Showing 102001 words to 105000 words out of 171357 words
Chapter 35 - Daurin Boye Book One Complete Hausa Novel
duk yaga yadda take appreciating film din,Allah ya rufa mata asiri ba wani film din banza take kalla ba,waskewa tayi tana tsaida film din tana son rufr system din,hannayensa ya saki yana zagayowa inda take,shi kansa film din yaji yana taba wani sashe na zuciyarsa,zai iya cewa tun wancan lokacin daya shude zuciyarsa ke a rufe,bai taba bada qofa ga wata ba bare yaji me ake ji koya dan dana irin abinda masu soyayya ke dan danawa,hannayensa yasa zai gyara qafafunta dake miqe don ya samu wajen zama,santala santalan qaurinta yabi da kallo wanda,cikin sauri ta tanqwashe qafarta tana dan hade rai,baice komai ba ya sanya hannunshi ya ya dauki system din ya janyo qaramin tebur gabansu ya aje samanta ya dannan play film din yaci gaba dayi,ji take ba zata iya zama su kalli film din tare ba,duk da bana badala bane amma soyayya ciki mai zafi ce akwai kunya,tana jin nauyinsa sosai saboda haka ta miqe da sauri,caraf ya kama tsintsiyar hannunta ya janyota baya wanda hakan yasa ta koma da baya ta zquna ba tare data shirya ba,har zaman datayi yafi na dazu kawo kusanci a tsakaninsu
"Zauna ki kalla abinki,ni tayaki kawai zanyi" ba yadda ta iya saboda yadda ya dabibayeta da idanunsa ta zauna din,tun tana a takure harta dan saki kadan fim din yaci gaba da garawa,ji tayi ba zata iya daurewa ba abun ya mata nauyi da yawa aka,ga zamanshi a gefanta dake qara raurawa zuciyarta,haka kawai zuciyarta taji kamar zata narke,saita rarumi system din ta soma yunqurin kasheta gaba days,a hankali ya dora hannunshi saman nata,dagowa tayi tana kallon qwayar idanunshi karo na farko,wani irin kallo yake binta dashi kamar wanda ke jin bacci,manyan idanunshi nan sun rusuna sun rage girma,wani abu taji yabtsirga mata saita soma yunqurin zame hannunta ta gudu tabar masa system din ma gaba daya amma yaqi bata space din yin hakan
"Kinsan me?" Ya fada cikin sanyi da taushi
"Indai kaga mutum na yawan kallon fina finan soyayya to aure yakeso" idanunta ta zare tana dubanshi,aure kaman yaya?,me yake nufi xai fassarata?
"Yaushe kika soma kalla humairaaa?" Ya kira sunanta da wani irin tune wanda ya qarawa zuciyarta bugu,saita kasa daurewa taci gaba da yunqurin zame hannunta amma duka a banza,tafin hannunshinya saka cikin nata yana murzawa a hankali yana ji cikin jikinsa kamar zai fita da control dinsa amma ya kasa tsaida kanshi,shi kansa baisan me yakeji haka cikin jiki da zuciyarsa ba
"Uhmm...tell me mana"
"Pls ya khalipha...ka sakarmin hannu" ta fada a narke kaman mai shirin sakin kuka,saidai kasalar daya saukar mata ya sanyata fidda sautin cikin wannan yanayin.
Sautin kidan da wayarshi ya dauka shiya dawo dashi,ya zame hannunshi daga nata a hankali ya soma laluben wayar,hakan ya bata damar miqewa ta fice daga falon zuwa dako cikin gudu gudu sauri sauri,binta yayi da kallo ta koma kamar qaramin yaron da aka biyo yakeson ya cimma mamanshi ya buya bayanta,mahmoud ne ke kiransa,sallama yayi bayan ya daga wayar
"Kana ina miscal kusan uku?"
"Da yaushe kenan?"
"Yanzu mana wannan ne kira na hudu dana yi maka fa" cikin mamaki ya daga wayar daga kunnenshi ya kalli screen din,tabbas ga alamun miscal nan ya nuna amma saiya dake
"To nidai banji ba"
"Kacemin kawai kana angonci,tunda ka dawo ba wanda yaji motsinka daga company" kalmar angoncin ita ta sashi sakin sihirtaccen murmushi,yana son yayi nazqri akanta amma surutun mahmoud ya hana,hakanan ya biye mishi suka tattauna maganganun dq zqsu tattauna,daga qarshe ya buqaci ko zai shigo company
"A'ah fa,gobe zanje legos"
"Kayi me a can?"
