Showing 147001 words to 150000 words out of 171357 words

Chapter 50 - Daurin Boye Book One Complete Hausa Novel

ganinki saini kadai" murmushi ta saki mai taushi,harga Allah kalaman khalipha ko da yaushe na sake dilmiyata ne cikin kogin qaunarshi,koda yashe kalamansa na sake nuna mata itama cikakkiyar macace wadda ta cancanci taso kuma a sota
"Ina godewa Allah koda yaushe daya qaddara zaka wanzu cikin rayuwata" shima murmushi yake mata,yana jin kaman ya janyota jikinss,saidai yana tsoron kada qiluta jawo bau,duk da yana fata komai yazo qarshe,saiya daga pillow din kujerar da yayi matashin kai dashi,ya ciro passport ya buda sannan ya miqa mata,hannu ta saka ta amsa,gabanta na faduwa zuciyarta na dukan uku uku,addu'a take Allah dai yasa ba cewa zaiyi zai koma ba,idanunta takai kai,visa ce ta shiga qasar saudiyya,wadda bata kowa bace face tata,idanu ta fiddo zuciyarta kamar zata fito,babban burinta a duniya?,mafarkinta ne zai zama gaskiya koko dai?,kai ta daga tana dubanshi da alamun tambaya,shima ya tattara dukkan hankalinsa da nutsuwarshi akanta,farinciki na ratsashi sakamakon farincikin daya sanyata a ciki
"Ya khalipha....da gaske?" Kai ya jinjina mata
"Da gaske ne uwaishata,rana ita yau in sha Allahu zamu tafi,kije ki gayawa Allah dukkan matsalolinki da damuwarki tsakaninki dashi,sannan mu roqawa kanmu samun dukkan wata rayuwa ta farinciki da ma'aurata kewa kansu fata,ya bamu zuriyya ta gari,yasa zamu fara rayuwarmu a sa'a" rungume passport din kawai tayi a qirjinta ruwan hawaye na bin kuncinta,abinda bata taba tsammatarsa ba cikin rayuwarta,dubanshi kawai take ta rasa bakin magana,idan ta bude baki ma me zata mishi?,dukkan wata kalma da zata fada ya riga daya saba jinta,walau a bakinta ko a bakunan al'umma,ya fahimci haka,saboda haka saiya ware mata dukkan hannayenshi alamar ta taho,ba taba lokaci kuwa ta kwasa zuwa gareshi ta zube a jikinsa tana sheshsheqar kuka,hannunshi ya sanya ya zame dankwalinta wanda tun dazu dama yaso zamewar ta hanashi,ya dinga shafar gashin kanta kawai yana shaqar qamshin jikinta,ganin ta kasa shuru sai ya soma rada mata
"So kike ki fasamin zuciyata kenan" idanunta dage jiqe da hawaye ta dago ta dubeshi dasu,saiya kanne mata ido daya yana murmushi
"Eh mana,kinsan abu mafi muni da kunnuwana zasu ji shine sautin kukanki?" Jin yace haka saitayi qoqarin hadiye kukan,ta kwantar da kanta saman qirjinsa tana goge hawayenta
"Na rasa me zance maka ne,na rasa me zanyi,dukkan wata kalma da zan fada gani nake bata gamsar ba,ka zamemin fitila a rayuwata,ka zamarmin haske mai kore duhu,kai daya ka bani farinciki da daruruwan mutane suka kasa bani,dame zan saka maka nikuwa aysha bayan bani da komai ban mallaki komai ba"
"Ke kike da komai,kuma kece kika mallaki komai" saitayi shuru tana sauraronsa gami da tunanin abinda yace
"Zuciyarki rayuwarki da gangar jikinki nakeso ki mallakamin,ki bani dukkan wata yardarki,ki soni ki qaunaceni,kici gaba kuma da sona domin Allah kamar yadda kikayi a baya" cikin sanyi da kwantar da murya tace
"Indai wannan ne ka gama samunshi har gaban abada"
