Showing 153001 words to 156000 words out of 171357 words

Chapter 52 - Daurin Boye Book One Complete Hausa Novel

ta saita sahu yadda ya dace ya kabbara sallah cikin mamakin sallar meye itama ta tayar,raka'a biyu sukayi sukayi sallama,yaja doguwar addu'a sosai wanda ke tattare da roqon dukkan alkhairi sannan ya shafa,jiyowa yayi ya zauna yana fuskantarta gami da tanqwashe qafa,janye idanunta tayi daga nashi tana jin zuciyarta na bugawa,wata fargaba na shigarta,sunanta ya kira wanda ya sanya ta daga kai ta dubeshi,a nutse yake mata tambayoyi game da abinda ya shafi addininta,sallah tsarki da wanka,kada kai kawai yake yana gamsuwa da bayaninta,kai karantse wata malama ce,sai data kammala sannan ya dora hannunshi ya karanta addu'ar nan da annabi ya umarcemu ga duk wanda Allah ya horewa yayi wani sabon abu,ko mata ko abun hawa,har ya gama tana saurarenshi,hannunsa ya sanya ya janyo ledar dake gafansa wadda suka siyo kayan ciye ciye a ciki,ya fidda komai ya aje a gabansu,itadai nata ido jiki a salube,donta shinshino wani abu,da kanshi ya dinga ciyar da ita,duk da taso ta turje da farko yayi kicin kicin ya nuna yayi fushi,cikin hikima ya dinga janta da hira wanda ya sanyata ta sake,sai gata tana qyalqyala dariya,bayan sun gama ita ta gyara wajen kafin ta kammala ya haye gado abinshi
"Malama a cire hijabin nan da after din mana haka?,banfa ga kwalliyar ba" sai ta dan diririce kadan saboda tuna yanayin rigar dake qasa,girarshi ya dage mata
"Yes....ko so kike nayi asarar kudina?" Ya fada yana zuba mata idanu,hakanan ta dinga fidda kayan kunya na saukar mata,sai daya ragw saura rigar baccin kawai,zuwa sannan numfashinsa ya soma masa nauyi,tunda Allah ya halicceshi bai taba ganin sura irin haka baka,ashe ayshan ta zarta dukkan yadda yake tunani,hannunshi ya miqa mata yana daga zaune saman gadon,bayanshi jingine da fuskar gadon qafafunshi miqe
"Kai zo nan muga wani abu....ya maqale miki a gashi meye haka kamar qadangare?"gaba daya basirarta ta tafi,dama atsorace take haka kawai,sai ta kwasa tayi wajenshi babu shiri,batasan cewa wayo yayi mata ba sai data ji ta shigo hannu,saqonni yake aika mata masu wuyar bijirewa,masu nauyi a qwaqwalwa,masu rikita lissafi,sai daya warware mata dukkan wani lissafinta sannan ya rada mata
"Zanso darenmu na farko ya zama cikin wannan garin mai albarka kamar yadda na jima ina burin haka a rayuwata a duk sanda Allah ya bani matar aure,saboda kwadayin albarkar dake cikin garin,kin bani damar cika wannan buri nawa uwaisha?" Kai ta gyada mishi tana rufe idanunta,tana son ta yaqi tsoto da fargabar dake taso mata
"Na gode,na gode" ya dinga maimaita mata yana cusa kanshi tsakanin wuyanta da sumar kanta ta sauko tayi musu rumfa duka su biyun.


Cikin wannan sassanyan daren,khalipha da ayshan suka zama abu guda,khaliphan ya samu ayshan fiye da yadda yake tsammani duk da cewa shi din farin shiga ne,ya bita a sannu yanda ya kamata saidai hakan bai hanata jin jiki ba,tunda ita dinma baquwa ce a fannin,saidai yanayin yadda ya riritata ya taqaita mata wahala qwarai da batasan yadda zata kaya mata ba.