"Nida humairaaa ne"
"Honeymoon?" Ya tambaya cikin shaqiyanci
"Laifi ne?"
"Ko kadan na wajena,amma legos inaga ta muku kadan fa,ka manta tsohon tuzuru ne kai daya ga 'yammata kala kala?" Ya fadi cikin tsokana,dariya taso kubce masa ya danne abarsa,shi sam baima kai can inda mahmoud din yakai ba ko kadan a ransa
"Kaga sai da safe"
"A miqamin gaisuwa" bai saurareshi ba ya yanke kiran abinsa yana murmushi,yana juya maganar da sukayi da mahmoud,haka ya dinga juya maganar cikin ransa kamar dai tana so tayi masa tasiri,a nutse ya janyo system din tata zai kashe mata,babban hoton haidar ne aka screen din,cikin shigar qananun kaya,yayi kyau sosai suna diban kaman dashi qwarai fiye da mus'ab,haka kota fannin halayya,saiya tsaya yana duban hoton,tsaki ua danja,sai ya juya bayan system yaga irin ta haidar dince sak,tsaki yadanja wanda baisan dalilinsa ba,kasheta yayi ya hada da charger din ya nufi study room dinshi da ita ya ajeta a can.
Tunda ta shiga dakin take kwance rub da ciki saman gado a side din da yake kaman nata ne nan take kwanciya shi kuma daya side din tun sanda ya tasota daga falo ta dawo ciki,a hankali komai ke dawo mata cikin qwalqwalwarta,wani yanayi da batasan na neye ba yana bin jiki jini da zuciyarta,ta jima a haka kafin ta gyara kwanciyarta ta juyar da fuskarta daya sashen,hoton fuskar khalipha ta soma yi mata yawo,manyan idanunshi masu kyau da haske,kwantancen sajen fuskarshi daya zagaye haba zuwa qasan hancinsa,dogon hancinsa mai dan tudu kadan,pink din labbansa suma masu tudu kadan,cikakken gashin gira daya sake qawata fuskarshi da zara zaran eyelashes,fararen haqora,saita cure waje daya tana jin kunya na kamata,cusa kanta tayi cikin filo tana tuhunar kanta me ya kaita fasalta siffar da namiji idan ba rashin ta ido ba,murmushi ya qwace mata tana sake cusa kanta tsakanin filalluka,ita daya kamar wadda za'a kama.
38
Farin bayanta yake iya gani wanda dogon gashinta ya sauka,tana ci gaba da tajeshi yana miqewa,da fari ya danyi mamaki yayi tsammanin jinnu ne sukeso masa yawo da hankali,saida ya saukar da idanunsa zuwa santala santalan cinyoyinta zuwa qafarta ya tabbatar ba aljana bace amma kuma wacece?,bai gama wannan tunanin ba ta ankara da mutum a bayanta can bakin qofa a tsaye cikin baqaqen suit,wani irin kadawa hantar cikinta tayi,ta zabura gami da qwalla qara ta shige bayi ta danna key tana karanto addu'o'in tsari,ba inda ajikinta baya rawa yana kakkarwa,kasa tsaiwa tayi saboda tsabar tsoro da rudewa saida ta samu gefan bathtube ta zauna,tuni hawaye suka fara tsatstsafo mata,yau ta shiga uku ta lalace,dama akwai aljannu a gidan?,don ta tabbatar tayi imanin babu mai shigowa inda take,bugu da qari ma waye zai iya shigowa dakin da tun daga falo ta sanya mauqulli har dakin gadon,saita barke da kuka mai sauti tana ci gaba da addu'a gami da qanqame jikinta waje daya.
Daga inda yake tsaye haushi ya cikashi taf,wannan wanne irin abu je?,daga ganin mutum shine zata wani zabura kamar taga aljani ta shige bandaki?,wai wace ma har ta samu lasisin shigo masa daki ta bararraje haka?,anya anni ta sani?,Allah yasa ba daya daga cikin yarancan bane da suke addabarsu da bibiyar rayuwarsu.
Parlour din ya koma ya zauna saman daya daga cikin kujerun falon yana dafe da goshinsa da hannu daya ya zaro wayarshi ya lalubi lambar anni,bugu daya ta daga,sai yayi qoqarin saisaita temper dinsa
"Anni,wace take amfani da bedroom dina?"
"Bedroom dinka?,wace banda matarka,aysha ce"
"Aysha kuma?" Ya tambaya cikin mamaki
"Eh ita,wani abu ne?"
