Showing 3001 words to 6000 words out of 94091 words

Chapter 2 - Saran Boye Hausa Novel Complete

13 Dec 2024

243

yaraf, taɗanja jikinta baya tana jan tsaki zata raɓata ta wuce. Saurin tashi Adawiya tai zaune ta riƙo hannunta. “Wlhy Addah inhar baku aura masa ni

ba saina kasheta!!”.
Baya Addah tai da sauri zata faɗi ƙasa tana mai waro idanu waje sosai akan Adawiya, bakinta na ɓari tace, “Ki kasheta Adawiya?!”.
“Da hannun nan nawa kuwa”. Adawiya ta faɗa tana zazzaro idanu waje itama da ɗaga hannunta tana nunama Addah............✍


Hummmmm!!!! Turƙashi. Masu karatu wannanfa shine ana dara sai ga dare yayi😲. Mi kuke tunani akan wannan labari? Wacece Adawiya? Sannan wacece Nu'aymah? Wanene Kuma Abdallah?. yaya zata kasance? Minene zai faru kuma? Wace amsa Addah zata bama Adawiya?......
Amsar waɗanan tambayoyin duk suna a Littafin SARAN ƁOYE!! da ke cikin tawagar littatafai biyar na zafafa 2021 dake shirin zuwa muku insha ALLAHU nan bada jimawa ba😉😋.

Wlhy karku bari ayi babuku, dan ZAFAFA BIYAR 2021 fa da zafinsu suke tafe, na tabbatar muku tafiyar wannan shekarar ta dabance MASOYAN AMANA😋🤗🤗😀😀.


ZAFAFA BIYAR 2021


Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

09033181070



💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍



ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.*_Typing📲_*



*_SARAN ƁOYE!!_*


*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*


Free page😋


No. 2

.................Tsaki Addah taja tana ballama Adawiya harara, ta tsallaketa ta wuce tana faɗin, “Sai kije ki kashetan shashasha kawai mara tunani”.
         Kuka sosai Adawiya ta sake fashewa da shi. Ta rarrafa har inda Addah take shirin kabbara salla ta riƙe mata ƙafafu. Cikin fushi Addah ta ƙwace ƙafafunta tana nuna Adawiya, “Wlhy idan baki shiga hankalinkiba Adawiya zan bala'in saɓa miki, wai wane irin iskancine wannan? Ki shiga hankalinkifa tunkan nai miki abinda zakiyi dana sani a taron bikin nan. Dalla tashi ki ficemin anan, ba kashe Nu'aymah ba ki babbakama gidan wutama mu ƙone ƙarewar hauka. Wawuya kawai!!”.
          Yanda Adawiya taga ran Addah ya ɓaci tasan zata iya cin ubanta kamar yanda ta faɗa, tana ganin ta kabbara salla saita tashi ta fita tana kukanta. Addah mace ce mai yawan wasa da fara'a, idan har kaga fushinta to lallai an kaita maƙura, shiyyasa idan tai fushin dolene kaji shakkarta. Su kansu ƴaƴanta tana rayuwa da sune tamkar ƙawayenta, hakama sauran yaran gidan. Wannan halayar tata tajan yaran a jiki yasa kowane yaro yazama ɗan ɗakin Addah a gidan, suna sonta sosai, hakama iyayensu sunajin daɗin yanda take son ƴaƴansu da basu lokacinta.
         
