Showing 69001 words to 72000 words out of 77617 words
ba, ganin tamak'i juyowa ransa yafara 6aci, k! Banason iskancifa, bakiji minacebane?.
Jiki a sanyaye Aysha tajuyo gareshi, wata 'Yar zabura ta mamaki yayi, yanunata da d'anyatsa zaiyi magana kenan saigasu Maleeka sun fito, 6oyayyar ajiyar zuciya ya sauke, ya wayance dafad'in k! Kikawomin tea.
Yana gama fad'a yakama hannun Adeel da Affan zuwa 6angarensu, Haleefa nabinsu abaya a6oye.
Itama Aysha ajiyar zuciyar ta sauke ahankali, su maleeka kam sai dariya suke saukewa, Tasleem tace kije kicika aikin oga, Dan wlhy ya khaleel babu ruwansa da bakuwa, kuma tunda ke yace babu Wanda zaikai shayin baikusa cinyeshi da jarabar masifarsaba, kema daga nan kun k'ullah kenan.
Miya farune? Mama dake fitowa ta tambaya.
Tasleem tafad'a mata ya khaleel ne yace Aysha takai masa tea.
Mama tace to shine take tsaye kuma? Kiwuce yana nan nama dafa masa tun d'azun, dan naga zaije masallacine shiyyasa ba'a kaiba.
Kamar Aysha zata fasa kuka haka takeji, kicin d'in taje ta d'akko k'aramin tire mai d'aukeda falas d'in tea, sai mug da cokali k'arami.
Falon tadawo tana tura baki gaba, tace, maleeka rakani, nibansan d'akinsaba.
Hararta mama tayi, tace kishiga nan aibazaki rasa d'akinba, anty Mamie data fito tace a'a Yaya fad'ema, kibari ta nuna mata, in bandama abin babana yazakasaka bak'uwa aiki, ai saiya bari tad'an k'ara kwana biyu ko.
Mama tace ko zuwanta kenan gidan yasakata aiki badole ta ajiye jakka tayiba, tayi shigewarta kichin.
Maleeka taraka Aysha 6angarensu samarin gidan, bin komai Aysha takeyi da kallo, komai Na falon bawanda tasani baneba, ancanja komai, saidai fes yake tamkar yamda tasani abaya, ak'ofar d'akin ya khaleel maleeka tatsaya, tace gashinan.
Aysha ta langa6e kanta tamkar zatayi kuka, kai maleeka please kirakani mana.
Idanu maleeka tazaro, kai Aysha rufamin asiri, tunda ke yasaka aikin walhy naje yanzu saiyaci k'aniyata, kedai jeki zan jiraki afalo, aii babu abinda zai miki, shifa sai an ta6ashi yake fad'a, kuma ma su Adeel suna wajensa aii.
Babu Wanda Aysha zatayi haka taja k'afa tamkar wadda kwai yafashema aciki, ciki-ciki tayi sallamar, yana zaune akan sofa, dagashi sai wando 3quarter da vest fara k'al, duk su Adeel suna jikinsa, ya ajiye musu lap-top d'insa suna kallon cartoon, shikuma idonsa a wayarsa yana danne-danne.
Rumtse ido Aysha tayi gabanta Na fad'uwa, bak'aramar firgita tayiba daganinsa haka, Dan damtsen hannunsa yamugun tsoratata, tai saurin kauda kanta daga kallonsa.
Har yanzu idonsa nakan waya, su Affan ko bama susan tashigoba, kallon cartoon yad'auke hankalinsu.
K! Idan bazaki ajiyeba ki koma dashi.
Haushi yaso kama Aysha, amma saita dake, tajawo k'aramin glass table dake gefensa tad'ora, saida tafara tafiya takusa k'ofar fita yace dawo. murgud'a bakinta tayi sannan tajuyo, alokacin kuma yad'ago suka had'a ido, Aysha tayi saurin janye nata, tunba yanzuba wlhy tsoron mayun idanun nan nasa takeyi, gashi yanzu sund'an shanye alamar haryanzu akwai sauran gajiya taredashi.
Kafeta tayayi da idon nasa, wannan yasakata gaza koda satar kallonsa, tambayar daya jeho matace tasakata d'agowar dole.