"Kinyi alqawari?" Saita zauna sosai tana dubanshi cikin ido,wanda hakan ya sanyashi shima gyara zamanshi yana dubanta
"Duk duniya babu wanda ya cancanci samun wannan matsayin sama dakai,idan ma akwaishi bana fatan Allah ya nuna minshi har abada,zan rayu dakai cikin kowanne irin yanayi,bana fata na saba maka dai dai da rana guda kona sauya maka matsayi daga wanda na doraka akai a yanzu,idan wannan yana cikin qaddarata shima ina roqon Allah ya dauki raina kafin lokacin" wani murmushi ya saki,yana jin wani farinciki na ratsashi,tabbas baiyi wuyar banza ba,addu'a bata faduwa qasa banza,hakanan dama Allah yake lamarinshi,haka ya fada cikin qur'aninsa _sau da yawa zaku qi abu amma alkhairi ne a tare daku_ gashinan tabbas hakan ya tabbata a kanshi,saitin zuciyarshi ya dafe da d'aya hannun nasa
"Karki kasheni ni mana tun yanzu,idan kika mutu uwaisha in zauna dawa?" Yadda yayin ya bata dariya,saita saki murmushi mai sauti tana dubanshi sanda yake cusa hannunshi cikin aljihun wandonshi ya ciro wani dan qaramin akwati mai kyau,tana kallonshi ya bude,ya ciro wata nannadaddiyar dubu daya da aka yiwa ninki mai kyau,saiya dagata yana dubanta sannan ya dubi ayshan
"Kin tuna wannan?" Kudin hannun nashi sosai ta kalla kana ta dubeshi tana dan tabe baki gami da girgiza kai,wani kishi take ji yana dan sukarta,tana tunanin ko wata budurwarshi ce ta bashi?,murmushi ya saki yana maidata ciki sannan ya dubi ayshan
"Tun daga ranar da kika bada ita a matsayin biyan bashi a gareni na tabbatar da cewa akwai banbanci mai tarin gaske tsakaninki da asma'u,sannan akwai wata boyayyar halayya da baiwa da kike da ita data sha banban data sauran mata,yau bari na baki labarin da baki sani ba" daiya gyara zamanshi yana daukar cup din coffen data zuba mishi ya kurba,sannan ya soma bata labarin dukkan 'yammatan daya tabayi da yadda suka qarke dasu,mamaki.ne ya kama ayaha,tsoron duniya da mutanen cikinta ya sake kamata,kowa ya lalace?,kowa mai kudi yakeso?,idan a familynka ne sai.kana dashi kake sa wata babbar daraja?,idan saurayine kai ko qur'ani kake hadiya saboda sanin Allah da tsoronshi ba mai baka aure idan baka tara koka aje ba koda kana da sana'ar rufawa kai asiri?,wannan wacce iriyar rayuwace mukeyi?,tunaninta ya katse mata sanda ya tura mata system dinshi gabanta yace
"Duba" ba musu taja ta soma dubawa,order ne da yayi mata daga store na rahamalls wanda tuni suka iso,har an bude katafaren wajen siyayya gashinan da hotunansu an tsara komai dauke da sunan UWAISHAH MALL
"Duk abinda kika gani a nan naki ne humairah ke na tanadarwa,na yiwa kaina wannan alqawarin tunda dadewa bawai yanzu ba,nayi alqawarin ninka miki dubu dayanki tun ba yanzu ba,wannan shine tukuicin da nayi niyyar yi miki a matsayin taimakon da kika yimin sanda ake bina bashin dari biyar kika sadaukar min da dubu daya duk da bakisan waye ba ni" kasa magana tayi wannan karonma,sai ta rufe bakinta kawai da tafukan hannayenta,kai ya girgiza yana jifanta da tattausan murmushinsa
"Karki ce komai,don bana buqata,na riga dana gaya miki abinda nake da buqata" ya fada yana ware hannayenshi,sai kawai ta rungumeshi tana sakin kuka.



