Showing 21001 words to 24000 words out of 24347 words

Chapter 8 - Rayuwar Rayhana Book 3 Hausa Novel Complete

Takori   

28 Dec 2024

211

wa Daddyn ke......”
Nan ma shiru ta yi masa. Bugun zuciyarta na kara tsananta..... tabbas shine suke magana a waya, wanda muryarsa kadai ta yi tasirori masu yawa a zuciya da gangar jikinta.
Ya ce,
“Wato wai ke Jumah ko? To Allah yasa Jummai ce yau gani-gaki, ki kara yi min karya ki gani in ban cinye bakinki ba. Wai ke ga wadda ta matsu miji ya zo har kike tambaya nine Ibrahim???
In ma Ibro ne ga ni, me za ki yi min? Me za ki bani kike nemana???”
Haushi ya kama Rahane, ba ta juyo ba ta ce (cikin kunkuni)
“Ni ban ce ka zo ba, ban ce ina nemanka ba. Tambayarka kawai na yi don in san da wa nake magana ba don wai wani Ibraheem ya zo ba.
Da za ka koma in da ka fito ka sakar min mara in yi karatuna yadda na faro shi ba tare da an takura min ba da na fi farin ciki.......”
Kama baki ya yi da mamaki mai yawa, dariya kuma ta kama shi da yadda take tura baki gaba tana zumbura shi tana cunoshi yana girgiza kai yana dariyar ya mika hannu ya janyo tafin kafarta keeey.... zuwa inda ya ke zaune, ya kama hannayenta biyu ya rike cikin tafin hannunsa na dama ya soma dalle mata baki da yatsunsa na hagu.
Ya ce, “Say it again, ashe baki da ta ido? Watch your words mijinki ne ni ba saurayinki ba....’’
Azaba ta ishi Rahane har leben ta na sama ya dan kumbura..... wasu matsiyatan hawayen azaba suka feso, kamin kuma ta yi aune Ibraheem ya rungumeta gaba dayanta cikin kirjinsa, runguma so calm har baka hango ‘yar Rayhanah cikin physique chest din Ibrahim.
Sannan ya kai bakinsa cikin nata ya soma yin abin da ya fi so a rayuwarsa, wato mouth to mouth kissing. Rikon da ya yi mata mai karfi ne da ta kasa kwatar kanta. Rayhanah ta tsinci kanta a wata duniya ta daban da ba ta taba tsintar kanta a ciki ba.
Abubuwa da yawa ke yawo a kwanya da zuciya da jikin Ibrahim a wannan lokacin. Wadanda shi kansa ya kasa fassarasu, ya kasa daina sumbar kuma ya kasa rabata da jikinsa. A lokacin ta fara kuka na ido, wato zubar hawaye, tunda kamar yadda ya ce din ne zai cinye bakin, ta yarda tareda yin amanna da gaske yake cinyewar zai yi, in tayi la’akari da yanayin yadda yake tafiyar dashi din. Ya ki sakin bakin balle ta koma magiya.
Hawayen da ke fita a idonta su suka sanyayar da jikinsa, ya daina abinda yake yi din ba don ya gaji ko ya gamsu ba, he don’t actually know what he’s deriving in it but it’s something pleasurable ever in his entire life...., amma hakan bai sa ya rabata da jikinsa ba. Data samu hakan sai ta soma ba shi hakuri cikin kuka dole ya karaya ya cikata.
Shi da kansa ya dauko ribbon din daya fadi ya tattara kakkarfan gashin da bai taba ganin relaxer ba ya daure mata...... a ranshi yana ta mamakin yadda mace zata bar gashin kanta in its naturality haka. Shi kuma ya koma da baya ya kwantar da bayansa a gadon kafafunsa na kasa.
Ya nuna mata hanyar kofa.......
“Ki je Daddy na kiranki”.
Ya fada da wani sauti kamar ba nasa ba.
Ta kokarta ta mike amma cira kafa ya gagara. Sai ya yunkura ya mike gaba dayansa yana binta da kallo sosai, ya mika hannu ya kunna fitilar data fi kowacce haske a dakin (ressaince) ta jikin ceiling, wadda haskenta yasa Rayhanah kai tafukan hannunta ta rufe fuskarta.