Hakan gaba dayansu bai hanasu tashi sallar asuba ba,tare sukayi jam'i,ya waiwayo yana kallonta sanda suka idar cikin tausayawa da wata tarin qauna,saidai taqi yarda su hada idanu,wata kunyarsa mara misali take ji,murmushi ya saka a sirrance don yasan kunyar me take
"Khalipha zan mutu,ashe dama baka sona?" Ya fada a hankali,sarai ta jishi kuma tasan ita yake tsokana,saitayi banza dashi saidai bakinta data dan zumburo
"Ina sonki mana my uwaisha,Allah sai yanzu ma nake sake jin wani sabon shauqi game dake,uwaishaahhh zan iya mutuwa saboda ke..." Salon yadda yayi maganar cike da tsokana da shagwaba ya sanyata sakim dariyar dole,shima tayata yayi kafin daga bisani yayi nasarar sanyata cikin jikinta yana shafar gashin kanta,addu'a ya dinga jero mata godiya da fatan alkhairi tana amsawa can qasa kanta na saman qirjinta,a haka har bacci yayi awon gaba da ita,shimfideta yayi a wajen yana gyara mata kwanciya idanunshi a kanta,ya jima ahaka yana kallonta kafin ya miqe yana shawagi kadan kadan a dakin kamar mai gadinta,zuciyarsa fes qal,wani farinciki na musamman na ratsashi,ashe da can ba rayuwa yake ba gashinan ne dai kawai?,ya godewa Allah da tasahon shekarun ya tsareshi ya kuma kare ayshanshi,duk irin gwagwarmayar rayuwar da suka fuskanta hakan bai sanya sun fada gonar daba tasu ba.


Bai taisheta ba sai dayaga lokacin sallar azahar yayi,tana zaune inda tayi sallar yana aukin kallonta yace
"Ko zaki shirya na kaiki wajen ummi?" Kai ta girgiza alamun a'ah,don tana ganin kamar idan taje ummin zata gane wani abu daya faru.


Da la'asar ta sanke wanka da ruwa mai zafo don taji dadin jikinta,taji din kuwa,har ta dan samu tayi mishi kwalliya,tana daura dankwalin kanta taji hannunshi a wuyanta,sarqar gold din da suka siyo ce wadsa duk ciki tafi kowacce kyau da tsafa,bata ce komai ba itadai tana tsaye tana kallonshi,yasanya mata dan kunnenta sannan ya kama hannunta ya zira mata awarwarayen,baya ya danja yana kallonta
"Kamar yadda na zata kin haskasu sosai" ido ta zare tana daga gira alamun neman qarin bayani
"Eh,kin haskasu,don kinfi qarfin su haskaki aysha basu da wannan kyan saidai ke haskasu" tilas ya sanyata dariya,idan yana yabonta wani lokaci yakan sanyata dole taji kanta ya kumbura,taji duk duniya babu macen da tayi sa'ar miji kamar ita
"Wannan shine dan qaramin tukuicin da zan baki kan farincikin da kika sanyani daren jiya" ya rada mata wanda kunya ta sanyata saka tafin hannunta ta rufe fuskarta,kamar yadda ya saba ya hanata godiya yace amma wannan karon ta adana godiyarta sai haduwa ta biyu,murmushi ta saki kawai,khalipha na sata jin kunya shi kuma babu ruwanshi.


Haka sukayi zamansu yana jinyar abarsa yana lelenta,saida sukayi kwana biyu cur sannan suka fita,zuwa sannan ta samu sauqi bata jin komai a jikinta,don ya bata tazara bai sake neman komai daga gareta ba,ranar tare da ummi suka wuni a masallaci,don suna saka ran a satin zasu bar saudiyya.


Cikin satin kuwa khalipha ya dinga daukarta suna zuwa siyayya,har gajiya tayi da siyayya,ya dinga sanyata tana diban kaya kamar banza,batasan cewa ba nijeria zasu wuce ba sai ana ya gobe zasu tafi,ya shaida mata suma zasu suga ruqayya ne,langabe masa tayi tana kallonsa
"Nayi missing din anni pls ya khalipha...."
"Na sani nima haka,amma inaso muje mata ne da babbar tsaraba" sam bata gane ne yake nufi ba sai tace
"Akwai tsarabar dana siya mata,kuma abinda tafiso shi na siya mata,nasan zataji dadinta" bakinsa ya tabe yana kada kai
"Duk tsarabar da zaki kai mata bata kai wanna ba,so nake ki samar mata jika....." Ai bai qarasa ba ta saki ihu tana rufe fuskarta,yayin daya bita ya danneta yana qoqarin saita bude fuskar ya qarasa gaya mata ita kuma ta qiya,daga qarshe shi yayi nasara dole sai rintse idanunta tayi tana saurarenshi a haka.



Karon farko da suka soma haduwa da ruqayya tayi aysha ta kwanta mata sosai,kamar yadda itama anty ruqayya ta kwanta mata,ta rasa inda zata saka ayshan,ta lura akwai sabo da qaunar juna sosai tsakaninta da khalipha,yaranta kamar aysha ta qwacesu,yara masu kyau da tarbiyya.