         Can bayan ɗakunan sashen samarin gidan Adawiya ta nufa, dan tasan canne kawai babu mutane. Waje ta samu ta zauna tasha kukanta, yayinda zuciyarta ke shirya mata mugayen abubuwa game da Nu'aymah da matakin da zata ɗauka a kanta na dakatar da wannan auren, tayi alƙawarin kota halin ƙaƙa saita mallaki Abdallah a safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu. Sai kuma ta rabashi da Nu'aymah, idan kuma har hakan bata tabbata ba to sai dai suyi zaman kishi ita da Nu'aymah kokuma kowa ya rasa. Dan ko sama da ƙasa zata haɗe bazata barma Nu'aymah Abdallah ba wlhy........
        “Adawiya! Adawiya!!”. ta jiyo ana ƙwala mata kira. Tsaki taja mai ƙarfi kafin ta miƙe tana kakkaɓe jikinta daya ɗan ɓaci da ƙasa, duk da ma ita ko shiryawa batayiba. Fitowa tai inda zata iya ganin mai kiran nata. Da sauri taja baya saboda karo da suka kusa ci da Yah Abdallah. Ƙirjinta yay wani mugun harbawa, a take ta fara neman nutsuwarta ta rasa. Kwarjininsa da matsanancin son da take masa suna neman birkitata gaba ɗaya ta kasa riƙe kanta....
         Sassanyan Murmushinsa ya sakar mata yana ɗan ware idanunsa a kanta, “Oh Hassanar amaryace haka bata ko shiryaba?”. Duk da maganarsa batai mata daɗiba saita saki masa murmushi, ta matsa kusa da shi tana shaƙar ƙamshin turarensa mai daɗi, “Yah Abdallah dama ka iso?”.
       “Ya za'ayi ki sani tunda ance kina nan kinata kukan rabuwa da Husainar ki”. Baki ta buɗe zatai magana sai kuma ta fasa tana kallon Amal data rako Yah Abdallahn. “Kiranmi kike ƙwalamin ke kuma?”. Baki Amal taɗan taɓe tana cigaba da latsa wayar hannunta, “Kiranmi zan miki ni kuwa, dama Yah Abdallah ne ke nemanki, shine akace anga kinyo tanan”.
      Kafin tace wani abu Yah Abdallah yace, “Nine na sakata, wani aiki zakimin, Amal jeki abinki”. Kai Amal ta jinjina masa, tai gaba abinta batare data sake kallon inda Adawiya take ba. Sai da tai nisa da su sannan Abdallah ya sake kallon Adawiya, ganin shi take kallo sai yay murmushi.
       “Yaya dai ƙawar amarya na canja miki ne?”. “Sosaima kuwa Yah Abdallah”. Adawiya ta faɗa cike da yanga tamkar ba itace ta gama darzar kukaba yanzun.
      Murmushi yayi yana ɗauke kansa da faɗin, “To na gode. Kinsan aikin da zakimin?”. Kai ta girgiza masa batare da tace komaiba. “Sonake kije wajen Walimarcan ki satomin amaryata nan inason ganinta”. Wani takaicine ya soki zuciyar Adawiya har fuskarta sai da ta nuna hakan. Da mamaki Abdallah yace, “Yaya dai?”. “Babu komai Yah Abdallah” ta bashi amsa da rawar murya.
          “Okay, to maza ki shirya saiki ɗakko min ita, karfa ki bari kowa ya ganki musamman ma Hajjo”. Kanta ta ɗaga masa kawai, dan tasan idan tai magana kukane zai ƙwace mata. Da kallo Abdallah ya bita harta ɓacema idanunsa, haka kawai tausayin yaran ya kamashi, kowa yasan irin shaƙuwar dake tsakanin Adawiya da Nu'aymah tun ƙuruciya, sun tasone tamkar tagwaye a gidan, komai tare ake musu shi, yanzu kam ace zasu rabu rana tsaka ai dolene kaji tausayinsu.

        Adawiya kam koda ta bar wajen sashen Hajjo kakarsu ta nufa, babu kowa duk ana wajen walima, dan ana idar da salla kowa ya koma, daga cikin gidanma kana jiyo lecture ɗin da aka fara. Kwanciyarta tayi dan ta rantse bazata kira Nu'aymah ba.

★★★

        Tun Abdallah na kallon hanya na jiran ɓullowar amaryarsa Nu'aymah da Adawiya harya koma duban agogo. Kamar wasa sai ga mintuna ashirin sun shuɗe babu Adawiya balle Nu'aymah, abinda zuciyarsa kawai ta basa Hajjo ta hana Adawiya ɗakko Nu'aymah ne, maybe kuma tanacan tana wayon yanda zasu baro wajen. Ɗan murmushi yayi yana lumshe ido, sosai yake cike da ɗoki da ƙaguwar son ganin Nu'aymahr sa, yanason yaga yanda ta sake komawa yanzun........
         Kiran da ake masa a wayane ya katse tunaninsa, ya zaro wayar daga aljihun gaban rigarsa ya duba. Zaid ne, kamar bazai ɗagaba sai kuma ya amsa tare da ɗorawa a kunnensa. “Hello Jibiya wai kana inane?”. Kamar bazaice komaiba sai kuma yay guntun tsaki da kallon agogon hannunsa. “Ina cikin gida mana, miya faru?”. “Cikin gida kuma? To mi kakeyi acan bayan kowa duk yana nan har amarya. Gashi nan Baba malam na nemanka to”. Baice masa komaiba ya yanke wayar. Badan yaso ba ya baro cikin gidan ya koma wajen walimar.
         Inda Nu'aymah ke zaune kusa kakarsu Hajjo ya kalla, tana zaune a yanda ya barta tun ɗazun, babu kuma alamar Adawiya a wajenma. Ɗan tsaki yayi a ransa ya ƙarasa inda Baba Malam yake.

