Showing 27001 words to 30000 words out of 34298 words

Chapter 10 - Asp Zarah 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

202

kuma ja sannan ya kalli Abdallah yace
"Akan wani dalili zaka dinga sake mata fuska haka.?"

Dariya yayi harda buga ƙafa kana yace.
"Ikon Allah! Tunda baza kayi mata fara'a ba ai saika bar masu yimata koh bawai ka dinga jin haushin mu ba."
Bai kulashi ba sai miƙewa da yayi ya nufi ɗakin Baaba, shima miƙewa yayi tare da bin bayan shi domin zuwa gaida Baabar.
Ganin basa cikin falon yasa ta shirya musu komai a dinning, ɗakinta ta kuma ta ɗau mayafi da makullin mota ta fita domin zuwa kasuwa tayi cefanen abubuwan da zata buƙata na girkin tarbar ɗan uwanta da kuma mahaifinta. Yayanta nason masa sosai shiyasa zata fita da kanta ta siyo sauran abubuwan buƙata na miya da basu dashi.
Tare suka fito falon da Baaba inda suka nufi dinning table yin breakfast.
"Bari na kirata ta zuba muku, Zara'u" cewar Baaba, Raliya ce ta taho da sauri ta iso gabansu tare da cewa
"Hajiya Baaba bari na zuba musu, Anty Zarah ta fita."
"Ina taje kuma."
"Wallahi bata faɗamin ba amma kaman ba nisa tayi ba, naga batayi shiri ba."
"Ai shikenan zuba musu, amma zata fita shine bazata sanar da ni ba."

Ranshi ne yaji ya ɓaci saboda mummunan zaton da shaiɗan ke kitsima mishi na cewar gurin wani ta tafi domin suyi lalata, baice komai ba ya cigaba da cin abincinsa batare da ya kula Abdallah dake cewa.
"Ko dai anyi mata kiran gaggawa ne."
"Ina tunanin haka nima, kasan Zara'u da ƙulafucin aiki bataji bata gani idan aka kira ta wannan aikin nasu duk wani abu da takeyi saita ajiye ta tafi."

"Yanayin aikin nasu kenan Baaba sunyi rantsuwar kare haƙƙin mutane."

"Toh Allah dai ya tsare."

"Ameen" Inji Abdallah

Ko da suka gama cin abincin falon suka dawo suka zauna, hira suka cigaba dayi da Baaba wanda yawanci akan dawowar da su Daddy zasuyi ne.
"Gashi shigowar yamma zasuyi kuma mu yau mukeson tafiya saboda aiki."

"A'a ku tsaya mana dai ku gana duk da ma zaku haɗu acan amma ya kamata ace kun tsaya an tarbesu da ku."

"Shikenan saidai muma muyi tafiyar jirgin kenan, bari na duba ko za'a samu jirgin dare."

"Mezai hana ku ƙara kwana?."

"Baaba nace miki fa akwai aiki."

"Ku zama na'ura saboda aiki idan kun so."

Dariya M.J yayi yace
"Duk rashin son magana da nakeyi sai kinsa ni."

"Yo me za'ayi da mutum miskili."

"Ba zaki gane bane ai Baaba, babu fa'ida ace mutum ya kasance mai yawan surutu."

"Shiyasa ma aka haɗa ka da wacce ta dace dakai gurin rashin son magana."

Bai kuma magana ba illa cigaba da danna wayar shi da yayi, itama Baaba miƙewa tayi ta nufi kitchen.

💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

"Raliya! Raliya!! Raliya!!! sau nawa na kiraki?" ya faɗa cikin fusata.

Cikin shessheƙar kuka ta amsa mai da "Sau uku ranka ya daɗe."

"Wai ke wace irin daƙiƙiyar yarinya ce da batasan abinda takeyi ba, duk tsawon lokacin nan da kika ɗauka a cikin wannan gidan aikin me kikeyi da har yanzu kika kasa samo wani gamsasshen bayani .?"

