Showing 114001 words to 117000 words out of 171357 words

Chapter 39 - Daurin Boye Book One Complete Hausa Novel

tuni khalipha ya gana hada musu kayansu tsaf,haka ya dauki wasu aliyu da mus'ab suka dauki wasu suka fice daga gidan,har bakin qofa ya musu rakiya yana jifansu da muggan kalamai kala kala,wadanda suka sanya anni zubda qwalla,yayin da khalipha idanunsa suka kada sukayi jawuri saboda bacin rai,zuciyarshi ce kawai ke tafasa,ji yake kaman ya koma ya rufeshi da duka,saidai yasan koda yaso hakan anni ba zata taba barinsa ba.


A bakin layi anni ta sake yanke shawarar suje gidan habibu,sam bayaso yayi musu da ita,hakan ya sanya baice mata komai ba suka kama hanya a qafa,duk da nisan dake tsakanin gidajen haka suka taka har gidan,tun daga yanayin yadda matar gidan ta tarbesu farkon zuwan gidan nasu sukasan cewa akwai babbar matsala,tunda khalipha yaga yadda yaran gidan ke sangarta yasan tafiyarsu ba zata taba dai dai ba,tunda suka je aka zubesu a falo ba wanda yabinta kansu,har aka gama girkin rana a gabansu yaran suka baje suka ci abinsu ba wanda ya basu koda loma daya,a sannan hajar ta soma yatsina fuska tana radawa anni cewa yunwa takeji,haquri annanin ta bata saboda tasan cewa da zarar khalipha yaji ba zaman lafiya saiya samo ya bata,wata iriyar qauna da shaquwa ce tsakaninsa da ita fiye da sauran 'yan uwanta,tun tana yi a boye har khalipha ya fuskanci abinda ke faruwa,tunawa yayi duk cikinsu babu wanda aka yiwa iyaka da abincin gidansu a sanda suke dashi idan sunzo,daga babba har yaro idan yaje kanshi tsaye yake wucewa ya zabi kalar abinda yakeso a dafa masa,sai kawai ya nufi kitchen din gidan da kanshi,yarinyar gidan ya taras (zeenart a sannan)da mai aiki tana dafa mata indomie,ya tambayi mai aikin abinci,budar bakin yarinyar sai cewa tayi
"Ba za'a bayar ba makwadaita kwadayayyu" ta fada tana murguda baki,zuciya ta tasowa khalipha yayi yunqurin danneta sabida fadan anni daya fado masa,sai ya zari plate kawai ya bude tukunya ya zubo abincin ya fito,aikuwa ta biyoshi tana ihun barawo,umma ga barawon abinci bawai kuna don batasan khaliphan ba,kawai tsabar rashin tarbiyya ce.


Mai gidan da tunda sukazo akace musu yana barci bayan sunsan tabbas yaji zuwansu shi ya sauko daga samanshi yana tambayar zeenart din ya akayi
"Alhaji zuwa yayi har kitchen ya diba mana abinci" hannu yasa ya wafci abincin yana rufe khaliphan da fada
"Wannan wanne irin sakarcin banza ne da wofi,saboda tsabar rashin tarbiyya har takai ka dauki abinda ba naka ba ba'a baka ba?,to ni wannan iskancin ba'a gidana ba" haquri anni ta soma bashi khalipha na kallo zuciyarsa na tafasa,sai daya mula don kanshi yana hura hanci yasa aka basu daki,abinci ko yace saidai su jira na dare,saboda bacin rai khalipha wuni yayi a waje bai zauna agidan ba,ba laifi wunin da yayi a waje yayi masa rana,don neman kudi yayi sosai,bai dawo ba sai bayan sallar isha'i,ya shigo gidan a matuqar gajiye,cikin tausayawa anni ke dubanshi,qwalla ce ta cika mata idanu amma saota maida saboda tasan yanzun hankalinsa zai tashi,tuna tsantsar gata da suka samu daga mahaifinsu take,amma yau rana daya rayuwa ta juya musu baya cikin qiftawa da bismillah,dubansu yayi daua bayan daya,ya tambayi kowa lafiya ko suka amsa masa da eh,awara ya ciro mai zafi ya miqawa kowa tashi,saidai ta 'yar lelen tashi hajar daban take,ya qara mata da goba irin manyan nan da yaga tana yawanso,ba qaramin dadi suka jiba kuwa,anni ta dauko wani ragowar abinci cikin kwano ta tura gabanshi
"Ga naka abincin nan kaci mu munci namu,hala ma fushi kake damu tunda ka fita baka dawo ba sai yanzu" murmushin yaqe yayi yana amsawa da annin da a'ah,tunda ya kalli abincin yasan cewa ba qoshi sukayi ba,saboda haka ya juye tashi awarar akai yace kowa ya matso yasa hannu suci abincin yafi albarka.

