Showing 6001 words to 9000 words out of 34298 words

Chapter 3 - Asp Zarah 1 Hausa Novel Complete

01 Jan 2025

198

kwana ukun nan duk wanda yaga halin da suke ciki saiya kuka, Baaba kawai mai ƙarfin hali a cikin su.
Ga Rahma da har yanzu bata farfaɗo ba.

Gabaɗaya suna zaune a falo a daren ranar ukun harda Daddy da Mustapha da shima kullum baya rabo da gidan.

Zarah na kwance saman dogowar kujera yayinda tayi filo da ƙafar Baaba.
Lokaci ɗaya ta miƙe a firgice.

Kallonta Daddy yayi tare da faɗin" Lafiya kuwa Zarah.?"

"Daddy CCTV , na jona CCTV a duka falon dake gidan nan." Ta faɗa lokacin da ta miƙe sannan da gudu ta nufi hanyar ɗakinta......

Da gudu ta nufi cikin ɗakin tare da nufar inda ƙaramar na'urarta take ajiye, sashin abubuwan da suka faru a cikin satin ta shiga tare da playing daga ranar farko.

Daddy da sauran mutanen gidan ne suka shigo ɗakin, gabaɗaya suka zauna domin kallon abinda ke wakana a cikin na'urar.
Saidai gabaɗaya babu abubuwan da suka faro a kwanaki uku da suka wuce wanda hakan ya tabbatar mata da cewa akwai wani wanda ya shaidama Alpha na'urar da ta saka.
Cike da takaici ta rufe na'urar tare da kwanciya akan gadonta.

Babu wanda ya tanka duk suka fice a ɗakin.

Babu daɗewa kira ya shigo wayar Zarah, hannu ta kai ta janyo wayar tare da kallon fuskar wayar domin ganin mai kira. Ɓoyayyiyar number ce ke kira, tamkar bazata ɗaga kiran ba saida ta kusa yankewa kafin ta ɗaga tare da karawa a kunnenta batare da tayi magana ba.

"Na tabbatar yanzu kin fara gaskata abinda Alpha yake da damar yi ga duk wanda ya shiga gonarsa." Daga ɗaya ɓangaren aka faɗa

Zaune ta miƙe batare da tayi magana domin ta gane wanda yake maganar.

Magana ya cigaba dayi ta hanyar faɗin "Kada kiyi saurin karaya ta hanyar ajiye aikinki Zarah domin kin riga kin shiga wasan da baki da damar fita, ba'ayi komai ba tukun. Kin shirya bada kadarar ko baki shirya.?"

Mamaki ne ya cikata jin abinda ya faɗa, tabbas Alpha ba ƙaramin shiri yayi akanta ba domin da Daddy kaɗai tayi maganar ajiye aiki kuma shiɗin ma bai goyi bayan hakan ba sannan tanada tabbacin cewa ba wajen Daddy yaji wannan batun ba. Ajiyar zuciya ta sauke a ɓoye kafin tace

"Bana zuwa akan lokaci amma tabbas idan na iso waje ina jan ragamar kowani wasa tare da kasancewa mai nasara, ka faɗama kowaye ya sanar dakai cewa Zarah zata ajiye aiki da yaje ofishinta a gobe ranar litinin domin ya samu maka cikakken bayani."

Bata jira mai zaice ba ta kashe wayar gabaɗaya.
Takalmi ta zura tare da fita zuwa falo, dukkan su suna zaune kamar yadda suke da farko.

Zama tayi kusada ƙafafun Daddy tare da faɗin
"Daddy inaso gobe zan koma bakin aiki."

"Zara'u wace irin magana kikeyi haka, kodai kema ƙwaƙwalwarki ta taɓo ne kamar yadda ƴar uwarki ta samu.?" Faɗin Baaba wacce maganar da Zarah tayi ya tadata Zaune daga kishingiɗen da take.
Sunkuyar da kai tayi batare da tayi magana ba.

