Showing 162001 words to 165000 words out of 171357 words

Chapter 55 - Daurin Boye Book One Complete Hausa Novel

juya zai fice
"Zo nan" anni tace dashi tana qoqarin zama,dawowa yayi
"Ka kora min yara shine zaka wuce kubarmin gida ni daya kenan ko?" Ta fada tana dubanshi,sai yayu shuru yana shafa kanshi
"Zauna" ta nuna mishi waje,zaman yayi yana kaucema kallon annin
"Duk inda musulmi yake ana son ya zama mai manta sharri,mara manta alkhairi,anason idan mutum ya maka sharri kai ka saka masa da alkhairi,a sanda duk Allah ya maka sauyin yanayi na alkhairi ganin damarshi ne,sanda Allah yayi maka arziqi ka wadata mabuqata,sabida wannan arziqin ba kai kadai ya bawa ba ya baka ne harda su,sai ya sanyashi a hannunka,babu abinda zai rageka dashi donka kyautatawa wanda ya zalunceka,sai qarin daukaka da zaka samu wajen ubangiji,na yaba maka sosai da yadda kayi haquri kuma kabi maganata,ka dauki ragamar kyautata musu kamar yadda mahaifinka yayi kafin yabar duniya duk da nasan tanqwara zuciyarka kawai kake,a yanzu bazan sake takuraka kan zamansu amal cikin gidan nan ba,don na tabbatar gudun faruwar matsala yasa kayi haka,nima kuma daga bisani na hangi hakan,zuwa yanzu dama yaci ace kowacce ta maida hankalinta jikinta ta fitar da mijin aure tunda gaba dayansu sun kai munzali"
"Hakane anni,kiyi haquri idan kinji babu dadi...yanzu haka mun gama magana da mijin anty ruqayya zai baki nadiya 'yarsa in sha Allahu taci gaba da zama dake,saboda ina tunanin...." Sai kuma ya kasa qarasawa ya soma shafa qeya,tasan yana jin nauyin abinda zai fada mata ne,saita saki murmushi
"Uhmmm"
"Cyprus zamu wuce nida humaira" har qasan zuciyar anni farinciki ne ya lullubeta,abinda take zato ya tabbata,tun ranar farko data gansu taga burbushin haka,dukkan alamu sun suna akwai wata dangantaka mai qarfi atsakaninsu,akwai wani lamari mai girma daya yiwa junansu dabaibayi,amma donson ta sake tabbatarwa sai tace
"Wani irin cyprus?,nata karatun fa?,ba inda zaka daukemin diya ka kaita"
"Wallahi anni bazan iya tafiya na barta ba don Allah karkice na tafi na barta,in kika ce haka kona tafi bazan iya qarasa nawa karatun ba kuma nawa yafi nata muhimmamci...."yayi subutar bakin fadan wadannan kalmomin ba tare daya shirya fadarsu ba
"Dakata..." Tayi hanzarin tsaidashi karya ballo maganar data fi haka nauyi
"Saikun dawo Allah ya kiyaye hanya,ke ayshatu tashi maza ku wuce gidanku nima nan kwanciya zanyi,idan kun fita ku turomin mus'ab ko atika" sai a sannan ya tuna abinda yace mata,kunya duka ta kamashi,amma da yake namiji ne saiya murje ya shigar da godiyarsa,don kada ma ayshan ta bata masa lokaci sai ya tsaya yana jiran ta gama laqai laqai dinta ta tashi,haka ta gama din kuwa ta yiwa anni sallama suka fice.


Tun a gidan annin dama takejin son tayi kuka,wani abu ya takoreta a wuya,tun a can take toshe kukan,suna shiga falon gidansu ta kasa haquri kawai saita saki kukan,juyawa kawai khalipha yayi yana kallonta baki sake,kamar wadda akayiwa wahayin kuka?,bai wani bata bakinsa ba wajen lallashi kawai ya sunkuci abarsa,bai direta ko ina ba sai dakin bacci,sai daya gama budurinsa ya biya dukkan bashin dake kansa sannan ya soma aikin lallashi,nan ta narke masa itama ta zuba shagwabarta son ranta shi kuma ya biye mata,sai daya sha rarrashi sannan ya samu kanta suka shiga wanka tare,wanda kusan al'adarshi ce haka,saboda koyi da fiyayyen halitta annabi muhammad S A W.