Doguwa ce sosai amma ya fita, siririya ce amma kirjinta da kugunta a cike suke. Har yanzu sanye take da suturarta ta dazu (belted -waist -shirt) da dogon bakin wandon jeans. Ta zargo belt din tsakiyar rigar ta daure. Sai ya kamo hannunta suka fito suka tadda Daddy da Inna suna hira a falo, tuni ya gama cin abincin.

Rayhanah ba ta taba jin kunyar Daddy a duniya irin yau ba. Ga kanta babu kallabi, sai ta cure a gefe daga can bayan Inna wai gaishe shi take, shi sam ma baya jiyota, balle ya San magana take ya amsa mata.
Abin da ya ce shine,

“Rayhanatu yau Allah ya yanke mana komai ga Ibrahimu ko?”
Daga mishi kai ta yi ba tare da ta dago ta kalle shi ba. Ya yi murmushi na jin dadi da samun kwanciyar hankali cikin kulawa yace
“Babu wata damuwa ko?” Ta sake daga mishi kai again. Da hanzari ya ce,
“Ki bari Rayhanah, kada ki bullo da wannan sabuwar mu’amalar tsakaninmu, wai saboda Ibrahim ya zo.
Ni ban san shi ba ke na sani a matsayin ‘yata, in kuma kin canza min matsayi daga uba zuwa suruki ne, ehh to ki gaya min?”.
Nan ma girgiza kai ta yi. Ya dai tabbatar yau Rayhanah surukuta ta musamman take yi da shi ba zai samu matsayin baya da yake so ba.
Sai ya hakura ya mike a lokacin Ibrahim yana wajen socket ya kunna wayar Rayhanah a inda tasa chaji ya dau lambarta ya zuba nashi lambobin a ciki na layin da ya saka anan Singapore, amma bai sa suna ba.
Daddy ya ce, “To Ibrahim mu tafi masauki, tunda ka yi min firraqu ni da ‘yata, kaima ba zan barka a gidan ba, wuce muje”.
Shi Ibraheem murmushi kawai ya yi ko Rayhan bai kara kallo ba ya yi gaba, ka rantse da Allah ba shine wancan mai deep kisses din ba.
Shi yake tukasu zuwa otel din su, sai dai ya karanta hira tsakaninsu, ya fi mai da hankali ga tukin.
Daddy ne kadai yake ta zuba yana gaya masa don Allah ya rike masa ‘ya amana, ya ji kanta ya tausaya mata, ya tausayawa maraicin ta da raunin ta, ba ta da uwa ba ta da uba sai shi a yanzu. Duk abin da ta nuna ba ta so don Allah kada ka takura mata.
Ibraheem ya ce a ransa,
“Saboda ni ba Da bane, tsinto ni ka yi a bola?”
*****
[12/27/2019, 17:59] Takori: Sabon dare a wajen Rayhanah! Bayan fitarsu ta dade ba ta motsa daga inda take ba, wato bayan Inna Juma. Ita Juman kicin ta shiga ta ci gaba da ‘yan kaye-kayenta da su wanke-wanke, tana yi tana ‘yan wakokinta.....
Wai “duk wayon amarya sai an sha manta....... na zama dauko riga, na zama dauko wando, na zama dauko hula.... shekara mai zuwa war haka zan fara goyo da wankin kashi da share tumbidi........”

Abin da Inna ba ta sani ba shine, ita Rahane ba jinta take ba don ta yi nisa cikin tunani mai zurfi. Da ta gaji da zaman falon sai ta lallaba ta shige daki. Kwanciya ta yi a gadonta don ta samu barci, amma idanun sun ce basu san wannan ba.
Duk motsin da ta yi, duk juyin da ta yi, jinta take a kirjin Ibraheem. Gaba dayanta ma in fact, kamshin Ibrahim take, wani irin kamshi da ba ta taba jin mai sanyi da dadinsa a duniya ba, ba ta kuma iya tantance kowanne turare ne ba. Ta kasa barci sai juyi a kan gado.
Jikinta, zuciyarta da kwakwalwarta ke karbar wani sabon sako mai kassara gabban jiki. Cikin wannan halin, wayarta da Ibraheem ya aje a bed-side ta soma kira. Ba ta yi niyyar dagawa ba, domin dare ya mika sosai, amma da kiran ya isheta sai ta mika hannu ta daga.
Sabuwar lamba ce, amma ta nan Singapore. Daddy ba zai kirata a irin wannan lokacin ba sai dai in ba lafiya ba.
Wannan tunanin da ta yin shi yasa ta daukar wayar ta amsa cikin sanyi. Wajen minti biyu ba a yi magana ba, za ta kashe ya ce,