"Kayi haƙuri yallaɓai wallahi ina ƙoƙarin ganin na samu masaniyar inda lu'u lu'un suke."

"Kullum abinda kike faɗamin kenan, amma sai yaushe ne zaki kawo min wani bayani mai amfani eye.?"

"Fashi da makami."

"Ke Raliya! Baki da hankali ne, kada ki kuskura ki fara aikata wannan mummunan kuskuren, wannan hanyar ba mai billewa bace. Da mai amfani ce bazamu kai war haka batare da mun mallaki wannan kadarar ba, ko zamu kuma aikata hakan ba nan kusa ba akwai sauran lokaci."

"Amma yallaɓai naji kamar batun aurenta akeyi."

A kishingiɗe yake amma jin wannan batun yasa shi miƙewa batare da yasani ba, cin hargagi yake faɗin.
"Aure! Aure dai? Meyasa baki faɗan hakan tuntuni ba Raliya, sai zuwa yaushe ne ƙwaƙwalwarki zata dinga yin abinda ya kamata ne."

"Kayi haƙur..."

"Hell with this fucking word Raliya! Hakurin me zanyi, abubuwa na shirin lalacemin kice wai nayi hakuri."

"Amma yallaɓai naga wanda zata aura ɗan gida ne shiyasa banyi tunanin komai."

"Wanene wanda zata aura ɗin."

"M.J ne."

Wani murmushi yayi mai sauti kana yace.
"Woow! Komai ya kusa zuwar mana da sauƙi, kin tabbata shine wanda zata aura."

"Na tabbata ranka ya daɗe yanzu haka ma yana garin Bauchi yazo ganinta."

"Ki tsaya ki saurareni dakyau Raliya, wannan ne lokacin mu na samu ko rashi, a yanzu ne muke da damar yin duk wani abu da muka daɗe muna shiryawa, inaso ki lura sosai da duk wani motsinta daga yau, saboda inada tabbacin cewa nan bada jimawa ba za'a nemi sauyawa diamonds ɗin nan wajen zama, ki sanar dani duk wasu bayanai da zaki samu, zan organising team ɗin da zakuyi aiki tare da zarar angano inda suke kiyi ƙoƙarin samu mana bayanai kawai."

"Zan kula sosai yallaɓai."

"Ohk" kawai ya kuma faɗa tare da kashe wayar.

Shiru tayi bayan gama wayar tasu tana tunani, tabbas wannan ita kaɗaice damar da take da ita domin ƙara samun kusanci da Alpha, ya zama dole yanzu ta shirya ɗamarar yin fito na fito da Zarah akan Diamonds ɗin nan, ba damuwarta darajarsu ba ko kuɗin da za'a samu akansu, babban abinda ya dameta shine ta wannan hanyar ne kaɗai Alpha zai dinga ganin ƙimarta har ta samu nasarar cusa soyayyarta a cikin zuciyarsa, saboda sanin yadda yake da babban buri akan Diamonds ɗin.
"Lokaci yayi da zanja ragamar wasan nima." ta faɗa cikin wani shu'umin murmushi.

💫💫💫💫💫💫💫💫💫💫

Gefen hanya ta samu tayi parking motarta saboda kiranta da Jidda keyi a waya, hannu tasa ta ɗauki wayar tare da maida kiran daya kuma katsewa.

"Ina kika shiga ne nake kiranki bakya ɗagawa."

"Toh shugabar masu ƙorafi tuƙi nakeyi."

"Kin fita aiki ne?."

"Aa cefane naje yi inaso na shiga kitchen da kaina na shiryawa Big Bros abincin."

"Nima ai naso zuwa wallahi Sa.Jid ne ya hanani wai saura kwana nawa ne ma da duk zaku dawo Gomben."

"Saboda ke gaki mai ƙafar yawo ko.?"

"Hmm! Kin cika ni da surutun ku na ƴan sanda baki barni na faɗi dalilin kiran nawa ba."

"Wato surutu ma na cika ki dashi ko.?"

