Showing 9001 words to 12000 words out of 22282 words
mamaki tace"au yanzu nan Besty har yanzu baki tashi kinshiga wankanba kenan ƴan ɗaurin aure har sunfara taruwa ko sokike anguna suzo hotuna aga baki shiryaba ko wani abunke damunki ne".
"Besty yau narasa meke damuna tunda na tashi gabana ke faɗuwa a jikina inajin kamar wani abunke ƙoƙarin faruwa dani mara daɗi".
"kinsandai banaso kina ɓata ranki a banza nasandai duk wannan sanyin da jikinki keyi be wuce na rashin wayarku da mijinki ba kuma wallahi banajin Uncle Zaid zeƙi kiranki haka kurum nasan hidima ce tayimasa yawa shiyasa kidena damun kanki dan Allah insha Allahu ba abinda zefaru dake se alkhairi oh ni Hauwa'uh Besty kinfitsare idonki ko kunyata bakyaji hardamun kuka waikan bakiji mijinki inaga kuma anhaɗe anzama ɗaya ai se addu'ah sede mu rife idanunmu ".
murmushi da iyakarsa fatar baki Inteesar tayi tare da cewa"Allah ba haka bane Besty kawai dai yau tunda na tashi gabana ke faɗuwa".
"naji dai kitashi ki shirya ki yawaita addu'ah ko wani abunne zesameki sekiga abun yazo da sauƙi".
"tom Bestyna ammafa zanyi missing ɗinki".
taƙarasa zancenta murya na rawa hawaye na ƙoƙarin zubomata saurin juyar da fuska Hauwah tayi domin itama Hauwahn hawaye ne ya zubomata tayi saurin sharewa takama Inteesar seda takaita har bakin ƙofar toilet taga shigarta sannan takoma ta zube kan gado tashiga kukan rabuwa da aminiyartata seda tayi me isarta sannan ta buɗe kayan lefan Inteesar ta ɗakkomata wani dakakken les brown me tsadar gaske da mayafinsa da danƙareren gwal ɗin da aka sako a lefan da takalmi da jaka black tana fito wanka tashirya baƙaramin kyau tayiba Hafsat tayimata simple make up sosai tayi kyau kayan sunyi mugun amsar jikinta kamar angwadata hotuna Hauwah tashiga yimata nan sukaita hotunansu.
Abbih da Abban Zaid suna zaune a gurin ɗaurin aure Zaid yazo ya zube gabansu hawaye shaɓe-shaɓe ya haɗa hannuwa a gaban Abbansa alamun roƙo yace"dan Allah Abbah ka fahimceni wallahi inason Jameelah bazan iya rayuwa bataba".
murya a kausashe Abbah yace"ka mutu inkana iyawa sakarai kawai tashi kabani guri".
yaƙarasa zancensa rai ɓace yana nunamasa hanya dakatar dashi Abbih yayi ta hanyar cewa"subahanallahi ya yaro yana roƙonka kaƙi saurarensa wanne irin abune Abubakar seka tsaya ka fuskanci matsalarsa asamu solution ".
harar Zaid Alhaji Abubakar yayi tare da cewa"rankashidaɗe ka rabu dashi wannan sakarci yake ƙoƙarin tsiromun dashi wanda nikuma bazan lamunci hakanba".
"menene ke faruwa kuma wacece Jameelah kuma ko amarya ce".
"ƙanwar amaryar ce".
"bangane ba".
nan Alhaji Abubakar ya labartawa uban gidansa duk yadda sukayi da Zaid da safe sauke numfashi Abbih yayi tare da buɗar baki zeyi magana kenan sukaji muryar Abbansu Inteesar yace"aida Inteesar da Jameelah duk ɗayane Allah yasa haka shine mafi alkhairi nabashi Jameelah duniya da lahira itakuma Inteesar ɗin Allah yazaɓamata mafi alkhairi a gareta Alhaji kabarshi ya auri zaɓin ransa yanzu andena auren dole ga matama bare ga namiji".
