Showing 63001 words to 66000 words out of 77617 words

Chapter 22 - Ciki Da Gaskiya Part 1 Complete Hausa Novel

06 Jan 2025

591

Anty Mamie akwai tausayi. Wannan yasaka hankalinta tashi tanufi gefin masu aikin taduba gwaggo bintu, ganin halin datake ciki yasakata kiran Hafiz yayi driving nasu zuwa asibiti itama tana nan tahowa zata gama wani aiki.

Hafiz yad'auki iya hama da gwaggo bintu dake kashir6an cikin halin rashin lfy yatafi.
Komai shiyayita k'ok'ari aka mata, har aka basu gado, sai a sannan Anty Mamie ta k'araso itada ya Zunnurain daya kawota.
Da taimakonsu aka kammala komai, gwaggo bintu tafara samun kulawa.



___________________________

Saida sukayi kuka mai isarsu sannan falon yay tsit, dad yace Abu miya dawo daku Kaduna? Nidai nasan harna bar k'asarnan kuna sokoto?.
Hawaye mama tashare, cikin nadamar abinda ta aikata tace yahaya ka gafarceni, tabbas ni azzalumace, kuma na cutar dakai kaida d'an uwanka.
Tabi su ya Naufal da kallo tana hawaye, tace bara nabaku labarin wacece zainabu 'Yar dije.


*Tuna baya*
Kamar yanda kuka sani mu 'yan asalin sokoto ne, amma a k'aramar hukumar Gwadabawa, Ni bama cikin gwadabawa nakeba, ina awani k'auyene Bamana, tallar kayan koli ke kawoni cikin gwadabawa, a k'auyenmu na Bamana babu Wanda baisan Zainabu 'Yar dije ba, tun ina k'aramata banajin magana, Dan ko'a gidanmu babu Wanda ya isa yasani nayi, babata dije bata yarda ko hararata ayiba agidan, kasancewar nikad'ai tahaifa aduniya.
Tallan kayan koli danake zagawa k'auyika da cikin gwadabawa yasaka idanuna suka k'ara bud'ewa, kokad'an bansan bariba.
Ayawon tallata nahad'u da Abdul'majedu, soyayya kuma tak'ullu a tsakaninmu, har akayi aurena da Abdul'majidu danginsa basason auren, musammanma yahaya, Dan yasanni sosai, idan nakawo talla har majalissarsu nake zuwa.
Wannan k'iyayya da yahaya ya nunamin yasakani tsanarsa, kokad'an bana raga masa bayan na auri yayansa, kullum babu abinda nakeyi sai had'asu fad'a, saidai abdul'majidu baya kulawa.
Hakan yana k'onamin rai, dan aganina Abdul'majidu yafison k'aninsa dani.
Saida mukayi shekaru goma bansami haihuwaba, zuwa sannan yahaya yayi aure. Harma matarsa tayi 6ari, 6arin datayi yatada hankalina, gashi tafini samun jin dad'i ajaken mijinta, hasalima arzik'insu mikeci.
Wata ranar talata muka tashi da alhinin rasuwar mahaifiyarsu yahaya, sosai yahaya yayi rawar gani akan hidimar rasuwarnan ta mahaifiyarsu, yabon da akaitama yahaya awajen rasuwar ya6ata raina Dan haka na kullaceshi a zuciyata.
Shiryawa nayi naje k'auyenmu, na fad'ama tsohuwata komai, ita tabani shawarar abinda yakamata nayi yahaya yabar gidan, shawararta kam tayi tasiri, Dan ina dawowa washe gari nakira yahaya d'akina akan zamuyi magana, lokacin Abdul'majidu baya gida.
Saida yashigo d'akina da sallama, ina la6e abayan labule nikam, yayta sallama nak'i na amsa mishi, saiya nemi guri ya zauna Dan azatonsa ina band'akine.
Ina nan ala6e ban fitoba saida naji motsin dawowar Abdul'majid, wuf nafito natsala ihu ina kiran kwarti-kwarto.
Kankace mi gida yacika da jama'a, yahaya dukya rud'e, mutane kuma sai tsinarsa sukeyi, babansu harda kuka da matarsa, awannan karonkam Abdul'majidu ya yarda yahaya yazo kwartanci d'akina.
Sannan ya haddasa fad'a sosai a tsakaninsu, ko kad'an Abdul'majidu yak'i sauraren yahaya, gashi ina k'ara kunna musu wuta daga gefe.
Matar yahaya kuwa takoma gida, tace bazata iya kallon wannan abin kunyaba, daga Bayama sai iyayenta suka nemi yasaketa.
Gwadabawa tayima yahaya zafi, babansu da yayansu suna fishi dashi, ga matarsa anrabasu, wannan yasa yashirya batareda sanin kowaba yabar Gwadabawa.
Wayyo hakan yamin dad'i, daga nan duniya tazama sabuwa agareni.
Shekarun yahaya kusan uku dabarin gida mukaji labarin wai wani Alhaji yatafi dashi k'asar waje, sai da naji babu dad'i, Dan banason naga yahaya yacigaba arayuwarsa.
Alokacin kuma gaskiya tafito. Mahaifinsu yahaya yasan gaskiyar magana akan tuggu nashiryama yahayan, abin ya6ata ransa, harya kwanta ciwon dayazama ajalinsa.
Tundaga rasuwar baba muka fara fuskantar matsaloli a k'auyenmu, sai zagina akeyi, shima kansa Abdul'majidu bai tsiraba, ahaka ALLAH yabamu ciki alokacin, munyi murna sosai kuwa, nahaihu da kwanaki 9 babata dije tarasu, nashiga tashin hanakali sosai, dama itace me k'arfafamu, aikam rasuwarta garin gwadabawa yagagaremu zama, dole muka d'akko d'iyarmu Suwaiba muka gudo sainan Kaduna...........
Kaf takwashe labarin zamansu na Kaduna tabamasu dad labari, harda barin Ameerah k'asar.
Da bala'in data shiga bayan tafiyar Ameerah, yanzuma basusan inda Suwaiba takeba, 'Daheera kuwa tazama 'Yar shaye-shaye, k'annen Ameerah biyu kam tuni suka koma sokoto, itakuma taita ciwo, dak'yar tasamu makwafcinsu ya taimaka mata zuwa asibiti, shine akace tanada ciwon sugar (diabetes), anasakamin dokoki akan abinda zan ringaci, amma nak'i bin doka, saboda lokacin duniya nakaimin, akwai kud'i a hannuna, shekara ta 2 kenan wani maruru yafitomin, yayi ruwa anmatse, amma saiya k'ara wani ruwan aka matse, yak'arayi, hakadai yayta girma harya zamemin gyanbo ak'afa, ganin k'afata zata ru6e nahad'a dukkan kaddarar dana siya dakud'in tafiyar amirah nasaida, shine makwafcin nan nawa mutumin kirki yasake kaini asibiti aka guntule k'afar, Dan since zata harbi dukkan jikina...
Tak'arshe maganar da rushewa da kuka.
Labarin ya girgiza su Naufal, mom kanta dabawani jin hausar takeba sosai saida tayi kuka, da mamakin wannan murd'ad'd'ar rayuwa.