"Baza dai ki barni na faɗi abinda zan faɗa ba kenan.?"

"Ohh sorry ina jinki."

"Akwai matsala fa"

"Wacce irin matsala kuma."

"Jiya naje gidan Momi take gayamin wai a ɗaya part ɗin nan zaki zauna kafin a ƙarasa muku gyaran gidan da zaku zauna."

"Yanzu ya za'ayi kenan."

"Baki zaki buɗe ki gayawa Daddy kin fiso a gyara muku gidan tukun, idan babu hali ma sai a ɗaga bikin tunda kinga abu ne mahimmaci zamuyi."

"Haka za'ayi zamuyi maganar."

"Toh shikenan sai anjima ki gaishemin dasu idan sun sauka."

"Ok bye."

Motar ta kunna bayan ta ajiye wayar sannan ta nufi gida kai tsaye, M.J kaɗai ta tarar a falon bayan shigarta ciki da sallama, bata kulashi ba ta nufi hanyar kitchen, juyuwa tayi tare da aika mishi wani sihirtaccen kallon jin abinda yake faɗa.
"Allah yasa dai kin wanke najasar tun a waje baki dawo dashi cikin tsarkakken gidan nan ba."
Shigewa tayi batare da tace komai ba, shikuwa tsaki ya furzar mai sauti tare da miƙewa ya bar cikin falon.

A zaune ta tadda Baaba a kitchen ɗin tana yankan ɗanyar kuɓewa, ledojin hannunta ta ajiye tare da faɗin
"Me zakiyi da kuɓewa kuma Baaba.?"

"Babanku ne yace yanaso a mishi shine nafara gyarawa kafin ki dawo, ina kikaje ne.?"

"Kasuwa naje na siyo sauran abubuwan da bamu dashi a kitchen ɗin."

"Gashi ki ƙarasa wannan bacci ne yaketa ƙoƙarin kamani tun ɗazu zanje na ɗan kwanta, saiki kira Raliya ta kama miki wasu aiyukan."

"Toh" tace tare da karɓar rubar da kuɓewar ke ciki, ita kuma Baaba ta fice a kitchen ɗin, saida ta gyara komai tare da fitar da duk wani abu da zata buƙata kafin itama ta wuce ɗakinta tayi wanka da sallah kafin ta fara aikin.

Tun ƙarfe biyu ta shiga kitchen ɗin tafara hada-hadar haɗa abincin tarbar baƙin nasu, ita kaɗai takeyin duk wasu aiyuka ba kamar yadda Baaba tace ta nemi taimakon Raliya ba, a dole ne kawai take haƙuri Raliy na kusantar inda take bawai dan tanaso ba, saboda tsanar da takeyiwa Alpha da duk wanda ya dangance shi.
Kasancewarta mai saurin aiki yasa kafin la'asar harta gama haɗa komai illa kawai masa ɗin da bata soya ba wanda shima rashin tashin da baiyi ba ne ya hanata soyawa. Baaba ce ta kuma shigowa kitchen ɗin da sallama tana faɗin.
"Yanzu Zara'u da nace ki kira Raliya ta kama miki wannan aikin shine kika ƙi koh.?"
Sai a lokacin Zarah ta lura da Raliya dake bayan Baaba, kau da kai tayi tare da faɗin.
"Naga aikin ba mai yawa bane shiyasa."

"Allah ya kyauta wannan halin naki, saka min tuwon nikam idan kin gama."

"Toh kije zan kawo miki."

"Ban yarda ba sakamin na tafi dashi ko kibawa Raliya ta kawomin."

Ba yadda ta iya haka ta saka mata malmalar tuwon guda biyu a plate sannan miya a ƙaramin glass bowl, a wani ƙaramin faranti ta jere mata tare da ɗora mata kwalbar soyayyen man shanu ta miƙawa Raliya farantin suka fice tare.
Saida ta wanke abubuwan da tayi amfani dasu kafin ta nufi ɗaki saboda kiran sallar la'asar da akeyi, cikin sauri ta watsa ruwa ta fito bayan shigarta banɗakin sannan ta shimfiɗa darduma tare da tayar da sallah.

