawarmu muma, kiyi haƙuri kimata addu'a kinji”.
      Kanta ta ɗaga masa tana haɗiye kukan da ya cika mata idanu, sai kuma tai ɗan murmushi domin ƙoƙarin danne abinda ke azalzalar ranta har yanzun. Kanta ya cigaba da shafawa a hankali da tofa mata addu'a har barci ya sake kwasheta. Ya sauke numfashi a hankali da sake sumbatar goshinta sannan ya miƙe ya koma inda yake da.

    ______________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
  
                 Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

____________________________

      WASHE GARI

   Tun kiran sallar farko wasu daga jama'ar gidan da makusantansu suka tashi aka fara ƙaƙainiyar ɗaura abinci. Hajjo data kwana da haushin Nu'aymah da batazo kirantaba ta nufi sashensu Nu'aymahn tana faɗa akan yau sai taci ƙaniyarta duk da ranar aurenta ce.
         Masu kai kawon fita can waje inda aka ɗaura girki sunata gaisheta, amma amsawa take sama-sam dan a ƙule take, tana nufar ɗakinsu Nu'aymah. Babu wanda ya tashi a cikinsu, dan mafi yawansu basuyi barici da wuriba, Hajjo ta kunna fitilar ɗakin tana kiran sunan Nu'aymah. “K Zainabu! Zainabu kina inane wai?”.
        Amal ce ta fara farkawa saboda bata da nauyin barci sam, ta tashi zaune da ƙyar tana murje idanunta da faɗin, “Kai Hajjo! Kinzo mu kin tadamu da kwakwazonki wlhy”. “Ubanki Lurwanu ne ke kwakazo, mara kunyar banza”. Tura baki Amal tai tana komawa ta kwanta dan taji haushi Hajjo ta faɗi sunan Abbansu.
       “K ni tashi dan gidanku ki faɗamin ina Zainabu take?”.
      “Ba tana sashenki ba” Amal ta faɗa tana juya ma Hajjo Baya. “K Safiya banson lalata, dan gidanku tana sashena zanzo nan nemanta ne?”.
        “ALLAH Hajjo tana sashenki, bayan ta dawo muka faɗa mata kina nemanta shine ta tafi can”. Nanah data tashi yanzu itama ta faɗa cikin muryar barci.
      Hajjo tace, “To sai dai idan tana ɗakin uwarta ko kuma wajen Fauza. Dan nidai ban gantaba, Adawiya ce kawai ta kwana a ɗakina”. Nanah tace, “To sai dai idan tana sashen Addah, dan ɗakin Umm su Mom ne suka kwana, nasan kuma Nu'aymah bazataje cikinsu ta kwanta ba Hajjo”.
       “To bara na dubata wajen Fauzan, kuma saiku tashi kuyi salla tunda lokaci yayi”. “To” kawai Nanah tace. Amal kuwa bata sake maganaba har Hajjo ta fita.

       Hajjo na fita Umm na shigowa, tadasu ta shiga yi dan su Nanah ma komawa sukai suka kwanta ganin Hajjo ta fita. Sai raba idanu Umm keyi a tsakaninsu nason ganin Nu'aymah, sai dai sam babu ita a cikinsu. Kafin ta samu damar tambaya Hajjo ta sake shigowa Addah biye da ita a baya.
       Cikin girmamawa Umm ta rissina tana gaida Hajjo. A taƙaice ta amsa mata da tambayarta ko Nu'aymah a ɗakinta ta kwana ne?. Gaban Umm yay masifar faɗuwa, ta girgiza kanta da haɗiye yawu da ƙyar. “A'a Hajjo ba can ta kwanaba”.
       “Yau mun shiga uku”. Cewar Addah tana ida shigowa ɗakin sosai. “Ku batare kuka kwana da Nu'aymahr ba ne wai?”.
        Yusrah tace, “A'a Addah, batare muka kwana da itaba, bayan kin haɗa mata ruwan turare kin fita suka shigo ita da Adawiya, to na faɗa mata dai ga ruwa can kin haɗa mata ta shiga ta amsa da to. Sai dai tana shiga bata jimaba ta fito ta fice daga nan, ni dai har barci ya ɗaukeni bata dawo ba, kuma kusan nice ƙarshen barci”.
         Tashin hankaline ƙarara ya bayyana a fuskar Umm dasu Addah, basu tsaya jan zancenba suka fito daga ɗakin domin neman Nu'aymah a sauran sassan gidan ko taje wani ɓangaren ta kwana.

          Ɓangaren Momy mahaifiyar Abdallah suka fara shiga tace rabonta da Nu'aymah tun a wajen Walima, amma bara a duba kotazo ta shiga ɗakin su Amal bata saniba. Sun duba ɗakinsu Amal babu kowa sai ƙannen Amal ɗin biyu dake barci. Sauran ɗakunan kuma duk akwai baƙi da wahala ace ta shiga can, amma duk da haka sai da suka shishshiga suma. Amma babu ko mai alamarta.
     Sun koma sashen Abba Musbahu nanma dai matarsa Ammi da Ummah sunce basuga Nu'aymah ba, an kuma shiga ɗakin su Yusrah da ƴammatan sashen yayun su Nu'aymahr nanma babu ita, sai su kaɗaine da sauran ƴammata sa'anninsu na gidan da baƙi. Sake dawowa sukai Sashen Addah aka duba ko ina nanma dai babu ita, suka koma sashen Hajjo nanma haka. Zuwa yanzu kam hankalin kowa ya fara tashi, dan ko sallar Asuba wasu sun kasa samun nutsuwar yinta.
      Duk da ba'a tunaninta a sashen samarin gidan haka dai aka shiga canma ko za'a dace. amma kuma bata nan. Yanzu kam dai kowa ya tabbatar Nu'aymah bata gidan, samarin gidan dasu Baba malam duk sun dawo massallaci suma an haɗu anata taraddadi, sai sake tambayar su Yusrah da akasan suna tare akeyi da Adawiya data dage take rusar kuka tamkar ranta zai fita.
       Gari ya waye tangaran, waɗanda basuyi sallaba suka samu sukaje suka yiyyyi batare da hankalinsu na tare da suba. Umm kam tama kasa magana sai ajiyar zuciya da taje faman sauke a jajjere. Shi kansa Baba Malam binsu kawai yake da kallo. Hajjo tuni ta fara kuka itakam. Ango Abdallah kam nasa tashin hankalin ai ba'ama magana, danshi ya dage sai sake bin ɗakunan gidan yake lungu da saƙo yana dubawa.