"kwarai kuwa a ɗaura da Jameelah kawai itakuma Allah ya zaɓamata miji nagari".
cewar Abbih haɗa baki sukayi gurin cewa"Ameen ya Allah".
harar Zaid Abbansa yayi cikin ɓacin rai tare da cewa"hankalinka ya kwanta ka nunawa duniya ban isa dakaiba" .
"haba Abubakar kamar bakasan illar auren dole ba abarshi ya auri wadda yakeso".
"toh Allah yasa haka shine mafi alkhairi".
"Ameen ".
suka amsa gabaki ɗaya nan suka isa cikin mutane aka fara gabatar da ɗaurin aure kamar yadda addini ya tanaza nan aka ɗaura auren Jameelah da Zaid ɗaurin auren daya girgiza kowa na gurin akan sadaki dubu hamsin bayan angama ɗaurin auren ne jama'ah suka shiga ɗauro alwala domin gabatar da sallar juma'ah .
Abbih na alola yaji wasu maza biyu dake kusa dashi suna alola ɗaya yace"gaskiya ba'ah yiwa Inteesar adalciba daka gani kuma nasan sharrin Uwar Gwarama ne domin matar nan ba Allah a zuciyarta ba abinda bazata iyaba waƙilama gurin bokanta taje ya asircemata angonnan domin a kwanakin baya nazo wucewa naji ta tari angonnan tanata sukar Inteesar wai karya sake ya auri ragowar wani ita dake gwano beyajin warin jikinsa kaf faɗin unguwarnan ba wanda besan Jameelah ba akan bin maza a kamata da wannan akamata da wancan aiko inaji angonnan yacemata shi Inteesar ce tayimasa ba Jameelah ba kaga dake duniya ba gaskiya sun juyar masa da hankali ya aureta yarannan da uwarsu suna zama haƙuri a rayuwarsu harfa iƙirari takeyi da indai tana numfashi ko zata rasa zanin ɗaurawa bazata bari ƴaƴan Aminah suyi aure gidan da zasu huta ba ya Allah ka kawowa wannan bayi naka mafita cikin gaggawa".
"Ameen ya Allah insha Allahu itakuma seta kwashi kashinta a hannu tsinanniya kawai shiyasa ƴaƴanta duk bana zaɓa duk wanda yace tukunyar wani bazata tafasa ba shi tashi ko ɗumi bazatayi ba gata ga duniyar nan".
murmushi Abbih yayi kawai ya nufi cikin masallaci yana zama ya turawa Ammih test bajima da turawa ba takira tare da cewa"hakan yayi indai hakan baze haifar da matsala ba".
"babu komai insha Allah Ammih ".
"toh Allah yayimaka Albarka".
"Ameen".
nan ya kashe yana sakin murmushi yasamu liman sukayi magana sannan aka tada sallah ana idarwa liman ya tsaida mutane dake ƙoƙarin fita cikin laudspeaker yace"jama'ah kuɗan dakata munada wani ɗaurin auren".
kallon-kallo mutane suka shigayi nan su ƙannan Abbih suka iso da goro da alawa aka shiga rabawa jama'ah se mamaki sukeyi aka ɗaura auren Inteesar da Abdallah akan sadaki kujerar makkah guda huɗu kabbara ƴan masallaci suka shigayi mutane se murna sukeyi.
Zaune take a gefan gado tana yiwa ɗiyar Aunty Badi'ah wasa ta miƙawa Hauwah ita ta miƙe dan gyara ɗaurin zane sukaji muryar wani maroƙi yace!!!!!!!!!