Ko da ta idar gaban dressing mirro ta nufa domin shiryawa, saboda ƙarfe biyar jirginsu Daddyn zai sauka, simple makeup tayi wanda ya matuƙar yi mata kyau saboda yadda ta tsara shi, wardrobe ta kuma tare da zaro wasu rantsattsun riga da siket na wani dark blue ɗin less mai ratsin fari, cikin hanzari ta saka kayan ganin lokaci na ƙurewa, ba ƙaramin karɓar jikinta kayan sukayi ba musamman data yafa farin gyale mai duwatsu sanna ta saka farin takalmi, wayarta ta ɗauka ganin har ƙarfe 4:40pm yasa ta fita da sauri, bata tarar da Baaba a falo ba hakan yasa tabarwa Raliya dake ƙoƙarin shiga kitchen sallahun soya mata sinasir ɗin tare da faɗama Baaba cewar ta wuce airport.

A farfajiyar gidan ta gansu suna ƙoƙarin shiga mota wanda tana da tabbacin suma airport ɗin suka nufa, inda motarta take itama ta nufa batare da ta kuma kallon inda suke ba.

"Amaryarmu irin wannan kyau haka kamar wacce ke shirin zuwa gasar kyau na duniya gabaɗaya." cewar Abdallah daya leƙo da kanshi ta window yana magana.

"Banda zuga dai."

"Da gaske fa, kizo mu wuce tare mana ko ba airport ɗin kika nufa ba kema."

"A'a kuje kawai yanzu zan biyo bayanku."

"Sai tayi yawon dandin nata kafin nan, kaga bazata haɗa hanya damu mu hanata aikata kudurinta ba." cewar M.J yana taɓe baki kamar yaga wani abin kyama.

Hawaye taji......✍️


*BY*
*JASMINE*🌸🌸

*ASP ZARAH*👩‍✈️

...Hawaye taji masu zafi suna ƙoƙarin silalo mata, da sauri ta buɗe motar ta shige domin batason M.J ya gano lagonta.
Ta rigasu isa airport ɗin dan haka ta samu guri tayi parking sannan ta fito da jingina da motar ta yadda waɗanda take jira zasu iya hangenta, batayi minti goma da tsayuwa ba jirgin ya fara ƙoƙarin sauka ƙasa daidai lokacin kuma motarsu Abdallah ta iso gurin inda sukayi parking a kusa da tata motar.
Matafiya ne suka fara saukowa cikin takon isa na hamshaƙan da suka baro ƙasar turawa, ɗaya bayan ɗaya suka jero akan matattakalar da zata sauko dasu daga jirgin, ido ta baza sosai ta inda zata gano ɗan'uwan nata. Duk da yawan video call da sukeyi amma dakyar idanuwanta suka iya ganeshi saboda kyau daya ƙara, nufowa suke domin ƙarasowa inda suke tsaye ita da su Abdallah, saidai bazata iya jira su ƙaraso ba dan haka ne ta ruga a guje ta ƙarasa inda suke tare da rungume ɗan'uwan nata cikin tsantsar farin ciki, shima hannayensa biyu yasa ka ya maida mata rungumar tare da ɗan bubbuga bayanta jin tana shessheƙar kuka.
"Bakyason ganina ne na koma inda na fito ko.?" ya tambaya cikin son yaga ta daina hawayen.

Da sauri ta sakeshi tana saka bayan hannunta ta goge hawayen kana tace.
"A'a dear murnar ganinka ce kawai ta saka hakan, idan kace zaka koma to nima binka zanyi mu koma tare."

Daddy dake tsaye yana kallonsu ne yace.
"Wato ni ko sannu fa zuwar ma bazan samu ba duk da ni naje na taho dashi, ai babu damuwa nikam naga warayya ƙarara a fili."Cikin zolaya ya ƙarasa maganar.

