Showing 24001 words to 24347 words out of 24347 words
asubahi, don Allah ka rufa min asiri, cewa za ta yi ni na kirawo ka.....”
Halin da yake ciki bai hana shi yin dariya ba, gaba daya ta gama firgicewa kamar mai fargabar kada mijinta ya kamata da kwarto.
A tausashe ya ce,
“Zan tafi, but on one condition....”
Ido ta zazzaro masa tana jiran jin condition din. Hannu ya kara miko mata.
“I only want to kiss you again! Rayhaanah don Allah.....!! Zan miki addu’a Allah ya saki a aljanna!!!”.
Ba ta motsa daga inda take ba, sai shi din ne ya taso ya tako a hankali ya tadda ita har inda take. Irin rikon da ya yi mata da amsar da yayiwa bakin nata, ya tabbatar mata he will go far beyond abinda ya roka din, za ta gayawa aya zakinta idan ta sake ta bashi dama.
A lokacin ne Inna ta fito don yin alwala, ta kuwa yi kyakkyawan gani, sai ta juya a hankali da baya da baya har ta buge keyarta da kofa.
Sai karfe shida Ibrahim ya bar gidan. Jikinta babu sauran kuzari ta zauna a kujerar falon tana nemo consciousness din ta da diminishing gigicewarta. Sai da Inna ta tabbatar ya tafi sannan ta fito ta yi alwalarta ta wuce daki ko uffan bata ce mata ba.
A ranta addu’a take musu tana kuma roqon Allah da ya bawa Rahane soyayyar Ibrahim cikin sauki. Ba kamar yadda suke tararrabi ba itada Baba Dacta. Yasa abinda ta ganewa idonta yanzun haka yake har zuciyar Ibrahim!!!
Littafi Na 4 na dauke da karashen labarin kuma tare suke da Dan uwansa. Taku har abada;
Sumayyah Abdulqadir
( TAKORI).