K wacece!?
Batasan sanda bakinta yasu6ce tace kamarya? Ni wacece?, ni mutumce mana, tak'arashe maganar da murgud'a baki.
Aransa yace akwaifa rashin kunya buhu-buhu awajen yarinyarnan..
Afili kuma saiya gallah mata harara, k banason tsiwa, mikikazo yi gidanmu?.
Baki Aysha taturo gaba, cikin shagwa6a tace nima kuma gidanmune, ahankali tace bare amin gori.
Su Halefa dake jikinsane yahanasa tashi, dasai ya saita bakin yarinyarnan wlhy, amma cikin tsawa yace anturokine lek'en asirina ko? Shiyyasa kike bibiyata?.
Aysha batasan sanda tasaki wani mugun murmushiba, harta samu kwarin guywar kallon cikin idonsa, amma kwarjinin dake taredashi yasakata saurin janye idon nata, da gudu tabar d'akin batareda ta bashi amsaba.
Kuttt! Yafad'a yana binta da kallo, yana rasa mizaice, saikawai yaja ajiyar zuciya, dolenema yayi bincike akan yarinyarnan, danyasan wacece ita?, shifa mamaki take basa, saikace aljana, tunda yake babu macen data ta6a kallon tsakkiyar idonsa sai yarinyarnan, duk girman mace kwarjini yake mata takasa masa kallon minti2 ma, bare cikin idonsa, duk jidakan yarinya da isarta, inhar zatazo wajensa tace tana sonsa, kotazo suyi wata magana, wlhy inhar yadasa mata idonsannan na 1minute kawai saikaga jikinta narawa, tashiga hankalinta daganin bakin Rijiya bawajen wasan makaho baneba.
Amma yau ga yarinya k'arama, wadda k'annensa nawajen 15 sun girmeta, ta kalli tsakkiyar idonsa.
Ya furzar da huci daga bakinsa, Wanda yasaka su Affan kallonsa.
Aysha kam koda suka koma babban falon wajen sauran yaran, batawani dad'e Na firaba tatashi takoma d'akin mama, firarce ta'isheta, dama can Aysha bamai son hayaniya baceba, Anty meerah takira sukasha hirarsu, wai gobe idan ALLAH ya kaimu zasu dawo daga Kd, harda mama Dan dad yabiya za'a kaita india asaka mata k'afar roba.
Aysha tayi farinciki sosai, Dan mama tabata tausayi, rashin k'afa bala'ine.
Fadeela zuwa tayi tad'auki kayan barcinta Dana Ummuhanee, d'akinsu Amal zata kwana, Aysha tace aii ina gadon uwata, saida safenki.
Bayan tafiyar fadeela mama tashigo ta kimtsa, baffah yadawo yanzu babu dad'ewa, kuma girkin mamane.
Ganin haka Aysha tace aikam bara Na shirya Nima d'akinsu Tasleem zanje Na kwana, bazan kwana nikad'aiba.
Mama tace a'a kiyi kwanciyarki, inasu Affan? Basai Ku kwana tareba.
Mama suna d'akin wannanfa mutumin, kuma k'ila a can zasu kwana.
Waye mutumi? Mama ta tambaya tana fesa turare.
Wanda yace nakai masa tea d'azun.
Zai dawo dasu indai babana ne, idan yana gida dama canne wajen hirarsu tunma basukai hakaba, dayaga sunyi barci zakiga ya kawosu. Mama bata jira amsar aysharba tafice abinta zuwa 6angaren baffa.
Mama nafita Aysha tamik'e tashiga wanka, bayan tafito tashirya cikin wando dogo da Riga Na cartoon kalar popul, sunmata kyau, tana gaban mudubi tana tufk'e gashinta Dan bataso tayi barci dashi ahaka, yaturo k'ofar yashigo, da sauri Aysha tajuya tana kallonsa.
'Dauke yake da haleefa da Adeel a kafad'a, sa6anin d'azun yanzu yasaka doguwar jallabiya, Affan nabiye dashi abaya, da'ala shi baiyi barcinba.
Ko kallonta baiyiba yad'orasu a gadon mama, saida yagyara musu kwanciya sannan yanufi Waldrop d'insu ya d'akkomusu kayan barci.