Ɗan durƙusawa tayi da hanzari tana faɗin
"Sorry Daddyna ai nafi kowa murnar son ganinka, barka da dawowa ayimin afuwa."

"Babu komai daughter mu hanzarta mu wuce gida naga hadari ya haɗo."

Hannushi ta riƙe kamar wata yarinya suka ƙarasa wajen motocin, cikin fara'a suma sukayi musu barka da dawowa, nan aka ɗanyi raha irin wacce ke tsakanin uba da ƴaƴansa kana suka fara ƙoƙarin shigar da kayansu mota domin shigewa gida, Zarah kam hannun Sadiq taja zuwa motarta ta buɗe mishi gidan gaba ya zauna sannan ta dawo domin ɗaukar wasu kayan ta saka a tata motar, daidai lokacin daya sunkuya domin ɗaukar wata jaka itama lokacin da sunkuya zata ɗauka, a hankali yayi magana ta yadda ko Daddy dake tsaye agun bazaiji mai ya faɗa ba yace.
"Wato ke a ko ina saikin bayyana salon karuwancin naki ko, saboda asan kin shahara a bariki ne zaki rungume mutum a bainar nasi kuma ki ƙi sakinsa saboda ke ga ƴar bariki ko? Toh Allah yasa dai rungumar iya ta ƴan'uwan taka ta tsaya bata kauce hanya ba."

Da sauri ta ɗaga idonta da sukayi jazir saboda ɓacin rai ta kalleshi, wato cin mutuncin nasa har yakai matakin dazai iya zarginta akan ɗan'uwanta da suka fito ciki ɗaya, abubuwan da M.J yake mata idan ta mutu bata rama ba toh tabbas bata yafe mishi ba, batace komai ba ta ɗauki jakar ta nufi motarta.
Cikin ƙoƙarin danne ɓacin ran da take ciki ta buɗe mazaunin direba ta shiga motar tana faɗin
"Sorry dear na barka kana jira."

Kasa amsawa yayi illa idanunshi daya kafeta dasu yanason gano wani abu tattare da ita.
"Zarahty kina kallon kanki a madubi kuwa.?" ya tambaya da alamun mamaki a tattare dashi, leƙawa tayi kaɗan ta kalli madubi motar sannan ta ɗan juya ta kalleshi tana cewa.
"Nifa Yaya banga inda kwalliyar nan ta ɓaci ba, kawai ka saba da ganin fuskar turawa ne shiyasa komai kake kallonshi sabo."

Wanj murmushi yayi da iyaka fuska ya tsaya yace.
"Ba batun kwalliya nakeyi ba, ke baki taɓa tsayuwa a gaban mirro kin fahimci how not ok are you ba, baki ga irin ramar da kikayi ba kamar wacce ta fito a prison, wai meke damunki ne haka little."

"Ka dawo kenan ai Yaya, toh nidai aikine sukemin yawa bana samun lokacin hutu shiyasa kaga ina ramewa, ni banga ramar danayi ba ma fa."

"Ke kam ai bazaki gani ba, amma nasan tabbas bayan aiki akwai wani abu daban a cikin ranki."

"Uhmm nidai babu komai fa"

"Shikenan I'll figure out myself tunda nadawo ƙasar, ja mota mu tafi gida gashi harsu Daddy sun wuce sun barmu."

"Toh" ta faɗa sannan ta tayar da motar suka bar farfajiyar wajen, suna tafe suna hira tamkar wasu sa'anni ko kuma abokai saboda yanayin yadda suke hirar cikin raha da tsokanar juna, wannan na ɗaya daga cikin tarbiyar da iyayansu suka basu a zamanin da suke raye, son juna da kulawa ba tare da la'akarin babba ko yaro ba.
Cikin Mintuna ƙalilan suka iso gidan horn tayi aka buɗe ƙofar sannan ta nausa kan motar zuwa ciki, a farfajiyar gidan suka tarar da Baaba tsaye tana jiran ƙarasowarsu.
"Sannu da zuwa angona na kaina." tace lokacin data ƙaraso jikin motar, Sadiq ne ya fara buɗewa ya fita ta gefen da take tsayen, baki ta riƙe tare da zaro ido kamar tsohuwar da ta kama kwarto a ɗakin suruka, saboda mamakin yadda jikan nata ya sauya gabaɗaya duk kuwa da yawan ganinshibda takeyi idan suna video call, dariya yayi mai sauti ganin yanayin Baaban da kuma irin tsayuwar da tayi yace.
"Haba amaryata irin wannan kallon haka, ko kina tsoron ayi saurin kwace miki ni ne.?"

