Showing 30001 words to 33000 words out of 37455 words
soma ma Amani wani irin zazzafan hot kiss, a lips din ta, kafin ya samu damar shigar da bakin sa cikin nata sosai, ta kuwa bude bakin tana jiran isowar sa, sai da Amani ta saki numfashi mai karfi (moaning), mai nuna deep and extreme pleasure din da Mukhtar ya sakar mata ba tare da ta sani ba.
Ta hakan ne Mukhtar ya samu access din da bai zata ba, domin Amani ta gama sallama masa kan ta, nan ya sarke halshen su wuri guda yana sumbatar halshen nata hungrily kamar yaron da ya samu sweet a cikin bakin sa.
Mukhtar ya gama kashe Amani a wannan lokacin ya kuma gigita kan sa ya koma kamar ya samu hauka, a irin yadda yake sumbatar Amani da yanayin da yake ciki ya tabbatar wa kan sa ba karamin kokari yayi ba wajen rike kan sa har zuwa wannan lokacin da ya cika shekaru talatin da biyar, bai taba zina ba, yana adduar har ya mutu kada ya yi, ya mayar da Amani ko dan yatsan ta bata iya motsawa domin ta hana shi abunda yake kokarin yi din, don nemawa kan sa da ita kan ta nutsuwa, maimakon hakan, sai ma samun kan ta da tayi tana enjoying sumbar da Mukhtar ke mata kusufa-kusufa yadda harshen ta ko biro bazai iya bayyanawa ba, amma ilahirin jikin ta ya karbi sakon Mukhy ta koina.
Mukhtar sai jin yatsun Amani yayi sun ratsa cikin lallausar sumar kan sa da take cunkus, ta tura duka yatsunta cikin gashin sa tana kiran sunan sa da muryar da bata yi kama da tata ba, wanda hakan ya kara triggering stuation din nasu beyond expression. A wannan lokacin daga Mukhtar har Amani sun manta a duniyar da suke, ko wata rashin jituwa ko kiyayya mai dogon zango dake tsakanin su, burin Amani shine a kai ga babban alamarin ta gama shirya yin sallama da kuruciyar ta....
Amma sai wani tunani ya darsu a ran Mukhy, na cewa; shin ya shirya fansar da samartakar sa ne ga Amanin da bata san darajar sa ba sam? Bata dauke shi mutum ba, bata dauke shi komai ba banda daukar sa da take yaron gidan su? Amani har yanzu bata son sa..... kuma ta fada har abada bazata so shi ba.
Wannan access din data sakar masa ya samu ba don SO bane, na shaawa ne da ya taimaka wajen kimsa mata ita, ta hanyar seducing dinta da kiss, kada ya yarda... kada ya sake, kada ya kuskura yayi saken da zai zama injin biyan bukatar gangar jikin Amani, alhalin ba shi da gurbin so da kauna na gaskiya a zuciyar ta. Matsayin sa da darajar da Allah yayi masa ya wuce haka!
Wannan ne ya dakatar da Mukhtar daga kokarin sa na cika sunnar aure, da farantawa kan sa, har ma da Amanin da jira kawai take Mukhtar ya maida ita cikakkiyar matar sa.
Ta gama sallamawa cewa a lokacin komai zai faru a shirye take, domin she cannot resist him a yau. Amani sai ji tayi tamkar an yi ruwa an dauke Mukhtar ya mike daga jikin ta ya koma gadon yana ta murkususun sa shi kadai. Sai a lokacin ta dawo hayyacin ta. Kunya da haushin kanta suka zo suka lullube ta, ta hau tambayar kanta me ya faru haka? Me ke faruwa yau kamar almara?
Ina ego din ta? Ina pride, ina class din ta, ina kuma gatan ta da dukiyar ta data warawa Mukhtar kafa haka yau, tana jiran sa da abinda bata taba kawowa ran ta amincewa da shi ba, gashi ya mata dandani haukaci, ya tashi ya bar ta da kunya da takaicin kan ta.
A haka suka kwana tana kuka, kukan ta baya ta rago in ji hausawa, kukan bakin ciki da haushi kan ta. Mukhtar kuwa falo ya koma bayan wani lokaci. A kan doguwar kujera ya kwana cikin wani hali na kaka ni kayi. Amma kafin asubah ya samu barci mai dadi, ko babu komai ya samu wani irin relief da bai taba samu ba.
