Showing 39001 words to 42000 words out of 60085 words
sa da ido yace, "Da gaske Salman abunda nake gani da ido na Narjeesah ce, da Amrah a gaba na ko kuwa mafalkin da na saba yin sane? ".
Jikin sa muka faɗa cikin kuka na ce, "da gaske ne Baban mu nice Narjeesahr ka, tare da Amrah a gaban ka, ba mafalki bane, daman sai da na faɗa masu cewar baka mutu ba, amman suka ƙaryata ni".
Shafa kaina ya keyi, nida Amrah, Amrah ta ce, "Baba mi yasa ka ƙi dawowa a cikin mu gashi gidan mu duk ya watse, akan yarka abar kaunar ka da jarabawa ta faɗa mata, amman idon wasu ya rufe Baban mu, Anty Narjeesh tasha wahala sosai nasan da kana a kusa ne da wanda ya isa ya aikata muna irin wula'kancin da akayi muna Baba! ".
Share muna hawaye yakeyi ya ce, "yan zun ba lokacin labari bane, saboda ƙurewar lokaci nima yan zun ne ganin ku nadawo cikin hayyacina da kyau na gane waye ni kuma na gane garin dana fito da iyalai na".
Da sauri na tashi zaune kallon Salman nayi sai yan zun ne, na ma gane shi ashe shine ya riƙe Baba ya hana sa faɗuwa ƙasa, ai kuwa muka haɗa ido na banka masa harara, shi kuma yayi murmushi, yayi ƙasa da muryar sa, yace, "wato kin kawo kanki gida na bama kijira har a kawo mani ke, kin ga yaro ɗan shala son kowa ƙin wanda ya rasa, kin biyosa har gidan sa".
Kallon kama raina mani da wayau na bisa dashi, nayi ƙasa da muryar ta nace, "malam kama shirya bani takarda ta, dan ina gama haɗa aikin da nazo yi a gidan ka, zan koma ƙauyen mu".
Harara ya watsa mani nima ramawa nake yi Amrah ce, tayi gyaran murya tana dariya ƙasa_ƙasa, kallon ta mukayi a tare sai muka ga ita da Baban duka idon su na akan mu, waskewa nayi, nace, Baba wane gurin ne aka ɓuye Shuraim? ".
Da sauri ya ce, "shin Amrah wane Shuraim Narjeesah na take faɗa ne? ".
Salman da sauri ya ce, "Abba ɗan mune nida ita, wanda muka haifa, shine aka kawo a gidan nan "
Sakin baki mukayi nida Amrah muna kallon sa cike da mamaki cikin jin haushin sa, nace, "ai daman kasan inda aka kawo sa, kayi kunnen uwar shegu dashi, ka barni ina ta wahalar da kaina har da kuka, kullum cikin kuka".
Na ƙarasa maganar ina murguda masa baki.
Cike da masifa ya taso mani, nima nataso masa, Amrah tace, "dan Allah ku bar wannan rigimar haka nan mu fuskan ci ƙalubalen dake gaban mu, kuma a gaban Baba kuke wannan rigimar taku da bata ƙarewa".
Sannan ta ce, "Baban mu yaron da aka rufe a gidan nan wanda Miss Yaseer ta baka kulawa da cin sa, da suturar sa, shine muka zo nema a gidan nan, kuma yaron su Yaya Salman ne da Anty Narjeesh wanda yake tsakanin su".
Cikin sauri Baban yace, "ku tashi da sauri muje ku gani kafin a riga mu ɗaukar sa".
Da sauri Salman ya ce, "ba zasu riga mu garesa ba, dan na zuba mata maganin bacci, kuma tayi baccin, sai dai masu yi mata aikin, masu tsaron gidan nan, amman nasan yanda zanyi dasu".
Tashi mukayi muka buɗe ƙofar cikin sanɗa muke tafiya muna kusa da shiga cikin ɗakin ne aka taƙa muna bindigogi ai da sauri nadawo bayan Salman na rungume sa, na rufe ido gam, saboda nafi kusa dashi Amrah kuma ta shige jikin Baba, wani daga cikin wanda suka taƙa muna bindigogin ya ce, "ku juya ko kuma mu kashe ku mu kashe banza".