Votes and Comments
_*Daga Alƙalamun ƴar Mutanen Gwarzo.*_
# Real eeshow
_*Paidbook ,Amount Nml grp 300,Vip 800, pc 1k, Account Detail 2411022356 Aisha Umar Ibrahim Zenith Bank, or Vtu mtn or airtel ga ƴan Niger kuma zaku turo da katin Airtel na daidai kuɗin da kikeson shiga aiko da shedar biyanka/biyanki ta wannan number 08108362334.*_
Book 2
4️⃣9️⃣➡️5️⃣0️⃣
" Masha Allah a yau mun sheda ɗaurin auren Inteesar da Abdallahi bangon sukari kowa ya raɓu dakai seya lasa namiji ɗaya tamkar da dubu lakadan ba ajalanba Zaidu da Jameelah akan sadaki dubu hamsin lakadan ba ajalanba munawa angwaye da amare fatan zaman lafiya Allah yabada zuri'ah ɗayyiba".
jikake luu ta faɗi a sume cikin tsananin tashin hsnkali gabaki ɗaya su Hauwah sukayi anta a ruɗe jijigata Hauwah tashiga yi tana kuka tana cewa"Bestyna ki tashi karki mutu kibarni nima bazan iya rayuwa ba".
tana kuka tana sambatu tana jijjiga Inteesar dako alamar numfashi babu a tare da ita cikin saurin Aunty Badi'ah ta nufi gurin pridge ɗinsu Hauwah ta ɗakko pure water me sanyi ta fasa tashiga yayyafawa Inteesar a jiki jan wani numfashi tayi me ƙarfi tare da miƙewa zaune ta fashe da wani marayan kuka tana cewa"Hauwah menayiwa Zaid dana cancanci irin wannan tozarcin daga garesa meye aibuna danya nuna yana sona na karɓesa ko inada wani aibune dase daka baya yaga nakasuna ya tsaneni meyasa zezo gareni danya jefani cikin wani hali menayimasa daya yaudareni a lokacin danake da buƙatarsa meyasa a rayuwata ni bani da sa'ah ne ya Allah ka ɗauki rayuwata na huta da wannan baƙar rayuwar da nike ciki meyasa Abbana zemun haka ya auramun wani can da bansanshiba abarni da abinda ke damuna man nasan tunda na rasa Zaid na rasa duk wani farinciki nawa dama zan mutu yanzu dana huta da
wannan masifar da nike ciki".
taƙarasa zancenta tana fashewa da wani marayan kuka meban tausayi cikin kuka Hauwah tace"Insha Allah Besty bazaki mutu yanzu ba sekinyi rayuwa me farinciki a rayuwarki Zaid kuma insha Allahu Allah seya sakamiki abinda yayimiki tsinanne mara imani bara naje gunsa ashe shiyasa yaketa faman yimana ƴan wulaƙance wulaƙancensa ashe da gadar daya taka wai a ina yasamu yarinyar daya aura ɗin kuma ya sunanta".
jin muryar Khadijah sukayi dake shigowa tace"Jameelah da kika fifita kikaita zagina akanta itace ta auri Zaid aikinga yanzu ta nunamiki baki da hankali ta auri muradin zuciyarki".
"what Jameelah kuma".
cewar Hauwah tana zaro ido tana kallon Khadijah samun guri Khadijah tayi ta zauna tare da cewa"eyi munada wata Jameelah ne bayan ta gidanmu itace ta aureshi aidama shi wanda ya nunamaka tun farko baya ƙaunarka to karka sake ka yarda dashi daka baya dan yazo ya nunamaka yana ƙaunarka to ƙarya yakeyi to kinga ashe datazo tayi kwance-kwance akan tadena duk abinda takemana harda kukanta akan mu yafemata ashe da plan ɗin data shirya shiyasa a lokacin nayita nunamiki kikaƙi fahimtata ke a tunaninki ƙinta nike duk abinda nakeyi inayinsa ne saboda farincikinki amma kikaƙi fahimtata harda dena yimun magana tokinga ai tayi maganinki cikin ruwan sanyi".
a zabure Hauwah tayi waje tana waje ta iske Zaid da abokansa sunata hotuna da Jameelah da ƙawayenta cikin annashuwa kamar ba abinda yafaru kallonsu tashigayi ɗaya bayan ɗaya taga ba Muhseen wani tuƙuƙin baƙin cikin Zaid ne ya tunƙure Hauwah tayi gurinsu rai ɓace.
