Showing 24001 words to 27000 words out of 32136 words
kara juyowa sosai ya kalli yarinyar don a da ya yi zaton idonsa ne bai gani sosai ba, ya dubi Mami ya ce, “Ina kika samo ‘ya?”
Ta ce, “Allah ne ya bani”.
Kamar zai yi magana sai kuma ya yi shiru ya ci gaba da cin abincinsa. Don ya ga bai kamata ya ci gaba da yiwa Mamin tambayar a gaban yarinyar ba.
Rahane kujera ta hau kusa da Jawahir, don ko kadan ba ta zama daf da Abida, sakamakon kisan mummuken da take mata, ‘yan yatsunta take murjewa da kafar kujerarta, ko ta faki idon kowa ta takata da tsinin takalminta da take sawa musamman don muguntar. Iyakaci a ga tana kuka in sun koma daki, tambayar duniyar nan Jawahir za ta yi amma sai ta ce babu komai Iya take tunawa.
Sai dai kuma ta yiwa kanta maganin abun, ta daina yarda ta zauna kusa da ita. Wanda hakan bai yiwa Abida dadi ba, don dai ita nan duniya babu wanda take jin haushi irin Rayhanah.
“Zauna mana Rayhanah”. In ji Mami.
Ta zauna sosai ta fara cin abincin da Mamin ta yi serving dinta. Sakwara ce da miyar alayyahu da ganda da kifi, musamman don Khalipha Mamin ta yi girkin da kanta, don nan duniya ba abincin da Khalipha ke so irin sakwara.
Sunanshi na ainihi sunan mahaifin su Mami ne da ya Musulunta wato (Abdallah). Dacta Mansur da bai iya fadi a matsayin sunan na sirikin sa mai rasuwa shine yake cewa Khaliphan, to sai kowa ya kama. Abdallah ta bace bat, sai Khalipha.
Da kyar Rahane ta iya cin abincin nan saboda kallon ta da Khalipha ke yi jefi-jefi. Ga kukan Azizah ya dameta, jinsa take har cikin ranta. Ko kadan ba ta son kukan yarinyar.
Garin kallon nashi ne ya hango aid din dake makale bayan kunnenta. Ya zare gilashin shi a hankali yana kara kalla ya ce, “Mami bakuwar taku ba ta ji ne?”
Ta bata fuska ta ce, “Wai kai Khalipha baka gani ka yi shiru ne sai ka ce dan jarida?”
Ya maida gilashin sa yace, “Sorry Mum, I’m curious in cases like these….!”.
Ta ce, “Iftila’i na rana daya, sun samu accident ne shine sanadi”. Yace “ta yaya accident zai zamo cause to hearing impairment? Ku dai kara bincikawa, haka kawai ma ji kan dauke, mostly as a result of typhoid fever ko meningitis, ko kuma hereditary factor (gado) na amosanin kunne (otesclerosis)”. Mami tace
“to Dr. Khalipha, babu daya kanwar biyu, professionals basu ga hakan ba har sai sun gudanar da CT Scan and MRI Scan wanda abune dake neman naira miliyan biyu cash. Kuma ba’ayin shi a Nigeria.
Mahaifinta kuma ya tabbatar lafiyar ta kalau ta baro gida kamin suyi hadarin kuma bata gada daga ko’ina ba (uwa ko uba)”.
Ya mikawa Rahane hannu wadda ta sunkuyar da kai......
“Shake my hands, Rayha.....”
Murmushi ta yi amma bata bashi hannun ba.
Ya ce, “To shi kenan tunda bakya abotar dani”. Ya fada cikin launin shagwaba da langabar da kai.
Ba ta san sanda ta yi dariya ba, fararen hakoranta yiri-yiri farare sol suka bayyana. Babba dashi yana shagwaba a gaban mamarsa.
Ya ce, “Do not your problem slow down, you will achieve a lot in life!”
Ita bata ma ji mai ya ce ba saboda yadda harshensa ke harde da Turanci gangariya, sai gwani a harshen ne kadai zai iya fahimtarsa.
Wannan ya samo asali ne da haihuwar Khalipha da Himu da Mami ta yi a Ireland (Dublin). Inda Khalipha ya yi karatun shi har zuwa aji biyar na sakandire kamin su tattaro su dawo Nigeria.
A haka aka kare cin abincin. Koyarwar Yaya Khalipha daban take, ko yaro shine jaki wajen dakikanci dole ya gane koyarwar Yaya Khalipha.
Da ya zo kan littafin Rahane, ya gane Rahanen na da rauni a lissafi (Mathematics) don haka ya tabbatar ta yi a gabansa dai-dai sannan ya kyaleta.
A daren ne Mami take ba shi labarin Rahane, ya saurara da nutsuwa. Yana tsaye jikin balcony na dakinsu yana kokarin kunna Marlboro da lighter ya hango Abida ta fizge hearing aid din Rayha ta yi cilli da shi tana cewa.