Tafe suke a motarshi saidai kana duban fuskarta kasan tsantsar baqinciki da bacin rai ke cinta,a yanzu ba abinda ta tsana irin auren hamid,neman kawai hanyar da zata yakiceshi take,saidai ta lura da idan natayi takatsantsan ba haqarta ba zata taba cimma ruwa ba.


Daga barkar haihuwa suke wanda ita sam batasan ma wadda suka jewa barkar ba,saidai ta cika da mamakin uban kayan da hamid ya siya din yakai,dama shidin ba dai neman suna da son burgewa da gwaninta ba,tunda sukayi aure bai taba yi mata siyayya irin hakan ba,sai gashi yayi ya kaiwa wasu,dai dai nan wayarshi ta dauki kuwwa,ganin kiran babanshi ne ya sanyashi dagawa,bayanin da daddyn nashi yayi masa ya daga masa hankali qwarai,ya tabbatar cewa gagarumar matsala ce take fuskantosu
"Yanzu daddy meye mafita?,ya zamuyi?"
"Ya kamata mu soma dakatar dashi,yanzu haka ancemin yana gidansa,idan kana kusa ka sameni nan titin lodge road saimu qarasa mu bashi haquri,ko qafa ne muce ya daga mana sai muyi tunanin abinda zamuyi a dan taqin"
"Shikenan daddy ganinan zuwa yanzu,ina kundila amma bari na qaraso"

*_wanan littafin na kudi ne,idan kika gani don girman Allah karki tura,ga mai buqatar siya ya tuntubi wannan number_*

08030811300


*mrs muhammad ce*👑
56

Cikin satin kafin tafiyarsu umara wani irin sabo da shaquwa mai qarfi ya shiga tsakaninsu,qaunar khalipha babu inda bata jinta cikin jiki da jininta,bata taba sanin tayi nisa a qaunarshi ba sai yanzu,haka ta nashi fannin ya gama sallamawa gaba daya,hakanan ya gama tafiya,dukkan wasu hakaye na aysha wadanda baisan dasu ba a yanzu ya karancesu,komai nata yayi masa,komai nata yadda yakeso ne,irin matar da yake mafarki da fata gami da burin aure a yanzu ya samu,wani lokaci yakanji kanshi kamar bashi ba,ayshan ta sauya dukkan wanin tunani nasa,burinta ya zama nashi nashi ya zama nata,qiris yake jira su zama abu guda,sai yanzu yake jinsa cikin wata sabuwar duniya,jinsa yake kamar an sauyashi,kamar ba shine khalipha ba na ainihi,ta wanke masa duk wani burbushin bacin rai da yayi saura a rayuwarshi,shi yasa yake da fata da kuma burin ya zama silar wankewar duk wata damuwa tata da tayi saura a zuciyarta.


Ana ya gobe zasu tafi da daddare ya sanyata ta shirya don ya kaita suyi sallama da daddy,tsaf ta shirya tayi adonta kamar yadda ta saba ya kuma zame mata jiki dai dai misali mai sanyi ba hayaniya,shi kansa khaliphan yayi kyau cikin shaddar daya buga,ya kawo hularshi gaban goshi shigar cikakken bakano abun sai wanda ya gani 🤪.


Tare suka jero shida ita,duk wanda ya gansu a lokacin saiya juya ya sake dubansu,cikakkun masoyan da sukayi nutso duniyar soyayya suka dandana zaqinta,masoyan da tun a siffa da kama suka dace da juna zuwa ga halaye,bude mishi motar akayi saiya matsa mata ita ta shiga,shi kuma ya bude da kanshi sannan suka rufe suka tada motocin suka fice.