"A'ah,ta tsorata ne kawai ta shiga toilet tayi zaton wani ne" yayi saurin fada don karta dago wani abu
"Aifa aysha ba baya ba wajen tsoro,saika gaya mata wane ai" daga haka ta katse wayar,jifa wayar yayi gefanshi sannan ya miqe qafafunshi ya soma zare takalmin qafarsa da socka din duka gaba daya,ya rage daya daga cikin three in one suit din dake jikinsa ya sassauta tie dinsa sannan ya sake komawa dakin,tsai yayi yana qarewa dakin kallo,komai a tsaftace yake,sai towel bressier da pant dake kan gadon,sai kayan gyaran gashi dake saman madubi da cumb din data watsar waje guda saboda tsoronta,dauke kanshi yayi ya shigo ciki sosai ya doshi toilet din.
Daga can taji 'yar qara alamun an sake bude qofar bedroom din,wani tsoron ya sake kamata,sautin kukanta ya sake qaruwa sanda taji ana taba qofar bandakin,yana iya jiyo sautinta kadan kadan,haushi ya kamashi,wanne irin tsoro ne da ita haka,knocking ya fara yi saidai maimakon ta bude sake firgicewa tayi,gabanta yaci gaba da bugun uku uku,ta duba duk bandakin ba wajen tsira,kuma ta tabbata ko ihu tayi ba wanda zai jiyota cikin gidan,ganin ba alamun zata bude sai kukan banza da takeyi ba tare da yasan me takewa kukan ba ya sanyashi bude bakinsa,cikin muryarshin nan yace
"Bude mana" saboda tsoro sam bata iya tantance muryar waye ba,sai kawai zuciyarta ta bata muryar aljanu ce,cikin sautin kuka tace
"Wallahi bazan bude ba"
"Kwana zakiyi a ciki?"
"Nidai kuyi haquri don Allah"
"Mu suwa?" Ya tambayeta cikin qosawa,bata bashi amsa ba sai dif da tayi,ganin tana neman bata mishi lokaci yasa ya koma inda ya aje kayan hannunshi ranshi fal takaici,ya lalubi muqullansa daya amsa a hannun anni ya koma yana gwada na toilet din,jin ana alamun budewa ya sake sawa ta tsure,saikawai ta qarasa shigewa cikin bathtube din ta takure waje daya tana dana sanin zama abangaren ita kadai,dama tun dazun take jin motsi,dazu kuma musa'ab ya gama bata labarin ya taba gamo tsohon gidansu,tana ta dariya da tsokanarshi duk labarin ya dan bata tsoro kadan ashe da gaske yake
Sai daya gwada muqullai kusan uku abinda ya sake gajiyar dashi sannan ya dace dana bandakin,a hankali ya tura qofar ya shiga,can ya hangota ta takure gu daya,gashin kanta da bata samu damar daurewa ba ya bazu ko ina har fuskarta,daga kai tayi cikin tsoro ta dubeshi,sai a sannan ainihin siffarshi ta bayyanar mata,khalipha ne sosai tsaye cikin bandakin,sanye cikin baqaqen suit,saidai a yanzu ya cire sun glasses din dake fuskarshi,ya sake haske da kyau,sumar kanshi data fuskarshi luf da ita tana fidda wani sheqin baqi,ya sake murjewa hakanan idanunshi sun sake kyau,daga tsoro sai yanayin ta ya sauya zuwa kunya da fargaba,ta tafka babban abun kunya,bugu da qari tuna abinda ke daure a jikinta kawai ya sake sawa hankalinta ya tashi,kamar ta bace ya daina gannta haka taji,sai kawai ta maida kanta taci gaba da dunqulewa waje guda gana pretending din firgitar dazu ce bata saketa ba
"Saiki tashi ki koma ciki ki bani waje zanyi wanka" ya fada yana dubanta,duk da qoqarin kauda idanunshi da yakeyi amma hakan ya gagara,jin idanunsa take yake ko ina akanta,batajin zata iya motsawa ta wuce haka ya gabanshi
"Ki tashi matsoraciya kawai ko har yanzu baki gane wane ba?" Ya tambayeta yana harde hannunsa a qirji,shuru tayi don bata da amsar bashi
"Ko ba zaki tashi ba sai nazo na daukeki da kaina?" Jin haka ya sanyata zumbur ta miqe,saidai da qyar take iya daga qafafunta ta fito daga cikin bathtube din ta raba ta gabanshi zata fice daga bandakin,caraf yayi ya riqo hannunta yana sani,a firgice ta dago kai suka hada idanu,saita soma neman wajen buya,wanda abin dariyar jikinsa takeson shigewa ko zai daina kallonta,ba shiri ya saketa yana dariya cikin ranshi,bai fasa kallonta ba har sai data fita din sannan ya koma ya rufe bandakin da muqulli ya dawo ciki ya tara ruwan wanka.