“Banza ‘yar kauye, wadda bata ji said a inji, ai sai ki ji mu gani”.
Da gudu Rahane ta bishi inda ta yar ta dauka, sai ta ga ya fashe. Abida ta gudu tana kyalkyala mata dariya.
Durkushewa ta yi a nan tana kuka don ba ta san me za ta ce da Baba Dacta ba, domin ya yi mata gargadi sosai a kan takula
da shi, ita kuma ba za ta iya ce da shi ga laifin Abida ba.
Da hanzari ya ajiye abin da ke hannunsa ya fito zuwa harabar gidan, tsugunawa ya yi gaban Rahane ya karba yana gyarawa. Ido ta dago ta dube shi sai ta hau share hawaye da hanzari, don bata so ya ganta tana kukan ba. Da ya gyara sai ya mayar mata ya ce, “Tafi gida”.
Tun daga ranar Khalipha ya sa ido a kan mu’amalar Rayha da Abida, Jawahir da kuma Azizah. Ya gane Abida bata son Rayhanah sam-sam, komi ta yi sai ta kushe ta gwale, ta wulakantata. Ya ci gaba da bibiyarsu da hankali, nan ya gane kaunar da Jawahir ke wa Rahane, suna son junansu sosai, da kaunar da Rahane kewa Azizah wadda ta sayo mata kauna a zuciyar Mami.
Tara Abida yake yi, bai yi kuma niyyar sanarwa Daddy ba shi zai yi maganin abin. Yau suna zaune shi da Malam Dahiru maigadinsu a kan benci suna hira, su kuma yaran suna can wajen shukokin grass-carpet suna wasanninsu ya hango Abida ta janyo mesar da ake bai wa shukoki ruwa ta saki ruwan a kan Rayhanah, tun daga kanta har kafafunta ta jikata sharkaf, amma ko uffan yarinyar nan bata ce ba. Ta ja mesar ta gudu da ta hango Jawahir na tahowa.
Tun daga ranar ya lura Rayhanah ta daina shiga cikinsu. Ba ma ya ganinta kwata-kwata. Daga baya ya lura kullum tana daki ne kwance a gadonta lullube da bargo. Sai ta ji Mami ko Baba Dacta a falo sannan take fitowa, amma ko abinci in basa nan ba ta ci.
Ganin haka shi kuma duk sanda zai ci abinci sai ya tura Azizah ta kirata, ya cika mata filet ya ce sai ta cinye a gabansa. Ya soma janta a jiki ta hanyar labarai da son jin damuwarta, da kuma ba ta misalan rayuwa kala-kala a kan kaddarar da Ubangiji ya yi nufi ga bayinsa, sai su karbeta su kasance masu godiya a gare shi, don in ya baka wannan, sai ya hana maka wancan, ya ga cewa za ka gode masa ne ko za ka butulce a kan wannan jarrabawar kankanuwa da ya yi maka?
Kwarai Rahane ke jin dadin hira da Yaya Khalipha, halinsa ba daya ne da na dan’uwansa ba, komai nasu opposite. Ita Rahane yadda Yaya Khalipha ya damu da lalurarta ita ba ta damu kanta haka ba. Ita fa ko babu injin nan za ta iya zamanta lafiya, tunda tana da lafiya falil-lahil hamdu.
Rannan da yamma kuma Jawahir tana falo, Abida ta ja Azizah daki ta cire mata pampers. Ta yi kashi fal! Rahane na kwance a gadonta cikin bargo kanta ke ciwo sosai ga zazzabi-zazzabi na neman kama ta. Ba ta son wannan na’ura mai mayar da daki kamar firinji. Duk da Mami ta ce a daina kunnawa sai lokacin zafi su kam basa iyawa sai sun kunna in za su kwanta in ba haka ba ba za su iya barci ba.
Abida ta kunso kashin pampers ta dawo dakin kamar abin arziki ta ce, “RAYHA!’
Ta dan janye bargon ta fiddo fuskarta idanunta duk sun kankance sunyi jawur alamun ciwon kai mai zafi. Ba ta yi wata-wata ba ta kifa mata kashin a fuska.
Dai-dai lokacin da Jawahir ta shigo. Cikin karaji ta ce, “Abidaaaa!”
Wannan ya janyo hankalin Himu da Khalipha wadanda ke zaune a falo suka yo dakin aguje saboda yadda ta yi maganar da karfi da kururuwa, tsammani suka yi Abidar mutuwa ta yi.
Ta ce, “Ku duba ku gani, kashin Azizah ta kifa mata a fuska”.
Ai kuwa Khalipa ya kama Abida da duka don dama bai iya fushi ba, kuma tarata yake yau ta kai shi bango.