Tana isa gaban Zaid ta nunashi da yatsa cikin tsananin ɓacin rai tace"kai la'ananne Allah baƙin munafuki mayaudari maha'inci wanda besan mutun kansa ba kai ko kunyar abinda ka aikata bakaji kanata raharka da mutane kamar baka aikatawa ƴar mutane komai ba insha Allahu haƙƙin Bestyna baze taɓa barinka kayi rayuwa da wannan maci amanar ba a tinanina naɗauka kunyar abinda kayi baze barka kazo gurin ɗaurin aure ba ashe dama can bada zuciya ɗaya kake son Bestyna ba mugu azzalumi mara imani wanda besan darajar ƙauna ba kekuma tinkiya kibar rawar ƙafa akan wannan bunsurun insha Allahu hakin ƙawata baze taɓa barinku kuyi farinciki ba tsinannu maciya amana insha Allahu auren Intee seya zamarmata alkhairi a rayuwarta ku kuma gaku ga duniyar nan".
a zafafe Zaid yakai hannu ze wanke Hauwah daketa danƙaramasu magana da mari seji yayi anriƙe hannunsa juyawarnan dazeyi sukayi ido huɗu da Muhseen daketa faman huci cikin kakkausar murya Muhseen yace"daka bari wannan banzan hannun naka ya taɓa tsarkakkiyar yarinyar dasena nunamaka true colour ɗina domin duk abinda takiraku dashi bawanda be cancanci da akiraku dashi ba domin gabaki ɗayanku kun kasance maciya amana musammanma kai baka cika ɗan halak ba mayaudari kawai wanda besan ciwon kansa ba".
cikin tsananin ɓacin rai Zaid yayi kan Muhseen zasu kacame da kokowa cikin kwarkwasa Jameelah daketa faman cin chewing gum ta rungume Zaid ta baya tare da narkar da murya cikin wani salo na ƴan bariki tace"ka rabu dasu Sweetheart banason kana gogamun tsarkakken jikinki daka daɗe kana tanazamun da jikinda ya daɗe yana kwasar zunubi ka rabu dasu kawai ƴan hassada ne magauta ne kasankuma shi mahaukaci duk inda kakai dashi seya nunamaka halinsa itakuma wannan ƴar koren wannan ƴar barikince da suka daɗe suna watsewa a titi shine da za'ah bugamaka ka auri fanko Allah ya tsareka daga sharrinsu ka hangoni me tarbiyya kuma nagadai duk baƙin cikinsu yanzu basu isa sun raba aurennanba anriga a shafa fatiha kaine dai se gani se hange daga nesa aje can gidan Almajiri a riƙa ɗumame koda sau ɗayane idanya samu domin almajirin da aka haɗata dashi ance gajanema ko gidan kansa bashi dashi kagako yadda akazo duniya a banza haka za'ah ƙare wofi da za'aimaka wayo anga inda za'asha jar miya har wani isa ake a cikin gida za'ah auri me kuɗi yanzu dai ƙarya taƙare sede aje gidan almajiri ayi isar me hujja kuma a tuɓemun kayan lefena tunda bame bara bane ya kawo ba ehe karuwan banza karuwan wofi saura kema ƴar korentata".
"naji ƴar korece ni gwarani banbar abun faɗaba a duniya dukko da yawon da kukeyi damu har yau ba'ah taɓa kamamu da wani ba kefa har duniya ta naɗe ɗan gaba da fatihar dakika haifa baze taɓa goguwa a idon duniya ba dukda ƙumuƙumun da kukayi kuka kasheshi".
Dariya rainin hankali Jameelah tayi tare da kallon Hauwah ta watsar takama hannun Zaid tace"Sweetheart ka rabu da wannan dirty girl ɗin harta fara haifarmun da ciwonkai ba wani abu ke dawainiya dasu ba face baƙin cikin Allah ya rufamun asiri na aure inda zan huta itakuma ƙawarta ta auri Almajiri wanda ko gidan kansa bashi dashi mubar gurinnan".