Ai kuwa da sauri Salman ya juyo ni nadawo gaban sa ya riƙe ni, ya kalle su, ɗaya bayan ɗaya, ya ce, "to ku aikata mana kuga abunda zai faru, kuma kubar gidan nan tunda ba gidan uban ku bane, jahilci banza da yofi! "
Ai da sauri suka juya suka bar gurin cikin tsananin tashin hankali, sakin sa nayi ina sauke ajiyar zuciya haka Amrah cikin ɗakin muka shiga kwance yake cikin duhu sai da muka kunna fitilar waya muka hango shi kwan ce cikin sanyi sai rawar sanyi ya keyi, ai da gudu muka isa, gurin sa har muna rige_rige hawaye keta ambaliya a idon kowa rungume sa muka, cikin kuka da tausayin yaro na na ce, "Shuraim tashi ka gani ga Mommyn ka a tare da kai, da Anty Amrah da Daddyn ka da kakan ka, kaji yaro na!? "
Buɗe idon sa yayi, ai kuwa ya fashe da kuka ya shige cikin jiki na ya rike ni da ɗan ƙarfin sa, ya na kuka kamar ran sa zai fita, nima ƙara shigar dashi nayi jiki na, sai kuka mukeyi sai jiki na ke rawa, amsar sa Amrah tayi ta rungume sa, itama kukan takeyi haka, Salman ansar sa yayi, idon sa yayi ja saboda tsananin ɓacin rai, jijiyar kansa duk sun tashi sunyi ruɗu_ruɗe, haka Baban ya anshe sa ya rum gume sa a jikin sa.
Mun kusa awa ɗaya a gurin, Salman ya buɗe bakin sa da ket ya ce, tashi muje na raka ku ɗakin da zaku zauna ba tare da kowa ya san mike faruwa ba, kai kuma Baba ka koma bakin aikin ka insha Allah ba zasu fahimci komai ba".
Ɗaukar Shuraim ɗin yayi ya janyo hannu na, ya ce, "muje Amrah ".
Muka fito waje ta wata ƙofar yabi damu, ai kuwa sai cikin gidan har ƙofar ɗakin da muke da kayan mu a cikin sa, yazo zai wuce da sauri na ce, "wannan shine ɗakin da kayan mu suke ciki".
Kallon Amrah yayi ya nuna mata ta buɗe, ai kuwa ta buɗe muka shiga daga ciki a, tsakiyar gadon ya kwantar da Shuraim nima ya janyo hannu na, ya ce, ki kwanta, anan sai ki san dabar da zakiyi kafin ta shigo cikin ɗakin ki fito falon ki zauna, Amrah ke kuma ki kula da motsin Shuraim kin dai san wane mataki, ake cikin sa yan zun gashi yan zun ƙarfe biyu ta kusa na dare, kar ku ɓata lokaci please".
Gyaɗa masa kai mukayi, ya juya ya fita, muka rufe ɗakin muka kwanta, muka sanya Shuraim a tsakiyar mu, muna shafa sa har yayi bacci.
Waya na ɗauko nayi ta kiran layin Mrs barr amman ba'a ɗauka ba, Mrs Nazeer na kira, tayi saurin ɗauka, na ce, "kin kira layin Mrs barr kuwa?, nifa nayi ta kiran ta, har yan zun babu reply, to kodai kunyi tafiyar ku ne kun bar ni".
A cikin damuwa nake maganar gashi murya ta muryar kuka ce, dan har ta soma shaƙewa.
Da sauri ta ce, "nima fa tun ɗazun nake kiran ta, babu, reply anya dai ko mijin ta ya dawo ne, ta manta da maganar cika alkawarin bokan, ai kuwa kada tasa mu tafka asara, ki kira muna Mrs Naseer mu gani ko suna tare? "
Kashe wayar mukayi, na shiga kiran wayar Mrs Naseer itama sai da nayi mata kira ukku ta ɗaga, na ce, "haba taya zakuyi tafiyar ku, kubar mu, nida Mrs Nazeer, sai kiran wayar Mrs barr mukeyi taƙi ɗagawa kema sai da nayi kira ukku zaki ɗauka, da kun san ba zakuyi dani ba, da baku sa na kwaɗai tuba, da wannan aikin haba dan Allah! ".