Daddy ne yayi gyaran murya tare da cewa.
"Baaba ina ganin mu barta ta koma bakin aikinta ƙila akwai wani muhimmin abu da zata gudanar ne bayan haka kuma zamanta a gida bashine zai dawo mana da waƴanda muka rasa ba. Hasalima aikin nata zai taimaka wajen binciko da masu hannu akan wannan lamarin."

Jinjina kai Baaba tayi cikin gamsuwa da maganganun Daddyn sa'an nan tace.
"Toh yaya batun Rahmatu kuma.?"

"Ehh Amminsu zata wuce da ita can Cairo a cigaba da duba lafiyarta tunda maigidan nata ya amince, Zarah kuma zata zauna anan saboda binciken da zata cigaba da gudanarw. Sannan ina neman alfarmarki Baaba da ki cigaba da zama anan tare da ita, kasancewar mace bai kamata ta zauna ita kaɗai ba saboda kare mutuncinta. Insha Allahu kuma zamuyi ƙoƙarin ziyartar ku lokaci lokaci kamar yadda muka saba." Cewar Daddy

"Babu damuwa Sulaimanu Allah yayi albarka ya albarkaci zuri'a."

Da Ameen sika amsa gabaɗaya kafin kowa ya miƙe domin zuwa kwanciyar bacci wanda a zahiri ba haka bane domin raba dare suke gaban mahalicci suna kai mishi kukansu.

Washegari tun ƙarfe bakwai Zarah ta fito cikin shirinta sanye da kakinsu na ƴan sanda, baƙin wando da shuɗiyar riga, inda ta ɗora baƙar Abaya mai ratsin shuɗi a saman kayan sannan tayi rolling da gelen rigar.

Ammi kaɗai ta tarar zaune a falo tana jan carbi, ƙarasawa tayi tare da zaunawa a ƙasan kujerar da Ammin ke zaune.

"Barka da safiya Ammi."

Kanta Ammin ta kwantar akan cinyarta tare da shafawa a hankali.

"Ina fatan kintashi lafiya.?"

"Lafiya lau Ammi, zan wuce aiki ina barar addu'a." cewar Zarah lokacin da take gyara kanta a cinyar Ammin.

"Allah ya kareki daga dukkan sharrin masu sharri, Allah ya nesanta zuciyarki da aikata abinda ba daidai ba, Ina roƙon Allah ya baki nasara ga duk abinda kikasa a gaba. Allah ya albarkaci rayuwarki."

Cike da jindaɗin addu'o'in Ammin take amsawa da Ameen kafin ta miƙe tare da mata sallama ta nufi hanyar fita daga cikin falon.

Gurin motarta da yaran Mustapha suka wanke mata ta nufa domin masu yi musu aiki tun bayan faruwar wannan lamarin suka aje aiki saboda tsoron kada a ƙara kawo wani harin a haɗa dasu tunda na farko dai hodar saka bacci aka shaƙa musu basusanai zai iya faruwa ba nan gaba.

Cikin mintuna ƙalilan ta isa ofishin nasu, tun kafin ta ƙarasa parking sergent Bala ya iso inda motar take ya buɗe mata ƙofa bayan ta gyara tsayuwar motar.
Ƙamewa yayi har saida ta fito sannan ya kulle motar.

"Ranki ya daɗe barka da safiya. Ya ƙarin haƙurin mu."

"Barka dai Bala, haƙuri mungode Allah." ta faɗa tana mai fara tafiya domin isa ofishinta.

Karbar jakarta yayi bayan yace" Allah ya gafarta musu."

"Ameen." tace a taƙaice.

Haka ƙananun jami'an suka jigaba da mata gaisuwa harta ƙarasa cikin ofishin ta.

Tana ƙoƙarin ajiye wayarta akan tebirinta kira ya shigo, ganin mai kiran ne yasata sakin wani kyakkyawan murmushi.