Itace a gaba kai tsaye zuwa sashen daddyn,saboda tun a harabar gidan mai gadin ya shaida mata mummyn na can sashen,dawowa tayi ta shaidawa khalipha saiya gyada kai
"Ki fara shiga ki sanar mishi shigowata ko?,kaman hakan yafi tsari"
"To" ta amsa mishi tana juyawa saiya bita da kallo
"Uwaishahh..." Ya kirata,ta waiwayo tana murmushi can qasan ranta,don idan da sabo ta saba,don khalipha saiya kirata sau nawa kafin taje waje musamman idan tayi kwalliya,kawai sai yace tafiyarta yakeson kalla,ko kuma kai kawonta yakeson gani,hakan kawai ya isheshi abun farinciki,saitinshi ta ranqwafo,saiya miqa hannunashi saitin bakinta
"Ciromin sweet dita,yanzu yaci ace kinsha rabi aiko?" Murmushi ta saki,cikin motarshi ta dauka,suna nan sunfi talatin,amma kawai bazai sha ba sai wadda tasha ta rage
"Kayi haquri ka barmin wannan ka dauki wata mana ya khalipha"ta fada tana langabe kai
"aifa bazaiyiwu ba,amma.idan kina so zan.barmikin,saidai da sharadi" sai yayi qasa da muryarshi yadda ita dashi ne kawai zasuji abinda yace mata,kunya ta tilastata rufe fuskarta da hannayenta tana son tashi a wajen amma ya danne mayafinta
"If kin yarda nima nafison hakan,saboda wannan bakin yafi sweet din dadi nesa ba kusa ba" da sauri ta ciro alewar daga bakinta tana miqa mishi,saiya turbune fuska kadan yana kallonta bayan ya narke kamar qaramin yaro
"Rowa ko?,tona fasa shan sweet dinma"
"Am sorry ba haka bane,yi haquri ka amsa kasha" hannu ya sanya ya karba alewar ya saka a bakinsa,sai ya lumshe ido yana cewa
"Nifa ban taba sanin haka alewar nan keda dadi ba saida kema kika soma sha,duk sanda ta taba miyan bakinki kamar yana qara mata dadi ne" dariya ta saki sosai tana ficewa a wajen,indai khalipha ne yanzu zai shagaltar da ita,tana murmushi gami da miqa godiyarta ga sarki Allah daya mata baiwa da miji irin khalipha har ta isa sashen daddy.


Asma'u dake tsaye can gefen wasu shukoki tana ganin abinda ke faruwa ta saki ajiyar zuciya,wani sashe na zuciyarta na bata qwarin gwiwar tunkarar khaliphan,komai nashi yayi mata,dukkan wani abu da take bida ta ganshi tattare da shi,matuqar zai amince mata kashe aurenta ba wani abu bane mai wahala a wajenta,bare a yanzu da take jin auren tamkar ana dorata saman qaya ne,ko qawaye yanzu ta yanke alaqa da kowa,don kada ma wani ya rabeta ya fahimci halin da take ciki,kayan da daddy ya mata order tuni sun taru sunci uwar kayan da kudin ita da qawaye tun suna wancan gidan nasu,bata iya adani ba,bata iya tattali ba,batasan ta juya biyar ta koma goma ba,ta riga ta saba tun agida saidai ta bid'a a bata,takowa ta dinga yi har zuwa inda khalipha ke zaune cikin motar tayi knocking,ya tsammaci aysha ce saiya sauke gilashin yana murmushi,idanu biyu sukayi da asma'u,take yayi gaggawar gimtse fuskarshi yana dubanta
"Ranka ya dade yau kaine a gidan namu da kanka?"
"Eh...yaron oga ne da 'yar aikin gidan sukazo gaida mai gidan" saita danyi dum saboda tasan magana dai yake gaya mata,cikin barikanci tace
"Banda dai tuna baya,abinda ya wuce ya riga daya wuce,na baka haquri amma na fuskanci har yau baka haqura ba" tsaki yaja yana shirin daga gilasanshi saboda sauraton tama sam baida amfani saita dafe cikin karyewar zuciya
"Don Allah khalipha kayi haquri,ka taimaka ka karbeni kamar yadda ka amshi aysha,ba sonta kake ba tun asali nice wadda kakeso,qaddara ita takawo faruwar komai,kai kadai kai zaka cikamin burina"
"Burinki na kudi ko?,baki da matsala waisaita kudi ne?,a duniya babu wani abu mai daraja bayan kudi?,inasom in miki gargadi na qarshe kar bakinki ya sake kuskuren cewa bana son aysha na aureta,har abada aysha itace zabina,tun kafin nasanta nake qaunarta,tin kafin nasan zatazo cikin qaddarata nakesonta,kin fahimta?"
"Kamar yaya?" Ta yiwa kanta tambayar,saidai bai tsaya bata amsa ba yadaga gilasanshi yana jan tsaki ranshi yana baci,wato a rayuwa ma ka aikatawa mutum ba dai dai ba kazo daga bisani kana jin kunyarshi ka rahama ne?,wannan kenan na nuna zuciyarka akwai ragowar danshi,idanunka basu qarasa qeqashewa ba.