Tun anty ruqayya na mata hira kan dabarun zama da miji tana jin kunya har daga qarshe ta haqura,a nan ta samu sirrika masu tarin yawa a wajenta,dauka mata wannan tasha,dauko mata wancan ta lasa duk wasu hadin na larabawa ne,sai data tsima ayshan da kyau cikin dabara,donta lura da take taken khalipha wanda ta fuskanci ayshan sam batasan me yake nufi ba,ana sallar magariba ta sanya ayshan tayi wanka da kyau cikin ruwan turaruka,ta bata wata rigat bacci mai kyau saidai tana da dan kauri wadda tasha turaruka kala kala,bayan ta gama shiryawa suna gefan gadon anty ruqayyan ayshan na sauyawa qaramin yaron anty ruqayyan pampers khalipha ya shigo dakin wanda dakin spare ne na baqi mata dake cikin gidan,dubanshi anty ruqayya tayi samda yake tsaye ya tokare bango da qafarsa guda daya daya yana tsaye a kanta,hannunsa harde a qirji ya dan shagala da kallon aysha wadda antyn ta gyara mata kanta yayi kyai qwarai
"Ya ne alhj halifa?" Saiya saki ajiyar zuciya a boye ya maida kanshi gunta
"Zuwa nayi ki bani matata,tunda na fuskanci so ake a qureni ana zaton bazan iya magana ba" dariya ta saki
"Allah ya baka haquri,aysha tashi ki bishi tun bao daukeki da kanshi ba" sauke qafarshi yayi yana tattare hannun rigarshi
"Kamar kuwa kinsan abinda nake nufi kenan ba?"kafin suce meye su duka ya daga ayshan cak yana fadin
"Allah ya bamu alkhairi saida safe anty" kunya kamar aysha tayi me?,sauqin abun daya duka yaran antyn na dakinsu suna assigment,tun daga hanya qamshinta ya soma rikitashi,suna zuwa daki ya qarasa birkice mata,ranar ya more angoncinsa qwarai,taso tayi dauriya amma daga qarshe saidata nuna raki,duk da akwai sauqi akan karon farko,shikam ji yayi kamar ma ranar yake ango.


Washegari qememe ya hanata fita sai daya sake morewa,kunya tasa ma ta kasa fita gaba daya,'yar halak anty ruqayyan saiga aiken breakfast ta turo babban danta ya kawo musu,koda yamma da suka fito zai zaga da ita gari antyn fuskewa tayi kamar ba'ayi komai ba,wanda hakan ya sanya aysha itama ta sake.


Kwanansu bakwai a dubai suna amarci sosai,randa suka dawo daga wani mall tana fitowa daga wanka saiga kiran wayar hanan,ta tsaya da tsane ruwan kanta da take ta amsa wayar,ta gaya mata an dawo daga yajin aiki,suka dan taba hira sannan sukayi sallama ta aje wayar tana duban khalipha dake ninke kayan da suka cire shi da ita,haka yake baida qyuyar aiki,wani lokaci har mamaki yake bata,baida girman kai ko kadan,baya jin yiwa iyalinshi aiki ko wata hidima,wani abunma kafin tayi musu shi yayi
"Komawa gida yazo kenan,kaga hanan ce ta kirani tacemin an koma strike" kanshi kawai ya daga ya kalleta,saiya maida yaci gaba da abinda yake ba tare daya ce mata uffan ba kamar ma baiji abinda tace ba,dubanshi kawai take,ta tabbatar yaji din,amma batasan me yasa yayi banza da zancan ba,saitaja bakinta itama tayi shuru taci gaba da sabgarta,saidai jikinta gaba daya a sanyaye yake.


Har sukazo kwanciya jikinta a mace yake,yayin da shi kuma har a sannan baice da ita komai ba,sai daya gama addu'at kwanciya ya shafa itama ya shafa mata sannan ya janyota jikinsa,a hankali can qasa yace da ita
"Karki wani zafafa da yawa,kar ki saka buri da yawa,Allah ya sani ni kadai nasan me nakeji a zuciyata a kanki,kici gaba kawai da addu'a kan ci gaba da karatunki a wudil,idan babu alkhairi Allah ya zaba miki abinda yafishi alkhairi"sosai gabanta ya fadi tana tsoro da fargabar fa yace ba zata koma ba,amma duk da haka saita danne kawai,tunda shine sila na komai hatta da karatun nata ma.