Shi kuwa Ibraheem juyawa ya yi ya fita ya ma bar gidan zuciyarsa na wani irin harbawa, tsigar jikinsa na tashi, don baya son ya yi kowanne action a kan Rayhanah balle har ya fassara reaction din sa a kanta.
Yana referring kowane motion dinsa a kanta da KARYA....... Bayan kuma sau tari tsoron kar zuciyarsa ta ce ya yi KARYAR yake kidima shi ya yi mata KARYAR. Ya damu da RAYHANAH fiye da kowa da komi a duniya, amma yana KARYATAWA da kalubalantar kansa a kullum. Wani gini ne ke tsiro na TAUSAYI da KAUNA tun ranad da suka baro Takai.
[12/24/2019, 17:56] Takori: Khalipha ya ci gaba da kallon labaran CNN da Mu’azzam Kanti ke kwararowa (Alkawari Bayan Rai). Lokaci-lokaci ya kan duba agogon (RADO) baki dake daure a hannunsa, sai kuma ya dan dubi kofar dakin nasu. Amma ko keyar Rayhana babu har karfe goma. Tuni Azizah ta yi barci a dakin Mami. Yana jin sanda Jawahir ta yi musu light off (wato ta kashe wutar dakin).
Sai ya mike a hankali jikinshi babu kwari ya nufi dakinsa ya sunce ya daura tawul ya sakarwa kanshi shower, amma zuciyarshi ta ki yin sanyi. A azabce take matuka da zazzafar soyayya, wadda shi kansa bai san ya zai yi ya amayar da ita ba ga kankanuwar yarinya kamar Raihanah mai shekaru goma sha biyar wadda kuma ke matukar ganin girmansa.
Ya daura Pjs ya kwanta a sofa, ya janyo kwalin Marlboro ya soma tada karamin hadari da hayakinta, duk don ya samu sassauci a zuciyarsa, ya danne wannan al’amari da ya kutso cikin rayuwarsa ba da tsammaninsa ba, zuwa sanda Rahane za ta kara girma ta mallaki cikakken hankali yadda za ta fahimci al’amarin, at least ko sakandire ne ta gama. Ya san Daddy ba zai hana shi ba idan ya ce yana so. To balle kuma Mami da ta mai da Rayhan diyar cikinta.
Barci a wannan daren rabi-da-rabi Khalipha ya yi shi. Karshe shida dai-dai ya ji Daddy na buga mishi kofa, abinda bai taba yi ba.
Idanunshi jajir kuma mitsi-mitsi cikin mugun barci mai dadi ya bude kofar. Kafin ya gaida Daddyn ya ce, “In ce ko ka yi sallah Khalipha
Ya amsa “Eh, Daddy na yi”.
To ka canzo kayan jikinka mu tafi Takai”.
Tuni ya nemi barcin ya rasa, ya ce, “Lafiya Daddy?”
Ya ce, “Shiryo dai mu yi sauri kamin yaran nan su farka”.
Saboda zullumi Khalipha a bai-bai yasa rigarsa, ya suro hula da takalmi ya bi bayan Daddy.
Sai da suka hau titi dodar, sannan ne yake gaya mishi Hakimi ne ya kirashi a waya ya ce da shi Malam Rashidu ya fadi a bayi (toilet) rabin jikinshi ya mutu (Pralysed) jiya da daddare.
Khalipha ya ce, “Subhanallah! To ai Daddy da mun taho da Rayha”.
Ya ce, “Zamu taho dashi asibiti ne ai, idan na ga yanayin jikin nasa. Ba zan so ta ganshi in a bad condition ba, ka san damuwarta da mahaifinta”.
Khalipha dai shiru ya yi, amma kar ki so ki tona zuciyarshi da damuwa ta yiwa yawa. Har ya fi Daddy damuwa. Har suka shigo garin Takai bai kara yin magana ba.
Da hantsi suka isa Takai. A kofar gidan Hakimi suka yi parking. A dakin Hajiya Karima suka karya kumallo, kafin su shiga wajen da aka warewa Mal. Rashidu.
Yana kwance bai san wanda yake kanshi ba, har Baba Dacta ya gama dube-dube da aune-aunenshi a kansa bai san ana yi ba. Bakinsa a karkace rabin fuskarshi ya mutu. Duk wani taimakon gaggawa da ake yiwa masu lalurar Dr. Mansur ya ba shi, sannan ya gayawa Hakimi za su tafi da shi asibiti, kwararru a fanninsa su duba shi.
La’asar lis suna cikin asibitin koyarwa na Kano. A take aka ba shi gado a (aminity) aka soma bincikarsa tare da gwaje-gwaje da dora shi a kan tretment din da ya dace da shi a (physiothearapy department).