             Masha ALLAH, anyi taron walima an tashi lafiya, inda malamai suka ragargaza lectures masu ratsa jiki ga ma'abocin saurare. Gaba ɗaya an gina sune akan zaman aure da kurakuran da muke tafkawa a cikinsa da hanyoyin magancesu, inda amarya da angonta sukasha addu'oin fatan alkairi da zaman lafiya.

______________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________

Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

____________________________

        Tunda aka tashi jikin Nu'aymah sai ya sake yin sanyi, maimakon ta nufi ɗakinsu da suke zaune da ƙawayenta sai ta nufi wajen Umm. Kanta tsaye ɗakin Umm ta wuce, sai dai bata ciki sai ƴan uwanta. Gaishesu tayi suna tsokanarta da amarya-amarya, ita dai kanta a ƙasa ta sulale ta fito. Sashen baba malan ta nufa, dan tasan Umm bazata wuce tana a canba ko wajen Addah.   
         Tun shigowarta corridor ɗin daya shiga tsakanin falon Baba malam dana Umm taga takalman Umm da Addah, ɗan murmushi tayi tana sake jinjina wannan irin ƙauna ta iyayensu, ƙofar falon ta ƙarasa tare dayin sallama, daga ciki suka amsa mata da bata iznin shiga.
       “Ah ah! amarya da kanta. Miya farune?”. Addah ta faɗa tana murmushi. Kallon Umm da batace komaiba Nu'aymah tayi, sai kuma ta duƙar da kanta hawaye na cika mata ido. Addah tace, “Kinga zonan”. Takawa tai a hankali zuwa garesu, ta zauna a ƙasa jikin ƙafafun Umm data cigaba da abinda takeyi tamkar batasan da shigowar Nu'aymah ba.
        “Ƴar albarka miya farune? Ko kewar Umm ne ya motsa?”. Maimakon Nu'aymah ta bama Addah amsar tambayarta sai hawaye suka gangaro mata a kumatu, ta kwantar da kanta bisa cinyar Umm tana jan ajiyar zuciya a jajjere.
      Dauriya kawai Umm keyi dama, taja ɓoyayyen ajiyar zuciya da girgiza kanta tana kallon Nu'aymahn. “Ke kuma wannan shashancin fa?......”
      “A'a babu wani shashanci Umm”. Addah ta faɗa tana kamo hannun Nu'aymah cikin nata. “Baby faɗamin miya faru? Ko har yanzu tsoron dai?”. Kai Nu'aymah ta ɗaga mata, sai kuma ta ɗago ta kalli Umm da itama kallonsu takeyi. “Umm dan ALLAH ni banason auren a fasa kawai”.
         “Afasa kuma Nu'aymah?! Miyasa?”.
       “Addah wlhy ni naji banaso yanzun kawai”.
        Sosai abin ya bama Addah dariya, ita kanta Umm sai da tai murmushi tana girgiza kai, dan babu komai a maganar Nu'aymah sai zallar ƙuruciya da sakarci. Umm ta janyeta a jikinta tana miƙewa da faɗin, “Wannan shashancin ba daniba, Addah bara nayi nan kinji”.
      Sauri riƙeta Nu'aymah tayi tare da sake cukuykuye ƙafafunta tana kukanta, “ALLAH Umm nidai banaso, gara na zauna a wajenku Please”.
       “Oh ALLAH, Nu'aymah banason sakarci kinji, sakarni naje nayi abinda zai amfaneni”.