Shima dad yabata labarin cigaban daya samu tundaga barinsa gida, har zuwansa turai, da karatu dayayi, yanuna mata matarsa daduk 'ya'yansa, harda had'uwar Naufal da Meerah a islands UK, Dama auren dake tskaninsu, harda k'yautar Raudat da ALLAH yabasu.
Mama tak'ara fashewa da kuka, da jinjina Girman mulkin ALLAH, tana Neman gafarar ameerah tana kuka, da nadamar abinda ta aikatama gudan jininta da kanta.

Ya Naufal yace nifa nayi mamakin irin wannan k'auna dake tsakaninmu da meerah, ashedai jininace ban saniba, ALLAH mai alkairi kenan, maji6incin al'amuran dake 6oye.
Mama kamar zata cinye Raudat danso, itace jikarta data fara gani aduniya, to cikin 'ya'yan natama wakeda niyyar aure, suwaiba ma Takai shekaru uku rabonta da gidan, 'Daheera kan saidai addu'a.
Hotel suka koma suka kwana, akabar meerah nan susha hirar yaushe gamo da mahaifiyarta.
Amma ina Raudat kuka takwanayi, zafi ya isheta, ga sauro, abinda bata Sababah.
Dole washe gari ya Naufal yanemo Generator da AC aka sakamusu, a daddafe sukayi kwana uku, washe gari kuma suka rankaya Kano da nufin idan sun dawo daga Raka Aysha Susan yanda zasuyi da mama, Dan baikamata abarta ananba.



*kano*
.................โœ




Kumuje zuwa Guy's๐Ÿ˜„, Sholyn Ku a kn๐Ÿ˜‰.











๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜˜
[8/25, 9:58 PM] Aisha Galadima: *_Typing๐Ÿ“ฒ_*



๐Ÿคฐ๐Ÿป
*_CIKI DA GASKIYA........_*
_{๐Ÿ”ชwuk'a bata hudashi๐Ÿ—ก}_



*_Bilyn Abdull ce๐Ÿค™๐Ÿป_*



*_NIKA'DAI WRITER ASSO........_*๐Ÿ˜œ


*_Sadaukarwa_*
_My sweet dady_
~(ALLAH ya gafarta maka)~
๐Ÿคฒ๐Ÿป๐Ÿ˜ญ



*_part 1_*
(littafi na d'aya๐Ÿ“•)


3โƒฃ5โƒฃ

Kano tadabo tunbin giwa, kofa dami kazo dagaske munfika๐Ÿ˜œ, amma banda tsiya๐Ÿค•.
Tunda akace sunshigo Kano farincikin Aysha ya bayyana, babu abinda kake gani tareda ita sai farin ciki tsantsa, itakam tsaf tagane gidansu, dukda canje-canje da'aka samu kuwa, gidanma gaba d'aya ya canja mata, danyasha sabon fenti sai d'aukar ido yakeyi, 'yan anguwa kam sai kalon zuk'a-zuk'an motocin sukeyi, hardasu Kansu masu motocin, ko kad'an babu wanda yagane Aysha, to yama za'ayi kad'auka Aysha bahaushiyace, balle tak'ara girma da k'yau, kaikace irin bak'ak'en Amurakawan nanne, itakam dayawansu ta shaidasu, saidai dukta mance sunansu, murmushi taketa zubawa abinta, dakanta tamusu jagora zuwa cikin gidan, tunda sukayi sallama tafara kwala kiran mama da Ummah.
Fadeela daketa faman jijjigar Ummu-hanee tana kuka talek'o Dan mamakin kiran da ake kwalama iyayen nata.
Tsam tatsaya tana tantama akan shin Aysha ce? Kokuma watace mai kama da Aysha?, gadai kamannina na Aysha ajikin matashiyar budurwar, amma ko dawasa ba'a fara kiranta Aysha ba.
Da gudu Aysha tak'arasa wajen Anty fadeelah, ta mamuk'eta tana ihun murnar ganinta, ihunne yatada Ummah dake barci saboda kanta dakeyin ciwo.
Ai Aysha naganin Umma tasaki Fadeelah taje ta d'are Ummah, wayyo ummanah nayi kewarki wlhy.
Ummah tarungume Aysha, hawaye nazuba a kumatunta tace Aysha dagaske kece? Dama zaki dawo garemu? Shikenan babuke babu bintu?.
Meerah mom ifteehal natsaye suna kallonsu cikin burgewa.
Dad da Naufal maheer suna k'ofar gida suna jiran amusu iso.
Fadeelah Ce taimasu mom marhabun, aka shiga dasu falon Ummah, haryanzu Aysha na nane da Ummah, sai tanbayar mama takeyi, babudai Wanda yabata amsa.
Bayan zamansu ne fadeelah takawo musu ruwa, Ummah kuma takira number mijinta da kawu bilyamin, hardasu Qasim yayunta wad'anda aketa shirin bikinsu.
Aysha tak'ara fad'in Umma wai ina mama?.
'Yar dariya Ummah tayi. Tace Aysha mama na Abuja abinta.
Abuja kuma Ummah? to wajen wa?.
Aure takeyi, Ummah tafad'a tak'aice.
Nan take fuskar Aysha ta canja, idonta tab da kwallah tace aurefa Ummah?. Kishin sosai a idanun Aysha tana taya mahaifinsu kishi.
Babu Wanda hace komai saboda shigowar Mijin mama da kawu bilyamin, saisu dad dake binsu abaya.