"wallahi kuwa Honey mema zanyi da wannan ƙarmasasshiyar ƙawartata data daɗe tana watsewa a titi ba abinda ke cikin yarinyar nan se rashin tarbiyya buhu-buhu bakiji warin da jikinta keyi ba saboda tsabar rashin tsafta".
"baƙin munafuki kasan da rashin tarbiyyartata kace kana sonta aiga me tarbiyya nan ka aura wadda har zuba takeyi a ƙasa tsabar tarbiyya insha Allahu kuma Almajirin da kuka raina seya baku mamaki ƴan iska a haka zaku watse da yardar Allah bazaku taɓa jin daɗin auren cin amanar da kukayi ba itakuma insha Allahu Inteesar se aurennan yazamarmata alkhairi".
"munji ɗin ƴan baƙinciki sede ku mutu".
suka juya da niyyar tafiya tafin da Inteesar keyi yasasu juyowa .
Murmushi me ciwo Inteesar tayi tare da cewa"Zaid nagode da abinda kayimun Allah ya saka da Alkhairi kema Jameelah nagode Allah ya saka da alkairi amma inaso Zaid ka rubuta ka aje kamar yadda nabar cikin uwata nabarka har abada kuma a tarayyata dakai idan har nina zalinceka ina roƙon Allah yabimaka kadinka idan kuma ni ka cuta na yafemaka amma dan Allah ina roƙonka wata alfarma kadena ɓatamun suna tunda dai Allah ya nufa niba matarka bace kayi haƙuri kabarni naji da abinda ke damuna haka hmm Jameelah kinbani mamaki kwarai dagaske akan abinda kika aikata saboda koda tambayata kikayi koda bani da abinda kike nema zan tayaki nemanshi bare mijin dazan aura nime iya barmiki namijice koda kuwa sunkai goma bare guda ɗaya daga ƙarshe ina tayaku murnar cikar burinku nasamun junanku a matsayin ma'aurata Allah ya sanya Alkairi yabaku zaman lafiya da zuri'ah tagari".
taƙarasa zancenta tare da juyawa zatabar gurin muryar Jameelah ce ta katseta mata hanzarinta dataji tace"Ameen dai kobada zuciya ɗaya kika faɗa idan kuma bekai zuci ba aniyarki tabiki kuma da kike cewa kinyafemana waye gaya muna neman yafiyarki ke awa sema mu da zamuce mun yafemiki saboda zalincin da kikayimana na rabamun da kikayi kika shiga tsakaninmu ko Honey kayan jikinki kuma kibarsu saboda nasan faƙirin almajirinnan naki ba lallai yasan irinsu ba kya riƙa yimasa kwalliya dasu".
"wallahi kuwa".
cewar Zaid daya zama tamkar raƙumi da akala tausayin Inteesar ne yakama kowa dake gurin jin duk sharrin dasu Jameelah kebinta dashi amma ita ta turamusu aniyarsu ta yafemusu murmushi me ciwo Inteesar tayi tare da cewa"nagode dabani kaya da kikace kinyi amma kibar abunki kya riƙa ko zaman gida dasu".
tana gama faɗin haka tayi wucewarta bin bayanta Hauwah tayi itama tsaki Muhseen yayi tare da cewa"kaidai kayi asara munafuki kawai".
yana gama faɗan haka ya wuce fuuu taɓe baki Jameelah tayi suka wuce abunsu cikin farinciki Abbih da Ammih dasukaji duk abinda yafaru ne sukayi dariya suka shiga jinjina dattakon da Inteesar tayi .
can na hango uwa a gurin jamila surika gurin Zaid anata gaisawa da mutane cikin annashuwa da farincikin burinta ya cika anata kawowa mutane abinci cikin kwanciyar hankali tana ƴan waƙe-waƙenta ana yadawa Umminsu Inteesar habaicin ƴarta anhaɗata da almajiri Dagauta ƙawar Uwar Gwarama ce tashigo tare da !!!!!!!!!!!