Da murmushi anni ke dubansu sanda suke cin abincin,ta dago wayon khalipha,zuciyarta cike da tausayinsu da kyakkyawar addu'a da kuma fata da data dinga binshi dashi,ta tabbatar cewa Allah ya bata jarumin d'a,daya tamkar da dubu.


44

Duk da cewa bai tashi a wahala ba bai kuma saba da ita ba amma data riskesu yasa hannu bibbiyu ya karbeta,ya kuma shiga bilhaqqi da gaskiya yana qoqarin ganin farinciki da walwalarsu
"Anni kema kici" khalipha ya fada yana dubanta,kai ta girgiza
"Kuci khalipha,ni cinku shine kwanciyar hankalina" sai shima ya tsame nashi hannun yaqici,sai data lallabashi da qyar sannan ya maida hannun nasa,a hakanma kusan sai suyi loma uku baiyi daya ba.


Zamanta a gidansu zeenart shima dai zama ne maras dadi,zaman qunci da takura,wulaqanci kyara da tsangwama,rashin kunya fitsara da sangarta babu wanda anni bata gani ba daga wajen yaran gidan,tsana da kyara qarara,yayin da khalipha ya dage ta wani fannin,duk hanyar da yasan zai samu kudi indai ta halas ce zaiyi komai kashinta,baida girman kai lalaci ko son jikinsa,amma da yake qasar tamu ga yadda ta zama samun sai addu'a kawai,ana samun amma da qyar,hakanan abinda ake samun bai taka kara ya karya ba,da haka ake jalautawa rayuwar yau fai gobe tsumma.


Barinsu gidan shima sanadiyyar sharrin sata da matar gidan ta dorawa anni,dukka yaran kuma suka dorar da cewa eh sun ga sanda annin ta dauka suna daki ta zaci bacci suke,haka aka musu korar kare a sannan khalipha baya nan ya tafi neman kudinsa,a qofar gidan suka wuni da kaya a gabansu,ga yunwa baci ba sha,sai yamma lis ya dawo ya samesu zube a wajen,cikin gigita ya qaraso wajensu yana tambayarsu
"Anni....lafiya?,me kike anni a waje?,kalli kayanki yadda sukai qura?,wadan nan kayanfa anni ke zakuyi dasu?" Murmushin qarfin hali ta soma saki duk don ta kwantar masa da hankali,haidar da shima ranshi ke bace tun a sannan shi ya shaida masa komao,cikin wani matsanancin fushi ya durfafi gidan gaba daya jijiyoyin kanshi sun tashi saboda bacin rai,cikinnzafin nama anni ta damqoshi,da qyar da iya tsaidashi
"Indai na isa dakai karka taka musu gida,ka wuce mu tafi" tilas ya dakata,saidai zubewa yayi a wajen ya saki kuka,yau ya kasa daurewa,bacin ran dake cin zuciyarsa yayi yawan da bazai iya daureshi ba a yau,hajar ita ta taso tana kuka ganin khaliphan na kuka,ta iso gabanshi ta soma share masa hawayen fuskarshi,kallonta yake rausayinta na kamashi,idan duk su maza ne zasu iya daurewa rayuwa,zasu iya rayuwa koda babu kayan more rayuwa babu qyale qyale ita kuma fa?,ta soma zama budurwa amma babu duk wani kayan alatu kona qyale qyale irin wadda diya mace keda buqata tattare da ita,bayason kukanta ko kadan,sai ya sakar mata murmushi yana riqe hannayenta,miqewa yayi tsaye ba tare daya ce da kowa komai ba ya isa gaban kayansu,ya goya daya ya riqe biyu a hannayensa yayi gaba,shi kadai yasan me yake ji cikin qirji da zuciyarsa,takawa ya soma yi zuwa bakin titi wanda hakan ya sanya suka bishi da sauran kayan.