"Assalamu alaiki ya habibaty." abinda aka faɗa kenan bayan ta kara wayar a kunnenta

"Wa'alaiki salam Dr. Jiddah amaryar Bar. Saleem." Zarah ta faɗa tanamai zama a kujerarta

''Ki faɗawa wanda bai sani ba, naga alama tsokanar da bakiyi kwana biyu ba kikeson yi kuma ba kulaki zanyi ba. Dafatan kin tashi lafiya yasu Ammi."

"Lafiya lau suke duka."

"Ya ƙarin haƙuri kuma."

"Alhamdulillah."

"Allah ya musu Rahama."

"Ameen Ameen. Ina kika baro maƙalematan naki banji motsinsa ba." Zarah ta faɗa cike da barkwanci.

"Ke dai bari habibaty, jiya kwana nayi ina mishi kukan nagaji da zama a cikin masu jajayen kunnuwa shine yau ba shiri ya fita domin fara haɗa tarkacensa." Jidda kenan take maganar cikin sanyi murya.

"Babu kyau abinda kike aikatawa fa, ki dinga damun bawan Allah yana miki abinda kikeso koda shi bayaso ɗin."

"Auren kenan ai kema kiyi kigani ko baza'a miki abinda kikeso ba."

Kafin tayi magana aka kwankwasa ƙofar ofishin nata da haka tace.

"Zamuyi magana anjima SA.JID zan fara aiki a ofis."

"Innalillahi! Yanzu Zarah tun ba'a sadakar bakwai bama har kin fara fita wannan ƙaddararren aikin, so kike ki jama kanki zance a gari."

Shiru Zarah tayi na wani lokaci kafin tace" Jiddah ya zanyi to, *Alpha* kinsani Idan ban kasance a ofis ba na wani lokaci mutane da dama zasu rasa abubuwa masu mahimmanci sanadin wannan mutumin."

"Shikenan Allah ya taimaka, nima dai Insha Allah zuwa wani watan zamu dawo." Jiddah ta taɗa cike da tausayin Zarah.
Sallama sukayi sannan suka katse kiran lokaci guda.

Umarni ta bada a shigo lokacin da take ajiye wayar a kan teburinta.

Sergent Bala ne ya kuma shigowa hannunshi ɗauke da farar takarda, saida ya sara mata kafin ya fara magana.

"Ranki ya daɗe wannan saƙo ne daga ofishin mai girma kwamishina, jiya da yamma ya aiko tare da bada umarnin lallai akai miki saboda abune mai mahimmanci. Dama yau nakeson kawo miki idan na tashi a aiki sai kuma gaki kinzo."

Kaɗa kai Zarah tayi kafin tace" Sau sa dama Bala ina gayamaka ka koyi saka maganganu a cikin kalma ɗaya, basai kayita dogon sharhi ba a matsayinka na ɗan sanda. Anaso maganar jami'i ta banbanta dana sauran mutane, anfiso idan kayi magana sai mutane sunyi nazari sosai kafin su gane ainahin abinda kake nufi ba kamar yadda kake magana yanzu ba."

Ƙamewa ya kuma yi kafin yace.

"Ayimin afuwa ranki ya daɗe zan gyara."

Bata kula da maganarshi ba tace.

"Me takardar ta ƙunsa."

"Ranki ya daɗe bani da damar buɗewa saboda a kulle take cikin envelop."

Hannu tasa ta karɓi takardar tare da buɗe envelop ɗin ta cirota.
Mintuna biyu ta ɓata wajen nazartar abinda ke cikinta.

Ɗagowa tayi daga kallon takardar tare da maida kallonta ga Sergent Bala sa'an nan tace.

"Taron ƙarawa juna sani a harkar aiki ne ake umartana naje wanda za'a gudanar a garin Abuja. Cikin sati ɗaya za'a gama gudanar da taron wanda zai fara ranar alhamis, sannan kaida Jennifer ne zamu kasance tare."

Bata jira mai zaice ba ta bashi umarnin tafiya.

Jingina kanta tayi da jikin kujerar sannan ta lumshe idanuwa.

