Showing 6001 words to 9000 words out of 77617 words
gaggauce tatashi.
6angaren tsit yake, alamun duk suntafi bautar data zaunar dasu agidan, ran Aysha babu dad'i tafice itama, cikeda fargaba tanufi 6angaren mutanen gidan, k'ofar arufe take, kuma bazata iya bud'ewaba, harta juya zata koma inda tafito saiga matasan gidan suduka, sunsako k'yak'yk'yawan dattijo a tsakkiya, kafin tabar gurin harsun k'araso gareta, dole tazube guywoyinta ak'asa tana kwasar gaisuwa, duk suka amsa mata, dattijo Alhaji Abdallah yakafama Aysha ido, haka kawai yaji gabansa yafad'i, girarsa ta dama ta harba, (in bilynku nace komiyasa?) yad'an lumshe idanunsa tareda maidasu kan yaransa yana tambayarsu da ido wacece?.
Mujaheed yace Baffah d'iyar Maman yarace.
d'an murmushinsu Na manya yayi batareda yace komaiba yacigaba da tafiya, matasan yaransa suka take masa baya.
Muslim ne yadawo baya yacema Aysha mikike nemane?.
Har yanzu tana a durk'ushe kanta ak'asa tace zanje wajensu Gwaggona natayasu aiki, shiru yayi yana nazarin waye gwaggonta?, saican yace, "kina nufin Maman yara?.
Kanta tagyad'a masa batareda tayi maganaba, yace, " OK tashi Na nunu miki.
K'ofar baya ta kichin Muslim ya nunama Aysha yace kishiga suna aciki. Baijira cewartaba yajuya abinsa.
Bayansa tabi dakallo harya 6ace mata sannan tashiga Inda ya nuna mata.
Aikam duk suna ciki, Rabi ce kawai babu, tanacan tana gyaran babban falon gidan, Aysha tagaida kowa, sai sannan talura da hajiyar jiya dasuka tadda akichind'in lokacin dasukazo, matsawa tayi tadurk'usa har k'asa ta gaisheta.
Yanzuma cikeda fara'a hajiya ta amsa mata, tad'ora dafad'in Aysha nazata kinacan kina barcin gajiya?.
d'an murmushi Aysha tayi tace, "a'a mama natashi nayi sallah. OK tojeki kwanta abinki kinji.
A'a mama banajin barci, zan tayaku aikin.
Kai Aysha bazaki iya da wannan aikinba yamiki girma.
Lah mama inayi aii, kullum mune mukeyi agidanmu nidasu yaya fadeelah, kubani komiye zan iya insha ALLAH.
Aysha tayi matuk'ar birge hajiya bilkeesu, harcikin ranta taji k'aunar yarinyar...
___________________________
Gaba d'aya yaran gidan sun hallara ak'aton dinning table d'in suna breakfast, wasu sanye da Uniform, wasukuma sunsha kwalliyarsu ta mayan guys, bakajin komai sai k'arar filets da cokula, sai surutun wasunsu k'asa-k'asa, Aysha da Bishirah suna daga kichin suna wanke-waken kwanikan da'aka 6ata.
Kwas-kwas Hameedah tafito daga 6angarensu, ko Inda sauran 'yan uwanta suke bata kallaba, haka suma babu Wanda yadamu da'ita, Dan kowa yasan k'arancin tarbiyyar 'ya'yan hajiya babba agidan.
Mintina4 tsakani dafitarta saigata tadawo tana k'unk'uni, dinning table d'in tanufa, babuko tausa harshe tace, "ya Ramadan kazo kacire motarka zan fita, dankayi blocking d'ina.
Yawancinsu duksaida suka kalleta.
Cikin 6acin rai Ramadan yace, " ank'id'in fitsararriya, kebaki iya gaida kowaba? Nangurin dukba yayyanki baneba, yaymaganar yana nuna sauran 'yan uwansa.
Baki Hameedah tamurgud'a tana k'unk'uni.
ran Ramadan yakuma 6aci, yace Dan Uwarki mikike fad'a?.
Baki takuma murgud'awa.
Yatashi afusace zai fallamata mari.......
Karka kuskura kata6amin yarinya....
Maganar hajiya babba tariski kunnuwansu, kowa yamaida Kallonsa gareta. Tacigaba dafad'in Dan Uwarka Bilkeesu ita tahaifamin 'yarne? dazaka ware kwanji kadakarmin ita?, wlhy koda wasa karwani shege yak'ara wannan kuskuren, inba hakaba rayuka zasu 6aci, kajimin shegen yaro.
