Showing 27001 words to 30000 words out of 37455 words
mata amma ya hada dan mutane nagartacce, kamamme mai alkunya da wahala, don ya gan shi mai hakuri da biyayya. Ga wata irin nutsuwa da kamala a tare da shi irin wanda tsayar da addini da kula da sallah ke haifarwa namiji, wanda bata taba gani a matasa kamar sa ba.
Ta shiga hangowa kan ta irin asarar surukin kwarai da zata yi, idan shashashar diyar nan tata tayi masa rikon sakainar kashin da zai gaji ya yakice ta.
Sai ta yi maza ta mike tana tunanin abun yi na gaggawa, don kankarowa Amani mutunci ka idon Mukhtar kafin ya karasa zirarewa.
Mukhtar yayi sallama duk suka amsa banda Amani, wadda a lokacin ta kai fork da ta cokalo dankalin turawa a jikin sa bakin ta, tana wata tauna a yangace kamar bata so. Jalan ta nuna masa kujerar da zai zauna mai fuskantar ta Amani ya tsugunna har kasa ya gaishe ta, yana ta kokarin kin dagowa ta ga fuskar sa, amma a kulawa irin ta Jalan, sai da ta hango yanayin da yake boye mata din, kuma a matsayin ta na babba ai ta san dalilin sa.
Amma sai tace lafiya Mukhtar na gan ka haka babu walwala?
Mukhtar ya ki zama a kujerar don ba zai iya tana kujera shima yana kan kujera ba, sai ya ce mata Mamma zan koma Freetown gobe da sassafe, daga can zan tashi Nigeria in sha Allah.
Ta kusa ce masa Amani fa?
Don sai ta ji kamar bata kyauta ba in ta rike masa mata har tsayin watanni biyu nan gaba, bayan bashi da wata matar a can gida Katsinan. Kamar Mukhy ya san me Jalan take tunani sai yace,
ita Amina Alhaji ya ce ta zauna da ke na dan wani lokaci, ta saba da nan din Jalan ta soma lalubo idon sa da yake boyewa da nata wayayyun idon na iyaye, ta ce.
Are sure you are okay with her stay here? Cewa nake daurin aure kawai aka yi muku baku tare ba ko sau daya?
In don ta ni ce ba abunda zata yi min alhalin tana da miji a gefe, gara ta wuce ku koma tare, zai fi min kwanciyar hankali da kai kan ka.
Ai jin haka Amani ta soma buga kafa irin wanda takewa Alhaji, tana fadin ita ta zo kenan, ba inda zata sake zuwa. Alhaji ne yasa take zaune a Katsina kuma ita kam yanzu ta barwa Mukhy shi halak malak. Sai ji kike gwajab! Mamma Jalan ta gwabje bakin da ya sha lip gloss, tace,
Amina!
Ashe baki da daa baki da ta ido? A gaban kannen ki kikewa mijin ki wannan diban rashin albarka? Tashi ku je ki bashi hakuri, na ce ki bashi hakuri har sai ya huce, ku yi sallama cikakkiya, kada in ganki a cikin gidannan sai da safe!.
Tuni Mukhtar ya kai bakin kofa don in ya cigaba da zama a wajen nan Amani ta kara magana ta rashin amincewa da umarnin ta, ko ta kara furta wani abu akan hakan ya san Mamma Jalan zata kara kai duka, da alama mai saurin hannu ce.
Sosai dukan Jalan ya samu bakin Amani, tuni leben sama ya kumburo. Zata yi magana ta ji bakin ta ya mata nauyi, sai ta fara hawayen da baya yi mata wuya, a ranta ta ce shikenan itama uwa ta yayi sumumu-kasau dinsa na munafurci ya raba mu, Mamma kuma ta yi rantsuwa ta kara ta tashi ta tafi wajen mijin ta ko ta sassaba mata kamanni yanzun nan.
Ko me ta tuna? Ta ja hannun Amani zuwa dakin ta da zafin nama saboda idanun su Fajur da suka bubbude suna kallon su, suna shiga ta rufo kofar da mukulli, ta dube ta da tausayi, don ta ga tsanar Mukhtar tsantsa a cikin idon ta. Ita victim ce ta kiyayyar auren dole ta san me Amani ke ji. Ta ce.
Amina, bana so ki zamo daya daga cikin matan da aure da hakkin sa ke kai su wuta. Ba sai ya ce bai yafe miki ba Allah zai dubi hakkin sa a kan ki ya fidda masa, na san a shekarun ki kin san aure, kin san maanar sa, amma a dolancin ki kina sa kafa kina takewa.