Da assalatun fari kiran sallah ya tashe shi, yayi maza ya shiga yayi wanka da alwallah, ya zo ya kunna fitilar dakin sai ya sameta ta hada kai da guiwa har lokacin tana kuka kamar ta kashe kanta.
Jakar kayan sa ya bude, yau a gaban ta ya hau canza kaya. Yo kunyar ta yaushe kuma ya ga komai itama ta ga komai, sai ita ne ta dukar da kan ta kasa don kunya. Ya kammala shiryawa ya dube ta kan ta a kasa, tana ta hawaye, yace,
to Madam, da alkhairi, Shege yayi harama zai koma Najeriya, ya bar ki a Saliyo ki yi yadda kike so da auren sa, a yi hutu lafiya, ko kina da sako gun Alhaji?
Amani ta mike ba tare data tanka masa ba tayi toilet. Kafin ta fito ya kammala hada komai nasa ya na jiran fitowar ta domin Faytoory har ya iso, ya kuma kira shi a waya ya gaya masa ya iso yana mota yana jiran sa.
Bata ce masa komai ba ta soma mayar da laffayar ta jikin ta. Mukhtar ji yayi kamar ya kara rungume ta, ganin har lokacin kuka take yi sosai kamar ta hadiyi zuciya, har da sheshsheka, amma ya hani kan sa da yin hakan. Ya yarda dai ta yi nadamar maganar nan da gaske, ta kiran sa mai kama da shegu, amma shi kuma ya rike ta bada wasa ba, har sai ta yi repenting iya repenting, yadda ya kamata, sannan zai daina tada wannan zancen.
Ya isa inda take hannayen sa biyu zube cikin aljihun wandon Jeans baki da ke jikin sa, kokari ya ke su hada ido amma ta ki, don yau bata da bakin rashi kunya tunda ta gama zub da ajin ta.
Mukhtar ya ce na ce baki da sako gun Alhaji? Hawaye fal idanun ta tace inada shi. Ka ce masa ina so ya mayar da auren sa da Mahaifiya ta, zan taya shi lallashin ta.
Mukhtar yayi dif! Meyasa shi bai yi wannan tunanin ba tuntuni? Amma Alhaji.... ba shi da lafiya yanzu, anya Jalan din zata yarda?
Sai ya ce in har zaki lallashe ta ta yarda Alhaji ba zai ki ba, sai dai ki tuna bashi da lafiya yanzu, bayan ta karfin jiki har da ta rashin iya aure. Amani tayi maza ta dago tana masa kallon neman karin bayani ta hanyar zazzafar harara, abu kazan uban sa take so ta zaga ko ta huce, wato rashin mutuncin sa bai bar kowa ba, har Alhajin ma! Sai ya gyada kai yace eh, Im not joking, sugar ya ci karfin sa, ba ya iya auratayya yanzu sam.
Amani ta daburce, ga kunya ga tausayin Daddy, sai ta hau masifa, ta ce kuma aka ce kowa ne irin ka? Kowa ne yake aure don ya taba mace? Ko kuwa an ce maka kowa ne yake aure saboda wannan rashin kunyar?
Baka san ana aure don mace ta dinga zuba ruwa a Buta tana kaiwa tsohon mijin ta bandaki ko dafa masa ruwan wanka ba?
Dariya ce mai tsanani ta kama Mukhtar amma ya gintse, sabida ta hau kan tsini sosai, yace,
irin naki auren ko?
Ta sa kai zata wuce ya riko gefen laffayar ta, yace Shege zai koma, sai watarana! Idanun ta rau-rau, ta ce Allah yayi mana hisabi ni da kai, sabida yadda kake cutar da ni da kuskure na.
Inda Allah ya cece ta daga Mukhtar shine kofa da ake bubbugawa, dole ya sakar mata laffayan, idanun sa kamar su hadiye ta, ya karasa ya budewa Fajur data kawo masa karin kumallo haka da wurwuri.
brother sabahul khair, an tashi lafiya? Ga nan breakfast inji Mammah.
