Showing 1 words to 3000 words out of 24347 words

Chapter 1 - Rayuwar Rayhana Book 3 Hausa Novel Complete

Takori   

28 Dec 2024

142

 [12/24/2019, 21:48] Takori: RAYUWAR RAYHANAH! 3
Ayadda Mami ta shigo gidan, ya tabbatarwa Jawahir dake zaune tana cin abinci Mami bata cikin nutsuwa. Bata tsaya anan ba ta wuce bedroom dinta ta maida kofa ta rufe ko magana bata yiwa Jawahir din ba, wadda itama bakinta ke cike da tambayoyi fal, data ke so ta yiwa Mamin. Amman ganin babu fuskar da zata yi tambayar yasa ta like bakinta tayi shiru. Tambayoyin data ke so ta yiwa Mamin akan Rayha da Khalipha ne.
Ina Yaya Khalipha ya shiga wata da watanni ta daina ganinsa? Har zuwa wannan lokacin da su Jawahir ke a matakin jami’a iyayensu basu basu iznin rike waya ba, ina kuma Rayha ta shiga? Ta wayi gari ta nemeta sama da kasa ta rasa ta?
Ko kadan zuciyarta bata kawo mata wani abu game da rashin ganin Rayhanah a ranar data wayi gari bata ganta ba, ba, tayi zaton sun je Takai ne da Daddy don shi dama sammako yakeyi in zashi Takai don ya dawo akan lokaci.
To amma bayan wasu yan kwanaki ta koma ganin Daddy cikin gidan bai ce mata komai game da tafiyar Rahane ba.

Wasa-wasa satittika da watanni suka shiga wucewa babu Rahane a gidan. Don haka a yammacin wata ranar Lahadi Daddy yana gida sai ta tambaye shi,
“ni Daddy ina Rayhanah ne?”
Murmushi yayi, yace
“ki kwantar da hankalinki Jawahir, nayi mata AURE!”

Idanun Jawahir duka a waje kamar sa fado abin dariya, cikin kidima da gigicewa. Haka Daddy ya fice ya barta yana dariyar razanarta.
Kwanaki biyu Mami tayi bata je ofis ba, tana fama da ciwon kan barin kai guda (migraine).
Wannan ranar tana kwance a gadonta ta mika hannu ta lalubo wayarta ta kira Ibrahim. Don ta sanar dashi al’amuran da suka cakude mata, suke kuma gallabar rayuwarta ko ta samu sanyin zuciya duk da tasan bazai yi mata maganinsu ba, amma akalla zata ji sauki daga nauyin da zuciyarta tayi, da azabtar da ruhinta ke yi.
Mace ce ta daga wayar, wadda bata tantama baturiya ce, ta sanar da ita cewa Dr. Ibrahim ya daina amfani da wannan layin. Ta nemeta data bata wadda yake amfani da ita tace babu waya hannunsa baya rike waya.
Takaici ya ishi Mami tace “dauki taki wayar ki kai masa har insa yake inyi magana dashi, ni mahaifiyarsa ce”.
Baturiya tace “ya shiga tiyata bazai amsa waya ba yanzu sai bayan awanni goma sha biyu”.
******





(Shekaru goma sha biyu a baya)

Abinda Mamin bata sani ba
shine, matsayin Dr. Ibraheem a yanzu ya zarce tunaninta a nephrology department din overall asibitin Chicago (ILLINOIS teaching hospital). Kai tsaye baka isa kayi magana dashi ba batareda appointment ba, a tun wani aiki da yayiwa shugaban kasar Brunei (sultan of Brunei) na dashen koda, wanda ya bashi damar zama consultant na nephrology department a babban asibitin ‘Illinois’ bayan wani kwas daya halarta na shekara guda a yankin‘Ohio’.

Matashin likitan mai shekaru talatin da uku, mai wasu irin unique akidu da dabi’u da suka hadu suka maida shi wani mutum na daban da sauran al’ummar da yake tare da su. Suka kuma zamo silar mataki iri-iri na cigaba da yake takawa a rayuwarsa at a very young age.
Manyan kasashen duniya ke daukar shi haya yayi musu aiki akan fanninsa, a kuma yi nasara ta ban mamaki.
Zuwa wannan lokacin, I.M Takai, wato IBRHEEM MANSUR TAKAI, ya gama taka duk wani matsayi da Dan Adam din duk da yasan ciwon kansa ke burin samu.
Matsayin da ko iyayen da suka haifeshi basu sani ba, basu zata ba basu san ya taka ba, basu kuma tsammana ba ko a mafarkinsu, kuma bai tsaya neman gaya musu ba, don ba halinsa bane yawan magana ko fadar halin da yake ciki ko abinda yake ciki ga kowa, bayan zuciyarsa, akan wanda aka tambayeshi ma balle wanda ba’a tambayeshi ba, sai ko wanda idanunsa suka gane masa, tunda bashi da halin rufe masa idon.
Yaushe ma ya rike wayar bare ayi doguwar magana da shi? Shekaru uku da suka wuce Mamin ta je Chicago, tayi kwanaki bakwai tare da shi cikin gidansa dake cikin jerin gidajen malaman jami’ar ta Chicago, bayannan Baba Dacta yaje amma bai jima ba alokacin yana lecturing da part time job da asibitin lllinois, abinda suka sani kenan.