Shin ya ta ko kin san irin kyautar darajar da Allah yayi miki kuwa da wannan salihin mijin da ya baki? Ina jiye miki ranar dana sani.... wadda aka ce ..... keya ce, tun da sauran mutuncin ki ki kankaro shi a idon Mukhtar, kafin ranar da zaki yi nadama mu kuma bama tare da ku.
Jalan ta cigaba da yi mata nasiha iri-iri mai kashe jiki amma banda jiki mai kunnen kashi irin na Amani. Don nasihar da waazin wani na shiga ne wani na fita ta daya kunnen. Ta kawo wasu kwayoyin magani ta bata ta ce ta hadiya yanzu tana gani kuma a gaban ta. Sai Amani ta tuno Haj. Muna, itama hakika ta bata irin wadannan kwayoyin kuma bata yarda ta sha ba, yanzun ma da Mamma Jalan ta dage sai ta sha a gaban ta, can kasan harshen ta ta kai su ta danne su da harshen ta ta kora ruwa. Mamma Jalan ta hada garwashin lantarki (burner) nan da nan ta zuba wani turare irin nasu na musamman tace ta tube ta turara jikin ta. Wanna ba musu ta yi, tunda turare ne kawai, sannan Jalan ta raka ta har kofar entrance na masaukin Mukhtar, tace ta wuce ciki tana kallon ta.
Haka ta tsaya daga nesa sai da ta tabbatar Amani ta buga kofar, ta ga sanda Mukhy ya zo ya bude, da farko kamar ba zai bata hanya ta shiga ciki ba, don ta ga kamar jayayya suke, bata dai jin me suke fadi sosai kasancewar (by nature) din sa, Mukhy bai da daga murya wannan sai Amani idan ta so yin rashin kunya.
Mukhtar yana bude kofar ya ga Amani ce, sai ya ki bata hanya, cewa yayi lafiya? Me kika zo yi wajen dan shege?
Idanun ta suka yi rau-rau, a rayuwar ta bata taba yin maganar katobara ta yi nadama irin wannan maganar ba.
Da ana amai a lashe da tuni ta lashe ta, ta maida ita cikin ta.
Banda Mamma ta sako ta gaba me zai kawo ta dakin sa da daren Allahn nan har ya gaya mata bakar magana?
Sunkuyar da kai tayi tana hura hanci da wasa da yatsun ta, sannan ta juya ta tofar da kwayoyin maganin da ke bakin ta, Mukhtar ya bi abinda ta tofar da kallo amma bai san mene ba, ta ce ai da gani na ka san nima takura ni a ka yi na zo, ka san da bazan zo ba, don bani da bukatar komai a wurin ka ya ce sai ki juya ji koma, shege baya bukatar komai a wurin ki shima.
Ta daga idanun ta cike da hawaye ta ce a rayuwa ta ban taba bada hakuri ga kowa ba, ban taba yin magana nayi nadamar ta ba, amma wannan na yi, na maida wannan kalamin ciki na, na kora su da ruwa nayi flushing din su tun daren dana furta su.
Ina baka hakuri a kan su, don nima na san basu dace ba, sharrin zuciya ne da fushi, amma idan ka cigaba da maimaita min su da rike ni da su a ran ka, hakika ka cutar da ni Mukhtar!.
Mukhtar sai ya juya ya shige ciki ba tare da ya iya ce mata komai ba, don (hes cool and shocked) da sunan sa data ambata yau, ya kuma san da gaske take bata taba baiwa kowa hakuri ba sai yau. Tabbas UWA daban ce, kuma uwa ta yi a rayuwar diya mace. Wadda ta rasa UWA ayi mata jajen rashin da bazata mayar ba, har abada!!!
(Allah ka yi wa iyayen mu gafara ba don sun mutu ba, wadanda suka rasa nasu Allah ka kai rahma da haske da kamshi kabarin su- Takori).
Ba don Mammah ta yi rantsuwa sai ta kwana a dakin ba, da daga nan zata juya ta koma, ai dai ta yi masa sallamar data dace, kuma da ya bata hanya bai ce ta shigo ba, itada kan ta data gaji da tsayuwa ta shiga dakin a fusace, amma bata rufe kofar ba ta bar ta a bude fayau.
Sai shi ne da ya ga sauro zai cika dakin, ya mike ya rufe ya wuce ya koma ya cigaba da abinda ta tarar yake yi kafin ta shigo wato booking din jirgin Lagos online, ta cikin system din sa.