Ya dubeta cike da kauna ya ce nagode Fajur, amma ki koma da shi ciki don na makara, kuma ban iya karyawa da wuri ba, tuni Faytoory ya zo dauka na. Brother zan bi ka in ji Fajur. Tana marairaicewa duk sai sai kamannnin ta da Amani suka bayyana. Ya ce kada ki damu matas, zaku taho tare da Yayar ki in ta gama hutun ta.
Da wannan duk suka rankaya suka fito Fajur na cewa ya cika alkawari fa, ya dawo ya tafi dasu Najeriya tana son zuwa kasar Najeriya, kullum Mamma na basu labarin Najeriya mai GREEN WHITE GREEN flag.
A harabar gidan suka samu Mamma tayi lullubi ta fito domin su kara sallama da Mukhtar, har kasa ya tsugunna ya gaisheta sannan ya shiga motar Faytoory. Amani ta wuce cikin gida ba tare da ta tsaya sun kara hada ido ba, balle ta kalli shigar sa mota, ko tace Allah ya kiyaye. Kuma a rashin tarbiyyah irin nata bata gaida abokin Baban ta ba wato Malam Abdussalam.
Faytoory ya ja motar Mukhtar na gefen sa suka fita daga gidan, Fajur da Safwan na masa adduar sauka lafiya. Mamma na daga masa hannu idon ta cike da kewa da kunar sa.
Tunda ta shigo gida take kuka, koma me ya same ta yau ta tabbata Mama Jalan ta jawo mata, don watakila magungunan data bata duk da ta zubar amma ai wasu sun narke mata a baki, da turarukan data yi mata ne suka sa Mukhy ya samu damar da ya samu yau a kan ta.
Yanzu ya tafi ya bar ta da cizon yatsa.
A haka Mamma ta zo ta sameta ta soma yi mata fada, a kan rashin gayar da Faytoory da rashin iya tattalin miji da kula da yi masa addua. Ta ce ban taba ganin sokuwa irin ki ba Amina, rashin tashi da Uwa hauka ne? Ai wani abun kana tsintar sa a social environment din da kake ciki da kuma aladu masu kyau na alummar da ka taso a cikin su.
Ke kam kin rako mata duniya!!!
Ta sake rushewa da kuka, tana son fadin Mamma taba ni yayi ta yi fa duk ya hargitsa ni amma ga mamakin ta wannan maganar ta yi mata nauyi a baki, a ce ta gayawa Maman ta ita. Gaar ta bar bakin cikin ya kashe ta. Sai ta yi shiru, tana jin ciwon kalaman uwar. Da tace ta rako mata duniya wajen rashin iya tattalin miji! Da ballagazanci!! Ta ce har da dolanci !!!
***** ***** *****
T
un daga wannan ranar Mamma Jalan ta maida hankalin ta da lokacin ta kacokam! A kan gyaran tarbiyya da dabiu da addinin yar ta Amani.
Gashi yau har Mukhtar yayi sati biyu da komawa Katsina, Jalan har girki tare suke yi da Amani don ta lura bata iya komai da ya shafi rayuwar mace a gidan aure ba. Kada girki ya ji labari.
Hatta sallahr ta ta tsaya tana dubawa da gyarawa da saka Safwan ya dinga koya mata karatun Alqur ani kullum. Ba don bata san ranar komawar ta Katsina ba da a islamiyya zata saka ta.
A hakan ma babu laifi don tana da kwakwalwa, tana daukar kananan surorin da Safwan ke kara mata kullum.
Shakuwa mai tasanani ta shiga tsakanin Amani da kannen ta biyu wato Fajur da Safwan da mahaifiyar su da ke kokarin samar da kauna da shakuwa da hadin kai a tsakanin su.
**** ***** ****
KATSINA
T
unda ya tafi bai kira Amani ba, ko sau daya, kai ko da kuskure, domin ya tarar da very tight schedules a kamfani da shagon ta, amma tabbas ya san yana kewar ta da rashin kunyar ta, kai har ma da fitsarar ta. Ya kan tun ranar su ta karshe with so much adoration.
Allah yayi mana hisabi ni da kai, sabida yadda kake cutar da ni da kuskure na!
Sune kalaman ta da kullum yake yawan tunawa yayi murmushi. Masu tabbatar masa da cewa (for the first) tima tayi maganar da ta zo ta yi nadamar ta a rayuwa.