Sai magariba suka koma gida a gajiye likis. Suka yi sallah suka ci abinci suka samu nutsuwa. Bayan sunyi sallar isha’i suka koma asibitin, zuwa lokacin ya bude idonsa amma baya magana, sai dai duk abin da suke cewa yana jinsu. Yana ta motsi da bakin yana son gaya musu wani abin amma ya kasa.
Albarkacin Baba Dacta duka likitocin dake kula da shi basu dauke shi da wasa ba, kula suke da shi sosai ba dare ba rana. Khalipha shi ya kwana da shi.
Washe gari da safe Dacta ya zo da Mami don ita kwanan asibitin ta yi, suka duba jikin nasa yana samun sauki ba laifi ba kamar jiya ba.
Har ya yiwa Khalipha murmushi, Khalipha ya matsa gare shi shima ya yi murmushin.
Ya ce, “Sannu Baba, Allah zai baka lafiya ka ji?”
Ga mamakinsa sai ya ga ya yi masa alamar ya daga kai. Khalipha ya ce, “Zan je in yi wanka in dawo Baba”.
Sai ya rike hannunsa da hannunsa mai lafiyar ya ki saki, yana ta kakarin magana. Da Khalipha ya nutsu ya fahimci cewa yake “Ka zo da RAHANE”.
Ya ce, “To Baba Rayhanah za ta zo”.
Da yake Asabar ce duk suna gida, Khalipha ya dube su daya bayan daya, Jawahir ce kewa Azizah kitso, Rahane na shafa mata lallen Rani a kan yatsunta. Abida dama ba ta dawo ba.
Basu ankara da shigowar shi ba saboda karar t.v don haka shima ya wuce dakinsa a hankali, babu wacce ta ankara da shigowarsa.
Sai da ya yi wanka ya shirya ya fito dining nan suka san ma yana cikin gidan. Kowacce gaishe shi take don tunda suka dan kara tasawa suka daina damukarsa sai dai gaisuwa ta ladabi.
Ya dubi Rayhanah kadan ya ce, “Ki shirya asibiti zamu yanzu Rayhanah”.
A hankali ta juyo ta dube shi tana son ta tambaye shi waye ba lafiya? Amma ta kasa sakamakon kwayar idanunshi dake sanya mata wani al’amari da ke taba zuciyarta da ilahirin gangar jikinta.
Tsam ta mike ta dauko hijabi irin dogon nan mai hannuwa ta saka ba tare da ta tsaya ko duba madubi ba, da takalmi flat. Ta bi bayan Yaya Khalipha wanda har ya tada mota.
Karo na farko a rayuwarta da ta shiga motar Khalipha. Wani ni’imtaccen sanyin A.C wanda ya cakude da kamshin (car fresh) din citrus da turaren da Khalipha ya yi amfani Azzaro Chrome (Legend) shi ya soma bakuntarta a sanda ta shiga gefen Khalipha ta zauna.
Ya dan juya kadan ya dube ta suka hada ido, inda ya gano alamomin tambaya fal cikin idanunta amma ta kasa furtawa. Ya fi minti uku bai yi magana ba kuma bai ja motar ba.
Rahane ta gaza hakuri ta ce, “Don Allah Yaya Khalifa waye ba lafiya?”
Ya kunna motar a hankali ya fara yin reverse, sannan ya ce da ita, “Ki yi hakuri Rayhanah, Baba Rashidu ne ba lafiya amma mun taho da shi nan asibiti har ya fara samun sauki”.
Kwalla fal idonta ta ce, “Tun yaushe ne?”
Khalipha ya ce, “Tun jiya, ai sammakon da muka yi ni da Daddy Takai muka tafi”.
Ta jinjina kai sai ga hawaye ya balle a ka kundukukinta. Ta yi saurin juyawa tana kallon titi kada Yaya Khalipha ya gani.
Yana gaba tana binshi a baya har dakin aminity na male-ward din inda Malam Rashidu ke kwance.
Da sauri Rahane ta karasa gaban Baban ta kama hannunsa, wannan lokacin kuka ne sosai ya kwace mata da ta fahimci halin da Babanta ke ciki.
Khalipha (cikin bugun zuciya) da hawayen da Raiha ke fitarwa ya ce,
“To kuwa zan maida ke gida Rayha, ciwo ba mutuwa bane, ke da za ki ba shi karfin gwiwa da kalamai masu dadi sai ki yi masa kuka?”
Ta soma share hawayen da gefen hijabinta. Dai-dai lokacin da Khalipha ya matso kusa da Baban, don ganin kamar ya bude ido.
Ya ce, “Baba ga Rayhanah ta zo, Baba Allah ya baka lafiya”.
Sai ya mika mata hannunshi mai lafiyar ta kama, jikinta har rawa yake yi. Kamar wanda ya warke a take ya bude ido garau yana kallon diyar tasa,