Da shigowar ta dakin atmosphere din dakin gabadaya ya canza da wani irin sihirtacccen kamshi irin na turaren da ake yiwa amaren kasar Saliyo, wanda a makwabtan su wato kasar Gambia kawai ake samun shi.
Yana tambayar kan sa wane irin fitinannen turare ne haka Amani ta fesa, mai barazanar daga masa hankali? Ga gashin nan ya sha wani irin setting an kanannnade shi ya zubo a gaban goshin ta ya zagaya ta bayan kunnen ta, ya kwanta akan wuyan ta, kasancewar laffaya ce a jikin ta sosai gashin ya fito ya kwanta a kan dogon wuyan ta.
Yana aikin amma hankalin sa ya rabu biyu, neman shidewa yake yi. Allah kadai ya san wane irin turare Jalan ta turarawa yar ta. Domin dai a karshe Mukhtar sai kashe kwamfutar sa yayi ba tare da ya san takamaimai ya gama booking din ko bai gama ba?.
Sai ga vedio call din Alhaji ya shigo masa ta whtsp dinsa, alamar yana son magana da shi. Kasa daga wayar yayi ya dai zuba ma kiran ido, sakamakon yadda kasala mai yawa ta rufe shi kuma baya cikin irin mood din da zai iya magana da Alhaji.
Tana kallon sa ya mika hannu ya kashe wayar bakidaya, ta tsaya taki motsawa daga inda take tsaye, ta harde dogayen kafafun ta ta kuma nade hannun ta a kirjin ta tana harare-harare, ita bata zauna ba ita bata rage laffayar jikinta ta kwanta ba.
Mukhtar da kyar ya iya mikewa ya rage fitilar dakin mai haske ya bar shudiya mai rangwamen haske, wadda a turance ake kira dim light daga nan ya lallaba ya haye gadon sa ya ja bargo har kan sa ya kudundune, ya bar ta a nan tsaye don ya fahimci neman rigima take yi da shi.
Amani ta yi kwafa, miskilancin sa ya kara fusata ta, sai ta karasa gadon ta dauki filo daya ta jefa a kasa, ta warware laffayar ta ninka ta biyu sannan ta rufu da ita, ta kwanta akan kafet mai laushi tana cewa a ranta me zai kaita hawa gadon nan ko da ya kula ta? Balle yayi wannan shakulatin bangaron da ita? Ai ko gadon zinare ne ta bar masa.
To amma ta kasa barci bayan ta kwanta din, jin numfashin Mukhtar ya sauya kasancewar dakin yayi tsit, babu komai sai bugun numfashin su da sururun iya kwandishan, yadda numfashin sa ke sauka da sauri da sauri a kunnen ta, tamkar zazzabi da masassara irin wanda ya same shi a Freetown ya ci karfin sa.
Tana jin sanda ya dauko filon sa ya dawo kasa shima, zazzabi sosai da sanyi yake ji, dumin jikin mace kawai yake bukata a wannan lokacin, ya fahimci cigaba da kwanciyar sa shi kadai a gadon daidai yake da ya haka rami ya kashe kan sa... akan matar da addini ya riga ya bashi damar komai yake so a kan ta. Akan me zai yi ta cutar da kan sa har haka?
Shi ya san matsayin sa na namiji kuma matashi mai jini a jika, sannan jinin Issouffou Masaoudou, yayi matukar hakurin da ba kowanne namiji kamar sa ne zai iya ba a kan mace. Ya san yana da hanyar da zai samu kan Amani ko da bada yardar ta ba, amma kasaitar sa bazata bari ba, yana ji a ran sa yafi karfin ya yi forcing mace ta kwanta da shi (by force). A yanzun da tura ta kai bango, kuma Jalan ta warware ego din sa, ta hanyar wannan kamshi na jikin Amani da su kadai matan Saliyo suka san sirrin da ke cikin sa, a yanayin da yake ciki yanzu, sai ya manta ko waye shi, da wannan pride din nasa, sabida ba shi ke sarrafa jikin sa a yanzu ba.
Hakanan ya tabbata suka kwana a haka Allah ma sai ya tambaye shi dalilin cutar da gangar jikin sa, alhalin jikin sa ma da kowacce gaba ta jikin sa na da hakki mai girma a kan sa, bai kamata yayi ta biyewa Amani yana cutar kan sa ba, yarinyar da kullum sai ta saka shi a tashin hankali da wankan janabar babu gaira babu dalili.