Mamaki dukya cika Aysha, aranta tace irin wannan samun waje haka.
Tana jingine da madubi tana satar kallonsu ya canjama yaran kayan barci su duka, sannan yamusu addu'ar barci ya shafa musu, Affan yace Yaya ni awajenka Jan kana.
Murmushi yayi tareda jawo yaron jikinsa, yace haba my lil bro d'ina, kaga zomu kwanta, nima yau a gadon mama zan kwana, amamakin Aysha saitaga ya kwantar da yaron a jikinsa shima yaja filo ya kwanta, ahankali yake bubbuga bayan yaron idonsa a lumshe
Aysha samun kanta tayi da sak'a wani Abu a zuciyarta, tasaki sassanyan murmushi, jitake inama tunanin nata yazama gaskiya.
Duk abinda takeyi ya khaleel Na kallonta ta k'asan idonsa, bakinsa yata6e ya kauda kansa daga kallon nata.
Saida ya tabbatar barcin Affan yayi nisa sannan ya kwantar dashi kusadasu Adeel yakuma yimusu addu'a yarufesu da bargo yafice abinsa, batareda ya nuna yamasan dawata hallita a d'akinba.
Da uwar harara Aysha taraka bayansa harya fita.
Yana fita tafad'a gadon tareda jawo filon daya d'ora kansa ta rungume tareda lumshe manyan idanunta, jitake kamar ya khaleel ta rungume, ga sassanyan k'amshin turarensa natashi ahankali, shidai baka ta6a cewa wannan shine turarensa Na dindin din.
Shima yana fita 6angaren mom yanufa.
Babu kowa afalon sai Mufeeda dake barci, itama nakula bawai barcin takeyiba, takune kawai naneman hanyar dazata fita anjima wajen saurayinta atafi shek'e ayar da'aka saba, Dan batama San ya khaleel yadawoba.
Ganinsa yasaka gabanta fad'uwa, amma saitayi lamo kamar tana barci.
Tashinta yayi yace tashiga d'aki, tatashi tana wani Mirza ido, kaikace gaske barcin takeyi, lah ya khaleel yaushe kadawo?.
d'azun. Yafad'a a tak'aice.
Yace Momy fa?.
Takwanta tun d'azun saboda tagaji tace, su Hasnama sun kwanta.
Yace kema shige ki kwanta.
Ranta A6ace tashige d'akinta, amma tana addu'ar ALLAH yasa fita zaiyi.
Samun kansa yayi dason zama afalon, saboda American film d'in dasuke nunawa a Fation yamasa k'yau, yad'auki remote d'in yakoma saman 3seter ya kwanta.
Kamar mufeeda zata fasa ihu haka taji, gabanta yaywata muguwar fad'uwa lokacim datajiyo wringing d'in wayarta dake gefen ya khaleel..................βπΏ
πππππβπ»
[8/28, 8:09 PM] Aisha Galadima: *_Typingπ²_*
π€°π»
*_CIKI DA GASKIYA........_*
_{πͺwuk'a bata hudashiπ‘}_
*_Bilyn Abdull ceπ€π»_*
*_NIKA'DAI WRITER ASSO........_*π
*_Sadaukarwa_*
_My sweet dady_
~(ALLAH ya gafarta maka)~
π€²π»π
*_part 1_*
(littafi na d'ayaπ)
3β£8β£
Biris yayi da wayar yacigaba da kallonsa, harta yanke aka kuma kira Na 2, kiran daya kuma shigowane yahasala zuciyarsa, wani uban tsaki yasaki, tareda kwala kiran mufeedah!!.
Dama tana la6e, jin kiran daya kwala mata yasaka 'yan hanjinta wuntsilawa, afili tace shikenan namutu yau, wlhy ya khaleel kasheni zaiyi kawai.
Wai dan ubanki bakiranki nakeyibane.
Jikinta narawa tafito, sai mutstsuka ido takeyi alamar abarci tataso, yawatsa mata wata harara da mayun idanun nan nasa, jitayi tamkar tasaki fitsari awajen.
'Dauka wayarki kibarnan kafin namiki dukan mutuwa.