Ramadan ya kalleta, amma momy kinaganinfa abinda takema mutane? Mu sa'annintane? Tazo tawuce bata gaida kowaba, kosu ya Mujaheed fa bata gayarba......
Tobazata gayar d'inba, kokuwa dolene saita gaishesu? Sud'in ubantane? Bare ace yawajaba agareta saita gaidasu?.....
Har Ramadan yabud'e baki zaiyi magana......hajiya Bilkeesu takatseshi da daka MASA tsawa.
Ramadan!!! Karna sakejin maganarka anan, kaje kacire motarka tafita.
Idonsa jajur yace, "amma Aunty......
Dakatamin, nace karka sake magana ko, wuce kajanye motarka.
Saida ya watsama Hameedah harara sannan Yakoma wajen zamansa yafigi key d'in motarsa a dinning yafita.
Hajiya babba da Hameeda suka take masa baya, hajia babba nak'ara zazzaga masifa da zagin Aunty.
Girgiza kai kawai Aunty tayi, tak'arasa dinning d'in Tanama sauran fad'a. cikin ladabi Sultan yace, " kiyi hak'uri Aunty, wlhy laifin yarinyarne, kinsansudai basuda kunya..
Komadai miye kukama girmanku, banason fitina kunsani.
Hak'uri sukaita bata suduka.
Hayaniyarmi nakejine?.....
Ammah dake fitowa 6angarenta tafad'a. dattijuwar kwarai kenan mai lafiya da tsawon kwana.
Aunty tarissina tagaisheta, cikeda kulawa ta amsa, tad'ora dafad'in Bilkeesu mike faruwa?.
Murmushi Aunty tayi, babu komai Ammah.
Wane babu komai, bayan naji muryar fitinanniyarnan tana shegantamin jikoki, wlhyfa aka k'ureni zand'au mataki agidannan, amma nasan maganin 'yar banza.
Hak'uri Aunty tabata, hakama yaran, sannan suka gaidata cikin ladabi, itakuma ta amsa tanamai farinciki da d'unbin k'aunar jikokin nata, masu matuk'ar sonta da tattalinta.
Su Aysha dake la6e suna kallon komai suka saki murmushi, Dan tsohuwar taburge Aysha.
Ramadan Na shigowa falon Baffah yafito cikin shigarsa ta kamala, wato farar shadda mai d'inkin 'yar ciki da malun-malun, tasha aiki sai maik'o takeyi.
Duk abinda ke faruwa yana jiyosu daga 6angarensa, wanka yakeyi shiyyasa bai fitoba.
Kallon Ramadan yayi, yace INA Hameedan?.
Baffah tafita, cewar Ramadan a ladabce.
Jinjina kai yayi, amma baice komaiba, yak'arasa Inda Ammah take yagaidata, yaransa mata suka gaisheshi, ya gaisa da mazan tun bayan dawowarsu masallaci.
Yakai dubansa ga Aunty, da ido yaymata magana, tareda ban hak'uri.
Tayi murmushi da nuna jin kunyarta gareshi.
Dayawan yaran sunga soyayyar iyayen nasu, wannan yasakasu murmushi, sunajin sanyi dak'ara k'aunar babansu harma da mamansu dukda ba dukansu Aunty tahaifaba.
Baffah yak'araso yazauna a dining d'in shima aunty tahad'a MASA break d'in. (Haka yakeyi, inhar yana gidan cikin iyalinsa yakecin abinci, wannan ak'idarsace).
Aysha sai juya lamarin gidan takeyi azuciyarta, itadai agidansu tatashi taga mahaifiyarta da kishiya, amma Bahaka taga anayiba, kuma suma yaran Kansu a had'e yake, babukuma Wanda ya Isa ya raina wani acikinsu, akwai Respect d'in nagaba tsakaninsu, idankace kuma zaka kuskure kaci uwaka, Dan Umma da mama kowanne tanada ikon hukunta d'an kowa, shiyyasa bakowa yake banbance yaran gidanbama.
Itakam tanason k'arin bayani gameda wannan family.
Haka taita tunani harsuka kammala aikinsu.
Basu samu gidan yayi hankaliba saida kowa yafice, yaran wasu suntafi aiki, wasu schools, hakama hajiya babba da hajiya saudah duksun fita.
Daga hajiya Bilkeesu sai Ammah, saikuma su 'yan aiki mazansu da matansu.
