Showing 159001 words to 162000 words out of 171357 words
Chapter 54 - Daurin Boye Book One Complete Hausa Novel
jin dadi,yana son yarinyar sosai saboda kama da take dashi sosai ita da jawad,jawad din ne ya tabe fuska
"Abbi.....abbi" yana langabe kai,yasan me yake nufi saboda haka ya shafa kansa
"Bakaga yadda kayi kyau ba my twinny(shima hakan yake kiransa wani lokacin saboda kamarsa da shi)" sunan yana yiwa jawad dadi sosai,saboda haka ya saki murmushi shima yana sakewa farha gwalo a boye,duka takai masa ya boye bayan khalipha
"Abbi....gwalo yakemin"kamo hannun jawad yayi ya dawo dashi kusa da ita ya kama hancinsa ya dan riqe
"Bana son tsokana,bata haquri" baki a tabe ya bata haquri,shi kuma ya juya ya kallo farha
"Ke kuma big sis ce.....saikinyi haquri" kaman xatayi kuka tace
"Hademin kai suke fa shida fu'ad abbi....."
"Qyalesu qanwata.....ki cewa anna ta samo miki 'yar uwa kinga kema kin huta"juyawa tayi bangaren da aysha take tana kallonsu,hannayenta ta hade waje guda,alamun roqo,dan hararar farha tayi kadan saita juya kaman zatayi kuka ta kalli khalipha ta daga kafadunta dukka biyu tana tabe bakinta tana nuna mishi alamun ayshan taqi,shima narkewa yayi ya mata alama yayi mata na abun tausayi ya girgiza kai yana duban ayshan
"maman yara....pls a taimaka mana a sake bamu baby girl" dubanshi tayi ta masa signa da ido na yadda yaran sukayi shuru suna jiran amsar ayshan,ta rasa yadda yaran keda shegen son yara,hatta da fu'ad da bai wuce shekara bakwai ba idan yaga yaro ko yarinya,sai kawai ta miqe ta fice a dakin tana murmushi qasa qasa.
Kayan jikinta ta fidda ta soma daura towel,tana tsaka da daurawar taji ya rungumota ta baya,amsar daura towel din yayi tana rungume a jikinsa yana daura mata kanshi saman kafadarta yake cewa
"Kinqi kawo mana agaji nida yarana ko?" Murmushi ta fitar kawai bata ce komai ba,yana gama daura mata ya birkitota gaba daya suna fuskantar juna,yana shaqar qamshin turaren jikinta,idanunshi cikin nata yana mata wani kallo mai tafiyar da xuciya
"Da gaske muke annah....muna son yara ba zaki agazo mana ba" hannunta ta dunqule ta dora a qirjinta tana murmushi
"Allah ya kawo abbi" dan jim yayi sannan yace
"Ameen....muje in wanke matata" cak ya dagata yana takawa a hankali tana dariya tace
"Abbi baka gajiya?,ka wanke yara ka wanke mamansu?" Murmushi ya saki
"Dama ce....ai ina da cikakken time ne,idan kuma ban muku hidima ba wa zan yiwa?" Shuru tayi tana gyada kai cike da jin dadi da hamadala ga Allah.
Sai daya sakata cikin bathtube ya juya ya fice yana cewa
"Ina zuwa" minti daya sai gashi ya dawo,tare sukayi wankansu sannan suka fito,tsaf suka shirya,shi ya bata wasu kaya wanda kalarsu daya da nashi da kuma na yaran,shadda ce irinta farha,tana ta tambayarsa me ake ina zasu baice mata komai ba yace su zuba ido zata gani.
Cikin sabuwar motarshi fara qal suka shiga suka bar gidan,ita dai tanata zuba ido,basu sauka ko ina ba sai gidan anni,sam bata gane meke faruwa ba sai da suka shiga cikin gidan,tafkeken falon annin cike yake da decoration da kayan ciye ciye da qyale qyale,matar mus'ab,basma qanwarta kuma matar haidar da yaransu gaba daya a falon,suna shiga dukka qwayayen dake falon masu dauke da kaloli suka kama,wasu rubutu suka bayyana,ta daga kai tana karantawa,sai a sannan ta gane me yake nufi,murnar cikar aurensu shekara goma sha hudu cif cif dayi ya hada musu.