Bayan kwana biyu akayi bikin bude katafaren shagon nata,wanda walima tayi dai dai gwargwado,donta rage wani abunma saboda mutuwar daddy amma tayi walima sosai anci an sha anyi sadaka.


Kwanaki bakwai suka qara a nigeria suka shirya don komawa cyprus ita dashi,ana washegari zasu koma taje gidan daddy donta qara ganin mummy.


Ba qaramin tausayi mummyn ta bata ba yadda ta rame tayi baqi ta zabge lokaci guda kamar ba ita ba,ba qaramin duka mutuwar daddy tayi mata ba,fuskarta a sake ta amshi ayshan har hakan ya bata mamaki,don bata tsammaci haka daga gareta ba
"Allah ya kiyaye hanya yasa aje a sa'a" mummyn ta fada cikin sanyin jiki,abinda bai taba hadata da mummyn ba,jakarta ta bude ta ciro kudi dubu dari da khalipha ya bata ta basu ta miqawa mummyn,kai ta girgiza
"Bazan iya karbar komai naki ba ayshah,na gode"
"Idan kika ce haka nima baki daukeni kaman asma'u ba kenan?" Kai ta kada hawaye na cika idanunta ta amsa
"Allah yayi miki albarka,ki yafemin aysha dukkan wata cutarwa dana taba yi miki a rayuwa,shaidan ya rufe idanuna,a sanda kike kyautata min idanuna sun rufe,bana ganin dukkan wani alkhairi naki,duk yadda kika kai ga kyautata mana bamu qareki da komai ba face sharri da makirci da muke bibiyarki dashi,mutuwar daddy babbar izina ce a wajena,tabbas dan adam ba'a bakin komai yake ba"
"Ban taba riqonki ba mummy dai dai da rana daya,na yafemiki mummy,Allah ya yafe mana gaba daya" da haka ta fito daga gidan jikinta a sanyaye,daga nan gidan anty safiyya ya kaita,sosai tayi murna da zuwan ayshan,ta dan jima zaune suna hira da ita,sannan ta gaya mata zancan tafiyarsu gobe,sosai ta mata fatan alkhairi
"Nikam kaman qiba naga kin soma aysha,karfa ki zama bindiga?" Murmushi ta saki
"Haba anty,nida na rasa uba wacce qiba zanyi?"murmushi anty safiyya tayi,har cikin zuciyarta tana jin dadin dace da aysha tayi
" ba daga nan take ba aysha,shi ciwon mutuwa Allah yake daukewa bawa shi,banda haka da mutane da dama sun hallaka saboda ciwon rasuwar makusantansu,kekam kinyi haquri a rayuwarki wanda ya zamemiki alkhairi"sai tayi shuru tana aje numfashi,ta gefe guda tana jin tausayin asma'u,tana jin ciwon rayuwar da take ciki,saidai bata karanci komai na nadamarta ko rashin nadamarta ba
"Ki daure ki yafewa asma'u koda bata nemi yafiyarki ba,ki kuma sanyata a addu'a"
"Ni babu komai tsakanina da ita anty,kusan zan iya cewa itace silar matakin dana ke kai yanzu"
"Batayi don alkhairi ya sameki ba,amma dai ki daure ki yafe mata"
"Nikam na yafe mata duniya da lahira" saida khalipha ya kirata sannan ta fito suka tafi.