Amma daga komawar sa Baba Idi har ma da Alhaji suka bude masa wuta kan sai sun dangana da iyayen sa ko danginsa don shima Baba Idi ya dage a kan hakan. Mukhtar kuma yafi son ya fara sulhunta Jalan da Alhaji tukunna kafin ya yarda su tafi Diffa, gabadaya har Mamma Jalan don dai ya kore curiousity din sa a kan cindon ta da na Ummami. Don haka ya gayawa Alhaji sakon Amani, na tana rokon su maida auren su shi da Maman ta.
Alhaji Usman sai yayi dariya, yace a da can ma dana ke da cikakkiyar lafiya Jalan bata yarda ta zauna da ni ba sai a yanzu da nake da rabin jiki shanyayye, kuma ba zan iya sa ta haifar wasu yayan ba? Dube ni a cikin wheelchair.
Mukhtar ya ji wani iri ya ce cikin tausayawa,
ai Amani ta ce auren zuba ruwa a buta a kai bandaki da zuba ruwan wanka zaku yi. Ba sai don wannan kawai ake aure ba Alhaji, in ji ta. Alhaji bai san sanda ya bushe da dariya ba, ya ce ai ka sani Mukhtar ni bani da say, in dai a kan Jalan ne. Na bar komai a hannun ku kai da Amanin, idan har ta amince a hakan da nake ni ai zan fi kowa farin ciki.
A daren Mukhy ya yiwa Amani gajeren text messege, yana so ko yaya ya tsokane ta, inda yace.
Shege ya zo gida lafiya, duk da baki nemi jin hakan ba.
Alhaji ya amince da bukatar ki na maida auren sa da Mamma, idan har zaki yi masa yakin neman amincewar ta.
Su Baba Idi zasu taho a maida auren. A kasan sakon sa ya rubuta;
_Mai kama da shegu.
Sanda sakon ya shigo wayar ta girki suke yi itada Fajur, don haka bata duba ba duk da ta ji alamar shigowar sa sai da suka kammala.
Ta runtse idon ta kadan, a kan wannan kalma da ya kara ambata mata, ta yarda Mukhy, mutum ne mai tsananin riko, irin wadanda da wuya a cuce su su yafe, ba tare da sun rama fiye da abun da aka yi musu ba ko mafiyin sa, ko da zasu huce din ma kenan.
A ranar ta nemi jin ta bakin Maman ta kan komawa mahaifin ta, ta ce for my sake Mammah!
Ta hada hannayen su wuri guda tana rokon ta. Har da hawayen ta.
A karshe Jalan ta amince zata komawa Baban Amani, albarkacin Amani da Mukhtar don su yi zaman aure na jinyar Alhaji, koko zaman auren zuba ruwa a buta da kai ruwan wanka kamar yadda Amani ta kira auren.
Wata biyu bayan nan Mukhtar ya yiwa Baba Idirisu da su Kamilu da Baba Sahura shirin tahowa Kenema, shi kadai ya tsaya tare da Alhaji da kamfani, cikin kwana uku da zuwan su aka maida auren Ahaji da Jalan, farin cikin da Amani ke ciki ne yasa ita da kanta ta hada musu kayan su don su taho Katsina tare da su Baba Idi, wai biki zata yi wa Daddy da Mammah, biki na kece raini, hararar ta Jalan ta yi ta ce,
ki fara shirin naki bikin dai, ni ba saar wasan ki bace.
Baba Idi dake wurin yace ai in suka isa Katsina ba zama zasu yi ba, mika ta wajen mijin ta zasu yi, zasu dunguma ne su wuce wajen iyayen sa a Diffa region, ta kasar Nijar. Kuma Mukhtar yace in sun tafi bazata dawo ba, sai ko da ganin gida.
Maganar sai ta tunowa Jalan da Yayar ta Aisata dake Nijar. To ai kamar a Diffa din ne ma dan aiken dake tsakanin su yace take aure. Tsakanin ta da Aisata sai aike, don bata taba fita daga gidan mijin ta ba tun ranar data shige shi. Ta sa a ranta zata nemi jin hakikanin inda take a Nijar din in sun je, bata dai tabbatar da inda take a can din ba don taba zuwa ta yi ba, zata nemo mutumin ya bata adireshin Aisata ko don ta yi wa Amani Uwa a can da jinin ta kuma uwar ta.
**** ****