Sun jima a gidan annin ana sada zumunta gami da ciye ciye da shaye shaye,dukkan familyn kana ganinsu kasan cewa cikin farinciki da walwala suke,basu tashi barin gidan ba sai bayan sallar magariba,tun kafin a soma maganar tafiyar dama su jawad suka soma nacin a barsu gidan annin,dama ya shirya hakan saboda haka yace su zauna din,har sun miqe suna mata sallama ta dakatar da khalipha
"Auren amal ya taso fa,inatason gaya maka ita da zeenatu za'a hada" dan sosa kunnenshi yayi kadan sannan yace
"Yanzu ya za'ayi anni?"
"Dukkan abinda ya dace yanda ka yiwa maryam"
"To shikenan ba damuwa.....za'ayi duk abinda ya dace in sha Allahu"
"To Allah ya taimaka ya yiwa dukiya da rayuwa albarka"
"Amin ya Allah anni,amin" da haka suka juya zasu wuce,babban yaron haidar affan dake zaune waje daya yana cin abinci khalipha ya kalla
"Affan ya jikin dai?"
"Da sauqi abbi"
"Ma sha Allah Allah ya qara lpy"
"Amin" ya amsa mishi
"Anty na asha amarci lafiya" fatima matar mus'ab ta fada qasa qasa tana dariya,hararta aysha tayi,sosai jininsu ya hadi da fatiman,tana girmamata kamar yadda basma take girmamata,hakanan itama ta dauketa a qanwa kamar yadda ta dauki basma
"Wane amarci shekaru sha hudu ba wasa ba,ko kin manta daku muka gama murna yanzu"
"Kullum jin kanku da daukar kanku kuke kamar sabbin ma'aurata,abun naku da ban birgewa yake daban sha'awa,kullum hirarku muke da abban ummu salma,wai ba za'a bamu sirrin ba muma mu hau network?" Dariya sosai ta baiwa aysha,tasha jin wadan nan maganganun daga bakin mutane da yawa,kada ma hanan taji labari,har wani lokaci ta rasa amsar basu,itadai tasan qaunarsu daga Allah ce,jigon tafiyarsu shine haquri da juriya,uwa uba kawaici da yiwa juna uzuri,soyayya ta domin Allah bata gushewa haka bata qarewa,indai dukkanku zaku yarda kuna bautar Allah ne sannan kowannenku yayi qoqarin sauke haqqin Allah na dan uwanshi daya da Allah ya dora mishi cikin girmamawa da kyautatawa,wannan sune kalaman data gayawa fatima wadandan ta jima tana yi musu dalla dalla,haqiqa sun qunshi abubuwa masu muhimmanci da dama wanda sai sun samu zama da ayshan sosai zata nemi sani da cikakken qarin bayani akai.
Ita ta soma gama shirin kwanciyarta tsaf ta haye gadon tana jiranshi,duk wani shiri ta gamashi don ta gama karantar mijinta,cikin satin da suke shirin tahowa nijeria yanata zirga zirga bai samu zama ba,tana kallonshi ya gama komai ya isketa,yana murmushi sanyata cikin jikinsa sosai yana shaqar daddadan qamshinta mai shiga rai da tsayawa a zuciya
"Uwaishahh......meye labari,naga bakinki akwai magana da alama" qanqameshi itama tayi sosai,ta zagaya hannunta a bayanshi tana murmushi
"Ina godewa Allah da baiwar da yayimin da kuma ni'imar nagartaccen miji wanda babu tamkarsa kamar kai,kaine baiwa ta farko kuma ni'ima ta farko cikin rayuwata,ina roqa maka alkhairin Allah rahamar Allah da kuma jin qan ubangiji a gareka nan duniya da gobe qiyama......my life...ina maka albishir ina dauke da juna biyu" idanu ya zaro cikin xumudi yake duban idanunta
"Are you seriouse uwaisha?" Kai ta kada
"Da gaske nake maka my babu irin wannan zolayar a tsakaninmu,bazan taba ja maka rai ba kan abinda nasan kana so"
"Allah na gode maka da dukkanin baiwa da ni'imar daka yiwa rayuwata,Allah na gode maka daka bani matar aljanna tun a duniyata,uwaishaaa,duk abinda zan gaya miki a kanki ina kin tamkar na rage darajar so da qimarki da nake gani a rayuwata"
"Ni ya cancani nayi wannan godoyar wa uba giji,farincikin daka baiwa rayuwata baya misaltuwa,ka zama silar warwarewa dukkan wani DAURIN BOYE da ya yiwa, rayuwata dabaibayi,ina sonka abbi,ina sonka sosai abban farha jawad da fu'ad"
"Da unborn ba....." Dariya ta saki tana sake shigewa jikinsa
"Zumudi dai your royal highness"
"Kinga lafina?,yara nakeson dozen biyu.....bari ma kiga ni na sake bada himma ko zasu zama biyu idan kin tashi haihuwa" dariya sosai ya bata,a ranta take cewa ko ina ake haka?,cikin aminci salama da kuma sallamawa suka shiga wata duniya mai cike da nutsuwa da aminci wa juna.