Cikin tashin hankali tace, kika ce bata ɗaga wayar ki keda Mrs Nazeer anya kuwa tana lafiya dan ban taɓa ganin ta kasa cika wannan alkawarin ba, bayan daga wannan ta gama wahala nifa inada shakku a kai, indai ba ta ɗauki wayar ku ba, to batada lafiya, nima bacci ne ya sace ni dan ina zaune ina jiran ta kira ni, amman shuru kake ji kamar anshuka dusa, gaskiya da alamar tambaya "!?.
Kashe wayar mukayi muka ci gaba da kira ba amsa har Asubahi Amrah kuwa murmushi takeyi, tana ƙara gyara wa Shuraim kwanciyar sa, alwala muka ɗauro muka fara nafila, har aka kira assalatu, mukayi raka atainin fijri, mukayi sallar Asubahi, mukayi lazumi da azkar, sannan na fito cikin falon gidan nayi zaune na buga uban tagumi, sai kusan ƙarfe takwas ta fito a har gitse bata ma lura dani ba zata raɓani ta wuce nayi saurin shan gaban ta.
Na ce, "madam miye ya same ki ne mukayi ta kiran ki duk hankalin mu a tashe? "
Dafe kai tayi ta zauna daɓas a ƙasa tace, "nashiga ukku ni Haulart na rasa wannan damar ban san miye ya same ni ba, nayi wannan kuskuren nayi bacci mai mugun nauyin gaske, kira mani su a wayar ki suzo yau a gidan nan mu san abunyi, tun kafin guguwar nan ta taso ta dun ƙule guri ɗaya ta haifar da illar da aka ce, zata shafemu dukan mu! ".
Gir giza mata kai nayi, na ce, "duk suna a hanyar zuwa gidan nan saboda kowa da far gaba ya kwana saboda kiran da mukayi ta maki harda Mrs Yaseer a ciki ".
Shiru mukayi dukan mu ƙofar aka buɗe Miss Nazeer Mrs Naseer Mrs Yaseer a tare suka shigo a har gitse dukan su, indon su na akan Haulart saboda yan da duk ta birkice.
Mrs Nazeer ce ta ce, "Bafa zama zamuyi ba, kawai shawara ce, zamuyi mu samu mafita "
Mrs Naseer ta ce, "mafita kam babu ta, ta tashi kawai ta shirya mu ɗauki saƙon mu doshi cikin dajin nan wannan shine mafitar kawai ".
Ai kuwa duk sunyi na'am da wannan shawarar da sauri ta shiga cikin ɗakin ta har tan tun tuɓe da capet, ko wanka batayi ba, ta chanza kayan jikon ta, ta fito ko mayafi babu.
Kallon su nakeyi cike da mamaki Mrs Yaseer ta ce, "kinyi brush kuwa?.
Cike da masifa Haulart ta ce, "ke brush ya dama ni damuwa ta, ta fiye mani komai malama, kallona sukayi suka ce, muje, kada ki sa mu ƙara ɓata lokaci ".
Waya tace tayi ringing na ɗauka, nayi shiri na ajiye wayar na kalle su da kyau na ce........
"Comment and share*
*Ummu Ihsan ce*🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
💐💐 *NARJEESAH* 💐💐
*Rubutawa*
*NANA KHADEEJATU*
*_UMMU IHSAN_*
*ELEGANT ONLINE WRITERS*
_*Bismillahir Rahmanin Rahim*_
4⃣1⃣⏭4⃣5⃣
➿➿➿➿➿➿➿➿➿ kafin na furta wata kalmar, Mrs Yaseer ta dakatar dani gurin faɗar, "kamar motar mijin ki nagani a waje shida yaran sa, kodai ido nane yake yi mani gizo? "
Cikin da mamaki Haulman ta ce, "barrister ka? ki kagani kuwa? ".