Hawaye ne ya sake qwace mata takaici na cinta na ganinta haka da yayi,gashinan shi yanzu ya saka muqulli ya kulle kanshi zaiyi wanka amma ita asirinta abayyane,qwafa tayi ita kadai tana zumburo baki.
Haka ta shirya tana qananun hawaye a gurguje don kada ya sake fitowa ya taddata a haka,duk da haka bata fasa yin kyau ba,doguwar rigar buba ce ta atamfa shadda baqa mai matuqar kyau da tsada,an mata zanen jajayen flowers manya a jiki,bata nemi dan kwali ba saita yane kanta da madaidaicin jan mayafi bayan ta hade gashinta ya bada jela daya data sauka har bayanta.
Har taje zata fita sai kuma ta kasa,bai kamata ba,ba wani magana da sukai tsakaninsu koda ta sannu da zuwa ce,saita koma kan kujerar falon ta zauna tana murza tafin hannunta a hankali tana tuna yadda abun ya faru,dama tun dazu a tsorace take da labarin mus'ab,shi ya sake tunzurata ta sake tsorata.
Idanunsa lumshe suke ruwan na ratsa jikinsa,tabbas haka ne kowa yabar gida gida ya barshi,wani dadi yake ji gashi a gida,Allah Allah kawai yake ya koma wajen anni susha hira,a hankali ya tuna abinda ya faru dazu mintina kadan da suka wuce,murmushi ya saki abun yana son bashi dariya,bai taba sanin matsoraciya bace har haka bayan sanyin da yasan a baya tana da shi ba sai yau,kai ya kada kafin ya dauraye jikinsa ya fito.
Tunani kadan tayi sai ta miqe ta fice zuwa cikin gidan,ya kamata ace tayi masa wani abu da zaiji dadi,tunda bata jin gidan sun tanadar masa wani abun don ba alamun suna da masaniyar zuwanshi a yau,ta tabbata da anni zata sanar mata,haidar da mus'ab ne kawai a falon suna shigo da jakankuna,dariya mus'ab ya sa yana dan satar kallonta,har ta wuceshi ta share sai ta tuna abinda taji yana cewa anni dazu na suprise,sai ta dawo da baya tana dubansa
"Zan rama fa,kaci bashi ne,yaa haidar harda kai aka hada baki ko?" Ta fada tana duban haidar,murmushi yayi yana daga hannu sama
"Nikam babu ruwana bansan me akeyi ba,yace min ne kawai nazo na rakashi airphort" kai ta jinjina tana wa mus'ab sign na alwashi ta wuce kitchen.
Duka 'yan aikin ma ciki sun kacame da aiki
"A'ah duk girkin meye wannan?" Ta tambayi baba atika
"Mai gida yayi zuwan bazata kinga dole a tashi a shirya masa lafiyayyen abinci" hakanan taji cewa dutynta ne wannan,ita ya kamata tayi masa wannan karramawar,koba komai ta dan nuna dan wani yanki na godiya kan kyautatawarsa a gareta,duk da baikai ya kawo ba amma zata kwatanta
"Bari ku gani,wannan girkin naku ai lokaci zai dauka baku gama ba" cikin qanqamin lokaci ta hado duk abinda take buqata ta dora,ta koma gefe ta niqa abarba tayi mishi pineapple juice wanda kafin ta garma dan qwarya qwarayar girkinta ya dauki sanyi.
Mintina talatin ta gama ta shirya komai kan wani faffadan tray mai azabar kyau,ba wanda yawunshi bai tsinke ba a kitchen din(harda ni mai rubutun 😜).
Tana goge hannunta da zummar idan ta gama ta fita da abincin amal ta shigo,kana ganinta kasan bata jima da yin kwalliyar ba cikin dinkin lace
"Wai baba atika me kuke dafawa baqonmu,qamshi ya cika gidan amma shuru baku gabatar masa da komai ba?"