Gaishe gaishe aka fara, kowa sai d'okin ganin Aysha yakeyi, ita kuma tana jikin Ummah rik'eda Ummu-hanee.
Su dad sunyima su kawu bilya bayani akan Aysha, amma sun 6oye komai kamar yanda Aysha tabuk'ata, Dan so take da kanta tad'au mataki akan su gwaggo bintu.
Sunce Aysha karatu taje, kuma tun farko a hannunsu take, kowa yaji dad'i kuwa, sunsha godiya sosai.
Kafin kacemi anhad'a musu cima mai k'yau da gamsarwa.
Dukda bawani sabawa da cimar sukayiba sunci babu laifi, ita kanta Aysha ta fara manta cimar k'asarta, (kowa yabar gida, aii dolene gida yabarsa)..
Aranar aka kira mama aka sanar da'ita dawowar Aysha, tayi farinciki, jitake kamar tayi tsuntsuwa taganta a Kano, lokacin suna shirin zuwa asibiti duba gwaggo bintu.
Tace zata taho Kano gobe idan ALLAH ya kaimu.
Kawu bilyamin yace a'a tayi hak'uri, insha ALLAH nanda kwana uku za'a kawo mata Aysha har gida.
Wannanne yasakata hak'ura da zuwan.
Aranar su dad suka baro Kano, Aysha harda kuka dazasu taho, sunyi sallama akan saita zo Abuja, suma daga nan Kaduna zasu tsaya, sai zuwa jibi zasu shiga Abuja, daga nan zasuje sokoto ma.

Zuwa yamma saiga Hafsat, su Rufaida da sadiya ma saigasu, gida yagama had'uwa, Aysha tana tsakkiyar danginta, jitake kamar ta shekara dubu basa tare, sukam sai sha'awarta sukeyi, danta canja musu gaba d'aya, saikace wata baturiya, anyi-anyi takira mama tak'i, dukda d'okin ganinta datakeyi wai fushi takeyi da ita akan tayi aure, hakama Ummah duk haushi suke bata ita adole kishin babansu takeyi.
Makwafta sai shugowa akeyi ganin Aysha 'Yar turai, kai kace wani abin kallo aka kawo gidan.
Koda yake Aysharfa ta cancanci azo kallonta, Dan komai nata ya canja, dolene kaganta ta burgeka harka lalace wajen kallonta.
Har washe gari bata canja zaniba, 'yan uwa sai tururuwar zuwa ganin Aysha akeyi, itakam kowa yazo kar6ar mutumci take masa, dama can ba halin Aysha bane wulak'anta jama'a.


_____________________________
Su mama sun isa asibiti itada Anty Mamie domin duba bintu.
Saida doctor d'in dake dubata yafito sannan suka shiga, gwaggo bintu na zaune akan gado, ta jingina da filo, bishirah nabata abinci, sallama dasu mama sukayice tasakata d'ago ido tana kallonsu da amsa sallamar ahankali.
Ganin mama yasaka gwaggo bintu wata zabura, har taune harshe takeyi wajen fad'in fad'ima! Kece?.
Mama ma tace, "bintu! Dama kece mara lafiyar?".
Hawayene suka shiga zarya a kumatun gwaggo bintu alokacin data tsinkayi muryar Anty Mamie na fad'a mata aii itace Baffansu ya aura kwanaki ko, kuma matarsace tunkan ya aureta, jikinta sai rawa yakeyi, tabbas tasan mama tata6a aure kafin ta auri yayansu, kenan Alhaji Abdallah jigawane dama tsohon mijin nata?, nan take zufa tafara ambaliya akowane sashe najikin gwaggo bintu, fad'i take a zuciyarta nashiga uku ni binta, yanzu yazanyi da wannan kulli? Ina zan samoma matarnan 'yarta? Nasan dolene ta tambayi ina Aysha, ni bintu nashiga Tara, nikuma k'arshena yazo kenan, hajia babba kin cuceni keda shaid'anin daya bani k'arfin guywar yarda daku.
Babu Wanda yazargi wani Abu tsakanin Anty Mamie da mama, duk zatonsu ciwon ne yake damunta, dukda mama tana ganin kamar mamaki gwaggo bintu tayi dakasancewarta matar mai gidanta.
Sunkai mintuna 30 a d'akina sannan sukai musu sallama suka fito, amota mama take sanarma Anty Mamie dangan takar dake tsakaninta da gwaggo bintu (wadda suke kira Maman yara), Mamie tayi dariya, tace haba shiyyasa naga ta nuna mamakinta da ganinki, lallai ALLAH kenen mai hikima.
Mama tace aikuwa dai, (bata fad'ama Mamie komaiba dangane da rashin k'aunar da gwaggo bintu take nuna mata, lokacinda tana matar yayanta).
Harda sukazo gida abin na'a zuciyar mama, amma bata damuba, tunda alhamdulillah 'yarta tadawo gareta.
Gobe idan ALLAH ya kaimuma, zatazo Abuja itada fadeelah.