Yaya akayi yaya akayi Amani bata sani ba don ta soma samun barci, sai kawai taji Mukhtar ya bi ya kwanta a gadon bayan ta, yana sakin ajiyar zuciya. Domin a yau dauriya da jarumtakar sa sun idasa karewa. Koko in ce, Mama Jalan ta karar da su da sirrin ta.
Hannayen sa ya saka ya riko hannun Amani dasu, cikin siga ta nuna bukatuwar miji zuwa ga matar sa, matar ma wadda yake tsananin so, ya ratsa yatsun sa sosai cikin nata, sannan ya damke su da karfi, kwanciyar sa a gadon bayan ta da yanayin rikon da yayi wa hannun ta a bazata, ya tsorata ta, domin bata zata ba ko da wasa, a tunanin ta Mukhtar ba zai taba iya hada jiki da ita ba, don yadda bata son sa ta tabbata haka shima baya son ta, kuma wannan alamari ta san cewa baya faruwa sai da soyayyah, daga haka ta ji Mukhtar ya janye laffayar jikin ta data rufu da ita, da zafin nama ya janye laffayar, ya saura Amani da tiny rigar robar jikin ta, Mukhtar ya ga body structure din Amani ta cikin hasken dim light wanda hakika Allah ya yi wa Amani halitta wadda ta kasance daya cikin dubu, a cikin na mata dubu kafin a samu irin na matan Saliyo sai an tona, bai taba zaton haka Allah ya kera Amani ba, wanda hakan ya karasa susuta komai nasa, ya birkita dan mutanen Diffa. Kafin ayi haka Amani ta ji Mukhy ya rungumeta ta baya sosai, da wata irin tight hug (runguma tsatstsaura), ya manne ta a jikin sa yana sauke numfashi mai matukar wahalar fita daga huhun sa.
Tana iya jin yadda jikin sa ke shaking, jijiyoyin jikin sa ke vibrating, yana kara shigewa sosai cikin jikin ta da kadan kadan har ya shige jikin ta bakidaya, wanda hakan ya gama tsorata ta, ta soma mutsu-mutsu na nuna rashin yarda da son ta kwaci kan ta, amma karfin ba daya ba, nan ta fahimci mai raba ta da Mukhtar yau sai Allah da ya halatta masa ita. Sai kawai ta soma hawaye masu zafi na tausayin kai, tana hango ego din ta yau ya tsiyaye a kasa..., tana hango budurcin ta zai kare yau a arha, ga wanda bai isa ba, mijin da aka baiwa sadakar ta ba don ya isa ba, bai kuma dauke ta da daraja ba duk da haka, kuma baya son ta kamar yadda bata son shi itama.
Ba kowa ya janyo mata ba sai Maman ta Jalan, cikin kuka-kuka ta ce Mukhtar, are you trying to rape me? Kamar a mafarki Mukhy ya ji Amani ta fada cikin muryar kuka don ta rasa karfin da zata yi kokawa da shi, kamar itama sakon Mamma na aiki a jikin ta, don a lokacin ya gama sabule rigar robar jikin nata bakidaya ba tare da ta ankara ba, sabon zautuwa ya same shi.
Sai yaji gaban sa ya fadi da wannan furucin nata, kuzarin jikin sa ya ragu, he hate the word RAPE don haka ya rage gaggawar sa, kamar a mafarki sai taji muryar Mukhtar yana kiran sunan ta yau cikin wani yanayi da yafi kama da lallashi na matsananciyar soyayya, ya kankame ta iya kankamewa affectionately, yana shafa bakin gashin kan ta cikin lallashi da neman hadin kan ta, kafin ya sanya bakin sa kasan wuyan ta ya saki mata wani sassanyar kiss, wanda ya kusan sumar da Amani daga kwancen da take.
Ai daga wannan lokacin komai ya sauya, domin bata kara sanin meke faruwa da ita ba, kawai ta sakar wa Mukhy jiki ta daina kokawar kwace kan nata.
Domin abunda ta ji a tare da ita da ya yi mata wannan kiss din, ya wuce misali. Mukhtar daya ji ya samu access tuni ya idasa sakin sauran kisses din sa a guraben da take jiran saukar su. A hankali ya ke moving upward da tattausan lips din sa yana sumbatar dogon wuyan nata wuri-wuri har ya isa ga bakin ta....
Amani couldnt explain whats happening from then, lokacin da Mukhy ya manne bakin su wuri guda, ya