Da sauri Mrs Nazeer ta ce, "kina nufin cewar baki san ya dawo ba ko miye? "
Cikin fushi ta ce, "taya zan san ya dawo ne, bayan nayi nauyin bacci amman wallahi sai ya haɗu da fushi na, bari nadawo gurin da zani zai gane kuren sa wallahi, ke kuma NARSAL tashi muje dallah! "
Dariya nakeyi harda dafe ciki na gir giza kai na, nace to ina ajiyar taki ne ko duk fushin yasa kin manta ne".
Tsaki kawai tayi tace, "nama manta ne" da sauri ta nufi hanyar kichin, ni kam da ido nabi bayan ta dashi, tayi kusan mintina goma sai gata ta dawo a har gitse cikin tsananin tashin hankali, ta ɗora Hannuwan akai duka biyun ta kwatsa uban ihu tana faɗar, "na shiga ukku na lalace sun sace, mani shi sun gudu dukan su, ban same su ba! "
Tafaɗi ƙasa tana shure_shure ƙafafuwan ta, a ƙasa, kowa cike da tashin hankali suke faɗar su waye ne wai!?.
Ƙofar da ta fito take nuna masu, duk suka saka salati suna faɗar, "mun shiga ukku dai zaki faɗa" duk sukayi zaune daɓas a gurin da suke, ai kuwa wata irin uwar dariya ce, na kece da ita har ina tafa hannu, na tashi tsaye ina kallon su ina ci gaba da dariyar, ai kuwa suka tsare ni da ido cike da mamaki in banda Miss Yaseer.
Takowa nayi har inda suke ina fara zagayen su duk su ukkun, ina tafa hannu, sakin baki da hanci sukayi suna kallona harda murza ido.
Sai da na gama zagayawa na tsaya a tsakiyar su, nace, "to yau dai anyi walkiya an haska kowa, yau ne zaku girbi abunda kuka shuka, Miss Nazeer Mrs Naseer Haulman, ina son ku bani aron ɗan sauran hankalin ku da ya rage a nan, tun kafin ya ƙarasa ɓacewa".
Kallon su na sakeyi ɗaya bayan ɗaya, na sauke mayafin nawa na ɗaure a ƙuna, na ci gaba da faɗar, "Amrah...! "Da ƙarfi yanda zata jini, na ce, "ki shigo daga ciki mana".
Ai kuwa duk suka maida idon su gun da Amrah ta fito ai duk sai suka tashi a tsaye suna sauke ajiyar zuciya, harda su faɗar wai har hankalin mu ya kwanta a gaskiya ki daina yi muna irin wannan wasar yan zun ba lokacin wasa bane, da sauri Mrs Naseer tayi niyar tun karar gurin su Amrah wadda take ɗauke da Shuraim a hannun ta,
Da sauri na dakatar da ita gurin faɗar, "dakata saurin miye kikeyi ne, ai bari kiji ƙarshen zan cen wanda kike ɗaukar sa da wasa, wannan yaron da kuke gani da kun san waye shi da hankalin ku yafi hakan tashi ba kamar Haulman "
Sake ɗaure fuska nayi ganin irin kallon da suke bina dashi naci gaba da faɗar "yan zun lokaci yayi da wannan guguwar da kuke tsoro zata haɗu guri ɗaya" Shuraim na kalla ina murmushi na ce, my lovely Son Come with me, "
Ai kuwa da gudu ya sauka jikin Amrah yayi kaina da gudun gaske ya ce, "Mommy I miss you ".
Da sauri na ɗaga shi sama ina juyi dashi muna dariya ina faɗar ɗan farin fitilar gida, ɗan farin mai maye gurbin soyayya ko wace, iri ce, ina son ka ɗana ɗan albarka ".
Dariya mukeyi, cikin giɗima da fir gita suka haɗa baki gurin faɗar, "ɗan kiii.....! Kuma!? Ta ya ya hakan ta faru ne!?.... Kodai kinyi hauka ne!? ".