_____________________________

Washe gari Aysha da fadelah sukayi shirin zuwa Abuja, da mortar haya zasu hawo, amma sai kawu bilyamin yabada motarsa akaisu.
Hakan yayma Aysha dad'i, dan dama batason hawa motar hayar.
Kasancewar tafiyar yamma sukayi sai around 6:30 suka iso anguwar ta mai-tama. Gaban Aysha ne yaketa luguden fad'uwa tunda suka shigo anguwar, danta gane anguwar data zaunace kafin barinta k'asar, mamakine ya isheta akan miya kawo mama nan?, batama tsinkeba saida taga mortar tatsaya k'ofar gidan alhaji Abdallah Jigawa tana horn, kallon fadeelah tayi, tace Yaya fadeelah anan mama take aure?.
Eh, nanne Aysha, fadelah tafad'a kanta tsaye.
Shiru Aysha tayi tana had'iyar yawu, aranta tace *Cakwakiya kenan*, lallai nabar *baya da k'ura*, wannanfa shine *Kwai cikin k'aya*.๐Ÿคฅ
Abubuwa dayawa sun canjama Aysha, bakamar zuwanta da gwaggo bintu ba, taga ancanja gate d'in gidan, hakama ansamu wasu sauye-sauye, fentin gidanma bawanda tasani baneba.dukda sun isa ana shirin magriba ne hakan bai hana anguwar kasancewa cikin hasken wutar lantarkiba, ko ina farr da haske.
'Dan gwari mai gadi dai haryanzu shine gateman d'in gidan, amma yad'an kara manyanta, bakamar sanda Aysha ta sanshiba.
Aharabar gidan baba bala yayi fakin, kamar ankwashema Aysha jini haka tafito daga motar, handbags nasu kawai suka d'auka, sauran kayan baba bala yace suje za'a shigo dasu, fadeela sai zumud'in Shiga takeyi dantayi kewar mama, amma ga Aysha Sam abin Bahaka baneba, tafiya takeyi kwakwalwarta na tariyo mata baya, jitakeyi kamar yauma tazo gidanne amatsayin boyi-boyi Mara 'yanci.
Rungumetan da akayine yasakata sakin ajiyar zuciya da d'ago kanta, Ashe harsun shigo falon batama saniba, mamace tarungume Aysha cikin matuk'ar kewar 'Yar d'iyar tata, itama Aysha ganin haka saita k'ank'ame Maman tareda sakin wani irin kuka dabasan dalilinsaba.
Fadeelah dai 'Yar kallo takoma.
Babu kowa a falon, Duk sun shige d'akuna Dan gabatar da sallah, 'yan uku ne kawai ke k'iriniyarsu.
6angaren mama suka yanda zango, saboda tsabar farinciki mama tama kasama Aysha magana, sai kallonta takeyi tana zuba murmushi.
Ayshar Ce tagaji tace Mamana nayi kewarki, ina sonki, amma shine kikayi aure bansaniba ko? Tak'are maganar da turo Baki gaba.
Daga fadeelah har mama abin yabasu dariya, Dan haka suka dara abinsu.
Mama tace to Aysha ayima mama afuwa, nasan kina kishin babankune, amma inaso kiyarda da k'addara, haka ALLAH ya hukunta mana, nima bawai da son raina baneba kinji.
Aysha ta jinjina kanta, saitaji tama daina jin haushin mamar, wanka sukayi sukai salloli, mama tayima umma-hanee itama, 'yan uku na nane zasu Aysha, Aysha sai dad'i takeji suma yanzu mama ta haifesu dayawa, gata da k'anne maza, abinda tadad'e tana sha'awa kenan.
Bayan sunci abincin da mama ta shirya musu suka mik'e danzuwa gaida mutan gidan, harsun fara shirin Fita saiga Anty Mamie tashigo, a'a inakuma zakuje?.
Fadeelah tace zamuzo gaishekune Mamie.
A'a fadeelah kuzauna Ku huta, wanan wahalar tafiya aii tayi yawa, da safe sai'a gaisa aii, nima sallah natsaya yi shiyyasa ban lek'oba tunda kuka shigo, Dan 'yan uku sunkaimin labari.
Mama tayi dariya, aii wad'annan 'ya'yan naki bilkesu sune redio mai jini.
Mamie ma dariya tayi, tace a'a a'a, ai abunda suka gani suke fad'a.
Aysha sai kallon Mamie takeyi tanajin k'aunar matar aranta, amma talura bata ganetaba, taji dad'in hakan, Dan dama bata fata kowa yaganeta agidan, hakanne zai bata damar aiwatar da aikinta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login