*Alhamdulillahil lazi bini'imatihi tatimmus salihat*🙏🏽
_muna miqa dumbin godiyarmu ga dubun nan masoyanmu da suka kasance damu,suka bamu goyon baya,suka kasance cikin group na zafafa biyar,haqiqa soyayya ba qarya bace,Allah ya qara zumunci ya sadamu da dukkan alkhairinsa,rabbi ya yafemana dukkan kurakurenmi cikin rubutunmu,ya hadamu a ladan amin summa amin_
*subhanakallahumma wabi hamdika,ashahadu an la'ilaha illa anta,astagfiruka wa'a tubu ilaika*🤲🏽🤲🏽
*mrs muhammad ce*👑
[3/21, 2:50 PM] +234 809 228 8954: 58
Wani jiri taji yana niyyar kayar da ita sanda taga tarin al'umma da rumfuna tun daga qofar gidan daddy zuwa cikin harabar gidan dake a wangale,kusan tunda tazo gidan ta gama rayuwarta ciki bata taba ganin an wangale qofar gidan irin haka ba
"Ya khalipha?,me yake faruwa?,me ake haka a gidan?" Ta tambayeshi cike da tsoron amsar da zata fito daga bakinsa
"Kinga saukarmu kenan nace bari na kawoki kiga jikinsa don hankalinki yafi kwanciya,wataqila maqota ke wani sha'anin koma daurin aure ake ne,amma kinsan me za'ayi?,shiga ciki ina nan ina jiranki idan kun gaisa saiki fito mu tafi"
"To" tace tana fitowa bayan ya bude mata murfin motar da kanshi,haka kawai ta dinga jin kamar zata fadi qafafunta sunyi laushi kamar ba'a jikinta ba haka ta dinga takawa har cikin gidan.
Anni ta soma cin karo da ita,mamaki dukka saiya kamata,meya kawo anni gidan to me akeyi?,ko dama ta sansu?
"Allah ya jiqan alhj,ba shakka anyi babban rashin da aka jima ba'ayi irinsa ba" kunnenta ya dauko mata muryar wani daga can wata rumfa dake bayanta da yazo gaisuwa,bata gama wannan ba ta dinga jiyo ihun asma'u tana kiran sunan daddy,da hanzari ta taka don shiga tabi ba'asin meke faruwa sai taji gangar jikinta ta kasa daukarta,ji tayi tana sulalewa zuwa qasa,daga haka bata sake sanin abinda ke faruwa ba.
Sanda ta farka dakin ta dinga bi da kallo sai daga bisani ta gane a asibiti take,a hankali abinda ya faru ya dawo mata kanta,saita fashe da kuka tana fadin
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" a hankali wanda hakan shi ya fargar da khalipha dake saman abun sallah cewar ta farka,gaba daya hankalinshi a tashe yake cikin hanzari ya isa gabanta anni dake zaune can kan kujera ta taso itama,ta dakatar da khalipha dake shirin dagata ta zauna,saiya fasa ya tsaya saitin kanta yana shafa sumar kanta a hankali yana tayata fadin innalillahin,har tsahon wani lokaci bai hanata kuka ba hakanan basu fasa maimaita innalillahin ba tare dashi,daga bisani ne ta saki ajiyar zuciya tana cewa
"Da gaske ya khalipha daddy ya mutu?,dama sallama jiya mukayi dashi kenan a waya?" Ganin shima ba wani a nutse yake can ba saboda yanayin da ayshan ke ciki ya sanya anni matsowa
"Allahn daya haliccemu shi ya fimu sonshi,ya kuma fimu sanin dalilin daya sanya ya dauke abinshi,kada mu yiwa Allah daya bamu shi butulci"
Kai kawai take gyadawa tana ci gaba da ambaton sunan Allah,wanda shi ya dafa mata ta samu nutsuwa,sai da anni ta tabbatar ta nutsu sannan ta taimaka mata ta tashi ta zauna,khalipha ya sanya daya daga cikin yaranshi suka yiwa likitar magana,macace likitan dalili kenan ma daya sanya khaliphan ya kawota wannan asibitin,ta tabbatar mishi komai ya koma normal,saidai ta kiyaye damuwa da bacin rai ta rubuta sallama.
Gidan anni suka wuce kai tsaye tayi wanka,saidai har a sannan hankalinta bai jikinta,ta matsa sai an kaita can gidan makokin,haka khalipha ya dauketa ya kaita.