Suna shirin kwanciya bacci saiga kiran anni ya shigo wayar ayshan,a ladabce cikin kulawa suka gaisa
"Bani khaliphan aysha na kira lambarsa a kashe"
"Toh anni" ta fada tana miqa masa dai dai sanda yake fitowa daga wanka,amsar wayar yayi da daya hannun nashi dayan kuma ya janyota cikin jikinshi ya rungumeta,runtse idanu tayi sanda fatar jikinta ta hadu da tashi,lemar ruwan dake gashin qirjinsa ta ratsa towel din jikinta zuwa fatarta,suna tsaye a haka suka gama gaisawa da annin
"Idris ne fa ba lafiya"idanunsa ya dan lumshe,ko sunanshi baison ji
"wanne idris"
"Gidanku,idris kawunka mana,bashi da lafiya sosai yana jin jiki,lafiya akwa kwanta dashi sai ihunshi aka ji,yanzu haka yana asibi an kwantar dashi,kayi qoqari gobe kafin ku wuce kuje ku dubashi"
"Zanje in sha Allahu"
"Yauwa saida safe"
"Allah ya bamu alkhairi" ya kashe wayar yana sake jan ayshan cikin jikinsa yana sauke ajiyar zuciya,dukkaninsu shuru sukayi,tasan yanzun zaya shiga damuwa daga ambato masa sunan idris,daga bisani ayshan ta juyo da wani irin hanzari ta rungumeshi sosai tana cusa kanta cikin qirjinsa,da qafa daya ta janyo tum tum din dake gefansu ta haye sannan ta samu tsahonsu yazo daya,saita riqe kanshi sosai ta hada hancinsa da nata,bakinta tasa tadan ciji lebansa kadan saiya saki qara
"Wayyo bakina anni zata cinye miki bakin yaro" dariya ta qyalqyale da ita tana daneshi
"Kasan kaci bashina jiya,kuma saika biya?...." Bai barta ta qarasa maganarba ya dauketa cak ya cilla saman gado ya bita yana cewa
"Aga matsoraci tsakanina dake,ke kike tsoron biyan bashi bani ba" tattare jikinta ta soma yi tana dariya gami da bashi haquri,bai yarda ba saida suka fafata ya gajiyar da ita tubus sannan yace ya haqura,tayi shuru na maida numfashin kokawar daya sanyata,tana jin dadi cikin zuciyarta na nasarar shafe masa bacin ran daya so yin tasiri cikin zuciyarsa data yi
"Yarinyar nan qiba naga kin fara yi fa" khalipha ya fada yana dora kanshi saman cinyarta,gami da zagaye qungunta da hannayensa,baki ta zumburo
"Ni ba wani qiba,bayan kaine duk ka hanani qibar,kai baka ga yadda ka soma tumbi ba" qayataccen murmushi ya saki yana maida kwanciyarshi rigingine yana shafa cikinsa da tafin hannunsa daya,ta yadda hakan ya bashi damar kallon fuskarta sosai
"Ni aike nakeso na gani da tumbi,irin tumbin da zaki bani baby fa" kukan shagwaba ta sake masa tana bubbuga hannayenta
"Da wuyafa ya khalipha da wuya..." Dariya ya saki
"Kinsan kuwa jiya nayi mafarki kin haifamin twince masu kama dani?kuma duk mata"
"Sonkai?" Ta fada tana zaro ido tana dariya
"Kona tashi maza zan haifa masu kama da anni koni" idonshi shima ya waro
"Da gaske baby girl nakeso ki haifamin uwaisha..."
"Ni kuma baby boy nakeso,so nake na haifa daddy"
"Shikenan,idan kika haifa mace ni zan saka mata suna,idan namiji ne ke zaki saka"
"Na yarda"
"Mu qulla alqawari" ya fada yana miqa mata qarmin yatsanshi,sai ta miqa masa ita wanda ya shammaceta ya jawota ya maye gurbinta.
[3/21, 2:50 PM] +234 809 228 8954: 59