Haka ta wuni a ofishin sam takasa taɓuka komai bayan kuma da shirin yin aiki ta fito saidai ta danganta hakan da saƙon kwamishina daya risketa.

Cikin kwana ukun ta kammala duk wasu shirye shiryen ta na tafiyar.

A gefe guda kuma su Ammi na shirye shiryen tarban Muhammad Jawwad da shima zai iso ƙasar ranar Alhamis wanda rabonshi da ita tun yana ɗan shekara 14.

Jirgin ƙarfe tara Zarah zatabi zuwa garin Abuja yayinda jirginsu Muhammad Jawwad zai sauka ƙarfe takwas da rabi.

"Daddy ina jin ku wuce kawai zanbj ta ofishin kwamishina kafin mu wuce." Zarah kenan ke faɗi bayan ta gama amsa wayar da Sergent Bala ya bugo mata.

"Babu rabon zaku haɗu da ɗan'uwan naki kenan saboda shima kwanaki biyar zaiyi ya koma saboda inaso ya dawo ƙasarshi ya cigaba da aiki." cewar Daddy

"Banji daɗin haka ba gaskiya amma tunda zai dawo ƙasar gabaɗaya zamu ga juna."

"Shikenan Allah ya kiyaye hanya."

"Ameen Daddy."

Sauran iyayenata ma addu'ar sauka lafiya suka mata kafin ta shige motarta ta fice a gidan.

Daddy, Momi da Ammi sune sukaje airport tarbar ɗan nasu domin Baaba batada damar fita saboda halin takaba da take ciki.

Basu jima da isa ba jirgin ya sauka, dubawa suke domin ganin ta inda zai ɓullo amma basu ganshi ba.
Wani kyakkyawan bature ne suka ga ya nufo inda suke tsaye, basu ankara ba suga ya rungume Daddy tare da faɗin" Nayi kewarka Daddyna."

Salati Ammi ta shiga rafkawa tana faɗin.

"Jawwad kaine haka.? Shikenan masu jajayen kunnuwa sun canja ka, ka koma jinsinsu."

Dariya sukayi gabaɗaya sannan suka nufi gurin da motarsu take, ita kuwa Momi kunyar fulani da kawaicin ɗan fari ne ya hanata magana.
Mota suka shiga tare da nufar gida.



A ɓangaren Zarah kuwa koda kwamishina ya gama zayyana mata tsarin yadda taron zai kasance saita miƙe domin tafiya, har ta kama hannun ƙofar da nufin buɗewa ta fasa tare da waiwayowa ta kalli kwamishinan da hankalin shi ya koma kan takardun dake saman teburinsa tace.

"Yallaɓai nace ba."

Kallonta yayi batare da yace komai ba.

Murmushi tayi mai cike da ma'anoni kafin tace.

"Yallaɓai idan ba damuwa ka faɗawa wanda ya baka umarnin wakiltani a matsayin wacce zata halarci wannan taron cewa _Babu ma'ajiyar CCTV a ofishin ASP Zarah sannan baya buƙatar na'ura mai ɗaukan sauti domin sanin abubuwan da nake gudanarwa a cikin ofishina._

Bata jira mai zaice ba ta buɗe ƙofar tare da ficewa a ofishin........ ✍🏼

*Jasmine*🌸🌸


*TALLA*! *TALLA*!! *TALLA*

*Uwargida!!! Shin ko kinsan zaki iya magance matsalolin da suka daɗe suna ci miki tuwo a kwarya cikin gidan aurenki.???*
*Uhmm riƙe sirri sai mai sirri, shin kinada labarin shahararriyar matar nan wacce ta shahara wajen ganin cewa mata basu wulaƙanta a gidan mazajensu ba.!? Wacce ta kware wajen gyara amarya har ma da uwargida.? Ita ɗin dai dake siyar da kayan gyara na musamman masu sauƙin kuɗi amma akwai aiki, mai kawo muku sirrika da dabarun gamsar da miji ta kowani fanni.*😍