Cikin dare ta tashi a firgice sakamakon mafarkin da tayi,gidan daddy ya cika anata kuka,shi kuma yana zaune yana ta bin mutane yana basu haquri,ita kuma waisai ta shigo ta fadi tana kuka,saiya dagata yana cewa ta fada kan maciji,sai macijin ya sareshi shima ya fadi anan sai kuma akayo kanshi anata jijjigashi amma ya daina motsi,tana cikin bawa khalipha labarin kawai saita saki kuka,harga Allah zuciyarta tayi gida a sannan,da qyar ya lallabata ya nuna mata sharrin mafarki ne,shi ya sanyata tayi alwala shima yayi suka dasa sallar nafila har asuba,bayan tayi sallar ne bacci ya dauketa.


Tana farkawa kuwa layin daddyn ta soma kira,babu jimawa ya daga,wata wawiyar ajiyar zuciya ta saki sannan ta soma gaidashi,a sake yake amsawa ta tambayeshi jiki yace jiki da sauqi sosai,don bai taba jin dadin jikin nasa irin yau ba,hira sukayi mai tsaho sannan sukayi sallama tace ya gaida mutanen gidan,yace zasuji don safiyya ma mutuniyarta nakan hanya tace saitazo ta kawo masa wani dahuwar nama,tana dariya tace idan tazo daddy kace ta ragemin,yayi dariya yana fadin
"shikenan kuwa zata ji,sai wani lokacin kuma"
"Zan sake kira daddy anjima in sha Allahu"
"Allah ya bamu aron rai"
"Amin" da haka suka rabu,khalipha na tsaye saman kanta yana kallonta yana dariya
"Yar daddy,kin kirashi dai kinji dadi ko,kuma kinji lpy lau yake sharrin mafarki ne,haka kawai jiya kika wani birkice,ina shirin da asuba adan sanmin na d'ana duka aka hanai" juya qwayar idonta tayi cikin kunya tana murmushi
"Hankalina ya tashi ya khalipha,ina son daddy" gefanta ya samu ya zauna
"Mutum ne na qwarai sosai" daga haka hirar daddyn ta balle a tsakaminsu,kowannensu na tuna alkhairinsa gareshi.



A ranar da yamma tana tare da anty ruqayya suna hira khalipha ya shigo yana shaida.mata ta shirya nan da wa daya zasu wuce nigeria,cikin mamaki anty ruqayya kanta take kallonshi bama ita ayshan ba
"Lafiya daiko?" Ta tambayeshi
"Lafiya,aikime kawai ya taso min a kamfani kiran gaggawane ya samu"
"Auto,har naji dadi" ta fada tana sakin ajiyar zuciya,itakam.aysha ba wani zumudi dataji wanda ta tsammaci zataji duk randa zasu koma gida,saita miqe zuwa dakinsu da zummar hada musu kayansu.
[3/21, 2:50 PM] +234 809 228 8954: 55

ko duban asma'u baiyi ba ya dauke kan motarshi ya canza hanya
"Wai malam ina zaka dani ne?" Banza yayi da ita donshi kadai yasan tashin hankalin da yake ciki
"Kaga malam ka saukeni ina zaka dani nina gaji fa"tsawa ya daka mata sannan yace
"kiwa mutane shuru,ke bakisan abinda yake damunsu ba zaki cikasu da surutu,koma meye kema kin taimaka wajen faruwar abinda ya farun,dole muje dake kema ki saka baki" ganin yana yi kamar zai daketa ya sanyata yin shuru kawai tana huci,haka suka ci gaba da tafiya har suka cimma daddy,cikin tasu motar ya shiga suka tafi yabar motocinsa nan wajen wani cin abinci dake lodge road din.


Qararrwar falon daketa kadawa ya sanyashi miqewa don zuwa duba wanda ke neman izinin shigowa
"Kinga yanzu kikai alqawari ba zaki sake kuka ba,karki karya" kai ta gyada mishi tana binshi da kallo,har cikin ruhinta tana jin wani alfahari na kasancewarsa miji a gareta,daya tamkar da dubu.


Daya daga cikin masu tsaron qofar gidan ne yake shaida masa yayi baqi,baisan su waye ba hakanan suma sun gaya mishi cewa baisan da zuwansu ba
"Qyalesu su shigo" ya bawa mai tsaron qofar umarni,falon ya koma yana dubanta
"Kinga duk kinsa coffen yayi sanyi,dan sake hadamin wani zanje naga wasu baqi,nasan ba jimawa zasuyi ba tunda banyi dasu zan gansu ba,nan da minti biyar zan sallamesu saiki kawomin coffe din a can zan sha"amsa mishi tayi yayin daya dan sunkuya ya sumbaci goshinta sannan ya zura takalminsa ya fice.