To bayan dawowarsu ne al’amuran Ibraheem Takai suka ci gaba da bunkasa. Manyan kasashen duniya dai-dai ne bai jefa kafarsa ba ya yi private aiki dasu ba. Musamman Ohio, Columbia, Bruce da Brunei.To kamar yadda yake ga kowanne lafiyayyen dan Adam, kaddara da nauyin aljihu kan canza da yawa daga halayen dan Adam, duk irin tarbiyya da tsantsenin iyayen da mutum ya tashi a ciki kuwa, Ibraheem is not exempted.

Da fari, wahalar karatu da kujuba-kujubarsa basu sa Ibraheem waiwaye ga al’amarin mata ba, duk da yadda suke binsa kamar kaza da ‘ya’yanta. Ina ya ga lokacin yin wata mu’amala ta soyayya ko akasinta, karatu yake ka’in da na’in kamar bai da sauran wani buri a rayuwarsa sai shi.
Amma da ya hattama karatun, ya samu nutsuwa da hutu, ya kuma soma jefa kafa (outside Chicago) don aiki da samun hutu, duk tsantsenin sa sai da wasu daga cikin tarbiyyar Uwa da Uba suka canza.
As a Proffesional Medical Doctor, Ibraheem bai kurba giya, baya zukar sigari balle wani abu da zai gusar da hankalinsa ko ya sa shi maye. To amma ‘yan mata fa (barin rayuwar kowanne lafiyayyen da namiji), musamman wanda bai da aure kuma jikakke kamar Ibraheem, yaro matashi mai cike da koshin lafiya da tarin ilimi da duk wata alfarma ta rayuwa.
Ya dade da fita daga gidajen malamai ya sayi nasa na kansa (American – mansion) a North-Eastern Chicago bayan wata kyautar bajinta daya samu daga (Sultan of Brunei) akan aikin dashen kodar da yayi masa ya samu lafiyar da yayi shekaru yana fama, da duk wata alfarma da manyan likitocin Amurka ke tinkaho da ita.
Duk da haka Ibrahim ba zaune yake wuri guda ba ko a cikin Chicago, sai ya yi watanni uku baya cikinta yana yawon (private jobs) a duk inda aka gayyace shi aiki tare da kungiyar (nephrology associate). Ita wannan kungiya ita ke tallata members din cikinta da ayyukansu da kwarewarsu ga duniya kuma ta kan turasu su wakilceta idan an bukaci likitocin koda daga cikinta. (It’s not a profit making organisation but for the benefit of its members). Abin nufi, ‘nephrology associate’ ba’a ginata don samar da riba ga kungiyar ba sai don amfanin ‘ya’yan cikinta. Haka da yawan kungiyoyin likitocin Amurka da Africa Ibraheem na cikinta, irin su AAPS (Association of American Physicians and Surgeons), NAD (National Association of Doctors), Alberta Medical Association, AMA (American Medical Association) Flying Doctors Society of Africa, AAD (African-AmericanDoctors Association), WAMA (West African Medical Association) da sauransu.
Cikin shekarun da Ibrahim ya yi a lllinois-Chicago, bai wani kara jiki ba, yana nan yadda yake (Dogo mai kirar karfi). Ma’abocin zati da kamala. Kalar fatarsa ce kawai ta canza sai karin hankali da nutsuwa bayyananniya da shekaru da zurfin ilmi suka karawa fuskarsa.
Baki ne shi kamar Dacta Mansur, jikinsu iri daya, tsayinsu iri daya, zubin jikinsu iri daya, amma a halin yanzu Daddy ya fishi kauri da cika ido na jikin girma. Amma idan ya juya baya yana tafiya ko yana wani abun daga tsaye tsammani zakayi Dr. Mansur ne.