Shima mai gidan yafice tuni.............๐
*I love you all my Fan's*๐
[8/7, 7:37 AM] Aisha Galadima: *_Typing_*๐ฒ
๐คฐ
*_CIKI DA GASKIYA.......!!_*
_{๐ชwuk'a bata hudashi๐ก}_
*_Bilyn Abdul ce๐ค๐ป_*
*_NIKA'DAI WRITER ASSO......._*๐
*Sadaukarwa*
_My sweet dady_
(ALLAH ya gafarta maka)๐คฒ๐ป
*_part 1_*
(littafi na d'aya)๐
0โฃ5โฃ
A kwana atashi babu wuya wajen ALLAH, yau kwanan Aysha 10 cif agidan Alhaji Abdallah Jigawa.
A tsawon kwanakinnan ta fiskanci k'alubale da dama, dakuma wasu abubuwa dasuka danganci mutanen gidan, taga abubuwan ban haushi, taga naban mamaki, taga naban dariya, taga Na birgewa, taga Na al'ajabi.
a6angaren dangantakarta da gidan kuwa tazama cikakkiyar 'yar aiki, Dan kowacce hidima da'ita aciki, saidai abinda batada sani akansa shine, kotanadaga cikin jerin masu albashi? Kokuwa itad'in 'yar tayice kamar yanda gwaggo bintu ta ambata aranar dasuka shigo gidan.
Babban kuma abinda kecin zuciyarta shine rashin tantance al'ummar gidan da matsayinsu, sunayen k'alilanne aciki tarik'e, suma dantaji ana ambatane.
Yauma kamar kullum sungama tik'ar aikin gyaran gidan, ko'ina yayi fes sai d'aukar ido yakeyi, ga k'amshin tiraren wuta natashi.
Bishirah data gama dai-daita gudun AC falon takai dubanta ga Aysha, to muje na gama, kinga muma ZAMU huta kafin sudawo su 6ata.
Murmushin yak'e Aysha tayi da tausayin Kansu, tanamai jin zafin katsewar karatunta da zama haidimar wasu adalilin maraici, dayanzu tana cikin jerin masu Shiga ss1, amma k'addara tadad'e da guntule wannan burin nata, tana rok'on ALLAH daya k'yautata rayuwar sauran 'yan uwanta karsu tsinci Kansu cikin hali irin nata.
ALLAH yasa iyayen ruk'onsu sucigaba dajan akalar tarbiyyarsu da iliminsu kamar da.
Dukda tana k'yautatamusu zato, dantasan gwaggo Asma'u da uncle Ahmad bazasu kasance irin gwaggo bintuba, to barema kawu bilyamin dake amsa suna tamkar mahaifinsu.
Damadai itace batayi dacen uwar rik'oba kafd'insu, shiyyasa kuwa yafi nuna tausayi akanta.......
Firgigit tadawo hankalinta saboda zingurar da bishirah Tamata.
Aysha tunanin mikikeyine haka?, yakamata kisaki jikinkifa, ai yanzu kinzama 'yar gida, gakida kwana har goma acikin garin Abuja.
Ajiyar zuciya Aysha tayi.
Bishirah tace, "jekiyi wankan saikizo nabaki labarin 'yan gidannan.
Cikeda d'oki Aysha Tace, " Dan ALLAH da gaske kikeyi?.
Wlhy kuwa da gaske.
Da Sauri Aysha tatashi tafad'a wanka, Dan yanzu komai NATA yadawo d'akin bishirah, tsakaninta da gwaggo bintu gaisuwace kawai, Dan bawani janta takeyi ajikiba.
_____________________________
*_Alhaji Abdallah Jigawa family's_*
Alhaji Abdallah Rufa'ee jigawa shine cikakken sunan maigidan, d'an asalin jihar jigawane a garin ringim, ALLAH yayima mahaifinsa Malam Rufa'ee rasuwa dadad'ewa.
Alhaji Abdallah yana sana'ar saida carpets ne a babbar kasuwar wuse dake Abuja, ahankali ubangiji yacigaba da bud'a masa harkokinsa harya bud'e kamfaninsa na kansa, Wanda yasami had'in guywa da k'asar Turkey, Alhamdullah kasuwancinsa yabunk'asa matuk'a ak'asar, yanzu haka sunada reshen kamfanin a Kano, Lagos, sokoto, Jigawa.
Matansa uku da 'ya'ya 21.
Hajiya Laurah itace uwar gida, wadda sukan kira da hajiya babba, yaran kuma suna cemata (momy). cikakkiyar 'Yar bokoce dantayi karatu mai zurfi, ko kad'an hajiya laurah batason talaka, macece mai tunk'aho da tak'ama, shikansa Alhaji Abdallah nuna masa isarta takeyi, tad'auki aikinta sosai da muhimmanci, kokad'an babu maijin dad'in zama da'ita agidan, saboda halayyarta, musamman hajia Bilkeesu. Yaranta 6, Zuwairah, Shukurah, Ibraheem khaleel, Hameedah, Hasna, Husnah.