          Kallon Umm Addah tayi, cikin magana da yaren ido taima Umm alamar ta lallasheta Please. Umm zatai magana Addah ta girgiza mata kai tana miƙewa ta fice ta barsu. Ajiyar zuciya Umm ta sake saukewa a sanyaye, kafin tai guntun murmushi da komawa ta zauna a inda ta tashi. Kama Nu'aymah tai ta tadata ta maidota kan kujerar kusa da ita ta zaunar. Hakan ya bama Nu'aymah damar faɗawa jikin Umm ta rungumeta.
         Karan farko Umm tai ƴar dariyar ƙarfin hali da rungume ɗiyar tata itama. “Ke wai bakisan kin girmaba Nu'aymah? Aurefa za'a ɗaura miki gobe idan ALLAH ya kaimu amma kike halin yara har yanzun?”.
        “Umm ni wlhy na fasa, zan zauna a wajenku nayi karatun kawai”. Dariya Umm ta sakeyi da ɗago fuskar Nu'aymah ta share mata hawayenta. “To naji ya isa haka nan kukan ko”. “To Umm za'a fasa ɗin?”. “Tambayi Abbanki ga shinan”. Umm ta faɗa tana kallon Abba daya shigo kusan mintina biyu kenan harya zauna kusa da Nu'aymahn bata saniba yana kallonsu kawai. Tashi Nu'aymah tayi daga jikin Umm takoma jikin Abbanta.
         “Maman nan nawa dai shagwaɓanta yayi yawa”. Ya faɗa fuskarsa ɗauke da murmushi yana shafa kanta. Ɗagota yayi ya zaunar sosai, tare da saka hannu ya share mata hawayenta gaba ɗaya. “Kinga faɗamin miya faru?”.
         “Abbah a fasa kawai”.
    Waro idanu ya ɗanyi cikin mamaki, “Mamana mi za'a fasa?”. “Abbah aur.....” sai kuma ta kasa ƙarasawa tai ƙasa da kanta.
          “Ina jinki faɗamin mana!”.
“A...Abbah auren, ni yanzu na fasa”.
           Kallon juna sukai shi da Umm dake kallon Nu'aymah cike da damuwa, Sosai ta basu tausayi da dariya, amma duk sai suka danne kayansu. Abbah ya riƙe hannayenta da sukasha ƙunshi cikin nasa, cikin muryar lallashi yace, “Mamana kin daina son yayan nakine?”. “A'a Abbah”. Ta faɗa kanta a ƙasa. “To miyasa kikeson a fasa?”. “Abbah banason rabuwa daku nidai”.
         Murmushi Abbah yayi tare da sauke ajiyar zuciya, “To ai ba rabuwa zakiyi damuba Nu'aymah, kuma shima Abdallah ai ɗan uwankine mai gatantaki ma fiye da kowa a gidan nan, duk kuma sanda kikeso ya kawoki wajenmu zai kawoki”. Idanunta cike da kwalla ta kalli Abbah, “To Abbah ina zai samu kuɗin jirgi yayta kawoni kullum tun daga Saudia?”. “To ai dama ba kullum ba Mamana, keda zakiyi karatu tayaya za'ace za'a kawoki gida kullum koda anan zaku zauna ma. Duk dai sanda kuka sami hutu sai ya kawoki, kuma muma zamu dinga zuwa ganinku ai ko”. Shiru tai batace komaiba, sai hawaye keta sake mata zarya.
       Cikin hikima da wayo Abbah da Umm sukaita mata nasiha da ƙara ƙarfafa mata gwiwa harta daina kuka ta koma dariya kamar ba ita ba, kusan awarta ɗaya da rabi a wajensu sannan ta tafi kiran da hajjo ta aiko Farida tai mata.