"Kwacewa ta nawa kuma Habu, ai yadda ka rikiɗe ka kuma bature nasan baza'a rasa wata baturiyar data kwace ka ba."

"Toh ki kwantar da hankalinki ni ɗin naki ne ke kaɗai kinji my one and only kakaty."

"Nifa banason wannan salon iskanci, daga dawowa zaka fara zagina tun daga kan iyaye da kakannina da wannan ɗan iskan yaren."
Dariya yayi sosai kafin ya dakata yace
"Toh yi haƙuri rabin raina, mu ƙarasa ciki sai muyi magana."
Juyawa yayi yana waige-waige yace
"Little ta shige ta barmu a tsaye ashe."

"Wannan mai baƙin miskilancin ai ba tsayawa zatayi ba."

"Ohh tana nan da halin ashe."

"Sai abinda ya ƙaru."

"Little ba dama Allah ya yaye mata."

"Amin idan mai barin ta ne."

Nan suka shige falon suka samesu idan Zarah ke zaune a ƙasan kujerar da Daddy yake kai ta ɗaura kanta akan cinyarshi, Abdallah da M.J kuwa suna zaune ne a kujera two seater. Zama sukayi aka shiga gaisuwar yaushe gamo da kuma ƙarin ta'aziyar da aka yiwa juna, sun jima suna hirar kafin Baaba ta umarci duk su miƙe domin zuwa dinning, Zarah ce tayi serving kuwa da abinda yakeso sannan suka fara cin abincin cikin nutsuwa da yadda addini ya koyar.
Ko da suka gama ita ta tattare gurin ta kimtsa shi yabkoma kamar ba'aci abinci a gurin ba, falon ta kuma inda ta samu Daddy ya wuce sashin baƙi domin hutawa, zama tayi a gefen Baaba akan doguwar kujera tace.
"Dear ba zakaje kayi wanka ka huta ba kaima."

"Ke Zara'u kowa saikin ɓata mishi suna ne, mene ne kuma giya ɗin da kike kiranshi dashi."
Dariya sukayi gabaɗayan su har M.J da hankalinshi yake akan wayarsa saida ya ɗan murmusa, tsagaitawa Sadiq yayi yace
"Gaskiya ba ƙaramin wauta nayi ba na barin Nigeria ko wannan comedy ɗin da kike cirewa ai ya ishi mutum farin ciki na sati guda, Little jeki haɗamin ruwan wanka ganinan zuwa."
Miƙewa Zarah tayi cikin dariya tabar falon.

"Turanci bai yi muku rana ba tunda kun zubar da al'adun ku."

"Kakaty kenan, bari naje nayi wanka na huta sai na dawo mu cigaba."
Shima miƙewa yayi tare da bawa Abdallah hannu sukayi musabaha, hannu kawai M.J ya ɗaga mishi lokacin daya miƙa mishi hannu da nufin yin musabahar, baiyi mamaki ba domin tun zuwanshi ya fahimci ɗabi'un M.J ɗin musamman a gareshi da yake ganin tamkar baiyi farin ciki da dawowar tasa bane, kaɗa kai kawai yayi sannan ya nufi hanyar side ɗinshi.
A tsaye ya tadda ta tana ƙara kimtsa mishi ɗakin, murmushi yayi mai sauti yace.
"Ke dai bakya iya zama bakiyi aikin komai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login