*Kardai na cika uwar gida da surutu, nice dai HAJIYA JAMILA SHARE KUKAN MATA. A wannan karon nazo ne da zafafan darussa da zan gabatarwa mata tare da kayan gyara na musamman. Bari dai na lasa muku zuma a baki, kaɗan daga cikin darussan da zan gabatar a wannan karon:*

*Sirrin TomTom*
_Shidai tom tom da kika sani uwargida, matsalar ki ta wajen kasa gamsar da mai gida ta ƙarw idan kika riƙe wannan sirri._

*Zuba ki lashe*

_Bazance komai ba a wannan fannin idan kinason sani to ki kasance tareda ni a cikin sati ukun dazan gabatar da darussa_.

*Kayan gyara na musamman zai iso ki har garin da kike idan kinyi odarsu, domin sanin kalar su da amfaninsu to ki kasance dani cikin zazzafan darussa na sati uku da zan gabatar a Special Group na ASP ZARAH FANS.*

*Kada ki bari ƙaramin kuɗi ya saki zama mara gata gidan mijinki.*

*Ki tuntuɓi wannan number 07048961623 domin samun damar shiga ASP ZARAH SPECIAL FANS GROUP, Inda ni HAJIYA JAMILA SHARE KUKAN MATA zan kasance daku.*
*Kada ki bari ƴar uwarki ta baki labari*.
*SAI KUNZO*

Ya kasa koda motsa yatsa ne saboda kaɗuwa da yayi da zancenta, yanzu kam ya fara zargin ko Zarah tana da aljanu masu faɗa matan idan anyi maganarta.
Kiran wayar sirri sukayi da Alpha lokacin da yake shaida mishi ya tura Zarah garin Abuja domin halarta taron ƙarin ilimi a fannin aiki, hatta da wayar da yayi amfani da ita tana killace a ɗakin barcinshi na gida.
Duk tunanin dayayi bai samar mishi da amsar inda Zarah taji labarin za'a sanya CCTV a ofishinta ba, yanke shawara yayi na kiran Alpha domin shaida mishi abinda ya faru.

Saida ya kira sau biyu kafin aka ɗaga kiran.

Cike da jimami kwamishina ya karanto mishi abinda ya faru a ofishin nashi kusan mintuna goma da suka wuce.

"Ya akayi tasan da batun CCTV.?" Alpha ya faɗa cike da masifa

"Kayi haƙuri Alpha nima bansan ina ta samu labarin ba." Ya faɗa kai a sunkuye tamkar yana gabanshi.


Shiru ya biyo baya na wani lokaci kafin Alpha yace.
"Ku bar batun saka camera ɗin tukunnan zanji da lamarinta a garin Abujan."

Ya kashe wayar batare da yayi magana ba.

Ƙayataccen ɗaki ne wanda yaji kayan alatu masu matuƙar kyau da tsada, tsaruwar ɗakin kaɗai zaisa mutum yayi tunanin na wani hamshaƙin shugaban ƙasa ne amma idan aka ƙurewa fitilun dake kawowa da ɗaukewa idon za'a gane mamallakin ɗakin sakamakon sunan Alpha da suke rubutawa a kowani kawowa da suke yi. A tsakiyar ɗakin wani haɗaɗɗen gilashi ɗauke da kyawawan kifaye a saman shi cikin ruwa suna ta shawagi yayinda ƙasan gilashin ke ɗauke da wasu kyawawan halittun ruwa da bazan iya tantance sunayensu ba.

Maganganun ke tashi a cikin falon saidai banga alamun ta inda nake jiyo maganar ba, muryar namiji ne ke maganar inda yake cewa.
"A matsayin marainiya mai neman aiki domin tallafawa mahaifiyarki zakije gidan, sannan ki tabbatar bata cikin gidan yayinda zakije neman aikin saboda kaucewa matsala."
Har zuwa wannan lokaci mai maganar bai bayyana ba illa wata matashiyar yarinya da tafito daga wata kusurwa a cikin falon, kyakkyawa ce daidai gwargwado sannan fatarta ta kasance kalar chocolate.
Kallo ɗaya mutum zaiyi mata ta gane tana cikin damuwa sosai sakamakon idanunta da sukayi jazir saboda kukan da tasha.