Aibama tabari yak'arsa fad'a tafisgi wayar dasauri ta runtuma da gudu tana mai godema ALLAH daya tserar da ita.
Tana shiga d'aki aka sake kira, d'agawa tayi dasauri, har taune le6enta nak'asa takeyi wajen saurin yin magana, haba babie tunda kaga kayi kiran farko ban d'agaba aikasan akwai matsala, yanzu dakaja ya khaleel yad'auki wayar yaduba wlhy da daga ni har kai mungama yawo.
Wai kina nufin wayar tana hannunsa?.
A'a tana kusadashine.........tabashi labari..
Ajiyar zuciya yasauke, kai my mufeey ALLAH ya taimakemu, wlhy karkiji wasa tsoron yayan nan naki nakeji, bashida mutunci idan kafad'a tarkonsa, ga wani abokina nan agidan yari zai k'are rayuwarsa ta dalilin yayanki.
Kai kajimin, ainasan laifi yayi yakamashi, Dan ya khaleel akan aikinsane kawai hakan kefaruwa tsakaninsa da mutane, saikuma mu k'annensa dayakeyi Dan kulada tarbiyyarmu.
Hakane, yanzu yaza'ayi kenan?.
Tab ai wlhy yau saidai mud'auki Na Annabawa, Dan yana falonmu zaunema yana kallo, nibanma San yadawo k'asarba.
To shikenan saida safe.
Baijira cewartaba ya yanke wayar yana mitar saidai ke, amma wlhy nikam sainaje Na more, ga 'yan mata nan buhu-buhu a birnin Abuja.
Bai bar falonba saida film d'in yak'are, sanda yafitama mufeedah tagaji da la6e-la6enta tayi barci.
*_Washe gari_*
Har 8:30am Aysha bata tashiba, tuni su Affan sunbar d'akin, ita kad'ai taketa juye-juyenta a gado.
Kowa ya hallara a dining har baffah kasancewar weekend ne, Ammah ce kawai babu tana Jigawa abinta.
Anty Mamie takalli dukkan yaran babu Aysha da ya khaleel, har mufeedah dasu hasnah suna nan, Dan dolene suzo tunda harda baffah, gakuma zakin gidan yana nan, Momy dama saita gadama take cin abinci dasu, babu kuma ya Sultan da ya mujahedeen, sunacan 6angarensu da matansu.
Muslim tashi kakira babana, kekuma maleeka kira Aysha.
Da to suka amsa.
Babu dad'ewa saiga ya khaleel sunfito shida musleem, har k'asa ya durk'usa ya gaida iyayen nasa, k'annensa suka gaisheshi.
Yaja kujerar ya zauna, saida mama takuma aika tasleem sannan su Aysha suka fito, da alama saida maleeka tasha dagama wajen tashin Aysha, dan kayan barcinema ajikinta sai hijjab data d'ora iya kugu a saman kayan barcin, daka kalli idonta kasan yanzu tatashi a barci, saboda akwai ja acikinsu, gasukama sun k'ara zama manya, durk'usawa tayi tagaida baffah, ya amsa cikin fara'a, harda dafa kanta yana mata lale marhabun dadawowarta kasarta, (dan mama tayi masa bayanin komai dangane da dawowar Aysha kasar dakuma zuwansu itada fadeelah, shikam yace Aysha tazo kenan, dan bazata koma kanoba, tunda yaso adawo da Ummulkhairi nan amma kawu bilyamin yabashi hak'uri saboda tana hannun uncle Ahmad ne, to yanzu kam shima tashi d'iyar tadawo gareshi acewarsa, mama dai dariya kawai tayi, amma ak'asan ranta tafiso Aysha tayi aure, dan tasan mijin nata akwai son karatu, harma tambayarta matakin karatun ayshar yayi, tace, "wlhy bata saniba, saidai ya tambayrta".)
Ta gaida Anty Mamie da umme Amarya, sannan tagaida sauran samarin gidan da 'yan mata, babu Wanda yaganeta, amma dai musleem ya kafeta da idanu.
Baffah yace tashi kizauna d'iyata yanuna mata kujera d'aya data rage wadda take kusada ya khaleel.
Jitayi tamkar tafasa ihu, amma babu damar hakan, dan baffah kallon mahaifi take masa ba mijin uwa ba.