Votes and Comments
_*Daga Alƙalamun ƴar Mutanen Gwarzo.*_
# Real eeshow
_*Paidbook ,Amount Nml grp 300,Vip 800, pc 1k, Account Detail 2411022356 Aisha Umar Ibrahim Zenith Bank, or Vtu mtn or airtel ga ƴan Niger kuma zaku turo da katin Airtel na daidai kuɗin da kikeson shiga aiko da shedar biyanka/biyanki ta wannan number 08108362334.*_
Book 2
5️⃣1️⃣➡️5️⃣2️⃣
Sakin wata uwar buɗa Dagauta tayi cikin tsananin farinciki tace"Allah ya yarda raƙumi yaci ƙaya ƙawata Jameelah ansamu mijin wuce sa'ah amma gaskiya naji daɗin wannan abu Allah yaƙara bayyana gaskiya ya rabamu da aikin danasani wai ƙawata ya akai haka tafaru".
"Ameen dai Dagauta aikinsan duk abinda bana Allah da annabi bane baze taɓa ɗorewa ba yaron yagane shigo-shigo akemasa ba zurfi ana niyyar haɗashi da fanko kowa ya fargar dashi oho seji mukayi ayam anɗaura aure da Jameelah kinsan shi ƙaiƙayi dama kan masheƙiya yake komawa mugun abinda ake aikatawa ne yakoma inmiki tamasu iya magana sukance Allahn da ke bari se anje lahira amma na yanzu tun a duniya kake kwasar kashinka a hannunka wataƙila a gari yajiyo irin yawon barikin da akeyi shine yaga baze iya haɗa iri da irin tsiyaba shiyasa ya fasa shiyasa koda yaushe akeson kayiwa yaranka tarbiyyar arziƙi ba kullum kariƙa saka yaranka a gababa kana koyamusu baƙin hali ba kinsan mutum me farin jini daban yake dake Jameelah ni ta biyo kuma kinsan mutum yana kallon nagari baze ɗauki ɓatacce ba".
taƙarasa zancenta taname yaɓawa Umminsu Inteesar magana dake fitowa daga bayi hannunta riƙe da buta murmushi Ummih tayi ta wucesu Uwar Gwarama da harara tabi Ummih tare da cewa"tsinau iyalin kaɗa kawai muje Dagauta na zubamiki shaɓa-shaɓa kifara kwasa ".
"aiko dai amma kuma ƙawata naji ance itama Inteesar anɗaura mata aure".
"kwarai kuwa anɗauramata amma kuma ƙararrawarta akayi aka rasa me kwasheta dakyar wani almajiri yayi shahada ya aureta shima seda akayi da wajewa inba'ah bashi sadaka ba bayaso jin haka yasa Mallam saurin ansar zancen aka ɗaura kingako anyi faɗuwar baƙar tasa ba nauyi".
"wai kina nufin kicemun duk isa irin ta yarinyar nan sadaka aka bayar da ita".
"kwaraima kuwa ai yanzu ayi isar a gidan almajirin idan ansamu anbun sawa a bakin salati domin dai yadda ƴar ƴar ƙanwa take bani labarin Almajirin daya aureta ko azara ɗaya bashi da ita bare filin daze ginin yau ina tsananin farinciki mun yarda kwallon mangwaro mun huta da ƙuda waiwai shiru itama ɗayar zan gayawa Malam da ansamu hali itama ayi gwajonta ma huta da baƙar rashin kunya".
"aiko dai ƙawata muje ɗaka kizubamun nafara kwasa kya ƙarasa shaƙamun".
"aiko dai muje".
"toh ".
nan suka shiga ɗaki inda sauran mutane data gayyato suke nanta zubawa Dagauta shinkafa da miya da haɗin salat da nama se zoɓo washe jajayen haƙora Dagauta tayi tare da cewa"wai duk yaushe akayi wannan dabge daba'ah kirani ba".
"tun shekaran jiya nakai kayayyakin