Kallon ban za nayi masu nace, "eh amman ba irin taku haukar ba, yan zun ɗan wannan abun har ya isa ya firgita ku hakan kuma harda zufa, ina ga nace, daku Shuraim ɗan manyan mutane ne, ɗan masu mulki masu, gari ba irin muƙamin iyayen wasu ba, wanda suke ƙare rayuwar su a gidan yari ba? "
Sannan na ce, Shuraim ina Daddyn ka su gan shi, ko da yake nasan yana kusa bisimillah ".
Ƙofar falon suka maida idon su dan ganin mai shigowa, kawai suka ga Salman ya shigo, suka ƙara kafe ƙofar da ido ko zasu ga wani ya sake shigowa amman sai sukaga babu kowa a bayan sa, sai suka maida idon su a kaina suna yi mani kallon raini.
Dariya nayi nace, "Shuraim Daddy...! " na nuna masa, ai kuwa da gudu yayo kan Salman, shi kuwa ya durƙusa ƙasa, ya tara masa hannu ya ɗauke sa, ya shigar dashi cikin jikin sa, yana juyi dashi, suna dariya.
Ai sai Haulman ta daka masa uwar tsawa kamar wani bawan ta, ta ce, "wannan wane irin salon wulaƙanci ne, malam ku ajiye wannan diramar haka, kuma wallahi sai ka gamu da matsanan cin fushi na! ".
Dariya ya yi, ya tako yazo inda nake, ya haɗani da Shuraim ya rungume mu, ya sakar muna pick ni a goshi Shuraim a kumatu, wani irin uban ihu Haulman ta saka, tayo kan mu amman kafin ta ƙaraso, taji muryar Salma na faɗar kada ki kus kura ki kai gurin da suke wallahi idan kuma ba haka nan ba, jikin ki ne zai gaya maki! "
Da sauri suka maida idon su akan Salma, sai suka ga Muhseen a tsaye yana murmushi shida Salma, Muhseen ya ce, "bisimillah ku shigo daga ciki ".
Ai kuwa Mai martaba ne ya fara shigowa shida fulani da Mom da Dad, sai Naseer da Nazeer da Yaseer, da Jafar Aliyu Humaira Hindu Auta Nusaiba sai Baban mu, hannu duk suka ɗora akai cikin fir gici, suka faɗi zaune sai jikin su ke rawa.
Salma ce tayi gyaran murya tace, "Narjeesh kici gaba please ".
Ni kuwa muna can muna halin da muka saba, mintsil sa nakeyi, harda cizo idan na faki idon mutane, shi kuwa magana yakeyi ƙasa_ƙasa, "yarinya komai abun ki tunda kika kawo kanki gida na ba zaki koma zuwa wani gurin ba, ehe! Kima zauna a kusa da mijin ki uban "ya"yan ki, wata kila naɗan sama maki guri a zuciya ta".
Tsaki na doka masa wanda ya fito fili, Amrah tace, "Auta jeki gurin su, kiyi masu magana suna can suna aikata halin su".
Ai kuwa da gudu tayo kan mu ta rungume ni ta baya, tana faɗar, "Anty Narjeesh nayi kewar ki keda my Shuraim".
Sai alokacin ne ya sakeni na jiyo na run gume Nusaiba muna dariya Shuraim da sauri ya ce, "Anty nima ban ganki ba, ki ɗauke ni ki goya ni kuma ki rama mani dukan da wan can tayi mani taci zali na, harda baki na ta doke har da jini da hannu na, kuma bata bani abinci bata, goya ni inyi ta kuka kuma bana buga boll bana, yin komai...! "
Hannun sa yana kan Haulman yana nuna ta da yatsan sa, da sauri Nusaiba ta ɗauke sa ta fashe da kuka tayi gurin Amrah dashi, itama Amrah kukan takeyi shi kuwa Baban ganin Nusaiba bata gane sa bane ya saka shi kamo hannun ta ya zaunar a kusa dashi, ya anshi Shuraim yana goge masu hawaye yana lallashin su.
Kallona, na maida akan, su Haulman naci gaba da faɗar, "Haulman kike koma waye, nasan yan zun kin fahimci