Karon farko data sake sallamawa Allah lamuranta ta tabbatar lallai mutum koshi waye ba'a bakin komai yake ba,kwana daya tak mummy da asma'u sunfi kowa fita hayyacinsu,tausayin kanta da tausayinsu ya kamata,kuka ta dinga sosai ta manta da duk wani sharadi na likita,anty safiyyace kawai mai qarfin halin lallashinsu,ranar mummy ce ke cewa aysha ta yafe mata,saboda gabanta ita da asma'u daddy ya rasu,sun tsorata matuqa da yadda mutuwa take,fitar rai ba wasa bane,kowanne dan adam lallai saiya taba yaji a jikinsa,saidai fata Allah yasa mu dace.
A nan khalipha yake barinta,kullum sai dare yake zuwa ya dauketa su koma gida,har a sannan aysha bata daina kukan rasuwar daddy ba,saidai tanayi a boye yadda khalipha bazai gani ba hankalinsa ya tashi,don dukkan wani qoqari nasa yana yi don ganin ta sake,saidai ita kanta batasan ma meke damunta ba,hatta da taste din bakinta ya sauya tun daga randa akayi mutuwar.
Ranar sadakar uku su inna yelwa suka zo,tunda sukazo aysha ta lura da ta sauya gaba daya,sai da ana hira takejin bata da cikakkiyar lafiya kwana biyu,yau da lafiya gobe babu,ba'ayi azahar ba umminta ta iso itama ita dasu basma,don ita kanta mutuwar ta daketa,taso qwarai ace Allah ya hada ganawarsu da mutumin daya ceci rayuwar 'yarta,taso sosai tayi masa godiya koda sau daya ne a rayuwarta amma Allah bai nufa ba.
Shuru dakin da suke zaune ya dauka gaba daya,baka jiyo komai sai muryar wata baiwar Allah dake harabar gidan tana wa'azi kan mutuwa,tun daga sanda mala'ikan mutuwa dubi bawa,zarar rai,wankan gawa kwanciyar kabari da yadda mala'iku kebi suna jin yadda jama'a ke fadar halayyar mamaci,da yadda hakan yake tasiri a kansa da sauransu,sosai jikin inna yelwa ya sake laqwas,tunda tazo gidan bata ji mutum daya daya fadi mummunan hali akan daddy ba,yau ga inna yelwa ga ummi,abinda ya dauki tsahon shekaru rabon daya faru,sai inna yelwa ta kasa sakewa gaba daya,sai satar kallon ummi take,ba dadewa fa fashe da kuka,ita kadai tasan me take ji a lokacin,ba abinda take tunawa sai abinda ta aiwatar a rayuwarta a baya,yanzu idan mala'ikan daukar rai ya cimmata fa?,tabbas tasan kadanne masu fadin alkhairi a kanta,idon kowa sai yayi kanta,Allah yasa dukka 'yan takai ne da wadanda suka jibanci aysha,anzo mata sosai saboda yanzun kowa neman fada yake da ita
"Don girman Allah ki yafemin naja'atu,wallahi na cuci kaina na cuci rayuwarki keda diyarki" abinda inna yelwa ta dinga fada kenan tana zabga kuka da majina,tsit dakin yayi,yayin da ummi tayi shuru tana hadiyar wani abu mai tauri,zuciyarta quna kawai take tana yunqurin danneta da cika alqawarin data dauka a gaban dakin Allah.
Inna yelwa ta jima gaban ummi tana kuka gami da gaya mata ita ta rabata da baffale,ita ta shiga tsakaninsu,lumshe idanu ummi kawai tayi,zuciyarta nason tuna mata irin abubuwan da inna yelwan tayi mataba rayuwa,yayin da daya sashen na zuciyarta ke tunasar da ita ni'ima baiwa da kuma musanyan alkhairi da Allah yayi mata ayanzu
"Na yafe miki" kalmar data baiwa inna yelwan mamaki,don bata taba tsammatar haka daga wajen ummin da sauqi ba,hakan ya sake karya mata zuciya,nadama ta shigeta sosai,tana son kallon aysha dake zaune waje daya tana jan carbi tace ta yafe mata amma tana jin kunyarta da nauyinta,tana jin idan tace ta yafe matan tamkar ta zama mai son kai ne,amma ita kadai tasan yadda akwanakin take yawan mafarkin baffale,yana kuka yana ta cuci su aysha,ta gaggauta hada tsakaninsu,ta gaggauta neman afiya da yafiyarsu,ta raba uwa da 'ya,saidai kuma cikin kyakkyawan yanayi take ganinshi,saidai kukan kawai da yake mata,babu randa zata kwanta bacci ta tashi batayi mafarkinsa ba,abun ya takurata qwarai,kusan shi ya haifar mata da lalurar da take fama da ita a yanzu.