Sai Hajiya Bilkeesu, tanada yara 11, Rufa'ee, ALLAH yamasa rasuwa wata uku dasuka shige sakamakon had'arin mota zaije jigawa. Yanzu akwai 10 Sultan, Mujahedeen, Amatullah, Ramadan, Zunnurain, Muslim, Muhseen, Amal, Tasleem, UmmuNoor. Itakam tanada hak'uri, ga kawaici da sauk'inkai, kowa natane, batada k'yamar talaka, saima tazauna tayita hira da 'yan aikin gidan, gatada taimako, batayi karatu mai zurfiba, iyakarta Secondary aka aurama Alhaji Abdallah ita, tana yarinya d'anya, kobayan aurensu batacigaba da karatuntaba, danhaka bata aikin komai saina kula da mijinta da 'ya'yanta, wannan yasa suka taso cikin tarbiyya. Alhaji Abdallah nasonta sosai saboda k'yautatawarta agareshi da mahaifiyarsa. Yaran gidan nakiranta (Aunty Mamie).
Sai amarya hajia saudah, itamadai balaifi akwai girman kai, amma batakai hajiya babba ba, itamadai ma'aikaciyar Ce, Lauya ce maizaman kanta, ita wata irin mutumce dabata damu da damuwar kowaba, cikikam harda 'ya'yanta, (shiyyasa yaranta duk sunfi shak'uwa da Aunty Mamie) takan bama aikinta muhimmanci fiye da komai, kakan dad'ema baka ganta cikin lamuran gidanba, hajiya babba taso suhad'ema hajiya bikeesu kai itada hajia saudah, amma hajia saudah tace ita ba wannane agabantaba. Yaranta 4 Hafeez, Shuhudah, Maleekah, Nurudden. Itakuma suna cemata Ummee Amarya.
Mahaifiyar Alhaji Abdallah tana nan gidan taredashi, itace tsohuwar dakika gani, anabata kulawa sosai agidannan, babu maison abinda zai ta6ata, idan kika cire hajiya babba da 'ya'yan tokowa jiyake da'ita, ya khaleel ne kawai halinsa ya banbanta ayaran hajiya babba, danshi babu ruwansa.
Wannan shine tak'aitaccen tarihin gidannan. Kinada tambayane??.
Ajiyar zuciya Aysha tasauke, cikin kafe bishirah da kallo tace, tambayata biyuce zuwa uku. Tafarko suwaye sauran yara uku danagani dakuma 'yanmata biyu?.
Dariya Bisheerah tad'anyi, cikin tsokana tace Ashe kinfahimci labarin sosai?, 'yan mata biyu dakika gani, Hamdiyya da Naseeba yaran k'anin Alhaji Abdallah ne, uncle Ma'aruff, suma suna nan zaune awajen Aunty Mamie, karatu sukeyi anan sudasu Amal.
K'anan su uku kam yaran aunty Amatullah ne, 'yan uku, suna k'asar Japan itada mijinta, shine aka kawosu nan gidan saboda school.
Jinjina kai Aysha tayi alamun gamsuwa, tacigaba da fad'in yaran hajiya babba fa? Dan uku nagani yanzu agida?.
Eh, biyu sunyi aure, Anty zuwairah tana Lego's itada mijinta, sai Anty Shukurah tananan abuja, amma yanzu suna kasar Jordan shekara uku kenan, wai mijin natane yake karo karatu, yaya khaleel kuma bansan takamaimai k'asar dayakeba, Dan shi yanzu zai iya cemikima yana Najeria, anjima kuma kiji yabar k'asar, haka yake yawo k'asashen duniya saboda yanayin aikinsa.
"Aikin mi yakeyi?."
Wlhy ban saniba Aysha, amma naji sunacewa ko d'an sandane, kamardai haka naji su iya hama nafad'a kwanaki. Amma kwanannanma zakiji yazo k'asar saboda hutun k'arshen shekara dakuma meeting na family dasukeyi.
Shiru Aysha tayi, Dan haka kawai tasamu kanta da fad'uwar gaba, Bishirah ta ta6ata tareda fad'in shikenan kin gama tanbayar taki?.
Jiki amace Aysha tad'aga mata kanta, kafin Bishirah tace wani Abu kiran da Rabi kemusu yakatseta.