Qarfe goma da wani abu na safiya suke takawa cikin asibitin hannayensu sarqafe da juna,duk wanda ya kallesu saiya sake juyawa ya dubesu,kana kallonsu kasan cewa masoya kuma ma'auratan da suka dace da juna,ba qaramin kyau sukayi ba,shi yana sanye da suit yayin da take sanye da atamfa dinkin doguwar riga,fuskarta tayi wani irin kyau,tayi fresh abinta saika dauka wani makeup tayi,saidai babu komai a fuskar tata sai powder kwalli da man lebe,gab da zasu shiga cikin asibitin ya daga waya ya kira annin ya tambayeta dakin da aka kwantar da kawu idris ta gaya mishi,ya kashe wayar ya maida aljihunsa yana sakin ajiyar zuciya,hannunshi ta riqe sosai tsam saboda tasan yanzun ranshi zaya baci,tasanya daya hannun nata ta zare glass din fuskarta ta lanqwasheshi cikin hannunta,juyowa yayi suka hada idanu saita narke masa tana tsayawa daga takawar da suke zuwa cikin asibitin,gira ya daga mata alamar tambaya,a shagwabe tace dashi
"Ya khalipha pls mana,idan kasan ranka zaya baci ba zaka saki ranka ba ka tsaya ni na shiga,sai na gawa anni kai baka shiga ba" kai.ya kada yana sake mata murmushi,ya kashe mata idonsa daya
"Noo princess uwaisha....muje" da haka suka ci gaba da takawa.


Tun daga varender da dakin yake suka dinga jiyo ihu,haka suka dinga takawa har zuwa bakin dakin,wasu daga cikin yaranshi da 'yan uwa ne tsaitsaye bakin qofar dakin jugum jugum,duk wanda ka kalla alamun tashin hankali ya bayyana qarara a fuskarshi,hango khalipha ya sanya sukayo wajenshi suna mishi sannu da zuwa,amsawa yayi yana zare glass din fuskarsa gami da kallon qofar dakin da ihun ke fitowa,zame hannun aysha yayi daha cikin nashi yadan sunkuya saitin kunneta
"Ki tsaya anan yanzu zan fito" kai ta gyada jikinta a sanyaye itama,bisa dukkan alamu mai mara lafiyan ne ke wannan ihun da qarajin.


Tura qofar dakin yayi bakinsa dauke da sallama,duk da ihun da kawu idris yake kwararawa bazai bari aji sallamar ba,ibrahim ne yake riqe dashi,matarsa tana gefe tana zubda qwalla,tsayawa yayi khalipha yayi yana dubanshi
"Ibrahim nace maka ka kwaramin ruwa,cikina...wuta ce,wutace take ci ajikina,baka ganta ba,nace baka ganta ba,jikina zafi yake min ibrahim jikina"
"Sakeshi" khalipha ya fada yana duban kawu idriss din,sakinsa ibrahim yayi yana share gumi da qwalla,addu'a ya soma yi yana tofa masa a jikinsa, hankali zafin da yakeji ya ragu sosai,ihun da yake ya tsaya sai qananun surutai
"Na gode khalipha,na gode" ya dinga maimaitawa,kana ji kasan sambatu yake
"Na gode khalipha ka yafemin naci dukiyarku,na cinye dukiyarku,nina kasheshi,nina kashesheki" gabansa ne yayi mummunan faduwar,sai ya zuba mishi idanu,a hankali ya bude bakinsa
"Kai ka kashe wa?"
"Babanku sa'idu,nine dasu hamza suka qi saina kasheshi ni kadai,saboda inason ayshatu inason na aureta" wani irin tuquqi yaji qirjinsa yanayi,take idanunshi suka sauya kala,sannu sannu ya dinga ja baya yana kallonshi,ya yunquro zai cafko khaliphan yana cewa
"ka tsaya karka tafi,tofamin addu'a tofamin,zafin da nakeji ya dawo....ka tsaya mana" juyawa yayi ya fice idanunsa jajur,tashin hankalin daya ji ba kadan bane a sannan,mutuwar babanshi da hajar ta dawo masa sabuwa fil,cikin wani irin zafin nama ya ja hannun aysha ba tare daya waiwaya ya dubi kowa ba suka fice yana jiyo ihun idriss.