Mota ya tsare musu,yana fadin sunan unguwar da zasu anni ta dubeshi,yana nufin zasu koma gidansu su zauna ne
"Khalipha,kanaso mu koma gidanmu kenan?"
"Allah yana sane damu anni yana kuma tare damu,mutanen nan dukkaninsu babu wanda zai iya riqemu,babu wanda ya tuna da halaccin abba a garesu sanda yana raye dai dai da rana daya,komawarmu gidanmu shine gata na farko da zamu yiwa kanmu" bata sake tankawa ba,duk da qarancin shekarunsa amma yana da zurfin tunani da kaifin hankali.


Tamkar kango haka gidan ya koma,babu komai a cikinsa,basusan wanda ya shigo ya kwashe sauran furnitures din dake cikin gidan ba,amma koma wane duk yadda akayi yana da spare key din gidan,duba da yanayin ginin gidan gini ne irin na masu kudi mai cike da security,ba yadda suka.iya haka suka gyara sauran abinda ya rage a gidan,suka hadu suka share gidan tas,abinda basu taba ba bazasuma iyaba saboda girmansa masu aiki ke musu,amma yau babu ko mutum daya daya zauna dasu cikin ma'aikatansu kowa ya kama gabanshi.


Khalipha shi yaci gaba da daukar dawainiyarsu,ya hana annin yin komai,duk wani aikin qarfi kona wahala yana ciki,saidai kuma qoqarin nashi yana gazawa,sakamakon dan abinda yake samun bai taka kara ya karya ba bazai wadacesu ba,nan da nan wahala ta sake bayyana muraran ajikinsu,kana kallonsu kasan yunwa ta samu gindin zama a jikinsu,ba'a maganar sutura dama ko karatu duk wannan tuni ya jima da fin qarfinsu,dole anni ta soma sana'a itama,wanda wankau ne zuwa daka,sai ya zamana ba'a samu sosai saboda yanayin yadda unguwar tasu take,uwa uba ma duk wanda ya kalli gidan nasu daga waje zaiyi dariya ne kawai yace rainin hankali akeso a yiwa mutane,jama'ar dake da gida irin wannan me zai kaisu yin wankau ko daka?,hajar ita ke fita maqotan unguwanninsu tana amso musu wankin ko daka ba tare da sanin khalipha ba,ranar daya sani din kiwa kwanan bacin rai yayi,yayi kuka yayi kuka har yaji babu dadi,kanshi kawai yake tuhuma yana ganin kaman qoqarinsa ya gaza,bayan kuma duk wani qoqari yana yinsa,duk wani aiki daya fado hannunsa matuqar bana haram bane to zaiy ya sama musu abinda zasuci koda kuwa kwasar kwata ne,ita kuma anni tausayinsa take,tana ganin wahalar da yakeyi tayi yawa,dalili kenan daya sanya ta kama sana'ar.


Tafi tafi sai aikin qarfin ma ya zama sai kana da hanya ko.kana da wani daya sanka,zaman gida saiya auri khalipha,yanaji yana gani gidan block din aljh idris yayan mahaifinsa yaje neman aiki suka hanashi,anni ita ta bashi shawarar yaje ya sameshi a gida suyi magana wala'alla yasakasu su daukeshi,da fari yaqi saboda shikam ya sare da halayyarsu gaba dayansu ya aje ta tasu a gafe,musamman alhj idris da dukkansu ya fisu mugun hali,daga bisani ne ya amince don baisan me annin ta hango ba.


Randa yaje din yayi kusan awa biyu yana jiran idris din bai bada umarnin ya shigo ba,sai daga bisani ne yaronshi ibrahim wanda baifi shekara daya ya baiwa khalipha ba yazo ya kirashi suka shiga falon alhj idris din tare
"Cire takalmanka mana malam" ibrahim din ya fada yana katsawa khalipha tsawa,dubanshi khalipha yayi donshi nashi takalman na daure a qafarshi bai cire ba,sai a sannan ya lura,takalmi ne da abbanshi shi ya siyo musu,kudinsa yakai dubu talatin ya dauka ana khaliphan ya baiwa ibrahim daya,nashi kam ya dade dacin kasuwarshi a lokacin da hajar bata da lafiya,basu da kudin magani babu dalilinsa ya saida ya siya mata magani,dama ba wani tayi arziqi suka masa ba kwata kwata dubu goma aka sayeshi.