Atare suka amsamata, sannan suka fito inda take.
Kichin suka shiga domin tanadar abincin rana, yaran gidan sunkusa fara dawowa, yaukuma aikin hajia saudah ne. Itakam tanama wajen aikinta.
Duk ranakun aikinsu itada hajiya babba 'yan aikine keyin komai, sa6abanin Anty Mamie dakan tsaya ayi komai da ita, shiyyasa yaran kanyi farincikin aikinta, Dan koba komai zasuci mai dad'i da tsafta...............๐
nagaji bara nahuta๐๐ข, kuma inajin yunwa๐, muhad'u a page 6 guys๐
*I love you all my lovely fans*๐
[8/7, 7:37 AM] Aisha Galadima: *_Typing๐ฒ_*
๐คฐ๐ป
*_CIKI DA GASKIYA........_*
_{๐ชwuk'a bata hudashi๐ก}_
*_Bilyn Abdull ce๐ค๐ป_*
*_NIKA'DAI WRITER ASSO........_*๐
*_Sadaukarwa_*
_My sweet dady_
~(ALLAH ya gafarta maka)~
๐คฒ๐ป๐ญ
*_part 1_*
(littafi na d'aya๐)
*_Dolene namik'o sak'on jinjina da godiya agareku 'yan group d'ina, ALLAH yabar zuminci, inajinku sosai aruhina, inayinku irin tamau-tamau d'innan, I love you so much_*๐๐
0โฃ6โฃ
Gaban Aysha sai fad'uwa yakeyi sakamakon kiran da hajia babba ta aiko karime Tamata. harsuka shiga falon tana addu'ar daduk ta iso bakinta.
Hajiya babba nazaune tareda wata hamshak'iyar mace, daganinta kasan naira ta zauna.
Karime tarissina tana fad'in hajia ga Ayshar nan.
Kai kawai hajia babba ta gyad'ama karime alamar taji.
Karime nafita daga falo Aysha ta durk'ushe tana gaishesu, babu Wanda ya amsa acikinsu, saidai suna binta da kallon k'urullah, musammanma bak'uwar ta hajia babba. bayan kamar 4mnt hajia babba tace, ''aminiya kingantafa, ai zata iya nake gani?.
Wani murmushin k'asaita hajia khaltum tasaki, tagyara zamanta tana k'arema Aysha kallo lungu da sak'o, Aminiya ai zancenma zata iya labarine, zan iya cemiki tunda muke business d'innan baki ta6a samun hajaba irin ta wannan lokacin, ai young girls irin wad'annan su ake so dama, ALLAH kad'ai yasan irin ribar daza'a samu anan ๐๐ป๐๐ปโโtayi maganar tana nuna Aysha datayi k'asa dakai tamkar munafuka.
Amma jikinta sai tsuma yakeyi saboda tsoro da firgicin zaurencen Nasu hajia babba, ko kad'an Aysha bata fahimtar komai a zancensu, saidai tanaji ajikinta ba alkairi baneba, addu'oin Neman tsari tafara a can k'asan zuciyarta......
Hajia khaltume takatseta da fad'in yarinya yasunanki?.
Muryarta Na rawa tace Aysha.
Nice name!.
Cewar hajia khaltume. Daga nan suka sallami Aysha tatafi.
Tana tafiya 6angarensu tana sharar kwalla, haka kawai taji tana tausayin kanta, gashi su hajia babba sun gargad'eta kada tasanarma kowa kiran dasukai mata, inba hakaba komi yabiyo baya ita tajama kanta.
Gaff taci karo da Abu, dasauri tad'ago kanta, amma kafin tasan wata bige ansauke mata Marika har biyu.
Dafe kuncinta tayi saboda azaba, ke Dan ubanki bak'ya ganine?....
Maganar matashiyar Husnah ta katseta.
Dan ALLAH kiyi hak'uri Anty Husnah wlhy bankula baneba, Aysha tayi maganar tana durk'usawa ak'asa, haryanzu hannunta Na dafe a kuncinta.
Muhseen yak'araso inda suke da sauri, yace k Husnah lfy kuwa?.
Cikin huci tace wai 'Yar iskar yarinyarnan hartakai ta bangajeni, Muhseen.
kiyi hak'uri to, tayi kuskure amma bazata sakeba, ke Aysha bata hak'uri.
Hak'uri Aysha takuma bata cikin kuka.
Hasnah taja tsaki sannan tara6a gefen Aysha tashige, harda takama Aysha yatsun kafa.
Aysha tafashe da sabon kuka dantaji zafin takawar. shikansa Muhseen