Tunda suka shigo gidan gaba daya ya tafi da imaninta,tasan cewa za'a rina hakan,don tun a mota ta fuskanci wajen uban gidan mijin nata zasu je,sai take ganin gidan kamar ta sanshi,sai taga yana mata zubi da gidan aysha da aka kawota,girgiza kai tayi wani bari na zuciyarta na gaya mata
"Haba wane mutum,ta ina khalipha yake da kudi kamar na mutumin nan,ta inama zai ginawa ayshan gida har haka?" Ko kusa bata ankare da khaliphan ba har suka gama parking suka fito,saboda idanunta nakan jerin motocin alfarma dake pake a inda aka tanada saboda ajiyar motoci na gidan.


Hamid da daddy suna gaba tana binsu a baya,zuciyarta cike taf da qyama da dana sanin auren hamid,bata taba tunanin kudin da suke tinqaho dashi ba nasu bane na rance ne ba sai yau,da zasu kula da ita da kyau ta baya kallon wulaqanci take jifansu dashi,gab da zasu isa wani guri datake hango wani mutum can zaune hamid ya dakata ya jata gefe
"Ki tabbatar da cewar kin bude baki kin bada haquri,idan ba haka ba wallahi Allah kinji na rantse miki duk wani abu da nasan na siya miki ke har motar da kike hawa saina saidata,saboda duk da kudin da muka karba da bikinki na cire wani abu a ciki na siya miki" dubanshi kawai take,a fuska gashinan mutum iya mutum,saurayi dan gaye maiji da kanshi,saidai a ciki duka hoto ne kuma kango ne,sam hamid baya burgeta yanzu dai dai da qwayar zarra,hakanan mamaki ma suke bata shida ubanshi duka a yanzu,koda zata bar gidan hamid batason ta rasa abinda ta shigo da shi,ta koma gida a tsiyace,wannan ne dalilin kawai da zai sanyata ta bada bakin,saidai bata ce masa uffan ba har suka qarasa wajen.


Ya amsa musu sallamarsu saidai ya maida kanshi kan wayarshi yana turawa aysha tex kamar ba yanzu ya barota cikin gida ba,baiyi tsammanin su bane da bazai bada damar su shigo ma cikin gidan ba,qamewa asma'u tayi yayin da take qare masa kallo,wani tashin hankali taji yana gewaye ilahirin qwaqwalwarta,wai dama khalipha ne wanda sukazo roqa?,dama alhj kutama surukinta da hamid mijinta dukkansu a wajen khalipha suke amsar bashi?,dama da dukiyar khalipha aka aurota?,take dukkan wani qaimi da kwadayin rabuwa da hakid ya sake ninkuwa cikin zuciyarta,taci gaba da qarewa khalipha kallo tun daga zara zaran yatsun qafarshi zuwa kanshi,tana kuma tantance banbanci tsakaninsa da hamid wanda ya yiwa kanshi mazauni daura da khaliphan,karon farko data soma jin haushin kanta da kanta a rayuwa,tun daga siffa khalipha ya gama cinye hamid murus,me ya kaita yin wannan ragon azancin?,wai me yasa ma batasanya daddy ya nashi jari gida da mota ba asanda take tunanin talakane ta aureshi ba?,inuwar daya gani kusa dashi ya sanyashi dagakai,sai yaga asma'un,yayi mamaki don baisan meye alaqarta da alhj kutama da kuma hamid ba,Allah yasanya ba son kudinta ya kaita qulla alaqa dasu ba,ya furta cikin zucuyarsa
"Ki zauna mana,ya zaki tsaya qerere kan mutane?" Hamid ya fada cikin fada fada,saita ja kujera a kunyace ta zauna,a mutunce ba wulaqanci ya gaida daddg sannan suka gaisa da hamid,duk da bai bashi hannu ba,don a yanzu qyamatarsu yake,yana mamakin yadda kana musulmi zaka iya saida abinda zai zama cutuwa ga al'umma,infact ma ruguza al'umma gaba daya kayan shaye shaye yake,saboda matasa sune qashin gadon bayan al'umma to an ruguzasu me yayi saura?.


Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login