Saida khalipha ya gama bayaninsa kaf sannan alhj idris yace
"To nidai bana jin akwai abinda zan iyayi gaskiya,don tuni na miqawa yakubu haqqin kula da wajen,baiga dacewar ya daukeka ba shi yasa bai daukeka ba,saboda haka sai kayi haquri" shuru khalipha yayi ba tare da yace komai ba
"Ka tashi kaje" ya fada yana nuna masa hanya,tsam ya miqe ya fice daga falon,yana gab da ficewa a gidan yarinyar gidan daya taras dasu a falo ita da mahaifiyarta ta qwalo masa kira,tsayawa yayi cak
"Abba yace kazo" kaman baxai koma din ba,amma yadda yarinyar ta tsaya tana kallonshi yasa yajuya yabi bayanta.


"Binta tace a barka,basu damai share share ya tafi jinyar babanshi,idan kanaso zaka iya karbar aikin nasa kafi ya dawo sai a san yadda za'ayi,za'a dinga baka albashi a wata dubu biyar,sai abincin rana dana dare amma fa ba kullum ba zaka yi?" Kai ya jinjina saboda kudin koda baikai hakan ba zai iyayi,matuqar zai samu abinda zai kaiwa 'yan uwa da mahaifiyarsa.


Sanda ya koma gida yake baiwa anni labarin yadda sukayi taji dadi koba komai zai samu abinda zai riqesu,saidai kuma wani bangare na zuciyarta suya yake mata sosai,ace yau idriss shi zai dauki dan sa'id boyi boyin gida?,sa'id a sanda yana raye numfashi ne kawai baiyi musu ba,shine cinsu shansu suturarsu da duk wani kasuwanci da sukeyi,uwa uba sune suka kwashe duk wata dukiya ta sa'id din da sunan bashin banki yaci,ba ita ba hatta da khalipha sun sani sa'id din tunkan yayi bunqasar da yayi mutum ne mai tsoron bashi koda na naira biyar ne kuwa,balle har yakai kanshi banki ya karbi dukiyarsu.


Aikin da akace khaliphan zaiyu sai yatadda yaci uban hakan,gida ne mai matuqar girma wanda mahaifinsa ne ya ginawa idriss din dab da zai rasu mai dauke da dakuna da sassa sassa ginin zamani,shi zai share gidan komai girmansa,idan ta kama ma har dakin ibrahim dansa namiji tilo da yake gwadawa gata khaliphan ne zai shiga ya share,wani lokaci hatta da falon gidan hajiya binta saita hada masa da shi,baya ga haka idan i rahim ya bushi iska saiya hado masa kayansa yace ya wanke masa,haka aike lokuta mafiya yawa shike musu,dukka wadan nan hidimomin cikin kudinsa ne,bawai wani albashi na daban aka qara masa ba.


A qalla khalipha sai daya shekara uku yana wannan bautar gidan yayan mahaifinsa,cikin gidan da mahaifin nasa shiya gina masa shi,a qafa yake zuwa a qafa yake dawowa,aninci kuwa sai a debi kusan kwana hudu ba'a bashi na rana ba bare dare,duk ranar da aka bashin kuwa bawai ci yake ba,yana hadewa ne idan ya tashi tafiya ya kaiwa qannensa,wani lokaci idan yaga aikinnyi akan hanya yakan tsaya ya karba yayi kafin ya qarasa gida dinsu samu abun batarwa kafin wata ya cika a bashi albashinsa,don shi kanshi albashin idan alhj idris yaso sai wani watan ya shiga yayinkwanaki goma sha bai bashi ba,ya dinga kuma qananun maganganu shi daya yana fadin dadin ya yiwa khalipha yawa,ga cinyarwa gashi ana biyanshi kudi?,shi ai ya cancanci ma ayi masa jinjina sabida yayi abinda dukka sauran 'yan uwanshi suka kasa,khalipha bai taba daga kai ya dubeshi koya tanka mishi ba,yakanyi qoqarin danne fushinsa sarai duk sanda wani abu mara dadi ya faru,suna cin albarkacin anni data roqeshi kada ya yarda ko sau daya ya biyesu ayi wani abu mara dadi,dalilin barin gidan ya fara samo asali ne daga sanda jama'ar gidan haj binta da ibrahim suka soma qorafin ana musu dauke dauke,kusan kullum Allah ne dakullum sai anyi cigiyar an nemi abu an rasa.