*****



Ya fito daga dakin tiyatar ya shiga (Doctor’s Changing Room) yana cire koren kyallen dake hancinsa da cire korayen kayan tiyatar dake jikinsa ya sanya wadanda ya zo dasu. Yana wanke hannunsa da sabulu a sink din dake cikin ofishinsa bayan ya zare ledar hannunsa, sakatariyarsa Rita ta nemi izinin shigowa, ya amsa mata, ba tare da ya juyo ba.
Ta shigo cikin tarin girmamawa ta mika masa wayar dake hannunta domin ita take hada mishi appointment kuma ita yake baiwa wayarsa take amsa mishi in ya ga mai muhimmanci ce a gare shi ya amsa, in ba hakan ba, ta ce a bada sakon a fada masa, ko voicemail ya hanata sanyawa a wayar.

“Your Mum has called......”

Ta fada cikin tarin girmamawa tare da mika masa wayar.
Ya karba ya duba ya tabbatar Mamin ce. Rita ta juya ta fita ta rufo masa kofar. Ya zauna a kujerar dake fuskantar tebirinsa, cikin nutsuwa ya kira lambar Mami.

Mami dake kwance cikin zazzabi mai zafi a dalilin damuwa da matakin kauracewa da Dacta Mansur ya dora mata, da tunaninsa na cewa ita ta hana Ibraheem daukar wayarshi, bayan ita ma fiye da watanni uku kenan rabonta da jin muryar dan nata.
Abin da basu sani ba shine, Ibraheem ya yi fama da matsananciyar rashin lafiya na (Ulcer). Ba komai ne mujazar rashin lafiyar Ibraheem ba, rashin Cin abinci ne, da tarawa kai aiki wanda ya fi karfin jiki da kwakwalwa su dauka (stress). Kuma ko da wasa bai gayawa Daddy ba, don a lokacin Daddyn ya rikice da murnar maganar da suka yi a waya wai ta zancen aure.
Don haka bai gaya masa ba ko da wasa ya tsallake zuwa wani asibiti a ‘San – Francisco’ ya yi jinya ta lokaci mai tsaho, diyar Ambassadan Nigeria a Amurka ko-ko a ce budurwar sa, Sapna, ita ta yi jinyarsa.
Cikin ‘yammatan bakar fata dake kara-kaina a kan Ibrahim musamman ‘ya’yan Jakadu da zaunannu (wadanda aka haifa a garuruwa daban-daban cikin yankin Amurka da Colombia) Sapna ce kusan a ce ta samu kallon kima daga Ibrahim, itama din a dalilin Babanta ne ya hadasu tun wani aiki da Ibrahim din ya yiwa babban dansa na dashen koda mai suna Ali.
Su mutanen Sokoto ne usul, Hausarsu ce take fallasa hakan. Za’a iya cewa Ibrahim na son Sapna, kasancewarta daban da sauran ‘yammatan sa, mahaifinta ba dattijon banza bane, a’ah, Basakkwacen Dan bokone dake maintaining nationality din sa dana iyalinsa a ko’ina. Yake kuma iya kokarinsa akan tarbiyyarsu.
Sapna ba ta shigar banza, ga kwakwalwa, daliba ce a jami’ar da Ibrahim ya yi (University of Chicago) gata da son addini, ga kyau kamar ita ta yi kanta. Itama baka ce (black beauty), don haka Ibrahim ke son ta. Ba ta da rawar kai da kula maza. Don haka mu’amalarsu ta yi tsayi.
Ibrahim zai iya rantsewa shine namiji na farko da ya kai hannu jikin Sapna, ya sanyata cikin wata rayuwa da baza’ace bata sani ba amma bata yin ta, tayi amanna da itane alfarmar kalmar SO da tasirinta musamman ga diya mace ma’abociyar rauni da gajartar tunani, bai kuma taba keta alfarmarta ba, ba ita kadai ba ma, bai taba ba, iyakacin abin kenan (refreshing).
Ya kuma dade da alkawartawa ransa duk rintsi ba zai taba keta alfarmar diya macen da ba matarsa ba, saboda fadar (S.A.W) a kan zina, idan ka yi da ‘yar wani, babu shakka za a yi da ‘yarka, kanwarka ko uwarka.
Wannan yasa Ibraheem sau tari kasancewa cikin azumi, domin danne sha’awar zuka-zukan matan dake neman cinye shi danyensa, ya kuma daurawa kansa al’adar kin rike waya, wannan kwarai ya taimaka sosai wajen gyara rayuwar Ibrahim.

Don haka ne da Daddy ya kawo zancen aure ya yi saurin amsawa, domin ya iso wani limit na tsananin bukatar auren, saidai ya yi zaton Daddy zai ja abin da dan nisa har ya gama da wasu ‘yan matsalolin dake gabansa, musamman zuwa San-Francisco jinya. Ya kuma fi son zaben Daddyn akan zabensa, don ya san ba zai taba zaba masa matar banza ba.
Ko da nan gaba zai kara da Sapna, a kalla yana da uwargidan da ta san kimar iyayensa; Mamin nan da Daddy da babu kamarsu, za ku ma ta san cewa zaman iyayensa take, kada ta kawo masa wata fiffika idan ta san shi ya ganta ya ce yana son ta.