Ƙofar dazata sadata da farfajiyar gidan ta buɗe tare da fita a falon, babban fili ne sosai dake ɗauke da gine gine a wani gefe sannan shukoki kala daban daban da suka ƙawata wajen ciki harda manyan bishoyin kwakwa wanda su sukafi yawa a wajen. Sai ƙananun shukoki da aka tsarasu tamkar a ƙasar turai, a ƙasa kuwa wasu kyawawan duwatsu ne masu haske da sheƙi waɗanda ke ƙara bayyana kyawu da tsarin farfajiyar wannan gida da ya kasance tamkar na sarauta. Jefi-jefi mutane na shawagi a farfajiyar inda yawancinsu suka kasance mata sa'an masu ƙananun shekaru.

Tafiya tayi sosai kafin ta iso wani keɓaɓɓen guri da ruwa ke gudana tsakanin waɗansu matsakaitan duwatsu, wasu mata ne ke zaune su uku suna ɓare kwakwa. Ta farko keyin hanya a jikin kwakwar, ta biyu kuma ke ƙarasa barewa yayinda ta ukun cikinsu ke ɗauraye jikin kwakwar bayan a ɓare tare da jerasu cikin wani kyawawan kwando.

Zama matashiyar yarinyar tayi a gefe tare da jingina kanta a jikin wata ƙaramar bishiya.

Gabaɗaya suka maida hankalinsu kanta, kafin wacce ke wanke kwakwar tace.

"Meke faruwa ne Raliya, wani abinda ya miki ne.?"

Ɗago kanta tayi tare da maida kallonta garesu tace.

"Zanso ace wani abu ne ya shiga tsakanina dashi saidai babu abinda yamin illa aiki dazai turani a gidan da waƴannan lu'u lu'un suke."

"Raliya wani lokacin kina saka mana shakku akanki, dukkan mu anan fata muke mubar cikin wannan azzalumin gida ke a lokacin ne keki fatan kasancewa da mai gidan ki dinga aikata haramtaccen abu dashi." Fadin ɗaya daga cikinsu bayan ta maida hankali kan ɓarar kwakwar da takeyi bayan jin furucin Raliyan.

"A yanzu bana fatan barin wannan wajen saboda waƴanda nayi fatan ƙara kasance dasu basa duniyar zan fiso na cigaba da kasance anan saboda ko bana nan ɗin zaiyi wuya na tserewa *ALPHA* tunda na rigada nasan wasu sirrika nashi, bazai taɓa barina a raye ba tunani zaiyi asirin shi zan tona." Faɗin Raliya

Ɗayar da tun fara maganar bata tofa ba tace.

"Ki dinga yiwa kanki kyakkyawan fata Raliya idan ba haka ba zuciyarki zata iya rikeɗewa ta koma irin tasa na marasa imani."

"Hauwa kenan ai yanzu haka banajin akwai abinda zuciya da gangar jikina zasu kasayi indai umarnin Alpha ne. Ku da iyayenku kawai ya rabaku ya kawoku nan amma nifa? Da hannayena guda biyu yasa na kashe iyayena, zuciyata ta gama bushewa tun a waccan ranar. Zan iya raba kowaye da jindaɗin sa kamar yadda akasa na raba kaina da nawa jindaɗin." Ta faɗa tana mai maida kanta ga kishingiɗar da tayi a jikin bishiyar.

Babu wanda ya kuma tankawa a cikinsu domin dai sun saba da jin kwatankwacin wannan furuci a bakin Raliyan tin bayan da tasamu kusanci da Alpha lokacin da tayi nasarar ganin yatsun hannunshi,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login