Haka ta zauna duk atakure, bayan mama tagama had'ama baffah abincinsa ta zubama Anty Mamie da umme Amarya, tazubama kanta, Aysha dake kusada ya khaleel tace tatashi ta had'a masa shima, bak'aramar kid'ima zancen Maman yasakataba, dukda wani sashe Na zuciyarta yana farinciki.
Babu yanda zatayi tahad'a masa komai, yanata danna waya abinsa tamkar baisan mi'akeyi a dining d'inba, tana gamawa tazagaya tazubama ya Zunnurain da ya Ramadan, ta iso kan Musleem daketa kallonta tun d'azun, magana yay mata k'asa-k'asa batareda kowa yajishiba, _Ammafa kin had'u wlhy_, Aysha tayi murmushi, itama tace kaima haka ya musleem.
Tsayawa yayi cak daga danna wayarsa, yad'ago fararen idanunsa yakafe Aysha da musleem da idanu, Muhsen ne yalura da kallon da ya khaleel yakeyi, ya zunguri musleem, kai Malam ka kulafa, babban Yaya yana harararka.
Da sauri musleem yad'ago suka kuwa had'a ido da shi, ya watsa masa uwar harara, kasa dakai musleem yayi damamakin hararar, babu yanda za'ayi yace yaji maganar dayakeyi da yarinyar. Amma irin sannan uwar harara haka.
Ita Aysha ma tuni tayi gaba, harta zubama Hafiz, tana kaiwa kan mufeedah ta ajiye bowl d'in hannunta tadawo wajen zamanta.
Wani tuk'in bak'in ciki yatokare makoshin mufeedah, wai agola tazo tana nuna musu Isa, wadda in auren wuri tayi saita kusa haihuwar kamarta.
Aysha kam ko'a kwalar rigarta, dan ita duk abinda yashafi hajia babba ta tsaneshi, ya khaleel ne kawai yafita zakka acikinsu.
Kowa yagama zuba abincin baffah yay bismillah, kowa yayi aka fara break, Aysha dukata takura, sai juya cokalin takeyi, shikam wandama takeyi da shi ko'a kwalar rigarsa, abincinsa yakeci hankali kwance, duk sanda zata d'ago saisun had'a ido da Musleem da Zunnurain, saita kuma zama atakure, tarasa wannan kallon kurullah dasuke jifanta da shi, hakadai aka kammala cin abincin kowa yafara kama gabansa Aysha bata wani ci abin kirkiba.
Itace ta biyard'in mik'ewa.
Hartaja kujerarta baya tamike tajiyo muryarsa yana fad'in dawo ki zaune.
Kowa saida yad'ago ya kalleshi, Aysha datasan da ita yake tayi kamar bata ganeba tafara tafiya, da d'an k'arfi yace Aee'sha dake nake.
Yanda yakira sunan saida tsigar jikin Aysha yatashi, kowa kuma kallonsu kawai yakeyi, babu Wanda yasaka baki.
Dawowa ayshar tayi ta zauna, yad'ago suka had'a ido, tayi saurin janye nata, filet d'in abincinta da cup d'in shayi yanuna mata, wakika barma wannaπ΅π?.
Kwal-kwal tayi da idanu, cikin turo baki tace nifa Na k'oshi.
Shiru yayi yacigaba dashan tea d'insa.
Mama ta dakama Aysha harara, wakike turama wannan shegen bakin? Koshi sa'ankine?.
No barni da'ita mama, tabari harna gama shan tea d'inan batayi abinda naceba taga yanda zanyi da'ita.
Anty Mamie tace a'a babana ba'ayi hakaba, Aysha zauna kici kinji, zama da yunwa bashida dad'i, INA kallonki bakici wani abincin kirkiba kam, kobak'yasonsa?.
Da sauri Aysha tace a'a Anty Mamie, to maza kici kinji.
Kai tad'aga, idonta tab da hawaye, bawai ta k'oshi baneba, har yanzu takasa sabawa da d'and'anon abincin 9ja, tafison taci snacks kawai tad'ansha Ice-cream d'inta.
Baffah dai baice komaiba sai murmushi, yatashi yabar wajen,