Tunda suka sauka a gidansu na cyprus ta kasa gane kanshi,duk wani abu tayi amma ba canji,data gaji kawai saita zauna ta sanya mishi kuka,a rude a janyota jikinsa yana tambayarta
"Meya faru uwaisha?,nine ko?,am sorry kiyi haquri,uwaisha.....shi ya kashemin abba na,me yayi masa haka arayuwa bayan tarin alkhairai daya musu?"sosai maganar ta daketa,saita daga kai tana dubanshi,yau taga ahalin da suka fi nata zalunci,taga ahalin da suka dara nata ahalin mugunta da watsi da zumuncin Allah,maganar ta kidimata,saidai ya zama dole ta rage razanar data yi saboda ta maidashi cikin mode dinshi
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,gaskiya ne ya aikata babban xalunci akan ran da bata jiba bata gani ba,abba ajalinsa ya riya yazo,koda kawu idris ko babu shi tilas saiya tafi,tsakaninka da abba yanzu haka addu'a ce,haqiqa Allah baya barin wanda ya kashe wata rai ba tare data cancanci hakan ba,ka zuba ido kaga shima zai tabbata ne a duniya?,komai daren dadewa sai ya tafi inda abban yaje" da kalamai masu dadi tayi amfani ta samu kanshi,ya dinga sauke ajiyar zuciya ajejjere,tsananin fushi bacin rai da rudanin daya shiga suna sauka.


Gab da zasu kwanta wayarshi ta dauki kida,ya duba sai yaga haidar ne
"Ya akayi haidar,ina fata kowa lafiya"
"Eh mukam lpy lau,kawu idris ne ya wuce,baku jima da barin asibitin ba yarasu"idanunsa khalipha ya lumshe,maganganun aysha na dawo masa fes aka,kamar a sannan take gaya mishi,sautin haidar shi ya katse masa tunaninsa
" yaya mutanen nan Allah ne kadai yasan zunubin da suka aikata bayan dukiyarmu da suka cinye,kasan gaba daya fuskar kawu idris tayi baqi?,har ya mutu bai daina kiran cikinsa wuta naci a ciki ba?"
"Allah ya riga daya fada ya kuma gargademu cewa,duk wanda yake cin dukiyar maraya da zalunci haqiqa wuta yake ci a cikinsa,da sannu kuma xai shiga wutar sa'ira,zai iya yiwuwa Allah ya nuna ishararsa ne saboda sauran abokan barnarsa su kawu hamza dake raye"
"Sun girgiza ya khalipha.....kafin a dauki gawar kawu idriss saida suka warwarewa anni komai suna kuka wiwi da neman gafararta saboda yadda sukaga gawar kawu idris ta koma,ya tabbata su suka jefamu a halin talauci a baya,su suka tattare komai namu suka cinye"
"Ai ubangiji baya bacci,kuma gashinan sun gani zahiri,Allah yasa mu dace,yasa muyi kyakkyawan qarshe"
"Amin ya Allah yaya" daga haka sukayi sallama ya kashe wayar yana ajiyar zuciya,gaskiya ne Allah baya zalunci daidai da qwayar xarra,ko yaya ka zalunci musulmi ko kaci masa haqqinsa koda qwayar gero ce bakai ba aljanna saika biyashi,koda iya ladar data rage maka kenan ka shiga aljanna ba ruwan ubangiji saika biya haqqin wani daka ci.