Rabon za'ayi ranar da khalipha ya shiga dakin dakin ibrahim yi masa shara,khalipha tun asali mutum me maison ado da qamshi,kwalliya na burgeshi qwarai,dalili daya sanya koya ya samu kudi bai rasa siyiwa hajar abun kwalliya na mata koda jambaki ne kuwa dan naira hamsin,koda shi bai saka ba ita ta saka,to ibrahim ba laifi akwai qwalisa da ado,duk sanda yayi kwalliya khalioha kan kalleshi,yana tuna sanda mahaifinsu keda rai,duk juma'ar duniya sababbin kaya suke sakawa,wani lokacima anko suke da babanshi,akwai wani turare da ibrahim din ke amfani dashi,kalipha na matuqar son qamshin turaren,ranar yaje yi masa shara saiya dauka ya fesa sau daya a jikinsa,yana shirin ajewa ibrahim ya shigo dakin,nan ya soma cuccusawa ma khalipha ashar yana fadin ashe shine barawon gidansu,ya gaya mishi don ubanshi mai ya dauka
"Babu abinda na dauka maka sai turare dana fesa,wanda shima nasan nayi kuskure kuma kayi haquri don Allah" khaliphan ya fada tunda yasan laifinsa ne,kafewa ibrahim yayi yace bai yarda ba sai khalipha ya tube ya dubashi
"Bazqiyiwu ba tunda na rantse maka ban dauka ba ban dauka ba,dana dauka din kai tsaye zan gaya maka na dauka,don nafi tsorin mahaliccina fiye dakai"
"Ni kake gayawa ba tsorona kake ba,kayimin sata ka dinga gayamin baka tsoro na?" Saifa ibrahim ya rufe khalipha da duka,a sannan ya girmeshi hakanan khaliphan ya rame ibrahim ya fushi gabaran jiki,hakan shi ya baiwa ubrahim damar yiwa khalipha duka bana wasa ba,ya gwara kanshi da bango sosai wanda yayi sanadiyyar sunewarshi,bai farfado ba sai a asibiti,tunda ya samu sauqi aka sallemshi ya koma gida,duk sanda ya tuno da abin yana qona mishi rai,sharrin sata abu ne ba qarami ba,amma anni tace ya barsu da Allah,ta kuma yi masa fadan fesa masa turaren da yayi,ta gaya masa shine silar komai,dabai fesa ba da duk hakan bata faru ba,wannan shine silar abinda ya gadarwa khalipha cuwon kai mai tsanani da yake shan wuya duk sanda ya tasarmasa har kwanan gobe.


sanda abun ya faru saura kwana biyu a biyashi albashinsa,kwana biyu na cika saiga kawu idris da albashin khaliphan,sunyi mamakin ganinshi don sunsan bata yadda za'ayi ya biyoshi da albashinsa,ilai kuwa bayan ya miqa albashin sai ya sassauta murya cikin murmushi,a lokacin khalipha na dakin annin yana kwance don bai gama murmurewa ba
"Wata magana nazo miki da ita mai muhimmanci aisha,wadda idan har kika amince da ita ni dake gaba daya kowa zai amfana"
"Inajinka,Allah yasa alkhairi" ta fada tana dubanshi a darare don ita har yanzu bata amince da zuwanshi ba
"Nace ba....me zai hana muyi aure ni dake,idan yaso saiki kwaso 'ya'yanki naci gaba da kuka dasu,'ya'yan sa'idu ai 'ya'yana ne" a zabure khalipha dake kwance ya miqe,cikin azama ya tashi tsaye ya fito falon
"Tashi ka fitar mana daga gida" kallonshi idris yayi
"Meyw haka khalipha?"
"Nace tashi ka fitar mana daga gida maciyin amana kawai,Allah ya tsare anni da aurenka har abada wallahi tafi qarfinka"
"Me kake haka khalipha?" Anni ta fada tana qoqarin tsawatar masa gajin yadda yataso haiqan kaman zai daki kawu idris,sam bai saurari zancan anni ba bai saurarawa kawu idris ba sai daya danganashi da gate din gidan sannan ya dawo,idanunshi kamar garwashin wuta haka suk a kada sukayi jajur,haka kawai ya kasa zaune ya kasa tsaye saboda bacin rai ya dinga kai kawo
"Anni,duk randa mutumin nan ya sake dawowa gidan nan saina nakasta shi" haka ya dinga fada saida annin ta tsawatar masa
"ka shiga hankalinka mana khalipha,ni din bansan me nake ba koko yaya?,idris ne fa na sanshi na kuma san halinshi da manufofinsa kaf tun kafin a haifeka" da qyar anni ta iya control dinsa,haka yake bai iya fushi ba,ya kuma qaro zafin zuciya sanadiyyar tsangwama da rashin kirki da azabar da suka dinga gwada masa da 'yan uwanshi.


Tun daga ranar bai sake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login