"Ai aikin uwar masu gida ne,gashinan da kanta ba saqo ba" baba atikar ta fada cikin murmushi wanda hakan yaja hankalin amal zuwa wajen aysha wadda take sake jera kwanukan,cikin yaqe take kallonta,nutsatsiyar kwalliyarta wadda girkin da tayi bai bata ta ba,yadda ta jera kayan abincin da qamshin da suke fiddawa,wani abu mai nauyi taji ya tokare qirjinta,sai ta kasa cewa komai ta juya ta fice cikin sanyin gwiwa.
A nutse take fitowa daga kitchen din zuwa falon,shi ta soma hangowa a gefan anni wanda hakan ya haifar mata da matsananciyar faduwar gaba wadda bata taba jin irinta ba,bata sani ba ko hakan yana da nasaba da abinda ya faru dazun?,fuskarshi fes,kyansa ya sake fitowa sosai,ganin yana niyyar juyowa ya sanyata dauke kai da sauri ta maida kan anni,dubanta yake sanda take tahowa din,sai yaga kamar an canza ta gaba daya,shidai yasan ba wannan ayshan ya tafi ya bari ba wata ce daban,abinda tayi dazun ya dawo mishi,sai yace da anni sanda ta iso wajen tana aje kwanukan
"Yaushe humaira ta koma haka?" Yayi subutar bakin fada ba tare daya shirya ba,sam anni bata fahimci tambayar tashi ba,tayi tunanin kyau da gogewar data qara yake nufi,saita saki murmushi tana jin dadi har cikin ranta,miqewa tayi tana cewa
"Sannu takwara,ki kai masa saman teburi,fita zanyi nima dubiya,drivan ma har ya iso" ta qarasa maganar tana miqewa,sai ya dubeta
"Ba hira kenan anni,kamar ma baki kewata ba?"
"Ni bance haka ba saikai khalipha?,watanka nawa?" Ya gane qorafi takeson yi masa,mafi a'ala kuma yayi shuru kar allura ta tono garma
"A dawo lafiya"
"Allah yasa,ya kamata idan ka huta kaima kaje ka dubashi,don yanzun ma tare dasu haidar zamu je"shuru kawai yayi yadan sadda kanshi,da alama baison zuwa wajen amma bazai iya musa mata ba,miqewa aysha tayi ta amshi jakar hannunta ta bita da ita a baya,suna zuwa qofar falon ta amsa
"bar aikin da ba lada kije kiyi na lada,ki kula da mijinki" kunya kaman zata nutse,kalmar saita mata banbarakwai,ba wanda ya fado mata a ranta a lokacin sai maman hunaifa da baban hunaifa,saita dinga jin girma da wani alfahari na shigarta kadan kadan,wai itama fa matar wani ce akwai igiya a kanta,hakanan taji tana son ta gwada yanda matan aure keyi,juyawa tayi zuwa cikin falon,har ta isa kanshi na qasa da alama tunani ma yake,bata tankashi ba ta kwashe kwanukan zuwa saman tebur wanda motsinta yasanyashi daga kai,saiya tsinci kanshi da binta da kallo,qamshinta daya buso zuwa hancinsa yaji ya burgeshi,ci gaba yayi da kallonta ba tare data sani ba yana jin qimarta na qaruwa cikin ranshi,zaman da sukayi da anni kafin fitowarta labarinta kaf duka kan ayshanne,irin kulawar data samu daga gunta ya tabbata ko shine iyakar abinda zai mata kenan,sai yaji tausayinta ya kamashi,lallai mahaifiyarta batasan baiwar da Allah yayi ma rayuwarta ba na samun nutsatstsiyar diya.
Sai data shirya komai sannan ta daga kai da niyyar duban me yake,sai suka hada ido,murmushi ya sakar mata saboda harga Allah bazai iya boye jin dadin kulawa da anni data yi ba,tamkar an dorawa zuciyarta wani abu haka taji,bugun zuciyarta ya sake yawa,idanunta ta lumshe tana qoqarin maida masa martanin murmushin nasa,sai kuma taji kunya ta mata dabaibayi,yanayin daya ganta da abinda ta masa dazu suka fado mata,ji take kaman qasa ta tsage mata ta shige ciki,a nutse ya taso har zuwa inda take tsaye,yaja kujerar dake kusa da ita ya zauna,saita motsa kadan ta matsa daga kusa dashi.
Ganin shuru batayi niyyar zuba komai.ba bayan shi kuma yunwa yakeji sai ya sanya hannunshi da niyyar bude flask din dake gabanshi,tare hannunsu yaje kai saboda arashin