       Kamar wasa saiga ƙarfe 11am ta buga babu Nu'aymah babu mai kama da ita, saima cin karo da akayi da takarda a jikin Windown ɗakinsu an ajiye. Sai kayanta ƙwara huɗu da alamu suka nuna jehosu akayi ta Windown maybe.
        Nanah ce taga takardan, dan haka ta nufi inda su Baba malam ke tsaye da sauran ƴan uwansa ta miƙa musu da faɗa musu inda ta gani. Abban Adawiya ne ya amsa takardan daga hannun Nanah, ya buɗe yana gyara tsayuwarsa. Duk idanu su Baba malam suka zuba masa da ƙaguwar sonjin minene a ciki.

        Assalamu alaikum iyayena.

                 Kuyi haƙuri da abinda zaku wayi gari da shi daga taskar kuskurena, wlhy yanzu bana son Yah Abdallah akwai wanda zuciyata keso. Nasan babu wanda zan faɗamawa a cikinku ya fahimceni balle akai ga yarda, amma wlhy ina masifar son Ameer fiye da yanda kuke zato da tsammani. Banason na wahalar daku wajen ɗauramin aure da Yah Abdallah nazo kuma na zama sanadin ɓata zuminci da aka gina tunkan samuwarmu daga baya, shiyyasa na zaɓi bin Ameer mu gudu, shi kuma ku aura masa wata a cikin ƴan uwana. Na muku alƙawarin idan komai ya lafa zan dawo gareku ku ɗaura mani aure da masoyina Ameer. Ina fatan bazakuyi fushi dani ba dan ALLAH 🙏🏻😭.
           Na barku lafiya.
Daga ɗiyarku Zainab Sooraj Hashim (Nu'aymah).

______________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
  
                 Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

____________________________

        Tsit wajen yayi babu wanda ya iya ko ƙwaƙwaran motsi, Baba malam sai faman kaɗa kai yake kawai zuciyarsa na kaikawo.
      Hajjo ce ta ƙaraso wajen ganinsu cirko-cirko. “Lafiya? Na ganku cirko-cirko? Ko anji labarin inda take ne?”.
       Duk kasa bata amsa sukayi, hakan yasa ranta ɓaci ta daka musu tsawa. “Wai kuna cikin hankalinku kuwa? Ina magana kunmin shiru kai ɗan Malam” ta ƙare maganar idonta akan Baba Malam (Abban Nu'aymah) dan bata faɗar sunansa saboda shine na fari, sai dai tace ɗan Malam.
       “Kiyi haƙuri Innah, da kanta ta gudu”. “Ban gane da kanta ta gudu ba? Kana haukane?”. Kasa amsa mata yayi, dan shi kaɗai yasan kalar tashin hankalin da yake ciki a halin yanzun.
      Abba Musbahu ne yace, “Innah inaga muje ciki, wannan ba maganar nan baceba”.  Zata sake magana ya kama hannunta suka nufi sashenta tacan baya inda falon mahaifinsu yake. Bin bayansu su Abban Abdallah sukayi, Baba Malam dai bai iya motsawa ba har tsahon wasu mintuna kafin ya bisu.

           Bayan haɗuwar duk wanda ya kamata a falon, Abba Musbahu ya sake maimaita abinda ke a rubuce a takarda, wadda Nu'aymah ta ajiye kamar yanda kowa yaji.
        “Kai wannan zancen ban yarda da shiba, ina Zainabu taga wayon wani yin wannan iya shegen? Wanene ma Amiru yake ko uwarwa? Tunda muke a gidan nan waya taɓa ganin Zainabu da saurayi ma?”. Hajjo tai magana ranta a ɓace.
      Shiru falon yayi, dan kowa yasan maganar Hajjo gaskiyace, babu wanda zaice ya taɓa ganin Nu'aymah da saurayi bayan Abdallah, dan Nu'aymah yarinyace mai shegen tsiwa da rashin tsoro, ko cewa akai ana sonta kai tsaye take faɗin an mata miji a gidansu. Bama ta yarda saurayi yay zuwa biyu wajenta........
      “Ina magana kowa yayi shiru, wlhy ni dai ban yardaba, sai dai idan wani munafukine ya sacemin jikata”. Hajjo ta faɗa tana fashewa da kuka.
       Baba Malam ne ya kalli Hajjon zuciyarsa na masa zogi, yace, “Innah karki saurin kareta, kinsanfa yaran yanzun ka haifesune amma baka haifi halinsu ba, mudai fara bincikar ƴan uwanta ƙila wani acikinsu yasan Ameer ɗin”.
       Girgiza kai Abdallah yayi shima cike da damuwa, “Baba ALLAH

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login