Kallo daya tayi masa tasan yauma baida lpy,hankalinta ya tashi sosai,tunda yayi wancan rashin lafiyar kullum saita kirashi amma ko sau daya bai taba nuna mata yana kwance ba,amma saboda qarfin hali irin na daddy nuna mata yake ba komai,ta sanar mishi tarr da khalipha suke,yace
"maza shigo dashi mana indo,yaron kirki dan albarka".


Tana juyawa daga wajen motar sukaci karo da aysha,kallon data jefa mata shi ya sanya jikin ayshan ya bata akwai wata a qasa,me take jikin motar khalipha?,tasan halin asma'u sarai shekarun da suka diba gida daya ba wasa bane,saita gifta ayshan ba tare data ce mata komai ba,itama ganin haka yasa ta kama kanta tunda tasan ba wani abu data yi mata.


Tare suka jero har cikin parlour din,a sannan mummy na zaune tana hada magunganan daddy daya gama sha,idanunta kan khalipha sanda yake gaisheta,banbanci muraran ta ganshi,qyashi ya cika ranta,saita kasa zama tabar musu falon ta koma sashenta,wanda hakan ya basu damar hira sosai duka su ukun harda khalipha,irin hirar da zata ce ma bata tabayinta da daddy ba,har tayi mamakin dadewarsu sanda suka tashi zasu tafi suna mishi sallama kan gobe zasu wuce umara,dai dai sanda asma'u ta shigo falon,sai ta samu waje ta zauna tana jinsu,cikin farinciki daddy yayiwa ayshan murna,saboda yasa yunqurin kaita sai mummy ta sako wasu qorafe qorafe da zai sanya a dage zuwan da ita koda daddyn bai shiryawa hakan ba
"Uhmmm,ba sabanba,su umara manya,kai bawa da baka taba zuwa ba daka shiga uku" asma'u ta fada qasa qasa yadda ayshan zata jiyota,murmushi tayi sannan itama ta mayar matan ta yadda zata jita da kyau
"Mun godewa Allah da bai banbanta saudiyyan masu kudi da talakawa ba,duka dai gurin daya ne inda kaje nima can zani,Allah ya kirani babu damar dakatarwa" saita miqe ta isa gaban daddy tana masa sallama bayan fitar khalipha wanda yadan basu waje ne suyi sallama
"Allah ya qara maka lafiya daddy,bansan wanne irin abu zan saka maka dashi ba a rayuwarta,don Allah daddy ka tambayi koda abu daya ne a wajena wanda kake buqata daga gareni" murmushi ya saki
"Aysha indo har kullum kedin ta dabance,haka Allah yake tsarinsa cikin halittunsa saiya fifita wani kan wani,dukkan abinda nayi miki nayi miki ne Saboda Allah,na miki saboda a lokacin kina cancanci kuma kina da buqatar ayi mikin,abu guda daya da zan nema a gareki shine,ko bayan raina karki manta dani kici gaba da yimin addu'a"zuciyarta ce taji ta karye da kalamanshi,wani rauni ya kamata,take hawaye ya balle mata,asma'u dake zaune gefe ta tabe baki
"Kalen dangin masifa,kamar ta fimu sonshi,sai kace ita ya haifa bamu ba" ta fada a zuciyarta
"Indai xan manta dakai daddy to lallai zan manta da kaina,baka cikin jerin mutanen da zan iya mancewa dasu har numfashina yabar gangar jikina,ubangiji yayi maka jagora a dukka lamuranka duniya da lahira"