"Nasan ban cancanci ki yafemin ba indo,amma na gamaki da Allah duk sanda kike jin kin huce na cancanci yafiya toki yafemin" ta fada tana fashewa da kuka,kai aysha ta kada kawai,itakam me zata cewa Allah banda godiya,komai aduniya da zai samu bawa koya sameshi yana damfare da yanayin rayuwarshi na baya,ba don qalubalen data fuskanta ba da babu lallai daddy ya daukota ya kawota nan,da bai kawota din ba da babu lallai asma'u ta hadata da khalipha,duk da yakedai duk inda bawa yake rabonsa baya kubuce masa
"Na yafemiki,Allah ya yafe mana gaba daya" kusan wannan shi ya kawo daidaito tsakanin gabar inna yelwa da ummi naja'atu.
Qarfe hudu da minti ashirin na yammaci yasa aka kira mishi ayshan,can wani waje da babu kowa cikin gidan suka zauna saman darduma,ya tsareta da idanunshi bayan ya aje abinci a tsakiyarsu,saita zuba mishi ido itama sonshi da qaunarshi na sake karyar mata da zuciya,hawaye ya cika idanunta,haka kawai take jin wani abu ya cunkushe mata wuya wanda shike hanata cin abinci
"Oya,bude bakin" ya fada bayan ya debo abincin a cokali yakai bakinta,sai kawai ta sake masa kuka mara sauti sai sheshsheqa
"Ya salam" ya fada yana aje cokalin cikin damuwa,ya rasa me yasa har yau zuciyarta taqi saki,a yanzun kuka baiyi mata wani wuya,yanzu yanzu ne zata saki abinta,bai manta ba jiya suna kici kicin tahowa zai kawota,zata sanya wata riga taqi shigarta tayi mata kadan,sai zuwa yayi ya sameta a zaune dirshan tana sharbar kuka abinta,daga lallashi nan ma cibi ya zama qari,hannunshi ya miqa mata batayi wata wata ba ta taho,cikin jikinsa ya sanyata tana shafar bayanta a hankali
"Uwaisha ba zaki sanya haquri cikin zuciyarki ba ehmm?,bakisan yadda zuciyata ke quna ba a duk sa'in dana ganki cikin damuwa?,so kike wani abu nima ya sameni?" Saita fashe da kuka tana girgiza kai tana fadin a'ah
"Ya Allahu.....kin zama makokiya gaba daya?" Ya fada yana share mata hawayen dake sauko mata
"Na daina...." Ta fada cikin muryar kuka,murmushi kawai ya saki yana ci gaba da riqeta cikin jikinsa,bai barta ba sai daya tabbatar taci abinci ta kuma sake sannan ya qyaleta.
Kwana goma da rasuwar da wani dare tana zaune gaban anni suna hira,tun dazu khalipha ke kaiwa da kawowa tsakanin sashen annin zuwa nasu,ya gaji yakai maqura yau haqurinshi ya qare,so yake ya dauki matarshi kawai su wuce gidansu amma ayshan tayi qememe kamar ma bata gane me yake nufi,sake miqewa yayi ya nufi sashen cikin qwarin agwiwa.
A nutse ya tura qofar yayi sallama,cikin sa'a ayshan ce kadai zaune tana shan fruit salad na musamman da aka zuba mishi zuma da madara,wanda a fakaice anni ta hada mata shi saboda qarin ni'imar jikinta,ita kuwa tunda ta d'an d'ana taji yayi mata shikenan ta samu abinyi,idonta ta daga ta kalleshi sanda shima yake dubanta bayan ya kalli bowl din gabanta mai dauke da fruit salad din,murmushi ta saki tana nuna mishi kwanon
"Ya khalipha bismillah" harara ya dan watsa mata qasa qasa yadda anni ba zata ji ba yace
"Bana sha...ki tashi ki shirya mu wuce gida" saita langwabe kai,tana jin dadin zamanta da anni sosai
"Ya khalipha ka bar....." Sai ya dora yatsanshi akan lips
"Shshshshsh.....bana son jin komai ki tashi kawai"
"Yaya dai khalipha?" Anni dake fitowa daga toilet ta ambata tana dubanshi,sai ya dan sosa kanshi kadan yana cewa
"Babu komai anni" juyawa yayi ya sake jaddadawa aysha maganar da ido sannan ya