Showing 171001 words to 171357 words out of 171357 words
Chapter 58 - Daurin Boye Book One Complete Hausa Novel
Ita ta soma gama shirin kwanciyarta tsaf ta haye gadon tana jiranshi,duk wani shiri ta gamashi don ta gama karantar mijinta,cikin satin da suke shirin tahowa nijeria yanata zirga zirga bai samu zama ba,tana kallonshi ya gama komai ya isketa,yana murmushi sanyata cikin jikinsa sosai yana shaqar daddadan qamshinta mai shiga rai da tsayawa a zuciya
"Uwaishahh......meye labari,naga bakinki akwai magana da alama" qanqameshi itama tayi sosai,ta zagaya hannunta a bayanshi tana murmushi
"Ina godewa Allah da baiwar da yayimin da kuma ni'imar nagartaccen miji wanda babu tamkarsa kamar kai,kaine baiwa ta farko kuma ni'ima ta farko cikin rayuwata,ina roqa maka alkhairin Allah rahamar Allah da kuma jin qan ubangiji a gareka nan duniya da gobe qiyama......my life...ina maka albishir ina dauke da juna biyu" idanu ya zaro cikin xumudi yake duban idanunta
"Are you seriouse uwaisha?" Kai ta kada
"Da gaske nake maka my babu irin wannan zolayar a tsakaninmu,bazan taba ja maka rai ba kan abinda nasan kana so"
"Allah na gode maka da dukkanin baiwa da ni'imar daka yiwa rayuwata,Allah na gode maka daka bani matar aljanna tun a duniyata,uwaishaaa,duk abinda zan gaya miki a kanki ina kin tamkar na rage darajar so da qimarki da nake gani a rayuwata"
"Ni ya cancani nayi wannan godoyar wa uba giji,farincikin daka baiwa rayuwata baya misaltuwa,ka zama silar warwarewa dukkan wani DAURIN BOYE da ya yiwa, rayuwata dabaibayi,ina sonka abbi,ina sonka sosai abban farha jawad da fu'ad"
"Da unborn ba....." Dariya ta saki tana sake shigewa jikinsa
"Zumudi dai your royal highness"
"Kinga lafina?,yara nakeson dozen biyu.....bari ma kiga ni na sake bada himma ko zasu zama biyu idan kin tashi haihuwa" dariya sosai ya bata,a ranta take cewa ko ina ake haka?,cikin aminci salama da kuma sallamawa suka shiga wata duniya mai cike da nutsuwa da aminci wa juna.
*Alhamdulillahil lazi bini'imatihi tatimmus salihat*🙏🏽
_muna miqa dumbin godiyarmu ga dubun nan masoyanmu da suka kasance damu,suka bamu goyon baya,suka kasance cikin group na zafafa biyar,haqiqa soyayya ba qarya bace,Allah ya qara zumunci ya sadamu da dukkan alkhairinsa,rabbi ya yafemana dukkan kurakurenmi cikin rubutunmu,ya hadamu a ladan amin summa amin_
*subhanakallahumma wabi hamdika,ashahadu an la'ilaha illa anta,astagfiruka wa'a tubu ilaika*🤲🏽🤲🏽
*mrs muhammad ce*👑