“Rayhanah kada ki kashe min waya, zamu bata”. Da muryar da ta kasa amincewa cewa ta Ibraheem ce.
A hankali ta ji idanunta sun lumshe da kansu. Ya kara cewa,
“Hira nake so muyi, Rayhaanah za ki yi min?”
Ta girgiza kai kamar yana ganinta. Amma ba tayi magana ba.
“Ba za ki amsa ni ba Rayhanahhh?”
Ya fada tun daga karkashin zuciyar sa in a subdued.
Ji tayi sunan yafi dadi a bakin sa fiyeda bakin kowa, fiyeda bakin duk wani Dan Adam data taba jin ya furta sunan a kunnenta, tun bayan da Allah ya yayemata lalurar ta, jama’a suke ambaton RAIHANAH!!!
“Ni fa barci nake yi, hirar me zan maka da tsakiyar dare haka Ya Himu?”
“Karya kike idonki biyu!”.
Ya fada kai tsaye. Kamin ta ce wani abu ya ce.
“Hira irin wadda mata take wa mijinta, kamin yayi barci”.
Ji ta yi kamar ya kinkimo katon dutse ya dora mata aka. Don haka ba ta amsa mishi ba ma wannan karon. A sanyaye ya ce,
“Rayhanah haka zamu yi da ke ko?”
Da likitan zai tsaga jikinta a wannan lokacin da ya ga yadda jininta ya daina ratsawa a jikinta. Mene ne haka? Yau wane irin dare ne a rayuwarta? Me ke shirin faruwa da ita?
Shirun nata ya matukar tuke Ibrahim, ya ce a dan zafafe.....
“Allah idan ba za ki bude baki ki yi min magana ba zan zo yanzu Rayhanah mu kwana tare, cikin bargo daya. Kin san kuma Inna ba za ta ki bude min kofa ba”.
Hawaye ya cicciko idanunta, wannan shine abin da ta fi tsoro a rayuwarta kenan yanzu (sake kadaicewa da Ibrahim).
Cikin ‘yar rawar murya da karkarwar jiki ta ce,
“To me..... me zan ce maka Ya Himu?’
“Labarin rayuwarki ta baya, da saurayinki Yaya Khalipha.......”
Hannu ta kai ta toshe bakinta.... ta fidda ido alama razana.
“Ka daina irin wannan maganar don Allah..... babu kyau Ya Himu”.
Ibraheem ya lumshe idonsa a hankali ya ce,
“Na bari, to amma samarinki nawa a Kazaure?”
Da sauri ta ce,
“Allah mu bamu da saurayi, Daddy baya bari”.
Dariya ya yi, domin yadda ta yi maganar kuruciyarta ta fito sosai. Sai ya kara tausasa murya,
“Ai an gaya min ne wai da Yaya Khalipha ne zai aure ki......”
“To Allah bai yarda ba”.
Ta fada da sauri. Ta ce a ranta “ko da yake son nawa nima nake son sa, ai kai nake gani a matsayin miji cikin mafarkaina, don haka ban mika masa soyayyar zuciyata gaba daya ba”.
Ba ta san cewa a fili ta fada ba.
Ibrahim ya runtse ido, cikin mamaki da hardewar harshe da nauyin American-accent dinsa ya rinjaya ya ce,
“Har mafarkina kike yi Rayhanahhh?”
Sai a lokacin ta ankara da subutar bakinta, ta ce,
“Lah! Ni fa ba da kai nake ba”.
Ya ce,
“To na yarda ba da ni kike ba, tadin zuci ne ko? Amma ya ya kike ganina cikin mafarkin? Da ‘ya’ya, da jikoki ko Rayhahhh?”
Muryarta na rawa cikin kidima da daburcewa ta ce,
“Don Allah zan kwanta, gobe (8 am) ina da test”.
“Da izinin wa za ki je yin test din?
Da kam kina bisa umarnin Daddy albarkacin cewa bana nan, amma yanzu na dawo, babu inda za ki kuma zuwa ba da amincewa ta ba, goben barin kasar ma zamu yi gobe insha Allahu......”
Ai dama kiris take jira, sai ta soma magana cikin son kecewa da kuka....,,
“Idan ka yi min hakan ka zalunce ni Ya Himu, na wahala a kan karatun nan, ga shi na ci karfinsa watanni tara suka rage min...”.Sai kuka.
Kyaleta ya yi ta yi ta yin abinta, bai kashe ba ita ma ba ta kashe ba. Gidan waya na ta kwasar kudi. Saida ta yi shiru don kanta, sannan ya sassauta murya.
“Na ce zan rabaki da karatunki ne?”
“Eh, ba haka ka ce ba?”
Ya ce cikin ‘yar dariya,
“Ni ban ce haka ba, barin Singapore na ce”.
“Eh mana, am not a kid, barin kasar na nufin barin karatun!”.
Murmushi ya yi mai sauti.
“Rayhanah bani da wannan amsar yanzu, muyi hirar da na ce muyi”.
Jikinta ya yi sanyi kamar ta soma rokonsa amma kawai sai ta fasa, muryarta abin tausayi ta ce,
“Tohh”.
“Has he ever held your hand?”
Da sauri kuma a razane ta ce,
“Wa?”
“Yaya Khalipha!”.