              Tafiya take tana ƙunƙunin haushin Hajjo, dan tasan kiran datai mata bai wuci sakata shiga cikin ruwan lalle ba, itako ta tsani abun dan ƙyanƙyami takeyi, amma jarabar kakar tasu bazai bari ta fito ta faɗa ba.
         Gabanta ne ya faɗi jin an kamo hannunta, ta juyo a firgice zata wage baki tai ihu aka rufe bakin.
      Cikin muryarsa mai sanyi da nutsuwa yace, “Matsoraciya nine. Na gaji da wasan ɓuyar da kikeyi dani malama”.
      Ajiyar zuciya Nu'aymah ta sauke jin Yah Abdallah ne, ya saketa yana cigaba da ƙawata fuskarsa da murmushi da ƙare mata kallo daga sama har ƙasa. “Saboda kinsan kin sake haɗuwa fiye da da shiyyasa kiketa faman ɓoyemin kanki ko?”.
       Hannu Nu'aymah tasa ta rufe fuskarta da shi tana murmushi, “Yah Ab banfa san kazo ba”.
        “Kutt!”. Ya faɗa yana zaro idanu waje, “Wato bama kisan nazoba?”. Kai ta jinjina masa da ƙyalƙyalewa da dariya.
          “Lallai yarinya na yarda kin girma kam, idan ba tsoroba buɗe fuskar ki faɗamin ido da ido mana”. “A'a ai basai na buɗeba tunda dai kaji na farko”. “Hahyh! Zaki min bayani gobe idan ALLAH ya kaimu ai”.
        Kasa cemasa komai tai a kan hakan, saima ta risina kawai ta gaidashi. Ya amsa mata cike da kulawa idanunsa na cigaba da yawo a jikinta, duk da akwai ƙaramin hijjabi tare da ita, rayawa kawai yake a ransa ‘anya baiyi gangancin ɗaukar alwashin rinon Nu'aymah ba kuwa? Kai da sakel wai anbama mai kaza kai’.......
          “Yah Ab bara naje hajjo ke kirana”.
     Maganarta ta dawo dashi hayyacinsa. Ajiyar zuciya ya sauke daɗan kallon gefensu, sai kuma ya kalleta sosai yana gyara tsaiwarsa. “Babie kinga manta da tsohuwar can kinji, musamu guri mu zauna muɗan zanta na yaushe gamo, ke koma ɗokin ganina baƙyayi bayan kuma shekara biyu kenan baki ko ganniba”.
          Murmushi tayi tana ɗan kallonsa ta gefen ido, a ranta godiya takema ALLAH daya mallaka mata Yah Ab matsayin masoyi, gobe idan ALLAH ya kaimu kuma iyanzu mijine. Ya haɗa abubuwa masu yawa na gwaranzan mazaje da kowacce mace zatai alfahari da samunsa, ita kanta tasan ta cika mai sa'a ta gaske, dan ba'a wajeba ko'a cikin yayyenta, ƴan uwanta tasan akwai masu tsananin sonsa, amma ya dage kai da fata sai ita, tun batasan kantaba, tun ana masa faɗan yay aure idan ta girma sai ya ƙara da ita har kowa ya zuba masa ido dan yaƙi amincewa, a cewarsa ita kaɗai ta ishesa rayuwa, dan haka zai jirata ko tsahon shekara nawane. Damuwa da rashin auren nasa ya saka iyayensu yanke hukuncin aura masa ita bayan sun kammala secondary wata uku kenan, acewarsu taje ta cigaba da karatun a ɗakinsa kawai..........
           “Ina kika tafi kika barni Noor?”. Ya faɗa yana kaɗa mata hannunsa saitin fuskarta. Ajiyar zuciya ta sauke da duƙar da kanta tana murmushi. “Muje” ya sake faɗa yana nuna mata hanya.
      Babu musu ta bisa zuwa can bayan sashen Hajjo, inda kuma ya kasance gaban sashen Abbansu Musbahu. Zama sukai a fararen kujeru dake a wajen, basufi mintuna uku da zamanba sai ga Adawiya. Sosai Nu'aymah taji daɗin zuwan ƴar uwar tata, dan dama a takure take da kasancewarsu su biyu kawai ita da Yah Abdallah. Shiko sam baiso hakanba, amma sai bai nunaba ya biye musu sukaita zuba masa shirmen surutunsu.
       Ganin hirar dai bazata yuwu shida Nu'aymah kawai ba sai ya miƙe bayan kamar mintuna 35 da zamansu, umarni ya basu suje su kwanta, shima zai koma wajen abokansa suna jiransa. Sam Adawiya bataso hakaba, dan wani irin farin ciki ta tsinta kanta a ciki na kasancewa da Yah Abdallah a ƙarƙashin inuwa ɗaya. Sai da yaga sunbar wajen sannan shima ya miƙe ransa duk babu daɗi, dan yaso su tattauna abubuwa masu muhimmanci shi da Nu'aymah

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login