A haka aysha ta shigo dauke da coffe sai tururi yake
"Ya khalipha....."
"Shshshshs...." Ya fada yana katseta
"Daga yau banason wannan sunan,yanzu fa haidar ya gama cemin yaya kema ki fada,meye banbancin kenan?" Ya fada yana dage girarshi yana kallonta,wani sassanyar murmushi daya ratsa zuciyarshi ta saki tana aje coffen a gefanshi,cikin zuciyarta tana jin dadin yadda ya sake,gadon ta hau sosai ta kama hannayensa gaba daya cikin lallausan tafin hannunta tana murmushi
"Ka zabi dukkan sunan da kakeso ni kuma zan kiraka dashi ko a gaban waye" murmushin shima ya saki,yana jin dadin yadda take fifitashi fiye da kowa,take fifitashi fiye da duk abinda takeso a duniya,take zabar farincikinsa saman nata,kamo fuskarta yayi ya sumbaci goshinta cikin alfahari da ita
"Na baki zabi matata,na amince miki ki zaba min dukkan sunan daya dace da ra'ayinki" murmushi ta sakar masa tana matsa 'yan yatsunshi
"Bazan iyakance wani suna qwaya daya da zan kiraka dashi ba,ka cancanci dukkan wani suna dake nuna qauna da soyayya your royal highness" idanu ya zaro yana jin dadj,ba shakka ta cika mace ta gari macen qwarai,wanda ma'aiki S A W yace idan ka kalleta zata faranta maka,idan ka umarceta zata yi maka biyayya,idan kayi rantsuwa zata kubutar dakai,idan kayi tafiya ko baka nan zata kare maka kanta da dukiyarta,shikam me zaya ce da ubangijinsa banda godiya?.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Da sallama ya shigo dakin nata bayan ya bar mahaifiyarshi da qannenshi a babban falon gidan,a hankali ta sauke ajiyar zuciya bayan dogon tunanin data gama yi kana ta dago tana dubanshi,gaba daya daddy kafin rasuwarshi ya gama yi mata dabaibayi da kalamanshi kamar yana sane da abinda take shiryawa na barin gidan hamid,ya gaya mata cewa muddin babu ce zata sanyata barin aurenta indai shi ya haifeta bai yafe mata ba,matuqar mijinta na bata kulawa iyakar qarfinsa to yana umartarta ta zauna gidanta,saidai idan yazo da wata cutarwa da shafeta ko addininta,to a yanzun hamid din ya sauya,ba rashin ci babu rashin sha,duk da cewa duk wani jin dadi dada yake dashi yanzu babu,dalili kenan daya sanya yawan yawan halayensa sauyawa,saidai ita sam ya fita a kanta,kallonshi kawai take.


Da tausayinta kan fuskarshi ya zauna hannun kujerar da take kai,yanzun ya gama tsawatarwa qannenshi kan rashin kunyar da suke mata
"Kiyi haquri asma'u,na tsawatar musu kuma in sha Allahu daga yanzu hakan ba zata sake faruwa ba,kimin addu'a Allah ya sake buda min ba don halina ba,in daukeki na sauya miki gida" kallonshi kawai tayi ta miqe ta shige bedroom dinta,yayin da shima ya bita da kallo,gaba daya ta sauya tun daga mutuwar daddyn tayi wani mugun sanyi,sai ya miqe ya bita,tana zaune gefan gado,kallonshi take da mamaki don ta manta yaushe rabon da tayi masa irin hakan ya biyota
"Ki daure ki yafemin asma'u,nasan cewa harda haqqinki na takureki da nakeyi da rashin wadataki bayan ina da damar haka shi yasa Allah ya jarabceni,duk da cewa ni maison kudi ne amma takaicin yadda kika dinga tatsata,quru quru ya bayyana ba don Allah kikesona ba,hakanan ba zaki aureni ba idan ban miki barin kudi ba yasa nima ma takuraki sanda mukayi auren,ashe Allah ba ruwanshi,na sauke haqqinki kawai dake kaina shine mafitata,ki yafemin asma'u don Allah" kwanciya tayi kawai ta juya mishi baya,a zuciyarta tanason tayi yaqi da khalipha ta karbi hamid,saidai hakan na nufin su zauna a qaramar rayuwa?,to idan ma bata amshi hamid ba ya za'ayi ya samu khalipha?,mutumin data tabbatar daya tsallake baya qasar,ko baya ga haka ita kanta idan ta zauna tana tuna abubuwan da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login