Wuta ta daukewa Rayhanah, ta rasa abin da za ta ce masa. Ba ta san sanda ta ce,
“Kai ka taba rike hannun Aunty Nabilah? Saboda kai ne ba ta so na!!!”.
Very shocked Ibrahim ya zama, ya dauke wuta dif! Ashe da wayonta take yin abu irin na yara, gidadawa. Kuma ashe har tayi masa farin sanin da har ta fahimci akwai wani abu tun tana karama tsakanin sa da Nabilah Abdulqadir. Yayi ta maza Ya ce,
“Ai ni namiji ne mijin mace hudu ne, ko na rike hannunta bani da laifi, tunda zan iya karawa da ita. Ke kuwa tare kuka balaga da Khalipha gida daya, ga soyayya da kusanci mai nisa a tsakaninku, INA KIIISHIIII Rayhanah.......!!! Has he ever did it???”
Duk da amsarsa ta farko ta bugi kirjinta, amma yadda ya yi sentence din karshe ya gigitata...... tana kokarin kashe wayar ya fadi da karfi.
“Kada ki kuskura ki kashe min waya Rayhanah..... zamu yi mummunar sabawa. Na ce Khalipha ya taba rike hannunki ko wani abu makamancin haka?”
Cikin rawar murya ta ce,
“Eh”.
“Sau nawa?”
“Sau daya ne Allah”.
“A ina?’
“A kafar benen gida”.
“Sai kuma me?”
“Wallahi Allah shi kenan”.
Sai ta fara kuka tun karfinta. Bata taba ganin irin wannan mutumin ba mai neman kada a zauna lafiya da titsiye no rhym no reason (babu gara babu dalili). Sai kawai ta ji ya kashe wayar.
Ba a jima ba ta ji shigowar mota harabar gidan, wayarta ta yi kara, shi din ne. Ta sake dagawa hannunta da jikinta duk suna rawa.

“Zo ki bude min kofa, bazan danna‘doorbell’ ba, kada in tada Inna”.
Ba karamin razana ta yi ba, da ta mike tsaye don cika umarninsa ji ta yi hajijiya na dibar ta. A haka ta bi bango ta fita daga dakin ta ratsa ta falo ta bude mishi kofar.
Kayan barci ne farare sol a jikinsa masu dan kauri. Ta ba shi hanya ya wuce cikin falon, amma ita ba ta matsa daga inda take ba, ta rabe a jikin kofar.
Ibraheem zama ya yi cikin tausasan kujerun falon ya nutsa hannuwansa cikin tarin sumar kansa, ya sunkuyar da kai ya yi shiru. Shudewar mintina goma a hakan sannan ya dago idanunsa jajir ya dube ta.
Tana rabe a jikin kofar kamar mai jiran ya gama abin da zai yi ya fita ta rufe kofarta. A zafafe ya ce,
“Ki daina yi min wannan kauyancin da gidadancin da kike mini, a Turai na ganki kina rayuwa cikin Singaporeans, har shigarsu kin iya, ba a Takai na dauko ki ba. Am not here for what you think, o.k?”
Ta sadda kai kasa. Hannunshi na dama ya mika mata......
“Zo mu yi hira!”
Jikinta na makyarkyata ta ce,
“Ni barci nake ji”.
“Tunda na kasa kema ba za ki iya ba”.
“Ya Himu don Allah ka zo ka tafi, Inna na fitowa alwalar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login