Akwai dai abinda ya taba takura zuciyarsa a can baya, wani lokaci can da ya shude na kuruciya.....Yeeeesss... kuruciya mana..... Amma mai GIRMA!!! It goes far beyond mere or casual assumption! Wanda ya yiwa yakin zuciya da kwakwalwa, har ya samu yayi fata-fata da shi ya fatattakeshi daga rayuwarsa, domin ya fahimci ba karamin barazana bane kuma kalubale ga ci gaban rayuwarsa, da abunda ya raboshi da gida, iyaye da yan uwansa.
Ya tabbata barin abin ya habaka ko ya fito sarari (a wancan lokacin) da yake determined matashi (matashi mai kuduri) zai rugurguza ginin da yake son yiwa rayuwarsa ne da burin iyayensa akansa.
Kuma yanada burirrika da al’amuran da yasa gaba da suka sha gabansa (al’amarin) suka dameshi suka shanye a muhimmanci.
Tun daga wancan lokacin Ibraheem bai kara takurawa zuciyarsa a kan diya mace ba. Kananan kura-kuran da yake yi ma (Lamamu), ya na rokon Allah ya yafe masa as soon as ya aikata. Domin a ganin Ibrahim da wautarsa a wancan lokacin (it’s something that a healthy human being cannot do without), ya na da kyakkyawan hope din cewa, daga ranar da Daddy ya ba shi auren da yake ikirari, babu shi babu lamamun.
Abu daya ma yasa yake refreshing din (bakin Sapna), labbanta da tsagar bakinta su ke fizgar hankalinsa kamar ita ta yankawa kanta, take kuma ba shi a araha, saboda son da take masa. Shima kuma yana jin zai iya aurenta ko a nan gaba, amma ba a matsayin uwar ‘ya’ya ba.
Dalilinsa shine gata ya yiwa rayuwarta yawa, ba za ta iya yiwa ‘ya’yansa irin tarbiyyar da yake so ba, irin wadda uwa da ubanshi suka dora su a kai.
*****
[12/24/2019, 21:48] Takori: Hankalin Ibraheem ya yi kololuwar tashi jin Mami na kuka. Ya kara rike wayar a kunnensa da kyau, sai ya ji cikin shesshekar kuka Mamin na fadin;
“Daddy no longer love me now........ a kan wani dan kuskure kalilan.... HEEMU ya zan yi???”
Ta ci gaba da rusa masa kukan da bai taba ji ko ganin ta na yi ba.
Abin da ya sani shine, Mami da Daddy na matukar son junansu, ta yadda har daya baya iya jure bacin ran daya na lokaci mai tsayi, ba tareda ya shiga tashin hankali ba, ba kuma ya daukar fushin dan’uwansa da sauki ba tare da ya yi exaggerating al’amarin ba fiye da kima.
“Cool down Mamee....... take it easy, kukan ki na gigita ni. Ban son in ji ko& laifin na mene ne, amma zan bai wa Daddy hakuri.
Nima ba cikakkiyar lafiya ce dani ba, last week akai discharging dina from bed a SanFrancisco. Zan kira Daddy yanzu........”
Ai sai Mami ta manta da nata damuwar, muryarta na rawa ta ce,
“Me ya sameka?”
“Ai na ji sauki Mami, ulcer na ce ta motsa irin motsawar da ba ta taba yi min ba. Ban gaya muku bane don kada na tada muku hankali ku zubar da aiyukan ku ce za ku taho wajena. But am more than fine now. Luv u Mum!
Kuma fa ya kamata zuwa yanzu ki dinga kiyaye lafiyar zuciyar Daddy, shekaru sun tura, yana bukatar stable family care.
A abubuwa da dama kuna da ra’ayi daya amma ya ce yanzun kin canza, saboda rudin kawaye. Kin zabi bin ra’ayin kawayenki akan nasa.
Kin daina bin ra’ayinsa, sai dai ke ya biki, sai abin da kawayenki suke so kike yi wadanda kin kasa gane ba masoyanki bane, anya Mami??? Ina nan tahowa Nigeria nan da wata daya”.

Dr. Asma’u ta kawo doguwar ajiyar zuciya. Wane irin zurfin ciki ke da Dacta Mansur da babu mai jin zuciyarsa sai Ibraheem? Hatta ita MATARSA Asma’unsa!!!
Ita ko a fuska bai taba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login