"Amin ya Allah ayshatu,idan na taba yi miki wani abu naba daidai ba tsahon zamanki a gidan nan ina neman afuwarki" kuka ta saki sosai harda sheshsheqa
"Daddy niya cancanci na nema afuwarka da zanyi tafiya,ba zaka taba laifi ba awajena daddy koda naman jikina kake yanka kullum"
"Daina kuka ayshatu,ubangiji yayi miki albarka duniya da lahira,idan kinje kimin dawafi na musamman kiyimin addu'a sosai"
"Zan maka addu'a daddy in sha Allahu fiye da yadda zan yiwa kaina"da haka sukayi sallama,haka kawai taji zuciyarta ta karye qwarai,hakanan taji kamar karta tafi,kukan da take yaqi tsayawa har a cikin mota,tun khalipa na daurewa har ya gaza
"uwaishah,ki taimakeni kiyi shuru,har cikin qirjina nakejin ciwon kukan da kikeyi" bata son bata masa rai ko qanqani,hakan ya sanya dole tayi shuru gami da yin luf a qirjinsa,kusan ranar wuni tayi a sanyaye,tunanin daddy fal zuciyarta.


🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Washegarin ranar jirginsu ya daga sai saudiyya,a garin makka suma soma sauka,suna sauka a masaukinsu dukkansu sukayi wanka suka dauki harama,saboda tsabar murna da zumudi ma ta rigashi kammalawa,ji take kaman tayi tsuntsuwa ta ganta bakin ka'aba,tana da abubuwa da yawa da zata roqa,tana da mutanen da takeso ta yiwa addu'a sosai,idanunta a kanshi sanda ya kammala daura hiraminshi,idanu suka hada sai suka sakarwa juna murmushi a kusan tare,kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarshi.


Sati guda sukayi a garin makka,iya ibada kam sunyita saidai fatansu Allah ya amsa,bata taba sanin khaliphan ta fannin ibada jarumi bane sai a wannan karon,duk nacinta da son ibada sai taga ashe ya kere mata,sau tari idan ta gaji tayi kaman zata huta sai taga shi a sannan ya saka qaimi,sai ya sake zaburar da ita,tabbas ta yarda ta kuma amince cewa kowacce mace halayenta idan zama yayi zama na kamanceceniya dana mijinta,kota debi wasu dabi'u nashi koshi ya debi nata,idan akayi katari na gari ne sai nagartarta ta ninku,idan kuma akasin haka ne walau ya rinjayeta ta ko ta koyi kaso mafi yawa daga cikin halayensa,shi yasa akeson ko aboki zakayi ka aboci na qwarai,don annabi ya kwantata aboki na qwarai da misalin mai saida turare ne ko.baka siya ba idan ka zauna dashi dole wataran zai san maka,kaima zakayi qamshi,hakanan nara gurbin aboki tamkar abota da maqeri ne,kana zaune feshin wutar zai dinga sauka atufafinka yana bata maka sutura,hakan shike nuna auren miji na gari shine babbar sa'a hakanan abu mafi muhimmanci da gata da mace zata yiwa kanta da zuriyar da zata samu a nan gaba.


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login